1️⃣
Tun da ta ji kalaman Bappansu na karshe cikin lumshe ido da qarfi tasakar musu wani irin tsumammen kuka me daga hankali tareda kara cukuikuyo shararar doguwar red colour bridal veil dinta daya rufeta rass har izuwa kasa kaidaga ganin yanayin shigarta kasan ta sabuwar amaryace wanda baifi mintina kadan ne ya rage adaura mata aure ba..
A hankli jikinta yake rawa rawa koinanta yadau kyarma tsaban takaici da wata iriyar matsanancin ruɗani dake famar cinta acikin ranta wanda bazata iya fasalta yawarsa ba, wasu maqudan hawaye ne kawai suka shiga gangaro mata akan fuskarta yuuu wanda daga ganinsu kasan bata shirya musu ba.
yanayinta mai cike da jin tsoro da kuma tsananin tashin hankali tadada sunkuyar dakai ayayinda take agurfane a tsakiyar babban falon nasu zagaye da dattaijai mutane hudu, inda tsiraran hannayenta da kafafunwanta masu sulbi da haske da sukaji wani irin hadadden xane na jan kumshi suke dafe akasa daf da inda ruwan hawayen nata ke diddiga kamar an kunnashi.
kuka kawai take rabzawa ahankali wanda zafinsa saida yy kama da kamarna wanda zata cire ranta ta fetar wajje, cike da dauriya tadago kai jin tsananin zafin maganganun bappan nasu nadawo mata kai, babu shiri kuma dakyar tadago kai takalli dattijuwar mata dake sanye da hijabi kusa da ita tana goge hawayen dake sauka acikin kwayar idonta tadan sunkuyar dakai da wani irin sanyin jiki babu wata alamar dai yau zata budi baki ta kareta, zuciyarta a raunace ta kalli bappan nasu da yay maganan shima fuskarsa still na hade ne tamau tamkar bakin hadari jitay bata samu kwarin gwiwar cemasa komai ba shima dan gabaki daya batasan ya zata fara fidda kanta acikin wann cakwakiyar ba
babban surkuwan gidan nasu anty rainahanatu da ake cewa Ammi babba dake falon itama duk tabi ta tsime sai tsaki take sakewa jifa jifa dan dama ta tsani auren, babu dai wanda yace uffan acikinsu, kara runtse ido ayaanah tay sosai tadinga rabza kuka me sanyi me kuma hade da zazzafar shesheka duk ta rasa ya zatayi, can dai hannunta dake rawa rawa ya fara motsi ba acikin hayyacinta ba ta capke bakin zanin wata tsohuwa data rabza uban tagumi agefen bappan nasu ta mugun tsimewa da tsananin fushi har idanunta sunyi jaaa zirr tanakan girgiza kafafunta a masife
cikin rawan murya da gunjin kuka takamo hannun tsohuwar ahnkli cikin raunateccen magiya muryanta bai fita sosai tace "Don girman Allah hajiya kice su bappa suy yi hakuri wallh wallah bansan komi ba banyi masa komi ba don Allah kice su dan saurareni ni ban san wanda yayi min haka ba..."
amugun fusace tsohuwar ta warce hannunta da wani irin fushi me tattare da buhun barkwanon masifa caraf ta mike tsaye tana cewa "Ni da Allah sakeni ki wallh haushi kike bani, wato ke har kinsan ki aje mu anan kiyita rabza mana uban rantsuwa akan karya alhalin ke din ashe babban munafukace ko Ayaanah?toh tirrr da halinki. makanki kikayi bawa mu ba dan ganan abu mun gani ido da ido me kq zakice mana kin cuce kanki, kin tozarni.. kin kuma kashe aurenki tun ba adaura shi ba. Allah ya isanmu ma irin tarbiyan da muka taru duka muka baki agidan nan nide Allah ya isa tsakanina dake muguwa kawai!wallah ko su zaidu zasu yafe miki nikam bazan taba yafe miki ba, baqar almuramura, Allah sai ya mana sharia, dan koda aka kawoki daga kauye ubanki saidai yaje har dakina yayimin zagin kaca kaca ya hadamin da mugun baki cewa zakizo gabana ki lalace a binni, wato shine kikeso ki dada tabbar masa ke asalin watsaiyace, kin zo gaban ƴayana kin zamo cikkyar marar mutunci marar kamun kai kika maida kanki yar kwaltaa abayan idanunmu yo shikenan ranar aurenki ne kika zabi ki toxartani kiji dadi ko? meye burge ki da wann rayuwan ynx uban wayema xai amince yakara aurenki a fadin duniyan nan wayyo na shiga uku ni me tuwo Wallah baki isa ki kasheni ba wani dan uban Dukan bazata takai mata ajiki abazata tana kuka cikin raki tana cewa...
..toh wallh ki sani uwata Azumi bata tsinemin ba, kafin ki dauko mana abun kunya gwara tun wuri mu mu kunyata ki yo meya burgeki da irin wannan rayuwar ta yan iska inba samun waje ba?
daga ita har ayanahn kuka sukeyii ganin ta kara tantameta duk dama dukanta take kanyi tanata kukan sosai kuma acikin ruɗani, bakinta har na rawa cikin kukq da magiya takecewa "Hajiya dan Allah ki saurare ni, nasan kinsan ban aikata komi ba, wallh zaki iya dubani kigani, wallah wallh wallh ban aikata abunda kuke tunanin na aikata ba.. sharri.. aka...bansan yaushe...
bata karasa me zatace ba taji saukar wani dan uban saukar ginannen mari da tsohuwar ta kai mata me mugun zafi a bqki sanda ta saketa tariqe bakin ma batasani ba.
"banace miki kiyi min shiru ba, makira kawai annamimiya duk za'a taru amiki karya ne bayan ga shaidu nan zaidu ya kawomin su kaca kaca?kece acikin bidion nan fa ayaana bayan kinsaka natara dangina da mutanen anguwa kafff, nayi shelar aurenki kina gani hakanan akayita zagina akanki, akace min naci amana, nayi son kai, har mayya sai da aka kira ni, kai meye ma ba acemin a anguwan nan ba? haka naruntse idona kyam sabida aurenki da yaron nan rufin asirine agaremu baki daya amma dan tsabr rashin sanin darajar kai saida kika kekeshe idonki kika tozarmu "Ayaanah.. ni menayi miki?...toh wallah wallah baki isa ki dora min hawan jini ba, muna da yadda zamuy dake inke ban isa dake ba ai akwai wanda na isa dasu agidan nan, ki tashi ki bace min ana kar na tattaki nakaiki har lahira.
Ayaanah ta mike jiki babu kwari duhu duhu take gani agabanta har ta fita a falon tana kuka sosai kamar ranta zai fita..
direct dakinta ta nufa don tasan komei xata ce anan babu wanda zai saurareta ders too much evidence dat are pointing againts her which she knew nothing about, bayan tashiga daki kan gadonta tanufa tana rabza kuka sosai ayayinda kanta da kirjinta ke bugawa dan harga Allah batasan wani irin hukunci kuma za'a yanke mata ba.
bayan wucewar ayaanah daki tsohuwar tana kan kuka ta kalle bappan nasu tace "yau naga ikon Allah Zaidu. dan Allah ayaga hotonan nan bideon ma duk agoge kaji? sann ayi maza arabata da wayann mutanen banzan datake bibiya, banason wani a dangi ma yasake jin labari bare ganin shaidun nan.
tun be amsa ba ta dada rushewa da wani kukan kmr an bugeta,
"Allah mun gode maka, wai sai ka haifi ɗa amma baka haifi halinsa ba wallah mahaifyar ayaanah mutuniyar kirki ce yanxu meye wannan take so maqiya na suce akaina kenan..
cikin sauke ajiyan zuciya bappan nasu yace Ahtoh nide nagaya muku hajiya Auren ayaanah dai ya fasu, shida bakinsa yakirani yace min ya fasa bazai aureta ba, snn shine ma ya tura min wann shaidojin ga kuma jama'a sun taro dama sai an daura auren ayaanahn ne kafin agabatar da na su zainab Arifah, ni duk rasa mafita yanxu kam ai jin kunyan mutane ne kawai ya rage mana saidai in....
wani caraf babban surkuwan gidan Ammi babba ta capke maganan abakinsa tanamai cewa 'a'a, yaa Zaidu tsaya, ai magana kam ya riga ya kare tunda auren ayanah ya fasu me kuma zamuyi ai kawai afito fili kawai aje a bayyana masu kawu babba komi kar abata musu lokaci kasan yadda yaci buri akan auren yarsa zainab Arifah yatara manyn mutane kar abata musu lokci akan aikin banza. hhmm ayyuriri dama anbar yarinya tana abunda tagama dama kam ai babu wani abun da za'a samu a karshen rayuwrta face jin kunya, kuma ai wanda suka taru sua bude mata hanya ta lalata kantan sunsan kansu..
da gefen ido ta jefa baqar maganan ga dayan dattijuwa dake sanye da hijabi agefe, ganin bata ko dago kai ba taji wani irin dadi aranta dan dama wnn irin ranar kawai take jira na jin kunya danta gumsa musu bakin ciki.
fade fade take inda take shiga bata nan take fita ba, ganin dai babu wanda yace mata uffan haryanxu yasa tafara daga musu hankli burinta kawai aje filin taro a fallasa komi..
hidima biyu ne ga lokaci nata tafiya inma tsoron zubda ma kawu babba kimansa akeyi, toh mezai hana kawai a tura ayanahn takoma inda tafito ace kawai guduwa tayi takoma kauyensu if not wallah kaf zuria sai munji kunya bana kadan ba dan abundai akwai zubar da kima da mutuncin manya aciki.
tunda ta fara maganar kauda kai kawai bappa zaidu yay kamar wanda baijin surutan nata ahnkli yanamai lallatsa wayarsa da alama yana rubuta wani sakone, yana gama rubuta sakon ya tura ya tabbata ya isa snn yakashe wayarsan, sai a sann ya juyo ya kalleta adan taikace amma baice mata uffan ba kawai ya girgiza kansa..nan take falon ya kuma dauka da wani irin shiru bakaramin hade rai ammi babban tay ba sabida ta tsani tay magana duk taga an shareta..
within 5 scnds karar waya yakatse shirun nasu,dayan dattijuwar matar dake zaune shiru tana hawaye ita ta dauki wayar after uttering few words ta katse wayr snn ta kalli bappa zaidu da sanyin jiki ayayinda muryanta ke fita a cikin nitsuwa kuma ahnkli tace
"yaa zaidu, Mujaheed ne yakira yace in sanar dakai cewa yaga sakonka kuma yana daf da isowa gidan nan shima yanzu".
babu yabo babu fallasa cikin sassauto da bacin ran dake fuskansa ya kalleta cikin sauke karamin ajiyan zuciya snn ya amsata da "toh fatima Allah ya kawoshi lafiya, komi yar hakuri ce dan haka ki kwantar da hankalinki everything will be fine.
kanta akasa tana share kwallanta Tace mishi toh Ameen. dan kadan ya mayar mata da sanyin murmushi ita kuma tay maza ta sauke kanta kasa adan kunyace.
kallonsu ammi abban takeyi kamar zata tashi tsaye ta haɗiyesu su da mugun bugu, dan ɗan wnn calm gestures da yake yawan wakana tsakaninsu bakaramin kona mata rai yakey ba, wato itace datake matarsa na sunna ma bazai amsata ya bata hakuri ba caraf yahau amsa wannan makirar matan. satar kallonsu kawai take tana raya abubuwa masu tsauri aranta ayayinda babu abunda idonta yakey face hararar fatimar tareda jan musu kananan tsaki
share hawaye tsohuwar tay adede lokacin da wani gulluton baqin ciki ya kara rufe mata kirji inta tuna hotonan nan
ganin datayi kmar babban surkuwan gidan anty rainahatu wato Ammi babba zata kara yin wani magana, nan tay marmaza cikin katseta a masife tace "haba, haba..ya isa haka mana ke kuwa Raihanatu, kinyi ta maganan nan duk anji ra'ayinki akan ayanah amma kisani nide ban aminta da gurguwar shawarar kin nan ba, yoo sai kuma aje har babban masallacin jumua ayi shela ace ma jama'ar Annabi S.A.W. cewa yarinyar nan tagudu ranar daurin aurenta sai kace muna kwapcen wasan kwaikwayo?,..
adan masifa ammi babban tace amma hajya kema kinsan halin kawu babba wallh bazai lamunci azo da batu daga gidanan a tozarta shi a bainar muhimman mutane ba aranar daurin aurensa yarsa zainab arifah ba.
fuskar tsohuwar ba asake ba takalle bappa tace "zaidu maganan nan fa ya kare bama sai anje ga tozarta zayyanu agaban mutanensa ba tunda abunda kuke gudu kenan, dolene kawai ayi auren Ayanaah ayau din nan, babu wata zancen guduwa ko fasa shi, tunda shi wanda ya sakar mata fuska ya mata alherin shi ta cutar ta tozarta, yau koma uban waye mukaga dama dashi za'a a daureta yau, inyaso taje can can gidansa ta karashe rayuwarta dashi inma kashe kanta zatayi a dakin miji gara tay da akanda tazauna min agabana ta cigaba da tonamin asiri tay karuwanci a birni ubanta juma nacan kauye yayimin dariya, aure kam kamar an daurashi ayau ko tanaso ko bataso
wani irin shiru wajen yakara daukawa a falon ayayinda fuskar sauran matayen looks soo soo confuse da furucin tsohuwar duk da alama basu wani gama fahimtar inda maganan tsohuwar ya dosa ba, to da waye kenan za'ayi ma ayana auren dolen? da mujaheed ne ko wani ne nadaban daga waje? saidai tun kafin dayansu ta budi baki tay tambaya bappa zaidu yakalle su duka biyun fuskarsa ba a sake ba still cikin gyaran murya yace ya kamata kubami wuri zanyi wata magana da hajiya"..
babu tantama kowaccensu cikin dattijan matan suka mike tsaye cikin hadiye tambayar dake ransu snn suka fice waje.
babban surkuwan gidan anty raihanatu da ake kira da Ammi babba nan tay wani sashe na gidan da sauri sauri tana bambami, dayan nitsatsiyar matan kuma dake sanye da hijabi anty fatima da ake cewa ammi karama nan tanufi dakin Ayaanah kai tsaye jikinta duk a sanyaye, ta iso kofar dakin Ayaanah bata sani ba, kife kai tay akan gadonta tana ta kuka me karsashi gashi ita kanta tarasa amsar da zata bawa kanta, kanta duk ya kulle, she was like is this actually happening to her aranar aurenta, abu ne da batay tsammani ba sai gaba daya sai taji ta fice hayyacinta, she wish zata bude idonta taga mummunan mafarki kawai take,
kwankwasa kofar dakin da akay da dan karfi yasa tadaga idonta da sukayi jaaa suka kumbura tana kallon kofar amma bata da niyyar tashi tabude har akagaji da Knocking aka bar wajen.
Sai can wajen after good 40 mins data dan dawo hayyacinta tana xaune saman gadon kafin ta jawo wayarta da kyar da kamar zata bude sai taji xuciyarta ya kara rauni, MTN sim card dinta take son cirewa ta karyashi sai taga tarin missed calls din kawar aikinta Ruthy yafi guda talatin da wasu irin zafafan text messages da ya ninka calls din daga wajen ango to be din nata, ko wani message data bude zance daya yake yi, " i trusted you, nina miki kaza nina miki kaza lokcin baki da kaza..kinci amanata ayanah, bazan yafe miki ba.." kowani kalma da ya rubuto mata suna daukene rashin mutunci da gori, tsana da zafin cin amana da butulci dayake famr tunanin tay masa.
wasu irin raunattun hawaye suka shiga bin kuncinta bawai dan zafin words dinsa ba sai gani datay wai har ya aminta da komi dayagani akanta kai tsaye, dan tay tunani in akwai wani wanda zai iya bada kwararren shaida mai kyau akan iliminta da tarbiyanta da shine mutum na farko da zai bayar, fita tayi daga Inbox din hawaye me zafi na sauka a idonta, ta bude WhatsApp shi ma dai duk messages din ne har da gori masu zafi aciki, gashi shidin ba yaro bane bare tace ko yana furta kalaman nan ne da gigin yaranta wai yau namijin datake ikirarin zata auresa kenan ke kirarta da watsatsiya karuwa hmmm.
kirijnta taji kamar sai fashe Kashe wayar kawai tayi ta ciro sim card din ta karyashi into 2 pieces kamar yanda tayi niyya snn tajefar da wayar can can saman gado tana goge hawayen da ya ki tsaya mata, sam batay tsammanin haka kwakwalar maza ke aiki akan zargi ba dan wasu tsauraran maganganun nasa ya mugun tsaya mata a zuciya har tanaji ina ma tun farko bata sake ta amince mishi zata aureshi ba.
Knocking din kofa aka sake yi, ta kalli kofar sai kuma tamike a hankali ta nufi kofar ta budeshi ahankli,dayan dattijuwar matan ta gani tsaye suna hade ido nan da nan wasu sabbin hawayen suka ciko idonta tabi ta sunkuyar dakanta kasa cikin sanyin jiki
matar ta shigo dakin ta kulle kofar ayaanah ta bi ta da kallo harta nemi waje ta xauna agefen gado snn ta karasa inda take ta durkusa kasa cikin sanyin murya me tafe da hawaye tace "Ammi karama don girman Allah kiyi hakuri, nasan kema zakice na tozarki wallah bansan komi akan wann abun ba.
matar ta sauke wani ajiyar xuciya ahnkli cikin nitsuwa tace "Ayaanah i am not here to judge you, bare ma ai an riga anyanke miki hukunci auren nan naki bazai fasu ba, su hjiya sunce za'a daurasa a yau, kuma tun da har bappanku ya amince da wann hukuncin da hajiya ta yanke miki kema kinsan babu me ja da wannan hukunci nasu ke dai naki addu'a, nima ina nan ina taya ki da shi..
wani irin numfashi me karfi ayaanah taja abazata wasu sabbin hawayen da bata san dasu ba suka cigaba da sauka mata yuuu amma batace komi ba
cikin lallami ammi karama tace is okay kiy hakuri ayaanah snn kisani nobody is perfect but as long as we learn from our mistake ai shikenen, dan Allah ki kwantar da hankalinki kinji everything will be alright kuma koma waye ya aikata maki haka sai dai mu ce Allah ya isa miki da ya janyo miki wnn masifar harda kuma auren dole da wanda ba musani bama tukuna.
a mugun mugun rikice Ayaanah tadan mike tsaye is like sai yanxu kunnenta ya farajin batun auren dolen da ammi ta ambata..
atake jikinta sai ya fara rawa cikin dafe kirji tare da sakin birkitacen kuka me tafe da rudewa tace "ammi Auren dole da wani wanda baku sani ba kuma? auren dole fa kikace Ammi? dama badashi za'a daura auren ba..?
jiki a sanyaye matar ta dan gyada mata kai tace shikam ai yace ya fasa saidai wani to wanin ne bansan ko waye ba.
a mugun ragwabe ayaanah ta fado kasa tare da durkusowa kasa cikin kuka mai kara, tarike hannun matar tana cewa dan Allah kar ayi min haka Ammi wllh xan iya mutuwa, ammi talk to him plss ai bappa yana jin maganarki sosai, dan Allah kiyi ma hajiya magana i can explain myself wallah wallah bansan komi ba, basai sun min auren dole ba nasan zata saurareki kodan karamin lokaci su karamin i will find a way out of this.
cikin runtse ido tare da jin tsananin tausayinta matar tace nima basu gaya min komi akai ba, amma dai mujaheed is on his way. kinga tunda angon shi yace ya fasa i have no idea what they are planning to do now, ga dai su can a falo inaga by now kuma inaji kmr ma har ma an daura. i am very sorry dear, kisani cewa I trust you. but i think wann ne kawai mafita agaremu duka gwara amiki auren kawai. snn koma waye suka miki auren dashi nasan dai bazai cutar dake ba Allah yasa shine miki mafi alheri.
Ayaanah ta dada rushewa da wani tsumammen kuka cikin mugun tashin hankali take cewa "Na shiga uku Ammi, yanxu baxa ki iyayin komai akai ba?auren dole fa zasu min da wanda kemafa kince baki san shi ba, ya xan yi da raina idan hakan ya faru, wallh ko ya mujaheed din ne bazan iya aurensa baaa innalillahi wa inna ilaihi rajiun..."
Mikewa matar tayi da hawaye taff idanunta da mugun tausayinta aranta tanufi kofa da sanyin jiki ta bude tana fita takulleta da keys ta waje........
saida tay jimm ajikin kofar tana jin kukan ayanah snn itama ta share kwallarta daya zubo mata juyawarta keda wuya suka hade ido da tsohuwar da alama ta fito daga falon kenan ta tsaya cak tana dan share sauran kwallanta da bakin mayafi itama
muryan ammin a sanyaye tace ahmm hajiya kardai har an daura?..
hjy me tuwo batace komi ba tagyada mata kai cike da had'iyar wani gulluton baqin ciki aranta tace eh an daura. "Fatima, dama ke nake nema, amma kafin muje can sama dakina inaso kiyi min alkwari tun anan, kar da mubi hanyar sashe na ynx wata zindikiyar magulmaciya annamimiyar mata taje ta tareki da tambaya akan auren ayanah tunda kowa leifinmu yake gani agidan nan, nide kimin alkwari ko yankaki za'ayi agidan nan bazaki taba yin kuskuren gayawa kowa cewa an daura ma ayaanah aure yanxu afalo na ba, dan wann aure na rufin asiri da sirri ne, bana bukatar uban kowa ya san dashi, kekam dai nasan bani da wata matsala dake...ynxu muje saman kawai zan miki shauran bayani.#08060712446 surayyahms
KIYI SHARING SNN idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[21/10, 18:59] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️2️⃣
kallonta ammi karama ta dingayi baki bude cikin rasa nacewa kawai tagyada mata kai snn tabita sama domin taji dalilin wnn Ɗanyen hukunci da suka yankewa Ayaanah wanda ita kanta zuciyarta acike yake da fargaban irin mijin da zasu zabar mata a wann kuraren lokaci kuma acikin fusata da fushi....
_Shekaru sha biyu (12yrs) BAYA KAFIN FARUWAR HAKA..._
Garin majiya
karaye LGA,
North-West of Kano State.
wata lafiyayyar kauye ne acikin nisan dajin karaye me taken garin majiya datake kusa da wani tsauni mai suna Dutsen Gulbi wanda Aka riga aka san su da daukaka al’adu na gargajiya masu tsauri da girmama haihuwar d'a na miji dan kuwa yawancin su fatake ne, jajirtccun fulani sadaukai, malaman tsubbu da bokaye, tare da buzaye, suna zamane cikin bukka mai shinge da laka.
mutanen kauyen basuda wani yawa dan basufi dubu ba amma sosai suka tsare kansu da tsabar ilimin tsafi na usuli tareda kaurin suna wajen iya farauta a daji, makiyaya da fataken cikinsu suna yawan fitowa birnuka domin cinikayya da kasuwanci na abinci da dabobi har can can zuwa bordern qasar niger da chad da ake hada-hadan yau da kullum wanda har yajawo suka kukkula zuria da alakar aure tareda kyawawan matayen buzayen dana fulanin usuli.
Anan kauyen garin majiya, duk shekara ana gudanar da wata muhimmiyar biki mai girma da ake kira da Gangamin Gwaninta. a Wannan rana ce da ake fito da zaratan maza masu ƙarfi, yara maza masu kwarewa, su fito fili nuna bajinta a wasan dambe,mashi da wuka, wasannin doki, da kuma rawa ta gargajiya.
A wannan shekarar kamar koyaushe yauma al’ummar kauyen gabaki daya sun tarune makil a filin ƙaramar haraban mei garinsu, Kowa ya shirya da rawani da rigunansu na gargajiya. daga nesa zaka iya hango samari buzaye da fulanin nan kyawawan yan maza dogaye masu dogon hanci suna shigowa daya bayan daya suna ɗaga hannuwa da takobi, wasu kuma suna bisa dawakai suna baza taƙama.
Daga can gefe wani ginannen mutum ne mei suna malam _Juma Maharouzo_ , asalin kayan buzaye yasaka ajikinsa data masa kyau dan shi kyakkwan mutun ne yana tahowa fuskarsa adan ɗaure, matarsa _Falmata tambazaou_ doguwar cikekkyr ƴa mace ce kuma kyakyawan gaske, half breed ne na fulani da buzaye, wani irin yolo yolon baqi sidik in suma takeji dashi wanda har wuce gadon bayanta, akauyen an fi saninta da suna _"Tàawuré"_ tana biye da shi a baya cikin sanyin yanayi, sai babban yarta inayah (innari) yar 12yrs yarinya ce me tsananin karfin zuciya da taurin rai, da karamar yarta me suna Ayaanah yarinya ce me sanyin hali da rauni wacce bazata wuce shekara goma ba da kaf kauyen akeyi ma inkiya da"annayo". tsabar yadda Allah ya zuba mata sassanya kuma kamilallen hali da rare beauty kyaun ayaanah irin me tsananin sanyin nan mesaka nitsuwa da kama zuciya, zakaganta always calm and peaceful like her healthy light caramel skin colour, sam bata fiye magana ba, tana rike ne da ƙaramar kwarya daf da mahaifyarta, inayah kuma tana tafe agefensu kanta na kallon kasa sabida tana da wani irin zuciyae zafi da kuma tsefaffen ido, har suka karaso cikin filin babu wanda ya tankasu face saida suka iso tsakiyar jama'a inda daga dosuwarsu wajen kai tsaye wani garjejen fatauki ya hau nuna su yana ihu yana tuntsinrewa da wata muguwar dariya cikin shakiyanci yana cewa
"yekuwa jama'ar gari, yeeehoooh haihuwar da namiji sai gwarzon namiji,.. ahalin maharaozou an gaisheku, jama'a nace sarki ya gaida cikakkun maza masu haifa ma kauyenmu yara maza gwarzaye. Toh, ga fa juma Maharouzo da ahalinsa mata duk sun shigo fili. Amma kamar kullum, babu ɗa namiji da zai tsaya musu a gasa.“sai dai da alaman kamar yau ya fitar mana da ƴaƴansa mata ne domin su shiga gasar rawar yn mata. fagen shaɗi, fatauci, da Dambe kuwa babu wanda zai wakilce shi.” hahahahaha
wani irin dariya aka fashe da shi awajen ana nunasu da yatsun hannu musmn inayah da ake ganin takai shekaru 12 amma haryau babu wanda ya nuna intrest akan aurenta sabida tsabar an tsangwamesu a kauyen. yadda zaka san jahilci yay ma wann garin illa babu mutum daya da baya musu dariya wasu har suna rike cikin su.
malam juma maharazou y'ay'a mata kawai ya haifa, babbar yarsa itace inayah ana cemata innaari yar shekara 12, da karamar yarsa Anayah da ake kira annayo yar shekara 10 cass, wanda dakyar ma Allah ya bashi su daga nan kuma sai Allahn bai kara bashi wani haihuwa ba.
Wannan dariyar da ake kwashe musu da shi atake ya ƙona zuciyar Juma. Ya tsaya cak, ya kalli wajen da aka fi tashin dariya. atake take fuskarsa ta hau kumbura idonsa ya dada ƙanƙancewa akansu sai dai babu abin da yasan zai iya yi har ransa, domin gaskiyar maganace ta fito fili duk yaransa mata ne bazai taba iya kaucewa wann babban abun kunyar ba kasancewar gidansa ba namiji face shi.
ana cikin musu dariyar wani samari acikin fulani irin bullies masu tashen balaga marasa kunya daga cikin masu rike sandan shaɗi ya daga sandansa sama yayo kansu da gudu yana tada musu kura anata dariya can yay wuf kamar zai gwada sandan akan ayaanah daya san cewa ta fi kankanta da rauni danyana so ne yaga yakara tsoratata ta razana ta firgita tay kuka dan kawai ayi dariya sosai, yana daga sandan kuwa caraf inayah tayi wuff ta cabe tareda kwacewa da karfi daga hannunsa ta rike anata hannun a zafafe yanayinta cike da gigin taurin kai da tsananin zafin zuciya da jarumta take kallon har cikin idonsa tana huci.
cak ido ya koma kanta ayayinda kunya ya rike ma saurayin kirji
wani huci yay yana kokrin daka mata tsawa kenan cikin datsar numfashinsa tazare mai manyan idanunta dake bushe tareda nuna shi da sandar a tsawace tace "kaiiii Garbati kar ka sake ka karayin mafarkin taɓamin ƙanwata annayo, idan bahaka ba saina dakeka anan wajen andau mushenka...
jarumtaccen muryan zaki me amon bacin rai datay maganan dashi yasaka kananan magana da dariyar da ake filin ya dauke cakkkk ganinta yar karamar yarinya me zafin zuciya irinna jajirtacun maza..
tsayawa duk akai aka dinga kallonta yadda idonta yajuya yay jaa kmr ruwa ga turirin zafin rai da ke fita a numfashinta koinanta na kyarma irinna jaruman maza ..
A memakon hakan yay ma mahaifinsu dadi sai kuma yaji mugun haushi ya rike sa, dan aganinsa kara tozarta shi inayah tay data nuna rashin kunyarta da rashin tarbiyanta a fili wajen kkrin kare yar uwarta anayah.
a tunaninsa da kuma tunanin yan kauyen kowacce mace me rauni ce da kunya, mace bata daga ido ko murya wa namiji ko da kasheta za'ayi akan gaskiyarta.
da mugun bacin ran ganin abunda yarsa inayah tay ya juyo cikin huci ya kalle Matarsa taawure data sunkuyar da kai cikin jin mugun tsoro da nauyi tana jin kamar ƙasa ta buɗe ta shige.
kallo daya yay ma inayah wanda tuni inayahn ta saki sandan sabida suna mugun dajara idon mahaifin nasu Ayanah kuwa na nan tsaye a gefenta, batako motsi tsabar uban tsoron da ya lullumeta, bacin ran da mahaifinsu ya fara nunawa a filin ya saka idanunsu yacike da ruwan hawaye suna ji aransu kamar duk duniyanan ne ma ake ƙyamatar halittar su na ƴaƴa mata bawai ubansu kadai ba.
mahaifinsu Juma ya yi ƙoƙarin ɓoye ciwon abun aransa amma inaa da ihu ya ce musu ku fita kubani waje anan, kunji me ake cewa wajen nan wajen yaya maza ne bana mata ba, ke kuma innari kije gida kijirani yau sai na tsine miki albarka da kika karbi sanda ahannun namiji.
yana huci ya kalli idon matarsa tawuree cikin tsananin gigin jahilci da fushi yace " ki tafi da yan iskan yaran nan naki anan. daga yau kuma kar na sake ganinku a fili, dama kin matsa muzo da yaran ne dan ku taru ku kunyata ni abainar maza, kije can..sanda kikayi jarumtar fito da d'a namiji duniyan nan saiki dawo filin wasa.
dariya aka faray musu, kuka me sanyi ya kufce ma taawure tafashe dashi tareda janye hannayen yaranta duka biyun izuwa waje dan already habaice habaicen da akemusu awajen akan abunda inayah tay ynxu ya mugun kara raunatasu su sosai..
wani ikon Allah kaffff kauyen gidansu ne kawai akwai ƴaya mata har biyu snn babu namiji ko daya..
kafafunsu har na hardewa suka fice a filin sunaji ana musu habaici sosai, a zuciye juma ya kalli masu dariyan akaro na biyu snn yace “Kai jama'a! saidai Ku yi dariya ku yi ba’a akan yaya na mata, aje dai na fi uban kowa ƙarfin aikin noma a kauyen nan. Wani ma gashi da y'aya mazan amma bai isa ya iyayin noma irin nawa ba.”
duk da zafin jarumta dake tafe acikin maganarsa already gorin nan da ake masa akan yaransa ya gama ratsawa cikin zuciyarsa har yau yana tuna tsananin baqin cikin dayaji aransa da aka haife yarsa na biyu Ayanah a matsayin y'a mace ba d'a namiji ba..
wasa ta cigaba a fili amma gori da cin fuskar da ake ma juma maharaozu baiyi sauki ba musmn ma da sarkin fulani ya fito filin wasan da duka y'ay'ansa maza kusan su guda goma sha bakwai shine mutumin da yafi kowa haifan yaya maza a garin majiya gabaki daya kuma shine yafi kowa kuntata ma juma akan batun yayansa mata guda biyu. abu kadan sai kaga ya gaya masa baqar magana me hade da gori abainar jama'a haka za'ayita ma juma dariya duk dama yana daya daga cikin jiga jigan manomar garin dayadace ace ana ji dashi saidai rashin samun da namji koda dayane a ahalinsa yasaka gabaki daya ya zama baida wani daraja a idanun hakiman fulani dana buzaye dan har kwatance da shi akeyi a kauyen.
Dagata bangaren su taawure kuwa tunda tajanye hannun yaran ta suka bar filin wasa tafiya kawai sukeyi suna masu tsaga cikin jejin da zaibi dasu madaidacin rugarsu dake can can gefen babban rafin kauyen inda babn filin noman su da tsaunukan kiwon dabbobinsu yake kusa azagaye dasu, they are kind of isolated daga main mutanen kauyen ko abu zasu saya sai sun yi tafiya mai dan nisa suke isowa kasuwa kusan ince rugarsu ne karshe a kauyen kusa da hanyar barin gari gabaki daya, gabansu kuma babban ruwa da jejine me duhun gske dake zagaye su.
tafiya suke da sauri sauri tareda wani irin rauni da kuma fargaba acikin zuciyoyinsu, koina yay shiru dan kusan kowa a kauyen anacan fili wajen gagarimin wasa, cikin sassarfa da sauri taawure tariko hannun karamar yarta ayanah gam tana janta ahnkli nan inda bakajin karar komi a hanyar face sanyin iskan yammaci da kukan tsutsaye tareda dirar sautin ajiyan zuciyar taawure datake saukeshi akai akai jin raunattecen ajiyar zuciyar da ayanah takeja wanda yagama narkewa cikin tsoro da matsanancin damuwa. daga ita har mahaifyarsun a dame suke da tunanin irin hukuncin da juma zai zo gida ya dauka akan su da kuma inaayah.
ita kuwa inayahr ko ajikinta daf dasu take tafiyarta zucyarta karau dan tun basu karasa barin filin wasan bama tabi ta shanye hawayenta idonta yabi ya bushe tsabar wann taurin zuciyar da Allah ya bata wanda yasaka tuni ta iya hadiye duk wata damuwa da kukanta aciki. duk dama kowa cikinsu na jin dar dar da tunanon dawowar baban nasu gida ayau amma ita kam gaba gadi take tafiyatta da zucyarta daya.
sunyi tafiya na akalla mintina ashirin kafin suka kawo kofar madaidaicin rugarsu da gininsa yayi mugun jimawa sabida asali gidan gadone da wani uban gidan juma a harkan noma ya taba mallaka masa halak malak saboda tsbaar jajircewr sa a harkan kiwo da noma. duk da rugar ta jima saidai tsabar tsafta da tattali irinna taawure yasaka muhallin nasu yake da kyaun gani, nan suka tsaya a babban filin kofar gidan suna kan tattara buhuhunan da suka shanya wasu kayan abincinsu kmr tarugu, ganyen zobo kubewa, da gyada da wasu yan hatsi, inayah da kanwarta ayanah suka dukufa suna kan kwashewa taawure kuma tana zubawa acikin buhun tana dinkewa da allura da zaren buhu.
tsabar kawaici da kunya irinna bafulatanar usuli yasaka har iyanzu taawure bata budi baki tace uffan ma yayan nata akan abun da ya afku a fili ba, dake ma sunsaba da irin wann halintan ya saka koda wani abu yafaru inde batay musu magana ba suma sukeyin shiru saidai kawai kaga suna aikinsu da ladabi da kawaici.
gasu da hatsi,dabbobi da kaji amma diss din datti bazaka gani a tsakar gidan nasu ba koina an tandesa tass da tsintsiya yanayin yaran da uwarsu kadai kagani zakasan Allah ya zuba musu kwazo kunya da kuma sanyin tarbiya me tafe a jini.
bayan sun gama kwashe shauran abincin taawure da Ayanah ne agaba wajen kaiwa cikin ma'ajiya, ayayinda inaayah tay maza ta shiga ban daki, kai tsaye tayi tsarki ta taho tazauna akan dutsin dake kusa da madafi tahau alwala
Daga cikin daki kuwa suna shiga taawure ta cire mayafinta snn ta daga ido ta kalli yarta ayaanah dake rakube kan taburma ta rike saman kirjinta bata ko motsi, Tun haihuwar anayah suka fahimce cewa kamar tana famane da wani irin ciwo na raunin zuciya wanda baya tashi sai tana cikin halin tsoro ko tsananin baqin ciki da fargaba.
bayan mahaifyarsu arayuwarta babu abunda take kauna aranta kamar addarta inayah dan sun taso ne da wani irin kakkafar yarda da juna, shakuwa da kuma tausayin juna meyawa a tsakaninsu.
ganin yanayinta na laulayi yasa cikin sauri taawure ta durqusa kasa tajawo wani babban kwarya daga kasan kujera ta bude shi, wani tsaftacen jikon maganine aciki marmaza tasaka ludayi tahau deban ruwan maganin tana zubawa cikin karamin kwarya inda ko rabi baikai ba tamika mata da yaren babansu na buzanci tahau tursasa mata shi abaki kiyi bisimillahi Annayo am, karkiyi raunin zuciya maza kisha wnn zai saka kiji karfii kinji?..
adan ragwabe ayanah tamike zaune ta amshi kwaryan da ladabi tafara sha kenan saiga inayah ta shigo gabobinta duk a jike da ruwan alwala
suna hade ido kallo daya taawure tay mata kafin nan ta mike tsaye da tsoro a muryanta tana cewa
"ke kuma muje in rakaki hanya innari, kijeki ki buya a garin tudu harsai nazo na nemeki, bana son babanki ya dawo gidan nan da fushinki aransa ya zo yayi miki lahani ko ya tsinemiki kibi duniya in shiga uku..
kafin inayah ta amsa taga mahaifyarta har tajuya tahau daga katifarsu da akayishi da ciyawar tim tim hannunta na rawa rawa ta dauko mata jakar buhunta inda suke boye littafan karatunta na boko da islamiya da ta jima tana turata yi acan anguwar tudu inda suke kasuwanci ta saka yaranta karatu a boye batare da sanin mahaifinsu juma maharaozu ba.
jakar karatun ta fara mika mata danta boye shi acikin rigarta snn ta jawo kullin kayanta tahau nade matasu a tsuman zani tana gama kullawa ta dora mata shi akai, tsabar zafin zuciya 'bari 'bari kawai jikin inayah yake dan bataga wani dalilin da za'a boyeta ba,aganinta ai kare yar uwarta kawai tayi a fili, kawaici da darajar da take mugun bawa mahaifyrta yasaka batace komi ba dan babu abunda yake cimata tuwo a kwarya kamar irin mugun tsoron mahaifinsu da taga taawure takeyi agidan, wanda inda anbarta dashi da tuni takara dashi dan ji take ajininta kmr itadin mace me kmr maza.
turjewa tay ayayinda taawure ta wafco hannunta zata jawota waje, suna hade ido da dan taurin kai ta tsaya tanata kallon cikin idanunta batay mata yaren buzancin ba sai tay mata da fulatanci tana cewa 'ummah miyyasa kike tsoron abunda baba zai min dan na kare yar uwata ayaanah a fili ko dama so yake wancan katon banzan ya kasheta da sandanshi dan ya nuna musu baya kaunarmu? ummah inkina jin tsoronsa wata rana za'a kasheki ko akashe annayo a filin nan, kidubeta bata da kwarin gwiwa kuma wnn jikon naku da ake bata kinsan zai sakata bacci me nisa zai kashe mata zuciya bazatay karatu ko ibada ba umma inde ciwon zuciya ke damunta ai akwai malaman asbiti a tudu
rufe mata baki taawuree tay da sauri tun kafin wani yaji abubuwan datake ambata musmn ma batun asibiti da karatu
hankli tashe cikin tsawatar mata tace ya isa haka innarii yanxu ba lokacin magana bane, kituna dake kawai na dogara dan ranar da mahaifinku yasan nasakaku kuna karatu a tudu zai iya kasheni ko ya batar dani, innari kece mini, nasan zaki zama karfina anan gaba, nasan koda na mutu kece kawai zaki iya rike ayanah tsakanin ki da Allah koda bana duniya, in nabari yaxo ya tsine miki yau ni aka cuta duniya da lahira, kawai kije ki cigaba da karatunki a tudu, nayi miki alkwari bayan ya huce daga fushinsa, zanzo saida nono wata sati zan dawo dake gida, snn nayi alkwakri wnnan karon da kaina zanzo da anayah tudu itama ta cigaba da karatunta acan naji ance anyi mata nisa kudin natan ne bangama tarawa ba. tun kan innari ta amsa idanunta ya cika da ruwan hawaye ganin yadda jikin mahaifiyrsu yake bari sosai yanayinta cike da fargaba me ban tausayi da tsanani.
marmaza taawuren ta warware bakin zaninta ta ciro kudi da basu fi dari biyarba ta damka matasu duka a hannu tace" kirike wnn inkinje tudun kice ma goggo mei tuwo ina gaisheta, har da ma malaminku. ki kula da kanki Allah hokku barka am. inayah ta kasa cewa komi ganin yadda hankli da jikin mahairfyrsun gabaki daya yarikide dukkan hanklinta atashe yake sai leke leken waje take da tsoro daga ganinta kasan tana mugun tsorone kar ace juma ya dawo ya iskesu anan atare dqn bakaramin son yaranta takeyi ba.
hawaye kwalli daya ya sauka idon inaayah musmn da ta daga ido ta kalli mahaifayarsun snn ta kalli ayaanah dake kan kwance a tabarma ta kanannede kanta bata iya ko da motsi sabida jikon da aka bata tasha tuni ya sakata bacci..
tawuree na jan hannunta da kyar dai ta iya dauke idonta akan yar uwarta suka fice waje suna sauri sauri haka ta rakata har gaban babban rafi ta turata bisa hanyar tudu, ita kuma ta damke kayanta snn ta falfala da gudu tabi jejin, saida taga tay nisa snn ta dawo gida
taqumi tay ta zauna kurkusa da ayaanah dake kan bacci wasu maqudan hawaye na zuba mata ahnkli cikin tunanin safetyn yarta inayah, harcan saida aka kira sallan magrib snn ta tashe anayah sukayi marmaza sukayi sallolinsu suka ci abinci wanda dede lokacin ne aka taso daga wajen wasa...
fitila me kwai kawai ta kunna musu tay shiru tanajin ayanah tanata bitan karatun da addarta inayan ta koya mata game da sallah , tun suna zaune acikin dar dar din ganin shigowar juma gidan har dai suka hakura.
washe gari da asuban fari sukejin labarin cewa ashe baram baram aka tashi a filin wasa, sarkin buzaye dakansa yay jawabi akan tarbiya, yana mai kafa misali da rashin kunya da kuma tarbiya irinna inayah dahar ta karbi sanda a hannun namiji a filin wasa, dan haka tun anan juma maharozau yayi zuciya, sabida ance masa ya haifa musu y'ay'a mata marasa amfani ga cigaban kauyen snn kuma bai iya tarbiyatan dasu ba, acewar sarkin fulani in har innari ta sake musu tsaurin idon karban sanda a hannun namiji a fili zai saka matasa maza su giciye ta.
wayannn furucin yasaka juma tsananin fushi, bai dawo gidan sa ba ya wuce jeji dan tsabar zafin zuciya ma akan wata bishiyan mangwaro ya kwana
jin hakan bakaramin kara tsorota taawure yayi ba, dan tafi kowa sanin mugun zuciya da tsananin rashn son kaskanci irinna mijinta juma. dan da a raina mazantakarsa ko aci mutuncinsa a fili gara a maresa a fuska.
Juma Maharouzo ba asalin ɗan Dajin rini ba ne. Kakanninsa sun fito ne daga ƙauyen Maharouzo kusa da iyakar Tamesna wato yankin da ke tsakanin Nijar da Arewa maso Yammacin Najeriya.
Sunan “Maharouzo” ma ya samo asali daga tsohon harshen Tamasheq wanda ke nufin “ɗan ƙura, mai ƙarfi a ƙaura”. ance Kakan kakansa bbn malamin addini ne wanda yayi suna wajen tafsiri da bayar da fatawowi musmn ga ƙauyukan kan iyaka amma babansa kuma jahili ne dake bautawa al'adarsu. yaki neman ilimi ne saboda kakan juman adacan ya ki shiga cikin yaƙin sarakunan Fulani a lokacin jihadin Shehu, sai aka koreshi da iyalansa daga garinsu. Sun yi hijira, suka shigo cikin karkarar Katsina duk ba'a kyale su ba, daga nan suka ratsa zuwa Rini inda aka basu ƙaramin fili don su zauna, Saboda haka shida ya taso sai baibi tafarkin ilimi ba har ya haifi babban dansa juma a maharazou cikin jahilci da tsananin son al'ada..
Juma ya taso ne da ɗan tsakanin ƙabilu biyu, akwai al’adun Hausa fulani a jikinsa, amma shi asalin Buzu ne tsatson su na Tuareg har a halayyarsa. shi mutum ne mai ɗaukar hankali koda bai yi magana ba, Fuskarsa tana da faɗi, idonsa yan dede masu zurfin haske, daga saman Goshinsa akwai wani dogon tabo mai layi guda biyu wanda labarin tabon nan shi kansa yana da ban aljabi, dan ana cewa a lokacin ƙuruciyarsa ya tsallake dajin mutuwa lokacin farautar wasu macizai, wasu kuma sunce yabuge kansa ne da itace wasu na cewa alamar ruwan gadon hatsice daga kakanninsa shiyasa noma ta amshesa
Dogon mutum ne mai lafiyayyen kafadu masu faɗi, gashin kansa baƙi, gashin gemunsa kuma ya fara tsufewa. a sutura Ya fi son dogon riga mai launin ƙasa ko shuɗi, da rawani mai kauri wanda yake nadawa fiye da yadda maza kauyen suke yi, shi baida hakuri sam, kuma zuciyarsa akusa take, babu abunda yakeso aransa kamar al'adarsa, babu kuma abunda yafi ci masa tuwo a kwarya kamar haifan yaya mata dayayi, dacan sai kaga kamar yana mutuwar son matarsa taawure amma tunda ta haifa masa mata banda wutar tsana da tsangwama babu abunda ke shiga tsakaninsu. already ya hana yaransa komi na nishadi, da amfani, daga aikin gida, talle sai kiwo, baya basu kulawa, ko ciwo suke an haramta musu shan maganin da addini ta amince dashi, saidai uwarsu ta jika musu magani na asalin malamn gargajiya susha, snn ba a karatu kowani iri a gidansa, ya hana zuwa asibiti sabida shi asalin al'adarsu ba jahilcin garin yake bi badon komi ba sai dan kawai yaga shima ya zama me fada aji snn ya samu shiga a fadan sarakunansu both fulani da buzaye ana darajashi kamr sauran zaratan maza.
Kamar ko wani zagowar shekara yauma al'adarsu ta bikin gangamin gwaninmta baima Juma maharazou dadi ba. tun safe taawure taje jejin tana rokonsa, hakama wasu Maza abokansa Wanda sukadan damu dashi a garin sukazo babu irin rokonsa da basuyi akan yay hakuri ya sauka akan bishiyan nan ya koma gida ba amma inaaa, yaki magana da kowa yay zuciya harda abinci.
wasa wasa saida ya kara kwana washe gari taawure ta fita tanabi gidan dattijai tana magiya dakyar akazo aka tallafosa ya hakura ya sauko ya koma gida, yunwa duk ta watayashi sanda ya sha kuna yay wanka ya dawo hayyacinshi, tsabar zuciya haka bai magana da kowa agidan ba, har saida da yazo yaga babu wulgawar innarin agidan snn ya dan sake ransa, dama kuma mugun tsoron sa ayaanah takeji bata sakewa suhade ido ko su hade hanya in zata gaishesa da sanyin asuba take fitowa ta bi taawure itama haka za ta durkusa ta sunkuyar da kai can kasa a kofar turakarsa tay shiruuu koda taawure ta gaishesa daga nan waje ya amsata cikii ciki, ita shiru takeyi inbe amsata ba kuma komin jimawar da zatay a tsugune haka zata kasance har sai ya fito daga dakin ya ganta snn take iya tashi tabar wajen.
#SURAYYAHMS
AYI SHARING idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
#SURAYYAHMS
[22/10, 19:02] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️3️⃣ Duk zafin zuciya da taurin kan inayah tsanar dayake mata baikai wanda yake ma Ayanah ba, dan akanta ne yafara samun rugujewar burinsa na samun ɗa namiji sabida shi dakyer ma yake iya samun haihuwa. a kauyen mutane da yawa sun haifi mata a fari saidai abinda yake biyowa baya maza ne, shima sosai yaci burin ace ayanaah tafito masa a matsayin ɗa namiji sai kuma ta fito mace kyakkwan gaske kuma me dauke da ciwo na raunin zuciya wanda saida aka sha wahala ma kafin ta rayu.
ranar koda aka cemai mace aka kara haifar masa tsabar bakin cikin dayaji aransa ko daukarta as a baby a hannunsa bai taɓayi ba,he despises ayanah ryt frm the very minute she was born dan haihuwarta ya jawo masa ababen gori bana kadan ba shiyasa har yau kuma baijinta aransa dan banda hantara, tsawa da tsananin dokoki babu abunda ke giftawa tsakaninsu.
yau shekaranta goma amma bai taba amsa gaisuwarta ba, kowani safe saidai tabiyo bayan mahaifiyatta cikin nuna biyayya haka zatazo ta durkusa masa abakin kofar turakarsa ta tsunkyar dakai kasa tay shiru bata kuma tashi awajen har saiya fito yaganta duk dama tasan bazai taba ce mata uffan ba.
bayan kamar sati da faruwan komi taawure tasha baqar walaknci da baqar magana a hannun juma kafin ya sassauto ya hakura har ya fara shirin tafiya zuwa boaden kasar niger saida sabbin buhunansa na hatsi, yana da akalla buhuhunan kayan noma kala kala yakai buhu dari da ashirin banda yan kananan abubuwa daya tara.
kullum matarsa taawure dake tay karatun allo sosai ita take tayasa lissafin irin uban kudin da zai samu duk dama baiya bata ko asi, dan gani yake tunda ita ta taba yin karatun addini me zurfi hala zata cuceshi
abinci kam kowani iri ne yana sakar musu suci su koshi amma bayan haka sisinsa basa ci. sanadiyar yar lissafin kudin datake tayashi sukeyinsa a kwana biyu yasa hartaci nasarar kawo masa batun yafewa innari, ranar haka ya zage ya gaggaya mata bakaken maganganu masu tsanann zafi da ciwo wanda ko wacce uwa bazataso taji an furta su akan yayanta ba, ya mata gorin tarbiya, yace mata yana ji ajinin jikinsa cewa watsatsstsu karuwai kawai ta haifa masa ba ƴaƴa ba, wanda yake da yaqini cewa sune zasu kawo zubewar duk wani kima da darajarsa a duniya.
sam maganan nan bai ma taawure dadi aranta ba dan bataso yay musu wnn mummunan bakin ba
hakanan tay hakuri sabida ya yafe kuma ta shawo kansa har ya amince akan inayahn zata iya dawowa gida, maganarsan ya mata ciwo aranta amma tanada yaqinin cewa Allah bazai tozarta ta ba tunda har tanata kkrin neman ma yaranta ilimin addini dana boko aɓoye in sha Allah bazasu taba zamowa karuwai watsatssu ba.
duk dama ta aminta da mutanenta na can tudu amma koda juma yay ma yaranta wnn mugun bakin sai kawai tafara jin kamar tafiso ace ita dakanta ne ta tarbiyartan da duka yaranta agabanta kafinsu samu mijin aure basai sunje university ba duk ma babban burinta kenan.
satin nan gabaki daya haka ta tasa ayanah agaba suka hau shirya madara, da kindirmon nono da fura da kwan zabbi masu kyau da yawa, sunata Allah Allah lkci yay juma ya wuce kasuwancinsa a bodar niger dan suma suje nasu kasuwancin a can tudu.
kwanaki basa karya yau kwana sha biyu shaf da gama hidima gangamin jarumai juma da abokanansa duk sun gama shirin tafiyarsu can boadern niger kasuwancinsu da suka sabayi ko wata shekara.
ranar da zasu wuce tun da asubahin fari na farko lkcin waje baigama washewa ba taawuree ta fito daga turakarsa da lullume tare da daurin kirji tanadan murmushi me sanyi tuna irin darensu na jiya.
mijinta juma yana iya walakanta ta akan komi amma daga zarar anzo maganar saduwar aure baya iya boye dumbin soyayyr dayake mata aransa dan bakaramin dadin ta yakeji akan gadon sa ba, albarkan niima da dandano dake kumshe a jikinta yana kawo masa wata iriyar cikakken gamsuwa da nitsuwa a duka sassan jikinsa tareda dadi marar misaltuwa, ruwa me tsafta ta hau zuba masa a babban butan karfe wanda take tsammnin zaiyi wankar tsarki dashi tanay tana murmushi badon komi ba saidan amince mata dayayi akan basai ta zauna anan ba, zai saka musu mai gadi inyaso itama tazauna acan anguwar tudun tay kasuwancinta na saida kwai da nono har saiya gama nashi cinikayyar ya dawo. hakan kusan babban alfarma ya mata.
lissafin wata ukun da zaiyi a boda tay, tasan kafin nan ya dawo ta samu kudi me yawa na kulawa karatun yaranta hala har ayanah tay nisa akaratunta itama.
babu yabo babu fallasa juma ya gama shirinsa komi ya fito, ta rakosa har waje yay kyau sosai yasha baƙar rawani, wanda yau da ace bai kara jadadda mata mugun harsashen dayakeyi gameda da tarbiyan yaransu ba da sai tace cikin dadin rai suka rabu amma inaa saida ya kara jadadda mata cewa yanaji ajikinsa cewa yaransa kaf karuwai ne...
haka ta dinke zafin maganar aranta har sukayi sallama dashi snn ta dawo gidan, bayan kamar kwana daya da tafiyarsa mai musu gadin rugarsu ya taho, ita da ayanah kuma suka shirya suka tattara kayan cinikayyarsu da kayan sawansu suka kama hanyar anguwan tudu ayayinda zuciyar taawure ke cike da tsananin damuwar irin mugun baki da fatar tabarbarewa da juma yake ma yarantan aranta. ayanah kuwa murna takeji anata ran tana Allah Allah taga har su isa anguwar tudu dan ta saka yar uwarta inayah a kwayar idanunta.
Basu da isa cikin anguwar tudu ba sai can can gabanin sallahn magriba sabida biye biyen wasu kananan anguwanni dake bisa ahanya da táawure tay domin saida nono da fura dan ta samu ta cike shauran yan kudaden makaranta na ayanah da ake binsu bashi, suna samun kudaden su suka doso masaukinsu, sun iso kofar gidan goggonta Hajy mairo metuwo lkcin duk sun galabaita sakamakon tafya me nisa da suka sha musmn ma ayanah dake fidda nunfashi sama sama sabida wann ciwon raunin zucya datake fama dashi..
Anguwan tudu kamar bariki ne, is more busy and civil Kamardai wajen kazo nazo ne amma dake yana nesa da garin kano duk kabilu irinsu hausawa, buzaye, katsinawa, kanurai, iyamurai, da fulani asalin irin kauyawan ne ke cin kasuwancinsu anan kowadai yana harkan gabansa .
adaf da gidan sarkin kasuwar tudu gidan goggon taawure yake,
dake shahariiyar Me sana'ar saida Abinci ne agarin, hatta bako inka tare shi a hanya kacemai gidan hajy maituwo zakaje zai iya nuna maka shi kai tsaye dan ta balain shahara wajen iya sarrafa abinci da abun sha kala kala da kuma saidawa, lafyayyar hajiya ce shekarunta ya dan jaa amma tay karatu wayayya ce, tun zuwa makka na naira dari hudu tajeta ta sauke farallinta yakai sau biu zuwa uku, tana da ma'aikata dake aika a rumfar abincinta dayawansu yan mata ne datake daukar nauyin karatun su, sai maza dake mata gadi da sauran abubuwa kmar aika da aikin karfi, itake rufa musu asirinsu kaf ta zame musu tamkar uwa da uba.
Tun a kofar gidanta suka sauke kayansu akansu, taawure na tafiyarta a hnkli cikin tsantsar nitsuwar dake tattare da yanayinta na mace mai kamala wanda babu shakku ko dar dar atattare da ita.
Tun a zauren farko take buga sallama cikin nutsutsaiyar sauti yarta ayanah na biye da ita har suka wuce can ciki ta Inda masaukinsu yake bata fasa sallamar ba, ayanaah kuwa tuni ta bude randa ta hau gwangwadar ruwan sanyi wai koda nunfashinta zai dawo dede, Adaf lokacin inayah ta idarda bitan karatunta kenan tana daga xaune akan wani darduma ta fara jiyo motsi tareda sallamar taawure, da wani irin sauri ta fito tun basu gama hade ido da ummanta ba ayanah ta jefar da kofin ruwan ta daka tsalle da murna ayanayinta ta taho da gudu ta rungume addanta inayah sosai, ahnkli inaya tace "annayo? baki washe ayanah tace naam adda na muma gamu ai munxo tudun. inaya tafara dariya tace" aito shannunku., tun basu gaisa ba ayanah tahau kkrin cikata da surutai musmm ma labarin samun karashin sauran kudin makarantarta da sukayi kan hanya wanda atake yasaka zuciyar inaya yay dadi da sanyi dan tasan tunda har anayah tana cikin tsananin farinciki to hala komi ya daidata ne harma awajen mahaifinsu juma
Tanakan murmushi ta janyota jikinta sosai tana share mata zufa tana cewa"toh ya isa haka anayo, Zo muje can wajen ki wanke sawunki kikalle yadda kikay futu futu da kura kamar delu me wasan kasa..anayah da bata wani damu ba sai washe baki takey yanayinta me cike da xumudin ganin addanta ga kuma batun komawrta karatu dan bakaramin son karatun boko takeyi ba.
suna kkrin barin wajen taawure tabisu da sanyi kallo tana dan murmushi har ta kusa cikin falon goggontan cikin nitsuwa
Hjy mai tuwo dake kwance bisa kujera da jikin tsufa tadan miko kanta cikin sauri tana amsa sallaman taawure adan rikice amma dake tanada shegen mita yasa bata gane muryanta bugu daya ba, Wani Caraf ta yatsina fuska tace 'ohni yau naga takaina waye kuma haka da yammaci tun bamu ci na dare ba? Kode sabbin masu saida abincin nan ne suka dawo zasu sakani agaba da mita akan kudi...ohh ni Yau mairo naga takaina Waye ne kam... shigo daga ciki mana..ke innari zoki dubamin
Gyara zamanta tayi akan kujerar tana dada gyara mayafinta akafadunta, sashenta Babban self contain ne amma na ginin laka me karfi da aka bi jikinsa da siminti yay fess fess duk da ba a fentashi ba, ciki da falo ne me dakuna biyu, ta kakkale koina da brown leda carpet da kujeru kananan seti da tv dan madaidaici da wooden center table iri daya da brown cupboard dinta datay wani irin jeren kwanukwanta akai.
Jim kadan saiga bullowar taawure cikin falon, gabanta gadi fuskarta dauke da Wani dattijuwar Murmushi wanda tun daga yanayin shigar ta Kamala yasa hjya mairo kara bada hankulanta akanta da sakin fuska tahau mata maraba har idonta na tara ruwa.
kullum taga taawure sai taji wani irin tausayinta aranta sabida asalinta yar gata ce da rayuwar maraici ya juyata ta dawo abar tausayi.
