Copied By
YAYA HAYAT
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
Cool novel, makeup and kitchen2⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen3⃣)
WHATSAPP NO:
+2349030159301
👩🏻💻.
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_story & editin_
*_aunty Bilyn Abdul_*
_Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty bilyn Abdul_*
*_Bismillahirrah manirrahim._*
*_gareku Readers._*
_assalamu alaikum, da farkodai nasan zakuyi mamaki, auntyna, bilyn Abdul itace tayi tallan buk d'in nan ABDUL-MALEEK, daga baya kuma sai tafasa rubutawa saboda wani aiki data zomata._
_to nikam nakaranta buk d'in danta rubutashi tuni a littafi yana ajiyene, littafin yayimin dad'i Dan haka nanemi izini tabarni na rubutamuku._
_nidai Marak'isiyya ba writer bace, wlhy koza'a kasheni bana iya rubuta page d'aya na novel, to amma yanzu zanyi muku copy insha ALLAH, ina fata zaku kasance dani kamar aunty bilyn Abdul, Dan labarin natane. Ngd._
*_sanda tayi tallansa ta rubuta sadaukarwa ga Abba Gana, batul mamman, bily giro, tonima zan cikamata niyyarta, Dan haka sadaukarwane ga wad'annan mutane uku._*
*_page 1⃣&2⃣_*
Kowa ka kalla yana harkokinsa acikin makarantar, wasu karatu sukeyi wasu kuwa hira da samarinsu ko k'awaye.
Shigowar wata bak'ar mota wulik cikin makarantar shine yaja hankalin mafi yawan d'aliban.
Safna tasaki Baki da hanci da ido itama tana kalo.
Motar tatsaya daidai wata bishiyar dalbejiya, ayanzu kallo yakomane akan Wanda zai fito daga cikin wannan mota mai k'yau da d'aukar hankali.
K'afarsa yafara zirowa k'asa maisanye da sauciki na farin takalmi, yakuma zuro d'ayar itama, saikuma yafito gaba d'ayansa.
Ajiyar zuciya safna ta sauke tareda fad'in ya salam!.
Zeenat tad'ago tana kallonta Dan ita kokad'an batasan bikin da akeyiba, tasaka iyafis akunne tana wayane.
Safna wai lfy mikike kallone haka kamar wata sakara?.
Safna da bakinta yaymata nauyi takasa cewa uffan, tad'aga hannu dak'yar tanuna mata matashin saurayin dake tsaye, Wanda ak'alla zaikai shekara 33 aduniya.
Masha ALLAHU zeenat tafad'a itama tana mik'ewa tsaye.
Farine sosai dogo kuma dankuwa yanada tsayi sosai, kallo d'aya zaka masa kagane k'ak'k'arfane saidai bashida k'iba, masha ALLAHU akwai k'yawun fuska, gashi kuma ya k'awata fuskar tasa da saje bak'i sid'ik, yakwanta sai wlk'iya yakeyi, sanyake da farar shadda wando da Riga d'inkin zamani, kayan sun masa k'yau....
Tunaninsu yatsaya lokacin dasukaga ya sunkuya yafiddo wata yarinya mai tsananin kama dashi, "bazata wuce shekara 6 ba aduniya.
Sanye take da doguwar riga ja iya kwaurinta Dan batakai k'asaba, ank'awata adon rigar da fararen filawoyi, kanta kam kalbace irin mai nannad'ewarnan kamar igiya (twisting), yasha ribom ja da fari, sai lilo sukeyi.
Ta rik'e d'an k'ugunta da hannu biyu tana kallon saurayin, baby inanenan mukazo?, tafad'a tana bin ko ina da kallo.
Murmushi yay mata Wanda yazauta dayawan 'yammatan gurin, musammamma safna, shima yarik'e k'ugunsa baby nan makarantace, munzo wajen uncle Hamza ne.
Lah baby dama uncle Hamza baigama makarantaba har yanzu?, yafayi babba sosai?.
🤦🏻♂kansa yadafe ya ce, "o,o me baby, kefa magana bata k'are miki, kinga muje ciki saiki tambayesa.
'Yar dariya tayi tareda kama hannunsa suka nufi office d'in uncle Hamza, Wanda yakasance lecturer a makarantar.
Cikin farinciki uncle Hamza yamik'e cike da murmushi yana fad'i oyoyo Nawal d'ina.
Itama sakin hannunsa tayi taje da gudu tashige jikin uncle Hamza, yarungumeta yana juyi da ita suna dariya.
Shikam yajingina da k'ofa yana musu murmushi, uncle Hamza ya ajiye Nawal suna sauke numfashi da dariya.
Sai sannan ya kalli saurayin, cikin zolaya ya ce, "oyoyo my Bobo!.
Shima hararsa yayi cikin wasa, kace hakafa yanzu, bayan baka kulaniba tun d'azu sai baby.
Hhhhhh afuwa kasan nida Nawal ba'a shiga tsakani, daga ina haka?.
Bobo yayi murmushi yana sauke numfashi, wlhy daga gidansu Ni'ima muke kasan mama babu lfy shine nace bari mubiyo mugaisheka.
Kai amma naji dad'i wlhy sosai, amma yajikin mama?, da sauk'ika gsky.
To ALLAH yak'ara sauk'i, nima anjima nashiga nak'ara dubata.
Okey ALLAH yakaimu.
Surutu Nawal takema uncle Hamza babu ko k'ak'k'autawa, shikam sai dariya yakeyi.
Bobo kam yamaida hankalinsa akan latsa wayarsa.
Aka kwankwasa k'ofar.
Uncle hamza ya ce, " ashigo."
Safna ce da zeenat k'awarta, risinawa sukai suna gaishesu, idon safna nakan bobo.
Uncle Hamzane kawai ya amsa, amma Bobo ko d'agowa baiyibama.
Safna incedai lfy?, uncle Hamza yatambaya yana kallonsu.
Zeenat ta zunguri safna dake kallon Bobo babuko k'yafta ido.
Uncle Hamza yana kallonsu, Dan haka ya girgiza kai.
Ina saurarenku yak'ara fad'a idonsa akansu.
Um....um sir dama..... Saikuma tayi shiru tana satar kallon bobo.
Bobo yad'ago yad'an kallesu fisha saikuma yamik'e, Ya Hamza bari muwuce mubarka da d'alibanka.
Baby oya tashi muje.
"Kai bobo da wuri haka?, cewar uncle Hamza yana kallonsa.
Karka damu gobe idan ALLAH yakaimu zanshigo na gaida aunty Ruky, baby taso mana.
Nawal ta mak'ale kafad'a zatayi kuka, a'a nidai zan zauna wajen uncle Hamza.
Harararta yayi baby banason rigimar banza fa kinsani, idan nabarki da aikinsa zaiji kokuwa da shegen surutunki magananniya.
Dariya uncle Hamza yayi, yashafa kumatun Nawal, kinga my durling kibisa kuje, idan natashi aiki, zanzo gidan Ammi na d'aukeki nakaiki wajen ya Ahmad ko?.
Da sauri ta d'aga kai tana 'Yar dariya, by by uncle.
By my Nawal.
Hannu bobo yabashi sukayi musabaha yafita rik'e da hannun Nawal.
Duk abinnan yana faruwane agaban su Safna.
Safna tabisu da kallo kamar ta had'iyeshi.
Murmushi uncle Hamza yayi, Dan yasan K'anin nasa yayi sata batareda yasaniba.
Ina jinku yafad'a yana maids hankalinsa kansu...........
_Ku kasance da Marak'isiyya_
*_(auntyna bilyn Abdul, abar alfaharina.)_*
Tana nan tana shiryo muku had'ad'd'en buk, saikungansa😉😘
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
3⃣&4⃣
........cikin in ina safna ta ce, "sir dama akan test d'in dakayi jiyane, wlhy banida lfy shiyyasa banshigo school ba.
d'an murmushi yayi kawai, yasan bayau yafara lecture safna bata nanba, amma bata ta6a neman afuwaba sai yau.
Ita kullum kanta Asama yake, tana gani tafi kowa, yasan yauma akwai abinda yakawota, bai wuce ganin bobo ba datayiba, Dan kallon datake masa kawai ya fallasa asirin zuciyarta.
Ajiyar zuciya yasauke tareda fad'in babu damuwa safna zan duba.
Godiya suka masa suka fice.
Binsu yayi da kallo yana girgiza kai, afili ya ce, " lallai safna kinada aiki, bakisan waye Abdulmalik bobo ba.
*_Wacece safna?._*
Alh Bilal mai Gold, shine sunan mahaifinta, cikakken bakano d'an asali, d'an kasuwane babba Wanda yake juya Gold yazama Naira.
Matarsa d'aya Haj Sa'adatu, suna kiranta (Ummi).
Yaransu hud'u mata biyu maza biyu.
Shaheed shine babba, yayi aure harda yara biyu, sai Muneer shima yayi aure, matarsa tanada tsohon ciki yanzu, sai Safna tana karatu yanzu, saikuma auta Rahma, bana ta kammala Secondary.
Yaran 'yan gatane sosai, saidai wannan baihanasu samun tarbiyyaba, iyayensu suna kula dasu sosai.
Saidai Safna batajin magana ko kad'an.
Wannan kenan.
++++++++++++
Suna fitowa daga office d'in zeenat taja tsaki, kai Safna ALLAH yau kinbani haushi, wai ina ajin nakine?, haba Dan ALLAH, jibafa kigani sabida wulak'anci kod'agowa yakallemu baiyiba yanata latsa waya, daga k'arshema saiyayi tafiyarsa.......
Kinga zeenat ya isheni haka, idanfa bazaki taimakamin nakai ga nasaraba tofa sauraramin, ninagani na ce, "inaso, angaya miki shi sakaran namijine da 1 time zai dubemu, ashema babu aji taredashi.
Mtsooow zeenat taja tsaki, aii idanshi ya iya rik'e NASA ajin, kekam naki yana hanyar zubewa.
Tana gama fad'a tayi gaba abinta.
Itama Safna abin yabata haushi, danhaka tashige motarta tayi gida
+++++++++
Bobo kam gida yanufa abinsa, yana tsaida motar Nawal tafita da gudu zuwa cikin gida, kansa yagirgiza yana fad'in ALLAH ya shiryeki baby.
(nace amin).
Bayan yakashe motar yakwashi wayoyinsa shima yay ciki.
Ammi dake zaune Nawal nakusada ita ta kwa6e fuska zatayi kuka, ta amsama bobo sallamarsa.
Yak'araso cikin falon yana kallon Nawal, kekuma lfy daga dawowarmu?.
Ammi tasauke ajiyar zuciya ta ce, " maganar kullumce dai takawo rigimar.
Shiru yayi baice komaiba.
Ammi takalli Nawal dahar tafara hawaye ta ce, "haba tagidan Appa kiyi hak'uri insha ALLAHU kinkusa ganin momynki kinji.
Da sauri bobo yad'ago yana kallon ammi, k'irjinsa sai harbawa yake da k'arfi, yakasa cewa komai.
Ammi takauda kai, ranta a6ace ta ce, " nagaji da ganin kukan yarinyarnan wlhy, amma babu komai bari Appanku yadawo, zand'auki mataki.
Hannun Nawal takama suka haura sama.
Bobo tamkar zai fasa ihu haka yakeji, yarintse idanu zuciyarsa na zafi, afili ya ce, "baby miyasa kikeson sakani a matsalane?.
Ganin babu maibashi amsa yamik'e yanufi d'akinsa.
*_Wanene Bobo_*
Abdulmalik d'ane ga Alh Aliyu Abdulmalik Hamshak'i.
d'an siyasa sananne wad'anda suke gwagwar Maya da ilimi dakuma nemawa talakawa 'yancinsu, matarsa d'aya Haj. Zahura (Ammi).
Yaransu shidda maza hud'u mata biyu.
Is'haq shine babba, yanada mata d'aya da yara hud'u, sai Sulaiman, shima yaransa uku da mata d'aya, sai Hamza matarsa d'aya shima da yara biyu, sai Abdulmalik (matarsa ta rasu) yarinyarsa d'aya, sai 'yan biyu duk mata basuyi aureba.
ALLAH ya azurta Alh Aliyu Hamshak'i da yara maza masu kwazo da himma, yaa is'haq ma'aikacine na banki, yaa Sulaiman kuwa likitane, sai yaa hamza lecture, sai Abdulmalik (bobo) cikakken lauya mai zaman kansa.
Kansu ahad'e yake, idan kagansu saika d'auka abokaine musamman ma yaa hamza da Abdulmalik, komai zasuyi saida shawarar junansu.
*_Abdulmalik_*
Mutumne mai zafi da sauk'i, gaba d'aya 'yan uwansa yafisu fad'a, saidai zasuzo daidai da ya is'haq (Dan shima mafad'acine).
Abdulmalik mutumne dabayason raini ko kad'an, baya wasa da mutane, baizama dolema kuzauna har kurabu kaga dariyarsaba, kullum cikin d'aurewa yake, amma yanada son jama'a sosai.
Abdulmalik bobo, yasamo sunan bobone tun yana k'arami, kasancewarsa mayen shan Bobo sai 'yan uwansa suke kiransa da bobo, ahankali sunan yay tasiri kowa Yakoma cemasa bobo, bayan ya girma saiya zama bobo na gsky saboda gayunsa ga k'yau ga kud'i ga ilimi, komaidai zam zam.
Bayan ya kammala karatunsa yafara aiki iyayesu sukace saura aure.
Yay tsalle yadire bashida budurwa, wannan yasa Appa yanema masa auren d'iyar k'anwar Ammi mai suna Ni'ima.
Da farko baya sonta ko kad'an, amma k'yawawan hali irin na Ni'ima yajanye hankalinsa harya tsunduma a k'aunarta.
Shekararsu biyu da aure ta haihu mace, wadda taci sunan Ammi, suna kiranta Nawal, shekarar Nawal d'aya Ni'ima takuma samun ciki, amma wajen haihuwa ALLAH yay mata rasuwa itada abinda ke cikinta.
Bobo yashiga rud'ani Dan saida aka had'a da addu'a sannan yadawo daidai.
Tundaga nan baisake kallon wata mace da sunan so ba, damashi matan bawani damunsa sukaiba.
Bobo yanada k'yau daidai gwargwado, gashi d'an gayu, akwai tsafta da iya d'aukar wanka, dolene mace mai lfy taga bobo ta k'yasa, kullum cikin k'amshi yake.
Shiyyasa Madeena ta k'yasa.
(To aunty bily dai ta ce, "ki kama kanki Dan bama kulaki zaiyiba, danshi aharkar mata ba gwani bane😜).
Shekarar Ni'ima 5 kenan da rasuwa amma bobo yak'i k'ara aure, iyayen sunata fama dashi amma yak'i sunata fama saidai yace zaiyi amma yak'iyi.
Kullum zancen Nawal akaita gurin momynta, haka take damunsu Ammi da Appa hardashi dadyn Nata, itadai tanaso taga momynta, kullum zancen kenan.
Abin yana damun yayyensa da iyayensa, shikam ko'a kwalar rigarsa, harkar gabansa kawai yakeyi.
Wannan kenan.
*_Mundawo labari_*.........
*_{Aunty bilyn Abdul na gaisheku masoya😘😍.}_*
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
5⃣&6⃣
........Safna tadanna hon afusace, da sauri maigadinsu yazo yabud'e mata get, ta danna hancin motarta cikin gidan, tana kashe motar tasuri jakarta da wayoyinta zuwa cikin gida.
Wani wawan tsaki tasaki Dan ganin Rahma k'anwarsu kwance akan cinyar ummi.
Daga Ummi har Rahma baki suka saki suna kallonta.
Ummi ta ce, "kekuma lfy daga shigiwa zakiyi mana tsaki?, wai Safna ban hanaki halinnanba ne?.
Baki ta turo gaba tana Harar Rahma, haba Ummi ALLAH wannan abun kunyane, wannan k'atuwar yarinyar shrkara 17 haryanzu bataida halin yaraba, aiiko jafar d'in ya Shaheed baya wannan ta6arar.
Rahma ta girgiza kai danjin akanta yayar tata take tada jijiyar wuya, tarasa miyasa basa shan inuwa d'aya da 'Yar uwarta, (ita aganinta abin yafara wuce fad'an sako da sako), afili kuma sai ta ce, " aunty Safna miyayi zafi shiba wutaba, zauna ki huta Dan ALLAH.......
