Bayan sun koma mazauninsu akace su yanka cake.
Mik'ewa sukayi suka k'arasa inda aka ajiye cake d'in mai hawa uku, Wanda tasha ado mai k'yau, Rahma aka umarta tafara d'ora hannunta akan wuk'ar, sannan Bobo yad'ora nasa hannun akan na Rahma, bayan k'irga uku suka yanka, tafi akayi Raf raf raf.
Akace Rahma taciyar da Bobo, kunya dukta isheta amma yazatayine, haka taciro daidai bakinsa ta rissina tasaka masa abaki idonta ak'asa, aka kuma sakin tafi, tasaka masa kofin lemo abaki, kur6a biyu yayi tajanye tasaka hanky tagoge masa bakin, ihu aka saka ana bata tafi.
Itadai kanta nak'asa tayi d'an murmushi, bobo madai murmushi yakeyi.
Shima akace yabata.
K'aramin shima yaciro, yamatsa daf da ita sosai tamkar zai shige jikinta, batayi auneba taji yasak'alo hannunsa ak'ugunta, ajiyar zuciya ta sauke ahankali.
Cake d'in yasaka mata abaki, tafi mai k'arfi aka bashi, fuskarsa d'auke da murmushi yasaka mata cup d'in lemo, ku6arta d'aya ta kauda kai, yasaka hanky shima yad'an goge mata baki kad'an saboda janbakinta, sai kawai taji yabata Sumba akumatu (kiss) wani ihu aka saki gaba d'aya wajen ana tafi.
Rahma jitake kamar zata nitse awajen Dan kunya, gashi yak'i sakinta.
Dahakadai taro yatashi lfy, bayan hotuna da aka yi.
Amarya da ango suka shiga mota aka maidasu gida.
Luv u oll⛹🏻♀.
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
2⃣5⃣&2⃣6⃣
Kowa yagaji, ana shiga gidan gurin kwanciya kawai mutane suke nema.
Rahma kam harma tafara barci a mota, saida bobo yatada ita, aiko ko kallonsa batayiba tafice saboda kunya.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Wanka yafarayi sanan yay shirin barci, kad'an kad'an saiyayi tsak'i dad'an cije le6e, candai yakasa jurewa yakira khursiyya.
Duk suna d'akin Ammi inda Rahma take harda matamsu ya Sulaiman Dan suma yau anan zasu kwana.
Sunata shirin Barci aunty Rasheeda na tsokanar Rahma tanata murmushi da 6oye fuska.
Aunty ummy tamik'oma Khursiyya wayarta.
Kai aunty waye Dan ALLAH a darennan?, ke Bobo nefa.
Ya bobo kuma?, lfy bayanzu muka rabuba?.
Cikin tsokana aunty Sameera ta ce, "kika sani ko muryar matarsa yakesonji........ Dariya sukayi yayinda Khursiyya tad'aga wayar tasaka akunne hello yaya.
Muryarsa can k'asa ya ce, " kidafamin Lipton kimatsa lemon tsami biyu manya aciki, baijira amsartaba ya yanke wayar.
6ata rai Khursiyya tayi tamkar zatayi kuka ta ce, ''kai wlhy nidai nabani, daga dawo ga barci inaji amma zaiwani sakani aiki, ALLAH yasa abaka matarka gobe kuwuce muhuta da saka aikin tsiyarka.......
Lafiya kekuma aunty Rasheeda ta tambayi Khursiyya?.
ALLAH ya Abdulmalik d'innan ne, wai atsohon darennan zaisha Lipton Dan iyayi harda lemon tsami, nibansan tsiyar dayakeji ashan Lipton da lemon tsamiba.
Dariya su aunty Rasheeda suka kwashe da ita harda tafawa, aunty Sameera ta ce, "aii dolene yay control kansa da lemon tsamin irin wannan Sumba d'azu dayabama amarya awajen Dinner, o ni Abdulmalik anaso ana kaiwa kasuwa, suka k'ara shek'ewa da dariya.
Itadai Khursiyya fita tayi tana k'unk'uni da kumbura Baki, Dan batasan Inda zancen matan yayen Nasu yadoba.
Itama Rahma ba fahimtarsu tayiba, Dan haka ta tashi tashige bayi dan k'imtsa jikinta.
Akicin ta iske Ammi tana d'ibar abinci.
Ke kuma lfy baki kwantaba?, wakikema k'unk'uni ma haka?.
ALLAH Ammi ya Abdulmalik d'innan ne mana, wai adarennan zaisha Lipton hardasu lemon tsami, kawai salon saka aiki.
To idan kinyi hak'urima aii yaune kawai, gobe iyanzu yana gidansa.
Hakane ammi, ammafa kullum kamar ibadar ALLAH saiyasha shayinnan. Azuciyar Ammi saitake mamakin halin Abdulmalik, yana cikin damuwa amma bazaiyi aureba sai ammasa ta k'arfin tsiya, shidai halinsa daban acikin 'yayanta, ALLAH ma kad'ai yasan tun yaushe yake acikin wannan halin.
Afili kuma saita girgiza kai tana fad'in kidafa masa to dare nak'arayi.
Bayan fitar Ammi Khursiyya tadafa Lipton tanata mita, ta matsa masa lemon tsamin sanan tasaka a k'aramin tire tafice zuwa d'akinsa.
Akwance tasameshi rufda ciki, sanye yake cikin kayan barci.
Yaya gashi tafad'a tana ajiyewo.
Baice mata k'alaba bare ya d'ago.
tajiye tafito cike da haushi, babu yanda za'ayi yasaka ka aiki kaimasa yaymaka godiya bayan kagama, duk cikin yayinyunsu shine halinsa da ban, duk masifar ya ishaq yafi yaya bobo sauk'i.
Shikam kobayan fitarta yakai Monti Biyar sanan yatashi zaune yana matse fuska.
Dukda turirin da shayin yakeyi saboda zafi, haka yayta shansa yana cije le6e, yana gamawa wata zufa tafara karyo MASA adukkan sassan jikinsa.
Kwanciya yayi ahankali yana sauke numfashi, bayan wani lokaci yasamu nutsuwar sarayar ciwon nasa.
Kwanciyarsa yagyara barci yay a won gaba dashi.
*_washe gari_*.
K'arfe 10:30am aka fara gudanar da sisters day aharabar gidan, masha ALLAH komai tayi k'yau, yaudai basuga idon bobo ba, yana d'aki kwance barcinsa yaketa kwasa na gajiya.
Sisters day kam yabada ma'ana, amaryama yau tasha k'yau, su khairiyya sun raba k'yaututtuka taro yatashi lfy.
2:00pm aka gabatar da walima, mutane suka fara kama gabansu, wasuma bak'in sun wuce tun safe, wassu kuma sai gobe idan ALLAH yakaimu.
Rahma dum jikinta yayi sanyi tunda aunty ummy tashigo tace ta shiraya da angama sallar isha'i za'a mik'ata gidanta.
Kallo ihsan dake zaune Kusada ita tayi, ihasan wai ina wayatane?, kwana biyu wlhy bangantaba nazata tana wajenki.
A'a wlhy wayarki bata a wajena, amma bari akira muji.
Kiran wayar suka farayi....
Bobo nazaune ad'akinsa yana danna laptop yaji wayar Rahma dake caji tana wringing, kamar bazai dubaba saikuma yamik'e yad'auka.
Ana d'agawa ihsan tamik'ama Rahma wayar tana fad'in and'aga.
Cikin sanyinta ta ce, "Assalamu alaikum.
Lumshe idanunsa yayi danjin sassanyar muryarta.
Wa'alaikissalam ya amsa cikin nutsuwa.
Gabantane yafad'i danjin murayarsa, taganeshi sarai amma saita dake ta ce, " Dan ALLAH wanene?.
Jin haka shima saiya basar ya ce, "kema wacece?.
Mai wayarce, Dan ALLAH ya akayi tazo hannunka?.
Murmushi yayi tareda shafa gemunsa na gayu, ya ce, " mijinkine, nasamu wayar ahanunkine kuma.
Ajiyar zuciya ta sauke, muryarta nad'an rawa ta ce, "to shikenan.
Yanke wayar yayi kawai yana murmushi shima.
Ihsan dataji komai bata Neman k'arin bayani dantaji komai.
Screen d'in wayar yadasama ido, photon Rahma ne ajiki da Safna, sunyi masifar k'yau ahoton.
Tunda wayar tazo hannunsa baita6a tunanin dubataba, Dan tunda ya ajiye baibi takantaba, yau yaji tanata kukan k'arewar caji shine yasaka mata cajin.
Yad'an lumshe idon yabud'e akan wayar, kowacece wannan kuma?, yafad'a aransa.
K'ila yayartace, (wadda tace bata sona kenan?) Afili yay maganar, bakinsa yata6e yana k'arema safna kallo, tabbas tafi rahma k'yau, amma Rahma tafita kwarjini da fuskar kamala.
Bakinsa yak'ara ta6ewa yamaida wayar a caji.
Hawowa gadon yayi yacigaba da aikinsa.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Bayan Sallar isha'i Rahma tagama shiri cikin kyakykyawar Shiga ta material siket dariya, tayi k'yau sosai kuwa, sai tashin k'amshi turare takeyi.
Haka wasu k'alilan daga cikin danginsu, dakuma su aunty Rasheeda sukai mata rakkiya had'ad'd'en gidan Bobo dayasha gyara tamkar sabo.
Idonta na rufe tanata sharar kuka, da tunanin gamonta da ango yau, koyaya zai k'ar6eta kuma?, dukda yanuna mata kulawa awajen taron bikin hakan baya tabbatar mata dazata samu kulawarsa ayayin zamansu.
Dan zai iya yuwuwa yayima iyayensa biyayyane kamar yanda itama tayima nata biyya......
Da wannan tunani su aunty Rasheeda sukaimata sallama harda su ihsan suka tafi.
Kuka sosai tashiga rabzawa harda shashsheka, tana tausayama kanta da rayuwarta. Amma tana rok'on ALLAH tazama mai hak'uri da juriyar biyayya ga ALLAH da MANZONSA, dakuma iyayenta.
Zamewa tayi ta kwanta tana cigaba da kuka maiban tausayi da tsuma zuciya.
.*......*.......*........*.....*.
A6angaren Bobo kam yana d'akinsa harya kwanta hankalinsa kwance.
Ammi takalli agogon falon karfe 9:53pm amma har yanzu Bobo bai fito yatafi gidansaba.
Mik'ewatayi ta haura saman Dan gidan mutane sun ragu sosai.
Kallon mamaki tabisa dashi.
Shima yad'ago yana kallonta, Ammi na lfy kuwa?.
Lfy lau, mikakeyi har yanzu baka tafiba?.
Cikin mamaki ya ce, "Ammi ina kuma zani?.
Gidanka mana.
Gidana kuma?, Ammi canakefa sai gobe?.
Harararsa tayi, cikin d'an fad'a ta ce, " tunda d'azu su Rasheeda suka dawo daga rakkiyar matarka, amma kananan zaune, katashi katafi gidanka anbarta ita kad'ai, nasan tanacan atsorace.
Bata jira amsarsaba tafice afisace.
Ajiyar zuciya yasauke yana turo baki gaba kamar wani k'aramin yaro.
Haka yatashi ya canja kaya kamar zaiyi kuka Dan haushi.
Farar shadda yasaka sai maik'o takeyi, yad'ora jar hula da silifas ja mai k'yau, turare yafeshe jikinsa dashi, sannan yajawo jakar lop-top d'insa yasaka duk abinda zai iya buk'ata na 6angaren aikinsa, yakashe kayan wutar d'akin yafito sai zabga k'amshi yakeyi.
Ammi yatarar afalonsa tana jiransa, ganin ranta ad'an 6ace yasa yasaki fuska, cikin murmushi da zolaya ya ce, "Ammi na nayi k'yau.
Itama fuska tasaki tana kallonsa, ta ce, " masha ALLAHU Mukarram d'ina kayi k'yau sosai, ALLAH yaymaka albarka kaji, yabada zuri'a tagari, ya albarkaci wannan aure.
Biyayyar dakake mana ALLAH yasa kaima 'ya'yanka suyi maka.
Ammin Ammi na ngd sosai da addu'arki gareni, bari naje wajen appa namasa sallama ina baby mutafi?.
A'a ita ba yauba, sai bayan sati d'aya tukkuna.
Ammi saboda mi?, cikin shagwa6a yay maganar.
Dariya ammi tayi ta ce, "shagwa6a66ena sai angama amarci tukkuna, idan d'iyata tagama hutawa da gajiyar biki saikazo kad'auki Nawal d'in.
Shike nan ammi, amma.......
Katsesa tayi da fad'in kaga jekayima Appanku sallama dare nak'ayi.
Haka yahak'ura yanufi d'akin Appa, bayan sun gaisa yaymasa nasiha sosai da saka masa albarka sannan yafito yatafi.
Mota yashiga yabar gidan cike dakewar iyayen NASA.
Awajen wani gasa naman kaza ya tsaya, yasayi guda biyar sai k'amshi sukeyi, yasayi kayan fruit dayawa yanufi gidansa zuciya acinkushe da tunani kala kala...........
*_" Alhmdllh. inaga 'yan uwa yakamata mudakata anan sai bayan sallah, gobe idan ALLAH yakaimu kowa zai nemi k'unshi da k'itso babu time d'in karatu, jibima haka ga aiki tunda daren sallah ne, Dan haka muyi hak'uri zuwa bayan sallah idan ALLAH yakaimu lfy."_*
_ina muku barka da sallah, inakuma baku hak'uri da godiyar had'inkai da kuka bani, ngd sosai, inaga ni anan zan barku Dan bayan sallah zan koma gida, gashi wayata ta lalace bana charting yanzu, dasai nacigaba damuku, dama da wayar aunty Billy nake typing d'in, amma ina rok'on ALLAH yasa tacigaba damuku, dukda naga tanada aiyuka agabanta._
_Na rok'ar muku ita sosai akan taringa muku typing d'in ko babu yawa sosai, Dan wlhy buk d'in yahad'u sosai masu karatu, shiyyasa Nima narikice nahau yimuku copy, lagwadar labarin nagaba, Dan akwai cakwakiya sosai acikin Novel d'in, kardai nacikaku da magana ALLAH yasa tayi muku._
_Wanda na 6atamawa Dan ALLAH ya gafarceni nabarku lfy._
*_taku Marak'isiyya ibraheem musa._*
Luv u oll.
By ✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻masoya, ALLAH yahad'amu da alkairinsa.
Ngd.
Aunty bilyna gareki, Dan ALLAH kicigaba da gashi🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻plzzz.
👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
🤝 *_Assalamu alaikum, ina mik'o muku sak'on barka da babbar sallah, ALLAH ya maimaita mana, muga ta bad'in bad'in bad'ad'a, saidai akwai matsala babu Wanda ya aikomin da kai da k'afafu, bare suya.☹😋😂_*
2⃣7⃣=2⃣8⃣
Hon yayi mai gadi yabud'e masa gate, saida yatsaya suka gaisa sannan yay cikin gidan, guri yasamu yay fakin zuciyarsa cike da tunani kala2.
Yafito tareda kwasan kayansa yanufi ciki, tafiya yake tamkar bayaso, zuciyarsa cike da waswasi, yaushe rabonsa da gidan nan a rin wannan lokacin?...... K'ofar falon yabud'e yashiga, wani k'amshin dad'i yadaki hancinsa, yashak'a ya lumshe idannunsa sannan yabud'e, bin ko INA na falon yakeyi da kallo, komai masha ALLAH, Iyayen amaryar tasa sunyi k'ok'ari gsky, komai na falon farine da ratsin golden.
Hasken fitilun yak'ara yalwata k'yawun falon sosai, ajiye ledojin yayi yad'au jakar lap-top d'insa kawai yanufi d'akinsa.
Yazube kayan tareda fad'awa saman gado yana fad'in wash ALLAH na.
Yay lamo yana tunani Wanda bansan namiyeba, yakai minti goma ahaka sannan yatashi, harya fara cire ma6allin wuyan rigarsa saikuma yatsaya yana tunani, koba komai yakamata ya lek'a d'iyar mutane, k'ilama bataci komaiba, mik'ewa yayi yafito falon, kicin yafara shiga yad'auki filet da Kofi yadawo falo yasaka kaza d'aya afilet d'in, hakama kayan fruits d'in yazuba awani filet d'in daban, yad'orasu saman babban tire harda ruwa da fresh milk sannan yanufi d'akin.
Tiren ya ajiye ak'asa saman kafet d'in dake gefen lafiyayyayen gadon nata, yabita da kallo tana kwance ta takure waje d'aya kamar tanajin sanyi, yad'anyi tsaki yana kauda kansa daga kallonta, "k! Yafad'a ad'an kausashe.
Komotsi batayiba Dan bama tasan yanayiba, fuska yak'ara had'ewa yana kuma fad'in " k!! Wai bak'ya jinane?, ganin bata motsaba har yanzu yasashi matsawa Kusada ita daf, ashema barci takeyi yak'arshe maganar da tsak'i. Hannunsa yasa ya bubbuga filon data saka kanta, firgigit ta tashi tana kad'a manyan danunnan NATA masu suffar kwai.
Kauda idonsa yay daga kallonta Dan idanunta suna masifar tafiya dashi babu k'arya, ga abincinan kitsashi kici yay maganar yana k'ok'arin ficewa daga d'akin.
Ngd, amma nak'oshi, nitsatstsiyar muryarta ta daki kunnuwansa, bai juyoba amma yatsaya, hannayensa cikin aljihu wandonsa ya ce, "wannan yarage kuma naki, yay waje abinsa.
(Ni bilyn Abdul nace sabon salo, bobo Yakuma zaka canja mana?, bamuyi zaton hakabafa☹).
Itakam Rahma hawaye tamatso takuma komawa takwanta, saida tayi kuka mai isarta sannan ta tashi zaune, afili ta ce, " dama nasan bazan samu farincikiba, duk wata kulawa Daka nunamin awajen taron bikin naganin idon danginane danaka, ya ALLAH ka kawoma rayuwata d'auki, kodan darajar biyayya danaima iyayena, nashare musu hawayensu alokacin dasuke zuba, Nima ALLAH kaji k'aina ka daidaita zamana da mijina yafuskanceni tamkar kowacce mace, takuma rushewa da kuka.
(Ayya Rahma tabani tausayi gsky).
Sauka tayi daga gadon tad'auki tiren tafito, kicin tanufa Dan saida su aunty Sameera suka Nuna mata ko INA na gidan kafin su tafi, firij tabud'e ta saka komai Inda taga yasaka sauran, tad'auki fresh milk d'in da kofin tafito.
ko tsayawa kallon falon batayiba takoma d'aki, saida ta kulle k'ofarta sannan tacire kaya tayi canji Dana barci.
Zama tayi bakin gadon tasha fresh milk d'in sosai sannan tashiga bayi tai burosh tadawo tai kwanciyarta bakinta d'auke da addu'ar barci.
Shima yana komawa d'aki kayan jikinsa yarage yasaka na barci yahau gadon yazauna, jakar dayazo da ita yabud'e ya fiddo lap-top d'insa yafara aiki.
Ganin ba kwanciya zaiba nayo waje nikam Dan barci nakeji sosai.
_washe gari._
Da asuba kafin yawuce madallaci saida ya kwankwasa mata k'ofa, saida yaji alamar ta tashi sannan yafice.
Jin yafita takoma tayi kwanciyarta Dan har yanzu tana Hutu.
Saida gari yay haske sannan bobo yadawo gida, barci Yakoma abinsa Dan yana buk'atar Hutu sosai.
