```The father Of Soldiers```
Story
&
Written
by
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Dedicated to my beloved sisters. 😍
Special thanks to Fadeela Lamido & Sadeeq Abubakar. Wannan littafin sadaukarwa ne a gare ku, jinjina ta musamman.
Proud Of My First Novel💋
Warning banyarda wani yayi amfani da wani sashe na littafina ba, kada a ta6amin komai na littafina in kuma mutun yayi shi da Ubangiji 😇
Sa'annan kada ki karanta Littafin nan in har yakasance lokacin Sallah ne !!! ko kuma lokacin da iyayenki suka saki aiki ko mijinki, in har kikayi hakan wlh ke zata shafa 👌
*Page 1-2*
Hannu tasa ta toshe kunnenta saboda ta gaji da jin masifar da Buzun maigadin yake ta surfa mata, "Ke wannan idan mayya ce kika kama mutun wallahi sai an yi da kyar za a samu magani."
"Na she miki hajiya ba ta nan kullum sai kin zo, ba ki da zuciya ne kare ya lashe ko? Yarinya karama da ke sai taurin kan tsiya, da wasu kwala-kwalan idonki kamar na kwarton mazuru, kina kallon mutane da su ba kunya ko? Kai ga d'an iska ko!"
Dagowa ta yi a hankali tana kallon sa jin cin mutuncin da yake yi mata , idonta ne suka ciko taf da kwalla, kananun labbanta suka soma kyarma, tuni yanayin fuskarta ya canza.
Duk a tunaninsa yarinyar za ta mayar masa da martani saboda ya san yaran zamanin nan ba ka taba su su yi maka shiru, zuba mata ido ya yi kuri yana kallon ta. Gani ya yi tana ja da baya a tunaninsa tafiya za ta yi tabar wurin amma sai ta samu wuri a jikin bangon gidan ta tsugunna tare da kifa kanta a saman guiwowinta sannan ta soma rera kuka mai tsuma zuciya.
Tsayawa ya yi yana kallon ta, da alamun nadama a tattare da shi, har cikin zuciyarsa yake jin bai kyauta mata ba, yana Musulmi da shi ya gaza fahimtar yar karamar yarinyar da ke zarya kullum a bakin gate din gidan, bai taba tambayar kansa dalilin da yasa yarinyar take zuwa wurin ba. Ba irin korar karen da bai yi mata ba amma hakan bai sa gobe taki dawowa ba.
Jiki a sanyaye ya matsa inda take ya tsugunna a gabanta ya ce, "Kai kukan ya isa haka! Dago ka gaya mini mene ke damun ka me yasa kake zuwa kullum kana neman hajiya?"
Dagowa ta yi fuskar nan ta yi jaga-jaga da hawaye ga majina cikin shesshekar kuka ta ce, "Ina zuwa neman hajiya ne saboda na ji an ce tana taimakon 'yammata ta sama masu aikatau ana biyan su kudi."
Jim ya yi yana kallon ta kafin ya ce, "Kai ko mai yasa kake neman aiki karamin yaro da kai gidanku ba manya ne?"
Girgiza kai ta yi, "A'a babu kowa, ba mu da kowa, ni da 'yan uwana ne kuma ba su da lafiya an kwantar da su a asibiti, kuna likita ya ce aiki za a yi musu, ba ni da kudin aikin saboda suna dayawa, shi ne nake so na samu aikin da zan yi ina samun kudin da zan tara a ayi musu aiki kada su mutu su bar ni ni kadai!" Karasa maganar ta yi tare da mayar da kanta kasa tana kuka.
Yanzu ya gane dalilin da yasa yarinyar ta nace sai taga hajiyar, a cikin zuciyarsa ya ce, "Baiwar Allah tana shikin damuwa karama da ita. Oh amma yana da tunani mai kyau!"
Riko hannunta ya yi tare da cewa, "Share hawayen ya isa haka, zan taimaka maka ka ga Hajiya, taso mu je ka zauna saman benchi ka ji."
Mike wa ta yi ta bisa, a tare suka zauna saman bencin, jim suka yi na d'an wani lokaci kafin ya ce, "Ka yi shiru kaji ka daina kuka Allah shi ne gatan bawanSa ko mutun bai da kowa indai ya yi imani da Allah shi ne zai zama gatansa, ka shi gaba da addu'a 'yan uwanka za su samu sauki har ku yi wasa da su."
Murmushi ta yi saboda ta ji dadin maganarsa, hannu ya kai ya dauko ruwan bunun da yake dafawa a saman 'yar butarsa, dama akwai karamin kofi guda biyu da yake amfani da su wurin zuba shayin.
Lekensa ta dinga yi tana kallon 'yar butar karfen da yake dafa shayin da ita, ta burge ta musamman abin da ke cikinta. Kofin ya dauko ya tsiyaya mata a ciki, mika mata ya yi. Hannu biyu ta sa ta karba don rabon ta da ta ci wani abu a cikin ta tun jiya. Sannan shi ma ya zuba wa kansa a d'ayan kofin yana kurba yana ba ta labarin gizo da koki.
Sam ba ta gane me yake cewa, d'an ruwan bunun da ya ba ta ya dauke mata hankali saboda dadinsa musamman daya sanya sugar a ciki, a hankali take kurbarsa, kusan so uku tana shanyewa yana kara mata, a karshe ya ce "Aradun Allah shegen ci ne da kai ga shi harka shanye mini ruwan bununa, idan hajiya ta samo maka aiki ka fara yi sai ka biya kudin shayina."
Murmushi ta saki tana sauraron shi tana mamakin yadda yake suffanta ta da namiji, ga shi shi dai ba makaho ba sarai ya gan ta da kayan mata a jikinta,
har marece ya yi hajiya ba ta dawo ba, da lokacin sallar La'asar ya yi da kansa ya bude musu kofar dake a jikin gate din suka shiga. Ruwa ya debo musu a buta, suka yi alwala tare sannan ya shimfida musu tabarma, shi ya ja su sallar yana gaba tana daga bayansa.
Bayan sun gama , suka ci gaba da zama a saman sallayar yana jan cazbi a hannunsa ita kuma ta shiga tunanin duniya, a haka har magrib ta yi suka sake kabbara sallar, tun kafin su sallame yake jin karar motar hajiya alamar ta iso.
Dadi har cikin ranta yau dai Allah ya yi za ta gana da hajiyar nan, yana sallame sallar da sauri ya tashi ya bude mata kofa, ta shigo da dankareriyar motarta, wucewa ta yi da motar zuwa wajen ajiya. Zuge kofar ya yi sannan ya bi motar hajiyar a baya yana mata kirari kamar yadda ya saba.
Farinciki ya sa ta kasa rufe bakinta sai faman murmushi take yi, ba ta tashi daga samman sallayar ba, zama ta yi tana jiran maigadin ya yi wa hajiyar maganarta. Bude mata motar ya yi ta fito, ma sha Allah irin matan nan ne masu jiki 'yar dumurmur da ita, ta ji hutu fara ce tas amma da alama tana karawa da man bleaching, jikinta na sanye da tsadadden leshi shudi wanda aka yiwa ado da stones, ba karamin kyau ya yi mata ba. Ta kashe daurin kallabinta, hannunta na sanye da diamond rings, haka sarkar wuyanta ta diamond ce, kwalliya ce sama-sama a fuskarta tana da dara-daran idanu ga hanci dogo, tubarkalla, sai jan-baki da ta shafa ja ne.
Cikin girmamawa ya ce, "Barka da isowa hajjaju makkatu!"
Ya mutsa fuska ta yi da alamun gajiya a tare da ita ta ce, "Yawwa Aku sarkin dumi akwai wanda ya zo ba na nan?" Ta yi maganar ne a yayin da take bude kofar motar ta baya, saboda ba ita kadai ta zo ba akwai 'yammatan da ta zo da su daga kyauye.
Maigadin ya amsa mata da cewa "E mutane sun zo sosai amma duk ban rike shunansu ba na dai ce musu ba ki nan kin yi tafiya, sai dai akwai yaro d'aya da ya zo neman ki kullum shai ya zo yau dai na ce mashi ya jira ki dawo."
D'aga idonta ta yi tana hangen 'yar yarinyar da ke sanye da hijab saman sallaya, mayar da idonta ta yi kan 'yammatan da ke zaune cikin motar, ganin ta bude musu motar amma sun ki fitowa, tsaki ta ja tare da cewa, "Kwana za ku yi ne a cikin motar?"
Washe baki su ka yi wata mai surutu a cikinsu ta ce, "Hajiya wallahi dadi motar nan ga wani sanyi da ke ratsa zuciyata kamar kada na fito."
Girgiza kai hajiyar ta yi tare da sakin guntun murmushi ta ce, "Ai irin wannan sanyin da kuke sha na A.C ne kuma in mun shiga ciki ma akwai A.C ko ina."
Cike da jin dadi suka fito daga motar su biyar ne, kai ka ce wadanda aka kwato ne daga bakin kura kayansu sun yi uban squeezing, ga shi riga daban zane daban dankwali daban, takalman kafafuwansu wari da wari ne, ga wata irin kwalliya da suka dambara a fuskarsu, janbaki ya sauka daga saman labbansu har kumatunsu, kamar wasu mayu. Ga black point din da suka diddiga a hancinsu har izuwa goshinsu, sai faman soshe-soshen kai suke.
A haka take dauko su daga kauyen kayau ta gyara su ta sama masu gidanje aiki, a nan take samun kasonta ita ma.
Kallon buzun ta yi ta ce "Ka shigo mini da yarinyar."
Sannan ta kalli 'yammatan ta ce "Mu shiga ciki amma kusa ni duk wacce ta yi mini hauka kauyensu zan mayar da ita ta je can ta ci gaba da tallar fura a bakin kasuwa."
Cikin falo ta shiga da su a daidai lokacin ita ma yarinyar ta biyo su, nan fa suka fara kalle-kalle ganin yadda wurin ya hadu, har kokawa suke yi wurin yunkurin hawa saman lumbutsa-lumtsan kujerun da ke a ciki, dakatar da su ta yi ta hanyar yi musu tsawa, "Kul! Kada wacce ta hau mini saman kujeruna, ga carpet nan shimfide ku zauna, haba ku rinka abu irin na mata mana."
Nutsuwa suka yi kowacce ta samu wuri ta zauna, ita da ma ba iri su ba ce da wayewarta wuri ta samu ta zauna ita kadai, yayin da su kuma suka cunkushe wuri daya kamar kifin gwangwani. Shiga ciki hajiyar ta yi tana kwalama mai aikin ta kira, "Larai, larai! Ina kika shiga haka gida sai ka ce ba kowa?" Karasowa ta yi tana hamma alamun daga barci ta tashi.
"Sannu da dawowa hajiya, wallahi barci ne ya yi awon gaba da ni da ma na sha maganin mura saboda ta takura mini."
Tabe baki ta yi ta ce, "Ni fa ban yarda da ke kullum shan maganin mura anya ba shaye-shaye kika fara ba?" Cikin zolaya ta yi maganar tana kallon ta,
Dariya Larai ta yi ta ce, "Haba hajiya Allah ya tsare ni dayin shaye-shaye tsofai-tsofai da ni."
Murmushi hajajju ta yi "Ya yi kyau! Yanzu dai akwai abinci gidan na zo da yara ne daga kauye."
Girgiza kai larai ta yi, "A'a hajiya sam ban yi tunanin yau za ki dawo ba ai, da na girka muku abinci."
A jiyar zuciya ta saki kafin ta ce, "Koma mene dai laifina ne da ban sanar da ke cewa yau zan dawo ba. Yanzu dai na san muna da bread, ko shayi ne ki hada musu da indomie."
Amsawa ta yi da, "To hajiya!" sannan ta juya ta nufi hanyar kicin din.
Hajiya ta nufi dakinta saboda tana bukatar ta d'an watsa ruwa ta canza kayan jikinta.
Rokon Allah yarinyar take yi a cikin zuciyarta, Allah Ya sa ta samu wannan aikin ko ta samu ta taimaki 'yan uwanta wadanda suke cikin wani mawuciyan hali, muryar d'aya daga cikin 'yammatan nan ta jiyo tana mata magana, "Ke kin iya kunna kallo ki kunna mana mu kalla."
Girgiza kai tayi alamar a'a, ba wai don ba ta iya ba sai don tsoron kada hajajju ta yi mata fada har ma ta kore ta ta hana ta samun aikin. Tana jin su suna cewa, "Karyar banza babu wani ta iya kawai ba ta kunna mana ne 'yar bakin ciki."
Dagowa ta yi ta kalle su harara ta watsa musu ta ce, "E na iya ba zan kunna ba ne ba ku da hannuwa ne ku?" Tsit suka yi ganin yadda ta daure musu fuska sun yi tunanin 'yar shiru-shiru ce, ashe ita ma ta iya fada. Fitowa hajjaju ta yi jikinta sanye da kayan barci, riga da wando ruwan madara, ta daure gashin kanta da ribbom, hannunta rike da waya kirar Infinix Hot 10, suna ganin ta suka gyara zamansu cikin natsuwa.
Wuri ta samu ta zauna a saman 3 seater, yadda za ta ji dadin yi musu magana, yarinyar na jingine jikin 2 seater wadda ke bangaren dama su kuma suna duban ta ta sashen hagu.
A nutse ta soma magana, "Ku na riga da na yi muku bayanin komai ko?" Da'ga kai suka yi alamar e.
Ta ci gaba da cewa, "Yanzu abin da ya rage mini shi ne na koyo muku yadda za ku gudanar da aikin naku don ba zai yi yu ku je gidan mutane a matsayin 'yan aiki ba, a haka kaca-kaca da ku ba tsafta ba. Dole ne kusan yadda za ku tsaftace kanku, da tsaftar muhalli da kuma yadda za ku tsaftace abincin da za ku girka. Kuna bukatar sanin abubuwa sosai daga wajena, kuma insha Allah zan nusar da ku."
Ta mayar da idonta kan yarinyar ta ce "Yammata kin yi shiru ga shi ni ban san ki ba amma yanzu ina son na san me yasa kike nema na ne?"
Bude baki ta yi za ta fara magana amma ganin yadda 'yammatan kauyen nan suka zuba mata ido kamar zomaye, hakan ya sa ta kakare ta kama in ina.
Muryar hajjaju ce ta sa su janye idonsu akanta, "Ku fa matsalarku ke nan sai shegen kallo salon gulma ko?" Sunkuyar da kansu kasa suka yi amma kunnuwansu na bude don su ji me za ta ce?
Cikin sanyin murya ta soma magana, "Da ma na ji an ce kina taimakawa ki sama wa yara aikatau shi ne na zo ni ma ki taimaka ki samo mini don Allah!"
Dafe kai hajju ta yi da hannunta na hagu ta ce "Kash! Da na san wannan ya kawo ki da tun dazu na ce ki koma gida saboda yanzu babu wadanda suka yi mini magana akan na samo musu 'yar aiki, wad'annan 'yammatan da kika gani su ne kawai suka rage na mika su ga wadanda na yiwa alkawarin zan sama musu 'yan aiki amma yanzu babu wani da ya yi mini magana. Ki yi hakuri 'yata!"
Tamkar an d'aga guduma an buga mata a kai haka ta ji, jikinta ya yi mugun sanyi tuni kwalla ta ciko mata a idonta, saboda ba karamin wahala tasha ba, kusan kullum tana fama zaryar zuwa gidan matar neman aiki, tunanowa da ta yi da halin da 'yan uwanta ke ciki ne ya sa ta ji ba za ta iya hakura ba komai zai faru sai dai ya faru, amma ba inda za ta je sai ta samu aikin da za ta samu kudi, saboda ta san ba wanda zai taimake ta ya ba ta kudi haka nan don Allah face ya nemi wani abin daga gare ta.
Tamkar za ta fashe da kuka ta ce, "Don Allah ki taimaki wallahi ko wane irin aiki ne zan iya yin sa. Ki taimaka mini 'yan uwata na kwance asibiti ba ta da lafiya kuma aiki za a yi mata, kudin da doctor ya fada ba mu da su kuma ba mu da wanda zai taimaka mana ni ce kawai nake fafutuka akan yadda zan samu na biya."
Ganin yadda yarinyar ta bi tana rokon ta cikin lallami ya sa ta ji tausayin ta ya shiga ranta, "Ya isa haka, share hawayenki. Nawa likitan ya ce kudin aikin nata?"
"Dubu dari takwas ne." Ta ba ta amsa tana kokarin goge hawayenta. Jinjina kai hajjaju ta yi jin kudin, "Da a ce ina da su da na taimaka da wani abu amma halin da muke ciki yanzu komai tsada hakan yasa kudi ba sa jimawa a wurina. Amma yanzu abin da nake so na sani ina ne gidanku saboda dare ya yi sosai, na mayar dake gid, idan kuma za ki tsaya nan is shike nan in yaso gobe sai ki koma ko?"
Cikin sauri ta ce "Zan tsaya a nan, ba kowa gidan suna asibiti kuma na yi sallama dabsu babzan sake komawa ba har saibna fara biyan kudin aikin, babzan iya jure ganin su cikin mawuyacin hali ba!"
Hajajju ta ce "To shike nan amma gobe zan bincika kuma za mu je asibitin tare saboda ba na daukar yaro ba tare da iyayensa ko wani nasa ya sani ba!"
Yarinyar ta amsa da, "To!"
Larai ce ta shigo dauke da faranti, ta jera sinkin bread guda 3, sai jug mai dauke da tea da kananan kofuna, a jiye masu tayi sannan ta koma ta dauke sauran abin da ta hada musu a kicin.
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Page 3-4
Tun da y'ammatan nan suka ga bread suka gaza samun natsuw, sai kokarin zura hannu suke su dauka, ganin haka yasa ta taso da kanta ta rarraba musu ta bawa kowa nasa, dawowa larai tayi dauke da karamin tray wanda ta baza musu taliyan a ciki ta ajiye masu, zama sukayi suna ta aikin ci, ita dai a hankali take ci tana kallonsu hannu baka hannu kurya suke cunkusa wa a bakin, bakomai yazo mata a ranta ba face y'an uwanta, in ta tuna irin wannan yanayin sai taji komai ya fita ranta.
Bayan sun kammala ci , hajjaju ta kai isu zuwa bedroom din da ta ware domin irinsu in ta dauko su anan suke kwana sannan ta yi masu sallama ta fice, tana fita y'an matan kauyen nan suka haye saman bed din dake ciki kuma shi kadai ne, bin su da kallo tayi ganin yadda suka wawware kafafunsu saboda kar tasamu wuri tace zata hau.
Murmushi tasaki, "Allah sarki rayuwa ni ina ne bazan iya kwana ba, bed is ur problem, Sisters dina sune damuwata,
Cire hijab din dake jikinta tayi, wardrobe din dake manne a bango, ta bude babu wasu kayan kirki a ciki, zannuwan atamfa ne kawai, saka hijab din tayi ciki ta rufe,
toilet din dake ciki ta shiga, komai na ciki a tsaftace yake, fari kal! Gaban mirror ta karasa tana kallon fine face dinta, fanfo ta kunna ta tarba hannuwanta tana wanke fuskanta, bayan ta gama tasa hannu ta cire head din dake kanta, ta yi holding dinsa a hannunta tana kallon doguwar kitson kalabar da akayi mata guda biyu ta zubo tun daga head dinta har zuwa west dinta, tana da Yalwatacciyar sumar kai dark brown colour very smooth ga kwantaccen saken gefen fuska.
Fitowa ta yi daga toilet din, samunsu tayi sai minshari suke ja tamkar raguna, wardrobe din ta sake bude wa daya daga cikin zannuwan da ta gani ciki ta dauko, ta shimfida a kasa, ta kwanta
Washe gari tunda sassafe suka fita, hajajju ce ke driving yayin da yarinyar take a gefenta , sai kalle kallen hanya take ta glass din motor, hajajju ta ce "Har yanzu baki fadamun sunanki ba ! da age dinki yakamata nasani ko"? tayi maganar ne a lokacin da take kokarin juya sitiyarin motar wurin canza hanya tabi titin da zai kai ka har izuwa asibitin.
