ABDUL-MALEEK BOOK1 CHAPTER 3

Saican yace halan yauma kazo kacikamin bakin office da yaranka?. Hhhhhhh kaima Kasan dolene Dan babu yanda za'ayi subarni nafito ni kad'ai.

 




    Saican yace halan yauma kazo kacikamin bakin office da yaranka?.

    Hhhhhhh kaima Kasan dolene Dan babu yanda za'ayi subarni nafito ni kad'ai.

    Bobo Yakuma ta6e baki, Sakai awahala kenan, haka kawai ace duk Inda mutum zayi ana binsa tamkar wata jela?.

    Girman kenan my guy Ammar yafad'a yana dariya.

        Ammar ya ce, "mutumina kafa rame wlhy mike damunka?.

    Bobo yafitar da huci mai zafi, babu komai Ammar.

   To shikenan tunda babu komai yafad'a yana mik'ewa.

  Da sauri Bobo yaruk'oshi Dan yasan haushi yaji, yi hak'uri abokina zauna muyi magana.

    Ammar yadawo yazauna, wlhy Abdulmaleek kana bani mamaki yanda kake iya 6oyrmin wasu al'amura naka awasu lokutan.

   Bobo ya ce, " kayi hak'uri Ammar bawai ina 6oye maka wani Abu baneba, saidai ina ganin wannan sirrin gidanane, dukda nasan babu abunda zan iya 6oye maka arayuwata, kai kad'aine abokina Dana yarda dashi, nasan kaima hakane.

    Hakane Bobo amma Dan ALLAH miyasa kake 6oyemin abinda ke damunka?, ina kula dakai tunda nadawo kana cikin damuwar datafi tada akan Rasuwar marigayiya Ni'ima.

   Sabodafa damuwar dakake ciki su Appa suka yanke shawarar yimaka Aure, to amma maimakon asamu sauk'i sai kuma damuwarka ta k'aru.

  Minene damuwarka Abdulmaleek?, kasanar dani mu nemo mafita.

   Bobo yataso daga kwanciyar dayayi ajikin kujera, yadafe tebir d'in gabansa da hannu bibbiyu.

   Wato Ammar da ina cikin kewar matatane Dana rasa, dakuma tausayin Nawal na rashin uwa, wannan yasa nak'iyin aure dukda dama Kasan matan bawai suna agabana bane, su Appa sun takura nayi aure harda kai aciki, amma na ce, "muku har yanzu ban shiryaba, an auramin Rahmane saboda bijirewar yayarta akan aurena.

  Tundaga randa aka kawo yarinyar gidana ban k'ara yarda ta ganniba saida na d'akko Nawal..  

    " amma kasan wani abin mamaki?."

   Ammar ya girgiza  kai.

  Koda muka shigo gidan saitamana tarba ta mutunci, ko kad'an bata nuna fushinta akan rashin zuwana garetaba.

  Wannan itace jarabawa ta farko data cinye, saikuma yanda take kula da Nawal, wlhy idan baka saniba bazakace ba ita ta haifetaba, abu na uku tsafta, iya girki, saidai akwai shegen muskilanci atareda yarinyar wlhy.


Ammar ya tuntsure da dariya, to aii indai miskilancine babu matsala tunda kaima halinkane.

   Harara Bobo ya galla masa malam aii wannan ta fini.

          Bobo acigaba da bandamuba kafin ayi auren, amma yanzu ganinta agidan saina shiga wani hali, Dan gsky ina buk'atar mace.

           Ammar yagyara zama, to aii ni banga abin damuwa ananba, ba matarka bace?, kawai kanemeta mana.

    Ammar baka fahimceni bane, haryanzufa yarinyar k'aramar yarinyace, bata wuce 17 ba, banafa ta kammala secondary, kosu khursiyya sun girmeta da shekara d'aya.

   Murmushi Ammar yayi, karka damu abokina aii yaranma sunfi bada Nutsuwa ka gwada kagani kuma.

   Amma Dan ALLAH karagema kanka damuwa.

    To aiini bakasan wani abuba, tayayama zan tunkareta na nuna mata ga abinda nakeso?, kasanfa banason raini wlhy.

     Dariya Ammar yayi ya ce, "Abdulmaleek Aliyu Abdulmaleek hamshak'i, wlhy AAA kana bani dariya, lokuta da dama nakan rasa kai wane irin mutumne?, wlhy da aikin Soja ka dace ba lauyaba, kaifa wani irin murd'ad'd'en mutumne, towai sanda kake gwadama Margayiya Ni'ima soyayaya kirana kayi na koya makane?.

    Ajiyar zuciya Bobo ya sauke, bazaka ganebane kawai kadai.

   To ganar dani cewar Ammar yana kallon Bobo.

   Komawa yayi yalafe jikin kujerar yanad'a lilata ahankali, Ammar ya ce, " my guy kafito kawai anamijinka kaji, kakula da matarka na tabbata Rahma Alherice arayuwarka, kaga kuwa yanda ka canja kak'ara fari, so ka kwantar da hankalinka kayi k'ibama, Rahma k'yak'yk'yawar yarinyace nitsatstsiya ga ilimin addini, wlhy randa na kalli vedio d'in bikinku jinayi inama ina wajen, bak'aramin birgeni tayiba awajen walimarnan.

  d'an iska awajen biki kanata tattalin yarinya amma yanzu kazo kana mata muzurai.

   Murmushi bobo yayi ya ce, ''kankadai akeji.

  Kaima za'aji nakane, amma saikaje hanun Rahma, mik'ewa yayi yana dariya kaga bara nawuce sumayya nacan na jirana harkaja na wuce lokaci.

     Bobo daketa murmushi tun d'azun ya harareshi iskanci zakamin kenan?..

   A'a babu wani iskanci gsky dai.

   Bobo ma ya mik'ewa yayi, nima tafiyar zanyi zanje na d'auki Nawal a school, yau direbanta babu lafiya.

   Ayya ALLAH yabashi lfy.

  Amin.


Tare suka fito, kowa yashiga motarsa, Ammar da tawagan 'yan sandansa suka tafi, shima Bobo yanufi school d'in su Nawal ya d'auketa sai gida.



.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

           Sun shigo gidan falo babu kowa, sai k'amshi da k'arar AC ke tashi, saikuma TV dake kunne amma babu k'ara sosai.

   Nawal ta ce, "papa momy na d'aki zomuje, tarik'e masa hannu.

   Rahma tana tsaye jikin wardrobe tana d'aukar kaya suka shigo, batayi zaton taredashi sukeba, Cikin farin ciki tad'auki Nawal tana juyi da ita suna dariya, babyn papa da momy ya School.

   Momyn lfy.

 Masha ALLAH my lovely daughter, muje namiki wanka to kiji dad'i.

   "K indai kina tareda Nawal baki ganin kowa sai ita?.

    Da sauri ta kalli gurin da maganar take fita, Dan batayi tunanin suna tareba.

   Kayi hak'uri basan tare kukeba aii sannu dazuwa, sai matse jikinta takeyi Dan daga ita sai tawul.

    Baice komaiba yajuya yafita, amma ya rikice daganin surar Rahma, dukda k'aramar yarinyace amma tanada sura mai k'yawun gani, yanaso yak'ara ganin ainahin Rahma d'in.

   Da wannan tunanin yak'arasa d'akinsa, kaya yacire yashiga wanka.



★★★

      Bayan wasu 'yan lokuta kowa ya kammala abinda yakeyi, suka had'u afalo sukaci abinci, itadai Rahma kanta ak'asa.

   Yakula tunranda yay mata abinnan bata sakewa dashi, kuma bataso su had'a ido, tak'ara birgeshi da samun matsayi a zuciyarsa Dan yana k'aunar mace mai kunya 


_(kunya tana d'aya daga cikin tarbiyya ga mace, amma 'yammatanmu na yanzu sun 6arar, aganinsu rashin kunya itace wayewa, gsky anama wayewa bahaguwar fahimta, yakamata mugyara, kunya tana d'aya daga cikin alamomin imanima wlhy, ALLAH yasa mugane.)_


Duk suna falo zaune, Rahma da Nawal suna game da aka had'a da TV, shikam boss yana karanta jarida.


Safna tayi hon maigadi yalek'a danyaga wanene, ganin bak'uwar motace yasa yaytsaye batarda ya bud'eba, cikin haushi Safna talek'o tana masa magana cikeda masifa, aii babu shiri yabud'e mata gate d'in tashiga, guri tasamu tai farking sannan tafito, sai harar mai gadin takeyi, sanye take cikin jan less Riga da siiket sun kamata sosai amma sunyi mata k'yau, ta d'ora siririn farin gyalenta a kafad'a, takalmi da handbag d'inta duk farare, tad'auki sak'on Rahma tanufi k'ofar datake zaton itace zata sadaka da gidan.

     Sallama tayi tareda kwankwasa kofar.

   Rahma tamik'e da sauri lah kamar muryar aunty Safna nakeji.

   Da sauri Bobo yad'ago kai yana kallonta danjin ta ambaci Safna.

   K'ofa Rahma tanufa, shikuma ya ta6e baki yaudai zaiga yarinyar datace bata sonsa...........    ‍  typing........


👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{BoBo}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*



4⃣5⃣


     Rahma tarungume Safna cikeda farinciki, itama rungumeta tayi Dan tayi kewar 'Yar k'anwarta abokiyar fad'anta, I miss you my lovely aunty.

    Miss u too my lili na.

     Safna tad'agota daga jikinta tana fad'in 'Yar lukutar ummi kinfa k'ara lukucewa, mi angon naki yake baki haka?.

    Rahma tarufe fuskarta saboda jin kunya, kai aunty Dan ALLAH ki bari.

   To na bari Safna tafad'a tana kama hannunta sukai cikin falon.

    Rahma ta kalli mazaunin Bobo wayam, Nawal ta kalla data maida hankalin akan game, baby ina papa?.

    Nawal tad'ago tana dariya, yashiga d'akinsa momy..... Tsayawa tayi tana kallon Safna, saikuma ta kalli Rahma, momy wacece wannan?.

    Aunty ce babyna.

 Nawal ta taso ta rungume Safna, oyoyo aunty na.

   Itama safna rungumeta tayi tana fad'in oyoyo babyn mom.

   Bayan  sun zauna Safna sai bin Nawal da kallo takeyi, gani take kamar tasan yarinyar.

   Rahma tadire tiren kayan motsa baki agaban safna, tana fad'in wlhy aunty banyi zaton ganinkibafa.

   'Yar dariya safna tayi ta ce, ''saikuma gani kin ganni.

  Zama tayi sukafara hira, kamar basu bane sukeshan fad'a ada.

    Sun shagala sosai akan firar idon Safna ya sauka akan hoton Bobo, wani k'ululu cikinta yabada, batagama dawowa daidaiba Bobo yafito daga d'akinsa.

   Ah bak'uwa mukayi agidan??.

   

Afirgice safna tad'ago tana kallonsa, fad'uwar gaba, bugun zuciya, murd'awar ciki, duk suka k'ara samunta alokaci guda, yanda take raba ido akan Bobo sai kawai ya d'aure fuska.

   Itama Rahma kallonta takeyi ita atunaninta Safna taji kunyane akan abinda ta aikata abaya.

      Safna taduk'e k'anta bisa cinyarta danjin falon yana juya mata, jikinta sai rawa yakeyi, lallai ta tabbata kuka rahamane tunda gashi ita yau takasayinsa.

   Bobo yana zaune saman kujera yad'ora k'afa d'aya kan d'aya, dagashi har Rahma idanunsu nakan Safna, Nawal ma tana mak'ale abayan Rahma tana lek'en Safna, bobo yakalli Rahma, dama tanada wani ciwone?.

   Kai Rahma ta girgiza masa ta CE, ''amma dai ban saniba ko bayan nabar gidan.

   Lumshe idanunsa yayi ya ce, "bata ruwa tasha, Rahma ta tsiyayama Safna ruwa a Kofi tabata, jikin Safna na Rawa takar6a ta shanye duka tamik'ama Rahma kofin, k'ara mata bobo yasake fad'a.

  K'ara mata takumayi, aii ko ta shanyeshi tas.

   Rahma takalli Safna kamar zatayi kuka, aunty ki kwanta kihuta, kiringa fad'in _innalillahi wa'inna ilaihirraji'un_ zaki samu nutsuwa insha ALLAHU.

    BABU musu Safna tabi shawarar Rahma ta kwanta, dukda ayanzu jitake babu Wanda tatsana aduniya sama da Rahma d'in, jitake tamkar tatashi ta shak'eta ta mutu, talumshe idanu tana ambatar innalillahi..... Danjin zuciyarta tana shirin fashewa.


Bobo dai tuni yad'auke kai daga kallon Safna, ya maida hankalinsa ga TV.

    Bayan kamar minti15 Safna tad'anji Nutsuwa tazo mata, tabud'e ido tareda tashi.

   Rahma tai saurin fad'in aunty Yaya jikin?.

    Murmushi Safna tayi Wanda yafi kuka ciwo, da sauk'i kuyi hak'uri na rud'aku, juwace nakeji dama tun ina hanya.

    Sannu Rahma tashiga jero mata, Dan ita tayarda da zancen na Safna 100%.

        Bobo kam azuciyarsa ya ce, " juwar kuma bata tashiba saida kika ganni?, shifa Sam bai yarda da maganartaba, Dan haka yacigaba da kallonsa batareda yak'ara kallon ko inda sukeba.

    Safna kam tafad'i hakane saboda tunowa da maganar malaminta, dayace kota had'uda bobo karta nuna masa komai harsaitaje wajensa yabata wani sirri, da wannan tunanin tad'anji sanyi aranta, shiyyasa ta tashi ta zabga wannan k'aryar.

   Takai kallonta ga bobo daya maida hankali kan latsa wayarsa, muryarta na rawa ta ce, "ina yini.

   Lfy, kawai ya ce, " yamaida Kansa ga waya.


Falon yay shiru nawasu 'yan mintuna, safna dai satar kallon Bobo takeyi, sai yanzu yak'ara tabbatarwa da k'yak'yk'yawane ajin farko, Ashe ranar kallon tsoro sukayi masa, lallai ALLAH yayi halitta awajennan masha ALLAH, sai sambatun k'yawun bobo takeyi ita kad'ai zuciyarta.

        Rahma kam tayi shiru tana tunanin halin da safna tashiga yanzun nan, kome ke damun 'Yar uwar tata?.

         Bobo yamik'e Dan ganin kallon k'urillar da safna take masa, yakalli Rahma bara nad'an kwanta kafin sallar la'asar, kitadani idan lokaci yayi.

   To. Rahman tafad'a kanta ak'asa.

   Shikuma yanufi d'akinsa, harya shige safna tanabinsa da kallo.


Nawal ma tamik'e momy zanje wajen papa.

   A'a Nawal kibar papa ya huta kinga ya ce, "barci zaiyi, Nawal ta kwa6e fuska tana shirin yin kuka, momy nimafa barcin zanyi.

   Tokije d'akinmu ki kwanta, kamar gsk tanufi d'akin Rahma, dataga basa kallonta saita gudu d'akira, papan ta.

    Safna ta ce, " wannan yarinyarfa ina kuma samota?.

      d'an murmushi Rahma tayi, aunty yarinyarsa ce wadda matarsa tarasu tabari.

    Baki safna ta ta6e shine kekuma aka jajibo aka kawomiki?, kedai sakaraice wlhy, kina 'Yar yarinyarki har anfara kiranki da suna momy mtsoooow, nibansan randa kanji zai wayeba wlhy, danice agidannan wlhy saidai yasan Inda zaikai 'yarsa.

    Itadai Rahma batace komaiba, saima wasa da zoben hannunta datakeyi, amma har zuciyarta bataji dad'in maganar 'Yar uwartaba, aganinta aii d'a na kowane, kuma shida gidansa tahanashi ajiye Wanda yakeso?, itafa har zuciyarta tana k'aunar Nawal, kuma yanda zata rik'e 'ya'yan cikinta haka zata rik'e Nawal.


    Yana zaune abakin gado yana danna laptop Nawal tashigo.

   Lah papa bakayi barciba?.

     Bobo yad'ago yana kallon d'iyar tasa, banyi barciba babyna ya akayi?.

   Na cema momy zanzo wajenka, shine ta ce, " a'a wai nabarka kagaji zakayi barci naje d'akinmmu na kwanta.

   To miyasa bakije kin kwantaba?.

  Ai bata ganniba nikuma na gudo nan, ammafa karka gaya mata.

  Murmushi yayi Dan ganin yanda Nawal tazaro idanu saikace wata babba, to shikenan bazan fad'aba yanzu ya za'ayi?.

   Ta ce, "papa barci zanyi.

  To zoki kwanta, kan gadon tahawo ta kwanta, kwantar da kanta tayi kan k'afarsa daya tankwanshe, tana kallon rubutun dayakeyi a laptop suna labari, dahaka barci ya d'auketa, yagyara mata kwanciya dankar wuyanta yay sanyi.


Afalo kam safna da Rahma suna hira, dukda safna dauriya kawai takeyi, Dan zuciyarta na cikeda tsanar Rahma, dakuma haushin tashin bobo Afalon, Dan bata gaji da ganinsaba.

   Tamik'a mata sak'on ummi gashi inji ummi.

   Rahma takar6a ta na dubawa, miye kuma ummina tabani?, safna ta ta6e Baki ta ce, " zata kiraki tamiki bayani, kinga bari nawuce, safna tafad'a tana mik'ewa.

   Kai auntuna tun yanzu?, Rahma tai maganar tamkar zatayi kuka.

    Kenifa banason iyayi, dama kika samu Nazo shine zakimin Ta6ara.

    Sanin halinta yasa Rahma tai saurin fad'in yi hak'uri aunty Safna wlhy nayi kewarkune sosai. Dan ALLAH yaushe zaki dawo?.

      Kallonta kawai safna takeyi, zuciyarta na raya mata yarinya karkiyi farincikin sake zuwana, Dan waywayowata gidannan ba alkairi bane ba agarekj, bazan ta6a barmiki bobo ba, abayama kuskurene da rashin sani, amma ayanzu kam sai Inda k'arfina ya k'are, bobo nawane nikad'ai.....

...

  Ta6ata Rahma tayi aunty mikike tunani haka?.

    Ajiyar zuciya Safna ta sauke, ta k'ak'aro murmushi, karki damu zandawo kwannann.

    Cikeda farinciki Rahma tarungume safna.

    Kayan kwalliya ta had'a mata hadda wasu k'ananun kaya masu k'yau da aka saka mata alefe, safna takar6a ko godiya babu ta tafi.

    Har bakin mota tarakata, saida taga fitarta sannan tadawo ciki.

   Batanemi su Bobo ba tahau gyaran gidan, da shirin girkin dare.


Safna kam tana fita saitaji hawaye sunabin kumatunta, abinda takesonyi tun d'azu amma sukak'i zuwa, gangarawa tayi gefen titi tasamu guri tai farking, kifa kanta tayi a sitiyari tanata rabzar kuka tamkar ranta zai fita, sai surutai takeyi kamar Sabuwar kamu.

    Wlhy Rahma bazan barmiki Shiba, wlhy saidai idan ki mutu na mallakesa, kota halin k'ak'a saina rabaki dashi, idan ban samesaba mutuwa zanyi, Rahma miyasa zakimin haka ki auri abinda nafiso fiyeda komai arayuwata?, wlhy saikin barmin bobona, saikin barmin.....tasaki wani wahalallen kuka.


(Ni bilynku na ce, "kaga wani salo, Safna kinyi sake Rahma ta dafe.)


    Cikin matsanancin kuka Safna ta kira basira ta zayyane mata komai, ita kanta tarazana sosai danjin labarin, safna ta ce, "baseera miye mafita?, kibani shawara, wlhy kwakwalwata na gab da tarwatsewa nashiga uku baseera namutu.

   Kinga safna ki kwantar da hankalinki, gobe idan ALLAH yakaimu zamu koma wajen malam.

    Baseera muje yanzu please.

   A'a kiyi hak'urin goben, wlhy yau Abbana yana gida, kuma yasan banida lectures d'in yamma, baza'a barni na fitoba, kiyi hak'irin giben saimuje da sassafe.

    Shikenan safna tafad'a jiki a sanyaye.

    Motar taja tanufi gidan, Dan kukan datayi yad'an rage mata wani abun.

      ......

     Rahma tagama komai tak'ara saka turaren wuta, jin kwala kiran sallar la'asar yasata nufar d'akin bobo danta tadashi, kwankwasa k'ofar tayi dukda tasan yana barci, bata jira amsaba tashiga da sallama.

   Hakan tayi dai dai dafitowar bobo daga wanka, yana d'aure da fad'in tawul ita k'ugu zuwa guywa, hannunsa rik'e da k'arami ya ratayo a wuyansa.

   Da sauri Rahma tajuya zata fita tana fad'in ashema ka tashi.