*_7:48am_*
Rahma ta tashi, wanka tafarayi sannan tagyara gidan tsaf dukda ko ina fes yake amma tak'ak'k'ara gyarawa, tabud'e ko ina da k'amshi, tana k'ok'arin komawa d'aki taji ana kwankwasa k'ofa, saida tad'anyi shiru nawani lokaci sannan. Tanufi k'ofar tabud'e, ganin khairiyya da khursiyya yasata sakin murmushi, hanya tabasu suka shigo sannan tamaida k'ofar tarufe.
Itama zama tayi suka gaisa (Dan zasu iya zama sa'anni itada tagwayen Ammin), ta ce, "yasu Ammi?.
Lfy lau tanama gaisheki, ga break fast tace akawo muku.
ALLAH sarki Ammi mungo sosai.
Khursiyya ta ce, " Yaya fa?.
Saida tayi k'asa da kai sannan ta ce, "yana barci bai tashiba.
Khairiyya da khursiyya suka kalli juna suna dariya, saikuma suka mik'e tomu bari muwuce sai anjima.
Kai haba dawuri haka?, ALLAH nazata anan zaku wuni.
Rufana asiri wannan mijin naki bayason warigi, khairiyya tafad'a ahankali.
Saida tarakasu har bakin k'ofar sannan tajuyo ciki, kwandon abincin ta d'auka takai dinning, ta ajiye komai inda yadace, taje kicin tad'akko duk abinda za'a buk'ata ta ajiye, abincinta tad'iba takoma bedroom taci.
Bobo kam ana gado ana kwasar barci, sai 10+ yatashi yay wanka yashirya cikin k'ananun kaya yayi k'yau sosai masha ALLAH, yaci sunan nasa Bobo.
Yaji dad'in ganin falon fes dagani kasan yak'ara shan gyara, baibi takan Rahma ba yanufi firij d'in dani danufi d'aukar fresh milk yasha saiyaga abinci, ganin kamar kulolin gidan Ammi yasa yazauna yaci abincinsa yay nak sannan yafice.
(Araina nace yadace ace yalek'a yaga yata kwana aii).
Rahma tanajin fitarsa, danhaka tarabga tagumi tana tunanin sabuwar rayuwarta ta yanzu.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Asibiti yanufa Dan duba yarinyarnan da akaima fad'e, jikinta yayi kyau sosai Alhmdllh, saidai har yanzu bata magana, tsakaninta da Bobo saidai kallo, tana bashi tausayi sosai Dan yanajinta tamkar Nawal, yasan idan Nawal ce ko cikin 'yayan yayensa ko k'annensa mata biyu wata tashiga irin wannan halin yasan zasushiga cikin tashin hankali fiyema da haka, ALLAH kad'ai yasan itama halin da iyayenta suke aciki yanzu.........jiyowa yayi dasauri danjin an ta6asa, ya Sulaiman ne.
Kaikuwa miya fiddoka da sassafennan?.
Haba Yaya yanzune safiyar?.
Harararsa ya sulaiman yayi, ya ce, "amatsayinka na sabon ango wanda aka kaimar sabuwar amarya jiya baikamatama duk yau aganka awajeba, kai daganan harma sati d'aya.
Hummm Yaya kenan, amma yanada k'yau nazo naga jikin yarinyarnan, kagafa tunda aka fara bikinnan bana samun damar zuwa.
To aii yanzu kaganta saika koma.
Yay...... Hannu ya sulaiman yad'aga masa alamar baya buk'atar jin komai.
Bayanda zaiyi haka yaymasa sallama yatafi.
Indai tak'aicemuku bayani yau tsawon kwanan amarya takwas bata saka angonta a idoba, sadai taji motsin shigowarsa da fitarsa, ko motsin cin abinci, kulum tana d'aki, inkaga tafito wani Abu zata d'auaka shima saita daidaici baya falon.
Aganinta shine yakamata yajata ajiki ya sake mata, tunda shine mai gidan, ita yanzu tamkar bak'uwa take agidan.
Shikam yana ganin ita yakamata taringa masa abinda zai sake mata d'in Dan da wannan halin Ni'ima tai saurin cafe zuciyarsa har yake ganin tafi sauran mata............
To masu karatu kuyi hak'uri da wannan yau naje anguwane, Marak'isiyya ta mannamin aiki tagudu.
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S)))......2017._*
👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
*_wannan page d'in nakine miss xoxona, inafata kinyi sallah lfy?, ALLAH ya maimaita mana._*
_Luv u wujiga wujiga_😂❣.
2⃣9⃣=3⃣0⃣
Kwance take akan had'ad'd'en gadonta Wanda yaji shimfid'u na alfarma, tajuya kwanciyarta zuwa rigingine, idanunta suka sauna kan agogon dake manne a bangon d'akin 3:42am.
Ta waro manyan idanunta Dan mamakin yanda lokaci yatafi, afili tafurta kai kenen na kwana banyi barciba?.
Taja dogon tsaki da k'arfi, dama da gsk ne idan mutum ya ce, "yakwana baiyi barciba?, gsky itakam tana k'aunar iyayenta, tanaso kuma tayimusu biyayya, saidai tunkan ayi nisa tafara hangen tarin matsaloli a rayuwar auren nata. Domin kuwa alissafinta yau kwana takwas da kawota gidannan, saidai tundaga randa aka kawota gidan bata sake saka angon nataba a idonta, saidai taji motsin shigiwarsa dakuma fitarsa, kocin abincinsa, idan tatuna kulawar dayayta bata awajen taron bikin saitaita mamaki wlhy, mutum tamkar mai aljanu, kodayake saitaga kamar itama akwai laifinta, tunda ad'aki take wuni, saidai idan taji yunwa tadameta tafita tad'ebo abincin da Ammi ta aiko musu, gidan kansa takasa nutsuwa taimasa kallon tsaf........
Kwala kiran sallar asubane yadawo da ita hayyacinta, tamik'e domin gabatar da sallar, jitayi jikinta duk yayi nauyi saida tayi wanka sannan ta d'auro alwala.
Tana idar da sallah taji wani irin barci na d'ibarta, tashitai ta haye gado ta kwanta, cikin 'yan mintuna barci yay gaba da ita.
A6angaren bobo kam yamaida dukkan hankalinsa wajen binciko Wanda yayma yarinyarnan fad'e, sukansu 'yansandan dukya addabesu da masifar basusan aikinsuba, sanin shi d'an babban mutumne yasasu dagewa sosai kuma ana hangen nasara zuwa yanzu.
Rahma kam yana buk'atar ganinta amma aganinsa ita yakamata tafara nemansa tunda shine babban, ganin kamar tana shamasa k'amshi shiyyasa yafita harkarta ya maida hankalinsa akan aiki.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Sai k'arfe d'aya Rahma ta tashi, takai dubanta kan agogo, kai harnakai haka ina barci?, lallai nasha barci sosai.
Wanka tashiga, bayan tafito tashirya cikin Riga da siket na atanfa kayan sun bala'in mata k'yau, tayi sallar azhur sannan tanufo kicin Dan cikinta yafara kiran ciroma, gashi jiya tacema Ammi adaina kawo musu abinci zata cigaba da girkawa, Dan aganinta yakamata tamik'e wajen juya akalar mijinta zuwa gareta.
Alokacin Bobo yana gidansu, Nawal tamak'ale masa saita biyoshi yakawota wajen momynta.
Ammi ta ce, "Mukarram inaga katafi da ita kawai nasan insha ALLAHU Rahma zata rik'eta da Amana, kasan yarinyarnan kullum burinta ta kasance da mamanta akullum.
Bobo yahad'iye yawu Ammi ba tafiya da Nawal bane matsalar ina ganin kamar idan nad'auketa ban k'yauta mukuba.
Ammi tayi murmushi Wlhy ko d'aya mukarram aii munsan ba k'waceta kayiba, dama tunjiya Appanku yay maganar yau idan kazo kawuce da ita.
To shikenan Ammi ngd, ahad'a mata kayanta to muwuce.
Ammi tahad'o mata kayanta, wasu kam sai ahankali aringa kaimata.
Nawal kam sai murna take yau zata wajen momynta.
Ammi bari mutafi naga Appa haryau bai dawoba, gobe idan ALLAH yakaimu ma had'u, Dan zan koma aiki.
Ammi ta ce, tom ALLAH yatsare, yakaimu lfy, tazo gefen Nawal tana d'aga mata hannu.
Bobo yatada mota, yauwa Ammi idansu khairy sun dawo suhad'amin kayana duka Nima.
To zan Sanar musu agaidamin da d'iyar tawa.
" zataji."
Haka suka fice ammi da Nawal suna d'agama juna hannu.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Rahma na zaune a falo tazurama filet d'in indome idanu, dukda 'Yar Karen yunwar datakeji amma abincin yagagara ciyuwa agurinta.
Tabi falon da kallo, caraf idanunta suka sauka akan wani hoton Bobo yana zaune akan wata kujera, fuskarsa d'auke da tsadadden murmushi mai kashe zuciya, saina kusadashi shida Nawal, wanikuma a can gefe shida yayyensa maza dasu Ammi da khursiyya da khairiyya, sunyi k'yau sosai, daka gansu Kasan ciki d'aya suka fito masha ALLAH....
DA gudu Nawal tashigo tana kiran Momy! momy!!, da Sauri Rahma tamik'e Nawal tafad'a jikinta, itama saita rungumeta.
Ahankali Nawal ta ce, momy I miss u.
Miss u too my baby Rahma tafad'a tana mamakin 'Yar waye kuma wannan?.
Nawal takatse mata tunani da fad'in , momy inakikaje kika barni?, kullum saina tambayi baby da Ammi sai sucemin kina zuwa amma baki zoba.
Cikin mamaki Rahma tad'agota daga jikinta tana kallonta, gata 'Yar mitsila sai zance irin na manya.
Bobo na a tsaye yana kallonsu, Wanda azahiri kallonsa akan Rahmane, Ashe k'yan dayake kallonta dashi awajen taron biki tafi k'yau a Natural batareda kwalliyaba..... Maganar Rahmace takatse masa tunani, ta kuma rungume Nawal tana fad'in tom gani nadawo babyna kiyi hak'uri kinji.
Ita sai yanzu tatuna ance mata Bobo yanada d'iyama, jitayi tausayin yarinyar ya mamayeta, ALLAH sarki Rayuwa, ALLAH baya Barin wani Dan wani yaji dad'i, tafad'a acikin ranta.
Nawal tazare jikinta tanufi Inda Bobo yake, hannunsa takamo cike da murna tana fad'in baby naga momyna yau.
d'an murmushi yayi ya ce, "natayaki murna babyna, karasowa cikin falon sukai yazauna.
Rahma ta daure ta ce, ina yini?.
Lfy ya amsa batareda ya kalletaba.
Rahma ta ta6e baki aranta ta CE, " dama baka amsaba aii, dama na gaidakaine saboda kana gaba dani.
Maganar Nawal ce tasakata dawo da hankalinta Kansu, Nawal ce takai bakinta Kusada kunnen Bobo wai zata masa Rad'a, amma kuma kanajin maganar tata.
"Baby mikayima momy tak'icin abinci?, koka duketane?.
Da sauri Bobo ya kalli Nawal a'a baby ban daketaba, k'ila batada lfyane.
Tamaido dubanta kan Rahma, momy waibakida lfy inji baby.
Rahma tayi d'an murmushi A'a lfy ta k'alau, to momy idan lafiyarki k'alau miyasa bakici abinciba?, ko kinaso baby yabaki dakansane?......
Kafin Rahma tayi magana Nawal tamaida dubanta ga Bobo, baby kabama momyna abinci abaki kamar yanda kake bani idan nak'ici.
Bobo ya ce, "to baby idan banda abinki....... Da Sauri ta ce, "baby indai baka bama momyna abinci abakiba mun 6ata daga yau, ta tashi daga kusadashi takoma kan cinyar Rahma data daskare azaune danjin furicin Nawal.
Rahma tadaure ta ce, ''kinga babyna zanci dakaina, Dan lfy ta k'alau, kibar Dady yahuta kinga ya gaji ko, tashima muci tare.
Nawal ta tashi zaune, Rahma taringa bata abincin itama tana dannawa badan yaymata dad'iba, saboda damuwar dataima zuciyarta yawa.
Bobo yanad'an satar kallonsu, tabbas yaji dad'in yanda Rahma takar6i d'iyar tasa wadda akullum yake zullumin sama mata madadin mamanta data rasa......
Yanata tunaninsa harsuka mammala, Nawal ma tafara barci, mik'ewa Rahma tayi da ita zuwa d'aki, dama zaman dukya gundireta.
Yabita da kallo k'asa k'asa babu laifi tanada k'yau daga na fuska harna jiki, saidai bazai sotaba Dan Ni'imarsace kawai keda gurbin zama azuciyarsa.
"na ce, "hummmm ALLAH yasa."
Itakam Rahma koda takwantar da Nawal saitayi zamanta bata sake fitiwaba, sai bayan sallar la'asar.
Sannan baya falon, tanufi kicin tana fad'in baridai yau nayi girki kodan Nawal, had'ad'd'en abinci na gargajiya tahad'a mairai da lfy, tagyara kicind'in tsaf kamar ba'ayi komaiba, hakama falon takuma bad'e ko ina da nau'in turarurrukan wuta.
Saida tayi Sallar magriba sannan tayi wanka tayima Nawal, shiri tayi cikin wando dariga na Pakistan sky blue, rigan iya cinya sai wandon yakamata sosai, amma tayi k'yau kamar kasaceta kagudu, itama Nawal tasaka mata 'Yar Riga Mara nauyi.
Harzasu fito Nawal ta ce, "saita goyata, Rahma taduk'a Nawal tad'ane.
Falon suka fito inda ta tarar da Bobo zaune akan kujera mai d'aya ya d'ora k'afafunsa saman k'aramin tebir na gilas yana karanta jarida, gefensa lemo na kwali da Kofi anzuba rabi, yana sanye da wando 3/½ fari da riga ja Mara hannu.
Masha ALLAHU Rahma tafad'a azuciyarta.
Baby kalleni Nawal tafad'a tana d'agama Bobo hannu.
d'an d'agowa yayi ya ce, " naganki baby yamaida Kansa.
Rahma tasauketa tana fad'in tonima gobe saikimin goyon.
Nawal tawaro idanu waje kamar wata babba, lah momy bazan iyaba saidai baby yay miki, taje tadafa bobo, baby.
Ya ce, "na'am.
Zaka ramama momy goyon data minko?, kagani ban girmaba, bazan iyaba..
Bobo yakalli Rahma dake zaune tana mamakin wayau da surutu irinna Nawal, Dan yau d'aya tafahimci Nawal d'in tanada shegen wayau irinna sai antona d'innan ake samun irinsu.
Ahankali ya janye idonsa yamaida kan Nawal eh zan rama miki.
Tanufo Rahma tana murna, momy taso baby yagoyaki kinji.
Rahma tayi murmushi k'arfin hali a'a babyna nayafe basai yagoyaniba, kinga muje kici abinci, tafad'i hakane Dan mantar da Nawal wancen zancen.
Ta kalli Bobo daya maida hankalinsa kan karatun jarida ta ce, "ga abinci dady.
d'agowa yay yana kallonta danjin takirasa da daddy, itakam tai k'asa da kanta, takirasa da dadyne Dan batasan yazatace masaba, kuma baikamata takira sunansa kai tsayeba.
d'an lumshe idanunsa yayi yana wani guntun murmushi, tabashi dariya wlhy, amma saiya dake, wai dady yakuma maimaita sunan azuciyarsa.
Haka yamik'e yanufi dinning d'in.
Tuwon shinkafane miyar Agusi wadda yaji busashshen Kofi da nama sai tashin k'amshi takeyi, saikuma lemon ayaba Wanda yaji had'i na musamman.
Aransa ya ce, " ya akai tasan abincin danafi so ko Ammice tasanar da ita?.
Itadai Rahma tazuba masa komai tatura gabansa.
Tayi mamakin yanda yaci abincin sosai, Dan ita tayi tunanin zaice bayacin tuwo, tunda taga d'an hutune.
Bobokam abincinnan yaymasa dad'i jiyayi Rahma tak'ara girmaba a idonsa, taburgeshi sosai gata yarinya k'arama amma ta iya girki mai dad'i.
Bayan sun kammala suka dawo falo..........
*_saidafa nace kuyi hak'uri dani, Dan wlhy akwai buk d'in danayi niyyar fara posting ba wannanba, amma babu yanda zanyi Marak'isiyya tafara wannan, naga kuma bai dace nabarshi ban k'arasa mukuba, randa nake da ishashshen lokaci zakuringa ganin 2page Dan inaso nakammala nafara wancan, randa kuma nake busy zakuga 1 kawai._*
_Bak'in Haure shine buk d'in dazan fitar muku Wanda zai fita akark'ashin wata k'ungiya dana sanar daku abaya, ina buk'atar addu'arku, ngd sosai da k'auna, ina k'aunar masoyana aduk inda kuke._
*_Luv u oll my fan's_*
*_(((S))).........2017_*
👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣1⃣=3⃣2⃣
*_SAFNA_*
Tun bayan biki 'yan gidan suka fita harkarta gabad'aya, gaisuwarta kawai suke amsawa, itama aciki cikin.
Itako hakan bai dametaba Dan ta ce, "sagaji su sakkone tunda itaidai ALLAH ya tsallakar da ita daga auren dolen da akayi nufin k'ak'aba mata, to duk abinda zasu suyi tayi daga baya kenan.
Yau tana school, zaune suke itada k'awayenta zeenat da Baseera, hirarsu suke hankali kwance sunata shek'a dariyar shak'iyanci ga wani d'alibi bai suna Rabi'u, yayi wani dressing ne waishi adole babban yaro, yazo gurunsu yana fafa sukuma sai famfashi suke suna masa dariyar shak'iyanci.
*boy ne yak'araso wajen, tunda Safna ta hangoshi tafara washe Baki, ta ce, R.. Boy kaga k'ara gaba sai anjima mun had'u.
Sanin halin rashin mutuncin safna yasa Rabi'u barin wajen.
A'a *boy yayane?, incedai akwai labari mai dad'i?.
Aiko akwai labari mai dad'i saidai........
Saidai me?, kai dad'ina dakai komai dad'in zance saika nemo abinda zai 6atashi, baseera tafad'a tana hura hanci, Dan halinsu d'aya da Safna, shiyyasa sukafi shiri.
Muzauna kabamu misha zeenat tafad'a cikeda shak'iyanci.
*boy yakalli zeenat, zee baby yanajiki tsit ne.
Zeenat tayamutse fuska, babu Marsala kawai ina mamakin k'awatane yanda tarud'e akan wanj, saikace wata sakarai.
Harara safna ta watsa mata, indai bazaki dad'i alkairiba to kiyi shiru, Dan indai bansamu guy d'innanba to bak'in bakinkine yajamin.
Ido zeenat tazaro to ALLAH ya k'yauta yasa kisamu guy d'inki k'awata.
Baseera ta ce, "yanzu kikayi magana *boy jamuje.
*boy yagyara zama ya ce, " guy d'inki sunansa Abdulmalik Aliyu Abdulmalik, amma ana kiransa da (BOBO), lauyane maizaman kansa, mai tausayin talaka da kwatar musu 'yancinsu, danshi kud'i ba matsalarsa bace.
*boy yafara bama su Safna cikakken tarihin bobo daga farko har k'arshe, har aurensa nafarko da mutuwar matarsa, da kuma d'iyarsa Nawal.