Murmushi yarinyar tasaki tare da cewa "Sunana SEHRISH amma Oumman mu tana ce mun RISHI , shekarata 17 cif ," jinjina kai hajajju tayi tace "Wow nice name and it really deserves , " cike da jin dadi Sehrish tace "thanks" har suka isa asibitin basu kara magana ,
Sehrish tayi ma hajjaju jagora har izuwa ICU intensive care unit , inda aka kwantar da sisters din nata, lokacin da suka shiga ciki, da gugu wata kyakkyawar yar matashiya ta taso ta rungume sehrish, tsananin mamaki yasa hajajju sakin baki, sai ta dinga ganin tamkar mafarki take yi, tun da Allah ya halicce ta bata taba ganin yara masu shegen kama irin wadannan ba basu da wani banbanci ko miskala zarratin komai nasu iri daya sak , lokaci guda ta rikice takasa gane wacece ma suka zo da ita, wacece sehrish din don ta saje da dayar, hajjaju bata gama mamaki ba sai da taga dayar wadda take kwance saman gadon marasa lafiya ansa mata Oxygen dakyar take jan numfashi gwanin ban tausayi , nan takara rikicewa saboda itama wacce take kwancen Sak kamaninsu ba banbanci hakan na nufi su y'an uku ne kenan.
Kankame ta tayi tana kuka , itama sehrish din kukan takeyi hannunta tasa tana d'an bubbuga bayanta tace "Jahad ki daina kuka hankalina yana kara tashi komai zai tafi dai dai insha Allah, janye jikinta tayi daga nata tace "ina kuka ne ba don kai na ba sai don Husanna dr yace in ba mu fara biyan kudi an mata aiki ba , mutuwa zatayi kuma ynx haka kudin gado ya kare sallamar mu zasuyi ko kudin magani babu ," hankalin Sehrish ba karamin tashi yayi ba,
Hajajju dake tsaye tana kallonsu, jikinta yayi mugun sanyi saboda tsananin tausayi, ita kanta wadda sehrish takira da Jahad akwai wound a goshinta, anyi mata dressing da bandage duk jini a jikin sa , hannunta ma akwai kanula alamun anyi mata karin wani abu jini ko ruwa , a kagare hajajju take da taji labarin wadannan y'an ukun lallai bakaramar wahalar rayuwa suka sha ba.
Muryar Sehrish ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta shiga "Jahad ga hajajju ku gaisa kuma kiyi mata godiya sbd itace zata sama mun aikin da zan fara yi nasamu kudi nabiya ayi maku aiki," matsawa tayi gaban hajjaju tana share hawayenta cikin girmamawa tace" ina kwana hajiya ," murmushi hajajju tasaki tare da dafa kadarta tace "lafiya lou ya jikin naku "? Jahad tace "Alhamdllh ni da sauki husanna ce abun sai kara gaba yake yi don dr yace koda an mata aikin ba lallai ta dawo yadda ake so ba...."
Kuka ne yaci karfinta har takasa karasa maganar , rungumo ta hajjaju tayi a jikinta tana lallashinta " am sorry my daughter stop crying insha Allah everything will be ok , cikin kuka ta amsa da "zandaina mungde ssai ," karasawa Sehrish tayi wurin husanna dake kwance rai hannun Allah , gefen gadon ta zauna tana kallonta idonta cike tab da kwalla tace "Allah ya baki lafiya yar uwata ina jin duk wani irin radadi da kike ji a zuciyarki wanda yayi sanadiyar shigarmu cikin wannan halin bazai taba gamawa da duniya lafiya ba Allah ya isa tsakanin mu dashi mugu azzalumi macuci ..." a karshe ta fashe da kuka ta kwantar da kanta a saman jikinta , har cikin ranta take kukan.
Tsohuwar dake kula dasu ce ta shigo cikin sauri hannunta rike da magunguna da takarbo masu , a nan tasamu hajjaju tsaye ita da jahad tana lallashin ta , jin alamar shigowarta yasa suka jiyo suna kallon , cikin sakin fuska tace "Sannun da zuwa hajjaju ke ce da kanki ," murmushi hajjaju tasaki dama sun son juna da alama , " kwarai kuwa nice gwaggo dama ke ce ke rike da yarannan amma ni ban taba ganinsu ba gsky ," murmushi gwaggo tayi tace "bakya leko mune shiyasa amma sun jima wuri na ni nake kula dasu ," jinjina kai hajjaju tayi tace "hakane amma gwaggo jikokinki ne su"? Goggo ta girgiza kai tare da cewa "a'a Allah ne ya hadani dasu nima labari ne mai tsawo , amma ynx bani da kwanciyar hankalin da zan zauna na baki shi , ki bari saina samu natsu," tana gama fadan hakan ta mika ma Jahad magungunan "karbi nan naki ne dakyar nasamu kudi na siyo su," godiya tayi mata ta karba , a tare suka taka izuwa inda sehrish ke kwance jikin Husanna , cike da nuna tsantsar tausayi hajjaju tace "Allah ya bata lafiya Allah sarki mutum baya sanin halin da duniya take ciki wani sa'in sai ziyarci asibiti nan zai ga marasa lafiya iri iri gwanin bantausayi hakika na tausayawa wannan yarinyar tana cikin hali Allah ya kawo musu sauki da duk marasa lafiyan dake fama da ciwo ," amsawa sukayi da amin , har time din sehrish bata dago da kanta ba , ita kadai tasan yadda take ji aranta.
Hajjaju ta mayar da idonta kan Gwaggo tace "idan ba damuwa muje ki raka ni wurin likitan zanyi magana dashi ,"
fita sukayi a tare , wuri Jahad tasamu ta zauna a chair din dake facing din gadon mara lafiyar, kallonsu takeyi su biyun tana kara jin kaunar y'an uwan nata , taji dadin zuwan rishi har cikin ranta , jajircewarta akan ganin sun samu rayuwar mai kyau yana kara mata ninkin son yar uwarta ta, tazama tamkar uwa agare su , alhalin ita age dinsu daya duk da tare suka zo duniya amma sun tsere wa rishi da mintina a wurin haihuwa , tunani iri iri ke zo mata a ranta runtse idonta tayi hawaye na kwaranyo wa daga idonta
Gabad'ayansu sun shiga cikin yanayi , duk sunyi zurfin tunani , numfashinta suka soma ji da karfi da karfi wani irin sauti mai matukar razanarwa , a firgice sehrish ta dago da kanta cikin rudu ta furta "Subhanallah! jahad husanna ta cire oxygen da aka samata," a rude jahad ta matso kusa da su hannu tasa ta tana kokarin mayar mata roban oxygen din , buge mata hannu tayi tana wani irin gurnani ga zufa sai ke to mata take yi ga wani irin tari da take yi cikin kuka take ambaton "Seh..seh..sehrish ,"
Dakyar sound din ke fita , hakan ya tambatar masu da cewa so take tayi ma Sehrish magana amma takasa , matsawa sehrish tayi kusa da ita tare da sa hannu tana shafa mata gefen fuskarta cikin kuka tace "pls husanna kiyi hkr kinji Allah zai baki lafiya , nasan mai kike ji a zuciyarki, zanyi kokari koda zan rasa raina ne wurin ganin kin samu lfy , wlh sai inda karfina ya kare , ina sonki sosai my sister," gaba dayansu kuka sukeyi , mayar mata da roban oxygen din Husanna tayi , bin ta su kayi da kallo ganin tana kokari kakaro murmushi a fuskarta , wani sabon kukan suka sake fashe wa dashi.
"Yar'uwata kada ki tafi kibarni ni nafiso na mutu a gabanku dan Allah kada ki tafi ," lokacin da sehrish ta tuna da wannan kalami na Husanna sai jikinta ya kara mutuwa lukus , kamar ba kasusuwa a jikinta, zamewa tayi ta zauna kasan tiles din tare da jingina kanta gefen gadon , wasu abubuwa ta dinga tunawa arayuwarsu wanda in har taci gaba da tuna su to tabbas zuciyata zata buga ne! komai ya dawo masu sabo fal , komawa Jahad tayi ta zauna tana shesshekar kuka hada majina a hancinta ,
Hannun husanna taji cikin nata , dayake ta aza hannun nata a saman bed din, ta rike shi gam cikin nata , dagowa sehrish tayi da fuskanta wadda tayi jawur , ga idonta sun kada , fuskarta tayi kwaba kwaba cikin kasalalliyar murya tace "Husanna ki daina zubar da hwayenki nasani abun da ciwo , zafinsa yakai kunar wuta amma ki daure pls , ba irin whalar da bansha ba wurin ganin nasamu kudi an miki aikin nan ke da jahad especially ke , kai karshe ma an kokarin bada kaina nayi amma dana tuna abunda mama ta fada saina gaza , duk da haka ban hkr ba na soma kokarin samun wanda zai siye ni yabani kudi kawai na kawo muku ni natafi amma saina tuna cewa in na tafi wazai kula daku ? duk da nasan akwai Allah shine gatan kowane bawansa ...' muryarta ce tashaqe ta gaza idasa maganartata saboda kululun bakin ciki daya tokare mata makoshinta .
Jahad da ke sauraron maganar yar uwarta su sai taji wani sabon kukan ya balle mata, domin duk wannan gwagwarmayar da Sehrish tayi sam basu sani ba a boye tayi kayanta.
Sun sha kuka kamar ba gobe nima na tayasu kukan duk da bansan takaimaiman tarihin rayuwarsu ba da kuma dalilin kukan nasu.
A haka goggo da hajjaju suka same su gwanin ban tausayi , wayar hajjaju dake cikin yar purse dinta sai ringing take yi don haka tace ma serish ta taso su tafi , cikin kuka ta tashi a hankali take tafiya tana waiwayansu , goggo tace " kada ki damu rishi hajjaju ta biya mana kudin gadon kuma tace zata samu koda bashi ne a fara biyan kudin aikin inyaso daga baya kin fara aikin kin samu sai ki biya,"
Ba karamin dadi sehrish taji ba , haka jahad ma godiya suka shiga yi mata , a karshe tayi masu sallama suka tafi ,
Har a cikin motan kuka takeyi dakyar hajjaju ta lallashe ta tayi shiru....
Time din da suka dawo , larai na kitchen ita da y'an matan kauyen nan tana koya masu wasu abubuwan daya kamata su sani.
A falon suka zauna gaba daya jikinsu a sanyaye, sehrish na zaune kasan carpet jingine da 2 seater , tana sauraron abunda hajjaju zata ce ,
magana ta soma mata "Sehrish ni yanzu bansan ya zanyi dake ba, game da aikin nan m, gashi ni already ina da y'ar aiki kuma gsky ko da ace ban da ita, ba zan iya daukarki sbd kina bukatar kudi masu yawa ni kuma iya salary din da nake biyan larai 10k ne."
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_*✍️
───────────────────────
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Page 5-6
Jin wannan bayanin daga bakin hajajju yasa jikin Sehrish yin sanyi , bata ce mata komai ba sai ma ta ci gaba da wasa da yatsun hannunta. Ci gaba da magana hajajju tayi "abunda za'ae tunda dai naga sisters din naki kuma munyi magana da gwaggo da take kula daku , ynx ki koma ki ci gaba da kula dasu saboda suna bukatarki kafin Allah yasa asamu aikin ,"
Kamar an dasa ta haka tazauna idonta suka ciko da kwalla, kiris take jira ta fashe da kuka , dama bata jima da gama wancan kukan ba
Wayar dake hannun hajajju ce ta soma ringing , picking tayi tare da karawa a kunnan ta tana fadin " Manyan manyan gari ! Abban sojoji ashe kana nan ba'a neman mu , koda yake dama ku hamshakan masu kudinnan ganin ku sai an cike file."
Natsuwa sehrish tayi tana sauraranta , ta lura da yadda hajjaju ke washe baki da alama koma wanene take wayan dashi Babban mutum ne ,
tuna damuwar da take ciki yasa ta daina sauraron wayar tasu ta shiga tunani kala kala a cikin zuciyarta , har hajjajun ta kammala wayar bata sani ba sai da taji tace "Ga samu ga rashi !!" dagowa tayi da idonta tayi tana kallon , hannu hajjaju tasa ta dafe kanta alamar takaici.
Sehrish tace "Hajiya meya faru?" Hajajju tace "Aiki ya samu mai tsoka , jin hka yasa sehrish ta soma murmushi "amma sai dai kash Namiji suke so mai aiki ba mace ce ba !" lokacin da hajajju ta idasa maganar tuni sehrish ta gumtse fuska hankalinta ya tashi.
Hajjaju ta ci gaba da cewa "ina tayaki bakin ciki gsky, sbd kinga mutumin nan daya kira ni ba karamin mai arziki bane , cos they can pay u 50k as your salary after that zasu dauki dukkan responsibilities din ! Ci da shan ki wurin kwana lafiyayye sannan har school zasu iya saka ki ga sutura ya kike gani "?
Takaici ya hana tace komai ga samu ga rashi , ji take kamar ta cire takalmanta ta watsa da gudu saman titi kota rage radadin da take ji a zuciyanta ,
"Sehrish kinyi shiru baki ce komai ba "? ta jima ba tare da ta ce wani abu ba sai da tayi zurfin tunani kafin tace "ZanJe ! Zan yi aikin a matsayin NAMIJIN akan y'an uwana babu abunda bazan iya yi ba don nayi basaja a matsayin namiji wannan abune mai sauki a wurina ,"
In serious matter take mgnan ba tare da jin wani dar a zciyarta ba dagaske take dai , murmushi hajjaju tasaki don ba karamin burgeta tayi ba saboda tana da confidence akan komai da take so , " hmmm sehrish kenan how can u change ur creator frm a girl to a boy i dont think u can act like a male zasu gane ki ne , "
Matsawa tayi kusa da hajiyar tare da rike kafarta tace "Don Allah hajiya ki taimake ni wlh zan iya , indai za'a samu makeup artist din da zai tsara ni ya mayar dani kamar namiji this is a simple thing , kawai amincewarki nake bukata,"
hannu hajjaju tasa ta cirewa Sehrish hannunta data rike mata leg dinta dashi sannan tace "Babbar magana ! tun da nake bantaba yin wannan kasadar ba , natura house maid mace a matsayin namiji , sannan wannan mutumin da kika ji ina magana akan sa wato Abban Sojoji , y'ay'ansa maza goma sha takwas kuma dukkansu sojoji ne masu rike da manyan mukamai , dalilin dayasa yace namiji suke so a matsayin d'an aiki saboda ba yadda za'ai mace ta iya , bai ma dace ba , balle ma yaransa da kwata kwata basa da sauki , zafin rai ga ji da isa , "
Kamar zata yi kuka ji take in har hajajju bata amince mata ba zata iya rasa ranta , cikin kasalalliyar murya tace "Hajiya ki amince mun kawai ae ni nace zan iya wlh idan baki amince ba shinkafar bera zanci kawai na mutu kowa ya huta don bazansu naga mutuwar y'an uwana ba , " zaro ido hajajju tayi jin ta anbaci zata je taci shinkafr bera , kuma dagaske take ba alamar wasa a mgnrta ,
ruko hannunta tayi saboda harta mike zumbur zata figi hanya , "Meya yi zafi haka dawo ki zauna kinji , ni bazanso nayi sanadiyar mutuwar wannan innocent face din ba ," komawa tayi ta zauna tana sauke ajiyar zuciya ,
Shiru suka yi na wani lokaci daga ita har hajajju , jin shirun yayi yawa yasa tace "Hajiya baki ce komai ba am so eargerly to hear frm u ," ta karasa maganan tana kallon ta ,
Wan nan shirun da hajajju tayi sake sake takeyi a cikin zuciyarta "taya zan kai yarinyar nan gidan soldiers a matsayin namiji ! duk ranar da asiri mun ya tonu daga ni har ita kashin mu ya bushe , maganar da sehrish tayi ce ta dawo da ita , " Sehrish i dont know what to do am just comfused ina tsoron hakan fa ,"
"Nima ina goyon bayan yarinyar nan" larai ce tayi maganar shigowarta kenan taji suna tattauna wa , bin ta su kayi da kallo , wuri ta samu ta zauna kafin taci gaba da magana "Wurin samun biyan bukata rai ba abakin komai ya ke ba , tun da har tace zata iya kawai ki amince mata ! saboda ni na taba kallon wani korean film irin haka actress din ciki ta yi shigar namiji ba tare da wani ya gane ta ba kuma tacimma nasara ," jinjina kai hajajju tayi tare da watsa hannayen ta tace "Shikenan Finally i agree tunda har larai ta Jefa miki kuri'a kun rinjaye ni ," dariya sukayi su duka ba karamin dadi sehrish taji ba , ynx hajajju ta yarje mata sauran shirin yarda abun zai kasance ,
Mayar da idon ta kan larai tayi tace "To ynx ta ina zamu fara "? Larai tace "ae magana ta kare kawai mu da muke da Professional makeup artist a hannu ko kin manta da Mariiiya ? murmushi hajajju tasaki tare da cewa " ae Mareeya karshe ce ! Indai wurin canzawa mutun kamanni ne insha Allah gobe zan yi inviting din ta kuma a gobe za'a kammala komai don ya ce mun Jibi suke son mai aikin ta je ,"
Har larai ta bude baki zatayi magana ta jiyo muryar yaran nan dake cikin Kitchen wadanda take koyama aiki , suna kokoyi muryar d'aya daga cikinsu taji tana cewa "Aunty larai gatanan xata wanke gas cooker da ruwa ," da sauri ta mike ta nufi hanyar kitchen din tana cewa "Allah ya wadaran naka ya lalace har waning nayi muku kada ku taba komai amma saboda kan kifi gare ku baku gane komai salon kujama mutane ko !?