"ooo taawure? ai sekice min kece kika lankayo sawun kafafunki kikazo, toh sannu da da zuwa lale maraba da xuwa.
taawaure nata sakin murmushi har ta nemi Waje ta zauna Adan dofane feeling so uncomfortable da irin kallon kurilla da hajy mai tuwo ta ke jefa mata. zuciyarta ne ya shiga mata Wani irin zafi ganin yadda taawure take kkrin dawowa kamar wata sokuwa kamar batay ilimi da take gidan ubanta ba..
Gaisuwa suka somayi
Irin gaisuwan Nan na darajawa da kuma kimantawa gwanin burgewa, hajya mairo tana tambayarta lpyarta tanayi tana hada mata da addua masu karama Inda basai angaya kasan tamkar uwa taawure take kallon hajy mairo
bawani alakar jini me yawa bane atsakanin su,saidai kuma kawun taawure wato alhj mamman me gareji daya rasu da jimawa wanda anan anguwar tudu yake zama shine mijin hajy mairo na biyu, mijinta na farko a kano yake, suna da yara maza har hudu shima din rasuwa yay, aurenta na biyun kuma bata haihu dashi ba sabida shekaru yaja kuma dake auren nata dashi bai jima ba ya rasu da ciwon cancer, toh a ahannunta taawure tazauna harsaida tay aure, duk wani abu dake tafe a rayuwar taawuren ta sani duk dama batawani shiri da juma, ko kodan jininsu bai hadu ba anma bashi yahana
take rikeda lamarin taawure da yaranta a tsakani da Allah ba.
hira sukayi na yaushe rabo da kuma abunda ya faru awajen wasan gasa, kmr kullum yauma juma yasha caccaka awajen hajy mai tuwo dan tsani irin zafafa al'adar jahilci dayakei akan iyalansa, can dai data gaji da mitan sai kuma tahau kara ma taawuren karfin gwiwa akan batun karatun yaranta sabida malaman nasu nayawan cewa dukansu suna da baiwa na musmn.
hira me tsayi sukayi akan yadda inayar tafi kwarewa akan karatun addini harma ana kwatance da ita a tudu, ayanaah kuma daga dukkan alamu bokon nan dai yafi dauke mata hankali, har dare yay nisa suna hira salla ne kawai ke tadasu, nan ma taawure ta sanar da ita cewa har tsawon wata uku suna nan tudu kafin nan juma ya dawo. da kyar suka rabu taawure ta koma dakin kusa da zaure da ake ware mata intazo da yaranta, ta samu anayah tay bacci akan cinyar addanta inayah wace ke zaune akan dadduma tana kkrin shafe mata nasi da falaki da ayatul kursiyu ajiki dan ta samu kariya. sabida kunyar haihuwar fari dake tsakaninsu hira kadan sukay da taawure kafin suka kwanta da niyyar washe gari sassafe duk zasu fada cikin harkokin gabansu na kasauwanci da kuma karatu.
washe garin ana kkrin zaa kiran sallan asubahi sassanyar sautin bitan karatun qur'ani da inayah take zubawa acikin yanayin kwarewa ne ya farkan dasu daga bacci. zaune take agaban fitila ta rufe kanta da zani, da wani irin farin ciki da zumudi ayanah ta diro daga gadon baccinta itama taje tay tsarki da alwala awaje snn tazo ta zauna daf daf kusa da addanta tana karanta musu suratul Duha itama nan ta jonata sunayinsa tare.
tsabar sanyi da dadin muryansu d ayadda suke karatun fuskokin su cike da murmushi da dumbin son da suke ma juna atake atake kwayar idanun taawure ya cuko da ruwan hawaye mai tattare da rauni da kuma tsantsan alfahari tareda farin ciki mai sanyaya zcyar kowata uwa.
saida suka kai har suratul mutattafifin snn aka kira sallah, nan suka mike duka sukayi ibadar su, suna gama azhkar na safe sukayi gaisuwa, tuni inayah dake ita tana da zafin nama tayo waje tafara shara tana kimtsa tsakar gidan.
ayanah kuma dake tana da rauni da tsoron sanyi ta tsaya tana gyara cikin dakinsun, bayan ta gama ne ta zauna bisa tabarma tanadan bitan dan gyarrarkin da inaya ta mata akan sallah. taawure kuwa tuni ta kwashe toka a murhu ta fara daura kunu da dumame, kafin kace wani abu gidan yayi fess, ya kuma dauka da qamshin kunu da dumame. da tsananin farinciki ganin sun gama komi hajy mai tuwo ta fito duk aka gaisa cikin raha, aka ci abinci akayi dam kowa yay wanka kafin ma'aikatan hjy me tuwo suka fara zuwa ana shirin wucewa shago, taawure bataje
kasuwa ba, yaranta biyu suna kammala saka uniform dinsu ta saka su agaba sukeje har makarantarsun ta biya sauran basuka da ake binsu na karatun ayanaah both islamiya da bokon duka snn ta musu sallama ta dawo gidan ta samu duk su hjy mero me tuwo har an wuce wajen sana'a, itama tattara nata kwaryan nonon tay ta wuce cikin gari saidai daga tadanyi shiru sai taji zcyarta baya mata dadi, dan har ynxu gani take kamar fa mugun bakin da juma yay ma yayanta akan karuwanci hala zai iya kamasu. dakyar da addua snn abun ya lafa mata. rayuwar su mai tsafta sukeyi a tudu, ayayinda kowa cikinsu yake cigaba da sanaarsa yaynta kuma sun balain jajircewa wajen karatu. inayah dake da 12yrs tana aji biyar na firamare dake a aji biyar din zata tsaya, qur'ani kuma saura mata shafuka shida ta hade haddar izu sittin, fiqhu, sira, hadisai, da tauhidi, duk saida ta kwarance sosai, asali ita bata da wani aibu face zuciya da taurin kai da Allah ya zuba mata. ita kuma ayanaah yanxu ne ma take kkrin kaiwa izu talatin a qur'anidake tafi saka ilimin bokon aranta, babban burinta shine ta dawo me ilimin bokon sosai dan tay kudi takai addanta da mamanta makka, she is soo frail nd innocent, duk dama mutanen tudu suna yawan nuna mata favouritism da fifiko sabida tafi addanta kyaun fuska amma hakan bai taba raba kansu ba, they love each oda deeply and immensely dan ko tafiya suke ahanya haka zakaga suna hira sosai suma alkwaru ma juna kullum kuma hannunsu makale da juna. inayah ke yawan koya ma ayaanar ilimin lissafi (mathematics) da bitan islmiya dake tay nisa. mahaifiyarsu taawure kuwa sosai take kara saka ido akan duk wani motsin su da kuma tarbiyansu, hakanan rayuwarsu ta kasance yau da gobe komi ya lafa suna zamansu anan acikin tsananin kwanciyar hankali da nishadi a anguwar tudu....
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[22/10, 19:03] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️4️⃣
No. 1 Al-Mansur Crescent, G. A. Extension, Nasarawa GRA, Kano.
kano tumbin giwa koda mai kazo an fika, dan haka kar kasha mamakin cin karo da anguwanni na zallan "old money" prestige, wato jikakkun masu kudin ɓoye ba ƴan fafar siyasa ko yan cirani ba, asalin kudi me amsa sunansa ake batu wato kudi marar hayaniya, mutane masu takama da karfaffan shahara, 'muƙami, da kuma power na juya uban kowa ahannunsu..
anguwace shiru babu hayaniya face yar shimfidadden titi me tsananin tsafta inda ko da mota ya wulga sai dai kaji wulgawar tashin tsunsaye daga dogayen bishiyoyi da suka kawata wajen gabaki daya. tsaka tsakiyar anguwar ba can can ciki sosai ba Wani tanfatsetsen gida ne kirar ginin masu saka guntun wando da hular malfa irin 3rd century british mansion style din nan wanda ko dison fenti babu ajiki, transitional multi million dollar mansionce mai dauke da both modern and traditional outlooks daga ciki har waje.
Kangon gidan da tsawon gaske, dan ance kafin ka yi toxali da asalin cikin muhallin sai ka shirya
shirgegen automated bakar drag gate ne ya katange shi mai gaba daya, akan ginin waje aka fafe wani waje me kyau snn aka rubuta _Al-Mansur Residence Est. 1972”_ da ruwan duwatsu. Babu wani mahaluki dake son wulgawa tanan wajen kasancewa shikansa layin an masa suna ne da wann me gida.
gida ne da ya mugun shahara sabida tsari marar tarkace dan kusan ince kominsa a kiyasce yake tundaga kan su muamala, da zumunci, da gogayya da jama'a da yamai dashi abun gujewa domin kare darajar arzikinsa da sunan gidansa, Iya zagawar ka anan Ba kowani lkci zaka iya cin karo da motsawar kofarsa ba..
asalin sunan me gidan shine _Alhaj professor zayyanu al-mansoor._ Shi ba jinin sarauta bane, ba kuma dan siyasa bane ko dan kasuwa, kawai dai Hakimtaccen bafulatani ne daya matukar tara dukiya da power na sawa ayi ko abari sabida baiwa na ilimi da daukaka da Allah ya riga ya basa. jajirtaccen namiji ne dayake da key importance a harkan siyasa duk da baya shiga cikinta, sune gaggan share holders da ake hada akai dasu adora mutum akan matsayi ko mulki, he is very well connected to the gorvemnt aides daga russia, france, har america. yana da wani irin karfi ne a internationl relations da gulf business, he has this elitic access to the high profile officials na duniya both international security, politics and organisations .
shi babban professor whose major was in international relations nd financial tech. haka zalika yanada manya manyan charitable foundations ko ince money loundering firms in disguise da ake zargi sune hanyar dumbin arzikin dayake dashi, ta wayann manyan charity foundations dinsa yana iya loundering mugayen kudade ma mafias, drug lords, oil executives, da gaggan kusosin masu kudi a kasashen waje kai harda shahararrun barayi. sai yay maza ya gina manyan fin. tech firms akasashe ana masa running tech businesses sabida kauda zargi da kuma kauracewa binciken masu kakale.
Duk dama cikakken bafulatani ne musulmi daya fito daga babban gida a arewa, shi sam baiya son fiye hidima wa addininsa sabida tsabar ilimin boko da wayewarsa dake irin gurbatacen wayewan nan ne.
su maza hudunsu mahaifyarsa hajiya mairo mai tuwo ta haifa da mijinta na farko daya rasu anan kano wato alhaji al-mansur makarfi, babban dansu na fari _Dr. Al-mustafa almansur_ shima ya rasu, bayansa sai shi _prof. zayyanu da twin brother insa bappa zaidu_ , sai autarsu _uncle muhammad_ .
prof zayyanun ma shikadansa Allah yay ma ƙazamin arxiki acikinsu, amma bai taba taimakon kirki wa uban kowa acikin yan uwansa maza ba, hasalima ya raina uban kowa, yadda yake murza jiji dakai da iko zaka dauka ko shine babba agidan musmn da mahaifinsu alhaj mansoor makarfi yake fifita shi sosai tun kafin ya rasu
toh bayan rasuwar babban wansu Dr almustafa da kuma rasuwar mahaifinsu almansur makarfi da kusan shekara guda sai snn hajy mairo ta sake yin aure acan can anguwar tudu, ta auri alhaj maman me gareji, akan aurenta na biyun ne prof zayyanu yayi fushi da ita harma ya fita a hanyarta dan dama bawani shiri sukeyi ba
..hajya mai tuwo yar gaskiya ce, sam sam bata son abunda zai raba kawunan yayanta shiyasa bata kaunar irin mugayen halin danta zayyanu duk da dumbin arxikin da yakeji dashi.
kwance tashi zuriar Al-mansur makarfi ya zama babban Ahali antara surakanai ga jikoki, Babban wansu marigayi al- mustafa ya rasu ne yabar matarsa, fatimatul mardiya(Ammi karama). da yaranta biyu, "Ibaadur-rayyan,(Ibaad) da kanwarsa safiya ya girmeta sosai dan tun tana ciki baban nasu ya rasu.
sai bappa zaidu shima ya auri matarsa anty raihanatu, shiya fara aure agidan wanda yasa ake ce ma anty raihanatun Ammi babba matsayinta na farkon surkuwan gidan. suna da yaransu uku Maheer, na biyun kuma ya rasu, sai mace ummu kulthum, Dake prof zayyanu din twin bro dinsa ne, shima yana zaune da da matarsa hajiya Dr. Hamida shettima amma shi bai samu haihuwar ta dadi ba..
sai karamin cikinsu uncle mohammad anacemai uncle moh
ya aure matarsa anty safeera achida yar gidan tsohon minister of agriculture, suna da babban dansu mujaheed duk dama he is the youngest, da kanwarsa shima ana ce mata sultana.
within all this years shide prof zayyanu abu daya ya nema ya samu dakyar wato haihuwa, dakyar da wahala ya samu one and only dotersa wato "zainab Arifah al-mansur" kusan a bazata tazo duniyar nan, bayan har prof ya fara cire rai ga batun samun haihuwa tareda matarsa hajya hamida shettima da yake mutuwar kauna sabida halayarsu iri dayane zak zak yadda baison taimakon addini da mutane hakanan itama take
tunda ya same haihuwar zainab- Arifah saiya dauki son duniyan nan yadora ma kyakkwar yarsan, kai duk wani burinsa na duniyan nan akanta yake karewa dan ji yake kmr ba'a taba haihuwa ba sai akansa, as his only child he gives her everything, yarsa yar hutu ce da ko spoon bata iya dagawa ba, kai tun tana karama aka raineta da vibes na ego da arrogance amma bana jahilci ba kaidai akwaita da fi'ili da shegen manyance, she lead a very stylish life,extremely spoilt nd pampered, zainab arifah sangartciya ne na bugawa a jarida ita kullum masu aikine a zagaye da ita ana kulawa da ita sosai dan ko hanyar kitchen din gidansu bata sani ba bare tasan me akeyi aciki.
komi na duniya tana samunshi awajen babanta, dan shine mafi kusanci da ita, yar hutu yar qwal take awajensa, just one thing he demands frm her is total obedience.
kuma ahaka ya raineta tana masa tsananin biyayya, like abject obedience bata iya saɓa masa ko kaɗan. zai iya kashe kowa ya binne komi akanta amma batun biyayya tsakaninsu kusan dolene.
Duk wani shikashikan sangarta da lalacewa sanadiyar so da gata Zainab arifah tana dauke dashi, saidai ita ta dan bambanta da iyayenta wajen son danginta, tana jiji da kanta but she is full of life, clumsy, nd so intelligent, tana iya sake fuska da kowa saidai akwaita da mugun rainin wayo da iya maganan banza.
damacan marigayi kakansu almansoor makarfi shiyafara raba kan yayan nasa yabi ya wargaza xumunci tsakaninsu musmn wajen nuna fifiko akan prof zayyanu gashi abun na kokarin binsu har kan ƴaƴa, saidai kuma babban dansa marigay al- mustafa sosai yay bakin kokari wajen hade kansu tun kafin ya rasu, arayuwa koda kowa zaiyi zuciya da irin walakncin prof zayyanu shide sam baiya rabuwa dashi, duk cikinsu yafi masa nasiha akan zumunci koda bada kudi ba, ya zamana dai anatare tunda uwansu ɗaya ubansu ɗaya kar kudi ya raba zumunci.
ahaka har Allah ya dauke ransa, kullum wa'azin dayake musu kenan. saidai kuma yana rasuwan, sake auren da hjy mairo tay a tudu yasaka profesor zayyanu ya kara barranta kansa da su shikuma bappa zaidu yana da dan banzan kamewa bai fiye son hayaniya ba, dake ma prof yasan bamai gaya masa yaji ynxu daga shi sai twin dinsa bappa zaidu kuma yanxu sune manyan gidan uncle moh dama asalinsa bai fiye son shirgin matsala ba.
andau tsawon lokaci ana tafiya ahaka kowa na kulawa da manyn hidindimun rayuwarsa dana yaransa, iyaka dai sanadiyar samun yarsa zainab arifah ne har ya zamana ynxu yadan sassauto har ana dan kokarin zumunci dashi sama sama duk dama har yau babu mai cin arzikinsa ta dadi sai ta bashi ko ta hnyr cin mutunci.
anan cikin anguwar nasarawa extension g.r.a prof zayyanu almansur yake zama da hadaɗdiyar matarsa hajiya hamida shettima da yarsu Zainab arifah and whole street is named after his resident,sabida kudi da power yasa kaf familyn al-mansur ma shi ake cewa Kawu babba, sai twin dinsa bappa zaidu shikuma anfi ganin girmansa da dattakonsa sabida shine yafiye daukar nauyi da damuwar kowa ynxu, yana zama ne kusa da GRA kano, gidan murtala. shi ma babban ma'aikacin gwamnati ne dan yakai matsayin Bank Director kuma yana da businesses dinsa a kasuwa, shi duk dama baiyi sa'ar mata ba, yana hidima ma yaran yan uwansa da kuma mahaifyarsa sosai, yanxu haka ma ya gina babban gidan abinci me shegen kyau ma zamani a can kasuwa musmmn dan mahaifyarsu hjy mairo mai tuwo, yana jirane duk sanda ta bar can tudu tazo cikin kano zai barta ta cigaba da gudanar da sana'arta na abinci anan tunda abunda take so kenan, shi mutum ne meson jininsa duk da baqin halin matarsa ammi babba bai hana ya ɓude kofar gidansa ma kowa da kowa ba.
koda babban wansu Dr al-mustafa ya rasu, yaso ace shine kawai yay jarumta ya aure matar yayansun wato anty fatima da ake cewa (ammi karama) sabida kamilar macece mai kyan hali kyakywan gaske kuma marainiya, yaso ace a dakinsa zata karasa rike marayun yayanta wato Ibaad da safiya har suyi aure, saidai inaaa.. tuni babban surkuwan gidan wato anty raihanatu dake ma itace aka fara aurowa tana mugun ji dakanta anacemata ammi babba tadaga hankali ma kowa tabi bokaye da malamai har saida ta hana yuwar komi.
sosai anty raihanatu ta tsane anty fatiman har bata iya boyewa, kamar kishiyarta haka take kallonta duk dama tay nasarar hana bappa zaidu aurenta, sau da dama taso talaka mata sharrin zina dan kawai akoreta a ahalin sabida wann uban kishin datakeji aranta nacewa haryau idon bappa zaidu yana kan ammi karama shiyasa ma aka nace ta zauna agidan akan yaranta har saita samu mijin aure..
sanadiyar yar wann hatsaniyrsun yasaka aka raba musu gida, ammi karama (anty fatima) da yarta safiya suna zama ne a can family house inda uncle moh da matarsa anty safeera da yaransa biyu suke nan zaune acikin anguwar rijiyar zaki. sashenta daban nasu ma daban sai babban self-con asama shima anbari ne ma hajy maituwo sabida hutun weknds da zumunci da duka jikokinta.
shikuma ibaad yafi zama ne a karkashin bappa zaidu, tare da cousins dinsa maheer da kulthum, toh dake hajy me tuwon ma acan gidansa aketa tsammani zata zauna duba da yafi kusa da kasuwa, yasa gidansa yake da girma sosai dan yariga ya mata babban flat aciki ga kuma sabon motarta na zuwa shago daya gina mata a kasuwan anata jira dai ta dawo.
kusan al'adar gidan ne duk weknds kawai ake dan tarkartowa duka azo cikin family house dinsu na rijiyar zaki domin hutu da kuma karfafa ziyara da zumunci, uncle muhammad ne dama aka bari anan wanda shi ne autanta kuma civil engineer ne, kowani wknds shi yake amsar kowa da kowa cikin aminci da fara'a da tausayi he is deir young nd happy uncle moh, still thriving in his career sabida political connection da iyayen matarsa suke dashi yasaka yana samun kudi sosai shima ba lefi dan shi baida matsala ko kadan.
idan anzo family house na rijiyar zaki ne ibaad yake samun cikakken ganawa da mahaifyarsa ammi karama, ita kuma ammi babban ko da sunzo family house din tafison harka da matar uncle moh wato anty safeera duk dama ta girmeta sosai amma itadin tana da sisterly connection da hajy hamida shettima sabida anty safeerar yar masu kudi ne kowa yasan babanta ya taɓayin minister, infact da ita kawai hajy hamidar take magana a dangin miji, anty raihanatu kuma dama akwai dan uban maganadisun gulma da kwadayin abun duniya kullum dai tana mugun son taga tana raɓuwa dasu babban burinta baifi dataga anware ammi karama ba.
ya kasance awajene anty safeera zainab arifah take sauka inta sace jiki da driver tazo ziyarar itama, tun jikokin gidan alhaj almansur makarfi suna yan kanana ake gudanar da xumuncin ahaka adaddafe sama sama, full of hidden malices, and classism na ciki duk na ciki.
maheer da Ibaad sun shaku da junansu sosai, duk dama uwayensu mata basa jituwa amma sosai ake zumunci, maheer din ya bada ibaad like 2yrs gap dake ammi babban aka fara aurowa, snn ya kuma bawa mujaheed 4yrs dake shi mujaheed sa'ar zainab arifah ne,
wacce ko tazo gidan kwainanenta na sangarta kawai takeyi bata fiye son harka da su ba, kulthum da sultana kuma are all almost same age da safiya duk dama sun bata 2yrs dan a gidan safiya itace karama as of now batafi 10yrs ba.
duk da hadewar kan yaran, ammi babba haryau tulin kishi na dawainiya da ita haka kawai ta tsani ibaad har cikin kokon ranta, zama dashi kawai take agidanta na dole sabida batason ta saɓawa mijinta bappa zaidu, amma bata kaunarsa ko kadan, dan wani bin ko amsa gaisuwarsa baso takey ba gani take kawai kamar duk shirin aure mata miji ammi karamar take kanyi shiyasa ake kan cusa ibaad a zuciyar bappa zaidu haryake daukar nauyin komi na karatunsa tun daga primary gashi nan har scndry.
haka rayuwa yake tafiya a familyn alhj almansur na tsawon lkaci, prof zayyanu adan dole kawai ya hakura yabar yarsa zainaba arifah take shigowa dangi, kamar yadda ammi babba take zaman dole da ibaad anata gidan na GRA.
gabaki daya yaran gidan sun kasance mabanbanta hali, but one thing they all have in common is deir natural striking pure fulani beauty da albarkan ilmi me amsa sunansa ilmi.
babban cikinsu yaa maheer is faintly chokolate skinned, calm, and reserved kamardai babansa bappa zaidu, inkaga yana surutu to musun ball suke da ibaad, yana da kama kai,da sanin yakamata hakan yasa sukafi jituwa da ibaad din sosai dan baifiye son mutum me kananan magana ba, shikuma ibaad din mutum ne murdadde, a walking puzzle in human form,yana da piercing hazel eyes da dark pink lips, farinsa kuma is more like a ethiopean beauty, soo calm, yellowish skin tone ba irin dau innan ba, babu karya yafi uban kowa kyaun jiki da tsarin fuska tareda farinjinin yan mata sabida mum dinsa farar shuwa arab ce yake da suma baqi qirin, saidai kmr yadda hajy mairo take yawan faɗa ne, ba asan gaban ibaad ba bare bayansa, yana da mugun son tsafta, in yay dressing damnnn kamar italian model, saidai birkitaccen mood swings da wnn emotionless face din nasa yasa ake ganin kamar ma shine babba agidan sabida baiya wasa ko kadan da kannensa msmn ma mata, komin rikici da surutun da akey agidan yana shigowa zakaga an watse waje yay shiru, he is deeply introverted with a touch of hot temper, highly emotional intelligent, sosai ya iya karantar halin da mutane ke ciki shiyasa ba masa karya, akan ra'ayin kansa ya fiye zama. baida tsoro sam, amma kwata kwata baison hayaniya, duk duniya babu abinda yake mutuwarso aransa kamar murmushin mamansa, itace kawai intacemai yayi abu ko da baiyason abun to zakaga yayi atake,
mujaheed kuma shi fari ne sosai kamr yellown inyamuri, MJ sarkin tausayi ne yana da saurin kuka ga rauni, baida raayin kansa his dad alwys tell him wat to do, he is hopeless romantic at heart, snn yanason soyayya mai zurfi da ma'ana. sai dai daga zarar ya gane mace batayinsa toyakan hakura hargara yabar abun dayakejin ya kashe shi acikinsa.
duk wani hali da MJ yake dashi ajikinsa kusan shi zainab arifah shitake ji dashi, a kyau babu ta inda takasa, itama fara sol ce sol kamar mjn din tanada kuma manyan idanu da pink lips me kyau da yar doguwa fuskarta, kawai dai tana da dan girman jiki ne tun tana yar karama, da tun lokacin datake at arnd age 10 shatin fitowar nono already yafara bayyana mata sabida irin kulawar datake samu na wuce kima, tana da rauni, she is so soo vulnerable nd hopeless romantic at age 7 tafara wani irin silent crushing akan yanayin dressing in ibaad, abun yafara mata kamar wasa, saidai tsoronsa da ake mugunyi yasa bata iya nunawa ba then the more she sees him the more obsess she bcm with him, hardai takai 12 yrs shikadai ne namiji aranta duk dama ko kusa dashi basa iya zuwa tsabar tsoronsa da sukeji.
inda kawai suka dan bambanta da mj shine inhar tana son abu koda abun bayasonta bata iya haqura dashi saidai a mutu. yar a mutu a love ce, bata san meye babu ba, bata san meye kalmar hakuri ba, she believe duk abun da zuciyarta yakeso kawai xata sameshi. sultana da kulthum kowacce tana kama ne zak zak da mahaifyarta, safiya ce kawai take kama da mahaifinta sosai, nd each of them are so beautiful in their own ways. saida zainab takai har 13 kafin ta fara nuna alamomi a fili cewa ibaad yana ranta sosai. kullum akazo wekdns inbata gansa ba bata sake fuska da kowa, ya zama kamar ganinsa shine kawai abunda yake kawota gidan.
wa Ammi babba hakan ya farayiwa zafi dan ta tsanesa sosai, toh amma sunsan zainab arifah yar gata ce na bugawa a jarida basu isa su fara juya brain inta ixuwa hana yuwar komi ba duk dama sunga aboye take zuba crushing inta akn ibaad sabida yadda taga ake mugun tsoron masa shirme. tun da zainab takai jss 1 ta dada fallewa da jiji dakai snn tagamu da kawaye irinta sangartattu yayan masu kudi"Nala, da rukky, haka zasu zugata tayi wann tay wancan domin ibaad, amma bai taba kulata ba dan ya tsane yadda ake nuna mata fifiko tare da sangartata agidan, nd worst part ma yadda take xuba ma uban kowa fi'ili da manyance ana kyaleta dan ba ason ran ubanta ya ɓaci, tun tana wannan kananan shekarun tafara koyan kwalliya da saka matsatsun kaya wai dan kawai ibaad yayi noticing inta amma inaa shi mugun haushi ma take bashi aransa.
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[23/10, 18:55] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE 'BOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️5️⃣lamarin boyayyr soyayya me zafi da zainab Arifah take kumsawa aranta akan ibaad yakan daure ma kowa kai musmn dake ita da kanta ɓoyewa takey sai ya zamana kowa yana dan dauke idonsa akan wasu abubuwan datakeyi, kafin takacika 14yrs duk matayen familyn al-mansur saida suka san da wannan ciwon obsession datakema ibaad wanda ynxu yafi karfin ace masa tsaftacyar soyayya dan wani bin inbata gansa ba iskar datake busan numfashi dashi kamar dauke mata yake a makwogoro, haka ma duk ran da akace tazo gidan ta gaishesa yahade rai ya wuceta be amsata ba haka zatayta kuka da tsananin fushi kamar me fama da aljanu a dakin anty safeera, wani bin har kaga tana zazzabi me tsananin zafi, haka ma inta koma gidansu xata kulle kanta a dakinta tay ta rabza kuka kmr an bugeta tanajan zuciya wai dan ibaad bai amsa gaisuwarta ranan ba,
gabadaya sai ta Ɗaga ma kowa hankalinsa agidansun, saidai duk rintsi duk wuya bazata taɓa iya furta ma kowa cewa ibaad ne matsalarta ba, kuma shine take mutuwar so aranta a fili ba, yanxu haka iya kawayenta na schl ne kawai suka san asalin meyake damunta aranta..
wasa wasa abun har ya fara zame mata kamar wani strange ciwon ODD wato (oppressive defiant disoder), kowadai ya damu, ganin iyayenta sun fara fita hayyacin su wajen bincike akan sabon sabbin bhvrs dinta yasaka tadan fara kamewa,musmn dataji prof dakansa ya farayin tunanin hanata zuwa can family house dinsun kwata kwata, anashi tunanin hala cutar da yarsa akeyi aɓoye dan baya yawan bada kudadensa ma dangi ana bushasha dashi, hjy hamida kuma gani take kamar maita ne kawai ake so alashe mata yarta kwalli daya dashi acan family house hala shiyasa yartan take behaving strangely dan har malamai takira anyi ma zainab din ruqiya da su hayaki basu san damuwar soyayyar ibaad ne kawai aranta ba.
Ganin iyayentan sun fara daukar zafi akan maganan har sun fara batun yanke hukunci akan zasu hanata zuwa family house din ma kwata kwata yasaka marmaza ta hau neman mafita dan bata kaunar wani abunda zai jawo ace bazataje can gidan taga kyakkwayr fuskar ibaad a wknds ba.
Sangartattun Kawayenta na schl Nala bala da rukky hamza sune suka soma bata shawara, sukace since her 14th birthday is coming up soon ai ynxu tawuce ajin ace mata yar karamar yarinya yanzu kawai taje ta samesa kai tsaye ita tafara masa magana akan abunda takeji akansa. abunka da yara kanana kuma sangartattu yan gata cikin iko da rashin tarbiya da nuna tsagwaron manyance
suka zugata sosai kuma ta zugu,ata fannin ibaad din kuwa lokacin anata rububin ganin sakamakon jarabawane na school of medicine nd surgery pre test zai shiga jamiar Bayero na kano, jarabawar ya fito kenan yacinye sosai yanata kkrin tunkarar karatun medicine dinsa daya ke buri, satin saiga zainab arifah tasha wanka tazota weknds as usual taci uban gaye sosai tasaka wasu purple and white english wears masu aji ,hakanan tazo ta hakimce a karamin falo tasaka anty safeera agaba da shagwaba da manyance akan dole dole taje kawai takira matashi tacemai yazo nan shashen ya samete inyaso snn sai tamasa maganan datake tafe dashi, ita sam bata san hakan ma rainin wayo bane. wai in tana da magana da mutum da mutum toh ita bazata daga kafarta taje ba saidan in mutumin yazo har inda take ya sameta koda kuwa ya girmeta sosai.
dake tariga tasaba komi tace musu tana so ana mata haba haba, kawai yau sai taji mugun mamaki dataga anty safeera takekeshe ido tace mata bazata iya zuwa sashen ammi karama dan ta kira mata ibaad nan ba saidai in ita taje ta samesa dakan ta, a wasa ta dauki maganan dake ba'a saba ce mata "no" ba can kuma sai taji haushin hakan sosai, saidai duk a tunaninta na yaranta ta dauka hala kawai tsoronsa suma manyan matan gidan sukeji, mugun yarda dakanta datayi yasaka tamike tana mao gyara zaman kayan jikinta cikin jan tsaki kai tsaye tajeta har sashen ammi karama tana takunta ahnkli kuma ayangace kamar bazata taka kasa ba.
cikin cin sa'a kuwa sai ta samesa tun a babban falon gidan da laptop agabansa yana kan kkrin registering kansa for clearance dan shi babban likitan zuciya (cardiologist) yake da burin yaga ya xamo dan haka karatu ne meyawa agabansa, lkcin kansa yadau zafi yanata cike cike sqi ganan zainab arifah ta doso, tsayuwar cak tay daga samar stairs tana kallonsa dan duk dama tana mutuwar sonsa babu karya dakakken kwarjininsa yana mugun girgizata, tafiya take kirjinta na tsananin bugawa amma data doso kasa ta falon tadan kare mai kallo duk sai taji takara mucewa da sonsa a tsaye, he was wearing this very clean plain cream shirt da yaji karin guga haɗe da plain coffe brown trousers, tsaftarsa da kwarjinin sa sosai yakara cike mata ido gashi bao saka turare me karfi saidai me sanyi wanda daga ka doso sa zakaji kamar a fatar jikinsa qamshin yake tashi.
jin kirjinta na bugawa fat fat kamar zai ballo waje taji tsoro yadan kara rufeta, dacan har zata hakura takoma dakin anty safeera ta kara shiri sai kuma ta tuna cewa iyayenta zasu iya hanata zuwa gidan kwata kwata in har batay wani abu akan abunda takeji akan ibaad ba, nan da nan kuwa sai ta cije ta danne tsoron, gashi dama bayan gaisuwa sama sama basu taɓa yin wani maganan 2 scnds dashi ba all this years is like baisan ma tana existing ba dan ya jima da tsanar behviours inta na raini da sangarta.
kwas kwas ta karaso cikin rangwadi da yadda da kai batay mai sallama ba iyaka qamshinta ne ya bule wajen tabi ta kuresa da manyan idanunta tanaji aranta kamar zata haɗiyeshi, idanun sa stiff suke akan system dinsa ko daga kansa baiyi ba haka zalika baice komi ba har tanemi waje daf da chair dinsa ta dan zauna ta kuresa da ido., shiru ne ya dauke wajen ganin bazai kulata ba aftr like 10 min cikin rollng idanu tace amm hi, can i have ur attention here. yay shiru kamr badashi takeyi ba
tweeking fingers dinta tay ayagance gaban screen din laptop din suna hade ido tace "hey, bakaji abunda nace bane ?? fusknsa a mugun harde yace "what? tace "you" i just talke to u .cikin katseta yace ohhhh "sallamar ki kenan?
"my bad"..assalamu alaikum.
dauke kansa yay saida yaja kamar 3 min snn ya amsata ciki ciki.. tace "can i talk now.. irin kallon ohonkin dataga ya mata yasata dan kyabe baki cikin sauke ajiyan zuciya tace "anyways.You should probably calm down before I actually admit I’ve been crushing on you. maybe your ego won’t survive it. ina so in gaya maka cewa ive been thinking about u, i think i am in love with you ibaad.. ina so..wani irin dakakken kallo yamata tunkan ta karasa ba cikin datsar numfashinta yace "i have heard enuf kitashi kibarnan.
karamin murmushin ko inkula tay snn tazuba masa manyn idanunta masu cike da tsagwaron rashin kunya atakaice tace
"excuse me?? iya abunda zaka ce kenan? Ugh i cant belive this, I don’t even know why I’m saying this, but I’ve kinda had a thing for you, wai ko baka gane me nake nufi bane...
wayar chagersa kawai ya cire a wuta ya miƙe tsaye har zatai mai magana cikin daka mata tsawa yace kee bance miki kibar nan wajen ba? sai zuttt zutt taji saukar bulalan ajikinta..
within mins akaji ihunta yana tashi agidan..
ahhh, wayyooo,wayyo daddy, daddy, daddy naaa, mummy wayyo Allah ibaad kayi hakuri..daddy kazo ka cece ni wayyo ihu kawai take zubawa me kara tana daka tsalle a mugun rude tana kuka me kara
kusan babu wanda bai razana da ihunta ba, kaf matayen gidan suka firfito duk akayo falon ammi karama arude dan basu taɓa jin zainab arifah na wann ihun ba, nan aka samu Ibaad ne ya rike hannayenta biyu yana cauda mata wayar chargensa ajikinta yana kuma tmbayarta "ko shi sa'arta ne? kiris ya rage ta sume masa dan tunda aka haifeta ko tsawa ba ataɓa mata na bare duka.
yaa maheer ne yay sauri ya karɓeta a hannunsa dan wani irin razannen kukan takey a mugun mugun tsorace jikinta na rawa rawa kamr ba ita ba, wanda hakan yasaka tuni idanun mujaheed ya tara ruwa dan yana da tausayi sosai, atake kowa yafara daga hanklinsa ana ta tuhumar ibaad ko me zainab arifah tayi masa, ammi babba da anty safeera duk sun dau zafi suna kiran sunan sa ana tuhumarsa falon ya kacame da hayaniya sosai.
baice musu komi ba yahaɗe ransa ya koma yazauna snn ya dauke kansa ya cigaba da latsa computersa anata surutu ko ajikin sa face saida uncle moh dakansa ya shigo wajen yafara tambayarsa, agaban kowa ya mike tsaye snn ya maida musu abunda zainab arifah tace mai nawai tana sonshi bla bla bla, ibaad ya nuna bacin ransa sosai, ya hada harda sauran cousins dinsa matan duka wato (kulthum da sultana) yace karda wata yarinya ta kara masa wann wasan shi baison hauka yaushe ma sukakai da su furta ma namiji batun soyayya tun suna early teenagers???
daga uncle moh sai maheer ne kawai suka nuna sun fahimce shi, mj kam baice komi ba saboda kukan balai da zainab arifahn tayi sosai ya jefasa cikin tausayi da rauni gashi dama suna dan shiri sabida shi yaron anty safeera ne kuma age mate dinta kenan dama agidan they are both going to tru the same age.
sauran yaran gidan ma sosai suka dada firgita da tsorota da fushin ibaad, sanin cewa babu mahalukin dayake da ikon taɓa zainab arifah ko ɓata mata rai agidan yadda ake mugun daukarta yar gwal saigashi ibaad ya zane yar banza ciki da bai kamr baisan waye ubanta ba.
duk dama dattijan matayen sun san cewa dagaske ne Zainab arifah tanason ibaad amma haka suka haƙikance suka bi suka dora masa lefin komi duk sukace ai kawai gigin yaranta ne yake damun zainab ibaad bai kyauta ba yayi over reacting yaci zalin yarinya baida haquri,..
kai wasa wasa wasu bakaken maganganun da ammi babba ta hau furtawa ma zaka dauka wani babban zunubi ya aikata, har cewa take zainab arifa din ma aitafi karfinsa a batun soyayya sabida ita tanada bright future ahead na gadon dumbin arziki daga kawu babba shikuma ibaad din yananan ba'asan ma yazai kare anashi rayuwar ba. tanayi kuma tana soka zagi ma uwarsa asakaye itadai ammi karama hakuri kawai ta bayar ma kowa sai bata kara cewa uffan ba ta koma daki.
haka matayen sukayi ta kananan magana a gidan ranan babu kalar rarrashi da kwalemar kwainane wanda ba ama zainab arifah ranar agidan ba,
ammi babba anty safeera Da mj duk suka taru akanta suna ta lallashinta a daki.
shikuwa ibaad ko ajikinsa har yanxu ma mamakin tsaurin idon zainab arifah din yakeji aransa yadda tazo masa gatsau ta samesa babu wani dandanin tarbiya ko kunya ajikinta tamasa maganar soyayya da dumbin tsaurin ido da shegen manyance kamar wata yar shekaru talatin, mugun hade ransa yay da kowa agidan shima, bai kuma bawa uban kowa haquri ba face saida mahaifyrsa takirasa daki snn ta masa faɗa tacemai da baidake zainab din ba da faɗa kawai yayi mata, nn ne ma ya sassauto ya ba da mum dinsa hakuri har yace mata bazai kara dukan musu ƴa ba tunda bataso. da kyar da wahala dai wann maganar tay sanyi ranar ma da dumbin zazzabi zainab arifah tawuce gida, taki sam iyayenta suga shatin zanan dukan ajikinta.
shiru shiru har ana zaton komi ya lafa washe gari da yamma ammi babba dataga alamar maganar zai mutu abanza aikuwa nan tadau waya takira gidan prof zayyanu wanda da kyarma aka samu aka haɗata da hajy hamidar suka dan gaisa babu ɓata lokaci tahau zuba zance cikin sigar makirci harta sanar da ita komi da ke faruwa bata rage ko aya aciki ba saima gishiri da maggi data zuzzuba dan labari yayi zaƙi ita kuma ta samu karbuwa.
bazan iya fayyace kalar tashin hanklin data ballo ranar ba, dan ranar gidan prof ko xama basuyi ba, hjy hamida tana gama aje waya jikinta yafara ɓari da tsananin bacin rai, nan da nan takira mijinta tacemai duk inda yake kawai yazo gida yanxun nan za'a kashe musu yarsu da duka, yana can airpot kano amma jin anfurta batun yarsa hakanan ya mance komi ya dawo, yazo gidansa ga samu matarsa cirko cirko duk ta birkice tana huci kamar zakanya tanakuma safa da marwa a wargagejen falonsu da hadadden wayarta a hannu dan tagama qudirawa aranta kawai sojoji zata tura aje har family house a zane kowa dake wajen ciki da bai snn akama shi ibaad din akaisa military gurd room amasa lilis sabida dukan yarsu dayayi
sosai abun yayi ma prof ciwo aransa bana wasa ba, danko shi bai taɓa yin tsawa wa yarsa ba bare duka, saidai harga Allah yasan bazai taɓa iya kama ibaad yakaisa gurdroom akan haka ba yasan za'aje ne akashe shi, kuma haryau yana dan girmama babban wansun aransa wato marigayi dr almustafa mahaifin ibaad, dake shine kawai adangi bai taɓa guje masa ba duk mugun halinsan nan yana tolerating dinsa har ya rasu.
hakanan dai yay masifa yay bori yay bambami snn yabi ya danne xuciyar matarsa aka bar maganan sojoji agefe, nan sukaje har dakin zainab Arifah suka tasota agaba da maganan ibaad, dacan taki sam ta gaya musu amma suma nace mata da nuna bacin rai da lallashi dai har saida ta hakura ta gaya musu dukkan abunda takeji na matsanancin soyayya akan ibaad.
lamarin ya matukar daure musu kai, ya saka musu tsananin baqin ciki tare da dumbin mamakin yadda at this young age soyayya me tsananin zafi ya kama zuciyar yarsu, tunda suke da ita bata taɓa musu kuka irin nayau ba, sai rokonsu take akan kar su masa komi har cewa take zata mutu in sukasa ibaad yakara tsanarta itade tana sonshi. it was pretty serious nd obsessive, amma dake suna matsanancin so ta kawai sai suka bar maganan, suka mata fake promises suka lallasheta sosai cikin nuna mata dumbin soyayya da kuma matsanancin gata, a tunaninsu duk yarinta ne sunaji aransu maybe tsabar kyau da kuma kwarjinin ibaad din ne kawai yake dan rudinta inta girma ma zata manceshi sabida matsayin rayuwarsa ma aiba daya bane.
suka mata wayo suka nuna sun fahimceta, hardai ta amince tay shiru, likitansu na musmmn aka kirawo yazo ya dudduba jikinta musmn wajen shatin bulalan aka bata wasu special pain relievers da kuma underage antidepresant drugs tasha sabida yadda ta bi ta galabaice sosai.
dan kawai hankalinta ya kwanta haka iyayen suka nuna mata cewa zasu mata dukkan abunda take so din, bazasu taɓa ibaad ba tunda ma bata so ataɓashi. amma fa sosai abun yayi ma mahaifyarta ciwo aranta bana wasa ba dan tabalain so ace taci mutuncin kowa agidan akan wann abun da akama yarta. shikuma prof zayyanu
ji yake ko a mafarki bazai taɓa aura wa yarsa talaka ba bare kuma har ajega batun auren dangi. dukkn su iyaye ransu bai musu dadi da lamarin nan ba. they just try to numbed it a fuskarsu, acting all fine nd supportive while they are not dan kawai kar zainab arifah ta gane basaso ta shiga wani mummunan hali gashi
dakyar Allah ya basu ita.
arana ranar da daddare bayan likita ya gama dubata nan danan prof yasaka hajy hamida ta shirya tawuce da zainab Arifah din izuwa kasar sydney on a 5 days daddys girl petting break waidan kawai hanklinta ya kwanta
ahakama prof bai daddara ba, suna wucewa sydneyn maza maza ya kira uncle moh a waya, ko sallamarsa bai amsa bare gaisuwa yahau sauke masa buhun masifa ta inda yake shiga batanan yake fita ba, kai tsaye babu sakayawa ya masa ihu ihu ya zazzagesa sosai yace musu da shi da bappa zaidu sune suke daure ma ibaad gindi dan ya kashe masa yarsa kwalli daya, yace dama can yasani bason suga ya haihu sukeyi ba kawai so suke ya mutu a dau dumbin dukiyarsa abasu,.
babu irin zage zagen da zarge zargen da baiyi ba. tun uncle moh yana shiru har kirjinsa ya fara zafi tsabar fushi kawai sai ya kashe wayarsa..
yana katse wayar yazo gida yahau sauke fushin akan ibaad tareda sakamai dokan cewa karya sake dukan kowacce yarinya agidan inba hakaba kuma shi gskiya zai kai kararsa wajen bappa zaidu.
har yagama masa fadar Ibaad dai baice masa komi ba san already ya riga yay ma mum dinsa ma alkwari.
daga fannin ammi babba kuma duk ta kasa zanne ta kasa tsaye tana Allah Allah washe gari yay taga anzo har gidan an ci mummunan mutuncin ammi karama tareda danta ibaad amma sai shiru kakeji, ita bata karajin bayani daga wajen hajy hamida ba hakazalika nan ma bataga anzo anyi hatsayina ba, kai hanklinta bai kwanta saida ta kira anty safeerah toh abakinta taji cewa ai prof ne kawai ya kira ya zazzage su uncle moh. ranta baiso ba duk dai ba haka taso aranta ba.
bayan kusan sati biyu da faruwar haka da kyar iyayen zainab Arifah suka barta ta dawo tana zuwa gidan duk weeknds, saidai wnn karon ta dan shiga hanklinta bata fiye wulgawa ta inda ibaad yake ba dake ma yanxu baya zama yana kan kkrin shiga jami'a ne abunsa. da mujaheed kawai suke dan magana sama sama intazo gidan dake shine sa'arta, shikansa Mjn wani irin mamakinta yake dada sha musmn yadda yaga duk ta sauya salo tanata kkri taga lallai tasaka hanklin ibaad ya dawo kanta, dan kamar ma kara hura mata wutan son ibaad din aka ɗadayi aranta kwana biyun nan..
_ANGUWAR TUDU_ ...
Da yamma ne lis gari yay sanyi yara suncike kan tituna da hayaniya da alamun lokacine na sakosu daga babban makarantar higher islam na yara dake anguwar dake mashi kadaine a anguwar duk wani yaro ko yarinya dake zuwa schl a wann yankin nan duk ake zuwa karatu.
daga cikin rububin yara yan mata inayah da ayanah suka fito suna tafe manne da junansu, yanayinsu na nuna dumbin soyayya na yan uwantaka da dumbin shakuwa a fili take nunawa, duk dama wuni sukeyi makarantar amma tsaf tsaf zakagan uniform dinsu, rigarsu fari kal ne sai hijab da wandon kuma dark green colour kowacce da yar jakar littafanta
ta saƙa akafadarta.
Fasalin jikinsu da kuma kamaninsu dake saurin fallasa mixed tsatsonsu na asalin jinin buzaye haɗe dana fulanin daji ya saka sukayi masifar kyau atare, yanayinsu gwanin ban sha'awa suke tahowa duk jikin su akillace yake acikin green hijab dinsu..
kalar bakaramin yi musu balain kyau tayi ba saboda yadda ta amshe kyakkwan tsarin fuskarsu da yanayin su na yan mata masu fallin tasowa, gaban su gadi suke takawarsu cikin nitsuwa da sanyin jiki dan inda sabo yanzu sun saba da yanayin yadda idanun kowa ke satan kallonsu msmn ma ayaanah datake da wani irin rare calming beauty ita ba fara sol ba ita ba baƙa ba ita ba cokolate ba, tana dai tsaka tsakiyar hasken fulani dana buzaye duk ta hada kamannin biyu, ita kuma inayahr akwai kyan ta dake nuna na fullo haƙƙ babu mix da kuma tsayin ƙafa na mahaifyarsu taawure data gada, duk da kankantansu kallo daya zaka musu kasan cewa tabbas wayann yaran zasu zuba dirin jiki me daukar hankali, kai daga nan ma zaka san sudin nadaban ne acikin mata.
Kamar yadda suka saba kullum adaidai hanyar da yabi kwanan gidan sarkin kasuwa sukeyin sallama da sauran yaran schl dinsu nan bayan sun rabu sai kowacce tanufi cikin gidar iyayen ta.
lokacin yamma ne liss masu zuwa kai haraji da reports gidan sarkin kasuwa anata kkrin kai da komawa yawanci zaka ga kofar gidansun da matasa sosai da yamma
tunda suka doso inayah ta sauke kanta kasa cikin sauri sauri sanin bamai yin lokacin kula gaisuwar su saidai ayita comparing kyanta dana yar uwarta, ayanah kuma mugun tsoron maza takeji dan haka tun kan su iso ta wajen ta fara ɓari ɓari ta kuma kara tantame hannun addanta inaya.
tafiya sukeyi cikin sauri sunajin yadda kananan zunde da gulma kala kala yake tashi ako wani tsirkon taro dake kofar gidan
nasu ,tabbas mafi yawan matunen dake zuba musu ido kullum ba dan Allah bane sai dan gulma munafurci da nuna hassadar su a fili dan kaf anguwa an ririta zancen cewa yayan tàawure me saida nono da suke ɓakunta a anguwar sune masu dumbin kwaxo a makarntar tudu gabaki daya gasu kuma da balain kyau har ana kafa caftersu agidajen mutane.
kamar kullum ido ne ratata akansu, inayah ce me karfin xuciyar kanta akasa sai jan hannun kanwarta take da sauri, suna kaiwa
kofa tsabar ɓari kawai sai jakar ayanahn ya subuce a kafadarta ya faɗi. da sauri inayah ta saketa ta tsuguna kasa zata dauka jaƙar tana tsugunawa kuwa a mugun gigice kuma abazata ta riƙe gefen cikinta da sauri tanamai furta innalillahi wa inna ilaihi rajiun.....da karfi
tun kan ayaanah ta dago kai gabaki daya sai sukaga idanun matasa da dumbin mata dake kofar gidan sarkin kasuwa sun dawo da idanunsu kan inayahn atake da wani irin mummunan kallon zargi....
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[24/10, 19:47] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️6️⃣
Da wani irin ƙarfi zuciyar ayaanah ya buga bisaga kallon reaction na zargi dake cikin kwayar idon mutanen da suke zubo musu ido sai taji ta mugun razana da yanayin inayan jikin ya dau rawa itakanta batasan sadda ta zube kasa tariko kafadun addan nata cikin ruɗewa ba...
"Subhanallah… lafiyá de kuwa adda? Méyé sàmèki haka..Mei yé sàmèki a cikin?”
muryanta maicike da tsoro da dumbin rauni yafito da rawa rawa ayayinda harshen buzancin nasu ya dada bayyana cikin kwababben hausarta ta abazata...
wani irin zafi inayah taji agefen acikinta dake tahowa tun daga wajen cibiyatta kamar ana zungurosa da icce irindai kamar ciwon ulcer ko irin ciwon cikin nan da ba asan asalinsa ba.
ganin idon mutane akansu yafara yawa yasaka inayahn tay ta maza tabi ta shanye dumbin zafin datakeji acikinta ta dagokai tana dan ƙoƙarin yin murmushi saidai ji take kamar bazata iya miƙewa tsaye ba..
kallonta ayanaah ta dingayi ganin wani irin sudaɗɗen hucin zufa yadan fansama asaman fuskar addanta me bayyana halin da take ciki na ciwo da tsananin zafi, tsamm inayah tay ganin irin kallon razana da anayahn take mata cikin dauriya tay saurin dauke idonta kasa ahnkli ta danne komi tadauki jakar tadan miƙe tsaye ahankli ahnkli dakyar tana cewa "hai kekam, à handi mboni baki da dauriya sham anyi babban matsoraciya ganin ayaanahn tanata kallonta har yanxu batace komi ba yasa ta kara mikewa
"karki damu Lafiyata lau… wataƙila yunwa ce ko saboda nagaji...
Abunka da yaranta wani irin nannauyar ajiyan zuciya ayanahn ta saki feeling a bit relieved ahnkli cikin sanyin murya tace tohm shikena,sannu da jin yunwa adda am. toh muje ciki ni zanje madafi na kawo mana abinci yau bake ba..ke aizaki huta yau ko??
a daddafe kuma a ɓoye inayah tay still a tsaye da hannunta ɗaya data zamarshi ta cikin hijabi tadan riƙe gefen cikin nata dake mata ciwon sosai sai murmushi kawai takey ma yar uwarta ayanah badon ciwon cikin ya tsaya mata ba sai danta dada kwantar mata da hankli.
not minding ydda ake satar kallonsu da yanayin gulma ahaka har suka saka kai suka karasa cikin gidan nasu atare. saidai dake yamma ne basu tarar da kowa agidan ba, lkcin duk dai ana kasuwa da alama dai izuwa nan bada wani jimawa kowa zaidawo dan ankusa kirar sallan magriba ynxu..
duk da rashin girma da wayon ayanaah yau sosai take saka ido akan yanayin addarta inayah da taga kamar ya dan canza, suna shiga harabar gidan tanema mata wajen zama akan dakalin kofar daki snn ta amshe jakunansu dukka ta kai daki ta ajeshi, aguje tadawo ta same ta tadan jingina da bango tana dan nishi har yanzu da hijabi ajikinta ta damke cikin nata taciki, da gudu gudu sauri sauri ayanah ta je wajen da ake aje musu kwanon abinci ta dauko musu tuwon dawa da jar miyan kubewa har da ruwan sha tazo ta ajeshi agaban addanta duk hanklinta ya tashi ta dauka kawai tsabar yunwace ke neman ya naƙasa mata addanta inayah..
ita kuwa inayah gashi dai ciwon cikin na mata kamar na yunwa yunwa amma koda ayaananh ta zubo musu abincin sai taji abincin kamar yana daga mata zuciya tana jin ɓacin rai sai tanaji kamar ta washe abincin aranta, saidai dake batason ta dagawa yar uwarta hankli yasaka ta daure
taci abincin kadan baifi loma biyu ba snn ta sha ruwa sai tace mata zataje ciki ta cire uniform ta dawo tunda ta taɓa abincin kadan. tafiya ahnkli ahnkli tayi har ta shiga dakin ta cire kayanta ta saka riga da zani jin ciwon cikin gabaki daya yane neman ya hanata tsayuwa da kyau, kawai sai ta nemi waje ta kwanta atake kuwa wani bacci me nauyi ya kwasheta abazata
wanda kusan abun al'ajabi ne kaga inayah tana bacci gabanin magriba sabida bata kaunar abunda zai saka tay lattin sallah a rayuwarta dan in batay sallahnta akan lokaci ba har kuka takeyi.. jim kadan koda su taawure suka dawo gidan gabanin magrin suka tarar da Ayaanah ita daya a haraba ta saka tuwon agabanta ta tsaya cak bata cigaba da ci ba, ta kuma rabza uban tagumi hawaye sun ciko acikin kwayar idanunta sosai abun yadaga musu hankli.
hajya mairo ce ta fara rufeta da tambaya toh ita bata gane komi ba, sai tahau gaya musu iya abunda ya faru, cewa takewa addanta tana jin yunwa amma taqi cin abinci dayawa kuma gashi nan bata baccin yamma sai yau taga tanayi, yadda ayanah ta daga musu hankli babu shiri taawure ta shiga dakin tahau tattaɓa jikin inayah ta na duddubata sai kuma taganta kalau, kaidai dakyar suka wanye maganan aka bari akan cewa ko yunwa ne ya haɗu mata da gajiya. hajy mai tuwo har da cewa kar asaka inayan aikin gida gobe da sassafe abarta tana dan samun isasshen bacci...
Bayan awanni biyu ana daf da ishai snn inayah ta farka lkcin zafin ciwon cikin nata yaƙara matsawa izuwa gefen dama kusa da kasan cikinta. but the pain is bit bearable, duk sai ta farka a ruɗe, ga kuma anxietyn rashin yin sallah akan lokaci kawai saita daure ta waske ta miƙe garau ta yi sallolinta har ta dan saki jiki ta zage ta koyawa ma anayah karatun sukayi basic _phytogoras theorem_ dan kawai hanklinsu taawure ya kwanta sosai.
washe gari basu barta tay aiki mai yawa ba duk dama ta nace saida tay yar shara da wanke wanke snn suka ci abinci nan ma sama sama taci snn suka wuce makaranta
yau suke cike wata daya da sati biyu a tudu, ana saura sati guda kenan ayi ma inayan saukar qur'ani, ga kuma tests na boko shima sun farashi dan anata tsammanin exams dinsu na zuwa ajin gaba yazoshi akan lokaci
sosai yaran suka kara zage damtse wajen karatu, saidai ata fannin inayah kmr kusan kominta ne takejin yana canzawa acikin jikinta, tun data fara ciwon ciki sai taji takasa gane ma jikinta gabaki daya amma dake tanada taurin zuciya sai ta matse komiii tana kaucewa duk wani abunda zai jawota baya a karatu dan batason tay wasting wann dumbin Risks da effort da kuma ubam kudaden da mahaifiyasu take zubawa akan batun ilimin datake basu.
kasancewarta ƴar fari, al'adar kunya da dumbin kawaici dake tsakanin uwa da ƴar fari bai ɓari sun shaƙu sosai da taawure ba, saidai fiye da kowa a duniya inayah ce take mugun mugun tausayawa ma mahaifyarta aranta, duba da tsauraran dokoki na al'ada da sukebi a kauyensu, da kuma irin jahilci, taurin kai da tsaurin ra'ayin irinna mahaifin su malam juma.
tasan bakaramin jarumta da soyayya me yawa taawure take musu aranta ba musmn data iya daukar wann babban Risk na rintse ido akan batun al'ada tare da saɓawa ra'ayin mijinta nazama acikin jahilci har tay burus tasakasu a makaranta a ɓoye donta ilimantar dasu addininsu da zamani duk dama abune wanda tasan zai iya ƙarar mata danata rayuwar, zai jawo mata mutuwar aurenta da juma, da kuma tsangwamar mutane duk sanda aka kamasu suna aikatawa.
shiyasa koda wann ciwon ciki ya fara mata taki sam tana nunawa a fili, babban burinta shine taga ta karfafawa taawure gwiwa, sun zamo silar farincikinta ita da yar uwarta ayanah, duniya da lahira. dan taawure jajirtacciyar uwace data musu dumbin sadaukarwan da bakowacce uwa bace zata iyashi.
bayan kwana biyu rayuwarsu ya cigaba ahaka, alamomin ciwo sunata zuwa ma inayah suna tafiya, wani lokaci ta ji sauƙi, wani lokaci zafin cikin nata sai ya dawo, musamman bayan cin abinci ko wani aikin wahala. wata rana koda ayaanah tayi kmr ta ganota sai ta ce mata gajiya ko ulcer ne.
satin sauƙar qur'ani na zagowa aka qaddamar, wanda kusan babban hidima hjy mairo me tuwo tay domin jikarta inayah
nan akayi mata gagarumin murna na zamowa gwarzuwan karatun qur'ani na gabaki daya yankin tudu, anyi abinci hilimi guda akay sadaka aka ciyar da almajirai sosai, kai dai tamkar bikin auren inayah haka hajy mairo ta daukaka abun har anko na kaya saida tay musu shadda me kyau. ayaanah duk tafi murna da cigaban da addanta ta samu na zamowa gwarzuwa kuma mahaddaciyar littafi me tsarki, ranar Taawure bakaramin dadi tare da alfahari da yarta inaya tay ba.
basu taɓa magana cikin nuna soyayya ta uwa da ƴa me tsayi ba ma sai aranar. bayan hidiman ne ciwon cikin ya fara taɓa inayah acikin dare sosai, wani bin da dadderen zata ji ciwon ciki da ba ta taɓa jin irinsa ba.