   Eh natashi, ina zaki? Kizo kid'auki yarinyarki gatanan tamin barci ad'aki.

   Rahma tajuyo kanta ak'asa, Ashe nan tazo?, nazata tana d'akina?.

   A'a tana nan dama ta ce, "karna gaya miki gudowa tayi.

   Murmushi kawai Rahma tayi tad'auki Nawal tafice abinta.

   d'an murmushi yayi danganin yanda take Sinne kai da had'e hanya, yasan danta gansa babu kayane.


Tana falo yafito sanye cikin blue d'in wando da jar Riga, yayi k'yau sosai, Dan dama bobo akwai gayu gakuma tsafta, uwa uba k'yawun haiba.

   Yad'an kalli Rahma, bara naje masallaci, daga nan zan wuce gidansu Ammi.

   To ALLAH yatsare. Saika dawo.

   Amin yafad'a akan la66ansa, yafita yanamaijin dad'in addu'arta gareshi.

   Rahma tayi shiru tana mamakin yanda bobo kan sakata cikin al'amuransa ayanzu, komiye dalilin hakan?.



.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

     Safna tadanna uban hon, babu shiri baba mai gadi yabud'e mata gate, aguje tashiga gidan, tai farking, handbag d'inta kawai tad'auka tayi cikin gida, anan tabar kayan da Rahma ta bata, ALLAH yasota ma ummi na d'aki babu kowa afalon.

   Ta fad'a saman gadonta tana kuka, wlhy saina raba wannan auren, Dan bobo nawane nikad'ai, bazan ta6a zuba ido ina kallonsa amatsayin mijin k'anwataba, saina mallakesa kota halin k'ak'a, konawa zan kashe kuma koyaya iyayenmu zasu d'auki lamarin itadai saita mallaki bobo.

    Haka taita kuka har aka kira magriba, dama batayi sallar la'asarba, kuma da alama magribar ma babu niyya.

    Ummi takalli agogo waini ina safna tamak'alene har yanzu shiru?.

   Talatu mai aiki ta ce, "Hajiya aita dawo tun d'azu.

    Kai talatu da gsk?.

   Wlhy kuwa Hajiya.

 Hankalin ummi ya kwanta takoma d'aki dama ko lazimi bata kammalaba tafito.


.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

     Bobo kam koda yay sallar la'asar saiya nufi gidansu, bayan sun gaisa da maigadi yashige ciki.

   Yakashe motar yafito, cikin kasaitarsa yanufi cikin gidan, afalo yatarar da khursiyya da khairiyya suna kokawa akan gyale.

    Tsaki yayi yana daka musu tsawa, kai dallah miye haka?.

   Da sauri suka nutsu.

   Ya ce, " Ku wad'anne irin shashashune?, kun kirma amma kunacin k'asa.

  Yaya gyalenefa na ajiye zansaka gobe idan zamuje gidanka, shine ta d'auka wai zata fitadashi yanzu......

   Karya take Yaya...

Katsesu yayi suduka, kumun shiru dallah, hannu yamik'a yakar6i gyalen, batareda yak'ara tankasuba ya haye saman Appa.

   Saida yaje k'arshen benen sannan yajuyo ya ce, "idan kun gadama kucigaba da fad'an harna sakko, yay shige warsa.


Khursiyya ta tura baki baba, hankalinki ya kwanta ya kwace duka, tobake kika jaba cewar khairiyya.

     Kardai Ku fasa, kuyi tayi harya dawo kune zakuci dukan banza tunda kunsan halinsa sarai, Ammi ce mai maganar tana fitowa daga kicin, Ashe duk abinda sukeyi tana jinsu.

    d'akinsu suka koma, kowa tana zum6ura baki gaba, Ammi ta girgiza kai tana nufar saman Appa itama............





*_tofa masu karatu yanzu aka fara, matsaloli sunyi yawa, Alh sunusi yana nan daburin koyama bobo hankali, koya zata kasance?._*

   _Safna taci burin mallakar bobo, ko zatayi nasara?._

   _Bobo da Rahma, koya zata kasancene?, shin zasu fara soyayyane?, koko Safna zata Shiga tsakaninsu?, kozaibi sha warar Ammar ne kafin safna tayi wani abu?._


To mucigaba dabin labarin *_Abdulmaleek bobo_* muji yazata kaya ga wannan cakwakiya, waye keda nasara acikin mutanennan 4?.

Bobo, Rahma, Safna, Alh sunusi.

      ~Karmu gajiya masu karatu yanzu aka fara game d'in saidai bamusan wazaiyi winning ba acikin mutanennen 4.~

     

*_acigaba da gashi!!!!!👌🏼_


Luv u oll my fan's

*_(((S))).......2017_*


👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{BoBo}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*



4⃣6⃣


     Appa yatashi zaune yana murmushi, oyoyo babana nida Ammi.

   Shima bobo dariyar yakeyi, yaje dafda Appa yazauna tamkar zai shige jikinsa.

   Appa yamik'a masa hannu su gaisa, amma saiya nok'e ya ce, "ina yini Appa.

  Dariya Appa yasakeyi, mukarram bakaso musamu ladan musabahane?, mirmushi yayi batareda yace komaiba, Appa yakamo hannun bobo yahad'e danasa yana fad'in ya iyalin?.

   Suna nan lfy Appanmu, sunama gaisheku.

    Muna amsawa. yau baka je aiki bane?.

   Naje Appa, amma nataso dawurine saboda d'akko Nawal a school.

   Ok, to ina direbanta?.

   Wai bayajin dad'in jikinsa, shine nacemasa yahuta kawai.

   ALLAH yabashi lafiya to.

  Amin.

Assalamu alaikum.

   Wa'alaikisslam. Appa da bobo suka amsawa ammi sallamarta, bobo yamik'e da sauri yakar6i kayan hannun ammi, kai Amminmu da kanki?, miye amfanin wad'ancan yaran?.

   Dariya tayi tazauna, to mukarram inbanyiba wazaiyi?, hidimar mijinace fa.

   Murmushi bobo yayi, shiyyasa kullum yakeson Amminsa haryau baiga macen datakai amminsu iya tattalin mijiba, gashidai sun tsufa amma har yanzu suna tattalin junansu tamkar yara.......

   Ammi tak'atsema bobo tunani da fad'in mukarram ga abinci.

   Firgigit yadawo da kallonsa Kansu, Ammi mikikace?.

    Tunanin mi kakeyine?.

  Bai 6oye musuba yafad'a musu abinda yake tunani, Dan akwai fahimtar juna da shak'uwa tsakaninsu da iyayensu.

   Daga Ammi har Appa dariya sukayi danjin firicin bobo, ammi ta ce, "toga abinci azuba?.

   A'a ammi nima matana tacikamin ciki da girkinta mai dad'i.

      hhhhhh d'an bantan uba, ashedai gaskiyar Hamza dayace kanason matarka, babanafa akwai iya taku.

   Dariya sosai bobo da Ammi sukeyi danjin zancen Appa, appa ya ce, " naji dad'i sosai wlhy, ALLAH yak'ara Baku zaman lfy da zuri'a tagari.

   Kansa ak'asa ya ce, "amin."

   Hira sukacigaba dayi, Appa yanacin abinci, bayan ya kammala ya ce, "mukarram!.”

    Yanda Appa yakira sunan nasa yasan tabbas maganar muhimmiyace, shima cikeda girmamawa da nutsuwa ya ce, " na'am Appa.

     Appa yagyara zamansa, yanamai tsurama bobo ido, mukarram mike tsakaninka da Alh sunusi Dala?.

    Ajiyar zuciya bobo yasauke, cikin nutsuwa yayma Appa bayanin tun farkon tsintar muheebat dakuma abinda yake faruwa a yanzun.

    Appa ya girgiza kai alamar gamsuwa, ya ce, "ina alfahari daku sosai 'ya'yana, ngd ma ALLAH dayayiku masu hankali dasanin darajar d'an Adam, lallai kaburgeni sosai babana, kuma Nagoya maka baya d'ari bisa d'ari ka kwatoma yarinyar hak'k'inta, “I'm proud of you my dear son”.

     ALLAH yatsare minku aduk inda kuka tsinci kanku.

    Amin Appa mungodema ALLAH dasamunku amatsayin iyaye nagari, bamuda abin biyanku saidai muyita binku da addu'a har k'arshen numfashinmu.

   Ammi dai sai murmushin jin dad'i takeyi.

   Appa yacigaba da fad'in dama abinda yasa kaji namaka maganar yaune Alhaji Sadiq muna hira yake bani labarin furucin Alh sunusi akanka, todaya fad'i sunanka shine yagano d'aya daga cikin 'ya'yanane, shine yasameni yake gayamin nasaka ido kar a cutarmin dakai, Dan Alh sunusi bashida imani ko kad'an.

      _(nasan har yanzu baima San kai d'ana bane shiyyasa yake rangwanta maka, Dan bama shiri sosai nidashi, siyasa tasakashi d'aukar gaba damu nida Abban Ammar)_ 

    amma kadage da addu'a muma zamu tayaka, ALLAH yana tareda mai gsky kaji my son.

    Murmushi bobo yayi, ya ce, " karka damu Appa wlhy daidai da second 1 banta6ajin tsoro ko Shankar Alh sunusi ba, ni duk sanda yay wani abunma k'aramin k'aimi yakeyi.

    Daga Ammi har Appa dariyar sukayi, sukace to ALLAH yak'ara tsareka auta, fira sosai yasha da iyayensa, saida suka dawo daga sallar magriba sannan yay musu sallama zai tafi.

   Appa ya ce, "gobe idan ALLAH yakaimu yanason ganinsu su duka, yanaso su tattauna akan maganar auren su khursiyya.

   To Appa ALLAH yakaimu lfy.

  Amin bobon Ammi.

  Dariyar bobo yayi yafice sai gida.




.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

     Bayan isha'i ummi tashiga d'akin safna danganin ko lfy?, akwance take tana chart itada baseera dawasu k'awayensu a group sunata zugata akan bobo, Dan tuni sunsan labarin bobo.

   Jin motsin tahowar mutum yasata tura wayar a k'ark'ashin filo, danbata buk'atar kowa yagane halin datake ciki.

    Azaune ummi tasameta tana duba takardunta na makaranta.

   Ummi ta ce, " o aini nazatama bakida lfy ne?, kimdawo baki nemeniba bare naji labarin autana.

   'Yar dariyar basarwa safna tayi, lah ummi wlhy fitsarine yakoroni shiyyasa banshigoba, daga baya kuma namak'ale ad'aki dankarki lik'amin girki.

    Dariyar ummi tayi, ta ce, "malalaciyar banza, ke koma auren akai miki yanzu aii mijin yabani, babu abinda kika iya sai kwalliya.

   Safna ta ce, " kai ummi, aidai nasan Kodan k'yawuna mijin ya zauna dani.

   Baki ummi ta ta6e ta ce, "keni rabani da shiriritarki Yakika ganomin autata?.

   Tana nan tak'ara k'iba, cewar Safna tana ta6e baki.

   Alhmdllh ummi tafad'a cikeda jin dad'i, ALLAH yak'ara baku zaman lfy autana, har hankalina ya kwanta aii wlhy.

    Itadai safna batace komaiba har ummi tafice.

 Raka ummi tayi da harara kamar ba uwartaba.


Na ce, " ALLAH yashiryaki Safna.



.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

          Sai bayan isha'i bobo yashigo gidan, farking yayi Inda yadace, yafito yanufi cikin gida cikin takun gayunsa da k'asaita, hannunsa rik'e da ledoji.

    Rahma da Nawal suna zaune afalo suna homework.

   Dagudu Nawal taje ta rungumesa, Yaya sama da ita yana sumbatar kumatunta, d'iyar momy ya gida?.

    Ta ce, "my papa lfy, ledan hannunsa tak'ar6a, ya ce, " zaki iya kuwa baby?.

    Lah papa momyna ta ce, "niba raguwa bace, ko momyna?..

   Rahma ta ce, " hakane my dear keba raguwa bace.

   Tad'an kalli bobo ta ce, "sannu da zuwa.

    Yauwa ya amsa yana mata munafukin kallon nan NASA k'asa², d'akinsa yanufa yana fad'in kid'an kawomin ruwa.

     Rahma tad'an turo baki gaba, mutum ace kullum fuska a d'aure kamar wani soja?, azuciyarta take wannan maganar.

   Tamik'e tana cigaba da mitarta azuciya, to miye nacewama nakai masa ruwan sha d'aki?, sabon salo wai gaida uwar miji akasuwa, dahakadai tad'auki ruwa da cup tasaka a k'aramin filet tanufi d'akinsa.


Harya cire kaya dagashi sai gajeren wando, yana zaune abakin gado yana waya da ya Hamza.

   Ta turo k'ofar tashigo da sallama, tai saurin kauda kanta Dan ganinsa babu kaya, aiko tazame zata fad'i suuuuuuuu.

    Da sauri yatareta tafad'o jikinsa, saurin kallon inda tafad'a tayi, karaf suka had'a ido, kallon juna sukeyi cikin kallon ido cikin ido, da sauri Rahma ta lumshe idanunta danbazata juri kallon cikin idonsaba.

    Shikam aituni tsigar jikinsa ta tashi, shima yalumshe nasa fararen idanun yana murmushi, haka kawai yatinci Kansa anishad'in kasancewarsu haka.

     Rahma tafara yunk'urin tashi daga jikinsa, duk kunya ta lullu6eta.

    Cikin muryar nan tasa mai sanyi da amo ya ce, "sorry."

   Itama ahankali ta ce, ''ngd, har yanzu yak'i bata damar tashi daga jikinsa, saima k'ara rik'eta dayayi.

    Wayarsa aka kira, suduka suka kalli wayar, Rahma tayunk'ura ta zame jikinta, tiren hannunta yakar6a Wanda ALLAH yatsare babu abinda yazube, tomiya tsorataki?, yay maganar yana watsa mata wani shi'umin kallo.

      Azuciyarta ta ce, ''Kaine mana, amma afili saitace babu komaifa.

             Murmushi kawai yayi Dan yasan ganinsa datayi babu rigane ya razanata.

    Batayi auneba taji anjamata hanci, matsoraciya kirage tsoronnan naki.

    Dad'an gudunta tafice daga d'akin.

    Murmushi yayi yana girgiza kai, afili ya ce, "k'uruci dangin hauka.


Falo tadawo tabud'e abinda yakawo musu, gasashshen namane da ice-cream, tana cikin dubawa yafito sanye cikin wando 3½ da k'aramar riga tashan iska, yau da alama babu karatun jarida babu danna laptop Dan wayoyinsane kawai ahannunsa.

   Kujerar dasu Rahma ke jingine ya zauna, Nawal ta ce, "papa zomiyi game.

     Baga shinan kinayi da momyn kiba, Nawal tayi shiru dantaji haushi.

        Yakalli Rahma wai INA bak'uwar takin?.

   Tafa wuce gida tun d'azun.

    Baice komaiba, Wayarsa yad'auka yafara charting Wanda saiyayi kwana uku bai hauba.

    Rahama ta ce, " azuciyarta ana nandai da hali.

   Ta daure ta ce, "papa akawo abinci, yad'ago yana kallonta, shikam mamaki take bashi idan tace masa papa, ya ce, "zuwa anjima.

    Daganan kowa yay shiru shi yana danna waya, sukuma suna game.


        Ajiye wayar yayi yana kallonsu batareda sun saniba, Nawal tafi Rahma iyawa sosai, Dan suna 'Yar tseren motocine, amma tuni Nawal ta tserema Rahma, yashagala sosai akallen nasu, can Nawal tayi winning, Rahma ta ce, " bata yardaba, sai dariya da murna Nawal takeyi.

    Nawal tamik'ama bobo handle d'inta, papa kar6i handle d'ina kuyi da momy naje nayo fitsari.

    Babu musu yakar6a, tanufi d'akinsu da gudu, shikuma yasakko k'asa kan carpet Kusada Rahma, har jikinsu nad'an gogar juna.

   Kad'an Rahma tad'an muskuta suka fara, anutse kowa ke controling d'in motarsa, saidai awannan karon Rahma tafi bobo iyawa.

    Dariya ta kufcema Rahma Dan ganin yanda bobo kek'ara k'aimi, shima dariyar yafara yana k'ara gudu danson wuceta amma yakasa, Nawal tafito taje bayan papanta tad'ane tana kallonsu, dariya sosai sukeyi kowa yana Nuna kwarewarsa, Nawal tana k'ara zugasu, momy gooo karki bari papa yakamaki, idan sukayi kamar zasuyi karo Nawal tabuga k'ara tamkar wad'anda suke agidan kwallo, bobo yana ganin Rahma zata masa game over sai kawai yafara k'ok'arin kwace handle d'inta, nanfa suka kaure kokawa suna dariya, itama Nawal tad'aresu tana dariya wai momy tafi papa k'arfi.

     Sun shagala sosai wajen tumurmusar juna, hardai Bobo yasamu nasarar kwace handle d'in Rahma, ya ce, "saidai kar kowa yayi winning, dadai nayarda na d'auki game over.

    Rahma tarik'e ciki tana dariya, cikin dariya ta ce, " wannandai game ta fin k'arfice, miyasa zaka karaya dawuri haka?, hhhhhh.

    Tsayawa yayi cak yana kallonta Dan dariyar tayi mata bala'in k'yau, jiyake kamar karta daina, yalumshe ido ahankali yabud'e akan Rahma data fara tsagaitawa da dariya tana d'aukar d'ankwalinta daya fad'i can gefe wajen kokawa.

   Shi saima yanzu yalura da bak'in gashinta sid'ik irin Wanda ake kira roba roba d'innan, Dan yacika kan dam, ta d'aureshi kamar acuci, dukda bata saka masa mai amma sai kyalli da shek'i yakeyi, ahankali yakai hannu yakama gashin nata mai d'an tsawo babu laifi, Dan dazata cire ribom d'in to zai sauka harkan kafad'arta.

    Jin hannunsa cikin gashinta yasakata dawowa hayyacinta, tayi saurin matsawa tareda d'aura d'ankwalinta.

    Murmushi shima yayi, yatashi yakoma bisa kujera shida Nawal.

   Itakam duk kunya tarufeta, mik'ewa tayi zata gudu d'aki, muryarsa ta dakatar da ita.

    Abamu abinci muci ko babyna?.

   Da Sauri Nawal ta ce, "eh momy yunwa mukeji.

   Dole Rahma tadawo tagabatar da abinda yakawo, zata tafi d'akinta yay saurin rik'o hannunta, cikin sauri tajuyo, aranta tace waishi baya ganin Nawal mai shegen wayau da surutu.

     Hannunta tashiga k'ok'arin kar6ewa, shikam yasake mata hannu, ina zaki? yafad'a adake.

   Ganin yanda yay magar saita kama kanta, kanta ak'asa ta ce, " d'aki.

   Abincinfa?.

Nak'oshi.

  Ashe zanmiki d'ura.

   Da sauri ta ce, "tom zanci.

    Murmushi yayi, itakuma tadawo ta zauna, babu yanda zatayi dole tasaka hannu sukaci naman a filet d'aya su uku.

    Dad'i Nawal taketaji, Dan haka idan tad'ako nama tasakam Rahma abaki saita sakama bobo shima abaki, cikeda nishad'i sukecin naman, bayan sun gama aka dawo kan ice-cream, babbar roba d'aya sukesha su uku.

   Rahma dukta kasa sakin jikinta, saboda kunya, bobo yana kula da ita amma ya share, yad'auke kansa yana maida TV wajen labarai.

     Nawal tad'ebo ice-cream tabama bobo abaki, takuma d'ebowa tabama Rahma.

   Shima bobo yad'ebo yabama Nawal, Yakuma d'ebowa yanufi bakin Rahma, k'asa tayi da kanta wai ita kunya, muryarsa kasa² kamar mai rad'a ya ce, " zan zuba abakina sannan nakama bakinki najuye miki, kuma agaban Nawal komai zai faru.

   Babu shiri Rahma tabud'e baki yazuba mata ta shanye.

   Nawal ta ce, "momy kema kibamu to.

   Babu yanda Rahma zatayi tunda an rutsata, ta d'ebo tabama Nawal, takuma d'ebowa amma takasa d'agowa.

   Cikin shagwa6a bobo ya ce, ''baby kinga momyn ki ko tak'i tabani ni.

   Lah momy kibama baby karyayi kukafa.

   Bak'aramar dariya abin yabama Rahma ba, wai k'ato dashi yanama 'yarsa shagwa6a, tana k'umshe dariya tad'ago tabashi shima, shikuma yad'aga mata gira.

    Kanta ta tura cikin cin yoyinta Dan abin yabata matuk'ar kunya.

   Hakadai suka riski wannan dare cikin nishad'i, bayan angama labarai suka tafi d'aki, shima yatafi d'akinsa cike da kewarsu, da mamakin Kansa a yau, yana Abu tamkar bashiba.

    Wani 6angare na zuciyarsa ya ce, " kafad'a tarko ne..............




