Bismillahir Rahmaanir Raheem.
*DUKAN RUWA...*
FARKO.
Ta yi zugum kanta jingine jikin kujera tana kallon halittun manyan duwatsun da suke ratsawa a wannan dajin, tafiya suke yi tamkar ba za su kai ba. Wani lokacin idan sun gifta bukkokin jama'ar wani yankin, takan yi murmushi cike da al'ajabin ta yadda mutum ΖAN ADAM ke iya rayuwa a wannan wuri. Tun tana kallon har dai ta zame ta gyara zama gami da lumshe idanu, bacci ke ΖoΖarin Ιaukarta tana yakicewa. Babu abin da ta tsana sama da bacci a hanya, hanyar ma da ko a mafarki ba ta taΙa ganin za ta bi ba, zuwa Nijeriya daga Nijar.
Ajiyar zuciya ta saki tamkar
wacce ta ci gudu, lokaci guda nannauyen tunanin da take ΖoΖarin kaucewa
na Ζara yi mata saukar aradu a kwakwalwa. Idanunta ta sauke akan matar dake
kusa da ita, baccinta take haiΖan har carbin da ke riΖe a hannunta tana ja, ya
faΙi. Sai dai duk da baccin da ta lula, hakan bai sa ta saki yaronta ba, yana
rungume a kirjinta Ιam! Kai ka ce wani ne zai Ζwace mata shi. Juya kai tayi ta
koma kallon hanya da murmushi Ιauke saman fuskarta. Soyayya da shaΖuwar dake
tsakanin Ιa da uwa na daban ne, a kowane yanayi, a kowace rana burin kowace uwa
ganin gudan jininta cikin walwala da annashuwa, ba ta fatan wani mugun abu ya
same shi. Shakka babu duk wanda ya rayu da uwa ya more.
Sai kuma kewa ya lulluΙe ta dalilin Dada da ta tuno,
watanni biyar kenan da rasuwarta amma jin sa take a rai tamkar jiya-jiya.
Kullum mutuwar kakarta kamar sabo ne fil a wurinta, mace mai hakuri da dattako,
ta yi namijin kokari wurin ba ta kulawa daidai gwargwado da kuma tarbiyyar
islama. Ba ta shaΖu da kowa ba sama da ita sai ko Kawunta Ιan uwan Mamanta,
Kawu Umaru. Shi ma ba ta jin za ta manta da irin namijin ΖoΖarin da ya yi a
kanta, koda dai dama barewa ba ta yi gudu ba Ιanta ya yi rarrafe, wannan kyawawan
Ιabi'un Dada ne suka kwaso. A wannan irin namijin ΖoΖarin ne a yau Kawunta ya
tashi haiΖan suka bi wannan doguwar hanyar kawai don ya sada ta da mahaifinta,
mutumin da tun da ta buΙi ido ba ta taΙa ganinsa ba. Hatta a waya ba su taΙa
koda gaisawa ba. Duka wannan bai sa ta riΖe mahaifinta a zuciya ba domin
kuwa ya samu kyakkyawar shaida a gurin Dada da Kawu. Ko sau Ιaya ba su taΙa
kawomata kushensa ba, asalima sun ce
yana sonta sosai, kuma acewarsu ya sha zuwa ganinta tana Ζarama, su Ιin ne suka
Ζi amincewa ya tafi da ita bisa dalilan da su kaΙai suka bar wa kansu sani. A
yau kuma da aka wayi gari babu Dada, Kawunta ya Ιauki Ιamarar cika wasiyyar da
Dada ta bari na cewar ya sada ta da Mahaifinta idan har rai ya yi halinsa.
Ζan girgizar da motar ta yi sakamakon taka wani Ιan
tudu ne ya sa ts ji saukar ruwa a saman leΙΙanta, sai lokacin ta gane kuka
take. Kukan kewa da damuwa ne, Dada ta tafi, tafiya ta har abada, ta tafi wajen
da ba za ta sake ganinta ba sai ko idan nata ajalin ya iso, ta je ta tarar da
ita.
_"Kar ki taΙa bakin ciki da zuwa wurin
Mahaifinki Shatu, mutum ne nagari mai sanyin hali, za ki yi farin ciki da
ganinsa. Yana sonki sosai Shatu."_
Kalaman Dada suka faΙomata a rai, ta sauke ajiyar zuciya na
samun nutsuwa, lokaci guda ta ciza leΙΙanta na Ζasa tana Ζara murmusawa karo na
barkatai. Ya mahaifinta yake? Da wane ido za ta Ιaga ta kalle shi ya kalle ta?
Dagaske tana kama da shi ko kuwa dai Kawu ya faΙi ne don ta ji dadi? To an ce
yana da wasu yaran, su ma tana kama da su ko aa?
Duka waΙannan tambayoyi ne da ta hargitsa lissafin
kwakwalwarta da su alhalin babu mai ba ta amsa. Haka dai ta yi ta saΖe-saΖenta
har suka fita gaba Ιaya daga Nijar suka nufi bodar Nijeriya.
Nan Ιin ma bayan kammala cike-cike da duba kayyakinsu, suka
gangara cikin Nijeriya, ta baza ido tana kallon yanda cikin iko da hukuncin
Allah, shuke-shukensu ya sha bamban da na Ζasar da ta fito.
***
"KATSINA" Ta karanta sunan a hankali, sannan ta
dinga bin garin da kallo tana Ζarewa bambance-bambancen garin da nasu.
Tunaninta ya katse sa'ilin da direba ya tsaya a gefen hanya domin ba su
damar gabatar da sallar la'asar. Mazan duk suka riga su sauka, su ma suka
sauko. Kawu ya dube ta.
"Ki bi su ku yi sallah kar ki je ko'ina kin ji
ko?"
Ta gyada kai ta amsa da toh, tana rungume da Ζ΄ar Ζaramar
jakarta ta hannu haka ta dinga bin matan su uku har zuwa wani Ιan wuri da aka
katange, suka samu gefe guda da ba mutane, masu jin fitsari suka yi sannan suka
Ιaura alwala. Bayan sun idar suka dawo motar, nan kuma kowa ya hau zuge jaka ya
na siyan abin motsa baki. Tana nan zaune cikin motar Kawu ya kawo mata ruwa da
lemu sai nama a leda, kaΙan ta ci bayan ta yiwa Ζ΄an motar bismillah, sauran ta
naΙe ya ajiye a gefe, lemun dai ta sha sosai.
Daga nan suka Ζara miΖa hanya har dai cikin hukuncin Allah
suka Ζaraso cikin garin KANO.
Ta nanata sunan a kan harshenta jin wata Mata ta ambata, ta
maimaita har sau uku, lallai idan ba ta
mance ba shi ne sunan da Dada ke yawan ambata idan ta tambaye ta sunan
garin Mahaifinta. Nan da nan zuciyarta ta yi fari Ζal, ta kasa rufe
bakinta, wannan karon murmushi take tun daga Ζasan zuciyarta har saman leΙΙanta
don har siririn wushiryarta na bayyana. Sai da suka Ζarasa tasha suka sauka,
daga nan ne kuma Kawunta ya Ιauki akwatin kayanta suka fito bakin titi. Suna
hawa taji ya ce unguwar Gadon Ζaya, daga nan direban ya hau tafiya ita kuwa
tana ta kallon hanya har suka sauka. Sun yi Ζ΄ar tafiya a Ζafa sannan ta ga ya
tsaya daidai bakin wani Ιan shago ya yiwa mai shagon sallama. Koda suka gaisa
ya ce.
"Don Allah gidan Alhaji Isuhu Maiagogo nake
tambaya."
Mai shagon ya gyada kai ya Ιan fito sarari ya hau yi musu
kwatance da hannu. Ya yi godiya suka nufi inda ya ce.
Koda suka karasa wajen wani Ζaton gini ta ga ya tsaya cak a
gaban ginin, ta bi ginin da kallo ta ji gabanta ya yanke ya faΙi lokaci guda,
ba kuma don tasan dalili ba. Ta kasa kwakkwaran motsi har Kawunta ya taka zuwa
ga kofar gidan yana tambayar wani dattijo ko nan ne gidan, amma ita kam ba ta
dauke kai daga kallon ginin ba, gwuiwoyinta suka yi wani irin saki, ganin
yanayin da ta shiga har zufa na tsastsafomata a goshi yasa ta dinga maimaita
kalmar innalillahi.
"Shatu ke!"
Kiran da Kawu ya
kwalamata ne ya maido ta hayyacinta, a hankali ta soma takawa har ta Ζarasa
gefensa, ba ta kuma san dalili ba ya ji ta sa hannu ta riΖo nashi yatsun gam!
Hakan da tayi ya sanya shi dubanta, itama shi din take
kallo, ya yi dariya.
"Tsoro gidan ya ba ki ne? To ki shirya yaΖar tsoron nan
don nan ne gidan zamanki daga yau in sha Allahu."
Dattijon ya taya shi darawa kaΙan duk da bai fahimci komai
ba. Amma ta lura da yadda yake ta kallonta har ya kasa hakuri ya tanka.
"Amma dai wannan Ζ΄ar uwar Alhaji ce ko?" Kawuna ya
yi dariya ya amsa da eh kawai. Ita dai ba ta ce musu uffan ba sai sadda kai
Ζasa da ta yi, ta na ji Dattijon nan na
kara zuzuta kamanninta da Alhajin wanda shi ya sanya shi tankawa. Suna
nan dai tsaye sai ga wani Ιan matashin yaro ya fito, ashe wai Dattijon ne
ya aika shi gidan don a shaida wa Maigidan zuwansu.
"Ya ce maza ku shigo ciki. Muje na raka ku."
Daga haka suka shiga ciki. Madadin faΙuwar gabanta ya
ragu, sai ma Ζara hauhawa da ya yi, ta ci gaba da maimaita innalillahi har
Ζarshe, sai ta ji gaba daya ta bar rawar Ζafar son haΙuwa da Babanta Isuhu.
Koda suka Ζarasa cikin Ζaton falo, wani irin
sanyi da Ζamshi mai dadi ne ya daki hancinta. Ta gefen ido take bin wurin da
kallo tana so tayi ido huΙu da Babanta, sai dai kuma duk irin girma da daular
da ke shimfiΙe a falon wanda ya Ζara Ζawatashi, babu rai ko Ιaya mai numfashi
face su ukun da suka shiga.
Wuri ya nuna masu saman kujera suka zauna, ita kuwa Ζasa ta zauna gefen Kawu
don ba'a ba ta tarbiyyar zama saman kujera alhalin manya na zaune ba. Matashin
ya kara juyowa fuskarsa a sake.
"Ku jira YallaΙai nasan ba zai jima ba zai
fito." Kawu ya amsa daga nan ya fice ya bar su a nan. Sun samu mintoci
goma da sakanni, don gaba daya hankalinta yana kan Ζaton agogon da ta zauna
saitinsa, kafin ta Ζarasa Ζirgenta suka tsinkayi sallama. Lokaci guda suka kai
duba ga gefen da muryar ta Ιullo, baki da ido ta saki tana kallon mutumin
yayinda shi kuma idanunsa ke kan Kawu, kallon mamaki da tsantsar farin ciki
yake binsa da shi.
A gefenta kuwa halittar fuskarsa take Ζarewa kallo. Eh,
tabbas suna kama, fuskarsa doguwa kuma siririya irin nata, yana da dogon hanci
masha Allah, sai kuwa bakinsa daidai. Idanunsa manya kamar naya hatta da cikar
halittar girarsa da gashin kai, duk kuwa da cewa shi nasa gashin ya yi fari fat
na manyanta amma kamanninsu da shi sun fito fes har tsawon. Ba ta Ζara gani ba
sai da ya saki dariyar farin ciki, anan kuma baki hangame ta ce.
"Kai!" Ta furta a fili ba tare da ta shirya ba. Gaba daya suka juyo
su na dubanta. Ta kama bakinta da sauri
gami da Ζara sunkuyar da kai, mutumin ya matso ya durΖusa a gabanta, zuciyarsa
ta yi wani irin nauyi, abubuwa da dama suka shuΙe a tsawon shekarun baya suka
dawo mishi sabo fil. Ita kuwa kunya ce ta kama ta, bata ma gaida shi ba, ta
gaishe shi a hankali don a zaton ta ma
bai ji ba, amma ga mamakinta ya amsa.
"Barka da zuwa Mamana. Ki saki jikinki nan gidanku ne,
gidan Abbanki, ba ki da inda ya fi nan kinji ko?"
Da ya fadi haka wai sai ta kalli Kawu, hakan da tayi ya ba
su dariya. Kawu ya gyaΙamata kai.
"Idan eh kike so nace ko aa, toh eh Shatu, gidan
mahaifinki kenan. Abin tunΖahonki."
Ta yi murmushi tana kara duban wanda ya kira kansa da
Abbanta, sai nan da nan kwalla ta cikamata idanu. Wannan fargabar ta kau, so da
kaunar suka dawo daga hutun da suka je, ta rungume hannunsa ta saki kuka sosai.
Abubuwa da dama take tunawa, tabbas ta yi kewarsa a rayuwa. Koda ace ba ta rasa
ci, sha da sutura ba daidai da kwana Ιaya a rayuwa, to ta rasa wannan kusancin
na Ιa da mahaifi, shi din na dabanne. Ko ma dai tace ta rasa soyayyar iyaye
gaba Ιaya.
"Kiyi hakuri Mamana, ba zan Ζara yin nesa da ke ba,
wancan ma Ζaddara ne, amma wannan karon in sha Allahu ni da kaina zan miΖa ki Ιakin
mijinki. Allah ya ji Ζan Mahaifiyarki da Hajiya Dada."
Suka amsa da amin. Nan kuma ya shiga jan ta da hira kadan
har ta sake, waya ya zaro a aljihu ya danna kira, sunan wata ya ambata, Ummita,
ya ce ta zo yanzu. Daga haka ya juya ga Kawu suka yi ta hira yana ba shi
labarin rashin lafiyar Dada har zuwa rasuwarta. Suna nan zaune ita kam ta kasa Ιquke
ido akan Abban, suka tsinkayi sallamar wata Ζ΄ar budurwa da ba ta wuce sa'arta
ba. BaΖa ce, irin baΖin da hutu ya ratsa, riga da wando ne a jikinta sai dai ba
su Ιame ta ba, ta saka hijabi iyaka kafaΙarta. Ta gaida Kawu sannan ta maida
hankali ga Abba.
"Yauwa Ummita, kama hannun Ζ΄ar uwarki ku je a ba ta
abinci ta ci ta yi wanka. Ki kuma faΙawa Maminki ina da baΖo a shirya masa
abinci kafin mu yi sallah. A kawo ruwan sha."
Ummita ta amsa da toh tana kallonta fuskarta a sake ta
ce.
"Lah Abba wallahi kuna kama sosai."
Duk sai ta ba su dariya, Abba ya dubi Aisha Humaira kafin ya
maida duba gareta.
"Itama Ζ΄ata ce, ita ce mai sunan Umma."
"Abba ita ce wacce ka ce tana Nijar ko?" Wannan
karon da wani irin zumuΙi ta yi tambayar. Ya amsa mata da eh. Ta kuwa karaso da
sauri ba tare da nuna kyankyamin komai ba ta rungumeta tana fadin.
"Welcome Sister." Ba ta gane me ta ce ba amma itama ta rungumeta tana
mai jin kaunarta har can Ζasan ruhinta.
Ummita kenan, tana daga cikin mutane masu girma da
matsayi sosai a rayuwar Humaira, har abada Humaira ba za ta cire ta a tarihin
rayuwarta ba, ta karΙe ta a yadda take, Ζ΄ar kauyen Maine. Ζamshi take a yayinda
ita kuwa ba ta ma sani ba, Ζarnin kifin da ta ci a mota take yi ko kuma naman
da ta ci ne. Kai ko ma mene ne, ta sani Ummita ba ta irin wannan Ζarnin, Ζamshi
ne a jikinta, amma ba ta duba komai ba ta rungumeta. Ta tabbata tana daga cikin
masoyanta na haΖiΖa. Ta kama hannunta Ιayan hannun kuma ta Ιauki akwatin
kayanta wanda duk ya ci gidansu, akwati ne irin na da da aka yi yayinsa, Dada
ta ce nata akwatin tun na auren Mamanta ne.
Suka nufi wata Ζ΄ar siririyar hanya suka fito wurin
wani Ζaramin hanya nan ma gefensa duk shuke shuke. Wurin ya burge Aisha Humaira
sosai, a daidai Ζofar shiga wajen ma, shukoki ne sun kewaye jikin Ζofar da
bango sun ba da zane mai kyau. Ummita ta ci gaba da tafiya har suka nufi wani Ιangaren,
baranda ne sai kuwa wata Ζofa, suka shiga Ummita ta shiga kwala ihun kira.
"Mami! Mami!! Fito ki gani!"
Ihun da take tana kira ya sa sauran mutanen dakin suka fito.
Maza da mata wadanda sun Ιan girme ta sai ko yara.
"Wai Ummita me ke damunki haka? Tun Ιazu bakinki ya
Ζi..."
Aisha Humaira ta lura haΙa idanun da suka yi ne ya sa sauran
kalaman bakin matar suka maΖale. Kallonta take kamar a razane, ita kuwa kallonta take tana so ta ga ta inda suka
yi kama da Ummita don ko kaΙan ba su yi kama ba. Ummita baΖa ce, wannan kuwa ta
tsaye a gabanta da alama ma buzuwa ce. Gashinta a tufke a baya, ta kai duba ga
wasu a cikin yaran, su ma farare ne Ζal, kyawawa da su.
"Wace ce wannan?"
Ζaya daga cikin Ζ΄anmatan ta tambaya tana bin Aisha Humaira
da kallon tara saura. Ummita ta yi dariya ta jawota ta rungumo kafaΙarta.
"Mami, mai sunan Umma ce ta zo daga Nijar, Aisha
Humaira. Abba ya ce shikenan ta dawo nan da zama cikinmu."
Wacce aka kira da Mami, ta tamke fuska babu ko Ιigon
annuri, suka kalli juna a kar na biyu.
Kallon da ya da ya sa Aisha Humaira ta ji hantar cikinta ta kaΙa, dariyar
matasan ne ya sa ta maida idanu kansu.
"Wai! Ni da yagwalgwal, amma wannan ma a Nijar Ιin a
can Ζauyen kike ko?"
Ζaya a cikin matasan ya furta yana dubanta, idanunta nan da
nan suka cicciko da kwalla.
"Kai Yassar, bana son haka. Sannu da zuwa Humaira, maza
Ummita kai ta Ιakinku ta yi wanka lokacin sallah ya gabato."
Da sauri na kalli matarnan, na sha mamaki ganin kamar ba ita
ba, ta saki fuska sosai tana murmushi har haΖorin makkanta ana gani. Har Ummita
ta faΙi saΖon Abba, Humaira ba ta iya tankawa ba hakanan ba ta iya Ιauke idanu
daga kanta ba, itama jefi-jefi tana magana da Ummita tana kallonta ta kuma rasa
dalili. Har Humaira ta bi bayan Ummita zuwa Ιaki ba ta daina waigenta ba, kuma
itama Mami ta Ζi matsawa balle ta dauke ido a kanta. Ita kam Humaira jikinta ya ba ta kamar akwai wani abu.
A hankali ta bi
kowace kusurwa a Ιakin da ido, gado ne kananu har hudu kowanne a nashi wurin, a
gefen kowane gado akwai sif na kaya kamar dai Ιakunan makarantun kwana, babban
daki ne mai yalwa wanda har akwai gurbin da ire-iren gadon uku za su samu
matsuguni. Daga can gefe jikin taga kuwa, Ζaton madubi ne a saman dirowar gaban
cike da kayayyakin kyalkyali na adon fuska da mayuka. Dakin tsaf-tsaf babu
Ζazanta, Ιakin Ζ΄anmata kenan. Ummita ta Ιaga akwatin tana shirin ajiyewa saman Ιaya
daga cikin gadajen nan, baki bude tana kallon Humaira da niyyar magana, aka
daka mata wani uban tsawa daga baya.
Muka juyo, wannan dai budurwar ce ta Ιazu mai Ζibar ciki. Ta
zo da sauri ta janye akwatin ta yi wurgi da shi gefe. Idanu cike da masifa ta
soma magana.
"Wallahi kar ki kara gangancin ajiyemin
jakar wannan korar yunwar a gadona, don gulma da kinibibi idan abin naki
dagaske ne meyasa ba za ki ajiye a naki gadon ba. Aikin banza kawai, uwar
shishshigi. Haka za ki Ζare."
Tana kai wa nan ta fice daga Ιakin tana mita,
Ummita ta kalli Humaira gami da jifanta da murmushin yaΖe.
"Ki yi haΖuri."
Ta gyaΙa mata kai tana maida mata martanin murmushin sai dai
can Ζasan ranta, tana maimaita kalmar da ta ambata "Korar Yunwa". Ta
fahimci manufarta tsaf, ta kuma gane ko wace ce ba ta samu karΙuwa a wajenta
ba. Koda dai, ba ma ita kaΙai ba, ta lura da irin kallon da Mami ta watsamata.
Ko ya zamantakewarta a wannan sabuwar duniyar za ya kasance?
"Hey, tunanin me kike? Amm..nidai bari kawai na kiraki
da Humaira, kinga babu damar ce maki Aisha kai tsaye saboda sunan Umman Abbanmu
kika ci ko? Hakan ya yi?"
Humaira ta gyaΙa kai karo na biyu tana mai sakin fuska, ta
lura Ummita akwai kirki. Bandaki ta nuna mata, ita kuwa ta yi
godiya, har za ta shige ta dakatar da ita.
"Yauwa Humaira ga wannan zanin ki yi amfani da shi ki
goge jiki."
Ta sa hannu ta karΙa, zani ne a wanke a goge. Ummita har ta
kama hanyar fita sai kuma ta dawo ta shiga bandakin gami da ba ta umarnin ta bi
bayanta. Su na shiga ta kunna mata famfo gami da faΙin amfanin kowannensu. Ta
fiddo mata sabon sabulun wanka daga cikin wata Ζ΄ar kwaba dake a gefe jikin
bangon, sai kuma ta tambayeta ko ta taho da soso, Humaira ta amsa da eh. Hatta
da Ζofar banΙakin sai da Ummita ta nuna mata yadda za ta Ζulle kuma ta buΙe,
daga haka suka fito, nan ma sai da ta ajiye mata dardumar sallah saitin gabas
sannan ta fice ita kuma ta ciro sosonta a akwti ta koma banΙakin ta rufe.
Wanka ta yi gaba Ιaya ta Ιauro alwalar Magriba, koda ta fito
wannan budurwar ta Ιazu tana zaune gefen gadonta tana waya, suna haΙa ido ta
bita da harara ba shiri Humaira ta kauda kai. Idanunta ya kai ga akwatin
kayanta, Ζarasawa ta yi ta buΙe sai dai gaba Ιaya ba'a nutse take ba sakamakon
idanun wannan budurwar a kanta suke duk kuwa da wayar da take amsawa. Turanci
zallah take zubawa har wani shagwaΙa take yi tana dukan gadon, kalmar I Lobiyun
da ta ce yasa Humaira ta fahimci koma dai wane ne toh masoyinta ne. Ba ta ko
Ζara kallonta ba gudun ganin abin da zai sosa zuciya, ta fiddo doguwar rigarta
ta yadi ta warware ta zura. A gurguje ta ciro hijabinta, ta linke kayan da na
cire na ajiye daga saman akwatin. Ba ta jima da tada salla ba sauran Ζ΄anmatan
nan biyu suka shigo suka cika Ιakin da hayaniya, rabin hirar tasu da harshen
turanci suke yi. Koda ta idar ba ta iya nutsuwar jan addu'a mai tsawo ba, ta yi
istigfari da hailala da salati ta shafa. Zama ta cigaba da yi anan ba tare da
ta miΖe ba gudun ma kar ta yi wani abin ya jazamata baΖar magana. Hankalinta
yana ga Abbanta wanda take da tambayoyi birjik da za ta yi mishi a
kwakwalwarta. Eh yana sonta yana Ζaunarta, amma meyasa bai Ζara waiwayarta ba,
meyasa ba ta taΙa ganinsa ba? Meyasa kuma koda a waya bai kira domin su gaisa
ba? Dukkan wannan rashin kulawar nasa da ba ta samu ba, ace yana kaunarta ya
kuma damu da itq? Ita kam tana son sanin amsar da zai fito daga bakinsa.
"Ke Indo."
Ta Ιaga kai ta dube su kawa, suka kwashe da dariya.
"Kai Raihana ba ki da kirki wallahi, au ba ma za ki
kirata Humairar ba sai Indo ko?"
Wacce aka kira da Raihana ta yamutse fuska.
"Aa, ina ce sunan Umma gareta, tunda kaka ce ai ko
Indon ma da na ce ta gode min. Ku ni ba wannan ba, wallahi mu tashi mu yi
magana fa tun kan a ΖaΖaba mana ita a Ιakinnan. Ni wallahi tsoro ma take
ban. Mu faΙawa Granny ta yiwa Abba magana don Mami ba za ta goyi bayanmu
ba."
Humaira ta kalle ta dakyau, doguwa ce kamar dai Abba, don ta
fi Maminsu tsawo, Mamin ba ta da tsawo sai jiki kuma gajeriya ce. Fara ce
tas itama kalar buzayen, gashinta da ya sha kalba ya sauka har gadon bayanta,
riga doguwa ce Ζ΄ar kanti ta sa mai kama jiki.
"Kallon me kike yimin kamar wata mayya? Kar ki ji ance
wai wani ke Ζ΄ar Abbanmu ce ki yi ΖoΖarin haΙa kanmu da ke, wallahi kar ki
kuskura don bakin rijiya ba wajen wasan yaro ba ne, atoh. Gwara ma Abban ya zo
a yi meeting Ιin a bambance tsakanin aya da tsakuwa."
Duka wannan bayanin daga bakin Raihana su ke fitowa, Humaira
ta sauke idanunta a hankali zuciyarta na zafi, dagasken dai ba ta samu karΙuwar
kenan ba, zuciyarta na da Ζarfin jure abu idan har wanda ya fi ta a shekaru ne
ya aikata gareta, amma ba ta jin za ta iya Ιaukar wannan rainin wayon.
"Futuha mene ne haka wai? Meyasa kullum burinku ku
tozarta mutum?"
Maganar Ummita ya sanya Humaira Ιago kai, ashe wai akwatinta
wacce aka kira Futuha ta nufa ta buΙe. Ita dai wacce ke faman waya tun Ιazun.
Ai kuwa kamar an mintsile ta haka ta miΖe tsaye a zafafe, ta
Ζarasa daidai sadda Futuha ta Ιaga akwatin da niyyar doka shi da Ζas, da wani
irin zafin nama ta ture ta, daga ita har akwatin suka faΙi, akwatin ya faΙa
saman gado, ita kuwa ta yi rashe-rashe a Ζasan gadon bayan Ζugunta ya
bugi katakon. Ai kuwa ta kurma ihu, Raihana da Ιaya budurwar da
Ummita ta ambata da Tasleem suka yo kai Humaira gadan-gadan, Ummita ta tare su.
Ita kuwa Humaira ko a jikinta ta nufi akwatin ta shiga harhaΙa kayan da
suka zube tana maidawa lokaci Ιaya hawayen da ta fi zaton na Ιacin rai ne, su
na kwaranya. Ya yi daidai da faΙowar Maminsu Ιakin wanda hakan bai wuce
sanadiyyar ihun Futuha da ya mamaye ilahirin Ιakin ba. Jin muryarta da ta yi
sai da gabanta ya faΙi, ta rasa dalilin da yasa take jin haka a kanta. Ta shiga
ambaton sunan Allah a Ζasan ranta.
"Lafiya? Me nake gani haka kamar waΙanda aka
Ζwato daga bakin kura? Ke Ummita sake ta, kyale su na ga gudun ruwansu. Au, don
ku nuna mata rashin tarbiyyarku ba komai ba ne ba ko? Har kun soma yada
halin?"
Tana maganar ne fuskarta a murtuke tana bin su da kallo Ιaya
bayan Ιaya, ita dai Humaira sam ba ta tofa ba sai ci gaba da tsince kayanta da
tayi tana harhaΙawa tana mayarwa ciki. Ba ta san ma'anar juya harshe zuwa wani
can daban da ba ta sani ba, ta dai ji Mamin a cikin yare ta yi musu magana
wanda ba ta fahimci koda harafi guda a ciki ba, sai gani kawai ta yi duka sun
fice daga Ιakin idan ka cire Ummita da ta durkusa tana taya ta haΙi da Ζara ba
ta haΖuri. Tana niyyar amsawa Ummita ta ji an shafa kanta, ta runtse
idanu ba tare da ta Ιago kai ba don tasan Mami ce.
"Ki yi hakuri kin ji Humaira, su Tasleem su na da irin
wannan halayyar na son yiwa baΖo shaΖiyanci. Kinga yau ki ka zo kuma kafin su
karΙe ki za'a Ιan kwana biyu, a hankali idan sun gane ke Ιin Ιaya ce a cikinsu
komai zai wuce kin ji ko? Ki Ιauke ni madadin Uwa, don mahaifiyarki mun yi
zaman mutunci da nutunta juna da ita. Kema kuma nasan muddin dai kyawawan Ιabi'unta
kika kwaso, ba za mu samu kowace iriyar matsala ba. Ina fatan haka?"
Jin bayanan Mamin sai ta tsinci zuciyarta da yin sanyi, ta
ji lokaci guda kaso saba'in na fargabarta akan Mami ya ragu, wannan furuci nata
na madadin Uwa, ba ta jin za ta iya kwatanta daΙin da ya sanya ta. Kai ta gyaΙa
alamar toh, Mamin ta maida dubanta ga Ummita.
"Sai ku hanzarta ku fito ta ci abinci daga nan zuwa
bayan sallar isha'i, Abbanku na neman mu duka."
"Toh Mami." FaΙin Ummita cike da girmamawa. Daga
haka ta fice ta bar mu. Ummita ta kalli Humaira da murmushi saman fuskarta.
"Sai fa kin yi hakuri sosai Humaira, da gaskiyar Mami,
dama ya lafiyar giwa balle an jefe ta da kashi. Su Tasleem ba su da kirki, har
gwara su Yassar a kansu, don su ba su kunyar ido, za su yi maka abin da suka
so. Ki yi hakuri don Allah. Nima haka nake fama da su, don ma dai babu yadda
suka iya da ni ne, Mamin na taka musu burki sosai a kaina."
Jin haka ta ji ta sosamata inda yake mata ΖaiΖaiyi. Aikuwa
ta kasa shiru sai da ta furzar.
"Yauwa nikam Ummita, amma ba Mami ce ta haifeki ba
ko?"
Ummita ta yi dariya.
"Kin gan ni Ζ΄ar baΖa ko?"
Sai kuma ta gyaΙa kai ta Ιan sauya fuska alamar damuwa.
"Ba Mami ce ta haife ni ba kuma ba Abba ne mahaifina
ba. Mahaifina Ζanin Abba ne, mahaifiyata kuwa Ζ΄ar asalin garin Bichi ce, gaba Ιaya
sun rasu ne a sanadiyyar gobara. Ni kaΙai ce rai da aka fitar a gidanmu ko
kwarzane tun ina da shekaru biyar a duniya, amma daga su har Ζannena jarirai
Ζ΄an biyu duka sun rasu. Tun daga wannan lokacin ne, na soma rayuwa a hannun
Kakarmu sai daga baya ne Abba ya maido ni gidansa ya damΖa amanata ga Mami.
Matar da ta riΖe ni har zuwa yau ba tare da ta nuna bambanci tsakanina da nata
yaran ba, kusan ince a zamanin dai samun irin Mami abu ne mai wahala. Ga kirki
da son mutane, ke ba don dai kar nayi hauka ba zan iya ce maki Mami ta fi
nunamin Ζauna da so fiye da nata yaran domin hatta da ragamar kula da Ιakinta
da na Anna ni ta damΖawa. Ke daidai da shawara wani lokacin da ni take yi. Sai
ta ture shawarar nata yaran ta Ιauki nawa."
Jinjina kai Humaira ta yi, eh lallai kam Mami ta yi abin a
yaba mata, a zamanin nan kafin a samu mai fifita Ιan wani akan nashi abu ne mai
matuΖar wahala.
"Wace ce Anna?"
Humaira ta watsa mata tambayar. Ta miΖe ta shiga rufe
akwatin a lokaci guda tana ba ta amsa.
"Anna kakar su Tasleem, wacce ta haifi Mami. Ai
anan gidan take rayuwa, a baya ma har da Ζanwar Mami da ba ta yi aure ba muka
zauna. Amma yanzu Allah ya taimaka tayi aure tana zaune a can Misra da mijinta,
ke kam ai Allah ya taimake ki ba za ki rayu inuwa Ιaya da ita ba. Don ta fi su
Tasleem zafi da tsangwama, ke ta dai tsani duk wanda ba jininsu ba. Hatta da
dangin Abba ba ta kaunar gani a gidannan, sai kuma Allah ya sa su Ιin ma ba su
fiye zuwa ba."
Humaira ta buΙe baki za ta yi magana kenan sai ga wani
Ζaramin yaro cikin yara Ζananu uku da ta gani Ιazun ya shigo a guje. Masha
Allah yaron kyakkyawa duk kuwa da cewar bai Ιau hasken Mamin sosai ba, ya fi
yin kalar Abba, amma kuma hakan ma sai ya Ζara mishi wani kyan na daban.
"Adda Ummi ku zo inji Mami."
Ya kai Ζarshe yana nuna su duka biyum da yatsa, alamun dai
mu biyun ake nema. Sai ma ya ba Humaira dariya. Suka miΖe a tare zuwa falon. Ko
Ιaya ba abokan faΙan nata a ciki, bada Ιayansu ba sa nan sai Mami da yaran, sai
kuwa Ιaya a cikin matasan nan na Ιazu kwance saman doguwar kujera ya toshe
kunnuwa da earpiece.
Suka Ζarasa ga Mamin, ta zauna a gefe a Ζasa. Duk yadda
Mamin ta so ta hau kujerar ta Ζi, haka dole ta rabu da ita. Ummita ta kawomata
abincin amma gaba Ιaya ta kasa sakewa balle ta ci, Ζarshe dole dai Ιakin suka
yi da abincin bisa umarnin Mami. Nan din ma dai kaΙan ta ci ta ce ta Ζoshi.
Hankalinta kuma ya koma ga Kawu da Abba, ba ta gaji da ganin Abba ba, ba ta
kuma gaji da jin muryarsa ba. So take ta samu damar da za su yi doguwar hira da
shi, tasan dai ba yau ba domin dare ya yi.
Suna nan da Ummita tana Ζara ba ta labari akan zuri'arsu har
lokacin sallar isha'i ya yi, koda suka idar kai tsaye falon Abba suka nufa
sakamakon kiran da ya yi musu. Nan suka tarar shima Kawu har ya ci abinci ya yi
wanka, hirarsu kawai suke yi da Abba wanda shima ya sha doguwar jallabiya ruwan
madara. Har Humaira ta zauna kallonta yake da murmushi saman fuskarsa kafin ya
maida duba ga Kawu ya girgiza kai.
"Allahu Mai Halitta." Kawun shima murmusawar ya
yi, ita kam sai ta yi kasa da kai. Zamansu ba jimawa sai ga Mami ta shigo ta
lulluΙe jikinta da Ζaton mayafi. Sai da ta zauna ne ta dubi Kawu.
"Umar, kwana da yawa. Idan babu Fatima a
gidan shikenan kuma sai zumunci ya yanke? Dama kun raba ni da Ιiyata, toh dama
Ζarshen alewa Ζasa, ka ga yau dai ungulu ta komo gidanta na tsamiya."
Kawu ya yi Ζ΄ar dariya.
"Hajiya Maryam kenan, idan dai kin yarda kin amince da
komai lokaci ne, ba za ki ga laifinmu ba. Sai dai kamar yadda kika ce, na yi
kuskure kuma na ji kunya da ban tashi zuwa ba sai bayan babu Adda Fatima, Allah
ya gafartamusu. Ina kuma neman afuwa."
Gaba daya suka amsa da amin. Abba ya yi gyaran murya
ya dubi Mami.
"Ina yaran nan suka shiga ne wai?"
"Su na can wurin Anna, na rasa me suke yi alhalin na
sanar da su. Bar..."
Ba ta Ζarasa ba sai ga su sun faΙo Ιakin kamar daga sama,
babu Ιaya cikinsu da ya yi tunanin yin sallama. Yaron Ιazu ne da ya je kiranmu
ya shigo a guje ya rungume kafaΙun Abba, wani da ya fi shi tasawa yana biye da
shi a gujen. Sai kuwa su Tasleem da samarin nan uku.
"Kai Muhsin, me ya yi maka ne?"
Wanda aka kira Muhsin ya turo baki ya nunawa Abba bindigar
ruwa da aka raba gida biyu.
"Ba shi ne ya karyamin bindiga ba. Allah kuwa sai ya
biya ni."
Abba ya ja hannun karamin mai suna Waleed ya maido shi
gabansa.
"Haba Autan Mami, ya haka? Ba shi hakuri toh."
Da dariya irin na yarinta ya furta kalmar sorry. Abba ya
maida idanunsa ga su Tasleem waΙanda suka yi Ιare-Ιare saman kujera ba su ko
gaisar da Kawu ba. Fuska ya Ιan Ιaure.
"Ba ku iya gaisuwa ba ne?"
Jin furucin Abban ya sa suja gaida Kawu ciki-ciki, ba tare
da jin komai ba ya amsa har da nema musu albarkar Allah. Babu wanda ya
amsa da amin a cikinsu. Mami ta kalle su ta yi musu alamar su sauko Ζasa su
zauna, ba a son ransu ba dole suka zaune a Ζasan kafet kamar dai yadda Humaira
da Ummita suka yi. Sai dai Abba ya buΙe taron nasu da addu'a sannan ya gabatar
da Humaira a wajensa. Ya kuma gargaΙe su da kar su kuskura ya ji wani zance na
daban koda nuna bambanci ne. A karshe ya sa kowannensu ya gabatarwa da Humaira
sunansa. Su tara ne cif, Mubarak ne babban Ιan Abban, shi kuwa yana Ζasar Ghana
yana karatu, sai Dawud, Yassar, Ζasim, Futuha, Tasleem, Raihana, Muhsin da
autansu Usman da ya ci sunan baban Mami suke kiransa Waleed.
"Humaira toh,
yanzu dai ba wanda ba ki sani a Ζ΄an uwanki ba ko? Sai babban yayanku shi kam
sai ranar da ya samu hutu idan ya dawo sai ku gaisa. Ko kuma ma ina iya haΙa ku
a waya wataran."
Jin abinda ya fadi ya
sa ta murmushi, ta gyaΙa kai tare da furta toh. Daga haka Abba ya sallame su baki Ιaya suka tashi.
A wannan daren dai
ba ta samu damar hira da Abbanta ba, ta koma Ιakin da ba ta kauna dalilin yadda
suka kaya da masu Ιakin. Mami ta sa aka yi mata shimfiΙar katifa a Ζasa kafin
nata gadon da sif ya iso, acewarta.
Hakanan ta kwanta, mutanen ba su Ζara tanka mata ba musamman ma Futuha
da ta sha Ζasa har lokacin Ζugunta na ciwo. Sun dai sha jinin jikinsu, sun kuma fahimci Humairar ba kanwar
lasa ce ba itama.
***
Washegari tun da
asuba ta ga Ζ΄anmatan ba su koma bacci ba, ita daman baccin safe ba ya daga
cikin Ιabi'unta, a can Ζauyensu daga sun tashi to sannan za'a hau Ιora ruwan
wanka da kuma abin kari, wannan dalilin yasa ta kwanta kawai tana kalle-kalle
da saΖe-saΖen zuci. Tana kallo suka yi wanka har Ummita, kowannensu ya hau
shiri. Ummita da Raihana cikin shigar uniform na makaranta, ita kuwa Tasleem
shigar fararen kaya ta yi na ma'aikatan asibiti riga da wando da Ιan Ζaramin
hijab. Sun mata kyau kwarai, gogar kuwa, wato Futuha, kayan gida ne jikinta,
riga doguwa ta atamfa da ya Ιame ta Ιam ya fiddo da surarta.
"Wai ke Futuha
ni ban gane ba, ina mamakin yadda kike rawar Ζafa da jiki duk sadda aka ce kuna
da English, ko uban me yasa oho." FaΙin Tasleem kenan sa'ilin da take Ιora
agogo a tsintsiyar hannunta. Kafin Futuha ta yi magana, Raihana dake fesa
turare a jikin uniform dinta wanda iri Ιaya ne da na Ummita, kalar fari da
ruwan makuna dinkin riga da wando sai Ιan hijab da ya rufe kirji kaΙan, dariya
ta yi ta amsa wa Tasleem.
"Wai ke ba ki
da labarin IBB Gusau? Tab, ai kusan kaf
matan department dinsu sonsa suke ban ciremaki matan aure ba, toh itama har da
ita a ciki, ba ki ganin kwalliyar ta
daban ce."
Futuha ta jefowa Raihana murfin man shafawa, Raihana ta
kauce tana dariya.
"Af, akwai Ζarya cikin maganata ne? Ke fa naji kuna
hirar da wannan Ζawartaki me wuya kamar mariΖin lema, ni me ma sunanta? Yauwa
Khalisat, kina wani koΙa shi kina cewa nan duniya shi kike so."
A fusace Futuha ta nufo ta, Raihana ta sunkuci jakar
makarantarta da waya a gefen gado ta fice daga dakin da sauri tana dariya.
Itama Tasleem dariyar ta yi.
Ummita kam dama ta
fice daga dakin tun da ta zura uniform, dakin su Muhsin ta wuce don yi musu
shirin makaranta.
Humaira lumshe
idanunta ta yi tana ji suna faman hira tsakanin Tasleem da Futuha inda Futuha
ke kara jaddada dagasken dai tana son Ibb Gusau.
"Ke malamin fa
Ζarshe ne wallahi, ya haΙu ba zan nuna masa komai ba. Nidai fatana Allah yasa
ya karΙi tayina ya aure ni. Wallahi zan jure dukkan wulakanci muddin zai yarda
ya so ni. Yau in sha Allahu sai na nemo lambar wayarsa."
"Lallai, kina
ruwa kusa da breaker." Cewar Tasleem.
Fuska dauke da damuwa Futuha ta amsa.
"Ai na yi nisa ma cikin ruwan Tasleem, ki dai yi fatan
kar Allah ya jarabceki irin yadda ya jarabtan."
Tasleem cike da
mamaki ta ce.
"To tsaya, don iskanci kwanakin nan da wa kike waya
kike kashe murya kina furta kalaman so?"
Yamutsa fuska Futuha ta yi.
"Mujahid ne, wallahi akan dole nake kula shi, shi ke fa
taya ni da attendance da ma test. Kinga
kuwa dole ce ta haifar da shiga lamarinsa. Ζan taya ni na ci jarrabawa
ne."
Suka sheΖe da dariya. Ba jimawa suka fice zuwa falo.
Ita Tasleem nursing
take karanta duk ta fi su kwakwalwa da basira, tana da kokari sosai shiyasa
wasu lokutan take samun alfarma daga Abba koda zai yi hukunci ba ya tsaurara
mata, yayinda ita kuwa Futuha ke karantar Mass Com, ba laifi tana da kokari sai
dai matsalar tun zuwan wani matashin malaminsu makarantar ta susuce ta zama
shiritacciya. Wannan yasa lokaci guda ta kwaso C.O a zango na biyu a aji na
biyu a makaranta, hakan ba Ζaramin Ιata ran Abba ya yi ba. Shi mutum ne da ya
tsani asarar kwandalarsa a abinda ba zai kawo mishi ribar komai ba sai asara,
hakanan mutum ne mai son abin hannunsa sosai, dakyar Mami ta shawo kansa ya
aminta da tura Mubarak karatu, ya kuma
ce daga kansa ya rufe, sauran kowanennsu sai dai ya yi a jami'o'in Kasarnan.
Dawud na ajin karshe a jami'a inda yake karantar Accounting,
Yassar wanda tare suke tafiya da Dawud din adalilin maimaicin aji da Dawud ya
yi a sakandire, shi kam Bussiness ya ke karanta, su biyun tare suke da Futuha a
jami'ar Bayero. Sai Ζasim dake karantar fannin Kasuwancin shima dai inda yake
aji na uku a jami'ar Maitama Sule Kano.