Hajajju tace "ke ma da laifinki akan me zaki baro min su a kitchen salon suyi mun barna ," mayar da idon ta tayi kan Sehrish "ki je ki huta time din sallah ma yayi nima bari na tashi ,"
Ta shi tayi ta shiga ciki , wanka tayi ta dauro alwala , ta fito ta shimfida prayer mat tayi sallah , kamar yarda ta sama kullum sai ta daga hannayenta tayi sama da 30mins tana rokon Allah cikin harshen larabci take jero addu'oin ta da bukatanta da damuwarta tana neman Allah ya yaye mata su ,
Bayan tagama ta tube hijabin ta ajiye , sannan ta hau saman bed ta kwanta dama jiya bata samu isasshen bacci ba , don haka lokaci guda bacci ya kwashe ta , tana cikin bacci y'an matan nan suka shigo , sai faman fadin wash Allah suke , koda sukayi arba da ita kwance ta baje gashi ta cire hijabin kan ba head tie, nan fa suka fara santin gashin kanta , ita dae bata son meke wakana ba tadai ji sama sama ana ja mata gashin kai ,
Zama sukayi kamar sun sami television sukai ta kallonta , ba karamin lalata sukayi ma kanta ba duk sun cukuikuye mata gashi yar kalaban nan sun warware mata ita , sun mai da karamar mahaukaciya ,
Nauyin bacci ne ya hana ta farka amma tabbas taji ana shafa mata kai kasa kasa ,
Sai da ana kiran sallan isha sannan ta farka , mika tayi tare da yin hamma , time din sun fita daga cikin bedroom zuciya sauko da legs dinta tayi kasan tiles din tana sauke ajiyar zuciya , kafin ta mike ta shiga toilet , tana cikin yin alwala tayi shafuwan kai ta shafo gashin kan ta mamaki ne ya kamata jin ba kitson dake kanta da sauri ta idasa alwalar ta je gaban mirror ita kanta sai da ta firgita da ganin yadda suka susuce mata gashinta , amma ba wannan bace damuwarta , zullumin kada husanna ta mutu da kuma aikin da zata fara ,
Zama taci gaba da yi a bedroom din , tana tunene tunane , ga yunwa tana ji amma takasa fita ta nema ,
Turo kofan sukayi suka shigo hannunsu dauke da tray abincin aka zuba musu shinkafa da miya ne sun cinye sun rage mata d'an kadan, ajiye mata sukayi suna dariya suka fice , abunda basu sani ba ita kallon Shashashu take masu ,
Bin a bincin tayi da kallon ba don tana jin yunwa ba da bazata ci Ba don sun jagula shi, haka ta zauna ta dinga turawa a baki kamar zatayi kuka , har dare yayi tana zullum abu daya kuma dashi ta kwana,
.......................................ABBAN SOJOJI
.......................Story by MrsBature
..................Part 1
In the morning
Around 10:30am makeup artist dinan ta iso gidan a time din duk sun hallara a falon hajjaju , bayan sun gama gaisawa , ma'reea ta bukaci ganin Sehrish , kwala mata kira hajajju tayi fitow tayi da sauri ta iso inda suke , bin ta da kallo mareeya tayi frm head to toe , sannan tace "Wannan ae mai sauki ne , naga tana da tsayi jiki ne dai babu sosai , abunda za'ae kayan maza za'a samo riga da wando oversize saboda su kara mata girma , sannan wadannan abubuwan , tayi magana tana nuna kirjinta da hannunta " dole a matse su don naga suna da girma ssae tubarkalla , " cikin jin kunya rishi ta dukar da kanta kasa , murmushi larai da hajajju sukayi , su kuwa y'an matan nan dake baje a kasan carpet dama basu da burki washe baki suka shiga yi wato anzo dai dai inda suke so ,
Hajajju tace "ynx me za'a sa a yi tighting dinsu "? Ma'reeya tace "mai sauki ne akwai wani abu da muke amfani dashi na matse tumbi shima zai iya yi ," hankalin rishi ba karamin tashi yayi ba har bata son lokacin da tayi subul da baka ba tace "in suka bace fa ya zanyi ,"? gaba dayansu suka kwashe da dariya mareeya tace "wato kada su bace a rasa nayiwa miji gayu ko ," cikin jin kunya ta dukar da kai , larai tace " dagaskiyar ta fa nono ae yana daya dagacin abunda ke kayatarda maza in suka bace ae ba magana ," ta karasa magana tana dariya , duk kunya ta gama kamata,
Ma'reeya ta ci gaba da magana "Sannan naga kamar tana da tsayin gashi ko,"? hajajju tace "Sehrish cire hijabin mana tagani , hannu tasa ta cire hijabin ta rungume a kirjinta ,
Hada baki sukayi wurin cewa "Tubarkalla masha Allah ," ma'reeya tace " yarinyar kamar balarabiya wurin tsawan gashi, gsky ni kishi nake da wannan gashin naki don haka dama dole indai zakiyi acting a matsayin namiji sai an datse miki shi ya koma guntu kamar nawa dai", nan fa hankalin ta ya tashi saboda tana bala'en son gashin nan nata , kamar zatayi kuka tace "don Allah hajajju karki bari ayimun aski ni inason gashi na ," takarasa maganar tana kallon hajjaju ,
Murmushi hajajju tayi tace " Sehrish ba Aski zata miki ba rage miki shi za'ae , ke da zaki neman kudi wake ta wani gashi , "
Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta , larai tace "Gsky yarinyar nan da ace a matsayin mace zata je aikin nan tsaf zata auren mai gidan," hannu hajiya tasa abaki tace "ke ! tab y'ay'an sa kuwa da sun yi farfesu da namanta sojoji fa akace hmmm !! " dariya sukayi su duka , mareeya ta cigaba da bada bayani "Sannan dole a canza mata suna daga SEHRISH zuwa TUKUR ," a tare suka hada baki wirin cewa "Tukur kuma !"? murmushi ma'reeya tayi tare da jaddada masu maganarta ta " kawai kuwa ! sannan zan sa mata gashin baki irin na maza wanda ake fixing dinsa tare da eyebrows na kanti.
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Page 7-8
Hajajju ta ce "Gashin baki dai. wannan dana nasani ? amma me amfanin hakan "? ma'reeya tace "Wannan wani salo ne kuma ina tabbatar miki da zaiyi aiki , duk da sehrish yarinya ce har a fuskarta amma indai nasa mata gashin baki dana jagira , zata kara suffanta da namiji zata koma kamar d'an daudu kuma dama in kin lura yanayin jikin y'an daudu basa da kiba sai tsayi ,"
Gaba daya sun amince da maganar ma'reeya , shiri na musamman akayi ma Sehrish a washe garin ranar cikin riga ta maza milk colour mai maballai a gaban rigar , sai wani burgujejan wando falazu da aka sama ta kamar kafar agwagwa haka yake pink colour , sun matse mata kirjinta , shafe ta koma kamar babu su , an datse dogon gashin kanta an barmata guntu irin nawa sai suka samu kallabi irin launin trouser din suka nannade mata shi akai kamar rawani , kallabin nada tsayi sai da yar jela ta zubo ta gefe , sai ta koma kamar d'an chali chali , ga gashin bakin da suka sanya mata , ya hau radau ya zauna , haka jagirar da suka samata , ta zauna cuf , duk wani abu na ado na jikin y'a mace babu shi a tattare da ita yanzu ,
Shin koya wannan wasan kwaikwayon zai kasance ? mezai faru ranar da suka gane cewa sehrish macace ba namiji ba ? Kowa yasan ya sojoji suke 👊.
Tunda a sussuba suka kama hanyar zuwa abuja , ita da hajjaju , zuciyarta sai dar dar take yi mata , a natse hajjaju ke driving dinsu , yayin da sehrish ke gefenta , idonta nakan glass din motar , tana kallon yadda suke wuce wurare daban daban , zahiri tana kallon bishiyoyin da suke giftawa na cikin dajijjikan da ke a side road kamar suna gudu da kafafuwansune , a hankali zuciyarta ta sauya mata akalar tunaninta izuwa rayuwarsu ta baya , nan take taji wasu zafafan hawaye na sintiri a idonta , zuciyarta ce ta soma yi mata magana "Sehrish kowane d'an adam yana da irin tasa kaddarar, Allah yana jarabtar bayinsa ne domin ya gwada imaninsu , kiyi kokari ki cinye wannan jarabawar , ki rungumi kaddara a duk yadda tazo miki dama can rutacce ne daga Allah dukkan tsanani yana tare da sauki ! Allah yana sane daku kuma shine gatanku ,"
Hannu tasa tana clearing face dinta saboda bata so hajjaju tagani , tunanin y'an uwanta shine yafi komai tayar mata da hankali , bata san wani gidan mahaukata bane zasu juri daukar nauyin haukan ta ba idan akace yau husanna tarasa ranta , haka abubuwa suka dinga zuwa mata aranta har suka isa garin abuja, wuraren karfe 2:30 na rana ,
Wannan ne karo na farko da ta fara yin tafiya mai nisa irin wannan ,
tunda suka shiga take kallon manya manyen gine gine , har suka iso gidan da zasu wato gidan Abban sojoji , sehrish ta razana da ganin katafaren ginin mai matukar girman gaske da daukar hankali , irin gidan da ta saba gani a cikin mafarki,
Lokaci da idonta suka sauka kan Narka narkan sojojin dake tsare da babban gate din gidan sai da taji gabanta ya fadi rass , bakake ne wulik dasu sanye cikin uniform dinsu , ga bindigu rike a hannunsu , ga wasu guns din soke a west dinsu ,
Wani irin miyau ta hadiye ganin an tsaida motarsu , nan take taji zufa na gangaro mata ta cikin sumar kanta , guda biyu ne suka karaso inda motar tasu take , d'aya ne yasa hannu yayi knocking , hajjaju ta zuge glass din , ita kanta a tsorace take cikin en ena tace "barka dai sannu ku da aiki ," amsa yayi da "yawwa muna bukatar sanin daga ina kke kuma wurin wa kka zo "?
Da sauri hajjau ta dauko wayarta cikin yar purse dinta ta shiga neman number abban, yatsun hannunta sai kakarwa suke , kira d'aya tayi masa ya daga , bayan sun gaisa ta sanar masa da abunda ke faruwa, ya umarce ta da ta basu wayar , mika musu tayi daya daga cikinsu yasa hannu ya karba tare da karawa a kunnansa , juyawa hajjaju tayi tana kallon sehrish wadda tuni ta ta gama tsuma , ta nannade wuri d'aya ta matse jikinta , idon nan sunyi furi furi kamar wadda tayima sarki karya , muryar sojan taji yana cewa "take your phone , u got permission to go in , but firstly we must check the car ," kallon sehrish tayi tare da cewa " mu fita zasu bincika motar ," bude mota sehrish tayi ta fita , itama hajjajun ta fito , suka tsaya suna jiran su gama binciken nasu ,
Matsawa Sehrish tayi kusa da hajiyar tayi kasa kasa da murya tace "hajiya amma nan barrack din sojoji ne ko "? cikin rashin natsuwa hajjaju tace " A'a gida ne na sojoji dae not a barrack ni bana cikin kwanciyar hankalin wadannan sojojin sun firgitani , sai kace wasu masu safarar miyagun kwayoyi za'a tsare mu ! that's why ban cika son zuwa gidannan ba ! ," takarasa maganar tana yatsina fuska ,
Jikin sehrish ya gama yin sanyi , bin jikinta tayi da kallo tasha kayan maza , ga uban burgujejan wandon da tasa kamar zata tashi sama, kara kankame jakar dake hannunta tayi wacce ke kumshe da y'an kayan da hajjaju ta bata kyauta ,
Hatta purse din hajjaju sai da suka bincika , zuciyar sehrish sai bugawa takeyi tunanin ta masu gadi sun kasance haka da ban tsoro ina ga y'ay'an gidan da taji ance they're all soldiers 😒
Muryar sojancce ta ratsa kunnanta "lemme see your bag "! cikin sauri ta mika mar jakan , zazzago kayan ciki yayi kasa yana duddubawa , trousers ne da riguna na maza , da hijabai da ta kudundunesu saboda sallah , bayan ya gama checking dinsu ya dago ya zuba mata ido yana kallonta , nan take taji fitsari ya cika mata mararta , sunnar da kanta tayi kasa , jikinta na rawa , Ji tayi yasa hannunsa ya dankwashi kanta yana cewa "mara kunya kana namiji baka iyasa Cap akan ka , kai ga d'an daudu ko ? sai dai kasa abu na mata ka nannade kai kamar wani limamin masallaci ",
Karasa maganar yyi tare da wurga mata jakar , sannan ya juya ya tafi , hannu tasa ta dafe wurin don taji zafin rankwashinta da yayi mata wannan gabjejan hannun nasa , dole ita ta zukunna ta kwashe kayanta daya zubar a kasa ,
A karshe dai Sun sami shiga ciki , a jiyar zuciya Sehrish tasaki , time dinda motar tasu ta wuce babban gate din ta shantalelen titin da zai kai ka can cikin gidan ,
A hankali take bin ko ina da kallo ta cikin glass din motan , tana kara jaddada haduwar ginin , taga wurare daban daban masu ban sha'awa , sai ta dinga tunanin cewa kodai tabar nigeria ne domin daga inda kasa kafarka cikin gidan kamar ka fita daga 9ja ne 😔
ihu da sowar da taji ne yasa takai idonta wurin , y'an matasan samari ne kyawawan gaske suke wasan football , acikin playing field n gdn , gwanin burgewa tabisu da kallo har sai da suka wuce su ,
A wurin da aka ware na parking space , hajjaju ta tsaida motarsu , wurin cike yake da motocinsu Na gayu ga kuma jibjibgan motocin irin na sojojin man
Waigawa hajjau tayi ta kalle ta tace "sehrish ki natsu dan Allah in mun shiga kada ki jamun , kuma kada ki manta sunan ki tukur daga ynx ," cike da gamsuwa ta masa mata da "Toh"
Fitowa sukayi daga motan suka miki hanyar data zata sada ka da babban falon gidan , tuni sehrish ta raina kanta , tamkar karta taka kasan tiles din take ji saboda wani irin design ne mai daukar ido , duk yadda ka taka saiya bada sauti kwas kwas ,
Komai na cikin living room din mai tsadar gske ne , kana gani kasan bana nan bane , an kawata shi da expensive furnitures , wasu hamshan royal sofa ne aciki , set shida ne a jere , ko da ido ka kallesu kasan zasuyi laushi da dadin zama , duk yawansu basu cike falon ba saboda girmansa ya isa a gina madai madaici gida acikinsa,
Komai da ake bukata acikin falo akwaisa sai da ba tarkacen nan na hauka komai a natse ,
Bin ceiling din tayi da kallo ba irin rufin da tasaba gani bane , wannan na glass , acikinsa akwai light bulbs masu haske wurin ,
Hankalin hajjaju ba karamin kwanciya yayi ba ganin falon tsit ba kowai sai sanyin a.c dake ratsa sassan jikin mutun, dama zullumin ta ace wadannan sojojin na nan ,
Ruko hannun sehrish tayi wadda hankalinta ke kan twin stairs din da tagani wato tagwayen bene guda biyu wadanda zasu kai ka upstairs, tsantsararrun gaske ,
Sehrish tace "hajiya naji tsit ko ba kowa ne ? hajjaju tace "ina ga duk suna wurin aiki , mu samu wuri mu zauna mu jira wata'kil mai aikinsu na nan ,"
Suna kokarin zama suka ji takon takalmi daga left dinsu , karfaffar maca ce irin giantess dinnan , tana da hasken fata , jikinta na sanye da doguwar riga ta atampa har kasa ta kashe daurin d'an kwalinta , tana ganin hajjaju ce ta saki fara'a tana fadin "me nake gani kamar hajjaju makkatin "? murmushi hajjaju tasaki tare da cewa "kwarai kuwa nice AZUMI ashe kina ciki , nayi tunanin ba kowa ciki ne ,"
Karaso wa tayi inda hajjaju take tayi hugging dinta tana cewa " I really missed u alot hajjaju kin boye mana nayi expecting din bakya kasar ne ," sakin juna sukayi hajjaju tana dariya tace "Ina nan mana ina zani an gaya miki ynx barin kasar nan sauki ne yadda komai ke kara farashi , yar dubai dinnan danake zuwa kamar hauka ynx nadaina saboda rashin kudi ,"
Murmushi azmi tasaki , tare da nuna masu wurin zama tace "bismillah ku zauna bari na shiga na kawo muku abin sha , firar zata fi dadi idan kuka jika makoshinku ,
tana gama fadan hakan tajuya ta nufi hanyar da zata kai ka kitchen dinsu , zama sukayi a tare saman 3 seater , har lokacin sehrish na makale da yar jakarta a kirjinta , sai karewa falon kallo takeyi tana jinjina kyansa , wai itace zata rayu a cikin katafaren gidannan , wayyo dadi boye farin cikinta kawai take yi , ta wani bangaren kuwa hankalinta a tashe yake , saboda batasan ya rayuwarta zata kasance ba a matsayinta na yar basaja , matsayin namiji a gidan sojoji ,
Dawowa azumi tayi hannunta dauke da tray , plate ne mai dauke da snacks , sai 2 cups da jug , a jiye su tayi a sman table sannan ta janyo shi izuwa gabansu ta ajiye ,
Koma tayi tazauna tana murmushi , Sehrish kuwa sai kallon matar take yi har taji ta burgeta saboda tana son mutum mai fara'a ,
Lemu ne a cikin jug din zuba musu hajjaju tayi ta mika ma sehrish , cikin sauri ta karba dama kishi take ji , kurbarsa tayi wani irin sanyi ya ratsa ta ga dadin gaske ,
Azumi ta bi ta da kallo cikin mamaki tace "in ce ko wannan ne d'an aikin da akace za'a kawo mana"? hajjaju ta danyi guntun murmushi tace "eh shine sunan shi tukur kwararre ne wurin iya sarrafa abinci ," saboda jin karyar da hajjaju ta shirgo akanta yasa ta kusa fetsar da lemun da takurba a bakinta , abunda ya kusa sata ta shake shine da ta ce kwararrene wurin iya sarrafa abincin shin yaushe ta son da wannan ?
Sauraron hajjaju ta ci gaba dayi jin tana introducing dinta a wurin azumi " yaro ne mai matukar basira ga wayau , zakiji dadin yin aiki dashi ," takarsa maganar tare da ajiye cup din dake a hannunta saman table din gabanta , sannan ta kalli sehrish tace "tukur wannan itace azumi , itama y'ar aiki ce a gidannan amma taji ssae tana kula da yaran gidan hakan yasa ta zama tamkar uwa agaresu , ina fata zakuji dadin yin aiki da juna ,"
Dakyar sehrish ta kakaro murmushin dole tace "Insha Allah hajiya ,"
Ita kadai tasan halin da ta shiga , wannan zaman da tayi ji ta , kamar ta dosa na ass dinta a saman wuta , saboda tsabagen tsoro , A ranta sai maimaita kalmar 'yaya goma sha takwas kuma duk sojoji take yi ,
Azumi ta janye idonta daga kan sehrish (tukur) ta mayar da idonta kan hajjaju tare da cewa "am inaso na tambaye ki tundazu maganar ke shigemin meyasa kika daina leko mu bayan ina da tabbacin cewa kina zuwa abuja zuwane kawae ke baki yi ,"
Murmushi hajjaju tayi tare da yin yar dariya tace "ai dole zuwa gidannan ko jaraba ! oh kin manta Abunda ya faru last time dana zo ko ? Ina wannan BABBAN YAYAN nan nasu wani mai shegen kyau tubarkalla kamar d'an sarkin aljanu mai kirar zakunan nan ," dariya azumi tayi tare da cewa "wai wa kike nufi cikinsu , kinsan suna dayawa , akwai major , akwai Captain ga janar , akwai Marshall ga kuma Canal da sauransu , kowa da sunan da ake kiransa " takarasa maganar tana kallonta
Sarai tasan wa take nufi amma tafiso taci gaba da zuzutashi don hajjaju ta iya bada labari ,
taci gaba da cewa "oho nidai nasan shi kadai suke ce ma babban yaya , ina gaya miki last dana zo , lokacin nazo dubiyar wannan younger bro dinnasu mai asthma wanda aka fidda kasar waje akayi masa aikin a kirjinsa , " azmi tace "oh nagane junaid kike nufi ae suna waje suna buga ball ynx yaji sauki Alhmdllh ,"
Hajjajun ta ci gaba da cewa "ina fadamiki daga zuwa abun arziki , wlh ina shigowa falon nan ni bansan meya faru ba , nasame shi da y'an uwannan nasa sae faman rirrike shi sukeyi sai huci yake yi just like a hungry lion from the bush gaba daya yayi watsi dasu kasa , ya daga dining table yayi wurgi dashi , gabana ya fadi rass banyi aune ba naji yace "don ubanki kama hanya ki fice, ashe ya ganni "
Wallahi a tsorace a fujajen nabar gidan don tsabagen rudi , da kafa nakama hanyar fita babban gate din saida wani soja cikin security din gidan nan yace mun hajiya kin manta motarki , sannan fa natuna jiki na rawa nakoma nadauko,"
Tun kafin ta idasa labarin azumi da sehrish suke ta faman tikar dariya , kamar cikinsu zai kulle , ita kanta hajjajun dariyar take yi ,
dakyar azumi ta tsaida dariyarta tace
"Hmmm sai ynx nagane wa kike nufi , ai da kinsani ba ki daina kawo mana ziyara ba domin shi ba sojan nigeria bane , US ARMY ne ba a kasar nan yake ba yna dai zuwa sometimes in yasamu hutun aiki ,"
Hajjaju tace "bazaki gane ba ne , yadda na tsorata , ai ko ba don shi ba , wadannan tantiran na gidannan marasa jin magana..." Azumi ta katse mata maganarta ta da cewa "twins kike nufi , tom & jerry suna nan haryanzu basu canza ba sai ma abunda yayi gaba ",
Hajjaju tace "ehen su nake nufi",
Ci gaba da fira sukayi , yayin da hankalin sehrish ke atashe , tunda taji sun ambaci babban yaya sai taji tsoransa har ya shiga ranta , sam ta nemi natsuwarta ta rasa ,
Sun jima suna fira har time din ba wanda yashigo daga cikin soldiers din , har hajjaju tayi shirin tafiya , bayan ta yiwa azumi bayanin akan nemawa tukur wato sehrish alfarmar in tayi one month da fara aiki ta taimaka a ansar mata kudin wata uku a dunkule ,
A tare suka fita har bakin motar ta , sannan suka tsaya suna idasa takarkare zancen
"meyasa bazaki jira abban ba yazo? koya yi miki sallamarki ne "? hajjaju tace "ae indai abba ne bani da matsala dashi nasan zanji alert kinsan hannunsa a bude yake , kuma Abunda yasa nake sauri zan shiga gwarinpa ne gidan wata goggo na "
Murmushi azumi tayi tana kallonta,
Ita ma murmushin tayi mata , harta bude mota zata shiga tasake juyo wa ta kalli azmi tace "pls game da tukur na baki amanarsa , ki kula da duk wani motsi nasa pls ,"
Azmi tace "in dai nice u don't ave to worry about it I will look after him insha Allah ," sallama sukayi hajjaju ta shige cikin motarta ta ja ta ,
Bayan fitarsu sehrish ta zabga uban tagumi tana jin kewar kasancewarta ita kadai a wannan hamshakin gidan da batasan kowa a cikinsa ba , gashi tazo a matsayin namiji , duk in ta tuna wannan hankalinta tashi yake , abu dayane ke kara mata karfin guiwa , y'an uwanta in ta tuna su sai taji ba irin kasadar da bazata iya shiga ba ,
Dawowa ciki azumi tayi fuskarta a sake tace da sehrish " tashi mu shiga ciki na nuna mka bedroom din ka , in ka huta zuwa anjima before magrib zamu shiga kitchen",
Sehrish ta amsa da toh tare da mike wa tabi bayan azmi , suka shiga ciki tayi mamakin bedroom din da azmi ta nuna mata a matsayin nata na yar aiki , wannan koda amayarce tasamu wannan falillahil hamdu , ba tarkace a ciki , single bed ne , ga beside drawer mai dauke da bedside lamp a samanta ga wardrobe madai-daiciya ta manne jikin bango , ga wadatattun curtains a kowane window , komai na cikin bedroom din brown color be banda labulayen da suka kasance milk colour , da zanen gadon ,
Ba abunda ya kara burgeta sai dressing mirriow din da tagani , duk da ba cosmetics a samansa , madubin yayi mata da yar chair din dake gabansa ,
Murmushi azumi tayi ganin yadda yaron yake ta farin ciki don haka tace "komai yayi ko "? da sauri ta amsa da "eh hajiya harma yayi yawa "
Dariya azumi tayi jin yace harma yayi yawa ,
"Ynx dai ni zan shiga ciki , ka zauna ka huta , sannan akwai bedsheets a cikin wardrobe din nan , in zaka canza saika dauka ," tana gama fadan hakan ta fice ,
Kamar jira takeyi azumi ta fita tahau ihu tana tsalle , kafin ta tsagaita da haukan nata ta shiga bathroom din dake ciki ,
Nan fa ta soma wani sabon kallon , ko a mafarki bata taba tunanin zata mallaki irin wannan tsantsararren bathroom dinba mai kama da bedroom saboda haduwarsa ,
Dakyar ta samu natsuwa , ta dauro alwala tafito , a cikin wardrobe din ta samu prayer mat (sallaya) ta dauko ta shimfida , ta kabbara sallah , duka ta hada tayi zuhr da isha saboda batasamu damar yi ba a kan hanya , gashi ynx ankira isha'e shiyasa ta hadesu duka tayi ,
Bayan ta idasa sallar , ta daga hannayenta sama tana addu'ei at the end ta fashe da kuka , Sbd tuna wa da halin da y'an uwanta ke ciki , magana ta soma yi cikin kuka " har ynx na gaza yarda cewa nice zan yi rayuwa a cikin wannan daular ba tare da y'an uwana ba , taya zanji ddin rayuwata batare dasu ba , ni ina nan sukuma suna asibiti cikin wani hali , Allah sarki rayuwa ! bazan taba yafe ma wanda yayi silar shigarmu cikin wannan tashin hankalin ba , Ya Allah ka hana sa jin dadin duniyar nan gaba daya , Ya Allah ka kaskantar da rayuwarsa kamar yarda yayima ta mu....." kuka ne yaci karfinta har ta kifa kanta saman sallayar tana cewa "I will never forgive u in my life and I will neva forgt u ! i must take revenge koda ace nikadai ce na rageda zan yafe maka ka shiga aljanna to tabbas bazaka taba shigar ta ba.