*_Happy juma'at Mubarak my lovely fan's._*

❤❤❤❤💋💋💋💋💋💋💋








*_luv  you oll my fan's_*

   *_(((S)))....2017_*




 *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{BoBo}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*


*_"Na gaisheki aunty na, aunty Ramlat muh'd, 'yan 9ja muna kewarki, kuma muna gaisheki, alkairin ALLAH yakai muku har k'asar Egypt keda ya Saifudden da my boy Abubakar Sadiq, ngd da k'auna i miss you  dayawa dayawa."_*

    BOBO da Rahma suna gaisheki kema.

        _mai gadon zeenari ce_    


4⃣7⃣


     Washe gari Safna sukayi sammakon tafiya wajen malam da'u, yauma dai k'arya tashirya ma Abba da ummi harta samu damar fitowa da sanyin safiyarnan.

    Ak'ofar gida suka had'u Baseera tabud'e tashigo.

   Kallon safna take cike da mamaki, Safna kinga kuwa yanda idonki ya kumbura?, amma dai kinyi kuka?.

   Humm baseera kenan, aii jiya kukan jijine kawai banyiba wlhy, amma fa yanda naga rana haka naga dare, nayi nadamar zuwa gidan banzar yarin yarnan jiya, Dan dabanjeba dabanyi gamo da abinda zai dameniba, amma kuma hakan alkairine Dan koba komai naga farin cikina, nakumasan Inda zan sameshi yanzu, ta k'are maganar da share hawaye.

   Kiyi hak'uri kibar kuka, komai zai daidaita nasan aikin malam da'u saikinyi farin ciki.


“nikam na ce, "shi d'in banza, shima ga ALLAH yake nema”.

     Mtsoooooow!!.


Suna tafiya sunad'an hirarsu, baseera ta ce, " amma ummi bata saniba ko?.

   Kai yazanyi tasani, kinsanma kuwa yanda takeji da shegiyar Rahma d'innan yanzu, kenifa inaga duk cikinmu ummi tafison Rahma ayanzu.

      Kai Safna aiiko bazakice hakaba, duk gidannan babu Wanda akaima gata sama dake, kitunafa, ummi tabamu labarin tunkan tayi aure take addu'ar ALLAH yasa tahaifi mace haihuwar farko, amma ALLAH saiyabata maza, bayan ummi ta haifi ya Shaheed da ya Munneer taso haihuwar mace sosai, saikuma haihuwar tatsaya ma gaba d'aya, saida ya munneer yay shekara 7 sannan ALLAH yabata cikinki, kullum itace addu'a da sallar dare, har umara sukaje itada Abba saboda ALLAH yabasu 'ya mace.

    ALLAH mai k'yauta da k'ari aka silli6oki duniya, gatadai kinshashi fiye da kowa agidan, abinda kikeso shi ake miki, shiyyasa kika taso 'yargata ta6ararriya, wlhy tsiyar dakikeyi agidanku Inda Rahma takeyinta datuni tashiga wani hali.

   Amma harzaki bud'i baki kice anfison Rahma, duk Wanda yasan tarihin gidanku to bazai yarda da maganar kiba wlhy.

    Shiru Safna tayi, Dan tasan gaskiya Baseera tafad'a.

   Da hakadai suka k'arasa gidan malam da'u.


°*°*°*°*°*°*°*°*°*°*°

         Tunda tatashi take hidimar gyaran gidan, bayan tahad'a breakfast tayima Nawal wanka tashiryata tsaf cikin kayan makaranta, tsaf yarinyar tafito tamkar kasaceta ka gudu, dama ga k'yau d'an asali, tana girma kamaninta nasake fitowa da mahaifinta.

   Rahma ta kalli agogo 7:6am, ta ce, "baby bara nayi wanka nima kafin papa yafito.

    To momy, Nawal tayi maganar tana k'ara gyara igiyar takalminta.

   Cikin d'an lokaci k'alilan tayi wankan tai shirinta cikin siket da riga 'yan kanti, d'an tsaki tayi Dan ganin rigar batada tsawo, aranta tace yanzu kanayin kuskuren d'aga hannu sai anga cikinka, da wannan mitar aranta suka fito falo.

    Harta zauna a dinning itada Nawal saikuma tamik'e Dan hangen labulen windown Kusada su ya nannad'e.

    Wani d'an kujera dake gefe wadda Bobo kan zauna idan baya buk'atar hayaniya ta janwo ta taka Dan tsawonta bazai kaiba, hawanta keda wahala koma labulen bata gyaraba tadai mik'a hannu zata gyara taji takun fitowarsa kwass kwass, tsintar kanta tayi da k'urama hangar tahowarsa idanu.

    Ya salam tafad'a yayinda bobo yabayyana, sanye yake cikin wando dariga farare tas, ya d'ora rigar suit jaa mai laushi, takalminsa agogonsa duk jajayene, sai zabga uban k'amshi yakeyi, sajen nan yakwanta luf luf sai shek'i yakeyi.

    Tashagala sosai akallonsa batareda tasaniba, shima gareshi hakan take, tsaye yake k'yam tamkar andasashi, idonsa nakan farar fatar cikinta data bayyana sakamakon d'aga hannu datayi zata gyara labulen daya nannad'e.

    Ganin ya motsa yasa ta firgita, abisa tsautsayi kukerar tad'an goce tayi baya kamar zata fad'i amma tayi nasarar rik'e k'arfen window.

    Ahankali yatako har inda take, fuskarsa babu yabo babu fallasa, baya murmushi bakuma a d'aure takeba, ahankali yayi maganar tamkar bayaso ko ammasa dolene.

    Mikike kallo haka? Dahar kike shirin fad'uwa?.

   Turo baki Rahma tayi, danta gaji wlhy, gashi Idan ta ce, "zatayi yunk'urin sauka fad'owa zatayi, Dan kad'an k'afarta take d'ofane akujerar.

    Yanda ta turo baki cikeda shagwa6a saita k'ara burgesa, dama ga kwalliyarta ta tafi dashi, yad'an lumshe idanunsa ya bud'e akanta, bazakiyi maganaba ko?, Ashe zan barki kifad'o d'iyarki tamiki dariya, yayi maganar yana kallon Nawal da hankalinta baya kansuma gaba d'aya, wasanta takeyi da cokulan da Rahma ta ajiye a dinning.

     Dawo da kallonsa yayi ga Rahma, cikin sanyin nan NATA tareda shagwa6a ta ce, " ALLAH hannuna zai karye please help me.

    Wani k'asaitaccen murmushi yayi tareda ajiye jakar aikinsa, yatura hanuwansa duka biyu a aljihu, idan na taimakeki kedami zaki biyani?.

     Shiru tayi tana kallonsa, can kuma ta ce, "mikake so nabaka amatsayin ramako?.

    Yad'an d'age kafad'a yana ta6e baki, nikomi kika bani fine.

    Ta marairaice murya tamkar zatayi kuka, ALLAH nagaji zan fad'o.

   Kauda kansa yayi gefen Nawal yana murmushi, ganin har yanzu hankalinta baya kansu yad'auke kai. Matsowa yayi Kusada Rahma tareda zare hannunsa daga aljihu ya tallafota, daga ita harshi lumshe idanu sukayi, tallafota yayi tamkar jaririya, ahankali yabud'e idonsa akanta, amma ita har yanzu nata alumshe suke, yakalli k'irjinta dayayi d'as a pink d'in rigar, ajiyar zuciya yasauke sannan yadireta ak'asa, saiyanzu tabud'e idanunta masu matuk'ar burkitashi, thanks tafad'a tana k'ara juya idanun.

   Shi ganima yake tamkar da gayya tamasa haka, lumshe idanu kawai yayi yana jinjina kai Dan bakinsa yayi masa nauyi, cikin salonsa ya ce, " nawafa?.

   Ta ce, "me?.

Ramakona mana, kokin manta da yarjejeniya mukayi.

    Kauda fuskarta tayi gefe Dan bazata juri kallonsaba, mikaso to?.

     Abu biyune kawai, kuma marasa wahala.

   Kafad'a inji idan zan iya.

    Nafarko dai gyaran d'akina, Dan yayi datti, nabiyu kuma..... Saikuma yayi shiru, tajuyo tana kallonsa miye na biyun?.

    Wani murmushin basarwa yayi, murya kasa k'asa ya ce, " kiss me".

    Idanu tazaro, saikuma tajuya zata gudu, da Sauri yadamk'o hannunta, tsayawa tayi cak amma takasa juyowa.....

     Momy papa!!!!. Zanyi latti fa.....

    Muryar Nawal ta riski kunnuwansu, da Sauri yasaki hannun Rahma, itama tayi Saurin k'arasawa ga Nawal.

    Break fast tashiga had'a musu, Bobo yak'araso dinning d'in, kujera yagyara tamkar zai zauna yakai bakinsa Kusada kunnen Rahma, kitabbata idan nadawo saikinyi, inba hakaba zanmiki abinda yafi kiss.

   Kafin tad'ago yaja kujera ya zauna.

    Dukta daburce, itafa mamaki bobo take bata cikin 'yan kwanakinnan, tamkar bashiba, awaje idan kagansa dolene kaji tsoronsa da masa kallon mutum mai Girman kai da tsabar shariya, amma daka zauna dashi nad'an wani lokaci saika fiskanci shi mutumne mai sauk'i da iya zama da mutane, tasauke ajiyar zuciya tareda tura musu abincin kowanne agabansa.

     Sunacin abinci yana mata munafukin kallon nan nasa, dukta takura awajen, adaddafe dai aka kammala suka mik'e.

    Takama hannun Nawal suka fice shikuma yana binsu abaya har wajen mota.

     Rahma ta rissuna taima Nawal kiss akumatu kamar yanda tasaba, itama Nawal Tamata, bobo yak'araso yana fad'in saura ni.

    Shiru Rahma tayi tamkar bama tajishiba, bata ankaraba taji yabata  summba (kiss) akumatu, dasauri tad'anja baya tareda lumshe ido, saikuma tajuya dagudu zuwa cikin gidan.

    Murmushi yayi tareda binta da kallo harta shige ciki, shima yabud'e mota yashiga yana murmushi.

    Saida yafara ajiye Nawal amakaranta sannan yanufi wani waje.

    Adaidai wani k'ofar shago yatsaya, batareda yafitoba, yamik'a hannu ta windown shagon aka mik'o masa wasu takardu.

     “banga  fuskar wayeba nima.”

     burka motarsa yayi yay gaba yana bin karatun alkur'anin dake tashi amotar ahankali.




.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

     Su Safna sun samu shiga wajen malam da'u, bayan gaisuwa ta labarta masa yanda komai yafaru tundaga randa suka bar wajensa, duk cikin matsanancin kuka takeyin bayani.

   Shima Kansa malam da'u yarazana dajin batun na Safna, amma dayake yana son cin kud'i saiya dake abinsa.

   Ya ce, "toke yama akayi haka tafaru dake kika kamu dason mijin k'anwarki?.

   Safna tashare hawayenta, cikin rawar murya ta ce, " malam katuna da labarin farko Dana Baka, saikuma kahad'a Dana yamzu zakagane bansan  *_“ABADUL-MALEEK”*_ BOBO me iyayena sukaso na auraba, sai yanzu daga baya.

     Jin jina kai malam da'u yayi, ya ce, "lallai kinyi Sake yarinya, amma zanyi iya bakin k'ok'arina Dan ganin kin mallakesa, Dan naga itama bata sonsa shima haka, Dan haka zamuyi nasarar rabasu cikin sauk'i, kid'aukama kinzama matarsa kawai.

   Wasu kayan tsubbunsu yabata, yamik'a mata wani ruwa a 'Yar jarka, ga wannan duk yanda zakiyi to kiyi Dan yasha abunnan, wannan kuma acikin abinci, sau uku zakiyi duka, Indai har yaci Yakuma sha tozaice ke yakeso, kuma zai saki k'anwarki.

   Wannan kwallin kuma kiringa sakawa a idonki, kiyi k'ok'ari kuma Ku kalli juna ido cikin ido.


To malam ngd sosai Safna tafad'a tana washe baki, to amma malam duk tayaya zanyi wannan aiki nida ba gida d'aya mukeba?.

   Malam yayi dariya, kekam saikace ba maceba, kiyi duk yanda zakiyi ki aikata, wannan yarage naki, nidai nagama nawa.


Tunda suka baro gidan malam babu mai magana da wani tsakaninta da baseera, kowa da abunda yake sak'ama zuciyarsa.

   Safna dai tunaninta nakan yanda zataci nasarar ciyar da BOBO wad'an nan magungunan.

    Amma zata gwada wata dabara tagani.

   

*_(“ni bilyn Abdul na ce, " hummmmm, muje zuwa Safna.”)._*



.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

       Jikake keyyyyyyyyyy yaja wani wawan birki da k'arfin tsiya Dan ganin wasu zaratan samari majiya k'arfi agabansa, sai faman huci suke suna mummurd'ewa, alamar jin karin k'aimi akan burinsu.

   d'an tsaki yaja tareda cije le6ensa na k'asa, afili ya ce, "wad'annan k'ananun karnukanfa nawaye?.


“na ce, " hummmmm.”


Murfin motar yabud'e cikeda Isa yafito, kuma fuskarsa tana nuna alamar hankalinsa kwance yake, yarufe murfin sannan yajingina ajikin motar, hannayensa yatura cikin aljihun farin wandonsa, ya hard'e k'afafunsa biyu dake sanye cikin Jan takalmi sau ciki mai k'yawun gsk, idanunsa sanye da siririn farin gilas, yad'an karkace kansa gefe yana k'are musu kallo d'aya bayan d'aya, shi dariyama suka bashi, Dan haka yasaki wani lallausan murmushi mai birkita ma'abocin kallonsa Wanda Ammar yasakama suna murmushin mugunta, Dan yafi bomb had'ari.

   Cikin muryarsa mai taushi da amo ya ce, ''yan samari halan lafiya dai?.

     Zaratan samarin suka k'ara babban k'aro k'irji gaba had'eda hura hancinansu danjin furucin BOBO maicikeda rainin wayo.

   d'aya daga cikin samarin ya ce, "lafiya idan kabamu abinda muke nema, amma babu lafiya idan kace zakayi kuskuren hanamu.

   Tofa, yafad'a yana k'ara sakin lallausan murmushi, lokaci d'aya kuma yahad'e fuska tamkar hadarin gabas, yasaka d'anyatsa d'a yajawo gilashinsa k'arshen hanci, saikuma yasakeyin murmushi, Yakuma gyara tsayuwarsa, ya ce, "to  yan samari miye buk'atar taku?.

    Kallon juna sukayi Dan aganinsu yaji tsoro, nafarkondai yasake yin magana, d'an uwa takardun dake cikin motarka Daka kar6a yanzu muke buk'ata.

   'Yar dariya yayi akaro na farko, yakai hannunsa na dama ya shafa lallausar k'asunbarsa ya ce, " tofa, aikin babbane Ashe, hannunsa yacire daga aljihu, yatako ahankali yak'araso har Inda suke, yakuma binsu da kallo d'aya bayan d'aya, sannan yamaida kallonsa akan mai maganar, Wanda nake k'yautata zaton shine ogansu.

   Cikeda Isa ya ce, "yan samari bayan takardu mikuke buk'ata?.

      Wata mahaukaciyar dariya babban yasaki, saida yayi mai isarsa, BOBO na tsaye yana binsa da kallo, shima yakalli BOBO cikeda izza ya ce, "d'an saurayi konace matashin lauya bama buk'atar komai bayan takardunnan dai, sukad'ai sun wadatar damu..............

    Kafin yarufe baki yaji wani shegen naushi akumatunsa na haggu.

   Tuni oga yazube ak'asa a sandare, BOBO yabishi da kallo yana murmushi tareda shafa gemunsa na gayu, 'yan samari har wannanma bakwa buk'atane????.

   Gaba d'aya sauran zaratan samarin sukayo kan BOBO, wani juyi yayi akansu saiga biyu ak'asa.

        ‍♀sum sum nakoma bayan motarsa namak'ale kafin a maujeni     kurasa mai d'akko muku rahoton kuma.

     Tabd'ijan masu karatu nifa azatona a film kawai ake irin wanga Abu, Ashe afilima anayi, cikin 'yan mintuna saiga 'yan samarin nan kwance ak'asa gaba d'ayansu.

   Daga mai karyayyen hannun saimai karyayyar k'afa, saimai zubabben hak'ori.

    Amma gwarzon naku ko zoben dake yatsansa bai fad'iba barema ayi zaton yaji ciwo.

    Yataka hannun wani yana tsaki mtsowwwwww shashashu k'ananan karnuka kawai.... Uban waye ya aikoku gareni??, Ku karnukan farautar wayeeeee!!!!!!?. Yay maganar cikin k'araji!!!!!..............

   

  " wayyo masu karatu, tsawar BOBO tarazanani, tuni nakwasa da gudu na6uya bayan wata bishiya, inaga kuyi hak'uri kawai zuwa gobe idan nasamu nutsuwa saina idabaku rahon yanda BOBO yak'are da karnukan farautarnan kamar yanda yake fad'a musu........



*"_hummmmm kowaye ya aikoma BOBO 'yan daba?. Shin Safna zatayi nasara kuwa?, towai ma ta Yaya zata iya ciyar da BOBO wanga kayan tsubbu?._*

     Kudai kucigaba da bibiyar 'Yar mutan kanawa da katsinawa danjin yanda zata kaya.

    _bilyn Abdul ce      _



👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{BoBo}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*


🤝 *_Assalamu alaikum. Happy new Islamic year 1439AH. Wish you all the best in this new Islamic year. Amen thumma Amen._*

4⃣8⃣


Mota yakoma yad'auki d'aya daga cikin wayoyinsa, sai hura hanci yakeyi, bugu biyu akad'aga, ad'an kausashe ya ce, "Ammar ina buk'atar yaranka.

    My guy lfy kuwa?.

  Mtsooowww wasu wawaye aka turomin, so nad'an koyar dasu zaman tarbiyya ne.

   Murmushi Ammar yayi, Dan yasan waye abokin nasa, okey kabani 15m. Katsal.

   Baice k'alaba ya yanke wayar, cikin motar yakoma ya zauna, amma murfin abud'e yake, k'afafunsa duk suna k'asa.

   Mintuna kad'an saiga motar police, tuni aka yayibi karnukan farauta acewar BOBO aka watsa amota.

   Bobo yakalli police d'in ya ce, " kukaisu asibiti, abasu kulawa ta musamman, zuwa gobe kuma natsincesu a Stations, yana gama fad'a yashige motarsa.

   Suma 'yansan Dan mota suka shiga, harya tada mota wani police ya kwankwasa MASA, sauke gilas d'in yayi yana kallon matashin police d'in batareda yayi maganaba.

  Umm yaya dama cewa nayi kozamu fara rakaka inda zaka tukunna.

   Fararen idanunsa yad'ago, wad'anda ahalin  yanzu sukad'an canja kala zuwa jaa, no karka damu Musadiq kuje kukaisu asibiti, sune keda buk'atar taimako baniba, saidai zuwa gobe kutabbatar da sunk'ara cin ubansu, harsai sunfad'i wanda yaturosu.

    d'an murmushi Musaddiq yayi wanda daga gani akwai sanayya tsakaninsa da bobo, ya ce, "ok yaya ALLAH ya tsare.

   Shima bobon murmushi yayi tareda jinjinama musaddiq sannan yaja mota yay gaba.

    Musaddiq yabi motar da kallo yana murmushi, shidai arayuwarsa yana k'aunar ya Abdulmaleek domin mutumin kirkine, yanzudai kalli anturo mutane dansu cutar dashi, yakuma sassanbad'esu amma saboda adalaci ya ce, " akaisu asibita abasu kulawa ta musamman, (ALLAH sarki aunty Ni'ima, ALLAH yajik'anki, inama kina darai har yanzu, daduk gidanmu sainace kinfi kowa dace da miji nagari).

   “araina na ce, "kenan k'anin marigayiya Ni'imane shi?.”🤔 




   Guri yasamu yay farking cikeda tak'ama yanufi office d'insa, sai rissinawa ma'aikatan wajen suke suna kwasar gaisuwa, ransa a6ace yake danhaka ko amsa musu bayayi, hannu kawai yake d'aga musu.

    Sakatariyarsa ta jinjina kai, aranta ta ce, " yau kuma boss afusace akazo?.

   Zama tayi bayan yashige, turare tad'auka tak'ara fesama jikinta tareda k'ara gyara  fuskarta, sannan tanufi office d'in.

       Kamilu masinja yata6e baki yana fad'in yarinya wahala bata ishekibane, nasan ko matan duniya sun k'are wlhy oga bazai sokiba.

    Ahankali ta tura k'ofar tashiga, yana zaune akan kujerarsa ta alfarma, kwance yake acikin kujerar idonsa alumshe yanad'an lilawa ahankali, tabishi da kallo zuciyarta na zungurarta da wani Abu, a zuciyarta ta ce, "ALLAH ya mallaka minkai amatsayin mijina.