Wannan kenan.
Humaira jin Ιakin ya yi shiru ta buΙe idanunta, ajiyar
zuciya ta saki tana mai jinjina wannan rayuwa ta Futuha, shakka babu ta Ιorawa
kanta wahala, koda dai faΙan da ba ruwanka, daΙin kallo gareshi. Mikewa ta yi
ta nufi banΙakin bayan ta Ιauki zanin wankanta da brush. Sai da ta wanke
jikinta tsaf kafin ta fito ta soma shiri cikin doguwar rigarta Ζ΄ar kanti ruwan
madara, tana daga cikin suturun da Kawunta ke siyamata. A dai fannin sutura
daidai gwargwado itama tana da su, sai dai ace ba wasu masu tsada ba ne, ba
kuma masu kyawun gaske ba ne idan an haΙa da na su Tasleem da ta gansu a
jikinsu a kwana Ιayan nan. Tana cikin kwashe shimfiΙarta sai ga Ummita ta shigo
da sauri, ganinta ta saki fuska sosai.
"Au Humaira ashe kin tashi, kinga mu ma makaranta za mu
wuce. Mami tace idan kin kammala ga abin kari can an rufemaki a kicin, idan ma
ba ki gani ba ki tambayi Ladidi mai aikin Mami tana falon tana gyara."
Duka wannan zancen tana yi ne lokaci guda da sauri tana
bincike dirowarta, littafi ta zaro ta dauki jakar makarantarta sai safarta a
hannu da takalmi ta kama hanyar fita.
"Toh, sai kun dawo."
FaΙin Humaira, Ummita ta amsa ba tare da ta tsaya ba
sakamakon hon din mota da ake faman dannawa. Ganin haka yasa Humaira Ζarasawa
jikin windon wanda ake iya hango farfajiyar gidan, ganinsu tayi gaba Ιaya a
motar sai Tasleem dake tsaye a waje rike da Ζugu, Ummita na karasawa ta hau ta
da masifar wai tana Ιata musu lokaci.
"Allah ya baku
hakuri."
Ta ji Ummitan ta fadi sannan ta shige motar da sauri, tsaki
Tasleem ta ja ta bita da harara sannan itama ta faΙa ciki, direban ya ja suka
fice. Ajiyar Zuciya Humaira ta saki ta bar jikin windon, mamaki fal a ranta na Ιabi'un
Ζ΄an matan. Ta lura ba su san wani abu wai shi kara da mutunci ba, haka dai ta
ture zancensu ta hau gyaran Ιakin. Abin ban haushi a saman gadon Futuha daidai
da Ιan kamfenta da ta cire anan ta bar shi a ajiye, aikuwa haka ta tsallake
gadon, ba ta yi karambanin gyara musu gadajensu ba, da ace dai Ummita ba ta
gyara nata ba to tabbas wannan kam za ta gyara mata, ita din mutum ce mai
mutunta DAN ADAM.
Fita waje ta yi,
falon babu kowa hakan yasa ta nufi hanyar kicin da ta nakalceshi tun jiya da
Ummita ta tattara kwanukan abinci ta nufi ciki. Anan ta iske wata mata da ba za ta girmi Mami ba tsaye tana
goge gas nan ta fahimci ita ce Ladidi.
Ta gaisheta a ladabce, matar ta amsa fuska a sake.
"BaΖuwarmu
Humaira ko? Sannunki da zuwa, ga abin karinki can."
Ta fadi tana nuna mata wani tireda aka Ιora filet da kofi
sai kayan shayi da flask a kai. Humaira
ta murmusa.
"Nagode, amma zan sharo dakin sannan na ci."
"Ai da kin bar shi, idan na kammala da nan sai na
share."
Girgiza kai Humaira ta yi.
"Babu komai kar ki damu zan yi ai ba wani girma ne da
dakin ba."
Ladidi ta amsa da toh gami da yi mata sannu. Tsintsiyar ta
nunamata da makwashin shara, ta dauka ta nufi dakin. Sai da ta kammala tas
kafin ta koma ta wanke hannu ta dauki abin karin ta koma daki don ba ta jin za
ta iya ci a falon. Bayan ta kammala ne ta fito da niyyar maida kayan kicin suka
yi karo da Ladidi.
"Yauwa, ki je inji Alhaji wai za ku yi sallama da
Kawunki zai wuce."
Ladidi ta karΙi kayan hannunta ita kuwa jin haka jikinta ya
yi sanyi, ta koma dakin ta dauki karamin mayafinta ta yafa a kai. Falon Abban
ta nufa, Kawun ne kadai a ciki ya yi shiri tsaf na tafiya, sallamarta ya sanya
shi dubanta. Ta durΖusa ta gaida shi, ya
amsa sannan ya ce.
"Toh Shatu, ni zan koma. Ina fatan zaman nan zai maki
dadi fiye da rayuwar da kika yi a Maine. Ina kuma roΖonki da ki zauna da kowa
lafiya, kamar yadda suka karΙeki da hannu bibbiyu, kema ina son ki rike su
haka. Gidan mahaifinki ne, nan Ιin dai shi ne gatanki, ba ki da sama da nan.
Sannan don Allah ki zama mai hakuri, na sanki sarai muddin aka taΙo ki ba
kya kai zuciyarki nesa. Abu na gaba, kar ki sake ki bada kofar da za'a ga
wallenmu, a ga kamar mun gaza a wurin ba ki kyakkyawan tarbiyya a iyaka zaman da
kika yi hannunmu. Sannan addu'a, ki yawaita addu'a da ibada in sha Allah sun
ishe ki."
Humaira wacce tuni fuskarta ta yi jage-jage da ruwan hawaye
ta sa hannu ta share su. Gani take yi tamkar shikenan fa za ta yi nesa da
asalin garin da aka haifeta, shi kenan ganin Kawu da Tanti Hafsatu
matarsa zai yi wuya a gareta. "Nagode Kawu, in sha Allahu zan kiyaye
abin da ka ce. Amma ai Abba zai dinga bari na naje maku wataran ko?"
"Me zai hana na
bar ki Mamana?"
Jin maganarsa gaba daya suka dub shi, sam ba su san ya shigo
falon ba balle kuma tsayuwar da ya yi a bakin Ζofar da za ta sada shi da
sashinsa na ainahi. Ya karaso da murmushi saman fuskarsa ya zauna, ta
gaishe shi, ya amsa.
"Ban maki
alΖawarin nan kusa ba, amma da yardar Allah duk sadda na tashi aurar da ke, zan
kai ki har Maine ki kwana biyu. Nidai fatana yanzu shi ne ki saki jikinki
ki zauna da mu bisa kauna. Kin ji ko?" Ta gyaΙa kai tana murmushi mai
dauke da kunya jin wai Abbanta ya ambaci aure. Ita duka nawa ma take yanzun a
shekarunta goma sha huΙu? Koda dai, akwai sa'anninta su Murja, Fatsima da ma
sauransu wadanda duka an aurar da su a can. Tashi tsaye da Kawun ya yi ne ya
maido ta hayyacinta. Ta mike itama, Kawu suka yi sallama da Abba. Daidai nan
Mami ta shigo da sallama, tana sanye da dogon hijabi har Ζasa, gaida Kawu ta yi
sannan ta yi mishi sallama. Sai a sannan Humaira ta gaishe ta. Humaira ta
takawa Kawu har wurin motar Abba inda direban Abban zai kai shi tasha. Tana
hawaye haka ta tsaya har Kawun ya shiga motar, hannu ya Ιago mata itama haka
har suka fice daga gidan. Ji ta yi zuciyarta ta yi wani irin tsinkewa, haka
kurum ta ji wani irin tausayin kanta ya kama ta. Kanta Abba ya dafa da muryar
rarrashi ya ce. "Haba Mamana, kukan fa? Ya isa haka, ba fa rabuwa ku ka yi
kenan ba, in sha Allahu zumuncin ba zai yanke a nan ba matukar akwai rai da
lafiya, ki kwantar da hankalinki nan ma gidanku ne." Ta gyada kai,
daga haka suka shige gidan. Mami dake tsaye a windon falon tana kallonsa, itama
juyawa ta yi ta koma Ιakin Abban hawaye a saman fuskarta wanda ita kaΙai ta bar
wa kanta sanin ma'anarsu.
A falon Abban suka
zauna yana fadin, "Bari dai nayi hira da Ιiyata kafin na fita aiki
ko?" Ta yi murmushi har sannan
yatsunta na saman fuska tana goge ruwan hawaye.
"Ba ni labari toh, meyasa ba ki shiga makarantar boko a
can ba? Kawunki dai ya cemin kina zuwa islamiyya har kin yi sauka, na kuma ji
dadin hakan."
Ta gyara zama ta amsa a nutse.
"Dada ce ta ce ba zan je ba saboda koda na fara ba
lallai na Ζarasa ba. Ta ce kuma faransanci ne."
Abba ya yi shiru, ya gane sarai manufar Dada, wato dai ta
san cewa ko ba jima ko ba dade ranar nan za ta zo da Humairar za ta dawo
hannunsa, sai dai ya so ace ko na faransancin ne ta yi, da irin haka biyu babu.
Ya tuna shawarar da Mami ta ba shi a daren jiya da suke maganar karatun
Humairan.
"Zai fi dai ka sanya ta a inda za ta koyi sana'a
koda kuwa na girke-girke ne, kasan can idan ma ta yi karatun faransanci ne, nan
kuwa turanci ake. Zai iya ba ta wahala."
Toh shi Ιin ma dai ya ga hakan ya fi mishi sauΖi, yanzun ma
dubunnan da yake fitarwa na karatun yaran kaΙai sai godiyar Allah kawai, ina
kuma da ace ya sanya Humaira wacce ya tabbatar kafin ta fara sai an yi mata
lesson a gida sosai, Ιaukar karatun ne ma abin tunani, bai san ya kaifin
kwakwalwarta yake ba.
"Abba."
Ya tsinci muryarta wanda hakan ya katsemishi tunani.
"Na'am Mamana."
"Abba meyasa ba ka taΙa zuwa ka gan ni ba? Meyasa ko a
waya ba ka damu da kira mu gaisa ba idan ma aiki ne ya tsare ka?" Ya tsare ta da ido, yanzun ya gama raina
kaifin kwakwalwar yarinyar, sai dai ya sha mamakin tambayoyinta duk kuwa da ya
sani lallai ne dama watarana ta yi mishi su. Sai dai bai tsammace su nan kusa
ba. Dogon numfashi ya ja ya furzar.
"Kiyi hakuri Humaira, eh na yi maki laifi amma hakan ba
wai yana nufin ban damu dake ba ne. Sai dai nayi hakan bisa alΖawarin da na Ιaukarwa
mahaifiyarki wanda hatta da bayan mutuwarta ban karya shi ba." Cikin sauri ta ce.
"Wane alΖawari?"
Ya yi shiru sai kuma ya Ιago da niyyar magana, muryar Mami ta katse
hanzarinsa.
"Wai nikam dai yau Abban yara ba ka da niyyar fita ko?
Gashinan har goma ta gota."
Suka dubeta, a Ιangaren Humaira ji ta yi gaba Ιaya zuwan
Mamin bai burgeta ba, sai da aski ya zo gaban goshi tana shirin ta san ta ya ya
aka haihu a ragaya lokaci guda kuma Mami ta yi mata katsalandan. Mami kuwa
ganin hankalin Humaira ba ya kanta sai ta girgizawa Abban kai cike da damuwa.
Abba shi din ma jinjina kan ya yi, ya fahimci manufarta. Don haka ya dubi
Humaira da murmushin yaΖe.
"Af, kinga na
sha'afa har lokaci ya ja, kar ki damu Mamana, muna tare ai yanzu, a kowane
lokaci idan na samu dama da kaina zan yi kiranki mu yi hirar nan kin ji ko?
Yauwa Maminki ma ta ba da shawarar a sanyaki a makarantar koyon girke-girkenku
na zamani, ina fatan za ki so hakan?"
Duk da yanayin rashin jin dadin da take ciki sai da ta yi
farin ciki da hakan. Dama tana da son girki, ko a can gida ita ke yiwa Dada
dahuwa daga lokacin da ta soma zama budurwa. Ta kuwa saki fuskarta har
wushiryarta na fitowa muraran.
"Eh Abba ina so."
Abba ya dubi Mami suka yi murmushi, Mamin ta karaso ta dubi Humaira.
"Yauwa Ζ΄ar
Abbanta, kin ga da girki adon mace ce. Kuma na tabbatar za ki iya sosai idan
kika mayar da hankali. Ana samun alheri sosai da girki. Kar ki wani damu idan
ba ki yi boko ba, da yawa babu bokon amma sun samu ci gaba ta fanni da dama a
rayuwarsu." Humaira ta jinjina kai, tabbas haka ne don ta ga mijin Mammati
wata Ζ΄ar uwarsu a Maine, shi ma babu bokon amma yanzu kaf Ζauyen nasu babu mai
kuΙinsa. Idan ya zo hutu da yaransa kowa sai ya san ya zo saboda alherin da
yake yi musu.
"Ki je ciki
nasan zaman da kaΙaici ke kadai, ki sa Ladidi ta kunna maki kallo a wayarta sai
ki yi." Ta fadi hakan saboda babu
wuta, Ζa'idar Abba tun sha biyun dare ake kashe masa inji, sai ko idan aka ci
sa'a Kedco sun hasko wuta. Humaira ta fice a falon bisa bin
umarni. Bayan fitarta Mami ta Ζarasa ga Abba fuska dauke da damuwa.
"Ya haka? Kana
son ka karyawa yarinya zuciya daga zuwanta? Ko kuwa so ka ke ta riΖi
mahaifiyarta da mugun zato a ranta alhalin ba ta ji ba ba ta gani ba? Don Allah
kar ka fara, kar ka yi wannan kuskuren. Tabo ne da yaro kan yiwa gurguwar
fahimta."
Abba ya numfasa.
"Hakane, sai
dai ki sani ba karamin taimakona ki ka yi ba don ba ki da masaniyar abin da zan
ce a sannan. Na gama iyakar nazari ban san Ζaryar da zan shirga don rufe zancen
ba. Na gode maki mace ta gari."
Ya karashe yana jifanta da murmushi, ta rausaya
kyawawan idanunta tana maida mishi martani.
"Nima na gode da
wannan yabon, muje ka shirya lokaci na Ζurewa. Idan ka dawo ni kuma kafin nan
na bincika wurin wacce ya dace a kai Humaira ta fara daukar darasi."
"Hakane, amma zan fi so ta gama shiga ta san Ζ΄an uwana.
Kafin a durfafi wannan."
Mami ta Ιan yi jim sai kuma ta amsa da toh. Bayan shigar su Ιakin
yana cikin shiri ta sanyo zancen kaya.
"Ka ga ya kamata a Ιan Ιinka mata suturu ko ba yawa,
mutumin da ya zo daga Ζauye na tabbata ba wasu kayan kirki ne da ita ba."
"Ke dai wato burinki kawai na karya bakin aljihu, toh
wannan na jikinta ba sutura ba ce? Kin fi kowa sanin ba na son kashe-kashen kuΙi
ko?" Ta yi Ζ΄ar dariya, an zo wajen.
Ai idan har batu na fitar da kuΙi ne toh nan suke kai ruwa rana, a karshe dai
hakanan ta ke cin nasara a kanshi, kafin ya botsare akan jima.
"Haba Abban yara, Humaira fa uwa guda ce, idan ba ka yi
mata ba wa za ka yiwa?" Ta Ζarashe
murya a narke kamar wata matashiyar budurwa, hakan ya tuna mishi zamanin tashen
soyayyarsu. Ya yi dariya gami da girgiza kai.
"Maryam kenan, ke kam ba a kayar da ke a magana.
Shikenan idan na dawo zamu ga yadda za'a yi. Na fita ai ko?"
"Eh ka fita kam, Allah ya kara buΙi." Ta ba shi
amsa tana dariyar itama.
Ya amsa da amin.
***
Washegari kuwa Mami
da kanta ta bada aka siyowa Humaira atamfa da leshin sai kuwa kananun kaya
dogayen riguna duka dai ba masu yawa ba, hatta da takalmin shiga taro Ζafa biyu
da mayafai kala uku sai da Mami ta siya mata, ba kuma ta tsaya anan ba sai da
aka haΙo da kayan shafe-shafen mata da na kwalliya da kuma undies.
Abba ya kalli kayan sannan ya kalli Mami.
"Yanzu dukkan kayan nan a dubu talatin?"
Mami ta Ιan bishi da hararar wasa.
"Au, ka yi zaton kowa irinka ne? Wannan dai ya fi
Ζarfin abin da ka bayar, Mami ta cika ta siyawa Ιiyarta. Wanda ka bayar ma mun
gode."
Ya yi Ζ΄ar dariya.
"Maryam mai halin girma, ai shikenan, wannan tsakaninku
kun fi kusa. Allah ya saka da alheri." Ta amsa da amin. Sannan ta
umarci Ummita dake zaune wadda ita ce ta dauko kayan zuwa sashin Abban akan ta Ιauka
ta ba Humaira na shafe-shafen, suturun kuwa ta sa a leda Humairar ga shirya su
kai wurin telansu.
Ummita ta amsa da
toh, sannan ta kwashi kayan ta fice.
A falon Mami kuwa,
Tasleem ce zaune a gefe daga ita sai vest sai kuwa wandon makarantarta da ba ta
cire ba, zaune take tana cin Ιan wake tana ba su Raihana labarin wata Ζ΄ar
ajinsu Suhaima da kusan kullum ta Allah babu ranar da ba sa taΙinta. Sosai ta
tsayawa Tasleem Ιin a ΖoΖon rai, a cewarta yarinyar ta fiye rawar kai, ga
nunawa sauran Ιalibai kamar ta fi uban kowa ΖoΖari. Tasleem ta cusa loma a
bakinta sannan ta dube su.
"Kun san yau
wallahi ta ci arzikin Babandi da ya shiga tsakaninmu amma da sai na gwabje
bakinta. Ζ³ar iskar yarinya ta dubi tsabar idona ta ce wai ina mata katsalandan
a harkokinta saboda kawai tana yin tutorial din sanya kai na ce ita kanta ba ta
gane ba shikenan fa ta tasomin, su kuwa Ζ΄an korenta su Teema Small saboda na taΙa
Hajiyarsu me zuwa da mota nan suka goyi bayanta."
"Ke dai Tasleem
ina raba ki da nuna bakin cikinki a fili ga Suhaima, kin kasa Ιoyewa har sun
harbo jirginki, ke ba ki iya kwantar da kai ba? Ai irinsu da sannu za ki shige
mata har ta yarda dake ki zama aminiyarta, kika san wane Don Ιin za ki samu ta
hanyarta? Ko kin mance cewa ubanta fa ya fi naki arziki, koda dai namun akwai
sai maΖo." FaΙin Futuha tana Ζarashewa da murya a Ζasa gudun kar ta yi
shuka a idon makarwa. Suka kwashe da dariya, shiru Tasleem ta Ιan yi sai kuma
ta ce, "Ke kuma fa haka ne wallahi, don ba ki ga wani arnen gaye da ya
taba zuwa wajenta a makarantar ba, wallahi Ζarshen dai haΙuwa ya haΙu, ba wai
kyawun fuska ba aa, motarsa ma kanta abin a kalla ce."
"Ahaf, to kin
gani. Ai kinga kakarki ta yanke saΖa muddin ki ka samu irinsa. Bare ma yanzu da
Abba ya yi sanyi da batun auren, da ace ban da Mami ta shawo kansa ya bari ai
da yanzun mun haihu. TaΙ ni nasan da yarana biyu."
Suka yi dariya, hankalinsu ya koma ga niΖi-niΖin kayan da
Ummita ta shigo da su daga bangaren Abba.
"Ke." Cewar Futuha. Ummita yarinya mai sanyi da
hakuri, ta juyo ta kalle ta. Da yatsa ta nuna ledojin kafin ta ce.
"Wannan fa?
Daga ina zuwa ina?"
Duk da tambayar ta rainin hankali ne, amma ta amsa,
"Aiken Mami ne, ta ce a kai wa Humaira."
Daga haka ta ci gaba da tafiya, dukkan su ukun ba wacce ta
tanka sai faman furzar da hucin Ιacin rai da baΖin ciki. Can sai Tasleem ta ja
tsaki tana ture kwanon da ta ci Ιanwake da Ζafa.
"Mami! Mami!! Wallahi ban taba ganin uwa irin tamu ba
wacce ba ta damu da lamarin yaranta ba. Kunsan Allah, ba don kamanni da kuma
Ann dake Ζara ba mu tabbacin cewa ita din mahaifiyarmu ce dagasken ba da zai yi
wuya na yarda."
Cikin taΙe baki
Futuha ta amshe zancen.
"Uhum, kema dai kya fada. Ai shiyasa nake so mu samu
mazan kece raini da za'a kalla a Ζara kalla. Ko ba komai za mu huta da baΖin
cikin Abba da Mami."
Tsaki Tasleem ta ja
ranta na zafi, sai dai ta kasa magana karshe kawai ta mike ba ta ko kara kallon
kwanon ba kuma babu niyyar Ιaukewa. Bayan wucewarta kallon Futuha ya koma kan
Raihana wacce ta maida hankalinta ga waya tana murmushi.
"Ke kuma ke da wa? Mu gani."
Raihana kamar wacce aka tsikara ta mike tana ja baya da
dariya.
"Toh sa ido, ina ruwanki da wayata?"
Futuha ta taΙe baki.
"Kya ji da gulmarki dai, kullum latse-latsen waya,
wayarki ta munafukai babu wanda kika taΙa bari ya ga meke ciki. Ni ban san
irinki ba, ko hoto za ki nunawa mutum sai dai ya kalla haka tana dunkule
hannunki kamar wacce za'a sacewa."
Raihana na dariya ta yi hanyar waje gami da fadin.
"Eh Ιin dai, wasu ma ba a san me suke shukawa ba. Gwara
ni ko failed ban taΙa samu ba sai ku masu C.O."
Futuha ta yi kwafa kawai tana huci, zafi biyu ya haΙe mata.
***
Murna sosai Humaira
ta yi da wannan kyautar ban girman. Ta Ιaga wata riga ja mai adon fulawa ruwan
madara tana mannawa a jikinta. HaΖora a buΙe ta dubi Ummita, "Kinga kamar
Mami ta auna, daidai da ni."
Ummita ta yi dariya.
"Eh mana, sai ki sa hijabi su na falon Abba kiyi musu
godiya. Kinsan Allah, Mami tana ban mamaki. Wai fa har cikawa ta yi da kudinta
ta Ζarasa yi maki siyayya, nidai ban taΙa ganin mace mai kirkinta ba."
Humaira ta jinjina kai tana murmushi cike da gamsuwa da
zantukan Ummita. Tabbas itama a farko ta yiwa Mamin gurguwar fahimta, amma
yanzu kam ta ga saΙanin tunaninta. Sai kuma da sauri ta dubi Ummita.
"Wai anya ban yi
wauta ba? Kin ga ban je na gaida Anna ba tun da na zo."
Ummita ta Ιan yi shiru alamar damuwa, har dai Humaira ta ce,
"Lafiya kika yi shiru?"
Girgiza kai ta yi.
"Anna fa ba ta wani murna da zuwanki, ta cewa Mami koda
wasa kar ta sake ta turo ki Ιangarenta. Ki share kawai, ni nasan Mami za ta
shawo kanta, kuma tunda kuna tare a gidan dole watarana ku haΙu ai. Zance ne
kawai irin na Anna. Kinga jeki ki yiwa su Abban godiya mu wuce, yamma na
yi." Humaira ta gyada kai kawai ta
numfasa, dama ba dole ne kowa ya Ζaunaceka ba. Ba tare da damuwa ba ta zura
hijabin ta fice a Ιakin. Humaira ta ware idanu tana Ζarewa garin Kano kallo a
hanyarsu ta komawa gida bayan sun kai wa telan Mami dinkunan an kuma auna ta,
sosai akwai bambanci da inda ta fito koda dai dama ita din a Ζauye take. Sai
dai kuma hatta da titunan garin burgeta suke yi. Ummita ta kalleta ganin yanda
gaba Ιaya hankalinta ke a waje, murmushi ta yi.
"Humaira kenan, idan dai garin nan ne har sai kin gaji
da shi ina tabbatar maki."
Jin haka sai ta yi dariya.
"Anya kuwa? Nidai sosai ya burgeni wallahi. Ji nake
tamkar kada mu koma gida."
Dariya Ummita itama ta Ιan yi.
"Shiyasa ai na ce a bi da mu ta wannan hanyar ba ta
farko ba, kinga sai ki Ζara kalle garin sosai ko?"
Jinjina kai Humaira ta yi tana murmushi sannan ta jefo mata
tambaya.
"Ni kuwa yar uwa su Abba su nawa ne a wajen Umma? Umman
na raye?"
"Umman su Abba tun ina firamare, yaranta uku kawai
Allah ya ba ta daga nan ba ta Ζara haihuwa ba sai ko yaran Ζ΄an uwa da ta riΖe
ta aurar. Kinga Abba shi ne babba sannan Babana, sai autar Ιakinsu Baba Amina,
ita a can gadon kaya take zaune da mijinta. Kuma Kakanmu wanda ya haifi Abba
shi ya riga ma Umma rasuwa, ita kadai ce matarsa har ya bar duniya. Kar ki damu
kedai, tun da kika zo garin nan babu gidan da ba zamu je ki ga Ζ΄an uwanki ba in
sha Allahu."
Murmushi ya suΙucewa Humaira har ta Ιan lumshe idanu ta buΙe
su, ranta ya yi fari sol, burinta ya cika. Yadda ta san kaf Ζ΄an uwan Mamarta,
yau Allah ya nufa za ta san na Abbanta. Haka suka karasa su na tafe Ummita na
mata nuni da wuraren Ζayatarwa a garin.
***
Dattijuwar mace ce hakimce saman kujera ta haΙe girar sama
da ta Ζasa. Banda tsufanta da ya fito muraran, kallo Ιaya idan ka yi mata za ka
ga tsantsar kamannin da ta yi da Mami har ta so ta fi Mami hasken fata. Ta
gyara zama gilashinta gami da amsa sallamar da Mami ta yi mata ciki-ciki. Anna
sam ba ta iya Ιoye abin da ke ranta wannan ya sanya a kallo daya Mami ta gane
fushi take da ita. Da harshen buzanci ta ce.
"Anna yanzu zancen nan ba zai wuce ba? Ina ce na yi
maki bayanin komai?"
Anna da sai a sannan ta dubeta ta ba ta amsa cikin yare don
ba kasafai take yin hausa ba, kaΙan-kaΙan take ji.
"Ki ka ce bayani? Yanzu ke har kina tunanin zan gamsu
da bayananki na wofi Maryam? Kina da masaniyar irin
wahalar da aka ci a baya? Wato ke dadi miji ko?"
Mami gaba Ιaya ta dube ta fuskarta duk a jagule.
"Haba Anna, idan ban godewa bawan Allahn nan ba
bai kamata na watsa mishi Ζasa a ido ba. Mutumin da ya amince na zauna tare da
ku, muke rayuwa. Duk da irin son abin hannunsa, hakan bai sanya shi watsi da
lamarinki ba. Duk wata kulawar da mai shekarunki ya dace ta samu, babu Ιaya da
ya taΙa nuna gajiyawarsa wajen yi. Toh mene ne aibu a ciki don Ιiyarsa guda Ιaya
ta zauna a hannuna?"
"Shashashar banza da wofi, dama nasan ba alheri ne zai
fito a bakinki ba. Wato dai gori za ki yimin ko? Dama nasan akwai ranar Ζin
dillanci ai, dadin abin da baza ta kike rawa. Shikenan zan sa maki ido na
ga inda wannan rashin hankalin naki zai kai ki. Kin fi kowa sanin wahalar da
aka sha a baya ai."
Mami dai ba ta ce komai ba, ta so a bar maganar a sanyo wata
amma sam ba ta samu fuska wurin Anna ba dole haka ta miΖe ta kama hanyar barin Ιakin,
daidai Ζofa ta Ιan dakata kafin ta juyo ta sakarwa Anna wani murmushi da ita
kanta Anna ya ba ta Ιumbin mamaki da baΖin ciki, to wannan sabon raini ne ya
gifta tsakaninta da Maryam din ko kuwa dai kishi ya taΙa kwakwalwarta tun a
shekarun baya? Haka Anna ta cigaba da saΖe-saΖenta da babu mai warware mata.
***
A kwana a tashi babu wuya a wurin Allah, har a yau
Humaira ke cika sati uku cif a garin Kano. Abubuwa da dama sun faru na alheri a
rayuwarta da suka rinjayi sharrukan ciki. Ζaya daga ciki har da Ζarin suturu da
ta samu, sai kuwa gadonta da sif din kayanta da Abba ya sa aka yi mata. A gefe
guda Abba ya mallaka mata wata Ζaramar waya Ζirar Vivo sai dai tana yin
whatsapp, kuΙin wayar dai dakyar suka fito daga aljihun Abban nan ma sai
da Mami ta sha fama har ta nuna Ιacin rai Ζarara, a duniya kuwa babu abin da
Abba ya tsana kamar ganin Mami ta sauya mishi, nan da nan take cin galaba a ka
sa muddin buΖatarta bai shallake tunaninsa ba.
Ummita ta yi mata rakiya wurin dangin Abbansu na
kusa, sun yi murna kwarai da ganinta. Sun kuma karΙe ta da hannu bibbiyu, babu
abin da ya fi faranta ran Humaira irin shaidar kirki da suka yiwa mahaifiyarta.
Ta kuma ji dadin hakan ba kaΙan ba. Rashin abin yi ne ya sa kusan koyaushe idan
ba ta komai tana kan wayar tana danne-dannenta ganin ta riΖe abubuwan da Ummita
ta koyamata tunda dai harshen turanci ne, ta kuma sani koda faransancin aka
mayar ba za ta tsinci abin kirki ba. Abba ya sanya mata lambar Kawunta, sun
gaisa sau Ιaya ta waya don ita kam ko whatsapp ma cewa Ummita tayi kada ta buΙe
mata, ba ta ga wanda za ta yi hira da shi ba. Ta dai gwammace ta kunna rediyo
ta yi ta saurare don hatta da waΖoΖi iri-iri na soyayya da Ummitan ta sanya
mata ba ta damu da su ba.
A wannan yammacin kamar koyaushe tana zaune a Ιakinsu
gefen gado ta buΙe labule iska mai daΙi na dukanta, garin wuni aka yi cikin
zafi yanzu kuwa sai ya Ιan huce. Rabin hankalinta yana ga farfajiyar gidan inda
take hango Yassar tsaye da abokinsa wanda ta ji ana kira da Affan su na hira, a
gefe Ιaya Muhsin ne da ball yana wasansa tare da Waleed, daidai nan Futuha ta
buΙe gidan ta shigo, dawowarta kenan daga makaranta, Humaira na lura Affan na
mata magana ko kallonsa ba ta yi ba, daga yanayin tafiyarta za ka fahimci ba a
nutse take ba, har ta gifta hankalin Humaira na kanta, ta san dai babu lafiya,
tana kuma fatan ba gurguwar shawarar da ta ji jiyan wata aminiyarta Aina'u da
ta zo tana ba ta ba shi ta gwada a yau Ιin, gabanta ya faΙi. Ba ta mance
kalaman da suka fito daga bakin Aina'un bayan Futuha ta gama amayar mata da
damuwarta akan mahaukacin soyayyar da take yiwa Ibb Gusau.
"Ke ki na ban
mamaki wallahi Futuha, ki na da kyawun da babu namijin da zai kalleki bai Ζara
ba. Da ace ni ce ke, wallahi babu abin da zai hana na kai wa Ibb Gusau kaina.
Kina da sura irin wadda da zarar kin tallata mishi kanki zai ji nan duniya babu
wata sai ke. Ke idan ma wannan bai yi ba, ki zo na raka ki wurin Malam Aci
Bulus, na rantse maki ko me kike so za ki samu. Ke wallahi sai kin mallaki
malamin nan kin juya shi kamar waina a tanda."
Gaban Humaira ya yi wata iriyar faduwa, ta ambaci Allah a
ranta, ta yi nisa da saΖe-saΖen zuci ta ji an banko Ζofar Ιakin an shigo, ta
juyo da sauri, Futuha ce. Ba ta ko lura da ita ba ta kife a saman gadon Tasleem
tana kuka har da sheshsheΖa. Humaira ta yi shiru, kafin ta lalubo abin faΙi duk
kuwa da cewar ba shiga sabgar juna suke yi ba, Tasleem ta shigo Ιakin da sauri
a bayanta kuma Raihana. Za ta soma magana amma idanunta na sauka kan Humaira ta
fasa, cikin haΙe rai ta ce.
"Malama ba mu waje za mu yi magana." Jin haka tsam, Humaira ta miΖe ta kama hanyar
barin Ιakin, bayan fitarta Raihana ta karasa ta rufe Ζofar har da sanya muΖulli
sannan ta dawo. Futuha suka Ιago su na magiyar ta sanar da su abin da ya faru.
Dakyar ta iya tsaida hawayenta ta shiga ba su labari.
"Ai na faΙamaku yadda muka yi da Aina ko?"
Suka gyaΙa kai duk sun Ζagu su ji komai.
"Shi ne..shi ne.."
Sai kuma ta yi shiru ta rasa me ma za ta ce. Tasleem ta zaro
ido.
"Shi ne me Futuha? Kada dai ki cemin kin gwada
aiwatarwa?"
Futuha ta runtse idanu gami da shafa gefen fuskarta tana
kuka sosai. Sai a sannan idanunsu ya kai ga gefen fuskar, ya yi ja ya yi ruΙu-ruΙu
alamun dai mari ta sha. Koda alama ma ba guda Ιaya ba. Ba ta bari sun
nemi ba'asi ba ta cigaba da maganarta.
"Na iske shi zaune a ofishinsa shi kaΙai yana aiki a
system, koda na shiga bai Ιaga kai ya kalle ni ba, daga motsawar leΙΙansa na
gane ya amsa sallamata. Duk da cewa gabana na faduwa hakan bai sa nayi Ζasa a
gwuiwa ba na karasa ga teburinsa. Na sauke mayafina yanda rabin kirjina ya
bayyana, na shagwabe murya ina mai batun ban gane abin da ya koyar a aji ba.
Koda naga bai kalle ni ba, sai na yi gangancin kai hannu saman nasa, shi ne ya
gaggauramin tagwayen maruka a kuncina. Ya kum rantse idan na Ζara shiga ofishinsa
sai ya Ιalla ni kuma daga kaina masu tunani irin nawa za su dawo
hayyacinsu."
Tana kaiwa nan ta ci gaba da kukanta. Tasleem da Raihana
kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya. Raihana ta ja tsaki.
'Kema dai Futuha wataran kina abu kamar Waleed marar wayo
wallahi. Ke kin manta tun farko itama Aina'un sonsa take yi wai? Ko don ta Ιata
ki a wurinsa ku yi biyu babu kinga ai za ta ba ki gurguwar shawara. Ai mun faΙamaki
amma ke idanunki ya rufe."
Tasleem ta amshe.
"Yanzu shikenan koda ace wannan mutumin na ganinki da
mutunci kin Ιarar da shi, yadda za'a yi ki gyara ma nikam ban sani ba. Kada dai
garin gyaran a Ζara jagula abubuwan shi nake tsoro. Ke!!! Wai don uwaki shi kaΙai
ne namiji a duniya ma? Aikin banza kawai! Ga samari Ζ΄an kasuwa da Ζ΄an bokon su
na matowa a kanki a instagram amma kin tsaya biyewa wani so, so, ke fa kike ban
shawarar na shigewa Suhaima don na samu na yi mata koda snatching ne, amma ke
nan kin tsaya Ιata lokaci akan wani kuturu gurgu."
Jin haka ran Futuha ya Ιaci, ta harari Tasleem kafin ta ja
tsaki.
"Da ace kun san mene so da duk baku Ιata bakunanku ba.
Sannan Ibb Gusau lafiyayyan mutum ne kar ki kara aibata shi. Tunda kuma ba ku
da shawarar da za ku ban, ni nasan me zan yi."
Tana kai wa nan ta miΖe ta yaye mayafin ta faΙa banΙaki ba
tare da ta amsawa Raihana da ke jefomata tambaya akan abin da za ta aikata ba.
***
Mami ce tsaye a farfajiyar gidan ta haΙa cikin atamfa
ruwan Ζasa mai adon fari, ta sha mayafi ruwan Ζasa hakanan takalminta. Ta dai
yi kyau Ζarshe, idan ka kalle ta ba za ka ce ita ta haifi yaran ba saboda
daidai gwargwado ta iya Ιaukar wanka. A gefenta Yassar ne su na magana yana
Ζorafin shi dai mota yake so tasan yadda zata yi Abba ya siya mishi. Mami jinsa
kawai ta ke yi tana yi kuma tana duban gate, da ta gaji ta ja guntun tsaki.
"Wai ina Yakubu ya je ne? Daga jeka ka sha mai shikenan
har yanzu bai dawo ba?"
Yassar ya taΙe baki yana zura hannu a aljihun wandonsa.
"Mami ina magana ba ki amsamin ba, koda dai nasan
wannan halin na Abba zai wahala ma ya siyamin. Amma fisabilillah ina Ιan jami'a
ina kallon abokaina har ma da matan da na raina su a makaranta su na da motocin
kansu ni kuwa ko keke Abba ya kasa siyamin saboda mammaΖo."
Ran Mami a Ιace ta dube shi.
"Yassar ka shiga taitayinka, mahaifin naka kake yiwa waΙannan
kalaman marasa daΙi? Toh ya yi maku mammaΖon, kai ai namiji ne, namiji kuma da
nema aka san shi. Guminsa ne ya gina wannan gidan, ya kuma mallaka mishi
motocinsa, kai ma ka yi zuciya ka mayar da hankali a karatunka watarana ba
Abbanku ba, da kanka sai ka siyawa kanka motar, ba na son shirme. Ni kiramin
Yakubu a waya ka ce ya yi sauri ya Ζaraso, ina Humairar take ne..."
Ba ta Ζarasa zancen ba ta waiga, Humaira na tsaye a gefensu
kasancewar su na magana ba su ko lura da ita ba. Itama ta yi shirinta tsaf
cikin atamfarta koriya wacce tana Ιaya daga cikin Ιinkunan da aka yi mata. Ta
yi kyau sosai, murmushi ta Ιan yiwa Mamin.
"Mami na fito ai."
Yassar ya ja tsaki ya bar wajen don takaicin Mamin da kuma
na ganin Humairar da yake jin haushi da kishin tattalinta da iyayen nasu suke
yi sai ka ce su ba Ζ΄aΖ΄a ba ne, Mami na kwala mishi kira amma bai ko waigo ba
sai amsawar da ya yi da Ζarfi.
"Zan je na Ιau wayar ne na kiramaki Yakubun."
Daga haka ya ci gaba da tafiyarsa, Mami ta girgiza kai
fuskarta Ιauke da matsanancin damuwa. Sai jikin Humaira ya yi sanyi, wannan
kalar zamantakewar mutanen gidan na ba ta mamaki, ace Ζ΄aΖ΄a ba sa ganin iyayensu
da gashi, kowace magana ta fito a bakinsu hakanan za su watsa musu ba tare da
taunawa ba, toh wace riba ake samu a hakan? Ita tunda ta zo ma ban da Ummita da
Raihana sai Muhsin masu Ζokarin zuwa islamiyya, ba ta ga wani cikin su Tasleem
na zuwa ba. Bar su dai da yawon gidan Ζawaye a Ιoye Abban bai sani ba. Itama
dai Raihanan ba zama take sosai ba amma takan tsaya har a biya karatu da
ita, wasu lokutan sai dai ta ji tana amsa wayar zasu haΙu da wani
saurayin idan ta fita makaranta.
A yanzu kuwa daga maganganun Mamin ta fahimci
watakila Yassar kuΙi ya nema ko wani abin da bai samu ba ya faΙi abu game da
Abban shi ne take goranta mishi.
"Muje Humaira, ya zo."
Ta amsa da toh ta bi bayan Mamin cike da jin tausayinta,
kowace uwa na son ta ga nata na bin ta sau da Ζafa, amma Mami ba ta samu wannan
biyayyar ba na yara. Daga manyan har Ζananan, koda dai ta ji Ummita na cewa shi
dai babban Ιan nasu ya bambanta da sauran, kuma su na masifar shakkarsa, akwai
abubuwa da dama wanda idan yana nan ba sa aikatawa. Ta ce daidai da hantarar da
suke yi mata idan har yana nan ba sa yi.
Har dai suka soma tafiya a titi tunane-tunane take yi,
hankalinta jiya bai kwanta ba sai da ta tsinkayi Tasleem na hira da Raihana su
na tsokanar Futuha akan marin da ta sha har su na faΙin gobe ma ta Ζara. Daga
baya dai ko don tana Ιakin ne sai suka juye harshe zuwa turanci, ta lura ba su
fiye yin buzanci ba su kam, a yadda Ummita ta ce ma, ba komai suka iya faΙi a
yaren ba, sun dai fi ganewa idan an musu magana ba su iya mayarwa yadda ya
kamata ba. Wannan sai babban yayansu. Shi dai yana ji sosai.
Daidai wani babban gida motar ta tsaya, suka fito suka nufi
ciki. Kyau da tsaruwar gidan har ya so ya kere na su. Da murmushi Mami ta dubi
Humaira lokacin da suka shiga farfajiyar gidan.
"Gidan aminiyata kenan Hajiya Lubna, ita ce za ta kai
ki wajen koyon girki. Ζanwarta ke yi."
Humaira ta gyaΙa kai ranta ya yi fari sol, ta san dai Mamin
ta ce ta shirya zasu je unguwa amma ba ta kawo a rai fitar ta shafe ta ba.
Daidai za su shiga babban falon suka yi karo da Ιan Hajiya Lubna shi kuma zai
fito, matashin saurayi mai jini a jika, ya sha Ζananun kaya abinsa ya yi tsaf.
A fuska ba za ka kira shi da kyakkyawa ba sai dai hutu da jin dadi ya sa
fatarsa murmurewa. Gaisawa ya ke da Mamin amma hankalinsa kacokam na ga Humaira
wacce daga kallo Ιaya da ta yi mishi ta kauda kanta don ita kam a duniya ta
tsani kallo. Mami na lura da yanayin kallon da yake jifan Humairar da shi, ita
kanta bai mata ba don haka don ta katse shirun ta ce.
"Hajiyar dai na ciki ko? Don na san ta yanzu sai ta iya
ficewa ta bar ni zaman jira."
Dariya ya Ιan yi yana shafo Ζeyarsa.
"Tana ciki Hajjaju. Ku shiga kafin na shigo."
Ta amsa mishi ta yi gaba Humaira ta bi bayanta da sauri har
tana tuntuΙe saboda kallon da yake bin ta da shi. Mami ta kalleta kawai ta
kauda kai ba ta ce uffan ba. A falon gidan suka iske Ζ΄an mata da yara ana kallo
ana hira, wuta tarr a gidan madadin gidansu wanda idan har ba wutar Nepa aka ci
sa'a suka kawo da rana ba, zai yi wahala ka ga hasken fitila a gidan sai
Magriba zuwa Ζarfe sha biyun dare.
Gaba Ιayansu suka gaida Mami, ta amsa. Ta dubi Humaira.
"Ki zauna ki jira ni bari na Ζarasa wajenta." Ta
amsa da toh ta nemi wuri ta zauna. Ta lura gidan dai Ζ΄an boko ne, ba su ko damu
da ita ba sai mai aikin gidan da ta miΖe ta kawo mata ruwa da lemu ganin da ta
yi tare suke da aminiyar uwar Ιakinta. Godiya ta yi mata amma ba ta sha ba,
hankalinta kacokam na garesu, wani shiri suke kallo na india, sun maida
hankalinsu kacokam. Itama sai nata hankalin ya tafi can. Ta shafe mintuna goma
a nan tana jiran Mami, can sai ga wani Ιan yaro ya sauko daga benen da Mamin ta
hau.
"Ki je ana kiranki a sama."
"Toh" Kawai ta ce ta miΖe ta nufi hanyar da yaron
ya fito, kafin ta Ζarasa ta tsinkayi wata muryar babbar mace na faΙin.
"Ke dai ki bi a hankali, kar ki yi garaje kamar yadda
ki ka so yi a wancan lokacin."