Safna tazaro ido waje, *boy yanada d'iyafa kace?.
*boy ya ce, "shiyyasa nace, " miki akwai Abu Mara dad'i alabarin, ayanzu danake gaya miki kwana goma kacal da aurensa......
Aure kuma!!!?. suka fad'a suduka arazane.
Jikin safna Yakama rawa, tamik'e arazane batareda sha'awar jin k'arshen labarinba.
Zeenat tarik'eta da sauri, safna ina kuma zaki?, hannunta tafusge cikin rawar murya ta ce, "gidan zanje.
Gida kuma?, munfa kusa shiga lecture.
Tsaki taja batareda tabata amsaba tayi gaba.
Zeenat ta ta6e Baki tana fad'in 'Yar wahala.
Cikin masifa Baseera ta ce, "dammi zakice mata 'Yar wahala?, soyayyafa ba k'arya baceba.
Nima aii bance k'arya bace, amma ta safna batada tsari, kuma kad'anmma tagani indai tak'amarta bijirema iyaye, ta tashi fuuuu tabar wajen.
*boy ya ce, "nifa kuji dani Basee, cikon kud'inafa".
kaga dan ALLAH kaje idan mun had'u agida zanbaka, itama ta tashi tabar wajen.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Rahma tare sukai kwanciyarsu itada Nawal, koba komai tasamu 'Yar tayon kwana da hira, barema harga ALLAH tanason Nawal, jiya kad'ai dasuka rayu tare taji son yarinyar sosai a zuciyarta, dawuri ta tashi ta had'a musu break, kasancewar su Nawal suna Hutu yanzu bata tada ita daga barciba saidai tagama komai na gyaran gidan.
Tana d'aki zatayi wanka Bobo yafito cikin shigar suit bak'ak'e hannunsa d'aukeda k'atuwar rigar lauyiyi, d'ayan hannun yarik'e da jakar aikinsa da hular lauyoyi, yau yanada shari'a k'arfe 9:30am.
Ganin babu kowa Afalon saidai yasha gyara sosai sai k'amshi ke tashi, yad'an lek'a d'akin Rahma batanan sai Nawal kad'ai kwance tana barci akan gado, ahankali yak'araso yaymata kiss akumatu sannan yafito, dinning yanufa Dan yanajin kwad'ayin k'aracin abinci Rahma ayauma.
Itakam tana bathroom tana shirin yin wanka taji k'amshinsa, takafar mukulli tad'an lek'o ta hangesa yanama Nawal kiss akumatu, a ranta ta ce ,"yau albarkacin d'iyarsa anshigo d'akina kenan?, dukda dai bai nemi inda nakeba tad'an ta6e baki.
Shikam yana gama lodama cikinsa abinnan mai dad'i dasaka kunnen maici mik'ewa yatashi tareda yin hamdala dasakama Rahma albarka, agurguje yafice Dan time yawuce sosai.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Ikon ALLAH ne kawai yakai Safna gida, tana shiga d'akinta tanufa Dan falo babu kowa tasan ummi tana barci k'ila.
Tafad'a kan gado jagwaf kamar wadda akacema Abba yamutu haka tashiga kuka rurus, saidai tayi mai isarta sannan tayi shiru danba mai lallashi, yauce rana tafarko dataji kewar Rahma, Dan dukda tsangwamarta datakeyi indai yarinyar taganta cikin damuwa ita take lallashinta da kwantar mata da hankali, amma yau tamata nisa.
Tacije le6enta tana k'ara zubda kwalla masu zafi, ta ce, ''nad'au alk'awarin kota halin k'ak'a saina auri guy d'inanan, kuma saina rabashi da matar tasa Dan bazanyi shearing d'insa dakowacce maceba, banta6a Neman Abu narasaba a duniyar nan, nasan kaima bazan rasakaba bobona.
Ban ta6a bin malamaiba ko bokaye, bammasan inda sukeba, amma awannan karon duk inda suke saina nemosu, kuma zan kashe konawane Dan in mallakeka mijina, wasu zafafan hawaye suka zubo mata, kuka takeyi sosai da zuba sambatu harma da sa6o.
( Na ce, "hummmmm safna kenan, duk d'an daya hana uwarsa barci tofa shima bazai yiba).
------------------------:::::::::::
Agidan Bobo kam Rahma da Nawal ne suke wasan 'Yar 6oye, Rahma tarufe ido da k'yalle Nawal kuma ta6uya Rahma na nemanta, Nawal ta ta6ata tana fad'in momy kin ganni, da Sauri Rahma tajuyo inda taji maganar Nawal.
Bobo yashigo da sallama wadda babu Wanda yajita, tsayawa yayi yana kallonsu cike da burgewa, Rahma dake laluben Nawal tak'aro inda yake tana laluben Nema, jitayi ta damk'i wani hannu mai laushi da santsi.
Da sauri tacire k'yallen data rufe fuska danjin Nawal tana tafa hannu tana dariya dafad'in shikenan baby zai goya momy.
Kallon ido cikin ido sukaima juna shida ita saikuma suka dawo da kallonsu kan Nawal.
Baby ka ajiye jaka ka goya momy kawai.
Da sauri Rahma ta ce, " nikam Nawal na yafe.
Nawal ta k'ya6e fuska tana fad'in um um nidai sai yayi miki goyon, saikitacewa kin yafe kullum kullum.
Kan Rahma ak'asa ta ce, "toki bari yahuta kinga yazu yadawo daga aiki, tajawota jikinta tana lallashi.
Bobo yawuce d'akinsa yana murmushin darun Nawal.
Bayan yayi wanka yafito sanye da wando iya guywa da Riga k'arama, Rahma tamik'e kanta ak'asa ta ce, " ga abincifa.
Baice mata komaiba yanufi dinning, itama baya ta take masa, bayan ya zauna tafara had'a masa komai, sai satar kallonta yake k'asa k'asa, tagama takoma falo taja Nawal suka koma tsakar gidan dansu sha iska.
Bayan kamar minti 30 suka dawo, sannan bobo ya kammala yanazaune da jaridar tasa ta fama.
Nawal ta ce, "yauwa baby tashi kagoya momyn to.
Da sauri Rahma tanufi d'aki dantaga rigimar Nawal bazata k'areba.
Bobo yajawo Nawal yad'ora kan cinyarsa, kinga babyna kibari zan goya momynki amma ba yauba, kinga yau nagaji, yak'are maganar da sumbatar kumatunta.
Nawal ta k'ya6e fuska ita adole bata yardaba.
Ganin zata takura masa, shikuma soyake yahuta saboda yagaji sosai, ya ce, "to tashi muje na goyata, tamik'e yarik'e mata hannu suka nufi d'akin Rahma.
Tana zaune bakin gado tana wasa da wani d'an babyn Nawal, suka shigo, ta d'ago kai tana kallonsu, suna had'a ido da bobo ta kauda idonta.
Nawal ta ce, " momy tashi baby yamiki goyonki.
Rahma tabud'e baki zatayi magana Bobo yad'aga mata hannu, karki damu yarinyar nan taki ba k'yalemu zatayiba inhar ba'ayi goyonnanba, Dan haka taso kawai nayi muhuta.
Da sauri Rahma takallesa danjin furicin bakinsa, yama za'ayi harta iya yarda ya goyata saikace wata yarinya.
Bata ankaraba taga ya tsugunna yana jiran tahau kenan.
Cikin sanyin murya ta ce, "Dan ALLAH kayi hak'uri bazan iyaba.
Juyowa yay yana kallonta fuska a d'aure, ya ce, "amma dai kinsan Nawal dashegen naci, indai ba goyonnan nayiba ba barina zatayi na hutaba, nikam natsani adameni da hayaniya.
Ganin yanda yake magana cikin fad'a amma hakan baihana muryarsa fita cikin nutsuwa da taushiba yasa dole tasakko daga gadon, amma tayi tsaye takasa hawa saboda tana matuk'ar jin kunyaarsa.
Momy kihau baby yana jiranki Nawal tafad'a tana kallonta.
Hararar da Bobo ya watso matace tasata saurin d'anewa bayansa.
Shikuma yamik'e yanufi falo da ita, Nawal nabiye dasu tana dariya.
Yajuyo yana kallon Nawal to nagama ko baby?.
Lah baby saikaje d'aki da'ita sau uku kana dawowa, haka yayta zarya daga falo zuwa d'aki harsau uku, ana ukunne yadireta saman doguwar kujera yana fad'in wash bayana, wlhy momyn Nawal kincika nauyi.
Rahma tayi k'asa dakai cike da kunya, yabata dariya wlhy, sai wani yatsine fuska yake da rik'e k'ugu tamkar zaiyi kuka, amma saita gimtse, wai yau itace namiji yagoya, da gudu tabar wajen tanufi bedroom.
Shikam dariyama tabashi Dan haka yad'an murmusa tareda zama saman kujerar, wani nishad'i na musamman yatsinci kansa aciki, yajingina kansa da kujera tareda lumshe fararen idanunsa yana cigaba dasakin lallausan murmushi.
Har aka kira sallar magriba yafita Rahma bata sake fitowaba, gani take bazatama iya had'a ido dashiba aii.
Saida akayi isha'i yashigo gidan dakayan kwalam da mak'ulashe, Rahma najin motsin dawowarsa ta tura Nawal itakam tayi kwanciyarta tak'i fita.
Nawal taje tafad'a jikinsa tana masa oyoyo, shima rungumeta yayi yana fad'in babyna kinyi sallah?.
Eh nayi nida momy, harta koyamin karatu.
Ya ce, "iye kaga 'Yar gatam momynta, ina momyn taki to?.
Tana d'aki wai zatayi barci, nikuma nazo wajenka nayi fira.
Murmushi yayi Dan yagano tanajin kunyane dankarsu had'u, ya ce, " jeki kiramin ita.
Da gudu tanufi d'akin, tafad'a saman Rahma dake kwance kan gado, momy kizo baby na kiranki.
Rahma tadafe kai banace kice masa ina barciba?, kuma daga yau kiringa cemasa dady ba beby ba kinji babyna.
To momy zandinga fad'a tashi muje to.
Badan Rahma tasoba tasakko suka nufi falo itada Nawal.
Yana zaune idonsa akan Tv yana kallon labarai ta ce, "sannu da dawowa.
Yauwa yafad'a batareda ya kalletaba, ya ce, "ga wannan yamik'a mata ledan kayan motsa bakin.
ALLAH yasaka da alkairi tafad'a tana kar6a, kicin tanufa itada Nawal suka juyo afilat, wad'anda bazasu ciyuba tasaka afirij.
Takawo masa nasa itakuma tad'auki nasu danufi sutafi d'akinta suci, ya ce, " ina zakuje kuma?.
Kanta ak'asa ta ce, "d'aki.
sabodani zakuje d'aki cin abinci?.
Dawowa tayi tazauna batareda tabashi amsaba, saidai akunyace takeci, shikuma yana satar kallonta har suka gama tashige d'aki tabarsu shida 'yarshi.
Shirin barci tayi tai kwanciyarta, dama kayan barcine ajikin Nawal.
Yana gama kallon labarai shima yamik'e da Nawal ajikinsa datai barci, yakashe komai sannan yanufu d'akin Rahma.
Ahankali yasauke Nawal akusada ita, yay musu addu'a sannan yaja bargo yarufesu idonsa akan Rahma, yanda take barci hankali kwance sai fuskarta tayi wani wasai.
Jiki asanyaye yanufi d'akinsa yay shirin barci shima yakwanta...............
[14:23, 10/09/2017] hm: typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣5⃣=3⃣6⃣
Hankali tashe Alh sunusi ya iso gidansa, ko fakin bai bari direbansa yagamaba yafice.
Matarsa na zaune afalo itada k'annen Haneef d'in yafad'o ko sallama babu.
Arazane suka mik'e suna binsa da kallon mamaki, dukda ba yaune rana tafarko daya fara shigowa gida ahakaba.
Ina my son?, yafad'a aburkice.
Cikin mamaki haj Falmata ta ce, "Haneef?.
"Eh," ya bata amasa afusace.
Yanzu babu dad'ewa yafita aii, wani abune yafaru?.
Wata uwar harara yasakar mata, waike wace irin shashashar uwace?, wai kina nufin bakisan 'yan sanda sunzo har gidannan sun kamamin yaroba?.
Afirgice ta ce, "naga takaina ni Falmi, yaushe hakan tafaru?, yanzufa Haneef d'in yashigo gidannan ya sauya kaya yafita.
Bai sauraresuba yafice yabarsu cike da tashin hankali.
Abin kamar wasa Alh sunusi har dare yana Neman Station d'in da akakai Haneef amma babu ko Alamarsa, ransa yak'ara 6aci da harzuk'a, aiiko wlhy saiya d'auki mataki akan 'yan iskan police d'in dasukai k'arfin halin shigar masa gida harda kama masa tilon d'ansa namiji.
Gida Yakoma danufin zaije ga Qumissioner of police gobe idan ALLAH ya kaimu, saidai zuciyarsa namasa rad'ad'i idan yatuna Haneef zai kwana a Station yau.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
*_9:30pm_* ya isa gidansa duk agajiye, jinsa yake yau fes tunda ankama masa d'an iskan nan, bayan sun gaisa da mai gadi yashige cikin gidan.
Babu kowa afalon, har TV akashe yake ga gidan tsit kamar babu kowa, da alama masu gidan har sunyi barci.
K'ofar yamaida yarufe sannan yanufi d'akinsa, yazube kayan hannunsa cike da gajiya, babu 6ata lokaci yacire kayansa ya fad'a bayi domin yin wanka.
Bayan yafito yagabatar da shafa'i da wutiri, 'yan dube dube yafayi da alama akwai abinda yakeson gani, amma babu, d'an k'aramin tsaki yayi tareda mik'ewa yafice.
Cikin barci Rahma taji ana bubbugata, afirgice ta tashi, Dan dama tsorace takwanta, saboda rashin dawowar mai gidan.
Ganin shine atsaye yasa ta sauke ajiyar zuciya, ahankali ta ce, "sannu da zuwa.
Bai amsaba ya ce, " ina shayina?.
Tad'an dafe kanta, wlhy na manta ne.
Aii yanzu na tuna miki, yafad'a yana ficewa.
Asanyaye Rahma tasakko daga gadon, Dan barcin data fara yasa jikinta yin lakwas, haka ta k'arasa kicin tana jan k'aramin tsaki, idonta cike da barci tadafa masa shayin, tajuye akofi tareda yanka lemon tsami ta matsa aciki, tad'ora akan k'aramin tire tafice.
Ganin baya falo gabanta yafad'i, kenanfa d'akinsa zata kai masa?, tai shiru kamar mai nazari, zuciyarta ta ce, "kije kikai karya huce Rahma ki k'ara jama kanji wani laifin", tunda tazo gidan yauce rana tafarko dazata Shiga d'akinsa, Dan haka k'irjinta keta dukan uku uku, haka tadaure ta kwankwasa, saida tayi kusan Monti biyu sannan ya ce, " tashigo.
Ahankali ta tura k'ofar tashiga, wani k'amshi yadaki hancinta tashak'a talumshe idanunta, saikuma ta bud'e ta sauke akan Bobo dake zaune abakin gado yana latsa laptop, k'afarsa d'aya ak'asa d'ayar kuma ya tank'washeta a gadon, sanye yake da kayan barci ruwan ganye mai turuwa, tana mamakin yanda yakeson latsa laptop da karatun jarida.
Jin shiru bata ajiyeba, bakuma tayi maganaba yasashi d'agowa ya kalleta, shima baiyi maganaba saidai tura mata k'aramin tebir na gilas dayayi.
Ganin haka yasa itama tad'ora batareda ta ce, "k'alaba.
Bayan ta ajiye saikuma tayi tsaye takasa tafiya.
Yana danna laptop d'insa yana shan shayi, tsawon minti 7 ita batayi maganaba shikuma ya shareta yanata aikinsa, yakula bazatace komaiba, kuma akwai magana abakinta, Dan haka shi ya daure ya ajiye NASA shan k'amshin ya ce, " kinada matsalane?.
Kad'an ta kalleshi taga har yanzu idonsa nakan laptop d'in.
gyara tsayuwarta tayi, muryartan nan mai kasheshi ta daki kunnensa, dama sonake naji yau ko lfy Baka dawo da wuriba?.
Cak ya tsaya da abinda yakeyi, yad'ago fararen idanunsa ya sauke akanta, sanye take cikin dogon hijjabinta har k'asa, sa6anin d'azu daya Tatar da ita da kayan barci.
Ahankali yasauke ajiyar zuciya, koba komai yaji dad'in kulawarta agareshi, cikin miryarnan tasa ya ce, "babu wata Marsala aikine yamin yawa a office.
" okey saida safe."
Harta kai k'ofa yana binta da kallo, yadaure ya ce, "incedai babu wata damuwa daga babyn taki?.
Bata juyoba amma ta tsaya, Dan furucinsa na k'arshe yaymata dad'i, muryarta araunane ta ce, " a'a babu Marsala, saidai tata jiran dawowarka, harta gaji tayi barci..... Bata jira amsarsaba tafice.
Ajiyar zuciya ya sauke tareda lumshe idanunsa, zuwa wani lokaci ya bud'e idon, d'an murmushi naga yayi Wanda bansan da liliba, saikuma yacigaba da aikinsa yana shan shayi.
Itakam Rahma tana komawa d'aki tahaye gado ta kwanta abinta sai barci.
::::::::::••••••••••••:::::::::
Washe gari Rahma ta tashi kamar yanda tasaba ta had'a break fast da gyaran gida, taima Nawal wanka itama tayi, kwalliya sosai taima yarinyar tai tsaf da ita, Dama ga ruwan k'yau d'an Asali, kan baby Nawal yasha gyara Dan jiya da yamma Rahma tayi mata kalba, kasancewar yau juma'a.
Tana cikin saka mata janbaki yaturo k'ofar yashigo da sallama ciki ciki kamar Wanda akaima dole
Da sauri Nawal ta hantsilo daga kujerar madubi danta hango daddynta ta madubi, oyoyo papa na tafad'a cike da farinciki tana rungumesa, shima d'aukarta yayi yad'aga sama yana dad'in "I luv u my child," yasumbaci kumatunta.
Ta shagwa6e fuska, papa shine jiya kak'i ka dawo ko?, lah nadawo mana, saidai kinyi barci sannan kitanbayi momy kiji?.
Nawal takalli Rahma dake kallonsu cike da sha'awa, wai haka momy papa yadawo jiya?, kai Rahma tad'aga mata tana murmushin daya kusan narkar da Bobo atsaye, hakane babyna yadawo kina barci.
Nawal tasunbaci kumatun babanta da k'asunba ta kwanta luf tanata shek'in gara.
Shikam hankalinsa nakan Rahma yana mata wannan munafikin kallon NASA k'asa k'asa.
Talura dashi tsaf dan haka tatsargu, rissinawa tayi ta ce, "INA kwana?."
Lfy, yafad'a cike da basarwa shi adole ba ita yake kalloba.
Rahma ta d'an ta 6e baki, dukda ta fahimci salon amsa gaisuwarsa kenan...... Muryarsa ta katse mata tunani, kushirya idan mungama break gida zamu wuce, Dan duk juma'a a can kowa yake yini.
Ahankali ta jinjina kai kamar wata k'adan garuwa.
Shikam yajuya yafice da Nawal ahannu.
Itama fitowa tayi tahad'ama kowa abinci agabansa, hankalinsa kwance yakecin abinci shida d'iyarsa, amma Rahma duk atakure take, haka kullum take cin abin ci atakure, bakuma danwai bata saba da ahakan bane, saidai kawai nauyinsa datakeji, tunda agidansu gaba d'aya suke had'uwa suci abinci tuntana yarinya.