Cikin nata kamar ana murɗa shi da icce mai kaifi, haka zata kasa bacci tayita juyi tana huci, Ayanah takan ji tsoron duk abunda ke faruwa da yar uwarta inayah da kuma mugun tausayinta amma hakanan inayan take hanata gayawa kowa halin da suke ciki dake kuma suna farkawa da safe sai taganta garau har suje makaranta.
tunda aka ma inayah sauƙa sai ta dan bude karamin islamiyatta na dare, bayan isha sai ta jawo ayaanah zuwa zauren gidan ko gindin bishiya inda take koyawa sauran yaran anguwar wanda iyayensu basuda halin sakasu a makarnta karatun qur'ani dana bokon sama sama ayaanah tana tayata.
hajy mairo mai tuwo ce ta dada daure mata gindi, dan ita macece me kaunar taga yaro karami mai dumbin kwazo tare da son kawo babban cigaba musmn ma ga dumbin al'umma, riƙe ƴayan taawure kusan abun alfahari ne agareta duk dama riketa kawai tay basu haɗa jini ba, duk safiyar Allah sai sun sakama inayah Albarka a rayuwrta.
kwanaki basu karya suna cika wata biyu sharp a tudu aka fara batun exams dinsu ayayinda shaƙuwar ayaanah da inayah yake cigaba da burge kowa dan babu wanda yasan halin ciwo da inayah take ciki kamar ayaanah, duk hanklin taawure yafi ta allaka ne ga shirin komawar su gida can kauye majiya sabida nan da sati uku taji labari cewa mijinta juma zwi dawo, at same time tanata kkri wajen kare sirrin ƴayanta, ko kadan bataso ace ankai gulman yaranta garin majiya musmmn ma da inayah tay kaurin suna kwana biyun nan, duk inda taje zakaji ana kiranta gwarzuwan tudu, sabida aikin koyarwa datakey wa ƴaƴan marasa karfi wanda ya jawo kusan babu wanda baisan sunan inayah a tudu ba.
babu irin addua da fatan alheri da bata samu daga bakin mutane. matsalarta daya ne wann ciwon ciki me tsanani dayake cinyeta ahankli ahankli, an shiga satin jarabawa ne amma bata samun isashen bacci sabida zazzabi, gefen cikinta yafara kumburi yana tauri tauri taciki, wanda ko tsugunawa tay ko mistakely ta taɓa tawajen kumburin cikin bakaramin zafi takeji ba. ahaka kuma ta dinga dauriya har suka fara rubuta jarabawa, hanklin ayaanah bai fara tashi ba saida taga kasala, rauni da rashin ƙarfi ya fara nunawa sosai ajikin addanta. ranar tana kuka tace addah bazan iya ba kawai zan gayawa ummah inyaso akaiki asibiti, amma inaaa, haka inayahn taki barinta tace tabari sugama jarabawa, tay mata alkwari ita dakanta zata faɗa musu komi.
soyayya da kulawa na musmmn ayaanah take nunawa addanta dan duk tafi kowa sanin halin ciwo datake ciki, ayan kwanakin nan daga sun zauna zakaji inayah tana mata nasihohi masu shiga jiki......
kano..9.30pm
wajajen ƙarfe tara na dare Rahma exclusive private Hospital Kano.
karamin asibiti me zaman kansa da akayishi domin ƙrban emergency na masu hannu da shuni dan yawanci turawa ne da indiyawa suke aiki anan asibitin wanda acikin masu kudin ma bakowa ne yake da arzikin kawo jinyarsa anan ba.
security ne kusan guda hudu sunsha uniform agaban wata kofa nan cikin special ward na private consultation dake nan ne kusan ƙebetaccen waje ne na manya.
babu wani hayaniya bare wulgawar wani mutum, koina tass yake da kayan alatu da naurorin kiwon lafiya na zamani kamar ba a nigeria kake ba.
Daga cikin Room 7 iyaka Sautin ƙarar “oxygen machine” da ƙamshin magani shine ya cika ɗakin ayayinda Zainab Arifah take kwance shame shame akan gado an lankaya mata na'urar taya nunfashi da kuma drip a hannunta na hagu.
idanuwanta a lumshe suke tamkar wacce take cikin nisan bacci saidai ahakikanin gaskiya babu abunda yake yawo acikin zcyrta da kwakwalrta face tunanin yadda dan uwanta ibaad zai zamo nata har abada
wanda tun bayan zaneta dayai basu kara samun wani ganawa dashi ba intaje gidan ta gaishe sa zai amsata normal saidai tunda yafara karatun jamia rashin yawan ganinsa da kuma samun sakin fuskansa sosai agareta shine yafi komi daga mata hanki yanzu. tsakaninta da ibaad a shekaru baifi ace 4-5yrs ba, tunda mujaheed dake sa'an ta agidan dai 4yrs 11 month yabata baima cika full year ba kuma tasan akalla dai shekara hudu ne cass tsakanin ibaad da mujaheed. ita bata ga wani dalilin mugun jan aji da miskilincin da ibaad yake mata ba shiyasa ma haryau take ji kamar bazata taba iya kiransa da inkiyar yaya ba.
gani take tana da komi na duniya kama daga kyau, ilimi, gata, da kudi to menene kuma zai saka wani ɗa namiji ja mata aji?
takaici take jin ita tuna kamar ibaad bai wani girmeta cancan ba nd she want noting frm him face for him to be free with her, tanaso taga tana iya masa magana a duk sanda taga dama, intace mai yayi mata abu shima marmaza yay, kamar yadda kowa yake haba haba da ita saidai amma duk ta tuna cewa yataɓa dukanta last time data gwada jan hanklinsa da maganan soyayya sai taji duk takara shiga damuwa sosai
gashi har ilayau tana mutuwar sonsa aranta wani bin inta zauna tana tunanin rasashi sai dai kawai aga numfashinta yana sarkafewa...
yauma kusan abunda ya afku kenan wanda har yajawo akayi rushing inta izuwa emergency, iyayenta duka biyu suna tsaye agefenta idonsu cike da damuwa gashi sam taki tabude idanunta barema har susamu dama su tuhumeta abunda yake damunta dake yanxun tadany wayo tamugun kwarencewa wajen boye feelings inta acikin zuciya..
jim kadan wani babban Likita sanye da farin labcoat da green file a hannunsa yashigo dakin, jikin rank tag dinsa an rubuta Dr. Yusef suleim ajiki, wanda daga ganin yanayin dattakonsa kasan tabbas kwararren likita ne, yana musu sallama kai tsaye ya ƙarasa kusa da gadon zainab din yay yan dube dubensa snn ya bude file din ya fito da dawata takardar sakamakon gwajin numfashi ya dudduba kadan yana rufewa ya juyo kan prof zayyanu da matarsa da suka kafesa da wata iriyar idanu
cikin gyaran murya yace ranka shi dade Alhaji, Hajiya. ina so mu je ofis ɗina mu dan tattauna daku kadan game da lafiyar Zainab Arifah if you dont mind please.
kafin su amsashi saida Suka kalli juna sannan hjy hamidar tacemai "sure" daga nan suka bi shi har izuwa ofishinsa. ofis ne mai girman gaske ga tsafta yasha set na pure white L shape cushions dan tamkr wani palorn haka zaka gansa.
Dr yusef ya zauna yana dan kallonsu har saida suka samu nitsuwa snn ya bude file din da calm voice dinsa yace Alhamdullhi ga sakamakon gwajin da muka mata ya samu fitowa saidai kamar yadda kuka tsara mana ne babu inda bamu duba ajikinta ba
cikin gyaran murya yace toh agaskiya dai alhji, bazan boye muku ba Zainab Arifah tana fama ne da provocked asthma wato tasowar ciwon numfashi da bai riga ya haɓaka ba, saidai da akwai wani abu nadaban da nalura cewa shinei ya jawo mata wnn ciwon wanda gwaje gwajen mu ya tabbatar mana da cewa ciwon Damuwa ce.
cikin katsetsa prof yace ciwon damuwa kuma kai kasan me kake cewa kuwa?
da calm voice Likita yace " yes sir, ayi hqri. ciwon Damuwa mai tsanani ne wanda yaketa kokarin ya jawo mata matsalar wahalar fitar da numfashi.”
dede nan Ya dan ja numfashi kafin na ya ci gaba cikin nutsuwa “shawarar da zan bayar shine a samu a kula da bangaren damuwartata cikin gaggawa tun yanxu inba haka ba zai iya rikidewa nan bada jimawa ba za zamo mata matsalar raunin zuciya ko kuma jikin nata ya gaji gaba ɗaya. in har ana son zainab arifah tay tsawon rai sai anjuri kwantar mata da hankali snn aguji komai da zai rinka shigewa cikin tunaninta.
kafin ya dora kalma na gaba gabaki daya idon hajy hamida ya cika da hawaye. prof dai ya yi shiru yanata kallon likita kamar baisan ma meyake cewa ba.
fuskarsa ba awani sake ba yace "toh shikenan likita munji bayananka amma ynxu meyene mafita?
doc yace eh to alhaj mafitar kenan she has to use a terminal inhaler for now, snn Zan rubuta mata wani magani, to be taken once daily ko wani rana sabida ya rage mata tunani. amma fa lallaine ta sha, snn ta zauna a gida na wasu kwanaki tadan huta a kuma tabbatar during dis time bata shiga wata damuwa ba..
hajy hamida dai batace komi ba dan sosai zuciyarta yake tafarfasa taciki dan haka kawai jikinta yake bata kamr duk akan lamarin yaron nan ibaad ne yasa har yarta kwalli daya take kan azabtuwa..
Likita yace inba wata tambaya inaga we can call it a day, i will make an arngemt so dat you can take her home with you within few minutes. prof ya gyada mai kai baice komi ba, dake manyan mutane ne shi likitan ne ya miƙe ya basu waje, yana ficewa kuwa prof ya miƙe tsaye yana kallon sama cikin tashin hankali tareda lumshe ido da budewa yace "ya salam, what is all this? mutanen nan ashe bazasu barni in cigaba arayuwata ba, ƴata kenan mini tall a duniya amma sukeso sai sun kashemin ita hmm hamida did u have any idea why my only doter is behving like this? damuwan uban waye tasaka aranta? kece nake barin miki amanar zainab arifah agida, babu abunda kuka taba cemin kuna buƙatarsa wanda ba baku ba, but why dint even the god damn family doc say anything to me..wallh inhar ƴata ta mutu toh duk duniya sai ansan antaɓoni.
daga jajayen idanunta da sukaji kwalliya tay ta kallesa muryanta a raunace abunka da farin fata har fuskanta yayi jaaa, hawaye na zuba mata tace alhaj ni ina zan san maka meke kumshe acikin ran yarka? bayan kaima kasan zainab tagama raina uban kowa, batajin maganan kowa sai naka, nima i just found out abt her health frm elizabeth daya daga cikin maids dinta dake shirya mata daki, wai each time home doc yazo dubata ashe wai ita takece mishi karya sake yana gaya mana halin datake ciki...our doter is clearly trying to kill herself bcos of one stupid local boy
..wallah ba haka ƴata take ba, Arifa tana da wayo da ilimi, saidan in sihiri aka mata tabi ta dora walakntaccen yaron nan aranta, kaima dai kasan zainab arifa ba matar karamin mutum bace, nide wallah wallahi bazan bada ƴata ma wann yaron ba, tafi karfinshi har abada, saidai in zasu kasheta su kasheta..
tana fadin haka dede nan ta rushe mishi da wani irin kuka..
yay sauri ya dafa kafadarta yana cewa ohh nooo hamida kinjiki ke kuma,toh meye haka?
a mugun harzuke tace alhaji kaima fa kanajin abunda likta yake cewa yarmu zqta iya mutuwa da ciwon damuwa ko zuciyarta ya buga anan gaba, shikenan sai ninasha wahala na haifi zainab dakyar bata taɓa saba maka ba amma sai gashi wai yau zainab tana boye mana halin datake ciki akan yaron nan? this is insane.. toh bagashi ance ma ciwon zuciya zai iya kamata ta mutu ba shikenan yan uwanka sunji dadi sun hadakai zasu kashe mana yarmu kwalli daya wanda da kyar muka sameta wayyo Allah na
shima sosai abun yake kuntata masa aransa amma yayita maza yace 'shushhh hamida calm down kefa ba yarinya bace kuma ban mutu ba tukuna..kidena kukan nan mana ehh. cmon darling its okay ninasan me zanyi i know what to do zainab arifa bazata taɓa mutuwa ba, i know she hides it sabida bata sone inhanata bare ta saɓamin, i knw my doter, abun kawai yafi karfinta ne shiyasa take boyewa..so, dole ne mubi abun ahankli cos is getting pretty serious with her health, ynxu haka rayuwar yarmu ne on the line. get urself together idan munje gida we will make some key decisions to save her life bazata iyayi iya kadai ba.
cikin gyada mai kai ta share hawayenta da wani hadadden farin hanky data fiddashi daga cikin jakarta mai matsanancin tsada ta maida hankun jaka kenan securitynsu yazo ya kirawo su akan angama komi..
dauƙar jakarta tay ta dada gyara zaman mayafinta dayaji original silver stones babbane sosai rare design daga mum ramlat collections, ya bi yarufe mata duma duman jikinta na manyan mata isasshu koinanta acike yake tamm bata da ko ƙashin wuya bare alaman rama, wani shegen abun wuyar gwal ne kwance a wuyartata, gata da farin fata koinanta yayi soll tana sheqi gata doguwa, tsabar iya daukar wanka zakace ko balarabiya ce dan bakaramin cika babban mace tayi ba.
tana gama yafe gyalen tabi bayan mijinta suka samu har na gama shirya musu komi, nan suma sako yarsu zainab arifahn atsakiya suna mata sannu sannu tun anan ta sharesu batace musu uffan ba har suka kama hanyar gida, tun a mota tay bacci dukunkune ajikin mahaifinta dake likita yagaya masa cewa ya mata allurar bacci dan ta samu isasshen hutu sai bai damu ba, suna isowa gida kai tsaye prof ya wuce da ita purple colour princess theme bedroom inta na yar gata ahnkli cikin kulawa ya shimfidata akan makaken italian gadonta me tuff board double spring saida ya fita kafin nan masu aikinta kusan su biyar suka karasa sauran gyara mata jiki da kwanciyar me gabaki daya..
fitowarsa falo tun daga saman stairs ya fara jiyo muryan matarsa tana kan amsa waya dagaji kasan kanwarta ne hajy hajara shettima
duk sanda kaji ta nemi wann matar to da akwai babban matsala itadai sam taki ta amince aranta cewa har yarta zainab arifah zata saka wani soko matsiyacin yaro aranta da sunan soyayya tunma bataje koina a shekaru ba gani take kamar kawai asiri ne akama yarta
jin motsin saukowar mijinta cikin falon yasaka ta karkare wayar tare da cewa hajiya hajjara dan Allah ace ma malamin nan its very urgent, inde sihiri aka ma ƴata kawai agaya min insan nayi kafin su kashe min ita..pls i will wait for ur call
..daga haka ga katse wayar tana sauke ajiyan zuciya me nauyi....
cikin tafiyar takama tareda nitsuwa prof ya karaso cikin palon wanda komi cikinsa golden colour ne, anitse ya nemi waje zauna yanamia dafe kai Hajiya hamida tay sauri ta ƙaraso kusa da shi a hankali ta dora hannunta dayaji jan kumshi akan gadon bayansa tana cewa Alhaji Idan muka ci gaba da barin zainab Arifah ahaka wannan ciwon numfashi nata ba zai taɓa warkewa ba honey pls we have to do sumtin fast. kasan bata saɓa ma umarninka why not ka rabata dashi ko kawai gobe gobe taɓar kasar nan taje tay karatunta gabaki daya akasar waje..
laushin hannunta dake yawo gadon bayansa yasa ya lunshe idonsa tare da kara relaxing yanamai cewa "Na san da hakan hamida amma fa duk wnn matakan naki bazasu saka ta daina tunaninsa ba inhar kuma bawai tunaninsa zamu cire a ranta tabbas abunda muke gudun shine zai faru damu duk inda zamu kaita a duniya hakanan zata cigaba da lalacewa.
Shiru ne ya dan ratsa falon kafin can hjy hamida ta kallesa tace toh me kake ganin zamu iyayi mu ciresa a tunaninta.
hannunta ya kamo yana kallom kwayar idanunta yace leave that part to me..
zainab Arifa yarinyace yanxu tabbas idan muka matsa mata ta rabu da yaron nan toh tabbas zamu rasa ta. so, i am going to have to use a reverse psychology here, mu jawo yaron jikinmu mu bata abunda take so ynxu, nan gaba zamu zo matsayinda inhar nasaka mata doka akan yaron ma bazata iya tsallakewa ba, but for now dolene mu saka rayuwarta da lafiyarta as our main priority.
shafa fuskarsa takey ahankli cikin sauke ajiyan zuciya tace honey, are you suggesting we just let her be with him for now?
amugun kasale yace yes my love..inason zainab ta samu nitsuwa ne kawai tay karatunta me zurfi ta cimma burikanta dana tsara mata tukuna
..just trust me..i will handle her personally inta girma ta mallake hanklin kanta Inhar kinga wani a dangi na ya aure min yata sai inbayan na mutu...
kiss kawai ta dora mai agefen kunci ahnkli da alaman taji dadin furucin nasa ahnkli tace "your wish is my comand my love. amma kuma nasaka hajiya hajara ta duba min lamarin awajen malamai
yace hakan ma yayi..
daga haka ya miƙe, ya ɗauki wayarsa "kije ciki ki shiryamin kanki da kyau zanzo gadon naki na sameki.
wani murmushi tay irin wanda tun dazu baigani tay ba face sai yanzu daya furta mata hakan, cike da kasaita mai haɗe da rangwadi irinna manyan mata ta miƙe tsaye tanamai cewa "okay love..Dont keep ur queen waiting.
gyada kai yay yace sure. tana wucewa ciki ya ciro wata sim a wallet dinsa ya saka awata yar karamar waya snn yay dialing lambar dan uwansa bappa zaidu tun wayar baiy ringing ba ya wani hade rai yafara jan tsaki.
wayar yana fara ringing ya fice waje dashi a kunne after like 30 min ya dawo ya same matarsa har ta gama shiri jikinta sanye da wata arniyar nite gown ta bude tuma tuman fararen cinyoyinta akan gado tana jiransa, yan kwabe garensa wani dira yay kan gadon ya dora mata kiss me zafi snn ya kalli cikin kwayar idonta yace "
"jibi yaron nan ibaad zaizo gidan nan zanyi magana dashi nd i need you to be cool with him too..
wani chak annurin dake fuskarta ya dauke a mugun hargitse tace alhaj bangane ba, akan me zaizo mana gida kuma?
atake ya dan haɗe rai yace "kin manta ne, is All part of my plan hamida. kedai kawai kiyi abunda nace miki..
tun bata kai ga budan baki ba yawani irin wawushota jikinsa yanamai susuta da kisses daga haka har suka fada kan gado...
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[27/10, 19:03] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️7️⃣
G.R.A..
5;30~AM
kirar sallahn farko ya dira cikin kunnen ibaad dake kwance lumui akan lallausar madaidaicin italian bed dinsa dayaji off white cotton bedsheet me taushi yarufe daga jikin shi har izuwa kan kyaywan fuskansa da bargo me laushi, da adduar farkawa daga bacci abakinsa yadan bude ido cikin kasala bai motsa ba sai after like 5 scnds bayan ya idda adduar snn ya dire kafarsa akasa da bisimillah ya mika hannu ya kunna wuta, tsaftacciyar farar riga ce ta bacci kuma marar nauyi ajikinsa da dogon wando shima marar nauyi, goran ruwan dake gefen gadonsa ya dauka ya sha kurbi kamar biyu sann ya mayar ya ajiye, adan gaggauce ya mike ya shiga bathrum yay alwala ya dawo ya cire rigarsa snn ya dora goggyar bakin jallabiya me tashin kamilallen qamshin kylian love ajikinsa, snn ya saka karamin farin hula, nan take ya saka bedroom sleepers dinsa yabude kofa ya fito just few steps daga inda room dinsa yake ya tsaya jikin wata hadadden kofa ya hau kwankwansata da dan ƙarfi. ahnkli kuma atakaice yace "maheer is time", jin ba amsa shi ba ya kara buga kofar one more time
after like 4 min yaji muryan maheer din faintly yana cewa 2 mins pls. bai kara cewa komi ba yaja ya tsaya yana jiransa can saigashinan ya fito shima agaggauce sanye da riga da wando duk ruwan alwala nabibyar hannunsa suna hade ido ibaad ya balla mai harara dariya yay as alwys yace ok am sorry nasan i am alwys late toh muje mana liman
ibaad yay gaba kmr baiji shi ba yasaka kai suka fara sauka akan stairs
suna daf sauka yace 'kayi ma bappa flashing din kuwa? cikin gyada kai maheer yace eh nama sa zai samesu a masjid dama kuma jiya yace ince maka muna idarda sallan mujira sa yana da magana da mu,
ibaad baice komi ya gyada kai daga haka suka wuce hargate suka bude cikin nitsuwa suka nufi babban masallacin kofar gidan nasu wanda already har mazan anguwa sunfara taruwa, ganin isowar su yasaka wasu kara gaggautawa dan an saba ibaad ne yake jansu sallah kowani lkci dan
farawarsa karatunsa na medicine shiya saka bai samun time yanxu, daga sallan fajr sai na magrib da ishai kawai yake iya jansu maheer ne yafiye yin azhar da asr dake shi law yake karantawa yana ajinsa na biyu..ibaad yana tada kabbara aka daidaita sahu nan saiga bappa zaidun shima ya shigo adan gaggauce. acikin nitsuwa akay sallahn for gud 5 mins ibaad ya jasu aka kammala komi. wani tsohon malami ne ya danyi jan hankali akan yanayin rayuwa da mutuwa snn aka dan watse akabar masu azkhr, lazimi da karatun qur'ani. ganin bappa zaidu yana zaune yana jan carbi bai tashi ba yasaka suka dan jirashi agefe dansu jirashi snn su masa gaisuwar safiya,
bayan ya idar ne suka karaso kusa dashi suka samesa a inda yake zaunen kowannen su ya rusuna kai cikin ladabi yay gaisuwa cikin darajawa da girmamawa, bayan ya musu few question akan karatunsu ya kallesu duka sigar nasiha yace todai kunji abunda malam ya faɗa, mutuwa bata bar kowa ba, tsoho da yaro..kai ana iya haifar jariri ko minti daya baya karawa a duniya zai koma ga mahaliccinsa bare mu da Allah ya bamu dama muna raye dan mu bauta masa, cikin tuna wayar da sukayi da prof jiya yace" ynxu kune manya, kune zaku hade kan dukan yan uwanku kusani hannunku bazai ruɓe ku yanke ku yar ba. shi rayuwar duniya kamar bakonta ne, duk fushinmu da haushin mu da juna wata rana kwasam babu sallama zakuga mutuwa ya dauke wanin mu na har abada. toh dan haka duk a nitsu inaso kuma ku manyan ku daure ku karfafa zumunci a tsakaninku da yan uwanku snn ban cire kowa aciki ba
kai tsaye ya kalli ibaad yace ka dage da karatunka jiya professor ciroma yace nagaya maka cewa zai baka official call acikin group dinsa na young cardiology doctors sabida yaga practical points inka kana da enuf skills for basic medical first aid. unbehalf of you dai nace masa babu damuwa zaka shiga, toh bansan dai ra'ayinka ba. kan ibaad na kallon kasa ahnkli yace badamuwa bappa duk abunda ka yanke min ai shine daidai i will just wait for his call..cikin gyada kai mai cike da apfahari bappa yace toh masha Allah. toh kuje ciki, ni zan gaisa da makwabta kuje ku fara shirin schl kafin na shigo. kai kuma maheer ka tabbata kabi schl dinsu sultana kaji min meyene matsalarta dayasa bata gane lissafi...aladabce maheer yace toh baba
daga haka bappan ya mike ya barsu kafin nan suka taso suma suka kamo hanya izuwa gida.
tafiyar kurmaye suke sai can suna cikin tafiyar snn maheer ya tsinke silence din dacewa ohh i hate going to dat schl. ibaad dake kallon gabansa yace kabari saida muka bar gabansa snn zaka fada min? maheer yace "hmm kai bazaka gane bane innaje they will waste my time ne so why not kai kaje min, kaga dama sunfi tsoronka, da sauri ibaad yace 'no please kawai kaje din ni yanzu haka ma inada 7:40am practicals a lab kuma nagaya maka na shiga wani reading group i need to be der on time. sai dai shawara inkaje ka fara lura shin matsalar daga itace ko na duka yaran ne dan kasan sumtimes gane karatun maths depends totally in the method of the teacher..maheer yace alryt good idea. inde kuwa daga wajen malamin ne kaga dole ne anema mata lesson teacher agida...bt do u have any idea why baba yake mana magana akan zumunci? atakaice ibaad yace "i dont knw..nd i dont care to know..kawai de nasiha ce me kyau.
maheer yace hmm jikina yana bani akan kawu babba ne, can you believe dat jiya ya kirasa da daddare bayan mun gama kallon ball?
adan miskilance ibaad yace and how is dat an issure..
baki bude maheer ya kallesa yace "a sudden call from prof after 7yrs of snubbing him kace how is dat an issure? hmm duk uban abunda ke faruwa wallah bai taɓa daukar wayarsa ya kira baba ba sai dai inzai bada sako kaga ya kira uncle moh kai tsaye amma jiya kawai wai saigashi ya kira.
.."dan shiru ibaad yay snn yace ohryt maybe ure ryt, akwai dalili, amma kuma dama ai shine baison ayi zumuncin dashi, maybe ya dawo hayyacinsa kenan. cikin kyabe baki maheer yace oho, but i dont think so, naji de ance yarsa ba lafiya. bansan masa ba but anyway sha mu aidama bama fushi dashi..ibaad ya saki umm sai baice komi ba har suka bude gate din gidansun suka shiga ciki daga nan kuma kowa ya wuce dakin sa domin shiryawa..
ibaad yana shiga room dinsa ya ciro wayarsa ya kira mahaifyarsa suka dan gaisa snn ya mike ya gyara koina a dakinsa, he rake care if his room kamar ƴa mace, kominsa sai ya kal kale ya gyara tsaf ya share tass, he is a very very neat guy. within few minutes wajen yay fess kafin nan ya wuce wajen wanka within 20 min shima ya gama shirinsa cikin sky blue fitted long sleeve shirt, da wandonsa baki sai gogaggen labcoat dinsa da system dinsa daya zubasu a jakar baya.
as usual he look mr neat and breath taking dake komi ya saka ajikinsa tana masa kyau dake Allah ya bashi kyau ne me daukar ido da hankali, 6:49am ya nufi kofa yana baza ssnyar qamshin turarensa na original dior souvage mixed with creed aventus na smart collection wanda inya wuceka dole ne zakaji kamar kabishi ka lasheshi..
yana kammala daura agogonsa ya bude kofar room dinsan zaii fito kenan yaci karo da cousin dinsa sultana, she is fair and slender a shekaru ita kusan sa'a ce da inayah, da plate din abinci a hannu ta taho suna haɗe ido jikinta yadan fara rawa, cikin rike nunfashinta a mugun tsoroce tace "ina kwana yaa ibaad, .kallo daya ya mata snn yace "ke lafiya? muryanta na rawa rawa tace uhmmm dama mummy ne tace inkawo maka abincinka daki
saidai tay 2 mun yana kallonta har saida jikinta ya tsananta ɓarin sai baice mata komi ba anitse ya saka hannu ya karbi abincin baiko damu ya bude ba cikin sauri yaga zata juya yace "sultana..da sauri tace na'am. daga ido yay ya kalleta yace next time aka baki abinci ki kawomin just use d landline nd calll me zanzo na dauka dakaina..da sauri sauri tace toh yaa
..tana juya kusan cin karo da maheer tay duk basu san ma yaushe ya iso ba a mugun tsorace ta kalleshi shima tace "sorry yaa, gud morning, da kallo maheer yabita yace morning, uban mikekyi anan .
cikin nunfashi tace ai mummy ne tace na kawowa yaa ibaad breakfast dinsa nayau anan..
cikin katseta yace 'what?..nikuma ina nawa abincin..
tace ya na kan dinning ai tacema ince maka ka sauko kasa yanzun nn zamuci abincu.. yace its alryt, jeki ina zuwa..tana barin wajen ya karaso wajen da ibaad yake tsaye da plate ahnnunsa looking confuse yace dude did you tell her dat u want to eat alone??
cikin kyabe baki ibaad yace 'nop, but its fine..
maybe she have a reason
.. maheer yace wani reason? bayan baba ya sha hanata saka maka abincinka daban, we are all suppose to eat on the table..kawai kazo muje
a dan shashance ibaad yace "maheer, let it go, i am not even hungry sauri nake zan fita. cikin share sa maheer yace "kajika kuma amma ai zaka taɓa abincin koda kadan ne, ban plate din bari inga meye ne ma aka dafa mana, kafin ibaad ya hankara maheer har ya saka hannu ya kwace plate din yana budewa yabi ya fidda idonsa waje in shock ganin walakntcen dumame ne na miyan busashen kubewa daya kwana a fridge ya fara sakewa bama agidansun akai ba, wanda ta aika ne jiya aka bata daga gidan matar me gadinsu maman ummi
..atake maheer ya dago kai cikin yatsina fuska yace "what d hell is this ibaad??
ibaad yay rolling idanunsa a mugun miskile yace "tuwo, dumame." maheer yace oh fuck it..am not eating this, this shit is smelling awful..anya ma an dumasa da kyau kuwa
amma ai dazu naji ana soya irish ko ce musu kay bakaci??..ibaad ya masa wani irin kallo da alaman baison yama amsa wann maganan ahnkli cikin nemn wakansa nitsuwa yace "guy pls i need to take my leave, inada practicals karnay latti, kawai bani abincina ka kara gaba, zan kai na aje inna dawo inci. da wani irin ƙarfi maheer yace noo you cant eat dis
..baridai naje na nuna ma mummyn hala kuskure akayi kode abincin me gadin ne sultana ta dauko ta kawo maka" ibaada yace "ohh toh inme gadi zaici ainima zan iya ci kenan, just give me."cikin zare ido maheer yace "no, i wont,this isnt ur food". yana gama rufe baki sai ganan bappa zaidu ya iskesu tareda binsu da kallo yace what is going on here..da sauri ibaad yace babu komi bappa, da sauri still maheer yace baaba abincin me gadi fa aka kawo mai as breafst shine nace ko mummy tay mistake ne ta aiko nan
da mamaki bappa zaidun yace "abincin me gadi kuma? let me see it,
maheer baiyi kasa agwiwa ba ya mika masa yana satar kallon ibaad dake harararsa da gefen ido, bude abincin bappa zaidu wanda atake yaji ransa ya mugun baci ya dgo ya kallesu duka yace waye aka aiko da abincin nan?nd why did ur mother sent the food here? dama ana kawo maka abinci..kai ibaad banace maka kowa yanacin abinci a table ba"
ibaad ya sauke kai kasa ahankli yace "kafada, a mugun dake bappa zaidu yace "so, what is this nonsense then? ahnkli maheer yace baa dama sultana tace mummy ne ta aikota ta kawo masa nd she had been.. ransa a bace cikin katseshi. yace enuf, just go nd call sultana here my friend.. da sauri maheer yace yess, snn ya sauka kasa bappa ya kalli ibaad yace kai kuma ka wuce dinning table yanxun nan bana son naji wani magana, cikin ladabi ibaad ya amsa da toh snn ya sauka kasa. bappa zaidu baijira ba kawai yabiyosa kasan da plate din abincin a hannunsa, kusan lokci guda suka isa dinning da ibaad suna kkrin zama saiga ammi babban ta fito jikinta sanye da wata doguwar riga A shape ta atamfa a hujajan ta doso falon sultana nabin bayanta adan tsorace
wanu dan uban hade rai tay tana cewa uban waye yake neman sultana, toh nina aiketa gani nan sai agayamin lefi na. ina shi ibaad din dayake neman ta in dukanta ma zaiyi gani nan saiya fara dani..
tagama furta hakan kenan zata sharo kwana caraf suka hade ido da bappa zaidu wani rasss taji gabanta ya tsinke ganin irin kallon dayake mata gabaki daya sai taji ta mugun tsorata da tarin kwarjinin dake cikin kwayar idanunsa sosai...
atake ta sauya murya kmr ba itace ke zuba masifa ba amakirce tace sallam alaikum, ibaad dakansa ke kallon kasa ne kawai ya amsa bappa zaidu baiko amsa taba, ta taho da rawar jiki yaa zaidu ashe har kafito, jikinta na rawa rawa ta dau serving spoon tafara bude warmers tana murmushi" abbansu, ai bansan kai ka aika a kira sultana ba toh baridai na xuba maka abinci..
wani irin shareta yay fuskarsa a mugun dake cikin hakimcewa
yace ke sultana zo nan..
kafafun sultana harna hardewa tazo gabansa ta dan rusuna tace gani nan baaa.. yace daga yau sai yau..karda ki kara kaiwa yayanki ibaad abinci a daki saidai in shine yace akai masa can bare ma na soke dokar cin abinci a daki, once is family time for breakfast lunch or dinner dolene kowannenku ya fito aci abinci atare
duk randa na sake jin an aikeki kin kai ma wani abinci during family time saina miki shegen duka..
hawaye na zubo mata tace toh baba kay hakuri dama mummy ne tace saina kai masa,..baice mata komi ba yace kindai ji abinda nace miki ko??? tace eh baba. tashi ki zauna kici abinci karki lattin schll. jikinta a sanyaye ta miƙe tazauna kusa da yaa maheer dinta tana share hawayenta sabida tana mugun tsoron fushin babanta..
basu kara cewa komi a table din ba suka fara cin abinci kowa ya share ammi babba.
..wani irin borin kunya ne yabi ya rufe kwayar idanunta taja wani irin tsaki zata bar wajen a fusace...wayar ibaad ne yay kara ya dan duba yace
uhmm bappa, ana jira na wajen practicals its urgent.
bappa zaidu yace its okay
..amma kaci abincin kadan. yana furta hakan ya juya ta kalle ammi babban kamar bada ita yake magana ba yace "ke raihanatu saiki gaggauta kiyi packaging masa breakfast dinsa a wani abu dazai wuce dashi school dan suna da important practicals da safen nan.
juyowa tay ta kallesa jin datay kamar zuciyarta zai tarwatse dan zafi, kasa motsi tay har saida shima ya juyo ya mata wani irin kallon sama da kasa snn ta kama kanta ta wuce kitchen ta dauko karamin food flask, abincin gaban ibaad din ta saka hannu zata dauke awalaknce ta juye masa aciki, bayabo ba fallasa cikin katsetsa bappa zaidu yace "wai meye haka ne kam da Allah. karkisa masa wnn da alredy ya fara ci yayo sanyi, just get him fresh ones daga warmers.
ranta a mugun dagule ta jawo warmer din ta bude tana deban irish da fried egg din rabi yana zuba akan table dama kuma gashi iya su familynta kawai ta dafa musu breakfast yau banda ibaad a budget dinta shisa ma ta duma masa tuwonsa daban..wanda ya ragen zataci shi ta zuba ma ibaad din dan kadan a cooler tana ajewa kuwa bappa zaidu yaja tsaki ya dauki sauran irish din dakansa ya juye masa duka saida coolern yacika tam snn ya mika wa ibaad baiko kula kumburin data keyi ba, cikin gyaran muryan yace ibaad maza tashi ka amshi dayan key dina na camry a wajen adamu driver kaje makarntar.
ibaad yamiƙe tsaye jikinsa a sanyaye yace nagode bappa..toh sai na dawo.. bappa ya gyada masa kai..ya juya ya kalli maheer sai yaga yana masa murmushi, jakar sa ya saba abaya zai dau food flask din yafice
ammi babba ta wani irin bangajeshi ta wuce kamr zata haura sama can kuma sai taji bappa zaidun nacewa yawwa ibaad namanta ma nagaya maka ka shirya zuwa jibi da yamma kaje can nasarawa extension ka same kawunka yana nemanka agidansa..just you.
wani irin faduwa gabansa yay amma bai nuna a fili ba yace toh in sha Allah zanje, saina dawodaga haka ya fice...
da wani irin gingimammen feeling na rawan jiki me cike da son jin gulma ammi babba tay maza ta dawo kan dinning table din tafara bambamin karya murya kasa kasa tana cewa abbansu to ni me zanci kabi ka dauka abincin duka ka bawa danka ya tafi dashi..
da kamar bazai kulata ba can ya mata kallo daya fuskarsa ba asake ba yace ga can dumamenki ai sai kici.
cikin yatsuna fuska tace Allah ya kiyaye Duk salon anuna min bani da gata ne zaa ce min ga dumame..ai dake masu gata ne agidan har kira na musmnn suke samu daga kawu babba..
a dake ya kalleta yace
"duk dai babu ruwanki da wann. ashe dama dan kinuna masa baida gata kenan kika aika masa dumame not after i specifically told you banason ana rabamin kan yara na...
wani irin bori ta tayar toh ni faɗa zakamin agaban yara its seems like nobody respect me in dis house... cikin katseta yace dont talk abt respect
bayan idan na fadi abu jira kawai kike na bada baya ki canza shi. kina hauka ne zaki raba mana abinci shikadai ki aika masa wani walaknccen dumame da ko karen gidan nan bazai iyaci ba..how will u feel in danki ko yarki ake ma haka?
ransa a mugun bace yace maheer how long has this been going on karka ka sake kamin karya
adan tsorace maheer yace baba wallah ban taɓa lura ba saiyau saidan in sultana dake ita ake aikawa
tun kan ya juya ya kalle sultanan ta fashe da kuka "baba infa baka nan ne suke abunsu da mai aiki ni wallah bantaba kaima yaa ibaad abincinshi daban a daki ba saidai atambaye sadika me mana aiki ai ita tasani.
a mugun hatsle ammi tace ke wallah zanci ubanki
kikamin sharri agaban babanki, ashe baki da kunya sultana?
rai ahade bappa zaidu yace raihanatu dont provock me, snn karki ma yarinyata tsawa agabana dan ta fadi gaskiya
cikin kukkuni me zafi tace ni fa yaya biyu kawai na haifa, kaga kuwa dan na manta dan wata acikin budget ina dole ne insaka masa nasa daban daga abunda ya sawwaka, yaron nan fa yana da uwarsa acan toh yakoma gabanta ya zauna mana inyaso sai tadafamai duniya a bashi yanaci nide bazan kashe kaina akansa ba, in de dan dumamen ne danayi kkri na taimaka nabashi ya baka haushi to Allah ya huche zuciyarka.. ai kasan abunda kakeyi sarai, haka kawai dai bazaka fifita dan wata banziya akaina ba.
tana fadin hakan ta mike da sauri ta wuce sama ranta a mugun bace
bappa zaidu yabita da kallo..cikin lumshe ido da budewa yace Allah ya kyauta. the tablw was quite for a moment sai can snn yy karamin nasiha ma yayansa akan karda su biye ma uwarsu suki zumunci, saida duk suka nuna sun fahimceshi snn ya sallamesu suka wuce makaranta..
wani irin makokon baqin ciki da haushi mai tsanani ne ya turnuke ammi babba kasama zama tay a dakin sai safa da marwa take tsakanin corridor da corridor tanaji tsanar ibaad din na kara ninkuwa aranta bana kadan babu kalar abunda bata raya aranta ba, can sai ta wuce daki da sauri ta dau wayarta kusan bugu ma uku sai aka dauka
atake take ta sauya murya izuwa na makirce tana maganan tana dan jan girma "wa alaikis salam safeera, Allah sarki na katse miki baccin safenki ko?
dagata dayan bangaren anty safeera tace bakomi ammi babba ynxun nan na dawo daga raka mijina zaije aiki
"Allah sarki..toh ya gidan naku..ya mijinki ya yaranku.. anty safeera tace duk lafya muke dama ammi karamace kawai bataji dadin jikinta ba..
yi tay kmr bataji hakan ba cikin sharewa tace "uhum kinajin labarin antynki kuwa? ina nufin hajy hamida shettima ..anty safeera tace a'a, amma dai naji ance yarta zainab arifah bataji dadin jikinta ba so bana tsammanin ma zatazo wnn wkends anjima dai nake so na kirata inji ya jikin.
tace ohhh ayyah hala ko shine dalilin dayasa kawu babba yace suna neman ibaad agidan, did she say sumtin abt him to them? ko har sun amince zasu bari ta kulla soyayyan ne dashi, hmm amma da abun baiyi ba..
adan mamakance anty safeera tace ahh toh gaskiya nide bansani ba amma kinsan abu me wuya ne dama su hanata abunda takeso..
wani irin zafin tsana da kishi me tsanani ammi babba taji na tsagawa aranta, tay shiruuu, san can sann taja nunfashi adan dakile tace hmm toh Allah ya kyauta..nidai nake xaune da yaron nan nine kuma nasan halinsa, inda ace zaku nemeni shawara ta danace muku karda a sake abar zainab arifah tay wannan mummunn zabin makanta..wallah yaron nan baida mutunci kigadai mugun bugun daya ma zainaba ranar gashi da girman kai sam baida kunya ko kadan
anty safeerah tay shiruu batace komi ba sai can tace yanxu dai bani da tacewa ammi babba kisan dai kawu babba ne keda ikon yanke duk wani hukuci akan yarsa amma in har anty hamuda ta neme shawarata i will try nd talk to them
cikin washe baki ammi babba tace toh ai shikenan bakomi, pls inkin kira kinji jikinta saiki gaya min snn ki gaida min hajy kice ina mata fatan alheri.
anty safeerah tace toh ammi mungode da gaisuwa duk dai abunda ake ciki zan taɓaki
...murmushi tay tace toh kardai ki manta nagode safeerah agaida yara insun dawo.
daga haka suka katse wayar..anty safeera bata kawo komi aranta ba duk dama tasan da cewa abun ammi babban harda zafim kishi da tsanar datakewa ammi karama aciki, deep in her heart tasan a nitsuwa da hankali da kyau da komi ibaad yafi karfin ya aure zainab arifah nesa ba kusa ba. infact banda gata da arzikin da ubanta yake dashi da ko kusa da ibaad akace tazo bazatazo ba. saidai bataga lefin ammi babba datake zafin kishi da ammi karama ba, ammi karama is almost perfect ga kyau, ga kamala, nitsuwa, ga kuma ilimi, itama kanta safeeran bata kaunar kalmar kishiya bare ƴayanta. kai kaf duniyan nan ma babu wani abunda ta tsanaji kamar batun kishiya. ji take ranar da uncle moh ya ce zai mata kishiya toh ranar zata iya kashe kanta kota kona gidan gabaki daya.
fannin su inayah kuwa yauma suna idar da Alwala a bore-hole din makaranta tadan miƙo tattausan hannunta tariko kyakkwan fuskar ayanah tanamai sakin sassanya kuma nakasshiyar mrmushi mecike da tsumayi wanda yake saurin fallasa wann dumbin kaunar datake yima yar uwantan aranta.
ahnkli tahau gyara mata zaman dark green hijabinta dakema ayanahn tana da yololon ɓakin suman gaban goshin mai hade irin wani kwantaccen shatin saje mai daukar hankali wanda yake yawan nunawa a fili sosai, idanuwanta masu cike da nuna kaunar da take mata ahnkli take fmr cusa suman ciki tana cewa "Ayaana am, Idan wata rana kikaji sanyin ruwa ko iska me sanyi tana busawa, har kuma tashafi gashin kanki, ki sani ina nan kusa da ke."koda ace ranar bana numfashi soyayyata zataci gaba da zagaye ki, "koda ace bani da murya,
addu’ata zata rika zuwa gareki tamkr yadda iska yake riskan ramin hancinki ayanzu, inaso koda bana nan a duniya kicigaba da kulamin dakanki, ina sonki sosai anayo am kinji ko??.
..ayaanah data zuba mata ido ta dan kyalyale da dariyar yaranta "addana ina sonki nima sosai ai bazamu taɓa rabuwa ba har abadan abada ko mutuwa zamuyi tare zamu mutu..bakiga duk kika tashi a bacci cikin dare kina ciwo nima sai natashi sai naji zuciya na yanamin ciwo ba?yo duk inaa kikaje aduniyan nan saina biki shiyasa ma Allah yayimu mu biyunmu awajen ummanko ko??
ahnkli inayah tay mata dariya me sanyi ta gyada kai sai batace komi ba..
..kusan duk rana sukan yi ire iren wnn maganan shirmen atsakaninsu amma dukansu basu taɓa daukarsa akomi ba inayah ne kawai takeji ajikinta da xuciyarta kamar dai wani abu nadaban xai faru da ita.
washe gari shine ranar da zasuyi papernsu na karshe sassafe tun kan akira sallahn fajr inayah tafarka jin jikinta ya dau zafi sai kuma taji cikinta na kugi kusan aguje tawuce bayi tayi zawo sosai sai snn taji dan dama dama
saidai tunda ta fito wani dan uban kasala ya sake rufeta, ko yar dauriyan nan yau takasa yi sabida tunda tay zawon kasalan yabi ya dameta ta zama bata jin karfi ajikinta ko kadan. yau ko abincin safen ma bata ji sha'awar ci ba, haka hanklin taawure yatashi sai kawai ta ɗeba mata fura da nono a gora akan idan tay jarabawar sai ta zauna tasha tunda jarabawar karshe ne anatashinsu da wuri..
tace daga antashesu yau suje kasuwa su zauna a shagon hajy mairo har saita dawo daga saida nono ne zasuje chemist abawa inayan maganin zawon daya jawo mata wann kasalan yau da safe
ahaka suka rabu kowa ya fita sana'arsa amma hanklinsu nakan inayar, dake gabaki daya yau ciwon yaki sam ya ɓoye kansa, kusan a daddafe ma tay jarabawa dama kuma shine mata na karshe, tagama firamare kenan, ba a wani bada wani kyauta a schl din amma ita sosai ta samu kyautar jinjina daga wasu malamai musmmn ma na lissafi, wasu suka bata kudi naira dubu biyar, wasu suka bata littafai da jakan baya, wani dan nysc har na tunanin biya mata kudin zuwa private scndry schl a cikin garin kano sabida aganinsa bai dace dumbin ilimin inayahn ya tafi a banza acikin kauye ba.
duk da ciwo na cinta aciki haka ta matse tay musu godiya, ta kuma nemi yafiyar kowa aka rabu cikin lumana da ita, ayanah na rike da ita duk inda zataje sabida wnn dan uban kasala da zafin datakeji ajikinta har yanxu.
ahnkli ahnkli suke tafiya manne da juna, but is like every few mins jikin inayahn ke dada sacewa karshe ayaanah ta nema musu wani gindin bishiya ahanya suka zauna dan ta samu hutu tay catching breath inta, suna zama ayaanah ta ciro goran nonon ta girgiza ta bude mata hankli a matukar tashe tace "tashi kisha wann adda koda zakiji karfi..tana faɗa tana kai mata baki.. idanunta duk yay jazir da damuwa aciki.
kurɓi biyu zuwa uku inayah tay sai taji gabaki daya taste din nonon yana ɓata mata rai sosai dan haka kawai ciwon yake sawa taji ta washi cin abinci ko shan wani abu gashi kuma matsanancin yunwa takeji. magiya ayaanah ta dingayi mata amma taqi sam takara kurɓa, can sai ga wani dan yaro almajiri yayi futu futu rigarsa duk ta yi dukunkun baida takalmi ga mtsnancin yunwa ya galabaitasa tsabar layi agigice ya zauna akasa snn ya riƙe cikinsa yana nishi daga ganinsa kasan yunwa yakeji bana kadan ba. ganin wann almajirin ne yasaka inayah ta mance da nata yunwa ta kuma dawowa cikin hayyacinta babu shiri cikin dauriya ta miƙe tsaye ta isa gareshi da gorar furan ta miƙa masa tace mai yasha kusan a gigice yaron ya karba muryansa da jikinsa na rawa rawa yana mata godiya yakai baki ƙwad ƙwad yafara gwankwadar lafiyayyen nonon like his life depend on it har saida ya shanye tass, ya daga ido ya kalli inaya yace "Allah ya saka miki da gidan Aljannah
ayaanah na kkrin yin mgn ta tsareta da ido tana murmushi ahnkli tace ameen, yaron ya tafi,suna wuceshi tace ma ayanah suje can kasuwan kawai sujira taawure inyaso awajen hjy mairo zata nemi wani abunda zataci. hakan yasaka ayanah jin dama dama aranta sabida tasan yunwa na damun addanta sosai amma kuma sau taga bata iyacin abinci
suka rike juna suna tafiya ahnkli ahnkli har suka kai cikin kasuwa, as usual babban shagon hajy mairo me tuwon acike yake tammm da customers ana shige da fice ga qamshin abinci kala kala yana tashi takoina, ta kofar baya suka shiga suka sameta a inda take yawan zama, dake kamar kaka take awajensu suna gama gaisheta maza tasaka aka kawo musu lafiyayyen abinci shinkafa da miya da ganye akai wanda sun fara ci kenan still inayah ta dau rabin nata ta fita waje taje ta bawa wani mai daƙo da yunwa ya mugun galabaitashi ya daure cikinsa da tsumma ya jingina akan wheel barron sa awaje har ya kasa motsi.
anan ma koda ayanah tamata magana akan meyasa ita bataci abincin ba tabashi, saidai tay murmushi tace mata sudin sunfita bukata ne shiyasa take basu. bare ma awajenta ai ciyar da wanda bai dashi yana ɗaya daga cikin manyan ayyuka mafi soyuwa awajen Allah ta gwammaci hakan akan komi.
bayan sun tattauna kaɗan akan hadisai da kissoshi tareda ayanah wani irin bacci ne ya dauke inayan batare da taci wani abincin kirki acikinta ba duk da uban yunwa dake damunta aranta, ayaanah kuwa tuni tamiƙe tawuce wajen hjy mairo mai tuwo ta zauna tanata kallon yadda ake shige da fice tareda hada- hadan abinci dakema sunfi shaƙuwa sosai tafiyeson balbale hjya me tuwo da surutai na yaranta....
sallah ne kawai ya taɗa inayah wajen yin tsarki hakanan ta amayo da duk wani abu data saka acikinta batare da kowa yasani ba, gashi dakyar take tsugunawa kasa tsabar ciwo da zafin da cikinta yake mata, koda ta fito sallahn ma yau addafe tayishi can da yamma liss sai ga taawure ta dawo shagon hajya mairo ta debesu suka wuce chemist direct akay ma inaya gwaje gwaje akace musu wai typhoid ne, haka aka siya ma inayan wasu magani tana sha kuwa tadan samu relieve har kamar ta warware, a kwana na ukun da yamma suka shirya tsaf sukay sallama da hajiya mairo me tuwo da sauran mutanenta, taawure ta debi fiye da rabin tarun kudin cinikinta ta zuba a asusun hajya mai tuwo akan idan hutu yakare daga sun dawo za'a nemawa inayah makrntar sekandari tadan fara kafin mijin aure ya fito amata aure. bayan hakan ya kammalu wajajen 4:30pm na yamma suka kama hanyar komawa gidansu acan kauyen majiya da zimman sai hutu yakare snn zasu dawo.
ba su da isa garin su ba sai wajajen karfe 6:30pm dake akafa suka taƙa, kafin sukai gidan nasu gabaki daya inayah ta zama wani iri tafiyar da suka kwasa sosai ya motsa mata da ciwon cikinta,still maganin dasuka amsa a can chemist taawure ta kara bata hardai ta samu tay sallolinta yauma ko abincin arzkii bataci ba ta kama bacci, can cikin dare kwasam ta farka da amai, da zazzabi me tsanani kumburi da taurin cikin nata kuwa sai karuwa dayayi, duk sanda tay numfashi ko tari zafin datakeji acikinta ya tsananta sosai da sosai.
kafin kace wani abu inayah tafara ficewa ahayyacinta tun abu na wasa wasa har maganin chemist ya ƙare amma basuga alaman sauƙi ba gashi sunriga sunbar tudu bare ma su je asibiti.
ganin basuda mafita da safe taawure tafito tasame su awaje akan tabarma, ayaanah tana fifita ma inayah dake kwance riƙe da cikinta cikin azaban ciwo da murkususu wanda ruwama ynxu da kyar take iya shansa sai nishi kawai take da juye juye.
cikin ran taawure cike da fargaban yuwar dawowar mijinta any moment saidai duba da jikin inayah yasa kawai ta runtse ido ta saɓi mayafinta da karfin zuciya tana fitowa tadube yaranta dukansu abun tausayi muryanta kasa kasa ahnkli tace shannu innari dakyar inayan ta dan dago ta kalleta
..zuciyarta sosai yay rauni sosai dataga inaya bata ko iya amsa magana saidai ta dan dago idanu, cikin jan ajiyan zuciya tace "ayaana ki kula da yar uwarki ni zan gudu gudu inje tudu na sake karbo maganin ciwon innari wajen likitan nan na tudu tunda jikintan yaƙi yin sauki..
ayanah ta share guntun hawayenta ahnkli tace "toh saikin dawo ummah addana batako iya magana kiyi sauri jikin nata yana kara zafi.
ko gama amsata taawure batay ba sukaji kakkausar sallama akansu wanda saida yasaka zuciyar taàwure ya tsinke sabida jiyo muryan mijinta juma datayi, ayanaah kuwa tuni taji hanjin cikinta yana kaɗawa sabida balain tsoronsa data keji, inayahr ce kadai bata bude idanunta ba dan banda nishi bata iyayin komi..
fuskarsa ba a sake ba ya shigo cikin gidan ganinsu cirko cirko a tsakar gida ga innari akwance akasa akan tabarama kamar ruwa ya kwasota yasaka ya mugun hade ransa kamar ma ɓe taba murmushi a duniyar nan ba..
taàwure ta kalleshi da karyayyen zuciya ganin ya zuba musu idanu mecike da tuhuma sai tay sauri ta taho gabansa domin ta amshi jakar dake hannunsa wanda tunkan ta karaso ya tsime tare da daka mata tsawa yanamai cewa "Ke da Allah. Dakata min awajen. ya dada haɗerai yanamai kare musu kallo"wai meke faruwa ne na ganku haka a tsakar gida cirko cirko? kuma ina kike nufin zakije da mayafi ajikin ki batare da izini na ba. kafin ta bude baki cikin masifa yace "ikon Allah wato abunda ake yawan gayamin akanki gaskiyane, dake da yaranki duka baku da tarbiya daga nasaka kafa nabar garin nan dandalin bushasharku kawai kuke buɗewa kina yawo kamar wacce bata da aure su kuma kmr wanda basuda uba, duk kinbi kina zubar min da mutuncina a garin nan ana gulma na akanki keda ƴaƴanki, toh wallh taawure nafi karfinki, karyanku yakare tunda na dawo gidana kuma da cikinki na dawo, zan nuna muku cewa ni juma, tsayyayen namiji nake agidana kowa cikinku sai ya gane kurensa agidan nan.. mtss yaja tsaki daga fadin hakan ya kama hanya yawuce turakarsa fuuuu ransa a mugun zafafe.
kallon bayansa taawure ta dingayi cikin rasa nacewa
jikinta a matukar sanyaye ta dawo jikin yaranta da suke zaune akan tabarma itama tazauna tay wani irin tagumi shiru ne ya ratsa wajen banda nishi nishin inayah babu abunda ke wulgawa, can cikin tunani taawure ta miƙa hannu tajawo sauran ruwan maganin zazzabi data jikashi acikin kwarya ganyen rai ɗore ne aciki tana kokarin bawa inayar abaki sai kuma taji jikin inayar yay mugun zafi harma fiye da kima.
hankali atashe ta tallabota ayayinda taji jikin inayar yafara mild convulsing kusan koinanta yana rawan ɗari, zanin inayar atake yadan subuce gefen cikinta na dama inda ya kumburo sai yay kamr wani babban kurji ne acikin nata.
a mugun tsorace taawure ta kai hannu kan kumburi zata taɓa taji meyene tana tabawa kawai inayah tay wani irin gigitacen ihuuu saida dukan su suka rude sukaja baya suna salati me ƙarfi
rawanin juma a hannu ya fito daga turakarsa a mugun razane shima kusan arude yana cewa wacce yar kafurar ce take mana ihu acikin gidan nan waye..waye waye me ihun nan...yan iska kawai marasa tarbiya da imani mutum ya dawo gidansa bazai huta ba kenan wata shegiyar yarinyace tay ihun nan inci ubanta.
da gudu ayanaah taje ta kara rungumar inayah tareda fashewa da kuka me tsananin rauni wanda kukan ayaanahn ne ya dan katseshi,taawure tay sauri tarufe kumburin cikin inayan da zani dan karma juman ya gani yayi musu wani fassara na daban dan talura kamar ransa a mugun baçe ya dawo daga boda.
#surayyahms
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[27/10, 19:43] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️8️⃣
juma yana gyara tsayuwarsa yace...
"Dabbobi ne agidan ina tambayarku kuna min shiru?
araunace taawure tace megida dama jikin innari ne babu dadi tunda muka dawo daga tudu yau kwanan mu uku kenan tana zazzabi..
wani irin yatsina fuska yayi cikin katseta da zafin kai yace "toh sai kuma me? akanta aka fara zazzabi ne?yo akan dan wnn ciwon zazzabin shine har zata daka min irin wann ihun jahilcin acikin gidana yo uban waye yasaka mata ciwon inba iskanci da sakacinku ba, nide wallah kar a sake min ihu agidana. ku karata tacan da abun kunyar ku ai da ɗa namiji kika haifa min da bazai zamo rago har haka ba. sai a zauna ana ihu akan zazzabi? _Ko waata nyiɗi, ɗum yoɓa wuro.”_
yana gama maganar sa still yaja musu tsaki a mugun zafafe ya kuma wucewa ciki lokcin kuka inayah da anayahn sukeyi rungume da junansu abun tausayi...
ayaanah bata taɓa ganin addanta cikin wann yanayin raunin ba sai gabaki daya zuciyanta itama ya fara mata ciwo amma take kkrin daurewa sosai danso take ta koya ma kanta jarumta..
tun bayan faruwar wnn hatsaniyar taawure ta kasa xama dan ko kaɗan bata iya ganin yaranta acikin rauni suna kuka gani take dolenta kawai ta neman musu mafita, acike da jarumta ta miƙe tabi bayan juma cikin turakarsa ta samu har ya gama warware jakansa yaciro kayansa mararsa nauyi daya saba sakawa inzai dan fita majilisansu na dattawa a kofar sarkin buzaye inda kowani gida ake kawo kwanon abinci aci atare. sanin cewa tunda aka haifo ayaanah aka dena cin abincinsa a majalisa ke dada bata mai rai, sabida al'adar kauyen ne inhar duk gidanka mata ne toh andena cin kwaryan gidanka kenan har sai ka haifi namiji ko da guda daya ne. ya dawo daga boda da tsananin fushin sanin kayan abincinsa bai kare ba, gashi yana so ya fita yabar musu gidan yadansha iska acikin mazaje, shikansa inya tuna cewa duk gidansa mata ne sai yaji wani makokon matsanancin bakin ciki ya ƙara rufesa.
taawure tana shigowa tun bata masa magana ba ya bita da wani irin kazamin kallo na tsana, bata damu tadan rusuna agabansa tafara rokonsa koda zai bata izini taje ta nemo ma yarsu innarin maganin zazzabi, cikin magiya tace masa na asibiti yafi ci dan tsabar ta damu batasan ma ta furta masa haka shaf ta mance cewa ya haramta musu ambatar asibiti agidan sa....
shiru yay yana jinta face har saida ta ambace asibiti yaji bazai iya daurewa ba,wani irin harquka yayi Ya sare sanda ya buge bango tare da yin tsalle yace Weehoo…taawure ni kina gayen kalmar asibiti Kangon kafuraye?? Taáwure, anin k’ombon ma yanka....
muryanta na rawa rawa jin ya soma cewa wuyanta yakai na yanka a mugun tsorace" a'a mai gida lafiya nake niman wa innari.. da karfin rauni tace _Jikko on wondi sokka, ɗum no feere magani ganya walaa ɗum waɗa._ nufinta Jikin yarta ya yi zafi sosai, wannan ciwo ne mai tsanani maganin jeji ba zai iya warkar da shi ba.
wani irin ja idanunsa yay ya ɗada murza sandansa tsabar bacin rai jikinshi na rawa bakinsa har na tara kumfa ya nunata da shi yana cizza labba yace “ _Wallahi, miɗo yoɓi maaɓe, on no wala ndiyan...”_
da mamakin jin yace zai ci ubanta ta budi baki kenan zata amsashi ya rufeta da wata harzukakn duka
yanayi taawure ta saka ihu tana neman tsira amma yabi ya shaƙeta kamr zai kasheta ayayinda yaransun suke jin abunda ke faruwa duk jikinsu ya dau rawa anayah tafara kuka me ƙara.
wani irin kukan tsoro sukeyi suka rungume junansu suna kiran umma umma umma
duk da acikin zafin ciwo inayah take amma wani irin ɓari jikinta ykey tamkar mazari yanayinta me cike da zafin rai da zuciya sai cixgewa take tana Allah Allah ta iya koda miƙewa ne tsaye koda da ja da gindi ne jitake za taje takarbe uwarta, saidai ganin ciwon ya hanata koda motsawa na da can yasa tayi ihu me karfi lkcin numfashin ta sama yayi kamr zai dauke jin irin dukan da ubansu yakey wa taawure aciki kamar ba mutum ya samu ba, kuka suke suna kirar taawuren gashi basuda makwabta sune karshen gari daga dabbobinsu sai gonayen su
kamar daga sama ayanah tasake kirjinta data damqeshi tamiƙe tsaye arikice kuma a zuciye kusan idanunwanta a rufe tana kiran sunan ummanta da wani irin zafin zuciya me radadi abunda bata taɓayi arayuwarta ba sabida kowa yasan ayaana da rauni.
yauda dan uban gudu ta tsallake inayahn dake kwance tana nishi ba acikin hayyacinta ba takai zuwa kofar batajira ba kawai ta fanjama cikin dakin baban nasu da dama bata taɓa shiga ciki ba
tana shiga ta faɗo kan jikin taawure ta riƙeta dam dam tana wani irin razanannen kuka tana cewa...