Duka takaima Rahma ummi ta kare, Safna kishiga hankalinki danifa, uwarmi tamiki daga shigowa?.
Cikin huci ta ce, "ummi kinajinfa maganar datake fad'amin, ALLAH yarinyarnan ta rainani, zan koya miki hankali kwanannan wlhy.
Ummi ta tamke fuska tana nunama safna hanya, kinga tashimin anan.
Ran safna a6ace tabar wajen tanufi d'akinsu tana mita.
Rahma kam ta sauke ajiyar zuciya tana k'ara gyara kwanciyarta.
Ummi ma kai ta girgiza ALLAH ya shiryaki Safna tafad'a tana shafa kan Rahma.
Safna tacire kayanta tanata masifa harta shiga wanka, (nikam mamaki take bani, Dan banga abin fad'aba anan).
Rahma tanason shiga d'akinsu tayi wanka tana tsoron masifar Safna, Dan tasan wlhy bata bartaba, k'ilama yau kwana zatayi bala inta da mitar tsiyarta.
d'akin umminsu tanufa dantayi wankanta kawai, yafi sauk'i.
+++++++++++++++
Bobo yana kwance ad'akinsa sai juye2 yakeyi, barci yakesonyi amma yak'i d'aukarsa, maganar Ammi ce kemasa yawo akwakwalwa.
Yasan Ammi sairai babu sauk'ice, indai Abu ya6ata mata rai saita d'auki mataki, shikam yana tsoron zancennan yaje kunnen Appansu, yad'an cije le6e yana sauke numfashi, tund'azu soyake yafita amma yana shakkar had'uwa da Appa.
Yasan fita tazame masa tilas Dan dole zasu had'u wajen cin abinci.......
Bai rufe bakiba aka buga k'ofar, batarda ya d'agoba ya ce, "ashigo.
Khairiyyace k'anwarsa, cikeda da tsoro ta ce, " yaya kazo wai aci abinci.
Hannu yad'aga mata kawai, bata gane nufinsaba Dan haka ta ce, "ka k'oshi kuma yaa Bobo!?.
Harara ya watso mata sannan yamik'e, da sauri tayi waje, shikuma yad'auki doguwar riga fara yazura yafito.
Kowa ya hallara shikad'ai ake jira, rissinawa yayi yagaida Appa da Ammi sannan yazauna.
Khursiyya ta ce, " yaya ina yini, harara ya watsa mata, ya ce, "k d'azu dasafe miya hanaki wankemin bayi?.
Kanta ak'asa ta ce, " wlhy yaya ina uzirin makarantane, dakuma nadawo na manta.
Tsaki yaja kawai baisake cewa komaiva.
Ammi tazubama Appa abinci, tasakama kanta, kairiyya kuma tasakama bobo shima, suma suka zuba.
Nawal tana kusada Appa.
Suna cikin cin abinci kamar antsikari Nawal ta ce, "aunty khursiyya.
Na'am Nawal miya faru?, khursiyya ta fad'a.
Cike da murna ta ce, " Ammi tace nima ankusa kawomin momyna.
Ayya my dear natayaki murna.
Ran bobo yak'ara 6aci, fuska ad'aure ya gallama Nawal harara, Appa da Ammi suna kallonsa, amma basuce komaiba.
Itama Nawal saitayi shiru kafin ya bibbigeta, Dan dukda yana wasa da ita hakan bai hana yaci k'aniyartaba idan ta k'uleshi.
Harsuka kammala cin abinci babu Wanda yakuma cewa komai, bayan sun kammala kowa yakama gabansa.
Bobo yaji dad'i Affa baimasa maganaba har dare.
Da daddare yana zaune a babban falo daga can gefe, wasu buks yake dubawa, khairiyya da khursiyya da Nawal suna zaune suma kallo sukeyi, Ammi tasakko daga d'akin Appa, takkali Bobo da hankalinsa kekan bincike ta ce, "Mukarram kaje Appanku na kiranka.
Wani irin fad'uwar gaba da tsinkewar zuciya suka sameshi a lokaci d'aya, bakinsa yana rawa yace Ammi lfy kuwa?.
Babu komai mikake tunani?.
" kai ya girgiza mata yana sauke ajiyar zuciya."
Asanyaye ya haura saman Appa, Appa nazaune yana kallon labarai Bobo yashiga da sallama.
Fuska asake Appa ya amsa, bayan yazauna ya ce, "Appa gani.
Appa dattijo mai hikima da iya kama mutum, saiyayi murmushi, dama bawani Abu bane, inasonjin ya shari'arku da B.. Sadiq?.
Ajiyar zuciya bobo yasauke wadda hartaso bama Appa dariya amma saiya dake.
Komai yayi Normal Appa, Dan insha ALLAHU zuwa Monday komai zai k'are, alk'ali zai yanke hukunci.
A to Alhmdllh haka nakesonji, daga nan Appa yacigaba dajansa da hira harya saki jikinsa.
Cikin hikima Appa ya ce, "Mukarram waini yamaganar aurene?, kodai haryanzu?.
Bobo yad'an Sosa gefen wuyansa Appa Dan ALLAH kudaina yawan damuwa akan aurena insha ALLAH zanyi amma ba yanzuba.
Tofa, bayanzuba sai yaushe Mukarram?, koso kake saika tsufa agidane?, ai ko bakayi aure Dan kankaba kayi Dan Zuhra, kullum maganar yarinyar nan momy momy to yakamata asamo mata momyn nan.
Inkuma bazaka iyaba ba awannan karonma zan samo maka matar aure, Dan naga kai tsoron matan kakeji.
Appa kayi hak'uri, ak'aramin lokaci, insha ALLAHU nanda k'arshen shekara zanyi.
Appa yad'an zaro ido, Mukarram karshen shekarafa kace?, kai kana ganin zamu iya barinka harnan da watanni Tara babu aure, nifa nagaji da ganinka hakanan gsky.
Ammi tashigo hannunta d'auke da tire, yaa is'haq yana biye da ita.
Appa ya ce, "yauwa aii gara dakukazo.
To miya faru Alhaji?.
A'a wai Murarram nakeyima zancen sure, shine yake rik'ona abarsa sai k'arshen shekara.
K'arshen shekara kuma ya ishaq yafad'a yana kallon Bobo dayake wani 6ata rai. Kai idan anbarka zuwa k'arshen shekarar saika yarda?.
" emana yaya aii nake ganin zaifi ko?.
shin wai Abdulmalik kodai bakada lfy ne?.
Yaya banida lfy kuma kamar ya?.
Harararsa ya ishaq yayi ya ce, " bansaniba.
Appa ya k'atsemusu zancen dafad'in Ishaq babu wani abinda ke damunsa iya shegene kawai irin nasa. Amma nima abin yana bani mamaki wlhy, hakamafa lokacin aurensa na farko mukaita fama, kokuwa maganar ishaq gsky ce?.
Ran Bobo yakuma 6aci, aii dama yasan tunda wannan masifaffen yazo saidai ALLAH, gashinan yak'arama wutar fetir.......
Appa yakatsema Bobo tunani da fad'in Mukarram baka jinane?.
Kansa ya girgiza, murya a sark'e ya ce, "wlhy Appa lfy ta k'alau.
Appa ya kalli ammi, kai ammi ta girgizama Appa kawai.
Appa yayi murmushi, ya ce, " shikenan Mukarram tashi kaje, ALLAH yakaimu k'arshen shekarar.
Yakwa mik'e yana washe baki yafice, azuciyarsa ya ce, "su yaa Ishaq ansamu game over.
(Nikam dariya yabani, Dan k'ila shine mai game over d'in).
Ammi ta ce, " Alhaji nifa ban fahimcekaba?.
Appa yay murmushi, yanzu zan fahimtar daku, shekaran jiya naje mun gaisa da abokina Alh bilal, anan nakemasa maganar ranshin auren Mukarram abin yana damuna.
To yanzudai azancen nan danake muku munyanke hukuncin had'a auren mukarram da 'Yar wajensa.
Ammi tayi murmushi tana fad'in Alhmdllh, kai nayi farinciki wlhy, ALLAH ya tabbatar da alkairi.
Amin ya ishaq yafad'a shima fuskarsa cike da annuri.
Ya gaida Appa Dan ko gaisawa basuyiba ma, daganan suka tattauna akan bikin, ya Ishaq yatafi...........
*_rubutu hikimace da baiwa ta musamman gsky, shiyyasa bazan gajiyaba da yabonki aunty bilyna🤙🏻❣👌🏼._*
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
7⃣&8⃣
_washe gari_
Da wuri Bobo yatashi yay shirin zuwa wani bincike akan shira dazaiyi.
Fes yakejinsa akan maganar dasukayi jiya da su Appa.
Yafito sanye cikin shadda ruwan k'asa d'inkin boda, kayan sunmasa k'yau sosai, sai tashin k'amshi yakeyi, wayoyinsa yad'iba da jakar aikinsa.
Babu kowa afalon ya kalli bak'in agogon fata dake d'aure a tsintsiyar hannunsa 7:23am, yasan yanzu babu Wanda yatashi, Dan al'adar gidance indai sukayi sallar asuba sukoma barci, ficewarsa yayi saboda yanada uzuri.
Yabude d'ayan gefen motarsa yazuba kayan hannunsa sanan yazagaya yashiga ya zauna.
Saida yatsaya suka gaisa da maigadi sannan yafice, anguwar shiru babu hayaniya saidai iskar Safiya dake kad'awa, gakuma rana tad'an hasko maibada d'umi mai dad'i, cikin nutsuwa yake juya sitiyarin tamkar bayaso, yafito daga layin gidansu yahau babban titi, tafiya kad'an yayi saiya hangi taron jama'a a tsaitsaye agefen titi, wasuma daka gansu suna cikin rud'ani, harya wuce saiya dawo baya yanemi guri yay fakin.
Fitowa yayi daga motar yanufi wajen taron jama'a.
Malam lfy kuwa?, yatambayi wani matashin saurayi daketa zage2.
Saurayin ya balla masa harara, kacemin lfy kuwa, aii dama duk irinkune, kud'i sunsaku bakwa tsoron ALLAH, gani kuke komai kukayi kunada kud'i zasu kareku........ Hannu Bobo yad'aga masa, kaga bawannan nake tambayarkaba nikam, mike faruwa anan?.
Saurayin ya share hawayensa sannan ya ce, "wani mara imanine yayma yarinya fad'e yazo nan ya yardata.
Fad'e!!, Bobo yafad'a arazane, da sauri yafara kutsa kai cikin taron jama'ar batareda ya saurari maganar da saurayin yake masaba.
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u yafad'a yayinda yay tozali da k'aramar yarinya kwace tamkar gawa.
Da sauri ya rarumi yarinyar batareda yakula da jinin dake zuba ajikintaba, wasu daga cikin mutanen suka fara tambayarsa koya Santa?.
Bai sauraresuba yabud'e mota yasakata abaya, harya shiga mota yakira saurayin d'azu ya ce, " shiga muje.
Babu musu saurayin yashiga, Bobo yaja motar a 360 suka nufi asibiti.
Azuciyarsa yana Addu'a ALLAH yasa ya Sulaiman yana asibitin.
Suna Isa aka amshesu cikin gaggawa Dan ansanshi k'anine gamai asibitin.
Ma'aikatan masu gaisheshi ya tambaya ya sulaiman yazo?.
A'a baikai ga k'arasowaba wata matashiyar budurwa tafad'a cikeda sanabe.
Baibi takantaba yafara kiran ya sulaiman.
Bugu d'aya ya d'auka.
Cikin zolaya ya ce, "Bobon Ammi ya akayi?..
Muryar bobo na rawa ya ce, Yaya kana ina?.
Ina hanyar zuwa asibiti miya faru?.
Alhmddlh Bobo yafad'a, saika k'araso kawai, nima ina asibitin, baijira amsar ya sulaimanba ya yanke wayar.
Gudu ya sulaiman yak'ara danjin Bobo ya ce, " yana asibiti.
Cikin k'an k'anin lokaci ya iso, atsorace yake kallon jikin bobo da jini ya 6ata.
Bobo daketa safa da marwa ak'ofar d'akin da aka shigar da yarinyar ya hango yaa sulaiman yashigo cikin asibitin arazane.
Cikin hanzari yatareshi, yayana Dan ALLAH ka taimaki yarinyar nan karta mutu plzzz.......
Cikin rashin fahimta ya sulaiman ya ce, "nutsu Abdulmalik miya samu Nawal d'in?.
Yaya ba Nawal bace wata yarinyace, kaje wajenta zanmaka bayani daga baya plzzz.
Ya sulaiman yasan halin bobo da rikici Dan haka da Sauri ya afka d'akin Dan ganema idonsa.
Kansa yadafe cikin tashin hankali yafara yima Nos masifa akan sunzubama yarinyar ido babu abinda sukai mata.
Kayi hak'uri sir aikin banamu bane dole saikazo, inazaton Fad'e akamata.
Ajiyar zuciya ya sauke, taimakon gaggawa yafara bama yarinyar.
A waje kam Bobo yakasa zaune yakasa tsaye, sai kaida kawo yakeyi, hankalinsa atashe, yanzunan haka al'umma suka lalace akan zalinci?, insha ALLAHU saiya k'ar6oma yarinyar nan 'yancinta, zaiyi bincike kod'an gidan ubanwaye saiya gurfanar dashi a gaban shari'a.
Wayarsa dake wringing ya Ciro a aljihu, Br..... Kamal yagani, yarintse idonsa Dan yamanta abinda ya fiddoshi daga gida, bai d'agaba har wayar ta yanke aka k'ara kira.
Daurewa yayi ya d'auka suka gaisa, AA Hamshak'i wai ya akayine?, kacemin kafito gida amma najika shiru.
Sorry Kamal ina nan zuwa, wlhy wani abune ya rik'rni ahanya, amma plz kabani minti talatin zuwa arba'in zan iso.
Okey saina ganka.
A can kuwa bobo nabarin wajen police suka zo, mutane suka sanar dasu wani ya d'auki yarinyar zuwa asibiti.
Wane asibin ne?, wani d'ansanda ya tambaya fuska atamke.
Muma bamu saniba wlhy, amma antafi damai shagonnan, suka nuna shagon dake kusadasu.
d'ansandan baice komaiba yashiga mota suka juya.
Gulma mutanen gurin suka fara da zagin 'yan sandan, wai sai yanzu suka gadamar zuwa, bayan tun d'azu aka kirasu.
Wani ya ce, "bar munafukai malam aii k'asarnan munga takanmu, buharine kawai ke k'aunar talaka, (ALLAH dai ya k'ara masa lfy).
Amin ya rabbi Garzali.
+++++++++++++
Safna tafito sanye cikin atamfa Riga da siket, sunmata d'am kamar zata fashe.
Rahma ta kalleta ta girgiza kai, wannan lamari na 6ata mata rai, ita bataga wayewaba ga mace mai saka suturar dake fidda jiki, shiyyasa fad'e yaketa k'ara yawa aduniya, to matan basusan darajar jikinsuba, (suyita fiddo jiki tamkar akuyoyi da sunan wayewa).........
Me wait lfy kike kallona?, karfa ki cinyeni wlhy.
Rahma takauda kai saga kallonta, ta ce, " aikinsan Nina mayya bace.
Da sauri safna takai mata duka, to ubanwaye mayen?.
Rahma ta kauce tana dariya, maida wuk'ar ta hannun damar Abba, Dan ALLAH zanbiki makarantar wlhy zaman gidannan ya isheni.
Safna ta harareta tozoki hau kaina uwata.
A'a ALLAH yabaki hak'uri, yi tafiyarki zanje gidan yaa Munir nama taya aunty Naja'atu aiki.
Yafimiki sauk'i, dama da 'yan aiki kike kama aii, safna tafad'a tana ficewa.
Baki Rahma ta ta6e tareda Jan tsaki.
Ummi tafito tana fad'in kekuma lfy?.
Lfy lay ummi nida aunty Safna ne.
Ina Safna d'in?.
Tafita makaranta.
Shine yau ko sallama babu?, dariya Rahma tayi ta ce, "haryanzu aljanun masifar nasu saukaba.
Ummi batace komaiba tashige kicin.
+++++++++++++
Asibiti kam lamura saidai addu'a bak'aramar mugunta akaima yarinyarba, amma cikin ikon ALLAH yaa sulaiman yayi nasarar ceto ranta.
Bak'aramin lokaci ya6ataba kafin yafito, zuwa yanzu bobo na tsaye jingine da bango ya hard'e hannuwansa biyu ak'irji, k'afarsa d'aya dogare a bango fuskarnan d'aure tamau.