Tananan tana juya cokali haryagama shida Nawal, yad'auketa suka koma falo suna jiranta.
Ganin yatashi yasata sakin jiki taci abincinta sannan takwashe kayan taje ta d'auraye.
d'aki takoma tacanja shigarta cikin wani had'ad'd'en doguwar rigar shadda pink colour, kayan sunmata k'yau sosai, tasaka k'aton farin hijjabinta sannan tafito, babu kowa afalon, danhaka takashe komai na kayan wuta, gamawata keda wahala yafito shida Nawal daga d'akinsa, hannunsa rik'eda jakar aikinsa.
Kallo d'aya yaymata yad'aukekai, saidai har azuciyarsa yaji dad'in hijjabin data saka, yanason kamilar mace arayuwarsa, gaba yay suka bishi abaya.
Tashaya kulle k'ofar falon shikuma sukai gaba cikin mota shida Nawal.
Ganin Nawal abaya itama tabud'e bayan zata shiga, ahankali yay maganar tamkar mai ciwon baki.
"Halan ni direban kine?."
Cak tatsaya tafasa bud'ewa, kuma tak'i dawowa gaban.
Yakuma cewa kina 6atamin lokacifa, kuma wajen aiki zanje, jiki a sanyaye tabud'e gaban tashiga, shima baisake cewa komaiba yatada motar suka fice bayan sun gaisa da baba mai gadi.
Karatun Alkur'ani yasaka musu, cikin k'ira'ar shiek Abdurraham sudes, ahankali Rahma kebin karatun, yana kallonta ta gefen idonsa, jiyay tak'ara girma a idonsa.
Har sukaje gidan Appa babu Wanda yay magana, garama Nawal takanyi jefi2.
Saida yatsaya suka gaisa da baba mai gadi, yaymasa alkairi kamar yanda ya saba sannan yashige ciki.
Yana faka motar Nawal tafice da gudu zuwa cikin gidan, sukuma suka fito cikin nutsuwa, da gudu khairiyya da khursiyya suka fito, rungume Rahma sukayi suna farin cikin ganinta.
Ta ce, "aini nayi fushi, daga zuwa d'aya baku sakeba.
Kiyi hak'uri auntyn mu, Ammi ce ta ce, " mubari sai nan gaba.
Bobo yak'araso yana harararsu to maganannu ai kwabari kushiga gida dai ko?, yay gaba abinsa.
Khursiyya ta ta6e Baki, aifa yau munga banu jarabatu yazo, ALLAH yasa aiki zai wuce cewar Khairiyya.
Rahma najinsu dai tayi murmushi kawai.
Cikin gidan suka shiga, hakan tayi daidai da sakkowar Ammi daga saman Appa, Dan Nawal nazuwa canta haura.
Ta rungume Rahma tanamai jin dad'in ganinta, cike da kunya Rahma ta rissina ta gaida Ammi, ta amsa cikeda fara'a, da tambayarta ya zaman babudai wata Marsala ko?.
Kan Rahma ak'asa ta ce, "Ammi babu matsalar komai, to Alhmdllh d'iyata haka nakeson ji.
A'a mukarram d'ina lfy dai ko?, Ammi tafad'a tana kallon bobo dayay tsaye yana kallonsu tun d'azun.
yaturo baki gaba kamar wani yaro, yo Ammi sai yanzu kika san dani?.
Ammi taje takama hannunsa, o ni na isa namanta da babana, kawai ina murnar ganin d'iyatane.
Yakuma turo Baki, Toni bari nakoma tunda bak'ya murnar ganina, yanda yay maganar ashagwa6e yasa su khairiyya kwashewa da dariya.
Harara ya watsa musu suka bar wajen, itadai Rahma murmushi takeyi da mamakin Bobo, irin wannan shagwa6a haka kamar wani d'an shekara 5, anace mata tanada shagwa6a toga Wanda yatakata iyawa.
Ammi ta lallashesa suka haye sama domin gaida Appa.
Appa yaji dad'in ganinsu sosai, Dan haka yaymusu nasiha sosai sannan bobo yamik'e yaymusu sallama Dan wucewa aiki, saikuma antaso.
Yakalli Rahma k'asa k'asa ya ce, "saina dawo.
Kanta ak'asa ta ce, " ALLAH yatsare yabada sa'a.
Yaji dad'in addu'arta Dan dama ita yake son ji.
Ammi taji dad'in addu'ar da Rahma taima bobo, hakama Appa, suma sukai masa yatafi.
Zuwa 10:30 gidan yagama cika, aunty Rasheeda da 'yayanta, aunty Sameera ma da NATA, aunty ummy ma haka, mazan kuma suna ajiyesu suka wuce wajen aikinsu.
Dan danan gidan ya haukace da hayaniya, yaran duk suna falon sama wajen Appa, sukuma iyayen suna falon k'asa sunashan hira kamar wasu k'awaye, babu wannan shegiyar ak'idar ta kishin Sauri, hirarsu suke sosai, Dan danan Rahma tasaki jikinta dansu, su aunty Rasheeda akwai saurin shiga rai, gasu khursiyya iyayen shafta............
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S))).........2017_*
[14:23, 10/09/2017] hm: typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣3⃣=3⃣4⃣
"K!, ina zakije da sassafennan?.
Safna ta kwa6e fuska, ummi munafa da Lectures k'arfe 7:30am kuma malamin baida kirki wlhy, gashi ya CE, " test zai mana, tak'are maganar da turo baki gaba.
Ummi ta ta6e Baki, ta ce, " shikenan jeki, amma idan kin dawo inason magana dake nida mahaifinku.
Gaban safna yafad'i ta ce, "ummi magana kuma?, tami to?.
" idan kindawo k'yaji, Dan inama son aikenki gidan Rahma.
Kai ummi gidan Rahma fa kikace?, saikace wata k'anwarta.
To tunda tarigaki aure aikin zama k'anwar tata aii, ko kina nufin dankince bak'yason mijinta bazakije gidantaba?.
Nifa Bahaka nake nufiba ummi, kawai INA dai ganin da kunya.
Harara ummi tasakar mata, o sai yanzu kika San kunyar?, alokacin dakikai shirin wulak'antamu kin manta da kunyar.
Nidai ummi ALLAH yabaki hak'u, ALLAH fa yariga yarubuta itace matarsa kawai, amma ni ban wulak'antakuba, kawai ina gudun kar asakamin kaina atunkunya ne, saina dawo, tayi saurin ficewa, Dan batason jin amsar ummi, tasan halinta sarai, yanzu saita hau sama ta 6ata mata shirinta, itako awannan lokacin bata fatan abinda zai hanata fita.
Ran ummi yak'ara 6aci, duk cikin 'yayanta babu Mara kunyar irin Safna, ita bata iya tauna magana ga mahaifaba, ta maidasu tamkar wasu k'awayenta, kodan gatan dasuka nuna matane abaya?.
Tana fita taci karo da Baseera ak'ofar gida.
A'a kice kina nan?, dafa shirin shiga gidanku nakeyi, to waima inbanda iskanci miye natsayawa anan?, gidan bak'onkine?.
Baseera tarufe murfin motar tana fad'in Bahaka baneba, banason nashiga mu 6ata lokacine kawai.
Dariya safna tayi, haba k'awata aganinki zan 6ata lokacine?, kenifa k'agara nayi gari ya waye, yanzun haka jinake tamkar nayi tsuntsuwa na ganni agaban malaminnan.
Baseera ta tuntsure da dariya kai k'awata kemafa bakida dama akan abinda kikeso, lallai guy d'innan yayi babbar sata.
Safna tak'ara dafe sitiyarin motar, ai wlhy Basee guy d'innan ba k'aramar sata yayiminba, wlhy gaba d'aya ya haukatani, saidai idan natuno kafinni harya zauna da mata biyu nakanji raina ya 6aci, badan ina sonsaba sosai da watsar dashi zanyi.
Shiyyasa Nima na d'auki alk'awarin saina mallakesa amatsayin miji kota halin k'ak'a, ke namiki mai kankat wlhy har yarinyarsa saina rabashi da ita, Dan dagani sai 'ya'yana nakeso mu zauna dashi.
Hummm 'yammata ace insha ALLAHU dai.
Safna ta gallama baseera harara, to aii dama komai insha ALLAHU ne, koko insha Baseera ne?.
A'a Dan ALLAH karki mana sa6o mudai kisa akifar damu, kefa wani lokacin kamar bakiyi islamiyyaba haka kike.
Banza Safna tai mata, Dan idan tabiye mata fad'a zasuyi, itakam lalla6ata takeyi tasamu arakata gun malami.
Sun isa gidan malam amma da mutane, Dan haka suka jira a mota.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*
Bobo a police tetion yasaka 'yan sanda gaba sai masifa yake musu, wai basu san aikinsuba.
Haba Dan ALLAH wai mikuka maida kankune?, yau sati nawa ace angagara nemo mai laifi, hanyafa mai sauk'ine gano koma wane d'an iskane, saboda anbaku no. d'in motarsa, wlhy nabaku nanda gobe idan ALLAH yakaimu inhar baku zomin da mai lafinnanba zan d'au mataki, Dan saina saka anta6a aikinku, tunda bakusan abinda kukeyiba...
Sudai 'yan sanda cikinsu ya d'uri ruwa Dan sunsan kowaye Abdulmaleek, tunda bayau yafara d'ora su akan aikiba.
Tsaki yaja yafice, afusace yashiga mota yafigeta.
Yayi nisa atafiyarsa sai masifa yakeyi shikad'ai amota, tamkar zai ari baki.
Wani haushine yak'ara turnik'eshi Dan ganin wani banzan Go slow mara dalili, kamar ance ya waiga idonsa yasauka akan number motar guy d'in dasuke nema.
Jikinsa har rawa yake yad'auki waya yakira 'yansanda, saidai yana yanke wayar ana sakin Go slow d'in, da hanzari yatakema motar baya, binsa yake cikin dabara har zuwa wani kantamemen gida, ya sauke numfashi afili ya ce, "gidan Alh Sunusi Dala kuma?, kenan wannan motar tanada alak'a da gidan?.
Wayarsa ya d'auka dake wringing 'yan sandane suke tambayarsa yana ina?.
Kusameni gidan Alh Sunusi dala.
Kansa ya kwantar jikin kujera, saiyanzu yagane abinda yasa 'yansandan suka kasa kama mai laifin, tabbas sunsan yanada alak'a da wannan gidan.......
Tunaninsane yatsaya alokacin da motar 'yan sandar ta iso, bai fitoba amma yabud'e murfin motar.
'Yan sanda biyu suka k'araso inda yake, fuska ad'aure yakallesu, nan gidan motar nan tashiga, Dan haka saikuyi aikinku.
Cikin d'an sanda d'aya yabada wani k'ululu, baki narawa sukace nan gidan kuma?.
Cikin daka tsawa ya ce, "e nan gidan, dama nasan kunsan Wanda ya aikata, amma kwad'ayi irin naku yasa kuka kasa d'aukar mataki, to yanzu saiku za6a, kamashi kokuma asarar aikinku......
Kafin yarufe baki sunnufi k'ofar gate d'in gidan, dak'yar maigadi yabarsu suka shiga.
Daidai nan Haneef yafito cikin sabuwar shiga danufin sake fita, harya fara k'ok'arin bud'e mota yadakata Dan ganin 'yan sanda.
K'arasowa sukayi har inda yake tsaye, sallama sukai masa, ko amsasu baiyiba, saima kallon banza dayake bisu dashi.
d'an sanda ya had'iyi wani yawu sannan ya ce, " yalla6ai u onder arrest.
Me!, Haneeff yafad'a cikeda rainin hankali, yacigaba da fad'in Ku harkunkai matsayin dazaku shigo cikin gidanmu kuce kunzo kamani?, toma awane dalili?.
Kayi hak'uri yalla6ai zamu maka bayani idan munje can, Dan duk abinda kafad'a anan zai iya zama hujja agareka a kotu.
Kan uba...... Saikuma yay shiru yakasa k'arasawa, yaja numfashi kumuje zan biku abaya, yayi hakane danya kafa musu tarko.
A'a kamuje kawai aiiba dad'ewa zakayiba.... Maganar Bobo tadaki kunnuwansu.
Kai kuma awa?, haneef yafad'a yana kallon Bobo.
Karka damu da matsayina, kaidai kadamu da kanka kawai my friend.
Cikin 6acin rai Haneef ya ce, "kadai iya bakinka k'aramin k'waro.
Wata banzar dariyar rainin hankali Bobo yasaki, wadda zan iya cemuku yauce rana tafarko danaga dariyarsa, ya kalli 'yan sandan ya ce, mikuke jira?, yana gama fad'a yafice daga gidan.
Cikin 6acin rai haneef ya ce, "kumuje to, ammafa yak'udiri aniyar wulak'anta d'an saurayinnan da 'yan barandarsa.
Haneef yashiga motar 'yan sanda, bobo kuma yashiga motarsa.
'Yan unguwar sai dad'i sukeji da ganin Haneef amotar 'yan sanda, yayinda agefe kuma tuni magulmata sunkira Alh Sunusi sunkai masa rahoton kama Haneef da 'yan sanda sukayi yanzu.
Hankalinsa atashe yabaro office yanufo gida.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Suna nan zaune har layi yazo kansu, sannan suka shiga.
Bayan sun gaisa da malam da'u safna ta ce, "malam......
Da sauri yad'aga mata hannu karkice komai, tunkafin kizo sud'an tsito sun sanar dani komai.
Kin kamu da son wani saurayi, kinkumasa ayimiki bincike akansa, yanada mata ba'a dad'e dayin aurenba, kuma yata6a aure matar tamutu harda 'ya atsakaninsu, koba hakaba?.
Cikin mamaki da rawar jiki Safna ta ce, " to amma ALLAH ya gafarta malam ta INA kasan wannan?.
Malam da'u yatuntsure da dariya, kai yaro yarone dai, kedai fad'i buk'atarki kawai 'yammata kiga aiki da cikawa.
Cikin tsoro Safna ta ce, "malam dama inaso shi wannan saurayin yazo dakansa gidanmu ya ce, " yana sona, kuma yasaki matarsa Dan wlhy inada kishi sosai malam, kuma inason sa sosai har inaji idan ban sameshiba zan iya mutuwa wlhy, Dan ALLAH malam ataimaka mini.
Malam da'u ya ce, "babbam taimako aljihunki 'yammata.
Baseera da dama tasaba indai bin malamine, hankalinta kwance ta ce, " malam kaima Kasan kud'i ba matsalarmu bace aii, inhar buk'ata zata biya to kad'auka kasamu kud'i konawane.
Malam da'u ya wangale bakinsa dake cike da damzar goro, wasu hak'oranma sun fita, ya ce, "baseera indai kece aii saidai nafad'ama wani, Dan haka kisanar da k'awarki tagama samun abin sonta.
Wani faranti yajawo dake cike da k'asa, yafara Zane Zane yana motsa baki, bayan yagama yamaida kallonsa Kansu, kince ya sunansa?.
Safna ta CE, " nidai bobo nasani, amma Wanda nasaka yamin bincike akansa ya ce, "Abdulmaleek.
Malam da'u yakuma maida kansa k'asa, shiru yayi Dan shikad'ai yasan miya gani, to ammafa yana fad'a mata gsky bazata sakar masa nairoriba, gata kallon d'aya zaka mata kagane kud'i sun jik'ata, Dan haka ya canja shawara, ya ce, " zaki gansa anan kusa kam, saidai bazan fad'a miki ranarba, sannan kuma saikun had'u zan fara aiki akansa, ga wannan yazama kwallinki, wannan kuma hoda.
Kar6a Safna tayi tai godiya.
50k suka ajiye masa suka tafi suna godiya.
Na ce, "hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Bobo har police tetion yaraka 'yan sanda, saida aka gark'ame Haneef Wanda tuntini hankalinsa yafara tashi, yaza'ai kamarshi d'an gata ace anakawoshi nan gurin?, gashi sun kar6e masa waya bare yakira dad nasa yasanar MASA halin dayake ciki.
Yad'au alk'awarin Indai yafita agurinnan saiya wulak'anta yan sandar nan da saurayin nan.
Saida yayama police d'in nanan gargad'i sosai akan wlhy kowaye yazo karsu bada belin Haneef, sannan yawuce yanufi office d'insa, yanason fara shirya yanda zasu shiga kotu.
+
Yaduk'ufa sosai wajen latsa lap-top, gaba d'aya hankalinsa yana wajen binciken family d'in Alh Sunusi Dala, da sauri yad'ago danjin an ta6ashi, jar uban nanan kai yafad'a cikin ihun farin ciki, rungume juna sukayi shida bak'on nasa.
Ammar yaushe a k'asar?.
Ammar yay dariya wlhy mutumin jiya da daddare, shiyyasa yau naimaka sakko amma natarar kafita.
Kabari kawai wlhy naje wajen yaranka ne sukamamin wani d'an iskan mutum.
Kai Bobo kana nandai baka canjaba?, yanzu kuma wa'aka kafama tarko ne?.
Wani murmushi bobo yasaki, kamar mai rad'a ya ce, d'a gurin Alh Sunusi Dala!.
Ammar yad'an zaro ido, Bobo Kasan kuwa sunanwa ka fad'amin?.
Kwarai kuwa nasani, ni kam ainafi kowa farincikin dawo warka wlhy, inason kaima yaranka magana su k'ara gark'ameminshi sosai, Dan ranar litinin nakeson mufara sharia.
Baka da damuwa da hakan abokina.
Yes sir!, Bobo yafad'a yana sarama Ammar.
Dariya ammar yayi yace d'an iska, ALLAH dai ya shiryaka, duk kabi katakurama 'ya'yan manyar garinnan, ina baby Nawal da amarya?.
Saida ya sauke numfashi sannan ya ce, "suna lfy.
Masha ALLAH, kasanar da amarya zanshigo weekend cin abincin amarci, daganan naga amaryar tamu, tunda ALLAH baisa ansha biki daniba.
ALLAH ya kawoka Bobo yafad'a.
Daga nana hirarsu suka cigaba dayi, dagani kasan sunyi bala'in shak'uwa da juna.
*Waye Ammar?.*
Ammar Khaleed Adam, d'ane ga Alh Khaleed Adam, abokin Appa na k'ut da k'ut wanda yayma Rahma k'yautar mota ranar walimar makaran tarsu, su 7 mahaifansu suka haifa, shine na biyar agidansu, yanada yayye maza da mata su hud'u, sai k'anne biyu mata, Ummy matar ya Hamza dakuma autarsu Lubna ita sa'ar su khairiyyace.
Tare sukayi karatu da Bobo tundaga primary har secondary, daganan kowa Yakama inda yafi wayau, Bobo yatafi karatun lauya, shikuma yafad'a aikin 'yan sanda, ayanzu haka shine Qumissioner of police na jihar kano, sun shak'u sosai da Bobo, bashida wani aboki sai Ammar da yayyensa.
Duk wani aiki da Bobo yarikito Wanda yake buk'atar tsaro to Ammar ne ke taimaka masa, yanzuma yayi wata 'Yar tafiyane ta wata biyu, shiyyasa baisamu damar halartar bikin Bobo ba.
Shima matarsa d'aya da yara biyu duk maza.
Wannan kenan.............