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Page 9-10
Bata tashi daga saman sallayar ba har aka kira Magriba tana tunanin abu daya, sai da ta kammala sallar sannan ta nad'e carpet din ta turasa cikin wardrobe , tare da hijab din duka.
tsayawa tayi gaban dressing mirror tana kallon kanta a cikinsa , sak namiji ba wanda zai gane mace ce sai yanayinta ya koma kamar d'an daudu , hannu tasa tare da shafa gashin bakin da ma'reeya ta sanya mata , murmushi ta d'an saki a ranta ta ce "Sehrish ke nan dramatic girl."
Kara kimtsa kanta tayi saboda azmi tace mata akwai aiki a kitchen da zasuyi, sai da ta fara rufe kofar dakin gudun kada Azumi ta same ta tana canza kaya , ta gane cewa maca ce ita ,
Cire kayan jikinta ta yi , ta maida su cikin bag dinta , sannan ta dauko wasu riga da wandon , ta rige a hands sinta gaban mirror din ta koma ta tsaya tana kallon jikinta , ziririn pant ne a ajikinta , takai hannu tasha fa flat tommy dinta , wanda yake a dam'e kaman bata cin abinci saboda shafewarsa ,
Mayar da hannun tayi saman boobs dinta wadanda ta matse su gam , da abun matse belly , har cikin ranta ba taso hakan ba tana son abunta ssae , amma ba yadda zatayi duk cikin aiki ne ,
ga hairs dinta da aka maida mata shi guntu , amma hakan bai dame ta saboda a iya sanin ta in aka aske mata gashi irin hakan cikin one month zai koma yadda ya ke tsayinsa ma harya karu ,
Jin alamar tafiyar mutun kamar bedroom ta ake nufowa shine ysa ta yin saurin , zura dogon wandon tare da rigar sa , tayi gaggawa gyara daurin da m'reeya ta yi mata , mai kamar rawani ,
Kwan ! kwan !kwan taji an knocking , cikin sauri ta karasa ta bude kopan azmi ce tsaye fuskanta da murmushi tace "tukur ina fata ka shirya sbd ynx zamuje na nuna maka yarda abun aikin yake ,"
Cikin girmamawa sehrish tace "toh hajiya ,"
Azmi tayi mata wani irin kallo har gaban sehrish ya tashi a tunaninta ta gano lagwanta , amma sai taji tace "stop calling me hajiya , my name is azmi call me by my name , cos we re d same , am a house maid just like u ,"
taka rasa mgnr tare da fice wa tana cewa "follow me" rishi ta bi bayanta tana d'an murmushi ,
Kitchen suka shiga amma sehrish ta gaza gane a ina suke , haduwar wurin ce ta rikitar da ita , an kawata komai na kitchen din da dukkannin abubuwan da akeso,
Sam ta manta aiki ya kawosu sai faman kalle-kalle take yi , sai da taji muryar azmi a kunnanta sannan ta dawo dai dai
"tukur ynx bamu da enough time , we'll make a dinner now in yaso zuwa tomorrow i will explain everything to u , Especially zama da samarin gidan nan darasi ne me zaman kansa duk zan koya maka ,"
sehrish sai take ganin maganar azmi kamar shiriri tace , ynx har akwai mutumin da za ace sai an koyi darasin zama dashi ?
haka suka fara aiki , azmi ce ke yin girkin , yayin da tabarma sehrish ferar dankalin turawa , ga yankan albasa , acewarta tafara da karamin aiki ,
Suna cikin aiki sehrish tafara jiyo karar shigowar motoci , rass taji gabanta ya fadi , da jiniya motocin ke shigowa ,
"Hmmmm wannan alama ce mai nuna cewa masu gidan sun dawo " a cewar azmi ,
Zuciyar sehrish sai harbawa take yi saboda tsananin firgicin da wa zata fara cin karo ,
"Ka'ida ne daga sun shigo babban falo zasu fara kwalamin kIra ka saurara kaji ," azumi ta fada tana murmushi ,
Hannun sehrish sai kakarwa suke yi ,
ita dai baza ta iya tantance muryar mutun nawa bace amma taji sauti iri iri
"Azumi ! Azmi !! Azam zam !!!" da karfi suke kwala mata kiran without any respect , cikin sauri azmi ta fice tana ce ma sehrish "pls ka kula da girkin am coming back now ,"
Sehrish ta amsa da toh , daga inda take tana iya hangosu saboda kitchen din irin model design dinnan ne wanda ba kopar shiga gare sa a bude yake bata iya identifying faces dinsu ,
Hankali a tashe azmi takarasa wurunsu tana fadin "welcome back Sirs ," ko arziki amsa bata samu ba sai complaining da suka soma yi mata, "Ina fata angyara min bedroom dina don bansan kazan ta ! in ma kinsan baki gyara ba let me know ," daya daga cikinsu ne yayi wannan maganar ,
matsawa tayi kusa dana gefensa don taji shi mai zaice , hannu ysa yana shafa ciknsa yace "Ni matsala ta abunda zansa ma cikina pls kafin na shiga ciki nayi bath na tarar da abinci jere saman dining table if not kinsan sauran ,"
matsawa azmi ta sake yi kusa dana gefensa dayake duk suna a jere kusansu takwas,
" Na fadamiki Injin wanki na ya samu matsala dazu da safe ga shi na tara kayan dauda , gajerun wanduna na ma duk sunyi dirty dafatan kin wanke mun su ,"
Haka ta dinga sauraransu ba wanda baiyi magana ba acikinsu , bayan ta gama sauraransu one by one tace " Komai da kuka lissafamin na kammala sa , abinci ne kawai shima ynx zan idasa ,"
Kama hanya suka yi kowa ya wuce bedroom dinsa , wasu na upstairs wasu na a downstairs,
Babu abunda ya burge sehrish sai kakin sojojin dake jikinsu , abunka ga handsome guys ga tsawo ga hadaddiyar sura sai abun ya bada citta 😘
tunanin ta soma yi a ranta "oh ni ko wanene babban yaya acikinsu , koda yake naji azmi tace ba sojan nigeria bane U.S ARMY ne , zanso nagansa daga ji ya hadu yadda hajjaju ke zuzu tashi ,"
takarasa tunanin tana murmushi ita kadai abunta , shigowa azumi tayi tana fadin "maza tukur a shirya abinci a dining before su fito, ai ina ji girkin ya isa ya kammalu ,"
Wasu hadaddun kuloli ta dauko daga kitchen cabinet kamar ranar aka budesu daga kwalinsu tsantsar kyansu kamar ba abinci za'a zuba ciki ba , saboda yadda murfinsu ke glowing har face dinka zaka iya gani aciki just like mirror ,
A wani faffadan tray ta shirya komai ciki , ta mika wa sehrish azuwan taje ta fara shiryasu a dining ,
Gaban ta na faduwa ta karba tsoranta da wa zata fara cin karo a cikinsu , time din da ta isa dining room din , mutun d'aya ta samu zaune shi ya rigasu fitowa jikinsa na sanye da white tshirt da black short , bai lura da ita sai da yaji cool voice dinta ta sauka a kunnan sa " sannu da hutawa " a natse ya dago yana kallonta ,
lokacin da suka hada ido kara ware idonta tayi ganin irin kyawunsa , dan matashi ne ba zai wuce 18years ba , a tunaninsa zai ga mace amma sai ya ga namiji tabbas shi muryar mace ya ji mai dadin gaske a kunnan sa ,
Wani kayataccen murmushi ya sakar mata , wanda yasa ta shiga yanayi , cool voice dinsa ce ta ratsa ta "am nace ko sabon mai aikin da akace za'a kawo mana ne?daga masa kai tayi alamar eh ,
Jinjina kansa yayi tare da d'an tabe small lips dinsa ,
Soma jera abincin tayi , bayan ta gama ta koma ta dauko sauran abubuwan da bata kawo ba ,
Allah Allah take ta kammala jera abincin kafin sauran su karaso , muryarsa ce ta kara katse ta " chicken pepper soup din nan zaka zuba mun ka hadamin da irish cikin plate din ," ta amsa toh kamar wata munafuka haka take sunnar dakai , Ji take kamr asirinta zai to nu ,
Plate ta zaro daga cikin set na filattan da takawo , bude daya daga dana cikin kulolin tayi , nan da nan kamshi ya gauraye wurin , saving spoon ta dauko ta soma zuba kazar a cikin plate din , sai faman hadiye miyau take yi , ga hannun ta dake kakarwa ga wani gumi dake sauka daga gefen sajenta ,
Kammala zuba kazar tayi sannan ta bude kular da ke dauke da irish ta zuba masa k'adan muryarsa ta sake ji "yayi mun k'adan ka take mun plate din "
cika masa plate din tayi dam sannan ta tura masa gabansa , cikin sauri ta kama hanya zata koma ciki "spoon din fa ko so kake na dauka da kaina ne sannan a gidan ku haka ake ba mutun abinci ba tare da drinks ba '? har zuciyarta taji wannan maganar a tunanin zaiyi saukin kai ganin da farko yayi mata murmushi ,
lallai ta jinjina wa izzarsa , ga cokulan kusa da shi ga kuma drinks din da ta jera amma yafi karfin yasa hannu ya dauka sai da ita ta mika masa ,
guntun murmushi tasaki koma tayi ta mika masa cokalin sannan ta zuba masa lemu a cikin glass cup ta mika masa , yamutsa fuska yayi tare da sa hannu ya karba yana cewa " gsky kana bukatar training don da ace babban yaya ko captain kayima haka da ka gane barno gabas take don sai kayi tsallan kwad'i ,"
Ya karasa maganar yana kurban lemun da ta mika masa , a wani irin yanayi sehrish ta juya wannan ne karo na biyu da taji an ambaci BABBAN YAYA , hakan nakara sa mata tsoransa a zuciyarsa ,
Komawa tayi kitchen ta samu azumi tana gyara wuraren da suka bata , jin shigowarta yasa ta dagowa tare da cewa "subhanallah meyasa ka dawo ka kammala saving dinsu ne "?
"A'a naga basu fito bane shiyasa na tafo ," tayi maganar fuska a yamutse sbd rashin natsuwa da take ciki , azumi tace "maza ka koma karka ja mun bala'i , bakasan halin mazan gidannan ba ,"
Ba haka sehrish taso ba , jiki a sanyaye ta kama hanyar komawa dining room din , hannu azumi tasa ta rike habarta alamun mamaki tace "lallai dole na mike tsaye akan yaron nan ! yana abu kamar mace anya wannan ba dan daudu bane ? ta tambayi kanta ,
Tunkan takarasa ta ke hangensu , a lokacin suke karasawa saman dining din kowannen su yaja kujera yazauna , Kasancewar table din dogone mai mazaunin mutum goma sha 12,
Tana jin dayansu na cewa "wai uban wa ake so ya zuba mana abincin ne? cikin sauri sehrish ta karasa tana cewa "ni ce yallabai ,"
Gaba daya suka d'ago suna kallon ta sai ta tsorata tayi wuri wuri da ido.
👮🏻♂️ *ABBAN SOJOJI* 👮🏻♂️
```The father Of Soldiers```
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•
Page 11-12
'Yan kame-kame ta shiga yi hankali a tashe tana wurwurga ido, " wannan d'an daudun daga ina kuma aka samo shi?" Daya daga cikinsu ya tambaya yana kallon ta , hantar cikinta ce ta ji ta kad'a , su duka sauraren ta suke yi su ji mai zata ce?
Motsi ta soma yi da lips dinta alamar tana so ta ce wani abu "Amm... Amm.." Duk ta bi ta dabarbarce. Jin muryar Azumi yasa Sehrish sauke ajiyar zuciya, karasowa ta yi tana fadin "Afuwan y'an samari ban yi maku bayani game da sabon d'an aikin da aka kawo domin ya rinka taya ni aiki ba."
Kasa kunne suka yi suna sauraron ta , dafa kafadar Sehrish ta yi tare da cewa "Sunan shi tukur daga yau zai rinka taya ni aikace aikacen cikin gidannan ,'
Ta kare maganar tana kallon kowannan su tabe baki yyi ba tare da sunce komai ba dama haka ta yi tsammani , don haka taci gaba da cewa "tukur bari na gabatarka maka da kowannan su saboda ka kiyayi zama dasu ,"ita dai ba ta ce komai ba saboda a rud'e take ,
Azumi ta soma gabatar mata da su daga na farko "Wadannan biyun da ka ke gani sune tagwaye in ka lura komai nasu iri d'aya , suna da son zolaya musamman idan abun mugunta ne sun fi auki a nan na farkon sunansa Jahan shine babba sai twin brother dinsa Ayaan"
Tana gama wa dasu ta matsa na kusa dasu tace "wannan kuma sunan shi Kanal yusif sarkin tsafta , bai cika son surutu ba kuma baya son kallo , na gefensa kuma shine Khaleed bai da matsala shi indai za ayi masa abunda ya ke so ba tare da ya tambaya ba ,
Duk Sehrish na sauraron wannan bayanin na azmi , bayan ta kammala da na hannun damarta ta koma other side din taci gaba da cewa "wannan Junaid kenan sarkin murmushi, duk yadda za'a bata mai rai baya fushi sai in an kuresa , yana da son wasa faran faran da jama'a, burinsa a bashi kulawa a bangaren ci kuwa ba'a magana ," karasa maganar tayi tana y'ar dariya , shima dariyar yake yi haka zalika wasu daga cikinsu sun d'an murmusa ,
Sehrish tagane sa shine wanda ta fara zuba ma abinci mai kyakkyawan murmushin nan
"n6a kusa da shi kuma fawan kusan halinsu daya da Junaid , sai jabir da irfan basu da matsala in dai ba tsokanarsu akayi ba."
Murmushi sehrish tayi taji dadin wannan gabatarwar , sai dai ranta na bata cewa wadannan kananun ne , akwai sauran mutun goma daga cikin sojojin da basa nan , su kuma koya zasu kasance !?
A tare da azmi suka yi saving dinsu abincin har suka kammala kowannnen su ya kama hanyar makwancinsa , tattara plates din da kulolin sukayi a tare suka kakkauda komai izuwa ma'ajiyarsa ,
daga nan sehrish tayi ma azmi sallama ta koma bedroom dinta , tana mai jin dadin fara kasancewarta a wannan awesome family din Babbar damuwarta shine , da tazo a matsayin namiji a maimakon mace batasan ya abun zai kasance ba ranar da asirin ta ya tonu.
Tunda samu gadon nan ta haye ta soma minshari bata kara sanin meke wakana ba sai da tajiyo kwankwasar kopar da azumi take yi mata ,
A firgice ta farka tana neman mayafin da take nad'e kanta da shi , can ta hangosa kasa ashe anan tayi wurgi dashi, daukowa tayi ta hanzarta daure kanta dashi, sannan ta tashi ta nufi kofan ta bude mata, fara'a azmi ta sakar mata " am sorry na Katse maka bacci ko naga ana kiran sallah ne raina ya bani baka yi ba nasan an sha gajiyar tafiya ga aikin da mukayi da dare ,"
Cikin y'ake sehrish tace "a'a wlh naji dadi da ki ka tashe ni saboda banyi sallah ba amma ynx zanje na yi,
Azumi tace "ok in ka kammala karfe 7 ka fito akwai aikin breakfast na jiran mu" reeshi ta amsa da "toh " sa'annan tajuya ciki"
Cikin sauri ta shiga toilet, sai da tafara cire gashin bakin da aka sa mata ta tura sa cikin aljihun wandon ta, sannan taje bakin fanfo ta daura alwala , ta fito tana yarfa hannun ta, hijabi ta dauko ta zura sannan ta shimfid'a kafet, ta soma yin sallar,
Bayan ta kammala sallar wata irin hamma ta rinka ji, ga bacci bai ishe ta ba ga kuma yunwa don jiya da daddare bata nemi abincin ba gashi available
Agogon dake manne jikin bango ta kalla akwai sauran lokaci don haka sai ta baje saman sallayar taci gaba sharar bacci, ba ita ta tashi ba sai wurin karfe 9 na safe hankali a tashi ta wartsake, ganin cewa wannan ce rana ta biyu da fara aikinta gashi zata fara bada matsala, cikin hanzari ta cire hijab dinta ta hada da kafet din sallan ta adana su a saman gadonta, sannan ta zaro gashin bakinta da take likawa ta manna sa a fuskarta, ta gyara nad'in mayafin kanta ta fi ce,
A kitchen ta Sami azmi ta kammala shirya komai na kalacin safen , duk sai taji ba dadi sukuku ta isa gare ta ta ce "barka da safiya nayi laifi dan Allah ayimun uziri,"
Babu alamun bacin rai a fuskar azmi ta ce " karka damu tukur, ba wani abu nan gaba dae aguji yin hakan"
Sehrish ta amsa da toh insha Allah yanzu wani aiki zan yi ?