Ya sulaima yafito yana shere zufa, da sauri Bobo ya taresa, Yaya ya jikin nata??.
Alhmdllh. ya sulaiman yafad'a, yaja hannun Bobo suka shiga office d'insa.
Koda ya zaunar dashi saiya bude firij yad'akko fresh milk ya tsiyaya a kofi yamik'ama Bobo.
Bobo ya ce, "ya.... Hannu ya d'aga masa, kaga k'ar6a kasha kasamu nutsuwa, nasan ko karyawa bakayiba kafito.
Ajiyar zuciya Bobo yayi, yakar6i kofin yasa abaki, ahankali yakesha harya shanye tas.
Cikin zolaya ya sulaiman ya ce, " Bobon Ammi damadai yunwa kakeji, ko a k'ara?.
Murmushi yayi batareda yace komaiba, ya girgiza kai.
Ya Sulaiman ya zauna yana dariya, saida yayi rubuce2 sannan yad'ago ya kalli k'aninnasa, Abdulmalik ina kasamo yarinyarnan?.
Ajiyar zuciya Bobo ya sauke shima yayan nasa yake kallo, ya ce, ''Yaya wlhy abakin titi..... Nandai yakwashe komai yasanar dashi.
Girgiza kai ya sulaiman yayi, ya ce, ''ALLAH ya saka mata, amma yanzu yakamata musan iyayenta kafin ad'au mataki, sannan ina yaron dakace kunzo tare?.
Yana nan awaje.
Wani Abu ya sulaiman ya danna, saiga Nos tazo, ya ce, "akwai wani saurayi anan waje shigomin dashi.
OK sir.............
*_kuyi hak'uri ina muku typing bakamar aunty billy ba, wlhy akwai wahala, writers suna k'ok'ari gsky, ALLAH dai ya biyasu._*🙏🏻
*_" luv u aunty bilyn Abdul"_*
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
9⃣&🔟
Assalamu alaikum.
Wa'alaikassalam yaa sulaima da bobo suka amsama saurayin.
Gurin zama yaa sulaiman ya nuna masa, bayan ya zauna yabasa hannu sukayi musabaha.
Ya sulaiman ya ce, "d'an uwa ance awajenku aka samu yarinyarnan ko?..
Eh anan akazo aka yardata wajen misalin k'arfe 6:44am, fitowa ta kenan zan bud'e shagona naga wata jar mota ta tsaya agurin, nasan su basu ganniba nida abokina Nura, Dan saida suka wawwaiga sukaga babu mai kallonsu sannan aka turota waje.
Bobo ya cije le6ensa zuciyarsa na k'ara zafi.
Ya sulaiman ya jinjina kai, Yakuma fad'in to kunsanar da police?.
Eh suna barin wajen muka kira 'yan sanda, amma har bawan ALLAH nan yazo ya d'auketa basu zoba.
Ya sulaiman ya sauke numfashi, babu damuwa ayanzu nasanar da wani d'an sanda dan kes d'in dolene police sushiga, namata abinda duk yadace, kuma narubuta bayanai akan komai.......
Kwankwasa k'ofarne yahana yaa sulaiman cigaba da magana, wata nos tashigo tana sanar dashi wani police nason ganinsa.
Shigo dashi mana ya sulaiman yafad'a.
Bayan d'an sandan yashigo shida wani suka gaisa dasu bobo sannan sukayi musu bayani akan komai.
Har d'akin da yarinyar take aka kaisu, bobo tamkar yay kuka danganin yarinyar, shidama haka yake da tausayi dukda kasancewarsa masifaffe.
Bayan sun kammala komai 'yan sandan suka tafi, shima saurayinnan yatafi akan zasu sake nemansa.
Ya ce, "insha ALLAHU duk sanda sukazo zai basu had'in kai.
Godiya sukai masa yatafi, bobo yay masa alkairi.
Ya sulaiman ya kalli bobo, Abdulmalik kaima yakamata katafi gida ka canja kayannan duk sun 6aci da jini.
Sai asannan yakula, yad'anyi tsaki wlhy yaya bamma kulaba, bari naje wajen Br kamal Dan yana jirana, idan muka gama saina koma gidan.
Dadai kafara zuwa ka canja kayan tukunna.
To yaya bari naje, saina dawo.
Okey saika dawo.
Saida sukad'an rungume juna sannan sukai musabaha yatafi.
+++++++++++++++++
Rahma tafito sanye cikin dogon hijjab har k'asa yake ja, hijjabin mai hannune Dan haka hannunta rik'e da fos, sallama tayima ummi sannan tafito.
Ta wawwaiga bataga idiris diraiba ba, d'an tsaki taja ta k'arasa wajen mai gadinsu, rissinawa tayi ta gaisheahi.
Ya amsa cike da fara'a, yana k'aunar yarinyarnan saboda hankalinta da girmama nagaba da ita, halinta ya banbanta da yayarta sosai.....
Rahma tak'atse masa tunani da fad'in baba ina Idris!.
aiko d'iyata Idris yaje gida yanzu babu dad'ewa, kinsan suna cikin tashin hankalin 6atan k'anwarsu tun jiya da yamma.
K'anwarsu kuma?, 6ata tayi?.
Wlhy kuwa haka yake gayamin d'azu, wai tunjiya bata dawoba daga aikenta.
Tofa ALLAH yabayyanata, Toni bari naje na hau adaidaita.
diyata dakanki?, toki tuk'a kanki mana.
Murmushi tayi ta ce, "A'a baba, Abba ya hanani tuk'i."
ALLAH sarki 'Yar albarka, aii haka akeson mutum yaringa bin maganar iyayensa, ALLAH yay miki albarka, yabaki miji nagari.
Murmushi Rahma tayi, ahankali tace ngd baba saina dawo.
To adawo lfy.
Rahma tafito daga gida, tad'an wawwaiga anguwar babu mutane sosai, sai jefi jefi, dakuma motoci dake fitowa daga gidaje inaga masu Fita aikine da kasuwa.
Ajiyar zuciya ta sauke sannan tafara tafiya da addu'ar ALLAH yasa tasamu adaidaita da wuri, Dan tsakaninsu da titi da nisa.
Tad'anyi tafiya kanta ak'asa, jitai ance a'a Rahma sai Ina?.
Ad'an tsorace tad'ago takalli inda aka ambaci sunan nata, tayi murmushi lah ya kamal kaine.?.
Nine Rahma ykk?.
Lfy lau yaya, lfy naganka anan?.
Wlhy lfy k'alau wani abokina nake jira, amma shiru bai zoba shine naked'an shan hantsi anan.
Ayya, yasu momy da aunty Ameera.
Lfy lay suke, bazaki Shigabane?.
A'a yaya gidan ya Muneer zanje wlhy ka gaidaminsu.
Zasuji, to amma ina direbanku kika fito ak'afa.
Hummm wlhy wani d'an uzuri yarik'eshi.
Okey, to amma ba girmanki bane.
Dariya tayi kai yaa kamal to miye girmana?.
Kafin yabata amsa wata mota ta tsaya adaidai saitinsu.
Kamal ya ce, "ga abokina nan ya iso.
Waigawa tayi takalli motar, saikuma tadawo da kallonta kan kamal, tom nikam nawuce.
Bazaki tsaya Ku gaisaba.
A'a yaya aii bai sanniba.
Bobo yafito daga motar fuskarsa babu yabo babu fallasa, yad'an kalli Rahma datazo zata gitta ta gefensa, kanta ak'asa ta gaisheshi.
Ya amsa da lfy, yana kauda Kansa daga kallonta.
Gaba tayi tana Jan tsaki, dukda bata kalleshiba abin yabata haushi, tana bak'in cikin ta gaida mutum ya ce, " mata lfy."
Bobo yak'arasa wajen kamal suka gaisa, sannan suka Shiga cikin gidan.
Rahma kam tana k'ara 'Yar tafiya tasamu adaidaita tashiga.
.+.+.+.+.+.+.+.+.+.
Safna Ana makaranta, yau itace harda zuwa office d'in yaa Hamza amma ta tarar baizoba.
Basira ta kalli safna daketa jan tsaki tana kallon agogon hannunta, wai safna lfy kuwa?, naga kinsamu zuwa office d'in malam Hamza miye dalili?.
Zeenat dake zaune gefensu ta ta6e baki, kazar wahala ALLAH ya yanka mata shiyyasa tafara figa.
Kazar wahala kuma kamar ya?.
Zeenat tabama Baseera labarin abinda yafaru jiya, Dan ita batazo school ba.
Wata dariyar mugunta Baseera tasaki, o, ni Baseera wai yau Safna kece saurayi ya sacema zuciya?, lallai zanso ganin wannan guy mai suna Bobo, nasan tabbas ya amsa sunansa bobo.
Hummm kibari kawai Baseera wlhy jiya banyi barciba, mafarkinsa nayitayi, harda mafarkin munyi aure harda yara.
Dariya zeenat da Baseera suka saka harda cafkewa.
Safna ta 6ata rai tana hararsu, kuga nifa banason ciki da iskanci kunsani, zeenat damafa haushinki nakeji, Dan maganar jiya ta 6atamin rai wlhy.
Cikin dariya zeenat ta ce, "afwan Tawan, ALLAH yabaki bobo.
Amin, namasan yabani tunda har yasamun sansa azuciyata.
Zeenat tad'an ta6e baki tana fad'in garadai adogara ga ALLAH.
Baseera tai saurin kar6ewa toda dake tace ta dogara?, Safna karki damu ina bayanki d'ari bisa d'ari, kota halin k'ak'a saikin mallaki Bobo.
Safna tayi murmushi shiyyasa nakesonki k'awata ALLAH yabarmu tare ngd.
Zeenat tana jinsu bata kuma tankawaba.
+.+.+.+.+.+.+
_3:30pm_ Bobo yashiga cikin asibitin, kai tsaye office d'in ya sulaiman yanufa, suka gaisa ya tambayi yamai jiki?.
Da sauk'i Bobo, aiina zata bazaka dawoba?.
Tab yaya wlhy hankalina yana asibitin nan, yanzu haka bamu gama aikinba nabarma Br kamal nataho, yaya ta farka kuwa?.
A'a har yanzu tana barci, ana buk'atar tahuta sosai yanda zata tashi k'wak'wal warta Normal, ta wannan hanyarne kawai zamuyi saurin samun bayanai daga gareta.
Okey tom ALLAH yabata lfy.
Amin Mukarram d'in Appa, mai suna kalakala.
Dariya Bobo yayi ya ce, ''yaya aii duk kune kuka mak'ala mini.
Sukayi dariya harda tafawa kamar wasu abokai.
Sai k'arfe 5:00pm dai dai sukabar asibitin, kuma har sannan yarinyar bata farkaba, kai tsaye gida suka nufa har ya sulaiman shima zai gaidasu Ammi.
Kowaya yafito cikin motarsa suka nufi cikin gidan suna 'yar hira.
Gaba d'aya mutanen gidan suna falon sama, Dan haka suma can suka nufa............
*_luv u oll fan's d'in aunty bilyn Abdul❣💓❣😁👌🏼._*
_Ngd da had'in kanku_
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣1⃣&1⃣2⃣
Da gudu Nawal ta taso ta rungume ya Sulaiman, yad'agata sama yana dariya, Nawal kin k'ara nauyifa yafad'a yana lakatar hancinta.
Ta kalli daddynta ta ce, "baby waikaji uncle yace nak'ara nauyi.
d'an hararta yayi cikin wasa, ya ce, "sai yanzu kika ganni baby.
A'a baby naganka tun d'azufa, nafara gaida uncle ne ko uncle?.
Ya Sulaiman yad'aga mata kai yana dariya, cikin falon suka k'arasa.
Bobo ya ce, "o kace yau family ya had'u?.
Ya Is'haq da ya Hamza, sukayi dariya suna mik'a musu hannu.
Khairiyya da Khursiyya ma dariyar sukeyi.
Guri suka samu suka zauna, ya Hamza ya ce, " ashe kuna tare?.
Eh wlhy muna tare, naje Asibitinne.
Tofa miya sameka?, cewar ya Is'haq.
No bani bane wata yarinyace......
Fitowar Ammi ta k'atse masa zance, tazauna cike da farin cikin ganin manyan 'yayan nasu.
Gaidata ya Sulaiman da bobo sukayi, fuskarta cike da fara'a ta take amsawa, tareda tambayar aikinsu dakuma iyalin ya Sulaiman.
Suna lfy wlhy Ammi.
Ammi ta kalli bobo, Mukarram yadai naganka wani iri?.
Fuska ya shagwa6e yana kallon Ammi, ALLAH Ammi nagaji over yau, kaina hard'an ciwo yakeyi.
Yanda yay maganar a shagwa6e saiya basu dariya.
Ya Is'haq ya ce, "Bobo shagwa6ar dakayi ko Nawal bata yinta.
Murmushi yayi kawai baice komaiba.
Ammi ta ce, " kubarmin Mukarram d'ina yayi shagwa6arsa lokacinsane ko bobon Ammi?.
Nanma dariya sukayi gaba d'aya, ya harari su khairiyya dake tuntsura dariya harda rik'e ciki.
Ku yarannan nakulafa kun fara rainani?.
Ya Hamza ya ce, "to aii abin dariya kayi, saika hanasu su dara?, kawai kayi maganin abun.
Bobo ya ce, " ta yaya kenan?."
Kayi aure kabar musu gidan cewar ya Sulaiman.
Mik'ewa Bobo yayi danjin and'akko maganar dabayaso, kunga bari nad'an watsa ruwa nadawo.
Baridai kagudu idan angama maganar kadawo, ya Is'haq yafad'a yana dariya.
Nanma dariya kowa yasaka harda Ammi.
Shikam yay shigewarsa d'aki yana fad'in kwa gaji kubarni.
Ammi ta ce, "nidai inaga Mukarram tare yake da aljana shiyyasa baya son maganar aure.
Ya Sulaiman ya ce, "Lah Ammi wane irin aljana kuma?, wlhy ras yake, shidai haka ALLAH yayosa bashida matsala da mace.
Hakadai kuke gani, nifa abinda na lura dashi ga Abdulmalik kawai bazai iya tunkarar mace ya ce, yana sonata bane, gani yake ajinsa zai zube kawai.
Hhhhhh wlhy hakane Hamza, Bobo dakake ji dagani akwai d'aukar kai agaban mata kai harma mazan, kamar wani jinin sarauta.
Dariya aka kumayi, Ammi ta ce, " aii yashafi sarautar, kunfa takurama yarona gsky.
Ya Is'haq ya ce, "ALLAH ammi yaron nan yawuce yanda kike zato, amma kwanannan zamuyi maganinsa, aure zamu MASA kawai.
Dakun k'yautamin wlhy, nidai nagaji da ganin Mukarram babu mata, nasan har yanzu rashin Ni'ima na damunsa, amma idan yayi auren ALLAH yasa aka dace da matar k'warai komai zai zama tarihi.
Insha ALLAHU ammi komai yazo k'arshe karki damu...
Daga nan suka cigaba da tattaunawa, annan ma ya Sulaiman take basu labarin yarinyar da bobo yakai asibiti da safe.
Zancen ya girgizasu daganan suka Shiga tattauna matsalolin fad'e da yara k'anan suke fuskanta ak'asar nan.
+
Bobo kam yana Shiga d'aki yacire kayansa, wanka yashiga yayo, yashafa mai yazura doguwar Riga blue da dogon wando bak'i.
Falo yadawo Inda 'yan uwansa suke akacigaba da hira da tattauna al'amuran rayuwa, ahaka har Appa yadawo.
Gaba d'aya suka mik'e cikin girmamawa sukayi MASA sannu.
Fuskar Appa cike da annuri yabi matasan samarin 'ya'yan NASA da kallo, masha ALLAHU yaukuma gidan cike yake da basawa.
Dariya sukayi danjin furicin mahaifin nasu.
Ya ce, " bari naje nawatsa ruwa sainazo ayi hirar dani ko?.
To Appa asakko lfy sukafad'a atare.
d'akinsa yanufa rik'e da hannun Nawal data k'ar6ar MASA jakka, dama kullum itace mai kar6a inhar tadawo school.
Hirarsu suka cigaba dayi, kiran sallah yasa suka mik'e sukayi alwala, Appa yafito ya samesu suka tafi masallaci abin gwanin sha'awa, shima Appa sai dad'i yakeji ganinsa cikin samarin 'yayansa ababen alfaharinsa.