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S)))...........2017_*
[14:23, 10/09/2017] hm: typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣9⃣=4⃣0⃣
_washe gari_
Rahma tatashi tayi duk abinda tasabayi dukda tasan yau weekend Bobo bazai fitaba, tana cikin saka turare a falo bobo yafito sanye da jallabiya ruwan toka mai gajeren hannu, rissinawa tayi ta gaidashi, kamar yanda yasaba ya amsa da lfy.
Amsa gaisuwar nan nabama Rahma haushi, amma babu yanda zatayi.
Yad'anbi falon da kallo komai tsaf, gawani k'amshi na musamman, yana jin dad'in kasancewarta mace mai tsafta.
Itadai cigaba tayi da abundan takeyi. Ya ce, "bari nad'anje wani waje nadawo.
Aranta tace kofa wanka bakayiba, amma afili ta ce, " to ga Break.
No barinaje nadawo, aiba dad'ewa zanyiba, yafad'a yana ficewa.
Itama ta ce, "ALLAH ya tsare.
Dukda yafita amma yajiyo addu'arta.
Bayan takammala saka turaren zuciyarta tabata shawara dataje ta gyara masa d'akinsa, kamar bazatajeba saikuma tatuna nasihar mahaifiyarta da ummansu Basma.
d'akin tanufa da tunanin ALLAH yasa bai rufeba, tana tura k'ofar tabud'e, k'amshinnan yana nan kamar kullum, yau tanutsu takalli ko ina na d'akin, komai farine tas, aranta tace farin Abu name tsaftane.
Sai manya manyan hotunanan Ni'ima Maman Nawal, bani gurin ita kad'a, wani gurin kuma shida ita.
Ko kad'an bataji haushiba bare kishinta, Bata 6ata lokaciba tafara gyara ko ina, Dan danan tagama d'akin yak'ara d'aukar haske komai yana d'aukar ido.
Bathroom tashiga zata wanke saitaga kaya ajik'e abokiti.
Shiru tayi tana tunanin ta wanke kota barmasa abinsa, wata zuciya ta ce, " ki wanke, kobabu komai zaki samu lada aii.
Haka tazauna tahau wankin gajerun wandunansa da vest, akunyace take wankin tamkar tana gabansa, gudu gudu sauri sauri tagama bataso yazo yataddata tanayi.
Dandanan tagama tawanke bayin, tad'auki kayan tafito waje, acan baya taje tashanyasu sannan tadawo d'akinta tashiga wanka, Dan Nawal bata tashiba.
Shigarta wanka babu dad'ewa yashigo gidan, d'akinsa yanufa kai tsaye, baki da hanci da ido yasaki yana kallon d'akin NASA, yalek'a bayi nanma fes, bokitin daya jik'a kaya wayam, wani lallausan murmushi yasaki, labulen window d'insa yad'aga, can yahango kayan ashanye.
Jiyay wani Abu nata6a zuciyarsa, afili ya ce, ''ALLAH yaymiki albarka.
Fitowa yayi yanufi d'akin Rahma, hakan yayi daidai da fitowarta daga wanka, daga ita sai guntun tawul iya cinya.
Wata tsayuwar sojan badakkare bobo yayi, sai Raba idanu yake akan Rahma, da wannan munafikin kallon nasa k'asa k'asa.
Itakam dukta rikice, waige waigen abinda zata rufe jikinta kawai takeyi, can ta hango hijjabin sallarta, amma dole saitabi tagabansa zata d'auka, ganin haka saikawai takoma cikin bayin da sauri.
Murmushi yayi tareda sauke ajiyar zuciya, yak'arasa inda hijjabin sallarta yake yad'auka, ahankali yak'arasa har k'ofar bayin ya kwankwasa, Rahma dake jingine da k'ofa tagwalo ido waje, k'irjinta sai dukan Tara Tara yakeyi.
Yak'ara kwankwasawa.
Muryarta narawa tamkar zatayi kuka tace yes, yanda tayi maganar tabashi dariya amma saiya gimtse ya ce, "bud'emin k'ofar.
Innnalillahi tace azuciyarta, wai mi mutumin nan yake nufi.........maganarsa ta katse mata tunani, " wai kobaki jinane?.
Bayan k'ofar takoma tala6e sannan tabud'e, gaba yay tamkar zai Shiga, saikuma yamik'a mata hijjabin, dasauri takar6a tamaida k'ofar burum tadatse.
Girgiza kai yayi yanad'an ta6e bakinsa, yazauna bakin gadon yana shafa kan Nawal daketa barcinta hankali kwance, shi mamakin kansama yakeyi, wai miyake jirane?, zuciyarsa ta ce, "kanason sake kallon Rahma ne.
d'an tsaki yaja yamik'e yafice, shi adole zuciyarsa tayi k'arya.
Saida taga yafita sannan tafito, taje tasakama k'ofar key, sannan tazauna tagyara jikinta, tasaka Riga da wando na Pakistan, nakula tana son irin kayannan sosai.
Nawal ta tashi itama tayimata wanka tashiryata cikin wandon Jin's da pink d'in T shert mai k'yau.
Falo suka fito, fitowarsu babu dad'ewa shima ogan yafito, haryayi wanka yashirya cikin jins blue da farar Riga sai zabga k'amshi yakeyi.
dinning suka nufa, Rahma sai sinne kai takeyi Dan kunya, shikam ko'a kwalar rigarsa, yanacin abinci Nawal namasa surutu, iyakarsa Yamata murmushi koya d'aga kai.
Rahma ta ce, " azuciyarta, muskili kafi mahaukaci ban haushi.
Suna kammalawa Nawal taja hannun Rahma wai suje tamata lilo, fitowa sukai sukabarsa kwance saman doguwar kujera yana kallon film.
Sunacan a lambu Rahma NATA biyema Nawal suna lilo, jiyay falon babu dad'i Dan haka yafito, jiyo dariyarsu alambu yasashi nufarcan, Rahma na zaune akan lilo, Nawal na shillata suna dariya, k'arasowarsa yasa Nawal cewa lah papa kaima zona lilaku.
Kai ya girgiza mata alamar A'a.
Takwa6e fuska zatayi kuka, cikin takun k'asaitarsa yak'arasa wajen lilo d'in, Rahma tayi yunk'urin sauka Nawal ta ce, "momy kubiyufa zanyimawa, sandarewa Rahma tayi azaune, kafin ta farga Bobo ya haye lilo d'in amma d'an nesa da ita.
Da k'arfi Nawal ta hankad'a lilo d'in, aiko sukayi gaba kamar zasu fad'i, da Sauri Rahma ta ruk'unk'ume Bobo, shima yarik'eta.
Nawal Yar kwal uba tacigaba da lila lilo da k'arfi, basuda za6i bayan rik'e junansu dak'yau, Nawal dai sai dariya takema iyayen nata, saida tagaji Dan kanta sannan tadaina lilasu.
Bobo yabud'e idanunsa ahankali danjin lilo ya tsaya, ga Rahma na mutsu2n kwace kanta, yana sakinta tasauka, da Sauri tabar wajen, binta da kallo yayi yana murmushi, Nawal takatse masa tunani, baby d'orani muyi tare tunda momy tagudu.
daukarta yayi yad'ora sukacigaba da lilonsu zuciyarsa cikeda tunani kala kala.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Safna zaune gaban Abba da ummi da alama fad'a ake mata, Dan fukarnan adagule take.
Abba ya ce, " wlhy nabakinan da wata uku zuwa hud'u kifito da miji a had'a aurenku keda amira, inbandama auren ameerar da sati biyu zan baki, amma Abubakarne yaceceki ya ce, "abari ahad'a bikin dan a samu sauk'i."
To saikiyi gaggawar sanar da Wanda kikace kinason harkikaso wulak'antamu akansa.
Insha ALLAHU Abba zan kawoshi, nidai kuyi hak'uri kubar ganin laifina, ALLAH yariga yarubuta Dama shid'in Mijin k'anwatane baniba...
Dallah yimana shiru!!, ummi takatseta atsawace, Mara mutunci kawai, Indai duniyace aigaki gata nan, kuma koyaya Wanda kikace kinason yake wlhy haka ZAMU aura miki shi, kijecan kiji da bak'in halinki, tashi kibamu waje mu.
Mik'ewa Safna tayi tabar falon tana k'unk'uni.
Na ce, " ALLAH ya shirya to.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Ad'an hanzarce takeyin aikin gidan, Sauri take tagama dawuri taje tayi girki Dan maigidan ya ce, "mata yau abokinsa zaizo da iyalinsa, tagama komai tsaf har girkin ta kammala d'akin bobone kawai yarage mata shima Dan yana kwance ad'akinne.
Saiwajen 12 yafito daga d'akin yafita danufin siyo ruwa datace masa babu.
Yana fita tashiga d'akin Dan gyarawa, tagama aikinta lfy lau, tsautsayi yasa takai hannunta kan wani hoton Ni'ima datayi bala'in k'yau, Ashe bai zauna da k'yauba aiko yafad'o jikake taratsatsa!!! ya tarwatse ak'asa abinka da gilas.
Hakan yayi daidai dashigowar Bobo falon, da hanzari yanufi cikin d'akinsa, aiko abinda yake zarginne yagani, dandanan fuskarsa ta canja kama idonnan sukayi ja danshi aganinsa da gangan Rahma tayi saboda batason ganin hotunnan tunda dai yasan mata da kishi.
Tunda yashigo jikinta ke rawa, tabud'e baki arazane zatayi masa magana yadaka mata tsawa.
Dallah yimin shiru, dama kina shigowa gyaramin d'akine danki kashemin hotuna?, to wlhy idanma kishi kikeyi da ita kidaina Dan babu yanda kika iya da ita, wannan dakike gani itakad'aice nabawa zuciyata, daga itakuwa babu wata mace dazata samu haka daga gareni, wlhy akan wad'an nan hotunan sainayi mugun sa6a miki, banason cikin da iskanci.
Rahma tamatso danufin tsugunnawa tabashi hak'uri amma abisa tsautsayi ta taka gilas ak'afa, runtse idonta tayi saboda azaba, dama ga hawaye tuni sun wanke mata fuska.
Tsawa yasake dama mata, dallah malama fitarmin ad'aki, kuma karna sake ganin k'afarki ad'akina.
Ran Rahma ya6aci sosai ganin yanda yake cimata mutunci akan hoto, Wanda inyanzu yaso zaikai amaida gilas d'in daya fashe, haka tataka k'afa tabar d'akin tana kuka, tanazuwa tazube akan gado, ga azabar da k'afarta take mata amma bata kulaba, sai kuka maicin rai data saki.
Duk abinnan yake faruwa Nawal tana can baya tana wasa, Rahma taturata wajene dantabarta tayi aiki, batason surutu.
Bobo kam tana fita yadurkushe agaban hoton, d'agosa yayi yana gogewa tamkar zai fasa kuka, muryarsa na Rawa ya ce, "kiyi hak'uri Ni'imana bada sanina tayiba, ALLAH ya gafarta miki ya yafe miki kinji.
Nawal tashiga d'akin Rahma tana kwala mata kira momy! Momy!!, tak'arasa cikin d'akin da murnarta, amma ganin jini ahanyar sai jikinta kuma yay sanyi, tak'arasa har bakin gadon tana kallon k'afar Rahma da gilas ke jiki ga jini yanata zuba ak'asan wajen.
Fitowa tayi da gudu tanufi d'akin Papan ta, har yanzu yana gaban Hoton adurk'ushe, papa papa zokaga k'afar momy jini yanata zuba dayawan tsiya.
d'agowa yayi yana kallonta, yanda tabirkice shima sai jikinsa yay sanyi, mik'ewa yayi suka nufi d'akin Rahma d'in, gsky shima abin yabashi tsoro ganin jinin dad'an yawa, ga gilas babba kafe ak'afarta, tana kwance rubda ciki tana darzar kuka.
Tsugunnawa yayi Kusada k'afar yakama gilas d'in zai cire tasaki wata k'ara wadda tasaka Nawal fashewa da kuka itama, ga gilas d'in yakafe dayawa, ganin karya k'ara jimata ciwo yasa yamik'e dasauri yaje d'akinsa yad'akko key d'in mota.
Dawowa yayi ya ce, " tashi muje asibiti acire miki wannan kwalban.
Banza tayi masa tacigaba da kukanta, wani haushi yak'ara turnik'eshi, baisan lokacin daya sungumetaba yay waje da itaba, Nawal nabinsa abaya, Nawal tabud'e masa k'ofar motar yasakata aciki, suma suka shiga sai asibiti.........
_kuyi hak'uri da wannan yau kaina namin ciwo._
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S)))..........2017_*
typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
4⃣1⃣
Asibitin ya sulaiman sukaje, ALLAH yasosu sun tarar dashi.
Aiko ansha fama wajen cire gilas d'in nanan, Rahma tasha kuka dukta fita hayyacinta, ga k'afar harta d'an kunbura.
Shikansa Bobo ya tausaya mata, saiyanzu yake ganin abinda yay mata bai k'yautaba, to amma idan yatuna miyakai hannunta wajen hoton saiyaji ransa ya 6aci.
Da hakadai aka kammala, ya Sulaiman yamata allurai tad'an samu nutsuwa.
Bayan an kammala bobo ya ce, "ya yarinyar nan kuwa?.
Jikinta kam saidai muce alhmdllh, ammafa yakamata asan iyayen yarinyar nan Abdulmaleek, gashi kace zaku fara shiri'a ranar talata, kasanfa Alh sunusi dala mutumne mai had'arin gsk, sarai zai iya bincike akan yarinyar, kuma zai iya aikata kimai Dan ganin d'ansa ya ku6ta.
Hakane Yaya, amma inata iya k'ok'arina wajen Neman iyayenta, saidai kutayamu da addu'a kawai.
To ALLAH ya taimaka.
Amin dai, bari mubiya muganta saimu wuce gida.
Okey, kardai kamanta kusiyi maganin.
Babu damuwa, k'arasawa yay inda Rahma take fuskarsa babu walwa, yakama hannunta ta sakko.
Ya Sulaiman dake kallonsu ya ce, " saidaifa kad'auketa kamar d'azu, Dan babu yanda za'ayi ta iya taka wannan k'afar.
K'ara 6ata rai yayi, kamar bazaiyi maganaba, saikuma ya ce, "Yaya ba ancire ba?, eh ancire, amma karfa manta yanda gurin yake a yanzu, idanmma kunje gida ad'an gasa k'afar da ruwan zafi.
Baice komaiba ya d'auketa, saiwani kauda kai yake daga saitin fuskarta, itama saita runtse ido Dan bata son ganinsa.
d'akin da yarinyar nan take yakaita, yadireta saman kujerar gaban gadon, lahh Muheebat! kece?, Rahma tafad'a tana kallon yarinyar.
Itama tashi tayi zaune tana dariya Dan ganin Rahma.
Bobo ya ce, " kinsanta ne?.
Eh nasanta, K'anwar direban muce idris, dama sunata nemanta tun tuni wlhy.
Ajiyar zuciya bobo ya sauke ya ce, "Alhmdllh, yaciro wayarsa yakira Ya Sulaiman, babu dad'ewa kuwa ya iso, shima yaji dad'i sosai dajin labarin.
Sun ajiye magana akan anjima zasuje gidansu Muheebat, dukda bata iya magana to tanajin abinda suke fad'a, Dan haka taita murmushi.
Bobo Yakuma d'aukar Rahma zuwa Mota, daganan sukayi gida, motar tsit babu mai magana kamar wasu kurame, Bobo sai shan k'amshi yakeyi, itama ganin haka saita d'auke kanta, dama can suka baro Nawal zatabi ya Sulaiman gidansa.
Koda suka shiga harabar gidan saiya bud'e motar yay tafiyarsa ciki yabarta.
Rahma tayi wata dariya azuciyarta ta ce, " kama dawo wlhy, dan babu inda zan motsa.
Aiko tayi zamanta amotar, shikam haryaje k'ofar falon saiyaji babu motsinta abayansa Dan haka ya waiga, can ya hangota cikin mota ko motsawa batayiba, afili ya ce, "wai mi waccan abar take nufi da nine?, koni bawantane dazanta d'aukarta ina ajiyewa mtsooow, yak'arashr maganar dajan tsaki.
Komawa yayi wajenta sai wani d'aurewa yakeyi, Rahma ta hangoshi yana tahowa, tayi murmushin mugunta tana fad'in kadaiji dashi.
Bemata maganaba yabud'e motar ya d'auketa, itako ta lumshe idonta kamar mai barci, haushine yak'ara turnuk'e zuciyar bobo, gani yake tana k'ara langya6ewa ne kawai.
Koda yadireta a gadon bai kalletaba yajuya ya fita.
Ita kuma taimasa gwalo , wai dole dai ad'auketa. lol.
Tana nan zaune har kusan minti talatin, harta fara tunanin yanda zata fita taci abinci Dan yunwa takeji sosai, tayunk'ura zata tashi taji wani azababben zafi, danhaka takoma ta zauna, wai miyasama tabar Nawal tabi ya Sulaiman ne?, yanzu da tananan ai data rage mata wani abun.........bata rufe bakiba taji anturo k'ofar.
Kamshinsane ya tababbatar mata dashine, Dan haka tak'i d'agowa danko sallama bataji yayiba.
Tire yadire ak'asa na kayan break, Rahma tayi kamar bata ganshiba, shima ko kallo bata isheshiba yad'akko kofin tee ya mik'a mata.
Kamar bazata amsaba saikuma ta amsa Dan ganin yayi tamau da fuska kamar bai ta6a dariyaba, yamik'o mata filet d'in soyayyar doya.
Saman kujerar dake d'akin Yakoma ya zauna yana danna waya, ganin haka yasa tadake taci abincinta Dan yunwa takeji sosai.
k'asa² yake kallonta, aransa ya ce, "k'aryar ciwo kikeyi yarinya, tumda har kika iya share filet guda na doya, Rahma ta kalleshi ta ce, " nagama.
Banza yay mata yacigaba da danna wayar, saida ya mula Dan Kansa sannan yataso yazauna saman durowar gefen gadon, maganin yacira yabata.
Tofa anan akeyinta, Rahma tayi kwalkwal da ido zatayi kuka, tsak'i yayi yana harararta, idan bazaki amsaba kibarsa kece zakisha wahalarki ke kad'ai wlhy, danni yanzuma zanbar miki gidan.
Yanda yake zabga ruwan masifa yasa ta k'ar6a, saidai tana hawaye tana sha, idan tasha d'aya saitayi kamar zatayi amai saikuma ta daure, shidai yana kallonta ta gefen idonsa Dan yacigaba da latsa waya, hakadai tadaure tasha maganin.
Tashi yayi ya d'auki kwanukan yafita dashi, babu dad'ewa yadawo da k'aramar roba da ruwan zafi aciki, sai k'aramin tawul.
Baiyimata maganaba yajawo d'ank'armin tebir na gilas dake kusada kujera ya zauna, Rahma ta ce, "kasada aranta.
K'afarta yad'auka yad'ora saman stool na madubi, itadai ikon ALLAH take kallo kawai.
Dukda yaga kallon datake masa bai kulaba yafara aikinsa batareda yabi takantaba, yasaka tawul d'in aruwan zafin yad'an yamatse, daganin yanda yake matsar tawul d'in kasan ruwan da zafi, amma Dan bak'ar mugunta ahaka ya nanama Rahma akan k'afar, wani wahalallen ihu tasaki, yay saurin rik'e k'afar yana harararta, kawai saitaji hawaye nabin kumatunta.
Raguwar banza yafad'a afili.
Itama ta ce, " ruwanfa da zafi wlhy, yanda tayi maganar ashagwa6e saiya tsaya yana kallon bakinta, ta kauda fuskarta tana tura Baki gaba.