Sallamarta yasa suka kalli hanyar da sauri, ba ta lura da
yanayinsu ba ta karasa ta durkusa gefe ta gaida matar wacce kamanninta sak da
wannan matashin da suka gani Ιazun. Matar ta amsa mata fuska a sake.
"Ah Maryam, ki ce Ιiyar tamu kyakkyawa ce masha Allah.
Humaira ko?"
Humaira ta gyaΙa kai tana sunkuyar da kai murmushi a saman
leΙbanta.
"Masha Allah, Allah ya yi albarka kin ji? Allah ya
gafartawa Hajiya Fatima, idan kika biyo halinta kin more. Mace mai hakuri da
kawaici. Allah ya gafarta mata."
Ta ji wani sanyi a ranta, a duniya tana jin daΙin a yabi
Mahaifiyarta. Ta amsa da amin ita da Mami.
Mamin ta dube ta.
"Toh Humaira, gobe idan Allah ya kaimu koda ba ni ba,
sai ku zo da Ummita a kaiki gidan koyon girkin. Na faΙamaki ta gida ce, Ζanwar
Hajiya Lubna ce. Sai ki mayar da hankali ga abin da ya kai ki. Nasan kina da
fahimta da saurin Ιaukar abu, don Allah kar ki ba mu kunya kin ji ko?"
Ta amsa da toh Mami. Kafin Mami ta Ιora daga inda ta tsaya
wannan saurayin na Ιazu ya hayo. Suka maida duba gareshi. Wani irin ajiysr
zuciya ya sauke yana duban Humaira sannan ya maida kallonsa ga Mami.
"Ai na Ιauka har kun tafi."
Mamin ta Ιan yi murmushi kaΙan ta girgiza kai.
"Ina nan Kabeer, amma yanzun za mu tafi. Abban yara ya
kusa komawa gida."
Ya karasa ya zauna. Hajiya Lubna nan da nan fuskarta ta
sauya ganin kallon da yake jifan Humaira da shi. Mami ta dubi Humaira ta bata
umarnin ta koma Ζasa ta yi jiranta za ta sauko su tafi. Daga fitarta shi ma ya
miΖe caraf ya bi bayanta. Hajiya Lubna za ta yi magana, Mami da sauri ta hana
ta ta hanyar Ιan dafe kafaΙarta. Dole ta fasa. Amma ta kudurce a ranta lallai
za ta yiwa abin tufka don ita kam Ιiyar ubangidan mijinta take so ya aura, ta
kuma lura da yadda yake bin Humaira kamar jela to akwai wata a Ζasa. Ζwafa
kawai ta yi ta watsar suka Ιora hirarsu daga inda suka tsaya.
A can kuwa Humaira duk ya takura mata, ita ba ta saba da
wannan rayuwar ba. Kawai wani garjejan saurayi ya zauna yana jan ta da hira ba
hadin uwa da uba, ita kam abin ya girmi kanta. Ta kula bai ko damu da jama'ar
falon ba waΙanda su din ma kallonsu kawai suke jifa-jifa su na mayar da
hankalinsu ga tv. Tambayoyi yake mata iri-iri, amma ba Ζ΄ar Mami ce ke ba?
Yaushe ki ka zo? Karatu kike? Da dai sauransu ita dai eh ko aa kawai take
ce mishi duk ta takura. Haka Mami da Hajiya Lubna suka sauko, ganinsu ya sa ya
miΖe yana shafar Ζeya.
"Wai Kabeer ina aiken da na maka ne? Idan ba za ka je
ba, ka fadamin na aiki Bala direba."
Hajiya Lubna ta faΙi rai bace tana watsa mishi harara, sarai
ya gane manufarta, amma shi kam yana ji a ransa ko karatu Humaira take yi zai
iya dakon jira ta kammala ya aure ta. Ya lura auren jari Hajiyartasa take so ya
yi.
"Sorry Hajjaju, bari na tafi. Mami ku gaida gida, sai
na tako har falonki na Ζara gaida ki."
Mamin ta yi dariya.
"Ai babu laifi Kabeer, ko da wacce ka zo ka shiryawa
amsar da za ka samu."
Ganin ta Ιago shi ya fice yana Ζ΄ar dariya gami da faΙin.
"Na shirya Maminmu, amma dai ba zan ja baya ba."
Mamin ta Ζara darawa. Humaira ta miΖe suka kara yin sallama
da Hajiya Lubna, har farfajiyar gidan ta rako su. Humaira dai har ta Ιan kwashe
mintuna a mota ba su gama tsayuwarsu a bakin Ζofar falon su na tattaunawa ba,
ba ta san me suke cewa ba dakyar dai Mamin ta taho ta shiga motar suka tafi.
***
Humaira ce zaune a
falo da safe, yaran gidan duka sun fice makaranta kasancewar sun soma
jarrabawar zango na uku (Raihana da Ummita kenan), a yadda Ummita ta ce mata,
daga jarrabawar to aji na gaba za su je.
Kallon tashar Arewa24 take inda ake hasko wani wasan
kwaikwayo na marigayi Ibro. Ta shagala gaba daya tana tuntsira dariya ta ji Ιif,
wuta ta Ιauke. Guntun tsaki ta ja, ita kam ba ta san matsalar wuta a nijar ba
domin koyaushe akwai. Ba ruwanka da tayar da janareto. Ganin haka kawai sai ta
miΖe da zummar komawa Ιaki.
"Humaira."
Muryar Ladidi ta katse ta, ta juyo ta amsa. Tire ne a hannun
Ladidin ta karaso gareta. Fuskarta duk ta yi narai-narai alamun roΖo.
"Ki taimakamin don Allah ki miΖa sashen Anna, kinga
suyar agadar Mami nake kada ya Ζone. Kuma Annar za ta sha magungunanta ne
lokaci na tafiya."
Kirjinta ya Ιan buga dam, ta kasa magana. Toh akan me za ta
cewa Ladidin ba ta taΙa shiga sashin Anna ba? A ganinta hakan su ta shafa.
Ganin yadda Ladidin ke magiya yasa ta karΙa, godiya ta yi mata ta koma kicin.
Ita kuwa Ιan hanyar da take ganin su Muhsin na yawan zirga-zirga zuwa wajen
Annar ta zubawa ido sannan ta sauke ajiyar zuciya ta nufi wajen. Anna Ιin ai
mutum ce ba aljana ba balle ta illata ta, za ta je ta ga me zai faru idan ta yi
karo da ita. Koro ta za ta yi daga Ιakin ko kuwa dai duka za ta yi mata. Da
haka ta tunkari hanyar.
A hankali ta tura Ζofar Ιakin da sallama, jin shiru yasa ta
maimaita. Wata murya ta amsa, ta tabbatar ba shakka muryar ta Anna ce. Shiga ta
yi ta karasa ta ajiye saman Ζaramin tebur dake wurin. Anna dake zaune gefen
gado ta soma magana tana laluben gilashinta.
"Ladidi sai yanzu ake kawomin abin karin? Yau me ya
tsaida ki haka? Ina gilashina na jefa?"
Humaira ta hadiyi miyau, kenan dai Anna ba ta san ma wace
tsugune a gabanta ba. Ta daure ta ce.
"Ina kwana. Ya karfin jiki?"
Jin baΖuwar murya ya sa Anna saurin sanya medicated
glass Ιinta wanda da shi ne ta ke gani sosai ba dishi-dishi ba. Yarinya budurwa
ce durΖushe a gabanta, fara sol. Kanta duk da cewar akwai hula, sumarta ba ta Ιuya
ba don hatta da goshi da bayan Ζeyarta sumar ce kwance. Ta Ζuramata idanu tana
Ζokarin tuno inda ta san fuskar. Sai dai a Ιan lokacin ba ta ankare ba don ita
shaf tuni ta mance da wata wai Humaira a gidan tunda ba su taΙa karo ba. Ba ta
damu da shiga sashin Ιiyarta ba, ya fi rayuwa anan dai Ιangarenta.
Daidai lokacin Mami ta shigo Ιakin kamar wacce aka jefo, ta
samu labari daga Ladidi cewar Humaira ta tura kai wa Annar kari. Shigowarta ya
sa Anna mayar da dubanta gareta.
"Ina kika samu yarinya ha..."
Sauran kalaman Anna suka maΖale a fatar bakinta, shakka babu
ta tuno komai. Ta tuna ashe akwai wani ran bayan jikokinta a gidan da aka ce
tsatson Fatima ce. Ta tuna Humaira kamar yadda ta ji sunanta a bakin su Yassar
masu yawon kawo Ζorafi a kan fifikon da Mami ke yi mata sama da su. Nan da nan
ta haΙe girar sama da ta Ζasa. Daidai lokacin Humaira ta Ζara gaidata wannan
karon muryarta har Ιan rawa yake. Ta nuna Humairar da yatsa idanunta akan Mami.
"Me wannan abar ta zo yi wurina? Me na faΙamaki? Ban ce
maki ba na son ganin baragurbi a wurina ba? Ke don uwaki wa ya ba ki
iznin zuwa wurina, ko ni na haifi uwarki?!"
Maganar sosai ta daki Humaira, nan da nan idanunta suka
cicciko da kwalla, uwarta kuma? Uwar dake kwance a kushewarta? Mene dalilin
sanyo ta ciki? Ba ta jira umarnin Mami ba ta miΖe a zuciye ta kama hanyar fita
daga Ιakin, Mami ta riΖe hannunta wannan ya dakatar da ita sai dai ba ta ko
juyo ba. Daidai nan kuma hawayen suka sauka saman kuncinta. Da harshen buzanci
Mamin ta yiwa Anna magana, Annar kuwa cikin harshen da Humairar za ta ji ta
amsa a fusace cikin Ιaga murya.
"Au! Don na zage ta kike kirana marar adalci? Ni
Maryama kike kallon idona ki ce ba na adalci? Toh anyi rashin adalcin. Idan
maye ta manta ai uwar Ιa ba ta mance ba. Ke da kika ga za ki iya haΙiye duk
baΖin cikin da kika risΖi kanki a baya, ki yi. Nikam ba da ni ba, kuma ke duk
radda kika kuskure ki ka Ζara gangancin takowa Ιakin nan sai na sa jikokina sun
nakastamin ke. Sauran yunwa kawai."
Humaira tuni ta janye hannunta a na Mami ta bar Ιakin da
sauri.
Kai tsaye Ιakinsu ta nufa ta zube saman kafet ta shiga kuka
kamar ranta zai fita. Ita fa duk abin da matar ta ce bai dame ta ba kamar sanya
uwarta da ta yi a ciki. To me Mamarta ta yiwa Mamin da har Anna ke batun ba za
ta mance ba? Wane irin zama suka yi a baya? Ita Mami da ma Ζ΄an uwan Abba, sun
yiwa Mahaifiyarta kyakkyawar shaida, amma me Anna ke nufi da kalamanta? Ko kuwa
dai ita ke taya Ιiyarta kishin kamar yadda Ummita ta taΙa faΙi?
Ba ta ji shigowar Mami Ιakin ba sai ji ta yi an kama
hannunta an Ιaga ta. Ta miΖe tsaye, Mami ta yi mata murmushi.
"Ki yi hakuri Humaira, kin san iyaye ne sai mun yi
hakuri da su mu samu a rabu lafiya. Ki taya ni yi mata biyayya, kar ki
kara zuwa Ιakinta har sai don kanta ta nemi hakan wataran wanda in sha Allahu
nake fatansa nan kusa. Kar ki sa komai a ranki, ki kuma shirya anjima da kaina
zan kai ki gidan koyon girki. Ki cire komai a ranki ki mayar da hankali, ni
kuma anan gida idan kin dawo zan dinga iyakar Ζokarina wurin ganin an samar
maki dukkan kayan girkin da ki ka koyo a can ki yi a nan mu ci mu ΙanΙana, kin
ga daga haka hannunki zai miΖa. Wataran sai a wayi gari kina odar biki da suna
har ma da wuraren party ko? Kin zama Hajiya."
Zancen Mamin ya sanya ta murmushin da har wushiryarta ta
bayyana. Mamin ma murmushin ta Ζara yi. Daga haka ta fice a Ιakin. Humaira tuni
ta share batun Anna ta tattara ta watsar.
***
Sun je gidan Anti Laila Ζanwar Hajiya Lubna tare da Mami, ta
ba da form bayan sun biya komai, Mami da kanta ta cikewa Humairar. Anan aka
ajiye ranar litinin matsayin ranar da za ta fara zuwa koyon girkin. Daga nan
suka yo gida ranta fari sol.
Kai tsaye Ιaki ta nufa hannunta riΖe da na Waleed wanda zuwa
yanzu daga shi har Muhsin sun sake da ita, fuskarta a sake, zuciyarta
wasai. Ummita ce kaΙai zaune tana karatun jarrabawa, ganin haka Humaira ta dubi
Waleed.
"Tafi wajen Muhsin ku yi wasa ka ga Adda Ummita karatu
take yi. Anjima sai ka zo ka koyamin turanci ko?"
"Okay! Bye."
Itama ta amsa da bye din tana dariyarsa, ya dage a lallai
zai koyamata turanci, haka za ta biye mishi tana Ιan tsintar wasu abubuwan da
ya iya. Ummita ta kalle ta tana murmushi.
"Yau dai fara'arki ta musamman ce. Kada dai ki cemin
har kin soma shiga aji?"
Dariya Humairar ta yi daidai sadda take zama a gefenta.
"Aa fa, amma an gama komai an biya, litinin zan soma
zuwa."
"Kai naji dadi wallahi. Allah ya nuna mana."
Ta amsa da amin, ta mike ta hau cire kaya da zummar shiga
wanka. Ta dai kula kamar Ummitan ranta a jagule ya ke, ba ta ce mata komai ba
har ta shiga wanka ta fito. Anan kuma ta ga ta amsa waya ta yi jifa da wayar
saman gado tana Ιan goge fuska. Jiki a sanyaye ta Ζarasa gareta ta zauna.
"Ummita, lafiya? Meyafaru?"
Ummita tana kallon littafin amma ta kasa karatun sai kawai
ta girgiza kai tana shirin cewa ba komai amma tuni hawayenta ya zuba saman
littafin. Humaira ta janye littafin.
"Don Allah meke faruwa? Anyi wani abu ne bayan fitar
mu?"
Nan ma girgiza kan ta yi. Ganin haka sai kawai Humaira ta
mike ta nufi sif dinta, har ta sanya kaya jiki a sanyaye Ummitan ba ta da
niyyar cewa wani abu. Ganin haka sai ta Ζarasa wajenta karo na biyu.
"Na tambayeki mene ne kin kasa cewa komai, kuma kina
kuka." Jin ta yi shiru ne yasa Humaira fadin.
"Toh bari na kira Mami mai yiwuwa ita za ki faΙamata."
Har ta miΖe da sauri Ummita ta riΖe hannunta. Suna haΙa
idanu ta girgiza mata kai, itama Humaira tuni idanunta sun cicciko don a duniya
ta tsani kukan mutum. Kuka ma irin na waΙanda ta ke yiwa Ζauna domin
Allah. Duk abin da ya shafi irin mutanen nan tana jin abin a ranta tamkar ita
ya shafa.
"Kar ki je, zauna na faΙamaki." Ta koma ta zauna
tana mai zuba mata ido bayan ta share kwallarta.
"Yayar Mamana ce ta kira ni daga Bichi, kwanakin nan
duk sun takura akan lallai sai na fiddo miji na yi aure wai karatun ya isa
hakanan. Su sam hankalinsu bai kwanta da zamana a gidannan ba. Ita Babbar yayar
Mamana, Anti Maijidda cewa take yi wai har mafarke-mafarke take yi a kaina don
haka za su yiwa Abba magana a dakatar da karatun nan, ida n ma aure ne dai a
yimin. Ni kuwa na dage akan ba zan yi aure yanzu ba, na ce musu ko zance ba na
yi, sun ce ai kuwa anan da Bichi ba zan rasa mijin aure cikin Ζ΄an uwa ba, Anti
Maijidda har cewa ta yi ga babban Ιanta Yusuf nan, wai ya kammala gininsa
za ta turo shi ya zo mu yi hira mu fahimci juna. Kin taΙa jin wannan irin abu
don Allah Humaira? Duka-duka nawa nake da za su ce za su aurar da ni yanzu?
Zangon karshe nake a Ss1 zan wuce Ss2, idan ma auren suke buri su ga na yi, ai
sa bari dai shekaru biyun da suka ragemin a sakandire na kammala su. Haka kawai
don wasu mafarke-mafarken da ba su da tabbas ku rushemin ginin rayuwata? Sun bi
sun kafawa Mami karan tsana, ban san hawa ba ban san sauka ba, amma nima su na
hantarata akan na mayar da ita tamkar uwar da ta haife ni, gani suke na fifita
dangin Babana sama da su. Toh don Allah faΙamin, mutanen nan sai na je wurinsu
duk shekara a can nake hutun dogon zango da ake ba mu na makaranta har ya Ζare,
amma su ko sau Ιaya ba su taΙa zuwa garin nan da zummar ganina a gidan nan ba
acewarsu su da Mami har abada don ba su yarda da zuciya Ιaya ta ke riΖe da ni
ba. Akan Mami na sha duka a wajensu idan na je domin duk wanda ya aibata
ta zan buΙe baki nace sam ba haka take ba, to fa anan sai na ΙanΙana kudata.
Yanzu wannan matsalar auren da ta taso ki faΙamin Humaira, ta ina zan kashe ta
ba tare da na samu matsala da su ba, nikam wallahi gaba Ιaya kaina ya
Ζulle."
Humaira ta sauke ajiyar zuciya.
"Wai Allah!" Shi ne abin da ta furta don ita komai
ma ya tsaya mata cak, ta rasa me za ta cewa Ummita. Mamaki take yi na yadda
suke yiwa Mami kallon baibai alhalin matarnan iyakar kokari tana yi a kansu,
irin kokarin da ko mahaifansu na usuli sai haka. Can kuma ta dubi Ummita.
"Toh kodai ki yiwa Abba bayanin komai? Na tabbata zai
fahimceki kuma ba zai rasa matakin Ιauka ba yadda zumuncinku ba zai taΙu
ba."
Shiru ta Ιan yi, sai kuma ta ce.
"Ko? Nima na yi wannan tunanin, wallahi maganganunsu ke
hargitsa ni tun wancan satin su ke huran wuta, tun fa ina dannewa har suka soma
sanya ni kuka. Amma hakan zan yi kawai, zan faΙawa Abba komai, ke nasan ma kai
tsaye zai nemi Kakana wanda ya haifi Mama ya yi mishi magana. Shi kaΙai zai iya
tsawatar musu, daman tsoro ne ya sa na kasa faΙa mishi, amma na tabbatar zai
magancemin."
Humaira ta jinjina kai.
"Sai dai don Allah kar ki faΙawa Abba zargin da suke
yiwa Mami."
Ummita ta kama baki.
"Rufamin asiri Humaira, dama me zai kai ni?"
Murmushi Humaira ta yi. Suka Ιan taΙa hira sannan ta kyale
ta don ta yi karatu.
Aikuwa a daren Ummita ta samu Abban ta zayyane mishi
komai, ransa ya Ιaci. Ζarshe dai ya ce ta tashi ta wuce zai san matakin da zai Ιauka.
A ranar kashe wayarta ta yi ta kuma yi alΖawarin ba za ta kunna ba har sai
komai ya wuce don ta tabbata zagi ne dai za ta sha a wurin su.
***
BAYAN WATA BIYU...
Gadan-gadan Humaira ta fara zuwa koyon girki, abin da ya
burge su Abba da Mami bai wuce irin hazaΖarta ba na saurin Ιaukar abu. Ita
kanta Anti Laila sosai take yabawa da Humairar. A farko-farko ne dai idan aka
koyar da su ta zo gida ta yi sai ya kasance bai yi dadi ba ko gishiri ya yi
yawa ko dai wani abin, har su Tasleem na ci don su yi mata dariya da kuma
kushe. Har su na cewa Abba ya yi asarar kuΙinsa. Amma yanzu kam duk da su na
kaucewa ba su son nunawa a fili yana musu dadi, to fa a Ζasan zuciyarsu su na
son su ΙanΙana idan ta yi. Amma fa ana ci ana yamutse fuska ana nuna ba laifi
ya Ιan yi dadi. Ita dai ba ta tanka musu tunda har Abba da Mami da Ummita su na
yabon girkinta.
A farko direba ke
kai ta, daga baya kuwa Mami ta nemi Ιan sahun da zai dinga kai ta kuma ya Ιauko
ta. Watarana kuwa da aka yiwa Ιan sahun
rasuwa da kanta ta Mami ta sanya yaron gidan me musu wanki ya raka ta titi ya
sanya ta a adaidaita, a dawowa da kanta ta dawo. Tun kuma daga nan ta soma zuwa
da kanta ta dawo, a karshe kuma ya kasance koda Ιan sahun bai zo ba ita ke zuwa
ta dawo. Ganin ta gane hanya ya sa Mami kawai ta sallami Ιan sahun ake ba ta kuΙin
mota.
Komai idan ta koya
tana samun Ιan littafin da Ummita ta bata ta rubuce tsaf da hausar ajami.
Rubutunta mai Ιan karen kyau da burgewa har ya kasance Ummita ta yi ta santin
handwritting din.
A bangaren
Islamiyya kuwa, kusan tare suke tafiya da Ummita a aji duk kuwa da cewar a can
karatunta ya zarta na su, akwai abubuwa da dama da ta sani na daga litattafan
addini wanda na ajin Ζ΄an gaba ne. Hakan ya sa idan ba sa komai ta ke zama
malamar Ummita. Su yi ta karatunsu musamman yanzu da ake cikin hutun dogon
zango na makarantun boko. Idan ka cire Tasleem da Futuha sai samarin, babu
wanda ke zuwa makaranta. Gidan sai yake yiwa Humaira daΙi fiye da a baya.
Ranar wata Asabar da yammaci su na zaune a Ιakinsu, Humaira
ke taya Ummita gyaran sif Ιinta, gaba Ιaya sun sauke kayan Ummitan saman gado.
Humaira sai tsokanarta take yi akan da tuni yanzu an sanya ranar aurenta da
Yusuf, ita kuwa tana kai mata bugu da ninkakkiyar rigarta. Sai kuma ta ja
guntun tsaki ta zauna gefe tana murmushi.
"Ke nifa ina da mijin aure a hannu, kawai dai bai taΙa
zuwa gidannan ba, ba na so kowa ya sani sai na kammala karatu."
Humaira ta zaro ido da wani irin zumuΙi ta ce.
"Don Allah dagaske? Waye wannan mai sa'ar?"
Ummita ta Ιan harareta sai kuma ta miΖe ta ci gaba da ninkin
da take yi.
"Oho, idan ta yi wari kya ji."
Duk irin magiyar Humaira dai ba ta samu Ummita ta furta
komai ba, da ta ga hakan ba mai Ιulla bane sai ta sauya ta ce.
"Toh abu Ιaya za ki faΙamin, Allah kuwan daga shi ba
zan Ζara tambaya ba. Na san shi, na taΙa ganinsa? Eh ko aa?"
Dariya Ummita ta yi.
"Wai ni za ki yiwa wayo ko me?"
Itama dariyar ta yi.
"Allah ba wayo ba, kawai ina son sani."
Ummita ta Ιan yi shiru, ta sani idan har ta ce mata ta san
shi to za ta Ζara damuwa da son ji ita kuwa duk data yarda da Humaira ba ta
shirya kowa ya ji yanzu ba. Sai ta girgiza kai.
"A'a toh."
Jin haka Humaira ta taΙe baki.
"Toh shikenan, idan ta yi wari ma ji."
Kafin Ummita ta tanka sai ga Muhsin ya shigo a guje.
"Adda Humaira, ki zo inji Mami za ku gaisa da Yaya
Kabeer."
Humaira ta ji kanta ya yi wani dum, wani irin Ιacin rai da
bakin ciki na taso mata da ba ta san silarsa ba. Nan da nan ta haΙe fuska tamau
kamar ba ita ke dariya yanzu ba.
"Ka ce gatanan zuwa." Ummita ta amsa jin ba ta da
niyyar amsawar. Ta sani Humaira ta tsani Kabeer, tun ganin da ya yi mata a
gidansu tare da Mami yake bibiyarta. Amma yadda fuskarta ta sauya ita kam ba ta
taΙa ganinta cikin wannan yanayin ba.
"Ke lafiya? Daga ance maki Kabeer ya zo?"
Tsaki ta ja ta miΖe a fusace cike da wata iriyar tsiwar da
ita kanta Ummita ba ta san ta da ita ba ta ce.
"Aikin banza da wofi, na tsani naci da takura wallahi.
Mutum sai shegen naci, itama Mami ta
biyemishi har da wani aikowa a yi kirana." Ta kara jan tsaki. Maganarta na
karshe kan kunnen Raihana da ta shigo Ιakin tana danna waya, baki buΙe take
kallonta.
"Ke, Mami za ki yiwa rashin kunya? Har da tsaki?"
Ko kallonta ba ta yi ba ta juya ta ci gaba da ninkin kayan
da alama ba ta da ko niyyar tashi balle ta je. Ummita ta kalli Raihana itama ta
dube ta, a fusace Raihana ta karaso ta fisge rigar dake hannun Humaira ta yi
jifa da shi. Humaira ta mike a zuciye ta ce.
"Malama na fada! Nace na fada! Kabeer din banza da
wofi! Ba zan je ba din akwai abin da za ki iya yi? Ko waye ya tilasta ni shiga
lamarinsa sai na gasa mishi maganganun da zai yi dana sani!"
Raihana gaba daya ta tsorata, kamar dai Humaira kamar ba ita
ba. Kawai sai ta gifta ta fice daga Ιakin ba tare da ta tanka ba don dama
Raihana akwai tsoro. Ummita ta mike ta kama hannun Humaira a sanyaye.
"Humaira, lafiyarki kuwa? Me ya yi zafi?"
Ba ta ce komai ba kawai ta zare hannunta a cikin na Ummita,
zama ta yi ta yi shiru sai huci ga gumi na tsastsafo mata. A haka Mami ta shigo
dakin, Raihana duk ta ba ta labarin abin da ya faru, kallon Humaira take yi a
nutse, sai kuma ta karasa ta zauna gefenta. A hankali ta dafe hannunta. Humaira
ta kalleta, kawai sai ga mamakinsu ta fashe da kuka.
"Mami don Allah kiyi hakuri, wallahi na tsane shi, ki
ganinsa bana son yi. Kiyi hakuri don Allah ki janye batun zuwa mu gaisa da
shi."
Wani irin kuka ne da sheshsheΖa tamkar wacce ake kokarin
raba ta da numfashinta. Mami da Ummita wacce duk ta firgice suka dubi juna sai
kuma ta rungumo Humaira.
"Kar ki damu, ya tafi ya bar gidan ma. Kuma na yi maki
alΖawari Kabeer ba zai Ζara takura maki ba. Kin ji ko?"
Sai a sannan ta gyaΙa kai ta bar kukan, lokaci guda kuma ta
fara dawowa hayyacinta. Ita dai Ummita ikon Allah ta zubawa ido tana kallo.
Abin dai kamar a wasan kwaikwayo.
Dare ne misalin karfe Ιaya da mintoci, Ιakin ya yi shiru ban
da munsharin Tasleem ba abin da kan addabesu kullum ba abin da ke motsi.
Humaira wacce abu biyu suka hana ta sukunin bacci, ta zubawa tagar Ιakin ido
tana kallon farin wata da ya hasko har cikin Ιakin nasu. Garin babu zafi sai
iska dake kaΙawa kaΙan kaΙan hakan yasa rashin wutar bai hana mutanen gidan
sukuni ba. Ta ja guntun tsaki ta miΖe zaune gami da runtse idanunta.
_'Humaira ba ki kyautata kalamai ga Mami ba. An sani maganar
Kabeer kika tsana, sai dai yanayin da kika yiwa Mami magana kamar wata Humairar
aka chanja ba ke ba. Idan kin yiwa Raihana wannan dama abokiyar yinki ce, amma
ga Mami, kin yi kuskure.'_
Ta tuno kalaman Ummita, wannan na daga cikin abin da ya damu
zuciyarta, Mami fa, matar da ta ke ba ta kulawa da zuciya Ιaya. Ta maye mata
gurbin Dada da Mamarta wacce ba ta buΙi ido ta gani ba. Ta kuma zame mata
abokiyar hira a lokuta da dama idan tana zaune ita kaΙai a gidan. Hakan za ta
dinga ba ta labarin Nijar itama ta ba ta na ainahin garin iyayenta wato Agadez
su yi ta nishaΙi.
Abu na biyu da ya tsaya mata a rai bai wuce na mamaki da
tunanin abin da ta yi Ιin ba. Eh ta san
ba ta son Kabeer, ta tsani ma ganinsa, amma tsanar har ta yi yawan da za ta
kasa Ιoyewa har haka? Ita kam abin ya sha mata kai.
Tana nan zaune dai
ganin Ιatawa kanta lokaci da tunani take yi da b zai magance mata komai ba sai
kawai ta maida kai filo a hankali bacci ya sure ra. Duka wannan zaman da ta yi
har zuwa kwanciyarta akan idanun Raihana wacce munsharin Tasleem ya hana ta
sukunin bacci. Tsoron yarinyar ya Ζaru a zuciyarta, ta kasa kwakkwarar motsi ga
fitsari cike fal a mararta amma ina, ga ni take ai tana miΖewa Humaira za ta
tashi ta shaΖe ta don ta gama ba zuciyarta cewar iskokai ne da Humairar. A
wannan daren dai bacci Ιarawo ne ya sace Raihana.
***
Ta kammala shirinta
tsaf kamar koyaushe za ta wuce wurin koyon girki, ta fito falon. Ummita na
zaune tare da su Muhsin a falon, Raihana kuwa na gefe Ιaya ta hakimce tana abin
da ta saba, latse-latsen waya. Ganin Humaira yasa ta kalle ta sau Ιaya ba ta
Ζara ba don ita ba ta so ma su haΙa ido, har ga Allah tun can tana tsoron mai
aljanu. Tana kuma shakkar yi musu rashin kunya tun wataran tana jss 2 da wata
abokiyar karatunta ta shaΖe ta akan ta zauna a kujerarta ta kuma yi magana amma
ta Ζi tashi. Da ta fusata ta shaΖo wuyanta sai da malaminsu ya kwace ta. Abba
har makarantar ya je, iyayen yarinyar suka ba da hakuri aka kuma sauya musu
aji. Tun daga nan ta ke tsoron duk abin da zai danganta ta da mai iskokai. Ko
kusa da su ba ta raΙa.
"Har kin fito
kenan?" Ummita ta tambaya tana kallonta fuska a sake. Itama murmushin ta
yi.
"Na fito, ina Mami?"
"Tana sashinta." Daga nan ta nufi sashin Mamin, a
falo ta iske ta tana waya tana dariya, ganinta yasa ta yi sallama da Ιaya Ιangaren
ta ajiye waya. Cike da walwala ta ce.
"Ζ³ar Mami har an fito?"
Kunya ta kamata, ita kunyar Mamin take ji wallahi, ta karasa
ta durkusanta gaida ta.
"To, wata sabuwar gaisuwa ce nan ban da wacce muka yi Ιazu?"
Mamin ta faΙi cikin wasa da dariya, Humaira dake sunne kai
ta Ιan murmusa, ita ta manta ma sun
gaisa Ιin. Mamin ta Ζara magana.
"Au, ashe gidan Laila za ki ko? Bari ma na ba ki
saΖonta ki tafi da shi." Mamin daga haka ta miΖe ta nufi Ιaki, can ta fito
Ιauke da leda wacce Humairar ba ta san ma ko mene ba ta karΙa. Ta ba ta kuΙin
mota tana fadin.
"Abbanki ya riga ya fita na mance ban karΙar maki na
motar ba, ki je kawai idan ya dawo sai na karΙa."
Ta gyaΙa kai ta sa hannu ta karΙa da godiya, ganin ta Ζi
motsawa balle ta tashi ya sa Mamin tattaro nutsuwarta gareta.
"Lafiya Humaira? Akwai magana a bakinki ko?"
GyaΙa kai ta Ζara yi a karo na biyu, cikin nutsuwa kuma ta
soma magana.
"Mami dama akan
abin da ya faru jiya ne, ina neman gafara."
Murmushi Mamin ta yi ta girgiza mata kai.
"Kar ki damu, ni nasan ba laifinki ba ne. Hakan ya sa
na yi maki uzuri. Ki cire komai a ranki kedai ki tattara nutsuwarki ki cigaba
da maida hankali ga darussanki. Laila na ta yabon kwazonki don haka ki Ζara
dagewa, na maki alΖawarin Kabeer ba zai Ζara shiga sabgarki ba, kin ji
ko?"
Sai a sannan ta sauke ajiyar zuciya ta samun nutsuwa, ta
amsa da toh daga nan suka yi sallama ta mike ta fita, Mamin ta bita da kallo
tana murmushi.
***
TuΖi Ιan sahun ke yi
cike da nutsuwa, sosai tuΖin ke mata daΙi yayin da iskar dake kaΙawa a garin ke
Ζara jefa ta cikin walwala. Damuwar da ta kwana da shi a ΖarΖashin ranta, tas
ya wanke ya koma annashuwa. Don haka murmushi take yi ma ba tare da sanin tana
yinsa ba. Ba zato ta ji ta yi wani irin hantsilawa sai ga ta a bayan Ιan sahun
nan hannayenta rungume a kan wuyansa kai kace wacce aka goyo. Shi kuwa Ιan
sahun kansa ya Ζumu da jikin gilashin da karfi har sai da gilashin ya tsage,
saura kaΙan adaidaitar ta wuntsila amma Allah ya taΖaita faruwar hakan, sai ya
koma baya da Ζarfi har tayoyin na bugun Ζasa da Ζarfi, wannan ya sa ta koma
mazauninta, lokaci guda ta saki Ζ΄ar guntuwar Ζara sakamakon cikinta da ya bugu
da Ζarfen jikin mazaunin direban yake mata zafi dalilin buguwar da ta Ζara yi
dalilin komawa baya. Ta runtse idanu daidai sadda ta ji salatin jama'a a kansu.
Gaba Ιaya ma ta kasa buΙe idanunta tana dafe da cikinta, ta yi shiru kawai don
hayaniyar ma ba burge ta take ba.
"Sannu Ζ΄anmata, sauko."
Ta tsinkayi Ιaya daga cikin jama'ar wurin na fadi, wasu kuwa
na hayaniya su na fadin ai laifin mai motar ne. Can kuma ta ji an ce.
"Alhaji kai ne da laifi, kai ka bugi motarsu garin cin
burki a kurarren lokaci."
Ta buΙe idanunta a hankali jin wani daddaΙan kamshi a gefe,
a hankali ta sa hannu ta Ιauki jakarta da ta tarwatse a Ζasa, duk tarkacenta
sun zubo. Wani matashi ya shiga tattara mata ita kuwa tana son ta fito a
adaidaitar kamar yanda Ιan sahun ya fita ya zauna gefen kwalta, amma ina
tururuwar mazan dake wurin ya sa ko motsin kirki ta kasa. Da murya irin ta
manyan mutane ya amsa.
"Baba, ba abin zafi ba ne. Na sani ni keda laifi, ina
mai ba da hakuri garesu. Zan kuma yi kokarin gyara Ιarnar da nayi. Ku yi hakuri
don Allah."
Humaira ta juya ta kai duba ga mai maganar, daidai lokacin
da shima ya Ιan rankwafo don ya yi mata sannu da kuma neman alfarma akan ta
sauko su je asibiti. Kalma Ιaya ta kasa fita a bakinsa da ya yi nauyi.
Ζafafunsa suka soma ΖoΖarin kayar da shi. Zai iya rantsuwa ba kaffara son
budurwar yarinyarnan yake da idan da ace Uwargidansa ta yi haihuwar wuri to fa
ya ci ya yi haihuwar fari da ita. A Ιangaren Humaira kallon da ta bishi da shi
bai wuce na son ganin marar hankalin da bai iya tuΖi akan Ζa'ida ba har yake
shirin kai ta barzahu. Babban mutum wanda ba gigin kuruciya tattare da shi, ya
sha manyan kayansa har da babbar riga da hula. Kana ganinsa dai ka ga wanda ya
ba arba'in baya. Ganin yadda ya Ζuramata
idanu sai nan da nan ranta ya yi masifar Ιaci, ta ja tsaki wanda ya ba Alhajin
nan mamaki, ba ta jira komai ba ta sauko daga adaidaita sahun ta Ιaya Ιangaren
mutane na mata sannu. Matashin da ya tattara mata kayan ta yiwa godiya ta karΙi
jakarta, ba ta so dubawa ba amma da yake ya matsa sai kawai ta duba, komai nata
yana nan cif ba abin da ya Ιata. Dakyar take tafiya dalilin gefen cikin da har
sannan ke mata Ιan zugi.
"Sannu baiwar Allah, kiyi hakuri ba da gayya hakan ta
faru ba. Direbana ne ya Ιauki waya bisa umarnina ba kuma mu ankara ba hakan ta
kasance. Akwai inda ke maki ciwo sai a karasa asibiti."
Ya karashe yana kai idanunsa kan gefen cikinta da take ta
faman dafewa. Ganin haka sai ta saki
cikin don ba ta kaunar taimakonsa saboda irin kallon da yake jifanta da shi,
kwatankwacin irin kallon Kabeer. Fuskarta a daure tamau ta amsa.
"Na ce maku babu abin da ke damuna, lafiyata kalau.
Nagode da taimakon."
Daga haka ta karasa tana cije lebba ta yiwa Ιan sahun sannu
kafin ta kai hannunta dake rawa don har lokacin ba ta dawo daidai daga razanin
da ta shiga na hatsarin ba ta fiddo kudi za ta ba Ιan sahun na hakkinsa dake
wurinta amma ta kara tsintar muryar Alhajin nan wannan karon muryarsa har Ζ΄ar
rawa take yi, kirjinsa kuwa bugu yake da karfi tsabar son da ya shiga zuciyarsa
farat Ιaya na yarinyar.
"Ki bar shi zan
biya. A wane unguwa kike sai mu sauke ki?"
Jama'ar duk idanunsu a kansu, wadanda suka lura da yanayin
mutumin ba su ga laifinsa ba don Humaira ta haΙu iyakar haΙuwa, sai dai a ganin
wasunsu, girma ne zai fadi muddin ya bari ta gasa mishi magana. Aikuwa masu
wannan tunanin ba su kai ga furtawa ba suka tsinkayi muryarya cike da tsiwa
tana magana tana kara zaro manyan idanunta masha Allah.
"Baba ina
mutunta furfurarka hakan yasa nake gargadinka akan ka fita a hanyata wallahi
tun ban gasamaka wacce za ta hanaka bacci ba. Haba! Wannan ai shiga sharo ba
shanu ne, ka kusan kaimu lahira na maka uzuri yanzu kuma me ya shafeka da kudin
da zan bayar? Da kai ke biyamin kudin motar? Ina ruwanka da ni?" Daga haka
ta ja dogon tsaki ta miΖawa Ιan sahun dubun gaba daya na motarta zuwa da komawa
ba tare da ta jira chanji ba, daga haka ta juya daidai sadda wannan matashin ya
kara miΖo mata ledar da shaf ta mance da batunsa, saΖon Mami zuwa ga Anti
Laila. Sai lokacin ta ga ashe ma leshi ne sai atamfa. Godiya ta yiwa matashin a
fusace ta bar wurin tana huci, ga cikinta inda ta Ιan bugu bai bar raΙaΙi ba.
Kunya da tarin bakin ciki suka lulluΙe Alhajin, bai taΙa zaton yarinyar ba ta
da kunya ba da tuni ya Ιoye zalamarsa a kanta.
"Sai hakuri
Alhaji, yaran yanzu ba su da kunya."
Ya basar da zancen yana maida duba ga Ζan sahun nan da ba da umarnin ya tashi su karasa asibiti ko
kuwa dai ya sallame shi yanzun a nan, Ιan sahun ya aminta da hakan, nan take ya
ba shi kuΙaΙe masu Ιan kauri gami da Ζara ba shi hakuri. Daga haka ya juya zuwa
motarsa har lokacin bai daina jin kunya da Ιacin rai ba su sake shi ba. Ya kuma
Ζudurta a ransa idan har haka yaran zamani su ke, to ya yi Allah wadai da ire
irenta, ba kuma ya jin zai kara kallonta da sunan wata da ya taΙa gani har ya
ji kaunarta cikin ransa.
***
A Ιangaren Humaira
dakyar ta karasa gidan Anti Laila, ita sai da suka yi nisa ma ta tuno ba ta da
chanjin da za ta sallami mai adaidaitan don haka ta ce ya jira ta kawo mishi.
Wajen Anti Laila ta karΙa bayan ta mata bayanin hatsarin da suka yi, nan kowa
ya hau ta da sannu. Anti Laila da kanta ta kira Mami ta shaida mata, hankali
tashe ko mintuna talatin ba a yi ba sai ga Mamin da direban Abba. Daukarta ta
yi suka nufi asibiti, koda likita ya duba ta ya tabbatar kawai buguwa ce.
Magunguna ya ba ta sannan suka wuce gida. Maganin ta sha bayan ta ci abinci ta
kwanta.
Abba har Ιakinsu ya shigo ya duba ta, ganin da sauki bacci
ma take ya sanya shi fita.
Sai da ta yi kwanaki uku ba ta leΖa ko farfajiyar gidan ba a
rana ta hudu ta koma zuwa koyon girke-girke abin ta.
***
Rayuwar ta ci gaba
da tafiya yau dadi gobe babu, rashin dadin a wajen Humaira bai wuce na yadda su
Tasleem ke kara nuna mata kiyayya a fili ba. Har ta kai da an wayi gari
watarana sun yi mata sharrin sata, domin an tashi Mami tana neman kudin har
dubi ashirin da ta ajiye Ζasan filo, gaba daya ran Mami a Ιace yake, sannan ma
ita Humaira ba ta nan kuma ita ce ta gyara Ιakin kafin ta fice gidan Laila.
Ganin an duba ko'ina sai Futuha da su Yassar suka ba da shawarar a duba Ιakunansu. Mami a farko ta Ζi, sai da Ladidi ta ce ya kamata a duba
ko'ina tunda dai nema ake kuma abin da yasa Ladidin faΙin haka ganin su na
neman Ιorawa yarinyar kirki Humaira ita
kuwa tana da yaΖinin idan har Humaira ce
ba za a sami ko sisi na wani a kayanta ba. Tasleem da ta dage tunda Humaira ce
ta yi gyaran Ιakin a soma duba kayanta ya sa Ummita cike da kwarin gwuiwar
sanin wace ce Humaira ta shiga fiddo kayan Humairar daga sif dinta. Sai dai tun
kan ta yi nisa Futuha ta zura hannu ta jawo wata doguwar riga.
"Kambu! Dama yarinyar nan ita ta Ιaukarmin wannan
rigar? Tasleem ku dubi rigar da nake tunanin ta Ιata a wajen wanki?"
Mami ta kalle su, ta yi shiru da mamaki. Can kuma sai ga Ιan
kunne da sarΖa sun faΙo. Raihana ta zaro ido tana Ιauka.
"Innalillahi, ku ga sarΖata da nake nema kwanaki? Ashe
ita ta Ιauka?"
Kai kamar wasa jikin Ummita na sanyi da wannan sharrin, ba
ta yi aune ba ta kai hannu kan takardun kuΙi, tsabar razanar da ta yi ya sa ta
fiddowa da sauri. Ladidi ce ta karΙa tana salati ta Ζirga, aikuwa dubu ashirin
cif ne wanda Mami ke cigiya, Ummita kawai sai ta fashe da kuka tana faΙin.
"Wallahi Mami wannan sharri ne, Humaira ba Ιarauniya ba
ce. Ko kwandalar mutum ta gani idan tana aiki ajiyesu take a wurin da ta gan
su."
Mami dai ba ta iya magana ba domin kanta ya Ζulle, a sanyaye
ta sa hannu ta karΙi kuΙin ta fice a Ιakin tana ji su Yassar na yiwa Ummita
masifa wai sai ta faΙi wa ke mata sharrin amma ba ta ko iya tankawa ba. Ita
kanta ta sani sata ba ya daga halayyar Humaira don ta sha ajiye kuΙin da suka
fi waΙannan kauri ba ta taΙa su ba, amma ta sani mutum ka iya sauyawa. Bare ma
a irin gidan nan na Alhaji Isuhu da ba a facaka da kuΙi.