  

Na ce, " hummm."


K'arasawa tayi Inda firij yake, tad'akko drinks da cup tanufi inda yake.

    Saida tagama tsiyaya lemon sannan ta ce, "oga ga abinsha ko kana buk'ata?.

    Baice mata komaiba, saidai yabud'e idanunsa dasukayi d'anja Dan 6acin rai.

   Waye yazo nemana?, yafad'a cikeda karsashi.

    Tuni takama kanta, cikin d'ari² ta ce, ''mutum 3 sunzo nemanka amma biyu sun had'u da yalla6ai Kamal.

   Ya ce, "d'ayanfa?.

 Ta had'iye yawu kuut, d'yan Ra'is ned'an gidan........ Hannu yad'aga mata alamar baya buk'atar k'arin bayani, yay mata nuni tatafi.

   Tafiya take cikeda salo tana juya mazaunai, hartakai k'ofa ya ce, "k zonan.

   Cak tatsaya k'irjinta na dukan uku², ahankali tajuyo saitaga bama ita yake kalloba waya yake dannawa, jiki a sanyaye tace sir gani.

     Idanunsa akan waya ya ce, "k sau nawa zan fad'a miki karki sake zuwamin nan da k'ananun kaya office?.

   A zuciyarta ta ce, " danka k'yasane, amma afili saitace sorry sir zan kiyaye.

   Tsaki yaja, har yanzu idonsa nakan waya ya ce, "wlhy daga yau kika sake banzar shiga kikazomin office abakin aikinki, 6acemin anan!!!!.

    Dasauri tafice Dan atsawace yay maganar.

   Yay kwafa tareda fad'in stupid gal kawai.

    Waya ya d'auka yakira kamal, bugu d'aya ya d'auka, kamal kana office ne?. Eh Abdulmaleek, ka isone?.

   " eh yanzu na k'araso".

   Okey ina zuwa.

     Laptop yajawo yafara danne dannensa, bayan wasu 'yan mintuna saiga kamal, hannu yabashi suka gaisa, sannan ya zauna.

   Wai ina ka mak'alene?.

   Laptop d'in gabansa ya ture gefe, yadafe tebir yana kallon Kamal, kabari kawai d'an uwa inacan an ritsani za'a kashe.

    Ban ganeba?, kisa kamar ya?.

    Ajiyar zuciya bobo ya sauke, ya CE, "wlhy kuwa kamal, wasu k'anan karnukan farauta aka turo waisu kar6i takardu a hannuna, nasandai bai wuce aikin wawayennan ba.

     Suwa kenan?.

Ra'ees da babansa mana, Dan babu wasu takardu ahannuna saina kes d'insa, kuma sakatariyata tace yazo nemana.

   Kwarai kuwa d'azu Nazo danmuyi magana baka nan, to ayayin shigowata mun had'u, zaifita nikuma zan shigo.

    Humm, kamal lokaci yayi dazan fito naci uban mutanen nan fa.

   A'a Abdulmaleek karkayi haka, har yanzu munada sauran bincike kaima kasani.

   Hakane, amma wlhy natsanesu.

   Wlhy nima hakantake, yanzudai bara naje, inada wata shari'a anjima kad'an, idan mungama zan dawo.

   Okey saika dawo to.

     

Tunda kamal yafita yabar office d'in bobo yafad'a duniyar tunani, tunanin Rahma ya kanainaye zuciyarsa gaba d'aya, haka kawai yarinyar tana birgeshi, ko kad'an batada damuwa.

    Murmushi yayi tareda kauda tunaninta yamaida hankalinsa ga tuno Wanda zai iya turo masa 'yandaba,  yamik'e Dan har yanzu ransa a6ace yake, wani wawan huci yafurzar tareda naushin iska, waini za'a turoma 'yan daba yafad'a cikin k'araji, yacije le6ensa yana gyad'a kai humm zanyi maganin koma wane d'an iskane.

     K'arasawa yayi gaban firij ya tsiyaya lemo akofi yakoma jikin windown office d'in na gilas ya tsaya, hannunsa d'aya a aljihu d'aya rik'eda kofin.

    Ahankali yakai kofin bakinsa yakur6i lemon, idonsa akan mutanen dake fitowa awasu bak'ak'en jeep,  Alhaji Abdurazak yafad'a yana gyad'a kai tareda ta6e baki, yad'anyi shiru alamar tunani, amma miyasa tunanina bai kawomin kai acikin wad'anda zasu iya turamin 'yan daba ba?.

   Yasaki murmushin nan nasa na mugunta.

    Sakatariya taturo k'ofar da sallama.

   Bai juyoba amma ya amsa sallamar.

   Ta ce, "sir.......

 Hannu yad'aga mata, ya ce, " kice yashigo.

            Tad'an zaro ido Dan abin yabata mamaki, bayau Alhaji abdurrazak yafara zuwa office d'innan ba, kuma duk sanda yazo oga baya bashi damar shigowa, Amman yau tunkan tafad'i ko waye yace yashigo, kuma tasan yagansa ta inda yake tsaye, kai lamarin da mamaki.

  Itadai haka tak'arasa tasanar da Alh Abdurrazak, shima abin yabashi mamaki amma saiyayi tunanin ko bobo yaji tsorone.

      

Bobo yana tsaye baikuma juyoba har Alhaji ya zauna, saida yaja tsawon Minti biyu sannan yajuyo, taku yakeyi cike da isa harya k'araso mazauninsa.

    Abin ya harzuk'a Alhaji amma saiya dake.

      Bobo dake lila kujerarsa ahankali, idonsa akan alhajin ya ce, "Alhaji mike tafe dakaine?, yay maganar cikin salonsa na isa.

      Alhaji yacije le6en jin haushi, saikuma yayi murmushi Barrister nazo maka da Business ne.


Bobo-- hummm wane irin business?.


Alhaji-- Akan aikine.


Bobo--- miyasa saini?.


Alhaji-- saboda ka cancanta.


Bobo-- kayi kuskuren fahimtar hakan.


Alhaji-- miyasa kayi gaggawar yanke hukunci?.


Bobo-- saboda hakane yadace, kuma nasanka nasan kaina, bamu dace da had'a business ba.


Alhaji-- a'a Barrister ka saurareni.


Bobo-- mizaisa na saurareka?.


Alhaji-- Saboda nayimaka bayani yanda zaka aminta dani.


Bobo yayi murmushin rainin hankali, Alhaji miyasa kakeson takuranine?.

      Kayi hak'uri maganata mai muhimmancice tasha banban data baya Barrister.

     d'an kafeshi da ido bobo Yayi, dayin tunani na second 20, yalumshe idonsa ya ce, " INA saurarenka.

    Murmushi Alhaji yayi, azuciyarsa ya ce, "dole ka saurareni aii, yagyara zama yana fad'in Barrister dama akan maganar yaron aboki nane Alhaji sunusi dala, nawa kakeso mubiyaka ka lalata shari'ar?.

    Bobo bai amsa masaba, hasalima hankalinsa yana kan bodyguard d'in Alhajin dake k'ok'arin zarar wata takarda da bobo ya ajiye akan Derk's d'insa. Murmushi bobo yayi ya ce, " mai gadi zaka saidama mai k'osaine?.

    Dasauri bodyguard d'in yacire hannunsa Yakuma matsa baya.

     Bobo ya girgiza kai yana maida kallonsa ga Alhajin, INA saurarenka.

     Alhaji da haushi yakashe, jiyake tamkar yasa aharbe MASA bobo Dan haushi da tsanarsa dayayi, yazaro sigari yasaka abaki, dasauri d'aya daga cikin bodyguard d'in yakunna leta zaisakama alhajin....hannu bobo yad'aga masa, yatashi tsaye tareda rankwafowa akan tebir d'in yasaka yatsunsa biyu yazare sigarin bakin Alhajin yana girgiza kai, sorry Alhaji ba'a shamin sigari a office, saboda yana lalata lafiyar maisha da mai shak'ar warin.

    Ya ajiye masa kusadashi akan tebir d'in, gata nan idan katashi tafiya zaka iya d'aukar kayanka, Yakoma ya zauna.

   Wani Abu ya danna yay k'ara saiga sakatariyarsa da Sauri tashigo, bai kalletaba ya ce, "kawoma Alhaji abin sanyaya mak'oshi Dan yana buk'ata.

     Okey sir, tafad'a cikeda girmamawa.

     Alhaji kam ya k'ame azaune, lallai yak'ara tabbatarwa yaron nan d'an iskane, amma zasu gyaramasa zama, a fusace Alhajin yamik'e yakar6i lemon da sakatariya tamik'o masa yay jifa dashi, kofin yadaki bango ya tarwatse.

     Wata dariyar rainin hankali bobo yayi, yamik'e yana tafa hannayensa wooow! Alhaji ammafa ka burgeni, kaga yanda kayi d'innan haka nayima yaranka Nima d'azu da safe, saidai banbancin d'ayane, kai Kofi kafasa, nikam mutane na jibga.

     Aburkice Alhaji yake kallon bobo kuma atsorace, amma saiya danne yahad'e fuska tareda Nuna bobo da d'anyatsa, kai k'aramin tantiri kashiga hankalinka, yaro kai k'aramin naman dajine idan yanzu mukaso saimu hallaka ka tamkar yanda muka hallaka.........haba Alhaji mikakeson fad'ane haka?.

       Bodyguard yay saurin Tatar numfashin Alhajin.

      Bobo yayatura hannayensa a Aljihu yana murmushi, ya ce, ''no no no mai gadi, Daka barsa yak'asa fad'a kaga ya ragemin nauyin bincike, amma babu laifi hakanma ngd sosai  yak'are maganar da d'aga fad'a yana ta6e baki, aii kobai fad'aba nasan yanaciki.

   Yakuma gyara tsayuwa, yataka daf da Alhaji ya tsaya, ya ce, "Alhaji kakirani k'aramin naman daji.

   Bakayi k'aryaba, tabbas ni naman dajine mai amsa suna *_ZAKI_*, ni zakine bana 6arnar banza, ammafa duk sanda naji yunwa kowa Shiga hankalinsa yakeyi, Ku saurari fitowata Dan duk sanda naji yunwa saina lak'umeku amatsayin abinci mafi Girman k'an k'anta darashin daraja............

    Kai!!!!. Alhaji yakatse bobo atsawace, yanunashi da d'an yatsa Abdulmaleek Aliyu kataka a sannu zakinma yanada nasama dashi ko'a cikin dajin.

   Dariya bobo yayi ya ce, " hakane Alhaji akwai manya manyan namun daji adokar daji, wad'anda sukafi zaki Girman jiki harda shekaru, amma girmansu baya hana zaki ya kacaccalasu aduk sanda ya harzik'o, barema idan yanakan ganiyar k'uruciyarsa, Dan haka Alhaji abdurrazak bulama Ku saurari matashin zaki yana nan tafe gareku, zaka iya barmin office kuma ka saurari sammaci, Dan zan maka ka akotu kaida karnukan farautarka, inason bin ba'asin bibiyar numfashina da kukeyi.......

   Fuuuuu Alhaji yafice batareda yaji k'arshen zancen bobo ba, jiyake idan yakara minti d'aya a office d'in zuciyarsa zata bugane kawai.

   Wani wawan tsaki bobo yaraka Alhaji dashi.


_(Na sauke nannauyan numfashi Dan ganin anrabu lafiya bobo baikai dukaba, danni yanzu tsoronsa nakeji)._



*_bayan kwana uku._*

      Yau tsawon kwanaki uku safna tanata sak'awa da kwancewa, kullum Neman hanyar dazai kaita gidan Rahma takeyi amma tarasa gaba d'aya, tayi wujiga² saboda rashin mafita.

    Ganin babu yanda zatayi yasa tasaki jikinta tanata harkokinta, agefe kuma kullum saita turama bobo message.

   Tunbaya kulawa har yaudai yaymata replay, wani uban tsalle tazuba Dan dad'i, tad'ane gado tanata tsalle abinta.

   Ganin yayi mata replay yau yasa tak'ara masa wani massage d'in na kalamun soyayya masu dad'i, amma har dare babu amsa, data kirama saiya katse kiran yakashe wayar duka.

    Lamarin ya Sosa ranta amma saita dake, tana fad'in k'ila baya kusada wayarne.

   

Nidai araina na ce, "hummm.


*_kotu_*

    Ayaune kuma su bobo suka koma kotu.

    Bobo bai k'asa aguywa ba yakawo manyan hujjoji da shedu masu k'arfi wad'anda suke nuna haneef ya aikata fad'e ga muheebat. Ciki kuwa harda muheebat d'in kanta, wadda ya sulaiman yayma aiki ayanzu haka tana magana.

     Bobo yak'arasa kusada muheebat ya ce, " muheebat kotu tanasonji miya faru dake aranar 16/8/2017?.

       Muheebat matashiyar yarinya mai wayo, tagyara tsayuwa, idonta na zubda hawaye ta ce, "yaya aranar  data kasance 16/8 mama ta aikeni shagon Haleedu domin nasayo mata sabulun wanka.

   Fitowata kenan Haneef yafito daga gidansu da mota..............





*_ina mai baku hak'uri saka makon jina shiru, hakan tafarune saboda matsala da screen d'in wayata daya samu adaren Dana turo muku page 47, tom yanzudai komai ya daidaita._*


   _Acigaba da gashi!!!._






*_imiss you so much my fan's._*😍😍😍💋💋.







*_luv u oll._*



👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{BoBo}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*



4⃣9⃣


      Kamar yanda yasaba duk sanda yaganni yakanyimin murmushi aranarma haka yamin.

    Nad'aga masa hannu nima ina murmushi.

   Ya ce, "min heeban baba ina zakije?.

    Kasancewar alokacin bana magana namasa nuni da shagon haleedu da hannu.

   Yayi dariya tareda kamo hannuna, amma saina nok'e saboda inna ta hanani, ganin haka yasa yad'akko alawar dayakan bani kullum idan zani makaranta.

    Nikuma namik'a hannu zan kar6a saiya jawoni gaba d'aya cikin motar, daga wannan lokacin ban sake sanin inda nakeba sai a asibiti, wannan kad'ai nasani.

   Murmushi bobo yayi tareda juyowa ga alk'ali, ya ce, " yamai shari'a wannan hujjar kad'ai ta isa tabbatarma kotu cewa haneef ya aikata keta haddi ga heeba,  abin lura anan shine haneef yadad'e yana  k'ullama yarinyar gadar zare tahanyar bata alawa, ganin bazaici nasara tasauk'iba shine yasaceta tareda shak'a mata wani Abu harta rasa hankalinta, yaje ya aikata yanda yakeso da ita, awashegarin ranar yazo bakin titi nesa da anguwarsu ya jefar da ita dankar aganeshi, saidai kuma yamakaro Dan angansa harma aka d'uki number motarsa.

   Dan haka ina rik'on wannan kotu mai adalci datayi dubi da d'unbin shedunmu kuma da maganganunsu ta kwatoma wannan 'Yar yarinya hak'inta.

     She data tak'arshe itace zuwan Alh Abdurrazak abokin Alh sunusi office d'ina, yamai shari'a INA buk'atar tv,  babu 6ata lokaci aka kawo TV, wani kaset bobo yasaka Wanda yayi copy d'insa daga computer office d'insa, duk abinda yafaru tsakanin bobo da Alh Abdurrazak saida suka gani.

     Tuni jikin Alhaji sunusi yay sanyi, yasan yau d'ansa yatafi saidai wani ikon ALLAH, amma tunda sunbama Alkali kud'i k'ila ya ku6ta.

    Bobo yay shiru tareda kafe alk'ali da ido tacikin gilas.

 

Jikin alk'alifa yay sanyi, yasan tabbas duk abinda bobo yafad'a gsky ne, saidaifa matsalar yaci kud'in Alh sunusi tareda masa alk'awarin zai ku6utar da Haneef, gefe kuma ga bobo yasan Barrister AAA hamshak'i sarai bashida sauk'i, kuma zai iyayin komai danyaga yakar6ama yarinyar hakkinta, azuciyarsa ya ce, "gaba kura baya damisa kenan.

    Dandanan ji6i yajik'e alk'ali dukda yawan fankoki dake bada iska acikin kotun, asaitinsama akwai guda d'aya da aka aje danshi kad'ai sai abin yabama bobo dariya, Dan haka ya murmusa tareda yin wata inkiya da yatsu biyu wadda alk'aline kawai yasan miyake nufi, kuma yasan abinda bobo zaiyi inhar ya danne shari'ar, yashare gumi yana maida kallonsa ga lauya mai kare haneef, ya ce, " lauyan Wanda ake k'ara kokanada abin fad'a?.

    Girgiza kai lauya yayi ya ce, "a'a.

   Alk'ali yamaida Kansa ga k'aton littafinsa yana dubawa.

    Gaba d'aya ran Alh sunusi ya6aci, jira yake kawai yaji hukuncin daza a yanke, lallai yaci burin saiya koyama bobo hankali inhar d'ansa yashiga cikin garari........

    Bai rufe bakiba maganar alk'ali ta dakatar dashi.

   Bayan Alkali yayi surutansa asashe nakaza zuwa kaza anyankema haneef d'aurin shekara 14 agidan yari, datarar nera miliyan d'aya da rabi domin inganta rayuwar yarinyar da karatunta. 


Wani ihu haneef yakurma, saida aka rik'eshi, sai d'urama bobo zagi yakeyi.

    Shikam bobo ko'a kwalar rigarsa Yakama hannun heeba suka fice yana murmushi jin dad'i da samun nasara.

     Awaje yatsaya har aka fito da haneef, yaja gilas d'insa k'asa yana kallon haneef fuskarsa d'auke da murmushi.

   Ya ce, " haneef sunusi dala, so ina fata yanzu ka shaida wanene Abdulmaleek Aliyu Abdulmaleek hamshak'i, yanzu idan kafito saikayi takunka da sand'a gudun karkayi gamo dani Dan ruwaneni inhar nabayyana saina cinye gari, yay kasa² damurya zanyi missing naka my lovoly haneef bye aci gabza lfy..

    Yaygaba batareda yajira amsar haneef ba.

     Daga Alh sunusi har haneef ido sukabi bobo dashi, haneef ma kuka yakeyi, Alhaji sunusi kam ALLAH kad'ai yasan miyake kitsama zuciyarsa.



.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*

    Bobo yakwashi su muheebat sai gida, sai saka masa albarka iyayenta sukeyi, har gida yakaisu, inna tashimfid'a masa tabarma ya zauna.

    Cikin nutsuwa ya ce, "baba inaso kuyarda kubini can gida wajen iyayena kamar yanda nabuk'ata d'azu da safe, saboda gsky zamanku bazai yuwu anan anguwarba yanzu, na tabbata Alh sunusi bawai ya hak'ura baneba, to Dan haka nama iyayena bayanin komai, kuma sun bani izinin yau idan anyankema haneef hukunci to nawuce daku can gidan kud'an zauna nawani lokaci har abubuwa su daidaita.

    Baba yagyara zamansa, ya ce, " abdulmaleek kana ganin bazamu takurasu ba?.

   A'a wlhy baba babu wani takurawa ka kwantar da hankalinka.

   To shikenan mungode ALLAH yayimaka albarka ya azurtaka da yara nagari, ya albarkaci iyalinka da zuri'arka.

    Amin baba ngd, yanzu Abu nagaba kuma shine idan kun koma can heeba zata cigaba da karatunta, za'a canja mata makaranta, kud'in da kotu ta kar6a mata kuma sai a ajiye mata a account harzuwa nangaba idan ta mallaki hankalin kanta saitayi abinda takeso dasu, yad'ago yana kallon idris da fuskarsa ke cikeda farinciki, dama kullum burinsa yaga tilon k'anwarsa tana karatu, amma yanayin rayuwa ya hana hakan.

   Mungode ya Abdulmaleek.

   Murmushi bobo yamasa ya ce, "karka damu, inaso naji kai INA katsaya anaka karatun, mikuma kakeyi yanzun?.

    Matakin secondary nagama yaya, yanzu kuma ina aikin direba agidan su Rahma matarka.

   Bobo yajinjina kai ya ce, " babu damuwa kabani takardunka insha ALLAHU zan nema maka makaranta.

   Baba d'aya su baba da inna da idris heeba suka kaure da godiya ga bobo inna harda kukan farinciki itada baba.

    Bayan sun had'a 'yan kayansu masu muhimmanci bobo yakwashesu sai gidan Appa.


Tarba akayi musu ta mutunci dan ansan da zuwansu.

    Su inna sun yaba da kirkin wad'annan mutane darashin k'yamar talaka, 6angaren da aka gyara musu aka saukesu.

    Bayan gaishe², bobo yamik'e yana fad'in Ammi bara nad'anje gidan sai zuwa anjima zan dawo, nasan su yayama Duk zasu shigo yau.