Shima bakin yata6e yacigaba da aikinsa.
Da zame zame da mazurai aka gama wannan gashin k'afar, yad'auki maganin shafawar ya shafa mata sannan yakwashe kayan yafice itakuma ta kwanta tana sauke numfashi.
Bai sake shigowa d'akinba harsu Ammar suka iso shida matarsa da yaransu biyu duk maza.
Cikin farinciki yataresu, yanda yaketa murmushi saika d'auka bashibane yagamawa Rahma mazuraiba yanzu.
Cikin falon suka k'araso, Sumayya matar Ammar ta ce, "nibanga amaryarba ko ka sakata ta 6uyane?.
Murmushi yayi ya ce, " 6uyan lfy, tana d'aki kwance batada lfy.
Ammar yashek'e da dariya mutumina komun samu k'annen Nawal ne?.
Harararsa yayi kaifa bakada kirki wlhy, to Abu ta taka ak'afarta d'azu da safe.
Ammar ya ce, "ayya ALLAH yakiyaye gaba, amma yanda na sanka d'innan ai yanzu munsami baby duk wani zame ²n ka.
Kadaiji dashi d'an iska, bobo yafad'a yana nufar d'akin Rahma.
A zaune ya Tatar da ita tagama saka kaya, Dan k'afar tad'an saki shine taje tayi wanka.
Ki taso su Ammar sunzo.
To. tafad'a atak'aice, haryaje k'ofa takatseshi dafad'in bafa zan iya fitaba.
Cak yatsaya kuma bai juyoba, yakai minti uku ahaka saikuma ya waigo, yawani saki murmushin mugunta danyasan maganar dazaiyi, okey kinaso nad'aukeki Dan kinji Ammar ya ce, " namiki ciki ko?, kinaso su tabbar kenan?.
Ido Rahma ta gwalalo waje ta ce, "nid'in?.
Baki ya ta6e tareda takowa har inda take, taho na d'aukeki nikuma namiki alk'awarin tabbatar musu da hakan.
Matsawa tayi gefe, ta ce, " kabarsa kawai zan iya.
Dariya yayi ya ce, "Yar rainin hankali, yana gama fad'a yafice yana cigaba da dariyarsa.
Rahma tarike baki o ni Rahma dama haka mutumin nan ya ke?, barikiga natashi kafin yaje ya nafkamin wani sharrin.
Haka ta d'ingisa har zuwa falon, ta zauna suka gaisa sunata tsokanarta, itadai bata iya cewa komai sai murmushi, mik'ewa tayi danufi basu ruwa da abin motsa baki, ya ce, " ina zaki?.
Ruwa zan basu tafad'a tana tafiya da d'ingishi.
Sumayya ta ce, "kinga dawo kizauna amarya, bari na d'akko mana aimu ba bak'i bane, Rahma ta ce, " haba daga zuwanku sai asaka ki aiki?.
Karki damu kinji, idanma kika kusa haihuwa nan gidan zan dawo, hannu tasa tarufe fuskarta Dan kunya, Ammar Kuma yayi dariya, Bobo ya ce, "Ashe na huta nikam?.
"Aiko ka huta."
Sumayya ce tamusu komai daya dace Rahma tayi, abincima atsakar falon sukaci, mutuminku sai wani kaffa² yakeyi da Rahma, ita abunma kunya da dariya yaringa bata, idan kukaga kulawar dayake bata saika d'auka haka suke kullum.
Har dare su Ammar suna gida, sai bayan isha'i suka tafi, bobo kuma yatafi d'akko Nawal Dan gobe zasu koma makaranta.
Rahma tad'an daddogara kamar gurguwa tad'an gyara abinda yadace sannan tayi wanka, shirin barci tayi tazauna jiransu.
Bayan wasu 'yan mintuna da zamanta saigashi ya iso da Nawal akafad'a tayi barci.
Saman gadon ya kwantar da ita, Rahma ta ce, " sannu.
Yauwa, tafad'a atak'aice.
Batabi ta kansaba harya sauyama Nawal kayan barci, shima baice mata komaiba yafita, babu dad'ewa saigashi da ruwa da Kofi, abakin gadon ya zauna yaciri magungunanta ya mik'a mata, tuni ta 6ata rai amma babu yanda zatayi haka ta amsa tana matse ido ta shanye, hawaye harsun cika mata ido.
Baki yata6e yayi kamar baiga hawayenba, yad'auki maganin shafawar yad'ago k'afarta yad'ora saman cinyarsa, maganin yashafa mata, ta lumshe idanu danji take kamar yana mata tafiyar tsutsa.
Shikanshi cikin nishad'i yake shafa k'afar, Dan yakai minti 7 yana shafa maganin, saida tad'an janye k'afarta sannan yadakata.
Mik'ewa yayi yamusu sallama yafita.
Rahma ta sauke ajiyar zuciya aranta ta ce, *_"Zaki na Ammi da Appa kafi karfin wargi"._*
_(Nikam Bilyn Abdul kirarin nata yabani dariya, nima zan kiya naringa yima my Abdul d'ina lol.)_
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Yau bobo dakansa yayma Nawal wanka, yaymata shirin makaranta, Rahma kuma tadaure tahad'a musu break da abincin Nawal na makaranta.
Sauri² sukayi break d'in suka fita.
Har harabar gidan Rahma tarakasu, tana musu addu'a, bobo daya tada motar yalek'o kansa yana kallon Rahma, 'Yar gurguwar gidanmu akuladai karkuma akarya d'ayar.
Yana gama fad'a yafigi motar suka fice.
Ita maganar tasama dariya tabata wlhy, afili ta ce, "dama yanama mutane wasa?.
Tayi murmushi tareda shigewa ciki.
---------------------------+
Yana ajiye Nawal a school yanufi office, amma duk saurin dayakeyi saida yatadda mutane na jiransa, ciki harda Alh Sunusi Dala.
Kasancewar kowa yasan waye Alh sunusi dala suka barsa yafara shiga domin ganin Bobo.
Hannu yabashi suka gaisa, sannan ya ce, " Alhaji mike tafe dakai?.
Alh sunusi yasauke ajiyar zuciya, Brr... abunda ke tafe dani babbane kuwa, d'ana 'yan sanda suka kama tun ranar juma'a, kuma sunk'i bamu belinsa wai saisun kaimu kotu, gashi lauyana baya k'asarnan naturashi wajen wasu kayana a k'asar Chaina.
Alh to yanzu ni mikakeso namaka?, bobo yayi tambayar kamar baisan komaiba.
Saboda sunce munemi lauya, nasa abincikamin kwararren lauya shine aka kawoni wajenka, kuma nima idona ya tabbatar mini da hakan.
Shiru Bobo yayi yana karantar Alhaji sunusi, saida yaja minti biyu sannan ya ce, "Alhaji kozan iya ganin takardar sammacin da aka baku?.
A wannan mai sauk'ine aii Brr, Alh sunusi tafad'a yana mik'ama bobo takardar.
Saida yagama karantawa sannan ya ce, " Alhaji gsky akwai Matsala?.
Matsalarmi kuma Brr......?.
Wato wad'anda suke k'arar d'anka sunzo sun sameni tun ranar juma'a, kuma nine lauyansu.
Wani huci Alhaji yasauke, saikuma yay k'ok'arin 6oye 6acin ransa, ya ce, "Brr kataimakeni kamaida musu, ni namaka alk'awarin zan biyaka nikin baninkin d'in abinda suka baka wlhy.
Murmushi bobo yayi, sorry Alhaji hakan bazai yuwuba, duk Wanda yad'aukeni aiki a farko shinake yimawa gsky, inabaka hak'uri akan hakan, saidai nace maka mutari gaba kuma........
Kai k'aramin shashasha!!!! Alhaji sunusi yakatse Bobo a tsawace.
Shima Bobo ya katseshi ta hanyar d'aga masa hannu, Alhaji sauraramin nan office d'inane ba gidan kallon boll ba, ra'ayinane kuma nayi duk abinda nakeso alokacin danakeso gakuma Wanda nakeso, Dan zaman kaina nakeyi bana waniba.....
Kwafa Alhaji sunusi yayi tareda mik'ewa, yanuna Bobo dad'an yatsa yaro yarone, nakula bakasan koni wayeba, amma ina gab da sanar dakai, ni nafika zafin kai Brr...... Dan haka muzuba nidakai.
Mtsowwww muzuba mana Alhaji, nidakai za'a tantance damisar takarda.
Fuuuuuuu alhaji Sunusi yafice, masu tsaronsa suka take masa bayan.
Bobo kuma yaja wani wawan tsaki tareda zama saman kujerarsa.
*_" hummm masu karatu, bobofa yad'ebo ruwan dafa Kansa, kokuwa Alhaji sunusi ne yay gamo da gamonsa?, to kudai biyo d'iyar malam Ibraheema mata agidan Abdus'salam kusha labari."_*
_labarin bobo bagajeren lbr bane, idan na gajarceshi kuma bazakuji dad'iba, Dan haka karku damu da basarwar bobo zai dawo hanyane ♂._
typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
*_Shafin nakune masoyan Bobo, bilyn Abdul d'in ma takuce gaba d'aya, gaisuwa da fatan alkairi su tabbata agareku masoyana, ngd da k'yauna sosai, duk masoyin Bobo ya d'auka wannan shafin nasane, Alkairin ALLAH ya tabbata agareku aduk Inda kuke._*
Luv u mazga mazga ♂ ❤ .
4⃣2⃣
_waye Alh Sunusi dala?._
Alh sunusi dala rik'ak'k'en d'an siyasane, kuma d'an kasuwa Wanda yay zarra akan canjin Dala, matarsa d'aya haj Falmata da yaransu hud'u, Surayya itace babba yanzun haka tayi aure yaranta biyu, sai Haneef shikam babuma auren a tsarinsa, sai Hafeeza da Shareefa suduk 'yammatane.
Alh Sunusi bashida kirki ko kad'an, mutumne mai matuk'ar had'ari, idan yanason Abu zaibi takowace hanya ya sameshi, yana matuk'ar Son Haneef kasancewarsa shikaid'aine d'ansa namiji, sosai Haneef yad'akko halayen mahaifinsa harma yaso zartashi, Dan Haneef tamkar d'an bunsuru yake wajen Neman mata, idan yakwafama mace tota shiga uku, kasancewarsa k'yak'yk'yawa gakuma kud'i saiya zama 'yammatan dakansu suke kawo Kansu gareshi, Ak'alla Haneef yakai shekara 36 amma yak'iyin aure sai iskanci da ta6ara.
Kwata kwata haj Falmata bata k'aunar halin d'an nata, kullum cikin yimasa nasiha take da nuna masa kuskurensa, amma yayi burus da zancen nata acewarsa har yanzu bata wayeba.
Halin Haneef da haj Falmata take k'yamata shine yasa Alh Sunusi yake ganin bata son Haneef d'in kwata², aganinsa tafison yaranta matane.
Itadai kullum cikin nuna fasa ba haka bane take, amma baya ta6a saurarenta, Dan haka tazuba musu ido shida Haneef d'in.
Yaranta mata duk halinta suka biyo, suma basa k'aunar halin babansu da d'an uwan Nasu, amma babu yanda zasuyi saidai addu'a kawai.
Toyanzu mugun halin Haneef yaja masa Shiga tarkon bobo, shikam bobo karanbani yaja masa shiga tarkon mahaifin haneef, Alh Sunusi dala, toko waye keda nasara?.
Saimun cigaba dabin labarin zamu tabbatar.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
K'afar Rahma ta warke, amma tasha bak'i 'yan dubiya, ammi kanta saida tazo dubata, Matansu ya Ishaq ma haka duk sunzo, harsu ya ishaq d'in kansu.
Itakam daga Rahama saitace gara dataji ciwon, Dan kobabu komai acinkin kwana ukun kullum gidan yana cike da dangi asha hira, su khursiyya kuwa kullum suna gidan.
Kwata² tadaina gyarama Bobo d'akinsa, tun ranarma bata sake kallon ko hanyar d'akinba, su khairiyyane suke gyara masa idan sunzo.
Dama bawani shiga harkarsa takeba, to akwana ukunnan ma talura yana matuk'ar busy, Dan kullum yana danna laptop, wani sa'inma saiyakai 10 baidawo gidanba.
Dukda abin na damunta tanason kuma tambayarsa abinda ke faruwa?, amma tana tsoron wulak'ancinsa, Dan haka ta shareshi itama, tanadai tayasa da addu'a samun nasara akan abinda ya burkitashi haka.
+++
A6angaren bobo kam ya ajiye komai gefe, gaba d'ayan hankalinsa yabada akan shari'arsu da Haneef, bak'aramin shiri yayma shari'arba, Dan yayi bincike na musamman akan halayyar haneef, wannan yasa yakeson ceto sauran yara daga gudun fad'awa tarkon Haneef d'in na gaba, Dan ance mai halin bata barin halinsa.
Tun washe garin daya kai Rahma asibiti taga muheebat kuma yaji tasanta, da safe yakar6i address d'in gidansu Idris, tare sukaje shida ya Hamza da ya sulaiman har gidan suka maida muheebat.
Dangin hebba sunyi murna da dawowarta garesu, sunkuma sakama su bobo albarka gameda taimakon dasuka bama yarinyar, saidai sunyi kuka sosai akanjin k'addarar data afka mata.
Nansu ya Hamza sukaita lallashinsu, sukace sukwantar da hankalinsu zasu kwatoma Hibba hak'inta dukda dai budurcinta yatafi bazai dawoba.
Sunji dad'i sosai tareda yimusu k'yak'yk'yawar addu'a.
Bobo ya ce, " zamu tafi, amma ga no. d'ina Indai dawata Matsala sai'a kirani, sannan akan rashin maganar heeba d'in kodama tanada wannan matsalar?.
Eh damacan bata iya magana tun bayan ciwon k'yanda datayi lalurar ta sameta, amma tanajin abinda ake fad'a cewar baba Hamisu mahaifinsu hibba da idris.
ALLAH sarki, amma baba kunta6a d'aukar mataki akan hakan?. Dr sulaiman ya tambaya?.
A'a yaro, gsky bamuta6a yiba kasancewarsa kada muyima ALLAH shishshigi.
Hakane baba amma yana da k'yau anema mata magani, Dan naga zata iya samun lfy, ban yimata aikin bane dama saboda inaso saida izininku, amma insha ALLAH zamu yimata wani aiki komai zai dawo daidai, Dan matsalarta bata cika tsananiba.
To shikenan mungode ALLAH yasaka muku da alkairi, yayma Rayuwarku albarka, ALLAH yajik'an mahaifa.
Ameen suka fad'a suna mik'ewa, sukai musu sallama suka tafi akan sai suhad'u a kotu ranar talata.
*.......................*
Washe gari talata su bobo suka shiga shari'a.
Tun azaman farko hankalin lauyan Haneef yatashi, dan tabbas yasan Bobo kwarone tunda bayau suka fara karawaba, yasan kuma bobo baya tsayama Mara gsky koyaya suke kuwa, komin k'arfin alak'arsu.
Zaman nan nafarko kawai bobo yakawo hujjoji da dama wad'anda suka saka mutane dayawa yadda Haneef ya aikata abinda ake zarginsa dashi, amma dayake alk'ali yaci kud'i saiya d'aga shari'ar sai nan da sati biyu masu zuwa.
Anan lauyan Haneef yanemi Belin haneef amma bobo yace Sam bai yardaba, Alk'ali yasan halin bobo dabin kwakwaf dama kuma bawani shiri sukeba, Dan haka yace k'orafi bai kar6uba, zasucigaba da rik'e Haneef.
Ran Alh Sunusi ya6aci, sai kallon miye haka?, yakema Alk'ali.
Alk'ali kuma yanamasa magana da ido akan subi ahankali.
Duk abinda ke faruwa bobo yana kallonsu, Dan haka yasaki murmushin sa na mugunta, Wanda Ammar kankira da yafi saukar Boom ban tsoro, amma ga Wanda yasan ma'anar murmushin ga bobo kenan.
Suna fitowa daga shari'ar gida bobo yay shirin tafiya, daka gansa Kasan yana cikin farinciki, bud'e motarsa yayi zai shiga Alh Sunusi da masu tsaronsa suka k'araso wajen, bobo yaja sirin farin gilas d'insa k'asan ido Wanda yadawo k'arshen hancinsa ya tsaya.
_( na ce, "anyi shirin rashin arzik'i kenan )?._
Alh Sunusi ya watsama bobo harara, yaro har yanzu kanka yana rawa ko?.
Murmushi bobo yayi, tareda bud'e motar yawatsa kayan hannunsa a sit d'in baya, yarufe murfin sannan yajingina da motar yana kallon Alh Sunusi cikeda basarwa.
Alh wai minayi maka hakane dazafi? kasaka rayuwata agaba.
Yakamata ka lura dawani Abu, ni lauyane mai zaman kansa, banida banbanci dad'an kasuwa, so saina gadamar saida maka hajata, idan banida ra'ayi saikaje gaba kasiya, Alhaji karik'e girmanka, banaso mufara game tare dakai, Dan akwai matsala.
da d'anka nake shari'a bada kaiba, so ka kalli gabanka kada katsaya kallon ruwa kwad'o yayi maka k'afa wlhy.
Yana gama fad'a yashige mota, Alh Sunusi kuma yana zabga ruwan masifa da bala'i, jiyake yak'ara tsanar yaronnan.
Fuuuuu bobo yaja mota tareda bud'ama Alh Sunusi k'ura, by Alhaji sai zama na biyu, bobo yafad'a yana figar motar yabar harabar get d'in.
Kwafa Alhaji Sunusi yayi, tareda fad'in zakasan koni waye yaro.
.×.×.×.×.×.×.×.×.×.×.
Da sallamarsa yashigo falon, saidai shiru babu kowa, yakalli agogon hannunsa 12:15pm Nawal bata dawo school ba, aransa yace to ina momynta?.
K'arar Rahma yajiyo daga d'akinta, da sauri yanufi d'akin, hakan yayi daidai dafitowar Rahma dagudu daga bayi, daga ita sai tawul, jikin bobo tafad'a tana rawar jiki, bashida za6i saina rungumeta, yanda jikinta kerawa kawai ya isa kasan wani abune yabata tsoro.
"K!, miya farune?."
Dadyn Nawal Dan ALLAH kataimaka ka kashemin shi wlhy inajin tsoronsa, kataimakeni plzzz, tafad'a tana kuma ruk'unk'umesa, tamkar zata fasa jikinsa tashige.
Bobo ya girgizata "k kinutsu kifad'amin minene mana?.
d'agowa tayi tana d'an hakki, tuni idanun nan NATA masu kasheshi sun wani sake fitowa, yakula duk yanda yarinyar tashiga rud'ani ko tsoro idonta baya canja kala..... Tunani takatse masa da nuna hanyar bayi.
Hannunta yakama suka nufi bathroom d'in, kinga Nutsu ki nunamin banason shirme, abayansa ta mak'ale, tashiga waige² Neman abinda yatsotata saidai wayam yabar wajen.
Yaja tsaki yarinyarnan ALLAH kinyi mugun rainani, yanzu inbanda raini minene a Bathroom d'innan?.
Wlhy naganshi da idona, saidai idan ya 6oyene, harara ya watsa mata yayo baya zai fita yad'an matseta da bango.
Sukur² taji abayanta, Dan haka tayi saurin turashi takalli bango, wani k'ara takuma fasawa tatafi luuuu zata fad'i.