Ko'a masallaci sun burge mutane, Dan a sahu d'aya suka jera reras.
Agidama khairiyya da khursiyya da Nawal sallar sukayi, ammi ma haka.
Bayan an idar ammi tasakasu suka shirya abinci a tsakkiyar falon Dan yau duk su ya Is'haq anan zasuci abinci, suka gama shirya komai da taimakon 'yan aiiki sannan suka koma d'aki domin gabatar da sallar isha'i da aka kira.
Basu dawoba saida akayi sallar isha'i, suka rankayo zuwa gida suna 'Yar hirarsu da tsokanar juna.
Afalon suka zube Appa ya ce, ''aini zuwannan naku yamin daidai, kamar kunsan dama ina nemanku.
Ya Hamza ya ce, "to Appanmu ALLAH yajishemu alkairi.
Amin suka fad'a gaba d'aya.
Ammi dasu khairiyya suka fito suma, rissinawa sukayi suka gaida Appa da yayyensu, Nawal taje jikin Appa tazauna.
Yashafa kanta yana fad'in amaryata kinyi sallah?.
Kai ta jinjina tana dariya.
Tomi kika rok'amana?.
Hannunta tasa abaki idonta na kallon p,o,p d'in falon alamar tunani, can takalli Appa tana washe wawulinta da hak'ori biyu yafad'i, ta ce, " Appa kasan mina rok'a?.
Saikin fad'amin amaryata.
Narok'i ALLAH ya kaimu Aljanna nida kai, da Ammi, da baby, da uncle Sulaiman, da uncle Hamza, da Uncle Is'haq, da aunty khursiyya da aunty khairiyya, da mom din gida uncle Is'haq, da momyn ya Ahmad da aunty Sameera, kuma nace ALLAH yasa muje makakka muduka sau dubu dubu babu iyaka muga kabarin Manzon ALLAH a madina.
Tafi sukai mata gaba d'aya suna fad'in ameen mai sunan manya.
Ya Is'haq dake kusada ita har sumbatar hannunta yayi.
Appa ya ce, ''lallai na more da amarya Ashe.
Ta ce, "Appa kasan mikuma na rok'a daga k'arshe?, ya girgiza kai yana murmushi, canayi ALLAH yasa nima naga momyna.
Gaba d'ayansu kallonta sukayi, tabasu tausayi sosai, Appa ya rungumeta cikeda tausayi, Bobo kam k'asa yayi da kansa zuciyarsa tayi rauni sosai, jiyake tamkar yafasa kuka saboda tausayin 'yarsa, tausayinta yana d'aya daga cikin abinda yasa yak'i k'ara aure, bayason ya auro wadda zata takurama d'iyarsa sanyin idaniyarsa.
Ya Hamza ya ta6ashi d'agowa yayi yana kallonsa, ya Hamza ya jinjina masa kai fuskarsa d'auke da tausayi.
Murmushi bobo yayi.
Saikuma ya kalli sauran 'yan uwannasa da iyayensa yaga dukshi suke kallo.
Kansa yamaida k'asa yana cigaba da murmushi mai ciwo.
Ganin haka Ammi ta katsesu da fad'in bismillah kusauka ga abinci.
Kowa ya sakko tskkiyar falon in da abincin yake.
Bayan Ammi tasakama Appa kowa yafa k'ok'arin zubama Kansa abinda yakeso.
Falon yayi tsit bakajin motsin komai sai k'arar filat da cokali, saikam surutun Nawal lokaci2.
Bayan sun kammala cin abincin 'yan aiki suka gyara wajen tsaf, Appa yakalli khairiyya ya ce, "auta zoki kaita d'aki ta kwanta.
To Appa khairiyya tafad'a tana mik'ewa, d'aukar Nawal tayi daga jikin Appa tanufi d'aki.
Falon yay tsit kowa ya maida habkalinsa kan Appa.
Appa yamusu sallama suka amsa.
Ya gyara zama cikin hikimar zance yafara musu nasiha da k'ara jaddada musu muhimmancin zuminci da hak'uri da juna, ahankali ya gangaro kan auren Bobo, Wanda tunda Appa ya ambaci sunansa gabansa yafad'i.
Appa yabasu labari kamar yanda yagayama su Ammi da ya Is'haq jiya.
Ya d'ora da fad'in yanzu dai mun yanke hukunci ranar juma'a idan ALLAH ya kaimu za'a tura dakomai har sadaki Dan badogon lokaci za'a d'aukaba, k'arshen watannan za'ayi bikin kowa ya huta.
Zuface tafara fita addukan sassan jikin Bobo, yakasa koda motsi dukda tsokanarsa da 'yan uwansa sukeyi suna fad'in ango kasha k'amshi.
Ammi ma sai dariya takeyi danjin dad'i, sai Alhmdllh take dad'i, su khursiyya kam harda 'yar bud'a.
Bobo ya galla masu harara.
Gaba d'aya akayi dariya harda Appa.
Daganan suka cigaba da tattauna yanda biki zai gudana da shagalin daza'ayi.
Appa ya ce, " suyi duk abinda sukeso bazai hanasuba, Dan Andad'e ba ayi wani shagaliba agidan.
Har k'arfe tara suna gidan, saida Appa yace yakamata sutafi gida hakanan wajen iyalinsu sanan suka mik'e kowa yanufi gidansa.
Bobo bayan yarakasu harabar gidan yanufi d'akinsa jikin a sanyaye, yama rasa wane irin tunani zaiyi shikam.............
_Tofa masu karatu, Yaya kenan?, shin ina Safna?, gafa gwaninta zai angwance, kowacece amaryar Bobo?, ya wannan zama zai kasance?, kudai biyoni kawai, basirar aunty bilyn Abdul ce, nikam copy nakemuku masoya._
*_hummm wasa farin girki, masoya yanzufa aka fara, kumuje zuwa wai mahaukaci yasai kura, yanzu muka dasa alk'alamin labarin Bobo!._*
*_masoya muna godiya ALLAH yanar zuminci._*
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣3⃣&1⃣4⃣
*_Gidansu Safna_*
Safna na kwance akan gado tana chart, sai faman murmushi takeyi, da alama tana jin dad'in charting d'in.
Rahma dake zaune akan sallaya tana karatun alkur'ani ta waigo ta kalli safna dataketa 6a66aga dariya harda rik'e ciki, kai Rahma ta girgiza tareda fad'in ALLAH ya shirya azuciyarta.
Kanta tamaida tacigaba da karatunta.
Safna kam bamatasan tanayiba, dariyarta taketayi cikin farinciki, hira takeyi da Baseera akan nemomata Bobo, Baseera tana gayamata akwai wani guy a unguwarsu sunansa *boy shiyakama subama aikin, Dan tasan cikin sauk'i zai samomusu bobo da labarinsa.
Tak'ara wani d'an ihun farinciki, tareda fad'in saini mata agidan Bobo.
Rahma takuma kallonta cike da mamaki, ganin bazata barta tayi karatunta cikin Nutsuwaba yasa tarufe alkur'anin tayi addu'oin ta tamik'e ta ajiye alkur'ani ama'ajiyarsa.
Hijjabinta tacire tana fad'in aunty Safna kofa sallar magriba bakiyiba har anyi isha'i amma kina kwance kina charting akan abinda k'ilama bazai amfaneki da komaiba.
ALLAHU Akbar maikaratu nagaba, Safna tafa idonta akan waya, tacigaba da fad'in malama Rahma jawo wata ayar na haddace wannan.
Ajiyar zuciya Rahma ta sauke, ta ce, "Niba malamarki bace, kuma ba wa'azi nake mikiba, ina tunatar dakene dannaga kin shagala.
Wani wawan dundu safna tasaukema Rahma abaya, Dan ubanki idan aljanna takice ki hanani, shegiya 'Yar iska uwar tsari, kenikam daba agabana ummi ta haifekiba wlhy danace anmata canji a asibiti, anya kuwa acikin 'yan barka wata bata sace ainahin d'iyar da ummi ta haifaba ta ajiye mata ke?.
Rahma tashare hawayenta ta ce, " kije kitanbayeta k'iladai kece aka canja mata, Dan halinki daban dana mutanen gidanna.
Afusace Safna taduro daga gado tana d'urama Rahma zagi.
Tuni Rahma tafice tabar mata d'akin.
Afalo taci karo da abbansu yadawo masallaci, sannu da dawowa Abba. Yauwa d'iyar albarka ina zuwa haka?.
Ba inda zani Abba, nadai fito falone nasha iska.
Masha ALLAHU, ina 'Yar uwar taki to?.
Tana d'aki Abba.
Yauwa jeki kiramin ita zamuyi magana, ina umminku?.
Ganinan Abba Shaheed ummi dake fitowa daga d'aki tafad'a.
Tamai sannu dazuwa sannan tafara shirya musu abinci.
Rahma tatsaya abakin k'ofa ta ce, "aunty Safna kizo Abba yana kiranki.
Shegiya munafuka gulmata kina kaimasane?.
Niba munafuka bace, yace dai kizo..., tana gama fad'a tafice.
Safna tasakko daga gadon tana mita, zan koya miki hankaline 'Yar banza maikan dankali.
(Araina nace kekuma maikan doya ko?.)
Kusada Abba taje tazauna, Abba gani.
Kanta yashafa yana murmushi haba safnan Abba miya faru kika k'unshe kanki a d'aki?.
Zamanta ta gyara tana ballama Rahma harara, babu komai Abba nayi sallane INA zaune ina Azkar.
Da k'yau 'Yar albarka.
Rahma kam ido tazaro waje danjin k'aryar da safna ta gilla, saikuma ta k'unshe baki tana dariya.
Safna na kallonta, Dan haka haushi yak'ara kamata.
_(Hattara iyaye kuringa kula da addinin 'ya'yanku, akwai yara dayawa masu wasa da salla irinsu Safna, wata zakiga tana zaune tana chart za'a kira salla, amma ko'a kwalar rigarta, har Matan aurema akwai masu halinnan, musamman yanzu da karatun Novels sukayi tasiri arayuwarmu, yakamata duk lokacin da aka Shiga sallah kiringa lek'a d'akin yaranki kitabbatar suma suyi, ALLAH yasa Mugane)._
Ummi ta ce, "kutaso ga abinci, atare suka tashi har zuwa dani, anacin abinci Safna na chart saida ummi Tamata magana sannan ta ajiyewayar tana zum6ura baki.
Bayan sun kammala Rahma takwashe kayan, takaima masu aiki su wanke.
Falon tadawo Inda iyayenta suke zaune harda safna.
K'asa ta zauna kusada Abbansu.
Zamansu babu dad'ewa ya Shaheed da ya Muneer sukayi sallam.
Cikin girmamawa suka gaida iyayensu, suma suka tambayesu ya iyalinsu?.
Kowa ya amsa da lfy k'alau.
Suma su Safna suka gaishesu.
Bayan gama gaishe2 Abba ya ce, "dama bawani abune yasa na tarakuba zancen auren safna ne yatashi.
Wata irin d'agowa Safna tayi arazane, aurena kuma Abba tafad'a da k'arfi!!!.
Suduka kallonta sukeyi, Abba ya ce, " eh aurenki safna ta, kiyi hak'uri abin yazo miki wani iri kuma 1time, wlhy nima haka lamarin yazomin babu shiri.
Kuka safna tafasa tana fad'in itafa wlhy akwai Wanda takeso Dan haka bazata yardaba.
Ya Shaheed ya daka mata tsawa, wlhy idan bakimana shiruba jikinki zaiyi tsami, iskancim banza kawai, Abban kike fad'ama haka?.
Toni Dan ALLAH baza'a bari aji uzurinaba haka kawai amin auren dole, narantse bana sonsa karma afara wlhy.
Idan bahakaba kuma wlhy zanbar gidannan.
Duka ya Muneer yakai mata tatashi dagudu tashige d'aku tana kuka da fad'in wlhy itafa bata sonshi.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke ya ce, "akwai matsala kenan?......
Babu wata matsala Abba Shaheed ashema ita ta haifemu bamu muka haifetaba, wlhy acigaba da hidima kawai, idan ankaita ta mutu aranar, ni wlhy dama halin Safna ya isheni agidannan.
Shikenan ummin Muneer yanzu dai munyi dasu ranar juma'a zasu kawo komai, nasanar da Alhaji Rabi'u, (yayan ummi), sannan kuma suma su yaya na sanar dasu shida Abubakar.
Tom ubangiji ALLAH ya tabbatar da alkairi yasa ayi damu.
Amin Abba yafad'a, ya kalli su Muneer ya ce, " to manyan yayye yakukace?.
Dariya sukayi, yayi daidai Abba ALLAH ya Sanya alkairi, insha ALLAHU zamu fara shirya biki.
Tattauna maganar bikin suka cigaba dayi har zuwa wani lokaci, daganan su ya Shaheed suka tafi gidajensu.
+.+.+.+.+.+.+.+.+.+.+.
A 6angaren bobo kam abubuwa biyune suka cinkushe masa tunani, ga tunanin yarinyar da akaima fad'e, gakuma tunanin zancen Appa na yau, yasan appa sarai mutumne mai sauk'i da sanyi, komai zaiyi zaiyishine cikin hikima da lallashi, to amma mutumne kaifi d'aya idan ya ve e babu maisakashi fad'in A'a, Dan duk abinda zaiyi baya yinsa da ka saiyayi bincike.
Yasan ko giyar wake yasha bai isa ya gujema Auren nan ba, to amma shikam harga ALLAH baiji zaiso wata mace bayan Ni'ima ba, duk macen datayi kuskuren shigowa rayuwarsa bazata samu wani farincikin saba, ya rintse idonsa, ahankali yak'asa gaban wani k'aton hotonsa shida Ni'ima, sunyi k'yau sosai ahoto, suna tsayene gaban wasu filawoyi sun fukanci juna, yad'an rissina yadafa cikinta sannan tanada cikin Nawal, itakuma tana kallonsa shida cikin tana murmushi.
Hoton sunyi bala'in k'yau, wasu hawaye suka zuraro akumatunsa, baidamu daya gogeba sai shafa hoton daya cigaba dayi, yad'au tsawon lokaci yana kallon hoton daga baya yafad'a kan gado yana hawaye kamar wani mace.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Babu 6ata lokaci aka su Appa suka kai k'ud'i da komai ranar juma'a, antarbesu tarba ta mutunci da girmamawa, cikin girmama juna komai ya gudana aka tsaida biki sati uku kacal, saidai daga amarya har ango suna cikin tashin hankali, garama angon yadaure sosai yamaida komai ba komaiba, harma yanad'an saka baki idan 'yan uwansa suna maganar shagalin bikin.
Haka yasa ammi taji dad'i sosai itada Appa, sai albarka suke saka masa.
Nawal ma sai murana take ankusa kawo mata momynta.
Shirye shiryen biki ya kankama sosai Dan hidima akeyi babu kama hannun yaro, abubuwa sosai su ya Hamza suke shiryawa.
+.+
Yarinyar da akaima fad'e tana samum sauk'i saidai har yanzu bata iya magana, kullum sai Bobo yaje asibitin safe da yamma, har yanzudai ba'a samu iyayentaba ana kan nema, gashi bata magana bare asamu wasu bayanai daga gareta.
'Yan sandama suna aikinsu na binciko Wanda ya aikata laifin ta hanyar Number motarsa da matashin nan ya d'auka.
To ALLAH yasa adace amin.
A6angaren Safna kam abubuwa sun cakud'e danta tsaya kaida fata batason auren, anbuga anbuga tak'i, anyi lallashin abanza, hardai takai yau ya Shaheed ya zaneta amma abanza, Dan tace wlhy aka matsa mata zatabar gidan.
Hankalin Abba yatashi sosai, yarasa mafita, gashi har anfara shirye shiryen biki, Dan gobe za'a kawo lefe............
*_Luv u oll fan's d'in aunty bilyn Abdul._*
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣5⃣&1⃣6⃣
Tana kwance agadonsu tana sharar kuka Rahma tashigo, da sauri tak'arasa gaban gadon tana fad'in haba aunty Safna yakamata kibar kukannan haka, ko sokike kizo kanki yana ciwone?.
Safna ta tashi zaune dolene nayi kuka Rahma kinajindai yanda ya Shaheed yace aure babu fashi, wlhy nikuma bana sonsa....