Ba wani aiki kawai abunda ya rage ynx kabi bedrooms din kowannan su ka Sanar dasu su fito su yi breakfast ya kammalu," azmi ta karashe maganarta ta tana kallon ta,
Cikin zullumi sehrish ta fita ta tunkari jerin dakunan dake a downstairs , na farko ta fara kwankwasa wa shiru ba'a bude ba , kara knocking tayi da karfi , har sai da ya isarwa mai dakin , muryarsa tajiyo ashake yana cewa "who's trying to disturb me? d'aga murya tayi tare da cewa "tukur ne sabon mai aiki,"
"Shigo ciki" ya ba ta izni , turo kofar tayi tare da kutsa kai ciki, har cikin ranta dakin ya yi mata kyau bedroom kamar na mace saboda kyau ga tsafta sabanin wasu mazan da idan ka shiga dakunansu kamar wurin safkar y'an gudun hijra saboda tsaban tarkace da har mutsi,
"Idan ka kammala kalle kallen naka sai ka sanar dani abunda ya kawo ka," muryarsa ce ta dirar mata a kunne sai lokacin ta mayar da idonta akansa , kwance yake a baje saman katafaren gadonsa rabin jikinsa yayi covering dinsa da lallausan blanket , Yusif kenan
Cikin en ina sehrish ta ce "am ..emm dama an kammala breakfast ne shine aunty azmi tace nazo na sanar daku."
ta kammala maganarta ta tana wasa da yatsun hannunta , jin shirun bai ce komai ba ya sa ta dagowa ta saci kallonsa , samun shin tayi yana yamutsa fuska alamar an takura masa cikin lallausar muryarsa ya ce "Idan ina jin yunwa ai ba sai anzo an tayar dani ba ni zanzo da kaina ciki na ne ko cikin wani? ya tambaya yana kallon ta ,
Cikin sauri tace "cikin ka ne" ok fi ce ka ban wuri , ya fada tare da jan bargonsa ya idasa rufe face dinsa ,
Kamar wacce kwai ya fashe mawa a kai haka ta fita salalau salalau , a cikin ranta kuwa tana jinjina ma isa irin tasa " tab aiki y ganni ni sehrish daga abun arziki, wannan shi ake kira da samun wuri tusar asuba, Allah sarki mukam ya'yan talakawa don uban mutun kar Allah yasa ya nemi abinci har rana ta fadi ya ga in za'a a damu dashi kasha iya barcinka yunwa ta taso ka, ka lallaba ka je neman kason ka wani sa'in ma an manta dakai, su kam wadandannan genius din bibiyarsu akeyi suzo suci suna make wa,"
Ta karasa tunanin nata a dai dai lokacin da tazo kofar dakin the next person , knocking tyi bugu d'aya taji ance "Come in"
turo kofan tayi ta bude Samun shi tayi zaune saman sallaya jikinsa sanye da jallabiya ga kur'ani yana karantawa gwanin burge w, da alama wannan zaiyi saukin kai a cewarta
"Barka da safiya yallabai an tashi lafiya" sai da ya kai aya sannan ya juyo ya kalle ta ya ce "da ban tashi lpy ba zaka ganni ina karatun Qur'ani ne? to fah ta ambata acikin zuciyarta , shin mai ya kawo ka ma tukunna ? ya tambaya yana kallon ta a matsayin namiji,
Muryarta na rawa tace "dama an kammala breakfast ne shine ....." Interrupting dinta yayi tare da cewa "shine me ? kai shashashan ina ne da zaka fadowa mutun haka kawai tunda sanyin safiya,kama hanya ka fi ce tunkan nayi football dakai" (Jahan).
Jiki na rawa Sehrish ta fi ce zuciyarta na bugawa saboda tsananin tsoro, dafe kirjinta tayi domin ta samu natsuwar karasawa ga daki na gaba,zullumin ta kar asamu wanda zai kai mata duka don ta lura cewa fusatattu ne, ba mai sauki a cikinsu farawa da iyawa ta fara fuskantar haka nan gaba batasan mezai biyu baya ba.
Next room kwankwasa tayi tana jira taji an bata iznin shiga amma shiru , sake buga kofan tayi da d'an karfi da alama kowanane mamallakin dakin nan ya datse kofar ne,
Jin alamar ana tunkaro kofar yasa ta natsuwa, bude kofar yayi fuskar nan a daure kamar Alkubus "lafiya"? ya ambata rai a bace.
Har ta bud'e baki zata yi magana tajiyo muryar wani daga can cikin ɗakin yana cewa "Wai wane ne"?
"Wannan shashashan sabon mai aikin ne," wanda ke tsaye a gabanta ne ya basa amsa, sai lokacin ta gane cewa dakin twins ne wato kamar yadda suke y'an biyu haka ma wurin kwanansu d'aya ,"
Tuni taji zufa ta ke to mata ganin wancan dake daga ciki ya taso , dukkan su sleeping dress ne riga da wando ajikinsu kala daya milk colour masu kyan gaske,
Jerawa suka yi tsaye a gabanta kowanne na kallonta alamar sun ma rasa wane hukunci zasu yi mata saboda ta katse masu baccinsu,
Gudun kar ta ja ma kanta bugu yasa ta ce "Am...Da ma breakfast ne an kammala shine aunty azmi tace a zo a sanar daku,"
Kallon juna su kayi tare da cizon labba atare, Ayaan ne yasa hannunsa ya kamo kunnanta ya idasa shigo wa da ita ciki , ba karamin zafi sehrish taji ba har sai da tad'an saki y'ar kara "ko da gigin wasa next time ka kara attempting zuwa tashe mu bacci na rantse saika yabawa aya zaki sususu kawai," ya karasa maganar tare da sakin kunnan nata cikin sauri sehrish ta fice tana sharar kwalla don ba karamin zafi taji ba,
Sai da ta samu wuri ta tsugunna ta gama matse yar kwallarta sannan ta tunkari sauran dakunan kowane daki taje da abunda zata tarar na wulakanci, yanzu dai gashi ta tunkari saman bene last room da ya rage ta shiga,
Sai da ta tabbatar ta share dukkan ruwan hawayen da ya zubo mata sannan ta kwankwasa , kusan 3 times tana knocking a na karshen ne taji wata sanyayyiyar murya tace" shigo ciki."
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
Page 11-12
'Yan kame-kame ta shiga yi hankali a tashe tana wurwurga ido, " wannan d'an daudun daga ina kuma aka samo shi?" Daya daga cikinsu ya tambaya yana kallon ta , hantar cikinta ce ta ji ta kad'a , su duka sauraren ta suke yi su ji mai zata ce?
Motsi ta soma yi da lips dinta alamar tana so ta ce wani abu "Amm... Amm.." Duk ta bi ta dabarbarce. Jin muryar Azumi yasa Sehrish sauke ajiyar zuciya, karasowa ta yi tana fadin "Afuwan y'an samari ban yi maku bayani game da sabon d'an aikin da aka kawo domin ya rinka taya ni aiki ba."
Kasa kunne suka yi suna sauraron ta , dafa kafadar Sehrish ta yi tare da cewa "Sunan shi tukur daga yau zai rinka taya ni aikace aikacen cikin gidannan ,'
Ta kare maganar tana kallon kowannan su tabe baki yyi ba tare da sunce komai ba dama haka ta yi tsammani , don haka taci gaba da cewa "tukur bari na gabatarka maka da kowannan su saboda ka kiyayi zama dasu ,"ita dai ba ta ce komai ba saboda a rud'e take ,
Azumi ta soma gabatar mata da su daga na farko "Wadannan biyun da ka ke gani sune tagwaye in ka lura komai nasu iri d'aya , suna da son zolaya musamman idan abun mugunta ne sun fi auki a nan na farkon sunansa Jahan shine babba sai twin brother dinsa Ayaan"
Tana gama wa dasu ta matsa na kusa dasu tace "wannan kuma sunan shi Kanal yusif sarkin tsafta , bai cika son surutu ba kuma baya son kallo , na gefensa kuma shine Khaleed bai da matsala shi indai za ayi masa abunda ya ke so ba tare da ya tambaya ba ,
Duk Sehrish na sauraron wannan bayanin na azmi , bayan ta kammala da na hannun damarta ta koma other side din taci gaba da cewa "wannan Junaid kenan sarkin murmushi, duk yadda za'a bata mai rai baya fushi sai in an kuresa , yana da son wasa faran faran da jama'a, burinsa a bashi kulawa a bangaren ci kuwa ba'a magana ," karasa maganar tayi tana y'ar dariya , shima dariyar yake yi haka zalika wasu daga cikinsu sun d'an murmusa ,
Sehrish tagane sa shine wanda ta fara zuba ma abinci mai kyakkyawan murmushin nan
"n6a kusa da shi kuma fawan kusan halinsu daya da Junaid , sai jabir da irfan basu da matsala in dai ba tsokanarsu akayi ba."
Murmushi sehrish tayi taji dadin wannan gabatarwar , sai dai ranta na bata cewa wadannan kananun ne , akwai sauran mutun goma daga cikin sojojin da basa nan , su kuma koya zasu kasance !?
A tare da azmi suka yi saving dinsu abincin har suka kammala kowannnen su ya kama hanyar makwancinsa , tattara plates din da kulolin sukayi a tare suka kakkauda komai izuwa ma'ajiyarsa ,
daga nan sehrish tayi ma azmi sallama ta koma bedroom dinta , tana mai jin dadin fara kasancewarta a wannan awesome family din Babbar damuwarta shine , da tazo a matsayin namiji a maimakon mace batasan ya abun zai kasance ba ranar da asirin ta ya tonu.
Tunda samu gadon nan ta haye ta soma minshari bata kara sanin meke wakana ba sai da tajiyo kwankwasar kopar da azumi take yi mata ,
A firgice ta farka tana neman mayafin da take nad'e kanta da shi , can ta hangosa kasa ashe anan tayi wurgi dashi, daukowa tayi ta hanzarta daure kanta dashi, sannan ta tashi ta nufi kofan ta bude mata, fara'a azmi ta sakar mata " am sorry na Katse maka bacci ko naga ana kiran sallah ne raina ya bani baka yi ba nasan an sha gajiyar tafiya ga aikin da mukayi da dare ,"
Cikin y'ake sehrish tace "a'a wlh naji dadi da ki ka tashe ni saboda banyi sallah ba amma ynx zanje na yi,
Azumi tace "ok in ka kammala karfe 7 ka fito akwai aikin breakfast na jiran mu" reeshi ta amsa da "toh " sa'annan tajuya ciki"
Cikin sauri ta shiga toilet, sai da tafara cire gashin bakin da aka sa mata ta tura sa cikin aljihun wandon ta, sannan taje bakin fanfo ta daura alwala , ta fito tana yarfa hannun ta, hijabi ta dauko ta zura sannan ta shimfid'a kafet, ta soma yin sallar,
Bayan ta kammala sallar wata irin hamma ta rinka ji, ga bacci bai ishe ta ba ga kuma yunwa don jiya da daddare bata nemi abincin ba gashi available
Agogon dake manne jikin bango ta kalla akwai sauran lokaci don haka sai ta baje saman sallayar taci gaba sharar bacci, ba ita ta tashi ba sai wurin karfe 9 na safe hankali a tashi ta wartsake, ganin cewa wannan ce rana ta biyu da fara aikinta gashi zata fara bada matsala, cikin hanzari ta cire hijab dinta ta hada da kafet din sallan ta adana su a saman gadonta, sannan ta zaro gashin bakinta da take likawa ta manna sa a fuskarta, ta gyara nad'in mayafin kanta ta fi ce,
A kitchen ta Sami azmi ta kammala shirya komai na kalacin safen , duk sai taji ba dadi sukuku ta isa gare ta ta ce "barka da safiya nayi laifi dan Allah ayimun uziri,"
Babu alamun bacin rai a fuskar azmi ta ce " karka damu tukur, ba wani abu nan gaba dae aguji yin hakan"
Sehrish ta amsa da toh insha Allah yanzu wani aiki zan yi ?
Ba wani aiki kawai abunda ya rage ynx kabi bedrooms din kowannan su ka Sanar dasu su fito su yi breakfast ya kammalu," azmi ta karashe maganarta ta tana kallon ta,
Cikin zullumi sehrish ta fita ta tunkari jerin dakunan dake a downstairs , na farko ta fara kwankwasa wa shiru ba'a bude ba , kara knocking tayi da karfi , har sai da ya isarwa mai dakin , muryarsa tajiyo ashake yana cewa "who's trying to disturb me? d'aga murya tayi tare da cewa "tukur ne sabon mai aiki,"
"Shigo ciki" ya ba ta izni , turo kofar tayi tare da kutsa kai ciki, har cikin ranta dakin ya yi mata kyau bedroom kamar na mace saboda kyau ga tsafta sabanin wasu mazan da idan ka shiga dakunansu kamar wurin safkar y'an gudun hijra saboda tsaban tarkace da har mutsi,
"Idan ka kammala kalle kallen naka sai ka sanar dani abunda ya kawo ka," muryarsa ce ta dirar mata a kunne sai lokacin ta mayar da idonta akansa , kwance yake a baje saman katafaren gadonsa rabin jikinsa yayi covering dinsa da lallausan blanket , Yusif kenan
Cikin en ina sehrish ta ce "am ..emm dama an kammala breakfast ne shine aunty azmi tace nazo na sanar daku."
ta kammala maganarta ta tana wasa da yatsun hannunta , jin shirun bai ce komai ba ya sa ta dagowa ta saci kallonsa , samun shin tayi yana yamutsa fuska alamar an takura masa cikin lallausar muryarsa ya ce "Idan ina jin yunwa ai ba sai anzo an tayar dani ba ni zanzo da kaina ciki na ne ko cikin wani? ya tambaya yana kallon ta ,
Cikin sauri tace "cikin ka ne" ok fi ce ka ban wuri , ya fada tare da jan bargonsa ya idasa rufe face dinsa ,
Kamar wacce kwai ya fashe mawa a kai haka ta fita salalau salalau , a cikin ranta kuwa tana jinjina ma isa irin tasa " tab aiki y ganni ni sehrish daga abun arziki, wannan shi ake kira da samun wuri tusar asuba, Allah sarki mukam ya'yan talakawa don uban mutun kar Allah yasa ya nemi abinci har rana ta fadi ya ga in za'a a damu dashi kasha iya barcinka yunwa ta taso ka, ka lallaba ka je neman kason ka wani sa'in ma an manta dakai, su kam wadandannan genius din bibiyarsu akeyi suzo suci suna make wa,"
Ta karasa tunanin nata a dai dai lokacin da tazo kofar dakin the next person , knocking tyi bugu d'aya taji ance "Come in"
turo kofan tayi ta bude Samun shi tayi zaune saman sallaya jikinsa sanye da jallabiya ga kur'ani yana karantawa gwanin burge w, da alama wannan zaiyi saukin kai a cewarta
"Barka da safiya yallabai an tashi lafiya" sai da ya kai aya sannan ya juyo ya kalle ta ya ce "da ban tashi lpy ba zaka ganni ina karatun Qur'ani ne? to fah ta ambata acikin zuciyarta , shin mai ya kawo ka ma tukunna ? ya tambaya yana kallon ta a matsayin namiji,
Muryarta na rawa tace "dama an kammala breakfast ne shine ....." Interrupting dinta yayi tare da cewa "shine me ? kai shashashan ina ne da zaka fadowa mutun haka kawai tunda sanyin safiya,kama hanya ka fi ce tunkan nayi football dakai" (Jahan).
Jiki na rawa Sehrish ta fi ce zuciyarta na bugawa saboda tsananin tsoro, dafe kirjinta tayi domin ta samu natsuwar karasawa ga daki na gaba,zullumin ta kar asamu wanda zai kai mata duka don ta lura cewa fusatattu ne, ba mai sauki a cikinsu farawa da iyawa ta fara fuskantar haka nan gaba batasan mezai biyu baya ba.
Next room kwankwasa tayi tana jira taji an bata iznin shiga amma shiru , sake buga kofan tayi da d'an karfi da alama kowanane mamallakin dakin nan ya datse kofar ne,
Jin alamar ana tunkaro kofar yasa ta natsuwa, bude kofar yayi fuskar nan a daure kamar Alkubus "lafiya"? ya ambata rai a bace.
Har ta bud'e baki zata yi magana tajiyo muryar wani daga can cikin ɗakin yana cewa "Wai wane ne"?
"Wannan shashashan sabon mai aikin ne," wanda ke tsaye a gabanta ne ya basa amsa, sai lokacin ta gane cewa dakin twins ne wato kamar yadda suke y'an biyu haka ma wurin kwanansu d'aya ,"
Tuni taji zufa ta ke to mata ganin wancan dake daga ciki ya taso , dukkan su sleeping dress ne riga da wando ajikinsu kala daya milk colour masu kyan gaske,
Jerawa suka yi tsaye a gabanta kowanne na kallonta alamar sun ma rasa wane hukunci zasu yi mata saboda ta katse masu baccinsu,
Gudun kar ta ja ma kanta bugu yasa ta ce "Am...Da ma breakfast ne an kammala shine aunty azmi tace a zo a sanar daku,"
Kallon juna su kayi tare da cizon labba atare, Ayaan ne yasa hannunsa ya kamo kunnanta ya idasa shigo wa da ita ciki , ba karamin zafi sehrish taji ba har sai da tad'an saki y'ar kara "ko da gigin wasa next time ka kara attempting zuwa tashe mu bacci na rantse saika yabawa aya zaki sususu kawai," ya karasa maganar tare da sakin kunnan nata cikin sauri sehrish ta fice tana sharar kwalla don ba karamin zafi taji ba,
Sai da ta samu wuri ta tsugunna ta gama matse yar kwallarta sannan ta tunkari sauran dakunan kowane daki taje da abunda zata tarar na wulakanci, yanzu dai gashi ta tunkari saman bene last room da ya rage ta shiga,
Sai da ta tabbatar ta share dukkan ruwan hawayen da ya zubo mata sannan ta kwankwasa , kusan 3 times tana knocking a na karshen ne taji wata sanyayyiyar murya tace" shigo ciki."