Da sauri yatareta tafad'o jikinsa, Tawul d'in jikinta ya kwance, yakai dubansa ga abinda tagani, wata 'Yar k'aramar k'adan garuwace, (Tsaka), da alama ta'inda zata fita ma take nema, yamaido kallonsa kan Rahma wadda yakeda tabbacin ta suma, runtse idonsa yayi Yakuma bud'ewa a kan k'irjin Rahma, shima jikin nasa rawa yafarayi, da sauri yakauda kansa yaja tawul d'in ya rufe mata jikinta, d'aukarta yayai cak, jikinsa dukya mutu yafito da ita zuwa kan gado.
Zama yayi yadafe kansa Dan yau surar Rahma ta tsokalishi, babu abinda yake ambata sai _"Hasbinallahu wani'imal wakil"_, tuni idonsa yakad'a yay jajur, zumbur yamik'e yafita kafin yayi aika², kichin yashiga yabud'e firij yakwaso lemon tsami har biyar, jikinsa har rawa yake wajen yankawa, dandanan yamatse ruwan lemon akofi yashanye, ko azababben tsamin baijiba.
Yadire kofin saman tebird'in tsakkiyar kicind'in, yadafe hannayensa biyu tareda runtse idanu, yakai minti10 ahaka sannan yabud'e ido yaja d'aya daga kujerun kicind'in yazauna yana sauke ajiyar zuciya, tamkar jinjirin daya kwana ya wuni baisha nonon mamansaba.
Nanma kwantar da kansa yayi atebir d'in, yad'an jima ahaka sannan yatashi jikin a sanyaye yad'auki ruwa mai sanyi ya kwankwad'a, yakusa shanye gora d'aya kafin yacire yana sauke numfashi, goran ruwan yad'ago ya kalla sannan yafice daga kicin d'in.
d'akin Rahma Yakoma, har yanzu tana nan inda yabarta, yak'arasa gaban gadon ya zauna, yayyafa mata sauran ruwan hannunsa yayi, ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, saikuma tamik'e zumbur ta kwakumeshi tana fad'in dadyn Nawal plzzzz kaje kafiddata wlhy banason ganinshi wayyo ALLAH ummi kizo ki ceceni na bani.........
Ganin yanda take gogamasa jikinta gashi tabi ta k'adandaneshi, idan suka k'ara d'aukar lokaci ahaka bazai iya jurewaba, sai kawai yadaka mata tsawa.
k!!!!!!!, dallah ki nutsu banason shashanci, miye abin tsoro a tsaka?, duk kinbi kin wani rud'a kanki har kina k'ok'arin illatamin lafiyata Mtsooooow, yaja tsaki.
Tuni Rahma tashiga hankalinta, amma har yanzu jikinta rawa yakeyi, harma batasan Tawul d'inta ya k'ara zamewaba.
Gaba d'aya hankalin bobo yakuma tashi, yatsurama k'irjin Rahma ido tamakar zai cinyeta d'anya.
Ganin kallon k'urillar dayake mata yasa itama ta kalli jikinta dantaga miyake kallone haka..... Idanu tawaro tareda jan bedsheet d'in ta k'udun dune jikinta.
Mik'ewa Bobo yayi yayo kanta................
typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
4⃣3⃣
Safna ga sir Hamza canfa yazo, baseera tafad'a tana kallon Safna data rafga tagumi kamar wadda akace ummi zata mutu yau.
Zumbur tamik'e tana fad'in habadai?.
ALLAH kuwa yanzu yashiga office d'insa.
Kinga tashi muje kirakani.
Mubari Zeenat ta iso mana tunda ta ce, "tana hanya.
Mtsooow dallah shareta tashi muje, kinsanfa bakomaine take Goya mana bayaba.
Mik'ewa Baseera tayi tana kakka6e doguwar rigarta, hakane kuma wlhy, kinsan zeenat ya ustaz CE.
Aii saitaji da ustazancin ta ita kad'ai.
Saida suka kwankwasa yabasu izinin shigowa, sannan suka shiga, bayan sun gaidashi baseera ta ce, " Sir mun biyo sawune.
Kallonsu yake cike da mamaki, amma baice komaiba yarubuta musu number Bobo, ya d'ago yana kallonsu, ban tanbayesaba Dan ina mantawane, amma baridai yau nabaku Dan kun fara bani tausayi, dukda bansan mizakuyi da no. d'in *Abdulmaleek!* ba.
Wlhy bawani mugun Abu zamuyi da itaba, kawai zamu sada zumincine.
Girgiza kai kawai ya Hamza yayi, yamik'a musu number, gashi to, nadai baku number sa gama gari tunda bannemi izinin saba bare nabaku number sa mai muhimmanci, amma insha ALLAHU zaku samesa da wannanma.
Mungode sir, ALLAH yak'ara girma.
Amin yafad'a yana binsu da kallo atak'aice, shifa mamaki suke bashi wlhy, koda yake basuda laifi k'anin nasa ya had'u, ga k'yau ga iya wanka, uwa uba kamun kai.
Cigaba yayi da aikin gabansa kawai.
A can kuwa suna fita Safna ta daka tsallen murna tareda rungume Baseera, wayyo k'awata yau na mallaki number Bobona.
Dariya baseera tayi, kinga Laila karki karyani nikam.
Miye kuma laila?, safna tafad'a tana yatsine fuska.
Dariya baseera tayi, laila majnun mana, aigara mufara kiranki Laila kafin bobo yazama majnun.
Dariya Safna tayi tareda Jan hannun Baseera suka nufi class.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Baya Rahma tashiga matsawa tana fad'in inna'lillahi wa'inna ilaihirraji'un.
Ina Bobo baisan tanayibama, kanta kawai yayo tamkar wani zaki maijin yunwa.
Gadon ya hawo yafincikota jikinsa, jikinta sai Rawa yake, ga kukanta ya k'aru, bakinsa da nata ya had'e yashiga wasa da harshenta tamkar yasamu alawar lollipop, agefe kuma hannunsane ke murza ko ina najikinta, Rahma dai sai dukansa da tsungune takeyi, amma baimasan tanayiba, shidai sak'o kawai yake burin isarwa.
Yakai tsawon minti 13 yana Abu d'aya, tuni Rahma tabar kukan tsoro saidai na ceton kai.
Shikam Bobo idonsa yarufe baimasan mi yake aikatawaba, shidai kawai burinsa yake son cikawa, jin hannunsa a k..... Yasata k'ara rikicewa.
Shima da sauri yasaketa danjin pad alamar tana period kenan.
Zubewa yayi agefe sai wani wahalallen numfashi yake saukewa, Rahma tayi saurin sauka daga gadon takoma jikin bango ta mak'ale tana kuka, sai kallon yanda Bobo yake fidda numfashi tamkar zai mutu takeyi, nan take kuma tausayinsa yakamata, jitai hawayenta sun k'aru.
Tanaso taje ta taimakeshi amma tana gudun karya k'ara damk'arta.
Sunkai minti15 ahaka, shi yana cikin wahalar ciwon mara ko magana yakasa mata, itakuma tana cikin tsoro da abinda yamata gakuma halin dayake ciki abin tsoro.
Bobo ya daure dak'ar ya ce, "ki matsemin lemon tsami please zan mut u..........yak'arasa maganar da k'yar danji mararsa da kansa tamkar zasu fashe."
Da gudu tafita zuwa kichin, cikin sauri tamatse lemon tsami wajen takwas, dama tasaka ruwan zafi kad'an awuta, tajefa lifton uku dantaga wani sa'in haka yakecewa ta dafa masa, juyewa tayi akan ruwan lemon tsamin tad'auka tanufi d'akinta yanata turiri.
Da k'ar ya iya tashi yakar6a, dukda zafin da shayin yake dashi bai sauraraba yakafa kai ya shanye kamar yasamu ruwan sanyi.
Mik'amata kofin yayi yakoma yakwanta, jikinsa har Rawa yake, ya ce, " lullu6eni sanyi nakeji, kuma ki kashemin AC.
Duk abinda yace tayi masa da saurinta, sannan takoma gefe tazuba masa ido.
Lumshe idonsa yayi, danda nan zazza6i ya rufeshi, jikinsa yad'auki azababben zafi kuwa.
Rahma sai kallon sa takeyi tana hawaye, yanzu ba kukan abinda yaymata takeyiba, kukan halin dayake cikin takeyi, tarasa yanda zata fassara al'amarin nasa.
Idonsa alumshe yake amma yana kallonta ta k'asan idonsa, saiyaji tama k'ara bashi haushi.
Tunda yake baita6ajin abinda yaji yau ga mace ba sai akan Rahma, shekararsa wajen 5 babu mace, dukda yasan yana cikin buk'atar macen, amma hankalinsa bai ta6a tashiba irin yau, yarasa wace irin mace ce Rahma da jikinta yazame masa tamkar wani magana d'isu, jiyake tamkar zai mutu Dan azaba, amma lemon tsamin data kawo masa yad'an rage masa azabar dayakeji, yamanta tsawon lokacin daya d'auka rabonsa da zazza6i mai zafi kamar haka, yarintse idonsa yana ambatar sunayen ALLAH.
Zuwa wani lokaci kuma sai barci ya saceshi.
Rahma ta sauke ajiyar zuciya, yanzu kuma matsalarta d'aya shine a ina zatayi wanka?, Dan bazata sake shiga bayin taba sai an kashe tsakar can.
Zuciyarta ta ce, "kije d'akin mijinki tunda barci yakeyi.
Aiko tayi na'am da wanga batu, d'akinsa tanufa ta shiga bayinsa tayi wankanta sannan tafito.
Harta shirya yana barci, kichin taje tafara girki, zuwa 2:00pm tagama takuma gyara ko ina, tana falo zaune tana kallon Hausa film Nawal tadawo, direbanta ya d'akkota.
Dagudu tashigo gidan tana kiran momyna! Momyna!!, Rahma tamik'e da sauri Nawal tafad'a jikinta, d'agata tayi tana juyi da ita afalon suna dariya.
Hayaniyarsu ce ta tada Bobo, yamik'e dak'yar Dan Marar tasaki saidai zazza6in shima kad'an, falon yafito, sukam bama su gansaba sunata murnar ganin juna itada Nawal d'inta.
d'an murmushi yayi yashige d'akinsa, ko babu komai yanajin dad'in yanda Rahma take kula masa da yarinyarsa, idan ba fad'a maka akayiba bazaka ta6a cewa ba ita ta haifetaba, saidai kawai idan ka kalli Rahma d'in zakaga yarinyace batakai ta haifi kamar Nawal ba, ammafa duk wata kulawa irin ta uwa akan d'anta Rahma tana k'ok'arin bama Nawal, kuma har zuciyarta takeson yarinyar.
Kama hannunta tayi suka shiga d'akin, tabi gadon da kallon mamaki to ina yaje?, tafad'a azuciyarta, tad'an lek'a bayi daga nesa taga wayam, inaga to yana d'akinsa.
Da wannan tunanin tacirema Nawal kayan makarantar.
‘Nawal!.’
Na'am momy.
Kije d'akin papa kigani barci yakeyi, idan barci yakeyi muje can namiki wanka.
Lah momy bayinmu fa?.
Akwai ojuju aciki ina tsoron shigane.
Kai, momy kema kinajin tsoron Ojuju.
Dariya Rahma tayi ta ce, "kinga kedai jeki duba kidawo.
Tamata hakane Dan tambayar ta tsaya haka.
Da gudu Nawal tafita sai d'akin Papanta.
Fitowarsa kenan daga wanka, yana zaune abakin gado yana shafa mai, Nawal ta shigo aguje tafad'a jikinsa.
Uccch yafad'a yana rungume Nawal d'in, saboda yaji zafi data fad'a jikinsa.
baby bana hanaki guje²n nan bane?.
Sorry papa nadaina.
Yalumshe idanunsa yana kad'a kai, toya School?, harkun dawo?.
Eh papa, tad'ago tana kallonsa, papa kaima bakada lfy kamar momy?.
Kallonta kawai yakeyi yakasa magana, ta girgizashi kaji papa, ajiyar zuciya ya sauke, a'a baby lafiya ta k'alau, itama momy aita warke ko?.
Eh mana ta warke, yanzuma catayi Nazo naduba idan kana barci saitazo tamin wanka a bayinka, wai bayinmu akwai ojuju tanajin tsoronsa.
Papa dama idan mutum yay babba yanajin tsoron ojuju?.
Bobo dake shafa mai yanajin zancen Nawal yayi murmushi, baby Momynki tacika tsaorene, amma zan koya mata yanda zata daina, jekice mata tazo tamiki.
Papa nima zaka koyamin Dan nadaina tsoron ojuju d'in?.
Eh zan koya miki, jeki kirata.
Fita Nawal tayi kiran Rahma.
Momy tahoto kimin.
To Babyna, amma papa fa?, yananan ad'akin.
Atunanin Rahma yana barci Nawal take nufi Dan haka takama hannunta suka fito zuwa d'akin bobo.
Kanta tsaye tashiga d'akin, saikuma tatsaya cak Dan ganin bobo tsaye yana saka ma6alin rigarsa, baya tayi zata koma, batareda ya kalletaba ya ce, " kizo kimata wankan mana.
Rahma tayi k'asa da kai kamar wata munafuka tanufi bayin rik'eda hannun Nawal.
Shikam baki yata6e yad'auki brush yana k'ara kwantar da sajensa bak'i sid'ik, yak'ara fesa turare sannan yafice daga d'akin.
Masallaci yanufa, saida yayo sallah yadawo sannan ya d'auki Jakar aikinsa daga fallo, yamanta a can yabarta, yacire laptop d'insa da wayoyi ya ajiye a tebird'in tsakkiyar falon sannan yakawo jakkar d'aki Yakuma fita.
d'akin Rahma yashiga, yanufi bayimta danya kashe matsa tsakar, dube² yahauyi, can yahangota kwance a bango, tsintsiya yasa yabugota tafad'o, Yakuma bugunta ta mutu, yawanke hannunsa yafito.
Daidai nan Rahma tashigo d'akin itada Nasal.
Batareda ya kalletaba ya ce, "gatacan na kashe saiki fidda.
Tuni hawaye sun cika idon Rahma, kanta ak'asa tace, " Dan ALLAH ka fidda wlhy bazan iyaba.
Eh tunda nazama yaronki ko?.
A'a Dan ALLAH ka taimakeni nidai.
Tausayi tabashi, yalura harga ALLAH tsoron tsaka takeyi, komawa yayi yasharota a faka, yay nufin tsokanar Rahma, danhaka gadan gadan ita yanufa.
Ganin tsaka afaka kuma wajenta yayo tadaka tsalle tareda kwallah k'ara.
Tabashi dariya amma saiya gimtse saida yafita sannan ya shek'e da dariya harda rik'e ciki, mai gadi yana hangensa abin yabashi mamaki Dan yadad'e baiga Bobo yana dariya hakaba, dama dariya mai yawa ba sabon bobo bace, sai Abu yakai matuk'ar tik'ewa yake bashi dariya, murmushinma saiya gadama yakeyi balle dariya.
Komawa yayi ya k'ara wanke hannunsa, sannan Rahma tana shirya Nawal.
Fallo yadawo ya kwanta saman doguwar kujera.
Ya d'auki remote ya canja tasha, babu dad'ewa suka fito suma, Nawal taje ta zauna kusadashi tana fad'in baby kamomin MBC 3 naga cartoon.
Rahma ta ce, "Nawal mikikace?.
Baki tarik'e kamar wata babba, momy yi hak'uri bazan sakeba, Dan ALLAH karkice kin fasa zuwa danifa.
Zanje dake ammafa idan kin daina.
To na daina, papa aidai yanzu bana cemaka baby ko?.
Bobo yakalli Nawal yana kad'a kai, yamaida kallonsa kan Rahma data nufi dinning, murmushi yad'anyi.
Baby ina momy ta ce, " bazataje dakeba indai kina cemin baby.
Nawal takawo bakinta saitin kunnen Bobo ta ce, "catayi bazataje dani makkah da madina ba muga kabarin Manzon ALLAH.
(S,A,W) BOBO yak'arasa mata, to baby yanzu kindaina cemin baby kenan?.
Eh bazan sake fad'aba, momyna ta ce, " nace maka papa.
Jawota yayi jikinsa ya rungume, yabata kiss akumatu, I luv u my baby.
Itama ta ce, "luv u too my papa.
Rahma tak'araso da kuloli ta ajiye a tsakkiyar falon bayan ta janye tebir d'in, saida tagama kawo komai sannan ta ce, "ga abinci.’
Mik'ewa yayi zaune yana satar kallon Rahma, itakam sai duk'ar dakai takeyi, yakula batason had'a ido dashi tun d'azu, ko kallan ma inda yake batayi.
Haka suka zauna cin abincin Wanda Bobo kejin dad'insa.
Yasani lokaci d'aya Rahma taja zuciyarsa rusuna akan burin daya d'auka nayi mata rashin mutunci agidansa harsai tagudu da k'afarta, yafara gudanar da shirinsa ta hanyar fita harkarta, hartayi tsawon kwana 8 a gidan bata ganshiba, amma daga randa yakawo Nawal gidan yaci girkinta sai zuciyarsa tayi sanyi da d'ora alamar ? Akanta.
Abi na biyu shine son datake nunama gudan jininsa Zuh'ra (Nawal), wad'an nan abubuwan suntaka rawar gani wajen ganinta da mutumci da daraja, dukda har yanzu bazaice yana sontaba, ‘Dan Ni'ima ce kawai macen dazaiso aganinsa‚’’ to amma yabama Rahma wani 6angare azuciyarsa kad'an kodan k'aunar Nawal datakeyi.............wringing d'in wayarsane yadawo dashi hayyacinsa, yakalli Screen d'in wayar batareda ya d'aukaba, bak'uwar number yagani.
Sharewa yayi yacigaba da cin abincinsa, aka k'ara kira akaro na biyu, nanma yay burus.
Rahma ce tad'ago ta kallesa danjin ank'ara kiran wayar, cikin sa'a kuwa suka had'a ido, tai saurin janye nata, shikuma yad'an lumshe idanunsa.
Ba'a sake kiran wayarba harsuka kammala cin abincin Rahma tagyara wajen.
Saman kujera yakoma ya zauna, yad'ora kafafunsa saman tebir, yad'auki laptop ya d'ora saman cinyarsa yana Dane dannensa na fama.
Rahma kam homework take koyama Nawal.
Falon yayi shiru kowa yana harkar gabansa sai k'arar TV kawai Dana AC, Wayar d'azuce dai aka k'ara kira.
Wani wawan tsaki Bobo yasaki, afusace yad'auki wayar yana mita, wai miyasa mutane suke San takuramin ne?, ina gidan nawama baza'a barni nahuta da iyalina ba mtsooooow.
Rahma dai tana jinsa bata d'agoba, aranta tace su iyali manya.
Wayar yad'auka yasaka akunnensa batareda yayi maganaba.............
_humm kowaye yakira Bobo ne?._
_muje zuwa masoyan Bobo & Rahma, abinfa yafara zuwa, Dan kunsan dai akwai matsala Safna tagane bobone mijin k'anwarta, kuma Wanda taguda adaliln son Bobo d'in, hum akwaifa cakwakiya wlhy, baridai nabarku karna cikaku da magana ......_ typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
_shafin nakune, gaisuwarma takuce, *Saffiya Galadanci, classic Feedo, & Sajna.* gaisuwa agareku mai tarin yawa da fatan alkairi, ngd sosai da k'auna, nima ina k'aunarku sosai._
ALLAH yabar zuminci ❤❤
4⃣4⃣
Safna ta mik'e zumbir danjin and'aga wayar, saisaita kanta tayi ta ce, "Assalamu alaika.