   To mukarram ALLAH yakaimu, agaidamin d'iyata da Nawal.

    To ammi zasuji, ina tagwayenkine?.

   Yo basuna gidankaba.

    Ayya aiban saniba bara najeto.

   Agurguje yafito yashiga mota sai gida.


.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

      Su Rahma duk suna zaune suna kallon wani India film, sunyi mugun shagala akallon film d'in Dan ana zuba soyayya ne.

    Bobo yashigo da sallama amma basujiba, tsayawa yayi yana musu kallon mamaki, TV yakalla danson ganin miya d'auke hankalinsa, shima shiru yayi yana kallon yanda mata da mijin suke zabga soyayya mai k'ayatarwa.

   Kamar ance Rahma takalleshi tad'ago, baya tayi da Sauri tareda zaro ido, cikin Rawar murya ta ce, "sannu da dawowa.

       Khairiyya da khursiyya suka d'ago alokaci d'aya suma suna kallonsa.

  Amamakinsu saisukaga yayi murmushi tareda fad'in lallai yarannan gaba d'a film yatafi da imaninku ko sallama bakwaji ko?.

      Wlhy Yaya bamusan kashigoba sannu dazu.

   Murmushi yayi tareda nufar d'akinsa.

   Khairiyya ta kalli Rahma, auntynmu yaufa mijinki yana cikin nishad'i wlhy.

    Rahma tad'anyi murmushi, nimadai nakula da haka khursiyya, komiye yasakashi nishad'i?.

    Dariya sukayi gaba d'aya, Rahma ta tashi dukda zuciyarta na dukan Tara Tara Dan kwana uku kenan baya cikin wata walwalar kirki, amma yau gashi yashigo musu cikin nishad'i, ruwa ta d'auka da cup tanufi d'akin.

     Ahankali tayi Knocking kamar bataso. Yana kwance akan gado fuskarsa cikeda nishad'i, yau jinsa yake sakayau dashi, jin Knocking d'in k'ofa yasashi juyawa tareda amsawa, ya ce, " shigo mana.

      Rahma tashiga a sanyaye tareda yin sallama a can k'asan mak'oshinta.

     Fararen idanunsa yad'ago yana kallonta, yad'an lumshesu sannan yabud'e akanta, hakan yayi daidai da rank'wafowarta zata ajiye masa tiren agabansa, wani nannauyan numfashi ya sauke yayinda idanunsa sukayi tojali da k'irjinta daya bayyana saboda wuyan rigar babbane.

      Itakam dabatasan miyakeyiba ta tsiyaya ruwa akofi tad'ago zata bashi, kallo d'aya tayi. Masa ta kauda kai Dan ganin yakafeta da mayun idanunnan nasa masu hasken tsiya.

    Ya lashi le6ensa nak'asa tareda kar6ar kofin tamkar wani soko, tana bashi takama hanya zata fice yay saurin damk'e hannunta.

   Gabantane yafad'i amma bata juyoba, shima baiyi maganaba hasalima ruwansa yake sha idonsa kuma akan TV dake manne abagon d'akin, sunkai minti uku ahaka sannan ya ajiye kofin hannunsa yadawo da kallonsa kanta, bayanta yakebi dakallo aransa ya ce, "yarinyar tanada sura mai k'yau saidai tacika yarinta..... Mutsu mutsun kwacewa da takeyine yadawo dashi hayyacinsa, yakuma rik'e hannun nata sosai, cikin muryarnan tasa mai sanyin dad'i ya ce, " jimana.

    Maganar tabama Rahma dariya wai jimana saikace Wanda yaga budurwa a hanya, shiru bata juyoba danhaka shikuma yamik'e, haryanzu hannunta yana cikin nasa, yamatso daf da ita hartanajin saukar numfashinsa akan bayanta, tad'an runtse idanunta Dan idanhar bobo yakusanto ta takanji tsigar jikinta tana tashi....   

    Bata k'are tunanin nataba taji yarungumota ta baya, yazagayo da hannayensa duk biyu saman cikinta, jikintane yakama rawa cikin rawar murya ta ce, "pls kayi hak'uri su khursiyya suna jirana a falo.

   Murmushi yayi tareda kawo bakinsa Kusada kunnenta muryarsa tayi low sosai can k'asan mak'oshi ya ce, " wato su khairiyya sunfi mijinki muhimmanci ko?, yanda yay maganar akunnenta sai duk ta dabarbarce, tajuyo akid'ime, kallo d'aya tamasa gabanta yafad'i, Dan ganin fuskarsa ta canja hartayi d'anja, hakama idanunsa sunyi ja, girgiza kai tayi tana fad'in bafa haka nake nufiba, munayin girkine Dan Nawal takusa dawowa daga school.

     Baki yad'an ta6e yana jinjina kai, idonsa akanta ya ce, "aikinga anraba kenan, su khairiyya sukula da Nawal, kekuma ki kula da baban Nawal ko?.

   Rahma tak'ara kasa da kanta, shikuma yayi murmushi tareda saka yatsunsa biyu yad'ago ha6arta, lumshe idanunta tayi, shikuma yashiga Raba idanu bisa k'yak'yk'yawar fuskarta, muryarsa ta canja Dan akasalance yake magana, ya ce, " Abu d'aya zakimin nabarki ki tafi.

   Da sauri tabud'e idanunta ta ce, "minene?.

     Gira yad'aga mata yana wani kasa k'asa da idanu, kibiya bashin danake binki na kiss, dankinsanfa ni bana mantuwa.

   Zaro idanu Rahma tayi, ta marairaice fuska kamar zatayi kuka, Dan ALLAH kayi hak'uri wlhy bazan iyaba.

   Yakuma narke murya to saboda mi?.

    Inajin kunya.

Kunya kuma?.

  " eh".

Lallai kinada aiki, dole ki shirya zama mara kunya kuwa indai kina taredani, danni mutumne dabayason kauce², sak nake kuma komai nawa sak yake, inaso da sauri shiyyasa nakasance mai sauri, inaso da k'arfin zuciya shiyyasa nakasance mai dakakkiyar zuciya, inayi da yak'ini shiyyasa nakasance mai nasara, inayi da ikilasi shiyyasa ubangijin al'arshi yake taimakona adukkan al'amurana, kizama jaruma sai duniya tasanki, kizama mai gaskiya sai azzalumai suji tsoronki, kizama mai zuciya saiki kasance mai k'arfi, kizama mai hak'uri saiki ganki dayawan riba, kizama mai tunani saikomai naki yazama namasu hikima da k'yak'yk'yawan tunani, Abdulmaleek nakowane amma bakowa bane na Abdulmaleek, 'yammata karki tsaya kallon ruwa kwad'o yamiki k'afa, kizama mai jarumta dankiyi nasarar maida jiyana da yau da gobena duk suzama naki kekad'ai da 'yayanmu.

    Yana gama fad'ar haka yasumbaci kumatunta tareda sakinta yashige bathroom.

     Kamar sokuwa haka Rahma tabishi da kallo harya shige, sai juya maganganunsa takeyi aranta da k'arfin tunani da kwanji, amma kaf tarasa fassara ko guda d'aya aciki, tama rasa inda maganganun suka dosa, takai tsawon minti 6 awajen tsaye amma takasa fasa koda magana d'aya aciki, takuma kasa barin wajen, shikuma har yanzu bai fitoba.

     Ahankali tafice tamkar munafuka, tunda tafito su khairiyya kebinta da kallo suna k'unshe dariya, tazauna tana binsu da kallon mamaki, khursiyya tamatso Kusada Rahma tana shinshina jikinta, dariya sosai khursiyya takeyi, Rahma ta ce, "wai miye abin dariya?.

     Cikin dariya khursiyya ta ce, " a'a babu komai nadaiji kinata zuba k'amshin turaren ya Abdulmaleek ne.

   Da sauri Rahma ta shinshina kayanta, ilai kuwa kamshin turaren bobo takeyi, da sauri tamik'e tashige cikin kichin, khursiyya da khairiyya suka shek'e da dariya harda tafawa.

    Itadai Rahma tana kichin itama dariyar takeyi k'asa², lamarin bobo yana bata mamaki wlhy.............










*_luv u oll my fan's_*

*_(((S)))..........2017_*


👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{🅱🅾🅱🅾}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*



5⃣0⃣

     

       Tana cikin kichin zaune danta kasa fitowa, jitake kamar su khairiyya sunsan miya faru, ihun Nawal ne yasakata fitowa dole, tasaki su khursiyya tanufo Rahma da gudu tarungumeta tana murnar ganinta, tana cikin cire mata uniform bobo yafito sanye cikin farar jallabiya, Shima Nawal taje ta rungumesa, yad'agata sama yana fad'in babyna yaushe kika dawo?.

    Papa yanzun nan.

Toya school?.

  Lafiya lau my papa.

    To masha ALLAH sauka naje masallaci yafad'a yana direta k'asa, ya kalli Rahma datun fitowarsa tayi k'asa da kai, ya ce, "bara naje sallah.

   Saika dawo tayi maganar kanta ak'asa.

    Baice komaiba yafice.


  Yaudai haka Rahma tawuni atakure Dan duk inda tayi idon bobo yana kanta, ko kunyarsu khursiyya bayaji.

    Bayan sallar isha'i yashirya zai maidasu khairiyya Nawal tamak'ale wai saitaje, harsun fita yaturo Nawal takira Rahma itama tazo su tafi.

   Murna tayi sosai Dan dama tsoro takeji wlhy.

    Abaya ta tararda su khursiyya, dole tabud'e gaba tashiga, har Nawal zata shigo gaban ya ce, " takoma baya, Rahma tadaure ta ce, "pls kabarta muzauna aii zai ishemu.

    Baice komaiba yatada motar, saida yafita daga gidan sannan ya ce, " kina 'Yar lukutarnan ne kujera d'aya zata isheku?.

    Da sauri tajuyo tana kallonsa, amma shiba ita yake kalloba, idonsa nakan titi, d'an harara tamasa tareda murgud'a bakinta.....

    Babu zato ya ce, "nikikema murgud'e da harara?.

    Kanta tadafe Dan batasan yana kallontaba, aranta ta ce, " kai mutumin nan ya iya munafikin kallo wlhy, afili kuma ta ce, "nifa ban hararekaba, tak'are maganar da turo baki gaba.

    Murmushin gefen baki yayi batareda yace komaiba.

      Tunda suka shiga harabar gidan sukai karo da motoci reras, wannan alamace ta basawan gidan duksun zo kenan, shima guri yasamu yay fakin suka fiffito.

     Yana gaba suna biye dashi, da sallama suka shiga falon daya k'awatu da haske.

  Ya sulaiman ya ishaq ya Hamza duk suna gidan, hannu bobo yashiga basu suna gaisawa, su Rahma ma suka gaishesu tareda hayewa sama Dan gaida Ammi.

   Ya Hamza ya ce, " kace tare kuke gaba d'aya, bobo dake k'ok'arin zama ya ce, "yana iya baby tamak'ale saitazo, nikuma bazan iya barin Rahma ita kad'aiba shine na ce, kawai tataho mu tafi.

   Ya ishaq ya ce, " kai bobo banwani yardaba, kaid'innan baban soyayya.

   Murmushi bobo yayi ALLAH Yaya kunyi bala'in sakamin ido agidannan amma babu komai dukzan ramane.

   Dariya sukayi gaba d'aya ya sulaiman yad'an daki kafad'ar bobo yana dariya, autan Ammi barsu kaji, sumafa suna soyayyarnan.......

   Sakkowar Ammi daga sama ta tsaida dariyar tasu, bobo yarissina ya gaidata, bayan sun gama gaisawa ta ce, "tom kutaso Appan naku yakammala.

    Gaba d'aya suka mik'e abin sha'awa da burgewa, cikeda fara'a Appa yatari matasan samarin 'yayan nasa, suma duk suka zauna suka zagayesa, Ammi ta ce, "to akawo abinci ko?.

    Kowa ya CE, " a'a.

Appa ya hararesu bangane a'a ba, tuni nak'icin abinci saboda nasan zakuzo shine yanzu zakuce wani A'a.

   Dariya sukayi sukace to akawo ko kad'an suci.


    Tare sukaci abinci da Appan su, bayan sun kammala sukashiga tattauna abinda yakawosu, dama akan bikinsu Khursiyyane, antsaida sati hud'u kacal, dama shi Appa haka yake saka bikin yaransa bayaso danisa d'innan, anan take suka tsara komai data dace, kowa yad'auki abinda zai iyayi, Appa sai sakamusu albarka yakeyi shida Ammi, daganan hira sukad'an k'ara ta6awa sannan suka mik'e zasu wuce, bobo ya ce, "Ammi ina yarannan muwuce.

      Suwaye yara? Ya ishaq yatambayi bobo.

     Rahma da Nawal.

    Lah matarka kakecema yarinyar? cewar Appa.

    Dariya sukayi gaba d'aya, bobo  kam murmushi kawai yayi, ya ce, " Appa yarinyace mana shekarartafa 17.

    O Dan shekararta 17 saika ringa cemata yarinya?, to aii yanzu tagirmi wannan sunan, cewar ya Sulaiman.

     Bobo yaturo Baki gaba nidai kunga tafiyata saida safe, suduka dariya suka saka harda Appa da Ammi shidai yayi tafiyarsa d'akin Ammi, a can kuwa yasamesu sunata rubuce²  itadasu kahiriyya yana shigowa suka 6oye, kallonsu yayi ya ce, "mikuke 6oyewane?.

      Babu komai Rahma tayi maganar dasauri tana mik'ewa, yasan basuda gsky amma yayi fitowarsa yak'yalesu, azatonsa ko tsare tsaren biki sukeyi.

    Rahma tad'auki Nawal datayi barci, saida taje tagaida Appa tamusi sallama sunata sakamata albarka sannan ta iske bobo aharabar gidan shida sauran 'yan uwansa.

    Mota tashiga tajirashi, bayan sun kammala kowa yashiga mota sai gida.

    Tunda suka tafi babu mai magana, daga Rahma har Nawal barci sukeyi, dahakadai suka k'arasa gida, harya kashe motar yafito babu Wanda yamotsa, yaduk'o yana kallonsu Yoshi yanzu yama zaiyi dasu?, d'an tsaki yayi yad'auki Nawal yanufi cikingida, har d'akinsu yakaita ya kwantar bisa gado sannan yadawo, azatonsa zai Tatar Rahma ta tashi amma INA barcinta taketa shek'awa da Alama kuma yanamata dad'i.

    Aransa ya ce, " kegaki orobo amma sai son d'auka.


(Nikam bilynku nayi dariya araina, koyaushe tagaya masa tanason d'auka?.)


Itama d'aukarta yayi, yarufe murfin da k'afa sannan yanufi cikingida, sunkusa zuwa k'ofar falin tasak'alo hannayenta awuyansa, kallon fuskarta yayi yaga har yanzu barcinta takeyi, dak'afa yatura k'ofar yashiga, itama yadireta akan gadon, saidai yazo mik'ewa amma tak'i sakar Masa wuya Dan haryanzu hannayenta suna nan asak'ale, tsayawa yayi yana kallon fuskarta dad'an bakinta, sosai yake k'are mata kallo, yana kallonta  amma bakamar yau dayake mata kallon k'urullaba, aransa ya ce, "babu laifi yarinyar k'yak'yk'yawace.

   Sunkai minti hud'u ahaka, yakai bakinsa kamar zaimata kiss, komi yatuna? saikuma yafasa yad'an kalli gefen da Nawal take kwance, cikin dabara yazare hannanu NATA wai duk ak'ok'arinsa nakar ta tashi, him baisan Rahma dashegen nauyin barciba kenan.

   Yacanjama Nawal kayan barci, yatsaya yana tunanin yanda zai canja na Rahma, zama yayi gefen gadon, yasa hannu ahankali yazuge zip d'in rigar atamfar dake jikinta, cikin dabara yasa6ule hannun Riga d'aya, Yakama k'arfen bra d'inta yacire.... Aiikamar ance tafarka tamik'e zumbur, ganinsa zaune kusada ita gakuma rigarta har Anfara cirewa yasakata d'an zaro ido, cikin muryar barci ta ce, " malam lfy?.

     Lafiya k'alau malama yafad'a yana mik'ewa, baijira cewartaba yafice abinsa, itakuma tabishi da kallo tana muci muci da idanu.



 Na CE, "humm kwadaiji dashi.




.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

      *_Bayan kwana Biyar_*

 

    🅱🅾🅱🅾 yana kwance yana barcinsa kasancewar weekend ne, sama sama yaji kamar ana wak'ar.

     _“happy birthday to you, happy birthday, happy birthday, happy birthday to you...”._

     Tashi yayi zaune aransa ya ce, "birthday kuma?, tonawa kenan?, ihun Nawal dayaji yasakashi mik'ewa da sauri yanufo falo.

  Tofa, yafad'a yana rik'e k'ugu tareda tsayawa kallon Rahma da Nawal, Rahma tanata zubama Nawal wani Abu mai k'yalk'yali itakuma tana tsale, yabi falon da kallo shima yasha decoration d'in balam balam.

   Saikuma wani kati mai k'yau anrubuta...

   *_“happy birthday my luvly Nawal, rice 100 may ALLAH bless you abundantly...... I luv yau so much”_*.💝

    Murmushi yayi yataka ahankali har zuwa inda suke tsaye, yatura hannayensa duka a aljihu yatsaya yana cigaba da kallonsu.

    Nawal ce tagansa, cikin farinciki ta ce, " my papa today is my birthday.

     Murmushi yayi yadurk'usa k'asa tareda bud'e mata hannayensa, tazo tashige ya rungumeta, sorry my habibaty gaba d'aya namanta yau birthday d'inki, amma kigodema ALLAH daya baki momy tagari d'iyata, wannan yak'ara nunamin baki tareda maraicin rashin uwa, wasu 'yan hawaye suka mak'ale masa agefen ido.

   Jiyayi ana goge masa, yad'ago ido yana kallonta, dasauri tamatsa baya saboda kunya, yayi murmushi tareda mik'ewa tsaye shida Nawal, k'arasawa yayi inda Rahma take daf da ita tamkar zai shige jikinta, cikin wata sassanyar murya yace my Cute ngd sosai ALLAH yabaki lada mai tarin yawa, ALLAH yakaimu ranarda zaki haifamin k'annen Nawal agidannan...... 

   Da sauri tad'ago takalleshi, yad'aga mata gira... Aii saita shek'a da gudu tabar waje, tabashi dariya sosai Dan haka ya murmusa.

   Nawal ta ce, "papa miyasa momy tagudu?.

   Murmushi yayimata ya ce, " babu komai, jeki tashiryaki yau yawo zamuje tunda ba'a shiya miki wani bikiba.

   Sosai Nawal take tsalle za'a yawo.


Bayan kamar minti30 Rahma tagama shirya Nawal cikin kaya masu k'yau, falo suka fito suna jiran boss, babu dad'ewa shima yafito cikin k'ananun kaya, sunbala'in MASA k'yau sai zabga k'amshi yakeyi.

   Rahma ta ce, "masha ALLAH, ALLAH yayi halitta awajennan, duk azuciya take maganar shiyyasa harya k'araso kusada ita bata saniba.

     Namiki k'yaune?, yay maganar acikin kunnenta.

   Da sauri tad'ago tad'an murmusa tana jinjina masa kai tareda rufe fuskarta da tafin hannu.

   Shima murmushin yayi, yakuma fad'in aiini nakine 'yammata, kiyyiata kallona harki gaji.

    K'ara rufe fuskarta tayi Dan maganganunsa kunya suke bata, kutashi mutafi time nadad'a k'urewa.

   A'a kuje kaida Nawal ni akwai abinda zanyine.

   d'an harararta yayi ya ce, " ban ganeba?.

    Rahma ta marairaice tamkar zatayi kuka, ALLAH akwai abida zanyi, gobe idan ALLAH ya kaimu masake fita tare.

     Baice komaiba danyaji haushi, azatonsa batason zuwane kawai, Dan haka yakama hannun Nawal afusace suka fice daga falon.

   Binsu da kallo Rahma tayi tana murmushi, ta ce, "ayya dadyn Nawal kayi fushine?, saikuma ta jinjina kai ta ce, " zaka huce idan kadawo kaga miya tsaidani.


Bobo sai zagayawa da Nawal yake wajajen shak'atawa na musamman, duk inda suka giftta sai an kallesu kuma sai an k'yasa bobo Wanda in ba kasaniba bazakace d'iyarsa bace Nawal, zaka d'auka irin d'iyar yayansace kokuma k'aramar k'anwarsa, bakowa yake yarda bobo yata6ama aureba bare akai ga haihuwa.

      'Yammata marasa hak'uri kam har magana suke masa, wasukuma suyima Nawal kodan yatanka, amma ko kallo basu isheshibama.