Comment and share
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Page 13-14
Da sallama tashi ga wani irin daddadan kamshi ne ya ratsa hancin ta, har sai da tasa hannu ta d'an matse hancin saboda scent din ya kai mata karo,
Samun shi tayi a kwance tsakiyar gado wani irin sabon salon kwanciya da bata taba gani ba, up yake fuskanta ya rungume fillow a kirjinsa ga wani filon a tsakankanin laps dinsa ya makalkalesa, fuskar nan dauke da murmushi just like always, Junaid kenan sarkin smiling,
Karasawa tayi gaban bed din yadda zaiji ta dakyau ta ce "barka da safiya' Zuciyarta na mata dar dar gudun karya yi mata abunda sauran su kayi mata,
A hankali ya bude idonunsa ya sauke su akanta "menene"? ya ambata cikin kasalalliyar murya,
"Breakfast ne ya kammala" ta fada tana kallon kyakkyawar fuskarsa da jajayen lips dinsa,
Cikin shagwaba ya ce"wlh naji dadin zuwanka tukur dama tundazu nakeso na tashi kasala ta hanani pls taimaka min na mik'e" ya idasa maganar tare da mika mata hannunsa ,
Waro ido waje tayi domin wannan yafi sauran iyayi, fuskarta tamkar zata yi kuka gaba daya ta rasa me zata yi tun nan sehrish tagane kuskuren da ta tafka na zuwa amatsayin namiji bata da wani zabi fa ce tayi abunda ya ce if not her secrets will expose,
Mika masa hannunta tayi ya ruko cikin nasa, nan take taji wani irin yanayi a tattare da ita mara misaltuwa, lallausar fatan hannunsa ba karamin gigita ta tayi ba saboda softness dinta, a cikin ranta tace "wannan wani irin hannu ne mai laushin gaske da dadin tabawa, daga jin wannan hannun bai taba wanki ba,"
Gam ya ruke hannun nata a yunkurin ya taso ya janyo ta gaba d'aya ta rikito ta fada masa, dalili kuwa karfinsa ya rinjayi nata nesa ba kusa ba,
Wani irin bugu zuciyarta ta shiga harbawa duk tabi ta susuce ta rasa inda zata tsoma kanta, tashi ga yanayi mara misaltuwa, tsigar jikinta duk ta tashi tsaye hai kam, karo na farko da ta fada jikin namijin da ba muharramin ta ba, gashi ko riga babu jikinsa d'an short ne dai-dai guiwarsa,
Kamar anyi mutuwa haka sukayi tsit, junaid kam yarasa meyasa yaji tamkar maca ce ta fada masa a jikinsa shaukin daya ji ya basa mamaki, ita kam sehrish ji take kamar an manna mata magnet a jikinsa sam tagaza yunkurin tashi
Kasala ce ta rufe mata jiki sai da ta tattaro dukkan sauran karfin daya rage mata a jikinta ta yunkura ta mik'e cikin sauri ta zame jikinta daga nashi ta fi ce da gudun gaske kamar walkiya haja yake kallon lamarin,
Tunaninsa me yasa d'an aikin ya shiga feelings haka kodai d'an daudu ne mai bin maza ba shakka kuwa haka ne, ya fada aransa
A bangaren sehrish kuwa da ta fita a guje dakinta ta koma, tana tura kofar tashiga ta maidata ta datse sannan ta jingina da kofan tana shesshekar kuka,
ta riga da ta san ta yi kuskure tun farko cikin raunanninyar muryarta ta furta " Omg! i ave made a mistake Ya Allah makes it easy for me,
A cikin 2 weeks sehrish ta gama fita hayyacin ta, a tunanin zata huta a wannan katafaren gidan amma ashe ba haka bane, aikinsu Junaid kamar zai kashe ta, ga wani karen tsana da twins dinnan Jahan da Ayaan suka sa mata, yini take tana aiki tun safe har dare basa so suga tana hutawa sunfi so suga tana aiki kamar ansa mata battery, kullum sai azmi ta turata taso su suzo suci kalacin su na safe, haka Zata bi dakin kowannansu daya bayan d'aya, kowa taje tadawa da irin wulakancin da zata kwasa saboda jan kunnanta da suke yi har fatar kunnan tayi jawur, ga gyaran dakunansu, wanke toilet dinsu, gugar kayansu duk ita ke yi, wani lokacin ma idan suka ga babu aiki tana hutu sai su tattaro kayansu dake cikin laundry basket su bata ta wankesu tas, in azmi tace musu ba da injin wanki suke amfani ba dak sai suce ae wankin hannu yafi fidda kaya suyi kyau,
Baiwar Allah lokaci guda ta zama wata zararriya wani sa'in ko bacci take yi sai ta dinga jin muryoyinsu nayi mata gizau a kunnanta suna cewa "tukur tukur tukur kur "
Girki kad'ai azumi ke yi saboda sunce sauran aiyukan bana ta bane na d'an uwansu namiji ne wato tukur mai aikinsu,
Akwai lokacin da suka shigo atare suka same ta, ta kammala goge goge tayi aiki ta gaji, ta samu wuri saman 3 seater ta kwanta tana hutawa asalima batasan bacci ya dauke ta ba,
Kayan wanki suka shiga suka dauko kowa dana sa, bata yi aune ba sai dai taji ana zazzage mata jibgin kaya a jikinta, haka take faman hakuri dasu,
Yau ba ta makara wurin shiga kitchen ba, azumi ta taras tana gyara naman kaji, ba qaramin mamaki azmi ke bata ba sam ba ta gajiya da aiki kamar engine, gashi ta kware a wurin iya sarrafa abinci ta iya girki
"Barka da safiya aunty azmi" ta fada tana kallon ta , da murmushi a fuskarta tace "yawwa mlm tukur ya gajiyar jiya? Sehrish ta ce "Alhamdllh"
"Yau ba a makara ba kenan" azmi ta tambaya, sehrish ta ce "eh"
Zame hannun tayi daga gyaran naman da take yi, can cikin kitchen din tashi ga kofar da store yake ta bude, wasu manyan doyoyi ne ta dauko guda 3 lafiyayyu, tazo ta ajiye a saman table din da suke yanke yanke a saman sa da sauransu, " gasu nan a fere su da kyau in ka gama ka shiga store za ka ga crack din kwai ka debo 20 a cikin roba a farfasa su,"
Amsa wa kawai take da toh, wuka ta dauko ta fara daddatsa doyar , a natse take ferewa , junaid ne ya fado mata a ranta tunaninsa ta soma yi "har yanzu nagaza gane masa ni bansan meyasa ya ke da shagwaba ba kamar karamin yaro gashi da shiga rai uwa uba ga kyau kai dukkansu ma kyawawa ne idan har akace mun na zabi daya cikinsu to tabbas zanyi ruwan ido, amma fa gaskiya junaid na daban ne inason namiji mai shagwaba mai kyakkyawan murmushi domin murmushi alama ce dake nuna cewa mutun nada saukin kai, matsala da shi son jikin tsiya shi a tunaninsa ni namiji ce baijin komai ya rika ruko mun hannu baisan yana sani cikin yanayi ba.
Muryar azmi ce ta katse mata tunanin nata "sai kayi sauri fa tukur naga alamar yau shiririta kake ji,"
Mayar da hankalin ta tayi ta ci gaba da ferar doyar, bayan tagama tayi mata shape, gaban tap taje ta zuba ruwa ta wanke ta tas, ta dawo kan eggs din da cokali ta farfasasu ta dauko Whisk abun ƙaɗawa ta k'ada shi ya haɗe jikinsa, kayan kamshi azmi ta miƙa mata ta karba ta zuzzuba a ciki, bayan tagama ta shiga soya wa da doyar.
A kalla suna yin abinci kusan kala 8 na breakfast hada kayan snacks irinsu bugger, donuts, pancake, soyayyiyar ayaba (plaintain) chips doya da kwai, chicken pper soup, pasta wit stew , coffee , slide bread, gasasshen kifi, fried meat tarkace iri iri ,
Mafi rinjayen aiki azmi ke yi hakan ba karamin taimakon sehrish ta yi ba saboda bakomai ta iya ba,
"Ka je ka fara tado su lokaci karya kure tunda mun kammala da wuri" A cewar azmi da take shisshirya kayan abincin wanda zata je ta jera a dining,
fita sehrish tayi da sauri gaban ta na ɗar ɗar gudun abunda zata taras wurinsu,
Dakin kanal yusif ta fara zuwa, bayan ya bata iznin tashigo, ganin shi daga shi sai short towel a west dinsa ya sa ta yin ƴan kame Kame da alama daga wanka ya fito duba da yadda ruwa ke ɗigɗiga daga jikinsa,
Sam ta gaza control ɗin kanta har sai da ya juyo ya kalle ta dayake a gaban dressing mirror yake, ganin yadda mai aikin ya zuba masa ido yasa shi jan dogon tsaki tare da cewa "Stupid ! Why are you Looking at me? Ina namiji kana namiji amma kake kallo na anya kai ba ɗan iska ba ne?
Sunkuyar da kanta ta yi tare da cewa, "An gama shirya...' Bai bari takarasa ba ya ce "Na ji but this is the last warning da zan yi maka as from today bana bukatar sai an zo an sanar da ni in sauko in ci abinci,"
Cikin girmamawa ta amsa masa da ta toh insha Allah hakan bazai sake faruwa ba, fi ce wa tayi ta wuce dakin khaleed har cikin zuciyarta taji dadin abunda yusif ya ce mata saboda ita hutu ne a gare ta,
Shima khaleed kusan hakance ta faru ya ce baya bukatar ana zuwan masa ɗaki da safe haka indai ba shi ya bukata ba,
Wuce wa tayi dakin twins kwankwasa tayi taji shiru ba a bata izinin shiga ba amma kofar a bud'e take, a matsayin ta na me ragaggen hankali sai ta kutsa kai tashi ga kwata kwata babu su a saman gadonsu sai dai wani abu daya tayar mata da hankali, gurnani da wani irin nishi tadinga ji daga cikin toilet dinsu alamun akwai mutun ciki kona ce mutane ciki, tamkar ana sukuwa saman doki yanayin sautin.
Hakan ba karamin firgitar da ita yayi ba sai ranta ya riƙa bata cewa kodai wani ne bai lafiya a cikin toilet ɗin da bukatar tayi sauri taje ta sanarwa azmi abunda ke faruwa, juya wa tayi da sauri zata fita sai taji ana koƙarin buɗe kofan, tsayawa tayi tana kallon kofan toilet ɗin taga ikon Allah, a tare suka fito daga toilet din Ayaan ne ya fara fito wa sai jahan biye a bayansa dukkansu sanye da gajeran towel a ƙugunansu,
Gaba ɗaya tabi ta firgita sam basu lura da ita ba don haka ta lallaba ta fice cikin saurin,
Jikin ta a mace take tafiya abubuwa iri iri ne suke zo mata a ranta " dama mutum biyu na shiga toilet a lokaci ɗaya, menene dalilinsu nayin hakan? Shin nishin da naji da gurnanin nan na menene ? Allah wa alamu ta tambayi kanta sam ba ta kawo wa ranta wani abu ba amma hakanan take jin tabbas da akwai matsala a tattare da twins din nan.
Bedroom din fawan ta wuce tun kan tashi ga take jin sa yana waya, tsayawa tayi bakin kofan tana saurarinsa "baby nifa bana so a samu matsala bakisan halin yayyen mu ba muddin suka gane cewa ina mu'amala da mata to tabbas sai sun kusa kashe ni,"
Rass taji gabanta ya faɗi " mu amala da mata kuma wata irin mu'amala kenan?
Ta jefa wa kanta tambaya zuciyar ce ta bata amsa "duk wata mu'amala da mutun ke gudun a san yanayin ta to tabbas ba mai kyau bace,"
Wani irin miyau ta haɗiye lokacin da ta samu amsar tambayarta , sai da ta samu natsuwa sannan ta kwaɗ'a sallama, jin muryar mai aikin nasu yasa fawan saurin yin rejecting kiran ya yi throwing phone ɗin nasa saman gefensa, rai abace yace " wai wanene "
Ko izinin shiga ba ta samu ba, murya na rawa ta ce "tukur ne dama an kammala shirya breakfast ne"
Wani irin dogon tsoki ya ja tare da cewa" Naji sai me"?
Jiki a sanyaye sehrish tabar kofan ɗakin nasa ta wuce na irfan, ita kanta ta shaida cewa yau babu sa'a ynx fargabanta me zata taras ɗakin sauran.
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Page 15-16
Kwankwasa kofar ɗakin nasa tayi , da wata irin kakkausar murya taji ya amsa mata da cewa"Uban wanene" kai kanaji kasan yasha ya bugu har takai masa aka.
Saboda tsoro bata basa amsa ba ta yi gaba da sauri, tun a lokacin ta gane cewa tabbas akwai matsala kuma sam bai kamata tana bin kowannan su ɗaki don tayar dasu ba, ta gama yanke shawarar sanarwa azmi cewa baza ta ƙara zuwa ba, tun da cikinsu ne in suna jin yunwa dakansu zasu fito su nema.
Gaba ɗaya a firce take da lamarin kan ta ya gama ɗaure wa, ɗakin Jabeer ta wuce tana sa hannu ta kwankwasa kofa , tana jiyo har mutsinsa ta ciki sallar karya ya kabbara , shiga ciki tayi abun saiya daure mata kai, Sallah karfe 9 na safe.
Har zata juya idon ta ya hango mata kwayoyi na shaye~shaye ga kwalabe kuma a gabansa.
Shi duk a tunaninsa yayansu ne kanal yusif amma jin shiru yasa shi katse sallar ya ɗago ya kalle mai aikin, wani mugun kallo ya wurga mata tare da nuna mata hanyar fita ya ce " karka kuskura ka ƙara zuwan min ɗakina in ba haka ba saina canzama kamanni shashasha,"
Abun da bai sani ba ita sam ba ta san kwayoyin menene a gabansa ba, a tunaninta bai da lafiya ne shine ya ajiye magunguna zai sha.
Ficewa ta yi a ranta tana cewa" Allah ya ba ka hakuri,"
Saura ɗakin shagwababben sarkin murmushi, har tsoran zuwa ta ke yi saboda manne mata da yake yi,
Tunkan ta shiga take jin muryasa yana faɗin "Coffee i need coffee pls " cikin magagin bacci ya ke wannan sambatun na neman coffee,
knocking tayi masa kusan sau uku kafin taji muryarsa yana cewa "wanene shigo ciki mana,"
Gyarawa tayi ta shiga ciki samun shi tayi kamar yadda ta saba samun shi irin kwanciyar nan tasa daya saba, kamar wani karamin yaro haka yake,
Karasawa tayi gabansa tare da cewa"barka da safiya junaid , tukur ne," ta idasa maganar tana kallon cikin idonsa daya buɗe,
A duk lokacin da ta kalle sa wani irin natsuwa da kwanciyar hankali ne ke shigarta, murmushi taga yana sakar mata dimple din nan nasa masu lotsawa guda biyu suka bayyana,
"Ohh tukur ne am really happy to see u, dama yau inaso ka taimakamin tun jiya nakeson wanke sumar kaina na kasa amma yau kam tare zamu shiga toilet ka taimakamin," a wani shagwab'e ya ke maganar.
Sehrish kuwa waro ido waje tayi jin abun da ya ce wannan da alama wata rana cewa zaya yi tayi masa wanka,
Cikin sanyin murya ta ce "ka yi hakuri dan Allah ba yadda za'ai na bi ka toilet sam a tsarin aiki na a gidan nan ba'a ba mai aiki izinin yin hakan ba,
Wani irin kallo ya wurga mata kafin ya ce" wa ye wanda ya tsara wannan dokar? bayan ni ne silar da aka kawo ka aiki a gidannan, tukunna ma kai ba jinsina bane? to kodai maca ce tayi shigar maza bansani ba,"
Jin wannan maganar tasa yasa sehrish jin faɗuwar gaba tuni ƴan hanjin cikin ta suka ƙaɗa har ta soma tunanin anya Junaid bai gane cewa ita MACACE ba NAMIJI ba !? duk tabi ta rikita kanta
Muryarsa ce ta sake katse ta "Am asking you ! answer me," dakyar voice ɗinta ke fita "ba haka bane, kawai a ganina bai da ce ba ina matsayin mai aiki nayi hakan,"
"I command you to do that! ae mu ne masu gidan kuma umarnin mu ake bi,"
Cike da isa junaid yayi maganar,ba yadda sehrish ta iya a dolen ta, tabi umarninsa, haka ya tashi yana yauƙi yana cika yana batse wa kamar bashi bane mai murmushin kashe zuciyarnan ba,
Miƙewa ya yi daga saman bed din ya sauko daga shi sai shorts a jikinsa, bin jikin shi tayi da kallo fari sol ba tarin gashin jiki a skin dinsa , ga kirarsa dai dai wa dai dai, kusan hasken fatarsa dana twins jahan da Ayaan ɗaya ne akan na sauran don haskensu ba irin na nan bane zai iyiyuwa cikin iyayensu akwai farar fata, mahaifiyarsu ko mahaifinsu,
"Idan ka gama kallon zamu iya shiga ciki ko" ya ambata yana kallon ta, gaba yayi cikin toilet din tabi bayansa zuciyarta na ɗar ɗar tsoranta kar ya ce zai cire shorts ɗinsa a agaban idonta batasan ya zata yi ba,
Da farga jikin ta na rawa ta dauko ɗaya daga cikin jerin shampoo dinsa na wanke kai, juya tayi da nufin ta nuna masa in da wanda ta dauko yake amfani kar asamu matsala, samun shi tayi yana kokarin cire shorts ɗin jikinsa, aiko a firgice ta saki roban shampoo ɗin ƙasa, ta karasa da gudu ta cafke hannayensa dake a saman mararsa gam ta ruke su, kallon juna suka shiga yi na wani lokaci, shi mamakinsa wai namiji ne ke gudun ɗan uwansa namiji a ganinsa is not a bad thing don ka cire kayanka gaban jinsin ka, ita kuwa miyau kawai take haɗiya gabanta na faduwa sai faman huci take kamar wadda ta yi ƴar tseral, Tuni hancin ta ya soma tsattsafo da zufa, tsoranta wane hukunci zai yi mata a sakamakon abunda tayi, ita dai tayi hakan ne don da abunda zata gani na tsiraicinsa kwara koma meye yayi mata tasan ba laifinsa bane, laifin ta ne da tayi shigar namiji,
Zame hands ɗinta tayi daga rikon da tayi masa, hannayenta ta aza a saman kanta tare da faɗin "nashiga ukuna am so sorry sir am just out of sense," duk a riki ce tayi maganar,
'Stop calling me sir! Cos may be am just your age mate, call me wit my name Junaid,
Ya karsa maganar tare da ƙara gyara gyara shorts ɗinsa yace " get out of my sign,"
Cikin sauri ta nufi hanyar fita har ta 6uɗe kofan tajiyo muryarsa yana cewa" Am watching you!" juya kanta tayi ta kallesa da yatsunsa yayi mata nuni da idonsa alamar zai sa ido akanta,
Cikin sauri ta fi ce tana faɗin " Insha Allah junaid bazaka gano komai ɗangane dani ba zan ta addu'a ina rokon Allah yaci gaba da rufamin asiri har nasamu na hada kudin aikin Husanna nabar maku gidanku,
ta fada acikin zuciyarta (abunda sehrish ba ta sani ba wannan gidan is part of her destiney)
Azumi ta kammala shirya musu abincin sai da kowannansu ya mula yasha iska sannan suka firfito, one by one duk sun shirya cikin kakin sojojinsu, banda mutun ɗaya junaid wanda ke sanye da jeans a jikinsa tare da farar tshirt mai dogon hannu ta ɗanyi tighting ɗinsa,
Kowannan su ya samu wuri ya zauna, sehrish ce ta fito frm the kitchen don ta fara saving ɗinsu, azmi kuma ta wuce bedroom ɗinta don dama already ta sanar da ita cewa zata shiga ciki tayi wanka don tasha aiki,
Hannu ta har kekkerwa yake yi saboda tsananin tsoran guyabarsu, junaid ta fara kallo tare da cewa"me zan zuba maka'? Kafin ya buɗe baki ya yi magana fawan ya kar6e da cewa"saboda shine babba acikin mu !"
Ayaan ya ce "thats what i was trying to say! Wannan house boy din ba karamin ɗan iska bane shi junaid ɗin special salary ya ware maka ne ɗayasa kke kokarin fara zuba masa abincin? ya tambaya fuska a ɗaure yana kallon ta,
nan fa hankalinta ya tashi ita batayi don wani abu ba ashe abun yana damunsu,
Muryar Jahan ce ta katse ta "Nima na lura da haka in banda iskanci ka rasa wanda zaka fifita sai karamin kanin mu wanda ko aiki baya zuwa sai dai yazauna kamar mace a gida,' ya ƙarasa maganar yana wurga masa harara.
Ran Junaid ba ƙaramin baci yayi ba, abun duk saiya bashi haushi musamman da Jahan yace masa kamar mace, wani irin ƙululu bakin ciki ne ya tsaya masa a maƙogwaronsa,
duk wannan abun da suke kanal yusif na jinsu bai ce komai ba haka zalika sauran y'an uwan nasa su irfan, sauraronsu kawai suke yi dama basu cika shiga faɗansu ba.