Saida yaja aji sannan ya ce, " wa'alaikissalam.
Safana ta ce, "ina yini?.
Lfy, ya amsa atak'aice.
Rasa mizata kuma cewa tayi, Dan duk muryarsa ta rikitata, gashi yana amsa mata magana ad'age.
Abinne yafara bashi haushi, amma kasancewar yasan number data kira ta harkar aikinsace saiya dake, yayi tunanin akan aikine.
Yakatse shirun dafad'in mikike buk'atane?.
Uhm....u...u Dan ALLAH kozan iya samunka office gobe idan ALLAH ya kaimu?.
Lumshe idanunsa yayi yabud'e, ya ce, " akanmi kikeson ganina?.
Gabad'aya ta daburce, tarasa mizata fad'amasa, jin takasa magana sai kawai ya yake wayar yay tsaki, gaba d'aya kashe wayar yayi ya wurgata gefensa yana mita.
Duk abinda ke faruwa Rahma tanajinsa, saidai batasan mi ake fad'a ad'ayan 6angarenba.
Aikinsa yacigaba dayi, itama yacigaba da koyama Nawal aikinta na homework.
Acan kuwa safna kaita dafe, takira Baseera danta bata shawara
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*
Safna wai mikikeyine har yanzun baki fitoba?, wannan wane irin yinine har k'arfe 2 ba'a tafiba?.
Ganina fitowa ummi, safna tafad'a tana figar handbag d'inta.
Afalo ta Tatar da ummi tsaye da bak'ar leda ahannu.
Ummi tamik'a mata ledar ga wannan ki kaimata, Safna Dan ALLAH ki kama kanki, kingadai gidan mijin k'anwarkine.
Karki damu ummi, insha ALLAHU babu abinda zai faru wlhy, ainamiki alk'awari zan canja nakoma yanda kikeso.
To ngd ALLAH yayi miki albarka.
Amin ummi na safna tafad'a tana fita.
Hartakai k'ofa saikuma ta waigo, ummi wai miye wannan d'in?, tafad'a tana kallon ledar da ummin tabata.
Karki damu zankirata namata bayani.
Ummi ni baza'a fad'aminba.
A'a lokacinki bai zoba, ai yanzu autana takwace girman, tazama Yaya kinzama k'anwa.
Baki safna tatura tafice, aranta ta ce, "ummi nasan kayan matane aii."
Tana Shiga motarta ta kalli wayarta, hankalinta dukya tashi ganin bai bata amsaba, tunranda takirashi yakashe wayar saita k'yaleshi bata sake kiraba.
Yaudai abin ya dameta shine tatura masa message akan yabata address d'in office d'insa tazo, amma shine har yanzu babu kira babu sak'o.
Ranta duk adagule yake, takirashi sau wajen uku yak'i ya d'aga, hak'ura tayi tatada motar tanufi gidan Rahma.
Dama Dan tanason zuwa wajen bobone ta ce, "ma ummi tanaso yau taje wajen Rahma.
Ummi tayi murna, azatonta Safna tafara hankaline.
“Araina na ce, "koya zata kaya?.”
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Yana zaune a office yaduk'ufa da duba wasu takardu, kallo d'aya zaka masa kagane yana matuk'ar busy, takardun dayake dubawa kuma sunada muhimmanci.
Yana kallon wayarsa tana wringing yay burus da ita, Dan baya k'aunar abinda zai dakatar dashi daga aikin gabansa.
Kwankwasa k'ofar office d'in akayi, sanin sakatariyarsa ce kawai keda wannan damar yasa ya amsa da yes.
Turo k'ofar tayi tashigo, haryanzu bai d'agoba ta had'iye wani yawu tareda tsura masa ido tamkar zata lashesa, sir kayi bak'o.
Waye?, bobo yatanbaya kansa har yanzu yana k'asa.
Cikeda salo ta ce, " bak'on jiyane Alh Sunusi Dala.
Sai yanzu yad'ago, aransa ya ce, "mi mutumin nan yakeso danine, afili kuma ya ce, " kigaya masa bana buk'atar ganinsa, kuma........saikuma yayi shiru ya ce, ''jeki wannan ba aikinki bane.
fita tayi cike da salo.
Batamasan shi tuni yamaida Kansa ga aikinsaba.
Zuwa tayi ta Isar da sak'on oganta ga Alh sunusi, maganar tak'ara Sosa masa rai, amma tunda bobo yak'i bashi had'inkai to lokaci yayi dazai d'auki matakin k'arshe akansa.
Fuuuu yabar wajen, masu gadinsa suka take masa baya.
“na ce, "humm kowane mataki kuma Alh sunusi ke shirin d'auka akan bobo?. ”
+++
Da sauri yad'ago danjin anta6ashi, danufin yin bala'i yad'ago azatonsa Alh sunusi ne yanunama sakatariyarsa fin k'arfi yashigo, ganin Ammar ne saiya sauke ajiyar zuciya tareda yin murmushi.
Ammar ya ce, " mutumina irin wannan fusata haka?, tamkar zaka bigeni.
Ajiyar zuciya Bobo ya sauke kayi hak'uri wlhy nazata wannan shashashanne Alh Sunusi.
Murmushi Ammar yayi ya ce, "munzo shigowa naga fitarsa Ashe na shaida motocin nasa kuwa.
Baki bobo yata6e batareda yayi maganaba.
Saican yace halan yauma kazo kacikamin bakin office da yaranka?.
Hhhhhhh kaima Kasan dolene Dan babu yanda za'ayi subarni nafito ni kad'ai.
Bobo Yakuma ta6e baki, Sakai awahala kenan, haka kawai ace duk Inda mutum zayi ana binsa tamkar wata jela?.
Girman kenan my guy Ammar yafad'a yana dariya.
Ammar ya ce, "mutumina kafa rame wlhy mike damunka?.
Bobo yafitar da huci mai zafi, babu komai Ammar.
To shikenan tunda babu komai yafad'a yana mik'ewa.
Da sauri Bobo yaruk'oshi Dan yasan haushi yaji, yi hak'uri abokina zauna muyi magana.
Ammar yadawo yazauna, wlhy Abdulmaleek kana bani mamaki yanda kake iya 6oyrmin wasu al'amura naka awasu lokutan.
Bobo ya ce, " kayi hak'uri Ammar bawai ina 6oye maka wani Abu baneba, saidai ina ganin wannan sirrin gidanane, dukda nasan babu abunda zan iya 6oye maka arayuwata, kai kad'aine abokina Dana yarda dashi, nasan kaima hakane.
Hakane Bobo amma Dan ALLAH miyasa kake 6oyemin abinda ke damunka?, ina kula dakai tunda nadawo kana cikin damuwar datafi tada akan Rasuwar marigayiya Ni'ima.
Sabodafa damuwar dakake ciki su Appa suka yanke shawarar yimaka Aure, to amma maimakon asamu sauk'i sai kuma damuwarka ta k'aru.
Minene damuwarka Abdulmaleek?, kasanar dani mu nemo mafita.
Bobo yataso daga kwanciyar dayayi ajikin kujera, yadafe tebir d'in gabansa da hannu bibbiyu.
Wato Ammar da ina cikin kewar matatane Dana rasa, dakuma tausayin Nawal na rashin uwa, wannan yasa nak'iyin aure dukda dama Kasan matan bawai suna agabana bane, su Appa sun takura nayi aure harda kai aciki, amma na ce, "muku har yanzu ban shiryaba, an auramin Rahmane saboda bijirewar yayarta akan aurena.
Tundaga randa aka kawo yarinyar gidana ban k'ara yarda ta ganniba saida na d'akko Nawal..
" amma kasan wani abin mamaki?."
Ammar ya girgiza kai.
Koda muka shigo gidan saitamana tarba ta mutunci, ko kad'an bata nuna fushinta akan rashin zuwana garetaba.
Wannan itace jarabawa ta farko data cinye, saikuma yanda take kula da Nawal, wlhy idan baka saniba bazakace ba ita ta haifetaba, abu na uku tsafta, iya girki, saidai akwai shegen muskilanci atareda yarinyar wlhy.
Ammar ya tuntsure da dariya, to aii indai miskilancine babu matsala tunda kaima halinkane.
Harara Bobo ya galla masa malam aii wannan ta fini.
Bobo acigaba da bandamuba kafin ayi auren, amma yanzu ganinta agidan saina shiga wani hali, Dan gsky ina buk'atar mace.
Ammar yagyara zama, to aii ni banga abin damuwa ananba, ba matarka bace?, kawai kanemeta mana.
Ammar baka fahimceni bane, haryanzufa yarinyar k'aramar yarinyace, bata wuce 17 ba, banafa ta kammala secondary, kosu khursiyya sun girmeta da shekara d'aya.
Murmushi Ammar yayi, karka damu abokina aii yaranma sunfi bada Nutsuwa ka gwada kagani kuma.
Amma Dan ALLAH karagema kanka damuwa.
To aiini bakasan wani abuba, tayayama zan tunkareta na nuna mata ga abinda nakeso?, kasanfa banason raini wlhy.
Dariya Ammar yayi ya ce, "Abdulmaleek Aliyu Abdulmaleek hamshak'i, wlhy AAA kana bani dariya, lokuta da dama nakan rasa kai wane irin mutumne?, wlhy da aikin Soja ka dace ba lauyaba, kaifa wani irin murd'ad'd'en mutumne, towai sanda kake gwadama Margayiya Ni'ima soyayaya kirana kayi na koya makane?.
Ajiyar zuciya Bobo ya sauke, bazaka ganebane kawai kadai.
To ganar dani cewar Ammar yana kallon Bobo.
Komawa yayi yalafe jikin kujerar yanad'a lilata ahankali, Ammar ya ce, " my guy kafito kawai anamijinka kaji, kakula da matarka na tabbata Rahma Alherice arayuwarka, kaga kuwa yanda ka canja kak'ara fari, so ka kwantar da hankalinka kayi k'ibama, Rahma k'yak'yk'yawar yarinyace nitsatstsiya ga ilimin addini, wlhy randa na kalli vedio d'in bikinku jinayi inama ina wajen, bak'aramin birgeni tayiba awajen walimarnan.
d'an iska awajen biki kanata tattalin yarinya amma yanzu kazo kana mata muzurai.
Murmushi bobo yayi ya ce, ''kankadai akeji.
Kaima za'aji nakane, amma saikaje hanun Rahma, mik'ewa yayi yana dariya kaga bara nawuce sumayya nacan na jirana harkaja na wuce lokaci.
Bobo daketa murmushi tun d'azun ya harareshi iskanci zakamin kenan?..
A'a babu wani iskanci gsky dai.
Bobo ma ya mik'ewa yayi, nima tafiyar zanyi zanje na d'auki Nawal a school, yau direbanta babu lafiya.
Ayya ALLAH yabashi lfy.
Amin.
Tare suka fito, kowa yashiga motarsa, Ammar da tawagan 'yan sandansa suka tafi, shima Bobo yanufi school d'in su Nawal ya d'auketa sai gida.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Sun shigo gidan falo babu kowa, sai k'amshi da k'arar AC ke tashi, saikuma TV dake kunne amma babu k'ara sosai.
Nawal ta ce, "papa momy na d'aki zomuje, tarik'e masa hannu.
Rahma tana tsaye jikin wardrobe tana d'aukar kaya suka shigo, batayi zaton taredashi sukeba, Cikin farin ciki tad'auki Nawal tana juyi da ita suna dariya, babyn papa da momy ya School.
Momyn lfy.
Masha ALLAH my lovely daughter, muje namiki wanka to kiji dad'i.
"K indai kina tareda Nawal baki ganin kowa sai ita?.
Da sauri ta kalli gurin da maganar take fita, Dan batayi tunanin suna tareba.
Kayi hak'uri basan tare kukeba aii sannu dazuwa, sai matse jikinta takeyi Dan daga ita sai tawul.
Baice komaiba yajuya yafita, amma ya rikice daganin surar Rahma, dukda k'aramar yarinyace amma tanada sura mai k'yawun gani, yanaso yak'ara ganin ainahin Rahma d'in.
Da wannan tunanin yak'arasa d'akinsa, kaya yacire yashiga wanka.
★★★
Bayan wasu 'yan lokuta kowa ya kammala abinda yakeyi, suka had'u afalo sukaci abinci, itadai Rahma kanta ak'asa.
Yakula tunranda yay mata abinnan bata sakewa dashi, kuma bataso su had'a ido, tak'ara birgeshi da samun matsayi a zuciyarsa Dan yana k'aunar mace mai kunya
_(kunya tana d'aya daga cikin tarbiyya ga mace, amma 'yammatanmu na yanzu sun 6arar, aganinsu rashin kunya itace wayewa, gsky anama wayewa bahaguwar fahimta, yakamata mugyara, kunya tana d'aya daga cikin alamomin imanima wlhy, ALLAH yasa mugane.)_
Duk suna falo zaune, Rahma da Nawal suna game da aka had'a da TV, shikam boss yana karanta jarida.
Safna tayi hon maigadi yalek'a danyaga wanene, ganin bak'uwar motace yasa yaytsaye batarda ya bud'eba, cikin haushi Safna talek'o tana masa magana cikeda masifa, aii babu shiri yabud'e mata gate d'in tashiga, guri tasamu tai farking sannan tafito, sai harar mai gadin takeyi, sanye take cikin jan less Riga da siiket sun kamata sosai amma sunyi mata k'yau, ta d'ora siririn farin gyalenta a kafad'a, takalmi da handbag d'inta duk farare, tad'auki sak'on Rahma tanufi k'ofar datake zaton itace zata sadaka da gidan.
Sallama tayi tareda kwankwasa kofar.
Rahma tamik'e da sauri lah kamar muryar aunty Safna nakeji.
Da sauri Bobo yad'ago kai yana kallonta danjin ta ambaci Safna.
K'ofa Rahma tanufa, shikuma ya ta6e baki yaudai zaiga yarinyar datace bata sonsa........... typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
_shafin nakune, gaisuwarma takuce, *Saffiya Galadanci, classic Feedo, & Sajna.* gaisuwa agareku mai tarin yawa da fatan alkairi, ngd sosai da k'auna, nima ina k'aunarku sosai._
ALLAH yabar zuminci ❤❤
4⃣4⃣
Safna ta mik'e zumbir danjin and'aga wayar, saisaita kanta tayi ta ce, "Assalamu alaika.
Saida yaja aji sannan ya ce, " wa'alaikissalam.
Safana ta ce, "ina yini?.
Lfy, ya amsa atak'aice.
Rasa mizata kuma cewa tayi, Dan duk muryarsa ta rikitata, gashi yana amsa mata magana ad'age.
Abinne yafara bashi haushi, amma kasancewar yasan number data kira ta harkar aikinsace saiya dake, yayi tunanin akan aikine.
Yakatse shirun dafad'in mikike buk'atane?.
Uhm....u...u Dan ALLAH kozan iya samunka office gobe idan ALLAH ya kaimu?.
Lumshe idanunsa yayi yabud'e, ya ce, " akanmi kikeson ganina?.
Gabad'aya ta daburce, tarasa mizata fad'amasa, jin takasa magana sai kawai ya yake wayar yay tsaki, gaba d'aya kashe wayar yayi ya wurgata gefensa yana mita.
Duk abinda ke faruwa Rahma tanajinsa, saidai batasan mi ake fad'a ad'ayan 6angarenba.
Aikinsa yacigaba dayi, itama yacigaba da koyama Nawal aikinta na homework.
Acan kuwa safna kaita dafe, takira Baseera danta bata shawara
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*
Safna wai mikikeyine har yanzun baki fitoba?, wannan wane irin yinine har k'arfe 2 ba'a tafiba?.
Ganina fitowa ummi, safna tafad'a tana figar handbag d'inta.
Afalo ta Tatar da ummi tsaye da bak'ar leda ahannu.
Ummi tamik'a mata ledar ga wannan ki kaimata, Safna Dan ALLAH ki kama kanki, kingadai gidan mijin k'anwarkine.
Karki damu ummi, insha ALLAHU babu abinda zai faru wlhy, ainamiki alk'awari zan canja nakoma yanda kikeso.
To ngd ALLAH yayi miki albarka.
Amin ummi na safna tafad'a tana fita.
Hartakai k'ofa saikuma ta waigo, ummi wai miye wannan d'in?, tafad'a tana kallon ledar da ummin tabata.
Karki damu zankirata namata bayani.
Ummi ni baza'a fad'aminba.
A'a lokacinki bai zoba, ai yanzu autana takwace girman, tazama Yaya kinzama k'anwa.
Baki safna tatura tafice, aranta ta ce, "ummi nasan kayan matane aii."
Tana Shiga motarta ta kalli wayarta, hankalinta dukya tashi ganin bai bata amsaba, tunranda takirashi yakashe wayar saita k'yaleshi bata sake kiraba.
Yaudai abin ya dameta shine tatura masa message akan yabata address d'in office d'insa tazo, amma shine har yanzu babu kira babu sak'o.
Ranta duk adagule yake, takirashi sau wajen uku yak'i ya d'aga, hak'ura tayi tatada motar tanufi gidan Rahma.
Dama Dan tanason zuwa wajen bobone ta ce, "ma ummi tanaso yau taje wajen Rahma.
Ummi tayi murna, azatonta Safna tafara hankaline.
“Araina na ce, "koya zata kaya?.”
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Yana zaune a office yaduk'ufa da duba wasu takardu, kallo d'aya zaka masa kagane yana matuk'ar busy, takardun dayake dubawa kuma sunada muhimmanci.
Yana kallon wayarsa tana wringing yay burus da ita, Dan baya k'aunar abinda zai dakatar dashi daga aikin gabansa.
Kwankwasa k'ofar office d'in akayi, sanin sakatariyarsa ce kawai keda wannan damar yasa ya amsa da yes.
Turo k'ofar tayi tashigo, haryanzu bai d'agoba ta had'iye wani yawu tareda tsura masa ido tamkar zata lashesa, sir kayi bak'o.
Waye?, bobo yatanbaya kansa har yanzu yana k'asa.
Cikeda salo ta ce, " bak'on jiyane Alh Sunusi Dala.
Sai yanzu yad'ago, aransa ya ce, "mi mutumin nan yakeso danine, afili kuma ya ce, " kigaya masa bana buk'atar ganinsa, kuma........saikuma yayi shiru ya ce, ''jeki wannan ba aikinki bane.
fita tayi cike da salo.
Batamasan shi tuni yamaida Kansa ga aikinsaba.
Zuwa tayi ta Isar da sak'on oganta ga Alh sunusi, maganar tak'ara Sosa masa rai, amma tunda bobo yak'i bashi had'inkai to lokaci yayi dazai d'auki matakin k'arshe akansa.
Fuuuu yabar wajen, masu gadinsa suka take masa baya.
“na ce, "humm kowane mataki kuma Alh sunusi ke shirin d'auka akan bobo?. ”
+++
Da sauri yad'ago danjin anta6ashi, danufin yin bala'i yad'ago azatonsa Alh sunusi ne yanunama sakatariyarsa fin k'arfi yashigo, ganin Ammar ne saiya sauke ajiyar zuciya tareda yin murmushi.
Ammar ya ce, " mutumina irin wannan fusata haka?, tamkar zaka bigeni.
Ajiyar zuciya Bobo ya sauke kayi hak'uri wlhy nazata wannan shashashanne Alh Sunusi.
Murmushi Ammar yayi ya ce, "munzo shigowa naga fitarsa Ashe na shaida motocin nasa kuwa.
Baki bobo yata6e batareda yayi maganaba.