Humaira ba ta dawo gidan ba sai yammaci bayan la'asar, da
murnarta ta tura kyauren gate ta shigo bayan ta gaida Baba dattijo dake zaune a
benci yana siyan rogo a wurin Ζ΄ar tallah. Farin cikin bai wuce na yadda suka yi
snacks har biyu a yau ba, samosa da springroll kuma cikin ikon Allah ta yi ya
yi kyau a ido ya kuma yi daΙi a baki har a foilpaper ta nannaΙe ta kawo don
Mami ta ci ta ji. Muryar Ζasim ta tsinta a kanta.
"Ζarauniya ta dawo."
Kallonsa ta yi gabanta ya faΙi, a duk irin wulakanci da
jefa-jefan mugayen sunaye da suke mata, babu wani cinikinsu a ya taΙa kiranta
da Ιarauniya wannan ya sa ta ji wani irin sanyi har ta kasa mayar masa da
martani yadda ta saba idan ya jefe ta da marar dadi. Ya Ιan Ιaga gira.
"Oh, bakin ta kanwa ya yi la'asar kenan saboda kin sani
kin sata shiyasa. Dama ustazancin ashe na Ζarya ne, toh yau asirinki ya tonu.
Ζan adam butulu."
Ta dafa kirji idanunta da suka cicciko da kwalla tun soma
maganarsa ta kafa mishi.
"Yaya Ζasim sata fa ka ce? Ni na yi satar?"
Ya harareta ya wuce kawai ba tare da ya ce komai ba. Ta
bishi da kallo har ya shige gidan, itama a hankali ta soma taka Ζafafuwanta da
suka yi mata nauyi saboda mutuwar da jikinta ya yi ta yi cikin gidan kirjinta
na harbawa.
***
Tasleem, Dawud, Yassar da Futuha ne zaune cikin falon sai
dai ba ta sha mamakin Ζin amsa sallamarta da suka yi ba, dama ya lafiyar giwa
ballantana kuma an jefe ta da kashi? Su na ganinta Tasleem ta miΖe ta yi kerere
gabanta hannuwa a Ζugu ta ce.
"Ζarauniyar banza da wofi, kin dawo kina wani sum-sum
kamar munafuka. Koda dai dama munafukar ce, Mamin da ta daukake ki tana maki
kallon kamar wata waliyya ai gashinan kin watsa mata Ζasa a ido. Ke ni ba
wannan ba ma, earpiece dina da na jima ina nema idan kinsan ke ce Ιarauniyarsa
wallahi tun wuri ki fiddomin abina. Atoh, bari ma Abba ya shigo gidan, ko Mami
ba ta faΙamasa ba sai mun faΙa."
Humaira wacce ta kasa tsaida hawayenta, kallon Tasleem din
kawai take har ta kai aya, lebbanta na rawa amma ko harafi guda ta kasa fitarwa
tsabar baΖin ciki. Wannan wace irin baΖar rana ce a wajenta haka da za a wayi
gari da yi mata Ζazafin sata? Ta kasa motsawa, haka Futuha ma ta taso da nata
kalar rashin mutuncin, su Yassar na taya ta. Ba ta iya cewa uffan ba sai kukan
da ta ke rusawa kamar ranta zai fice. Tsawar da ta ji an daka musu ya sa ta
kallon hanya, ruwan hawaye ya sa ganinta komawa dishi-dishi, sai a hankali
bayan ta Ιan runtse idanu sun Ιan zuba ne sannan ta lura ashe Mami ce. Ζarasowa
ta yi fuskarta a Ιaure, sai ta koma mata Mamin da ta fara cin karo da ita a
ranar farko na zuwanta gidan. Kirjin Humaira ya hau dukan tara-tara, ta runtse
idanu saboda ta gama hasaso abin da zai afku, wato mari za ta sha a wajen Mami,
sai dai ga mamakinta ta ji akalar faΙan sam ba a kanta yake ba, su Tasleem ta
shiga yiwa tamkar za ta ari baki.
"Ashe rashin mutuncin naku ya kai har haka? Raini ne
wannan ku ka yimin ko mene? Ban hana Ιayanku yiwa Humaira maganar abin da ya
faru ba? Ina ce har Ιaki ke Futuha kin biyo ni akan sai an Ιauki mataki na ba
ki saΖo ga Ζ΄an uwanki cewar na kashe maganar kada wanda ya tayar? Oh saboda ku
nunamin ni banza ce wurinku, hukuncina ma na banza ne shi ne dalilinku na yin
watsi da zancena a kwandon shara ko?! Toh wallahi ku fita idona tun wuri, kuma daga
rana irin ta yau ku ka Ζara tada wannan batu sai na saΙamaku kamanni."
Tana kai wa nan ta ja hannun Humaira zuwa Ιakinta. Ta bar
yarannata a tsaye tamkar su haΙiyi zuciya su mutu don haushi, Yassar ne ya soma
jan wani dogon tsaki kafin ya sa kai ya bar falon, Dawud ya mara mishi baya.
Tasleem kuwa Ζwafa ta yi.
"Innalillahi, ke Futuha na soma tsoro, na yarda dagaske
ne da ake cewa Ζ΄an Ζasarsu na da asirai, anya wannan shu'umar yarinyar da
Kawunta hakanan suka bar mana uwa? Anya ba sai da suka shuka tsiyarsu
sannan ta dawo wajenmu ba?"
Futuha da ta kasa magana kawai sai ta ja tsakin itama ta Ιauki
wayarta ta wuce sashen Anna idanunta cike da kwallar baΖin ciki.
***
A gefen Mami kuwa, su na shiga Ιakinta ta rungume hannuwanta
a kirji ta daure fuska tamau har sai da Humaira ta sha jinin jikinta.
"Zauna." Ba musu ta zauna a saman kafet, ita kuwa
ta hakimce a gefen gado.
"Na tsawatarwa yarannan saboda na riga da nasan takun
saΖar da ke tsakaninku, ba na son a samu fuskar da za su Ζara Ιora maki karan
tsana a matsayinki na yar uwarsu ta jini. Wannan Ιin ma da suke gwada maki
fatana su daina na kashe shi gaba Ιaya. Amma meyasa haka Humaira? Har yanzun
ina kokwanto akan kin aikata wannan laifin na Ιaukar kudi a Ιakina, amma
idan na tuna ganin da na yiwa kuΙin a cikin kayanki sai zuciyata ta
tsinke. Ki faΙamin iyakar gaskiyarki, kamar yanda idan na ci karo da Ιaya cikin
su Tasleem sun aikatamin laifi zan hukunta su, kema matuΖar da zuciya Ιaya nake
zaune da ke ya zama wajibi na dauki mataki idan kin yi ba daidai ba."
Humaira ta ja majina tana kallon Mami. Girgiza kai ta soma
cikin muryar kuka ta ke magana.
"Wallahi Mami, Allah Ιaya, ba zan yi wasa da Ubangijina
wurin yi maki Ζarya ba, ban taΙa Ιaukar ko abin sakacen haΖori a Ιakinki ba
tare da izninki ba ballantana kuma kudin da ba nawa ba. Mene ne bakya kokarin
yimin a gidannan da zan yi maki sakayya da hakan? Kina yimin kyautatawar da ko
na rayu da mahaifiyata abin da za ta yimin kenan. Toh a wane dalili zan zama
butulu har na Ιauka daga asusunki? Mami wallahi ban Ιauka ba, ba ni kuma da
masaniyar yanda aka yi kudin suka je cikin kayana, nidai na san na maki gyaran Ιaki,
na kuma adana su a inda na gansu, na fita zuwa gidan Anti Laila."
Mami ta yi shiru tana nazarinta, duk kushen mai kushe ba zai
taΙa zama da Humaira ya ji ta masa karya ko sau Ιaya ba. Toh wannan dabi'a ce
ta mahaifiyarta, ta sani sarai mahaifiyar Humaira haka take da faΙar gaskiya.
Ta san kuma ko a gaban Abban maganar ba za ta chanja zani ba. Sai ta yi nufin
kasheta a yanzu ta hanyar numfasawa ta dafa kan Humairar cikin taushin murya ta
ce.
"Ya isa hakanan, bari kukan kar ya ja maki ciwon kai.
Na yarda dake ai dama, sai dai kin san kudi ba zai kai kansa cikin kayanki ba
ko? Koda ace ba ke kika kai ba akwai yadda aka haihu a ragaya, kin ga kuwa dole
na bincika matsayina na matar gida ko?"
Humaira ta gyaΙa kai har sannan tana sauke hardadden
numfashi irin na wanda ya ci kuka ya Ζoshi. Mami ta dora da fadin.
"Toh don haka kar ki fahimce ni baibai don na tuhumeki,
ya zama dole na aikata hakan ne ko don sauke hakki, yanzu kuma da ya kasance ba
ke ba ce, zan bincika a sannu gaskiya za ta yi halinta. Tashi ki je ki ci
abinci ki huta."
Humaira ta gyada kai kawai ta mike ta fita. Har sannan
jikinta bai bar Ιari ba, sharri ya fi komai Ιaga mata hankali, ta tsani sharri,
ta kuma ci alwashin ita kanta za ta dage da addu'a har sai gaskiya ta yi
halinta don a yanzu kam ba ta da amsar ba su Tasleem sai lokacin da komai zai
bayyana muraran.
A can Ιaki ma Ummita ta tarar tana nata hawayen, sai ya
zamana ita ce mamai rarrashin Ummitan da nuna mata ai Mami ta fahimce ta.
Ummita ta labarta mata yadda komai ya faru. Ta kara da fadin.
"Ba ni da tabbaci akan ko su Tasleem ne da aikata
hakan, amma shakka babu ina zarginsu."
Murmushi Humaira ta yi.
"Kar ki damu yar uwa, idan ma su ne ina mai tabbatar
maki wataran gaskiya za ta bayyana."
Daga haka suka bar zancen, koda Abba ya zo, babu wanda ya
tunkareshi da zancen don ba karamin gargadi da jan kunne Mami ta yi musu ba,
koda Anna ta hau faΙa, sai Mami ta sanyayar mata da jiki da faΙin abin da ta fi
tunanin akan sharrin da aka yiwa Humairar. Dole itama Anna ta lallaΙa su akan
zanceya mutu. Daga ranar kuwa ba a kara tayarwa ba kuma basu fasa kiran Humaira
da wannan sabon suna na Ιarauniya da suka laΖaba mata ba. Wanda hakan ya fi
komai yi mata zafi, duk kuwa da Mami ta tsawatar amma a fakaice a bayan idon
Mamin ba sa fasa faΙi.
***
WATA BIYU BAYAN
HAKA...
Ranar ta kasance yammacin Asabar, gaba Ιaya ahalin gidan su
na nan idan ka cire Abba wanda ya fita zuwa kasuwa tare da Dawud. Fuskar Mami a
kallo daya za ka shaida tana cikin farin ciki. Su Tasleem dai murnarsu ba yabo
ba fallasa. Humaira kuwa da Ummita aiki suke tare da Mami ba kama hannun yaro,
Raihana na can Ιangaren yayannasu tana aikin gyara bisa dole don ba yadda za ta kaucewa umarnin Mami, sai dai
rabin aikin tana yi ne amma hankalinta na ga chatting din da take yi da sabon
saurayinta wanda ya kasance abokin yayan Ζawarta.
Humaira ta zage
damtse wurin yin kayan snacks yayinda Mami da Ladidi su ke aikin girka masa
dambun shinkafa da kuma kunun aya, kamar dai yanda ya buΖata. Sun kammala da
wuri suka jera komai a saman tebur, Humaira a gajiye ta nufi hanyar Ιakinsu da
zummar watsawa jikinta ruwa adalilin zafin da ke tasomata, Mami ta dakatar da
ita ta hanyar kiranta. Juyowa ta yi gami da amsawa.
"Maza je dakin Yayanki ki dubamin waccan mashiriciyar
ko ta kammala gyaran nan, idan ta kammala ki dawo ga charcoal ki kunna a sanya
turaren wuta."
Ta amsa da toh sannan ta juya cikin bin umarnin Mamin. Tana
zuwa daidai kofar dakin Yaya Mubarak ta ji muryar namiji kamar ta waya ya na
fadin.
"Um um sweetheart, ban gaji da ganin su ba, ni da ace
za ki Ιan buΙemin ko saman ne kaΙai na kalla zai taimakamin ya magancemin wani
abin. Please taimakamin kin ji? Gaba Ιaya ta miΖe wallahi."
Humaira ta zaro ido, sam ba ta fahimci komai ba, ta na
shirin faΙawa Ιakin don ta ga meke gudana ta tsinkayi muryar Raihana na amsawa
da wata murya tamkar ba nata ba tana wata iriyar shagwaΙa.
"Um um Baby, ba zan iya buΙemaka ba ina jin
kunya."
"Toh naji, ki yimin hotonsu na miki alkawari ina kalla
zan goge, nima zan aikomaki da hotona nikam ko ace ba ki goge ba ba zan damu ba
saboda ina maki son da nake jin cewa komai na jikina mallakinki ne koda ba mu
yi aure ba. Uhum?"
Humaira ta dafe kirji, yanzu kam ta fahimta, ta gane komai.
Nan da nan ta nemi gajiyar da ke Ιibanta tana tafiyar rangaji ta rasa, da wani
irin azama ta daga labulen dakin ta fada ba ta ko tuna da sallama ba. Raihana da ke fuskantar
madubin dakin rike da waya tana videocall da wanda ta kira Baby, ta hango Humaira
ta cikin madubi, ba ta san lokacin da ta kashe kiran gaba daya ba gami da
saurin ajiye wayar saman madubi. Cikin rawar baki da danne firgicin da ta shiga
na irin kallon zargin da Humaira ke watsa mata ta ja guntun tsaki tana kama
gefen bedsheet wanda tuni ta kammala gyaransa amma ta hau kara cusawa.
"Ke kuma Malama kawai sai ki faΙomin haka babu sallama
babu komai?"
Humaira ta karasa, ita ban da haushin Raihana da ta ji, har
da wani irin bakin ciki da tsanar saurayin da Raihanan ta yi waya da shi ta ji.
Ta yarda ba su ga maciji da yan uwanta, amma fa tana kaunarsu kuma tana ji a
jikinta sai inda karfinta ya kare matukar ta ga Ιayansu zai cutu. Don haka tana
zuwa saitin Raihana ta fizgo hannunta suka kalli juna, Raihana har sai da ta yi
taga-taga za ta fadi kafin ta warce hannunta a tsorace, da karfi ta ce.
"Ke kuma Malama wai mene haka? Me na yi maki za ki
nunamin hauka?"
Ta fadi ne cike da karfin hali domin a tsorace take, tana
gudun ace aljanun Humairar ce suka tashi. Humaira wacce idanunta har sun rine
tsabar bacin rai ta kalleta sosai.
"Raihana kina da hankali kuwa? Kin san me kike shirin
aikatawa kanki? Ζangare masu muhimmanci da girma a jikinki wani jakin banza ya
ke so ki tura masa? Kina hauka ne? Wannan saurayi ne da za ki kula? Toh wallahi
muddin kika yarda kika aikamasa kin gama cutar da kanki har abada, balle kuma
akai ga ya nemi ku hadu da shi a waje. Ina iliminki ya tafi? So ba hauka ba ne
ki bude idanuwanki ki fidda baragurbi cikin rayuwarki."
Raihana da tun da ta fahimci dagasken Humaira ta ji dukkan
hirarsu sai ta hau borin kunya ga zufa na yankowa saman goshinta har yana jiΖa
sumar dake kwance a wurin.
"Me kike nufi? Ni ba ni da hankali ne da zan tura masa?
Ko kin dauka shashasha ce ni? Toh ni nasan yanda nake tafiyar da ire-irensu don
haka ki rabu da ni. Wannan rayuwata ce. Zan gudanar da ita ne yanda na so. Bai
shafeki ba."
Humaira ta yi shiru, can ta nisa za ta kara magana wayar
Raihanan ya hau kara, aikuwa da azama ta nufi wayar har tana ture Raihana.
Ζagawa ta yi ta sa a kunne, Raihana na son dakatar da ita amma tana tsoron kar
ta sha duka a hannunta.
"Sweetheart na ji shiru, muna waya..."
"Ba ita ba ce, wannan yayarta ce. Zan kuma yi maka
gargadi da babbar murya. Wallahi wallahi ka kara gangancin neman yar uwata da
tura maka wani hoto na sassan jikinta sai na nunamaka ba kowace mace ake taΙawa
ba a sha ba. Sai ka raina kanka. Banza dan akuya kawai! Tirr da matasa irinku
wadanda ba su ajiye komai a cikinsu ba sai tsabar iskanci da baΙala. Mu zuba ni
da kai mafashi ya fasa!"
Ba ta saurari me zai ce ba ta datse kiran ta wurgawa Raihana
wayar tana jifanta da muguwar harara, Raihana dai kasancewar ta yi amannar
wannan jinnun Humairar ne ke magana ba ita ba, ta kasa kataΙus sai rawar jiki
tana ji kamar ta saki fitsari a gefe guda tana jin bacin rai da tsanar shiga
hanci da kudundunen da take mata amma ba dama ta yi magana, ta kuma sa a rai za
ta yi duk yadda za ta iya ta ga ta ba shi hakuri kar ya kai zancen Humaira zuci.
"Idan kin kammala wayar ashararancin sai ki yi sauri ki
kammala aikin Mami na jira. Shashasha da ba ta san ciwon kanta ba."
Daga haka Humaira ta ja tsaki ta fice cikin zafin rai. Wayar Raihana na ta
Ζara amma ta kasa Ιagawa don gani take yi da zarar ta Ιaga aljanun Humaira za
su isar mata da saΖo ta kuma dawowa, wannan karon kam ta sani lugudar ta za ta
yi mata. Hawaye na zubomata tana ci gaba da gyaran dakin, hawayen na bakin
cikin abin da Humaira ta yi mata ne, tun da take samari a duniya ba ta taΙa yin
wanda har a zuciya ta ji tana mishi son aure ba irin Musaddam, yanzu ga shi nan
ta Ιata mata shirinta. Tana mishi so da zuciya daya wanda take jin ko mene ne
za ta iya yi a kansa. Don haka a gaggauce ta share dakin ta fice zuwa bangaren
Anna domin ta samu damar ba shi hakuri sosai.
Ai kuwa duk kalar hakuri da karyar taΙin hankalin da ta
dorawa Humaira duk domin ya aminta da ita ya kasa, cewa ya yi shi din son da
take mishi bai je ko'ina ba tunda har za ta bari wani ya ji sirrinsu. Raihana
kamar ta mutu don bakin ciki, ta tsinewa Humaira ya fi a Ζirga.
Ita kuwa Humaira umarnin Mami ta cika ta sanya turaren wuta
a dakin ta fice nasu dakin. Koda Ummita ta nemi sanin abin da ya jefa ta cikin
Ζunci, cewa ta yi babu komai. Har ta yi wanka ta shirya ba ta cikin walwala.
Misalin karfe takwas da mintoci Mubarak ya iso gidan. Su
Muhsin suka cika gidan da Oyoyo, Tasleem su ma duk yanda su ke ganin yayannasu
da shige musu hanci da kudundune sun yi murna da ganinsa. Humaira na gefe tana
murmushi ba ta karasa ba tana karemishi kallo. Shi kam kammaninsa da Abba har
ta Ιaci, shima dai ba ya kama da Mami, sai ko baΖi da laushin gashi irin na yan
uwansa da ya dauko. Kansa cike taf da suma ya tara. Bayan ya zauna ganin Ummita
ta karasa ta gaida shi ya amsa cikin sakin fuska ne ya sa itama karasawa su
gaisa. Ya nunata da yatsa ya yi shiru alamar dai so yake ya tuno wani abin. Can
kuwa ya ce.
"Humaira, right?"
Ta dai fahimci so yake ya tabbatar ko haka sunan ya ke sai
ta gyada kai. Su Tasleem suka kwashe da dariya, ya tambayi dalili suka amsa da
ba komai. Mami ta fito fuskarta cike da fara'a, ganin mahaifiyarsa ya mike tsam
ya karasa ya dan rungumo kafaΙarta, ta dan tureshi tana murmushi.
"Ba ka girma ko?"
Ya kuwa kara marairaicewa.
"Girma fa kika ce Mami, yaushe rabonki da ni don
Allah?"
Har lokacin murmushin take yi ta amsa.
"Amma ai ana waya da videocall ko?"
Da wasa ya sake ta ya juya.
"Shikenan bari na koma inda na fito tunda kin Ζoshi da
ganina."
Da sauri ta riΖo rigarsa har duka falon aka dara. Ya ja hannunta suka nufi bangaren Abba su na
hira.
Abba ya yi murna da ganin Ιan nasa, ya kasa rufe baki. Nan
suka hau taΙa hira karshe kuma Abban ya ce ya je ya kimtsa ya ci abinci
tukunna. Da wannan ya mike ya fita, daga uwa har uban suka zuba mishi ido cike
da kauna kowannensu kuma da abin da yake ayyanawa a Ζasan rai.
***
Zaune yake a babban
falon dake cikin Airport din Abuja, ya kalli agogon dake Ιaure a tsintsiyar
hannunsa mai cike da gargasa ya fi a Ζirga, ya maida duba saman wayarsa yana
latsawa. Cikin sa'a kuwa ya ji muryar ma'aikaciyar ya karaΙe wurin inda take
umartar fasinjojin da za su je Kano akan su nufi ciki. Ya mike kuwa don dama
abin da ya zaunar da shi kenan. Hannunsa Ιaya riΖe da trolley Ιinsa yana ja,
tafiya yake da sassarfa. Bayan komai ya kammalu jirginsu ya Ιaga. Isar su keda
wuya, ya yiwa abokinnasa IBB GUSAU waya. Kafin ya kai ga magana ya ji saukar
muryarsa daga gefe.
"Barka da zuwa."
Juyawa ya yi yana dubanshi da idanunsa dake Ιoye cikin wani
arnen baΖin gilashi, sai kuma ya ja guntun tsaki yana Ιan murmushi, lokaci guda
ya ba shi hannu suka yi musabaha kafin su rungume juna suna cike da farin ciki.
Bayan sun saki juna da mamaki ya ga idanun Ibb sun kaΙa, nan da nan ya daure
fuska.
"Ok, hakan na nufin ba ka yi murnar ganina ba kenan na
koma inda na fito ko?"
Girgiza kai Ibb ya yi ya sa hannu yana karΙar trolley dinsa
yana fadin.
"Hakan ba zai taΙa faruwa ba, in sha Allahu ka dawo
kenan. Tafiyar kuma daga ni har Alhaji ba za mu Ζara bari ka yi irinta ba.
Shekarun da ka yi sun isa hakanan."
Ya shafi sumar kansa bai ce komai ba ban da baki da ya Ιan
taΙe ya yi gaba kai kace ya san inda mazaunin motar amininnasa ya ke. Ibb da
murmushi ya mara mishi baya. Suka jera su na gifta filin wurin, Ibb ba gajere
ba ne, amma fa duk tsawonsa bai kama Ζafar abokinnasa ba, kusan su biyun duka
sai ka rantse ba su ne suka gama yiwa juna murmushi da runguma ba, tafe suke su
na kallon hanya kai ka ce ba su san juna ba, duk inda suka gifta sai an bi su
da kallo, Ζ΄an matan dake wurin kuwa ji suke inama inama, inama za su yi nasarar
samun sa'a a cikinsu Ιaya ya yaba, da sun tabbata masu sa'a. Shi yana sanye da
Ζananun kaya yayin da Ibb ke sanye cikin manyan kaya dinkin babbar riga har da
hula kai kace wani Ango.
"Ina ka nufa?" Ya yi tambayar fuska a haΙe a sadda
Ibb ya murza sitiyari ya nufi gate din Airport din, shi ma ba tare da ya kalle
shi ba ya amsa.
"Ka fi kowa sanin inda ya dace mu soma manufa. Tushiya
masomin dawa."
Girgiza kai ya yi.
"No Ibb, i am not ready for it, muje ka kai ni hotel.
Hakan na fi buΖata. Please."
Ba musu Ibb Gusau ya amsa da Alright, ba ya so fadi tashin
da ya jima su na yi da Alhaji ya tashi a tutar wofi, ai an yi mai wuyar da suka
samu ya dawo garin. Don haka kai tsaye Bristol Hotel ya kai shi ya kama mishi
masauki, da wani irin walwala da annuri dauke saman fuskarsa ya fito ya rabu da
shi ya kama hanya don ya je ya ba Alhaji kyakkyawan albishir. Lallai ya san da
zuwan Ιan nasa, amma bai taΙa kawo wa a rana irin ta yau ba da ake shagalin
bikin Ζaninsa mafi soyuwa ba a rai.
Kasancewar gidan
cike yake da jama'a Ζ΄an uwa, makwafta har ma da abokan arziki ne ya sanya Ibb
zagayawa ta Ιangaren Alhajin ya shiga ainahin falonsa na karΙar baΖi. Kamar
yanda ya yi tsammanin hakan ya tarar, wato dai Alhajin ba shi Ιaya ba ne a
falon, yana tare da babban yayansa Baffa Gidado sai Ιan gidan Baffa Gidadon,
HarΙo. Sai ko Ζannensa guda biyu dake zaune su ma a gefe ana Ιan taΙa
hira, kallo Ιaya za ka yiwa fuskokinsu ka fahimci su na cikin annashuwa.
Sallamarsa ce ta katse hirar tasu wadda ke gudana da harshen fulatanci, suka
dube shi gaba daya, ya karaso yana Ζara miΖa gaisuwa a karo na biyu domin dazun
daga gidan ya fita. Alhaji ya amsa gaisuwar yana bin fuskar Ibb da kallo ganin
yadda yake wata irin fara'a na musamman wadda rabonsa da ganin kwatankwacinta
tun a baya kafin afkuwar wasu lamura marasa daΙi. Ganin bakin Ibb na ta motsi
amma ya kasa magana ya sanya Alhaji miΖewa tsaye wannan karon kirjinsa bugu
yake da sauri-sauri.
"Muje." Shi ne kawai abin da Alhajin yace, aikuwa
kamar jira yake har da tuntuΙe a kokarinsa na bin bayan shi. Wata Ζofa suka bi
wacce kai tsaye main parlour din Alhajin na cikin gidan suka faΙa. Ko zama
Alhaji ya kasa hakurin yi su na karasawa tsakiya ya juyo gaba Ιayansa.
"Ibrahim, ya ake ciki? Meke faruwa?"
Madadin ya amsa sai kawai ya rungume Alhajin kafin ya sake
shi yana dariya.
"Mafarkinka ya tabbata zahiri Alhaji."
Alhaji hannunsa har rawa yake ya kama kafaΙun Ibb har
idanunsa sun cicciko da kwalla.
"Ya..ya..ya..da..wo?"
Ya yi maganar da rawar murya, jinjina kai Ibb kafin ya amsa.
"Eh, FADEEL ya dawo."
Alhaji ya sauke nannauyan ajiyar zuciya.
"Alhamdulillah, Alhamdulillah. Yana ina yanzu? Muje ka
kai ni na gansa."
Ibb zai musa amma babu dama domin dagasken dai ba abin da
Alhaji zai saurara. Don haka sai kawai ya juya, Alhaji biye da shi suka fito. A
farfajiyar gidan suka yi kiciΙus da Ango Fu'ad wanda shigowarsa gidan kenan
daga Hotel din da abokan karatunsa suka sauka. Ya karasa ganin irin rawar jikin
da Alhajinsu ke yi, ga Ibb na kokarin buΙe mota.
"Alhaji, fita za ku yi ne?"
Alhaji ya dafa kafaΙarsa fuska a sake ya ce.
"Maza shiga mota." Ba musu ya zagaya ya shiga har
sannan fuskarsa dauke da mamaki, ya kuma kasa tambaya. Ibb bai ko hana Alhaji
wannan yunΖuri ba don ya sani Fadeel zai yi farin ciki kwarai da ganin
Ζaninnasa.
***
Ya yi wanka ya shirya tsaf cikin riga body hug fara
Ζal sai blue jeans. Yana zaune yana kurΙar ruwan shayin da aka kawo mishi,
hankalinsa kaf yana wajen Mahaifinnasa, wata zuciyar na ce mishi ya je ya gan
shi, wata kuma na kwaΙarsa. A hankali ya ajiye mug din dake hannunsa ya jingina
kai jikin kujerar yana mai lumshe idanunsa. Dogayen gashin idanun suka kwanta
luf saman fatar wurin. Ji ya yi ana buga Ζofar, ya buΙe su kafin ya miΖe. Yana
da tabbacin Ibb ne. Hakan yasa koda ya bude bai tsaya kallonsa ba ya juya ya
koma cikin Ιakin gami da faΙin.
"Wato gadina ka koma kenan?"
"Muhammadu." Ya tsaya cak a tsakar Ιakin, kaf
duniya mahaifinsa kaΙai ke kiransa da ainahin sunansa, da hanzari ya juyo, tuni
lumsassun idanunsa sun kaΙa. Alhajin ya taho da sauri ya rungumeshi, shi kuwa
ya tsaya kamar wanda aka dasa a wajen ya kasa motsi. Fu'ad da bai san wainar da
ake toyawa ba sai yanzun, kawai kuka ya sanya tsabar murnar ganin yayannasa da
ya nisanta da su saboda wasu dalilai. Ya karaso da sauri ya haΙa daga Alhajin
har Fadeel ya rungume yana kuka. Duk jarumta irin ta Fadeel sai kawai ya ji
hawayensa sun zubo. Suka saki juna Alhaji da kansa ya sa hannu yana share masa
hawayen.
"Ashe da raina da lafiyata ban mutu ba zan ga wannan
rana? Alhamdulillah."
Abin da Alhajin ya furta kenan. Fadeel ya yi murmushi da
gefen kumatu yana dafa kafaΙar Fu'ad.
"Ango, har ka girma za ka yi aure."
Suka yi dariya har Ibb, Fu'ad kuwa yan sunkuyar da kansa
gami da shafar Ζeya. Nan fa Alhaji ya matsa akan lallai sai ya tattara sun tafi
gida da shi. Anan ne kuma ya tamke fuska kwarai, ya koma Fadeel Ιinsa na
ainahi.
"Muddin tana gidan nan ba zan iya shiga ba. I am sorry
Alhaji."
Jin haka Fu'ad da Alhaji suka kalli juna suka yi murmushi.
Shi sai a lokacin ma ya ji nauyin Fu'ad din, wai uwarsa yake ikrarin ba zai
shiga gidan idan tana ciki ba.
"Yaya Fadeel, Mama ba sa tare da Alhaji, tayi wani
auren a garin Kogi. Sai dai ko Anti Amarya our new Mum."
Sai Fadeel ya kasa cewa komai, ya maida dubansa ga Alhajin,
ya gyaΙa masa kai don ya Ζara tabbatar da abin da Fu'ad ya faΙi.
"Yanzun ka shirya bin mu?"
Ya jinjina kai yana murmushi. Ibb tuni ya soma haΙa mishi
shirginsa. Fu'ad ya karΙi akwatin suka fito baki Ιaya, suka yi mota yayinda shi
kuma Ibb ya tsaya a reception.
Isar su gidan kai tsaye suka nufi sittingroom wajen su Kawu
Gidado, sai dai tuni sun fice masallaci gabatar da sallar La'asar. Koda
dawowarsu ganin Fadeel gaba Ιaya dakin ya kaure da murna. Magana dai ta bazu a
gidan Fadeel ya dawo, babban Ιa namiji a wurin maigidan. Nan fa mata
gwaggonninsa Ζ΄an uwan mahaifinsa kowa ya fito zuwa falon. Murna kam ba a
magana. Yayyunsa mata waΙanda kaf dinsu su na da aure sai guda Ιaya bazawara da
aurenta ya mutu take zaune a gidan da yaranta, su din ma kowaccensu ta halarci falon.
Kallonsu kawai yake yi yadda kowacce ke haba-haba da shi, murmushi kawai ya ke
yi don ba shi da tabbacin ko abin nasu ya kai zuci ko aa. Sanin da ya yi musu
daban a baya, ba shi da masaniya akan yanzu.
***
Raihana ce zaune a can lungun gadon Tasleem ta maΖure
a gefe tana zuba kuka ga waya saman kunnenta. Musaddam take ta ba hakuri
adalilin ya Ζi ya huce tun sadda Humaira ta gasa mishi zafafan maganganu. Ya
kuma ci alwashin ko don ya nuna wa Humaira ba ta isa ta tsaida shi daga abin da
ya yi niyya ba, sai ya kusanci Raihana ko ta Ζarfi kuma ya yi hotuna don ya
shayar da ita mamaki. Yana sane da gangan ya Ζi ya huce saboda kawai ya Ζara
fahimtar irin matowar da Raihanan ta yi a kansa.
Sati Ιaya kenan da dawowar Yayannasu amma ko kaΙan
walwalwarta ba ta dawo daidai ba ga wani irin tsanar Humairar da take ji a
ΖoΖon rai amma shakkar kada ta tona mata asiri da ma tsoron ita kanta Humairar
ya hana ta labartawa koda Tasleem ce balle Futuha. Sai Ζawarta da ta ba
labarin, ita kuwa Ζara hure mata kunne ta yi akan kar ta yarda wata can bare ta
raba ta da abin sonta. Da wannan huΙubar da kuma mahaukacin son da take yiwa
Musaddam idanunta suka rufe ruf. A wannan yanayin walwalarta ba ta dawo ba sai
da ta tabbatar ya haΖura bisa alΖawarin za ta zo gidan su Munirat su gaisa.
Humaira ta shigo Ιakin daidai sadda Raihanan ke fadin.
"Shikenan zan zo goben idan har ganina zai samar maka da nutsuwa."
Wannan kalmar ta daki zuciyarta, sai dai ta dake ba ta ko
kalle ta ba ta Ζarasa ciki, dama mayafin abayarta za ta Ιauka zasu je Shoprite
ita da Ummita, Mami ta aike su.
Raihana kuwa ganin Humaira ya sa ta shan jinin jikinta. Ta
kasa magana kwakkwara sai um da humm ina jinka. Guntun tsaki Humairar ta ja ta
fice, ta sha alwashin ko ina ne a goben sai ta bi bayanta ta kuma kama Ιan
iskan dumu-dumu ta ci uwashi.
A falon ta haΙu da Ummita, har suka soma tafiya ta ga
dai hira suke amma ita ke kiΙa da rawarta hakan yasa ta dube ta.
"Wai ke lafiyarki kin wani haΙe rai kamar wacce aka
aikowa saΖon mutuwa? Koda dai Ιata bakina nake dama ai halinki ne. Amma naga ai
yanzun ba kiciΙus kika yi da maΖiyinki naki ba ko?"
Tana nufin saurayi, Humaira ta ja tsaki ta girgiza kai.
"Ba komai fa."
TaΙe baki Ummita ta yi ba ta Ζara magana ba sanin hali. Sai
kuma can don kanta ta saki fuska suka hau hira. Kayan maΖulashe irin su Jam,
Ketchup, Mayonnaise da sauransu, shi Mami ta bada su siyo na Yaya Mubarak. Sun
kammala suna dab da ficewa suka tsinkayi sallama a gefensu. Lokaci guda suka
juya ga mai shi, wani matashin saurayi ne gajere mai Ζiba. Irin Ζibar da ba ta
da muni. Daga yanayin yadda ya saki fuska za ka fahimci mutum ne mai fara'a.
Humaira wacce kallo Ιaya ta mishi ta dauke kai gami da ci gaba da tafiya, ganin
haka itama Ummita ta mara mata baya, ya kuma bin bayansu da sauri ya sha gaban
Humaira.
"Ranki ya dade, kiyi hakuri na tsayar da ke. Nima kuma
na san darajarki da Ζima ta zarce a tsayar da ke a hanya a..."
"Kai Malam saurara don Allah! Ni nan da ka ke gani da
mijina a hannu don haka kama kanka. Muje."
Ta fisgi hannun Ummita ta bi gefe suka fice a nan. Hakan da
ta yi ba karamin Ιatawa Ummita rai ya yi ba, ba yau farau ba, idan da sabo ya
ci ace ta saba da ganin irin cin kashin da yar uwarta ke yiwa samari. Ita har
mamaki take yadda gaba daya Humairar ke sauyawa kamar ba ta taΙa zama haΙa
hanya da wani abu wai shi mutunci ba. Ta fara gasΖata zancen Raihana da
ta ce jinnu ne da ita. Kamar kuma ba ita ba, sai ga shi a hanya ta saki rai sun
ci gaba da hirarsu lafiya lau.
***
Washegari tun safe take dakon Raihana tana jira ta ga
sadda za ta fita ta mara mata baya. Aikuwa wuraren karfe biyu tana zaune a
falon da littafi a hannunta na koyon rubutun hausa tana Ιan duba inda muhsin ya
biyamata, Mami kuwa na gefe tana yankewa Muhsin farce sai ga Raihanar, ta
tambayi Mamin zuwa gidan Ζawarta Munirat. Farko Mamin ta hana sai can kuma da
ta dage da naci ta samu Mamin ta aminta. Humaira ba ta ko Ιaga kai ba balle ta
yi yunkurin miΖewa, har sai da Mami ta soma barin falon, tana nan zaune ba ta
ko motsa ba har Raihana ta fito cikin shigar fita, ta ci wani arnen kwalliya ta
sanya riga da siket da ya yi matuΖar kama ta sai ta dora afterdress a sama
wanda da shi da babu duk Ιaya. Tana fita Humaira ta yi wuf ta miΖe ta zari
hijabinta dake hannun kujera. Tuni ta yi shirinta dama ta sa kuΙi a bayan gidan
wayarta. Bayan Raihana ta bi, sai da ta kai Ζarshen layin ta nemi can jikin
wata bishiya ta Ιoye fuskarta cikin facemask. Haka ta shiga Ιan sahu ta
bi bayanta har gidan su Munirat. Kamar yanda ta zata kuwa hakan ne, wani
saurayi matashi ne tsaye jikin wata mota suna hira da wata budurwa. Raihana na
karasawa ta cafke da budurwar da bayan ta matso ta gane Munirat ce saboda ta taΙa
zuwa can gidannasu ba sau Ιaya ba ba biyu ba.
Can kuma sai Munirat ta shige gida ita
kuwa saurayin ya buΙe mata gidan gaba ta shiga ya maida Ζofa ya rufe.
BaΖar mercedez ce mai baΖin tinted wanda duk iyaka hangen mutum bai isa ya ga
na ciki ba.
Humaira ta ji Ζirjinta na dukan tara-tara da wani irin sauri
ta soma takawa ta nufi wajen kai ka ce kafin ta karasa abin da take tsoron
afkuwarsa ya afku.
Da tsayuwarsu a wajen, da shigar budurwar motar, duka ya
faru ne akan idanun Ibb da Fadeel wadanda ke tsaye a Ζofar gidan su Fadeel Ιin
su na taΙa hira. Ya rako Ibb ne zai wuce gida suka tsaya. Ganin shigar budurwar
ya sa Ibb jan tsaki.
"Wallahi ina mamakin rayuwar Ζ΄an matan yanzu da ba su
da kunya kuma ba su san mutuncin kansu ba. Yau da Ζanwata ce daga ita har shi
sai sun raina kansu."
Ya faΙi ransa na wani irin Ζuna, Fadeel kuwa da zuciya ta
kai mai wuya bai san sadda ya soma takawa ba da sassarfa hakan da ya yi ya sa
Ibb bin bayansa da sauri ya dakatar da shi sanin hali.
"Aa Fadeel, please don't, ba ka san waye ba a.."
"Sai nasan waye? Idan Ζanwartaka ce za ka zuba ido kana
kallo rayuwarta ta Ιaci!"
Yana kai wa nan ya fisge hannunsa, sai dai kafin ya kai ga
tafiya suka hangi Humaira wacce gadan gadan ta nufo motar a fusace. Zuciyar
Humaira har wani tafarfasa ta ke yi, tana isa ta sa hannu ta ja murfin motar
cikin sa'a kuwa Ζofar ta buΙe. Raihana wacce yatsunta ke sarΖe da na Musaddam
gaba Ιaya ta kasa sukuni amma Ζarfin soyayyarsa a ruhinta ya sa ta daurewa
ranta, daidai sadda ya kai bakinsa ne da nufin sumbatar hannun aka wangale
Ζofar hakan ya sa a firgice gaba Ιaya suka juya. Humaira ta fisgo Raihana, ba
shiri ta fito har tana tuntsirawa. Ba ta yi wata wata ba ta Ιauke ta da mari
hagu da dama ga wasu zafafan hawaye da suka zubo saman fuskarta lokaci guda.
Musaddam tuni ya fito ya zagayo wurinta, hannu ya Ιaga shi ga marar kunya zai
ramawa Raihana marin, amma tuni Humaira ta riΖe hannunsa ta ba shi nasa rabon.
Hannunta har rawa yake ta sa hannu ta fisge facemask din da ke rufe a hanci da
bakinta.
Fadeel ya yi mata Ζuri da idanu babu ko kyaftawa yana jin
tamkar gangar jikinsa ne kawai tsaye a wurin, hannu ya sarΖe a kirji yana so ya
ga matakin da za ta Ιauka. Humaira da ba ta san wainar da ake toyawa ba, gaba Ιaya
ba ta tattare da nutsuwa hankalinta kacokam a tashe yake, yana kan Musaddam da
take jin kamar ta shaΖe shi. Ζan firit da shi sai sirantaka, fari ne yayinda
lebbansa suke baΖake wuluk shaidar yana shan sigari. Hannunsa dafe da Ζunci
yake duban Humaira rai Ιace ya ce.
"Ke! Ni kika mara?"
Bai yi aune ba ta kara wanke shi da mari.
"Yanzun ka daina tantama? Eh marinka nayi! Da kuma ace
ni wata mai ikon ce, abin da ya fi mari shi zan maka. Ζan iska marar tarbiyya!
Ka yi amfani da son da ka ga yarinya na maka za ka cutar da ita saboda a
gidanku ba a baka isassan tarbiyyar islama ba sai na bokon da bai amfaneka da
komai ba. Idan har ba ka raba kanka da kanwata ba ina maka rantsuwa da Allah
sai na yi maganinka ta yadda rayuwarka za ta Ζare a kurkuku. Ke kuma..."
Ta juya gaba Ιaya ga Raihana wacce ke kuka ga dukkan
ilahirin jikinta na rawa. Ba ta jin an taΙa tozarta ta irin yau, a gaban
saurayin da take yiwa son duniya? Lallai Humaira ba ta da kirki ko kaΙan.
Aljanun nata ma Ζ΄an iska ne na Ζarshe da alama.
"Kin Ιauka ba shi jikinki shi ne zai sa ya ga
mutuncinki ya gane irin son da kike mishi har ta aureki? Toh kin yi kuskure,
wallahi wallahi duk sadda kila bari wannan Ιan akuyan ya kusanceki kin cuci
rayuwarki har abada Raihana, za kuma ki yi kukan nadamar da babu mai share maki
hawaye. A haka kuke kirana da Ζ΄ar kauye, wannan ita ce wayewar? Toh wannan
birnin naku na jahilai ku ke ciki, idan za ki farka tun wuri ki farka idan kuwa
ba haka ba wallahi muddin irin haka ta Ζara faruwa a kunnen Abba. Wuce kuma mu
tafi tun ban kakkaryaki ba."
Raihana ta dubi Musaddam da ya haΙe girar sama da ta kasa
yana kallonta, ta maida duba ga Humaira wacce ke cika da batsewa kiris take
jira ta fashe ga hawaye kace-kace a fuskarta. Ta lura ma jikin Humairar har
rawa yake.
"Muddin kika bi umarninta ki sani daga yau babu ni babu
ke Raihana, alaΖarmu ya zo karshe. Sannan ke kuma ba ki san waye ubana a Ζasar
nan ba ko? Zan nunamaki daga kaina ba za ki Ζara gangancin marin wani namijin
ba."
"Musaddam Ιan gidan Alhaji Jafar Nababa, right?"
Gaba daya har Humaira suka juya a inda suka tsinci muryar,
Raihana ta yi mutuwar tsaye ganin Ibb Gusau mutumin da yar uwarta Futuha ke
mahaukacin so tare da wani haΙaΙΙen guy wanda ko fuskarsa da take a haΙe ka
kalla, sai ya burgeka. Kunyar da ta ji ne ya sa ta saurin amfani da gefen
mayafinta ta rufe baki da hancinta gudun kar su gane ta. Humaira kuwa kallo Ιaya
ta musu ta maida duba ga Musaddam Ιin fuskarta har lokacin a mugun Ιaure tana
jiran ta ji amsar da zai ba da.
