DUKAN RUWA HAUSA NOVEL
Bismillahir Rahmaanir Raheem. *DUKAN RUWA...* FARKO. Ta yi zugum kanta jingine jikin kujera tana kallon halittun
manyan duwatsun da suke ratsawa a wannan dajin, tafiya suke yi tamkar ba
za su kai ba. Wani lokacin idan sun gifta bukkokin jama'ar wani yankin, takan
yi murmushi cike da al'ajabin ta yadda mutum ƊAN ADAM ke iya rayuwa a wannan
wuri. Tun tana kallon har dai ta zame ta gyara zama gami da lumshe idanu, bacci
ke ƙoƙarin ɗaukarta tana yakicewa. Babu abin da ta tsana sama da bacci a hanya,
hanyar ma da ko a mafarki ba ta taɓa ganin za ta bi ba, zuwa Nijeriya
daga Nijar. Ajiyar zuciya ta saki tamkar wacce ta ci gudu, lokaci guda nannauyen tunanin da take ƙoƙarin kaucewa
na ƙara yi mata saukar aradu a kwakwalwa. Idanunta ta sauke akan matar dake
kusa da ita, baccinta take haiƙan har carbin da ke riƙe a hannunta tana ja, ya
faɗi. Sai dai duk da baccin da ta lula, hakan bai sa ta saki yaronta ba, yana
rungume a kirjinta ɗam! Kai ka ce wani ne zai ƙwace mata shi. Juya …