"Baba no ɗuka umma maa! No waɗa umma maa. babaaa.. babaaaa no ɗuka umma..
sanadiyar kanannede taawuren da ayaanah tayi tana kukan cikin firgici yasaka juma ya hakura da dukan ransa a matuƙar bace ya dau rawaninsa ya dora bisa kansa jikin shi harna kyarma muryansa tamkar tsawa ya dube su duka yace falmata Wann ma kadan kikakga gani tunda rainin ki har yakai in saka doka agidan nan ki taka. dama can ana gaya min cewa na sake miki dayawa bansani ba saiyau dakike neman ki nuna min kuskure ne toh wallh baki isa ba. in kuma kika kara ambatar wani asibitina kafuraye agidana saina hallakaki daga ke har yayan naki dama ba amfanin komi kuke min ba banda kuci kuyi kashi. kai bari ma ingaya miki,' daga yau sai yau idan kika kara ficewa agidan nan abakin aurenki..shashasha mutuniyar banza mutuniyar wofi
daga haka ya saka kai ya fice baiko lura da inayah dake kwance awajen cikin tsananin murkususun ciwo kukan zuci da gushewr hankali ba.
ranar taawure tay kuka ranar bana kadan ba har sai bayan da abun ya lafa musu snn ta daure ta aike aayanaah jeji ta dan debo musu wasu ganyen ta aje kurkusa duk baqin cikin dake ranta haka tazauna tayita hadin maganin gargajiya ma inayah tana bata tanasha tana amai har dai zafin jikin ya sauƙa.
kwana daya bayan haka yasakance Yaune bappa zaidu sukay da ibaad akan zai kai ziyara da yammaci izuwa gidan su zainab Arifah, abun ya mugun tsaya ma ammi babba a wuyanta anma shi sam abun be wani ɗarashi ba, shide aransa yasan umarnin bappa zaidu kawai yake bi .
yau tun bayan sallahn asubahi ibaad ya dawo dakinsa yana ta rera karatun qur'ani for almost 50 mins ya dauko tundaga kan suratul ma'ida izuwa suratul taubah cikin hadda, bayan yagama ne ya dau lokaci sosai yanaima mahaifinsa adduar samun rahma a kabarinsa,snn yay ma mahaifyarsa adduar samun lafya da miji nagari, yayima da shikansa kafin yay ma sauran ahalinsa gabaki daya bai rage kowa ba, baitashi a wajen dayay karatun ba har saida zuciyarsa tay masa sanyi cos there’s always smthing heartbreakingly disciplined about him, shi namiji me dauke da wata inner wounds aransa na kalubalen maraicin uba ata young age that made him sharper nd not bitter nd hot tempered kamar yadda wasu suke fassarashi
bayan yagama karatun ne ya dan samu dama ya runtsa idonsa just for few min kafin ya tashi ya kimtsa dakinsa sosai, snn yayaje shi club na medical first aids and emergency practicals na Dr prof ciroma babban abokin bappa zaidu, inda anan kadai ne ake koyarda wasu additional medical skills. is not a schll routine, kawai de babban club ne na yaran masu hannu da shushi da ake budewa a killace dan kawai su kwarance sufi kowa ilmin sanin makamin aiki tun basuyi nisa a karatu ba.
kusan ma ibaad ne kaɗai awajen ba asan asalin miye matsayin ubansa ba andai san daga familyn almansur ne, daga yaran powerful govrs ne saina ministers sai na sarakuna da manyan yan kasuwa, duka duka basufi 30 a killatacen medical club dinsun ba amma dake ibaad yana amfanine da family name dinsu na al- mansur ne kusan koina suka shiga saikaga anata respa masa dan duk ansan tashen sunan gidansu na masu dumbin dukiya ne da power sosai..
tunda ya kwanta bacci bai farka ba sai can around 8:30am, yana lullube acikin bargo bai bude idanunshi ba tukuna, karamin motsin bude kofar da maheer yay yadada tadashi a bacci yanaji maheer din yashigo yana cewa"Dude kati na ya kare pls can i use ur phone? baima jira amsar ba ya dau wayar ibaad din akan table yakira uncle moh ya zauna akan chair nan suka cigaba da magana akan wata yar project da uncle moh din ya samu ta hannun wani dan siyasa toh dama shi babban dansa abokin maheer ne, ana ce masa Abdul gaffar tafida shine ma yake dan kkrin taimaka ma uncle moh din tawasu bangarori.
surutunsu yasaka ibaad ya miƙe ya nufi bathrum, white towel ya dauka ya Dora a kugunsa sannan ya tsaya agaban sink yy brush, ruwa yahada mai dan uban dumi a tsaftaccen bathtube dinsa da kyar sabida kasala yadan zuba shower gel nanda nan bayin ya cika dawani irin mugun kamshi ya shiga cikin ruwan ya lumshe ido yanadan tunani, yakai kusan 10min ahaka maheer yai knocking kofar rike da wayarshi dake ta haske murya chan kasa kasa yace bad your phone is ringing..dan yatsine fuska yayi yana dada karasa rufe tsaraicinsa da kumfa cikin kasalalliyar murya yace"who is calling?" kallon screen din maheer yayi ganin "m" da emojin heart ajiki,a hnkli yace "Ammi ne..ibaad yace ohhh ok talk to her first dan Allah duk hirar da zakuyi katabbata kace ce mata my schedule are soo tight, yanzu zan fito, daga can kofa maheer yadany kwafa ya hararesa yana ficewa ya saki ajiyan zuciya me dan nauyi dan he knows his mum is kindof desperate to see him today yasan inyaje kuma basa rabuwa da wuri toh gashi ya riga yay alkwarin zuwa gidansu zainab arifah ma bappa yaudarar mum dinsan ne kawai banson yi.
wayar na daf da tsinkewa maheer ya dauka yasaka a handsfree "salam alaikum gud morning Ammi. kin tashi lafya? Daga Jin yankewar sautin muryan tan yasan mamkin Jin muryansa taji dan tasan batare suke kawana da ibaad din ba, ahnkli cikin nitsuwa"..tace wasalam ikon Allah maheer Babban Mutum, ka tashi lpya?inashi rayyan din yau naga baiko neme ni ba.
dan murmushi yay yace ammi muna tare ne dashi karatu ne yadan masa yawa amma anjima da dare namiki alkawari insha Allh zamu taho gidan tare mu dubaki..
Tace toh bakomi Allah ya kaimu lkcin Allah ya maka albarka maheer ,yace Ameen ammi. daf zai katse wayar tace nd wen he comes around kace yanemi ni..tell him I have a surprise for him tonite he shudnt miss it.
Maheer yanadan murmushi yace copy dat ma..,baijira jin mezata karacewa ya dan katse wayar...yazo daf kofar bayin yace Kaikuma Saikayi sauri ka fito ka saukeni agidansu abdul gaffar cos I hate to be late.
Ibaad dake kkrin dauraye kansa da ruwan dumi baiko amsa ba saida ya gama gyara kansa da toilet dinsan tsaf snn ya fito...
A gurguje ya kimtsa kansa cikon kananan kaya suka fito haraban mansion din bappa zaidun kusan atare kai tsaye Suke baza takunsu a hnkli Mai tafe da tsantsar nitsuwa da kasaita irinna zaratan maza masu ilimi da aji Inka gansu tare gwanin sha'awa dake ma yanayin dirin jikin su kusan iri daya ne, banbaci baifi kadan ba, dake shi ibaad yariga yafara zuwa gym yana training sai yadan fi maheer din fasalin kyaun dirin jiki harda Dan tsayi shikuma maheer yanada wani irin tsiririn fuska ne mai mugun dauke hankli dirin nashi jikin Bai Kai na ibaad ba dake shima yana buga kwallo sosai..
key din babban baqar mercedez din bappa zaidu maheer ya miƙawa ibaad, ministrs qtrs suka wuce kai tsaye anguwan su abdlgaffar wanda yakasance ma maheer din tamkar babban abokinsa tun suna secndry suna tare. ibaad yana sauke sa agaban gate dinsu ya juya abunsa. saida har ya isa club dinsu snn yaga text dinsa akan ya riga yacewa ammi karama akan zasuje gidanta su dubata anjima da dare"..karamin scoff ibaad ya saki, kafin nan ya jefa wayar a silent ya tsunduma
aikin practicals dinsa dakema
introductory lessons ake ta koya musu akan field din su, dake shi likitan zuciya ne burinsa anfi jefasa wajen trial robot patients masu matsalar ciwon numfashi da basic first aid help da ake bawa masu ciwon zuciya. dake baida aboki awajen he had been more nd more focused than his seniors dake wajen shine yanxu yafara karatun nasa., hakan yasaka mutane dayawa suka fara jansa ajiki, wasu suyi challenging dinsa wasu kuma su dada zurfafa masa kaifin tunani.
dake yau baida lecture da wuri sosai ya jima anan, break da sallah ne kadai yake fitar dashi, arnd 2:40pm lkcin kusan kowa ya gaji aka farawucewa gida amma shibai gama ba sai da karfe uku da rabi yay snn yay hamdala ya tattara reports dinsa yasakasu ajaka kafin ya wuce masallaci...
yana idar da sallahn ya buɗe jakarsa ya ciro wayarsa da tun safe ya sakata a DND,missd calls takwas hudu aciki duk na bappa zaidu ne saida da sakonni guda biyu, dialing lambar bappan yafarayi dayaji lambar akashe sai ya duba sakonin ya karanta daya kudi ne me yawa da bappa ya turo masa, dayan kuma sakon mamansa ne sai yay mata reply, snn ya miƙe ya nufo waje ya bude motar dayazo dashi ya shiga, ahnkli ya dinga tuki har ya kai kansa gaban wata mayyar "velour palor" irin vintage boutique din nan ne dayake da wajen sayan kaya ,da fitting room da babbn refreshment palor da kuma luxury changing rooms. yana gaba parking benz dunsa ya dau iya wallet dinsa da wayarsa ajakarsa snn ya shiga wajen kai tsaye, bai kula kowa ba ya mule cikin sashen maza yafara duba kayan da zai saka dan shi mutum ne me mugun son tsafta ji yake kmr bazai iya zuwa gidan mutane da kayan da suka wuni ajikinsa ba.
sashen kananan kaya ya nufa cos he wants to look low tone and high standard, ko kadan kuwa bai kawo batun zainab arifah aransa ba kawai de yay tunanin cewa dole ne akwai babban dalilin da kawu babba nasu yake son ganin sa agidansa. within few minutes ya zaro wata maroon polo shirt irin fitted hugo boss din nan, da dark chinos, sai simple maroon colour designer loafers, yabi ya hada da agogon fata ɓaka me silver face na raymond weil,
da dior souvage perfume, kai tsaye ya wuce fitting. snn ya fito yaje ya bada katin sa ya biya kudin duk abunda ya suka mqsa acikin wanda ya dauka, daga nan refreshing lounge ya shiga sashen maza yasakar ma kansa shower yacire zufar dake jikinsa tass yana fitowa ya shafe jikinsa da disposable lotion yay fess, snn ya wuce private changin room, ya saka clean new boxers da sabbin kayan daya dauka kafin kace wani abu ya fito rass kamar bashi ba. he look plain nd simple but with high standard vibes irin nasu na masu shi...
duka duka minti kusan
ar'abin shirin ya dauke sa, kayansa daya cire ya zuba a jaka snn jefa a seat din baya
ya kunna karatun qur'ani all the way yanayi yana duba adress din da bappa zaidu ya basa har Allah yasa ya gane anguwar..
A bangaren zainab Arifah kuwa tun bayau ba dama babu wani mahalukin daya isa ya tasheta a barci,komi ma jiranta yake komin muhimmancin sa.
At half past 8am ta farka shima da kyar sabida yau tariga tasaka aranta bazata leƙo koda kofa dan taga menene yake gudana agidan ba sanin cewa duka iyayentan zasu iya tutsiyeta da maganan ciwon tan nan. tana cikin wnn tunanin iphone inta da yasha tsadadden purple phone case yay ringing as usual tay banza dashi tanakan jira ya yanke kafin ta sauka taga ko zata iyayin alwala,ganin ba'a dena kirar ba yasa ta dan leƙa saman screen din tana dubawa kuwa taga sunan Dad dinta ne akai, kasallen mikewa zaune tayi kafin ta dauki wayar takara a kunnenta dan batay tsammanin shi bane duk ta dauka mahaifiyarta ce take kirarta akan maganan ciwon nan, cike da shagwaba tace good morning daddy, Daga ta dayan bangaren prof yay murmushi yace "morning princess, kin tashi lafya, how are u feeling now? Tayi rau da ido tare da ƙarewa dakintan kallo snn tace "not bad" yace inde bakijin dadin jikinki ki gayamin..cikin katsesa tace noo dad pls krmuyi wnn maganan i am fine. yace uhum haka kike yawan cemin even if ure not, but anyway, abar maganan tunda baki so..cikin turo baki tace 'And don't ask me to come down and eat cos i am not hungry yet
..cikin nuna mata soyayya da gata yay murmushi ya ce no problem princess bamai takura miki i jst want to let u know dat i have invited ur brother ibaad over for dinner, this evening, lkcin ai zaki sauko ki kulani ko?
cikin kwalo ido waje ta miƙe tsaye buttt ta tsaya jikinta har na rawa rawa tace "what??dady kace ibaad zaizo gidan nan?
karamin murmushi yay yace "yess" and is just for ur sake..
wani irin ihun murna na bazata tamasa a kunne kamr ba ita ba tafara tsalle ohhh my god i love u i love love u super daddy..i love this surprise .
..saida har ya barta ta gama murnan ta snn ya dan tsime yace 'okay listen, kema kinsan There will be rules my princess.
rungume pillonta tay ta koma ta zauna akan gado tace i am all ears.
muryan sa cikeda yaudarraen salo yace zainab, kinsan babu wani abu a duniya dazai kawo miki farinciki wanda bazan iya nemo miki shi a duniyan ba, so pls i want u to behave arnd him my doter.. whos doter did i tell u you are???
cikin sauke ajyan zuciya tace " i am her fathers doter, born of strength and love, i am the storm i dont break, i always rise...dariya me sanyi yay yace now thats my girl...i have to make this work for ur sake, amma saikin min alkwarin zaki nitsu mubi komi ahankali. i need u to focus on ur studies more, be who you are meant to be. kowani namiji kikeso zaiso ace ya aureki ne idan kika zama wata abu a duniyan nan. snn ki dinga tuna cewa kece kadai magajiyar babanki komi sai kinbi ahankli. idan ina raye kome kikeso a duniyanan zaki sameshi, nothing shud break u kinji ko?
da wani irin tsananin farinciki aranta tace naji dadyna..i love u soo much. kuma tunda har kamin haka toh duk abunda kakeso nayi zanyi, nd i will make sure i make our dream come true.
dada zurman da ita yay akan zai tsaya mata akan batun ibaad ita kuwa ta dinga masa alkwari ma cewa zata maida hankalinta akan karatu dosai
bayan sun gama wayatr wani miƙa tayi game da lumshe idanuwanta ahankli jin kanta a wani matsayi nadaban dan tasan lallai ita din na daban ce, a doughter of a multi billonaire and probably a queen with a brigh future,to meye ynzu ta rasa a duniya tunda babanta ya fara kkrin jawo mata ibaad cikin rayuwarta?
Yawan Girman kai da jiji dakai da shaidan yay mata wahayinsa ayau ta kuma amsa na daban ne, Dan kuwa ji take kamar ma ta rigada ta auri ibaad din ta gama tunda har babanta ya fara shiga lamarin.
Kyakkwar Juyi tayi tanamai sake pillolin dasuke kanta izuwa kasa, Ayayin da kamshin hot coffe dake aje neatly akan tray tare da nutella agefen gadonta ya wani mamayeta wanda bata ma lura da shi ba sai yanxu..
Ahankli ta Lumshe idanunta snn ta budesu ta kalli kan tray din tare da sakin dan tsiririn tsaki jin Wani qwiyuwar daukar coffe cup din takeji har kaman zata dauki wayarta ta kira downstairs domin a turo mata maid tazo ta miƙa mata coffe din sai ta tuna da cewa ashe itace jiya ta basu umarnin karsu kara tsayawa akanta intana barci.
Tsaki mai kauri taja snn ta jefar da wayar akan gado adan dole tadaure ta dauki coffe din tasha kadan,snn ta aje shi ta dauki nutellan ta tafara sha،dan duk duniya babu wani abunda tafi kauna a rayuwarta sama da taga tana kwalliya, bacci, shan chokolate na karshen su kuma mafi muhimmancin shine zuwa "shopping".dan har gani take kamar bazata taba rayuwa in bataje shopinh ba a sati kusan sau goma ma zata iya fita shoping bai kuma dameta ba.
A kasaitacciyar yanayi mai daukar lokaci ta fada wajen wanka inda tay umarni ma maid inta elizabeth akan ta cikka bath tube da kumfa sann aka kawata wajen wankan da wasu irin flowing red flowers da kuma red candles da hot coffe.
daga yau har kullum haka ta umarce Elizabeth datana shirya mata wajen wankankart dan babu shakka tasan damuwa rta yadau hanyar gushewa dan arayuwa bata taɓa sanin wani abu waishi rashi ba, bare kuma kalmar qaddara,toh inma akwai qaddarar to nata qaddarar kenan na zamowa matar ibaad a future.
Bayan ta kammala wanka ta fito aka fara shiryata kanta nitse,ta saka white mcqueen maxi gown mai makahon tsada
Saukowar nata ma daban ne dan haka kowani masu aiki kusan shida ne suka matso kusa domin serving mata abunda zata karya dashi.
Ita kadanta ta zauna akan doguwar royal dinning table dinsu 45 mtrs long maicin royal chairs guda sha biyu, maids din dake a tsaye akanta tana zama suka fara aikin jejjera mata dishes kala kusan sunfi goma da uwarta hajya hamida tasa aka dafa mata da safen nan musammn dominta
Saida ta kammala karewa abincin kallo kafin da kyar ta samu ta tattaba abincin kan plate daya tanaci kmr wanda kwai ya fashe mata aciki can dai tamiƙe tsaye tareda ce musu sutattara sauran su zubar ta koshi.
daga inda take ta kwallawa mum dinta kira batajira amsarta ba tace "mum nikam na tafi shoping da driver, tana fadi hakan kuwa tayi ficewarta.
ba ita da dawowa ba sai wajajen karfe sha biyu na rana, jakar sayayya yakai takwas da masu aiki suka biyota dashi ciki, tabi ta daga wa kowa hnkli tun karfe daya aka fara mata spa har izuwa 2:30 kafin tay wanka aka zauna mata kwalliya wajen zaben kayan da zata sakama saida har taji elizabeth tafara cewa ga baƙon nata ya iso yana gate snn ta iya zaɓa.
wajajen 5pm na yamma ibaad sharp yay horn agaban gate dinsun dat took almost forever to open sabida scanning dinsa da masu kula da cctv cameras sukeyi kafin can dai suka budemai gate din ya shigo.
security ne aharabar gidan here and dere amma dake anriga an gaya musu wani yaro zaizo sai basu wani damu su tambayesa ba, calmy ibaad ya kashe mota ya sauko daga shi sai wayarsa
wani security yaxo suka gaisa daga nan baice masa uffan ya masa jagora suka shiga cikin gida...#surayyahms
share
08060712446
[28/10, 18:44] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️9️⃣
Door bell securityn ya danna within 2 mins wata maid sanye da torqouise colour uniform ta buɗe kofar tafito, suna hade ido da ibaad ta tsaya cak tana kallonsa cikin haɗiye yawu a fixge ta dauke idonta a nitse tace ma security "i will take it frm here. kai ya gyada mata baice komi ba yajuya yabarta tare da ibaad din awajen, cikin kare masa kallon rudewa ganin kamanin jini da prof a fuskarsa yasa tace "please come in ure welcome sir.."fuska ba yabo babu fallasa ibaad yace thank you gaba tay yana biye da ita abaya suna shigewa ciki aka rufe kofar gidan kirif.
Katafaren Parlour ne mai wani irin girma da tsari dayaji Lumtsattsun kujeru na royal chairs golden and red colour. labulaye da chandelliers suma golden colour sai baza qyalli suke snn Duk wani abu daya ƙawata Falon ya zamto shima golden nd red colour dinne da wasu irin manyan turkish carpet, manya manyan Airmores da incence burners kusan kowani kusurwa suna aikin bada Dadaddan Qamshin turarruka na alfarma da kuma iska mai sanyi wanda already sanyin ma yakama falon takoina sabida wata irin dukiyace ta musamman aka narkashi acikin wnn falon.
Babu kowa acikin falon tasu ta farko wanda shine zai sadaka da babban falo na biyu wanda ya kasance falon zama daganan kuma har zuwa sashen cin abinci.
Ratsa dogon Falon tayi ibaad na biye a bayanta ta nufi kofar da zai kaita ainihin falon prof zayyanu na musamman tana isa dede wajen kofar ya budu ta tsaya cak anan tamasa alama akan da yakarasa shiga shikaɗai sabida prof already yana ciki, uffan baice mata ba cikin takunsa mai sanyi da aji ahankali yashige ciki ita kuma takoma gef ta tsaya daga nan tana jiran fitowarsa.
Katafaren falone na alfarma an masa kwalliya da dusty rose da wani irin cool black furnishings, wanda shirun da wajen yay tamkar babu kowa aciki banda qamshi da ƙarar ac dake tashi ahankali.
Ajiyar zuciya ibaad yay tareda ta sakin masa nitsatsiyar sallama ayayin da prof ya dago kai yanamai sauƙe ruwan idanuwasa akan ɗan yayan nasa.
Zaune yake cikin shiga ta alfarma jikinshi killace da manyan kaya wanda tuni tay bajintar fallasa siffarsa na kyakkwan namiji mai cikar zati,jarumtacce mai kuma cikar ƙirar halitta da dirarren siffar jiki. Kallon daqiqa biyu yayi ma ibaad din,ganinsa lafiyayyan yaro mecike da tsananin sanyin kyau da cikakkaer kwarjini me rikitarwa zak zak irinna mahaifinsa wanda hakan ya kusan rudasa atake, ji yay aransa inama ace Da Shine Allah ya bashi wnn darajar samun ɗa namiji dakakke irin wann ba babban wansun daya rasu ba.
saurin daidaita kansa yay cikin tattaro makansa nutsuwa da ƙarfin hali yanamai sakin masa murmushi adan dake har ya amsa sallamarsa tare da umartansa akan ya karaso ciki.
ibaad na karasowa ya tsuguna kasa daf cikin
nitsuwa ahnkli yace "ina wuni kawu, fatan na sameka lafiya?
prof ya karemai kallo sama da kasa cikin yanayin kamiya adan tsime yace masa lafya kalau, shiru ne ya dan ratsa kafin yace" Kaine babban ɗan marigayi ko? bayabo ba fallasa ibaad yace eh nine, prof ya gyada kai, but u can see the provocking jelousy nd envy wailing tru his eye balls, dan yafiso ace kowani abu mekyau a duniyan nan shine zai mallaka msmn yadda yaga ibaad yafara girma cikin nitsuwa izuwa hadadden namiji mai kwarjini da aji sai yakeji aransa inama ace danshi na cikinsa ne bana yayansa ba.
cikin kaucar da wann tunanin yace ohh babu shakka, i can see the resembelence, "wai har ku nawa ne ya haifa haka? batare da dago kai ba ibaad yace "mu biyu ne. prof ya kara zuba masa ido da mamaki ayayinda shiru yadan ratsa tsakaninsu sai can snn yace umm well, dats fair amma kuma dukanku maza ne? nasan da babanka bai rasu ba hala da ƴayansa sunfi haka yawa,..baima bar ibaad din ya amsa shi ba cikin yanayin mita yace" babanka shine babbanmu a ahalin nan amma bansan mesa yaje ya auro yarinya karama ba, uwarkun tana raye ko itama tabishi?..
ibaad ya dago kansa ahnkli suka haɗe ido fuskansa adan daƙile yace mishi "she is alive. prof yay dan kwafa a shashance "tou hakan yay dai-dai alhamdullh tunda kuna da wacce zatana ciyar daku kai tashi muje ciki nagaji da wann surutun..ibaad yay shiru kamar baiji shi ba, har saida prof din yamiƙe yafara tafiya snn ibaad din ya mike tsaye shima yafara binsa abaya,
wani katafaren hallway suka ratsa, acikin izza prof yake tafiyarsa yana lallatsa wayarsa kai daga ganinsa kasan ba har cikin ransa yake son wnn yanayin ba, shidai kwata kwata baison yan uwansa na jini suna raɓar gidansa bare arzkinsa wnn karon ma babu yadda ya iya ne rayuwar yarsa tafi mai komi muhimmnci a yanzu
suna shigowa wani katon white hall mai tattare da babban dining area sai ga nan matarsa hajy hamidan tabude wani babban kofa ta fito amugun mugun kasaitance wani irin kwalliya tayi tamkar ɗawisu qamshin hadadden turarenta tuni ya bule wajen da qamshinsa, tana taku dai dai kmar bazata taka kasa ba, tasaka wani ubansun boubou na original shadda lace royal blue colour wuyanta da hannunta sunci uban su da gwalagwalai.
suna hade ido da ibaad ta tsaya turus tanata kallon yaron cikin fallasashen ruɗewa dan acikin ranta batay tsammnin wai harya girma ya ƙara kyau haka ba, tasan dai zainab arifah tana yawan zuzuta kyansa ita a mind inta she expects to see notin but a hungry local boy with no social class, dan rabonta da ganin fuskarsa tun ahoton haihuwarsa datagani awayar anty safeera.
cikin neman wakanta nitsuwa tay gyaran murya me aji tabi ta tsime batako musu sallama ba dake taga mijintan nakan amsa call kai tsaye ta shigo cikin dauke kai tayi kamr batagan ibaad a tsaye ba.
tana zama akan chair ibaad ya daga ido ya kalleta daga tsayen yace"ina wuni ? ranta a harde ta masa wani irin kallon sama da kasa me shaqe da rainin wayo muryanta ciki ciki tace "lafiya. snn ta dauke kai tay banza dashi, shima sai bai kara kallonta ba, shiru ne ya ratsa tsakaninsu dan wani mugun haushin yaron ne ya riketa kamr zai fasa mata kirji irin feeling feeling dinnan najin anrainata dake ta riga ta saba ana yawan mata fadanci ko mutum ya girmeta zakaga yana rusuna mata kai kasa sabida matsayi da dumbin ikonsu, yadda tagama raina ma labarin kyan ibaad wayo sai kuma tazo taga ya ashe ma wuce yadda take tsammani tun daga siffarsa har izuwa kan dressing insa me mugun dauke ido da uwa uba yadda dadin turarensa me aji ya kusa danne nata me matukar tsada.
shi mutum ne wanda iya tsaftarsa ne zai soma dauke maka hankali, he always look so smart nd very neat, shi baya son tula kayan sawa ajikinshi amma kuma sutura me bala'in aji yake yawan sawa.
prof ya gama wayarsa kenan ya kallesu duka ganin kowa ya dauke kai sai yay gyaran murya yace hajiya hamida wann fa shi ne dan gidan marigayi babban yayana late dr almustapha almansur.
cikin rolling ido ta juyo tanamaiyin kamar tuntuni bata ganesa ba, da wani irin yaken makirci tace ohhhhh ayya, Allah sarki ashe dan marigayi ne, gashi kuwa ya girma da kamannin mahaifinsa, gosh jishi duk ya zama abun tausayi toh Allah dai ya jikan babankan, ran ibaad yafara baci bt still ya kwantar da hanklinsa yace Amin. ido ta zuba masa ta kara kallonsa ita dai gaba ki daya ji tay kmr taƙi jinin yaron dan daga ganinsa tasan zaiyi girman kai yadda taga ya hade ransa baya ko murmushi, saida ta gama kare masa tanaɗi aranta sann tace Alhaji sai ku karasa dinning din i am sure we are all famished.. prof yace aa hajiya kinsan ni bawani son cin abnci da yamma nakeyi ba amma dai tou bakomi muje dai zan taɓa.
tay murmushi yawwa my darling ai kuwa dazance kar kayi haka
ta kalli ibaad da rainin wayo a kwayar idonta cikin rage murya kasa kasa inda tasan ibaad din zaiji tace "ohh ni hamida dama haka yaron yake abun tausayi, alhaj ya naga duk yunwa ne ajikinsa kasan me? kuje kawai kan dinning din zan sameku acan i need to check on our princess,
prof baice komi ba ya gyada mata kai tana barin wajen ya kalle ibaad wanda already zuciyar yarinta na raya masa akan kawai yaqi cin abincin ya tafi sai kuma yay wni tunanin kawai sai ya danne zcyrsa yabishi suka zauna akan dinning table din kusan atare.
nan ma shiru ne ya ratsa tsakaninsu har saida hajya hamidan ta dawo ganin ita daya ta fito babu zainab arifah yasaka tun bata zauna ba prof ya fara tambayatta inq yarsan take, fuska ba yabo ba fallasa tace "alhaj ka kwantar da hankalinka she is coming kasan dai yarkan sarauniya ce mai son kwalliya da tsafta, so she will be here in few minutes dai tacemin, cikin jin dadin hakan yace its awryt let her take her time she will alwys be the prize, atare sukayi dariya. shide ibaad baice musu uffan ba,
daga kan long luxurious table din ido kawai bazai iya kirga abincin da ake jera masa agabansa duk dan a nunasa nasa bambamcinsa da su.
abincin gargjiya har tuwon biski ta saka anyi wai a tunaninta ko yaron baisaba cin na yan gayu irrinasu ba, itafa komin arzikn ka inhar ajinku ba daya bane to A talaka kawai take kallonka.
sunfi 10min suna zaune ba ataɓa komi na abincin ba sabida suna jiran yarsu yar gata zainab arifa ta gama duk abunda takey snn ta karaso.
hirar business suka faray sama sama tsakaninsu ganin ibaad bamai son magana ba yasaka basuma tsomasa aciki ba.
after like 10 more mins tahowa zainab Arifah takeyi akan golden steps cikin shan qamshi tana taku kamar bazatay ba domin itakanta qamshin turaren data fetsa ajikin nata tsabar yawansu da karfin qamshinsu ji take kmr suna bugar da ita, daya bayan daya take dora kafafuwanta akan step, cikin tattalin kai
can saiga ta bullo ta wajen inda suke wanda tundaga sama ta zubawa ibaad dake zaune akan luxurious dining table din da aka kawatashi da ababen tabawa ido tanajin kamar mafarki takeyi, wani irin sabuwar farinciki takeji mai yawa na mamayarta har kwakwalwa data gansa.
Kasaitaccen sautin takunta shi yadan janyo hanklin iyayen nata bisa gareta dan tay masifar kyaune na kure hankli saide duk gigin zumudintan nan kuwa bata wani tula kayar tashin hankli ajikinta ba, doguwar riga slay queens gown styles marar hayaniya sosai tasaka ajikinta na babban atamfa original engila red colour snn ta cakkara dauri tare da zubo da sumarta kafadunta, cos at this young age already ta fara saka irinsu nails da curtex da gashin doki duk dama babu laefi itama din tana da dogon suma., cikin nitsuwa ta sauko cos she rmbers clearly cewa babanta yace mata kar tay rawan kai agaban ibaad, dan haka tay balain kkri wajen danne abubuwa dayawa na zumudin ganinsa dake yawo cikin ranta da zucyarta.
faduwa gabanta ya dingay har ta iso tana satar kallonsa, iyayen atake suka hau yaba kyanta kamar yadda suka saba, itakuma tana fmr shagwabe musu fuska, ibaad yadago kai kenan suka hade ido da ita, gabanta ne ya mugun fadi saikuma taji takasa motsi tabi takafe shi da kallo mai sanyi kamar bata taba ganin kyakkawa irinsa a duniya ba.
ganin ya dauke kansa a kallo daya yasaka itama ta dauke kantan ahnkli cos she was lost in her tots for a moment dan batama jin me iyayen nata suke cewa kawai satar kallonsa ta dingayi harta karaso gefen baban nata ta nanike ata gefensa yarike mata hannu cikin tsantsan nuna mata soyayya da gata a fili, a shagwabe ta zauna daf dashi batace ma iyayenta uffan ba, tay cunen baki tanajin kanta a matsayin yar gata sangartacciya kuma ƴa guda awajen iyayentan wanda tasan zasu iyayin komi akanta a duniyan nan, yau yadda kasan danyen tuwo haka take narkewa jikin babanta. Tun data nemi waje tazauna acikin yanayin shagwaba batace uffan ba bare tay gaisuwa daga ta turo musu baki, sai tay rau da idanunta cikin tsinannen rigima.
hanklin ibaad gabaki daya baikansu jin yadda iyayen suka fara jajayya da ita wajen gaisuwa dan tun safe bata gaishe da iyayen nata ba.
yau sosai yakara lura da cewa zainab arifah din sangartacciya na kure hankali da tunani kalar wanda tsarin rayuwar banza ya riga yashige musu jikinsu sosai.
da kyar dai suka sakata tay gaisuwar harta gaishesa ya amsa atakaice kafin nan baban nata dakan sa ya bada oda masu aikin gidan dake akansu suka fara aikin serving dinsu abinci wanda gabaki daya wajen ya gamutsu da wani irin qamshi me shegen dadi ga nan dadadan aroma na garnished soups da gasashun namar kaji.
sama sama ake hira akan table din..shide ibaad sam ya kasa fahimtar kalar rainin wayo irin tasu cos all this traditional food tagabansa kawai ake tarawa hakama idan za'a samai abu a plate dinsa sai ancika plate din kamar sun ga mayunwaci ko mabaraci. shide tun da ya rike spoon yana jujjiya wa bai isa yace yayi loma yakai uku ma abincin ba..
prof ne yake magana time time yana kushe kokari, ilimi, da arzikin kowa cikin familyn su al-mansur, at same time yana dan sako labarin mahaifin ibaad din dake duk zuria shine kawai bai taɓa yin zuciya dashi ko ya rokesa kudi, ko wani taimako ba. hasalima badon shegen son zumunci irinna mahaifin ibaad ba da tuni prof ya raba kansa da zuriarsa sabida bappa zaidu da uncle moh sai suyi shekara fiye da hudu ma basu kulashi ba.
shi bawani cin abincin yqke ba kallon ibaad kawai yake yana cewa..."babanka mutum ne mai mutunci duk zuria shine kawai be taɓa nunamin baqin cikinsa ba,shi yasa nake jin kamar ba zaidace mubari zumuncin daya kulla da gidan nan ya yanke gaba ɗaya..
duk da prof baison zumuni bt he try to pursuade ibaad dan yaji aransa cewa zai iya amsarsa agidansa a mtsayin ɗa kodan albarkacin mutuncin mahaifinsa.
hajy hamida kuma tafi matsuwa datasan educational level din ibaad bawai dan zai mata amfani ba saidan ta samu wani makafar ci masa mutunci da kaskantar dashi in the future, she was highly expecting to hear some mediocre course. saidai tun ya ce musu medicine mbbs yake karantawa a jamiar Ado Bayero sai taji ranta ya baçi wann karon batama iya boye tsanar da take masa a fili ba..,
cikin furucinta na rainin wayo sai nuna mai take kamar bai kai ya karanta wann course din ba. sai tambayar ya uwaka tay ta haifeka take masa akan karatun. tanamai nuna masa karara cewa medicine yafi karfin brain insa like he cant just afford to be a doctor. tafara masa suggesting su hospitality managmnt, zoology, french, islamic, political science, library science, history, hausa e.t.c..shide ibaad bai iya raina babba amma tunda ya gane salonta na rainin wayone sai ya zamana da daddaya yake bata amsa me kaifi da nauyi wanda yasan hakan yana mata ciwo aranta sosai. duk courses din data kirasu mediocre saida ya gaya mata relevance insu a real life. ta dage masa wai saidai yabar medicine ya karanta wani course dede dashi. shima ya dage da ce mata aiwann dinne ma kawai dede dashi.
duk wadatar da bappa zaidu yake dashi na kudi da rufin asiri still zaginsa takeyi tana cewa wai aibazai iya ilimantar da yaransa snn yazo yq ilimantar da ibaad dake maraya ba. yanayin datake sakayawa tay zagin hakanan shima ibaad yake sakayawa ya cakka mata amsa tare da mata tambayar ko ta taɓajin bappa zaidun yazo gabanta ya durkusa yana nemam taimakone akan harkan iliminsu
it was so clear dat jinin hajy hamida sam bai hadu dana ibaad ba.
ganin hirar tasu is bcming a bit awkward yasaka prof ya fara kawo batun karatun zainab arifah, ryt in d midst of their heated conversation yafara yaɓa ilimin yarsa yana nuna cewa itama yar baiwace, kuma business kawai zata karanta infact sai takai matsayin higher doctorate, yace yarsa bata bukatar dagewa sabida ilimin gidansu ta gada, amma shi fa ibaad din nuna masa sukeyi baida wann gadon ilminin dolensa sai yadage. duk dai yabi ya rasa menene takamamen abunda yasaka mutanen nan suka kirawoshi gidan su dan banda baqar magana da cin fuska baiga abunda yake karba a hannunsu ba.
har saida suka gama kammala cin abincin snn prof ya fito fili ya fara masa magana akan alakar sa da zainab arifah cikin sakayawa, sai yake nuna masa tunda yafi aminta dashi yana buktarsa da yadinga sake fuska wa yarsa zainab arifah dan tadada sanin danginta with his supervision. wasu kalamai, da karairaye da cin fuskar daya gaggaya ma ibaad akan familynsu ma hankli bazai dauke ba, its obvious gani yakeyi kamar kowa ne yake masa baqin ciki akan daukakar da Allah ya basa kuma kudinsa akeso ba shi ba.
ibaad yay shiruuu harsaida prof ya gama kushe kowa adangi ya koshi snn yabashi baki....
nan ne kuma hajiy hamida ta fara kawo nata surutun cikin irin hikimarnan na mata dan ita haryau bata yafe dukan dayay ma yarta ba, kai tsaye ta fara kawo masa batun dukan dayay ma zainab Arifah kai tsaye tafara cak cakka masa magana wai "sun yafe masa ne sabida sungane ba lefinsa bane lefin uwarsane data tarbiyantar da namiji kamrsa me dukan mata tun yanada danyen shekaru.
wann maganan sosai yamasa zafi aransa musmn yadda prof ma kansa yake cewa ai ammi karama a danyen shekaru aka aurota bata da wayo hala ma mahaifin ibaad dayake raye dukanta yakeyi agaban ibaad shiyasa itama bata san yadda zatay ta tarbiyantar da danta namiji ya dawo ɗa na gari ba.
ganin ibaad yadena cin abinci yay shiru baice musu komi ba, jikinsu yafara basu hala ransa ya baci ne,
sai kawai suka wanye cikin hira suka ce ma zainab arifahn wai ta bashi hakuri agaban su dansu tabbata cewa komi ya wuce tsakaninsu. dakyar zainab din ta amince tacemai yay hakuri wanda dashi da babu kusan duk dayane dan abune anayi ana masa iyeyi, gashi tsabar iya manyance da shagwaba irintata wani bin intana magana ma basajin metake cewa.
ibaad sosai yagama gane yanayninsu, mutane ne marasa mutunci, ya lura so kawai suke sukulla wata friendly alaka tsakaninsa da yarsu zainab arifah amma bawai dan son ransu suka nemeshi ba. they want him to blindly tolerate zainab arifahs spoilt brat behaviour, ace kome tace masa kar yay mata tsawa, fada, bare duka, he can clearly read what is behind their selfish fabricated gestures and intensed fake smiles amma dake shi yarone duk sai ya danne abun aransa ya biye musu har suka gama surutansu bai musu rashin kunya ba duk da zagin uwarsa da sukayi wanda duk shi yafi masa ciwo aransa sosai.
bayan kamar awa guda da zuwansa yace musu zai tafi gida..wani irin murna sukaji dayace hakan acikin ransu, amma a fili har wani ɓata rai prof yay yahaushi da masifa "haba haba kai kuma sai kace wanda ake korarka...cike da makirci hajy hamida tafara fada" hmm alhaj ainni gani nayi kamar be wani sake jikinsa da mu ba, he barely eats kuma nace amasa packging din abincin nan yace min a'a, karshensa sai dai azubar kenan kasan dai mu bama cin irin wann local abincin, yo ko maganan kirki fa basu zayna sunyi da yar uwansa ba gashi yanace mana wai zai tafi..
atake zainab arifa tafara hararar mum dintan dan duk wani surutun cin fuska da suka masa yasa ita bata wani ji dadin haka ba. yadda take mutuwar son ibaad ko kadan batason taga ransa ya baci.
cikin katse mitar mum inta da muryan shagwaba tace mummy pls nidai kidena masa fada kibarshi ya tafi hala dai ya dan gaji ne kmr fa daga schll fa ya taho he need to go and rest.
ammkance hajya hamidan tace nd who told u daga schl ya fito da duk wann uban kwalliyar ke kuma yar azarbabi...
ckin rolling idanu ahnkli tace kai mummy haka fa shi yake dressing, nd i have my ways mum
kinsan elder bro na kawata nala kin tunashi? ayatsine hjy hamidan tace eh, tace toh ai ajinsu daya da ibaad so dazu muna chat da nalan ita tacemin a schl suka wuni yau so pls just let him go..okay?
murmushin yake kawai prof yay ganin yadda zainab din take ta kkrin kare ibaad wajen mahaifyarta
shide ibaad baice musu komi ba yama juya kansa gefe kmr baya wajen,can prof yadan kallesa yace toh bakomi sai Ka maida hankali sosai, shi zumunci da karatu kusan shi ne abin da mahaifinka ya fi so arayuwarsa, saika dage snn idan kasamu lokaci ka dinga zuwa kana taimakawa yar uwarka zainab arifah da karatu agidan nan, i know my princess is smart amma ai tana buƙatar kwarin guiwar daga yan uwanta.
babu yabo babu fallasa ibaad yace toh bakomi kawu. ni zan wuce. Nagode sosai da kulawarka. hajya hamida ta ɓata rai ganin har zai juya baice mata uffan ba..
prof ya ma zainab Arifah ido akan tabishi waje, duk dai burinsa baifi yasa zainab taji cewa yana tare da ita akan ibaad ba, dan hakan ne kawai zaisa tay tunanin zata same soyayyarsa harma ta cire damuwar soyayyn aranta ta warke snn tamaida hankli wajen karatunta sosai.
tunda taga babanta ya bata go ahead da rawar jiki ta kama bin ibaad abaya wanda tun basu gama ficewa a hallway din ba suka fara jiyo muryan hajy hamida datake fmr mita da masifa "alhaj kaga rainin yaran nan ko? waima "hajiya" fa yake cemin kamr ni bankai na haifesa ba nide next time yazo gidana nd he stands to greet me wallhi zanci masa mutunci inhaka yake gaida uwarsa atsaye agida toyasani nide nafi karfin yaro kmrsa ya gaida ni a tsaye masifa take ta inda take shiga bata nan take fita ba..
ibaad kuwa tunda ya saka kansa bai kara juyowa ba barema surutunsu ya damesa dan already ransa ya baci sosai. har me aiki tabude musu kofa duhu duhu yake gani bai daga ido ya kara kallon kowa ba, yana ficewa harabar waje zainab Arifa ta karaso da sauri harta jikin motarsa tana haki da wani irin rangwada tace hey ..ibaad, please wait..
Miskillalliyar Ajiyar zuciya ya saki snn ya juyo adan takaice Suna hade ido ta dan sakar masa murmushi maisanyi, sai snn ta tuna zcyarsa a kusa yake baison magana musmn ma na raini so da wurwuri tace mai "salam alaikum, Hi .
kallo ɗaya yamata ya amsa sallamartan a dakile tare da dauke kansa yanamai kawar da idanunsa can gefe.
"i just want to say thank you for coming..
kallonta kawai yay baice komi, da sauri tace "toh ya su anty safeera agida? tun be amsa ba tace ohhh just forget them.. uhm u know, i have been hospitalized. jiya da darema aka dawo dani gida bakaga na canza ba.. i have this..
ganin zata cikasa da surutu banza cikin datsar numfashinta yace toh its okay, saiki koma kije ki huta Allah ya kara sauki..
sounding childish and desperate ta rolling masa ido tace okay, "thank you, thank you soo much for seeing me,wont u like to knw daf ciwon damuwa ne kawao likitta yace yake damuna, nd i have...
ibaad ya mata wani irin dakakken kallo kmr na wanda ake sakashi tsyuwar dole yace ciwon damuwa kusan kowa na fama dashi nd am sure u u ave a therapist by now so why are u telling me?..
ɗan shiru tayi tanata kallonsa kafin can tace mishi umm notin, kawai so nake kasani, kasan ba kowa bane yake iya mantawa da wani abun dake yawo acikin ransa.
kai tsaye cikin datsar numfashinta yace 'toh ke Ki koya mana, Zai taimaka miki fiye da tunaninki. dede nan yabuɗe ƙofar motarsa agajiye takasa cewa komi tanata kallonsa har yashiga motar ya zauna snn takuma cewa thanks for ur time ibaad, it means alot..
..da emotionles face nasa ya dubeta yace "Allah ya kara sauki
..daga haka ya daga glass dinsa ya kunna motar cikin kankanin lokaci ya doshi gate aka bude mai yafita.
zainab arifa ta jima a tsaye anan kafin can ta koma ciki tana jin wani irin sanyi a ranta dan baitaɓa tsayawa tayi magana me tsayi da shi kamar nayau ba, da wani dan uban murna ta koma gida ta rungume babanta tana masa godiya
fannin ibaad kuwa tun be bar titin anguwar ba abubuwan da yafaru agidan ya dinga dawo masa akai sai yanaji kamar zucyarsa na mugun tafarfasa waima ahakama bappa zaidu ya bashi key dib babban mota da kudin sayan sabbin kaya kenan da baisan wani irin mugun cin fuska za'a masa ba, can dai wayarsa yafara ruri ganin sunan maheer ne akan screen babu bata lkci ya jawo ya dauka ya duba sakon dake kai daga nan bai bata lkci ba yakara ma motar wuta tareda shan kwana yanufi anguwan abokinsu abdl gaffar, anan ya samesu dede sunfito gate suna tsaye suna jiransa, sama sama suka gaisa tsakaninsu maheer yabude motar ya shiga suka kama hanyar gida..
tunda suka hau titi ibaad wasnt looking fine at all kawai tuki yakeyi duk kalaman cin fuskar da akama uwarsa tafi masa zafi, wani irin nadama yakeji aransa dan daya san dukan zainab arifah dayay ranar zai iya jawowa har azagi mahaifyarsa comfortbly agabansa ba dabai fara ba
maheer nata shan mamaki ganin yay shiru baice masa uffan akan zuwansa gidan kawu babba ba har suka isa gida kuma baice masa uffan ba.
yana gama parking ya bawa maheer din keys na motar snn yakai kayansa daki baijima ba ya fito agurguje sukayi alwala awaje atare, as usual shiyaja su sallan magrib da ishai a masallincsu na kofar gida, har yanxu kuma baice ma kowa komi akan ziyarar da yakai gidan prof ba suma kuma basu tambyesa ba sabida yanayin fuskarsa.
bayan sun idar da sallanne yaje ya gaya ma bappa zaidu akan zasuje can family house shida maheer wajen maman sa dan tun safe tace tana son ganinsa.. kai kawai bappa zaidu ya gyada musu, kowa jikinsa na bashi wani abu, har suka kama hanya suna hirar ball sama sama har suka kai kwanan anguwar rijiyn zaki maheer baiwani gane kansa ba...
#surayyahms
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[29/10, 19:23] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️1️⃣0️⃣
Wajajen karfe takwas na dare saura suka shararo kwana cikin anguwar rijiyar zaki, dakema tsohon famly house din nasu na al-mansur babban gida ne me tashen daraja sai yasaka layinsu ya shiga can can ciki inda kwata kwata babu yawan hayaniyar jama'a kebetaccen layi ne me tsafta gidan nasu yake kusan shine babban gida na farko,
Ahnkli maheer yake tukosu yana jan tsaki sabida buga musu bayan mota da wani dan adaidaita yayi shide ibaad baice komi ba har suka iso kofar gidan nasu yay horn a bakin gate mai gadinsu yazo agurguje ya buɗe snn ya shigo da su ciki batare da bata lokaci ba.
Babban compound ne sosai dake dauke da gungimemen baqin gate da bishiyoyin kwaiba da kwakwa da umbrella guda hur hudu masu daukar hankali a kowani kusurwa, kai kana ganin tsakar gidan kasan wadata da kwanciyar hankli ta zauna kusan dai babu abunda suka rasa na arziki sede a idanun prof da matarsa ne kawai suke kallonsu tamkar almajirai..
makeken tsakar gidan nasu na dauke da manyan sassa har uku masu design iri daya ko wani side akwai coridors da matakala mai dan tsayi tsakanin sa da wani sashen, sashin farko wanda shi zaka faracin karo dashi bayan shigowar ka cikin gidan shine yaksance babban morden bungalow yana da girma sosai ananne main family house falo yake me girma mei cin setin kujeru hudu da katon dinning area, sai wani dan karamin falona privacy asama, anty safeera da uncle moh da ƴayansu biyu sune suke zama ata nan fannin don sashin ya fi kowanne girma sosai, yana da extra rooms nd big luxury falo dake tsakanin sashen da sashe, sai yar medium self contain da aka tanadashi wa hajy mairo mai tuwo intazo musu hutu.
dayan Sashen da baida girma sosai su ibaad suka wuce kai tsaye dan anan ne mahfiyrsa take zama wanda na musamn bappa zaidu yasa aka sake gyara yanayin building dintan tun alokacin da mahaifin ibaad ya rasu badon komi ba saidan dan ammi karama taraini yaranta acikin nitsuwa da kwancyr hankali, hatta ibaad da baiya zama da ita sai wkends yana da nashi bed room din da closet dinsa inda ke lode da kayan sawarsa kala kala masu tsada da kyau. In ka shiga Bangaren nasa zaka san indeed shi dan gatane awajen mahaifiyarsan inyazo gida yakan xabi xama ananne sabida anan ne yafi sakewa.
karasowa sukayi cikin karamin parlournta iya muryoyinsu kawai tajiyo tamiqe zaune kadan jin motsinsu a kusa tay murmushi cikin furta kushigo daga ciki
Gyara zamanta tayi akan dark red colour daddumarta tana dada gyara zamn wata white cotton lafaya lace ajin farko data sayeshi from mum ramlat's clothing collection,tayi masa dinkin riga da zani irin maiduguri style innan dayagaji da haduwa wanda duk dama dare ne amma Wani dan uban qamshin turaren wutane na dutches da sandal wood original already yagama cikke sashenta da azaban qamshinsa traditional incence burners dake ci da wuta agefe da gefen kowani kusurwa na famar kara masa kaimi..
sanye take da farin gilashi à idonta na karatu, Gabanta kuma nadauke da hadadden royal flask sabo daga uwargida kitchen utensils collections shima badai dauke ido da rike zafi ba, tashakeshi tam da herbal tea, sai tazuba Kadan adan karamin transparent kofi na shayi tanadan zuƙa ahankli,a shekaru dai kwata kwata ammi karama bazata wuce 40yrs ba dan kuwa da danyar shekarunta mahaifin ibaad din ya aurota tun tana yar 18yrs a duniya, bayan aurenne ta haifa ibaad while she was just 23 Sai kuma tay ta samun ɓari Allah bai kara bata haihuwa sai da ibaad yacika 7yrs a duniya tana daf kuwa da haifar yar autarta safiya mijintan kuma ya rasu..
kwance tashe gashi wai har ibaad dinta yadoshi 18yrs kuma har yafara karatun dream course dinsa shida babansa wato medicine, wanda yasaka take dada mika dumbin godiyar ta ma Allah da kuma bappa zaidu dayayi tsayin daka akan rayuwarta dana y'ay'anta wajen ganin sun cika burikansu na rayuwa tun mutuwr ubansu har gobe.
da fara'a ta tarbe su maheer ne yafara neman waje akasar capert ata gefen hagunta ya xauna yana murmushi me sanyi shikuma ibaad din ya karaso tagaban ta tare da zama dab da ita kusan atare suka hau gaisheta tanamai saka musu albarka cikin fara'a da dattako.
hirar karatu suka fara da maheer kadan dake sun saba da juna sosai akabar ibaad din yana kalle kalle, can cikin katsesu yace Ammi yana ganki ke kadai anan, safiya fa? badai taje tazuba kananan idanunta tana kallon indian series ba. dan murmushi ammi karama ta yi tace.."a'a..tasan ai zaka zo, so i am sure tana can dakinta tana fmr duba karatu...tun kan ya fara mita tay saurin maida hanklinta kan maheer tana cewa babban mutum tashi ka zauna kan kujera toh bare naje na kawo muku abin taɓawa, kan maheer a kasa yana dan murmushi ya amsa da toh dan bakaramin kaunar tsaftaccen qamshi da taste din girkinta yake yi aransa ba, shi hasalima abunda yafiye sakawa yake mutuwar son babansa ya aurota kenan, tana da tsafta, gayu, ga kamala, da nutsuwa snn yafiso ace sun zama tamkar uwa daya uba daya da su ibaad acan gidansu,bai fiye nuna wannan raayin nasa ma kowa bane sabida baison mahaifiyarsa ammi babba taga kamar yaci amanarta har tay fushi da shi.
ammi karama tana wucewa kitchen bada jimawa ba sai ga 10yr old safiya ta fito kanta babu dan kwali tanata callara wakar tashar style life its a beautiful world sabida batay tsammanin har sun iso ba. wani yaye labulen tayi caraf kuwa suka hade ido da ibaad da wani irin sauri ta sunkuyur da kanta kasa jikinta ya fara rawa ahnkli ta mannu da bango tace "i ii na wuni yaa ibaad? sama da kasa ya kalleta da daurarn fuska muryansa a mugun shake yace 'sallamarki kenan?
wani zirr hawaye ya ciko mata a ido cikin matsanancin jin tsoronsa ta girgiza kai tace" a'a, sai kuma ta fashe da kuka ahnkli, mikewa yay kamar zai falla mata mari, tay sauri taje taɓuya ajikin maheer da yay saurin tarota jikinshi dan bakaramin tsoron ibaad takeji ba, wani uban tsawa ya daka mata .."kee, uban me aka miki da kike kuka anan, ina wasa dake ko? dada shigewaa jikin maheer tay sosai muryanta na rawa tana cewa kayi hakur yaa aini bansan kazo bane, cikin kara daka mata tsawa yace au sai nazo gidan nan kenan kike abu kamar mutum ko,? toh maza kiwuce kije kisaka dankwali akanki, snn ki dawo nan..ina dai saikinji zanzo ne kike karatu, seee, i am giving u 3 scnds to grab all ur books and come back here yau saina ci ubanki...
da wani irin mugun tsorata ta saki jikin maheer din taballa da gudu kamar zata fadi kasa ta koma ciki tana kuka sosai, maheer dai kallonsa yake yasan dai wann bacin ran bana lfiya ba dan jikinsa nata bashi cewa lallai da akwai abunda ya bata ma ibaad ransa yau sosai,
kmr kiftawa da bismillh sai ga safiyan ta dawo da jakarta na makaranta tun daga kofar falon ta doka musu fulll sallama jikinta sai rawa yake hawaye na zuba mata tana kan tarewa da oversized veil din data rufe kanta dashi ,wani irin mugun kallo ibaad ya mata snn ya bata izinin shigowa ciki, still ta gefen maheer din taja ta tsaya, yaja tsaki yana juyowa zai kwace jakar suka hade ido da maheer girarsa sama a dage ahnkli yace hey mr temper, please kabarni da ita i will take it frm here..ibaad baice masa komi ba ya kalli safiyan yace ke zo nan..da dan uban sauri ta karaso ta tsuguna agabansa, yar nasiha maheer din ya mata akan tana nitsuwa, snn ta rage kallon series at dis young age ta fuskance karatunta kawai, ya mammata nasiha cikin lumana, ibaad na shiru bai kara cewa komi ba, dede ta bude assignmet dinta na farko da batay ba kenn sai ga ammi karama ta dawo da katon tray a hannunta mai dauke da manya manyan matured colour cooler dan kusan duk kayan kitchen inta daga wjen uwargida collection kawai take odersu.. cikin nitsuwa ta shigo tana cewa i am sorry i kept u waiting ko wsu ababen packagin nake nema bansamu da wuri ba.. tun bata gama surutun nata ba cikin sauri ibaad ya miqe yaje ya amshi tray din a hannunta suka karaso cikin falon tare, murmushi me sanyi tay ganin maheer na kan nuna ma safiya yadda zatay asigment dinta ayayinda safiyar ta bashi hanklinta sosai ta nitsu..