Musaddam ya kai duba ga me maganar, nan da nan ya ji gumi ya
karyo masa, Malaminsa ne a jami'a da ya taΙa yiwa gadara da matsayin Ubansa,
shi kuwa ya nuna masa nashi Uban da matsayi sun kere na babansa. A sanadin wani
rikicinsu sai da Musaddam din ya yi kwanaki uku a ofishin Ζ΄an sanda kafin a
fiddo shi. Ya kasa cewa komai sai shafar Ζeya, Ibb Gusau ya nuna shi da yatsa.
"Kai ba za ka taΙa nutsuwa ba kenan a rayuwa ko? Ina
mai gargadinka, wannan ya zama na Ζarshe, ke kuma zan ba ki lambata duk sadda
kika Ζara ganinsa da Ζanwarki ki kirani kai tsaye nasan maganinsa. Ke kuma ki
yiwa kanki faΙa Ζ΄anmata, kar ki bari shaiΙan ya kaΙa maki ganga, irin su
Musaddam ba su dace da ke ba. Daga ganin yanayin Ζ΄ar uwarki an san daga gidan
mutunci ki ka fito saboda haka please be careful."
Raihana da ta yi mutuwar tsaye da mamakin mutumin da Futuha
ta ce ba ya magana mai tsawo yana zuba zance ta gyada kai. Ga kuma wani iri da
ta ji cewa wai zai ba Humaira lambarsa. Aikuwa Humaira ta miΖa mishi wayarta ya
sanya mata lambar ya danna kira ta fito kan wayarsa sannan ya miΖa mata.
Musaddam dai na tsaye kamar an kafe shi a wurin ya kasa motsi sai wani Ιaci da
ya ke ji a maΖoshi ganin an dake shi an kuma hana shi kuka. Ya yi biyu babu
kenan.
"Ko za su bi ka ka sauke su a gida?" Ya yi furucin
da sassanyar murya. Sai a sannan ma hankalin Humairar ya kai gareshi karo na
biyu don ta mance ma da wanzuwarsa, ranta ya yi fari sol da taimakon da
Ibb ya yi mata, ko ba komai ta ga tsoro fal a saman fuskar Musaddam wanda hakan
ya fi komai faranta mata. Ganin irin kallon da Fadeel ke jifanta da shi ya sa
ta kauda kai.
"Aa mun gode, zamu hau Ιan sahu."
Fadeel kamar ya tanka sai kuma kawai ya basar bai ce uffan
ba. Humaira ta kalle su, kalmar godiya ce kadai ta fito a bakinta kafin ta juya
ta dubi Raihana.
"Muje." Ba musu kuwa Raihana ta bi umarninta, zuwa
yanzu jikinta a mugun sanyaye yake. Ta dai tabbata Humaira ta fi Ζarfinta. Ba
kuma ta son tada wani borin su Ibb su Ζara ganin rashin kunyarta Ζarara.
Bayan tafiyarsu, Ibb ya shiga yiwa Musaddam faΙa mai haΙeda
nasiha, a karshe ya ba shi damar tafiya. Sai da ya bar wurin sannan ya
dafa kafaΙar Fadeel yana murmushi.
"Toh ya aka yi?"
Fadeel ya zura hannuwansa cikin aljihu ya fiddo hannunsa na
dama riΖe da waya ya miΖawa Ibb gami da Ιan Ιara gira kaΙan. Dariya Ibb
ya yi ya girgiza kai.
"No, haba Malam, da wuri haka?"
Ya narkar da wuya.
"Please, ina rantsuwa da Allah ban taΙa jin abin da na
ji a kan wata ba sai ita."
Murmushi Ibb ya faΙaΙa.
"Alhaji da sannu dai Allah zai cika masa
burikansa."
Guntun murmushi Fadeel ya yi.
"Ko? Kai kuma kana neman ka dakile faruwar hakan."
"Ah wane ni? Ba ni na sanya maka."
Ya karΙi wayar Fadeel da tuni ya buΙe, lambar Humaira ya sa
a ciki sai kuma anan ya dafe goshi.
"Oh no, ka ga ko sunanta ba mu sani ba. Da me zan maka
saving?"
Jin haka ya lumshe idanunsa yana hasko kyakkyawar fuskar
Humaira wacce kumatunta har wani sheΖi suke saboda fushi, ya kuma lura ko ya ya
ta buΙe bakinta sai wushiyarta ta bayyana. A hankali ya ce.
"Mrs Fadeel."
"What?" Ibb da kunnuwansa kamar ba su ji ba ya
tambaya. BuΙe idanunsa ya yi ya dube shi dakyau.
"Yes, haka za ka yi saving lambar."
"Aa, riΖe ka yi da hannunka. Ka gani koda wani abun ya
je ya zo, ba za ka kalle ni da shi ba."
"Babu abin da zai je ya zo face alheri. Da yardar Allah
ba ta da miji sai Fadeel."
Ya ba wa Ibb amsa sa'ilin da ya sa hannu ya karΙi wayar.
Aikuwa da hakan ya yi saving sunan. Ibb dai mamaki ma yake, to kodai Ιan
lokacin da ya kwashe ba ya tattare da su ya sauya ne daga yadda ya san shi?
Mutum da zancen aure ma ba ya so a yi mishi, daidai da hira idan ta budurwa ce
aka Ιauko cikin abokai yanzun gayyar za ta watse a wurinsa don tsam yake tashi
ya bar musu wurin yana mitar ba shi da lokacin shirme.
"Sai goben?"
Maganar Fadeel ta katse mishi tunanin, ya sauke ajiyar
zuciya.
"Allah ya kaimu. Amma ina mai ba ka shawarar kada ka
zurfafa, duk abin da aka zurfafa ana shan wuya a cikinsa. Balle kuma irin
wannan faΙawar da ka yi lokaci guda."
Madadin ya amsa sai ya yi murmushi ya soma tafiya kawai,
sanin da Ibb ya yi shikenan sallamar tasu ya sa shima ya nufi motarsa cike da
fatan shi din ma Allah ya kawo mishi mace ta gari ya huta da gorin Ζannensa sun
yi aure sun bar shi da Mahaifiyarsa ke yawon mishi.
***
A can gida kuwa, Mami tun da ta ji wai Humaira ta
fita ba da saninta ba gaba daya ta ji ta kasa sukuni. Har ta kasa Ιoye Ιacin
ranta ta hau faΙa a falon.
"Wannan wani sabon salo ne da har Humaira za ta sa Ζafa
ta fice a gidannan ba tare da neman iznina ba? Me take so na faΙawa Abbanku
idan ya tambaye ta?"
Tasleem da Futuha suka kalli juna suka taΙe baki, yayinda
Ummita da aka kira tuhumar ko ta san inda take, ta ke gefen kujera a zaune.
"Toh wai Mami, ba Humairar na da waya ba? A kira
mana." FaΙin Mubarak wanda ke shigowa falon daga masallaci, tun kafin
fitarsa Mamin ke faΙan fitar har dai ya dawo ba ta chanja zani ba. Ganinsa ne
ya sanya su Tasleem nutsuwa. Mamin kuwa dubansa ta yi kafin ta kauda kai ta ja
guntun tsaki na takaici.
"Kira na nawa kuma? Wayarta idan ba a kashe take ba to
na fi tunanin babu network."
Ya kai duba ga Ummita.
"Ke ba ta faΙamaki komai ba?"
Kafin Ummita ta amsa, Futuha ta yi caraf.
"Nima dai ita nake zargi don babu ta yadda za ta fita
ace ba ta sanar mata ba. Bakinsu daya wallahi Yaya."
Kallon da ya watsa mata ya sa ba ta Ζara cewa uffan ba, Mami
ta ja tsaki karo na ba adadi ta nufi Ιakinta. Ganin haka Ummita ta miΖe ta yi
nasu dakin da zummar gabatar da sallar La'asar, ita kanta tunanin da take yi
bai wuce na inda Humaira ta je ba tare da neman iznin Mamin ba kamar koyaushe.
Tsoronta kar Abba ya dawo ya tambaye ta
ace ta fita alhalin ba ta da makaranta yau.
Aikuwa dai sai wuraren biyar da mintoci suka shigo gidan, ko
ci kanki ba wanda ya cewa wani a cikinsu. Su Yassar dake zaune cikin abokansu a
kofar gidan su ka bi su da kallo.
"Ga uwar girman kan gidannan ta dawo." FaΙin wani
abokin Yassar yana nuni da Humaira. Tun ranar da ya yi gangancin kulata da
sunan so ta ci mishi mutunci yake jin tsanarta. Yassar tsaki ya ja.
"Kai ka so ai dama ka ga kalar nata girman kan, amma ga
mata a gari kamar Ζasa ka rasa ta kulawa sai wannan Ζ΄ar Ζauyen nijar din?"
Sauran suka yi dariya. Shi kuwa Yassar miΖewa ya yi ya bi
bayansu ganin kamar Raihana na sharce hawaye, jikinsa har mazari yake don
muddin ya kasance Humaira ce sila to ya rantse sai ya rama mata koda kuwa gaban
Abba ne ba Mubarak ba.
***
A falon gidan suka
iske su Futuha zaune, sallamar Humaira ta dakatar da Ummita daga shiga kicin,
ta dawo cikin falon da sauri don ta ganewa idonta ko ita Ιin ce. Futuha da
Yasmeen kuwa ido suka bi Raihama da shi ganin yadda fuskarta ta yi ja ga shatin
yatsu kwance saman fuskarta.
"Ke, Raihat, me nake gani haka? Uban waye ya
mareki?!" Tasleem ta faΙi da buΙaΙΙiyar murya tana kallon Humaira. Humaira
da ita dinma kiris take jira ta dube ta dakyau.
"Ni ce nan, ko za ki rama mata ne?"
Aikuwa jin haka gaba daya Tasleem da Futuha suka yo kanta,
ta kuwa shiga tarewa, duk wacce ta bugeta sai ta sa hannu ta rama da iyakar
Ζarfinta, duk da cewar su biyu ne a kanta, ta yi iyakar kokarinta amma itama ta
ji jiki. Ummita ta hau kwala ihun kiran Mami, ga Yassar a gefe da ya Ζi ya
tsawatar don dama ya jima da haushin Humaira a ΖoΖon ransa. Raihana na ihun su
kyaleta akan ba ita ce ta mare ta ba amma inaa dama sun jima su na dakon rana mai kamar ta yau din hakan
ya sa da gayya suka yi biris da ita. Yayinda a Ιangarenta shakkar tonuwar
asirinta take musamman da ya kasance Yaya Mubarak na gari, ta sani koda ace
Abba bai taΙa lafiyarta ba, shi kam ban da lafiya ma, hatta da wayar da take
tunΖaho da ita sai ya raba ta da shi.
Kusan a tare Abba da Mami suka shigo falon. Wata tsawa Abba
ya daka da ta sa gaba daya suka saki juna, Humaira gefen kumatunta na fidda
jini sakamakon yakushi da ta sha da dogayen faratan Futuha. Su kuwa daga mai
riΖe baya, sai mai riΖe gefen fuska da naushin Humaira ya kumbura har ya tasa.
Mami zuciyarta ta yi wani iri, ta kasa magana ta yi shiru tana kokarin hadiye
abin da ke cinta. Abba ya karaso falon ya dube su gaba daya. Humaira tuni ta
durkusa, ganin haka su ma suka durΖusa.
"Mene ne hakan? Wane sabon shashanci ne haka? Ke
Humaira wadannan ba su girmeki ba? Ku kuma manyan wofi ba kanwarku ce ba? Duk
me ya kawo rigimar ne?"
Humaira ba ta ce uffan ba, Yassar ya yi saurin sa baki.
"Abba ba fa wani abu ba ne, Humaira ce ta mari Raihana
har fuskarta ya yi shatin yatsu, shi ne don Tasleem ta yi magana kawai sai ta
taso mata da faΙa wai ta mara ko akwai shegen da zai rama mata. Kalmar shege ya
fusata su suka yi kanta da duka." Murmushi mai ciwo Humaira ta yi lokaci
guda hawayen da take dannewa suka zubo samam fuskarta, zubar hawayen a inda
Futuha ta mata rauni ya sa ta jin zafi amma ba ta ko damu da sharewa ba don
wata azabar ta fi wata, ita daya ta san me take ji a zuciyarta. Ummita ma hawayen
take na ganin yadda gaba daya Yassar ya juya magana. Ita kuwa Mami, karasowa ta
yi ta Ιaga fuskar Raihana tana kallo. Tabbas mari ne, fuskar ta yi ja, ga yatsu
kwance ta ko'ina a gefen fuskar.
"Mari?! Mamana dagaske ne kin mari Ζ΄ar uwarki? Me ta yi
maki da zafi har haka da kika Ιau hukunci da kanki?"
Raihana nan fa ta shiga zare-zaren ido, Humaira ta kalleta
na Ιan dakiku, har abada ba za ta tona mata asiri gaban iyayensu ba. Mami ta
kai matsayin da ko laifin Ιiyarta ta gani za ta iya rufa mata asiri don haka
dakyar ta haΙo abin fadi.
"Ka yi hakuri Abba. In sha Allah ba zan kara ba."
Nan kuma Abba ya kara fusata.
"Oh, dagasken kenan kin mare ta ko?! Wannan ai hauka
ne! Kamar babu manya a gidan? Ke waye ya mare ki?"
Nan ya shiga bude mata wuta, sai da ya gama sannan ya maida
hankali ga su Futuha wadanda duniyarsu ta yi dadi, ko babu komai wacce suke
yiwa kallon ta fi su a wurin Abban yau ya rufe ido ya wanketa tas kamar zai kai
duka. Hakan yasa ba su ji zafin nasu faΙan sosai ba. Sai da Mami ta sa baki
sannan ya bar wurin. Humaira na ta kallon fuskar Mamin don ta hasaso yanayinta
amma ba ta fahimci komai ba sai dai jikinta ya yi sanyi ganin ko kallonta Mamin
ba ta yi ba. Hakan na nufin ba ta ji dadin hukuncin da ta yiwa Raihanan ba?
***
"Ban da abinki
Humaira, duk son da Mami za ta nuna mana ai ba zai kai son Ζ΄aΖ΄an da ta haifa da
kanta ba. Ni ba abin sa ya fi ban haushi irin yadda ba a damu da tambayar inda
ku ka je ba. A jikina nake ji ba hakanan kawai za ki mari Raihana ba, akwai
abin da kike Ιoyewa. Amma wace rana zai maki? Zai siya maki daraja ne a gun
Raihana da yan uwanta kike zato? Babu Ιaya fa, halinsu ne ba na jin za su taΙa
sauyawa."
Ummita ke zubo mata zance sa'ilin da suke kicin su na
gudanar da girkin dare, awanni kusan biyu bayan afkuwar komai, Humaira wacce
tuni ta yi wanka ta sauya shiga cikin riga da siket Ζ΄an kanti ta yi murmushi
daidai sadda ta motsa tukunyar miya ta rufe gami da rage wuta. Juyowa ta yi
tana kallon Ummita da ta mayar da hankali tana juye farar shinkafar da ta dafa
a cikin Ζaton warmer.
"Ban damu da abin da kowannensu zai ce ba, ban kuma
damu ko Raihana ta sauya ba ko aa, abin da na sani shi ne, ko a gaban waye,
kuma a ko'ina ne, su din ko naΖi ko na so, Ζ΄an uwana ne na jini, ba zan taΙa
ganin abin da zai cutar da su na yi shiru na zuba ido ba, sai inda karfina ya
kare. Kar mu ja zancen Ummita, ni yanzu damuwata Mami, ta ina zan soma wanke
kaina a wajenta? Na mari diyarta har shatin yatsuna sun bayyana Ζarara a saman
fuskarta, anya kuwa za ta karΙi dukkan hanzarina? Ni dai na san soyayyar uwa
akan nata, dagaske ne Mami na yi mana so na hakika, amma wace uwa ce za ta kara
kallonka da Ζima alhalin ka sa hannu ka daki nata?"
"Sai ni nan, Maryam."
Gaba daya suka kalli bakin Ζofar shigowa kicin din, Mami ce
wacce ta tsinkayi zantukan Humaira na karshe. Humaira ta zuba mata idanu tana
so ta ga ko za ta fahimci yanayinta, ba ta gane komai ba sai murmushin da ta
gani kwance saman fuskarta. Kicin din ta karasa shigowa sosai ta ce.
"Sai ni nan Maryam, haba Humaira, kina zaton ba ni da
hankali ne? Na sani duk yadda aka yi akwai wani abu da Raihana ta yi kika yi
mata wannan hukuncin. Kar ki manta tazarr fitarku ba nisa, da nayi nazari sai
na ga kodai wani wurin za ta je da bai kyautu ba kika bi bayanta? Kar ki sa
komai a ranki, koda ba ki faΙi komai ba ni na fahimceki kinji ko?"
Humaira ta sauke nannauyan ajiyar zuciya na samun nutsuwa.
Wai mami wace iri ce acikin matan uba? Komai nata daban ne, kirkinta da
kawaicinta akwai mugun yawa. Sai kunya ta lulluΙe ta, ta sunkuyar da kai.
"Kiyi hakuri Mami. Ban yi..."
"Bana buΖatar ji ko sanin komai kinji ko? Komai ya
wuce. Ku hanzarta shirya kayan abinci, Abbanku na jin yunwa."
Suka amsa da toh a gaggauce suka ci gaba da aiki, Mami ta
fice daga kicin din fuskarta ba yabo ba fallasa.
***
Kwance take saman
gadonta tana buga game a waya, hankalinta kacokam ya tafi a game din sai ga
kira ya shigo. Ta yi tsam tana duban wayar, lamba ce da ba ta da masaniya a
kanta. Ganin haka sai ta katse kiran ta ci gaba da game dinta, aka kara kira,
ta katse, a na uku ta Ιaga a fusace amma sai ta danne ta yi sallama. Jin muryar
namiji ya amsa sallamar ya sa ta jin wani abu tun daga tsakiyar kanta har zuwa
yatsun Ζafa, ba ta san ma'anr hakan ba.
"Ina mai ba da hakurin yi maki katsalandan a rayuwa.
Hope ba za ki damu ba idan na ce jiya na karΙi numbernki wurin Ibb Gusau."
Shiru ya biyo baya, ita ba ta fahimci komai ba don har ga
Allah ta mance da su. Jin shiru ya sa Fadeel Ζara magana a tausashe.
"Ok, ba ki gane ba ko? Jiya ni da abokina da ya ba ki
numbernsa akan wannan saurayin Ζanwartaki, Musaddam nake tunanin sunansa
ko?"
Nan da nan ta tuna komai, wannan me kama da aljanun ne mai
shegen kallo. Ta ja guntun tsaki kaΙan.
"Uhm, na gane. Ina fatan lafiya?"
Ya yi shiru yana jin amsarta a wata kala na daban, madadin
ta ba shi haushi sai kuma ya ji bai ji haushin nata ba.
"Lafiyar ce ta sa na kiraki. Suna na Fadeel, magana
nake son mu yi amma ta fi Ζarfin waya, idan kin ba ni dama ko zan iya sanin
kwatancen gidanku?"
Ranta ya soma Ιaci, ta ji wani abu na taso mata.
"Idan maganar ba za ka iya yinta a waya ba don Allah
kada ka Ζara gangancin kirana. Hakan zai fi maka alheri, sannan ina bukatar ka
goge lamba ta a wayarka, tunda ba wani
muhimmin abu ne ya sa ka kira ba."
Tana kai wa nan ta katse kiran, ta yi wurgi da wayar saman
gado, game din ma ya fice a kanta. Ita kaΙai ce a Ιakin, sai ga Raihana ta
shigo. Ko kallonta ba ta yi ba ta mike ta faΙa banΙaki, koda ta fito ganin
Raihanan zaune saman gadonnata yasa ta mamaki. Fuska a Ιaure ta Ζarasa.
"Malama lafiya?"
Jiki a sanyaye Raihana ta soma magana.
"Kiyi hakuri Humaira, na ja an maki faΙa an kuma
zalunceki. Don Allah ki yi hakuri. Ina neman gafararki bisa dukkan abin da na
taΙa yi maki a gidannan. Ban kara gasΖata kaunarki gareni ba sai a jiya da kika
shanye faΙan Abba ba ki faΙi ainahin abin da ya faru ba. Wallahi na ji kunyarki
sosai, kiyi hakuri ki yafemin."
TaΙe baki Humaira ta yi tana fadin.
"Ya wuce. Kar ki damu."
"Dagaske kike?"
Ta tambaya da sauri kamar za ta yi kuka don muryarta ta
karye, Humaira ta zauna a gefe.
"Ni ban taΙa binku da kallon maΖiyana ba, kallon da
nake maku na Ζ΄an uwana ya bambanta da irin wanda ku ke yimin. Sai dai dukkan
wannan ba zai sa na ga abin da zai cutar da ku na kasa magana ba. Idan na yi
hakan na ci amanar kaunar da Mami ke nunamin. Raihana mutunci da darajar mace
ya fi gaban ta tsaya ta siyarwa wani Ζaton banza a waje. Musaddam da kike gani
wallahi ba zai taΙa aurenki ba matuΖar kika yarda kika ba shi kanki a waje, ke
koda ba ki bayar ba, yaron ba aure ne a ransa ba face iskanci. Idan kuma
dagasken auren yake sonki da shi, meyasa bai taΙa zuwa nan Ζofar gidanku da
sunan zance ba, kema kin san karya ne kawai. Tun wuri ki yiwa kanki faΙa ki
rabu da shi zai fiye maki alheri."
Raihana da tuni ta soma hawaye ta kamo hannun Humaira.
"Toh naji Humaira, amma wallahi ina sonsa, wani irin so
ne da ban san yanda zan fara yakice shi ba a rai. So ne da ya rufemin ido naji
ko me Musaddam zai nema a wurina zan iya yi mishi."
Sai kuma tausayinta ya lulluΙe ta, tana kuma godewa Allah da
bai Ιora mata son kowane Ιa namiji ba
balle har ya wahalar da ita.
"Wannan son za ki yaΖa, domin halaka ne a wajenki.
Musaddam ba sonki yake yi ba muna nan da ke watarana za ki ban labari. Ki kai
kukanki wurin Allah sannan ki shagaltar da kanki wajen duk abin da kika san zai
dauke maki hankali daga tunaninsa. Nima kuma zan tayaki addu'a har sai Allah ya
amsa, ya rabaki da wannan makahon son. Ke ina kika hango dacewarki da shi wai?
Wallahi ta ko'ina ke din ba ajinsa ba ce, ban da ma dai shi son da kike ikrari
bai san inda zai je ba, ai sawun giwa ya shafe na raΖumi."
Murmushi Raihana ta yi cikin jin salama, sai kuma hira ta buΙe
tsakaninsu, tana ba ta labarin ainahin yanda aka yi ta hadu da Musaddam din.
Humaira ta gefen ido na kallon wayarta da ke silent tana ta haske alamar
shigowar waya amma ta yi biris da ita. Su na a haka Futuha ta dawo daga
makaranta ta iske su, mamaki ya dabaibayeta, ta cire facemask din da ta sa don Ιoye
kumburin gefen bakinta da Humaira ta daka, ba ta cewa Raihanan komai ba sai
zama da ta yi gefen nata gadon tana ci gaba da kallon ikon Allah. Ita kuwa
Humaira ko ta nuna ta san da wanzuwar wata a dakin bayan su. Can kuma Raihana
na juyawa tana yiwa Futuha magana ta ga hasken wayar Humaira ta jawo.
"Lah, kinga fa kiranki ake ta yi. Lamba ce. Kodai Ibb
ne?"
Jin sunan da ya fito bakin Raihana ya sa Futuha zaro ido
waje a razane. Ita kuwa Humaira fuska ta yamutse.
"Waya sani, tun dazu ya kira wai wani kwatancen
gidanmu."
"Wane Ibb din kika nufi Raihana?"
Suka dube ta, sam Raihana ta mance, yanzu me za ta ce idan
Futuha ta dage akan son sanin komai? Kada dai allura ta tono garma. Ita kuwa
Humaira sai a sannan ta tuno ashe fa a hirarsu tana jin Futuha na yawan maganar
son da take yiwa Ibb Gusau da haduwarsa. Kodai shi ne Ibb din da take magana?
"Ibb Gusau wanda kika sani."
Humaira ta furta da murmushi saman fuskarta, ta karbi
wayarta a hannun Raihana ta katse kiran amma sai ta sa a kunnenta kamar gaske
ta hau fadin.
"Assalamu Alaikum, ina neman afuwa ka kira bana kusa. Fatan ka karasa gida lafiya?"
Tana kaiwa nan ta sa kai ta fice daga dakin, sai da ta isa falo sannan ta
kwashe da dariyar ganin yanda Futuha ta cika tayi tam har gefen bakinta da ya
kumbura sumtum yana kyalli. Ta dai san ta harba mata bomb a zuciya. Dariya take
yi har ta shiga kicin Ιin, Ummita dake amsa waya tana lumshe idanu ta yi azamar
katsewa tana dubanta. Humaira kuwa ganin haka ta karasa fuska dauke da walwala
tana bin ta da kallon tsokana.
"Waya kike amsawa ko? Shi ne ina shigowa kika yi saurin
katsewa. Nidai ya kamata zuwa yanzu na san waye wannan majnun Ιin naki."
Ummita dai ba ta tanka mata ba sai maida hankalin da ta yi
wajen Ιarar tafarnuwa tana murmushi, sai kuma ta share zancen da hanyar fadin.
"Wai dariyar me kike yi ne?"
Sai a sannan ta tuna abin da ta yiwa Futuha, dariyar ta kuma
taso mata. Ta fayyacewa Ummita labarin, baki buΙe take kallonta.
"Ke kuma ina kika samu lambar shi?"
Ita shaf ta mance Ummita ba ta da labarin komai, ta yi
ajiyar zuciya. Labarin da ba ta so bayarwa ba amma ya zama dole ta sanarwa
Ummita don ba ta da yar uwa kuma aminiya sama da ita. Ta labarta mata duk abin
da ya faru da sanadiyyar marin Raihana ta kara da jan tsaki da fadin.
"Shi ne wannan mayen ya takuramin da kira fa, toh ita
Raihana ta yi zaton ma Ibb din ne. Ni kuma don na shaΖawa Ζ΄ar banza shi ne na
sa wayar a kunne ina wayar gangan na soyayya."
Ummita da iyakar burgewa yar uwar ta burgeta sai ta
shiga murmushi kawai da mamakin kaifin hankali da tunaninta, ta sani ko ita ba
lallai ta iya shiru a irin wannan gaΙar ba. Amma ta gwammace kowa ya yi mata
kallon rashin kyautatawa akan dai ta bayyana gaskiyar abin da Raihana ta
aikata. Sai kuma karar wayar Ummitan ya katse tunaninta. Da sauri har su na
rige-rigen Ιauka ita da Humairar, sai dai a karshe wayar ta faΙa hannun Humaira
tana dariya, ga nata wayar ta na ta haske shaidar faΙowar saΖo amma ko a jikinta.
"Ki yiwa girman Allah kada ki Ιaga." Gwalo ta yi
mata suka hau zagaye a kicin din.
"Sai kin rantse cewar za ki fadamin ko wane ne mai
kiran."
Da sauri ta amsa.
"Eh wallahi zan fadamaki, yanzu dai ban wayar."
Ba musu ta ba ta tana dariya, ta ja kujera Ζ΄ar tsugunno ta
zauna tana duba nata wayar da saΖon ya faΙo tun Ιazun.
_*Kar ki yi tunanin akwai abin da zai sa Fadeel ja baya ko
tsoro. Ki tambayi wadanda suka san waye shi, yana da naci akan abun da zuciya
da gangar jikinsa suka yi na'am da shi. Ba shi da saurin karaya, ba kuma ya jin
zai soma daga kan Ιiya mace. Ina kuma farin ciki shaida maki ke ce halittar
farko a mata da na ji zuciyata ta yi na'am da kasancewarta rabin jiki kuma
abokiyar rayuwata. Nasara tana tare da wanda ya miΖa lamarinsa ga Allah. Have a
nice day.*_
Ta karanta har da karkata kai kusan sau uku, sai ta ji ma
abin kamar irin a fina-finan da ake haskowa a tashar Hausa da su Tasleem ke
kunnawa. Ranta na wani irin huci da zafi, a gefe guda kuma duk da wannan
radadin wai sai ta ji tana so ta san ma'anar kalmomin karshen da ya rubuta mai
kama da farasanci da turanci.
"Lafiya ki ka ba waya hankalinki?"
Muryar Ummita ya katse mata tunani, ta isa wajenta ta miΖa
mata waya. Har a sannan hausarta ba ta dawo daidai irin ta Kanawa ba.
"Ζan fassaramin Ζarashen saΖon nan, me yake nufi?"
Ummita ta karanta tun daga farko, tun kuma somawarta take
zabga murmushi don ba Ζaramin burgeta ya yi ba.
"Fatan alheri ya yi maki a wannan rana. Kai Humaira
wannan mutumin akwai iya tsara kalami, ina ji a jikina kin samu mijin
aure."
Guntun tsaki Humaira ta ja gami da warce wayarta tana Ζ΄ar
harararta.
"Ai ke ce mijin, ni raba ni da wannan shirmen soyayyar
kin ji ko. Ba ni da lokacinsu."
"Anya Humaira kalau kike kuwa? Ko dai sai an haΙa da
addu'a?"
Yamutse fuska ta yi kawai ta kwashi tafarnuwar ta dauraye ta
watsa a turmi ta hau daka. Ganin haka itama Ummita ta share batun.
A gefen Futuha kuwa, gaba daya ta yo kan Raihana.
"Ke! Wane Ibb din ki ke nufi ne?"
Raihana ta yi jim, ba ta son ta ce Ibb Malaminta allura ta
tono garma don haka sai ta kife ta da fadin.
"Ba fa wanda kike zato ba ne, wannan wani Ibb ne
Ibrahim sunansa suka hadu da ita a hanyar islamiyya."
Nannauyan ajiyar zuciya Futuha ta yi kafin ta juya ta koma
gadonta tana jan tsaki.
"Toh barkanta, amma da ace Ibb da nake mutuwar so da
kauna ne wallahi sai na koyamata hankali. Ke kuma wani sabon salon gulma da
munafunci tun da ta wanke maki fuska da mari kike wani shakkarta har da taya ta
hira. Ke kika sani."
Raihana dai ba ta tanka ba ta mime ta bar mata Ιakin. Amma
ta sa a ranta babu wani abu da zai sa ta kara biye musu wurin nunawa baiwar
Allah da ba ta ji ba kuma ba ta gani ba Ζiyayya kawai saboda don zuciya irin
nasu.
***
Gidansu cike taf da jama'a sakamakon daurin auren Fu'ad da
aka yi a ranar, haka ya dinga kutsawa ransa duk a Ιace har ya shige bangarensu,
kai tsaye dakinsa ya nufa, tun daga falo ya cire hularsa ya yi jifa da ita,
hakanan babbar rigarsa blue itama ya ajiye saman kujera kafin ya zauna ya shiga
kokarin cire covershoe din da ke a Ζafarsa da kuma safa. A duniya Fadeel ya
tsani hayaniyar jama'a, wannan ta sa kansa har wani sarawa yake yi. Ya ja
guntun tsaki gami da kwantar da kai jikin kujerar ya lumshe idanu. Zafi biyu ya
haΙe mishi, ga na rashin samun haΙin kan yarinyar da yake jin ta a ΖoΖon rai,
ga kuma wata irin yunwa da yake ji domin ko karin kumallo bai yi ba suka fice
masallaci wurin daurin aure. Kowa kuma a dangin sai ya yo kansa da tsokana a
wajen, su na fadin saura kai babban yaya. Wadanda ba su da labarin dawowarsa
kuwa, sai a ranar suka gan shi. A hankali ya bude lumsassun idanunsa ya murza
yatsunsa suka yi Ζara, har wani zogi suke yi mishi saboda gaisuwar da ya dinga
yi da jama'a. Lokaci guda kuma ya miΖe ya nufi bandaki, hannun ya wanke tas da
hand sanitizer sannan ya fito rike da karamin tawul yana gogewa. Ya yi daidai
da shigowar Ibb tare da wani dan uwansu Imran.
Sallamarsu ya amsa ya koma mazauninsa har da kwanciya wannan
karon. Kafin Ibb ya yi magana ya riga shi.
"Wai so ku ke na mutu? Yunwa fa nake ji."
Harararsa ya yi.
"Kai dai an yi Ιan iska, muna can Alhaji ya sa mu
nemoka ku gaisa da abokansa ashe kai nan ka yo? To sai ka tashi ka shirya muje
idan ya so kafin mu dawo na yiwa Anti Amarya magana a kawo mana abinci."
Fadeel ya lumshe idanu.
"Kasan Allah ba zan iya fita ko'ina ba, ni fa ji nake
idan ma na kara sa Ζafa na fita cikin wannan ranar hanjin cikina za su fito
waje."
Imran ya kwashe da dariya, shi kuwa Ibb kamar ya shaΖo
amininnasa haka yake ji. Yana niyyar magana kuma sai ga kiran Alhaji karo na
uku. Ya Ιaga ya mishi bayani, dama bai tsammaci faΙan Alhajin ba, cewa ya yi
babu komai maza ya yi waya a kawomusu abinci. Da wannan suka yi sallama shi
kuma a nan take ya yi kiran Anti Amarya ya sanar da ita.
A bangaren Anti Amarya wacce ta ci ado cikin arnen leshi
ruwan toka da ya sha adon stones, ga Ζunshi ta yi sai baza Ζamshi take, jin
wayar Ibb ya sa da rawar jiki ta amsa ta ba Ιaya daga cikin hadiman gidan
Larai umarnin haΙawa Fadeel da abokansa abinci za ta turo a kai musu. Ta shiga
falonta inda yan uwanta hudu ke zaune su na shan hira. Uku a cikinsu matan aure
ne, Ιaya yayarta sai sauran gaba daya Ζannenta. Ζanwarta Murja dake kwance tana
danna waya ta kai wa duka a Ζafa. Ba shiri ta mike zaune.
"Ke tashi maza ga dama ta samu, jeki wurin Larai na sa
ta haΙa abincin su Fadeel ki kai musu, kika sani ko Allah zai sa a dace ko
cikin abokansa wani ma ya ce yana so?"
Jin haka babbar yayarta Saddika ta amshe.
"Ke wallahi hakane kam, tashi Murja, Allah ya Ιora ki
akan su."
Murja ta haΙe girar sama da Ζasa.
"Nikam wallahi Fadeel nake so. Shi dai za ku taya ni
addu'a ya ce yana sona."
"Kin ji wawiya, ke kanki kinsan kaf abokansa ma babu na
yar wa musamman Ibb. Ai dai kinga irin jama'arsa da suka kawo masa ziyara muna
nan dake a gidannan tun zuwansa ko?"
Murja wacce ta zo hutun makaranta gidan Ζ΄ar uwarta ta, ta
mike tana gyara zaman Ιaurin dankwalinta.
"Nidai kam shi nake so, ai duk kyawunsu ba su kai shi
ba. Malam ga aji na musamman. Kiga fa ko sadda su Sholy suka zo gidannan ko
kallo basu ishe shi balle su ga haΖoransa. Nima din ba.."
"Ki yi zaman hira har sai ya gaji ya turo wani ya karΙar
musu abincin. Shashasha marar wayo kawai. Ana kai ki kina Ζin zuwa. Ke kika
sani. Zauna har ki yi biyu babu."
Jin haka da sauri ta fice daga falon tana dariyar maganar
Zuwaira, mai bi wa Anti Amarya.
A kwando ta ga Larai ta haΙa komai har da cokula da
farantai, ta kinkima ta yi gaba inda ta tsallake yan uwan Alhaji da suka zo
daga Ζauye ko kallo ba su ishe ta ba ballantana ta yi tunanin gaishe su. Su kam
suna hau gulmarta da harshen fulatanci. A Ζasan ranta ta ja Allah ya isa.
Tana zuwa Ζofar ta kwankwasa, Ibb ya ba da umarnin a shigo.
Lokacin dukkansu har Imran sun cire babbar riga ana shan iskar fanka ana hira,
sun zama su biyar a Ιakin sakamakon shigowar abokan Ibb biyu, Saifullahi da
Idris. Da sallama a bakinta ta shiga, kasancewar Fadeel ne a saitin Ζofa ya bi
ta da kallo Ιaya ya kauda kai ya maida saman kwandon dake hannunta. Dama abin
da yake jira kenan, ita kuwa kusan zaucewa ta kusa yi sakamakon kwayar idanun
Fadeel da suka haΙu da nata, gaba daya ta ji ta Ζara narkewa a tekun sonsa. A
ranta tana ayyana ba gudu ba ja baya shi din dai ranta ke so. Babu wani
abokinsa da ta ga ya burge ta, gwara ma Ibb don a baya tana mishi kallon
hadadden saurayi duk sadda suka hadu ya zo gaida Alhaji, ita kuma ta zo gidan,
yanzu kuwa ta fahimci Fadeel ya kere shi.
"Ba sai kin zuba ba, bar shi za mu yi serving da
juna." Fadin Ibb fuska a sake ganin ta sauke kwandon ta hau fito da
kayayyakin tana shirin buΙe warmer.
Ta kalle shi kadan tana dan murmushi.
"Lah ba komai, bari na zubamaku, wannan ai aikinmu ne
mata."
Bai kara magana ba sai mayar da hankali ya yi ga Imran dake
nuna mishi wani hoto a waya. Shi kansa Ibb ba mai yawan zance ba ne sai ta
kama, don haka bai hanata ba. Shi kuwa gogan kallonta bai kara ba, sai Idris da
ya zuba mata ido kamar ya haΙiye ta. Shi dai kam lokaci guda ya ji ta kwanta
masa a ΖoΖon rai. Don haka bai yi Ζasa a gwuiwa ba ya dubi Fadeel.
"Wannan Ζanwarmu ce?"
Tsaf Fadeel ya karance shi, don haka ya gyada kai kawai
fuska Ιaure. Ita kuwa da rawar jiki ta miΖa kwanon abinci ga Fadeel. Madadin ya
karΙa sai ya dube ta. Ta ji kallon tun daga tsakar kanta har tafukan sawayenta.
"No, ki fara ba su tukunna."
"Kai Malam, idan za ka karΙa ka soma ci ka karΙa. Tun Ιazu
ka ke mana raki da kukan yunwa kamar wanda ya shekara bai ci ba. Wannan ta ya
ya kake azumtar watan Ramadan?"
Jin haka ya ja filo ya jefawa Imran a fuska, gaba daya aka
sa dariya shi kuwa ya shafi sumar kansa yana mai lumshe idanu lokaci daya ya
bude su akan Murja, wannan karon sai da ta ji miyan bakinta ya sarΖe ta sai ga
shi ta soma tari ba ΖakΖautawa. Idris da sauri ya miΖa mata ruwan roba dake
gefensa saman kafet. Ta karba ta sha tana satar kallon Fadeel da bai Ζara
dubanta ba sai waya da ya ke faman dannawa. A haka da rawar jiki ta zuba kowa
ta miΖa mishi. Friedrice ne da hadin coslow sai chicken pepper. Ta bude firij
ta ciro musu lemuka ta ajiye. Daga haka ta sa kai ta fita. Tana fita Idris ya
gyara zama ya shiga rantse musu akan ya ga matar aure shi dai yana sonta idan
za'a ba shi. Fadeel ba ya fahimtar komai ban da ta cikinsa da ya ke yi, ganin
duk da fankar da ke busawa yana gumi kawai sai ya mike ya cire rigarsa daga shi
sai dogon wandon shadda da vest ya koma ya zauna. Sai da ya tashi da abincin
tas kafin ya Ιauki ruwa ya kora ya dubesu. Kowannensu bai kai ga kammala ci ba,
suka kwashe masa da dariya, shi kansa murmushi da tsaki ya yi lokaci guda kuma
yana sa hankicif ya goge fuska.
"Ku na da matsala wallahi, ba za ku gane illar da yunwa
ke min ba. Yanzu sai ta tayarmin da ulcer."
"Ai mun gane komai ranka ya daΙe. Ko za ka Ζara?"
Saifullah ya faΙi da zolaya. Fadeel ya Ιan harareshi.
"Saboda na zama rumbu ko?"
Haka suka yi ta zolayarsa shi kuwa tuni ya maida kai kan
wayarsa yana kiran abu na biyu da ya tsaya mishi a ΖoΖon rai amma har ta
kammala ringing ba a Ιaga ba. Haka ya kira har sau uku, sai a na huΙun, aka Ιaga.
Kafin ya kai ga cewa komai ta soma faΙa.
"Wai Malam kai din maye ne?! Na ce ka bar kirana ka Ζi!
Dole ne zuwanka gidan namu? Haba, wannan jaraba da naci har ina wai?
Mtsw."
Daga haka kit, aka kashe kiran, nan da nan kansa ya yi wata
irin sarawa, dama ga ciwon kan da tun Ιazun yake ji. Gumi ya karyo masa saboda
tsananin Ιacin rai, idanunsa tuni suka kaΙa. Sauyawar yanayinsa ya sa Ibb
Ζuramasa idanu. Sai dai bai ce komai ba ganin ba su kaΙai ne a falon ba. Sai
bayan da gaba daya suka fice don gaisawa da Alhaji sannan Ibb ya dube shi,
lokacin ya mayar da kai jikin kujera ya lumshe idanu don har su Imran suka fita
sun yi zaton bacci ne ya kwashe shi su na mishi tsiya. Shi kuwa duk yana jin su
ba shi dai da karfin biyewa shirmensu.
"Fadeel, wai meke faruwa haka?"
Jin muryar Ibb yasa shi bude idanun, ya mike zaune sosai.
"Yarinyarnan nema take ta kashe ni, daga ranar da na
gan ta har zuwa yau ban huta ba."
Cikin rashin fahimta Ibb ya dan wurga hannu.
"Wace yarinya ce haka? A rayuwarka har ta hanaka sakat?
Wace ce?" Tsakaninsa da Allah ya yi furucin don shi gaba Ιaya ma ya manta
da wata Humaira.
"Wacce muka haΙu da su tare da wannan Ιan iskan
yaron."
Shiru Ibb ya yi cikin nazari sannan ya dube shi a hanzarce.
"Are you serious? Kana nufin ka kira ta?"
Cikin ido Fadeel ya dube shi.
"Yes, mun yi waya, amma duka ba masu dadi ba ne."
Ya kora mishi bayanin duk abin da ya faru, Ibb ransa ya Ιaci.
"Unbelievable! Yanzu akan mace ne ka shiga wannan
yanayin? Fadeel kai ne dagaske dai wanda na sani? Mutumin da gaisuwar kirki abu
ne mai wuya a ganka kana yi da wacce ba muharramarka ba, kai ne yau da bakinka
ka ke faΙin cin kashin da wata shashasha can take maka? Kuma har ka ke
tolerating in the name of love? Is this love or madness?"
A fusace Fadeel ya soma magana, tun da Ibb ya jefi Humaira
da kalmar shashasha ya ji ransa ya yi masifar zafi.
"Oho! Idan ma haukan ne naji ni na jefa kaina ai ba da
sa hannunka ba ko? Ban damu da duk wani tunani da za ka yi ba. Ina sonta, ka zo
gabana kana kiranta da shashasha ba zan iya jura ba Ibb! Ina haΙa ka da Allah,
idan har ba goyamin baya za ka yi ba toh kada ka kara kuskuren zaginta a
gabana. Kawai dai ina ji a jikina wataran za ta gane ni din masoyinta ne na
gaskiya."
Yana kaiwa nan ya mike ya nufi hanyar Ιaki, Ibb kuwa baki a
wangale yake binsa da kallo har ya Ιace masa. Meke damun Fadeel? Ya jefawa
zuciyarsa tambaya, a take kuwa amsar ta zo masa, Soyayya ce. A fili ya ce.
"Idan kuwa har wannan ita ake kira da soyayya, ina
nemawa kaina tsari da ita. Kai kuma Fadeel ina roΖon Allah ya yayemaka wannan
haukan son."
Daga haka ya mike ya fita a dakin domin shi har ga Allah ba
ya fatan wannan rashin hankalin da mace za ta zage shi ya kasa daukar mataki a
kanta. Ko Ζ΄ar uban wace ce ba zai Ζara yi mata kallon wata abar so ba,
ballantana har ta ci galabar yi mishi son ranta.