"Nima abunda nagani kenan Jahan kullum zaman kashe wando ya iya bai da wurin zuwa daga buga ball sai atake masa abinci a plate yaci yayi haikam ƙarshen wata nayi Babban yaya ya turo masa da dollars a account shiyasa gayanan duk yafi mu kyan gani,' fawan ne yayi maganar yana kallonsa daya ke suna facing ɗin juna a table ɗin,
ganin yadda suke ta faman yada masa magana a gaban ɗan aikinsu tukur yasa shi cewa "Ya Isa haka ! Ku ce koma me zaku ce! in da na gode ma Allah ma ba da son raina nima nake zaune gidan ba! Ciwo ne kuma zai iya samun kowa acikin ku!,' ya karasa maganar idonsa sun cicciko da kwalla,
Ran sehrish dake tsaye ba ƙaramin baci yayi ba ganin yadda manyan suka kasa dakatar dasu daga gaya masa magana musamman kanal yusif da yake babbansu a yanzu,
Dariya fawan yayi tare da cewa " aikin kenan! daga magana ƙaɗan sai ka nemi zubarwa mutane da hayawa kamar kafi kowa ruwan hawaye a ...' bai idasa maganar ba yaji saukar ruwan tea mai zafi a fuskarsa Allah yaso ba tafasasshe bane, ihu ya saki tare da faɗin "innalallahi junaid baka da hankali ne! ni ka watsa wa ruwan tea! wlh bazan yarda ba saina rama,
Hannunsa ya zura ya dauki kular da farfesu ƴan ciki mai zafin gaske ke aciki ya yunkura zai watsa wa junaid, da gudu junaid ya tashi , shima fawan ɗin yabisa kamar tom& jerry haka suka rinƙa zagaye wurin,
Hankalin sehrish ba karamin tashi yayi ba bata ta6a sanin haka suke ba wannan ai sai suyi kisan kai.
Ga haushin ƴan uwan nasa da take ji hankalinsu kwance sai ma umarni da suka bata ta zuba masu abincin nasu su ci, saving ɗinsu take yi amma hankalin ta nakansu Junaid da fawan dake ta faman ƴan guje guje , tsoran ta kada fawan ya zuba masa farfesun nan a farar fatar nan tasa mai laushin gaske don tasan tuni zaiyi mummunar ƙuna.
Har ta kammala saving ɗinsu ta koma ɗaki cikin rashin kwanciyar hankali, a bangaren su fawan kuwa dake faman faɗa tunda junaid ya samu ya shige room ɗinsa ya datse kofar, a dole fawan ya haƙura a zuwan Zasu haɗu ne ae ba kwana zaiyi a rufe ba,
Gaba ɗayansu sun fita tana jin tashin motocinsu, cikin sauri ta fita domin da ma ta ƙagara su fita taje ta sanarwa junaid ko ya samu yazo ya ci kalacinsa,
A falo ta gamu da azmi tana goge goge, cikin girmamawa tace"sannu da aiki aunty azmi me zai hana ki bani na idasa aikin tun da dama ni nake yi kinyi aiki sosai nasan kin gaji,"
fuskarta a sake ta ce" kada ka damu tukur ai an jima na nan, yanzu dai abinda zaka yi kabi bedrooms ɗinsu ka gyaggyara tsaf don Allah,'
Sehrish ta amsa mata da toh wuce wa upstair tayi ɗakin junaid babbuga kofan tayi, muryarsa taji yana cewa"wanene"?
Gyara muryarta ta yi tare da cewa"tukur ne mai aiki dama naga baka ci breakfast ɗinka bane,'
Ɗan guntun tsoki yaja tare da cewa"Naji a kawomin a ɗaki na zanci,'
Amsa sehrish tayi da toh sannan ta juya time ɗin da ta sauko azmi har ta kamma gyara falon yayi fes gwanin burge wa sai ƙamshi dake tashi, kai matar taji daɗi ga iya girki ga iya gyaran wuri ya koma kamar sabo uwa uba ga kyan hali, sehrish ta faɗa a ranta tana dan murmushi,
Kitchen ta wuce nan ma ta samu azmi ta gyarasa komai tsaf, shirya masa abincin tayi a tray, ta koma ɗakinsa nasa sai da ta jira ya 6uɗe mata sannan ta shiga.
Page 17-18
A wani madaidaicin table dake a bedroom ɗin nasa ta aza tray ɗin ta matsar dashi gabansa, yana zaune a gefen gadon yana daddana wayarsa,
satar kallon wayarsa tayi ba kowa ya faɗo mata a rai ba fa ce husanna da jahad tabbas tana bukatar tayi waya da su, amma babu hali cos bata da waya, kuma ba yadda za'ai ta ce zata ari wayar sa, hauka ma take yi ashe?
Muryarsa taji a kunnanta "Thank you zuwa nan da 30 mins ka dawo ka dauki tray ɗin,''
Ta amsa masa sannan ta fi ce, acikin ranta tana faɗin' tabbas ya kamata nakira naji wani hali husanna da jahad suke ciki wayyo Allah na gashi na lura kamar aunty azmi bata da waya a hannunta,
A ɗakinsu twins ta tsaya domin gyarawa masu shi, a hargitse ta samu ɗakin sun tarwatsa komai, haka ta kama aikin gyara masu shi, bed ɗin ta soma gyarawa bed sheet din takai hannu zata cire, tsayawa tayi tana kallon wani abu a jikinsa, wani irin ruwa ne mai kitib kitib kamar kokko mai yawan gaske a jikin zanin gadon, tunani ta soma yi' shin wannan menene ajikin zanin gadon a iya sani na gidan nan basa shan kokko to kodai madara ce ta zube a wurin gsky i na tunanin haka,
kasancewar zanin gadon maroon colour ne hakan yasa abun ya fito sosai raɗau, cike da jin kyankyami ta tattare bedsheet ɗin ta zuba a laundry basket ɗinsu,
Kammala gyaran gadon tayi sannan tayi mopping ɗin dakin tsaf ta gyara komai, gaban dressing mirror ɗinsu taje, mayuka tagani tsadaddun gaske iri iri, karaf idonta suka sauka akan wani kwalban magani, hoton dake a jikin kwalbar kawai take kwallo namiji da namiji ne zir babu kaya a jikinsu ɗaya yayi holding penis ɗin ɗayan,
Gabanta ne taji yayi mugun bugawa duk da batasan ma'anar hakan ba sai ranta ya bata cewa kawai magani ne na wani ciwon nasu na maza,
Kammala gyarawa tayi afterwards ta koma bathroom ɗinsu, anan ne fa kwalwarta ta ƙara rikice wa ganin wannan farin abun da tagani a bedsheets ɗinsu, gashi nan a har jikin bathtube ɗin ko'ina sun hargitsa shi, haka ta daure ta wawwanke ko'ina tass,
Bayan ta fito sai da ta sake duba kwalbar maganin nan a jiki taga an rubuta (Homosexual) shi kaɗai ta iya ganewa amma ita kanta bata san ma'anar kalmar ba don ba komai ta sani ba.
Sam ta manta da sakon junaid na ta koma after 30mins ta kwashi tray din abincin sa takai masa.
Sai da ta kammala gyarawa ɗakunan kowannansu ba ƙaramin gajiya ta kwasa ba, sauƙin ma ɗakunan sauran ba hargitsi ba kamar nasu Jahan da Ayaan ba,
Har yanzu sehrish ta gaza mantawa da wannan abun da tagani ɗakin su twins, akwai wani abu da ya tsaya mata a rai wanda take tuna shi da jima wa daya faru dasu tana kokwanton cewa kodai wannan abun ne, bakomai bane fa ce Sperm !!!
Tafiya take yi jikin ta a kasalance wata irin kasala ce ta dabaibaye ta, labari mara daɗin ji, abunda take kokarin yi musu shine (Kyakkyawan Zato)
Dakyar take taka matattalar benen, idonta a cike taf da hawaye 'Ya Allah kada kasa abunda nake zargi ya tabbata Ya Allah kasa nayi aiki na ba tare da na fuskanci wata matsala ba cikin salama na tafi nabar masu gidansu, ni kuɗi kawai nazo nema domin na taimaki ƴan uwana dake kwance asibiti bayan wannna bana bukatar wani abu,
Tura kofan room ɗin junaid ta yi, samun shi tayi ya gama cin breakfast bacci ya kwashe sa, sai sharar baccinsa yake cikin kwanciyar hankali da natsuwa,
ɗan murmushi ta saki tare da cewa" Ya Allah ka tsare wannan bawan naka bansan halinsa ba amma ina yi masa kyakkyawan zato"
Hannu takai zata ɗauki tray din karaf idonta suka sauka akan wayarsa dake ajiye saman nightstand, ba komai ya fado mata a rai ba fa ce ta saci wayarsa ta kira goggonsu taji ya lafiyarsu Jahad, murmushi tasaki a hankali ta soma tafiya cikin sanɗa, saɗaf saɗaf ta tafi,
Sai da tasha wahalar daukar wayar tasa sannan taga ashe thumbpring gare ta, dole sai da yatsansa sannan za ta 6uɗe, ɗafe kanta tayi tare da faɗin "wayyo Allah na" dama sarar ta ce,
Juyawa tayi tana kallonsa yadda ya ke kwance yana baccinsa a natse, sama ya ke fuskanta ya wawware hannayensa, murmushi tasaki tare da fadin 'abun zai zo mun da sauƙi,'
Hawa saman bed ɗin ta yi a hankali cikin sanɗa kamar mage, rarrafe a hankali tayi ta isa inda hannun damansa yake, yatsun hannunsa a buɗe suke gasu nan tsirara masu kyan gaske, bayan wayar ta juya inda thumbprint din ya ke, kwafa wa tayi a yatsansa na tsakiya, yasa mata wrong, matsar da wayar tayi ana gabansa cikin sa'a wayar ta bude, tsananin farin ciki ne ya bayyana a fuskarta, cikin sauri ta sauka ta lalla6a tafita ta tsaya a bakin kofan room din nasa, jikinta har kerma yake yi karta ya farka, tuni zufa ta soma tsastsafo mata a hancinta,
Time ɗin da ta aza idonta akan wayar, Hoton da tagani a wellpepper ɗinsa ne yasa jin zuciyarta wani irin bugu,
Zuba ma hoton ido tayi wato ainihin wani haɗaɗɗen matashin saurayi ne, ko a mafarki bata ta6a ganin mutun mai irin kyansa ba, kwayar idonsa ce tafi ɗaukar hankalinta, blue eyes ne da shi, wannan wani irin zazzafan kyau ne! irin wannan kyan shine mutane ke neman tsari da shi, jikinsa na sanye da kakin sojoji ba ƙaramin daukarsa su kayi ba, yayi hoton ne kamar a shirin film a saman mota yayi irin wannan zukunnawar da suke yi in zasu yi harbi da bindiga, hannunsa riƙe da bindigar yayi hoton, doguwar sumar kansa wanda ya ɗaure ta tsayin ta har bayan wuyansa baka wulik,
Kyawawan lips ɗinsa tabi da kallo dark pink kamar ya shafa janbaki, ga wani dogon hanci tubarkalla masha Allah,
Tayi nisa cikin ƙurewa hoton kallon, sam ta manta da abunda take kokarin yi sai da wayar hannunta tayi ƙarar shigowar sako sannan ta dawo hayyacin ta,
Da sauri ta shiga wurin contacts, numbar goggo ta rubuta ta danna mata ƙira, ba tayi tunanin ko akwai recharge card a phone din nasa ba, amma ranta ya bata cewa ba zama a rasa ba, su da kullum cikin kuɗi suke,
A jiyar zuciya ta saki jin numbern ya fara ringing, sai Allah Allah take suyi sauri su ɗaga before he get up,
Jin muryar goggo yasa sehrish sakin murmushin jin dadi
"Assalamu alaikum goggo sehrish ce! Ina jahad don Allah inason magana da ita cikin sauri," ta karasa maganar tana waige waige kar wani ya ganta,
On the other hand goggo ta miƙa wa jahaad wayar, cikin dauƙi ta ƙarba tare da fadin"yar uwa ! dagaske ke ce ! Wayyo Allah na farin ciki,"
Dariya sehrish tasaki jin abunda jahadar ta ce, kamar zatayi kuka itama ta ce"I really missed you my sisters, so much, dana ji voice ɗinki i just felt like to cry," ta karasa maganar idonta cike taf da hawaye,
"sister dama akwai abunda nake na fada miki amma narasa taya zanyi magana dake,"
Sehrish ta ce "yanzu ina jinki pls kiyi sauri ba wayata ba ce ta yaron gidan ce baisan ma na dauka ba,"
Cikin fargaba take sauraron jahaad ɗin"sister doctor ya ce ƙarshen month ɗin nan indai ba ayiwa husanna aiki ba, to ciwon nata zai habbaka sai dai a fidda ita ƙasar waje in ba haka ba mutuwa zata yi, sun sa mana ranar aiki 5 ga watan da zamu shiga...." kuka ne ya ci ƙarfin ta, itama sehrish ɗin kukan take yi haka suka dinga kuka ta wayar, babu mai lallashin wani,
"Idan kin gama wayar ina jira!!!
A firgice ta juya idanuwanta azare jin muryar junaid, rufe idonta tayi tare da buɗe su ashe kunnanta ne suka jiyo mata hakan sam bashi bane ,
Ganin ya fara yi mata gizau yasa ta ce da jahad ta ajiye waya, zasuyi magana next time in ta samu chance irin wannan,
Cikin sauri ta goge numbar goggo da ta sanya, a wayarsa da duk wata shaida da zata tona cewa tayi amfani da wayarsa,
Cikin sanɗa ta lalla6a ta mayar masa da wayar, har time din bacci yake yi,
Haka ta koma ɗakin ta tana sharar kwalla, safa da marwa ta shiga yi tana zagaye ɗakin, tunanin ta yadda zatayi ta samun kuɗin nan,
"Yanzu yaya zanyi! kada husanna ta rasa rayuwarta! sam bata cancanci haka ba, tazo duniya a wahalce kuma ta koma! Ya ilahi i dont ave any other choice fa ce kai Ya Allah, nayi imani dakai, kai kaɗai ne gatan mu, Ya Allah ka kawo mana mafita Albarkacin manzon Allah (SAW) ❤
Dakyar ta samu ta shiga toilet don wanke jikinta, ganin cewa basu da wani aiki a kitchen saboda guys ɗin gidan in suka fita sai da marece suke dawo wa, hakan yasa basa making lunch da wuri,
Don haka tana kammala wankan ta, da alwalarta tafito domin time ɗin azhar ya yi, har ta kammala sallah bata tuna cewa tabar gashin bakinta a cikin toilet ba,
A saman sallayar ta kwanta tun tana shesshekar kuka tana rokon Allah har bacci ya ɗauke ta,
Sehrish ta manta bata rufe kofan ɗakinta ba kamar yadda ta saba, shin na tuna mata ko kuma na kyale ta? tuna wa da cewa ba'a so a tashi mutun in yana bacci indai ba abu mai mahimmanci bane kamar sallah yasa na ƙyale ta, me zai biyo ba?
"Babu amfanin zama da mutun fasiƙi irin ka ! Ka saida mun ƴaƴa ! Saboda son abun duniya da son siyasa kai mutunne ko dabba! hakan baiyi maka ba sai da kabi ƴaƴana ka lalata musu rayuwa wannan wace irin masifab ce?
"Wayyo Allah abba kadaina dukan oumman mu, jini ke zuba a jikinta, oumma ki daina kada ya kashe ki ! Oumma! Oummahhhh!
Da ƙarfi ta ambaci sunan a firgice lokaci ɗaya ta farka, kukan da take a mafarkin har a fili sharkaf haka tayi da zufa, zaune ta tashi a fujajen tana kuka bil haƙƙi,
Dafe kanta tayi saboda wani matsanancin ciwo da yake yi mata, cikin shesshekar kuka take ambaton "umman mu,' fuskarta duk ta jagule dama dama da hawaye, da alama wani mummunan abune daya taba faruwa a rayuwarta ta tuna,
Haka ta dinga maimaita "Innalallahi wa inna ilaihirraji'un,
Cike da jimami ta tashi daga saman sallayar, agogon dake manne jikin bango ta kalla ƙarfe 4:00 dai dai time ɗin la'asar yayi har yana kan wuce wa,
dole ne ta canza sabuwar alwala saboda tayi bacci mai nauyi,
Cire hijab ɗin dake jikinta tayi ta aza asaman gadon, ta jiƙe sharkaf da zufa, shiga toilet ɗin tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, hannun na dafe da chest ɗinta, cire kayan jikinta tayi , ta sakarwa kanta shower , yadda sassanyar ruwan ke sauka a jikinta haka zuciyarta ma ke sauka daga hawan da tayi, (ruwa rahama Ne!) duk yadda kake cikin kunar rai indai zaka shiga ka watsa ruwa a jikinka to tabbas zaka samu natsuwa,
Bayan ta kammala bath ɗin ta karasa gaban mirror ɗin dake cikin toilet ɗin, tana bin jikinta da kallo, tana da tsayi ba laifi , sam bata da ƙiba amma ƙirjinta cike suke da boobs, sannan daga kasa akwai hips sosai faffadan gaske, launin fatarta choculate colour ce, expensive skin colour, tana da sexy eyes masu lumshe wa sometimes kamar na mai jin bacci wani lokacin kuma sai kayi tunanin tana shaye shaye ne, kwayar idonta fara ce tass mai launi brown colour, hancin ta ba dogo bane ƙarami ba ƙaramin kyau yayi mata ba, a bangaren lips kuwa tamakar shape ɗin love ❤ red colour masu tafshin gaske (macen novel ke nan komai nata is 100% 😂
Hannu tasa tare da shafa gefen wuyanta inda ke akwai wani rubutu a jikin fatar wurin da bakin rubutu kamar na tattoo aka rubuta (Sb) murmushi ta ɗan saki tuna wanda yayi mata rubutun, mayar da hannunta tayi akan sumar kanta wadda tayi tsayi yanzu ta sauko mata har kafaɗar ta , asalin gashin kanta har ƙugunta ya dira, amma silar hajjaju da ma'reeya suka datse mata shi saboda gudanar da aikin ta a matsayin namiji,
Tunawa da sallah yasa tayi gaggawar mayar da kayanta, ta dauki gashin bakinta da ta bari a gaban mirror, ta fita
Cikin sauri tayi sallar , bayan ta gama ta nufi kitchen wurin azmi taga in akwai aiki, samun ta tayi tana a ciki tana shirye shiryen fara aiki,
"Barka da aiki aunty azmi " sehrish ta faɗi hakan tana kallonta, ɗagowa tayi da fara a fuskarta tace "ke ke da sannu saboda naganki kina ta sharar bacci,"
Ras! Sehrish taji gabanta ya faɗi hankali a tashe take kallon azumi, itama kallon ta take tana sakin wani bazawarin murmushi, lokaci guda sehrish tabi ta susuce murya na rawa tace "dagaske kin ganni ina bacci !" dariya azmi tasaki tare da cewa "kwarai malam tukur ɗan basaja naganka kona ce naganki, "
Kallon kallo suka shiga yiwa junansu sehrish na tunanin tabbas ƙaryarta ta ƙare saboda azmi ta kira ta da ke amaimakon kai sannan taganta tana bacci da hijabi kuma ba gashin bakin nan nata da take sawa ya ilahi,
Yayin da azmi ke mamakin wayau irin na wannan yarinyar, har tasan tayi shigar namiji tazo gidan sojoji aikatau ko tsoro bata ji, gskya ba ƙaramar ƙuruwa ba ce,
Sai faman wurga ido sehrish take yi,hannu tashiga tafawa tana faɗin "nashiga uku shikenan komai ya ƙare"
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~
Page 19-20
sai faman wurga ido sehrish take yi,hannu tashiga tafawa tana faɗin "nashiga uku shikenan komai ya ƙare"
Kana kallonta ka ga tsananin tsoro a fuskarta, lokaci guda tabi ta rikice ganin bata da wani mafita fa ce ta roƙi azmi ta rufa mata asiri, don haka jiki na rawa takarasa gaban azmi ta zube saman kneel ɗinta tana roƙonta "nasan nayi laifi amma bani da wata mafita ne don Allah ki rufamin asiri aunty azmi kamar yarda Allah ya rufa miki,"
Hmmm ja da baya azmi ayi tare da cewa"am sorry to say bazan iya rufa miki asiri ba ! laifin zai shafe mu mu biyu, wannan babbar qarya ce a girma na bai kamata na goyi bayan hakan ba, sannan bugu da ƙari sojojin gidan nan suka gane cewa ke maca ce ba namiji ba to tabbas ƙasusuwanki za'a fidda daga cikin gidan nan! kinsan matsalarki ? Cikin sauri ta ce "a'a "
"matsalarki shine kin aikata laifi biyu, na farko namiji suke so a matsayin ɗan aiki ba mace ba, ke kuma kinyi shigar mace kinzo, duk sunyi tsammanin ke namiji ce hakan yasa suka amince da ke rinka shiga har ɗakunansu kina gyara musu da sauransu, nabiyu laifin ƙarya! sun tsani maƙaryaci, kinyi karya baiwar Allah idan har suka son da wannan zancen ko ! Ba ma ke ba ni kaina ta shafa! don haka cikin salama ki tattara kayanki ki bar gidannan kafin su ankara"
Azmi na kaiwa nan ta juya mata baya ta ci gaba da abunda take yi,
Jiki a mace sehrish ta miƙe, hawaye na gangarowa daga idonta kamar an kunna fanfo, cikin sanyin murya ta ce "shikenan...bakomai naji daɗin hakan zan tafi insha Allah,"
Fi ce wa tayi a guje tana shessheƙar kuka, fadawa tayi ɗakinta ta datse kofar ta faɗa saman gadon ( kamar a indian film 😂)
Tasha kuka kamar ba gobe lokaci guda fuskarta ta kumbura tayi suntum, idonta suka yi jawur suka ƙankance kamar na ƴan chaina,
Haka ta taso daga saman bed ɗin tana bin bedroom ɗin da kallo "ko a mafarki ban taba tunanin haka zata kasance dani ba, yanzu zan tafi nabar wannan daular, ni bama wannan bane damuwata ba ya rayuwar su husanna zata kasance su da suke cikin wani hali a asibiti, gashi bansamu kuɗin ba, wayyo Allah na, bansan wane irin zunubi muka aikata ba da rayuwarmu bata tafiya adai dai ba, tun kafin mu mallaki hankalinmu mu ke fuskantar ƙaddara iri iri meyasa !?