A6angaren Rahma kam suna fita babu dad'ewa saiga Khursiyya da khairiyya sun iso damasu decoration, nandanan aka share harabar gidan suka fara aikinsu, tsaf suka gyara ko ina yad'auki k'yau, suka jere kayan kid'ansu..  

     Haba zuwa k'arfe biyu ai gida yafara cika da yara, matansu ya sulaiman da yaransu duksun iso, tare suketa hidimar had'a abinci, ga kayan rabonan ank'ukkula, zuwa k'arfe hud'u duk Wanda suka gayyata ya iso gidan.

     Awannan lokacin kuma bobo da nawal suna can sun lodo kaya daya sayama Nawal sun kamo hanyar dawowa gidan, dukda abinda Rahma ta masa da safe saiyaji baiji haushintaba sosai, tun awaje yakebin motocin da akayi fakin awaje da kallo, aransa ya ce, "k'ila wani gidanne a anguwar sukayi bak'i, yay hon maigadi yalek'o, ganin shine yasa yak'araso wajen mortar batareda yabud'e masa gate ba.

     A'a yabaka bud'emin gate ba kuma?.

    Aii oga wlhy babu wajen fakinne aciki.

    Kamar ya babu wajen parking?, mike faruwa acikin Gidan?.

     Mai gadi yad'an Sosa kai Dan Rahma ta ce, " karya fad'a masa, ya ce, "saidai kashigo kagani oga.

   Bobo yagirgiza kai kawai batareda ya tankaba yanemi waje awaje yay fakin suka fito shida Nawal, wayoyinsa kawai yad'auka amotar Yakama hannun Nawal suka nufi cikin gidan, bin ko ina yake da kallon mamaki yajinjina kai tareda nufar cikin gidan, suka shiga falon nanma shiru babu alamar akwai mutane awajen, baigama tunanin mike faruwaba yaji yara suna tafi dafad'in.

   *_“happy happy birthday to you, happy happy birthday to you...... Saikuma gasu Rahma suma sun fito”._* 

   Aibaisan sanda yasaki lallausan murmushiba, dama abinda Rahma tashirya kenan shiyasa tak'i binsu?, jiyayai tak'ara girma da daraja azuciyarta. lol



Na ce, " hummm gaba gabadan bobon Appa.


------------------------

     Daganan aka shirya Nawal cikin kaya masu k'yau, shima ogan kwalliya yakuma ci, aka fara gudanar da biking birthday d'in Nawal.

    Masha ALLAH komai ya k'ayatar abin burgewa.

   Wajen bada cake Nawal tacuro tasakama babanta tasakama Rahma, tabi sauran iyayen matansu ya hamza dukta basu, su khairiyyama haka, daganan aka fara cashiya.

   Biki dai bai tashiba sai gab da sallar magriba.

    Masu tafiya suka tattafi, akabar yaransu ya hamza kawai da matansu, bayan isha'i suma mazansu suka iso, saida sukaci sukasha akasha hirara zuminci sannan kowa ya kwashi family nasa sai gida.

    Bobo ya tsarama kansa wani Abu yau, amma saiyaji wai agidan su khursiyya zasu kwana, ba k'aramin haushi abin yabashiba amma saiya dake tunda bashida yanda zaiyi.


_bayan kwana hud'u_

         Duk burin da bobo yaci akan Rahma ya rushe Dan har sannan su kursiyya suna gidan, doledai yad'aga k'afa.

     Ranar Litinin da safe su khursiyya suka koma gida abinsu, shima bobo yafita aiki, Nawal kuma tana makaranta sai Rahma kawai agidan.

     Tayi aikinta tagama komai tsaf, 1:30pm tana zaune afalo tana kallo wayarta tayi wringing da sauri ta kalli wayar bak'uwar no. ce, shiru tayi Dan yau tunda tatashi gabanta ke fad'uwa, har wayar ta yanke bata d'agaba aka sake kira, ganin babu dacewa arashin d'aukar yasa ta d'auka tunda batasan ko wayeba.

      Sassanyar muryarsa tadaki kunnenta, ta sauke ajiyar zuciya wadda yajita har yatsan kafarsa, yad'an lumshe idanunsa yabud'e tareda jingina da kujerarsa, ahankali yake d'an lulita, ya ce, ''matsoraciya da kinzata waye to?.

     Murmushi tayi ta ce, "nifa ba tsoro najiba, baki yata6e tamkar yana gabanta ya ce, " dama zancemikine kid'aukko babynki a school yau aiki yamin yawa a office bazan samu damar d'akkotaba.

    Okey babu damuwa.

     So zaki iya deriving d'in ko?.

    Eh zan iya.

 Okey tom ALLAH ya tsare, saina sake kira.......

    d'if ya kashe kafin tayi magana, murmushi tayi kawai tamik'e tacanja kayanta.

   d'akinsa tashiga Dan key d'in motarta yana hannunsa, tagama dube dubenta bata ganiba, sai wani na jar motarsa a durowar gefen gadon, shita d'auka tafito.

      Tashiga motar daketa tashin k'amshi, tana mamakin turaren da Bobo yake amfani dashi haka, komai nashi Yakama k'amshin turarensa, mai gadi yabud'e mata gate tafice.

       Tafiya take ahankali saidai wani Abu mai kama da tsoro yana ta6a zuciyarta Dan tunda tafito daga gida take gani kamar wata bak'ar mota nabinta abaya, ajiyar zuciya tayi dataga motar kamar ta6ace, dahakadai tak'arasa makarantar su Nawal ta d'akkota.

         Labarin makaranta Nawal keta bata, amma itafa hankalinta yafara tashi Dan yanzuma k'ara ganin motar d'azu takeyi.

       Sunzo daidai danja ta rik'esu saikawai taga anbud'e motarsu anshigo, atsorace takalli bayanta saitaga wasu zaratan samari majiya k'arfi zaune tamkar motar gidansu, d'aya yanunata da bindiga, d'ayan kuma yatoshe bakin Nawal.

    ga Motar bak'in Gilas ce, nawaje baya ganin naciki...............





*_“😳masu karatu nikamdai atsorace nake, kosuwaye wad'annan mutane?, mikuma zasuyima Rahma da Nawal?.”_*

     Hummmm koya zata kaya?????????.








_kutayamu murna my sister d'ina ta haihu mace._





*_luv u oll my fan's_*

*_(((S))).....2017_*


👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{🅱🅾🅱🅾}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*



5⃣1⃣


          Babu dad'ewa aka basu hannu, tuni jikin Rahma yajik'e da gumi dukda AC dake aiki amotar, jikinta sairawa yakeyi, duk addu'ar datazo bakinta karantawa takeyi.

     Dakansu suke nuna mata hanyar dazatabi, sunyi nisa sosai datafiya awata hanyar k'auyen da Rahma batasan ko inaneba, wayartace tayi wringing harzata d'auka Wanda yake rik'e da bindiga yadaka mata tsawa, kina d'agawa zan tarwatsa kanki.

    Janye hannunta tayi da sauri akan wayar, Wanda yake rik'eda Nawal ne yad'auki wayar, saidai kafin yad'aga ta katse, wata uwar dariya yashek'e da ita Dan ganin sunan daya kira Rahman, *_dadyn Nawal_*.

       Wani gida suka kaisu, zuwa sannan Nawal tayi barci, Dan sun shak'a mata wani abune, Rahma tarungume Nawal tana kuka maiban tausayi, aranta tana tunanin misukayima wad'an nan mutane dazasu kawosu nan??.


Bobo kam hankalinsa yafara tashi Dan ganin yayima Rahma kira wajen 10+ amma bata d'agaba, dukda d'umbin aikin dake gabansa haka ya tureshi yabaro office d'in.

       Makarantar su Nawal yafara zuwa, auntyn su ta ce, "aii tund'azu bayan yakira kamar yanda ya ce, " momynta ce tazo ta d'auketa, to babu dad'ewa tazo ta d'auketa.....

    Bai tsaya yagama saurarentaba yayo waje, daga nan gidansa yanufa, tun a gate yatambayi mai gadi, amma ya ce, "basu dawoba.

    Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un kawai yake ammabata azuciyarsa, amma dukya birkice, da sauri yaciro wayarsa a aljihu yakira khursiyya, itama ta ce, " basu zoba, Abu kamar wasa dukya rewad'e dangi dakira amma kowa amsa d'aya yake bashi *_basu zoba_*.

     Cikin rawar jiki yakira Appa yaturo masa number Abbansu Rahma.

    Cikin girmamawa ya gaidashi, tareda masa bayanin shine, Abba ya ce, "ALLAH sarki Abdulmaleek ngd ALLAH yayimaka albarka, ya su Rahma d'in?. Tun anan jikin bobo yayi sanyi, murya asark'e ya ce, " dama ita zantanbaya ko sunzo nan gidan?.

     Kai A'a gsky Rahma batazoba, kunyi da'ita zatazone?.

     A'a Abba dama...... Nan yafad'a masa yanda akayi.

     Abba yaja numfashi, to mud'an k'ara hak'iri zuwa d'an anjima mugani kota biya wani wajen, dukda dai nasan wannan baya d'aya daga cikin halayen Rahma, tabbas da Safna cema bazan damuba Dan nasan tanada rawarkai, amma Rahma kam batada wannan halin.

     To abba. Kawai bobo yafad'a ya yanke wayar, kuma kiran Number Rahma yayi amma ank'i d'auka, yadafe Kansas tamkar zai FASA ihu, yana nan tsaye ak'ofar gate saiga ya ishaq da ya Hamza, suka tambayi yanda akayi yasanar dasu.

     Ya hamza ya ce, "kasanarda Ammar ne?.”

    Girgiza kai kawai bobo yayi danya kasa magana, ya Hamza yakira Ammar yayamasa bayanin kimai, salati ammar yashiga yi, bai tsaya 6ata lokaciba yabaza yaransa ki ina.


Al'amarifa kamar wasa hardare babu wani bayani, zuwa yanzun labari yakarad'e dangi, bobo kam dukya fita hayyacinsa, sai kuka yake tamkar mace, shidama haka yake akwai jarumta amma Abu kad'anne ke karya azuciyarsa.

      Duksun dawo daga sallar isha'i, suna zaune afalo gidan Appa zugum², harda Abban Rahma da Umminsu, momyn ya Kamal da dad d'insu Ameera ihsan ya Muneer ya shaheed duk suna gidan Appa, Safna CE kawai babu, dantana makaranta abin yafaru, bayan tadawo mai gadi yashaida mata komai, yad'ora da fad'in 'yangidanma duk suna gidan surukan Rahma d'in.

     Safna ta ta6e Baki ta ce, " kaga baba bud'emin gate nashiga nahuta tukunna, Dan bazan iya zaman jigum jigum ba wlhy tunda ba mutuwa akace sunyiba.

     Maganar tata tarazana baba mai gadi, bayan yabud'e mata gate yabi mortar da kallo yana jin kina kai, aransa ya ce, "lallai yau nakuma shaidawa yarinyarnan batada mutumci ko kad'an, inbanda rashin mutumci d'an uwanka uwa d'aya uba d'aya ya6ata kanuna rashin damuwarka, kai ALLAH dai ya k'yauta to.

     Safna dai bamatasan yanayiba Dan tuni tashige cikin gida abinta, sai wata fara'a takeyi wadda nadad'e ban ganiba daga gareta.


🤔araina Na ce, " safna Kodai kidai??.




    *_3days_*

Tsawon kwana uku kenan da 6atansu Rahma, Abu tamkar  wasa, zuwa yanzu kam aii kowa yajigata, Appa yabaza rok'on ALLAH amasallatai, hakama gidan redio Dana TV, social media ma haka, amma shiru kakeji wai malam yaci shirwa, kuma tun ranar ba'a sake samun number Rahma ba.

      ALLAH sarki bobo acikin kwana ukunnan Yayi wata uwar Rama, ko abinci bayasonci sai ammi ta tsareshi tamkar yaro tabashi abaki, shima lauma hud'u zuwa Biyar zaice yak'oshi, saitata lalashinsa sannan zaiyarda yak'ara kad'an.


Nikaina yabani tausayi k'warai da gsk😥.


      Yanzuma suna zaune afalo Ammi tana lalla6ashin sa akan yasha shayi amma sai yatsine baki yakeyi, ya mararairaice murya tamkar zaiyi kuka, ALLAH Ammi nak'oshi.

      A'a mukarram kadaure kasha koda kad'anne, kaga rabonka da abinci tun jiya da yammafa, komai na rayuwa hak'uri yakeso, Addu'a suke buk'ata daga garemu kaji, ALLAH ya ku6tar mana dasu idan suna Raye.

      Hawaye suka ziraro bisa kumatunsa, Ammi ta share masa..

    Yana shirin yin magana sukaji sallmar ammar, suka amsa, yashigo ya zauna.

    Ammi yarissina yagaida sannan yabama bobo hannu suka gaisa🤝, cikeda tausayi Ammar yake kallon bobo.

    Ka kwantar da hankalinka Abdulmaleek insha ALLAHU za'a gansu, yanzu inaso naji time d'in Daka kira Rahma kafin tatafi d'aukar Nawal?.

    Wayoyinsa yakwaso dukya yamik'ama Ammar Dan yanzun bayason yawanyin magana sosai.

    Bincike sosai Ammar yakeyi a wayoyin Bobo yanayi yana waya da office d'insu, bayan sun kammala yabama bobo wayoyinsa, ya ce, "kabar wayiyinka akunne daga yanzun Duk Wanda yakiraka zamu gani, zakuma mu iyabi ta wannan hanyar dangano ko waye.

   Jinjina kai kawai bobo yayi batareda yayi maganaba.

    Ammi ta ce, " Ammar karinga yima abokinka fad'a yaringa cin abinci jibifa yanda yaketa ramewa.

    Ammar ya ce, "kik'ara hak'uri Ammi insha ALLAHU zai ringaci yanzu yana cikin rud'anine.

    To ALLAH yasa Ammi tafad'a tana mik'ewa tabasu waje.

   Haka Ammar yatsare bobo yad'ansha shayin da soyayyen dankalin sannan yaymasa sallama yatafi.


      Tafiyar Amma babu dad'ewa saigasu ya Hamza sudukansu.

    Guri suka samu suka zauna suna k'ara kwantarma da bobo hankali, yana kwance saman doguwar kujera yana jinsu, badai ya iya cemusu komai amma sunsan yana saurarensu, wayar bobo tafara wringing yayi burus da ita tamkar baijiba harta tsinke aka sake kira, ya ishaq ya ce, "kad'auka mana, 6ata fuska yayi tamkar zaiyi kuka amma baice komaiba, ganin wayar tana niyyar tsinkewa ya sulaiman yay saurin d'auka ya ce, " hello.

     Muryar data daki kunnensa CE tasakashi mik'ewa zumbur yana fad'in Rahma Rahma....... Kuna ina ne?.....miya faru daku?........

     Aiikafin yafarga bobo ya warce wayar, muryarsa har rawa take ya ce, "Rahma Ku........

     Bai k'arasaba wata muryar takatseshi da fad'in ba ita bace ta cancanta tabaku amsar tambayoyinku  mine nan.

    Ku suwaye!!!?, Bobo yay maganar Afusace.

    Daga canma aka Daka masa tsawa, kai malam karka d'aga mana murya.

      Bobo ya ce, " kaga bawannan bane damuwata, miyasa kuka kamamin matana da d'iyata?, misuka muku?, waye yasakaku?, mukuke buk'ata?, idan kud'ine kufad'i konawane za'a Baku, pls karku cutar dasu.

     A'a a'a muba kud'i muke buk'ataba domin anrigaya an biyamu, kai kanka muke buk'ata, inkuwa bakazoba tom ran 'yarka da matarka zaizama fansar ranka amaimakonka.

     Bobo yarintse idonsa tareda cije le6ensa, saboda 6acin rai yagaza cewa komai.

   Daga can akace haba zaki kardai ace ka tsorata?, hhhhhhhh, bai kamata kaji tsoroba, munbaka daganan zuwa jibi idan bakazoba tom zaka tsinci gawar matarka da 'yarka, idan kuma kana buk'atarsu darai tom fine sai ka fanshi ransu.

    Saidai zuwan naka yanada sharad'i, wlhy koda wasa kada kayi gangancin zuwa da police zamu gane, na biyu saika taho zamu ringa fad'a maka hanya,, na uku idan ka 6ata mana lokaci zamu kacaccala matarka da 'yarka mu watsar, gashi kasakejin muryarta.

    Kafin bobo ya ce, "wani Abu saiyaji muryar Rahma cikin kuka tana fad'in dadyn Nawal karkazo pls, Dan ALLAH karka bada ranka akanmu, insha ALLAHU zanfanshi rayuwarku dagakai har Nawal, Nawal tana buk'atar mahaifi tunda tarasa uwa pls karka salwantar mata da ranka, Dan girman ALLAH karkazo, I luv you so much my Abdulmaleek.

      I luv you too my cute Rahma na, bobo yafad'a da saurin Baki,....kafin yakuma cewa wani Abu suka kwace wayar, cikin k'araji sukace kai wawa harka samu damar yimana soyayyane??.

   Wlhy kacika mana baki sai munmata fad'e hhhhhhhhhh dama gata daga gani zata bada feeling.

   Kaiiiiii!!!!!!!!!! Wawa, Bobo yadaka masa tsawa, wlhy kabari zuciyarka takuma kissima maka wani Abu akan matata saina tarwatsa kanka da bullet, na rantse maka da ALLAHn daya halicceni saina shayar dakai gidauniyar azaba, tabbas ni *_Zakine_* kujira zuwan zaki gareku, saina lak'umeku!!!!!!!!!, yanda yayi maganar cikin tsawa harsu ya ishaq da Ammi Appa su khursiyya duksun tsorata da yanayinsa, gabad'aya jikinsa yayi jajur abinka da fari, gashi jikinsa dukya mimmk'e, hakama jijiyoyinsa duksunyi rud'u², yay jifa da wayar, da sauri ya Hamza ya cafeta.

   Kowa yasan kuma ransa ya6aci kenan, k'arasawa yayi gaban Appa da Ammi yana yawaye ya ce, "iyayena kusamin Albarka zanje nataho dasu yanzun nan da kaina.

     Yanda yake magana dukya basu tsoro da tausayi, Ammi ta ce, " mukarram kayi hak'uri Ammar yazo kutafi tare, kai yagirgiza mata ya ce, "Ammi kedai sakamin Albarka kawai, basu musaba suka dafa kansa tareda saka masa Albarka da k'yak'yk'awar addu'a.

   Ya mik'e afusace zai fice, ya sulaiman yay saurin shan gabansa, wata irin hankad'awa bobo yayma ya sulaiman yay taga taga zai fad'i ALLAH yasoshi ya ishaq nakusa yarik'eshi yafad'o jikinsa.

    Bobo kam kota kansu baibiba yayo waje, yana fitowa ammar yashigo gidan, da sauri yatsayar da bobo, badan yasoba yatsaya yana kallon ammar dayaci wanka cikin shadda harda babbar Riga, wani d'an guntun tsaki bobo yayi danshi Ammar d'in yabashi haushin kwalliyar dayayi.

    Ammar baice masa komaiba yamik'o masa babbar Riga ta shadda.

   Galala bobo yatsaya kallon Ammar, wannanfa? yafad'a yana huro hanci.

    Kaga kasaka mutafi, Dan mungano Inda suke tasanadin wayar dakukayi yanzu, kasandai babu yanda za'ayi muje kai tsaye dole saimun canja kama gudun karsu San da zuwanmu su cutar dasu.

    Bobo yanajin haka yakar6i babbar rigar shaddar yasaka shima harda hula, duk abinda ke faruwa su Appa Ammi ya sulaiman ya ishaq ya Hamza khursiyya khairiyya duksun futo sunajinsu.

   Appa ya ce, " ALLAH yayi muku Albarka yayi taimako.

   Amin suka amsa.

Bobo da Ammar dawasu police uku suka shiga mota d'aya, su ya ishaq ma mota d'aya, saikuma mota biyu itama duk police ne aciki amma da kayangida Dan kowa shadda yaci tamkar zasu d'aurin aure, ganin haka shima Appa saiya shiga motar su ya Hamza, su khursiyya sukace zasuje suma, AMMAR ya ce, "suyi hak'uri su zauna suyi ta musu addu'a.

    Ammi ma kuka takeyi, hakadai suka fice.

      Amota Ammar yake sanarma bobo yatura mutane biyu amashin dansuyi gaba.

     Jinjina kai bobo yayi Dan har yanzun ransa a6ace yake Musamman idan yatuno da maganar wawan nan wai Rahmar sa zata bada feeling, wlhy saiya cirema d'an iskannan hak'ora....


Da sauri yashige cikin wata gona ya6oye bayan bishiya, boss gafa wasu motocinan har guda hud'u suna zuwa.

     Akwai motar 'yan sandane?.

   A'a gskiya wad'annanma duk wankan shadda sukayi.