"babban mutum ka kyaleta kazo kaci abinci safiya kam ma ai na gaya mata aure zan mata kwanan nan dan naga gabaki daya wasa ne aranta bata kaunar karatu sai ta ganku, gidan nan dai duk wayake suwa 3rd position a schl in ba ita ba, ko kunya fa bataji
maheer na murmushi me sanyi yace aa Ammi haba aibaza ai mata haka ba she will grow up nd bcm a very succesful Data anlyst dan naga tafi iya lissafin computer ko ba haka bane safiya?
hawayenta ta share snn ta dago kai zatay magana wani mugun harara ibaad ya kara balla mata da sauri ta maida kanta kan littafin bata kara dagowaba.
suna kammala zama akan dinning ahnkli ibaad yakasa haquri with serious tone a muryansa yace ammi dan Allah kidena saurin gayamata cewa aure zaki mata da wuri karma ta sa shirmen soyayya aranta taki yin karatu, cikin katsesa da mamaki maheer yace dude relax, this is all fluff.. tsorata ta kawai ammi takeyi dan ta nitsu, cikin kyabe baki ibaad yace "auren ne zai sakata nitsuwa? in ana gaya mata haka babu wani tsoratar da zatay saidai ma ta kara saka abun aranta if not at dis age menene take kalla a indian series inba shirmen soyayyar karya ba, dahaka ne da suke saka abun aransu kaga yarinya karama wai tafara bin namiji... ammi dake kan jinsu batace komi ba tanakan bude warmers inta ahnkli wani irin qamshi ya katsesu maheer zaiy magana cikin katsetsa tace ya isa haka nifa bance kuzo kuyita musu agabana ba abinci kawai zakuci maheer please grab ur plate for me..da zumudi maheer ya bar maganan ya tura mata plate dinsa dake ta gabansa
wani dan ubansun Dambun Shinkafa da Nama tay irin nasu na mutenen maiduguri she steamed it with beef, onions, garlic, and butter, but she infuses it with Arab baharat spices dan ya kara masa dandano na musamman.
wani irin lumshe ido ibaad yay cos dambun shinkafar mamansa is his long time favourite maheer yafara lashe baki tun bata gama zuba masa ba ya dau cokali ya rike suna kallon juna da ibaad da tunanin irin dukan da zasuy ma abincin
ganin yanayin reaction dinsu yasa ammi ta zuba wata sasasnyr murmushi, tana gama zuba ma maheer nashi ta zuba ma ibaad shima snn ta bude wani cooler ta debo surprise din data ce zata masa yasha mamaki kuwa da yaga Fattah Lahm, special shuwa danderu ne da bata fiye yi ba dake da flat bread ake cinsa kamr shawarma. yana da mugun dadi dan is A whole hearty dish of slow-cooked lamb in spiced butter, layered with irin torn flatbread din nan, and the whole combo is soaked into a rich romon nama dayake tashen kayan yaji dana qamshi.
maheer nakaiwa baki yace wayyo Allah na ammi kin kasheni this is the besttttt food ever, dariya ammi ta farayi ganin banda bismillah ibaad bai ce komi ba kawai cin abincin yake kmr wanda yay shekara baici abinci ba, duk hirar da suke sai dai kaji ana uhmm uhm
safiya ta kafe kanta a asgment qamshin abincin yacikata amma sabida ibaad yasa batakoy gigin dago kanta ba.
bayan sun gama ci to the fullest ammi ta basu herbal tea inta me lemon tsami aciki suka sha, suna kan sha ana hirar karatu sama sama wayar maheer din ya fara kara ganin lambar mamansa ne yasa yayi excusing dinsu yabar sashen cikin gaggawa dan ya san halinta sarai ta tsani taji zancen yabiyo ibaad sunzo wajen ammi karama.
fitar maheer bada jimawa ta kalle ibaad din dake famar gode mata da abincin ahnkli tace its okay, dama haka kawai yau naji in maka abincin daka fi so yau and since u liked it ai shikenan
..ynx tayani tattarawa muje kitchen i want to have few some words with you alone.
..baice komi ba ya miƙe dan shikansa badon wnn yummy food treat din nata daya samu ba hala da tsananin bacin rai daya kwaso agidan kawu babba dazu zaiyi bacci..
cikin tsaftaccen kitchen inta dayaji jeren yan gayu suka shiga dede wajen sink ta juyo ta amshi tray in a hannunsa snn ta bude fridge ta fito masa da ruwa me sanyi wajen miƙa masa suka hade ido
daya kalleta saikuma yaji mugun tausayinta da kuma haushin shirun dayayi dazu ana zagar masa ita
suna daga tsayen taga mood dinsa ya fara canzawa cikin nitsuwa ta juyo dakyau tanata kallonsa ahnkli tace 'yadai rayyan, nikam ko baka jin dadi ne nide tun jiya kaketa faɗo min araina..ina fatan..
cikin katseta yace "Ammi, i am fine. kidena daga hanklinki pls
cike da yar maraicewa tace hmmm, badon kar yaa zaidu yay fushi ba yau danace ka kwana min anan but i get it, akwai schl kuma dama shi zaifi saka maka ido acan kayi karatun saidai bansan matarsa ba..did she still treat u diffrntly.,
ahnkli ya girgiza kai yace aa, cikin kauda hirar yace ammi, bappa bai gaya miki cewa kawu babba ya kirani gidansa bane???
waje ta kwalo idonta tace wani kawu babban? kana nufin bappanka prof zayyanu ya nemeka gidansa dabai barin uban kowa yaje?
tun be amsa ba adan tsorace tace 'why? wani abu marar kyau yakara shiga tsakanin ka da yarsu ko rayyan? dan Allah ka rufa min asiri mana ka fita aharkan yarinyar nan..ransa a hade cikn katseta yace haba ammi in fita aharknta kode sufita aharkata? tace ban gane su fita aharkan ka ba bayan kaine ka dakar musu yarsu yar kwai, wai kuma kana tunanin zasu yafe maka ne cikin sauki?
yace but dats like many months ago ammi. karamin scoff tay tace" okay, just tell me what was the meeting all about. kar ka boyemin komi..bana son wani fitina ya shiga tsakaninka da su musmn ma akan yarsu kana gani dai har hajy mairo prof bai kyaleta akan yarsa ba bare kai da baka da ubanka araye.
dan lumshe idon sa yay kadan kafin nan ya bude ya kalleta da sanyin jiki snn ya fara gaggaya mata duk abubuwnda suka faru muryansa kamar na wanda zai mata kuka, yace ammi, bayan cin fuskar da sukamin wai they still want me ina zuwa gidansun akai akai dan kawai hankalin yarsu yana kwanciya, nide ammi dan Allah u have to talk to bappa zaidu abt this, inajin nauyin inje ingaya masa kai tsaye cewa bazan kara zuwa ba batare da na bashi kwakkarn dalili ba,amma wallh bazan iya kula musu da yarsu ba,akan me? ni kaina abubuwa sun fara min yawa na karatuna i need to focus..nd for god sakes bazan je inda za'a na zaginki da sauran yan uwana a gaban idona ba..
wani irin shiruuuu ammi karama tay batace masa uffan ba for almost five mins tana jinjina maganan sai can taja ajiyan zuciya tace hmmm toh Allah ya kyauta,
cikin kwayar idanunsa ta juyo takalla ahnkli tace "rayyan, toh duniyar ma nawa take bare abun cikinta.. jarabawa ne kawai ..kaima kasan kafi karfin amaka gori da maraicinka tunda ban mutu ba ina raye kawai hakuri duk zamuyi dasu. bt in sha Allah zan yi magana da bappan naka kai kuma sai ka cigaba da masa biyayya dan Allah kar kadinga saba masa, know dat i am alwys here for you..Allah zai kawo mana sauki, kaji ko? ajiyar zuciya me nauyi ne ya kusan kufce masa ahnkli yace toh Ameen ammi and thank you alot for spoiling us i wish i can eat dis all day long.
..kyakkwn fuskarsa ta shafa kadan tana yar murmushi tace karka damu i hve packed some acikin take aways wanda zakuje gida dashi sai kuci dede nan aka kwankwasa kofar kitchen din maheer ne ya shigo looking so awkward, ya samu dede ammi tana kkrin ciro take away rubbrs din madaidata har guda uku babu jira ya shiga tayata har suka gama tasa musu a ledoji, wani sabon shafin hirar sukayi cikin wasa da dariya wajajen 9:40 suka ce mata zasu koma gida lokcin safiya ta gama duka asigment dinta still ibaad ya mata fada akan kallon series snn yace mata bazata kara cin abinci ba kawai ta wuce taje ta kwanta haka kuwa tawuce daki taje bacci har suka bar sashen sukaje suka gaida uncle moh da anty safeerah a shashensu snn suka bar gidan mai gabaki daya
cikinsu a matukar koshe suka kamo hanyar GRA maheer yana ta tsokanan ibaad wai kodan abincin da sukaci ne yasa yadan saki ransa, shide bai wani bashi amsa me kama hankli ba har suka isa gida me gadi yana bude musu gate sukay parking suka sauko da ledan abincin riki riki ahannun maheer suna isowa sama ibaad ya mika masa key din mota yay sauri ya haura gaba, da wani abu aran maheer yace hey Dan Allah kazo muje wajen baba atare mana waime haka inbazaka je bama ka amshi ledar abincin toh ka rike, ibaad yana ci gaba da tafiya akan stairs yace aa bazanje wajensa yau ba kaidai kayi sauri kafin afara wasar psg da chelsea bakazo ba, kai tsaye dakin maheer din ibaad ya nufa tun be amsashi ba, dake shi maheer har tv yana dashi adakinsa.
cikin girgiza kai maheer ya rabi hanya yawuce sashen bappa zaidu har ya kai kofa da sanyin sallama a bakinsa samunsa yay a zaune akan arms chair shi daya yanata kallon tashar larabai wanda tunkan ya amsa sallamar daddn qamshin abincin ya fara bugosa nd its sound really familiar dan yasan irin wnn qamshin inba girkin fatima ba toh saidai in mamansa hajy mairo mai tuwo ce ta dawo
cikin ladabi maheer ya rusuna yace ina wuni baà, idon bappa nakan ledan abincin yace lafya har kun dawo? ya mutane gidan kuma.. yace lafyarsu kalau dama uncle moh yace in gaya maka wai zaizo ya sameka da safe a office akan batun dawowar hajiya..
bappa zaidu yace "toh Allah ya kawosa sunyi waya da hajyar ne? inaga karshe ibaad kawai zamu tura ya dawo da ita tunda abokin fadanta ne amma kuma tafi saurararsa. gskiy she needs to come home yanxu kauyukan nan are not safe att all.
maheer yace hakane uncle moh yafara gaya mana wai jiya an mata satar generator a shagonta case kawai ta wuni tanay a police station da mutane acan..
bappa zaidu yace hmm mama kenan koda tana da kudin siyan dubunsa sai ta so akama barawon nan just to put him into justice nd dats way more scarier, ynxu fa duniyar ta zanca mai gaskiya bayayin farin jini. ina shi ibaad din inafatan dai baka barsa acan ba?
dan shiru maheer yay kafin ya dago a nitse yace aa tare muka dawo amma yana can daki na.'..
bappa yace ohh, to mesa bakuzo nan tare ba, lfya kuwa naga bai gaya min komi game da zuwansa gidan kawun nasa ba..
cikin gyaran murya maheer yace umm about that.....
bappa zaidu ya dada mikewa zaune yana kallonsa cikin nitsuwa yace "wani abu yafaru ko?
kansa akasa yace baa is not like he talked to me directly amma i overhead him yana gaya ma mum dinsa cewa wai so kawai suke yana zuwa gidan dan hanklin yarsu ya kwanta and.....sai yay shiru...
bappa ya masa wani irin kallo yace and what maheer karkay wasa dan hanklina anan mana..
yanadan sosa keyan kansa ahnkli yace 'baa, i dont think they treat him well..he mention sumtin abt zagin da sukama mahaifyarsa agaban idonsa akan zainab, baba cemishi fa sukay wai hala dad dinsa yana dukan mum dinsa ne yana gani shiyasa shima ya girma ba'a bashi tarbiya ba kuma wai duk yunwa ne ajikinsa, they even cooked him a separate meal hmm maganan dai da yawa..
komawa jikin chair bappa zaidu yay yana girgiza kai ahnkli ya furta hmm, snn yace "rubbish, sai kaga mutane kamar sun waye but they are so petty
..wann ai karanta ne. dama nasan za'ayi haka, idankaji kiransu badai don Allah bane saidai in suna buktar wani abu ajikin mutum suke kulasa, but i wont let them insult him again karya suke wallah, kai.. tashi kaje nasan me zanyi ai bakomi..
maheer baice komi ya aje keys din benz din akan table zaija ledarsa ya fice kenan bappa zaidu yy gyran murya yace "waimeye ne acikin ladan nan ka shigomun dashi me qamshi...
da zumudi maheer ya juyo yace ammi karama ce ta mana abinci me masifar dadi dama sauran ne tabamu wai mukawo gida mu karaci...
cikin mugun muradin son yaga yaci abinci me tattare da wata iriyar kamiya bappa zaidu yace ohhh toh dama wakanku kawai kuka kawo kenan..
maheer yace a'a ai tabamu hada extra nagawai baka cin abinci ne in dare yay sosai, but if u will like to eat saina serving maka, cikin jan aji bappa zaidu yay shiru sai can yace kawo dai in gani, what did she have here dan ban fiye son cin abinci late ba..
nan da nan maheer ya bude ledar ya ciro roban take away din guda daya ancika shi dam ga dambun ga babban sokar nama ga kuma phatta lahm da romonsa agefe an shiryashi very neatly komi gwanin sha'awa, ana mika masa tunbai kai ga gama budewa ba qamshin yasakashi lumshe idon dole domin karyay zumudi agaban dansa ya dan hade rai maheer yana ta batun kawo masa spoon yaga gogan har ya buɗe abincin ya aje murfin akan table yana kkrin tashi yaje ya wanke hannu a hand washing sink dake falon aikuwa suna hada ido ya balla masa wata dakalken kallo yace" kai baynxu kace min kunci naku abincin acan gidan ba to uban me kake ta kallon nawa kuma??
maheer yay kamar zaiy dariya yabi ya gintse kayansa ya kama hanyar waje
bappa zaidu yana gama wanke hannu ya jawo abincin hannu abaka yay bisimillah yay wata makahuwar loma wa dambun ya kai bakinsa wanda tuni yaji wani nitsuwa dan baisan wani dunia dadin girkin yakai sa ba,.. ahankli lumshe idonsa ahnkli yana furta kai masha Allah, but fatima can cook oo, da ynxu ninace tamin irin haka bazata taɓayi ba saraunyar kunya...
kusan kasar wuyarsa ya furta hakan amma xurum kalaman nan suka fada acikin kunnen matarsa ammi babba da zuwanta kenan ko sallama batay masa ba tun ganin maheer da tay awaje da ledan abinci tasan za'a rina, ranta a dagule ta shigo tana kan huci ta bi ta tsaya masa akai a mugun tsime tace "yaa zaidu kenan ma aka samu haka aketa hanɗama kamar baka tabacin abinci aryuwarka ba"
..romo dumu dumu abakinsa ya dago kai ya kalleta yace" yaran nan ne suka dawo dashi daga can gidan shine nima suka sammin".
wani irin runste ido tay cikin daga murya tanamai cewa "aa malam dakata min, karka raina min hankali mana kawai ka fito fili kace dai kaine ka aikesu wajen tsohuwar farkanka da Allah baiyi zaka aurota ka tozartani akanta ba, sunje sun karbo maka abincinta kazonan kana ci ham ham sai kace bantaba maka girki agidan nan ba yaa zaidu gaskiya cin fuskr da kake min agidan nan fa ya fara isata..
cikin katseta da dakakken muryansa me razanarwa yace keeee, da Allah ya isheki haka baki gani inacin abincine kifita kawai kiban waje inci abinci na cikin kwancyar hankali dan duk wnn kananan maganan dakikey duk ke kika san su can miki.
wani kukan kura tay zata kwace kwanon ya wapce abunsa gefe suna hade ido yace raihanatu am warning you.. kinsan dai idon yaran nan biyu basuy bacci ba banason inci mutuncin ki anan wjn agabansu kiga lefina so just get out...inna gama ci kya dawo kiyi baccinki...
tsabar bacin rai kirjinta har na dokuwa take harararsa a zafafe tafara daga murya tana cewa ohh hakama zakace min?
toh wallh wallah ba a isa ba
ganin bakulata zaiyi ba kuma bai fasa cin abincin ba yasa ta fashe da kukan takaici ta fice waje a mugun zafafe..
dakin maheer din ta nufa kai tsaye tahau bubbuga kofaraa kamar an korota lokcin har sun kunna tashar ball sun fara kallon kwallo shida ibaad, it was hell of a ryd tsakanin chelsea da PSG...
buga kofar datay da karfi yasa suka razana maheer ya mike tsaye cikin sauri ya fito, da mugun sauri ibaad shima ya taso yana biye dashi abaya baya
..suna bude kofa suka gan ammi babba atsaye sai huci take kamar kububuwa hawaye taf fuskarta
kan maheer a daure yace mumy lafya kuwa? muryanta har na sarkfewa tace "Ina tsinannen abincin da ka kawo gidan nan
zai magana sai wani tasssss yaji diran yatsunta akan kuncinsa shikansa baisan sanda tasakar masa wata makuhar mari me kara ba..
ranta a mugun bace cikin dakamai tsawa tace Baqin munafuki kawai... Allah wadai naka ya lalace,.maheer wato ma dakai ake haɗamin baki anayin barbade ana asirce ubanka ta hanyar abinci ana kawo masa gidan nan haryana walakntani akai dan kawai a fitar dani agidan mijina wata shegiyar karuwa ta shigo toh wallh wallh bari kaji inma baka sani ba ranar da kasaka fatima ta shigo gidan ubanka ƴayanta ne kawai zata cigaba da cusawa a zuciyar baban na ka kai da kanwarkan kuma saidai ku kare abin titi kamr marayu, ince dai nice kawai baka so agidan nan? wawa, banza kawai shashasha wanda baisan abunda yakeyi ba...munafuki kawai.
wani irin shirrruuu dukansu sukay sunata kallon ta har hawaye yafara zubowa idanun maheer musmn data juyo kan ibaad ta fara zaginsa ta uwa ta uba tana kiran uwarsa karuwa, mushrika shikuma ya daure sosai sai haquri kawai yake bata sabida yana mugun ganin girmanta
kusan a zuciye maheer yasake kofarsan da karfi jin abin yafara ishenshi kusan tureta yay ya wuce ya fice can can waje da mugun sauri yana wani irin hawaye me zafi, tana tsaye har ibaad ya sauko shima yabi bayansa hanklin sa atashe saida suka kai kusa da gate snn yaci nasarar riko sa suka ja gefe dukan su da hawaye kwance akan fuskarsu...
ganin yanayin maheer yasaka ibaad ya share hawayensa cikin dauriya dan maheer yakai minti goma yana hawaye ji kawai yake ibaad din na danne nashi yanata bashi haquri amma bai iya dena kuka ba..
sai can ibaad yace 'okay fine tunda baza kace min komi ba gara naje sama ynxu na same bappa na gaya masa ni zan koma gidanmu kawai, i can't deal with this shit...kusan a sanyaye ibaad ya sakeshi ya juya zai bar wajen sai ji yay maheer din ya damko hannunsa da karfi tun kafin ya gama juyowa ahnkli yaji ya fado mai ajiki suka dan rungume juna araunane...
tantame ibaad din yay yana hawaye muryansa na rawa rawa yana cewa ibaad dan Allah kayi hakuri karka gayama baba ko Ammi wann maganan izuwa ynzu kusan kowa ya san halin mumy amma nasan da ciwo ana alakanta mahaifyarka da wann kalmomin datake furtawa, i am begging u pls dont take it to heart wallah baaba yana kaunarmu tsakani da Allah nasan duk abunda take fada maka borin kishi ne kawai pls dont take it to heart....shikansa inyaji wann maganan zai iya mata hukunci me tsauri musmn ma ynxu inkaje kace mai zakabar gidan nan sabida ita..
cikin katsesa ahnkli ibaad yace "i am not leaving maheer..'i am apologising to u sabida nine nake jawo muku matsalar ita kuma ai mahaifyrkace, maheer dan Allah kadena kukan nan ya isa haka wnn misundertanding ne tsakaninsu mukanmu bazamu taba iya ganewa ba kawai mubar komi wa Allah
..dakyar maheer ya shanye emotions dinsa ya dago ya share hawayensa ya kalle ibaad cikin ido yace "promise me bazaka bar gidan nan sabida halin mummy ba..
..ibaad zai budi baki ya kara katsesa sounding desprate yace please ibaad..for his sake..nd for my sake..i know ure going tru alot amma kasani i wll neva let u carry all this burden alone
..i will alwys be der for u as my friend nd brother, nasan abubuwa suna maka yawa nd i am sorry, i also overheard abunda kawu babba suka maka agidansa u dont have to worry abt all these things.
...cikin lumshe ido da budewa ibaad yace ohh please, lets not talk abt that..'
maheer yace "we will, dan nina gaya ma baaba iya abunda nasani, duk abunda suka maka wanda naji nagaya masa.
cikin kwalo ido da mamaki ibaad yace kumawai a ina kaji?
..maheer yace just forget it, nide nafiso koma me zamuyi lets not do anything da zai kara raba kan familyn nan u need to just hold on abit..
yace what? "maheer, did you think i am not holding on? inba dan ina danne zuciyata ba wallah da bazantaba zuwa gidan ba har abada dan yarinyar ne kawai gabaki daya bata min ba, yes, she is fine princess, with her insanely rich parent, but she is this batterly spoilt, damn arrogant, mannerless nd so so much more.... classeless... halayenta da i cant even stand them..duk da ban taba mafarkin yin soyayya ba, but i know in my hrt dat i wont eva be able to like Zainab arifah..she is not my type and she is not going to be.
kafadunsa maheer ya dafa ahankli yace 'But Ibaad, somtimes u cant beat a river into submission if not it will drown you, mafi maka alheri shine try and submit to the waves ahakane kawai zaka iya kwatar kanka, i think she is just obessed with u..in ita yarinya ne ai kai ka girmeta. nd by the time tazo fa mallake hanklin kanta she will grow tired of ur attitudes and plus i am sure kawu babba ma zaizo ace mawani mashurin mai kudin zai aurar da ita...just chill with her for now kay hakuri kawai ka biye musu..wani fadar ba acinsa da yaqi.
ibaad baice komi ba kawai ya dan lumshe idonsa for a while kafin can ya bude idon cikin kyabe baki yace ure probably ryt, i may need to just let it be, cos i bet bfr she reaches 18yrs ma hala ta tsaneni dan ba lokacin ta zanyi ba
..dariya mai sanyi maheer yay baice komi ba ya girgiza kai snn suka samu waje suka zauna awajen subiyun su suka dan kara tattaunawa akan wasu abubuwa dake gudana acikin gidansu harma da batun dawowar hajy mai tuwo gida, after a while arnd 12.30pm na dare suka koma cikin gidan suka samu waje yay shiruu tvns maheer ne kawai a kunne harma angama ball din daga sai kawai kowa ya wuce room dinsa ya kwanta....
washe gari sa safe tun bayan fitarsu sallahn fajr da suka dawo suka fara fahimtar kmar tsakanin bappa zaidu da ammi babba ba ai kwanan lafya ba,dan kwata kwata wani gigin rashin mutunci ne a idanunta, yaran nata na cikinta ma kaf tadena amsa gaisuwarsu tace duk munafukaine suna goya ma babansu baya yana soyayyarsa a boye da ammi karama, haka kuma batay breakfast a gidan ba, hasalima wakokin zube na hausa masu cike da tsagwaron habaice habaicen banza da wofi ta kunna asashentan jiddidin wala hairan tanatajinsu shikuma bappan zaidu ko ajikinsa dan tun jiyan dq sukayi fada akan marin maheer datay sai ko kala bai sake ce mata agidan ba,abincinsa dana iya wanda yaransa zasuci kawai yakeyin oder daga restaurant akawo musu suci snn kowa ya wuce makaranta, mugun shareta data ga kowa yay sai yayi mata ciwo aranta bana kadan ba musmn ma maheer daya fara nuna mata danyen kai da fallin balaga waidan ta maresa shima sai yadau zafi da ita sosai tsakaninsu daga gaisuwa baiyace mata komi haka zai hade ransa yawuce schl, kai ko irin hakurin nan na lallashin uwa baizo ya mata ba, haka tay ta fushi tana cin magani tsanar datake ma ibaad kuma sai ninkuwa yakeyi aranta, gashi ansama ma sultana private lesson teacher ba wuni takeyi a gidan ba har yamma tana schll haka zata wuni ita daya agidan tana famar sake sake
saida aka ci kusan kwana hudu tana wann haukar borin kafin ita dakanta tayi yaji tabar musu gidan can da dare kuma wani babban yayanta wanda baiya daukar nonesense yadawo da ita gidan yamata masifa snn yayita bawa bappa zaidu hakuri akadan yi musu nasiha snn ta dawo daidai.
a satin gabaki daya gidan ya kasance sam babu wani armashi, Maheer yanata kkrin fara exams ne dake law yakeyi ayayinda ibaad din shima yake fafutar nasa karatun a fannin medicine wanda acikin satin ne kuma prof da yarsa zainab arifah suka fara kafamai ƙahon xuka, duk yamma ko dare sai ya kirasa awaya snn yabi ya hadashi da zainab Arifah hirar dole, surutun banza da wofi dana tarukucen yaranta duk zatayi ta masa akunne kuma agaban babantan sam batajin kunyar kowa,
hakama tun daga daga schl prof zai aika driver ace ma ibaad maza ya samesa a office dinsa
yana zuwa kuwa zai bashi key yace masa yajeshi makarantar su zainab Arifah din yadauko masa ita a schl yakaita gida, ko yace masa bata da lafiya tanata kuka taki tabi driver wai sai shi, ko yakawo masa wani silly uzuri nadaban dan kawai suna kasancewa tare.
kwana biyun nan prof bakaramin zagewa yakeyi yanata kkrin cusa yarsa acikin rayuwar ibaad ba,
gashi kai tsaye yake nuna iko da gadara dashi sam sam baiya masa uzuri, badon komi ba saidan kawai yarsa tasamu tagama cire ciwon damuwar soyayyr nan nasa aranta tanitsu har tay karatu dan bakaramin bright future ya shirya mata agaba ba.
tun bappa zaidu yana dakatar masa har abun yaso ya dawo musu babban rigima ganin sosai da sosai suka fara takurawa rayuwar ibaad din.
dan haka kawai in ya kira Ibaad zai sakashi yin wani silly abu wa zainab din daga yace bappa zaidu yace a'a prof ne dakansa yke kira ya zage zage yayta bori yanamai cewa wai anaso ne anuna masa warayya akan ibaad in har bai isa yay iko da ɗan yayanshi ba. tun bappa zaidu yana fito na fito dashi har ya hakura ya dawo bawa ibaad din hakuri, ita kuma zainab arifah rayuwa ta dawo mata sabuwa mai cike da nishadi da jin dadi, dan tsabar ta samu daurin gindi da dama kusan duk snda taji aranta tanason ganin ibaad haka zata narkewa babanta har sai an nemo matashi..
satin nan kusan shine masa lokaci mafi wahala da takurawa, ga fitinan ammi babba agida ga kuma prof da yarsa zainab arifa ga karatunsa...
bayan kamar sati guda wani tunani bappa zaidu yay yau sassafe ibaad ya fito daga sallah zai wuce daki kenan ya kirasa agefe yace masa ya shirya kawai daga ya dawo daga schl yau zai bashi mota yajeshi anguwan tudu domin ya duba musu meyake faruwa da case dn sata da akeyiwa hajy mairo mai tuwo acan, snn in abun bazaiyu ba kawai ya lallaba musu ita tabar kauyen ta dawo nan gida.
ibaad baiwani son yin tafiya on short notice musmn ma da bada maheer ko dayan kaninsu mujaheed zasu je ba, but, the joy of geting a break daga fitinar zainab arifah da mahaifinta yasaka yay murnan wann tafiyar aransa sosai.....
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[30/10, 20:10] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️1️⃣1️⃣
the same day
6.30am
thursday
garin majiya
Azaune kusa da inda inayah ta idar da sallahnta na fajr data dawo yinsa a zaune wani bacci me mugun nauyi da minshari yawuce da ayaanah, duk dama sanyin safiyane amma su biyune kacal acikin dakin maman nasu
daga inda inayan tay sallan tazuba farqren raunattacun ruwan idanuwanta masu cike da rauni da tsumayi akan kyakkwar fuskar kanwarta ayaanah wanda hasken kwan fitila mai gauraye da ketowar hasken alfjr ne kadai yake dada illuminating dakin wanda ya dada kawata nitsattsen kyaun ayaanah mai tsananin sanyi da kawata ruwan idanun duk wani mai kallo,
daga gani baccin kawai takeyi amma da alaman cewa batasan yaushe baccin ya dauketa ba dan tun da addanta tafara ciwon nan itama ta kasance sam bata samun wani nitsuwa...
wani irin shiru dakin yay tamkar babu kowa aciki dan akai akai inayahn take sauke ajiyan zuciya me nauyi da kuma tsananin rauni ayayinda ruwan idanunta suke akafe akan kyakkwar fuskar yar uwata ayaanah datake matukar kauna
can sai taji tsillin hawaye me tsananin zafi yana sauko mata akan kuncin ta, hannu takai zata goge su sai kuma taji gabaki daya hawayen nata yana kara tulowa da masifar yawa da tsananin zafi mai tsaga kahon zuciya..
wani irin lumshe ido tay dan aranta ji kawai take kamar yaune ranar ta na karshe da zataga fuskar yar uwanta a rayuwarta, dan ciwukan datakeji ajikinta haryau bata isa ta faɗi irin azaban da suke dandana mata agangan jikinta ba, itade aranta bata kawo batun mutuwa, ko rabuwa ba, amma tabbas tanaji kmar kallon karshe kawai takey ma ayaanah yanxu batasan kuma meyasa takejin ahakn aranta ba.
tun wajajen biyar da rabi tawuure ta saci jiki taje jejin daketa bayan gidansu neman wa inayan saiwowi na magani dan yau kusan sati guda kenan suna fama da jikinta, yau yay sauki gobe yay muni, gashi maganin datake yawan batan kafff ya kare da kyar da wahala juma ya sauko daga fushinsa harma ya janye kalamansa na cewa koda kofar gidansa ta taka toh abakin auren ta, anguwar tudu kuwa haryau yana kan bakansa nacewa inhar ta taka kafafunta taje tudu batare da izininsa ba ta dauka kawai tamkar ya saketa saki uku kenan har abada, ahakan ma wai saida yaga zahiri jikin inayar yana dada ragwabewa kullum da matsancin ciwon ciki me tsanani ne kafin ya basu wnn dama
ciwon cikin inya tashi mata har kamar kyarman mutuwa takey, hakan daya lura yagani ne yasaka ya kyale taawure tafara fita cikin jeji tana neman saiwowi wanda duk dq ta jika su tana bata amma duk baima inayan komi.
yauma da asubahin fari ta sake komawa jejin dan ta zanzo wasu saiwowi, dan izuwa yanxu ita kanta duk ta galabaice zuciyarta da jikinta sun fara sanyi da yanayin ragwabewr jikin yarta inaya, inaya bata iya cin abinci ta rame sosai, duk tasa abu abaki saita amar dashi, ga rashin samun bacci, ga ciwon ciki me tsanani mai kumburi da uban zafin ciki duk inayahn ta rame ta kanjame kamar ba ita ba kusan kominta ynxu a zaune takeyinsa daga bayi, wanka har sallah sam bata iya mikewa da jikinta a tsaye kamar normal mutane.
tun asuba taawure ta fita amma kafin ta samu wasu saiwowin saida ta kure tafiya can can cikin jejinsu dakyar ta debo ganye da saiwowin binida zugu, lemon grass na jeji, da goruba,goga masu da ganyen kuka dana rai dore da wasu saiwowi na jejin fulani duk takamo hanyar gidanta dasu cikin sauri dan already har karfe bakwai ya kifta sosai, saida ta zo daf zata fice acikin jejin snn taci karo da wani mutum acikin ciyawa yana tattaran itace akan kekensa,
kallo daya ta masa tagane Dandanko ne, da wurwuri ta dauke kanta bata ko masa magana ba, cos just as his name implies, dankando mutum ne daya kwarance wajen iya yaɗa gulma da ƙarya dan kawai ya tada zanne tsaye.
tun hangota dayayi ya gama saka mata ido yakarance duk ganyen magani da saiwar dake hannunta, dama kuma yaji kishin kishin anacewa acikin yaran juma akwai wacce take kwance tana ciwon ciki aransa kawai ya riga ya kudura hala cikin shege ne tunda ya jima yana kawo suka da tsegumi ma juma akan barin taawure dayayi tana zuwa tudu tay watanni acan tana kasuwanci da yaransa mata, acewarsa ai tudu kamar bariki ne kuma yayansa duk balagaggu ne zasuje ne su koya halayayyar banza mazan bariki zasuna kwana dasu acan, ya jima yana cusa wann maganan a kunnen mutane bai samu nasara ba, dake juman bawani zama yake a gari sosai ba idan yaje can boda yin kasuwanci dayaga ya dawo kiwo ko noma kawai yakeyi gulma bai fiye riskansa ba....
tun dayaga taawure da saiwowi haka ya dinga binta yana mata tambaya akan wasu ganyykin maganin data debo duk dama taki sam ta kulashi amma be fasa ba
adai dai kan gaba suka rabu, tay sauri ta shigo cikin gidanta bata ko leƙa yaran ba ta wuce madafi ta samu har ayaanah ta farka ta fito ta kunna wuta ta dora ruwan kunu ta kuma shirya dumamen tuwo cikin tukunyarsu na kasa amma bata dora ba.
Albarka tasaka ma ayaanahn a zuciyarta dan tunda inayah tafara ciwo ayaana ce ke kkrin yin aikin gidan sosai. nan ta aje mayafinta kafin ruwan kunun ya tafasa ta jawo wano baho ta zuba maganin aciki tana wanke kasa da dattin dake jiki, sai can data mike tsaye zata lekasu ta windo snn tafara tsinkayo sautin karatun qur'ani da ayaana take rerawa addanta dake fita ahankli dan kar juma yaji, ganin suna nan yadda ta barsu yasa ta koma madafin ta dama kunun tay marmaza takaima juma nashi har cikin turarkarsa ta same sa haryanxu yana sharar bacci da alama ko sallan safiya baiyi ba gashi har ana neman karfe takwas ynxu,.
koda tay mai magana acikin baccin ya dura mata ashar ya kara juyi abunsa, fitowarta waje kenan ta sharo kwana bangarensu taji wani irin kuka mai kara muryan inayah na fitowa a raunace tana cewa" wayyo Allah na, innalillah wa inna ilaihi rajiun, umma, umma mutuwa zanyi, wayyo ayaanah huramin cikina cikina hasbinallah wa neemal wakeel
sanda jikin taawure ya fara rawa ma bata sani ba kusan a guje tayo dakin ta samu ayanah ta riƙo inaya dake murmukukusu akasa da wani irin matsanancin ciwon ciki wanda tsabar zafinsa har wani tsinkakken yawu ne yafara zuba mata abaki kamar ruwa.
taawure tana zuwa ta amsheta ahannun ayaana ta rungumeta ajikinta already tafara zubar da hawaye sosaiii
subnallah innari?? meya faru, chikiin ne?
kiyi hakuri innari am na samo miki magani ajeji ynxu zan sarrafa mikichi kisha kiji sauki
sai nishii me zafi kawai inayah take y tana furta innalillah wa inna ilaihi rajiun dukkansu saida suka raunatu yayinda ayaanah ma ta kara fashewa da kuka me sanyi tana cewa 'sannu adda Allahu yashfiki.. ganin ciwon yaki saketa taawure tay tamaza ta kwantar da ita ajikin gado snn tace ma ayaanh tazo ta daukar ma inayan kunu halama ulcer ne yake motsa ma inaya jiki,kusan da gudu suka fito ayanah ta dauko kofin kunun da abun sassaitawa ita kuma tawure ta sauke dumamen tay sauri tadora wasu ruwan maganin a wuta danta sarrafashi agurguje, wanda kuma bana tafasawa bane tahau sarrafa su...ayaanah tana kuka tana fifita kunun a ludaye tana kaiwa bakin addanta, wanda a loma na biyu ta fetto kunun waje, jin gefen cikin inda ya kumbura sosai ya kara tokarinta da wani irin matsancin zafi ga wani dan uban kakarin amai me gigita yanayi dayake kkrin tason mata
marmaza ayaanah ta rikota suka fito bakin kofa tafara aman wanda yawu ne mafi akasari yake fita sai dan ludayi daya na kunu data kurba shima kamr zata fidda ranta yake fita
jin tana aman tana wayyo wayyo cikina innalillah umma zan mutu yasa taawure tay saurin tahowa da kwaryan maganin datake hadawan a hannunta, tun ma bai tafasa sosai ba, cikin sauri ta rike kan inayah tana mata addua tana kuma sassaitawa zata kai mata baki kenan sai ga dandanko ya doka sallama daga waje yana lekowa taciki..
tun basu ma gane shi ba yafara daga wargajin muryansa daga kofar xaurensu yana cewa ba'a amsa sallama ne agidan nan? kai malam juma kai buzu juma salama aleku... waye yake amai haka..
taawure ta daga kai zata amsa sai ga juma ya fito fuskar sa a mugun dore yana kkrin kafa hularsa akansa ko kallonsu baiyi ba yasakai zai fita..
tunda taawure ta bawa inaya ruwan maganin sai aman kawai takey jikinta na wani irin kyarma kr kar kar ayanah ta riketa sosai tana hawayen itama
daga kofar zaure juma ko amsa gaisuwar dandanko baiyi ba yahaushi da masifar katsemai baccin da yayi da sallamrsa
shikuwa nan ya fafuko makirci ya soma gaya ma juma ai ya gamo da tawure ne ajeji ta debo magani shine yazo ya dubasu ko lafya
suna cikin wanga tattunawa suka kara jiyo sabuwan ihun inaya tana cewa wayyo Allah cikinta cikin matsancin yanayi mai rikitarwa ga ruwan maganin na fitowa ta baki ta hanci,
da wani irin mugun tsinkakken gulma da tsegumi dandanko ya kusa ture juma ya shigo ciki har suna rige rigen karasowa tsakar gida
jikin juma har na rawa yahau cewa kai kai kai lafiya kuwa innari meye haka kukam kun shigga uku da wanga kazanta wani irin ragoncin ne haka?
cikin katseshi taawure tace me gida ciwon cikintan ne ya tashi..
wani caraf dandanko yace ciwon ciki ne har shine take amai? kai taawure ki rika fadin gaskiya kode taciyo wani abu awani waje awajen maza?
banza tay dashi ta kyalesa da juma dayake tuhumarsa akan manufar maganansa, ita kam zage karfi tay ta dauke inayan cak takaita kan tabarma ta dan wanke mata jiki snnn ta shimfidata tana mata fifita ayanah kuma tuni ta dau tsintsiya da abun kwashe datti tafara kwashe aman tana gyarawa..
musu ya kaure tsakanin juma da dandanko dan har waje ya rakasa yana tuhumwr sa akan abunda yke nufi da yarsa
dake dandankon mugun annamimi ne sai bai fito fili ya gaya masa cikin shege yake harsasshe wa inaya ba, baqaqen magana da misalai na yan matan kauyen da suka taba gumtso cikin shege kawai ya dinga kafa masa misalin ciwon inayan dashi yanamai ce masa saishima yay hankali, dan yanzu haka sarakunan garin sunsaka doka muddin yarka ta mutu d cikin shege bazasu mata sallan gawa ba shureta kawai zasuyi a rami kamar dabba snn su binneta a walaknce dan karta lalata musu kasa da kazantan zina.
duk dama juma mutum ne mai kaifin tunani yakuma san halin dandanko da gulma da son yaɗa karya dan ya tada zanne tsaye saidai sosai maganganun suka fara taɓa mai zuciya dan yawancin zarginsa akan yaransa yana tsayawa ne akan su mazinata ne kuma abun kunya kawai zasu jawo masa
da wnn tunanin aransa yaƙi ma dawowa gidan kawai ya miƙa sawun kafarsa ya shiga gari neman abincin karyawa da zimman kafin ya dawo hala innarin ta dawo cikin hayyacinta zai hadasu duka yaci ubansu har sai sun amayo masa gaskiya game da ciwontan nan...#surayyahms
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[01/11, 15:51] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: Susum writer:
_ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
1️⃣2️⃣
tafiya me dan nisa juma yay kafin ya samu ya shigo cikin asalin kauyensu ta majiya, lokcin daf ana neman wajejen karfe goma na safiya kai tsaye gidan da ake saida yar tsame da dan wake ya wuce batare da ɓata lkci ba yabiya aka masa hadin dafa duka na wake da danwake ga kuma yar tsamensa da zazzafar kokonsa agefe yana turiri..
saidai tunda ya zauna akan teburin gabaki daya saiyaji ya kasa taɓa abincin, lura da dabi'un kananan yan matan dake taya aikin saida abincin kawai yaketayi musmn yadda yagansu yara kanana suna magana da maza anyhow babu alamar kunya da kamun kai atattare dasu da kuma yadda suke muamala da duk wanda yazo siyan abinci. har cikin ransa kallon marasa tarbiya dama yake musu, suna giftwa agabansa gaba daya sai yaji hanklinsa na tashi , zantukan dandanko ne suka soma dawowa masa kai batun rayuwar yaransa ayanah da inayah, dan shide yasan acan tudu baisaka musu wani mutum yanamai bincike akan rayuwar taawure da yaransan acan ba sabida gani yay agidan hajy mairo me tuwo suke kuma hajiya ai matsayin goggonta ne sai baikawo wani zargi ko matsala da zai afku da tarbiyansu acan ba, saidai tunda yaji har dandanko ya fara kawo tsegumin ko hala wnn irin rayuwar banzan sukeyi acan saiyafara ji aransa kmr fa biri ne yay kama da mutum da irin ciwon ciki da amai da inayah take dayaki warkewa sam.
gidan hajy mairo gidan jama'a ne kuma yasan dolene hala yaransa suma suna hulɗa da mutane acan sosai, kasa hadiye kunun da ya kurba yay ya zauna shiru cikin tunani, cikin ransa yace toh wayasan ko dagaske ne innari takwaso masa abun kunyane suke raina masa hankali duk atake saiyaji yarasa meke masa dadi.
cin abincin yake tmkr na dole yana Allah Allah ya fita kawai ya fara bincike, can sai ya tuna cewa da akwai wasu fulaninsu nan nan majiya masu saida dabbobinsu acan tudu toh hala zasu iya gaya masa wani abu game da rayuwar yaransa.
bayan kamr minti 20 ya gama cin abincin tare da gudanar da duk wata lissafinsa,ya taso kenan zai fita sai ya lura kame yanayin garin ya fara sauyawa kamar ma haddari ne keson tasowa, hakan yasa bai wani bata lkci ba ya biya masu abinci kudinsu cifff snn ya nufi cikin anguwa agaggauce domin neman masu basa shaidoji
ata fannin taawure kuwa matsanancin damuwa da tausayin yarta inayah sosai ya fara hanata sukuni, dan banda kuka, addua, da wayyo wayyo cikina babu abunda inayahn take kanyi gwanin ban tausayi, ganin halin da inaya take ciki wanda tamkar magungunan data bata gabaki daya basuy aiki ba yasaka taawure tay shahada aranta tayanke wani babban hukunci na zaɓar ran yarta akan aurenta da juma..
wann ba tunanin me sauki bane, bakomi hukunci me dadi bane har a idon Allah
amma tasan in har batakai inaya tudu inda akwai likita sun same taimako ba hala yarta inayah zata mutu anan da ciwo kuma awahale, at same time cikin zuciyarta tasani inhar ta fice agidan taje tudu toh saki uku tabbas ya shiga tsakaninta da juma kenan rabuwa ta har abada..
duk sai ta rasa abunda ke mata dadi but the more ta kalli yanayin inayah sai taji rauni me tsanani ya kara rufeta
cikin wnn zullumin she waited for a while cikin da nisan tunani, can dai dataga garin ya fara hada hadari jikinta amatukar sanyaye ta miƙe tsaye tabi ta shiga dakinta, kallo daya tay ma dakin ta tuna ranar da aka kawota ciki tun aurensu na danye tana amarya, lokcin mijinta juma na sonta sosai, kai bazaka taɓa tsammanin cewa wani abu na tsana da cin mutunci zai shigo cikin rayuwar aurensu ba. wasu abubuwan inta tuna takejin gwiwarta yay sanyi, cikin rauni ta tsuguna adan wata kusurwa hawaye na zubo mata da tsananin karsashin zafin rusa aurenta da zatay ynxu aranta tayi kuka tay kuka sosai tagode ma Allahnta
dakyar ta iya bushar da zuciyarta tamiƙe tahau tattara duk wani savings inta na kudi da few kayanta na sawa ta sakasu a yar jaka saura ta daure su da tsumma,. tana gamawa ta fito da kominta a jakan snn ta daga ayaanah tadora mata jakan akai tace mata taje maza ta sako takalminta a daki ynxun nan snn ta fito su tafi,
ayaanah bata fahimci komi ba ta shiga dakin sun da kayan akanta tanamai lura da yanayin rauni da taurin rai dake kwance akan fuskar mahaifiynta wanda sosai ya bata tsoro da kuma fargaba. ta shiga ciki bada jimawa tazo ta samu tawuree har ta lallaba ta saɓa inayah abayanta ta daureta da zani kamr ba yar 12yrs ba, nishi me tsanani kawai inayahn takeyi batama hayyacinta banda ma dauriya irinna yaran buzaye da fulanin jeji da bazakace a age intan nan har zata iya daurema azaban zafin ciwon ciki datakeji ajikinta ba.
kafin kace wani abu taawure ta umarce ayaanah akan ta wuce gaba. kai tsaye suka fice agidan suka dau hanyar tudu, dan tsabar wahalan dataji inayahn takesha sai taji ko nauyinta bataji tafiya kawai take da sauri sauri kuma ƙarfin zuciya dukansu ukun suna ambaton Allah yanayinsu cikin rauni har suka isa garin tudu acikin kankanin lokci sai gasu kofar gidan hajy mairo mei tuwo..
lokacin kusan daf ake da karfe sha biyun rana amma dake hadari ya dan rufa sai wajen yay duhu da sanyi, suna isa taawure tay maza ta sauke inayah akan dakalin tsakar gidan dan izuwa ynxu inayahn tama dena yin motsi sai shure shure fuskarta yay fayau yay fari sosai, dan tsaban azaban datakeji acikinta wani dan uban nishi kawai takeyi idanunta sunyi farare soll sun jujjuya tay lagwas kmr lokcin mutuwarta take jira
ayanah tana aje kaya dake kanta tun taawure bata furta mata komi ba tay marmaza ta falfala da gudu ta fice kasuwa domin kira musu hajiya mairo me tuwo, daga nan kuma ko minti biyar da zama a dakalin basuyi ba inaya tafara jin wani irin sanyi sai kawai tafara ririike jikin taawuren tana shigewa jikinta sosai kamar wata mai ciwon nakuda tana nishi ahnkli kuma me nauyin gaske inda yake ciwo acikinta sosai yay tozo agefen dama ya kumbura
acikin matsanancin rauni baƙinta dake bari yahau cewa umma am, umma...ina ganin kamar mutuwa xanyi umma
atake idon taawure ya cika da hawaye tana juyowa idonsu ya sarkafe cikin na juna, ahnkli cikin nishi inayah me sauka tare da wani irin makodan hawaye tace "umma dan girman Allah kiy hkri ki yafemin musmn ma da aurenki da baba ya mutu yau a sanadiyata..umma dan Allah ki yafemin.. umma ki yafe min dan Allah karna mutu da wann shaidar akaina,.. kusan maganartan dakyar yake fita cikin nishi amma kuka take yi sosai taawure dake hawaye bata iya cewa komi ba ta rungumota ajikinta sai a sann ta itama fashe da kuka mai rauni itama inayahn sai ta kara fashewa da kuka sosai, ahnkl cikin lallami taawure tahau shafa mata baya tanacewa" yi ishiru abunki innari, ni bakimin lefin komi ba, ai danabarki ki mutu acan majiya gara auren nawa kawai ya kare..kinga shi mutuwar aure qaddara ne zanyi hakuri dashi, amma idan na barki kika mutu banyi komi akai ba hakan zai zama mini babban ciwo a rayuwata da zuciyata har na mutu baza yafema kaina ba.
kara kankameta inayah tay tanata bata haquri dukansu suka taru sunata kuka sosai...
sunjima ahaka sai can kafin taawure ta share hawayenta tafara ma inayahn nasiha masu ratsa jiki akan tay hqri da ciwon nan jarabawa ce kawai da Allah ya aiko musu.
ayayinda ayaanah taje har kasuwa tana haqi, koda ta shiga shagon hajiya taci neman duniyan nan ma hajy mairon a shagonta amma bata sameta ba, hanklinta ya dada tashi, gata yar yarinya badon ma tanada rare beauty ba da babu wanda zai kula metake cewa, da kyar dai ta samu wata yarinya yar karama kusan age mate din addanta inayah anace mata Ruthy, kallo daya zaka mata kasan chirista ce sabida yanayin shigarta da kuma gashin doki dake kanta, she is like 12yrs old amma tana da girman jiki, ankawo ta shagon ne a matsayin sabuwar mai aikinsu wanda hjy mai tuwo ne taje ta daukota cikin satin nan agidan wata magajiyar karuwai dan kusan sau biyu kenan ana case nakkrin abusing in ruth sexually at dis very young age of 12yrs, sabida angane batada iyaye tsintar ta akayi a kwali anjefarta a kwalbeti, irin yaran nan da karuwai keyin cikinsu su haifa su zubar dasu a kwali..
hajy mairo tunda taji labarin ruth hakanan tay ruwa tay tsaki har saida ta kwato wann yarinyar daga shiga ukubar karuwanci a danyen shekaru a gidan magajiyan ta bata aikin shara da aika a shagonta dan kar acigaba da lalata mata rayuwa.
ruth din ne tazo tafara kula ayaanah sukayi magana harta gaya mata cewa ai hjy nacan police station suna case da mai anguwa yauma wata sabuwar case ne tsakaninta da wasu kidnappers aka bude
,..abunka da yarinta damuwar aayana kawai naga jikin addarta ne, haka ta sako ruth din agaba da magiya har sanda ta mata jagora takaita police station da kyar ma aka barsu suka shiga snn taga hjy mairo wanda suna hade ido rauni ya rufeta tafara panicking tana hawaye tana gaggaya mata cewa har sunzo da ita da mamanta da addanta jikin addanta yaki yay sauki.
ba agama rufe case da su mai anguwan tudu ba hajy tay maza maza taje ciki ta rokesu aka bata daman zuwa da dawowa aka bata 2hrs sabida case din nata da yan kidnappers kusnn babba ne so kawai ake a cimma wata matsaya yau basai ankai gobe ba.
ana basu 2hrs din nan hajya mairo tariko hannun ruth da ayanah wujiga wujiga suka kamo hanyar gida a abun hawa, tun daga zaure ta doka sallama suka samesu a manne da juna taawure ta tungume inayan ajikinta inayah tay lumui ta lumshe idanunta sosai ,
hjy nazuwa tadora idanunta akan yanayin inayah ganin yadda ta dawo wani iri kmr me kanjamau yasa ta fashe da kuka cikin kankanin lkci tafara raki tana salati tana sallamewa tana tambayar taawure meya faru cikin tashin hankli, tun ba amata bayani ba tasaka marmaza aka tada kura aka dauki inayahn abaya kamar yar tsana suka fito wqje wujiga wujiga aka sata abun hawa dukansu su hudun suka wuce da ita dan karamin Primary health care facility dake cikin tudun agaggauce.
suna isa cikin asibitin kuwa ruwa ya fara sauƙa kmr da bakin kwarya, da Allah ma yaso su yau akwai likitan dayazo daga cikin kano, duk dama sauri yake shima zai karkare aikinsa zuwa gobe juma'a zai koma cikin garin kano yanayin jikin inaya dayagani yasaka ya tsaya dan ya taimekesu
gurgura inayan akay a gado mai taya aka kaita har wani daki aka fara saka mata ruwa snn aka ja jininta aka fara mata yan gwaje gwaje ayayinda taawure da hjya mairo da ayaana da ruth suke tsaye likita yana musu tambayoyi,
ayaana ce tafi bada amsarsu sabida kusn komi na alaman ciwon addantan a idanunta ya fara..
bayan likita ya dau duk wani rahotonsu ya tafi dashi ciki nan hajya mairo tafara mita da masifa wa taawure kamar Allah ne ya aikota, akan meyasa tuntuni taawure bata dawo tudu sun nemi waraka ma inayah ba,
saidai koda taji taawure tahau furta mata labarin danbanzan duka da kuma tsauraran kalmomin da juma ya furta akanta tare da jarumtar datay yau na kashe aurenta danta ceto rayuwar inaya sai gabaki daya jikin hajya mairon yay mugun sanyi, atake kuma sao ta koma lallashinta tana bata hakuri.
lokcin ruwa akeyi amma ba sosai ba tunda sukaga likita yanata aiki baice musu komi sai suka dan samu sukuni aransu, har hjy mairo take basu labarin case inta da wasu mutane da aka samu rahoton cewa yan kidnappers ne kuma sunce zasu saceta, shine fa aketa case da ita har da mai anguwa akan zasu kafa vigilante group a kusa da kofar shagonta snn za'a basu daman rike bindiga sabida tsaro..
jin abun babba ne yasaka tawuree tace mata tunda jikin inayan ma da alaman sauki kawai takoma station agama case din in yaso in tagama ta dawo, da kyar dai hajy mairo ta amince da haka, koda zata tafi ita dayanta taje har ta dakin da aka kwantar da inayahn ta sameta wanda suna hade ido hawaye ya cika idonta tazo tadan rungumeta tayita mata adduoin samun sauki masu yawa tasaka mata albarka sosai.
itadai inaya sai cewa take ayafeta takuma gode tagode da irin kulawar da suka bata sai kuma tay murmushi me cike da hawaye me rauni.
ahaka dai da wann kalman har suka rabu da hajy maituwo dukansu suna zubar da hawaye ma juna at same time suna murmushi ma juna. hjy tana ficewa a asibitin tabi ta aje ruth a shago snn ta koma station agurguje da gunjin tausayin inayahn a zuciyarta
bayan tafiyar hajy maituwo ba da jimawa taawure tay zamanta a reception daga ita sai ayanah, sallahn azhar ne kadai ya dagasu lokcin kuma already ruwan saman yadan lafa sosai saidai wani sabuwar haddarin ne yake kan sake tasowa gashi har yanxu likita baice musu komi ba.
Dagata dayan bangaren at around 3:40pm na yamma ibaad ya bar school of medicine ya dawo gida agaggauce dan kansa har wani irin ciwo yake masa tsabar practical activities da yay a club dinsun yau.
tun 11am na safe ya gama normal school lectures, frm 12-3.30pm dinnan duk acikin club practical lab dinsu ya kareshi sun dukufa sunata practical kala kala akan major field dinsa na cardiology at an introductory level.
yana isa gida kai tsaye yahaura sama dama kuma dakinsa is always neat, wankansa kawai yay sharply yasan dake maheer bai dawo ba so baida wanda zai iya bata mai lkci, within few minute ya fito ya kintsa kansa anitse yasaka kananan kaya ajikin sa farin rigan raymond T shirt original cotton me dogon hannu da bakin wando suade da wata sleek sneakers yabi ya saka wata original black baseball face cap data masa mugun mahaukacin kyau kagansa kamar balabe except that he had this glowing yellowish body tone. shigarsa simple yet classy nd smart, bakaramin kyau yayi ba musmn da ya toshe idanunsa da fararen rayban spec da shirin zuwa anguwar tudu agaggauce dan yana so ya samu yajeshi ayau din nan dan komin dare yay makansa alkwari yaudin zai dawo gida dan yanada abubuwan yi a lab dinsun gobe sosai.
bayan ya gama shirinsa tsaf ya fetsa turarensa original dior souvage me sanyi snn ya fito ya dau jakar bayansa da wayansa yana tafiya anitse har ya same ammi babba a falo tana kallon indian wani series..
qamshin turarensa me aji ya saka ta tafara daga ido ta kalleshi itade duk ta kallesa kyaun fuskar uwarsa take gani dan haka takejin ta tsanesa kamar mutuwarta.
kallon tsana take masa har ya karaso ciki ya dan rusuna ya gaisheta ta amsashi ciki, snn ya sanar da ita inda zaije nanma tay kamar batajishi ba, after few scnds of silence dan kansa yagaji da attitude inta yamiƙe shiru ya fice agidan yanaji tana binshi da tsaki tare da cewa Allah yasaka mutuwarka ce ta kiraka a tudun mayen yaro kawai Allah yasa gawanka ne zai dawo bakaiba.