Rahma ta katsemata zancen da fad'in toni aunty Safna ganinake tunda bawani kike soyayya dashiba kawai kiyima su Abba biyayya mana. Tunda kinsan bazasu cutar dakeba.
Safna takamo hannun Rahma tarik'e gam kamar tana gudun kar'a kwace mata ita, ta ce, "Rahma bazan 6oye mikiba, zan gaya miki dalilin bijirema su Abba.
Wlhy sati hud'u dasuka wuce zuciyata tayi tuntu6en kamuwa dason wani bawan ALLAH, a makarantarmu muka had'u kuma wlhy ina bala'in sonsa, kullum sainayi mafarkinsa.
Lokaci k'an k'ani guy d'in ya sace zuciyata, nikam nad'auki aniyar nemoshi duk inda yake, inaji ajikina shine uban 'ya'yana, yanzu haka nabada kwangilar nemosa, shiyyasa duk abindasu Abba zasuyi saidai suyi bazan yarda amin Auren doleba.
To amma aunty kina ganin kinyi dai dai kenan?.
Da Sauri tad'aga mata hannu kinga baneman shawara nakeba, nabaki labarin sirrin zuciyatane kawai, Dan haka sauraramin, ragamar rayuwata ahannuna take Dan haka bazan yarda azalunceniba inaji INA gani.
Ainaga kema kin isa auren, miyasa Abba bazai aura masa keba saini?, idan kinajin banyi daidaiba toke kice su aura masa ke, nikuma abarni da Wanda nakeso, danhaka tashimin anan banason shishshigi da k'wala kai afaranti.
Haka Rahma ta hak'ura dukda k'ok'arin datakeyi na fahimtar da yayar tata muhimmancin biyayya ga iyaye, da illar bijire musu, amma firr Safana taki'i saurarenta, daga k'arshema abin fad'a yaso yazamar musu.
Rahma tabata hak'uri ta tashi tafita.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Bikifa ya kankama, bak'i harsun fara sauka, ayau kuma za'a kai lefe Dan haka matansu ya Is'haq duk suna gidan.
Akwatuna har goma sha biyu nagani baje afalo, dangi anata d'agawa ana jinjina kai dayaba k'yan kayana, Appa da babban yayane sukayi lefe, ya sulaiman yad'auki nauyin duk wani abincin daza'aci, ya Hamza kam suna 6angaren cashiya, shine yahad'a faty za'ayi dina da daddare bayan an d'aura aure ankawo amarya.
Ammi ta had'a mother night ana gobe d'aurin aure.
Suma su khairiyya da matan su ya hamza ba'a barsu abayaba sun had'a Sisters day washe garin d'aurin aure da safe kafin ayi walima.
(Nace hummm kaga bikin d'an gata).
Ango kam babu abinda zaiyi saidai gyaran gidansa, Dan za'a canja MASA fenti da abundan ba'a rasaba tunda andad'e babu kowa agidan, "tun bayan rasuwar Ni'ima daya Shiga rud'ani kamar yayai hauka yasa Appa ya tattaroshi yamaido gida kusadasu.
Kayan lefe kam sunyi masha ALLAHU saidai mak'iyi aunty Rashida matar ya is'haq tafad'a tana fesama kanta turare.
Dariya suka shek'e da ita suduka, aunty Sameera matar ya Hamza ta ce, "k'yaface haka aunty Rasheeda tunda kina ragema amarya turare.......
To aii gara kafesa, k'ila idan amaryar tazo wannan mijin nata maikama da soja ya hanaka fesawa.
Dariya suka kuma shek'ewa da ita harda tafawa kamar wasu k'awaye.
Adai dai wannan lokacin kuma Bobo yashigo falon shida ya Hamza.
Ahankali suka fara tsagaita dariyar tasu, ya Hamza ya ce, " kukuma lfy?, miya sakaku dariya haka?.
Aunty Sameera ta maimaita musu abinda yafaru, dariya ya hamza yayi, bobo kam saiyayi murmushi yana kallon aunty rasheda dake dariya, ta ce, "ka kafeni da ido konayi k'aryane?.
Kauda Kansa yayi yana murmushi, ya ce, " aunty Rasheeda kenan, kisanifa saikin biyama matana turarenta babu d'aga k'afa.
Nanmadai dariya akayi, Aunty ummy ta ce, "lah bobo dama kanason auren nan amma idan anyi magana kaita wani basarwa?.
Okey da kin d'auka banasone aunty ummy?, tsaya kiga ikon ALLAH bayan d'aurin aure zakisha mamaki Romeo zan zama.
Dariya sosai sukeyi harda ya hamza da Ammi dake sakkowa daga saman Appa.
Shikam bobo d'akinsa yashige yana murmushi.
Bayan sunyi dariya mai isarsu suka koma tsokanar bobo ya Hamza yana kare masa, danshi tunda yashige d'aki yak'i fitowa.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Alhmdllh yau lefe ya iso gidansu Safna, anyima 'yan kawo lefe tarba ta girmamawa, kowa ya kalli lefen saiya jinjina kai, Dan kayane masu k'yau da birgewa.
Sund'an dad'e agidan sannan suka tafi cikeda tukuyci na girma.
Cikeda zumud'i Rahma tashiga d'akinsu, Safna tana zaune tana chart da baseera daketa k'ara zugata wai karta yarda da wannan auren, *boy ya ce, " yana gab da samo mata bobonta.
Murmushin jin dad'i taketa zabgawa, k'arar rufe k'ofa da Rahma tayi yasa Safna d'agowa, Rahma tak'araso gurinta tana washe baki, aunty Safna kinga kayan lefenki kuwa jar ubancan kai, wlhy kamar basusan ciwon kud'iba.
Baki safna ta ta6e sannan tagallama Rahma harara yarinyarnan na kula kemafa kanki da motsi, banace kidaina jingina aurennan danibane Dan uwarki, kakin yakamata kitaya farinciki Dan lefennan nakine baniba kam, saikuma tayi wata 'Yar dariya Rahma lefena yana nan zuwa daga Bobona, k'ilama sannan kinada ciki hhhhhjhhhh ta shek'e da dariya harda rik'e ciki.
"Na ce, " hummmmm".
Rahma kam girgiza kai kawai tayi, tana mamakin halin kafiya da dagiya irinna Safna, tanayin Abu kamar batada ilimin addini, ALLAH ya k'yauta tafad'a afili tana ficewa ad'akin.
Amin safna tafad'a ita tana Raka Rahma da harara.
Ran Abba a 6ace yake, sai safa da marwa yake afalonsa, gobe d'aurin aure amma Safna ta tsaya kaida fata bata son aurennan, yau Uncle Abubakar sau biyu yana dukanta shida ya Shaheed amma tace Sam batasan zancenba, daga k'arshema kayanta tahad'a waizata bar musu gidan.
Ya Shaheed ne yashigo falon Abba da sallamasa, Abba ya amsa yana mai tsurama Shaheed d'in ido kamar yau yafara ganinsa, ya Shaheed ya rissina ya gaida Abba sannan ya zauna ak'asa kan kafet.
Shima Abba saiya nemi waje ya zauna.
Ya Shaheed ya sauke numfashi Kansa ak'asa ya ce, "Abba dama wata shawarace nazo da ita.
Ina jinka Shaheed Abba yafad'a da hanzari.
" Hummm Abba inaga tunda Safna tak'i har yanzu, dataje tamana abin kunya inaganin kawai mubarta, inhar zasu yarda kawai abashi Rahma.
Abba yazaro ido waje, Shaheed baka ganin Rahma batayi k'ank'antaba!?.
Abba batayi k'ank'antaba, tafa gama secondary, kuma yanda nasan Rahma da hakuri da biyayya bazata bijirema umarninkaba kamar yanda safna tayi, nasan zata yarda ta auri Abdulmalik indai Rahma ce......
Dai dainan Rahma tashigo falon, tiren dake hannunta ya su6ce, abinda ke ciki yazube jikinta sai rawa yake saboda jin furucin ya Shaheed na k'arshe.
Ya Shaheed ne yamik'e da sauri yakamota ya zaunar, cikin taushin murya ya ce, kiyi hak'uri Rahma kibi umarnin Abba kifiddashi daga kunyar mutanen daya tara, kikalli gidannan cike yake da danginmu, wasuma daga wani gari suka taso, kituna d'unbin mutanene da Abba ya gayyata wad'anda zasu halarci taron d'aurin aure gobe idan ALLAH ya kaimu.
Rahma kema kinason Abbanmu yaji kunya?, kamar yanda Safna tayi, jibi kiga yanda hankalin Abba yake atashe akan abinda baifi k'arfiba daga garemu.
Rahma tad'ago kai takalli mahaifinsu dashima su yake kallo, gabad'aya fuskarsa ta canja, Abbansu muntum mai sauk'in kai da hak'uri amma yau 6acin rai ya maidashi wani iri, ita saitagama kamar yarame.....
Ya Shaheed yad'an ta6ata, da sauri takalleshi, ya ce, "baki aminceba kema ko?.
Yanda ya Shaheed yay maganar saiya bata tausayi shima, ahankali ta jinjina kai, cikin kuka ta ce, " nayarda yaya wlhy na amince zan fidda Abba kunya... Shashshekar kuka tahanata k'arasawa."
Cikin farin cikin ya Shaheed ya rungumeta, Abba kuma yarungumesu gaba d'aya.
Sai albarka suke saka mata da addu'ar fatan alkairi, itakam tana kuka tana sharar hawaye.
Abba yakira Appa ya sanar masa komai bai 6oye masaba.
Appa ya ce, "babu wani damuwa da Safna da Rahma duk d'ayane tunda daga tsatso d'aya suka fito, shima yayta sakama Rahma albarka.
Abba yaji dad'i sosai, sukayi sallama.
Ummi ma Abba yakirata tazo d'akin, jin abinda yafaru yasa ta rungume 'yartata cikeda farinciki dakuma saka mata albarka, saidai gefen zuciyarta tana tausayin Rahma, aganinta nawa Rahmar take, amma babu yanda zasuyi, sun tara d'unbin mutane wannan ne kawai mafita agaresu Baki d'aya.
Fatanta ALLAH yasa mijin nata yakasance mai kula da tausaya mata, Dan Rahma tanada rauni sosai, dukcikin 'yayansu babu Wanda yakai Rahma hak'uri, daga ita sai ya Muneer, sune suka d'ebo halin mahaifinsu Sak, na Rahma ma yafi nasa, Dan Rahma akwai hak'uri, kuma yaran gidan duk sunfita k'yau sosai.
Rahma ba fara bace amma tanada d'an haskenta daidai gwargwado, zamu iya kiran rahma tsaka tsaki batada tsawo bakuma gajera bace, tanada d'an jiki Dan 'Yar lukutar ummi ma da akece mata, idan akafad'a tayita kuka bataso, tanada k'yanta daidai gwargwado (saidai Safna tafita k'yau nesa ba kusaba), Abu mafi d'aukar hankali ajikin Rahma shine idanunta, wasu irin idanu Rahma take dasu masu hasken tsiya da girma kamar suffar kwai, duk yanda ran Rahma ya6aci basa canja kala saidai su k'ank'ance.
ALLAH yabama Rahma baiwar juya idanu, gasu masha ALLAHU da girma, sau dayawa idanun Rahma kan fisgi hankalin mutane kanta Dan danan tashiga ransu Dan ita mutumce mai saurin Shiga rai, indai zaka zauna da ita saita shiga ranka.
Wannan kenan.🤸🏻♀👌🏼
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Labaridai ya isa kunnene Bobo "wai Amarya bata sonsa", amma abin bai bashi haushiba sosai, tunda dama shima ba auren yakesoba, Dan haka da yarinyar tasoshi da karta soshi duk uwar ubansu d'aya ko akwalar rigarsa, shi dama wadda za'a bashi yanzu d'in ta ce, " itama bataso, da wlhy har k'yauta zai mata.
Na ce, "hummmm.........
❤❤❤❤❤❤❤ *_masoya kumuje zuwa yanzufa aka fara gashi suya sai ran sallah_*😂👌🏼
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣7⃣&1⃣8⃣
Kafin la'asar zazza6i yarufe Rahma, tana d'akin Abba kwance ak'udundune, ya Muneer yashogo da Dr kaleed har cikin falon Abba.
Abba da kansa yashiga d'akinsa yatasoda Rahma daketa rawar sanyi, saman kujera ya zaunar da'ita Doctor yashiga aikinsa, babu wata matsala Alhaji 'Yar damuwace kawai Dr Kaleed yafad'a.
Abba ya ce, "to Dr babu wani taimako da za'ad'an bata kenan?.
A'a zan mata allura da magani tad'an samu barci, insha ALLAHU daga nan zuwa yamma zata koma Normal, yanzudai idan namata allurar tad'an samu koda tee ne tasha saitasha magani tayi wanka da ruwa maid'an sanyi ta kwanta, insha ALLAHU normal zata tashi nanda anjima.
To madallah Dr mungode sosai.
Babu damuwa Alhaji aii aikinane.
Babu 6ata lokaci Dr yayma Rahma duk abinda yadace, ummi tabata shayi tad'ansha kad'an tabata magani Wanda tashashi da k'yar Dan Rahma akwai tsoron allura da magani, bataso ko kad'an allurarma saida lallashi akayi.
Bayan tasha maganin ummi ta taimaka mata tayi wanna a bayin Abba, kaya aka d'akko mata tasaka takuma kwanciyarta a gadon Abba sai barci.
Hummmm wai ina Safna?.
Tana nan acikingidan kuma labari yakai mata, ancanjeta da Rahma, Dan haka tadage tarink'a tsallen murna ita taci nasara, shikenan zata mallaki bobonta nanda lokaci kad'an, har ruwa tazuba k'asa tasha Dan dad'i.
Cikeda farinciki takira Baseera ta guntsa mata, murna sosai ta tayata harda jinjina da yaba k'ok'arinta na dagiya.
Bayan sungama da baseera takira zeenat itama, zeenat ta ce, " wlhy Safana kin tafka babban kuskure a rayuwarki, na tabata nangaba saikinyi Dana sani Mara iyaka, son zuciya yasa kin bijirema iyayenki akan Wanda baima San da zamankiba, ke kanki bakisan Inda yakeba yanzu, bakida tabbacin zai kar6eki kobazai kar6i soyayyarkiba, wlhy kidaina biyema hud'ubar baseera zatayita kaiki tana baroki a tashar wahala ne......
Safna ta k'atseta atsawace, kee!!! Dallah malama yimin shiru, nakiraki nafad'a mikine danki tayani murna ba surutun banzaba, aiikin banza kawai mtsowww taja tsaki tana yanke wayar.
"Daga can Zeenat ta girgiza kai tana fad'in ALLAH ya shiryeki Safna, amma zakiyi nadama wlhy na tabbatar."
Babu Wanda yakumabi takan Safna shagalin biki akacigaba da gudanarwa, itama tafita harkar kowa agidan lamuran gabanta kawai takeyi harda yima Rahma dariyar mugunta.
Na ce, "hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*
Bobo ya lalubo wayarsa dake wringing daga aljihun jins d'insa, ido yad'an zaro tareda kallon Ya Sulaiman dake duba yarinyar da akaima fad'e.
Lfy kuwa bobo?.
Tab ya Is'haq ne kasanfa sunacan suna jiranmu..... K'ara kiran da akayine yasa Yakuma kallon wayar, ya is'haq d'innedai, d'agawa yayi tareda yin sallama.
Abdulmalik wai kuna inane kaida sulaiman?, ya Is'haq yafad'a daga can.
Wlhy muna asibiti wajen yarinyarnan amma gamunan zuwa Ku k'ara hak'uri.
Tom yakamatafa kuyi sauri Dan akwai abubuwa agabanmu masu yawa.
Gamunan yanzunan insha ALLAHU.
yanke wayar yayi tareda dawo da kallonsa kan ya sulaiman, ya Sulaiman yakamatafa muje kasandai masifar babban yaya, muk'arasa kafin ya k'ulu.
Gsky ne muje kawai aii nagama harma takoma bacci.
Bobo yad'an lek'a fuskarta, ya ce, " baiwar ALLAH, wlhy rashin maganar yarinyarnan yana damuna, yakamatafa ace iyayenta sunsan halin datake ciki.
Hakane gsky to amma yazamuyi? tunda bamusan idan takeba, saidai mucigaba da addu'a. Idan kuma tak'ara samun lfy mubi shawarar Ammi mumaidata wajenta kawai.
To shikenan bobo yafad'a yana fitowa.