    Mtsoooww kaiwane irin wawane, bana gayamaka akwai wani d'aurin aure daza'ayi acikin k'yauyen damuke ba, na tabbata wannan d'aurin auren sukazo, angayamaka su wawayene dazasu taho tun yanzu?, ko ka manta yanzu muka gama waya dashi?, nasan saisunyi shiri sosai kafin su ce zasuyi gigin zuwa, tabbas nasan zuwa gobe saisunzo nan Dan haka karka damu da wad'annan motocin.

     Okey boss nafahimta, yafad'a yana gyad'a kai tamkar k'adan gare.

    Yana yanke wayar yaji anshak'eshi tabaya, ido ya zazzaro waje Dan mamaki, shikuma wannan daga ina haka? Yaya maganar azuciyarsa.

    Wani wawan naushi musaddiq yabama guy d'in tareda k'ar6e wayar, a ina suke?, musaddiq yatambaya yana k'ara shak'eshi.

     Zan zan zan fad'amaka kaga sakeni Dan ALLAH karka kasheni.

    Wani wawan mari yasake bashi, fad'amin ahaka, cikin Rawar baki yasanarma musaddiq, shikuma yakira su Ammar yafad'a musu.

   Musaddiq yakuma fad'in kunawane aka baza Dan kawo rahoton zuwanmu?.

   Mu mu mu mu goma shabiyar ne.

   Murmushi musaddiq yayi, yad'auki waya yakira sauran 'yan uwansa yace su bazu akwai sauran mutum goma sha hud'u.


 _(ALLAH sarki musaddiq bayan Ammar yaturosu amashin su biyu, sunyi shiga k'auye kamar 'yan k'auyen gsk, shikuma yazagaye yakuma samun 'yansanda goma suka taho batareda sanin Ammarba, shine yanzu yakira su dansu bazu adajin)._

     Su bobo kam sunatabin hanyar kamar yanda waya take nuna musu, suna zuwa daidai  wani wajen mararraba wayar tatsaya wannan alamune na sun iso wajen.

   Mutum biyune suka fito suka k'arasa ga wani matashin saurayi dake tsaye yana kallonsu, da alama shima yana cikin mutum 15 da'aka baza Dan kawo rahoto, Dan kallo d'aya Ammar yay masa yagane bashida gsky.

    d'an saurayi Dan ALLAH tambaya Muke?.

    ALLAH yasa nasani yay maganar yanata zazzare idanu.

   Wani hanyar k'auye muke nema da ake d'aurin aure.

   Ajiyar zuciya saurayin yayi tareda wale baki, ya ce, "to to zan nuna muku, yana motsawa danufin nuna musu hanya d'ansanda d'aya yanuna masa bindiga, kana motasa zan tarwatsa kanka, ina kuke 6oye dasu?.

   Yawu saurayi ya had'iye ya ce, " zan nuna muku yanzun nan....

   K'asa yay da bindigar yanda baza'a ganeba yatasashi gaba, suma su bobo suka fiffito, amma sun rarrabu.


Su Rahma suna zaune tana rungume da Nawal suka farajin k'arar harbin bindiga, da sauri takali Wanda yake tsaronsu, duk taron 'yan iskannan shikad'aine mai bindiga ahannu, ganin yana barci Dan tund'azu yake lodama cikinsa wuywuy, mik'ar da Nawal tayi ahankali daga jikinta, cikin sand'a tak'arasa inda yake him akujera zaune, tamik'a hannu ahankali zata d'auki bindigar saiya motsa, tayi saurin ja baya tamak'ale ajikin bango, zamansa yagyara yakoma barci, takuma kai hannu zata d'auka Nawal ta ce, "mo...... Da sauri Rahma tayi mata alamar tayi shiru, lek'awa tayi ta window saita hango k'artai biyu suna zuwa aguje, takuma hangawa d'ayan gefen ta hango uku, innalillahi tashiga ambata dantasan yau saidai ALLAH kam.

   Hannun Nawal takama da sauri suka shige bayin d'akin taisaurin buga k'ofar tarufe dak'yar....

    Adaidai lokacin ogan yafarka yamik'e zumbur yanufi hanyar bayi, shigowar yaransa biyu da gudune yadakatar dashi.. Oga oga wlhy 'yan sandane......

    Basu k'arasaba sauran ukun suka k'araso suma, 'yansanda wajen hud'u suna take musu baya, harbi ogan yayi, yasamu d'ansanda d'aya ak'afa, suma suka fara harbi, nanfa aka fara musayar wuta, suma 'yan sandan suka samu nasarar Harbin mutum d'aya acikin 'yan iskan.

    Ana cikin haka  bobo yak'aso wajen, tuni duk sun cire Babar riga, bullet yak'arewa oga, 'yan sanda biyu kuma sun sami harbi, ga yaran oga sun k'aru Ashe sunada yawa, danbe aka fara tsakanin bobo dasu dansu Ammar sunacan nesa da wajen shikad'aine saikuma 'yan sanda biyu anharbi biyu.

    

Hummm masu karatu yaufa inashan kallo😳.


Dukan juna sukeyi sosai Dan suma gardawane majiya k'arfi babu abinda bobo zai nuna musu, gashi sunfisu yawa, sun daki juna duksun galabaita, kowa yaji ciwo sai sukaji k'arar harbi, gaba d'aya suka juyo Dan ganin Wanda yay harbi daga cikin d'akin, Rahma ce tsaye abakin k'ofa ta harbi Wanda yake k'ok'arin sokama bobo wuk'a ta baya, shikuma yana can hankalinsa nakan ogansu dasuke cin uban juna.

    Gaba d'aya sukayo kanta, ALLAH yabata sa'a takuma harbin wani ak'afa shima yazube, gani suka itama anyi kutubal da ita tadaki bango goshinta yafashe yafara jini.

   Adaidainan su Ammar suka k'araso da sauran gayyar 'yan sandan, dakuma 'yan dabar da aka kamo.

    Hankad'a Rahma musaddiq yayi da sauri Dan hango Wanda yabugata da bango yayo harbi.

   Fiyyyy bullet d'in yawuce tagefen hannunta, harya d'an ta6ata, tayi taga taga zata fad'i ya ishaq yay nasar rik'e hannunta.

            Gaba d'aya anyi nasarar kamasu, Nawal tafito dagudu daga inda Rahma tasakata ta 6oye, bobo yadurk'ushe k'asa tareda bud'e mata hannunsa tafad'a jikinsa, yarungumeta tsam yana hawaye.

    Papa yaushe kukazo?, wad'annan mutanen sunata dukan momyna, papa niko inata kuka ina kiranka, momyna ta ce, "su kasheta subarka da rai, kuma tana hana su dakeni..

    Kowa kallonsu yakeyi cike da tausayi, bobo yad'ago ido yana kallon Rahma dake tsaye agefe itama tana kallonsu tana hawaye, murmushi yayi mata tareda mik'ewa tsaye, yaware mata hannayensa alamar itama tazo.................










*_luv you oll my fan's_*

*_(((S)))....2017_*



👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{🅱🅾🅱🅾}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*


*_gaisuwar takuce 'yan TASKAR LITTATAFAN HAUSA, alkairin ALLAH yakaimuku har gidajenku, ina sonku sosai wlhy, ALLAH yabar mana zumunci da k'aunar juna._*

      _luv u wazga wazga❤💋😂._

    

5⃣2⃣

    

    Kafad'a ta d'an nok'e tana girgiza kai dantanajin  kunyar mutanen dake wajen.

   Tayi k'asa da kanta tana kallon k'asa, bata ankaraba taji an rungumeta, ahankali tasauke ajiyar zuciya, shima ajiyar zuciyar ya sauke, cikin kunnenta ya ce, "haba my cute bakiyi missing d'inaba ko?.

    Batace komaiba saidai yanajin alamar murmushin datakeyi.

      Ya sumbaci wuyanta, Ya hamzane dayaga bobo na Neman ruftawa gakuma Appa awajen sai ya k'araso inda suke, ya ce, " baban soyayya kuzo muje gida saikuyi ko?.

  Da sauri Rahma tazare jikinta, bobo yad'an kalleta sannan yadawo da kallonsa ga ya Hamza, Yaya karfa kazama..... Hummm kodayake baradai nayi shiru kawai.

    Dariya ya Hamza yayi ya ce, "a'a fad'i karta kasheka.

    Um um bazan fad'aba narufa maka asiri dai, my cute kona fad'a miki?.

     Girgiza kai Rahma tayi tana murmushi.

   Ya Hamza ya ce, " karki damu Rahma cemasa yafad'a mana, nima saina tona aii yanzunnan.

   'Yar dariya bobo yayi Yakama hannun Rahma suka tafi, ya Hamza yabiyosu abaya suka tafi.

    Yanzun ya Hamza da bobo da Rahma amota d'aya suka tafi, Nawal kam tana wajen Appa, tunda bobo yarungume Rahma Appa yakama hannun Nawal sukabar wajen yana murmushi.


Suna zuwa gida asibiti aka wuce dasu Rahma, Alhamdllh babu wata matsala saidai 'yan raunukan da Rahma taji, ya sulaiman ya dubata tareda basu magunguna sai gida.

     Tunkan su iso gidan yacika da dangi, su Rahma suna shigowa dangi suka rungumesu anata kuka, bayan gama murnar ganin juna Rahma tashige d'akinta tayi wanka tayima Nawal.

    Aka kawo musu abinci sukaci sukasha magani sai barci.


.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

          Haba ummi yazakice bandamu da 6atan su Rahma ba?, 'Yar uwatace fa, Dan ALLAH kibar fad'a kadama wani yaji zata gskyne.

    Oh da k'yarya nakeyi?.

   A'a ummi nidai bance kina k'aryabafa.

    Banza ummi tayi da ita, tajuya zata fita.

    Safna ta marairaice murya ummi toyanzu mikikeso nayi dazai sakaki farinciki?.

    Kafin ummi tabata amsa sukaji sallamar baseera.

   Tarisina ta gaida ummi, cikin fara'a ta amsa sannan tafice.

    Ummi na fita basira tamatso Kusada safna, k'awata mike faruwane wai naga ummi akanki?.

     Mtsoooww kibari kawai akan 6atan Rahma ne........ Takwashe komai tafad'a mata.

     Baseera tazunguri safna kefa banzace miyasa bazakice zakije kizauna da ita harta samu lfy ba, daganan basaiki gwada sa'arkiba kema.

    Kai hakanefa baseera, wlhy banyi wannan tunaninba ma, duk kaina yakulle baya kawo wuta.

     Aikin 6urrr inji tusa, kinga tashi maza ki shirya.

   Gudu gudu sauri Sauri safna tashirya kayan dazasukai fiye da sati d'aya, tad'auki duk abinda zata buk'ata ta shirya sanan sukanufi d'akin ummi.

    Tana zaune da Alana tana wayane da wata 'Yar uwar tata Dan tana bata labarin 6atan Rahma dakuma dawowarsu yau.

    Tsayawa sukayi harta gama, takalli safna da akwatin kekuma INA zaki da kaya haka?.

     Ummi zanje gidan Rahma na zauna danna ringa taimaka mata har jikinta ya daidaita, naga baikamata ace anbarta da dangin mijiba tamkar batada kowa.

    Baki ummi ta washe ta ce, "kai naji dad'i wlhy safna ALLAH yayimiki albarka, aihaka akeso, kuma tahakane zuminci ke k'ara dank'o.

    Ki gaisheta muma insha ALLAHU gobe zamuzo mu dubasu.

   ALLAH yakaimu ummi, saikunzo safna tafad'a tana murmushi.

    To saimunzo, baseera kigaida mutanen gidan.

  To ummi zasuji.


Safna da baseera suka fito sai gidansu Rahma, sanda suka iso mutane duksun tafi, daga Ammi da inna sai khairiyya da khursiyya suka rage, har k'asa su safna suka durk'usa suka gaida su Ammi.

    Safna ta ce, " Ammi inasu Rahman?.

     Murmushi Ammi tayi ta ce, "aii har yanzu barci sukeyi safna, yawajen su Maman taku?.

    Lfy lau suke Ammi, suma saigobe idan ALLAH yakaimu zasuzo.

    To ALLAH yakaimu lfy.

    Inazaku haka da akwati? Ammi tayi tambayar tana kallon safna.

     Safna tagyara zamanta tana k'ara marairaice fuska tamkar mutuniyar kirki, Ammi dama canayi bara nazo na zauna da ita harta samu k'arfin jikinta, Dan baikamata atakura su khairiyyaba ga bikinsu yana matsowa.

   Murmushi Ammi tayi ta ce, " lallai kinyi tunani Safna, ALLAH yay miki albarka.

      Bobo dake bakin k'ofar Rahma yana niyayyar fitowa yatsaya sauraren tattaunawar Ammi da safna.

       Ransa a 6ace yakalli Ammi suka had'a ido, yaturo baki gaba, murmushi Ammi tamasa tareda yimasa magana da idanu, wai karyace komai.

   Kauda kai yayi yana d'an sassauta turo bakinsa, shifa wlhy yatsani yarinyarnan, amma shine yanzu za'ace tazauna taredasu mtsoooww yaja siririn tsaki.

     Takowa yayi ahankali zuwa cikin falon, jin k'amshinsa da takunsa yasaka safna da baseera juyowa, kan ubancan kai, aii ba safnaba har baseera yau saida tashiga rud'ani.

    Dukda yad'an rame amma k'yawun haibarsa na nan, kuma yak'ara haske sajennan yakwanta luf luf, sai k'amshin turarensa ketashi afalon mai sanyin dad'i, har yazauna Kusada Ammi idon baseera da safna na Kansa, baseera ta ce, "a ranta lallai dolene safna ta haukace,” Ashe haka guy d'in ya had'u masha ALLAHU.

      Bobo yay d'an guntun tsaki Dan baya son kallo, ganin bazasu daina kallonsaba shikuma sun gundureshi, saiya katsesu dafad'in yakuke?.

      Dandanan suka dawo hayyacinsu danjin saukar muryarsa mai ratsa jiki da 6argo.

     Cikin in ina suka gaisheshi, ya amsa da lfy, tamkar yanda yasaba.

    Khursiyya da khairiyya suka fito saga kichin bobo ya kallesu, harkun mammala abincin?.

      Ya Abdulmaleek ai yau abinda kafiso muka dafa zakacidai ko?.

           Murmushi yamusu tareda gyad'a kai kawai.

    Suma dariyar sukayi suna mai farincikin ganin yayansu yau acikin farinciki, khairiyya ta CE, " Yaya tunda aunty Rahma tadawo yanzu saika Dage dacin abinci kayi k'iba.

    Harara bobo yasakar musu yana fad'in Ammi wlhy yarannan sun rainani.

     Ammi da inna suka tuntsure da dariya, inna ta ce, "Abdulmaleek aiko kura da 'ya 'yanta take wasa a daji, ammi ta ce, " wlhy kuwa inna.

    Ammi takalli su khairiyya ta ce, ''kutaso heebba mutafi gida hakannan ko?, tunda kungama aikin, fuska suka shagwa6e, khursiyya ta ce, "Ammi wai kina nufin harda mu?, harararsu ammi tayi hardaku mana, tunda ga safna nan tazo kukuma basaiku koma gidaba, dama ga hidima fall cikinku, dasafe saikuringa zuwa ko?.

     Su saima yanzu suka kuladasu safna dake zaune.

     Ammi takallesu tareda fad'in kuna 6ata mana lokacifa gakuma Deriver yana jiranmu.

    d'akin Rahma suka shiga sunata zum6ura baki, haryanzu su Rahma barci sukeyi abinsu.

   Hibba dake barci suka d'akko suka fito, suna son yarinyar sosai, yanzu haka komai NATA Yakoma d'akinsu, har anmaida mata suna Autar Ammi.

     Har mota safna da bobo suka raka ammi.


Bayan su Ammi sun tafi shima bobo ficewarsa yayi batareda yasake ko kallon indasu safna sukeba.

     Suma cikin gida suka koma suka Shiga d'akin Rahma wadda har yanzu suna barci.

    Suna nan zaune har aka kira magriba baseera tamik'e zata tafi, bayan Safna tarakata k'ofar gida tashiga adaidaita, baseera tana k'ara jaddada mata karfa tayi wasa da damarta, tayi k'ok'i kimai ta aiwatar yanda yadace.

     Safna ta ce, " karkiji komai insha ALLAH zanyi k'ok'ari.

    Okey sainajiki k'awar rai da rai.

   Dariya safna tayi ta ce, "hakane my sweet baseera, suka tafa mai adaidaita yaja suka wuce.


              Safna tana Shiga gidan ta Tatar Rahma ta tashi, tayi farinciki daganin 'Yar uwarta danhaka ta rungumeta, aunty safna yaushe kikazo?. Tun d'azun Nazo kina barci ya jikin?. Da sauk'i saidai jikina yana ciwo tayi maganar tana yatsine fuska, to sannu auta cewar safna, kai kawai Rahma tad'aga mata.

Ta ce, " aunty safna yasu ummi?.

    Suna nan k'alau suncema a gaisheki gobe zasuzo, tom ALLAH yakaimu lfy, Yakuma naji gidan shiru?.

    Kowa yatafi saini kad'ai, Nima zan zauna anan ne harki samu sauk'i.

   Lah da gsk?.

Eh mana safna tafad'a tana murmushi, Rahma tana juya baya safna ta galla mata harara.

    Itakam rahma dabatasan tanayiba ta rungumeta tanamai farincikin faruwar hakan.


Bayan anyi sallar magriba bobo yadawo gidan, kaitsaye d'akin Rahma yanufa, har yanzu suna zaune da safna suna hira, safna tana hirarne kawai amma jitake tamkar ta shak'e Rahma tamutu.

   Sallamarsace tasakasu d'agowa suduka tareda amsawa, suna had'a ido da Rahma yay mata murmushi, ya jikin? Yafad'a cikin sassanyar muryarsa, Rahma tai k'asa da kai sannan ta ce, "da sauk'i.

   To Alhamdllh, kinyi sallah ko?.

   Rahma ta girgiza kai alamar a'a.

   Miyasa?, kobak'yayine?.

    Girgiza kai Rahma tasake yi cikeda kunya, mik'ewa tayi tashiga bayin.

   Harta Shiga bobo yana binta da kallo, saida tashige sannan yajuya yafita.

    Safna tabishi da kallo zuciyarta na suya, jibi Dan ALLAH yama nuna tamkar baisan da ita ad'akinba, tayi k'wafa da fad'in zakazo hannuna ai.


Na CE, " hummm.



.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

      Yau kwanan su Rahma 2 da dawowa, dangi kam kullum sunata tururuwar zuwa dubasu damusu jaje, A6angaren bobo kuwa kulawa yake basu ta musamman, dai dai da abinci saiyace shine zai bata abaki, itakuma taita zame zame, wata shafta sai anzo shan magani, saida lallashi da mazurai takesha.

     Ran safna na 6aci, Dan aganinta wani abunma bobo yanayi da biyune, Dan haka take k'arajin tsanar Rahma aranta, kullum kuma zuciyarta tana k'ara nunkuwane wajen son Raba Rahma da bobo kota halin k'ak'ane.


++++++++++

     Yau tsawon kwanan safna hud'u agidan amma takasa aiwatar da burinta nasakama bobo magani, Dan ko abinci bayaci taredasu saidai a d'akinsa, kuma su khairiyya suna gamawa zasu d'auki nasa sukai d'akinsa, itakam har yanzu bata ta6a shiga d'akinsaba.

    Bobo kam bak'aramar tsana yayima safna ba, Dan sai yanzun yakejin Kalmar bata sonsa azuciyarsa, kuma dukkan take takenta yanzu yana lura dashi, takan bashi dariya wlhy Dan ganin yanda take nuna masa alamomin so.


    Yaukam bobo yana cikin damuwa Dan yana buk'atar kasancewa da matarsa, tunda yanada lfy, sai juye juye yake agado, jiyake d'akin yayi masa girma, ya kalli agogon dake manne abangon d'akin 1:5pm na dare, yad'anyi tsaki tareda mik'ewa.

   Wani story book yad'auka da filo yafito harabar gidan, wasu kujeru yanufa masu k'yau dake k'ark'ashin wata rumfar bunu, handky d'insa yasaka yashare kujerar da tebirin sannan ya zauna, yad'ora k'afafunsa bisa tebird'in.

    Duk abinda bobo keyi akan idon safna ne, murmushi tasaki sannan ciki sand'a tafito dankar Rahma taji motsinta.

   Kai tsaye wajensa tanufo..........






_kumin uziri Dan zandinga kawo muku guntayen page saboda nafad'a muku sister na ta haihu ina busy, maimakon ace banyiba gara ayi koda kad'an d'inne.._

     Ngd sosai da k'aunar dakuke nuna mini, nima ina k'aunarku wlhy, kuma kuna karamin k'arfin guywa da k'aimi akan littafin.