..koda ya dauki mota ya fice haka maganan nan nata yarinka masa yawo akai cikin wata karamar toyota jeep da bappa zaidu ya bar masa zaiy tafiyar dashi, yana tukin ahnkli ya kira bappan zaidun awaya suka fara magana ya sanar da shi cewa ynxu zai wuce tudu wajen hajy mai tuwo, hira sukeyi har ya isa cikin anguwar rijiyar zaki inda family house dinsu yake dan ya amsho wasu sakonin da za'a kaiwa hjy mai tuwo daga wajen mahaifiyarsa ammi karama, kusan kaf gidan babu karya ammi karaman tafi samun karbuwa awajen uwar mijinta, dake ita tasan wani abu waishi nitsuwa, dattako, gata da biyayya da sanyin hali, tunda taji uncle moh yasanar da cewa ibaad kawai zasu tura wajen hajiya ayau din taje kasuwa tasiyo dukkan wasu abubuwan masu kyau datasan hajy mairon tana mugun so snn ta dafa mata abinci me rai da lafiya tay packaging insa a close basket dan yawuce mata dashi.
ganin hakan datakey na kyautatawa yasaka sumtimes har anty safeeran ma take gani tana daukar darasi, dan anty safeera is a calm young nd wise lady, a shekaru dai bazata wuce 35-36yrs ba duk dama babanta yana da kudi itama tana gama secndry din ta aure uncle mohd har suka samu first son insu mujaheed dayake sa'a da zainab arifah, sai yar autarta kulthum bayan nan ne ta koma karatu, she is curently studying msc micro biology amma a private university., duk duniya babu abunda take mutuwar kauna kamar mijinta uncle moh, shi mutum ne meison jin dadin rayuwa, he is all about this flashy rich guy life, kominsa is loud, tun daga way of life insa me aji, har sutura, kominsa me tsada kawai yake sawa, he is the finest nd the youngest engineer of the almansur's elders, ryt in his early 40s, shi farine sosai dogo mijin novel, mai cute red lips da kwantaccen saje, gashi da saurin fara'a, mutane suna yawan cewa dansa mujaheed yagado farin fatarsa ne sosai.
anty safeera can do anything to please him, wani irin soyayya na amana take masa, ganin ibaad agidan yasa sai itama tajeta sashenta tadan tarkato turaruka masu kyau da tsada ta bashi danta burge mijinta, agabansa tace asaka ma hjyn kayan nata tsarabar aciki.
lafiya lafiya ibaad yay musu sallama, uncle moh ya rakosa har gaban motar jeep in yanamai dada jadadda masa cewa in har ruwan sama ya tsaresa a tudu karyace zai dawo sabida akwai fatake masu kidnaping da barayi kawai yayi haquri ya kwana agidan hajy mairo inyaso gobe da sassafe sai ya dawo
sude babban burinsu shine ibaad ya samu yaje tudun ya gano musu asalin menene ke faruwa da mahaifyar sun acan, snn ya lallaba musu ita taji aranta cewa zata iya barin wajen ta dawo cikin kano ta zauna tare da su a gida.
gabaki daya tabi tahana yayan cikinta binta can tudu sukuma anan cikin kano hanklinsu sam baya kwanciya, sai tace sam za'a sace matasu in sukazo, saidai kawai ayi waya tsakanin ta da bappa zaidu da uncle moh akai akai, dake suna yawan tura mata kudi kowani wata ko cikin sati, prof zayyanu kam dama tun tuni ya dena nemanta kuma bata wani damu da baqin halin sa ba dan abune data saba dashi tun bai kai ma haka ba, ko surukanyenta da jikokinta ma knsu bata fiye kiransu ba sabida tsaro.
at around past 5 ibaad ya kammala duk wata maganansa da uncle mohd snn ya shiga jeep din yakama hanyar anguwar tudu dake wata bangare ne me nisan gaske acikin kano wajen tafiyar awa uku ne da rabi sabida hanyar shiga garin babu kyau ko kadan
tun kafin ibaad ya dauko hanya, ata can bangaren juma kamr dai kullum, zuwansa wajen fulani jin labarin rayuwar da taawure takey a tudu bai kare masa ta dadi ba.
dan kuwa daga isarsa majalisan dattijai ya tarar da su kaca kaca anata raha, toh yay dasu aje gefe suyi magana amma sukaki suka bige da tsokanansa kamar yadda suka saba kullum. dakyar da wahala suka dan sauraresa suka koma gefen kai tsaye ya fara musu tambyar dake tafe dashi, dayan bafulatanin ana cemai sajo shi yafara ce masa ai wnn tsohon zance ne, yaran sa kam dama cikakkun yan barikine dan sun mugun shahara a anguwar tudu msmn ma inayah itace ma ake cewa gwarzuwar tudu.
hanklin juma sosai ya tashi da jin wann furuci, saida suka ganema cewa bada saninsa yaran suke karatu ba aikuwa su suka hau fede mai biri har wutsiya na batun karatun da su inayah da ayaana sukey, komi da komi saida aka gayama juma abaibai wanda tun bai bar wajen ba mazan dake wajen aka fara yaɗa labari nacewa juma cikakken lusari ne baida gindin haifan yaya maza gashinan ashema matarsa taawure tafi krfinsa akan harkan gidansa da yaransa taje tudu ta saka yaransa a makarantar kafuraye batare da izininsa.
ranar kamar kan juma zai fashe da feshin wuta haka ya kamo hanyar gidansa da gudu idanunsa sunyi jajizir ruwan saman nan da aka fara sabo kaf akansa ya kare...
yana dawowa gidan ya shiga turakarsa ya dau wata igiya ya cusa a wandonsa snn ya dau wata addansa mai kaifi akan yau xaima tawure dukan mutuwa snn ya sare kafafunta dashi..
hakanan yaci nemansu agidan har wajajen daya saura na rana bai samesu ba kuma kwata kwata bai kawo aransa cewa har taawure zatay tsaurin idon kashe aurensu akan ciwon inayah ba, adan dolensa yaje jejo ya nemo kasurkurmin magulmacin nan dandanko, sabida yasan duk tsiya abakinsa kawai zaiji labarin inda taawure takai masa yayansa,
haka ya bazama jejin kmr mahaukaci da kyar ya sameshi, dandanko dayaga juma wujiga wujiga sai yaki sam ya gayamai komi saida ya sha cikinsa yaji labarin asalin meke faruwa tukuna.
bayan yagama jin komi sann yahau kara masa wuta yana cewa aidazu ance masa anga matarsa taawure ta goyi innari sun wuce tudu da kayansu, snn yabi yace ma juma toh tabbas cikin shege ne inayah take dashi sukaje zubarwa a tudu awajen likitocin kafuraye, inba hakama ba, wani irin ciwo ne haka inayah takeyinsa da amai da rashin cin abinci da kuma ciwon ciki me tsanani..snn kuma ace duk saiwoin kauyensun nan ya kasa magancewa...
yace ma juma kawai dai cikin shege innari taje ta kwaso taawure take kokarin boyewa kawai yaje ya dau mataki sabida kar martabansa da kimansa ya kara zubewa a garin majiya.
hakanan ya kara pumpa zuciyar juma da zugi da kuma zargi harsaida yasaka ta karayin baqi qirin da mummunan fushi da kuma bacin rai, daga nan babu wani jira juma ya saɓi sandan sa da addarsa ya wuce garin tudu acikin yayyafi, ya iso around 2pm dede na rana lokcin jikin inayan yafara rikicewa
likita ya fito yana kkrin ceto ranta da taimako da ake bayarwa na emergncy sabida sun riga sun gano cewa chronic appendix ne yake damunta gashi bayan ya girma harma yafara ruɓewa acikintan dolene kawai amata tiyata aciresa agaggauce.
tun bayan sallahn azahr suke cikin wann tashin hankli anata kkrin stablizing din inayah kafin ace zaa nemo motar da zai kaisu cikin birnin kano dan amata tiyatar nan agagguce gashi lkcin ana wani irin kwaxa ruwan sama me yawa da kuma tsawa
duk da zafin ciwo wasiyar hakuri da neman yafiya kawai inayah take nema awajen taawure da ayanah dan ciwon ciki takeji mei tsananin ciwo da bazata iya fasalta azabansa ba,
anata rububin nan ashema kudin tiyatan nasu bai cika ba, gashi taawure bata da waya haka tafita tabar ayana ajikin inayah ruwa na dukanta duk abun hawa sundauke da kafa ta dinga tafiya cikin sauri tay hanyar police station neman hajy mairo dan tabata aron sauran kudin tiyatan agaggauce..
ficewarta a asibitin bada jimawa ba Allah yay ma mijinta juma isowa har cikin asibitn da taimakon wasu matasa dake yawan zama daf da kofar gidan hajya mai tuwo dake zaman saka ido dama suke sune suka dada tabbatar masa cewa tabbas taawure da yayanta suxo amma sunbi hjy mairo sunje asibiti tun da jimawa
ransa a matukar dagule ya farabibiyar kwatancen asibitin tun abakin matasan dayake tambaya yaji kusab kowa ana cewa inayah gwarzuwan tudu, shi duk ya dauka gwarzancintan nan a karuwanci ne da tsabar iya bin maza baisan gwarzuwan karatun qur'ani suke nufi ba.
zcyarsa baki kirin ya diro cikin asibiti, daf lokci ciwon cikin nata ya tsananta sai nasiha take ma ayaanah akan karda tay rauni koda ta mutu bata duniyan nan ta tabbata ta tashi tsaye tazama wata jajirtcciyar mace snn ta mata alkwarin zata cika ma mahaifyarssu taawure bban burinta naganin sunyi ilimi sun zama mutanen kwarai.
tsabar kukan da sukeyi rikeda hannun junansu in an intense emotional state basuma san sanda juma ya shigo kansu ba.
ji kawai sukayi ana huci daga bayan su ankuma zaro katon sanda kmr za'a je yaqi a mugun zuciye yana huci yadaga sandan sama zai bugashi akan nurses din dake tsaye duk suka saka ihu suka bar dakin aguje ganin sa gabjeje babu wacce tay gigin taresa. dayaga haka sai girman kansa ya kara hautsina yafara dirin masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba yabi ya haukata asibitin da zage zage
ayanah ta mugun tsorota, yadda kasan zucyarta zai fice daga kirjinta ya fice, amma haka ta cije ta ki sam tatashi ajikin inayahn tabi ta rungumeta tana kuka mai mugub karsashi wanda hakanne kawai yasaka bai kai musu dukan atare ba.
muryansa kamr zai tada asbitin yake kiran taawure kamr wani tabbabe yanamai zaginsu yanamai cewa inayahn karuwa tsinanniya kawai, yar bariki irin uwarta, yace wallh kinyi asara innari Ashe dama cikin shege kikayi kuke boyemin keda uwarki?? da yaren buzanci da fulatanci duk ya hada yana tsine mata dashi.
itade inayah kuka takey tana furta innalillah wa inna ilaihi rajiun....idonta a lumshe taki tace masa komi taki ta masa bayani bare ta bashi haquri..
..duk wani xafin xagi me tafe da amon muryansa dayake saukewa aknsu ji take kmr ranta yake zarewa dan zafi.
ayanah da tsabar tsoronsa ma bata iya masa magana ido da ido amma yau babu irin tsaurin ido da yaren da bata masa rantsuwa da bayani dashi ba.
tabi ta rungume inayah sosai tana kareta dagashi cikin kuka mai rauni, tanacewa baba ciwon appendix ne yake damun adda inayah ba cikin shege ba
hargagi yake ko ajikin sa kamar baijinta tanakan maganan ma ya ficokota ya tureta ya faffala mata maruka masu karfi, yaki sam yaji komi, shide yanaso ne ma yaga kawai ya gwada ma inayahn sandansa ya kashe ta,
dakyar likitan da wasu maza suka shigo suka samu suka rirrikesa snn aka kwace sandan daga hannunsa, ahakama sai zagin yaransan yakeyi kamar bashi ya haifesu, anfi minti ashirin ana wann hayaniyar da juma...
ayaanah ce ta fara jin daukewar numfashin inayah, ta mike da sauri jikinta na bari tayo kanta tun bata bude baki ba ahankli tajiyo kalmar shahadarta daya kufce mata abaki very faintly.,
akace wai duk inda malaikar mutuwa yazo sai iskan wajen yayi daban wani irin dimmm taji wajen ya dauke mata cakkkk, dan tunda tajiyo wnn numfashin ta na karshen taji kirjinta da jijiyon zuciyatta duka sun tsinke jikinta na wani irin rawa atake ta juyo sai kuma tazube aragwabe ajikin inayah tafara wani irin kuka mekara tana jijjigata tana kiran sunanta kamar tabbabiya..
da gudu likitan ya sake juma ya karaso wajen aka dudduba aka samu rai yay halinsa kowa yana furta innalillah aayana ta zube kasa tana kuka kamar ranta zai fita amma juma ko gizau baiji ba dan ya mugun tsanar asbiti da duk mutanen dake cikinta, anata batun yarsa ta rasu amma masifa yakeyi yana cewa sam cikin shege akazo zube mata tay mutuwar kafirci.
ran kowa saida ya baci a asibitin ko ajikinsa, shi mutuwar inayahn ma dadi ya masa gani yake data haifi shege agidan sa gara ta mutu, hakanan ya fizgo aayana waje, lkcin ana yayyafi sosai ya tsare adedeta ko ciniki baiyi ba ya cusata ciki yaciro igiyansa daga aljihunsa ya daure mata hannunta biyu da igiyan ajikin karfe ta cikin keke, snn ya koma ciki yanamai kara saukar musu da jakar balai yabi har kan gadon ya dauki gawan inayan akafadarsa, itama ya saka acikin keken, duka dashi da yaransa ya debosu agabansa suka kama hanyar garin majiya aganinsa sai ynxune ya cika namiji, snn zai nuna ma kowa tsananin jarumtarsa for once dai zaiyi abunda ya dace akan yaransa bisa tsarin al'adarsu ta kaka da kakanni dan martaban sa da kimarsa ya dawo.
lokacin ruwa aka farayi sabo kamar da bakin kwarya wanda shine yasaka har taawure bata samu abun hawan dawowa da cikaton kudin tiyatar data amso wajen haj mai tuwo akan lokaci ba
ko cikakken minti biyar juma baiyi da dauke yaransa ba ta iso asbitin wujiga wuijga kusab agigice jikinta yay jagwab da ruwa tazo musu da cikaton kudin tiyatar cass har tana haqi, tsabar tausayin data basu da kyar aka samu wata dattijuwar health worker data gaya mata cewa Allah yay ma inayahnta rasuwa snn gadai jahilci da haukar da ubansu yazo yay asibitin kuma ya tafi da duka yaransa gida ynxu
tunda aka fara mayar da maganan kusan kangare taawure ta suma daga tsaye har saida sukaga bata motsi snn aka bambamreta daga sudden shock din data shiga ciki aka samu itama bata ko motsi dan mummunn bugawa zuciyarta yay atake kuma ta suma aka bata gado ana kkrin reviving inta dan karta samu sudden heart attack due to shock.
tundaga hanya ayaanah take rabza kuka mai kara da karsashi, keken yana sauke su juma ya taso keyanta da haryanzu take rabza kuka kamar ranta zai fita wanda duk yawan ruwan nan da akeyi duk jejin saida ya dauka da karar kukanta, tanajin matsanancin tsoron abunda ke faruwa ga tsananin baqin cikin mutuwar addanta na dada gigita mata kwakwala tare da tsinka mata jijiyoyin zuciya..
sun iso gidansu babu takalmi akafara bare dankwali, haka juma ya turata akasa yabi ya kulleta adaki tareda gawan inayan snn ya fito waje ya wuce gari yakirawo mutane dan a masa shaidan binne yarsa da zaiyi bisa hukuncin al'adansu na kauyen, gashinan ruwa fa akeyi sama sama dake la'asr ya riga ya shigo ana neman kusan 4;45pm on dot amma hakannan magulmata da yan son ganin kwaf kwaf suka bazama yana bude kofar ya samu aayana tayita kuka harta sume tay karau ajikin gawar inayah dake dauke da fuskar murmushi.
wani irin shure aayanan yay gefe ta fadi akasa snn ya iyo ma maza biyu suka shigo, cikin masu fidda gawan inayahn dum mamaki ya rufesu ganin ynyin fuskarta da murmushi har suna tsammanin cewa ko ba mutuwa tay ba sabida wnnn hasken da fuskarta yay sosai kamar ba ita ba.
al'adace ya zamo basu yin jana iza wa wacce tay cikin shege agarin, dan haka juma ya sanar ya kuma nuna ma shaidunsa cewa yana Allah wadai da abunda ya faru da yarsa snn a shirye yake amata binnewar al'ada tunda cikin shege taje zubarwa.,
dakyar aka samu mata wanda suka mata wanka aka suturtata, ko kabari ba akaita ba kawai aka haƙa rami a bayan gidansan ta cikin jeji
normally bisa koyarwan addini ladubba ake bi ma saka gawa a rami ahnkli snn ta hannun dama amma koda sukazo saka inayah anata kabarin gungurata kawai sukayi sai suka shushhure mata kasa akanta har saida kabarin nata ya rufe......
(muna rokon Allah ya kare musulmi daga sharrin jahilcin wasunmu musulaman a duk inda suke, true life story, wata sabuwar makwafcyrmu christace baikai ko wata biyu haka ba data tataɓa furta min cewa ita babu abunda zai sakata taso musulunci ko tayishi harta mutu sabida musulmai mugaye ne, dalilinta nafarko shine babban yarta tabar christanci 2yrs back ta musulunta ta aure wani musulmi amma tunda ta shiga hannsa bakaramin tozarci da walaknci me tsanani takesha ba ga duka ga horon yunwa ga zagin cin mutunci, na biyu kuma awani kauyensu a jos tace mana da idonta tagan anyi ma wani mutum bawan Allah irin wannan walakntaccn binnewan da akay ma inayah, wai lefinsa shine shi tubabbe ne ba a musulnci aka haifesa ba, tace sanadiyar wann incident din mutane dayawa sunbar addinin. it was a sad reality in that remote villlage, it took alot of convincing kafin matar nan tazo ta fahimce mu harma tagane cewa ba haka musuluncin fa yake ba, snn zatama iya kaiwa kara kotun sharia dan akarbawa yarta yanci..kalubale garemu ne musulmai, addinimu bawai sai a fuska ko a baki bane. yakamata ace kyawawan halinka ko halinki shine zai fara bayyana kyawun addininki a duk inda ake, lets all make sure we set a good example of our religion no matter whom we are dealing with...bissalam)
*a saurare sabon Update ranar monday in sha Allah*
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[03/11, 21:06] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: ABUNDA KE BOYE..1️⃣3️⃣
ruwa akeyi sosai amma bashine yahana jama'ar kauyen majiya tahowa gidan juma kwansu da kwarkwartansu dan sugane ma idanunsu abunda ke faruwa da yayan juma ba. hatta wazirin sarkin buzaye saida aka dagosa da lemansa dan yazo yagani yakai rahoto gaban sarki...
agaban kabarin inayah inda suka gama shushhure mata kasa aka tayar da wani sabuwar hayaniya tsakanin fulani da buzaye, kowanne kabila tana kirga a wanne bangare ne akafi samun abun kunya, inda atake wazirin sarkin buzu cikin izza yake nunawa jama'a cewa dolene kawai juma ya amshi lefinsa snn ya tashi tsaye ya cigaba da daukar tsatsauran matakai akan iyalansa domin kare martaban al'adarsu da mutuncinsu na buzayen majiya, saƙo na farko da sarkin buzaye ya aiko shine marmaza akawo masa juma da yarsa ayanah a fadansa agurfanar da ita, snn a aurar da ita ma almajirin gonan sarki ayau dinnan sabida gujewa afkuwar wani sabon abun kunyar, ko kuma juman ya tattara inashi inashi da yarsa yanzun nan subar garin majiya batare da ya dauki komi daga arzikinsa ba wanda bakaramin tashi hanklin juma yay dajin wann babban maganan ba..
duk dama cikin yayansan duk yafi tsanar ayaanah aransa, amma gani yake kamar daya aurar da ita wa almajirin gonan sarkin buzaye gara kawai ya tsine mata tabi duniya ko ya bada ita kyauta ma kafurai,bisa
a'ladan kauyen babu wani tozarci da kaskanci dayafi ace maka yarka tana auren almajirin gonan sarki, lamari ne babba me shaqe da rayuwar kaskanci, dan muddin almajirin gona ya aure mace no matter how minor she is koda yar kasa da 10yrs ne,toh uban gidansa ne zai soma saduwa da ita kafin nan mijin shima ya sadu da ita, haka zasuyi ta passing passing da ita har iya karshen rayuwarta,iyaka hatsin gona ne zasuna bada ubanta kowani wata amma ko sadaki bazasu biya na auren ba.
bisaga al'adansu haka abun yake tun tun kaka da kakanni shiyasa kowa a kauyen baison ace wani qaddara ya fadawa yarsa ta aure almajirin gona dan kmr babban purnishment ne da ake bawa mace dan a kaskantar da rayuwarta na har abada bisa wani leifi data aikata ko iyayenta suka aikata.
tunda aka sanar wa juma abunda sarkin buzaye yace akan yarsa ayaanah aka fara tada hayaniya da shi agaban kabarin dayan yarsa inayah.
tsawa da kuma hayaniyar mutanen da suka binne gawar inayah ata bayan gidansun shiya soma farkan da ayanaah daga doguwar suman datayi, A mugun razane ta farka rike da kirjinta dayaketa bugu kamar zaifita bakinta dake ɓari na dauke da kalmar innalillahi wa inna ilaihi rajiun ciwon zuciyarta sosai yake son ya tashi da karfinsa saidai wnn mental shock da surpressed survival mode din datake ciki ahalin ynxu shi ya hanashi nunawa, mikewa tsaye tay arikice dabataga gawar inayan akusa da ita ba cikin tsananin razana ta kara fashewa da kuka cikin mugun rauni ta rike kanta dake mata juyayi Wani irin runtse idanunta tayi tana kukan me cike da zafin mutuwar yar uwarta wanda yana tahowa ne da radadi tana ji kamar bazata taɓa iya rayuwa babu addanta inayah a duniyan nan ba,cikin yanayin tsumayi take kukan, koinanta na rawa rawa da alaman cewa tana cikin yanayin tsananin fushi, rauni, da tashin hankli.
acikin ranta addua takeyi na neman teimakon Allah musmn daga alkaryar wannan mummunan qaddara dayake shirin tunkarosu, duk saukar numfashinta acike yake da uban nishi mai mugun tada hankali da kada ruwan ciki dayake biyo baya..
tanacikin kukan tafara tsunkayo hayaniyarsu wanda sai a sann ta dawo cikin hayyacinta jikinta na rawa rawa ta iso har bakin windonsu inda hayaniyar yafi tashi din ta kasa kunnunwanta taji inda aka kai gawar addanta inayah dan itama taje..
mannuwa tayi abakin windon ta jingine babu abunda yake tashi face razanannen sautin muryan wazirin sarki yana tada jijiyar wuya yana zagin babanta agaban mutane tare da jadadda masa cewa bazasu bashi wani uzuri ba laifukan da ahalinsa suka aikata yay yawa, na farko yaransa sunje suna karatun kafirci (boko) aboye, na biyu matarsa taawure ta raina maganinsu ta al'ada takai yarsu inayah asibiti wanda tsabar tsanar asbiti da sukay shine suke kiran sa da "kangon kafuraye". na uku kuma yarsa ta mutu musu da cikin shege agari. dan haka, sukace.. baza ai masa wani uzuri ba, ko yabayar da yarsa ayaanah su aurar da ita yau, ko kuma a koresa agarin majiya batare da ya dauke kominsa ba kuma korace na har abada babu dawowa.
tamkar feshin wuta haka ayaanah ta dingajin saukar maganganunsun acikin kunnuwanta, jin duniyar na juya mata, gata da ciwon raunin zuciya wani irin jiri ne ya kwasheta abazata dan batama san sanda tasake windon ta sulale kasa amugun takure tana kkrin cusa kanta a tsakankanun cinyiyonta ba maganan auren kawai ke dawo nata kai tsabar yadda zuciyarta yake bugawa da azaban tsoro yasaka ta cije takara ƙarfafa speed in fitar numfashinta dan kada ciwon raunin zucyar nata ya tashi mata aynxu..
cikin azama ta miƙe tsaye adaddafe bugun balai kirjinta yake sai diffff difff difffff diff numfashinta yakey dakansa yana sauka kamar wanda zai dauke gaba daya..
kara leka windon tay jikinta yadau tsanannin zafi hawaye masu tsananin rauni na zubo mata musmmn data kara zuba ido tanata kallon kabarin addanta rauni me yawa ya rufeta tanaji kamr wuƙa aka soka mata akan kirji.
tana kokarin dauke ido akansu kenan daga can nesa ta hango wani mutum dake kkri ya kalleta suna hade ido kuwa kafin yayi magana da wani damugun sauri ta tsuguna jikinta na rawa rawa atake taji kmr she need to act fast fast kawai de ji take kmr bazata tsaya akamata amata auren dole ayauba itakanta bata san daga ina wani irin karfi yazo mata ba da gudu tamike ta nufi can bakin kofa ganin da tayi kofar ya budu kadan ta leka waje tsakar gidan taga har yanzu babu wanda ya shigo ciki.
tafi mintina uku cikin tsananin tsoro tana tsaye tana ta kallon tsakar gidan ganin kamar babu motsin kowa anan yasata tayi mustering courage da kyar tacire tsoro tafito ahankli a hankli tana tafiya ruwan saman da akeyi na wani irin zuba na dukanta kirjinta na bugawa da karfi karfi kafafunta har suna sarkafewa danji take kmr bazatakai bakin zaurensu ba.
cikin tsananin rauni da tsoro har ta fito waje inda tanajin kanta asararin kofar gidansu bata tsaya ba ta saita hanyar jeji ta falfala da wani irin gudu kamar damisa ne ya korota..
gudu takey batare da ta juyo bayaba tana gudun tana rabza kuka tafadi kasa ta tashi, kai tsaye ta dauki hanyar anguwar tudu amma tacikin ciyawa dan tsabar tsoron karwani ya ganta daga nesa, haka tarinka bibiyar ciyawan jikinta na tsnnin rawa ciyawan yana mata rumfa tana zagaye cikin tsananin tsoro da fargaban kar akamata, gashi ko yar takalmi babu akafarta sai dankwali daya gama jikewa da ruwa
daga doguwar rigarta har doguwar yololon sumanta me shegen tsayi da tsantsi sun balain manne mata awuya da jiki, inda wani dan uban silky smooth natural beautynta yake haskawa bana kadan ba. cikin wnn yanayin ta rarrafa zatafito acikin ciyawar tasaiti hanya da zai sadata da hanyar tudu kenan tana qusa kai kuwa wani dan aikan sarki dake tahowa da lema yay caraf yaji motsinta
arazane ya koma baya da tunanin ko maziji ne aikuwa suna hade ido cikin daka mata tsawa yace keeee ayaanah fito nan dan bura ubanki shegiya ni zaki tsorata? amugun tsoroce mai tattare danyen taurin kai wanda bata taɓa sanin tanada irinsa ba ta shareshi batacemai uffan ba takoma cikin ciyawar da sauri sauri tafara rarrafawa aciki tana komawa baya tanaji yana ihun sunanta amma batako amsashi ba harsaida ta sabule ta fita tawani hanyar da bata taɓa saninsa ba..
haka mutumin ya ci nemanta acikin ciyawar da bai ganta sai yadauki dankwalinta daya samu akasa wanda agarin rarrafen ne ya zame akanta ya fadi batama sani ba. girgiza kansa yay ya wucewarsa da dankwalin yana sauri sauri ya isa wajen su juma dasauran mutanen dan ya gaya musu saqo snn yace musu yaga yarsa ayaanah ahanyar tudu zata gudu. bangaren ayanah kuwa tunda ta fice aciyawar gudu take da iya karfinta, bata ko juyawa. kuma ahalin ynxu bata san ina ta dosa ba sabida canza hanya datayi gudu ta dingayi har saida tay nisa taga ashe babu wani hanyar billewa gaba jeji baya jeji cike da karayar zuciya ta nemi wani waje tafadi akasa tanata rabza kuka me kara ruwan saman nan kaf dinsa akanta yaketa zuba taji tarasa abunda yake mata dadi..
tafi minti goma ahaka akwance daga can can nesa sai ta fara jin motsin kafafu can kuma taji muryan samarukan majiya suna tahowa suna ihuuu yadda suke tahowa yuuuu da alama dai an biyota ne za'a kamata.
arikice ta miƙe jiknta yana wani irin kar karwa sabida gabaki daya karfinta ya kare har tangal tangal take bata tsaya duban inane gaba ba kawai ta duru cikin jejin da sauri tadinga bin ciyawa tafadi ta tashi tanawani irin kukan tsoro, bata hankara ba wani irin mugun tsantsi me hatsari ya jawota phewwwww kamr iska sai jin kanta tsuuuuu tay tana tafiya akasa kamr ana janta amugun firgice ta tsala wani irin ihuuuuun razana sai ji tay tsantsin ya fettota kan hanya wani irin karan taka burki da wawan tsayuwar motar dataji a kunnunenta yasa atake tabi taja zuciyatta ta suma..
innalillahi wa inna ilaihi rajiun
cikin lunshe ido da budewa ibaad ya furta hakan da karfi ayayin daya bude lumshahen idonsa da suka tsaya cakkk dan bazai iya bayanin yadda yaga fettowar yarinyar waje daga jeji kmr an jehota acikin kiftawar ido ba.
cak ya tsaya yanakan salati baikuma motsa ba, dan shi ba mutum bane me saurin rudewa iyakan hannunsa dake rawa rawa akan stiring yasake da tunanin ko ya bugetane ko kuma karar gudun motarsan ne ya razanata, after like 3 scnds yabude motar yafito cikin tafyarsa mai kama da sauri sauri dan ruwa ake sosai, cike da jan aji gami da lura jin kirjinsa na matuƙar bugu ya karaso wajen ganin ashe motarsan baima taɓata ba yasa yaji sanyi aransa kasar wuyar sa ya furta hamdala snn ya mayar da hanklinsa kanta da sauri
wanda tun bekai ga tsugunawa ba yahau kare mata kallo duk ya dauka ma tafi haka girma saiyaga ashe yarinyace karama jikinta tay futu futu da turbaya tabita dukunkune akasa asume da alaman kamr anjefota dan fuskrta kasa yake kallo tadan kwanta aringine acikin ruwan datti dake kasan hanyar duk turbayan data debo ya rufe mata kafafunta, yy tsammnin ko tafito wasar banza ne kawai na yara but something feel soo odd abt her, da niyyar masifa ya karaso kanta, ya tsuguna yanakai hannu yana taɓata kuwa tamugun firgita ta farfado a suman cikin dawo hayyacinta. kallonsa take a mugun tsorace kamar taga aljani dama can gata da mugun jin tsoron maza.
tsananin survival instinct post-traumatic stress da take fama dashi aynxu yasa tazama very scared nd alert, kota suma kana taɓata sai ta firgita ta farka a mugun tsorace, a cikin rauni da kasala take kallon kwayar idanunsa ayayinda idanun nata sukayi luiiiiii kmr zasu rufu baisan sanda yay sauri ya tallabota jikinsa ba gani dayay tana numfashi daddaya ga panic attack and palpitations nishi sama sama kmr zata mutu masa ynxun nan.
she was subconsiuosly a bit relieve dataga a hannun stranger ta farfado ba ahannun samarukan kauyensu ba, ibaad yana jira yaji tay magana amma sai shiru sai nishi, like she is figthing to breath...a daddafe ya tallabo fuskarta suna hade ido cikin wani iriyar baqon shauƙi ta damke masa hannunsa da karfin tsiya da sigar neman taimako tana kakalo iska daga kirjinta amugun wahale jin karfin ruwan dayake sauka akansu na karuwa harta saman kirjinta yana raunata mata gangan jikinta sosai.
shide tunda ya rikota jikinsa gabansa yaringa faduwa da wani irin balain ƙarfin bugu wanda bai san namene ba. the girl is too fragile nd beautiful to be termed a human being, gata yar karama kiris ya rage ya kawo aransa ko aljanace but she looks too real to be unreal, dan tsugunawar scnd biyu yy akanta ganin takasa dena kallonsa arude da alaman distorted confusion kmr batama sanda isowarsa ba wnd hakan ya kara ruda mai tunani
she looked so scared and in dire need of his help, tamkar yadda ruwan ke zuba akansu haka nan ruwan hawayenta yake zubowa ahannunsa datay ma mugun damkar karfi.
voiice dinshi adan ƙasaitance game da sake wata shakuarryar gyaran murya Yay tapping face inta ahnkli kuma cikin sauri yace "keeee...keee...ina iyayenki? daga ina kika fito, meya kawoki nan acikin ruwan nan?
jin yay magana sai ta kara razana dashi, duk abubuwan da suka faru na mutuwar addanta suka fara dawo mata kai a mugun firgice ta sakeshi zata mike tsaye ta arce da gudu jiri me karfi ya karo wainota jikinsa caraf kuma taji ya riketa, suka kara haɗe idanunsu waje guda jin wani irin electric shocking mai tsananin qarfi daya sarkafe su waje guda tanajin sassan jikinta yana kara ragwabewa da mummunan tsoro. kirjinta na tsananta bugu tanajinshi fat fat zucyarta yana racing yana daka tsalle tamkar wnda zai ballo waje..
wani azababben kuka ne ya kwace mata, tana kkrin kwace kanta ahannunsa danta gudu taga sam yaki ya saketa, cos he is trying to observe her, waiko kurma ce dan yaga numfashi kawai take iyayi dakyar bata magana shima numfashin datakejan dakyar take janshi waje...
ya dada rikota yace "nace ina iyayenki suke ko ke kurma ce? daga ina kika fito?? kina ji kuwa... tun be gama rufe bakinsa ba yaga ta kalleshi, snn ta juya ta kalli jejin ta fashe da wani irin tsoraccen kuka
daskarewa yayi a tsaye shima yana kallon jejin ransa yace kode kidnappers ne suka saceta ta gudu babu abunda baisaƙa aransa akanta ba.
gabaki daya saiyaji ya kasa samun karfin gwiwar barinta, she is soo young, gata da kyakkwar halittarta da kwayar idanunshi bai taba ganin irin sa ba, he was lost for a moment cikin rasa nayi da ita, first time in his life dayaji gabansa nq mugun fadi akan stranger gata karama sosai ta bashi tausayi,
hasken fatar jikinta dayake nan kamar an wankeshi da ruwan madara yay wani irin kyau wanda ya mugun tafiya da imaninshi yanajin dukkan tsigar jikinshi suna mimmiƙewa duk dama karamace but she sure loook absolutly sexy nd breathtaking barin ma da jikakken sumar kanta ya mammanu agefen wuyarta da kyakkwan fuskarta da wani jarababben diso dison ruwa daya salkafe kan labban dan ƙaramin pinkish lips dinta atake koinanshi ya dauka da wani irin rikitaccen yanayi mai tafe da wata muguwar azabar kokonton ko dagsken ita ba mutum bace.
,..itama dukkan kallonta zage ta ƙare masa ta rasa yadda zatayi dakanta sai uban rawa rawa da jikinta yakeyi tana kuka tabita tattara wuyar rigarta da sauri ta makureshi har wuyarta cikin jarumta, dan takwaco kanta da ga hannunsa tayi, tana shirin barin wajen da wani irin snyin kasaitacyar murya mai daskarar wa taji yace mata "suwaye suke binki? please tell me, ni zan taimaka miki kinji ko?? wani cak kukan ya dauke mata ta juyo tana kallonshi da sigar rashin yadda, dan shiru tayi tana shirin kufcewa taji ya kara damko hannunta wani irin lumshe idanunta tayi cikin sauƙe karyayr numfashi dan har tsagar kanta taji wani irin tsoro me tsanani na tsaga mata zuciya.
yana kkrin juyata ta wani irin kufce hannunta daga nshi da sauri wani irin juyi tayi tare da yarfa masa shauran burbudin jikakken sumanta acikin kwayar idanunshi, da sauri ya sake ta yana kkrin goge ruwan dasuka feppetu masa acikin idanun kan ya gama ya bude idanun sa yaganta can gaba ta arce da gudu, ya tsaya cak baiyi motsi ba ya yanata kallon yadda take falfala gudun tana zuba kukan
tashin hankali da tsoro da bai taɓajin irinsa ba, step daya biyu zuwa na uku tay agabansa sai ragwaf jiri ya kwasheta tafadi kasa wann karon da mugun karfi ciwon raunin zucyarta ya tashi....
he stood der for a while da tunanin ko kawai yashiga motarsa ya shareta ya wuce inda zashi ne koko ya karasa ya dagota inta sake farfadowa sai ya kyaleta ta karata atacan tunda bazatace mai komi ba
wani abu acikin ransa kuma ya kasa idda lissafi, cos he knows when a person is soo scared kamr haka and is experiencing sudden symptoms of heart failure they may exhibit a range of behaviors and physical symptoms irin natan nan, ryt from her Behaviors yaga tulin Anxiety, with panic attacks she is Restles nd agitatated, kmr she is Confused, disoriented, duk dama yay zaton kurma ce amma yasan Difficulty speaking or responding coherently maybe a clear sign of sumting serious musmn ma dayaga afari ta suma kuma ta farfado a firgice so weak nd scared, acikin duka alamomin ciwon raunin zuciya abu dayane tall yarage bai gani ba wanda shine loss of consciousness sai kuma gashinan yaga ta sake sumewa yanzu...
yana gama wann lissafin yakarasa kulle motarsa ya jefa key din a aljihunsa ya juyo, lkcin ruwan saman ahnkli yafara raguwa, motsi motsi ya soma ji daga nesa cikin jejin amma bai kula ba cikin sauri ya karaso kanta yaga bata ko dandanin motsi duk dama ya taɓata.
acikin sauri yafara duban physical symptoms na hrt failure ajikinta yana kuwa dora kansa asaman kirjinta yaji faint parpalpitations with strong Shortness of breath ma'ana ba suma tay bama kawai numfashinta ne yakage ataciki yana mata wahalar fita waje, she started to look so pale nd more weaker, yasan badon ana ruwa ba da zufa tuni ya rufeta
thank god for his elite private club practicals da duk bazai san wayannan abun ynxu ba, dagota yay hannunsa yakaita motarsa seat din baya danya bata up front emergency help dan karta mutu masa ya shiga ukku,
niyyarsa saita farfado kafin ya wuce da ita can wajen haj mairo inyaso daga can anemi iyayenta dagatacan
kai tsaye yafara Loosening zip din doguwar rigarta then he sat her down comfortably ajikinsa ya fara Monitoring vital signs inta kafin can ya fara supplying mata extra oxygen baki da baki cikin ikon Allah kuwa tafara responding...
daga yadan hade bakinsu yahura mata iska yana shafa mata gadon baya ahnkli ahnkli sai kaga ta saki nishi me dan uban karfi wani hammmm sai tasake komawa lagwas ajikinsa amugun raunace, suna cikin wann yanayin bai hankara ba kawai yaga maza da sanduna suna ihuuuu suna fitowa wasu tagaba wasu ta bayansa duk sunga ayaanah kwance ajikinsa yadda yake fmr hura mata iska abaki yay kamar kiss sukeyi ga kuma hannunsa zagaye da ita ta baya nd he had no way to loosen her up face saida ya zarge zip din bayan rigarta..
kafin kace wani abu matasan fulani da buzayen nan kaf suka zageye masa mota suna kkrin zasu faffasa motar da sanda yay sauri ya kullesu aciki bai tsaya kintsa ta ba ya haura kan driver seat ya kunna motar ya taka motar da karfi ya dan razanasu har saida yaga sun ja baya baya.
ihuuu da hayaniyane ya cikkke wajen shikansa ibaad yasan inhar ya fito toh tabbas zasu kashe shi da duka dan yaga ga dukkan alama jahilai ne sosai kuma sunfishi girma da karfi
he was confused as to keep driving them off koya dau wayarsa ya kira gida akawo masa dauki, gashi aayanah ta kankame jikinta abayan seat, ko zip din rigarta bata mayar ba sai kuka kawai take mishi a motar kamr wanda yasota duk yarasa abunda ke masa dadi minti goma basuyi ba sai gasu juma da wasu dattajai sun faso..
nan akafara hayya hayya matasa sukace aisun ga me mota anan suna iskanci da ayaana shiyasa suke so su kashe su atare.
dakyar wani dattijon da ake ganin girmansa ya dakatar da hayaniyar ya karaso wajen ibaad ya kwankwasa masa window ibaad ya bude dan kadan, dacan har mutumin ya fara masa magana cikin bude ido dayaga ibaad din bai nuna alaman tsorata ba ne yatsaya yaji ba'asin sa. ibaad ya gaya masa shima ana ya sameta, snn zai basu yarsu amma inkuma suka tabashi already ya riga da ya kira hukuma ya basu information na inda yke ynxu haka suna hanyar zuwa nan kawai ajirasu su iso shi bazai ma fito ba sai hukuma sunzo.
dake yan kauye akwaisu da mugun tsoron hukuma sai kuma aka samu rarraben kai suka fara negotiating dashi, wai lallai saidai ya fito daga motar, ya basu yarsu hannu da hannu kawai ya wuce dama nemanta sukeyi in kuma be fito ynxu anyi magana ta nitsuwa dashi ba zasu kasheshi anan da duka inyaso duk wani abunda zai faru ya faru
dakyar da wuya ibaad yadau risk ya bude motarsa yafito tare da ayaanahn datake kukan tsoro sosai da alama ma batamasan zip din rigarta yana bude ba.
daga dattijon sai kuma juma sune akurkusa da motarsan sauran matasan dukkansu an umarce su da su tsaya agefe
...yawansu da makaman dake hannun su da ibaad yagani yasa kansa yafara juyawa kamr abun arxiki su juma suka fara magana da shi, da juma da dattijon ibaad ya musu bayani dalla dalla yadda ya same ayanah anan.
fuska ba yabo ba fallasa juma yace mish sun gode dama shine mahaifinta.....neman ta sukeyi ɓace musu tay.. amma tunda ansameta shikenan.
ibaad was kind of relieve dayaga sun fahimceshi, dan juyawa yay bayansa zai cewa ayaanahn ta karasa wajensu yana budan baki kamar kiftawa da bismillah yaji an buga masa wani abu akai da mugun karfi for good 30 minutes baisan inda yake ba sai kamr bayan mintina talatin masu kyau ya bude idonsa yaga hannunsa adaure gashi nan awani fadar kauye agurfane agaban wasu sarakuna su biyu, taron mata da matasa da dattajai sun zagaye su...
yana daga kai abunda yafara ji a kunnensa shine "ni juma maharazou naba da auren yata ayanah, inyaso yaje canshi bariki ya karasa abunda ya farayi da ita, danko mun kashe shi bamusan dan waye bane kuma yariga ya kira hukuma gara abashi yarinyar tunda yafara lalata yaje can da ita nayafeta ma duniya su je duk inda zasuje suyi iskanci suyi muna fatan har abada karta sake dawowa mana wann gari....
ran sarkin buzu ya turmusa ya baci baice komi ba dan sosai yaso abashi yarinyar sabida yaga tana da kyau sosai, amma kuma tunda akace musu a motar kafiri aka sameta harkuma ya cire mata riga yana shafa mata jiki sai yazama na bazai iya fitowa fili yace abashi aurenta mashi da almajiransa bakuma.
sarkin fulani ne yace shin kowa ya amince da wann auren??
kusan kowa ya amsa da ehhhh..
sarki ya mike tsaye ya kalle ibaaad cikin ido yace toh kowa ya shaida ayau Mun bayar da auren ayaanah yar gidan juma maharazou wa wnn mutumin mai mota..
agogon ibaad me tsada da suka cire a hannunsa sarkin fulani ya daga sama yace jama'a ashaida wann shine sadakinsa...
amugun rude ibaad ya daga kansa cikin daka ma sarkin burkitaccen tsawa yace 'a'a dakata min malam...wallah ban amince ba.
SURAYYAHMS
08060712446
[04/11, 21:22] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: ⏯️1️⃣4️⃣
wani irin shiru wajen ya dauƙa ayayinda ibaad yagama daka ma sarkin fulanin nasu tsawa da wata iriyar kakkausar murya me razanarwa
"ban amince da wann auren ba, wllh yadda kuka kullashi ann haka xaku warwareshi..what in the world is wrong with u people haaaa daga taimako?...
cikin datsar numfashinsa tare da kai ma bakinsa duka dogaren sarkin yace "kaiiiiiii yaro ka iya bakinka!!kasan cewa agaban sarakuna biyu kake magana zamu iya kashe kafiri, mubinne mushen gawansa ann abanza, dan haka kama mutane shiruuuu ka rusuna kasa kayi ma sarakunanmu godiya da irin dumbin adalcin da sukamaka suka baka mata snn maza maza ka dauki matarka ka kara da gaba...
adaddafe ibaad ya miƙe tsaye jini ya taro a bakin sa still hannun sa biyu duka a daure cikin tsananin tashin hankli da bacin rai yace"wallh baku isa ba ku kukasan wani aure ni bansan shi ba, kuma baku isa ku lakamin wani auren karya ba, tunda har kunsamu yarku, ku kwance ni kawai na kara da gaba, inba tsaban hauka da jahilci ba kun sanni ne da zakumin aure???? kunsan daga ina na fito? waye ubana? haka kawai daga taimakawa yarinya akan hanya sai kucemim wai na aureta a ina aka taba daura aure haka...
Da wani irin zafi zafi dogare ya baaje rigar sa zai zaro dorina ya zanesa cikin tsananin izza da mulki sarkin buzu ya daga masa hannu snn ya kalle ibaad din cikin ido yace "kaiiii yaro kalleni nan..babu tsoro ibaaad ya daga kai ya kallesa duk mamakin yaron sai ya rufe jama'ar majiya da sukay shiru suna kallo
sarki yace duk tashen rashin kunyarka akwai wanda sukafika anan dan haka mu muka daura auran snn babu wanda ya isa yazo ya kwance shi.. akwai wasu sharuda da dole ne zamu gindaya maka akan auren nan inka gama rashin kunya da surutun banzan kan saika sanar damu ka shirya.
acikin kyabe baki sarkin fulani yace "kyaleshi, yana nufin daya lalata mana yarinya zaisha abanza ne bai aureta ba? tomu anan garin majiya duk wanda ya lalata mana yarinya yay iskanci da ita koda bamu daura masa aure ba aure tsakaninsu ya dauro..dan haka tun kafin raina ya baci na saka matasa su maka shegen duka anan gara ka fadi gaskiya snn kay niyyar tattara kafarka da matarka kubar mana gari..
atake jikin ibaad yafara rawa rawa cikin rasa abunda ke masa dadii tsaban bacin rai he was just in a total confused state kmr zai zauce...
cikin tattaro makansa nitsuwa dakyar ya dubi sarakunan yace banfa gane me kuke nufi da na lalata muku yarku nay iskanci da ita ba? ni a ina nasanta da zan lalata, wann karaman yarinyar har me zan dauka ajikinta...
cikin katse shi da hatsala juma yace" kaiii kafiri, karya kakeyi wallahi, karka sake ka raina mana wayo duk cikin mu babu wanda baigane ma idonsa abunda yafaru atsakanin ku ba...
da bacin rai "ibaad yace meyafaru wanda ban maku bayani akai ba?? me kuka gani, innalillahi wa inna ilaiji rajiun
..yallabai dakai fa awajen komi yafaru ni banyi ma yarku komi ba kuma kasani
juma baice masa komi ba ya jawo aayana a wani irin walakntcyrr ya finccikota gabansu a walakance kamar yar baiwa snn ya jefota har cikin fili tare da juyata yanamai nuna masa bayan zip dinta dake nan haryanzu a bude
yace "inba iskanci kukeyi ba uban mezai saka har kacire mata riga snn ka kulleta a motarka kana tsotsan bakinta? tunda ka riga ka lalata min yata toh fa dolene ka tafi can barikin da ita kaje ka karasa iskancin da ita acan wallah bazamu amsheku anan ba.
muryan ibaad na rawa rawa cikin tsananin tashin hankli da rudewa mai gauraye da bacin rai ya lumshe idonsa ahnkli yace "To hell with you malam!! ni ba dan iska lallatacce bane, kuma babu abunda ya hadani da yarka face mutuwar da ta tashi yi na ceto ran ta waiku wasu irin mutane ne haka abunnan ya faru a idonku ne snn kazo ynxu kana kawo wani xancen...just let me go out of this damn place
nan take juma ya hatsala yace au zagina zakayi da yaren ku na kafirai?dan iska kawai makaryaci, baqin kafiri, lallataccen banza dan wuta,..karya kake wallhi
ibaad ya rasa mema zaice dan ransa ya mugun baci, nan take ya bushe idonsa yafara amsa juma azafafe suka fara musu sosai yana cewa shi be lalata musu yarsu ba kuma shi bazai aureta ba infact babu inda zaije musu da ita.
wajen ya cikke da hayaniyar musu tsakanin uban amarya da ango da kuma dukan dattijan fada suka nunamai karara cewa basu aminta da shi ba..cewa ma sukay guduwar da ayanahn tay dama wajensa tadosa.. case upon case ya tashi.
ga matasa birjik sun fito da wukake sanduna da adduna suna jirane kawai sarakuna su bada oda ahau kan ibaad da duka da sara..
basuy tsammanin har zai iya tsaurin idon tambatsa taurin kai da muna zafin kai meyawa agaban sarakunan su ba espclly knowing dat shidayane kuma bai da makami....
sosai lamarin ibaad ya daure musu kai basu taɓa tsammanin akwai tsegeru irinsa ba, suna fada yana fada, ko sarki ne yay magana kuwa sai ya amsashi.
Wani irin runtse idanu aayanah tayi tanata kuka mai zafi atsakiyan wann hayaniyar cikin yanayin tsumayi jikinta na rawa rawa da alaman tana cikin yanayin tsananin neman temakon gaggawa daga alkaryar wannan mummunan qaddara dayake shirin tunkarota yanxu..
batasan waye ibaad ba amma haka kawai aranta sai tanajin kamar ta gwammci ya
tafi da ita kawai danta bar garin ta denama ganin babanta da sauran mutanen da alama dataga kmr kowane ya tsaneta..
tambayar duniyan nan ibaad yay mata akan cewa ta fadi abunda ya faru tsakanishi da ita da bakinta koda su juma zasu yarda amma haka tayi masa shiru tanata kallonsa banda kuka batace komi ba,
duk sai akaga kamar eh dagaske ne hala shine kawai baida gaskiyaaa tabbas iskancin sukayi a motarsa shiyasa ma yake budewa aayanah ido agaban mutane har takasa budan baki ta fadi gaskiyan abunda ya afku.
kan ibaad har juyayi yake tsabar baqin ciki da bacin rai the worst was when aayanah taki sam tay magana dan ta wankeshi daga zargin zina, infact emotional kukan datake tanakan kallon kwayar idonsa da wani siga tana dan girgiza masa kai sai yadada sawa aka dada maidashi makaryaci taɓabbe.
gabaki daya ransa ya hautsina ya mugun baci yadda ya ki sam ya karbi auren yasaka ran juma ma ya matukar baci dashi, yafara cewa abashi sanda kawao wann yaron bai daku bane shiyasa yake da bakin yin musu dasu...
ibaad na tsaye in total shock anger nd intense disbelieve har aka kawo mukeken sandan juma yakarba azafafe yay wuf ya daga sama zai warɓa masa akafarsa niyyarsa ya masa jina jina da duka koda zai dawo hayyacinsa ya amshi auren...
yana daga sandan sama zai rafta kusn ajarumce ibaad yay wufff ya riƙe tamm da daurareen hannunsan jajayen idanunsu suka sarkafu acikin na juna
shikansa juma yasha mugun mamakin irin karfi da taurin ran da yaron yake dashi
matasa masu ruke da adda nan suka fara shirin shigowa fili ganin haka ayaanah tay sauri tazube gwiwarta a kasa jikinta nawani irin rawa ta kama kafafun juma da wani irin kyarma me tattare dakarfin tsumayi kanta acan kasa kamr baiwa muryanta bai fita sosai tsabar kuka take cewa Baba, baba, baba, miɗo waɗi hakuri...dan Allah ka tsaya.
duka suka tsaya kallonta cikin lumshe ido takara fashewa da kuka mai karfin tsumayi tace "hoto maa ɗakku mo, baba karka dakeshi, kayi hakuri karka dakeshi _ko fii Allah_ . Mi waɗi woni waɗde mo,..da mugun karayar zuciya takuma cewa "min njahi jooni kay hakuri...wallh zan bishi mutafi yanxu..
wani irin shiru wajen ya dauƙa dukansu rike da sandan jikin kowa na ɓari da tsananin bacin rai, ibaad ne yay saurin sakewa ahnkli dan duk da mugun haushin da ayanah tabashi, sosai yanayinta ya ragwabar mai da jiki yanajin kmr hawayen ta nasakamai raunin da bai taɓajin irinsa a aduniya ba
jin ibaad yasake sandan yasaka juma ya hankadeta tareda fettataa da kafarsa data kama tafado kasa
cikin masifa da hatsala yace "haa lewru, wawiya kawai..ki tafi,karda kisake barin wnn walakantaccen hannun kin ya kara tabani.."Hoto ɗuum wakkitmo am, da wani irin tsawa yace "Yah!.... Miɗo yi'i maa heɓɓude, tsinanniya kawai, tunda har ni zaku tozarta, ita tay cikin shege, ke za kibi mijinki kafiri mazina ci.., ya kalle idon ibaad da hatsale yace"marar kunya ma irinsa kwarto lalatacce..kuje can gaku ai ga duniyar.
wansu irin zafafan hawaye masu daci ibaad yaji sunciko masa a idanunsa our of no where yaji kansa na juyawa kawai ya tsaya yanata kallon ikon Allah
...daga ganinsa kasa he is very very angry and emotionally dis-armed,yaji mugun haushin ayaana, amma ko kadan bayajin dadi ganin cin zarafi da zagi da akemata at this little fragile young age gata da serious ciwo ajikinta abun sosai yadaga mai hankalinsa bana kadan ba
aayanah tana kuka jikinta na rawa rawa ahnkli ta motsa kanta dake kallon kasa da niyyar zata dan miƙe daga tsungunen datake ta tashi tsaye, tana yin motsi wani jiri me karfi ya debeta tayoo luioo zata fado jikin juma memakon ya riƙeta sai yy saurin yaja jikinsa gefe wani rigib tay tangal tangal kamar zata sulale kasa daf da kafarsa agarin gyara tsayuwa by mistake saita wantsolo mai ruwan datti ajiki dake wajen a jikke yake sosai.
wani irin ihu yay ya kalleta suna hade ido a mugun tsorace ta mike tsaye dakyau ta fara bashi hakuri, dama kmr babban burinsa ne ya ga ya daketa cos all his life ita tafi bashi haushi
yana huci ya daga sanda sama zai warba mata ajiki da wani irin tsorata ta fasa ihu from no where taji ibaad ya ture juman gefe da karfi ya sha gabansa tareda kareta inda sandan direct ya sauka masa atagefen goshinsa duk da haka suga baiko motsa ba yana tsaye yana kareta ita kuma ta boye fuskarta ata bayansa tabi ta tantame rigarsa ta baya amatukar tsorace
....cikin ido suke kallon junansu da juma kowa idanunsa yay matukar jajur, tunkan juma yay magana cikin runtse ido da budewa ibaad yace "ya isa haka!! ka kwance min hannu na kawai ai nace zan tafi da ita....
wani irin mugun sanyi ayanah taji daya furta hakan, batasani ba shi niyyarsa shine in ya dauketa sukayi nisa zai jefar musu da yarsu awani waje ajejin ya kama gabansa inyaso ita tasan nayi dan shide yasan bazai iya kaita gidansu yace komi akanta ba....
Rai abace juma ya ciro wata wuka snn ya saka wukan akan igiyan hannun ibaaad yana gurzawa har a garin kwanceshi saida ya ji masa ciwo sosai a hannnu snn aka kawo su tsakiya aka gurfanan dashi agaban sarakuna aka kira wata muguwar bokanya tasha jan yadi da bakin mayafi wanda daga ganinta kasan da mugayen aljanu datake aiki dan kuwa baqar buzuwace.
nan akafara sakamai dokoki tsaurara, akace tunda har ya amince zai tafi musu da yarsu zasu na tracking insa ta hanyar tsafi, sharadin shine idan har yaje yar musu da yarsu toh duk inda yake a duniyar nan zasu kashe shi, tunda har shi ya lalata dolen sa ne kawai ya zauna da ita,.. cewar sarkin buzaye ahakan ma gata sukamata, sbida hannun su bazai rube su yanke su zubarba
..duk dama yayan juma sun jawo musu tozarci me tsanani yazamana dolene dodon tsafin su na garin yakaresu snn atabbata sundawwama acikin ynyin tozarcin da suka zabar makansu snn duk wnda ya lalata musu yarsu dolensa ne kawai sai ya aura.
ibaad yaki cewa komi har suka gama maganan su shide yana rike da hannunsa da juma yaji mai ciwo da wuƙa dan har jini ke diga awajen sosai,
babu kalar tsoratar dashi da bokan batay ba, har dakinsa saida ta nunamai acikin kokon tsafinta, snn ta gayamai tarihin gidansu, da komi da komi, tace mai uwarsa dayafison zasu fara kashewa muddin yabar Aayana ta bata ahannunsa, idan kuma shine yaje ya yarmusu da ita toh shi din zasu kashe...
shide yasan basu isa sumai komi wanda Allah bai masa ba amma abun sun ya mugun daga masa hankli sosai.
bayan komi ya lafa hakanan aka sakaso agaba dashi da ayaana
dandazon matasa da sanduna da adda da wukake suka sako su agaba sukarakasu har gaban motarsa ajeji lokacin sosai magriba ya rufa ga garin yayi wani irin mugun sanyi
a seat din baya ayanah ta zauna ta hade kanta da gwiwarta tanata zubda hawaye cikin rasa mema takeji akanta ynxu...
wucewarsu bada jimawa ba aka naɗawa juma lambar yabo sabida jarumtar da ya nuna wajen hukunta yayansa dukansu biyu bisa tsarin al'ada akan washe gari duk zaa hadu za'a tattauna tsakanin sarakuna asan wani matsayi za a bashi agarin sabida jarumtar da ya nuna wajen kare mutuncin garin majiya da kuma al'adarsu.
bangaren ibaad kuwa tuki kawai yakeyi yana tsaga jejin da gudu amma gabaki daya hanklinsa baiya jikinsa
tunda suka kama hanya zuwa tudu basuce ma junansu komi ba sai kuka ayaana takeyi tun yana jinta haryazo ya dena jinta gabaki daya
within 20 minutes drive suna danno kwana gidan hajya mairo jinin dake famar diga agefen kansa da hannunsa gabaki daya suka bata mai farin rigansa baja baja ransa a mugun bace kowani sake kula yatake baiyi ba yana tsayawa akofar gidan hajya mairo ya sauka a motar ganin kofar gidan akulle da kwado kai tsaye ya wuce ya samu wasu dattijan maza su biyu akofar gidan ya musu sallama sunata kallon jnin daya batamai jiki dai suka amshi adar dar, bayabo ba fallasa ya tambayesu ko hajy mairo tana ina yaga kofar gidanta akulle
dayan dattijon ne yay jarumta yahau gaya masa ai hajiya kam bakanta yau babu kanta tana can asibiti ance jikarta inayah ta rasu snn yar rikontan ma taawuren ta bace a asibitin badq jimawa ba kuma asan ina taje ba anacan dai ana nemanta....ibaad ya rasa meke masa dadi, gashi mutanen suna ta kallonsa wani iri da rashin yarda mussmn ganin jini ajikinsa baja baja. "yaso ya tambaye su kwatancen asibitin amma bai samu fuska ba. kawai sai ya musu godiya ya koma ya shiga motarsa, gabaki daya yanajin wayarsa tanata ringing amma ko kadam baida nitsuwar amsawa yawo yay kadan agarin yana tambayar asibiti toh dama karamin PHC ne guda daya bawani wahalar samu yake dashi ba.
wani matashi ne daya bashi dubu biyu ya amince ta shiga motar yakaisa har asibitin wanda tunkan ya gama parking ya hango hajy mairo curko curko da polisawa ta birkta wajen ta tada buhun barkwanon bala'i tana cewa kawai a fito mata da yarta taawure snn dolene su mata bayanim dalilin dayasa aka bar juma yazo har nan ya tafi da gawar inayah, inba haka ba kuma zatakaisu kara babban kotu acikin gari..
tsabar masifa har rirrike hajya mairo akeyi tana kumfar baki
polisawa biyu aka tura da matasa kusan su uku cikin jeji domin neman taawure wanda hajiya aranta tanada kyakkwan tabbacin cewa bacewar taawure a asibiti bana lafiya bane, kode zata je ta dau mummunan fansa akan mijinta juma ne ko kuma zataje ta dauko gawar yarta inayah a hannunsa tazo dashi.
cikin sauri ibaad ya sallame yaron da kudi snn ya taho wajen da ake hayaniyar da sauri
hajya mairo batama gansa ba saida ya fixgo ta jikinsa tay baya suna hade ido dashi ta rushe masa da wani dan uban kuka tace "Rayyan??? rayyanu wayooo rayyanu bawan Allah wai kaine nake gani ko mafarki nakeyi?? tunbe amsq ba cikin mugun kukan raki tace ohhh Allah nagode maka da ka aiko min rayyanu daga sama aigara dakazo kagani da idonka, dan banda cin mutunci da zalunta na babu abunda akeyi agarin nan....sabida da Allah gawar jika ta da yata sukutum fa aka sace asibitin nan, kawai ka gaya musu su fito min da ita yanxun nan ko mu hadu mu tada tarzoma...
ibaad yay rolling idanun sa amugun gajiye baice mata komi ba ya kama hannunta da wni irin mugun karfi ya jawota can gefe yace "hajiya dan Allah kimin shiru duk naji abunda ya faru
wanda ya kawo nin yaban labari cewa uban yarinya ne yazo ya dauke gawar yarsa snn ai ance miki ficewa yarki tay dakanta ba sace ta akai ba kuma ba anje neman yarkin ajeji ba?? cikin yanke kukan rakin cak ta daga ido hawaye zuru zuru a idonta ta budi baki tana kallonsa "ohhh ohhh Allah wani dan uban magulmacin ne ya gaya maka haka kai kuma sarkin jin gulma ?? kai ammaaaaa akwai yan maganadisu kanen malaika jibirilu iyayen baza rahoto agarin nan
ibaad ya rasa meke masa dadi yace hjy ki tsaya dan Allah ki saurareni...kallonsa take tsaf taaf adan sashence tace ai ina jinka..ya budi baki zai magana kenan cikin raxana tace menake gani ajikinka haka rayyanu? yoooo kai kuma wani sabon gayen ne haka da jini kaca kaca ajikin riga, fisabillahi rayyan meye haka nake gani kaida nasanka da mugun son tsafta, tattabashi tafarayi tanajansa cikin haske sosai tana haskawa ta doka salati tareda cewa innalillah wa inna ilaihi rajiuna jini ne fa duk ajikinka?meya faru...ibaaad karde agarin zuwa kaje ka fadi a mota...wayooo Allahna na shiga uku ai saida nacewa ma zaidu yadena baku motarnan shikenan daga cewa ubanka ya mutu kaima aketa so kallai sai ankashe min kai..
tun be amsa ba tay wufff da sauri tabarshi zata koma cikin aabitin da uban gudu tana ihun sunan nurse tana cewa ..ke nass kee nasss..nasss..nasss, nurse tana fitowa ta jawota har gaban ibaad din tana cewa kiga jini ne kaca kaca ajikin jikana dan Allah kushiga ciki kiduba min shi kinji yar albarkata,.shine kadai mini gata na..na tabbata ji yaya ana so akasheni agarin nan shine yazo zai taimaka min gashi shima ansakosa min shi agaba da maita nashiga uku na tana fadin haka ta kara rushewa da kuka...
nurse din tana kkrin tabashi yadan haɗe rai yace "kibari kawai, nagode.. please i have someone that may need urgent attention in my car.. nurse tace toh.. da sauri ya juya tunkan hajy mairo tacakumo rigarsa danyasan zata iya masa hakan suna kaiwa motarsa da nurse yay maza yabude gidan bayan agaggauce snn yajawo ayaanah da already bata motsi ya dauko cak ahannunsa...
hajiya mairo duk ta rikice tana bibiyrsu tana share hawaye tanata lallekawa tana binsa abaya tanacewa waye wann kuma rayyanu?? waye wann kamar ayaanah, laaaahhhh ayanahn ce, duk ta kasa nitsuwa sai binsa take tana cewa...kai kuma rayyanu a ina ka samu ayaanahn toh, ganin bai kulata ba ta dada rushe masa da kuka tana cewa innalillahi wa inna ilaihi rajiun kardai yar nan mutuwa itama tayi...
hade ransa yay bai ko kulata ba sabida uban attention din jama'a data jawo kansu da koke kokenta a cikin sauri yabi nurse din da ayaanan ahannunsa kai tsaye yakaita ciki aka bata gado snn ya dawo wajen biyan kudi ya ciro wallet dinsa ya kirga kudin ya biya kai tsaye..
yana juyowa suka hade ido da hajiya mairo tsabar ta damu taji bayani jikinta har rawa yakeyo dakansa da muryan kuka tace rayyanu dan Allah ka amsani kawai ina ka samo ayaanah??
a nitse yace kinsantane?
da sauri tace ehh mana, itama ai jikata ce anan garin, itace fa aka musu rasuwar gashi nan uwarta ma ta gudu. rayyanu inma kaine ka buge musu yarsu ta mutu ahannunka gara kawai ka fara gaya min gaskiyarka anan duka tsakaninka da Allah, ai shi Allahu gafhurahimi ne, saimu rufawa kanmu asiri mu roke taawure muyi biyan diyyya...dan wallah asarar yaya biyu arana daya bakaramin abu bane...
dan shiru yay yanata kallonta tareda jin wani irin intense relieve asaman kirjinsa sanin cewa hajy tasan yrinyar ma, shiru yay har saida tagama rakinta snn yace hajiya pls..nifa ba bugeta nayi ba she is just weak snn mahaifinta ne ya bani ita...in akayi stabilizing inta anan zan gaya miki komi akan haka pls kizauna anan kijira ni zanje ne nay sallah waje na dawo,
dan share hawayenta tay tace toh, toh muje sai in rakaka mana kayi sallahn..
kai tsaye ya juyo fuskarsa a mugun daure ya kalleta kmr wani boss yace "a'a kizauna nace miki hajya waike mesa kike min hakane kam duk kinsa anata min kallo kawai barawo
..cikin kyabe baki tace yooh to kaiwaye da ba za'a kalleka ba, cemaka akay dan adam abun yarda ne? yoh gadinka mana zanyi karkaje ka gudu binni abarni da gawan ayaanah ni bansan me zance ma taawure ba. cikin lumshe ido da budewa yace "saiki basu kanki akashe ki amadadi na
baki bude tace.."ehhhj yooo dama ai nasan ka tsaneni rayyanu, duk baqin cikin ganina araye da kakeji dan kar naga aurenka bqzai tqba yuwa ba inanan daram, toh ynxu de kaje ka dawo din kamin cikkn bayani dan wallah juma buzu ne kuma yafi ka rashin mutunci.
karamin tsaki yay baice komi ba ya kama hanya ya fice abunsa, acikin motarsa yabude kai tsaye ya jawo jakarsa yaciro wata plqin riga me tsafta snn ya nemi bayi a asibitin yay tsarki ya wanke jikinsa sosai snn yay alwala abune me wuya kaga yahada sallah biyu yaukam a dan dolensa ya haɗa magriba da ishaiii snn ya tura text ma bappa zaidu da mum dinsa...
yana idarwa still baibi takan wayarsan ba ya dawo cikin asibitin baiko kula kakar tasa ba yajeciki ya duba jikin ayaanahn, she is still unconsious amma bana suma ba, bacci kawai takeyi sabida alluran da aka mata na sedatives, yasan it will keep her alive till tmwr morning yasan duk ƙinsa da karban yarinyar kusan dole ne kawai yayi tunanin yadda zaiyi akaita babban asibiti gobe gobe dan amata proper treatment.