Waje yanufa shikuma ya sulaiman yashiga office Dan ajiye kayan hannunsa.
Babu dad'ewa yafito, mota yashiga Inda bobo ke zaune a mazaunin direba, bobo yatada motar suka fice daga asibitin.
.+.
Gidansu Safna kuwa anyi shirin kamu Wanda aka had'a a babban harabar gidan nasu, saidai matsalar amarya babu lfya tana d'akin Abba kwance tana barci.
Hafsat matar ya Shaheed ta kalli ummi, ummi to yanzu yaza'ayine harfa dangin angon sun iso ga babu amarya, dama Safna zata mana alfarmar yanzu kawai saita zauna amadadin Rahma d'in.
A'a barta kawai hafsat, nibanamaso muna saka Safna acinkin sha'anin bikinnan, takalli agogon dake hannunta, hafsat inaga bari kawai atada Rahma d'in dukda dai bata dad'e da kwanciyaba.
A'a ummi abarta kawai likitafa ya ce, tana buk'atar Hutu, gashi dangin ango since k'arfe tara akwai mother Night, yakamata tasamu ishashshen barci kafin sannan, yanzu bari nayima Basman aunty Yahanasu magana saita shirya tazauna amadadin amarya tunda kusan kansu d'aya.
Yauwa hakama yafi, dama gasu suna kama ba laifi.
Haka suka saka Basma aunty yahanasu k'anwar ummi tashirya tsaf tamkar amaryar, idanma baka saniba saika d'auka Rahma d'ince Dan suna matuk'ar kama, idanuwa kawai Rahma zatafi Basma.
Dahaka aka gudanar da kamu Wanda yak'ayatar da dangin ango, su khairiyya da khursiyya dasu aunty Rasheeda sai zuba lik'i suke wa amarya, Dan basusan ba amaryarsu bace.
Dahakadai taro yatashi gab da magriba Alhmdllh.
Duk shagalinnan da akeyi Safna tana d'aki kwance abinta, da barcima takeyi kid'an da'aka sakane yasa tatashi tana mita da tsaki anhanata barci wai, wayarta ta d'auka takira *boy danneman k'arin bayani akan aikin data bashi.
Ya ce, "mata yana nan yana k'ok'ari.
Tana yanke wayar takira Baseera sukaita labarinsu Rabi duk akan bobone.
Na CE hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Su bobo suna isa gidan suka Tatar da ya Is'haq da ya Hamza zaune aharabar gidan, harda wasu samari wajensu bakwai, cikin samarin danginsune, ya Hamza yana cikinsu sunashan shafta.
Ya Is'haq kam yana gefe zaune saman mota Dan bakomai yake Shiga cikinsuba kasancewarsa babba.
Bayan bobo yayi fakin suka fito, wajensu ya Hamza suka k'arasa, hannu sukaita bama matasan samarin ana musabaha🤝.
Bayan sun gama gaisawa Bobo yanufi Inda Ya Is'haq yake.
Hannu yabashi shima suka gaisa.
Ya ce, "kunje kun wani mak'ale a asibiti tamkar kun manta da abinda me gabanku.
Sorry babban yaya, bobo yafad'a yana had'e hannayensa waje d'aya alamar tuba🙏🏻.
Dirowa ya Is'haq yayi, to yazanyi idan ban hak'uraba ma.
Motocine suka fara shigowa gidan, bobo yabisu da kallon yana fad'in wannan gayarfa daga ina?....
Daidainan ya Hamza da ya sulaiman suka k'araso garesu.
Ya Hamza ya ce, " daga gidan amaryarka suke, sun halarci kamune.
Baki bobo yad'an ta6e ya Hamza miye kuma kamu?.
Kafin ya Hamza yabashi amsa aunty Rasheeda da aunty ummy suka k'araso, aunty sameera dasu khursiyya suna biye dasu.
Bud'a aunty Sameera tarangad'a akunnen bobo, yay saurin toshe kunnansa, saida tagama sannan ya kalleta fuska a shagwa6e, kai aunty Sameera dodon kunne zaki kashemin?.
Dariya suka shek'e dashi suduka, yayinda aunty Rasheeda tafara fesama bobo turare mai shegen k'amshi, kaima ankamaka kamar yanda mukaje kama amaryarka.
Dariya su ya Sulaiman suka saka danganin yanda bobo ya kwa6e fuska tamkar zaiyi kuka, ALLAH matannan nakula kun rainani yafad'a yana hararsu.
Dariya sukayi gaba d'aya harda wasu daga cikin dangi dasuka zagaye wajen.
Aunty ummy ta ce, "tab wlhy Bobo matarka ta had'u jar ubancan kai, kaiga wasu idanu masha ALLAHU, (" nace hum danma bakiga na asalin amaryarba kenan), tacigaba da fad'in aifa inaga aka kawo amaryarnan bazaka ringa fitaba, aikinma hak'ura zakayi dashi.
Dariya sosai ake shek'awa, dukda haushi da yacikama bobo ciki wannan bai hanashi murmusawaba, ya ce, ''yan sa ido, kunje kunata k'arema yarinya kallo, halan har muninta kun gano?.
Wata Zainab acikin danginsu ta ce, "wlhy ya Abdulmalik babu mai iya gano munin Rahma amarya, masha ALLAHU kam komai yaji zam zam..... Tak'are maganar da rufe baki.
Nanma dariya akayi, shikam ya ce, kwadaiji dashi sa'idinniya kawai masu barci da ido d'aya, yana gama fad'a yafito daga wajen.
Wasu daga cikin 'yammatan jisuke inama sune da wannan guy d'in, lallai yaci sunansa Bobo.
Wasukam kishine yacika zuciyarsu, Dan sundad'e suna nuna masa so yana basarwa saboda jin kai, wasukam har iyayensu saida sukai masa talla amma ya ce, "kai kasuwa.
Cikin gidan yashiga Dan soyake ya d'auro alwala, babban falon k'asa cike yake dam da mutane, yanashiga suka hau tsokanarsa wai angon k'amshi angon k'amshi."
" aransa ya ce, "za'a gogudai".
Haka yagaida wad'anda zasu iya jinsa ya haye sama d'akinsa bayi yashiga yad'auro alwala yafito, su aunty Sameera ma duk sunshigo ciki.
Yazo zai fita Ammi ta ce, " mukarram!.
"na'am Ammi ya amasa yana juyowa, k'arasowa tayi Inda yake takama hannunsa suka fito.
Wani d'an lungu tajashi ya ce, " Ammi lfy dai ko?.
Lfy lau mukarram dama tambayarka zanyi d'azu kuwa kaje gidansu amaryar taka?.
Gefen wuyansa ya sosa, afuwa ammi, wlhy abubuwane sun mana yawa.
Kanta ta girgiza haba mukarram ya inamaka kallon mai hankali amma kanason 6ata wayonka?, babu dad'ifa, iyayen yarinyarnan bazasuji dad'iba ace bakaje gidanba tunda aka fara maganar aurennan, shin kai zakaso ayima su khursiyya hakane?.
A'a wlhy ammi bana fata, amma Dan ALLAH kiyi hak'uri nayi kuskure, insha ALLAHU zan bata hak'uri anjima idan munje mother night.
To shikenan ammadai Baka k'yautaminba, Bahaka nasoba.
Tom kiyi hak'uri Dan ALLAH.
"Ya wuce."
Yauwa ammi an kar6o d'inkin Nawal kuwa?, wlhy namanta shaf, kuma harda wanda zata saka anjima.
Eh khairiyya ta amso d'azu kafin sutafi wajen kamu.
Yauwa harnaji dad'i, bari naje sallah ammi har an tayar inagama su yaya sun wuce.
To saikun dawo.
Masallaci yanufa ammi kuma takoma ciki.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Anayin Sallar magriba Safna ta sid'ad'e tabar gidan, sai gidansu kamal, acewarta bazataje wajen wani mother Night ba, saikuma tana zuwa gidan ta tarar dasu Ameera suna shirin zuwa harda momynsu.
Dayake momynsu kamal tasan komai Dan baba abubakar yasanar da ita, (k'anin Abba ne, kuma mahaifi gasu Br kamal abokin aikin bobo) batace mata komaiba itama, safna tashige d'akin Ameera tayi kwanciyarta, sukuma suka nufo gidansu Safna d'in, akabarta itakad'ai agidan sai 'yan aiki.
Rahma ta farka bayan sallar magriba, kasancewar tana fashin Sallah saikawai aunty Madeena matar ya muneer tasata tayi wanka.
Mai kwalliya tafara aikinta na fente fuskar Rahma.
Itadai Rahma bin kowa kawai takeyi da ido, kad'an kad'an saita share hawaye, saida mai kwalliya tamata magana sannan ta tsagaita da kukan aka tsantsara mata kwalliya ta d'aukar hankali.
Wani doguwar riga bubu aka bata tasaka, tawani material Orange da d'igo d'igon lemon green ajiki, aka nad'a mata lemon green d'in d'ankwali, sai fashion na 'yankunne da sark'a maid'an tsawo, tasaka bak'ar coka wadda ta manne awuyanta.
Yasalam nafad'a yayinda naga amaryar k'amshi tafito ras kamar ba Rahman ummiba, tayi k'yau masha ALLAHU.
Fos aunty hafsat tabata, wadda itama takasance lemon green, sannan tasaka takalmi lemon green shima mara tudu.
Hummm komaifa yaji ajikin amarya.
Ihsan k'anwar Br kamal tamatso kusada ita, kai Rahmana kinyi k'yau wlhy, na tabbata angonnan yaganki saiyace gwamma da akayi, wlhy saikin susutashi.
Basma ta ce, "ni tsorima nake karya rikice yace daganan sai gidansa.
Duka Rahma takai musu, cikin dasashshiyar muryarta datasha kuka ta ce, " yan iska kawai, aii dama halinku d'aya.
Dariya suka shek'e da ita harda tafawa.
*_Bobo_*..........
*_godiya muke masoya, ALLAH yabar zuminci._*
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
*_"wannan page d'in nakine Maman useey alkairin ALLAH yakaimki har gidan baban useey, ni marak'issiya naji sak'onki wajen aunty bilyna."_*
Luv u🤸🏻♀👌🏼
1⃣9⃣&2⃣0⃣
A 6angaren bobo kam bayan sun dawo daga masallaci aharabar gidan suka sake zama, hira aketayi da barkwanci, saida aka k'ara kiran sallar isha'i sannan suka mik'e, masu sake alwala suka sake, wadda tasu bata karyeba sukayi gaba.
Ana idar da sallah suka shigo gidan, shiri suka fara, kowa yana k'ok'ari kada time ya k'ure.
Bobo kam wanka shima yashiga, yafito d'aure da tawul fari a k'ugunsa, k'arami kuma yana goge kansa zuwa fuska da wuya har k'irjinsa zuwa k'asa.
Wurga tawul d'in yayi saman kujera, yaja kujerar madubi ya zauna, mai yafara shafawa, hardasu farar fauda afuska, yashafe kansa da mai mai k'amshi har zuwa sajensa dad'an gemunsa na gayu, yasa kum yak'ara taje kansa da gemunsa, sannan yay amfani da burosh wajen kwantar da sajensa, yako kwanta luf sai walk'iya yake da tashin k'amshi.
Turarurruka yad'auka kala kala yafeshe jikinsa, sannan yanemi guri abikin gado ya zauna batareda niyyar saka kayaba.
Atsakar gida kam mutane harsun fara fita, Dan kowa bayaso atafi abarsa, dandanan motoci suka fara d'aukar mutane, kowa ya cakire da kalar kayan dayakeso, manyan iyayene kawai suka saka wani Dan datsetsen less fari tas, suka nad'a Orange d'in gwagwgwaro, masha ALLAHU abin sai Wanda yagani.
Su khairiyyama ba'a barsu abayaba, sunci ado da dogayen riguna na lemon green d'in material sunyi k'yau masha ALLAHU, suda matansu ya sulaiman duk iri d'aya suka saka.
Nawal ma anshiryata cikin farin less irinnasu Ammi, doguwar riga aka mata, aka nad'amata Orange d'an kwali, yarinyar tafito d'as kamanninta da bobo ya k'ara fitowa.
Tare suka shiga Mota da Ammi.
Ya Hamza yafara waige waige, cikin Jan tsaki ya ce, "wai mi Bobo yakeyine tun d'azu yafasan saiyaje sun taho da amarya, gasu ammi harsun wuce.
Ya is'haq shima yay tsaki ALLAH yaron nan d'an wulak'ancine, Hamza kaje d'akinsa kaga miyakeyi?.
Ya Hamza yanufi d'akin Bobo, ya Sulaiman dai baice k'alaba.
La'ilah Abdulmalik minene haka?.
Bobo dake zaune yana latsa waya yad'ago yana kallon ya Hamza daya had'e cikin Farin Suit sai k'amshi yake.
Minayine yaya?.
Bansaniba, dallah malam kana 6atamana lokaci katashi kasaka kaya, su Ammi harsun wuce.
Baki yaturo kamar wani k'aramin yaro, nikam wlhy ya Hamza barcima nakeji.
A'a kakan barci kakeji ya Hamza yafad'a ahasale, wlhy zankira ya Is'haq.
Da Sauri bobo yamik'e, yafara saka gajeren wando da bes, ya warware had'ad'd'un Suit lemon green sai d'aukar ido sukeyi.
Wandon yafara sakawa da Orange d'in Riga mai dogon hannu, ya tsuke k'ugunsa da belt, ya Hamza yad'auki nektayit d'in green yafara saka masa, shi abumma dariya yabasa, amma baiyi dariyarba gudun kar ya Hamza yasake k'uluwa.
Da taimakon ya Hamza yasaka rigar Suit d'in, yafara saka botiran ya hamza na gyara ma kwala d'in. Takalmima saida ya taimaka MASA yasaka, sannan yak'ara feshe jikinsa da turare, yad'auki wayarsa d'aya yazura a aljihun Suit d'in, suna tafiya yana d'aura agogo.
Na ce o'o me bobon Ammi sai a slowly.
Saida ya Hamza yaga yashiga mota a baya, sannan shima yashiga mazaunin direba Nasiba d'iyar k'anwar Ammi na gefensa.
Suma su ya is'haq suka tada mota, suna gaba su bobo na bayansu har anguwar su Rahma.
Ak'ofar gida suka faka, ya Hamza yafita shida Nasiba har cikin gidan suka Shiga sukace afito da amrya ango yazo.
Gaban Rahmane yafad'i Ra's, jitake tamkar tafasa ihu, kowacce irin tarba angon zai mata ta tanbayi zuciyarta?.
Batada mai bata amsa, tana cikin zancem zuci aunty Ruk'ayya ta ce, taso Rahma angonki yazo.
Jitake tamkar ta ce, bazataba amma yazatayi.
Haka aunty Rukayya takamo hannunta sukayo waje, dama dayawan mutanen sun tafi sai k'alilan suka rage.
Kowa yashiga mota amarya kawai akejira.
Ya Hamza yabud'e d'ayan gefen da Bobo yake zaune Dan ganin amarya tafito. Azuciyarsa ya ce, ''masha ALLAHU, gsky amaryar auta ta had'u.......
Isowarsu ta k'atse masa tunani, yayinda gaban Rahma keta fad'uwa azatonta Ya Hamzane angon, kanta na k'asa aunty Ruk'ayya tasakata amotar.
Wani k'amshine da sanyi suka bigi hancinta, tashak'a talumshe ido azuciyarta ta ce, ''oh ALLAH, wannan wane irin k'amshine?.
K'ok'arin gyara zama tayi saitaji ta dunguri mutum, dasauri tajuyo ta kallesa, yana zaune ak'ame kamar wani jinin sarauta, saidaifa k'amshin amaryar tasa ta narkar da zuciyarsa, saiwani lumshe idanu yakeyi, ahankali yajingina bayansa da kujerar ya lumshe ido.
K'irjin Rahma sai dukan uku uku yake, jitayi wani sabon zazza6i yana neman rufeta, dukda kallon fisha tayima angon nata ta tabatar ya had'u masha ALLAHU.
YA Hamza dake tada mota ya ce, amaryarmu ykk?.
Muryar Rahma na rawa ta ce, "ina yini.
" lfy lau, ya fara hidima?."
Alhmdllh tayi maganar ahankali.
Tad'an kalli gefen Bobo ta ce, ina yini.
Dukda yagane dashi take amma yay shiru.
Takuma cewa ina yini, sai asannan ya amsa da lfy, ykk?.