***
Humaira na kwance a yammacin ranar juma'a ta ji ihun
Ζ΄an matan gidan ya karaΙe falo, ta mike zaune tana mutsistsiΖa idanu. Hayaniyar
ta mene ne? Kafin bacci ya gama wartsake mata sai ga Ummita ta shiga fuska ba
yabo ba fallasa.
"Wai hayaniyar me ake yi?" Fadin Humaira. Tsaki
Ummita ta ja haΙi da taΙe baki.
"Aunty Jannat ce ta zo, kanwar Mami."
Humaira ta zaro ido, ba ta taba zama da ita ba amma ta sha
jin labarinta a bakin Ummita na irin uΖubar da ta sha a wajenta sadda tana
rayuwa a gidan.
"Dagaske? Ki ce mun shiga uku."
Ganin ruΙewae Humairar har ya so ya fi nata ne yasa ta
dariyar dole wanda ba ta shirya masa ba.
"Ke da ba ki taΙa zama wuri guda da ita ba? Ba lallai
ki fuskanci matsalar da na fuskanta ba ai."
Ita dai Humaira ta ji ne kawai ba don ya zauna a
kwakwalwarta ba.
Suna nan zaune
Humaira na cewa ita kam za ta so ganin ya wannan Jannat din take mai
shegen son mulki sai ga Muhsin da Waleed sun faΙo Ιakin a guje. Kira ne
daga Mami akan su fito a gaisa da Jannat. Ummita ta dafe kirji, yayinda Humaira
mikewa ta dube ta.
"Wai ya haka, kinsan fa yarannan akwai daukar zance
yanzun sai su fasalta musu yanayinki."
Ummita sai ta maze ta mike. Suka kama hanyar falon, tun
kafin ma su kai ga Ζarasa shiga ta hange ta. Kamanninta sak da Mahaifiyarsu
wato Anna. Kusan har ta so ta fi Mamin hasken fata, siririya ce ba ta da tsawo
duk kuwa da cewar tana daga zaune ne. Yaranta Ζ΄an biyu tamkar an tsaga kara an
karya, ba su wuce sa'o'in Muhsin ba. Wato shekaru goma a duniya. Riga da wando
ne a jikinta sai abaya dake ajiye a hannun kujera wanda ga dukkan alamu cire ta
ta yi. Gashinta ya sha kananun kalba an tufke a tsakiyar kan ya yi kamar ta sa
ribos din acuci. Gaba daya iyalan Mami na falon ciki kuwa har da Anna wacce ba
kasafai ta fiye fitowa ba. Humaira ita kanta sai da ta sha jinin jikinta ganin
Anna a falon, sai da itama ta ji kamar ta ja hannun Ummitan su juya. Aikuwa su
na ganinsu Anna ta tamke fuska gami da juya harshe zuwa buzanci. Ko me ta fadi
oho, gaba daya suka kalli su Humaira, matasan suka gimtse dariyarsu sakamakon
Mubarak dake zaune, sun tabbata muddin suka ce fiddo shi waje to fa kashinsu ya
bushe wurinsa. Hatta da Raihana ba ta ji dadin zancen Anna ba domin har
ga Allah yanzu ba ta da matsala da su, ta riΖe su Ζ΄an uwan na gaske kuwa.
Ita kuwa Jannat kallon Humaira ta ke yi kamar wacce ta ga
kashi. A yatsine ta amsa gaisuwarta, Ummita kuwa gaisuwar ma ba ta samu ba sai
harara da ta watsa mata ta ja tsaki.
"Wai Anti Jannat har yanzu wato kina nan yadda na
sanki."
Mubarak ya fadi ransa duk ba dadi, tun daga kalmar agolar da
Anna ta kira Humaira da shi har zuwa yanda Jannat ta karΙi gaisuwarsu.
Rai a Ιace ta amsa.
"Toh ko za ka sa hannu ka buge ni ne? Dama ai kai na faΙa
can dai dangin uba ka biyo ba mu ba."
Zai yi magana da sauri Mami ta Ιaga mishi hannu, aikuwa abin
da take gudu shi ya afku domin Anna faΙa ta hau yi kamar ta ari baki wai laifin
na uwarsa ce da ta fifita bare a kan nata. Ganin dai abu ya Ζi Ζarewa Humaira
ta miΖe tana mai jan hannun Ummita, itama ba shiri ta miΖe sun kama hanya tana
ji Jannat ta kwalawa Ummita kira tana ba ta umarnin ta ja Hassan da Hussein Ιakin
su Muhsin ta musu wanka. Ita dai Humaira a fusace ma ta karasa Ιakin don ta
matsu ta daina jin muryar tsohuwarnan da ma Jannat din wacce ta ji tsanarta
lokaci guda ya rufe ta. Me ake da wanda bai san daraja ta DAN ADAM ba?
Ita kadai a dakin ta yi ta mita tana tsaki. Ji take kamar ta
je ta shaΖe wuyansu baki Ιaya. Sai kuma ta yi kwafa tana cije lebbanta, ita
kadai ta san damuwar da take dannewa a ranta, amma a kwanakin nan abin yana
neman fin karfin zuciyarta. Damuwar bai wuce Abba ba, mutumin da ya kasance
bango majinginarta a gidan, wanda shi take yiwa kallon uwa kuma da uba. Wannan
kauna da soyayyar da ya nuna mata a farkon zuwanta gidan yanzu ta rasa laifin
da ta yi mishi ya sauya. Hira ma ya Ζi ba da fuskar ta ja shi da shi, idan har
ita Ιaya ce a falonsa, nan da nan zai hau wasu Ζ΄an aikace-aikacensa kamar gyara
takardu ko kuma kiran abokan cinikayya, shaida dai ta cewar ba ya son ta ja
wani dogon zancen. Ba dai za ta ce ba ya mata fara'a ba ne, sam a'a, sai dai
babu ja a jiki balle har su shaΖu tamkar yanda ya nuna a farkon zuwanta. Toh
wanda ma ka ke taΖama da shi bai wani damu da sha'aninka sosai ba ina kuma ga
wasu can da har gobe sun Ζi karΙarta matsayin Ζ΄ar uwa ta jini? Kewa, kewar Dada
da Kawunta duka suka mamaye ta, ba ta san cewar ta soma zubar da hawaye ba sai
bayan ta sa hannu saman fuskar ta ji danshin lema. A hankali ta share su, ya
kuma yi daidai da shigowar Raihana Ιakin. Ganin hawaye a fuskarta gaba daya sai
ta ji ba dadi, ko ita ce ake yaren da ba ta ji tsarguwa yake sanya ta
ballantana kuma wannan da dama din sun san ba da kowa ake ba sai su.
"Humaira kuka? Don Allah ki yi hakuri."
Ta fadi a sanyaye gami da zama a gefenta. Jin haka ta yi
murmushin da ya fi kuka ciwo lokaci guda tana gwale idanun da hannu tana share
su.
"Ke ba fa komai, ba kuka nake ba. To me aka yi da zan
yi kukan?"
Raihana itama murmusawar ta yi ba don ta yarda ba, ta sani
Humaira akwai juriya da nuna jarumta, sai dai kuma itama ai Ζ΄ar adam ce, tana
da zuciya ta kuma san meke ma ta zafi. KafaΙarta ta dafa.
"Na sani su Anna ba su ..."
"Raihana mu bar zancen, ya wuce wallahi. Ai komai mai
Ζarewa ne. Lokaci ne." Cewar Humaira da sauri tana katse Raihana don a
duniya yanzun idan da abin da ta tsana bai wuce a ambaci sunan Anna ba. Ta
tsani mutum da ba ya ganin kowa da gashi. Tsohuwar sam ba ta riΖe girmanta.
"Kinga kuwa mutuminki koda wasa bai Ζara gangancin
kirana ba?"
Maganar Raihana ya katse tunaninta. Cikin rashin fahimta ta
ce.
"Wa fa?" Ta yi tambayar don har ga Allah ta mance,
sai kuma bayan ta yi ta tuno da Musaddam din. Ta Ιan Ιaga gira.
"Au, Ιan iska za ki cemin."
Suka Ιan yi dariya. A haka su Tasleem suka shigo Ιakin suka
iske su. Zuwa yanzu Raihana ba Ζaramin haushi take ba su ba don haka daga
kallo daya ba su kara bi ta kansu ba. Tasleem ta nufi sif din kayanta ta buΙe
ta sa hannu a Ζugu tana kallo.
"Oh God! Ni wane kaya ma zan saka? Wallahi gaba daya na
diririce."
Futuha da ta faΙa saman gadonta ta yi dariya.
"Atoh, sai ki Ζure a daka ko ba komai dai wannan ne
first meeting Ιinku."
Raihana na jin haka ta mike da sauri ta karasa ga Futuha.
"Wai Hamza D ne zai zo?"
Harararta suka yi a tare, Tasleem ta ja tsaki.
"Ina ruwanki? Ai ke yanzu munafuka kika zama. Ba a
sirri da ke."
Humaira ta yi tsam ta mike ta fice a dakin ba ta ko kalle su
ba. Cin fuska ne ta san za a yi mata.
***
Rayuwar ta ci gaba da gudana, Humaira tun tana ganin
ire-iren bautar da Jannat ke sanya su na Ζare ne abin dai ya ci tura. Daidai da
wankin pant da rigar mama su take ba, Mami ke tsawatarwa a wasu lokutan shiyasa
kawai su ke hakuri. Idan kuwa ta kai Humaira abin ya ishe ta rantsuwa take yi
da Ζari cewar ita ba za ta wanke ba, sai Ummita ke tausarta ta karΙa ta wanke
gudun samun matsala.
A wannan gaΙar kuma ba irin takurawar da Fadeel ba ya yiwa
Humaira, iyakar Ζularwa ya yi mata, ta yi bakaken maganganun amma ko gezau,
kusan kullum sai ya aiko mata da saΖonninsa da ke yiwa Raihana dadi. Ita ke karΙa
ta yi ta karantawa har a wasu lokutan ta yi yunkurin ba shi amsa, Humaira ta
nuna ba ta so.
Jannat ba ta bar gidan ba sai da ta yi wata Ιaya cif. A
sannan tuni Mubarak ya tattara ya koma, shima daf yake da kammala Masters.
Yayinda Yassar da Dawud suka soma jarrabawar Ζarshe na kammala
degree dinsu a jami'a. Su Ummita ma tuni an koma karatu, Humaira kam ta yi nisa
a fannin girke-girke don yanzu girki ΙaiΙaiku ne ba ta iya ba, kama daga cimar
fulawa har dai sarrafa shinkafa da sauran kayayyakin abinci. Girkin gidan zuwa
lokacin ya koma kan ta rankatakaf don kowa burinsa ta girka ya ci. Ita kam ko a
jikinta, za ta yi girkin ba son jiki amma fa ba ta yarda da wulakancin su
Yassar da Tasleem masu cewa su na son cin wani abu daban.
Yassar su na dab da kammala jarrabawarsu ne suka tada
hankalin Mami lallai sai ta tambayar musu Abba kuΙin da za su haΙa party da
abokan karatunsu sai dai duk inda suka Ιullo Mamin ta Ζi asalima cewa ta
yi su tuntuΙi Abban da kansu.
Yassar ya mike tsaye yana huci.
"Shikenan, idan Abban ya zo zamu yi mishi maganar. Mu
dai gaskiya wannan karon ya sakar mana mu fita kunyar abokai. Wannan rayuwa har
ina."
"Ni ban san irin Abba ba wallahi, Mami ke ma ba kya
mishi magana, tun farko ai Anna ta fadi, ke kika ba da damar ba ya hidimta mana
sosai. Nifa Allah kuwa har kunyar nace Babana mai kudi ne nake, saboda ba a
gani a jikina."
Dawud ya fadi yana daga tsaye dafe da kujera. Mami ta yi
mishi daΖuwa.
"KarΙi nan Dawud, shi uban naku sa'anku ne da ku ka
tsaya ku na wannan Ιarin zancen a kansa? Kuna maganar kamar yau idan kun je
gabanshi za ku iya maimaitawa? Kunsan Allah ku kiyaye ni, gaba daya zan
tattaraku na kai kararku wajensa tun da dai shi kuna shakkarsa."
Suka Ζara tunzura, Humaira na gefe tana gogewa Mami mayafi
bayan ta kammala goge nata kayan dalilin wutar nepa da aka kawo, biki ne Mamin
za su je har da ita na Ιiyar mijin Anti Laila malamar girkinta. Katin gayyatar
har ita aka ba da ta kuma tabbata saboda mutuncin da suke yi da Shema'un ne,
sannan Anti Lailar ma ba ta da matsala ko kaΙan. Gaba Ιaya hirarsu babu
wanda ba ya shiga kunnuwanta, tana mamakin irin wannan rashin tarbiyya na su
Yassar da ba sa tauna zance kafin su furzar kan kowa ma. Haka suka yi ta mita a
karshe dai kiran sallar la'asar ya sanya su tattarawa su bar falon.
"Allah ya shiryamin ku."
Humaira jin furucin da Mami tayi kafin ta wuce dakinta yasa
ta amsa da amin, zuciyarta sai ta cika da tausayin Mamin. Matar dai na iyakar
kokarinta a kansu. Ba zato ta ji an watso mata kaya saman kafafunta da ke miΖe
a harΙe. Ta Ιaga kai ta dubi mai wannan aiki. Futuha ce tsaye daga ita sai vest
da leggings. Gashinta a barbaje a gadon bayanta take duban Humairar fuska a
yamutse.
"Ζan dannemin kayan nan kafin su dauke wuta."
Kallonta ba ta kara yi ba ta hadiye zafin da ta ji na wannan kalar rashin
mutuncin na Futuha. Itama daga haka ta juya zuwa daki, Ζwafa ta yi ta kuma
rantse ba za ta yi ba. Hakan yasa tana kammala na Mamin, ta hada da nata kayan
da ta goge ta miΖe bayan ta Ιauke dutsen gugar a wajen gudun kar su Waleed su
taΙa.
Dakin Mamin ta soma shiga, sallah ta iske ta
tana yi don haka ta ajiye mata a saman gadon kusa da wani haΙaΙΙen leshinta
peach colour da ya sha adon duwatsu, ya hau sosai da mayafin. Humaira har sai
da ta murmusa don tuni ta hango Mamin a ciki, karshen kyau ko ba a faΙa ba ta
sani kalar da kuma kayan za su karΙe ta. Abar ka da farar mace.
Koda ta shiga Ιakinsu Tasleem na tsaye tana fente fuskarta
da hoda. Ita kuwa Raihana tuni ta shirya tsaf cikin wata maroon atamfa mai
haske an yi adon yellow colour jikinta sai dai bai yi dau ba. Tana tsaye ta
karkace sai hotuna ta ke yi a gaban window. Futuha da alama tana bandaki. Suka
dubi juna da Raihana, da wani irin zumudi ta karkace hadi da Ιan Ιaga gira.
"Ya? Na yi kyau?"
Humaira ta yi mata murmushinnan nata mai fiddo da zahirin
kyawunta.
"Kin fito tsab. Masha Allah."
Raihana ta yi dariya, ita kuwa Tasleem dogon tsaki ta ja. Ba
wanda ya ce mata ci kanki a cikinsu. Kasancewar ta yi wanka kafin zaman guga
kuma ba ta da sallah hakan yasa ta kawai ta shiga sauya kaya. Itama atamfar ce
amma nata dark brown ce mai haΙe da milk colour. Tana cikin shafa hoda Futuha
ta fito daga wanka tana baza Ζamshin sabon showergel da suka ci arzikinsa a
zuwan Antinsu Jannat gidan. Kallon Humaira ta yi kafin ta kalli gadonta ta gani
wai ko ta ajiye mata kayan amma wayam. Don haka a fusace ta dube ta.
"Ina kayan da na ba ki guga?"
Humaira ta kalle ta da irin kallon wulakancin da suka saba
yi mata itama.
"Ai gugan Mami kika iske ina yi ko?"
"Shekara kika yi kina gogewa Mamin mayafi? Don tsabar
is..."
Ba ta kai ga Ζarashewa ba Ιif aka Ιauke wutar, aikuwa
Raihana ta tuntsire da dariya itama Humaira sai da murmusa a ranta tana fadin
Allah ya Ζara.
Nan fa Futuha ta hau zuba fada wai Humaira na sane iskanci
ne ta fara sabo, tunda har ba a isa a sanya ta aiki ta yi ba. Ta tattara ta ba
banza ajiyarta duk da cewa ranta wani irin tafarfasa ya ke yi na irin zagin da
Futuha ke yi mata. Korar yunwa dai ya Ζi fita a bakinsu, ta kasa jurewa ta
juyo, kamar ta maida martani da cewa su dinma asalin uwar Maminsu Nijar din ne,
daga can suka fito can kauyen Agadas sai dai ta haΙiye tuna albarkacin Mami.
Ummita ta shigo dakin, ita tuni dama ta shirya cikin atamfarta mai kyau ruwan
sararin samaniya. Fitar da ta yi aiken Mamin ne zuwa siyan kati.
"Mami ta ce ku yi sauri."
Wannan ne ya katse zancen, kayan da Futuha ba ta sanya ba
kenan sai kuwa wani ta sauya. Ba wata kwalliyar hayaniya Humairar ta yi ba amma
iyakar kyau ta fito tsaf. Ba su suka yi haramar tafiya ba sai biyar da kusan
rabi.
Koda suka fito baki daya, Ladidi kawai aka bari tana musu a
dawo lafiya sai kuwa su Muhsin dake can Ιangaren Anna, Ummita ta dube ta da
murmushi.
"Kin yi kyau sosai."
Ta riΖe haΙa.
"Idan babu wadannan buzayen a kusa ko?"
Suka yi dariya. Anan farfajiyar gidan suka sha hotuna a
wayar Raihana dake faman jan su, su Tasleem na gefe su na kallonsu ita da
Futuha, ko me suke tattaunawa?
Mami na fitowa suka shiga mota, kai tsaye Ζawataccen hall Ιin
Marhaba suka nufa inda anan ne taron bikin.
"Ba ku mance katinanku ba dai ko? Ba na so a je wurin
taro mutum ya yi tsaye kamar wanda ya zo gayyar soΙi."
Tasleem ta haΙiye dariyar muguntar da ya so kwace mata har
sai da Futuha ta Ιan zungureta akan ta nutsu. Katin Humaira tun fitarta kiran
Mami, ta Ιauke shi ta raba gida biyu ta wurga shi bayan gadonta.
Ummita da Raihana suka amsawa Mamin bayan sun duba sun ga
katinansu, ita kuwa Humaira ko jakar ba ta buΙe ba tunda dai ta riga ta sani
duk wani abun buΖatarta ta jefa a ciki.
"Humaira, Tasleem da Futuha fa?"
Suka amsa da eh su ma yana nan.
Su na isa bakin Ζofar kowaccensu ta fito, motoci ne na
alfarma fake a wurin. Yanmata har ma da manyan mata Ζ΄an gayu kawai kake gani a
wurin, kasancewar Angon Shema'u Ιa ne ga kwamishinan Ζ΄an sanda hakan yasa motar
Ζ΄an sandan har biyu a wurin su na lura da shige da fice.
Mami ce ta soma gaba suna gaisawa da wata Ζ΄ar uwar
aminiyarta ta miΖa kati ta shige. Hakan ba karamin dadi ya yiwa Tasleem da
Futuha ba sanin muguntar da suka shiryawa Humaira. Suka shige abinsu zuciyarsu
fari kal bayan sun miΖa katinansu, Raihana ma tuni ta yi gaba. Ummita kuwa
ganin yanda Humaira ta rikice da bincike jaka ya sa ta tsayawa gami da ja baya
ta ba wasu hanya.
"Lafiya? Ya kika tsaya?"
Humaira ta ja guntun tsaki.
"Wallahi ban ga katina ba. Kinga ba ya cikin
jakar."
Ta dafe kirji.
"Ba dai a gida kika bar shi ba?"
Ta girgiza kai cike da takaici, ta kasa cewa uffan ma. Ganin
su na tsaye kawai ya sanya ta duban Ummita.
"Shiga ciki kawai, ni sai na koma gida."
Girgiza kai Ummita ta yi.
"Aa wallahi, sai dai ni na koma. Keda Shema'u da kanta
ta damΖa maki kati?"
Nan fa suka yi ta ja in ja a Ζarshe dai Humaira ta ce.
"Toh naji, shiga ciki sai ki sanarwa Mami mu ji me za
ta ce. Allah kuwa ba inda zan je ina nan zan jiraki."
Ummita duk sai ta ji ba dadi, sosai Humaira a daren jiya ta
ci burin bikin ba don komai ba sai cewa da ta yi tana so ta ga ya ake gudanar
da biki a Ζasarnan. Ba ta taΙa halarta ba. Ganin ta tsaya yasa Humaira dafa
kafaΙarta.
"Rantsuwa fa nayi, kinsan ina nan din babu inda zan
je."
Jin haka yasa ta gyada kai ta juya ta shige ciki ita kuwa ta
ja baya ta koma can gefen titi jikin wata baΖar mota me tinted ta tsaya.
FADEEL
Fitowarsu kenan daga Bristol Palace dake kam
titin farmcenter, Ibb ke jan motar yayinda shi kuwa ya kwantar da kai jikin
kujera idanunsa lumshe. Babu abin da ya kai su face gaishe da abokin baban Ibb
da ya zo daga Kaduna zai tashi zuwa Egypt sakamakon rashin lafiya.
"Hall dinnan ba ya rabo da biki."
Jin haka ya sa a hankali Fadeel ya buΙe idanunsa. Cikin iko
da hukuncin Ubangiji, dubannasa ya sauka kan Humaira dake tsaye ta harΙe
hannuwa a kirji fuskar nan a Ιaure kamar koyaushe.
"Wait please."
Yanda ya yi maganar da sauri ya sa Ibb shima soma tafiya a
hankali gami da neman wurin parking. Sai da ya daidaita motar a gefe kafin ya
dube shi da alamar tambaya.
"Lafiya?"
Fadeel ya soma kokarin cire seat belt.
"Ita ce. Ba na so na Ζara rasa damar da za ta
kubcemin."
Ganin yana kokarin bude Ζofar yasa Ibb saurin dafe hannunsa.
Fadeel ya dube shi.
"What? Kana nufin kar na je?"
Girgiza kai Ibb ya yi.
"No, ba haka nake nufi ba. Sai dai ina so ka ba ni
damar muje tare, idan kuma da hali kar ka ce komai. Ma'ana kada ka yi mata
zancen soyayya da ma sauransu. Ni zan san ta yadda zan Ιullo mata, ok?"
Fadeel ya sauke ajiyar zuciya yana hangenta ta jikin side
mirrow. Ba tare da ya dauke idanunsa ba ya amsa.
"Ok."
Daga haka Ibb ya kashe motar, suka fito kusan lokaci guda.
Gaba Ιayansu Ζananun kaya ne jikinsu. Fadeel baΖar tshirt ne a jikinsa mai
Ζaramin hannu sai blue jeans. A tsintsiyar hannunsa kuwa, agogo ne Ιaure
na fata baΖi, sumar kansa baΖa wuluk sai sheΖi take yi. Ya fiddo gilashinsa
baΖi a aljihu ya rufe Ζwayoyin idanunsa, a yanda ya karanci Humaira a farkon haΙuwarsu
hatta da kallo ta tsana. Ba ya jin kuma abu ne da zai iya jure bari ne, wato
kallonta, musamman ma da ya kasance sun fi watanni biyu ba su sake haΙuwa ba.
A Ιangaren Ibb kuwa, blue tshirt ya sa da baΖin wandon
jeans. Kallo Ιaya idan ka yi musu sai ka kara. Fadeel fari ne tas kuma dogo,
har ya so ya fi Ibb tsawo. Shi kuwa yana da Ιan duhun fuska balle idan ya jera
da Fadeel, kai tsaye za a kirashi baΖi.
Tana nan tsaye ba ta motsa ba har suka Ζarasa wajenta. Wani
irin bugu kirjin Fadeel ke yi, kallonta yake tun daga sama har Ζasa, ba ya jin
ta haura shekaru sha takwas, idan ma ta cika hakan kenan, amma Ζirarta ko a
yanzun abin a kalla ne ina kuma ga nan gaba? Ya ja numfashi daidai sadda suka
ci burki a gabanta. Sallama Ibb ya yi gareta, ta bar duban wayar da take yi a
kokarinta na kiran Mami ta ce mata ita kam gida za ta koma. Zaratan samarin
suka sanya wani irin kwarjini ya mamayeta da har ta kasa tantance su Ιin ko su
wane ne, ta mance ma a inda ta san su. DaΖyar ta amsa sakamakon nauyi da
harshenta ya yi, daga haka kuma ta dauke kai ta raba jikinta da motar da
nufin barin wajen.
"Kamar ba ki gane ni ba ko?"
Cike da Ζosawar ta tafi ta dube shi. Kallo na Ζurilla don ta
fahimci ko dagaske yake ta san shi Ιin, duk da cewa ba wannan ne karon farko da
samari suke mata irin rainin hankalin nan ba idan sun ga ba ta kula su ba, amma
hakanan a ranta ta ji wannan dai ya yi kama da kamilallan mutum, ba ta jin zai
yi mata Ζarya. Bayan gama kallonsa ta maida kwayar idanunta kan Fadeel, ba ta
ci nasarar ganin halittar kwayoyin idanunsa ba, shi kuwa wani yarr ya ji tun
daga tafin Ζafarsa har tsakar kansa. Dakyar ya iya jarumtar juya fuskarsa gefe
kafin ita Ιin ta kai ga Ιauke nata kwayar idanun a kansa. Ta tsuke baki ta ce.
"Ban gane ku ba."
Ibb ya yi mata bayani a taΖaice, nan da nan kuma ta Ιan
sakar mishi fuska. Ko babu komai ta ji dadin mutunta da ya yi a wancan ranar
wanda tun daga shi, Musaddam bai Ζara gigin shiga hurumin Raihana ba. Ba ta da
masaniyar ko Fadeel mai yawan kiranta shi ne tsaye a nan ko kuwa dai wani
abokin na Ibb ne daban kusa da ita hakan yasa ta gaishe su a jam'u. Suka amsa,
Fadeel kam lebbansa ne suka motsa amma tuni ya yi nisa a kallonta, bai san
lokacin da ya Ζara mayar da hankalinsa kacokam kan kyakkyawar fuskarta ba.
'Wallahi ina sonta.' Ya yi furucin a can Ζasan ransa kafin
ya sa haΖori ya cije lebbansa ya sauke numfashi nannauya.
A cikin Ιakin taron kuwa, Tasleem da Futuha suka hana Ummita
zuwa ga Mami, karshe suka ce ta zauna su za su je su shigo da Humairar wurin
taron. Suka fito suka kara amsar katinsu suna dariyar mugunta, kawai burinsu su
ga fuskar Humaira a karshe su ce Mami ta ce ta wuce gida ba za ta sanya ta
roΖon kati a nan ba. Haka suka fito su na ta rarraba idanu, Futuha idanunta ya
kai kan Ibb dake tsaye yana zuba wannan murmushin nasa mai tsada, a gefensa
kuwa wani haΙaΙΙen matashi ne da ya zarce shi a haΙuwar. Ta dan murza idanu
tana kara dubawa, tabbas Ibb ne.
"Ke, zo ki raka ni. Wayyo zuciyata, me Ibb ke yi a
wajen bikin nan? Ko abokin Ango ne?"
Tasleem ta juyo, tuni Futuha ta soma tafiya ganin haka kawai
ta mara mata biya.
Shi kuwa Ibb babu abin da ya sanya shi murmushi illa gani da
ya yi Humaira ta Ιan saki jiki da shi tana sanar mishi cewa ai kam daga ranar
Musaddam bai Ζara shiga rayuwar Ζ΄ar uwarta ba.
"Alhamdulillah. Hakan na da kyau. Sai ki ci gaba da yi
mata nasiha. Allah ya Ζara nesanta ta da ire-irensu."
Murmushi Humaira ta yi lokacin da ta ke amsawa da amin.
Kallon Fadeel ba ta Ζara ba balle ta fahimci hankalinsa kacokam a kanta yake.
Har za ta tafi sai kuma ta kara duban Ibb.
"Yauwa, nikam ranar da abin ya faru, akwai wanda ka ba
lambata?"
Fadeel ya yi saurin dubansa, girgiza masa kai ya yi don haka
ya dube ta kamar bai fahimce ta ba.
"No, meyasa zan ba wa wani lambarki alhalin ko ni ban
taΙa kira ba?"
Ta Ιan yi shiru, haka kawai ta ji abin kamar rainin hankali
amma ta rasa tsakaninsa da wancan Fadeel din me kiranta a waya wane ya raina
mata? Don haka ta ce.
"Ba ka da aboki mai suna Fadeel?"
Fadeel dake tsaye ya ji tamkar ta ci gaba da ambaton sunansa
sanadiyyar hakan ba Ζaramin daΙi ya yi mishi ba. Ibb ya Ιan yi gyaran murya
domin ankarar da Fadeel ganin yanda ya harΙe hannuwa a Ζirji yana faman zabga
murmushi. Sai kuma ya ce.
"Yau na fara jin sunan gaskiya, wani abun ya faru
ne?"
Ta girgiza kai.
"Aa ba komai."
"Humaira."
Gaba daya suka juya ga inda kiran ya fito, Tasleem ce.
Futuha kuwa idanunta sun cicciko da kwalla, ji take kirjinta na wani zafi.
Mutumin da take kwana da tashi da tunani, shi dai wanda ya gagari kowace
budurwa da ma zawarawa a jami'arsu, shi ne tsaye a gaban Humaira kucakar da ba
ta kamo sawunta a kyau da hasken fata ba yana mata murmushinsa mai tsada da
take ji a ranta za ta iya kashe ko nawa ne ganin ita ta sami wannan damar. Amma
a banza gashinan ya na jifan Humaira da shi. Tasleem kuwa ta yi mutuwar tsaye
wajen kallon Fadeel, sai yanzu take jin ba son Hamza D take yi ba, son Ζarya
ne. Wannan abin da take ji game da Fadeel a yanzun shi ne so, soyayya kuwa ta
haΖiΖa.
Fadeel ya nanata sunan da ya ji Futuha ta ambata. Humaira,
shakka babu ta dace da masu sunan. Ibb kuwa ganin Futuha ya sanya shi tamke
fuska kamar ba shi ke yiwa Humaira murmushin ba. Sai gaba daya matasan suka yi
musu kwarjini, ita Futuha da ta yi niyyar wulaΖanta Humairar a gabansu sai ta
yi laushi, yayinda Tasleem dama tuni miyan bakinta ya kafe, tunani take irin
wadannan tsadaddun ai sai irin su masu zubin larabawa.
Dakyar Futuha ta yi magana.
"Mami ta ce ki wuce ki tafi gida tun da dai kin manta
katinki."
Jin haka sai ta ji babu dadi kadan, ta kwallafa ranta a
bikinnan ba don komai ba sai na son ta ga yanda tsarin biki yake a nan. Hatta
da fuskarta ta nuna rashin jin dadinta.
Tasleem kuwa da sauri ta gaida Ibb da Fadeel har da Ιan
ladabin Ζarya. Suka amsa.
"Sorry to ask, ba ta samu shiga wurin event din ba
ne?"
Fadeel ya tambaya a sanyaye, tun zuwansu wurin sai a sannan
ya yi magana. Humaira ta dube shi, kamar muryar mutuminta na waya, ya kauda kai
ya kara shan mur kar ta samu fuskar tambaya. Tasleem da ta kusa shiΙewa jin ya
yi mata magana duk kuwa da cewa akan Humaira ne ya sa ta saurin tankawa da wata
murya cike da yanga.
"Eh ta bar katin nata a gida ne, so shi ne Maminmu
kawai ta ce ta koma tunda ba za ta samu shiga ba."
Humaira ta tsaya kallon ikon Allah kawai, mamaki da haushin
irin wannan karairayar murya na Tasleem ya cika ta. Har sai da ta ja guntun
tsakin da sautinsa bai fito sosai ba.
"Muje."
Yana fadin haka ya yi gaba, Ibb ya kalli Humaira.
"Ku je za ki shiga yanzu in sha Allah."
Ta amsa da toh, ta bi bayansa ita da Tasleem, ita kuwa
Futuha ta ja burki gefen Ibb. Ya kauda kai tamkar bai san da ruwanta ba.
"Amm, Malam ba ka gane ni ba ko? Ni Ιalibarka ce
a.."
"Ban sanki ba." Ya tari hanzarinta da sauri, daga
nan ya taka ya nufi wurin motarsa ya tsaya. Futuha ido ya raina fata, ta dubi
wasu maza a gefe tsaye da wasu Ζ΄anmata da ma matan auren da ba su kai ga shiga
ciki ba suna mata dariya, tana kallonsu suka Ιauke kai. Gwuiwa a sake ta kama
hanya ta bi bayan su Tasleem, ranta ya yi tsananin Ιaci. Ita kam ta soma
gajiya da wulakancin Ibb, amma za ta yi hakuri tunda Anti Jannat ta haΙa ta da
wata Ζawarta dake garin za ta yi mata rakiya gurin wani Malami a yi musu aiki a
kansa. Amma zuciyarta na kokwanton aikin don ta ji wadanda sun buga sun kasa a
kanshi.
Humaira kuwa na tsaye gefe Tasleem na tambayarta inda ta san
su Ibb ta yi banza da ita kamar ba ta ji ba. Hankalinta na ga Fadeel dake
magana da Ιaya cikin masu tsaron wurin. Ba ta san ya aka yi ba sai juyowa ya yi
wannan karon gilashin da ya rufe Ζwayar idanunsa ya cire, lumsassun kyawawan
idanun suka bayyana, suka kusan susuta Tasleem har ba ta san ta ce "Masha
Allah." a fili ba sai da Humaira ta Ιan dube ta. Shi kuwa cikin ido ya
kalli Humaira ya mata alama da ta zo. Sai da ta karasa dab da shi kafin
ya samu damar magana.
"A sha biki lafiya. A gaida Mami."
Ta ji dadi sosai ganin da ta yi an ba ta damar shiga. Ta
kuwa buΙe masa haΖoranta har wushiryarta na bayyana a fili.
"Nagode sosai."
Ga Fadeel shima murmushin ya bita da shi, ji yake kamar ya
jawo ta jikinsa ya rungume. Da ace shari'a ta halarta masa ita ma, sai ya
sumbaci kuncinta wadanda har gani ya yi kamar su na sheΖi idan ta murmusa. Bai
taΙa ganin murmushinta ba sai a yau, sai ya ji inama za su dauwama ta na
jifansa da shi.
"Always welcome."
Ita dai ta yi gaba don bai san ba ta jin turanci bane, ta
dai tsinci welcome din. Zuwan Mubarak ta ji yanda su Tasleem ke faman welcome
welcome har ta nemi fassararsa a wajen Ummita. Babu wani iyaka kuwa aka bari ta
shige, tana Ιacewa ganinsa ya maida gilashinsa. Ganin Tasleem tsaye tana
kallonsa ya dauke kai, har zai wuce sai kuma dabara ta faΙo masa. Ya dubeta.
"Gidanku Ιaya?"
Ta yi wani farr da idanunta.
"Eh, babanmu Ιaya da ita."
Ya Ιan jinjina kai.
"Idan ba damuwa, ko zan iya samun full address na gidan
naku?"
Ba musu jiki na rawa ta hau yi mishi kwatance, ta kara da
fadin.
"Ko na ba ka phone number dina kaga ko da ace ba ka
gane ba sai na yi maka bayani ta waya idan ka tashi zuwa."
Kamar ya ce aa, sai ya tuna ba lallai ya samu cikakken
bayani daga Humaira ba dalilin haka kawai ya amince. Wayarsa ya ciro ya miΖa
mata. Tasleem ji ta yi kamar ta daka tsalle ta yi rawa da juyi, hannunta har
rawa yake yi. Ya dubi yanda take danna wayar cikin rawar jiki ya Ιan taΙe baki.
Ya fahimci inda ta dosa kwarai amma ya basar. Babu gurbin wata Ιiya mace a
rayuwarsa, madallah da Humaira da ta ciri tuta har ta yi nasarar sace
zuciyarsa.
Ya karΙi wayar kafin ma ya tambayi sunan da zai yi saving da
shi ta riga shi.
"Sunana Tasleem. Kar ka manta ka yi flashing Ιina kaga
koda ka kira zan gane kai ne saboda ban fiye Ιaga unknown number ba."
Bai sake kallonta ba kuma bai tanka ba ya fice yana zura
wayarsa cikin aljihu. Ta bishi da kallo kamar ta haΙiye shi. Futuha ita kuwa
tuni ta shige ciki saboda kunyar yanda Ibb ya yi watsi da ita. Ta kuma rantse
koda ace son Humaira yake, sai ta yi yanda ta yi ta raba su har abada. Tana ji
a jikinta ba lallai ta sami Ibb ba, toh kuwa Humaira ta yi kaΙan ta samu abinda
ita din ta rasa shi. A Ιangaren Tasleem kuwa gani take yi kawai ta tsinci dami
a akala, ta samu mijin aurenta. A farko har ta amincewa Hamza D da zuwa gaishe
da Abba, amma yanzu kam za ta dakatar da shi tunda ga Fadeel nan.
Wannan kenan.
***
Tun daga wannan ranar Futuha ke tsananin sanya idanu akan
Humaira. Daidai da wayarta idan ta yi Ζara sai ta yi saurin kallonta ta ga wane
ne. Rannan ta titse Raihana sai da ta titse wai wato Ibb ke kiran Humaira amma
ta nuna mata sam ba shi ba ne, tsabar ta koyi munafunci.
Raihana rai a Ιace ta amsa.
"Wai ke meyasa kin fiye son kanki ne? Toh koda ace
soyayyar ce tsakaninsu ai ke kin fi sauran masu haukar sonsa cin riba tunda ko
ba komai Ζanwarki yake aure."
Wannan magana ta fusata zuciyarta nan kuwa ta hau kilar
Raihana kamar an aiko ta. Lokacin Humaira na can gidan koyon girkinta. Ita kuwa
Tasleem ba ta dawo daga asibiti ba don yanzu su na asibiti an tura su daga
makaranta. A falon daga su Muhsin sai Ummita. Hankali tashe Ummita ta ruga
kicin ta kira Mami. Ganin abin da ke faruwa yasa Mami dakawa Futuha tsawa. Sai
a sannan ta miΖe daga ruwan cikin Raihana, gaba daya fuskarta ta yi tabo. Kuka
kawai take da ihun fadin Allah ya isa, raini kam ta daΙe da raina su.
"Wane irin hauka ne wannan? Kashe ta kike son
yi?!"
Cewar Mami tana duban Futuha dake faman huci. Sai kawai ta
fashe da kuka.
"Wallahi Mami ba don kamannin yarinyar nan da mu ba sai
ince ba Ζanwata ba ce! Wai saurayina ne Humaira ke so har da karΙar lambar
wayarsa suna waya. Raihana ta san komai tsakaninmu, kema Mami kin san shi, wai
shi ne take fatan da ace ya auri Humaira. A gaban idanuna."
Mami ta saki baki galala tana duban irin kukan da Futuha
take yi, lallai abin da zai sa ta kuka har haka ba Ζaramin abu ba ne. Tana da
taurin zuciya a wasu lokutan, ita kanta zancen ya shige ta don ba ta mance
yanda ta sha ba ta labarin wani Ibrahim ko kunyarta ba ta ji. Daidai da Anna ta
san da zaman soyayyar da Futuha ke yiwa Ibb, sun kuma ji daga bakin Tasleem da
ma su Yassar cewa mutumin bai damu da ita ba. Ta sauke ajiyar zuciya.
"Allah ya kyauta, shi ne akan wanda bai damu da ke ba
za ki kashe yar uwarki? Kar ku kuskura na Ζara ganin wannan rashin
hankalin."
Haka kawai ta fadi ta juya, madadin kicin ta wuce dakinta.
Futuha ranta ya yi baΖi, wato ma abin da Mamin za ta ce kenan? Ita dai ta tsani
halin rashin kulawar da Mamin ke nuna musu. A fusace ta yi sashin Anna har tana
bangazar Raihanar. Ita dai Ummita ba ta ce uffan ba, toh ban da abin Futuhar
ma, koda ace son Humaira yake, ta tabbatar ba zai samu fuska ba. Ita ta lura
kowa ma Humairar ta tsana muddin zai furta mata kalmar yana sonta.
***
Anti Amarya ta Ζurawa Murja dake zaune tana faman jijjiga
Ζafafu ido waya ta ke amsawa amma gaba daya fuska a jagule sai bayan ta kammala
ta ajiye wayar, sannan Anti Amarya ta soma magana.
"Yanzu ke wannan Idris din kinsan matsayin babansa
kuwa? Meyasa Murja ba ki da wayo da tunani? Kin maΖale akan yaron da idan ya
shigo gidan nan kallo ba ki ishe shi ba? Komai kika yi ba ki iya ba, amma Idris
tun haΙuwarku a bikin Fu'ad ya manne maki kuma dagaske aurenki ya ke son yi.
Kinga ina raba ki, wannan fa shi ne saki reshe kama ganye. Kin gani sarai da
idanunki yanda Ubansa ke ji da shi kamar ba shi da wasu yaran bayan sa, ko a
haka ya dace ki fahimci babu wanda zai yi mishi auren dole. Ko da ace kuwa ba
namiji ba ne, tun da ya sa Ζafa ya dawo Ζasar nan, Alhaji ke gudun abin da zai
Ζara sanya wa ya yi nesa da shi. Toh kuwa ki kama kanki tun wuri ina
shawartarki, soyayyar Fadeel ba za ta kai ki ko'ina ba. Ina kara faΙamaki
wallahi ba ya sonki ba ya kaunarki."
Ta sani gaskiya ne tsagwaronta yayarta ke faΙi, amma ina, ta
riga ta yi nisa da son Fadeel. Ta gama tsara yanda za su yi rayuwar aurensu
wannan ya sa maganganun ke shigarta su na fita ta kunnen hagu. Ta furzar da
huci.
"Shikenan, na yanke shawarar abin da zan yi."
A zaton Anti Amarya, ta dauki shawararta don haka ta
murmusa.
"Ko kefa."
Ita kuwa murmushi ta Ιan yi, ta kuma Ζudurta a ranta za ta
tari Fadeel kawai ta ce mishi tana sonsa. A yanda ta ga yana ganin mutuncin
Antinnasa, ba zai watsa mata Ζasa a idanu ba.
***
BAYAN SATI ΖAYA...
A wani yammacin ranar
Juma'a ne, Humaira na tsaye tana ninkin kayanta tana jerawa a sif. Futuha kuwa
ta Ζure volume Ιin waΖar Kalmar So na breaker tana bi tana daukar bidiyo na
kanta a tiktok. Riga gown ne a jikinta lemon green fuskar ta sha make up.
Gashinta a waje ko Ιankwali babu, sai raye-raye take. Raihana da Ummita na zaune su na aikin lissafi na
makaranta da aka ba su, su na Ιan taΙa
hira jifa-jifa da Humaira. Su na yi suna kallon ikon Allah wajen Futuha da ta
saita Camera ta waya sai raye-raye ta ke yi. Wannan karon ta sauya waΖar zuwa
Warr na Ado Gwanja.
Kusan yanzun aikinta
kenan, ta yi rawa ta Ιora a Tiktok da Instagram, babu laifi kuma ta samu mabiya
sosai, wannan ya kara fasa mata kai, a farko hotunanta kawai take Ιorawa
iri-iri a instagram, amma ba ta jima da soma Tiktok ba ta ga ta samu karΙuwa
wannan ba karamin Ιauke hankalinta ya ke ba a yanzu. Su na a haka sai ga
Tasleem ta faΙo Ιakin da gudu. Jiki na rawa ta karasa sif din kayanta ta bude.
Futuha wacce ta kammala tana editing kafin ta dora ta dakata tana dubanta.
"Ke kuma lafiya?"
Ta juyo da wani irin zumudi.
"Kalau, babban baΖo zan yi fa. Kin tuna guy dinnan da
na hadu da shi ranar bikin Shema'u? Abokin Ibb?"
Futuha ta gyada kai. Tasleem ta daka tsallen murna.
"Shi ne ya yimin waya ya kara neman kwatance, yau zai
zo."