Zube wa kasan tiles ɗin tayi tana kuka jikinta har jijjiga yake yi,
Sam bata ji shigowar azmi ba sai dai mutyarta taji ta dirar mata a kunne" Ya sunanki ? ta jefa mata tambaya ,
yunkurawa tayi ta tashi tsaye tana matse hanci ta ce "SEHRISH"
Jinjina kai azmi tayi tare da ƙarasawa inda take, tafin hannunta ta sa tana share mata hawaye, sam sehrish bata yi tunanin hakan ba,
sannan cikin natsuwa ta ce" nayi takaici dana sa wannan kyakkyawar fuskar zubda hawaye am so sad," cike da mamaki sehrish ke kallonta, azmi ta ci gaba da cewa "kiyi hakuri ko kusa bazanso na raba ki da aikin ba! duk da ina tsoran abunda zai biyo baya, amma zan iya jurewa don ganin na taimaka miki," jin wannan bayani yasa sehrish sauke nannauyiyar ajiyar zuciya,
mayar da hannunta tayi a saman shoulders ɗinta taci gaba da cewa" da farko ina so ki fadamun dalilin dayasa ki kayi basaja a matsayin namiji"?
Muryar na rawa ta soma magana cikin sheashekar kuka" ƴan uwana ne basu da lafiya rai hannun Allah an kwantar dasu asibiti, kuma doctor ya ce aiki za'a yi musu, shine nake kokari naga nasamu ƙudi na biya musu, ɗayar ma dr yace in har ya wuce 5 ga watan da zamu shiga sai dai a fidda ita Qasar waje ko tarasa ranta.....' kukan ne yaci ƙarfin ta,
Cikin lallashi azmi ta ce "daina kuka ya isa haka, na fuskanci matsalarki, duk da ina buƙatar bayani amma bani da enough time, riƙe wannan zamuyi magana an jima yanzu dai taimakon da zan miki shine, zaki ci gaba da aiki a matsayin Namiji kamar yadda kike yi, ko da gigin wasa karki bari su gane cewa ke maca ce ! sannan maganar kuɗi kuma nawa ne ake bukata ?
Azmi ta tambaya tana kallon ta, sehrish ta ce "dubu ɗari tara ne" a tunanin ta azmi zatayi shock in taji kuɗin amma sai taji tace"zan iya ansar miki albashinki na wata na shekara ɗaya da rabi ! a baki a ɗunkule amma inaso ki sani ! duk runtsi duk wuya duk kuma duk irin wahalar da zaki fuskarta da wulaƙanci a wurin masu gidan nan, dole kiyi haƙuri ki jure! kiyi musu biyayya sau da ƙafa, ba maganar barin aiki , in kuma har kika ce zaki bari toh sai fa kin biya sauran kuɗin da kika ƙarba kin amince!!? 😰
taji ma tana nazari kafin tace"Eh na amince !!! zuciyarta na wani irin bugawa ba kowa ya faɗo mata a rai ba face Ayaan da jahaan , ynx ana nufin ta ɗaura aure da kaddararta na zama cikin gidan nan! ya ilahi,
"Yanzu account number zaki bani na wanda za'a turawa kuɗin aikin nasu," azmi ta faɗa tana kallon cikin idonta, tsananin farin ciki ta gani a fuskar sehrish 😇
cikin jin daɗi tace "babu a wuri na amma zuwa anjima ko gobe zan samu na kawo miki," azmi ta amsa da toh sannan ta kama hanyar fita har takai bakin kofa xata buɗe ta juya ta kalli sehrish dake ta faman sakin murmushi tace "kada ki manta ynx kina ƙarƙashin Iko na! komai zakiyi saida umarnina, idan har kika saba hakan, hmmmm,
bata ida ba ta fi ce,
sam sehrish bata damu da hakan ba, ita dai indai akan sisters ɗinta ne toh ko fiye da hakan ma zata iya jurewa,
Jiki na rawa baiwar Allah ta shige toilet ta dauro alwala taci gaba da zabga nafilfilin miƙa godiya wa ubangijin mu Allah subhanahu wata'ala,
Matsalar su husanna tazo ƙarshe, sauran damuwa ta kau, shin yaya kke tunanin rayuwar sehrish zata kasance a gidan ABBAN SOJOJI ? 😢
yinin ranar da fara'a a fuskarta hakoranta a washe kamar mai tallar maclean, cikin jin daɗi suka gudanar da aiki a kitchen tare da azmi don shirya dinner,
tunanin yadda zata sake ɗaukar wayar junaid takira husanna ta ce su turo mata account number, har zuciyarta take jin ƙaunar azmi saboda tayi mata rana ! Har abada kuwa ji take bazata taba sa6a mata ba! tayiwa kanta alkwarin zatayi mata biyayya bazata taba bijire mata ba ko taci amanarta ba,
A 6angaren junaid kuwa, bayan ya tashi daga bacci da jimawa ya wuce masallaci daya dawo ya tsaya a filin da suke buga ball na gidan tare da wasu daga cikin sojojin dake tsaron gidan,
yunwa ce tasa shi shigo wa ciki after magrin prayer, muryasa suka dinga ji yana kiran "tukur ! ,
Wani irin farin ciki ne ya lullu6e sehrish, cikin ɗauki ta ajiye wanke wanken da take yi agaban fanfo, na kayan da suka yi amfani dasu,
Karasawa tayi wurinsa yana zaune saman 3 seater, yana daddana wayarsa, cikin girmamawa tace"gani ya ya junaid" ta kirasa da hakanne saboda ya hana ta ce masa yalla6ai, girman jiki ne kawai dashi da kuma tsawo fuskarsa ce kawai zata nuna maka cewa yaro ne sharkaf,
ta6e baki yayi tare da ɗan jefa mata kallo ya ce" ƴunwa nake ji, " ya faɗa a shagwa6e, yana kallon ta
cikin zumuɗi ta ce " a shirya ma abinci a dining ko nan zan kawo maka,?
ta tambaya tana kallon wayar hannunsa kamar ta fisge ta saboda ita take bukata,
ɗan yatsina fuska yayi kafin ya ce" No a tsarin gidan nan bama iya cin abinci in ba tare da junan mu ba, duk yunwar da mutun ke ji dole sai an tattara an haɗu a table aci a tare, don haka kawo min coffee kawai, zan jira brothers ɗina su dawo sai mu ci dinner a tare,"
Wannan haɗin kan nasu ya burge sehrish sosai, suna son junansu, juya wa tayi, taje da tadawo hannunta dauke da cup din saman ɗan plate ɗin da ake aza sa, miƙa masa tayi tana kallon fine face ɗinta,
Ƙarba yayi tare da faɗin"thanks"
komawa dining room ɗin tayi, tana goggoge chairs ɗin dake kewaye dashi, daga inda take tana satar kallonsa shi da yake zaune a falo,
Bayan ta kammala ta koma kitchen ɗin, azmi ta samu tana a ciki tana ganin ta ta ce "yawwa mlm tukur ayi maza a fara jera abincin a dining ko," sunnar da kai ƙasa sehrish tayi cikin jin kunya, azmi tace "gsky hajjaju yar daru ce! da ita duk aka shirya wannan ƙaryar," murmushi kawai sehrish take yi tana wasa da yatsun ta,
Ba tare da bata lokaci ba, suka soma shirya abincin, tana kaiwa tana jera masu,
Ƙiris ya rage a fara kiran sallar magrib, bayan sun girma shiryawa azmi ta wuce ɗakin ta , sehrish kuwa falo ta wuce, anan ta samu Junaid yana sharar bacci, ya mimmiƙe kafafuwansa a saman doguwar kujerar, Alhamdulillah thanks to Allah ta fadi hakan, ƙyalle ido tayi ta ga inda ya ajiye wayarsa saman chest ɗinsa,
Cikin sanɗa ta soma tafiya a hankali a hankali take takawa, har ta idasa isa gabansa, leƙa fuskansa tayi kyakkyawa mai annuri, dimples ɗin nan nasa a lotse, kamar ba bacci yake yi ba,
Hannu takai a hankali ta ɗauki wayar tasa cikin rashin sa'a ta zame daga hannunta ta faɗi kasa ta daki haɗaɗɗen tiles ɗin dake kasa, har cikin zuciyarta taji faɗuwarnan, tsadaddiyar waya irin wannan, dafe ƙirjin ta tayi tana kallon wayon, ƙarar faɗuwar wayar tasa junaid yunkurin buɗe idonsa daga baccin da yake, cikin sauri ta boye bayan hannun kujerar tana sauke ajiyar zuciya, gyara kwanciyarsa yayi ya ci gaba da bacci, jin sakin ajiyar zuciyarsa yasa ta gane ce ya koma baccin nasa, hannu ta zura ta janyo wayar tana kallon screen ɗinta, Alhamdulillah ta fada ganin ba abunda ya same shi,
Yunƙurawa tayi ta tashi tsaye, tana kallon sa, ya aza hannunsa ɗaya a saman stomach ɗinsa, ɗayan kuma a saman kansa, abun yazo mata da sauƙi, don haka cikin sauri ta jona wayar a yatsarsa, nan take wayar ta buɗe,
murmushin jin daɗi ta saki, wannan hoton ta sake gani a wallpaper ɗinsa na wannan haɗaɗɗen matashin saurayin, har ranta so take tasan wanene wannan sarkin kyawun nan,
Ja da baya tayi a hankali tayi nesa dashi, izuwa gefen stair ta tsaya, contacts dinsa ta shiga ta rubutu numbar goggo, bugu ɗaya wayar ta shiga kuma aka ɗaga, cikin sa'a muryar jahaad taji tana kwaɗa sallama, da farin ciki ta ce"Jahaad ni ce Sehrish! banda isasshen lokaci pls listen to me," a can 6angaren jahad ta natsu tana sauraron abunda sehrish zata ce mata"Nasamu kuɗin aikin account number zaki turomin cikin gaggawa saboda na fadamiki wayar ta yaron gidan ce nake dauka shi kansa baisani ba,"
tsananin farin ciki ne yasa jahad yin ihu da fadin Alhamdulillah a cikin wayar tasu, ta ce "narasa inda zansa kaina don farin ciki ƴar uwa kice mun kusa barin asibitin nan dama wlh nagaji da zamansa...." sehrish ce ta katse ta ganin zata ja masu lokaci ga tsoran kar junaid ya farka "ke ba surutu zakiyi mun ba ki anso acct number ɗin likitan yanzu yanzun nan ki turamin kada fa ki 6ata lokaci asiri na zai tonu,"
Tana gama faɗan hakan ta yi rejecting kiran, ta tsaya nan tana jiran shigowar saƙon jahaad, jikinta har rawa yake gudun kar junaid ya farka, har leƙen sa take yi taga ko yana motsi,
Safa da marwa tashiga yi kamar mai ɗawafi, Allah Allah take jahaad ta turo saƙon tayi sauri ta kwafa ta mayar masa wayarsa,
tana nan tana jira, tajiyo ƙarar shigowar motarsu Ayaan,da wata irin jiniya motocin nasu ke shigowa, aiko nan take junaid ya soma motsi , saboda tsabagen ruɗu 😳, maimakon taje ta ajiye masa wayar ta ruga , sai ta haɗa da wayar duka ta watsa aguje sai bedroom ɗinta.
Ana dara ga dare yayi ?😳
tashi zaune yayi tare da yin miƙe, da hamma lokaci guda hannu yasa ya rufe bakin nasa, wayarsa ya soma lalube yaga bata nan bai kawo komai aransa ba sai yayi tunanin ko ya barta a room dinsa ne,
Shigowarsu brothers ɗin nasa ne yasa shi, sakin fara'a , a jere suka shigo su 7, ƙarasa wa kanal yusif yayi ya russuna tare da rungumesa yace"barka da hutawa my bro ina fata kana cikin koshin lafiya," da fara'a ya amsa masa da cewa "am fine bro kun dawo lpy," kanal ya masa masa da eh, kafin ya wuce, shima khaleed karasawa yayi inda junaid ɗin ke zaune ya rungume sa tare da cewa"My sweet bro ya enjoyment," bai basa amsa ba sai murmushin da yayi masa, haka irfan da jabeer duk suka rungumesa kafin suka wuce ɗakunansu,
Ya rage saura twins da fawan, harara fawan ya sakar masa tare da wuce wa ta gabansa yana rera waka cikin zolaya yake cewa"Lalatacce lalatacce ne ko a gidansu wannan haka yake," ɗaure fuska junaid yayi don ya tsani tsokanarsa da fawan ya ke yi,
A tare Ayaan da Jahan (Masoya 😂) suka ƙarasa kowanne ya manna masa kiss a cheeks ɗinsa kafin suma suka wuce ciki,
Shima junaid ɗin tashi yayi ya shiga ciki domin ɗauro Alwala saboda liman na ta kwaɗa kiran sallah,
A bangaren sehrish kuwa, tana nan maƙale da wayar junaid a hannunta, zuciyarta na harbawa, sai zagaye ɗakin take tana faɗin, nashiga ukuna ynx ya zanyi in junaid ya nemi wayarsa ya rasa, in kuma ya ganta a hannuna nasan dukan tsiya zan sha, kuma su kore ki daga aiki ace mun 6arauniya, yanzu ya zanyi ni nasamu na mayar masa da wayarsa wayyo Allah na,
Ƙarar shigowar message ne taji ƙirrrr! da sauri ta duba, account number ne jahad ta turo mata, cikin sauri ta laluba cikin drawer chest, inda ta ajiye diary din da take rubutu acikinsa Wanda tazo dashi , biron da ta saka a tsakiyar littafin ta dauko ta bude page tayi copying numbers ɗin, tana gama wa , ta mayar ciki ta ajiye,
Sannan ta yi hanzarin deleting sakon daga wayar tasa, fitowa tayi daga ɗakin tana leken ko akwai mutun, duk basu kai da fito wa,
har tasa hannu zata koma ciki taji alamun mutun, junaid ɗin ne ya fito yana naɗe hannun rigarsa, da alama masallaci zai wuce,
Ba karamin dadi taji ba, yana fi ce wa, ta lallabawa cikin sauri ta shiga ɗakinsa ta ajye masa wayar a saman nightstand,
Fito wa tayi tana sauke ajiyar zuciya, yanzu abunda ya rage mata takai ma azmi acct number ɗin,
ɗaki ta koma, ta ɗauki diary ɗin ta yago papern data rubuta numbar, ta fito ta tunkari ɗakin azmi, dayake ba nisa yana kusa da nata, wannan ne karo na farko da ta fara shiga ɗakin ta,
Sallama tayi, azmi dake zaune saman sallaya ta amsa da "wa'alaikum salam shigo ciki,"
Cikin natsuwa sehrish ta shiga ciki, wuri ta samu ta zauna kusa da ita ta lankwashe kafarta tayi zaman cin tuwo,
Cazbaha take ja, a hannunta ɗan murmushi tayi tace"wai malam tukur ne yau a ɗakin namu kodai mafarki nake ne? Cikin jin kunyarta sehrish ta ɗukadda kai tana murmushi,
"tabbas kuwa shine to mara ba lale marhaban daga ganin wannan gashin bakin naka akwai magana," dariya ce ta kubce ma sehrish, ta shiga 6a66aka ta,
daga bisa ni ta tsagaita tare da cewa "aunty azmi dama acct number ɗin ne na kawo miki," ta karasa maganar tana miƙa mata paper ɗin, karba azmi tayi tare da fadin"kin tabbata ta likitance? Sehrish ta ɗaga kai tare da cewa "Eh tashi ce,"
"Toh shikenan kije kawai insha Allah zuwa gobe za'a tura masu kudin,"
Azmi ta fada tana adana takardar a saman carpet din.
~ABBAN SOJOJI~
Written by
~HAFSAT BATURE~
~Boss Lady~
Page 20 to 21
sai faman wurga ido sehrish take yi,hannu tashiga tafawa tana faɗin "nashiga uku shikenan komai ya ƙare"
Kana kallonta ka ga tsananin tsoro a fuskarta, lokaci guda tabi ta rikice ganin bata da wani mafita fa ce ta roƙi azmi ta rufa mata asiri, don haka jiki na rawa takarasa gaban azmi ta zube saman kneel ɗinta tana roƙonta "nasan nayi laifi amma bani da wata mafita ne don Allah ki rufamin asiri aunty azmi kamar yarda Allah ya rufa miki,"
Hmmm ja da baya azmi ayi tare da cewa"am sorry to say bazan iya rufa miki asiri ba ! laifin zai shafe mu mu biyu, wannan babbar qarya ce a girma na bai kamata na goyi bayan hakan ba, sannan bugu da ƙari sojojin gidan nan suka gane cewa ke maca ce ba namiji ba to tabbas ƙasusuwanki za'a fidda daga cikin gidan nan! kinsan matsalarki ? Cikin sauri ta ce "a'a "
"matsalarki shine kin aikata laifi biyu, na farko namiji suke so a matsayin ɗan aiki ba mace ba, ke kuma kinyi shigar mace kinzo, duk sunyi tsammanin ke namiji ce hakan yasa suka amince da ke rinka shiga har ɗakunansu kina gyara musu da sauransu, nabiyu laifin ƙarya! sun tsani maƙaryaci, kinyi karya baiwar Allah idan har suka son da wannan zancen ko ! Ba ma ke ba ni kaina ta shafa! don haka cikin salama ki tattara kayanki ki bar gidannan kafin su ankara"
Azmi na kaiwa nan ta juya mata baya ta ci gaba da abunda take yi,
Jiki a mace sehrish ta miƙe, hawaye na gangarowa daga idonta kamar an kunna fanfo, cikin sanyin murya ta ce "shikenan...bakomai naji daɗin hakan zan tafi insha Allah,"
Fi ce wa tayi a guje tana shessheƙar kuka, fadawa tayi ɗakinta ta datse kofar ta faɗa saman gadon ( kamar a indian film 😂)
Tasha kuka kamar ba gobe lokaci guda fuskarta ta kumbura tayi suntum, idonta suka yi jawur suka ƙankance kamar na ƴan chaina,
Haka