     I luv you so  much❤❤❤❤💋💋💋💋💋💝💝💝👌🏼












*_luv you oll_*

*_(((S)))........2017_*



👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{🅱🅾🅱🅾}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*



5⃣3⃣


          Jin motsin takun mutum yasakashi d'agowa, dararan idanunnan nasa masu haske yasauke akanta, wad'anda ayanzu sukad'an canja kala zuwa jaa.

     Da sauri takauda nata idon Dan bazata juri kallonsaba, lokuta da dama idanunsa suna saurin rikita mata lissafi.

     Lafiya dai?, bobo yay maganar fuska ad'aure.

   Yanayinsa yasaka jikinta yin sanyi, danya d'aure mata fiye da kullum, amma saita fuske, ta ce, "kayi hak'uri inaso muyi maganane Dan ALLAH.

     Idonsa yamaida ga littafin tareda jan d'an k'arami tsaki, da hannu yanuna mata wajen zama batareda yad'agoba.

      Safna tagyara kujera tareda d'aukar handky d'insa dake gefen k'afarsa ta goge kujerar sannan tazauna.

     Shikam cigaba yayi da karatunsa.

    Saida tayi masa kallon tsaf, sanye yake da kayan barci wandonsa iya guywa sai k'aramar riga mara hannu kayan duka jajayene sunyi bala'in haska farar fatarsa, aranta ta ce, " kai guy d'in nan yahad'u tako ina, komai nasa maik'yawune, kowacce irin sutura yasaka takan zauna daidai da tsarin hallittarsa, kallidai yanda kayan barci suka masa k'yau, shiyyasa idan yad'auki ainahin dressing yake rikita kwanyar mata........

      Jin tayi shiru saiya d'ago idanunsa yana kallonta, saiyaga tak'ura masa ido, k'ara d'aure fuska yayi fiye da d'azu, ina saurarenki, yayi maganar cikeda karsashi..

    Tuni safna tashiga hankalinta, ta tattaro nutsuwarta guri d'aya, tawani lankwashe murya tamkar wadda take agaban mijinta.

    _“ya Abdulmaleek Dan ALLAH da farkodai ina mai neman gafararka.”_

    Idonsa nakan buk ya ce, "dakikaimin mi?, ince sai anma mutum laifi ake bashi hak'uri?, nikuma bakiminba.

      Tunda yafara maganar tak'urama bakinsa idanu, Dan inbaka kasa kunnenkaba bazakaji abinda yake fad'aba, itama kanta Dan darene gari yayi tsit shiyyasa takejinsa, ahankali yake maganar kuma muryarsa cikin wani yanayi, mai lurane kawai zai fahimceshi ko kuma fahimtar halin dayake ciki.

     Ahankali tasauke ajiyar zuciya tareda gyara zama, takuma marairaice murya can k'asan mak'oshi ta ce, "namaka laifi my Boboo!,".

     yanda tafad'i sunan nasa tareda jansa cikin salo saida yad'ago Jan idonsa yakalleta, baidaice komaiba yamaida idanunsa yalumshe.

      Wani murmushi safna tasaki sannan tacigaba dafad'in nikuwa namaka laifi Dan ance na aureka amma nak'i, alokacin bansan kai baneba wlhy dabazan k'iba.

    Ya maleek tunranar Dana fara ganinka a school d'inmu nakamu da sonka mai tsanani.

     Da sauri yad'ago kai yana kallonta, saidai yakasa furta komai Dan mamakinta.

    Tacigaba, wlhy sonkane yahana nayima iyayena biyayya dakuma rashin sanin kaine mijin dasuka za6amin.

    Saidai randa ummi ta aikoni wajen Rahma nashiga matuk'ar rud'ani danadamar bijirema iyayena, lallai ranar zuciyata yayi tamkar zata fashe......

        Bobo yakatseta da fad'in no wonder shiyyasa kikamana pretending wai kina jin juwa koma mine?, yafad'a yana yatsine fuska tamkar yaga wani tutu.

    Safna tasakko tatsugunna agabansa tana hawaye, Dan ALLAH my boboo kataimakeni ka aureni?.

     Wata uwar harara bobo yajefeta dashi, cikin kaushin murya ya ce, "bakida hankaline?, kokin manta nid'in *_MIJIN K'ANWARKI NE!!?._*

     Itama cikin d'aga murya ta ce, " inacikin hankalina kuma INA kan sani, Maleek nasan bakason Rahma, itama batasonka, Niko ina Sonka.......

    Da Sauri yakatseta dafadin ubanwaye yagaya miki?.

      Tazaro manyan idanunta, ta ce, "zamankune yafad'amin, Dan wlhy ko rantsuwa nayi bazanyi kaffaraba baku ta6a had'a shimfid'a da Rahma ba, wannan yana cikin dalilin zamanka anan gurin, idan kuma nayi k'arya karantse mini da ALLAH kata6a had'a shinfid'a da ita, nikuma indai kayi zan hak'ura dakai nabar mata.

     Harara bobo yasakar mata, to ina ruwanki?.

    Tayi wani murmushin mugunta, daruwana maleek harda d'an tsaki, domin kuwa Sonka nakeyi, sokuma mai tsanani, Dan ALLAH kasaki Rahma kamaye gurbinta dani, wlhy namaka alk'awarin maka biyaya, zankuma cire maka duk wani kunci da damuwar dake tare da kai....

     Cikin tsawa bobo ya ce, " Dallah malama yimin shiru, yay murmushin nan nasa na munguta sannan yasauke k'afarsa k'asa, Yakuma gyara rungumar fillonsa yana kallonta, ya ce, "yarinya bakida abinda zaki iya mayemin gurbin my cute dashi, dantafiki komai wlhy, k'yawun sura ilimin addini iya zama da mutane hankali nutsuwa k'yak'yk'yawan tunani uwa uba hankali, yoni nayi canjinki da Rahma aina fad'o wlhy nakuma ci baya arayuwata, kisa azuciyarki dama can ALLAH yarubuta Rahma CE matata bakeba, ubangiji yagwada kine kawai danyaga k'arfin imaninki, amma saikika Nuna masa kinfisa wayo, to wallhy kisani kullum godema ALLAH nake dakikace bazaki aureniba, mahalliccina maisona da nasara yabani Rahma amadadinki, zuciyarki tadaina shirya miki k'aryar zan iya rabuwa da Rahma, wlhy yaudararki kawai takeyi, nida Rahma mutu karaba takalmin kaza.

   _Yay k'asa da murya tamkar mai rad'a, ya ce, "Rahma sai Abdulmaleek, Abdulmaleek kuma sai Rahma k'yak'yk'yawa mafi k'yawu acikin mata._

    Yafigi filonsa da littafi yay cikin gida yana 'Yar dariyar mugunta.


Durkushewa Safna tayi awajen tana kuka, wlhy baka isaba saika saketa ka aureni kokak'i kokaso, danni kad'ai ALLAH ya halicceka shiyyasama yakashe matarka tafarko yabarminkai, k'arya kake kace Rahma CE k'yak'yk'yawa acikin mata, ko makaho yashafa yasan nafita k'yau, kuma kaima kasani, boboo wlhy saika rabu da rahma, kuma muzuba nidaku d'an halak kafasa, daga yau zamu saka k'afar wando d'aya daku, saina addabi rayuwarku wlhy, duk cikin kuka take sambatunnan, saida tayi mai isarta sannan tamik'e, wlhy *_Abdulmaleek_* saina mallakeka koda ta hanyar kashe Rahma ne.


😳munga banu, safna!!.

   Tabd'ijan masu karatu akwaifa Marsala, safna kuwa tanada hankali?.

    


Muje zuwa danjin yazata kaya.



.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.

           Haka bobo yakwana tunanin maganganun Safna da yadda zai 6ullo musu, tabbas yayi kuskure dayake barin Rahma tana kwana d'akinta tun zuwan Safna, d'akinsa yadace tana kwana aii, haka yayta juye juye da tunani har asubahi baiyi wani barcin kirkiba.

   Itamadai Safna haka tafaru gareta, batayi barcinba kwana tayi tunani.

   Sai bayan sunyi sallar asubane barci yakwashesu suduka biyun dayake weekend ne.

    Rahma da Nawal ne kawai keta kaikawo agidan, suka gama had'a break fast suka gyara gidan tsaf.


*_10:6am_*

      Bobo yatashi, yagama komai na al'adar rayuwarsa sannan yafito falo cikin dogon wandon jins blue da farar t-shirt mai gajeren hannu, sai zabga uban k'amshi yakeyi.

      Rahma da Nawal suna zaune afalo tana ma Nawal kalba, da gudu Nawal taje ta rungumeshi tana fad'in my papa ina kwana.

   Lfy lau baby yafad'a yana rik'e hannunta sukazo suka zauna.

   Rahma ta gaisheshi ya amsa  amma fuskarsa babu walwala.

    Azuciyarta ta ce, "boss yaukuma muskilancin ne yamotsa?, afili kuma ta ce, "ga break.

    Yad'an kalleta, atausashe ya ce, ''kawomin tea kawai.

    Mik'ewa tayi tahad'o masa tea mai k'auri takawo masa, ya amsa yana binta da kallo, ahankali ya ce, "ngd, itama d'an kallonsa tayi takauda ido.

    Yana shan shayi yana kallon film d'in dasuke kallo wani India film yakula Rahma tanason film d'in India komiyasa?.

   

Safna tafito itama, Rahma ta kalleta aunty harkin tashi?.

     Saida tad'an ta6e baki sannan ta ce, " eh natashi.

   Takalli Bobo dayayi tamkar baima san da shigowartaba kuma yanajinsu.

   Ta ce, "ina kwana?.

    K'ara d'aure fuska yayi sannan ya ce, " lfy."

     Rahma bataji dad'in yanda ya amsama auntyn ta gaisuwaba amma yaza yayi.

   Takalli Safna dake zaune tana kallon bobo ta gefen ido, aunty gafa break.

   Uhum kawai safna tace mata.

    Haka akaita zaman kurame afalon, saidai Nawal daketa surutunta, shi bobo yanayine saboda Safna, itakuma Rahma tanajin haushin yanda yake share 'Yar uwarta, itakuma safna suduka haushi suke bata.

     Shima yalura da Rahman amma sai itama ya shareta.

   Bayan takammala abincin Rana tajere a dinning tak'ara gyara gidan tsaf, dama Safna bata tayata, saidai idansu khursiyya sunzo, to sukuma yanzu sunk'ara zama busy Dan bikinsu baifi saura 12days ba.

     Rahma tanufi d'aki zatayi wanka, Dan Nawal nawajen dadynta.

     Yaukam ALLAH yabama safna sa'ar zuba magungunanta acikin abincin bobo, bayan tagama takoma falo ta Fiske abinta.

      Mintuna kad'an Rahma tafito cikin doguwar rigar material ja, kayan yayi mata k'yau sai zabga k'amshi takeyi.

   Ta kalli safna dake zaune afalo, aunty bara nakirasu muci abinci ko?, tawuce batareda jiran amsar Safna ba.

     Baki safna ta ta6e tareda raka bayan Rahma da harara.


Yana kwance rigingine Nawal tana gefensa tana barci, idanunsa na kallon p,o,p d'in d'akin da alama yana duniyar tunanine.

    Rahma tashiga d'akin da sallama, shi baima jitaba sai k'arar rufe k'ofar yaji, yad'ago kai yana kallonta, tamasa k'yau kwarai da gsk, idanunta suna k'ara narkar dashi akanta......

    Takatse masa tunani dafad'in dadyn Nawal gafa  abinci yana jiranka.

     Bai tankaba amma yatsura mata ido tamkar zai cinyeta.

    Tasake maimaita masa sannan yay ajiyar zuciya, dama inason ganinki yafad'a yana yunk'urin tashi, saida yazauna sosai sannan yanuna mata bakin gadon alamar ta zauna.

    Tad'an zauna nesa dashi kamar mai tsoron wani Abu.

    *_RAHAMA!!._* 

taji sunanta har cikin kwakwalwarta, Dan ya iya fad'ar sunan.

   Yakuma fad'in _Rahama!._

     Itama akasalance ta ce, "na'am.

      Yagyara zamansa sosai yana fuskantarta, tsareta yayi da mayun idanun nan nasa ya ce, "inaso daga yau kidawo kwana d'akin nan.

     Cikin sauri tad'ago takalleshi, hanjin cikinta ma saida suka yamutsa danjin furucinsa.

    Fuskarsa babu alamar wasa Dan haka tamaida kanta k'asa, muryarta na rawa ta ce, "saboda mi zandawo kwana d'akin nan?.

      Ya ce, " saboda ni *mijinki* ne, umarni nake baki ba shawara ba, kuma daga yau nakeson ki fara.

    Bata iya cewa komaiba Dan yau yakoma mata ainahin *_Abdulmaleek_* data fara gani ranar aurensu.

    Shima baisake cewa komai yamik'e yashiga bathroom.

    Tana nan zaune tamkar gunki harya fito daga bayin yacanja kayansa zuwa shadda milk colour d'inkin boda yayi k'yau masha ALLAH.

   yad'auki Braun d'in takalmi yasaka agogoma haka, yafesa turarurrukansa tareda kwasar wayoyinsa da key d'in mota, saina dawo yay maganar yana k'ok'arin fita, itakuma tabisa da kallo tamkar sokuwa, ganin zai fice daga d'akin ta ce, "abincinfa?.

    Tsayawa yayi amma bai juyoba ya ce, nak'oshi yay gaba abinsa.

     Safna tana zaune afalo yafito, tamik'e da sauri tasha gabansa..............






Kuyi hak'uri dajina shiru, munyi sunan babyne, sunanta *_ummu habeeba_* (Iman).





*_luv you oll_*

*_(((S))).....2017_*


👩🏻‍💻typing........


❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣

      _•{🅱🅾🅱🅾}•_



*_NA_*

_*Bilyn Abdul*_


_sadaukarwa_

*_Abba Gana_*

*_Batul mamman_*

*_Billy giro_*


*_Happy independence day, God bless you and God bless Nigeria. 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 We love Nigeria._*

5⃣4⃣

   

       Wani kallon sama da k'asa yamata ya ce, "bani hanya.

     Ta ta6e bakinta tareda fad'in aidama zan baka, amma inaso na tunatar dakai maganar jiya.

    Ya watsa mata harara amma baice komaiba.

    Murmushin ko a jikina safna tayi, ta ce, "Nasan bakason Rahma, Dan dakana sonta bazaka fice batareda kaci abincin taba.

      Tsaki yayi cikin nuna razanarwa da kaushi ya ce, "dallah bani hanya kokuma wlhy yanzunnan namiki abinda har jikokin jikokinki saisun samu labari, banza jahila kawai.

     Ganin gaba d'aya kamaninsa Sun canja tamkar zai daketa yasa tabashi hanya tana murgud'a baki da yin k'unk'uni.

    Ficewa yayi yana Jan tsak'i, adaidai lokacin Rahma tafito, amma bataga abinda yafaruba.

      Itakam Safna bak'incikine yarufeta da fargaba, kardai ace mutumin nan yak'icin abincin nan, lalai daya cuceta.

     Rahma takatse mata tunani, auty Safna lfy kuwa?.

     Safna taja numfashi tana wani kicin kicin da fuska, lfy lau mikika gani?.

     Rahma ta ce, "a'a nagadai kamar bak'ya cikin nutsuwarkine?.

     Cikin masifa safna ta ce, " to k'alau nake, tatashi tabar wajen.

    Rahma tagirgiza kai, Dan indai dasabo tasaba da halin yayar tata.




%%%%%%%%%%%%

              Sai dare bobo yadawo gidan, Nawal taje dagudunta ta tarosa.

     Rahma da Safna suka masa sannu suma, ya amsa fuska ad'aure, d'akinsa yawuce itama Nawal tabisa.

    Itama Rahma tamik'e tad'auki ruwa tabi bayansu, Safna taja tsaki tareda mik'ewa tashige d'akin Rahma.

      Rahma ta shiga d'akin da sallama, saidai bayanan yashiga wanka, Nawal ce kawai take zaune tana wasa da wayarsa, ta ajiye ruwan ta ce, "Nawal zomuje ki kwanta.

    Nawal ta nok'e k'afad'a tareda kwa6e fuska, ta ce, " um um momy ni ad'akin papa zan kwanta,

    Rahma tayi tayi amma Nawal tak'i Dan haka ta k'yaleta takoma d'akinta.


Bata dawo d'akinsaba sai 10:34pm, yana zaune yana danne dannen laptop tashigo, Nawal kam tayi barci.

      Takai minti 3 da shigowa sannan yad'aga kai yakalleta sau d'aya yamaida kansa ga laptop, ki d'auki Nawal kikaita d'akin ki mana, yay maganar cikin nutsatstsiyar murya.

        Rahma ta shagwa6e murya ta ce, "Dan ALLAH kabarta anan mana.

     Yanda tayi maganar yasa dole yad'ago yana kallonta, tawani narke fuska, saiyaji wani Abu ya mintsini zuviyarsa, yad'an lumshe idanunsa harda yin wanid'an murmushin gefen kumatu, Wanda itakanta Rahma bataga yayibama, ya ce, "yaza'ayi ta kwana anan? aitayi girma da kwana tare da mu, in dama babu kowa a d'akin saikice anbarta ita kad'ai, amma tunda dakowa acan zata kwanta, yamaida kansa yacigaba da aikinsa abinsa.

        Haka tad'auketa badan tasoba tanufi d'akinta da ita, Safna tana zaune tana danna waya Rahma tashigo tacanjama Nawal kaya sannan tagyara mata kwanciya.

       Ta kalli safna, aunty Safna saida safe.

       Safna takalleta cikeda mamaki, cikin yatsine fuska ta ce, " ina zakije? Kike fad'in saida safe?.

     Cikin d'anjin nauyinta Rahma ta ce, "d'akin dadyn Nawal".

     d'akin dadyn Nawal kuma?, tofa sabon salo kenan wai gemu akafad'a, yaukuma?.

     Rahma dai batace komaiba tafice abinta.

    Har yanzu yana gaban laptop, tashigo tazauna akujerar d'akin.

     Yad'an kalleta bayan yakalli agogo, sannan yamaida kansa kan aikinsa.

     Bayan kamar minti biyu ya ce, bakijin barcine? Kobakiga agogoba?.

     Murmushi kawai tayi batareda tace komaiba, ya ce, " kije ki kwanta abinki wannan aikin Nawal k'areshi ba yanzuba.

      Dukda zuciyarta cike take da fargaba hakan bai hanata tashiba, gadon tahau amma dagacan gefe ta kwanta, tayi addu'oin ta, shiru tayi tamkar tana barci, amma duk motsin da bobo yayi sai gabanta ya fad'i, ganitake tamkar kanta yayo.

   Dukda Rahma ba yarinya bace mai yawan kwaramniya kuma batada yawan surutu dan haka bata cika shiga cikin k'awayeba, bare ayi firar aure da ita, k'awayenta basa wuce basma ihsan, to amma ana koya musu wasu abubuwan a islamiyya, kuma takan d'an ta6a karatun hausa Novels idan tagani awajen Basma ko ihsan, wad'an nan dalilan yasa tasan wasu abubuwa da yawa akan zaman takewar aure, saidai yanda taga bobo yayi burus da lamarinta yasakata sakin jikinta sosai da manta sirad'in daren farko, saikuma gashi zuwan safna nashirin jamata.....

    Hakadai taita tunane tunane har barcin gsky yay awon gaba da'ita.

   Shikam bobo dabaima san tanayiba hankalinsa nakan aikinsa dan zuwa gobe idan ALLAH yakaimu yanada wata shari'a.


    Ad'akin Rahma kam Safna takasa zaune takasa tsaye, wato saboda tayi magana jiya shine yau yagayyaci Rahma kwana d'akinsa? Yanaso yanuna mata maganarta ba gsky baceba kenan.

    Tacije le6enta tana hawaye, aiko ya kusanceta saiya saketa ya aureni narantse, Dan INA sonsa sanda banta6ama wani mahalukiba aduniyarnan, tafashe da kuka.

    Waya tad'auka takira Baseera, can aka d'auka ko gaisuwa bata tsaya sunyiba ta CE, "baseera inacikin matsala.

     Wace irin Marsala kuma k'awata?.

     Baseera duk shawarar dakika bani na aiwatar jiya, nasameshi namasa magana, shine ya CE, " yau Rahma taje d'akinsa ta kwana, yanzun haka zancen nan danake miki tanacan.

     Baseera ta sauke ajiyar zuciya safna ki kwantar da hankalinki babu abinda zai mata, nasan yayi hakane Dan kawai ya 6ata miki rai, Rahma d'in nawa take dahar zai kusanceta Indai yanada tausayi......

     Safna tayi saurin katseta, Baseera bazaki ganeba, sufa mazan yanzu babu ruwansu dawani k'ank'antar mace, kema kuma kinsani, balleshi d'an hutu yana ganin komai yana tafiya daidai arayuwarsa,, kinsan dolene yabuk'aci mace aii.


Post a Comment