Ita kanta Futuha ta jiye mata dadi, amma haka nan ta ji Ιan
kishin yar uwar a ranta. Me Tasleem ta fi ta da har za ta yi kamu me zafi haka
lokaci Ιaya amma ita kuma ta kasa samun Ibb? Tun su na yara an sha cewa ta fi
Tasleem kyau, balle kuma yanzun da suka girma. Kowa ita ya fi kira kyakkyawa a
kan dai Tasleem. Wannan ma na daya daga cikin abin da ya fasawa Tasleem kai a
yanzun, itama tana jin takaicin kusheta da yan uwan Mami har ma da na Abba ke
yi a lokuta da dama su ce wai Futuha ta fi ta kyau. Sai Futuha ta kasa ce mata
komai bayan "Inyee, na maki murna." Daga nan ta ci gaba da
latse-latsen wayarta tana murmushin da bai kai zuci ba. Tasleem ta maida
hankali ga duban sif dinta, ta san Futuha mace ce mai kishi, ta fi kaunar komai
ta fi kowa, kuma sai gashinan nasarar a kanta take. Tashi guda ta yi kamun
babban kifin da ya fi wanda Futuhar ke hari.
Raihana kuwa duban Ummita ta yi. Cikin sanyin muryar da ba
lallai su Tasleem su ji ba ta ce.
"Kada dai ace Fadeel me son Humaira ne zai zo?"
Ita ma Ummita hakan ta ke zargi, Humaira na jin su ta yi
kamar ba ta ji ba. Ta sani tabbas shi ne, sai bayan sun rabu ta kara tabbatarwa
shi ne mai kiranta adalilin saΖon da ya turo mata bayan shigarta wurin bikin
Shema'un, inda ya ce mata ta yi kyau kuma ya yaba da murmushin da ta yi mishi a
lokacin. Sannan bayan sallar juma'a a yau din, ya bar mata saΖo inda yake
shaida mata batun zuwansa gidansu a yau. Ya kuma roΖe ta kar ta Ζi fitowa. Ita
kuwa a take ci kanka ba ta aika mishi ba balle ta kira ta dakatar da shi daga
zuwan, ta fi kaunar ya zo ta jaddada masa ido cikin ido cewa ita ba ta soyayya,
kuma ba ta sonsa ya rabu da ita.
Tunano hakan sai ta ji dariya ya kama ta, dakyar ta danne ta
hanyar murmusawa. Wato dai yau din akwai kallo kenan. Ta kara duban Tasleem da
ta sauya kaya zuwa wani leshinta ja mai Ιigon baΖi a jikinsa mai Ιan karen
kyau, murmushin ta kara saki wannan karon har da sautin dariyar da ya sa su
Raihana dubanta, suka kuma dubi junansu, sun tabbatar Fadeel Ιin Humaira ne a
hanyar zuwa. Akwai dai matsala kenan.
Wayar Tasleem da ta Ιau
Ζara ne ya sa ta saurin jifa da kwalbar turaren dake hannunta a saman gado, ta
zari mayafinta da ya hau da leshin Ιan firit wanda ko kirjinta bai gama rufewa
ba, ficewa a dakin ta yi bayan ta kara wayar a kunne tana fadin ga ta nan
fitowa waje. Futuha ta mike ta bi bayanta wai za ta gani ko dagaske Tasleem din
ta ke. Suna fita Humaira ta tuntsire da dariya har da faΙawa saman gado.
Raihana da Ummita su ma dariyar suka shiga yi.
"Ni dama ya ce yana son nata dagaske ai da naji dadi,
ko ba komai na huta da alaΖaΖai. Haba, ina dalili mutum ana korarsa yana
mannewa sai ka ce mayen Ζarfe."
Ta ja guntun tsaki ta mike ta ci gaba da ninkin.
"Kai Humaira anya a duniya za ki yi aure kuwa? Wannan
abu har ina wai? Duk kyau da kwalisa na saurayi ba kya sonsa? Meke
damunki?"
Ummita ta ce tana duban ta, ji take kamar ta kai hannu ta
buge ta tsabar haushi. Itama Raihana ta cafe
"Rabu da ita Ummita, ai kanta akwai alamar kuncewar
notina. Da ace ma ni ce ke, ko don na nunawa Tasleem ita Ιin ba komai ba ce a
wurin Fadeel ai wallahi da hannu bibbiyu zan tarbe shi, shima dai Fadeel din da
ba shi da zuciya ya kyaleki ya Ζi, ya bari kina ta wulaΖanta shi son rai. Da ni
ce shi ko?"
Ta yi Ζwafa amma ba ta ce komai ba, Humaira wacce tun soma
maganarsu take kwaΙa musu harara, ta ja tsaki.
"Matsalarsa, ni dai ai ban yaudareshi ba, tun farko
kuma na faΙamasa ya rabu da ni, ya ficemin a rayuwa amma ya Ζi. Aikuwa babu
abin da zan ce mishi, ya je can ya Ζarata da Tasleem."
Ba su ce uffan ba sai kallon mamaki da suke mata, dagaske
dai take ko a jikinta don ba su ga wani Ιigon kishi a saman fuskarta ba.
A Ιangaren Tasleem kuwa, tana Ζarasawa falon ta ci karo da
Mami a zaune tana amsa waya. Ganin ta da shirin fita ya sanya ta yi sallama da
abokiyar wayar ta dube ta dakyau.
"Ke kuma sai ina haka?"
"Mami baΖo fa nayi, bari na shigo da shi falon saukar
baΖi sai na zo."
Ba ta ma kara jin abin da zai fito a bakin Mamin ba ta yi
wuf ta fice, Mami ta yi kasake tana duban hanya, fitowar Futuha ya sanya ta
maida akalar tambayar a kanta.
"Wannan wane baΖon ta Ζara yi a yanzu ne? Duka-duka
yaushe shi Hamzan ya zo da har zai Ζara zuwa?"
TaΙe baki Futuha ta yi cike da jin kishin Ζ΄ar uwarta ta
amsa.
"Uhum, wai fa abokin Ibb ne yake sonta shi ne take
wannan rawar jikin."
Wani Ιan murmushi Mami ta yi.
"Wato dai ruwan ido ne abin nata kenan? Ya za ta yi da
shi wanda ta yiwa iznin zuwa su gaisa da Abbanta?"
"Mami, wannan fa ya fi Hamza kudi da haΙuwa, na tabbata
abin da ya ruΙe ta kenan."
Mamin ba ta ce komai ba face Allah ya kyauta.
***
Yana zaune a cikin motar hankalinsa rankatakaf akan Ζaton
Ζyauren gidan da Tasleem ta yi mishi kwatance, ji yake tamkar ya yi tsuntsuwa
ya shiga ya yi ido huΙu da abar Ζaunarsa, ganin ya kwashi mintuna babu alamar
Tasleem sai ya ji gaba Ιaya ya karaya. Kodai ba gidan ba ne? Waya ya fiddo da
niyyar Ζara kiranta sai ya hange ta ta fito daga gidan. Da farko sam bai gane
ta ganin tamkar wannan Ιin shirin fita unguwa ta yi, ga dukkan alamu ma ba
gidan ba ne. Amma a hankali tana matsowa ya gane ita ce don haka ya sauke
tinted glass din motar wanda ya katange ta daga ganinsa sai waige ta ke.
Tasleem kuwa yana saukewa ta ji numfashinta na barazanae Ιaukewa
ba don tsoro ba sai domin tsananin burgeta da ya yi, ga kuma wani irin kyau da
ya yi mata. Shadda ce a jikinsa coffee colour, ya Ιora hula a kansa, wannan
karon babu gilashi a idanunsa don haka kyawun fuskar ya Ζara bayyana muraran.
Ta kasa furta koda harafi har sai da don kansa ya fito daga motar ya rufe.
Murmushi mai tsada ya sakar mata.
"Ashe kin iya kwatance."
Ta yi farr da idanu haΙi da sakarmasa nata kalar murmushin
itama. Cike da yanga da kwarkwasa ta ce.
"Kai kuma kana da basira tunda har ka iya ganewa. Barka
da zuwa, bismillah mu shiga daga ciki."
Ba musu ya karΙi tayinta, bayan sun gaisa da maigadi dake
zaune a benci, tana gaba yana biye da ita yana Ζarewa gidan kallo. Hatta da
gidan sai da ya ji kaunarsa a zuciya, ya kuma rantse albarkacin masoyiyar tasa
ce. Falon suka shiga ya zauna bayan ta mishi bismillah, sai Ζamshi kuwa
ke tashi a ciki don dama tunda ya yi mata kiran farko ta ba mai wankin Abba
dari biyu akan ya taimaka ya kara share mata a sa turaren wuta.
"Ina zuwa." Ganin ta furta haka tana niyyar ficewa
sai bai ce mata uffan ba, ba ya son ya yi garaje da tambayarta Humairar, tunda
har ta ce tana zuwa to ya sani ba zai wuce ita za ta rako ba.
Ya lumshe idanunsa kafin ya buΙe ya sauke saman hoton Abban
dake maΖale jikin bangon. Ko wani bai faΙamasa ba, wannan mahaifin Humaira ne,
kamannin ya Ιaci kwarai. Sai ya ji kaunar Abban ya lulluΙeshi, Ζauna dai
kwatankwacin irin kaunarsa da Alhajinsa. Sallamar Tasleem din karo na biyu ya
katse dukkan tunaninsa. Ganinta Ιauke da tray na kayan sanyi nan da nan ya Ιan Ιaure
fuska, shi fa duk ba wannan ne a gabansa ba. Tana ajiyewa ya ga tana kokarin
zama ya karya bille ya ce.
"Where is she?"
Ta dube shi cikin rashin fahimta, ta yi Ζarfin hali ta ce.
"Who?"
Ya dauke kai daga kallonta, ya soma hasaso wani abun, ya
gane ita Ιin manufarta daban, tunaninta ya tafi wani wajen. Mafarkinta daban.
"Wacce na zo domin ta, Humaira."
Kirjin Tasleem ya hau bugu, har ji ta yi ganinta ya Ιan
dusashe. Miyan bakinta haka ta neme shi ta rasa, dakyar ta tattaro jarumta ta
ce.
"Humaira kuma? Dama wajenta ka zo."
Sai a sannan ya dube ta tsakar ido.
"Yes, wurinta na zo. Ko sadda muka haΙu dama haka nace
wujenki zan zo?"
Tasleem da har ta soma hawaye ta kasa magana, eh bai furta
cewa wajenta zai zo ba, amma wane rainin hankali ne ya sa bai nemi kwatance
daga Humaira ba sai a wurinta? Ta kuwa daure fuska tamau, ta rantse daga ita
har Humairar sai dai su yi biyu babu. Kowa ya rasa don hana ta ce.
"Toh Humaira ban santa ba, asalima a wurin biki muka haΙu.
Na yi zaton gidanmu kake nufin na kwatanta mana. Don haka babu Humaira a
gidannan."
"Ko?" Ya furta idanunsa a saman hoton Abba, itama
ta kalli hoton. Ranta ya Ιaci ainun, ta san kamannin Humaira muraran da ya gani
a fuskar Abba ya sanya shi furta hakan. Ta mike tsaye ta koma gefen
Fadeel ta zauna. Zuwa yanzu ransa ya kai maΖura wajen Ιaci amma yana
tausar zuciyarsa da tunanin bai dace ba, ta ci alfarmar abin sonsa. Ko babu
komai tace masa mahaifinsu guda. Ita kuwa da muryar kuka ta soma magana.
"Wallahi ina sonka. Tun ganin farko da nayi maka
zuciyata ta kamu da begenka. Me za ka yi da Humaira? Da me ta fi ni? Na rantse
babu abin da za ta nunamin."
Ya runtse idanu, ransa Ιaci yake ya na kokarin danneshi,
amma jin ana kushe abar sonsa ya bude idanunsa da suka yi jawur tarr a cikin
nata. Sai da ta ji rishin kukan ya tsaya na Ιan lokaci tsabar fargabar kar ya
shaΖo ta.
"Ki san kalaman da za ki faΙi a kanta. Idan kuma kina
son kanki da mutunci, ki yakice ni a ranki. Ki sani kuma ki kara, Humaira ta
fiyemin ire-irenki dubu. Kyau da sura ba su ne a gabana ba. Da ace su ne, na
bar da yawansu a inda na fito, ba na sonki, ba kuma na son kowa sai ita Ιin.
Idan za ki iya ki shiga ki yimin sallama da ita, idan ba ki iyawa ni zan sa a
kira ta."
Da gudu Tasleem ta mike ta yi hanyar fita tana kuka sosai.
Fadeel ya mike tsam ya fito farfajiyar gidan inda ya ci karo da Muhsin na wasa
da keke. Ζarasawa ya yi wurinsa ya Ιan durkusa daidai tsawon yaron yana
murmushi kamar ba yanzun aka Ιata ransa ba.
"Boy, ya sunanka?"
"Muhsin."
Ya jinjina kai, da alama duka sunayen yan gidan su Humaira
masu dadi ne, shi kam dadi yake mishi, ya ji ance Futuha, Tasleem yanzu kuma ga
Muhsin.
Ganin yaron na shirin janye keken ya sanya shi saurin riΖe
keken.
"Ζan shiga ciki ka ce Humaira ta zo, Fadeel ya
iso."
Jin haka Muhsin ya amsa da toh, ya juya kan kekensa bayan
Fadeel ya saki ya wuce ciki.
***
A can kuwa, Mami da Futuha na zaune sai gani suka yi
Tasleem ta fado falon a guje, tana zuwa ta zube cinyar Mamin tana kuka.
"Ke lafiya? Meyafaru?" Cewar Mami cikin Ιaga murya
gaba daya ta ruΙe. Wannan ya yi sanadin fitowar su Humaira daga Ιaki sai a
sannan Tasleem ta Ιago ta dubi Mami.
"Wai ba ki yake so ba, wajen Humaira ya zo."
Jin haka Futuha ta ji zuciyarta dan yi sanyi, ko ba komai
Tasleem ba za ta Ζara hura mata hancin ta yi wanda ya fi Ibb ba kuma ta gane ba
Ibb ne masoyin Humairar ba. Amma a gefe kuma kishi da tsanar Humaira ne ya kara
mamaye ta, mene ne da ita wanda har namiji irin Fadeel zai gani ya maΖale mata,
su da suke buzaye ma ta kasa shawo kan Ibb ya kaunace ta sai wata can
bafulatanar ruga?
Mami kuwa gaba daya fuskarta ta sauya, kafin ta yi magana
dai ga Muhsin a guje da kekensa ya shigo falon, yana cin karo da Humaira ya ce.
"Adda Humaira, ki je inji wani a waje."
"Ka je ka ce ba za ta fito ba! Kada ya kara gigin zuwa
gidannan!"
Gaba daya suka dubi fuskar kowannensu dauke da mamaki
idan ka cire Humaira da kalaman ya yi mata dadi ainun, haba ta gaji da naci
irin na Fadeel, shi bai san ba ta son komai da ya danganci saurayi ba. Meyasa
ya Ζi fahimta? Ai gwara Mamin ta kora mata shi. A bangaren Raihana da Ummita
kuwa tunaninsu daban da nata. Akan me Mami za ta ce Fadeel ya tafi? Wato don ba
ya sin Tasleem shikenan kowa ma ya rasa? Tasleem da Futuha kuwa dadi ne ya
mamaye su, wato dai uwa uwa ce, ta damu da yaranta. A farko sun yi zaton
kwata-kwata Mamin ba ta kaunarsu ta fi kaunar Ζ΄an riΖonta musamman ma Humaira.
Amma a hukuncin da ta yi abin ya musu dadi, Tasleem ta ji gwara ma kowa ya
rasa.
Muhsin kuwa tuni ya fice don cika umarnin Maminsa. Humaira
dai ta juya zuwa daki don ci gaba da abin da ya rage na ninkin da take yi,
ganin haka Ummita ta bi bayanta, Raihana kuwa da sauri ta bi bayan Muhsin.
Futuha na kwala mata kira ta yi mata banza.
***
A can farfajiyar gidan kuwa, Muhsin ne ya karaso har kusa da
Fadeel, yana shirin faΙin saΖon Mami da sauri Raihana ta kwala mishi kira.
"Kai Muhsin." Suka juya har Fadeel suka dube ta,
ta karaso da sauri ta ce.
"Jeka zan faΙamasa." Ya kuwa tura kekensa ya ci
gaba da zagaye a gidan yana waΖe-waΖensa da ake musu a boko. Ta gaida shi ya
amsa, zuwa yanzu ya karaya da ganin Humaira.
"Suna na Raihana Ζanwa ce ga Humaira, don Allah ka yi
hakuri ba za ka samu ganinta ba a yau sai dai ko watarana idan an Ιan kwana
biyu."
Murmushin da bai kai zuci ba ya yi, ta tabbata shi kadai ke
kiΙa da rawar sa, wacce ya ke yaΖin don ita ba ta san yana yi ba, ko kuma ya ce
ta sani amma ra'ayinsu ya sha bamban.
"Kar ki damu, ba komai. Idan kin shiga ki ce ina gaishe
ta, na kuma cika alΖawarin da na daukarwa kaina na zuwa gidansu. Amma hakan ba
ya nufin ko a mafarki zan iya fita a rayuwarta. Ina sonta."
Daga nan ya juya ya fice. Raihana ta zuba masa idanu har ya
fita daga gate din gidan, tausayi sosai ya ba ta, Humaira dai tana neman cutar
da kanta. Samun masoyin gaske irin Fadeel abu ne mai matuΖar wahala. Ta ji
haushin Humaira a zuciyarta kamar ta je ta rufe ta da duka. Gwuiwa a sake haka
ta juya ta koma ciki.
***
Tun faruwar wannan lamarin Fadeel ya shiga damuwa ainun,
yana da tabbacin shi yake so ba a sonsa, ya kuma shirya rungumar wannan
jarrabawar ya yaΖe shi. A gefe ga mahaifansu da suka soma matsawa akan su fito
da matan aure shi da Ibb. Satinsa guda bai kira ta ba balle ya aika mata saΖo,
jarrabawa ya yi domin ya ga ko zai iya yakice ta a rai bisa shawarar Ibb amma
sai ya ji kamar yanzun ne ma ya soma kaunarta. Ba kuma ya jin zai iya haΖura da
ita. Ya miΖe daga saman gadon da yake kwance wanda tashinsa kenan daga bacci
mai cike da mafarkan Humaira, kamar daga sama ya ji ana kwankwasa Ζofar falon,
agogon dake maΖale a bangon Ιakin ya kalla, Ζarfe goma har ta gota. Ya Ιan ja
Ζaramin tsaki, ya tuna yau suka yi da Alhaji zai soma zuwa kamfaninsa ya kama
aiki, jin Ζarar kwankwasar yake har cikin kansa dake radadin ciwo, iya sati Ιaya
zuciyarsa ta jigatu da rashin ji ko ganin Humaira, ta ina zai soma fidda ta
daga rayuwarsa? Wannan abu ne da ba zai yiwu ba sam. A hankali ya miΖe daga shi
sai vest da dogon wando ya fito falon.
"Waye?"
"Ni ce Yaya Fadeel, abin kari na kawomaka."
Guntun tsaki ya ja jin muryar Murja. Ζofar kawai ya bude ya
juya ba tare da ya ko kalle ta ba ya ce.
"Ki ajiye ki fice. Na gode."
Ta ji ciwon hakan amma da ta tuno da batun Malam na cewa
idan har ya ci abinda ta girka da laΖanin da ya ba ta to fa ba makawa
hankalinsa zai karkato gare ta. Ya yi mata gargadi akan lallai ta tabbata ya
ci, idan kuwa bai ci ba to fa haka za ta kara narka uban kudade a yi mata wani
sabon aikin. Don haka sai ta zauna a falon ta Ζi bin umarninsa, shi kuwa wanka
ya shiga bayan sun yi waya da Alhaji ya buΙe mishi wuta akan rashin zuwansa
ofis da wuri, hakuri ya dinga a shi ya ce yana tafe. Suka yi sallama. Koda
ya fito wankan a gaggauce ya shirya cikin kananun kaya, dark green din tshirt
sai wandon jeans. Ya Ιaura agogo a tsintsiyar hannunsa, ya gyara sumar kansa.
Fitowarsa falon ya ga mutum zaune, nan da nan ya tamke fuska, ita kuwa Murja da
rawar jiki ta ce.
"Barka da safiya, bari na haΙa maka shayin."
Ba tare da ya kalle ta ba ya ce.
"No ki bar shi nayi latti, Alhaji na jirana. Ki je da
su kawai."
Murja cikinta ya bada sautin kululu, ita dai ta shiga uku,
wannan rashin sa'a har ina? Yanzu shikenan ta yi asarar dubu tamanin? Ita kuwa
wa za ta je ya ba ta wasu kudaden a Ζara maimaicin aiki?
"Ba kya ji ne?"
Wannan karon ya yi maganar yana ji kamar ya Ιauke ta da mari
hagu da dama, abu Ιaya da ya sa yake raga mata bai wuce na tunanin shi Ιin ma
fa haka yake fama da soyayyar wata ba ta sonsa.
Ganin yanayinsa sai ta maida kayan kwandon ta dauka ta fice
har da kwallarta. Fadeel yana so ya kashe ta, yanzun ma ji take kamar ta faΙa
wannan faΙaΙΙan kirjin nasa ya yi mata rumfa da hannuwansa, sai dai kash!
Wutsiyar raΖumi ta yi nesa da Ζasa. Amma kuma komai nisan jifa Ζasa zai faΙo
kuma sannu sannu ba ta hana zuwa, ta na ji a jikinta watarana haΖanta zai cimma
ruwa.
***
Abba ne zaune fuskarsa cike da walwala, babu jimawa iyayen
Hamza suka tafi bayan sun nemawa Ιansu auren Tasleem kuma ba musu ya amince ya
ba su. Tasleem da kanta ta kira Hamza ta ce ya turo saboda bakin cikin abinda
Fadeel ya yi mata, ga faΙan da suka yi da Futuha me yi mata dariyar ta
rasa shi, ita kuma don ta nunawa Futuha tana da mai sonta dagaske ba irin ita
me bin Ibb ba ya sonta ba yasa ta kiran Hamza ta ce matukar dagaske yake toh ya
turo a nema mishi aurenta a kwana uku, idan kuwa ya wuce haka to kaunar da yake
mata a baki ne. Dama kuma shi abin da yake jira kenan, don haka sai kawai ya ba
da kai bori ya hau.
Mami ta shigo itama fuskarta dauke da walwala ta zauna gefen
Abba. Kafin ma ta ce wani abu ya riga ta.
"Maryama yau ina cike da farin ciki, ba ni da burin da
ya wuce naga na aurar da yarannan mata lafiya kowaccensu ta tare a Ιakinta. Ina
tsoron sharrin wannan zamani. Ita ma Futuha zan mata magana, ta fito da miji na
haΙa aurensu baki Ιaya zai fi min. Karatun can su je su Ζarasa a Ιakin
mazajensu, naji da kannensu masu tasowa."
Mami ta jinjina kai,
"Hakane Abban yara, in sha Allahu itama zamu yi magana
da ita naji ko tana da tsayayye. Na san dai wani yaro da ta kwallafa rai a
kansa amma shi bai san tana yi ba."
Abba ya Ιan yamutse fuska.
"Ai kinji irin shirmen yaran yanzu masu biyewa soyayya,
ban da shiririta ke ba manema kika rasa ba, mutane nawa ne suka tare ni akan
suna sonki amma ki nacewa wanda ba ya so? Allah ya kyauta, lallai ki ce mata
nace ta nutsu ta fiddo miji a haΙa aurensu da Ζ΄ar uwarta. Kina ji dai iyayen
shi Hamza sun ce nan da wata shida suke so a yi komai a Ζare."
"Shikenan, zan mata magana." Mami ta amsa a
sanyaye, fatanta Allah yasa Futuha ta cire ran da ta kwallafa akan Ibb ta kama
wani.
***
Futuha na zaune tana danne-dannenta a waya kamar
koyaushe, bidiyo mai zafi ta Ιora tana bin waΖa, ta ci ado a bidiyon har ta
gaji, ta yi Ιaurin ture ka ga tsiya da dankwalinta na leshi, karanta comments
kawai take tana jin dadi tana zabga murmushi, wasu kuwa zagi ne da addu'ar nema
ma ta shiriya. Irin wannan sai dai ta ja tsaki ta wuce. Ta ci gaba da kallon
bidiyoyin jama'a nan ta ci karo da wani bidiyo da ya Ιaga hankalinta wacce wata
Sa'a Ζ³ar snow ta yi a kanta, zagi ne na cin mutunci da sharri, wai Baby Futuha
ta tiktok karuwa ce kuma tana da hotunanta da shaidu akan hakan. Tashin
hankalin har da hotonta daga Ζasa gefen bidiyon. Ba ta san sadda ta kwalla Ζara
ba a Ιakin bar ya farkar da Humaira me baccin sha biyu. Su biyu ne dama kaΙai a
Ιakin, ita Humaira ma ba ta san Futuhar ta shigo ba domin gaba daya sun fita
makaranta, kenan ta dawo ita. Kuka sosai Futuha ke yi hannunta har yana
kakkarwa. Humaira ta ji hankalinta ya tashi, duk kuwa da cewar ba sa shiri ta
miΖe ta Ζarasa gareta.
"Anti Futuha lafiya?"
Ba ta ko kalleta ba ta wuce da sauri ta yi hanyar fita.
Humaira dai na kallon ikon Allah. Toh me ya yi zafi haka? Ta watsar da batunta
gami da buga hamma.
Futuha kai tsaye falo ta nufa, babu kowa, cikinta ya Ιuri
ruwa, yanzu wa za ta faΙawa wannan abu? Muddin Mami ta ji ranta zai Ιaci don
dama ba da son ranta Futuhar ke Ιora bidiyo a Tiktok ba. Anna kuwa, ba lallai
shawararta ya yi wani tasiri ba. Don haka kawai sai ta yi Ιakin samarin
yayyunta. Kwankwasawa take iya karfinta, babu kowa sai Dawud dake baccin rana.
Ya taso a firgice, har zai soma masifa amman ganin yanayinta sai ya fasa.
"Meyafaru?" Ya tambaya a ruΙe. Ta bude wayar da
tuni ta shige lock, miΖamasa ta yi. Ya kalla tun farko har karshe, ya dafe kai
yana mai runtse idanu.
"Kinga irinta ko! Kin ga abinda nake faΙamaki. Na faΙamaki
matan nan na Tiktok muddin suka ga kina musu shiga hanci da kudundune zasu
sanyoki a gaba. Ballantana ma ganin kin kama hanyar shahara. Sa'a Ζ΄ar snow!
Yarinyar ba ta da mutunci ko kadan, matar da ke ikrari a fili ita karuwa ce
kuma ba ta ga ranar da za ta rabu da karuwanci ba sannan ta shirya tone-tonen
yan barikin tiktok."
Futuha ta jinjina kai har sannan tana sheshsheka, ta san da
wannan, haka Ιin ne ma ya sanya ta shiga ruΙu da tashin hankali, waΙanda za su
yarda da zancen sun fi waΙanda ba za su Ιauka ba yawa. Ko ba komai jita-jita ya
fi saurin yaΙuwa koda kuwa akan Ζarya ne.
"Ya zan yi Dawud? Na shiga ruΙani, me zan ce jama'a su
yarda sharri ne aka yimin?"
Dawud ya yi shiru, shima dai kansa ya yi masifar Ζullewa. Ya
rasa me zai ce, daga kuma irin yanda ake zuba ruwan comment na zagi da
ma masu rubuta ai za ta aikata lamarin ya samu karΙuwa kenan.
Kafin su ce komai sai ga wayar Aina'u ya shigo, Dawud ya Ιaga.
"Ke Futuha! Kinga wani Ιan iskan bidiyo da Snow
ta yi a kanki? Wallahi na shiga rudani, mene gaskiyar abin da ta ce game da
ke?"
Hankalinta ya kara tashi.
"Aina'u ke ce mafi kusa da ni a Ζawayena, yanzu kin
yarda da abin da aka ce a kaina? Idan kika yarda waye ba zai Ζi yarda ba?
Wallahi Allah karya take yimin, ni Futuha ban taΙa zina ba a rayuwata. Ke kanki
kin sani."
"To ai kuwa wallahi kinji na rantse sai kin yi dagaske
za ki wanke kanki a idanun duniya musamman Ζ΄an Tiktok, yanzu na faΙamaki a
whatsapp na ci karo da bidiyon an turo group dinmu na makaranta."
Zaro ido Futuha ta yi, ji take komai tamkar a mafarki, ta
kasa amsawa. Ga Aina'u a layi tana faman hello hello, ga kuma sunan Babban Yaya
(Wato Mubarak) yana yawo a saman screen din, shaidar kiransa ya shigo. Dawud
zai katse na Aina'u ya Ιaga cikin sauri Futuha ta warce wayar ta kasheta
gaba Ιaya. Cikinta ya murΙa ba ta tsaya ba shi amsa ba ta ruga Ιakinsu. Ta
tsallake Mami wacce fitowarta kenan daga bangaren Anna su na tattaunawa akan
auren Tasleem da wadanda ya dace su gayyata cikin yan uwansu na Agadez. Mami ta
bi ta da kallon mamaki da tunanin ko lafiya, wayarta ta yi Ζara, ganin Mubarak
yasa ta Ιaga.
"Mami, kina sane da abin da yarinyar can ta aikata
ko?"
Cikin rashin fahimta da tsananin ruΙewa ta ce.
"Wa kake nufi? Meyafaru wai?"
Nan ya ba ta labarin ire-iren raye-raye da Futuha ke Ιorawa
a Tiktok, ya kuma cewa Mamin ta duba whatsapp zai aikomata da wani bidiyo ta
gani. Hannayen Mami har rawa suke yi, ta hau online bayan ta kunna data,
saΖonni suka shiga faΙowa har na Hajiya Lubna wacce itama bidiyo ta aikomata.
Sam hankalinta ya yi gaba akan saΖon Mubarak, ta buΙe ta soma kallon irin ruwan
rashin mutuncin da wata wai Sa'a Ζ΄ar Snow ta saukewa Futuha, ga hoton Futuhar
nan daga Ζasa. Mami tuni hawaye sun wanke fuskarta, ban da innalillahi ba
abinda take furtawa, ya yi daidai da shigowar Dawud falon, ganin yanayin Mamin
sai ya tabbatar abin da yake gudu ya afku, wato dai Mubarak ya sanar da Mamin
komai. Ya kuma san halinsa, maganar ba iyakar Mami za ta tsaya ba, sai ya
dangana da Abbansu.
Ganin tsayuwa na neman gagarar Mamin sai ta zauna a hannun
kujera mafi kusa da inda take tsaye. Dawud ya karasa da sauri.
"Mami, yi a hankali."
Ta girgiza kai, ina batun hankali anan bayan Ιiyarta ta
jawomusu abin kunya abin kuma magana. Kamar kuma wacce aka tsikara ta mike da
sauri ta nufi hanyar dakin su Futuha sam hankalinta ba ya tare da ita. Ganin
haka Dawud ya mara mata baya, fadi yake "Mami wallahi sharrin Ζ΄an Tiktok
ta hadu da shi, ke kin sani diyarki ba za ta aikata maki abin kunya ba. Don
Allah Mami ki saurare ni, nasan wace wannan Sa'ar, ba ta da mutunci na
Ζarshe."
Inaa! Ba ta san ma yana yi ba, shigarta Ιakin ya yi daidai
da fitowar Futuha daga banΙaki, har a lokacin sheshsheΖa kawai ta ke yi.
Humaira tuni ta tashi tana zaune gefen gado ta yi shiru, ita dai ta san babu
lafiya. Ba ta taΙa ganin Futuha na irin wannan kukan ba kamar na wacce aka yiwa
mutuwa. Shigowar Mamin ya sa ta maida hankali gareta, ba ta yi wata-wata ba ta
hau dukan Futuha tana kuka tana fadin.
"Shegiya marar
tarbiyya! Wato ke ga yar iska ashe raye-rayen da na nunamaki bana so shi ne
kika cigaba da yi har ya jawomaki kalmar karuwa?!"
Mami bugu take ita kuwa Futuha tana ihun kuka. Humaira da
Dawud hakuri kawai suke ba Mami, su kansu hankalinsu ba a nutse ba. Babu
kamar ita Humairar da ba ta san hawa da
sauka ba. Mami don kanta ta ture Futuha ta juya, har za ta fice ta dawo ta nuna
ta da yatsa.
"Na ba ki mintuna uku ki gaggauta goge account dinki
kaf na social media da kike raye-rayen banza, wallahi kika bar ko guda daya ban
yafemaki ba. Shashasha kawai!"
Tana kai wa nan ta fice daga dakin har tana bangazar Dawud.
Jikin Humaira a sanyaye ta kalli Dawud, kamar jira yake kuwa ya watsa mata
banzan kallo.
"Algunguma,
ficemin daga daki za mu yi magana da yar uwata."
Kamar ta ce mishi ai Abba ya hana su shigowa dakin sai dai
ta hadiye ta fice sum-sum zuwa falon da babu kowa ta zauna jugum. Yau ba ta je
gidan Anti Laila ba sakamakon rasuwar da
aka yiwa Anti Lailar a can dangin mijinta. Tana nan zaune ta ji muryar Abba a
bangarensa yana tashi har zuwa cikin falon, faΙa yake kamar zai ari baki.
Mamaki ya kama ta, Abban bai fita kasuwa ba ko kuwa dawowa ya yi? Yanzun tare
suke tafiya da su Yassar har Dawud wanda shi yau din bai jw ba sanadin ciwon
kai da ya addabe shi Abban ya ce ya zauna, ya ce musu sam ba ya son zaman
banza.
Humaira ta mike tsaye kirjinta na bugawa da sauri. Ta dai
tsinkayi Abban na cewa "Cire ta zan
yi daga makarantar! Itama ta fiddo miji na aura mata ko kuma na aurar da
ita ga koma wane ne don wallahi ni dai Isuhu ba za ta yi sanadin zubewar
mutuncina ba a garinnan!'
Gaba daya jikin Humaira ya hau rawa, ko ba a faΙa ba ta sani akan Futuha ake
tashin hankalin nan. To me ta aikata mai muni har haka da maganar ta yi zafi?
Tana nan tsaye Yassar ya shigo falon bai ko kalle ta ba ya yi hanyar dakinsu,
shi ma Dawud na ciki. Ba ta motsa ba kuma sai ga yan makaranta sun dawo.
Hankalinta ya dan kwanta ganin Raihana da Ummita. Ta karasa da sauri.
"Ku gidannan fa ba lafiya. Kin sani ne?"
Ta jefawa Raihana tambaya ganin yanda hawaye suka wanke
fuskarta. Jikinta ya kara yin la'asar. Raihanar ce ta ba ta labarin abin da aka
yiwa Futuhar, dafe kai Humaira ta yi gami da ambaton sunan Allah.
"TirΖashi!" Abin da kawai ta ce a baki kenan. Dama
tun sadda Futuha ta soma yayin Ιora bidiyo Tiktok ta so ace ta mata magana amma
ta sani ba za ta ji komai ba. Watakila ma ta kira ta da mai hassada kamar yanda
ta kira Tasleem sadda ta yi yunΖurin hana ta Ιorawa. To na kusa ma an mishi
wannan ikrarin ina kuma ga ita da suke mata kallon bare a cikinsu?
Yinin ranar dai gidan ya kasance babu dadi, Abba ya yiwa
Futuha kaca-kaca ya kuma rantse ya dakatar da karatunta har sai idan ta samu
miji ta yi aure. Ya ba ta lokaci kankani akan ta fitar da daya cikin masoyanta
a haΙa bikin da na yar uwarta. Idan kuwa ta Ζi shi da kansa zai nema mata
abokin rayuwa.
Tasleem haka ita ma ta dawo daga asibiti ta iske wannan abin
wanda tuni tana da labarin komai. Futuha ranar kamar an aikomata saΖon mutuwa
haka ta wuni babu ci babu sha, Mami ta ce a kyale ta. Ganin ba ta da mafita ya
sanya ta komawa Ιangaren Anna inda anan ne ta samu sassauci domin Anna goyamata
baya ta yi, ta ce Mamin su yi mata uzurin kuruciya. Ta dai lallaΙa ta kwantar
mata da hankali.
***
A sati biyun da Abba
ya Ιibarwa Futuha don ta fiddo mijin aure, a wannan satin kafin su cika gaba
daya ta rame ta zama mai wani irin sanyi, yan uwan Abba babu wanda ya goyi
bayanta balle ya lallaΙa mata shi. Ganin haka Mami ta tashi takanas ta je ga
aminiyarta Hajiya Lubna ko za ta amince Khalil Ιanta ya auri Futuha
su rufawa junansu asiri. Amma ina, Hajiya Lubna ta nunamata
ita gogaggiyar yar boko ce ta biyo mata ta kissa ta nunamata ta amince, amma
bayan kwana biyu ta kira ta tace Baban Khalil ya ce shi kam ya riga ya gama
magana da abokinsa akan Ζ΄arsa da yake son Khalil din ya aura. Ta kwantar da
Mamin hankali akan Futuha fa kyakkyawa ce son kowa Ζin wanda ya rasa, ta
kwantar da hankalinta komai zai tafi daidai.
Aikuwa cikin ikon Allah dai ga wani matashin Ιan chanji
Alhaji Yakubu ya zo takanas ya samu Abba akan yana son aurenta. Mutumin ya jima
yana ganin fuskar Futuha a Tiktok, kasancewarsa Ιan duniya, yana son mace mai
irin wayewarta ya kuma jima yana bibiyarta akan ta amince ya aure ta, tana
wulaΖatanshi. Tashi guda da ya ga abin da Sa'a ta yi mata ya ga dama ta samu da
zai yi wuf da ita. Yana da mata Ιaya da yara uku, ya kuma tabbatarwa Abba koda
Futuha ba ta son zama da matansa shi Ιin zai nema mata wani muhallin daban
cikin waΙanda ya mallaka. Abba ya yaba da salon nutsuwa da ladabin da ya zo
mishi da ita don haka ya ce ya je nan da kwanaki uku ya turo iyayensa. Wannan
lamarin ya yiwa Yakubu daΙi sosai. Ya yi ta godiya.
Bayan tafiyarsa Abba ya yiwa Mami zancen, ta yi murna da
hakan a fili musamman ganin yana da rufin asiri. Abba ya san shi don Alhaji
Yakubu ba Ιoyayye ba ne, yaro ne abokin tafiyar manya. Yana da kuΙi sosai
sannan akwai shi da kyauta. Ko kusa abin hannunsa bai rufe mishi idanu ba. Ya
samu kyakkyawar shaida wajen jama'a da suka san shi a waje, a halayyarsa kuwa
na baΙini wannan daga shi sai Mahaliccinsa sai kuwa wadanda ya buΙamusu suka
sani.
Futuha fashewa ta yi da kuka sadda Abba ya yi mata zancen.
"Wallahi Abba bana sonsa, mutumin yana da son mata
kuma..."
Wurgin da Abba ya kai mata da carbin dake gefensa ya sanya
ta saurin yin gum da bakinta.
"Rufemin baki nace! Ke har kina da fuskar da za'a gani
a aureki da ita, ban da ma shi so ba ruwansa, mutum mai mutunci da Ζima irin
Yakubu mai zai yi da Ζ΄ar rawa? Macen da ba ta killace jikinta ba ta sake shi
ko'ina yana yawo ana kallonta? Toh bari ki ji, muddin ni dai mahaifinki ina
raye, ba ki da miji sai Yakubu. Na kuma ba shi damar turo magabatansa nan da
kwanaki uku, karatu idan ya amince maki ki cigaba wannan shi ya ga zai iya,
nidai ubanki ba da yawuna ba saboda ni yanzu tsoro kike ba ni, nema kike ki fi
karfinmu. Wannan wayewar ta banza kuma da kika Ιaukarwa kanki, ki je can ki
Ζarata da ita, Allah ya shiryeki idan ke mai ganewa ce. Tashi ki fice ki ban
wuri, saura ki je ki kai Ζarata tun da ban isa da ke ba."
Yana nufin kai Ζara wurin surukarsa Anna kamar yanda ta yi a
farko da ya yi batun auren har sai da Annar ta tako sashinsa da zummar lallaΙashi
ya janye. Cike kuma da ba ta girma ya ce ta yi hakuri amma ba zai zuba idanu
tarbiyyar yaransa su lalace ba. Ganin ba ta taΙa neman alfarma a wurinsa bai yi
ba sai wannan ne ya sanya ta kama mutuncinta ta yi shiru da baki.
***
Su Humaira na Ιaki sai ganinta suka yi ta shigo tana aikin
da ta saba kullum, wato aikin kuka. Humaira kukan yanzu kam ko a jikinta, ai
tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka, ta lura hatta Tasleem itama abin ya
bar sosa ranta, kowa ya fice a harkarta ya gaji da rarrashi. Tasleem dai waya
take amsawa da Hamza, ganin ihun kukan Futuha ya cika dakin kawai sai ta ja
guntun tsaki ta fice. Su din ma hirarsu ta tsaya, kowa ya shiga danna waya, su
kansu Abba ya ja musu kunne sosai ya kuma rantse duk wacce a cikinsu ta yi irin
gangancin Futuha ba zai duba komai ba zai aurar da su. Wannan ya sa bakinsu ya
mutu murus.
Humaira ta bude saΖon
da ya faΙo wayarta a lokacin. Ta sani, shi kadai ne zai yi mata saΖo don haka
ta buΙe.
_"Ko kinsan mai
hakuri ba ya taΙa karo da rashin nasara a rayuwarsa? Ki sani ni Ιin masoyi ne a
gareki, ba kuma hakan zai sauya komai ba. Ma'ana, koda ace zamu shekara kina
wahalar da zuciyata, Humaira ki sani, Fadeel bai fara sonki domin ya daina ba.
Muddin rai ba zan fasa neman soyayyarki ba."_
Ta karanta kusan sau uku, ta rasa dalilin da yasa ba zai taΙa
turo kata saΖo ta karanta sau Ιaya ba, kuma ko kadan ba ta iya goge saΖonninsa.
Abin da yake ba ta mamaki shi ne, ta ga yana hawa whatapp amma ko sau daya bai
taΙa yunkurin yi mata magana ta can ba. Kira ma da ya ga ba ta Ιagawa ya bari.
Sai dai akwai lambar da take zargin ko shi ke kiranta da shi. Za a kira ta Ιaga
amma ba za a ce komai ba sai dai ta yi ta sallama tana sababin anΖi magana
Ζarshe kuma ta ji Ιif an katse kiran. Wannan abu na ba ta mamaki, tana kuma
zargin Fadeel ne. Ta yi shiru tana so ta hasaso dalilin wannan Ζiyayya da ta ke
yiwa Fadeel amma duk iyakar tunaninta ta kasa, karshe ta ja guntun tsaki. Ta
bar shi akan kawai ita ba ta kaunar soyayya, ba ta kaunar kowace mu'amala da za
ta haΙata da namiji. Da wannan ta watsar da tunaninta.
***
BAYAN SATI UKU...
Garin aka tashi da
shirye-shiryen shiga wata mai alfarma wato Ramadan, wanda ake kyautata zaton
ganin wata a ranar ko washegari hakan yasa Mami suka yi dogon list na cefane
ita da Humaira. Mamin ta dube ta bayan sun kammala tana murmushi.
"Wannan azumin
a daΙinmu, girkinki zamu ci. Kin ga kina yi idan kin shirya komai sai ki yi
hoto, Raihana ta buΙemaki account a instagram kina Ιorawa da sunan tallah, idan
Allah ya taimaka zuwa sallah sai mu samu odar girkin sallah ko su samosa da
sauransu. Da kaΙan-kaΙan kuma ki ji an soma neman ki yi na biki. Ina mai
tabbatar maki da wannan iya girkin naki za ki samu alheri mai yawa da zai yi
maki amfani har na kusa da ke."
Humaira cike da jin dadi ta hau murmushinta mai bayyana
wushiryarta ya kara fiddo da usulin kyanta. Ta ma kasa magana don murna. Mami ta yi dariya.
"Allah ya kyauta, wannan dariyar duk ta murna ce? Tashi
dai maza ki je kar yamma ta kawo kai. Kinga siyayyar da yawa."
"Toh Mami." Ta mike ta gyara zaman mayafin doguwar
abayar dake jikinta ruwan madara mai dark brown din mayafi. Ζafarta sanye da
safe ba ka ganin komai sai tafin hannunta sai kuwa fuskarta da ta shafa hoda ta
zizira kwalli. Ta yi kyau tsaf duk kuwa da cewa ba kwalliya ta yi ba. Irin
matan nan ne wadanda ko ba kwalliya su na kyau. Har ta fice a Ιakin Mamin na
bin ta da kallo tana murmushin da ta ba kanta sanin ma'anarsa.