SURAYYAHM/08060712446
[06/11, 14:55] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: 1️⃣5️⃣
cikin sauke wata nannauyar ajiyar zuciya mai tsanananin sanyi ibaad yadauke kasalallen kwayar idanunsa akan kyakkwan fuskar ayaanah dake kwance akan gadon asibitin tana bacci har yanzu bata bude idanunta ba
jikakken sumar kanta ya mammanu agefen wuyarta da fuskarta da wani jarababben diso dison ruwan hawaye daya salkafe tun daga long curly eye lashes inta har zuwa kan dan ƙaramin lips dinta dat is blush pink in colour, perfectly lined da baƙin zanen baki kamar an zana matashi da gazal, kallon ta yakeyi cikin yanayin da baisan ma mayake ji akanta ba, haushi ne, tausyayi ne, shide duk rasa wanne yafi ji aransa..
..abubuwan da suka farun ne kawai suka shiga dawomasa kai gabaki daya yarasa tainama zai nitsu ya fara warwaresu.
shide yasan duk tsiya bazai taba iya komawa gidansu da ayaanah snn ya sanar dasu cewa anbashi matar aure kwasam awani gari ba, matar ma yar karamar yarinya kmr wann, he just cant imagine the scandalous chaos this situation will bring upon his life, kusan dolene kawai ya samu kakarsa hajiy mairo a warware maganan nan auren nan anan tun wuri.
yana cikin wann tunanin yaji karar bude kofa ya juyo ahankli wata nurse ce ta shigo a natse da sallama abakinta, jikinta sanye da All white uniform na nurses riga da wando da white hijabi me dan girma sabida yadda ta manyanta sosai, haukar da juma yazo yay musu dazun yasaka aka kira musu local gorvenment chairman na yankin yay maza-maza ya sa aka turo da security da kuma older nurses nd midwives for immidiete duty shift replcment wanda dai akasan zasu iya tunkarar kowani irin jahilin mutum musnmn ma irinsu juma masu shigowa gatsau cikin kananan asibitin gwamnati da maqami suna masu yin barazana.
Ibaad ya zauna a kujerar gefen gadon Hannuwansa a dunkule, idanunsa suna kan ayaanah harsuka gama gaisawa da nurse in ayayinda tafara duban jikin ayanahn sosai.
tana gama dubata ta juyo tace "Alhamdullahi, she is resting, sedatives in nan yataimaka mata sosai, “zaku iya tafiya sai Ku dawo da safe. Idan ta tashi lafiya,an tabbatar komai daidai yake, sai ku tafi da ita gida.”
atakaice ibaad yace mata toh mungode...
yan rubuce rubucenta tay ta miƙa masa papern snn ta wuce tabarshi anan, baiko karanta papern ba ya cusa a aljihun wandonsa kallo daya yay ma ayaanah da hazel eyes insa dat are piercing nd emontionless da bazaka taɓa iya banbance ko kallon tausayi yake mata ko na mugun jin haushi ba...
for abt 3 mints yana kallonta can snn yasaki karamin ajiyan zuciya ya fice ya samu hajy mairo tanata surutu a waya da matasa wanda suka fice jeji neman taawure da polisawa, duk ance mata ba aga taawuren ba dan har garin majiya anje amma ba aganta ba. police dinne ya kwantar mata da hankli yace sun baza idanun su snn bazasu bar jejin majiya ba har sai sun samu labarin inda taawure take snn hanklinta ya kwanta.
kallonta ibaad yake harta gama ta sauƙe wayar a kunnenta cikin rauni hawaye ya sauka acikin kwayar idanunta ahankli tabi ta share hawayen da bakin gyalenta araunace snn ta kalleshi tace ya jikin ayaanahn?
kureta yay da kallo for a while snn yace "sunce muje gida sai gobe zamu iya tafiya da ita.
kara rushewa tay da kuka tana girgiza kai tana cewa 'aa wallah ba'a isa ba. babu inda zamuje hakanan daga zuwa caji offis ko wani kwakwaran sallama banyi da inayah ba akazo akacemin wai ta rasu kuma juma yazo ya dauki gawarta, wallah wallah bazan je koina ba bare hakan ya kara faruwa akan ayaanah,inaa karya akeyi, ni anyama ba haɗa baki da nass din asibitin nan juma yay ba kuwa??...
cikin katseta ibaad yace toh me kikeso muyi ynxu bayan ga security ko a tsayawa kikeso muyi anan har gobe nifa agajiye nake . tana share hawayenta tace ni bance maka ka kwana a tsaye ba, ai akwai masallacin asibiti inda kaje kayi sallah muje can babu kowa aciki kagama hutunka sai ka kwana anan ni zan kwana agefen ayaanah
gyada mata kai kawai yay suka kama hanya suka fice harabar asibitin wani irin dan uban sanyi ne yasauka agarin tsabar ruwan sama da suka sha sai ɓari hajy mairo take ta riko hannun ibaad kam kam direct masallacin ya wuce da ita suka samu kuwa babu kowa aciki sai hasken fitilan solar tana zama ya fice yaje motarsa ya dauko jakarsa da basket din abinci da sauran aikan ya taho mata dashi.
samunta yay tanata kuka ahnkli tana maganganu, shide baice komi ya zauna gefenta yay shiru yana jinta har saida ta gama duk mitarta da masifarta akan juma da kuma mutuwar inayah da babu tantama kaidaga yanayinta kasan mutuwar tan yay mata zafi bana kadan ba
can tay shiru dan tariga dasanin cewa ibaad ba rarrashinta zaiyi ba, kusan sa'a ma taci dayake kulata yau sosai, yo dama ace jikanta mujaheed ne tasan shikam da har kukan sai yatayata yi shikuma maheer tasan sosai zai lallasheta, da haushin hakan ta harareshi yay kwafa yana kallonta girarsa na sama adage ahankli yace "Inkin gama kukan ga abinci nan ammi tace inkawo miki. tsinin baki tay kamar bazata amshi ba ganin ya kara dauke kai akanta yana daddana wayarsa yasa tay wuf ta jawo basket din gabanta tana budewa tana masifa "Allah wadarar naka ya lalace mutum sai kace dutsi kaga tsohuwa tana rabza kuka amma sannu common bazaka iya gaya mata ba, rayyanu wallh ka zanca hali dan babu wanda zai baka matar aure da wnn baqin halin naka ahto...
baice mata komi ba tana bude abincin wani dan uban qamshin kaza ya budeta cikin lumshe ido da budewa tace "masha Allahu.. wann koda bansani ba fatima ne tay min wnn bandashen, a raunace ta dan cijja labbanta sai kuma ta rushe da kuka "ohhh fatima, Allah ya miki Albarka fatima, yar albarka haihuwar ki ne kawai banyi ba wallh duk kinfimin su zaidu da muhammadu kedai Allah yakai haske kabarinki...ibaad ya mata wani irin mugun kallo a mugun dakile yace "au addua kike ma uwata ta mutu kome? adan hatsale ta kallesa "yo mexan fada ka kulani inba haka ba? rayyanu rasuwa fa akamin amma kocemin ya hakuri bakayi ba wann wani irin rayuwa ne kakeyi haka da dakkken zuciya fisballahi abu babu tsari babu tausayi aciki.
hade rai yay yace bazan baki hakuri ba kawai kici abincinki in mun gaisa zan miki duk wani abunda kikeso haba mutum yacemiki yagama gajiya kinzo kin zauna kinata cikamai kunne da koke koken banza
...baki bude take kallonshi tay kifi kifi da idanu zata amsa cikin katseta yace" kinga tsohuwa babu wani abunda zance miki face saikin nitsu kinci abincin nan...hawaye na zuba mata yarrrr a idonta ta karkada kai cikin kyabe baki tace "Allah ya fika rayyanu, wallah Allah ya fika tunda harni kake min fada kamar ban haife ubanka ba dadinta dai kaima kasan zafin mutuwa. batare da ya kulata ba ya karbe abincin ya bude very swifly cikin nitsuwa da tsafta yaje ya wanke spoon da plate ya dawo ya zuba mata isasshe, yasa mata ruwa da fresh juice din da aka hado mata dashi ya aje mata agabanta snn ya kalleta yace bismillah"
..hawayenta ta share ta dau abincin tay bismillh tana kaiwa loma daya bakinta jin dadin abincin yasa takara rushewa da kuka..ganin ibaad ya hatsala yaja tsaki yatashi zai bar wajen
tay wuf ta cakumo gefen rigarsa kamar barawo, cikin lumshe ido da budewa yace haba hajiya waime hakane kinga ainace miki nagaji kawai inbazakici abincin nan ba ne kigayamin in rufeshi what is wrong with u
tanakan tauna naman tace"toh shikenan mutum bazaiy kukan dadi ba uban waye yake ji dani a duniyan nan inba fatima ba badan ita ba ina ce saide in kwana da yunwa yau
yace toh saiki ce inkiramiki ita kimata kukan nide wallah kika sake baremin baki zan fita waje i am so tired..
cikin yatsina tace toh naji naji Allah ya huci zuciyarka magajin babansa. cikin shareta ya dan kwace rigarsa ya dawo ya zauna kusa da ita daga nan sai bata kara cemai komi ba tanitsu taci abincin tanaci tana karkada kai ita dayanta tanakan tunawa da surkuwanta fatima...in sha Allahu zaidu saiya auri fatima haka kawai gidanmu bai koshi ba bazan kai fatima dawa ba.
.ita kadanta taketa raya hakan aranta har saida tay nakk da abincin ta koshi sosai, ibaad ya tattara plate din yaje waje bakin borehole ya dauraye tasstass
yazo da tsintsiya mai kyau daga waje yakara share wajen yay fesss yay kyan gani, tay tagumi sai kallonsa take tana kyabe baki itade duk ta rasa wani irin aljanun son tsafta Allah ya zuba masa.,
bayan ya gamane ya tura mata sakon anty safeeran agabanta tanata kallo tana yabawa sosai shikuma ya zuba makansa sauran abincin dan kadan yy bismillh ya fara ci anatsa, baiy kamr loma biyar ba ta matso kusa dashi tafara bashi labarin duk ydda ake ciki da lamarin juma da taawure from A-Z tana tashan mamakin ganin ibaad baiko girgiza da jin labarin ba ita kuwa dake bada labarin har tana kuka tana tara majina..
shiru yay har saida ta gama snn ya juyo ya kalleta cikin nitsuwa yace mata kukan ya isa haka kartaje tay ciwo. dakyar tay shiru saida ta nitsu snn shima yake gaya mata labarin abunda ya faru dashi, sosai tasha mamakinsa, tabi ta rushe masa da kuka kamar an bugeta tahau rufeshi da masifa najin irin taurin kan dayaje yy agaban sarkin fulani da na buzaye"
kai rayyanu na lura asirina kake so ka tonamin inba haka ba meye wann fisbillah, meye zaikai ka yin sa'insa da matsafa, jahilai, bokaye, baqaqn mugaye, azzaluman mutanen nan??? yo shikansa juman ai ba sallan yakeyi ba inba auren qaddara ba mema taawure zatay da jahili irinsa gashi gabaki daya ya lalata mata rayuwarta dana yayanta shine zai baka auren aayanah sadaka, lallai bansan juma ya tsane yarinyar nan har haka ba...toh ynxu inda ace bakaibane fa da saidai mu nema ayaanah a duniyar nan mu rasa ta har abada wayyo Allah, Allah ya isa, Allah ya isa tsakanina da juma Allah saiya saka ma taawure baiwar Allah babu abunda takwasa a auren nan sai baqin ciki da damuwa kajjje kacewa surkin naka Allah yafishi. mugu kawai azzalumi boka ma dashi, uban waye zaiy surki dashi inba irinka ba..
yadda duk ta rude tana masifar shirme tana rabza kuka tana bori yasaka ibaad yay shiru
baice komi ba, sai can daya lura kmr abun dagaskene ya girgizata yamata ciwo snn ya dan jawota jikinsa ta lafe ya rungumeta ya lallasheta sosai har saida ta nitsu tay shiru.
can sai ta dago kai ta kallesa tace "toy yanzu ya ake ciki? ka amshi auren kenan ko ya?
kai tsaye ahnkli yace "a'a ban karba ba. akan me zan karba?? kijiki da wata maganan banza
tace "a'a ni karka haura min rayyanu lokacin da kukayi abunku ina nan ne? amma ai ynxun nan kace sun dauke agogonka sunyi sadaki dashi kenan kuma sun baka yarinya ka karba aayanan ta zama matarka kenan ai...
yace awani addinin ne ta zama mata ta..wann fa ba aure bane hajiya dan wallah bai dauru ba inkuma baki amince da hakan ba gobe sassafe ki kiramana malami yazo nan yamiki bayani kiji, ni badon walakanta yarinyar da ciwo danaga anayi ba da saidai su kasheni awajen amma babu abunda zai saka in kawota nan dan babu abunda ya hadani da ita..
wani irin harararsa tay kmr ruwan idonta zai duba kasa tace "tokai yanxu saima a dauke ayaanan abaka kyauta kuma ka karba? yarinya wankakkeiya kyakkawa, me ilimi, da asali wacce harka mutu bazaka same kamarta ba,karka ga juma yay maka bozonta ka dauka ko shi yana dakai ne, toh wallh wallahi barikaji kakanta da kakan kanta hanshakan malaman addinin musulunci ne shikansa uban taawure hamshakin manomi ne me arzikin gaske ciwo da yaki ne ya cinyeshi mutuwa kuma ya raba taawure da gatanta har qaddarar aure yafado mata akan juma. toh ka iye bakinka akan yar jikata ahtooh ayaanah tafi karfinka..
tunda tafara maganan wani irin kallo kawai yake binta dashi tana rufe baki yace "wann duk ke ta shafa nidai bana sonta. kuma bazan karbi wani aure ba. kawai kisan nayi akashe maganar nan tun anan. snn kisani ina da duk wani labarin abunda ke faruwa dake anan garin tun daga kan satar da ake miki har da yan ta'adda da kike case dasu kina kaiwa maganan auren nan gida wallah saina tona miki asiri dake da sana'ar taki duk za'a kwasheku akaiku gida inga ta tsiyar..
baki bude ta dinga kallonsa cikin tafa hannu ohhh ni mairo ashe har cctv aka saka min kenan toh uban waye ya gaggaya maka wann uban karya haka rayyanu har kuma ka yadda?wani case? ni har ina nagamu da yan kidnaping..
fuskarsa a dore yace "zaki sani...kinsan ni bana wann wasan. har police station zanje a dauko min file din cases dinki da yan daban garin nan harda wanda kike boye masu bappa
rushewa da kuka tay tafara maganganu masu tsananin ban dariya ko ajikinshi haka ya hade rai ya dinga razanata..da kyar dai suka gama case dinnan sukayi bacci.
washe gari kusan da asubah ta farka taga yadda ya cire rigarsa me qamshi ya rufeta dashi dan kartasha sanyi da uban sauro shikuma ahakan ya hakura ya kwana atakure duk data farka ta kallesa atakure sai taji mugun tausayinsa ya kamata sosai, tashi tay ta rufesa da rigar snn ta koma cikin asibiti taje dan tay sallah snn ta duba jikin ayaanah
samu tay ayanah harta farka but she is very weak dakyar ma take magana..ga yunwa ga gajiya ganin kanta kwance akan gadon da yar uwarta ta rasu shiya kara dawowa mata da radadin zafin mutuwarta sabowa.
dakyar hajya mairo ta sakata sukayi sallah snn tanemi ruwan zafi ta bata tasha tazauna ta dinga lallashinta tana tambayarta duk abunda ya faru dan gabaki daya so take tasake jin sauran labarin yiyuwar auren nasu da jikarta ibaad, Allah Allah take taji inhar ibaad amince toh bazata sake a raba auren nan ba kodan ta samu kwakkwan dalilu nawucewa da ita birni na har abada...
dagata dayan bangaren kuwa daga cikin zauren wani gida dake can can jeji taawure ta fito, wata yar tsohuwace agidan wacce koyaushe taawure ta haihu ita take zuwa tay mata wankan gida har tamata jinya sosai sabida tuntuni juma ya hana hajya mairo taka gidansa.
anan wajen tsohuwar taawure taji dukkan labarin yadda aka binne yarta inayah awalakance da irin zargin zina da juma ya laƙaka akan yarsun snn ta bata labarin komi daya wakana akan auren ayaanah tace mata ai wani kyakkwn yaro jarumi me mota shine ya tafi da ayaana.
taawure kamar zata zauce haka tay kukan rasa yayanta acikin wnn daren musmn ji datay an aurar da ayanah wa wani wanda batasan sa baa abubuwa sai suka taru suka mata yawa sosai
zuciyarta ya cika da neman fansa bata damu ko zata mutu ayau ko zatay rai ba saitaji ta gwammaci ma gara ace abata duniyar data zauna cikin baqin cikin sanin cewa inayah ta mutu snn ayaanah ta aure wani wnda basu sanshi ba batama san ta ina zata fara nemota ba.
ranar yadda taga rana hakanan taga dare, kuka kam batasan kalar wanda batay shi aranar ba, can da asubah da sukayi sallahn fajr tsohuwar tana dan runtsawa kadan taawure ta bar kan sallahya ta fice ta zaga ta dauko katon sandan bugun shinkafa, igiya, wuka, da roban kananzir da ashana idonta a bushe tabi hasken almuru babu shakka ko tsoro ayanayinta ta saita hanya sai gidansa.
as usual dake sune ata karshe karshen gari babu wanda yasan da zuwanta wajen da aka binne yarta ta wuce direct yadda taga kmr kasa aka shuhhure akan kabarin yasa ta sulale kasa ta fashe da wani irin kuka me balain tsuma ayayin da koinanta ya shiga karkarwa mai tsanani koinanta ya nuna alaman firgita da baqin ciki me tsanani, bude bakinta tayi da niyyar yima inayar addua atake sai kuma taji wani irin nakason zuci ya mamayeta.
daci da baqin cikine ya rinka bin jinin jikintta har izuwa sassan gabobinta sai tayi lagwas jikinta babu kwari sosai tamkar wata nakasashiya haka ta dawo, cikin yanayin rasa me zatayi da rayuwarta ta sulale kan kabarin rigib ta kifu a kan gwuwarta, sai a sann adduar yazo mata tanayi tana wani irin razanannen kuka mai tsananin tsuma zuciya da shiga jiki wanda bata shirya masa ba
kuka tay har saida baqin cikin abun ya ragu mata aranta snn ta miƙe jikinta na rawa rawa idanunta ya mugun rufuwa da baqin ciki da batun daukar fansa tana ganin kamr inta kyale juma tay makanta da y'ay'anta butulci,yadda ya mata asarar yaranta yau takejin ko ta kashe shi, ko tay masa asarar duk wani abunda yakeji dashi masu muhimmanci a duniyansa agabaki day. an eye for an eye
ji take...inhar bata lahanta juma ba gani take kamar bazata kai gobe ba itama..
da makaman yaqinta ta shiga gidan, aurensu shekara 12 kenan babu abunda bata sani gameda arziki da kuma rayuwar juma ba, gogan dama ba tashi yakeyi yay salla akan lokaci ba wata rana ma bayayi bare ma yau da akace za'a tattauna abashi a matsayi afadan majiya ya tabbata babban burinsa na zama namiji me daraja agarin majiya zai yau zai cika...
turakarsa ta shiga kai tsaye batay wata wata ba ta farmasa da dabara yana cikin baccin ta dauresa tam da jikin gadon tun daga kafa har hannaye da jiki irin daurin goron nan tay masa, tana gama kullawa kuwa ya farka a firkice zai magana ta watsa masa makahon mari snn tabi tasamai ihu tafara tsine masa da yarensu tana kuma zaginsa ayanayin da ya mugun bashi tsoro...
tace mai bazai taba yin farinciki arayuwarsa ba, yadda ya binne mata yarta awalaknce shima haka yayansa agaba zasu zo su binneshi a walaknce, kuma inde tana raye bazai taba yin arziki ba har abada...
haka ta bugeshi da sanda tay masa jina jina, snn ta fice da kalanzir din tabibiye dakin ajiya da kan rumbunan abincinsa daya tara dumbin kayan abinci buhunai hatsi sunkai dari uku banda kananan shanya na su barkwano da gyada, waken suya da baqin cikin jin ya rabata da duka yaranta idonta a rufe ta bunka ma duk wani abunda ya tarana arxiki da wahalansa wuta ta kuma tabbata yakama sosai yana ci bal bal snn ta zubar da makamanta ta arce da mugun gudu tay hanyar tudu godiyan Allah da polisawa basu ganta ba harta isa gidan hajiya mairo agalabaice tana haki...
daga bangaren hajy mairon kuwa duk bataji dadi da ayaana ta gaya mata cewa ibaad bai amshi auren ba, hasalima cewa kawai yay zai tafi da ita amma bai furta da bakinsa cewa ya amshi aurenta ba wanda tun anan jikin hajy yqy sany ta san cewa dagasken babu aure. duk dama batay tsammanin hakan zai bata haushi sosai ba sai kuma taji kmr abun bai mata dadi aranta ba sam. kyale ayaanan tay akan ta huta bayan an idar da sallahn fajr awaje salun alun tafita taje tanemo musu malami, ibaad yana kofar masjid din yana zaune suna waya da bappa zaidu sai ga kirar mujaheed ma ya shigo, sun fara magana kenan basuy nisa ba wata nurse tazo har wajen ta kirashi akan anemansa acan ciki dakin ayaanah sallama yay da mujaheed din snn yabita suka wuce ciki kusan atare.
da sassanyar muryan sa yay musu sallama ayaana tanajin muryansa tay sauri ta lunshe idonta da alaman bata son ma ta kara kallonsa ita har yanzu mummunan tsoronsa takeji ganin yadda jiya ya tunkare babanta da kuma yan kauyensu da mugun taurin kai da jarumta har kuma ya kareta duk dama bata wankeshi da zargin zina da aka masa agaban kowa ba.
babu ko shakka tafi kowa farinciki data ji cewa shima jikar hajy mairo ne sai kuma ta bari akan cewa Allah ne kawai yake kareta daya turosa wajen shiya sa tafado ahannun na gida da ynxu batasan ma ya zatay da rayuwarta ba
dama kuma addanta tay mata alkwari akan cewa kota mutu bazata bari wani abu ya cutar da ita ba.. cikin wann yanayin hawaye masu sanyi suka dinga sauka maga daga cikin lunshashun idanunta, tanaji ibaad ya rusuna ya gaida hajiya mairo a mutunce kamr ba itace abokiyar fadarsa ta kullum ba, snn ya gaida malamin nann suka fara magana akan auren agaban kowa su hudun anaji ibaad ya sake maimaita ma malamin yadda auren ya faru.
acikin kankanin lokaci malamin ya warware musu bayani...
daga hajiya mairo, zuwa kan ibaad har ayaanan duk sunajin bayaninsa yace shi siffan daura auren a musulnci yana bukatar Ijāb da Qabūl wato bayarwa da amsa, nd it has to be a mutual offer & acceptance which must be done willingly. muddin ibaad baice “ya karɓa” with his own free choice ba, then auren bai dauru ba, musmn ba da akayi auren while he is still very much uncounsious, bada cikkaken saninsa ba, bada izininsa kona iyayensa ba, given by this alone auren bazaiyu ba ko shariance ne there is no real nikah. yace koda kuwa duk duniya ne aka taru aka shaida, a musulinci irin wnn aure still remain (invalid)
bayan haka Islam does NOT accept a forced marriage for either man or woman musmn while unconsious.
tsadadden agogonsa sa da aka nuna a matsayin sadaki shima malamin yqce ya haramta tunda bada izininsa ya miƙa musu ba daukawa sukayi bada saninsa ba,shima kuma za'a iya alaƙanta musushi da lefin masa sata.
malamin yace tunda auren bai dauru ba babu saki tsakaninsu sai dai "Faskh" wato annulment
Ma'ana auren ya haramta legally not bounded a shariance, snn a addininace dede yake da auren da ba'ayishi ba..
##idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[07/11, 18:44] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: ⏯️1️⃣6️⃣Abunda ke ɓoye!
malamin yana kammala musu bayani cikin lumshe ido da budewa ibaad yafurta alhmdullh acan kasar wuyarsa yanajin wani sanyi na ratsashi taciki ayayinda ayaana kam batasan ma me takeji aranta ba, tagumi hajy mairo tay da alaman bata wani ji dadin bayanan malamin ba, shide ya gama bayani bisa haqqin sharia da kuma nassin musulunci, agabansu akay ma ayaanar wasu yan tambayoyi game da auren wanda dakyar ta iya budan baki ta amsasu, dama ajine ko ibaad ya amshi auren agaban iyayenta da bakin sa, toh da sukaji bai amsa ba, nan aka warware duk wani kananan confusion dake tsakaninsu a shariance batare da wani dogon ɓata lokaci ba.
acikin nitsuwa da girmawa ibaad din ya tashi ya raka malamin waje, suna ficewa hajy mairo tahade rai ta juyo da bambami tanata kallon ayaana
da kmr bazatace komi ba can cikin girgiza kai da rage murya kasa kasa tace "hmmm, ke kuma yannan ai dabaki nuna musu bakison auren nan ba, wann aure ai kariya ne agareko ayaanah, duk taurin kan rayyanu yana girmama nagaba dashi hala ynzu da malamin nan yasaka mana baki ya roqesa ya amsheki a matsayin matarsa kodan kisamu kibishi binni da cikakken lasisinki, inba haka ba dayuwar mahaifinki juma zai zonan yakafa wani kwakkran dalilin da zai karbeki ahannun taawure kuma dai kinsan duk wani kalubale da zaki sha ahannun jikana rayyanu bazai kai rabin dumbin wahala da kuncin rayuwa da zaki kwasa a garin majiya a hannun ubanki juma ba.
dan shiru aayanah tay kmr bada ita hajyn ke magana ba, a mind intq gani take harma yaushe ta isa amata aure bare har ta zaɓi ta zauna da ibaad da tuntuni banda kushe lamarinta babu abunda taji yanayi. hawayen ta na zuba ahankli cikin tunani taki cewa komi, iyaka yawan surutu da lissafe lissafe da hajy mairon takeyi akan hakan saiyasa tadinga jin rauni da mugun tsoro maihade da fargaban yuwar komawarta hannun juma yanamai kare lullumeta, ahnkli wasu sabbin raunattacun hawaye suka dinga fitowa daga cikin idonta cikin rasa abunda zatace mata ta dadayin shiru tana sauke ajiyan zuciya ahankli....
karar bude kofar yasa hajy juyowa katse maganan da sauri, caraf kuwa suka hade idanu da ibaad, wani irin kallo tamasa da shirin masa masifar akan kin auren dayay saidai ganin yanayin daure fuskan daya tunkarota dashi yasaka ta sauko kasa da tempernta suka fara magana cikin hankli ayanah tana hawaye tanajinsu, yadda haj mairon take raki tana kara fahimtar dashi kalar hatsarin da rayuwar ayaanah zai shiga in suka bari hakan ya jawo ta koma kauyen majiya, da irin sharrin tsafi da mugunta dake cikin kauyen, ce masa take duk runtsi duk wuya ayaana saidai inzata zauna ahannunsa dan bazata taɓa bari aji labarin cewa baya tare da ayanah amatsayin ma'aurata ba inba haka ba juma da mukarabansa akauyen majiya zasu tsafeshi tass koma su kasheshi.
tace inma bazai riketa wajensa ba dole ne kawai ya tafi da ita birni inyaso zata gaya ma danta zaidu, ko muhammadu ko kuma surkuwanta fatima su rike mata ayanahn acan. da wani abu aran ibaad ya kalleta bayabo ba fallasa yace "hajiya duk hakan dakike fada fa bazaiyu ba, yarinya da ubanta da uwarta a raye sai ke kice akaita wani waje tay rayuwa, nidai bazan sace musu yarsu in kaita koina ba...ita kanta hjyn fada yay mata yace koda take matsayin kakarsu yakamata ta dinga tuna cewa ba alaqar jini ne ya hadata da taawure ba, taawure yar rikontace, wacce ta sameta sanadiyar aurenta na biyu, dan haka bata da wani hurumin yanke musu wann babban hukuncin akan yarsu..
kusan musu suka dingayi da kakar tashi akan wnn magann duk saikaji ka rasa waye me asalin gaskiya acikinsu...
sunq cikin musun har tawuree tasamu isowa asibitin dake taje gidan hajiya bata sameta ba, tun daga kofar dakin ta tsaya cak tanajin bayaninsu sai jikinta yayi sanyi sosai musmn data gane kmr ansamo yarta ayanah, Allah Allah take ta shigo saidai yadda taji ibaad din yake tsagewa hajy mairo gaskiya akan alakarsu matsayinta na matar kanin uba ga taawure yasa ta dan dakata kadan
yace "sam shi bazai tafi da wata ayaanah birni ba, inma kareta sukeso suyi toh ta zauna mana agaban mahaifyarta anan, hjy mairo taci kuka, tamasa zagin duniyan nan amma ko ajikinsa,
duk ta dauka tsabar baqin hali ne da ra'ayin banza yasa yake ture maganan tafiya kano da ayanahn gefe yana nuna bayaso, batason harga Allah tun jiya ya riga ya shirya yin haka aransa ba. babbn burinsa shine yajawo wata babban yarjejeniya a tsakaninsu dan ya zamana tay saurin jin maganansa akan batun dawowarta gida, in return shikuma saiyace mata zai wuce da ayanah binni. kawai de so yake yaga yadaureta da jijiyar wuyarta, dan ta amshi dukkan bukatansa, hajiya mairo tsohuwa ce mai son rikici yasan saiyay da gaske kafin ya iya rabata da kauyen nan na har abada.
suna tsaka da wann musun ahnkli taawure tabude kofar tare da musu sallama sabida bata da wani dogon lokacin batawa ya zame mata dolene taje wani waje me nisa ta ɓoye kanta nadan wani lokaci sabida aika aikan da ta rattabawa arzikin juma..
tanayin sallama kusan kallo daya ibaad yay mata jikinsa ya bashi ko ita wacece, caraf kuwa hjy mairo ta juyo baki na rawa ta ambace sunanta tana hamdala a raunace suka dan rungume juna cikin fashewa da sabon kuka tana tuhumarta ina taje
jin muryan taawure yasaka ayaanah tay firgit ta bude idanunta da suka gama jiƙkewa da ruwan hawaye dan yadda taji ibaad yanata rejecting inta yadada sawa jikinta yay sanyi bana kadan ba, sai ta dada aminta dacewa duk duniya ne aka tsaneta, ba zallan babanta da yan kauyensu ba, ita de da alama kowa ne baya son riketa.
muryan taawure dataji yasa ta kara fashewa da kukan itama ta firgita tana cewa umma umma jikinta na rawa har zata diro kasa daga gadon ibaad yay sauri ya rikota ajikinsa da karfi duk da firgicin fushi data farayi masa bai saketa ba har kafin nan taawuren ta sake hajy ta karaso wajensu ta amshe a hannunsa ta rungume yartan tsamm da wano mugun karfin shauqi ta lullumeta kamar za'a kwace mata ita dan ko kadan batay tsammanin zata zo nan ta tarar da ayanahnta ba...
sosai nauyin datakeji a zucyarta ya dan ragu data rungume ayaanah..koba komi tay riba tunda ta samu yarta Alhamdullh
dake taji duk abunda suke fada tun a kofa bata kula bayanin aayana ba har saida ta fara gode ma ibaad tanamai sakamai albarka da ya dawo mata da yarta wajen hajy mairo
kalamanta masu sanyi sosai suka ratsashi, idanunsa suka ciko da ruwan hawaye, tausayin taawuren ya hanashi furta mata komi kai kawai yake gyada mata cikin sanyin jiki har snn yay excusing dinsu ya fice waje agaggauce ya nufi motarsa ya shiga yazauna aciki tare da kifa kansa akan stiring dan yay catching breath insa...
hajy mairo batay kasa a giwa ba ibaad yana ficewa kusan tass ta kwashe labarin yadda akayi da batun auren ibaad da ayaanah tagaya ma taawure, itama taawuren bata tsaya ba tagaya mata iya abunda taje tayi ma juma acan kauyen majiya amatsayin daukar fansa wanda hakan ya razana hajy mairo sosai dan ta jima da sanin cewa taawure mace ce mai kunya da dumbin haquri.
sai kallon bakinta take tana salati.."la ha ila ha illahu, anya taawure kina da hanklin kuwa da kikaje majiya kika aikata musu irin wann tijara da dumbin asara? toh da yanzu sun kamaki sun suka kashe ki fa ma ubam waye zakiwa asara inba yarki ba.
kusan a zuciye cikin fushi taawure tace "hajiya koda naje majiya a shirye nake, akasheni mana,dama..meye zan samu na farinciki a duniyan nan bayan juma yay wa ƴata sharrin zina ya tozartata snnn ya walaknta gawarta, yanzu inba don ahannun jikanki ayanaah ta fado inace da har na mutu bazan san inda yata take ba? hajiya, gaskya bazan iya yafe masa ba, inda ace ma nabiye wa zafin zuciyata da har lahira saina kaishi wallah, yayi kadan ya kasa..amma kinga ai bankasheshi ba, dukiyarsa da lafyarsa na rabashi dashi kuma banajin dandanasani yin haka, dan ko yanzu akace na sake masa haka wallah wallah zan iya sakewa, kaf majiya ba'a isa a walakanta ni snn a walankanta rayuwar yayana ba. ..
tana maganan ne tana kuka sosai rungume da ayaanah
ganin irin birkicewa da fushi da taawure tay yasa hajy mairo kasa cewa komi kawai ta karkada kai tana hawayen itama can dai tafara bata hakuri tana lallashinta kana ganin taawuew kasan ba acikin hayyacinta take ba dan sosai mutuwar inayah ya ruguza mata duk wani kofar tunani ya kuma saka mata baqin ciki me tsanani.
tun hajya na lallashinta har ta hakura ta kyalesu da ayaanahn dan suyi jimamin rasa inaya da sukayi atare..
jikinta a sanyaye ta basu waje tana rufe musu kofa ahnkli ta tsaya agefe tanamai share hawayenta, can kafin tafito har waje ta isa gaban motar taje ta samu ibaad ya jingine kansa da stiring motarsa idanunsa a lumshe yay shiru kamar wanda yay nitso acikin tunani
kwankwasa mai kofar motar tay ya daga kai suna hade ido ya bude motar ya sauko kasa, wani iri hajy tay da fuska kmar wacce zata masa kuka, tuni ya bi ya hade ransa, tun kafin ta fara kukan cikin katseta yakawo mata offer cewa kafin ya amince yawuce mata da ayanah can gida sai inhar zata amince tazubar da makaman neman gaskiyarta ta tattara inata inata tabar garin tudu, if not shi bazai kai ayanah ko ina ba, snn zaije kano yagaya ma su bappa zaidu da uncle moh cewa tazonan ta sato yar mutane tariketa bada cikakken izinin iyayen yarinya ba. sabuwar musu suka dingayi, kusan ince ma wayo ya mata sosai, ya nuna mata kawai bata da mafita, ai tunda aurensun ma is invalid uban kowa ma yasan labarin shi baidamu ba, inkuwa har bata amince zata bar tudu ta koma kano ba saidai abari har juman yazo tudu ya dauki yarsa kawai inyaso yaje can ya kasheta.
still suna cikin wnn musun sai ga nan taawure ta fito da sauri saurinta tana share hawayenta da suka ki tsayawa, anan ta samesu agaban motar ibaad, tana isowa ibaad ya rusuna har can kasa cikin nuna tausayi da ladabi ya gaisheta, ya mata proper gaisuwa, snn yamata ta'aziyar mutuwar yarta inayah yadan babbata hakuri shima haka tadinga bashi hakuri akan abunda ya faru dashi akan taimakon ayaanah dayi..
cikin kwantar mai da hankali tace masa babu komi itama tafahimce shi, tasan kuma gidan su babban gidane, bazata so wani abu na rashin mutunci yazo ya faru tsakaninsu da juma ba, inde bazai wuce birni da ayanan ba babu damuwa zata san yadda zatayi a rike mata ita har sai ta dawo.
hajy mairo da ba akasa da ita ba, nan ta tuma ta cafe zancen tace sam sam bata aminta da wann hukucin ba, inde har zata kwashe inata inata tabar tudu r yadda yakeso, saidan inshi ibaad din zai amince ya zama guardian in ayanaah, snn ya wuce da ita cikin kano ayau ta zauna agaban fatima kafin itama tagama parking din tadawo ta samesu acan.
ibaad yay shiru yaki cewa komi ba, duk rakin da hajy mairo tayi, taawure tace musu ita zata wuce wani kauye acan jigawa dan batason matasan garin majiya susan me tay bare azo a dauketa anan tudu aje kasheta a majiya. dan haka zataje can yankin jigawan dama tana da yan uwan mahaifyarta awajen, su irin fulanin tashin nn ne suna yawan zuwa kiwo zata nemesu tazauna awajensu kafin komi ya lafa...
haka sukasha kukan rabuwarsu agabansa da hajya mairo har gwanin ban tausayi...duk kudin ajiya dana jinya dake wajenta hajy mairo tace mata ta rikesu kawai halak malak taje tanemi tsira.
jikin taawure amatukar raunane ta juya, da shirin komawa cikin asibitin dan tay sallama da aayanah, ibaad yana gama shanye hawayensa daya kusa zubo masa ya bi bayanta anatse ya tsareta, saida suka koma can gefe inda babu idon mutane akansu ya tabbata she feel safe with him, snn ya mata bayanin duka duka manufarsa akan hajiya da kuma ayaanah, sosai ya zage ya nuna mata cewa ya fahinceta ya gane halin datake ciki kuma karta damu, yay mata alkwari zai tsaya mata akan yarta har tasamu tay karatun, he will be her quide, snn ya ciro wallet dinsa duk ya rasa inda zaisamu paper, sai ya rubuta mata number wayarsa kawai ajikin sabon dubu daya, snn ya kara fitowa da sabbi sabbin 1k notes din masu yawa baima kirgasu ba ya damka mata su duka ahannunta batare da ya sake hannuntan ba yace mata "Dan Allah kartace masa a'a, tay amfani da kudin duka tay kudin mota dashi, taje duk inda zataje tanemi tsira daga juma snn duk abunda takeso kawai ta kirasa he promised her dat yarta will be in safe hands with him in sha Allahu..
yana maganan nan kawai kuka taawure take masa kamar zata cire ranta, dan bata taɓa samun wani wanda ya iya karantar duka turirin damuwa da baqin cikin dake yawo aranta ba kamar shi..yaro ne, amma gashinan da hankali da tausayi da halin manya atattare dashi.
cikin nuna mata tausayi da girmamawa ya tausasata da kalamai masu sanyi ya kuma lallabeta har saida ta amshi
kudin, fadin irin albarka da godiyan data masa ranar bazai kiyascu ba, ganin lokaci na tafiya yasa tay marmaza ta karasa ciki dan tay sallama da ayaanah
babu wani bata lokaci
tadagota suka rungume juna ta masa nasiha masu ratsa jiki tare da jadadda mata cewa mutuwar inayah ba shine karshen rayuwarsu ba, su hada hannu sucika manyan burikan su, tay mata hakan, dan tasan inayah zatafi jindadi in rayuwarsu tay kyau ba muni ba,
..,snn umarni tabata akan da tay ma ibaad biyayya, ta kallesa a a matsayin dan uwanta kuma yayanta karta saɓa masa..tare damata alkwarin wata rana inkomai ya lafa zatazo har kanon ta nemesu...
gabaki daya ayaanah ta raunana sai tanajii kamr magangnun sun mata tsauri da mugun nauyi dan bama ganewa take ba dan bakaramin kukan rabuwa da mamantan taci ba, haka kuwa tana kallo taawure tabar asibitin taje waje tasamu ko magana ibaad basuyi da hajy mairo ba.
sai fushi take dashi wai yaki karban ayaanah, taawuren tana zuwa ibaad ya mata sallama sukayi bankwana sai yawuce ciki yabarta da hajiya.
anan ne ta sanar da hajiya duk yadda sukayi dashi tabi ta nuna mata kudin daya bata, duk mamaki saiya rufe hjya, suna hawaye ta rakota har waje ta tsare mata abun hawa har saida taga tay nisa snn ta dawo.
dawowarta kenan tazo ta samu har ibaad ya gama biyan kudin jinya da duk wani abu da ake binsu ita sai tawuce ta dauko ayanahn suka fito, tun da suka kama hanya, basuyi wani magana ba har saida suka isa gidanta nan ma sharesu yayi ya hada ruwan zafi a heater yayi wanka yazo ya samu hajya ta sa anhado masa break fast mai nauyi yazauna yana ci itakuma ayaana aka kaita wajen wanka
hawaye duk yaki tsayawa a idonta dan duk inda ta zaga a gidan saitaga kamar zataga addanta da mamanta, she was seriously ill, nd grieving. gabaki daya memories dinsu yanata dawowa mata kai...
dakyar ta shirya adayan dakin hajy mairo ta sakata dan dole taci abinci snn aka kawo mata riga da zani brown colour na coté d' ivoiré kayan yama mata oversized ma amma haka ta saka tana gama cin abincin bacci me nauyi ya dauketa awajen..
tsakanin ibaad da hajiya mairo dakyar suka sauko sukafara magana musmmn data fara tsokanoshi da batun alherin da yay ma taawure, ya hade ransa tamau, yace mata aidqma can ta daukesa mugu ne shiyasa bata yadda dashi ba, dan haka karta damesa kawai tunda zai wuce kano da yarinya ta gaya masa exct ranar da zata gama tattarawa ta dawo gida itama.
badon son ranta ba hakanan suka warware maganan, aka sa ranar, 14days lissafin ranar da zata gama parking da kudin sallamar wasu wokers intan, da wanda zata basu incharge dan su cigaba da mata sana'ar abincin anan tudu dan akwai katon gidan almajirai datake ciyar dasu atunaninta inhar tabar tudu gabaki daya wazaina ciyar da yaran nan. duk suka gama lisasafi, taso ya bata tsawon wata guda amma ibaad yace sam sati biyun kawai ya isheta tunda tana case da yan ta'adda. shi zai gaya ma bappa zaidu da uncle moh ranar tahowarta inyaso za'a kawo mota kawai azo a dauketa da tarkacenta gabaki daya.
ganin babu yadda ta iya dashi yasata kyaleshi, ibaad ne kawai yake iya mata haka tayi shiru saboda sosai take kaunar sa aranta duk dama koyaushe acikin fada zaka same su, jim kadan bayan sun yi hirar karatun sa yace mata shi zaiwuce kano yanxu sabida zai kai ayanahn asibiti adubata acan
wajajen karfe 10:30am saura nasafiya aayanah ta farka duk baccin bai wani isheta ba, haka haj. mairo ta sakata agaba tay mata nasiha mai shiga jiki, duk kusan irin abunda taawure ta gaya mata ne dazu akan tay ma ibaad din biyayya sann ta sani cewa mutuwar inaya ba shine karshen rayuwarta ba, nn ta hadata da ibaad din ta musu atare akan suy hakuri su zauna lafiya tunda qaddara ne ya hadasu. shide baice komiba harta gama surutun ta within few minutes ya fita yabarsu, yagoge motarsa tsaf, yana shigowa yadau jakarsa yace mata kawai su tashi shizai tafi yana da practicals karfe 2 na rana..
daga ayanahn har hjy mairo kuka sukeyi rungume da juna tazo tasakata a mota harda sakamata seatbelt yana sallamar kakansa ko kallo daya bai kara ma ayanah yasa kai ya kunna motar suka kama hanyar kano.
tafiyar kurame sukayi banda kukan da ayanah takeyi babu abunda kakeji, baison yace mata tay mai shiru ba dan yariga yasan abunda takeji is alot to carry, ga zafin mutuwa gana abunda yake faruwa da su, iyaka da abun ya ishehi ya kunna karatun qur'ani ya dan kure musu volume tun tana cigaba da kukan har zuciyanta yay sanyi tafarabin sautin karatun da zuciyarta tana tuna addanta inayah, her fav thing in this world was qur'an ..sai kuka mai zafi take tana tuna irin murnan da sukayi ranar da inayahn tay sauka har bacci me nauyi ya kara daukarta.
ABUNDA KE ƁOYE
SURAYYAHMS
08060712446
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[07/11, 20:04] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: ⏯️1️⃣7️⃣Abunda ke ɓoye
bayan tafiyarsu hjy mairo na shiga gidanta ko aje mayafinta batay ba matasan majiya suka diro kofar gidantan yuuuu wai sunzo neman taawure haka hajiya mairo tabirkice da ihu tahau sauke musu bambalastar ruwan bala'i ta tara musu taron jama'a tabi tajuya maganan kaf akansu tace sune suka sace mata yar rikonta taawure dan haka kawai ace musu su fito mata da yarta ko kuma hukuma ne zata rabasu, haka akayi ta hatsaniya tsakanin matasan majiya da hajiya mairo, can dai da sukaga ta fisu bori tanace musu akan su susuka sace taawure tabita laka musu harda sharrin da ko shaidan bai isa ta ciresu aciki ba ahaka ahaka abanza aka bar maganan suka koma garin majiya batare da sun cimma komi ba, ga dumbin zargin su na tunanin taawuren tazo nan duk ya gushe, basusan kuma ina zataje bayan nan din ba, yau dayakamata ace ranar farinciki da samun daukaka ne awajen juma sai ya zamo masa tamkar wata baqar rana dan bakaramin muguwar asarar dukiya taawure ta masa ba,
shikansa dakyar ya tsira da ransa, sanadiyar wasu fatake masu fitowar jeji da sassafe da sukaga wuta na tashi a rumbun abincinsa suka kawomai dauki yau kaf garin majiya sai da aka tashi da labarin abunda ya faru da juma masu tausayinsa suna yi mahassadansa masu masa dariya suna kai, yau tsabar baqin cikin ganin konewar dukiyarsan kurmus koda aka kwanceshi ya fito sarari suma kawai ya dingayi ana yayyafa masa ruwa...
yarasa meke masa dadi, gashi yafi kowa sanin cewa da akwai kakkarfan aikin tsarin jiki na usalin fulanin daji ajikin taawure da yayanta, yasan koda zai dau fansa ta hanyar musu sihiri ko sammon da zaisaka rayuwarsu ya lalace bazai iya ba saidaima abun yadawo kansa..
iya ka dabbobinsa ne kawai tabar masa su araye ahakanma waidan bataso ne tay ma abu me rai azaba da wuta yasa bata konasu da ransu ba.
ranar gabaki daya duniyar juya masa ta dingayi yanata suma ana dagashi yana komawa musmn ma da aka dawo gida akacemai ba aga inda taawuren ta nufa ba duk anje har tudu suma can tudun nemanta akeyi har ansaka hukuma ajeji suna nemanta. yau ya kasance ma juma ranar tsananon bakin ciki da jimami wanda bazai taɓa iya mancewa arayuwarsa ba.
bayan komi ya lafa wajajen karfe daya da rabi saura ibaad ya shigo garin kano kai tsaye baije gidansu ba yawuce Al-eeman private hospital inda babban kawar mamansa take aiki a matsayin babban nurse snn ya damka mata ayanahn a hannu shikuma ya wuce private club dinsu domin halartar practical da sukeyi agefe nasu na yayan masu shi, few minute drive just few minutes away from his main school of medicine na buk, ya gaji sosai ga uban stress din hanya a jikinsa amma baidamu ba hakanan ya shiga aji ya fada aiki. yau ana kkrin koya musu sabuwar darasi ne game da introductory practical anatomy amma gabaki daya sqi yanaji kamar yarasa nitsuwrsa dan harga Allah baisan ma tayadda zaiyi ya cika dumbin alkwarun daya dauka ma tawure nacewa zai kula mata da rayuwar yarta ba...aiki sukayi sosai don komi practical ake nuna musu, har zuwa 3:30pm snn yaje yay sallahn asr aka koma lab still saiga wani visiting doctor yazo musu daga kasar india shima, shi yafara fayyace musu basics introdction naduka duka courses din da zasuyi a main cadre nasu da medicine gabaki daya, kai daga ganin yadda yake koya musun ma zaka san babu me iya karawa dasu a ajinsu yanzu, bcos they are far far advance, sun kamo hanyar wuce mates dinsu na aji sosai, kusan dukkan wasu abubuwan da ba a musu tukuna a ainin lectures dinsu ba shi ake ta kkrin koya musu anan just like private lesson. can da magrib aka sakesu sukabar wajen kusan kowa yagama gajiya. hanklinsa dam kwance dake yariga yagaya ma amminsa dasu bappa zaidu awaya cewa ya dawo kanon already amma bazai wuce gida ynxu ba.
yana shiga motarsa asibitin inda yabar ayanahn ya wuce ya samu waje ya zauna yay shoru yanamai cigaba da zaman jiran jin me likitocin zasuce, anan yay sallan isha, ya fita yaje yaci abinci, kawar maman nasa har ta gama duty ta wuce gida, bashi da samun kan doc ba sai wajajen goma na dare, mace ce, nd she is a well know cardio doctor ana ce mata Haj sakeena shehu dakyar ake samun hanklinta sabida yawa da mutane suke mata. at arnd that time of 10pm na dare tay ushering ibaad cikin office inta ,yana zama suka gaisa a natse snn tafara mai cikakken bayani akan ciwon ayaanah
tacemai bincikensu ya nuna cewa yarinyar originally was born with a strange congenital heart weakness wanda baya nunawa kwata kwata sai inta shiga mummunan hali na tsorata, bacin rai me tsanani ,kakkarfan rauni, jimami me yawa, ko wani nau ikan intense fear ko emotional overwhemlness. daga zarar hakan ya sameta zuciyarta zai fara kokari wajen ganin yay coping da pain in amma akokarin hakanne yake kawo mata symptoms kala kala na raunin zuciya, kmr zafi da ciwon kirji,wahalar fitar numfashi da su panic attacks da zufa me dan banzan yawa har izuwa loss of counsiounes. hoto nan scan da suka dauka ta nunna masa snm takara da cewa Abu mafi muhimmanci ynxu shine a tabbatar mata da samun natsuwa. Kada a tada mata hankalinta. Kada a matsa mata tayi magana ko tana tuna wasu abubuwan da suka wuce mata abaya. snn Idan ta fara jinsu ko suka dawo mata kawai a zauna kusa da ita cikin shiru da bata kulawa cikin tausayawa,yarinyar yar karamace, so zata fi bukatar kulawa da kwantar da hankali fiye da duk wani maganin da zaa bayat yanxu..."jin yau shiru yasa ta kara kallomsa ahnkli tace 'are u her elder brother?babu yabo babu fallasa ya gyada kai, Dr tace okay, toh ga wannan. wano paper ta miƙamai ya karba tace" zaku iya komawa gida, there are the list of her drugs, snn zakuje nan pharmacynmu ku saya alluran sedatives amata su ynxu. idan jikinta bai sarara ba after 3 days adawo mana da ita. gyada kansa still yay cikin nitsuwa yace mata ya gode snn ya rike takardan ya fita dashi a hannu..
baije ya duba ayaanahn ba kai tsaye yajeshi pharmacy ya basu papern snn biya kudi akazo har dakin da ayaanah take kwance aka mata allurai har guda biyu...
hawaye ta dingayi sabida ta tsani allura har cikin kokon zuciyarta, but the more tana kallon fuskar ibaad a bakin kofa sai tanaji kamar ma tafi jin tsoronsa fiye da komi ynxu. jiri me dan banzan yawa takeji amma yadda ta tsaya kyam cikin shanye zafin alluran kamr wata soja yasaka nurse din data mata allurar tace masa
"yallabai zaku iya tafiya..
ibaad ya gyara zaman jakar laptop dinsa kallo daya yay ma aayanahn tay maza ta gyara zaman zaninta da dan kwalinta cikin saibin jiki ta saka takalmi, har saida yawuce gaba snn tafara takawa ahnkli tana bin bayansa yanayin fuskarsa da tazarar dake tsakanin su zai iya sakawa kai tsaye kace basusan junansu ba...
tafiya take kirjinta na tsananin bugawa, with each step sai taji kamar akan rolling coster ball take yawo, kanta nawani irin juyawa kmr tana sararin sama cikin gajimare, kafin kace wani abu tafara ganin mutane bibbiyu, hatta dakin ya dawo yana mata duhu duhu hanklinta gabaki daya na neman gushewa
suna isowa daf da bakin kofar asibitin batare da ta shirya ba jikinta ya sake tayanki jiki ta fadi
wani securityne yay sauri yazo kanta da tunanin "she is all alone dacan har zai dagata sai kuma ibaad ya juyo, suna hade ido yace ma securityn its okay sir, i am with her. security ya masa wani irin kallo, "yace amma shine ka kabarta haka but you are suppose to hold her
ko za'a ko koma ciki a kira muku nurse ne..ibaad yace masa "a'a Allura aka mata bai saketa ba but she will be fine
...suna cikin maganan ayaana ta fara bude idonta cikin layiii tafara fulatanci tana cewa zata kwanta, ita tagaji zata kwanta, bazata iya takawa ba.."
yarensa ne shima yanaji sarai amma yay kamar be gane me take fada ba, wani cak taji ya dagata tay firgit kmr ta tsorata suna hade ido sai kuma ta lafe akan kirjinsa tare da tantame masa riga, qamshin turarensa atake ya bugar da ita saii luuuu ta koma bacci daga nan bata sake sanin me yafaru da ita ba.
yana fitowa waje ya ajeta seat din gaban motar ya saka mata seat belt ganin tana zufa ya kunna musu A C a low snn yafara driving dinsu calmy yana tukin very calm bazaka taba iya fayyace abunda yake rayawa aransa ba.
frm time to time yakan juyo ya kalle fuskar ayanahn cos u cant ignore the fact that she is girl with a rare beauty, kyau me dauke ido da sanyi irin wanda bai taba gani ba..ita abar tausayi ne, she is calm, and peacefull. any man in his good will senses may want to love nd spoil her bcos of her calm aura nd fragility, saidai shi aransa ba wann kadai yakeji ba, da akwai wani awkward feeling da yakeji akansa kmr wasu dabiaun ta yana mugun bashi haushi, he just can't seem to forget dat agabanta aka taru ana masa sharrin zina duk dama ya tambayeta gaskiyar abainar jama'a amma tay shiru takasa budan baki ta wankesa. yasan he is not even supose to be angry bcos of that amma wnn shegen rauni, da mugun tsoron dayake kallo acikin ayanayinta abune wanda bazai taba iya tolerating ba, inhar dagaske ne zaicika alkawarin daya daukarma taawure kusan dolene mishi ya kasance atskaninsu akwai kakkarfan ginin tarbiya, gyaran hali, da kuma ladabtarwa.
wajajen karfe sha daya saura na dare suka iso GRA cikin gidan bappa zaidu, tsabar gajiya har ji yake kamar bazai isa dakinsa ya kwanta ba, yana kammala parking kuwa ya juyo ya kalleta yaga har yanzu tana kan baccin ta peacefully.
kallon scnds biyu yay mata kafin ya dauki jakarsa da kominsa ya rataya snn ya zago ta inda take ya buɗe motar ahlkli yadda ya jawota jikinsa da karfi ya ratayata akafadansa nan da nan kuntacen dan kwalinta ya sulale kasa abunsa. haka wnn doguwar curly nd wavy hair dinta dat is so soft and shiny ya barbazu masa a fuska da kafada, ahnkli ya dinga takawa da ita har suka kai bed room dinsa snn yay saurin ajiyeta akan gadonsa tare da sauke ajiyan zuciya mai nauyi
yana tsaye amma idonsa gabaki daya nakanta dan bai taɓa ganin natural buzu hair irin nata ba duk dama dukan kannen sa suna da kyau da dogon suma.
na ayanah nada wani irin cika ga yawa ga uban yauqi da tsayi , tagaban is so wavy nd damp, kasan lenght din kuma is curly nd very dark. yadda ya ajeta a ringine haka suman ya zubo yarrr ya rufe mata fuskarta kirif
it was hard for him to stop staring sai da yay minti uku atsaye cikin tunanin me zaiyi kafin ya dauke idonsa ya saukar da jakansa daga kafadarsa ya zauna akan chair ya ciro duka kayan ciki da suke da datti, snn yacire takalminsa da komi na jakan yay empting ya aje komi awajen zamnsa neatly
dan coridor dake tsakanin bathrom ya shiga da kayan ya jefasu cikin engine wanki, ya wanke 2 blood stained shirt din har da kayan dake jikinsan duka machiine din ya matse su, yay masa drying sama sama snn yay pressing dinsu so neatly kafin ya kaisu hanger ya rataye su.
blue shower trobe mai kauri ya nannade ajikinsa bayan ya kimtsa dakin kadan ya shiga wanka, he spends like 20 minutes just washing his hair and face kadai with this luxurious swiss brand na la praire, brand inda is excellent for lifting, firming nd anti aging saikaga kullum fatarka rass da karfinsa baiya yamushewa kamar dai bazaka tsufa ba.