Kasa amsashi tayi, sai kawai tayi k'asa da kanta tana wasa da zoben hannunta.
Sunkusa isa wajen faty d'in Bobo yatashi zaune sosai, wata leda yad'akko agefensa yazaro rafar 'yan 200 guda hud'u yad'ora saman cinyarsa.
Rahma data k'urama zonen hannunta ido saikawai taga mutum ya d'oro hannunsa saman cinyarta, gabanta ya ce, "wani Rasss!, fos d'inta yazare data d'ora saman cinyarta ta d'ora hannunta akai.
Tabud'e idonta ahankali daga rintsewar datayi, Fos d'in yabud'e yaga 'yan 50 rafa biyu sai wayarta, wayar yaciro yasaka kud'in daya ciro aleda yasa a fos d'in maida wayar yayi zai rufe fos d'in amma tak'i shiga dan tacika dayawa.
Ciro wayar yakumayi yarufe fos d'in yad'ora mata saman cinyarta, wayarta kuma yasaka cikin aljihun suit nasa, nufinsa idan sunje angama taron talik'a kud'in saiya bata.
Itadai Rahma batace masa k'alaba Dan batasan miyayi da fos d'inba.
Har gaf da d'akin taron ya Hamza ya faka, yafito yabud'e musu k'ofa, asanyaye Rahma tafito, duk kunya ta isheta tasaba duk inda zataje saida k'aton hijjab, amma yau gata kod'an gyale babu, sauk'intama Rigar bubuce kuma tabud'e bata matsetaba.
Su yaya Ishaq suma fitowa sukayi daga motarsu, suma kayansu iri d'aya dana ya Hamza.
Suma sun yaba da amaryar k'anin Nasu sai masha ALLAHU suke jerowa.
Ya Hamza yashiga d'akin taron yasanar da MC amarya da ango sun iso.
Aiko nanfa yafara kayayato, falon taron yay tsit anzuba ido aga amaryar Bobo d'an gayunnan maiji da kansa.
Ahankali Bobo yatako har zuwa gaban Rahma data duk'ar dakai k'asa kamar ace ar ta gudu.
Ahankali ya ce, "bismillah muje.
Jerawa sukai suna tafiya ahankali har cikin wajen, bayansu kuma su ya Sulaiman ne suka take musu baya.
Tunda suka shiga wajen taron jikin Rahma yay sanyi, Dan ita irin mutanan ne masu tsoron shiga mutane, dandanan tafiyarta ta sauya, sai wani sassarfa takeyi.
Raf raf raf raf!! d'akin taron yad'auki tafi lokacinda Rahma ta hard'e taigaba kamar zata fad'i, da sauri Bobo yaruk'o hannunta yana fad'in ezeee madam.
Ajiyar zuciya tasauke danjin bata fad'iba, a u okey?, yafad'a yana kallonta. Kai tad'aga da sauri.
Tom kiyi ahankali plzz karki ji ciwo.
Ngd tafad'a tana kallon k'asa, to muk'arasa ya nuna mata hanya.
Ahankali suka taka zuwa inda aka tanar musu, sunbirge mutane gsky saidai mak'iyi, kowa fad'i yake sun dace da juna, Ammi saijin dad'i takeyi Dan harga ALLAH Rahma tashiga ranta.
Suna zama DJ yasaki wak'ar because, i luv u. Wannan wak'ar Bobo ce dayake bala'in so sosai, ya Hamza yabada wak'ar asaka Dan Bobo.
Aikuwa sai sakin lallausan murmushi yakeyi danjin dad'in wak'ar.
Masu hotuna kam sai aikinsu suke, itadai Rahma kanta yana k'asa tana shak'ar daddad'an k'amshin turaren Bobo.
Bayan wak'ar tak'are aka fara gudanar da abinda ya tara mutane.
Ammi tayi bayani da godiya ga d'unbin mutane dasuka halarci mother's Night d'in, sannan taima amarya da ango fatan alkairi.
Rahma taji dad'in bayanin ammi itada danginta, wannan kad'ai ya isa yanuna mata dangin mijin nata suna sonta.
Ankira amarya da ango filin rawa, shuru sukayi kamar bazasu tashiba, kowa da abinda yake kitsawa a zuciyarsa, saida mc yasakeyin magana sannan suka mik'e ahankali.
Afilin rawar suka tsaya k'ik'am babu mai motsi balle rawa, itakam Rahma dama bata rawa da dadai safan ce kam wannan gwanace.
Bobo yafiddo rafar kud'i yafara lik'ama Rahma idonsa k'yam akanta, itakam kanta na k'asa, Dan danan guri yad'au ihu da tafi, jiki a sanyaye Rahma itama tabud'e fos d'inta danufin d'akko 'yan wazo d'inta saitaga kud'i dayawa.
d'agowa tayi ta kalli bobo, shikuma yad'aga mata gira kuwa, da sauri tamaida kanta k'asa, yamatso da bakinsa wajen kunnenta cikin muryarsa mai taushi da laushinnan ya ce, "ko bakisone?.
Ajiyar zuciya ta sauke itama ahankali ta ce, " ngd sosai".
Hak'k'ine akaina aii yafad'a idomsa agefe kamar bashi yayi maganarba.
Batace komaiba itama tazaro kud'in tafara lik'a masa gashi yamata tsawo, amma ahaka taringa masa lik'i ihun mutane da tafi yak'aru, masu hotuna da video sai haskasu sukeyi.
Ammi ta taso itama ta rungume Rahma tana saka mata albarka, tafara lik'ama Rahma 'yan dubu dubu, (abin na manyane masu karatu), Bobo ma yakoma lik'ama Ammi sai murmushi yake saki itama Ammi haka, Rahma kam kanta ak'asa itama tana lik'ama ammi.
Su yaya sulaiman ma suka taso, dandanan gurin ya kaure da lik'i kamar ba'asan ciwon kud'iba, k'awayen ammi da danginta duk suntaka rawar gani, hakama dangin Rahma ba'a barsu abayaba, kai wannan taro ya k'yatar masha ALLAHU.
*_(can na hango Aunty bilyn Abdul tana lik'a 'yan naira 5🤣😜🤐, ba ruwana kartajini)._*
_karfa kuce nina fad'a🤸🏻♀_
Sai k'arfe 11:30pm taro yatashi lfy, kowa yafara k'ok'arin tafiya, Rahma duk barci yacika mata ido, cikin mota take zaune tana jiransu bobo sugama sallamar bak'i shida yayunsa, saida kuwa suka gama sannan suka shigo, yanzu kam wani d'an uwansu bobone zai maidasu ba ya Hamza ba, su ya Hamza matansu suka d'auka da yaransu sukayi gida.
Rahma ta kifa kanta kan cinya harta fara barci, kallonta kawai yayi baice komaiba, shifa koma sunanta bai saniba, bai tada itaba har sukaje gidan.
Yay shiru yana tunanin yanda zai tasheta.
Lukman ya kallesa Bobo kona baku gurine?, a'a malam wane kabamu guri gida zata shiga, ita barcima takeyi.
To ka tada ita dare na k'arayi shabiyu saura fa.
Daurewa yayi yad'an ta6a bayanta, ko motsi batayiba, yakuma d'an bubbugawa, firgigit ta tashi da addu'a abakinta, tad'an kallesa, shima idonsa na kanta, munzo yafad'a akasalane.
d'auke kanta tayi tabud'e motar, saida safe tafad'a cikin muryar barci, harta rufe motar Lukman ya ce, "haba malam aii ka rakatadai kasani kotanada magagin barci.
d'an tsaki bobo yayi shima yafito, harta fara tafiya yad'an hanzarta ya cimmata, dama ita kad'ai mai gadi yake jira Dan haka k'ofar abud'e take.
Dariya Lukman yashek'e da ita, sai Bobon Ammi yafad'a harda dukan sitiyari.
Har k'ofar falonsu yarakata, saida takama k'ofar zata bud'e sannan ta ce, " saida safe.
ALLAH yakaimu yafad'a yana juyawa.
Amota yasamu Lukman yashiga gaba suka wuce gida suma..........
_masoya I luv u._
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
*_"dolene na gaisheku Nice Hausa novels, mungode sosai da k'auna, ALLAH yabar zuminci, Alkairin ALLAH yakai muku aduk inda kuke."_*
Luv u oll⛹🏻♀.
2⃣1⃣&2⃣2⃣
Jiki a sanyaye Rahma tak'arasa cikin falon, tamaida k'ofar ahankali tarufe.
Ajiyar zuciya ummi dake zaune a fallo tana jiran dawowar Rahma ta sauke.
Dama ita take jira dantaga kowa yashigo amma banda Rahma.
"Lah ummi bakiyi barciba?, Rahma tafad'a a sanyaye. Mik'ewa ummi tayi tana murmushi, inani ina barci auta bata dawoba.
Murmushi Rahma tayi kanta ak'asa.
Ummi ta taso takama hannunta suka nufi d'aki, mutane duk sunyi barci, wasukuma suna gidansu ya Kamal.
Rahma tarage kayan jikinta sannan tazauna bakin gadon inda ummi take zaune itama da wasu tarkacen robobi agabanta.
Ummi miye wad'annan?, Rahma tafad'a tana d'aukar wata robar Zuma tana kallo.
Maganin basirne, kinga k'ar6i wannan takardar kiduba, d'azu malam saddiqu na islamiyyarku yakawo bayan fitarku.
Cikin mamaki Rahma takar6a tana bud'ewa, murmushi tayi tareda d'agowa tana kallon ummi da itama kallonta takeyi, ummi wai kinsan miye?.
A'a saikin fad'a.
Sak'one daga islamiyyarmu, wai gobe idan ALLAH yakaimu sun shiryamin walima k'arfe 9:00am to 12:00pm, dukda abin yazo babu shiri.
ALLAH sarki bayin ALLAH, ummi tafad'a cikeda jin dad'i, aiko mun gode musu da wannan karramawa.
Aiko dai, Rahma tafad'a.
Abubuwa ummi ta rink'a dannama Rahma a darennan, harsaida Rahma ta ce, " ALLAH ummi nak'oshi cikina zai fashe.
Dariya ummi tayi ta ce, "to barshi haka saida safe.
Daga nan wasu kayan gyaran jiki ummi ta murjema Rahma jiki dasu sannan suka kwanta.
*_BOBO._*
suna Isa gida yanufi d'akinsa, kayan jikinsa yafara ragewa, yana k'ok'arin zaro wayarsa a aljihu saiyaga ta Rahma, Kansa ya dafe O ALLAH, namanta ban bata wayartaba, zubesu yayi a durowar gefen gadon harda tasa, daganan yacire kayan jikinsa, bayi yashiga, bayan wasu 'yan mintuna yafito, badai wanka yayiba.
Shirin barci yayi ya kwanta, saidai barcin yak'i d'aukarsa, fuskar Rahmace take MASA gizo, k'yawawan idanunnan NATA yake hangowa, yasaki wani lallausan murmushi Wanda bansan na miyeba, saikuma yaja siririn tsaki yana gyara kwanciya.
Nima waje nayo nabarsa.
*_Washe gari_*
Tunda sassafe Rahma ta tashi tai wanka kasancewar tana fashin sallah, Basama tafara yarfa mata k'unshi, masha ALLAHU nafad'a Dan k'unshin yana bada ma'ana.
Jikin Rahma duk yayi sanyi, ta tabbata yau babu fashi saita bar gidansu, cikin dabara take share hawayenta dankar Basma tagani dansukad'aine a d'akin.
Zuwa 8:00am angama k'unshin, yayi k'yau sosai, 8:30am akasa Rahma yayi wanka agurguje dantafiya walimar makarantarsu.
Shiri tayi cikin zani da riga na atanfa pink, ta d'ora bak'ar alk'yabba mai shara shara wadda amaren zamani ke yayi, tayi k'yau sosai dukda yau babu kwalliya afuskarta, dak'yarma tayarda Basma tasaka mata pink d'in janbaki Wanda shiga da kwalliyar alk'yabbar.
Wajen walimar yayi k'yau sosai, acikin harabar islamiyyar za'ayi, malaman sunyi k'ok'ari gsky dukda abin yazo babu shiri.
Wajen da'aka tanada na musamman dan d'alibai su Rahma suka zauna, iyayen yara dayawa sun halarci wajen, su Abba ma duk sunje, su ya kamal ya muneer ya shaheed, da sauran matasan anguwar da iyayensu, dan Rahma mutuniyar kirkice, tsakaninta da kowa a anguwar sai girmamawa, batada hayaniya wannan yasa takasance mai jama'a kowa yana sonta.
Gurin yayi tsit ana addu'a, shigowar wasu motoci hud'u yaja hankalin mutane kowa soyake yaga suwaye?.
Appa yafara fitowa shida wasu dattijai uku, da alama abokansane, mota ta biyu kuwa matasan family nasune, ta ukuma haka harda ya ishaq da wasu zasukai sa'anninsa, motar k'arshe kuwa, ya Hamza da sulaiman, Lukman da tauheed ne, sai Bobo Wanda yakashe kala cikin manyan kaya, purple d'in shaddace mai haske ajikinsa, rigar iya guywa d'inkin zamani, yayi k'yau sosai harda d'ora bak'ar hula.
Wow! Wasu 'yammata dake gefen Rahma suka fad'a, d'aya tace kai Ruma guy d'incan ya had'u wlhy, dama ya ce, "yana sona?.
Rahma tad'ago dantaga wanene wai suketa kurantawa haka?, gabantane ya fad'i tayi saurin kauda kanta.
Abbane yataso shida abokansa da shuwagabannin makarantar suka tarbi su Appa.
Masauki maik'yau aka basu kamar ansan da zuwansu.
Bayan gaishe2 akaima bak'i barka da zuwa.
Itadai Rahma tunda tamusu kallo d'aya bata sakeba.
Dukda da daddare yaganta hakan bai hanashi ganetaba, babu laifi yarinyar tanada k'yau da nutsuwa, bobo yafad'a azuciyarsa.
Mayun idanunsa yadasa mata batareda ya saniba.
Rahma datakejinta atakure, jikinta yana bata kallonta akeyi, tana d'agowa sukaima juna kallon ido cikin ido, Dan suna fuskantar junane.
Da sauri ta janye nata gabanta na fad'uwa, hular alk'yabbar taja takuma rufe fuskarta.
Samun kansa yayi da sakin lallausan murmushi, ya sauke ajiyar zuciya yana kauda kai daga kallonta.
Addu'a aka fara gabatarwa sannan aka buk'aci Rahma tafito tayi karatu.
Gabantane yafad'i, tatuna d'unbin mutanen dake wajen amma acikinsu akeso tafito tayi karatu?....muryar malaminsu taji yana k'ara nanata sunanta.
Ihsan ta ta6ata Rahma kitashi mana.
Ihsan inajin kunya wlhy.
Kinga saka wannan gilas👓 zaki rage jin kunyar.
Siririn farin gilas d'in takar6a tasaka, o ALLAH nafad'a danganin k'yawun da gilas d'in ya k'ara mata.
Ahankali tamik'e tak'araso har inda ake buk'atar ganinta, malam jamilu yabata abin magana.
Tunda tatsaya gaban tebir d'in da aka ajiye alkur'ani mutane ke kallonta, wasukam halittar ALLAH suke yabawa da nutsuwa Rahma.
Appa sai dad'i yakeji Dan yarinyar tashiga ransa.
Gurin yayi tsit danjin zazzAk'ar muryar Rahma tafara fidda sautin karatun alkur'ani mai girma cikin suratul Maryam.
Bobo yalumshe idanunsa danjin muryar Rahma na ratsa ko ina na sassan jikinsa, ALLAH ya albarkaci rayuwarki yafad'a azuciyarsa, ahankali yabud'e idonsa yasauke akan Rahma dake karatu tana hawaye Wanda gilas d'in bai hana agansuba.
Masu hotuna sai k'allata suke, wasu kuma da waya suke mata, harda masu vedio d'inta.
Saida takai har k'arshen surarar sannan taje ta zauna tana cigaba da share hawayenta Wanda narasa namiye?.
Angabatar da nasiha ga amarya da Ango mai ratsa jiki da 6argo, har malam yana tsokanar Rahma da ALLAH yasa wata shekarar su taru haka a sunan baby, dayawan mutanen wajen sunyi dariya dafad'in ameen, (bobo kam murmusawa yayi kawai).
Angabatar da k'yaututtuka ga amarya Rahma, Wanda makaranta suka karramata da yaba k'ok'arinta na hazik'ar d'aliba mai ilimi da girmama manya da rashin karya dokar makaranta.
Abba sai dad'i yakeji.
Cikin abokan Appa dasukazo tare yamik'e shima ya ce, "yayma Rahma k'yautar mota sabuwa dal saboda namijin k'ok'arinta.
(Kabbara akayi da tafi).
Rahma tamik'e tayi godiya, takuma godema iyayenta da malamanta dasuka taka rawar gani arayuwarta, ta ce, ''iyayena sune gatana dasuka tsaya tsayin saka Dan ganin ingantuwar ilimin mu na addini dana zamani, tana kuka tana godiya ga iyayenta abbanta da umminta da yayyaensu da malamanta,....... Kuka mai k'arfi yaci k'arfinta takasa magana sai shashsheka."
Ahankali bobo yamik'e yataka har Inda take, hanky yamik'a mata fari tas daketa tashin kamshin daddad'an turarensa.
Jiki a sanyaye takar6a idonta ak'asa ta ce, " ngd tafad'a cikin shashshekar kuka.
Abin maganar yakar6a daga hannunta, yafara mik'a godiya ga iyayensu da kuma malamai da 'yan uwa da abokan arzik'i dake wajen taron, yahad'a da sakama Rahma albarka da yaba mata.
Kabbara akayi da tafa MASA, abin ya burge mutane gsky, Rahma taji dad'i sosai, dukda tasan ba Sonta yakeba tunda had'asu akayi, amma yay mata wannan karamcin.
Abba da yayuntama sunji dad'i abinda bobo yayi.
Hakama su Ya Hamza bobo yaburgesu, fatansu ALLAH yasa yad'ore haka har gidan aurensu.
'Yammata kam dayawa sun k'yasa saidai sun 6oye kodan Rahma.
Bayan jawabin manyan bak'i da nasihohi taro yatashi lfy, daga nan akayi hotuna kowa yakama gabansa.
Kowa yana zuwa gida yafara shiri a gaggauce Dan ana sakkowa daga masallaci za'a d'aura auren.
Kowa yafito anata shiga mota Dan tafiya sallar juma'a da d'aurin aure.
Masha ALLAH nafad'a yayinda na hango muku ango Bobo yaci kwalliya cikin Sky blue d'in shadda harda babbar riga, wayyo masu karatu bayyana muku k'yan dayayi 6ata lokacine, ammafa ya had'u.
Masallaci suka nufa.
Bayan sakkowa suka wuce anguwar su Rahma.
_Alhmdllh anguwar tacika mak'il da jama'a, wasuma akan mota suke zaune, gurin yacika har babu gurin faking, dukda nisan da su Rahma suke dashi da titi, wasu sai abakin titi sukayi faking motarsu._
K'arfe 3:30pm d'umbin al'ummar Annabi suka shaida d'aurin auren *_"Abdulmalik Aliyu Abdulmalik hamshak'i, da amaryarsa Rahma Bilal Basheer mai Gold. "_*
(To ango da amarya saimuce ALLAH yabada zaman lfy da fahimtar juna ameen).
Dak'ar na iya samo muku Rahma amarya ad'akinsu itada gayyar k'awayenta Wanda yawanci duk yaran family nasune, wasu kuma 'yan islamiyyarsu da boko.
Tahad'u cikin less ja mai adon farin siton masha ALLAHU, amarya tafito ras saidai mak'iyi.
anacewa and'aura auren tafara kuka, su Ihsan suna lallashinta.
(To Rahma sai hak'uri aii).
*_Safna_*
Safna ana gidan su ya kamal, ita adole tayi gudun hijira, ko wanka batayiba bare kwalliya, tana kwance ad'akin Ameera tana chart abinta hankali kwance, fira suke da k'awayenta a group suna tsokanarta wai tamusu bak'inciki, dayanzu sunata shan shagalin biki.
Dariya tayi ta ce, " karku damu aii kwanannan zakusha bikin nida bobona.
Toma ALLAH ya kaimu...
Kafin tabada amsa Zainab autarsu Ameera tashigo tana fad'in an d'aura aunren.
Wata gagarumar fad'uwar gaba tariski safna dake kwance, tadafe k'irji tana fad'in ya salam, saikuma ta sauke ajiyar zuciya takoma takwanta, haka kawai taji jikinta yayi sanyi, zuciyarta tayi k'unci.
Zuwa wani lokaci kuma saitaja tsaki, tomima zai dameni tunda ALLAH ya tsallakar dani daga wannan auren k'addarar.
Rahma ALLAH ya yanka miki kazar wala sai aje aita figa.
Sainazo gayyatarki aurena da Bobo na.....
Na ce, "hummmmm.
*_" kuyi mana afuwa jiya bamuyi posting ba, mai copy d'ince take mura, nikuma nayi busy, amma gashinan yau nadage nayi muku kafin ta warke tacigaba."_*
Luv u oll.
_bilyn Abdul ce⛹🏻♀._
*luv u oll my fan's_*
*_(((S))).......2017._*
👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
2⃣3⃣&2⃣4⃣
Biki yacigaba da gudana cikin farin ciki da Annashuwa, gidajen biyu anata hada hada.
Bayan kammala d'aurin aure anguna suka shigo cikin gida akayi gaishe gaishe da hotuna, itadai Rahma koda wasa bata yarda sun had'a ido da Bobo ba har aka gama hotuna suka tafi.
Shikam jinsa yake wani iri kuma cikin nishad'i, komai na Rahma yana burgeshi, musamman yanda take komanta cikin sanyi.
Haka suka k'arasa gidasu, nanma cike yake da mata, tunda suka shigo akai caa kan bobo, sai tsokanarsa su aunty Rasheeda sukeyi, baya cewa komai saidai murmushi.
+.+.+.+.+.+.+.+.+.+.+
*_5:30mp_* aka gama shirya amarya domin mik'ata gidan angonta, tana falon Abba inda dangi suka zagayeta anata nasiha gareta, sai rabzar kuka take tamkar zata shid'e, ummi ma kuka takeyi Dan takasa cewa komai yayinda aka kaimata Rahma gabanta dan taimata nasiha, babu abinda take fad'i sai ALLAH yay miki albarka Rahma, yanda kikai mana biyayya kema ALLAH yabaki 'ya'ya masu yimiki, kuka yaci karfin ummi takasa cigaba.
Haka aka hak'ura aka fito da Rahma, Abba dakansa yasakata mota tanata kuka, ya Hamza dazai tuk'a amarya jiyayi tabashi tausayi, shima kamar yay kuka yakeji.
Kuka sosai Rahma takeyi abin tausayi, momyn su Ihsan da Maman Basma suka shiga motar suma, tsakkiya suka saka Rahma daketa kuka har numfashinta na d'aukewa.
Yayinda Abba yaga motocin amarya sun Lula, yatabbatar da gsk yau Rahma ta barsu, sai kawai yaji hawaye sun cika masa ido, yasa gefen rigarsa ya share tareda juyawa gida.
Canma tararwa yayi ummi NATA kuka, yashiga lallashinta damata nasiha.
Gayyar amarya ta isa gidansu Bobo, Dan nan za'a ajiye amarya sai gobe idan ALLAH yakaimu amaida ita gidanta.
Har cikin harabar gidan aka shiga da motar amarya.
Suna fitowa saiga Ammi da gayyar k'awayenta, wasu sosuke kawai suga mace mai sa'a data samu bobo amatsayin miji, Dan sunsha bashi 'yayansu amma ya ce, a'a, (basu San itama had'asu akayiba ba soyayya bace).
Sanye Rahma take cikin shadda ruwan madara zani da Riga, ta lullu6a da k'aton mayafi ruwan k'asa mai turuwa, hakama takalmin k'afarta, kanta arufe yake shiyyasa masu tsogumi basu ganiba, Ammi tarungume Rahma tana lallashi, kama hannunta tayi takai har cikin d'akinta na sama, lallashinta tad'anyi na minti biyu saida taga tad'an tsagaita da kukan sannan tafito aka tura k'awayenta.
Gida ya harmutse Dan cike yake dank'am da jama'a, gashi yau Ammi takeyin yinin biki dama.
Sai bayan magriba dangin amarya suka juya domin zuwa suyi shirin tafiya wajen dinner daza ayi k'arfe 8:30pm to 12:00.
Gidan yad'an rage hayaniya kad'an tunda mutanen sund'an ragu babu laifi.
Duk wannan hidimar da akeyi bobo yana can cikin lambun gidansu da aka k'awata da haske, shikad'aine zaune akan kujera mai lilo idonsa alumshe yana duniyar tunanin rayuwarsa shida marigayiyya Ni'ima.
Yatuna itama haka akaiyi aurensu baya sonta, Dan ko taro d'aya bai halartaba alokacin na shagalin bikinsu, shiyyasa yake mamakin wannan karon komai Appa yace yayi baya musu saiyaje yayi.
(Wata zuciyarsa ta CE sannan ai kana kan hayak'in samartaka ne).
Hakane kuma yafad'a afili.
Bud'ar data cika gidance da k'aruwar hayaniya ta tabbatar MASA da amaryarsa ta iso, yamatse idonsa dake arufe tareda fad'in ALLAH yajik'anki Ni'ima ta, kifahimceni ba laifina baneba, nima sakani akayi dole badan inason aurenba."
Jiyay tamkar maganar Ni'ima acikin kunnanensa tana fad'i masa, _"karka damu mijina Nima zanyi farincikin kasancewar Rahma amatsayin matarka, kodan tarin alkairai dake tartare da ita, na tabbata Nawal tasamu uwa tagari wadda kullum take maka nacin samu, INA tayaku farincikin mallakar Rahma kaida Nawal, ka kwantar da hankalinka kakuma rik'eta amana"._
Shirun dayajine yasakashi mik'ewa zumbur yafara dube dube da mutsike idanu, Kodai mafarki yakeyi?, da gsk fa muryar Ni'ima yaji wlhy.
Jikinsane yafara Rawa, cikin Sauri yabar cikin lambun Dan aganinsa wata aljanace takeson bud'e MASA ido.
Cikin hanzari ya iso harabar gidan inda su ya ishaq suke, Dan bandasu wajen maida 'yan kawo amarya.
Najeeb abokin ya Ishaq ya ce, "ango lfy kuwa naganka a hargitse?, ko duk murnar zuwan amaryarne?.
Saurin saisaita nutsuwarsa yayi ya sauke ajiyar zuciya yanajan farar kukera d'aya ya zauna, babu komai ya Najeeb yafad'a ad'an d'arare.
Wai tun d'azu kana ina?, ya Ishaq ya tambayeshi.
Ina lambu." Yabada amsa atak'aice.
Hira su ya Ishaq sukeyi amma bobo kokad'an baya sakamusu baki, addu'oi kawai yake zabgawa azuciyarsa, fatansa ALLAH yasa abinda yaji ya tsaya iya haka.
Suna nan zaune har aka kira sallar isha'i suka tafi sukayi.
Amarya tanacan ana zabga mata kwalliya, da k'yar aunty Sameera da aunty ummy suka lallasheta tayi shiru aka fara kwalliyar.
Hummm amaryafa tagama had'ewa abin kamar babu gobe.
Shiryata akayi cikin farar doguwar riga ta aure, amma mai dogon hannu, aka nad'a mata d'aurin d'ankwali da bak'in d'an kwali, tasha sark'ar gold wadda k'yautace daga Abba, kai jama'a yaufa take sallah, amma awajen amarya da ango, amaryakam tayi d'am kamar kasaceta ka gudu, na tabbata ko bobo yagani yau saiya narke.
Shimadai ba'a barsa abayaba wajen d'aukar wanka cikin farar shadda harda babbar riga, ya murza bak'ar hula sai kyalli takeyi, sajensa da sumarsa sun kwanta luf luf sai tashin k'amshi yakeyi, cikin hanzari yake d'aura agogon azurfa ahannunsa saboda masifar da ya sulaiman yake masa.
Haba Abdulmalik kai kullum sai anjiraka?, aurenka nefa, kai yakamata ace komai kana gaba amma kaine abaya haba Dan ALLAH."
yi hak'uri nidai ya sulaiman muje nagama aii.
Haka suka fito sai zabga k'amshi yakeyi, yaukam amarya tarigasa, Dan tuni tana mota, bud'e masa Ridwan yayi yashiga inda Rahma take.
K'amshinsu yahad'e Dana mortar ga sanyin AC saiya bada wani yanayi mai dad'in gsk.
Rahma kam lumshe idanunta tayi dataji shigowar Bobo motar, kanta na k'asa Dan bataso su had'a ido ko kad'an.
Shikam saida ya zauna sosai harma sun fita daga gidan sannan yakai kallonsa kan Rahma da k'amshin turarenta ya addabesa.
Tsigar jikinsace ta tashi yarrrrrrr O ALLAH, yafad'a ahankali wandda har Rahma taji furicinsa, wani Abu yaji yana mintsinin zuciyarsa, da k'yar yay control d'in kansa, murya k'asa2 ya ce, yauma aramin fos d'inki.
Bata kalleshiba tamik'a masa bak'ar fos d'in wadda tasha adon fararen duwatsu sai kyalli suke.
Jiki a sanyaye yak'ar6a, yauma kud'i yazuba mata, rafar 'yan d'ari biyar Biyar, sababbi k'al.
Bai bata fos d'inba har suka isa wajen taron, itakuma bata tambayeshiba.
Bayan tsayawarsu Ridwan yabud'e musu suka fito, Rahma tana tsaye har bobo yak'arso wajen, hasken wutar lantarkin daya yalwatu awajen yabashi damar k'are mata kallo sama da k'asa, itadai kanta na k'asa Dan dukta Raina kanta kallon dayake mata.
Murmusawa yayi Dan ganin yanda take sinne kai k'asa, fos d'inta yamik'a mata, tasaka hannu biyu takar6a tareda fad'in ngd.
Baice komaiba yagyara tsayuwarsa suka jera.
A Bokansa da 'yan uwa samari da 'yammata duk suna bayamsu kowanne shida budurwa d'aya, gabansu kuma Nawal ce da Kaleel d'in ya Ishaq, suma anmusu kwalliya cikin kaya kamar su Rahma doguwar Riga Nawal, Kaleel ma kwalliyarsa kamar ta bobo harda malum malum.
Abin ya k'ayatar da jama'a masha ALLHU.
Ahankali taji Bobo yasak'a hannunsa mai azabar laushi da sanyi cikin nata, da sairi ta kalleshi, shima kallonta yayi da sauri danji wani laushi na musamman da hannun nata yakeyi, k'asa ta maida kanta danjin wani yarrrrr ajikinta saboda lallausan murmushi da Bobo yasakar mata.
Tafiya sukeyi ahankali Rahma tana zancen zuci, tunda aka fara bikinnan koda wasa bobo bai ta6a jikintaba sai yau, saikuma jiya data kusa fad'uwa awajen mothars night, wannan kuma takalleshine amatsayin taimako daya bata dankarta fad'i. Dan haka k'irjinta ya hau luguden daka, (zuciyarta ta ce, "yanzu kinzama matarsa sa6aninda daba halalinsa bace ke.)
Kobabu komai ya burgeta, tunda yakasance mumum mai sanin muhimmancim addininsa da bin dokokin ALLAH.
Har suka k'arasa inda aka tanadi kujeru biyu ajere dansu, saida tafara zama haryanzu hannunta na cikin nasa, sakin hannunta yayi ya tattare babbar rigarsa ya zauna shima fuskarsa ad'an sake babu laifi.
Nawal dasuka rakosu tazo kusada shi tatsaya, baby tafad'a ahankali.
Kallonta yayi yamata murmushi tareda kamo hannunta, babyna kinyi k'yau yau, miya faru?, tayi 'Yar dariya bakomai baby amma wacece wannan?.
Juyawa yayi yakalli Rahma da kanta ke ak'asa tana wasa da duwatsun jikin fos d'in ta, yay murmushi.
Zan fad'a miki amma ba yanzuba, kije ga ya Kaleel can yana kiranki Ku zauna wajensu momy.
To baby bye, tafad'a tana sauka daga wajen.
Shima hannu yad'aga mata yana murmushi.
Taro aka cigaba da gudanarwa yanda yakamata, yauma amarya da ango basuyi rawaba, saidai lik'i dasukaita zubama juna, yayinda dangima suka rufesu suna lik'a musu suma, mai wak'a yaga ruwan kud'i yakuma haukacewa yana wak'e ango da amarya.