BHA made face scrub da enzyme exfoliant dinsu yay using kafin nan ya shiga shower, wato idan kaga tulin kayan gyaran jikinsa ryt frm hydrants, retinols, SpF, sheet mask, da cleansers, shaves set ,dss. zakasan kowata ƴa macen ma bata isa tanuna ma gayen nan son gyaran jikinsa ba. he is a very neat guy dat priotise his looks nd skin health.
bayan kamar minti talatin ya fito a warm shower sulbabben fatar jikinshi yana qamshin sabulai da shampoos din la praire din cos all his men luxury items are of the same brand baya hada tarukuce, brush yay agaban sink yay rinsing bakinsa da ruwan kanunfari snn yay kamilallen alwala ya fito da wani sabon bathrobe din ajikinsa.
kallo daya yay ma kan gadonsan yaga kmr yadda ya aje ayaanahn haka ya dawo yasameta batako motsa ba banda sautin numfashinta dake fita ahankli ahankl. cikin kyabe baki ya dauke kansa walking gently kamr wanda baison ya tasheta yaje gaban mirrorn ya tsaya, after dabbing his skin with a clean white towel yafara jawo set na skin care items insa musmn na amfanin dare, kusan yadda komi na wanka, wanke kai da gyaran jikinsa ya kasance brand daya hakama komi na shafawa a jikinsa ya zama brand daya, he use only "la mer" for his body, hair nd face. a very luxurious american brand na mutanen da suke son zallan jikinsu yana glowing bana haske ko bleaching ba. with good skin barrier repair, rich hydration and luxury feel. anan ganinka ansan jiki duk madara duk A.C..
abu uku kawai ya shafa dake yasan dare ne is merely time for his serum, vitamin nd retinol kafin nan ya mulke jikinsa da soft soothing moisturizers, ya shafa turare ya gyara kansa tsaf ya jawo doguwar wando dark blue colour marar nauyi na CK da rigarsa me kamr t shirt yasa. yay lisafin duniyan nan a brain insa amma yarasa ta ina zai aje ayaana ta kwanta, gashi baison takuri shiyasa bai iya kwana akan kujera ba.
tsaftaccen cotton comfortersa ya jawo ya shimfida akan soft couch dinsa ya dawo zai dauketa wani cakk ta firgita acikin baccin ta kara cakuikuye masa riga kmr wacce za'a saceta, gently yariko hannun nata anashi, sann ajeta akan couch din tukun ya samu ya kwace rigarsa ahannunta ya dauko katon rigar sanyinsa da yake sawa in sunje holiday a united state me dauke da fur ya lallubeta da shi kirif.
kara gudun Ac yay jin kmr duka gabobin jikinsa na masa ciwo yasha kwayar magnessium glycinate for deep relaxation nd quality sleep, after like 5 minutes ya iddar da adduar bacci saiya kashe wutansa gabaki daya ya kwanta hankli akwance baijima ba wani bacci me nauyi ya daukesa...
wajajen 2pm nayi cikin nisan bacci ayaanah tay firo da rigar sanyin daya rufeta dashi da alama allurar sedatives da aka mata ya fara raguwa, wani dan uban zafi da zufa tasoma ji ajikinta. tunda tay firo da bargon ta cigaba da sheƙa bacci me nisa ba ita da farkawa ba sai can ana daf za'a kira sallan farko da sanyin asuba ya hadu dana ac ya bugota, kallon dakin ta dingayi acikin duhu tana jin kanta wani iri kamar ba ta cikin duniyar, tsoro me matsanancin yawa sai ya riƙe mata kirji dan bata san yaushe sukazo nan ba, itade tasan sunbar asibiti gabaki daya sai taji ta rude sosai, fitsarin daya tasheta a baccin takejinsa kamar zai fasa mata mararta ya tsulalo waje duk sai ta rasa me zatayi.
lkcin is just few mins ya rage ma ibaad ya farka daga bacci amma dake yariga yasha wnn magani yasaka yau ko motsi bataga yanayi ba.
dake yaran taawure akwai jarumta inuwar sa kawai tagani acikin duhun tagane cewa shine yake kwance akan gadon, da kyar da karfin hali irin na mutumin kauye ta tashi ta dada lekensa kafin nan hanklinta yay sanyi ta miƙe tsaye jikin ta na rawa rawa dan kwata kwata batasan ina zata dosa acikin duhun ba ga fitsari ya mugun cika mata mara sosai
lalume ta dingay har saida ta isa gaban inuwarsan ta durkusa, hannunta dake rawa rawa ta miƙa kansa amma ta kasa taɓashi, tay hakan yakai sau biyar mugun tsoron sa datakeji ya hanata iya taba masa jiki.
nishi take fitarwa ahnkli tana dan mammatse kafafunta
jin fitsarin yafara jika mata pants,cikin dauriya ta dan taɓa jikin gadon da karamin muryan ta mai tsananin sanyi tace" umm umm dan Allah me mee..mme...mai..mota zan
..zanyi fitsari..ina jin fitsari sosai...maganan nata sai ya fara fitowa tare da maqudan hawaye masu zafi itakanta batasan mesa take yawan jin matsanancin kuka intaga ibaad ba.
a mugun shagwabe cikin fashewa da kukan tace ..mai mota..nifa zanyi ajikina dan Allah ka tashi ka nuna min wajen fitsari ...mai motaaaaa....
can cikin duniyar baccinsa yaji kmr ana jajjan masa bedsheet
yay tsam sai yafara ji harda sautin sheshhekar kuka da sauri ya bude idonsa ganin ayaanah agabansa ta durkusa tanata mammatse kafa tabi tazuba masa ido tana rabza uban kuka sosai..
gam ta rike bedsheet dinsa tana jajjansa tana cewa wayyo Allah na zanyi ajikina faaa
a firgit ya kunna bedside lamp haske yadan karede dakin fusknsa mugun daure yace "ke kuma meye haka..meye zakiy ajikin ki..uban wa ya bugeki kike kuka da tsakar daren nan..are u a child?
maƙe kafadunta tay a shagwabe tana hawaye tace
"nifa fitsari nakeji..
cikin galla mata harara yace "bakisan hanyar bayi bane...sai kuma ya tuna batasanin ba cikin dafe kansa yace shittt.. "tashi..
dakyar ta miƙe tsayen tana rawa rawa tana mammatse kafarta..
kai tsaye ya kunna asalin switch na wutan dakin wajen yay haske sosai kamr rana ya kalleta snn ya kalle kofar bathrum dinsa yace kizo kishiga kiyi fitsarin anan
da wani iri sauri ta gyada mai kai zata daga kafarta kenan sai zurrrrr fitsarin ya sace ya fara zuba mata ajiki..
ahnkli ta runtse ido tay tsamm jin fitsarin na bibiyar kafarta taki sam ta kara bude ido ga kalle ibaad daya zaro manyan idonsa waje yanamai shirin daka mata wani irin hatsalallen tsawa.
#SURAYYAHMS/08060712446
ENJOY THE WEEKDNS
SAI MONDAY...IN SHA ALLAH!!
[10/11, 18:48] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: 1️⃣8️⃣⏯️AKB💫
zararren idonshin take kallo jin matsanancin tsoro ya tiƙeta tunma kafin yay magana tabi tarushe masa da wata iriyar uncontrllable kuka mai kara, ƙwafa yay bai fasa bakuwa, a mugun tsawacen yace"..what d hell did u think ure doing? fitsari fa kikeyi ajikinki kuma atsakar dakina dan baki da hankali ke wata irin kazama ce ?
runtse idonta tay tam cikin datsar numfashinsa da muryan tsoraccen kukan tace "toh kayi hakuri mana mai motaaa fitsarin ne ya dan matseni ai bansan zai zubo ynxu ba.."
wani dan uban harara ya watsa mata yace fitsari ya matse ki ko tsabar iskanci, da girmanki ne zakimin fitsari kuma tsaye toh badani zakiyi wann kazantar ba, karaso nan ko nazo na wajen na wanka miki mari..
dake bada tsawa ya fadi hakan ba, kukan ta tsagaita jikinta na rawa rawa tafara tahowa tana takawa ahankli ahankli tkmr bazata taho ba kukan nata na fita ahankli...
wani irin fixgota yay ta firgita zata fadi ya rikota jin tana jan wani irin numfashi me karfi, kasar wuyarsa yace.."ke da Allah kimin shiru kinbi kincika min kunne da kukan banza dama uban waya aike ki kiyi fitsarin toh..mtss.
shiru tay tana hawaye ganin ya mugun hade ransa sai batace mai komi ba har saida ya dora hannunsa akan kyakkwar fuskarta ya tattaba wuyarta zuwa goshinta just to make sure she is fine, snn yakuma tabbata cewa ba zazzabin bane yasakata fitsarin dan ya mugun tsanar kazanta..
yana kan observing dinta yana mita akan fitsarin sai hawaye take zubarwa kmr ruwa batare da ta kallesa ba ahankli cikin runtse ido tace kayi hakuri aifa ya matseni ne. shiru yay kmr badashi take ba har ya gama snn yakamo hannunta tareda tura keyanta cikin bathrum dinsan ya rufe kofar ahnkli daga wajen yace "ki karasa fitsarin awajen ina zuwa" tun bata amsa shi ba da sauri ya wuce corridor ya dauko clean self absorbed mopper da ruwa me tsafta ya zuba awajen ya goge tasss kafin ya koma ya dauko dettol yasaka awajen yakara gogewa snn ya fitar da mopper waje..
..dakin maheer ya wuce yasamu ko farkawa a bacci baiy ba, kai tsaye ya wuce bathrum dinsa yay sarki yay kamilallen alwala snn yazo ya tashesa, maheer yana bude ido ya dinga shan mamakn ganin sa yana tambayarsa yaushe ya dawo ganin ba kulashi zaiyi ba kawai shima ya miƙe dakyar yay alwalan suka nufi masallaci atare.
sosai masallacin ya cika sabida yau monday kusan kowa ya farka da wuri dan shirin zuwa aiki, ibaad ya ja su sallah within few mins duk maza aka watse shida maheer ne kadai suka tsaya sukayi karatun qur'ani atare can around 6:20am suka kamo hanyar gida suna tafiya ibaad ya sanar dashi kalar rikicin da yake faruwa da hajiy mairo acan tudu batare da ya gaya masa komi akan rayuwar taawure bare zuwan sa gidan da ayaanah ba....
suna shigowa cikin gidan kai tsaye suka wuce part din bappa zaidu,Zaune yake a babban falon sashensa dayagaji da haduwa jikinsa sanye da wata original dubai jallabiya black colour mai ratsin fararen duwatsu...
wani irin qamshin hadin lime basil nd lemon grass tea with pinch of cinnamon mai dadi ke tashi a falon,hannun sa dake rike da white tea cup maikyau yakara mikawa gefe ya hau tuntuda wnn hadadden herbal tea dinsa dan yana matukar son shan wann herbal tea da safe musamman dayagane amfaninsu wajen digestion nd detox, kara lapyar garkuwar jiki da rage kumburi nd the best part yadda tea din yake mugun calming anxiety da boosting na clear mind. kusan rabi ya zuba tea din a cup sannan yakai bakinsa idanunsa a lumshe ya dan shaqa qamshin ta ramin hancinsa sann ya bude idon tare da furta bismilla ,a nitse yakai kan labbansa sann yadan kurba harya masa kyakywaan kurbi biyu, bayan nan ya mayar da cup din ya ajeshi agefe acikin tray dinsa tare da wasu hadaddun royal tea set da babban flask na zallan ruwan zafi
Tsohon jarida yagani agaban sa zai dauka Sautin takunsu daya jiyo tun daga bakin kofar ya dakatar dashi, kansa ya dago yanamai gyara zamansa mai cike da kamiya ido ya kafawa kofar yana jiran ganin mai shigowa aranshi ya bari kawai ibaad ne dan tunda yadawo jiyan basu wani samu kyakkwan zama dashi ba, sometime he wonders if he will eva had a break time in his life dan tunda yafara karatunsa na medicine ya zama he is always busy and ocupied da wasu abubuwan.
Haka kawai kuma sai yaji hanklinsa na yawan tashi kwananan, musmmn akan lamarin strange obsession din zainab arifah akansa, barin ma inyatuno da abubuwan da prof zayyanu yake yawan cewa da yadda yake bude musu ido da tada jijiyar wuya wajen nuna musu shima yana da cikakken iko dashi, shide yasan koma menene bukatarsu akan ibaad da yarsu zainab arifa bazai wuce na kaskanci da son zuciya ba kuma abun dai bazai taɓa ma ibaad sauki aynxu ba musmn ma da aka hado sa da sabuwar responsibityn ayaanah.
Duba da yanayin ibaad din wani bin har sai an mance dashi agidan sabida baida fitina sam sam yamafi saka karatunsa agabansa fiye da komi, No one in his right senses zaice yaron yanada lokacin kulawa da kansa bare wasu..
shida maheer da mujaheed kusan sune musu manyan ƴaya maza agidan, in tun ayanzu ba su samuwa cikakken nitsuwa sun zamo wani jigo da jagora wa yan uwansu da familynsun ba gani yake kmr nan gaba insuka barsu a duniyar da wuyane rayuwa tay musu sauki da armashi. har ransa Yana mugun alfahari da jajircewa da kuma gwazon ibaad, amma harga Allah cikin zuciyarshi zaiso ace rayuwarsa ba hakan take ba, he thinks there is more to life than taking too much responsbilty musmn daya zamo shine kawai silar farinciki da gatar mahaifyarsa ynxu.
Kwafa yay jikin tunanin maganan da yay da hajy mairo jiya akan zuwan ayaanah yadda ta jadadda masa cewa dolene saida saka hannun ibaad arayuwar yarinyar nan sabida uwarta taawure tafi nuna amincewarta da shi, cikin ransa yace Shknan rayuwar yaron nan babu hutu? dada leka bakin kofarsan ya dadayi yana Allah Allah ace shidin ne yake shigowa saboda akwai tarin maganganun da zaiso yaji amsar su daga bakinsa direct..
"Assalamu Alaikum"
kusan atare suka furta hakan shida maheer cikin nitsuwa suka bude slide door da akayi da glass suka karaso..
bappa zaidu yay gyaran murya snn yace wa'alaikum sallam warahmatullahi wabarkatuh.
Kai tsaye dukansu suka bayyana acikin main falon takalmansu suka cireta tundaga bakin kofa fuskn ibaad yay makutar kyau da haske duk dama a hargitse ya tashi yau wani dan uban gamshin oud ne yake binshi kamar ba sallan fajr suka fito ba.
straight suka nufo inda bappa zaidun yake, ibaad yana tafiya kansa na kallon kasa, maheer ya zauna bisa lallausar turkish carpet ata gefen dama, shikuma ibaad a kasa kusa da kafafun bappan yanemawa kansa wajen zama cikin yanayin nade kafafunshi dayake bayyana tsananin ladabinshi da boyayyiyar sanyin halinsa..
bappa zaidu ya kasa daga ruwan idanunsa akansa dan Allah ne kadai yasan yadda yakeji aransa game da ibaad
haka kawai yakan ji tausayi da kuma farinciki inya tuna cewa shine ya riƙesa har yakai wann lokci, ata wanni fannin kuma yakanji kamar yatakurashi ne daya dauke shi gabaki daya agaban mahaifyarsa ya zauna agidan san, ko hala yarage mai freedom din sa nayin rayuwa irinta yam hutu kmr age mates dinsa duba da bashine asali ya haifesa ba amma he wants nothing but the best for him cos deeply in his heart yanajin kamr he is more than just a uncle to him, arayuwar sa yakanji kamr yafiye ma ibaad din kallon dan cikinsa daya haifa fiyeda alakar kanin uba dayake tsakaninsu kamr yadda ya lura shima ibaad din kmr amatsayin uba kawai ya ajeshi.
maheer ne ya soma gaishesa cikin nitsuwa da ladabi, ya tattaro hanklinsa duka cikin bashi kulawa ya amsa shi cikin nitsuwar shima..
ajiyan zuciya me sanyi ibaad ya sauke cikin gyaran murya Yace" bappa..katashi lpya?.
ya amsa da lpya kalau ibaad masha Allah ya hanya kuma?
Yace alhamdullhi..
nan ya hau tambayar sa akan abubuwan da suka asalin faru a anguwar tudu dan hajiya mairo sama sama kawai tadan tsakura mishi awaya kuma tafi zakewa ma akan batun zuwan ayaanah cos she deeply want them to create a safe space for ayaanah's new life with them.
cikin nitsuwa ibaad ya fara fayyace masa komi yadda ya faru bai boye musu komi ba face wajen auren daya sakaya bai fito fili ya gaya musu cewa batun aurene yafara hadasa da ayaana ba, since d weding is void and invalid a musulunce sai baiga ma amfanin kawoshi cikin zancen ba. shide kawai ya musu bayanin cewa ahanyar zuwansa tudune ya fara samunta akasa tasuma cikin ruwa, snn bata da lafya kafin nan kuma sai yan kauyen suka kama shi suka tafi dashi acan akauyn suka bashi yarinyar ya taho da ita wajen hajya mairo.
maheer yanata kallon ibaad da mamaki dan ko kadan bai tsakura masa wayannan maganganun ba, he told them how he met ayaanahs mother da duk yadda sukayi da ita akan batun rayuwar ayaanah bai boye musu komi anan ba.
duk jikinsu sai yay matukar sanyi tare da jin matsanncin tausayin labarin taawure da duka yaranta..
nasiha bappa zaidu yay musu sosai, snn yace zai kira lawyersa inya je office zasu tattauna dan ayi wani abu legally akan zamansu da ayanah dan tazamo tana da full legal custody na zamanta awajensu sabida nan gaba kar mahaifinta juma yazo yace yana da cikakken ikon karbanta a hannunsu ko tafiya da ita. tun anan suka yanke hukuncin cewa ahannun mahaifyar ibaad wato ammi karama zata zauna na din din amma sai bayan ta gama jinyarta anan gidansan ta warke sosai.
maheer bai wani so hukuncin da aka yanken har ransa ba amma sanin baqin hali irinna mum dinsa da ganin yadda haryau take cin mutuncin ibaad kawai yasaka ya haqura duk da bai san ayanah ba tukuna yaso ace ayaanan agidansun zatay rayuwarta har tagirma ko dan kanwarsa sultana ta samu soul sister itama. dan sultana ita daya take rayuwarta anan, bata da wata abokiyr hira saina schl sabida duk su ba sa'ointa bane gashi tana mugun jin shakkar ibaad intagansa yawnci tsorata takeyi jikinta sai yahau rawa rawa, shiyasa most time batason saukowa kasa ta sake jiki sai lokcin cin abinci ko in sunfita schll basu nan, acan gidan kuma akwai kulthum da kuma safiya they had each oda all the time, nd mujaheed being the eldest is kinda cool guy asalinsa baida wani matsala da duka kannensa.
Hira suka taba kadan bappa zaidu yanayi yana hada musu da nasiha sosai, shi sam baiya iya zama da mutum walau nashi ne walau bana shi ba, face ya tsinci kansa cikin tunatar dashi kalmar Allah da manzonsa tare da zurfafa musu tunani akan muhimncn zumunci a tsakaninsu.
karfe bakwai yana cikawa suka bar wajen sa, ibaad ya sanar da maheer akan yaje ya kawo masa aron kayan sultana da zai bada ayaanah ta saka just for today inyaso insun dawo daga asibiti zasu dawo musu dashi, maheer baice komi ba yaje dakin sultana ya sameta tana zaune da farin glasses a idonta tana kan solving algebra akan reading table dinta, cikin ladabi ta rusuna ta gaishesa ya amsa batare da ya mata bayanin komi ba ya umarceta akan ta bashi complte spare cloths aro zai dawo mata dashi.
mamaki ya cikata amma dayake tasan basu fiye wasa da ita ba yasa ta tashi da sauri ta bude wardrobe tq dauko masa sabon spare pants da bomb shot sabbi kall daga ledarsu da wata loose abaya mai kyau peach colour mai igiya, baima tsaya duba yanayin tsayin kayan dakyau ba ya amsa yafice duk sai taji she is confused, koma waye za'a bada aron kayanta oho dai ta cigaba da karatunta bata kara kulawa ba...
yana isowa sashensu ya samu ibaad a bakin kofa yana jiransa suna hade ido baice masa komi ba ya miƙa masa kayan cikin sauke ajiyan zuciya yace "can i see the girl? fuska ba yabo ba fallasa ibaad ya bashi short "no..as answr. dan shiru maheer yay snn yace "i just want to see what she looks likes . ibaad yay kwafa yana kallonsa ahanlkli yace "she is sick nd scared maheer, dan Allah kabari sai na fito da ita zaka ganta, gyada kai maheer yay ashashance yace fine toh bari naje na shirya i think i have 9:30am lectures amma zan fita da wuri inada wani business da abdll gaffar
..cikin gyara tsayuwa ibaad yace wai harkun bude shop din naku ne, see i pity u ranar da bappa zai san kana wann abubuwan abayan idonsa. kyabe baki maheer yay ahnkli yace "isit a bad thing? sana'a fa na budewa kaina witout asking for his help he shud be proud of me, ibaad yay murmushi me sanyi cikin gyada kai yace "yeah he shud.,i am proud of you too,kayi kokari sosai...but he shud also scold u abit for squandering millions of naira over a secret investmnt witout his knowledge.
dariya me sanyi maheer yay yace inda a america muke fa da yanxu bama gidansa.. suka dan fashe da dariya"yace toh ibaad da kudi fa ake neman mugayen kudi, i want to be rich as early as possbile dan wallah aure zanyi da wuri...kuma in sha Allah befr i graduate my law schll in few yrs to come i will be a multi millionaire u just wait nd see...ibaad yay murmushi yace i trust you on that..u're a go getter!
dariya yay yace "so yaushe kai zaka fara setting naka business din ko likitoci basa kasuwanci ne? yafadi hakan yana zura maa ibaad ido batare da ko kiftawa ba..
ibaad ya kallesa da kyababben baki yace "seriously? ohh pls, not now mana.. saina settling a karatuna kadan kafin na fara tunanin me zanyi da rayuwata nan gaba. cikin rolling idanu maheer yace "ok fine, but the earlier the better. see yhu at d table. gyada kai ibaad yay har saida maheer din ya wuce part dinsa snn shima ya bude kofar dakinsa ya shiga ahnkli kuma cikin nitsuwa hoping to see ayaanah tagama wanke jikinta ta fito waje tana zaune akan kujera caraf saiyaga wayam snn dakin ya dauka da wani irinn shiruuuu kamar babu kowa aciki kusan ma yadda yabar dakin haka yazo ya sameshi..
kirjinshi har yana bugawa ya aje duka kayan akan gado da bala'in sauri sauri yay kofar bathrum din ya bubbuga da tunanin koma suma tay awajen yana can waje yanata bayani baisani ba...
kusan sau uku zuwa hudu ya buga dabaiji ta amsa ko tay motsi ba hannunsa harna rawa rawa wajen sauri da karfin tsiya ya bude kofar yashigo ciki adan gaggauce wanda karar budewa da shigowarsan ne yasaka ayaanah bude lumsashun idanunta data rufesu tamm tabi ta takure kanta akasa awani lungu tay shiru idonta nakan zubowa da hawaye.
yana hangota akasa arakube kusa da sink yaji ransa ya mugun baci, kai tsaye ya haɗe ransa kmr bai taɓa murmushi ba cos despite his bathrum floor is sparkling clean nd dry sam sai baiga dalilin da wani zaiso yazauna akasa acikin wajen ba...
tsawa yay niyyar daka mata sai kuma yaji ya kasa yin haka ya dan tsaya cak sabida rauni da tsoro dayake hangowa ajikinta sosai....kallo daya kamata zakasan cewa she is u can still grieving the loss of her sister inayah.
tunda ya shigo kallonsa takey a mugun kasale cikin jin tsananin tsoronsa ta kankame jikinta tareda jin matsanancin fargaba tana nishi nishi kmar wacce take shirin sumewa.
akanta yatsaya tareda zuba mata manyan hazel eyes dinsa that are sharp nd piercing, baice mata komi ba for a minutes sai can cikin tattaro makansa nitsuwa ayayinda fuskarsa take a mugun dore ya daga kirarsa sama yace "keee, menace miki kiyi? kanta ta sauke kasa ahnkli bakinta na rawa rawa tace "kace nayi fitsari'yace dakikay fitsarin sai kuma nace miki kizauna anan akasa wai ke wata irin kazamiyace iyeee daga kiyi fitsari ajiki saiki zauna a toilet?
shiru ta masa hawayenta na diddiga gwanin ban tausayi,
cikin sauke sihirtaccyar ajiyan zuciya yace toh "tashi"
a daddafe ta miƙe tsaye kanta na kallon tiles din, baice mata komi ba ya juyo wajen towels dinsa yasa hannu ya dau blue colour me kyau ya miƙa mata ta karba, ya dauki spare brush dinsa yasa tooth paste ya aje mata akan sink snn yay setting showersa zuwa warm yajawota gabansa kamar yar tsana giving her sound stern warning cikin zare mata ido yace "ki cire kayan jikinki, ki aje acan, snn ki daura wann towel din dana baki ajikinki, kishiga shower can kiyi wanka snn kidawo nan ki yi brush..kina gamawa ki fito..do not allow me to come back here for you for the scnd time.
shi baisan ma kotana jin turanci ba amma ganin yadda take gyada mai kai da sauri sauri cikin jin mugun tsoronsa yasaka ya kyaleta ya fita waje.
bayan ya rufe mata kofa kai tsaye ya fara kimtsa dakinsa kamr yadda ya saba, ayaanah stood for a while tana bin inda yabin da kallo, can kafin nan ta share hawayenta ahankli ta aje towel din ta kunce zaninta ta cire kayan jikinta duka ta ajesu agefe kamar yadda yace mata tayi
wani irin sanyi ta dingaji
sabida akwai A.c har a toilet din dakyr ta shiga shower sabida bata taba wanka aciki ba komi tanayine da tsoro tsoro har saida ruwan dumi yafara malala ajikinta sann taji kamr hanklinta yafara dawowa jikinta sosai.
she saw all his expensive gels nd soaps collection dake ta iya karatun turanci sosai kuma tana da ilimin ganewa amma dake batasan ya ake amfani dasu ba sai batay gigin taba masa abunsa ba.
acikin shower tay tsarki ta tsuguna ta wanke koinanta sosai da ruwa tafita tass, ta murda wani abu taga ruwan ya dauke sai tazo gaban sink din tay brush ta wanke bakinta, tay alwala tabi ta dauki dankwalinta ta rufe sumanta daya jike shataf jikinta na ɓari sosai ta bude kofar ta fito...
samunsa tay a zaune akan reading chair yana duba wani katon text book na anatomy and physiology sama sama sabida duk sun wuce basics din a private club dinsu...
irin kallon daya ma fatar jikintan ryt from head to toe yasaka ta sunkuyar da kanta can can kasa jin yay shiru ahankli muryanta na rawa rawa tace "uhmm mai mota...cikin katseta da mugun kallo yace "kee??? arazane ta kallesa yace uban waye mai motar ki? wani irin kankame dankwalinta tay zata fashe da kuka yaja tsaki yace"kar in sake jin kin kirani da wannn sunan now go on nd tell me meye matsalarki
bakinta na bari tace "na gama wankan ne..
yana miƙewa tsaye da sauri ta ja baya ta mannu da kofar a mugun tsorace tana hawaye
baiko kalle ta ya wuce ya shiga bathrum din kallo daya yamata ta karaso ciki, a miskilance yace "go back in der. ya kara nuna mata shower. snn yace kijje ki kara wankan and dis time use soap on ur body kingane me nake fada? da sauri ta gyada masa kai tunma bai fice ba tay sauri ta koma cikin shower ta tsaya, she read all the product on scrolls, har saida tagane wanne zata dauka aciki, koda ta rarumi katon shower gel dinsa tafi mintin biyu tana kokawar budewa, dakyar tazo tagane inda abun yake da yadda ake amfani dashi tana matsawa da karfi kuwa ya fantsama mata a fuska sauran yabi ya zube all over the floor, wanda ya zube ajikinta ta karasa mulkawa sann ta saka ruwa ajikinta wani dan uban kumfa da qamshi da tsantsi atake ya rufeta tana gama dauraye jikinta ta jawo towel din ta dora batare da ta lura ba tana saka kafa waje kuwa wani uban tsantsin gel din data zubar ya jawota waje suuiiiiii ya fetta ta akasa wani dan uban ihun razana ta zuba shikansa baisan sanda ya turo kofar agaggauce ya shigo ciki ba..
ganinta akasa yasa bai yi wata wata ba ya karaso wajenta yace meye faru? kuka take rabzawa dakyar ta nuna masa kasar floor din yaga duk gel dinsa ne akasa ya karkada kansa ya dauketa cak ya fito da ita ya ajeta akan chair snn yadan tsuguna agabnta ya kama kafarta ya dudduba koina yana mammtsa shi tsabar dadin dataji ita dakantan ta dena kukan tay shiru... dabai ga komi ba ya miƙe tsaye yay wani lungu after few mins ya dawo da white bathrobe dinsa ya lullube mata ajiki dashi snn ya umarceta data tashi ta karasa sawa sai ta bashi wet towel din, cikin saibi tamike ta aiwatar da hakan tana bashi towel din yace mata ta zauna, tana zama ya tattara jikakken suman ta duka acikin towel din ya daure mata shi tam tam snn ya kunna room heater acikin dakin for about 5 min, ya je ya dauke men hair dryersa ya kwance mata daurin kan ya fara bushar mata da gashinta yadau lokaci sabida yawa da tsayin sumanta har saida ya gama busharwa tsaf,lokacin ayanah kallon kasa kawai takeyi dan ko motsi batay iyayi bare tari.
tunda ya gama bushar mata dakai taji dumi ya dan gaurayeta daganan sai bai sake kulata ba, kyaleta yay anan for a while yaje ya wanke cikin bathrum dinsa ya tattaro kayantan data jika da fitsari yazo yasaka a engine ya wanke ya matse kafin nan ya dauke body oil insa ya bude yazo yana zuba mata kadan kadan a hannu tana shafawa a hannu fuska da kafarta, daga inda suken ya mata nuni da kayan sawanta akan gado yace yabata 3 mint ta saka kayan ajikinta ta jirashi yana zuwa, tun kafin ta amsa taga har ya fice abunshi, he went out of the room for a while, at exctly 3nd half minutes saigashi nan yadawo yazo ya sameta har tasaka sabon pant din da short ataciki da doguwar rigar da ya dan mata yawa kadan amma baiwani damu ba
suna hade ido tadan sunkuyar dakanta can kasa, ahnkli tace "umm.. zanyi sallah"yq kalleta da mamaki kafincan ya gyada kai kasar wuyarsa yace good for you. wucewa gaba yay barta a tsaye ya dau sallayarsa ya shimfida mata yana tsaye yana kallonta har ta cusa gashinta ciki ta dauresa gamgam sosai sabida yanada tsantsi snn ta gyara zaman mayafin gown in akanta tafara sallanta a nitse,
da gefen idonsa yake kura da ita she really looks pale nd light weigh, kamar jiri jiri yana janta har dai ta idar, tay adduarta hawaye ya cika mata ido ta juyo da sanyin murya tace mishi ina kwana?? sosai ya sha mamakin unxepected halin nitsuwarta daya soma gani sai kawai ya amsata da kai...adan dakile yace mata"are u done? tace uhm. yace "tashi ki biyoni..
babu musu ta miƙe yay gaba tafara binsa abaya tafara takawa ahnkli ahnkli kamr wacce kwai ya fashe mata ciki dan bakaramin rashin karfi da matsancin rauni takeji a zuciyarta da jikinta ba.
kan steps suka bi direct sashen bappa zaidu yakaita kusan kowani takawa sai taji kirjinta ya buga hardai suka iso wani mayen falon da bata taɓa ganin irinsa a kyau da girma ba suna shiga bappa zaidu ya bude kofar masters bedroom na gidan already ya gama shirinsa yay kyau cikin wata dakakkiyar coffe brown shadda ya dora matching colour borno cap mai kyau da kyalli wanda ko ba agaya maka ba kasan naira yay kuka ga designer cover shoes dinsa sai shinning take qamshin turarensa na original hugo boss tuni ya cikke falon da dadin qamshi..
ayaanah na baya baya har ibaad ya karaso da ladabi yace bappa ga yarinyar nan, i tot i shud bring her since she is ready.
kan ayaanah na kallon kasa bappa zaidu yadan lekota ganin ta kyakkwan gaske yasa yay murmushi yace masha Allah.. shigo ciki mana yan mata..
tana karasowa gabansa ta sulale kasa ta durkusa bisa ladabi da sanyin muryanta dake rawa rawa tace "i..ina kwana...?da fara'a sosai bappa zaidu yace lafya yannan tashi. tashi ki zauna akan kujera mana ai nan kamr gida ne...tana zama da tausayi a muryansa yace "ya jikin naki..kamar zatay kuka tace..lafiya..da sauki..
daga nan yafara mata gaisuwar ya hakuri snn ya tambyeta wasu abubuwa game da mahaifyrtan kadan kadan take amsashi a raunace
ibaad yay excusing dinsu ya koma dakinsa feeling relieved tunda ya damƙata ma bappa ita kuwa ganin ibaad ya tafi baiko kalleta ba tuni sai taji tsoro da raunataccen kuka yazo mata tafara ma bappa zaidu hawaye sosai. ibaad kuwa yana shiga dakinsa baiy wata wata ba ya faɗa wanka baikara sanin me suke ciki anan ba.
daga falon kuwa babu irin nasiha da hakurin da bappa zaidu bai bata ba dakyar tay shiru ta dena kukan, after assuring her to calm down, kuma shima kmr ubane agareta snn ta dauka nan kamar gida tazo suduka zasu riketa har saita cimma duka burikan rayuwarta..
dakyar nasihansa ya shiga kunnen ayaanah har taji dan dama dama aranta ta sake jikinta kadan dashi, ganin ta samu nitsuwa ta kuma fahimce shi sai ya miƙe tsaye da niyyar shiga cikin dakinsa domin dauko babban wayarsa, yabarta ita daya a falon tana zaune da hot cup of herbal tea daya bata tana shansa ahankli ahankli.
yana shiga daki ko minti biyu baiyi ba ayaanah taji motsin mutum abayarta wani irin faduwa gabanta yayi dake ba'ayi sallama ba duk saita dauka ko ibaad ne yadawo da sauri ta aje cup din shayin tana juyowa caraf suka hade ido da ammi babba.
wani tsayuwar cak ammi babban tay tareda furta "innahu man suleimanu wa innahu...a mugin rude tace".... minal shaidanarrajeem. tsayawa cak tay ayayinda kirjinta ya buga da wani irin karfi da tunanin ko gizo ne take gani na aljana a zaune
ganin ayanaahn ta tsura mata manyan idonta a tsorace yasa ta kara dafe kirjinta tanamai kallonta a matsayin aljanar dagaske cos the girl has this rare calm beauty gatadai ba fara bace soll amma ko kadan bazaka kasata a chokolate ko baqar fata ba, kamar wacce zata cire hanjin cikinta take kallonta musmm dataga kayan yarta sultana ne ma a jikinta
kallon da ammi babba take mata yasa ta miƙe tsaye da tsoro da kuma ɓarin jiki sai batace mata komi ba...
haka ma ammi babban ta dauke kai cikin dauriya ta wuceta da kokon to aranta. dakin mijinta ta shiga da sauri sauri kmr ankorota tana cewa Baban maheer, baban maheer..kazo kaga wani abu wani halitta fa nake gani a falonka kmar aljana amma kuma kayan sultana ne ajikinta ni dan Allah kazo katayani gani, katse wayar dayake yay ya daga kai ya kalli matar tasa yace "calm down raihanatu Bakuwa ce" cikin sauke tumin ajiyan zuciya ta d'an yatsina fuska tace "Bakuwa kuma? Daga ina? Kuma ina za'a kai ta?.... Yace "Eh bakuwa.... Daga Tudu. kuma nan gidan zata xauna for a while in sha Allahu rabbi.... Da mugun mamaki tace "toh? kuma Yar wacece ita din? Yace "itama jikar hajiya ce acan tudu..."
A mugun kufule tace "jikqr hajiya? Plss duk jikokin hajiya basu wuce maheer, sultana, mujaheed, kulthum, zainab arifah, safiya da ibaad ba... kawai ka fito fili kagaya min ina ka samo wann yarinyar? yace "Gashi nan na gaya maki, what else did you want to know, me kuma kike son sani...
kamar jiran tambayar take ta mayar masa da amsa da sauri tace "Manufar kawota gidan nan, sannan mun hada wani dangantaka ne da ita da zakace zata zauna anan for a while??"
Ya gyara zama yace "raihanatu yarinyar nan zata zauna damu ne na wani d'an lkci tay jinya kafin hajiya ta gama parking ta dawo kano, dangantakar mu kuma shine kasancewar ta yar uwarmu musulma kuma yarinya karama datake bukatar taimako da kulawa.
kallonsa ta dinga yi looking amazed, confused, and mad at the same time....
tay rau da ido bluntly tace sannu philantropher, the great humanatarian indeed,ohh dama itace wacce ibaad din ya je kauye ya dauko? ni ban gane abinda kke nufi ba, dama kiransa tudu akayi dan ya dauko mana wata karin responsibitliy while we already have enuf ko kuwa a ina kasamo wannan yarinyar nifa bangane komi ba"
jin ransa ya fara baci da tmnbayoyintan sai Ya mike tsaye yace raihanatu ki saurareni, wann umarnin hajiya ne, nd all that aside, she is sick, jinyarta zamuyi anan ynzu..."
azafafe tace toh fine...anji umarnin hajya ne..amma baga kaninka muhammad ba? safeera ce karama ya kamata sai bata ajiya ko akai ma waccan makirar matar..meyasa zaa kawota gidanan nan inba tsabar anraina min wayo ba, ko gidan miji na ya dawo babban opharnage ne bansani ba da za'ana kawo tarukuce ana laka min dan kawai anga bana aikin gwamnati.
batare daya kalleta ba yace " "sanin kanki ne safeera tana zuwa school, snn tana aiki ta same time, fatima kuma kinsan bata zama ynzu sabida aikin bude foundation innan ya riga ya gabato da zafi zafi, ga kuma yarinyar bata da lafya, kinga kuwa dolene anan gidan zata zauna mu hadu muyi jinyarta har sai hajiyn ta dawo sai akaita can...tunda nace mimi yarinyar nan ba zaman har bada zatay agidan nan ba you have no reason to be over reactive.
Yana fadin haka ya fita daga dakin ya barta a tsaye
.... da wani irin kallon mamaki ta bisa lkci daya cikin girgiza kai da tsananin kishi tace tabdi jamm...kajimin wani irin rainin hankali wato safeera yar masu shi baza'a takurata da rainon ko jinya ba, fatima kuma ai dama farkarka ne kowa ya sani baka kaunar abunda zai taba maka ita. to wallah wallah ba a isa raina min wayo ba. wani za'a gayawa foundation? foundation din banza foundation din wufi ai munsan kaine kabude matashi da kudinka amunafurce shiyasa kake neman nika kawomin wata siyasar banza, wato ma nice yar iskanku da zaku dauko wata miskiniyar aljanar kauye alaka min jinyarta to wallah bazaiyu ba....daga ku har yarinyar sainaci uban kowa agidan nan...
ayaanah dai na zaune sai kallon direction din da masifar ke tashi take yi har bappa zaidu ya fito da sauri baice ma ayaana komi ba banda murmushi me sanyi dayamata ya fice da sauri yay waje domin duba wani bakonsa akofar gidan daya kawo mai wata aika
gaba daya a tsorace ayaanah take lkci guda taji sabbin hawaye ya kawo cikin manyan idanuwanta tana Allah Allah ibaad yashigo....
Bayan kamr minti biyar Ammi babba ta fito daga dakin tana wani cika tana batsewa kmr wata boss take kallon ayaanan tana huci, tana kawo dede kanta ta tsaya, cikin sanyin jiki ayanah ta sulale kasa ta rusuna zata gaisheta atake taji an daka mata tsawa me karfi "Ke maza tashi ki fita ki ban waje kar in illata ki, munafikaaa kawai..."
amugun rude ayaanah ta miƙe da sauri tareda fashewa da kuka tana laluben hanyar ficewa
muryar ibaad ta ji atacan sama da alaman yana waya sai ta tsaya cak tana kuka sai kuma bata gansa ba jim kadan wani kyakyawan mutum ya bayyana agabanta yana saukowa kasa yasha expensive tailored black suit insa irin na typical law student..
#Surayyahms
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[11/11, 21:38] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: ⏯️1️⃣9️⃣
suna hade ido da maheer wani irin shirun bazata tayi tabita tsura masa raunatattun idanunta dake famar zubowa da ruwan hawaye masu yawa kamr ruwa a mugun tsorace ta tsaya cak kmr yadda taga shima ya tsaya yakuma tsura mata nashi sexy eyes din in complte awww of her rare calm beauty danko motsi baiyayi at the sight of her dayay freezing dinshi ya tsaya cak kmr an dasa shi da kankara...
sunfi minti biyu suna kallon juna sai can ta sunkyar dakanta ahnkli cikin tattaro makanta wata nitsuwar karfin hali tay shiru idonta na kallon kasa kamr wacce take neman wani abu aka tiles din
ajiyar zcyar bazata ce ta kwacewa maheer yay murmushi me sanyi danko ba agayamai ba yasan wannan ne yarinyar da ibaad yazo da ita, karasowa yay tare da dawowa cikin hayyacin sa ya kalli sunkuyayyen kan ayaanah yana murmushi me sanyi yace "Hi preety one..
shiru tay taki sam ta daga kanta...dada karasowa yay zai dafa kafadarta yana kawo hannunsa tay wuff ta firgita zata arce aguje ya riƙeta, wani dan uban kuka ta fashe masa dashi yace hey hey calm down..ina zakije? tay masa shiru a tsorace take waige waigen baya, bayan shima ya kalla snn yace toh "waya koroki" kara sautin kukan tay yace ya salam toh..ina shi ibaad din? ko wajensa zakije ne,...da mugun sauri cikin kukan ta gyada masa kai har sau biyu..cikin muryan lallami yace" okay, toh zan kaiki, kidena kuka kinji?big preety girl like u ai basa kuka..share hawayenki. dan gyada masa kai tay shisai ya saka hannunsa dake zuba qamshin tonka notes yafara share mata tears dinta dashi yanamai dada kare ma halittar ta kallo, like the girl is so soo perfect nd flawleess, yadda take famar sauƙe ajiyan zucya me nauyi kuma a tsorace yasa bakara min tausayi ta bashi ba...
yana cikin share mata tears din ne sukaji motsin mutum abayansu yana daga kai yaga mahaifyarsa ammi babba ce ta fito ranta a mugun harde
baice mata komi ba ya dan kalleta snn ya kalle ayaanahn sai atake ya fahimce abunda ya faru
jira take taga ya gaisheta sai taga ya wani irin haɗe rai ya kara dauke kansa ya mayar kan ayaanahn yanakan lallashinta ahnkli harsaida ta nitsu snn yace "preety. muje inkaiki wajensa ko..
har ayaanah ta daga kafa cikin daka tsawa ammi babba tace "..maheer!!! yana juyowa tace "babu inda zaka kaita..ka saketa anan inyaso ta tafi duk inda zataje..
kara juyowa yay azafafe zai amsa cikin tsananin bacin rai tare da katse shi da zafi zafi tace "enuf. yau bana bukatar jin lectures dinka see me in my room ryt this minute, maheer wallah bana wasa dakai..kanaji na ko??
sake hannun ayaanah yay da sauri ransa a mugun bace ya haura saman stairs sabida shi mutum me saurin bacin rai kuma daga zarar ransan ya baci dakyar yake controlling kansa
yana wucewa sama tabi ayaanah data sunkuyar dakanta kasa da wani irin muguwar kallo, cikin taɓe baki ahnkli tazo dede wajen kunnenta ta kama da karfi snn tace"..wallah wallh zamanki agidan nan saiya miki daci, munafuka kawai me kama da aljanu..
tana fadin hakan ta dungureta snn taja wata iriyar kakkauran tsaki tawuce, ayaanah taji wani irin kuka me cike da tsoro da tashin hankali na shirin barke mata saidai tun kafin kukan ya subuce taji motsin mutum yana tahowa, qamshin turaren sa dataji yasa ta hadiye kukan tsaf, for a while her heart skip a beat tay shiruuuu kanta na kallon kasa tanamai lumshe ido tana shakar qamshin turarensan tana sakin silent hawaye har ya sauko..
kallo daya yayi mata ya wuce gaba abunsa bai tsaya ba har saida yay kmr 2 steps snn yajuyo muryansa na fita ahkli kuma adan miskilance kasa kasa yace" ke wai komi sai angaya miki ne? toh sai kicigaba da tsayuwa awajen harta dawo ta sameki taci gabada cimiki mutunci."
lumsashun idanunta ta bude tanadaga kai caraf suka hade ido dashi wani yarrr taji ajikinta silent hawayen nata ya tsaya cakkkk tabi ta kuresa da wani irin rudadden kallo kmr ma wacce bata taɓa ganinsa a rayuwarta ba sai gaba daya taga kmr yacanza mata, sosai yay matukar kyau daya saka wata gogaggen all black designer half jumpa na wata simple yadi marar nauyi wann fresh healthy yellowish skin tone dinsan kuwa bakaramin hasakaka bakin kayan yayi ba, kayan har wani kyalli yake tsabar tasha guga he is damn handsome nd smart babu karya, ita kanta batasan sanda takage takasa motsi ayayinda take kan kallonsa ba
acikin moment din kallon datake masa yaji kansa ya daure sosai sai ya kara juyowa yace" ke lafiyarki kuwa? cikin sauri ta girgiza kai at same time sai kuma ta gyada mai kai..
sabbin hawaye suka kara sauko mata zirrrr ya hade rai yana shirin dawowa gabanta sai ga nan bappa zaidu ya zagayo ta wajen cikin sauri, ganin su atsaye awajen yasa ya isa ga ayaanahn da muryan tausayi yace yan mata ya da kuka kuma ko bakijin dadin jikinki ne? da sanyin jiki tagyada masa snn tace mishi eh kaina me yakemin ciwo..
hannunta ya rike cikin nashi yace subhannllah cikin tsantsan nuna kulawa ya shafa kanta ahnkli yanacewa i am sorry my dear tomeda me yake miki ciwo bayan nan?..kafin ta amsa ya juya atake ya kalle ibaad dake tsaye yana kallonsu a nitse yace"ibaad nace meyene asali yake damunta ne a yanzu take ta kuka? or have u noticed anything since dis morning koma zaku wuce asibitine kawai in yaso maheer saiya biyoku da breakfast dinku acan"..
babu yabo ba fallasa ibaad yace "bappa dama ai it will take time kafin jikintan ya sake harma ya warware, likitan danace maka mungani jiya tace zuwa nan da kwana uku inbata samu sauki bane sai mukoma for now allura kawai za'a mata...cike da qamsuwa da hakan bappa zaidu yace toh its okay..but i dont like it when she cries..wont it affect her progress? ibaad yay shiru baice komi ba..saiga nan maheer yana saukowa kasa da sauri sauri ransa a mugun bace
daga can bayansa muryan ammi babba ne yake tashi cikin masifa tana cewa "Ko kaki ko kaso ni din daka tsana nina haifeka kuma yau innna tsine maka albrka wallah sai ya bika maheer marar kunya kawai...
jin wann kalman yasa bappa zaidu sakin hannun ayanah yadda suka hade ido da maheer yaga idanun sa sunyi jaaa da bacin rai yaji hanklinsa shima ya mugun tashi witout saying a word to him ya wuceshi ya haura sama zuwa sashen nata da sauri..
ibaad ya kasa cewa komi yanata kallonsa ganin ya tsaya cak awajen ayaanah looking at her cute innocent face trying to calm himself down abit...
cikin shanye fushinsan ya kalli ayaanan da sanyin murya yace"preety one kinga ibaad din yanzu ko? bata amsa ta kallesa ahankli, yace to muje can kasa kiyi breakfast dinki nasan dai kinajin yunwa. kafin ta amsashi taji harya riko hannunta yafara janta ahnkali kanta na kallon kasa batace mai komi ba har sukazo suka wuce ibaad akan stairs din daga bisani shima ya biyosu abaya...
sultana ta gama shirin school dinta kenan ta fito cikin clean white nd grey suit uniform dinsu na jss 1 tay wani irin parking suman ta dayaji gyara cikin grey beret tsaf tayi kyau gwanin ban sha'awa, tana takun tame aji ta rataya jakarta iri daya da light grey sneakers inta na gucci me mugun tsada,
sashen babanta tafara nufa danta gaishesa da bata gansa ba tawuce gefen mum dinta wanda tun bata iso bedroom dinta ba taji wani irin hayaniya na tashi tsakanin iyayen nata sosai, tsam tay ajikin bango dan bata gane meke faruwa ba musmn data ji sunan yaaa maheer na tashi acikin masifar sosai
rai a matukar bace taji ammi babban tana cewa"Ehh ehhh nafada din zan tsine masa albarka din, ina dai nina haifeshi? toh akan me zai maidani sa'ar sa agidan nan, daga yay fushi dani sai bazai gaisheni ba snn inzo ina bashi umarni yanacemin bazaiyi ba kai tsaye, toh wallah wallah muddin bazai min biyayya ba kuma yasa haraman cigaba da rainani agidan nan saina masa abunda har ya mutu bazai manta dani ba
da tsawa bappa zaidu yace mata "da Allah kirufa ma mutane baki raihanatu ina duk akan dan yana gaya miki gaskiya akan mugayen halinki dakikeyi ne kike so kisako shi agaba, toh wallah kisani,.. kika sake furta irin wannan mummunan kalman akan maheer abakin aurenki..
amugun razane tace whaaat? abakin aure na akan maheer dinn??sai kuma ta rushe masa da kuka tanata kallonsa da dumbin mamaki ayanayinta
wato baban maheer mani kake gayawa wann maganan ko?
hade rai yay yace ehh angaya miki tun da ke bakida hankli bakisan darajar mutane ba baki san zafin danki ba, toh tunda nima na haifesa nasan zafin ɗana kuma baki isa ki lalata masa rayuwarsa da mugun bakinki ba dan Allah ma bazai karbi tsinuwarki akansa ba yaron nan babu abunda yamiki face gaya miki gaskiya da dama bason ji kike ba. idonsa a rufe yace now u hve to move out there, and get us our breakfast ryt now cos we are runing late..shashasha kawai
..fitinanniya!
wani irin kuka ta kara rushewa dashi tanata bin sa da wani irin kallo, dede nan sultana tay sikinini ta bar sashen da mugun sauri ta sauko kasa abunta har bappa zaidu yasako kai shima ya fice ya bar ammi babba anan bata dena kuka tana zage zage cikin kukan ba...
"munafiki kawai macuci Allah ya isa min zalunta dakakeyi agidannan, ina ce dan dankan yana goya maka bayane kana neman mata yasa kukeso kuyi min taron dangi ku kashe min aurena toh wallah baku isa ba..ina nan zama daram agidan nan wata me suna fatima bata isa ta shigo gidan nan ba sai bayan raina..
ita dayanta ta dinga maganganu tana kuka jin babu motsin kowa anan kusa yasa ta miƙe tsaye da gunjin kukan cikin rasa abunda ke mata dadi ta dau wayarta gaggauce ta kira babban aminyarta hajiya ramatu, wayar nayin ringin sau uku aka dauka tana cewa helloo dagata dayan bangaren aka amsata da cewa raihanatu lfya kuwa yana ji muryanki haka?
...cikin kara rushewa da kuka tace ina kuwa kikaga lafiya ramatu na shiga uku, na haifo maqiyi na duniya ɗana maheer ya tsane ni fatima ta tsafe min miji na ya dawo karenta yanxu kuma ta dawo kan ɗana na shiga uku na lalace...
daga ta dayan bangaren matar ta rusa wani dan uban ashar "kutumar babban buran ubann fatimar... ke kuma saiki tsaya kina mata kuka kai kai kai amma raihanatu kinfara bani haushi wann sakacun har ina zaki tsaya wata bazaurar mace awaje tana wargaza miki gidan mijinki gaskiya kina so ki bata min raina akanme zaki tsaya ana miki cin kashi aka..wai uban meye tamiki kuma yanxu.
neman waje ammi babba tay ta zauna bisa kan gadonta snn tahau gaggaya mata karya dagaskiya tana fadi tana kuka...
"Dan tsabar an rainani za'a shine harda kawo min raino? wallh wallah ramatu bana cire tsammanin acikin abinci fatimq take saka musu magani ni gabaki daya nakasa gane kan mijina bare kuma dana maheer, juya kansu takeyi ynxu kamr masa kinga haka ta nanika ma miji na rainon danta ibaad haryau munakan zama dashi gashi wai anje kauye an sake kawo min wata yar iskan aljanan yarinya ankara kawomin itq gidana dagayin magana shine duk suka taru akaina sunacimin mutunci ramatu baki ga irin rashin kunyar da maheer yayimin dazu ba wai harda cemin wai inda sultana ne zanso acemin tanq fuskantar hakan danakeyi ahnnun wata waifa cemin yay bani da imani...
hajiya ramatu tace "kutuman uba can shine baki wanka masa mari ba? yaushe aka haife maheer din da har zai gaya miki wann baqar maganan.
tace nima ganemin hanya ramatu, fada kawai na masa nace ya fita ahanyar yariinya shknan shine yafita yaje ya turomin ubansa yazo yacimin mutunci har da cewa inna kara taba masa dansa abakin aure na.
"innalillah wa inna ilaihi ke kuwa rainhanatu abun ashe har yakai haka ne?to wallah zama bata kama ki ba gara ki tashi tsaye kiyi dagaske ki tabbata yarinyar nan da aka kawo ba agidanki zata zauna har abada ba..dan wallh wann salob rainin wayo ne kawai fatima take miki..tana janye mijin ki a makirce tanacan tana bashi kulawa abayan idonki, shiyasaka duk wani abunda tagaya masa yakeyinsa babu jayayya kamar wani itace uwarsa..
cikin cizza labba ammi babba tace tabbbb ai wann makirar nakega tafi masa uwarsa ma tunda just last week tay maganan cewa zata kara bude wani babban foundation caraf this week sai gashi wai har ta bude, kuma wallah wallah bana kaffara mijina ne ya bata kudin budewa inba haka ba a ina taga uban kudin nan a lokaci daya..naga ai gadon dq tsohon mijinta yabarii duka na yayansa ne, akan da ya bani 50 million na kara karfafa sana'ata shine yaga gwamma yaje yabawa karuwarsa ta bude musu gidan marayu..cikin kara rushewa da kuka tace na shiga uku ramatu yay zanyi da raina?....
cikin kyabe baki da baqin ciki a muryanta ramatun tace ikon Allah toh raihanatu wallah kibar wann kukan kawai ki shirya ynxu ki fito mqza muje wajen malamin nan enuf is enuf, haba...kina zaune da namiji amma an mayar dake bakomi a idonsa ba
cikin kuka ammi babba tace a'a ramatu, mubi ta wani hanyar kawai dan malamin nan naki banda kudina babu abunda yake ci kuma tsakani da Allah dan iska ne kuma kinsani dan bansan uban meyasa kullum sai ya nemo yataɓa nonon mutum kafin yake bashi maganiba kiga dai azaban danasha lokacin da ake son amin kishiya....
cikin katseta ramatun tace "kai raihanatu amma baki da godiyar Allah..nikuma sai ince me da har kwanan gida ina zuwa masa? ke ma dai kinki ki saki ranki ne kisha romon dadi wallh malamin nan yasan kan yadda ake juya mace agado gashi Allah ya zuba ma gabansa albarka kamar aljanu ne suka bashi karfi burarsa fa inya tashi baiya sauka da wuri haka zai sosa miki har sai ke kinji kingaji da dadi kinbarsa, hanklina kwance, mijina sai abunda nace yake min..ga biyan bukata ga kuma lagwadar dadi..
toh meye?
cikin share hawaye ammi babba tace toh nide baza'ayi wann rayuwar dani ba. kece kawai yake zagewa yamiki aiki ni inbanda hana yuyar auren mijina da fatima dayay banga amfnin komi da maganinsa yamin ba tunda haryau miji na is crazily in love with that evil woman ga kuma babban dana yajona su yana goya ma ubansa gindi yana walakanta ni akan wata banziyar mata yar iska tababbiya
cikin jan tsaki hajiya ramatu tace toh ai shikenan saikizo muje wajen zinariyar mace ai tana da kayan mata da zakiy amfani dasu ya dawo miki dashi kan saiti cikin kankanin lokaci, amma zafa ki kawo mata duk abunda tace miki .koba komi kafinn mijinkin ya dawo hayyacinsa kin karbi wani kudin kema ahannunsa amma kin zauna sakaci wata yar iska awaje tana cin kudinsa abanza toh wallah kece kikayi banza, ni anya ma bazakiy bincike akansu ba...kode kode yana zagawa ne tana bashi gindi yanaci.