Ta yi tafiya daga gidan zuwa titi na Ιan mintuna sannan ta
fito babban titi. Garin akwai rana sosai duk kuwa da cewar an yi sallar azahar
amma hakan bai sa ya Ιan yi sanyi ba. Dakyar ta samu abin hawa ta shiga. Sun yi
tafiya mai Ιan tazara sun tsaya a daidai junction din sabon titi wayarta ta Ιau
Ζara. Ta ji gabanta ya fadi don tsoro, Ummita ta ce mata ana satar waya a Ιan
sahu wannan yasa kodayaushe idan za ta fita ta ke sanya ta a vibration amma yau
sauri ya mantar da ita. Ta Ιan kalli mata biyun da ke gefenta sai ta ga ba su
yi mata kama da Ιarayi ba don haka ta ciro ta da sauri, ganin sabuwar lamba ya
sa ta Ιagawa da sallama. Madadin ta ji shiru an yi kamar yanda aka saba yi
mata, sai ta ji wannan karon an amsa. Duk da ta Ιau muryar hakan bai sa ta
tambayar "Wa ke magana." ba.
"Wallahi ina
sonki."
Ya furta cike da kasala, abinda bai taΙa faruwa ne ba gareta
ta afku a sannan. Ji ta yi tsikar jikinta ya tashi, ta ji lebbanta sun mata
nauyi ta kasa buΙe baki balle ta rufe shi da faΙan da ta saba. Sai kawai ta
zame wayar daga kunnenta ta katse kiran. Daidai lokacin da aka ba su hannu,
juyawar da za ta yi suka yi ido hudu da shi, kallonta ya ke bilhakki har sai da
na bayansa suka cikamasa kunne da hon, ta yi saurin kauda kanta. Kallon ya dawo
mata da sabuwar tsanarsa, ta ji ranta ya Ιaci, ta kuma rasa dalili. Ba ta kara
juyawa ba har suka yi mishi nisa, ba ta kuma san inda shi ya yi ba. Ζarar
shigowar saΖo wayarta ya sanya ta buΙewa.
_"Kin min kyau.
Ina roΖon Allah ya nunamin ranar da Fadeel zai mulki zuciyarki gaba Ιaya. Ya
zame maki haske maganin kowane duhu. Ameen."_
Ta yi saurin maimaitawa sau Ιaya ta jefa cikin jakarta. Ana
zuwa kasuwar rimi ta sauka bayan ta fidda facemask dinta a jaka ta rufe hanci
da baki. Haka ta dinga kutsawa ta kammala siyayyar Mami, ba ita ta bar
kasuwarnan ba sai yamma lis duk ta jiga ta. Washegari ma haka ta kara tashi ta
fita zuwa haΙo kayan kwalam na yin Snacks iri-iri. Hatta da kayayyakin haΙin
salad sai da ta siyo. Wannan karon dai Abba ya saki bakin aljihu domin shi dai
idan har watan azumi ne yakan yi bakin kokarinsa wajen wadata gidansa, hakanan
da sallah. Ya kuma ce lallai lallai su Tasleem da Futuha su dinga shiga kicin
su koyi girki wajen Humaira. Rana Ιaya idan suka yi fashi, za su yi karo da
fushinsa.
***
Murja ce durkushe gaban Alhaji, ya kalleta dakyau jin ta
kasa magana. Da murmushi dauke a saman fuskarsa ya ce.
"Kin yi shiru
Murjanatu, kiyi magana."
Ta ga dai shirunta zai sa ta cuci kanta don haka ta muskuta
ta soma cewa.
"Dama Yaya
Fadeel nake so a auramin."
Jin haka kan Alhaji
ya Ιaure, ya yi sakato yana kallonta.
"Shi Fadeel din ya sani?"
Ta girgiza kai tana kara sunne wa kamar mai jin kunya.
Alhaji ya yi shiru sai kuma ya ce.
"Shikenan, ni dai ba na yiwa yarana dole balle kuma
namiji. Zamu yi maganar da Fadeel duk amsar da ya bayar za ki ji daga
Antinki."
Ji ta yi kamar Alhajin ya harba mata mashi a Ζahon zuciya,
da irin wannan amsar ai gwara kawai ya ce mata aa kansa tsaye. Abu ne da ya
sani kamar yanda ta sani, zai wahala Fadeel ya amince da shi, ta yi zaton yanda
Alhajin ke yabawa da nutsuwarta zai ce ya amince ya zaΙawa Fadeel din ita
matsayin matarsa. Haka ta mike ta fice gwuiwa a sake. Bayan fitarta Alhaji ya
yi shiru, ta ina zai soma Ιata ran Ιannasa wanda a baya ya sha baΖar wuya a
dalilinsa da mahaifiyar Fu'ad? Ya musguna mishi, bai duba maraicinsa ba na
rashin uwa ya yi watsi da shi. Karshe don kansa da ya gaji bayan ya yi hankali
ya fice ya koma dangin mahaifiyarsa a can Ζasar Kamaru. Sai kuma bayan da ya
kwashe dogon shekaru har kusan biyar ya dawo yanzun kuma ya hargitsa shi komai
ya Ζara hargitse mai? Yaransa biyar kacal a duniya, Fadeel ne babba sai Fu'ad
sai kuwa Ζanwar Fadeel uwa Ιaya uba Ιaya Hannatu dake aure a can Adamawa, sai
yaran Anti Amarya biyu, Khadija da Abdulmaleek. Shi hakanan Allah ya yi shi ba
mai yawan haihuwa ba, matansa babu me yin tsarin iyali.
A Ζarshe dai ya yanke zai mishi maganar auren don shi
kansa yana damuwa kwarai akan zaman yaran haka(wato Ibb da Fadeel) ba tare da
iyali ba. Har ga Ζaninsu Fu'ad ya yi auren ya bar su.
***
Fadeel ya nutsu a gaban mahaifinsa, bai katse shi ba
har ya kai aya. Sai a lokacin ya yi magana.
"Na ji bayananka Alhaji, ina neman addu'arka
musamman a wannan wata mai alfarma da za mu shiga akan neman zaΙin Allah. Sai
dai kuma ba na kaunar Murja, ba na sonta matsayin matar aure. Don Allah abar
zancenta."
Jinjina kai Alhaji ya yi, ya Ιan murmusa kaΙan.
"Shikenan, Allah ya sa hakan ya fi alheri. In sha
Allahu zan tayaku kai da Ιan uwanka. Ya kamata ku maida hankali."
Fadeel ya amsa a ladabce. Daga nan suka rufe wannan babin
suka cigaba da tattaunawa akan abubuwan alheri na sadaka da neman lada da
Alhaji ke yi duk shekara idan watan azumi ya kama. Kamar yin kunu da abincin
sadaka, kyautar butoci, ruwa, dabino da ma sauransu a masallatai., daukar
nauyin tafsir, sai kuwa idan sallah ta matso ya yiwa Ζ΄an uwansa marasa Ζarfi da
marayu da dama sutura. Da wannan suka rufe babin Murja da ma batun aure. Anti
Amarya dake laΙe a bayan labulen Ιakin Alhaji, ta ji ciwon cewa da Fadeel ya yi
ba ya son Ζanwarta. Ta yi Ζwafa, ai idan ya san wata bai san wata ba.
***
A daren ranar Lahadi gaba Ιaya garin aka dau murnar ganin
watan Ramadan. Lokacin Sahur gaba Ιaya gidan suka tashi aka yi idan ka cire
Tasleem wacce ba ta da sallah.
Lokacin shan ruwa na kawo kai, Humaira da Ummita har
Raihana ana kicin ana faman kai da kawowa, Tasleem ba ta shiga ba don langaΙewa
ta yi wai mararta na ciwo. Ita kuwa Futuha tana tsaye kawai tana
yatsine-yatsine da gwatsale wani abun idan Humaira ta yi wai ba haka ake yi ba.
Ita dai ba ta tanka mata ba albarkacin watan da suke ciki na ibada. Sai da suka
kammala komai sannan suka jera a tsakar falon bayan shimfiΙa Ζatuwar ledar cin
abinci. Na Abba kuwa can Ιangarensa suka kai aka shirya komai. Itama Anna,
Raihana ta kai mata komai ta bar ta tare da su Muhsin don a duniya Anna ba ta
fiye son zuwa falon Mamin ba sai da kwakkwarar dalili.
Sai a sannan Tasleem ta shiga kicin din ta Ιibi
abinci ta dawo falon tana ci ta a yatsine fuska wai gishiri ya yi yawa. Ba ta
ko jin nauyin yan uwanta maza dake zaune a falon su na taΙa hira. Haka aka sha
ruwa aka yi zaman cin abinci bayan kowa ya yi sallah. Mazan suka dinga santin
girkin amma da zarar sun yi ido da Humaira su watsa mata harara idan ka cire
Ζasim wanda tun wata rana da ya shiga Ιakin Mami zai Ιau kuΙi ta gan shi kuma
ta rufamasa asiri ba ta faΙawa kowa ba, tun a ranar ya soma ganin ta da Ζima a
idanunsa. Ya ke kuma jin kunyarta. Yassar kuwa faΙi yake ai ba basirarta ba ce,
koyamata aka yi. Futuha ta ja tsaki.
"Wai kai kana wani zance, ina abin yake? Ni ba
abin da ya kara Ιatan rai wai sai da Abba ya ce wani mu shiga kicin mu koyi
girki wajenta. Don Allah ku ji wani abu."
Dariya suka yi idan ka cire Ζasim dake faman cin sandwich da
ya ji kaza da su cheese yana santi.
"So ya ke ki je ki yiwa Alhaji Yakubu kar a ji kunya
mana."
Jin an ambaci Alhaji Yakubu nan da nan ta Ιaure fuska. A
duniya yanzu babu wanda ta tsana irinsa, mutum dai kamar maye. Abu daya da ta
sani shi ne, daga maganar zuwa kamawar watan da suke ciki na azumi ya yi mata Ιarin
kuΙi sama da dubu Ιari, wannan kaΙai shi ne ya burgeta musamman ganin cewa
Tasleem ba ta samu hakan ba. Rabu dai da Hamza akwai kulawa a baki amma
babu ko asi da ya taΙa kawomata. Wannan abu na yiwa Tasleem ciwo kuma yana
fasawa Futuha kai, tana son ta ga ba ta son mutum yana bibiyarta kamar jela.
"Kar ka sa na tashi, har wani tsami na ji abincin ya
soma yimin a baki."
Yassar da Dawud suka kwashe da dariya. Tasleem ta yamutse
fuska ta ce.
"Gulma, a bakya so kike kwace Ζ΄an chanjinsa. Fuska
biyu."
Futuha ta dire fork din hannunta da ta ke cin haΙin salad da
shi, tun ba ta kai ga haΙiyar wanda ta ke tauna ba ta soma balbaleta da masifa.
"An kwata Ιin, ina ce albarkacin kaza dai Ζadangare ke
shan ruwan kasko? Ko kin manta abin da Mami ta ce akan amfanin kudin?"
Tasleem ta hadiye zancenta, ta tuna Mamin cewa ta yi Futuhar
ta saki jiki da Alhajin ta dinga nuna masa kulawar koda iyaka baki ne, muddin
dai zai bayar da kuΙin ba za a ji kunya a auren ba tunda ba su da tabbacin
samun yanda ake so daga wajen Abba. Wato na siyayyar kayan Ιaki da sauransu.
Maganar Futuha ta katse ta.
"Kuma ko banza gwara Yakubu tun daga nan an san zai iya
riΖe mata biyu, wani kuwa da ko Ιayar ma ya kasa nunawa zai iya sai afkin waya
da ΖalΖalar turanci kamar tsatson sarauniyar Ingila." Suka kwashe da
dariya. Ran Tasleem ta kai kololuwa a Ιaci, su Humaira na zaune su dai su na
shan ruwa abin su daga gefe suna kallon ikon Allah. Raihana ce ta tofa.
"Kai Adda Futuha, ramuwar gayya fa akwai zafi kar ki
kai Adda Tasleem bango."
Aikuwa tana cewa haka kamar ta kara zuga Tasleem sai kuwa ta
yi caraf ta ba ta amsa.
"Kyale ta Raihana, ai mugun abu ya Ζare a gindinta
tunda ko ba komai nidai auren soyayya zan yi, Hamza gani ya yi yana so a
mutunce. Wata kuwa sai bayan an jefe ta da kalmar karuwanci, Ζ΄ar rawar Tiktok
sannan ta yi na'am da Alhaji mai zubin moΙa."
Lallai, baki idan ya san me zai faΙi bai san me za a mayar
masa ba. Aikuwa Futuha ta yi kukan kura har ta na cilli da bowl din salad dake
saman cinyarta zuwa Ζasa, ta yi kan Tasleem da kokawa. Itama Tasleem kasancewar
a wuya ta ke kawai sai ta biye mata suka hau jibgar juna. Dakyar Yassar ya
shiga tsakaninsu gudun kar Abba ya ji.
Tasleem na huci ta ce.
"Ni kuΙi bai dameni ba tunda zan auri wanda yake sona
nake sonsa. Arzikin dai ai na Allah ne, kuma ko makaho ya shafa ya san Hamza ba
talaka ba ne. Alhamdulillah ba a taΙa yimin wannan mugun Ζazafin na
karuwanci ba."
"Shegiya! Ni kike kira karuwa, ai gwara ni sharri ne,
ke kuwa sau nawa kina yiwa Mami sata? Ko ranar da aka yi na Humaira, ina ce ke
ce kika kawo shawarar a yi mata wannan sharrin don ki wanke kanki. Ke ce kika Ιauki
kuΙaΙen, ganin Yassar ya kama ki sai aka shiryawa Humaira tuggu don kar Mami ta
zarge mu."
Humaira da ke shirin kai kofin kunu bakinta ta yi saurin
ajiyewa, ashe ma Ιarayin biyu ne? Ba ma wannan kadai ba sai ganin yau dai Allah
ya karΙi addu'arta gaskiya ta yi halinta. Tasleem gaba Ιaya ta yi wuri-wuri da
idanu, ko kaΙan ba ta zaci Futuhar za ta yi mata wannan tonon sililin ba.
Yassar ya dakamusu tsawa amma kasancewar girma ya faΙi ko a jikinsu, sai dai
tsawar farko daga Abba ya sanya gaba daya suka yi tsit. Ashe yana tsaye a bakin
Ζofar falon tun sadda suka soma kokawa, Mami na biye da shi a baya. Gaba Ιaya
hankalinta a tashe, wato dai ya allura ta tono garma? Ba wannan ba ma, babu
uwar da za ta so ganin yaranta kansu a rabe. Gaba daya falon ya yi tsit su
Tasleem sai rarraba idanu ake.
Ya shigo tsakiyar falon ya wanke su ganin ba su duba girman
watan da ake ciki ba na ibada su na yi mishi faΙa a falo. Daga nan ya nemi
sanin abin da ya faru da Humaira a baya, nan fa Raihana kamar wacce ake tsikara
ta ba shi labari. Humaira kanta a Ζasa tana hawayen farin ciki, wato da Allah
ya tashi wanke ta sai ya sa Abba da kansa ya ji zancen ba iyaka Mami ba. A
ranar su Yassar da Futuha sun ga tashin hankalin Abba, ya kuma ci alwashin saΙawa
duk wanda ya Ζara jarraba musgunawa Humaira. Hatta da Mami mai kokari akan
Humaira a ranar har da ita ya haΙa ya ce ai laifinta ne da ba ta tsawatar musu
shiyasa suka samu sake. Haka Abba ya yi faΙan da ba su zata ba har Humairar
daga nan ya fice daga falon. Mami ta bi yaran da kallo sai kawai ta juya ta bi
bayan mijinta. Humaira ta mike ta kalle su fuskarta dauke da murmushi ta juya
zuwa Ιaki. Ranar jin ta take ranta babu ko Ιigon bakin ciki sai dai ba ta
ji dadin dorawa Mami laifin su Yassar da Abba ya yi ba. Amma ta yi mamakin
Abban, a baya tana tunanin ko sonta ne ya daina, ko ya manta ma da ita a
lissafin Ζ΄an gidan sai kuma abin da ya yi yau Ιin ta fahimci tana nan daram a
zuciyarsa kawai dai ba shi da lokacin kansa balle na hira saboda yanayin
kasuwa. BanΙaki ta shige ta Ιora alwala ta dawo ta zura hijabinta ta
shiga lazimi. Ta na nan zaune ta yi shiru, wani lokaci can take tunowa ita da
Dada musamman a wata irin na azumi yanda suke zama bayan shan ruwa a yi hira
kafin lokacin sallar isha'i.
Ζarar wayarta ya katse mata tunani, ta sa hannu ta Ιauka.
Fadeel, shi ne sunan da ya bayyana saman screen din, haka Raihana ta
adana mata lambar ba da son rai ba. Albarkacin watan da suke ciki ya ci ta Ιaga
da sallama. Ya amsa daga can ransa fari sol.
"Ina fatan kin sha ruwa lafiya?"
"Lafiya kalau." Ta amsa a taΖaice. Shiru ya Ιan
biyo baya, ya rasa me zai ce yana gudun ya yi furucin da zai sa ta katse wayar
gaba Ιaya. Ya kasa hakuri balle ya danne don haka ya ce.
"Sai yaushe Humaira? Sai yaushe za ki samarwa wannan Ιan
marayan gurbi a zuciyarki? Ba zan gaji da roΖo ba, ki ba ni dama Humaira. Wai
kin san so kuwa?"
Nan da nan ta ji ya har ta soma harzuΖa a sanadin kalmar so
da ya ambata, cike da gatse ta ce.
"Sai nan da shekara."
"Kin yi alΖawari nan da shekarar za ki amince ki
yarjemin da batun aure?"
Ta dauki maganar a zancen banza, ta sani babu wahalallen da
zai yi dakon shekara ya auri budurwar da ba ta ko son zancen auren balle auren.
Don haka babu dogon tunani ta amsa.
"Eh, na yi muddin za ka rabu da kirana ka bar
takuramin."
Shiru na wasu lokutan sai kuma ya sauke nannauyan ajiyar
zuciya.
"Za ki same ni da bin umarninki, amma kiyi hakuri koda
saΖo na dinga aikomaki ta waya. Ke kuma ki daure ko da sallama ki amsamin domin
na san kina sane da ni."
"Naji."
Ta amsa gabanta na faΙuwa ba tare da ta san dalili ba, ta ji
zufa ta keto mata. Tsanarsa ta ke ji yayinda a wani gefe can a Ζasan ranta ta
ke jin wani abu da ba ta tantance ba.
"Na bar ki lafiya, ki yi hakuri na adana dukkan
wayoyinmu, abin nufi nayi recording tun daga farkon wayarmu har na yau. Hakan
kan Ιebemin kewa wasu lokutan idan son jin muryarki ya ci Ζarfin kwakwalwata.
Ki dage da addu'a a wannan wata mai alfarma. Ina roΖon Allah ya yi maki zaΙin
abokin rayuwa nagari, koda ba Fadeel ba."
Yana kaiwa nan bai jira cewarta ba ya katse kiran. Ta yi
Ζuri tana duban wayar, hakan na nufin wayar Ζarshe ce tsakaninsu sai nan da
shekara? Ta taΙe baki, ta sani cewa ta ba shi aiki mai wahala. Kuma ba zai ma
iya shekara yana wahala a kanta ba. Watakila ma kafin sannan ya yi aurensa. Ta
watsar da tunani ta yi jifa da wayar ta mike jin an soma kiraye-kirayen sallar
isha'i.
***
Anna ce ke yiwa Mami faΙa kamar ta ari baki.
"Kin bari miji ya rainaki ya raina uwarki, dama tun
akan batun auren Futuha na san cewa Isuhu ya sauya daga yanda na san shi. Wato
yanzun ya ci moriyar ganga ya yar da koren, ke yanzu ban da ke sakara ce
wawiya, kina tunanin har wani karfin iko kike da shi a wajensa? Mutumin da ya
dubi tsabar idon mahaifiyarki ya ce ba zai janye kudurinsa na aurar da Futuha
ba? Toh wallahi Maryama ki shiga taitayinki tun kafin dare ya yi maki, mazan
nan dai babu amana bar ganin wai girma ya soma kama shi, don ya dankaro maki
kishiya Ζ΄ar zamani ba komai ba ne. Tun wuri ki Ζwatarwa yaranki Ζ΄anci a wajen
mahaifinsu, ki murje idanunki dakyau ki daina bari yana wulaΖanta min jikokina
akan wasu bare can. Ban da ma mutum mai shegen mantuwa, Isuhu ko kare ne ya
fito daga gidan su Fatima zai kalla da daraja? Matar da ta nunawa duniya cewa
ta tsane shi har kwanciya ciwo take akan sai ya sauwaΖe mata ta koma garinsu?
Mts, Allah ya wadaran naka ya lalace."
Har Anna ta kai aya ita dai Mami ba ta ce komai ba banda
huci da take furzarwa, daga ita sai zuciyarta ta bar wa sanin abin da take
tunani. Dakyar ta taushi zuciyar ta soma magana bayan sakin ajiyar zuciya mai
nauyi.
"Anna ki yi hakuri, babu amfanin mayar da hannun agogo
baya tunda mai afkuwa ya riga da ya afku. Na ba ki wuΖa da nama akan Ζwatarwa
jikokinki Ζ΄anci, ki yi abin da kika ga ya dace. Sai dai ki sani, ni Maryam ba
da yawuna ba saboda daidai gwargwado yarannan su na kyautatamin, ba ni na haife
su ba amma su na bi na sau da Ζafa fiye da ma yaran da na haifa a cikina. Kiyi
hakuri idan maganata ta maki zafi."
Anna ta wurga mata harara.
"Au haka kika ce ko? Toh shikenan, ni zan san abin yi a
kai kamar yanda kika ce. Koda kuwa zan rasa kwabo a asusuna, zan kwatarwa
jikokina Ζ΄ancinsu, sai ya zama Isuhu ba ya ganin kowame Ιa a gabansa idan ba su
ba. Mu zuba ni da ku."
Mami ganin yanda ta Ιauki zafi kawai sai ta miΖe itama ranta
a jagule ta bar mata Ιakin. Da ace Anna ta san damuwar da ke cin ranta da ba ta
soma Ζara mata fetur a kan wutar da ta riga ta soma babbaka a zuciya da
kwakwalwarta ba. Ta ja tsaki ya fi a Ζirga a hanya har ta Ζarasa Ιakinta.
***
Azumi yana ta tafiya har a yau sun kai goma sha shida,
lamarin su Tasleem da Abba ya Ζara tsauri musamman da ya fahimci ba su bi
zancensa ba na shiga kicin. Futuhar da ta soma shiga, tun bayan faΙan da Abban
ya yi ya goyi bayan Humaira sai ba ta Ζara leΖawa ba. Cikin ikon Allah wataran
kwatsam sai ga shi a kicin din abin da Humaira za ta ce tun zuwanta gidan banda
ranar da ya ji fitar gas ya cika gidan ya shigo, ba ta taΙa ganinsa a ciki ba.
Ganin daga ita sai Ladidi da Ummita a kicin din ya shiga bambamin faΙa, a
sannan Raihana na fama da Malaria mai zafi har allurai ta sha. Aikuwa har Ιakin
ya shiga ya titsa Ζeyar Tasleem da Futuha zuwa kicin din yana gargadin Humaira
akan lallai duk sadda ba su shiga ba ta sanar mishi. Tun daga wannan ranar ba
su Ζara fashin shiga ba. Sai dai shigar da rashinsa ba amfani don kusan zama
suke yi kawai ba sa komai.
Abba ya yi siyayyar
kayan sallah, kamar kowace shekara wannan ma da kansa ya yiwa kowa zaΙi idan ka
cire samarin da ya ba kowannensu kudi su siya shadda. Yanmatan kuwa atamfa ce
iri Ιaya sai dai bambancin kala, sai dubu uku da ya ba kowace budurwa a siya
takalmin sallah. Shikenan bai Ζara daga haka ba, su Futuha aka dinga kauΙi
ganin Alhajinta ya kawo mata shadda da atamfa har da leshi masu tsada sai kuwa
dubu ashirin na mayafi da jaka da kuma Ιan kunne. Tasleem kuwa dayake ta soma
shaΖa sai ta budewa Hamza wuta akan ko kyautar biyar bai taΙa ratsawa
tsakaninsu ba. Ranar shi kansa ya yi mamaki da ta iya karya bille ta tambaye
shi kuΙi, aikuwa ya ce ta turo acc no, take ya yi mata transfer dubu goma sha
biyar. Tsabar rainin da ta yiwa kyautar ko faΙawa su Mami ba ta yi ba sai dai
sun mata amfani ta siya abin da take so. Su Humaira kuwa Mami da kanta ta kara
musu dinki, leshi mai kyau na Ιankwarai ta siya musu su uku kala Ιaya. Ana
saura kwana biyar sallah sai ga Anti Jannat a gidan. Zuwanta ya yiwa su Futuha
daΙi ko ba komai mace ce mai sakin bakin aljihu ga fankama. Burinta ta buΙa ko
don ta nunawa Mami ita fa mijinta mai bayarwa ne, yana da kyauta sosai. Daidai
da Anna ta fi ji da ita, abinda ya hana ta zama wajen Jannat din bai wuce na
ganin surukanta sun nuna ba su kaunar hakan ba. A farko ta gwada amma aka so
samun matsala, dole ta tattara ta dawo gidan da ta raina, gidan Abba.
Suna zaune a Ιaki
bayan sun kammala gwada dinkunansu na sallah, ya yi musu cif da cif, washegari
kuma sai tafiya kitso da Ζunshi. Sai faman tsokanar Ummita suke yi ganin
saurayinta ya kira tana kashe murya a waya, koda ta ajiye Raihana ta dube ta.
"Wai ni yaushe
za ki ba Ya Sayyadi damar zuwa gidannan?"
Kasancewar zuwa lokacin sun sani ba kowa Ummitan ke soyayya
da shi ba face Ya Sayyadinsu na makaranta hakan yasa suka samu abin tsokanarta.
Ashe wai dama yawan tashinta da yake yi ta biya musu karatu mai dalili ne.
Ummita ta Ιan harareta.
"Ke me ya hana ki ba Jafar daman zuwa gida? Ni ai mun
kashe magana da shi, na ce ya bari sai nan da shekaru biyu ko ma ince Ιaya da
rabi idan mun yi candy, tunda yanzu muna
SS2."
"Kai Ummita, shekara Ιaya da rabi fa? Gaskiya sun yi
yawa ina laifin ma shekara Ιaya?" FaΙin Humaira dake tsaye tana maida
kayanta sif. Raihana ta tari numfashinta da sauri ta ce.
"Wai ke ce mai yiwa wata faΙan shekaru sun yi yawa?
Allah ya ba Fadeel hakuri. Wallahi idan na tuna abinda kika yi masa sai na ji
kamar na yi maki dukan tsiya."
Ummita ma kwafa ta yi cikin kunar rai ta ce.
"Bar ta kawai Raihana, nima ba ki ji raina ba. Kuma
babu kunya ba tsoron Allah har faΙamana take yi ya hakura sai nan da shekara.
Shi marar zuciyar ina ne da zai biyemaki ya yi zaman jiranki? Ai tana sane,
kora da hali ne kawai ta yi mishi. Ba fata nake maki ba, amma wallahi kafin ki
samu kamar Fadeel a maza sai dai tsananin rabo."
Humaira ta taΙe baki gami da jan guntun tsaki.
"Kanku ake ji, ni na faΙamaku ina so nayi auren ne?
Auren ku yake burgewa ba ni ba. Sai me? Idan ba auren zan fasa rayuwata yanda
ya kamata ne? Ya yi ma gangancin zaman jirana ya gani idan haΖansa zai cimma
ruwa. Ya Ζare rayuwarsa a tuzuru."
"Allah ya kiyaye wallahi, bakinki ya sari Ιanyen kashi.
Fadeel ya wuce nan, kuma ina masa fatan alheri, ya samu haΙaΙΙiyar da ta fi ki
komai Ζ΄ar kwalisa in sha Allahu."
Cewar Raihana.
Haka kawai sai ta ji zafi a ranta, ta ji tana son yin kukan
da ta rasa dalili, kawai sai ta fashe da kukan ba tare da ta yi shawara da
zuciyarta ba. Raihana ta dubi Ummita kafin su dube ta jiki a sanyaye. Tun tana
kukan su na ganin kamar wasa su na rarrashinta, har dai suka ga kamar kukan ba
na lafiya ba ne suka fita da sauri suka yiwa Mami magana. Kai abin tsoro
Humaira duk iyakar rarrashin Mami ba ta yi shiru ba, hakanan harafi Ιaya ya
kasa fita a bakinta. Mami ta juya garesu.
"Meyafaru ta soma kukan?" Nan suka ba ta labarin
komai, ta ja hannun Humaira kawai suka fice a Ιakin. Su Raihana za su biyo
bayansu ta dakatar da su, can falo suka tsaya yayinda Mamin ta shige Ιaki da
ita. Sun yi jugum kuma sai ga Mamin ta fito ta dube su ranta a Ιace.
"Don me za ku dinga yi mata batun saurayin da ba ta
so?! Ina gargadinku daga rana irin ta yau koda wasa kada wanda ya kara kuskuren
ko ambaton sunansa balle ya yi mata zancensa. Fadeel ko? Daga yau sunan nan ya
fice a bakinku." Suka ce toh, su ma abin ya tsorata su, sun kuma kara
gaskata zancensu, Humaira na da aljanu musamman da suka ji Mami ta mike tana
fadin wai ta samu bacci idan ta tashi komai zai wuce a ranta. Tabbas zarginsu
ya tabbata gaskiya, aikuwa ga mamaki Humaira sumul ta tashi tamkar babu abin da
ya faru. Yanda ba ta yi zancen ba hakanan su ma ba su kara tada shi ba. Ba ma
kamar Raihana mai shegen tsoron aljanu, Ummita sai dariya take mata ciki-ciki
ganin ko zama kusa da Humairar ta Ιan rage yi a ranar. A gefe guda kuma ta yi
alΖawarin muddin ta je Bichi za ta yiwa mijin yar uwar mahaifiyarta magana akan
lamarin Humaira, yana ba da hayaki da maganin jinnu, in sha Allahu za ta karΙo
mata.
***
*LITTAFIN NAN NA KUΖI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA
TARE DA SHIGA HAKKI BA.*
*5407827015*
*FCMB*
*Farida Abdullahi*
09034973645
Ibb ya mike tsaye yana safa da marwa kafin ya naushi bango a
zuciye ya juya ya nuna Fadeel da yatsa.
"Wai kai wace irin soyayya ce wannan da ba ta da mafaΙi?
Wace irin soyayya ce mai neman kai ka ga halaka?"
Murja wacce ke shirin kwankwasa Ζofar Ιakin don ta miΖa musu
fruitsalad da ta haΙa ta tsaya cak jin abin da ke fitowa daga bakin Ibb,
kirjinta har wani lugude ya ke yi.
Fadeel kuwa jin an danganta soyayyarsa da sunan halaka ya Ιan
Ιago idanu dakyar ya dubi Ibb sanadiyyar ciwon kai da ya wuni da shi ga azumi a
baki. Ibb ya kara jaddada masa furucinsa.
"Yes halaka mana, mutumin da ya amince da zaman jiran
gawon shanu alhalin yana da damarmaki da yawa da ma Ζ΄anmata masu ilimi da aji
da ke rububin ya amince ya aure su ai kuwa ya jefa kansa a halaka tunda wacce
ya ke zaman jiran kora da hali ta yi mishi. Fadeel wake up, ka runtse idanunka
da kyau ka fahimci yarinyar nan kora da hali ta ke maka, ba soyayya ba ce. Ba
ta sonka, a wautarta lokacin da ta Ιibarmaka zai sa ka Ζosa har ka gaji ka
sauya sheΖa amma ba ta san yanda ka mace a kanta ba, ka shirya aikata komai!
Toh ni abin ya ishe ni, zan je na sanar da Alhaji komai a je a nema maka
aurenta."
Fadeel dai ya yi shiru kawai yana cigaba da kurΙar ruwan
shayi don ba su jima da shan ruwa ba. Jin maganar tunkarar Alhaji ya
sanya shi Ιago kai ya daure fuska.
"Ban saka ba Malam, kar ka sake ka aikata wannan
gangancin. Ba za ka taΙa fahimtar ya nake jin Humaira ba, ni dai na yarda ita Ιin
mahaΙi ce ga rayuwata. Kai duk fa son da za ku yimin ba zai kai yanda ni nake
son kaina ba, tun farkon ganina da ita nake addu'ar neman zaΙin Allah amma
daidai da sakan guda ban ji ta sauya a raina ba. Ni dai na sani, ina mata so ba
iyaka wanda nake da tabbacin ko ba ta sona, nawa son ya yi Ζarfi da isar da zai
wadace mu gudanar da kyakkyawar rayuwar aure, na koyar da ita yanda za ta fara
sona. Ballantana kuma ina ji a jikina tana kaunata."
Tsaki Ibb ya ja ya koma ya zauna, tabbas ya ji daΙin dawowar
Ιan uwansa wajensu, amma ya yi danasanin haΙuwar da suka yi da Humaira. A can
Ζasan ransa tausayinsa ne lulluΙe, son maso wani akwai wahala. Don haka sai
kawai ya ja bakinsa bai kara cewa uffan ba ya tsiyayi ruwa mai sanyi a kofi ya
soma kurΙa.
Daga can bakin Ζofa kuwa, Murja tuni tsayuwar ta gagareta,
don haka ta ja Ζafafunta da suka yi mata nauyi ta bar wajen cikin sauri ba tare
da ta miΖa musu abin da ta kawo ba. Dama na gulma ne ta kirkiri aikinsa don
kanta kawai domin ta burge Fadeel, daga abin da ta ji yanzu ta fahimci babu
abin da za ta yi ta burge shi tunda ya makance har haka a san wata banza wacce
take da yaΖinin ba lallai ta fi ta kyawun zubin jiki ba. Kafin ta karasa falon
Anti Amarya idanunta sun yi jage-jage da ruwan hawaye, ta gifta yaran ta shige Ιakin
da kusan yanzun ya zama mallakinta bayan ta ajiye kwanon fruitsalad a falo gami
da ba su umarnin shanyewa idan su na so. Kuka sosai ta fashe da shi, babu
kalamin da yake mata baΖi kamar na jin da ta yi Fadeel na ambaton wata Ιiya
mace da sunan so har yana ikrarin wai yana mata son da ya ishe su rayuwar aure
koda ita ba ta sonsa. Ta nanata sunan a Ζasan zuciya, wato Humaira. Sai ta yi
Ζwafa gami da tsaida kukanta, a fili ta ce.
"Fadeel muddin ina numfashi sai na mallake ka a rayuwa
koda ace hakan na nufin na Ιatar da Humaira a doron Ζasa."
Wannan shi ne alΖawarin da ta Ιaukarwa kanta.
***
A daren da aka yi shelar ganin wata kowa ya tashi da farin
ciki da walwala. Humaira tuni sun sha kitso da Ζunshi abinsu, a wannan daren
wuni ta yi a kicin tare da Ummita su na aiki ita kuwa Raihana tana can falo
tana taimakawa Tasleem jera stones a atamfarta da tela bai samu damar yi ba.
Shirin waina, sinasir da miyar taushe ake yi, tun safe suke aiki inda Humaira
ta yi snacks har kala hudu, samosa, springrolls sai meatpie da cincin. Ko kusa
ba ta huta ba, wata iriyar gajiya ce tattare da ita dukkan gaΙΙanta ciwo suke,
kusan ita kadai da Ladidi ne karfin aikin don Ummita ba ta zauna ba, tana kula
da yaran Anti Jannat, ko mintuna biyar ba ta yi a kicin din take kiranta ta
sanya ta aiki. Dahuwar indomie, haΙa cornflakes, wankin kashi da sauransu.
Ita kuwa Futuha ta tare can sashin Anna wajen Anti Jannat
suna hira kamar ba gobe. Mami sai dai ta leΖo ta bita da sannu ta kuma ga
yanayin tafiyar aikin sannan ta koma. A wannan daren ba ita ta bar kicin ba sai
wuraren karfe Ιaya da mintoci. Da asuba dakyar ta tashi ta yi sallah ta faΙa
kicin aikin suyan waina. Kasancewar Ladidi a gidan ta kwana bisa umarnin Mami
ya sa ta kama mata. Sai dai duk da gajiyar dake tattare da ita, ranta fari sol,
kowa ya san irin murna da farin ciki da bayi ke tsintar kansu ciki idan aka ce
yau sallah. Wannan murnar ne ya Ιan Ζara mata kuzari, kafin dai zuwa karfe
takwas sun yi sun kammala. A gaggauce ta sanya zuba komai kamar yanda Mami ta
umarce ta, ta dauki na Abba za ta kai sai ga Ummita wacce ta tsaya shirya yaran
Anti Jannat ta shigo tana mata sannu. Ta karΙa ta Ζarasa da shi. Ya yi daidai
da fitowar Mami wacce ta ci adonta cikin doguwar rigar atamfa dinkin
three-quarter da zani, peach colour ya sha adon stones. Ta yi kyau sosai abinka
da farar fata. Humaira ta gaishe ta, fuska a sake Mamin ta amsa tana mata sannu
da aiki.
"Kin yi kyau sosai Mami."
Ta yi Ζ΄ar dariya.
"Nagode. Muje na ga aikin naki sai ki je ki
shirya."
Ta amsa da toh, suka koma kicin ta bubbuΙa tana jinjina kai.
Cike da farin ciki ta dube ta.
"Girki ya yi kyau Humaira, na kuma sani a baki ma zai
fi haka. Sannu da aiki. Ladidi kun sha aiki, Allah ya bada lada."
Ladidi dake tsaye tana Ιan tattara kwanuka ta amsa fuska a
sake. Daga haka Mami ta juya itama ta bi bayanta. Dakinsu ta nufa, tun kafin ta
karasa ta ji Ζamshi iri-iri na turare yana busowa. Hakan sam bai burgeta ba don
ta sani Futuha ce da wannan aikin, yarinyar babu ruwanta da haramcin fesa
turare mai Ζarfi ita kusan ma turaren maza ya fi burgeta akan masu sanyin
Ζamshi marasa Ζarfi. Futuha ce kuwa tana tsaye an ci ado cikin atamfarta super
mai kyau sky blue da ratsin fari da ruwan toka mara turuwa cikin wanda Alhaji
ya kawomata, ta yafa blue mayafi mai kauri da girma kasancewar sallah za ta je
yi sai takalminta mai shegen tsini shi kuma baΖi. Ko mahassadi ya sani ta yi
kyau sosai, sai hotuna take Ιauka tana cuno baki. Ita kuwa Tasleem bata kai ga
zuwa kayan ba tana tsaye gaban madubi tana gyara fuskarta, Allah ya taimaka an
kwana da wutar nepa kuma an wayi gari da shi. A gajiye take likis, ta zauna
gefen gado zaman jiran fitowar Raihana daga wanka, babu wanda ya ce mata ci
kanki kamar yanda ita Ιin ma ba ta kula su ba. Tun tsawatarwar Abba ta samu
suka sakarmata mara kaΙan, duk da a wasu lokutan ana bin ta da baΖar magana ko
kuma kallon banza amma ko kallo ba su ishe ta ba. Su din ma ba kasafai yanzun
suke shiga harkarta ba, sun fi maida hankali a hirar bikinsu. Kusan kullum sai
an shiga instagram an ga tsarin bikin Ζ΄an Ζarya ana cewa irinsa za a yi, ko
kuma kayan amaryar sun yi kyau shi za su yi.
Har ta soma buga hamma bacci na son
kwasarta sai ga Raihana ta fito, ta mike Raihana na mata sannu da aiki ta amsa
ta Ιau zanin wankanta ta shige. Tana fitowa ta hau shiri, itama Ummita tuni ta
yi wanka kafin ta ta je shirya yaran Anti Jannat don haka tana shigowa shirin
ta hau yi. Atamfarsu na wurin Abba suka sanya. Sun yi kyau abinsu tsaf kowacce
da jilbab wanda ya hau da kayanta. Humaira kalar maroon ne nata, ya fito da
farar fatarta sosai ta yi kyau sai rama da fuskarta ta yi ba ma ita kadai ba,
dukkansu babu wanda bai rame ba a watan azumi. Itama Ummita ta yi kyau tsaf
cikin jan hijabinta mai haske, sai kuwa Raihana da nata brown. Sun yi kyau gaba
Ιayansu. Fararen Ζ΄aΖ΄an Mami kamar wasu larabawa. Haka suka jera har su Muhsin
da Waleed da suka sha adon babban riga farare tas zuwa farfajiyar gidan. Nan ma
su Yassar ne ke faman Ιaukar hoto hannun kowannensu saΖale da darduma. Yaran
Jannat ma har da su, mota uku suka yi har da motar Jannat wanda mijinta ya
siyamata tun kafin kamawar watan azumi kafin su iso gari saboda zirga-zirga da
yaransa. Kasancewar ta iya tuΖi ita ta shiga su Futuha abokan hirarta suka
shige motarta sai kuwa yaranta. Ummita da Humaira su na tare da Mami sai motar
Abba da matasan yaransa ke ciki. Haka suka jera zuwa masallacin idi kasancewar
akwai tazara da gidansu. A mota Jannat suka yiwa Raihana caa akan yanda take
shigewa harkar Humaira da Ummita, ita dai ta hademusu rai kawai ta Ζi cewa
uffan. Bayan sun yi parking suka karasa da Ζafa.
Koda suka isa gida nan kuma aka tsaya yin
hotuna a farfajiyar gidan, anan ne Raihana ta dinga yiwa Humaira hotuna
kala-kala, ita kaΙai ta san me take niyyar yi. Ta kuma ranta sai ta aiwatar.
Suna kammala cin abinci ana santin girkin Humaira, Abban da bai fiye kyauta ba
shi ne har da ba Humaira dubu uku barka da sallah sakamakon girkin da ya yi
mishi dadi sosai. Mami ta zuba na makwafta aka miΖa. Humaira ta ji dadi kwarai
na yanda kowa ya ci sai ya yaba, hakanan abokanan su Yassar har da neman Ζari.
Ita dai tana kammala ci ta yi daki ta sauya kaya zuwa doguwar riga marar nauyi
ta shimfiΙe a gado ta hau ramuwar bacci. A sannan ne Raihana ta shigo ta dauki
wayarta dake a gefenta ta fice zuwa falon.
Ummita da ta kammala tattara falon ta dube ta.
"Ke kuma me kike shirin yi da wayarta?"
Ta yi murmushi ba tare da ta kalleta ba ta amsa.
"Lambar masoyinta zan Ιauka na turamasa hotunanta. Ko
ba komai zai rage zafin takunkumin da ta sanya mishi."
"Um um Raihana, kada fa ta ji babu dadi."
Raihana ta Ιan harareta.
"To ke za ki faΙamata?"
TaΙe baki Ummita ta yi gami da neman wuri ta zauna.
"Me ya yimin zafi? Ke ce dai abin ji tunda bakinki ba
ya shiru."
Raihana dai ba ta Ζara tankawa ba, sai da ta tabbatar ta
kwafi lambar Fadeel ta yi mishi sallama ta whatsapp gami da gabatar da kanta
sannan ta mike ta maida wayar inda ta Ιaukota, baiwar Allah ba ta san ma meke
faruwa a duniyar ba tsabar gajiya da baccin da ke kanta.
***
Mintuna kusan sha biyar da shigowarsu gidan daga masallaci,
Fadeel wanda ya sha gayu da babbar riga fara Ζal mai kwalliyar baΖi, ya shige
sashinsa ya bar Alhaji anan falon saukar baΖi tare da makwafta an kai musu
abinci iri-iri. A duniya idan akwai abin da ke damunsa to fa babbar riga, ya
matsu ya cireta. Hakan yasa tun kan ya Ζarasa Ιakin ya cire hularsa ya riΖe a
hannu, yana shiga kuwa ya fidda ya Ιora saman kujera. Zama ya yi sannan ya
fiddo waya ya hau kan whatsapp. Anan ya tadda missedcalls din Ζanwarsa Hannatu,
ya danna mata videocall kamar jira take ta Ιaga. Sun jima su na hira har ya
gaisa da mijinta da kuma Ιanta Ζarami kafin daga bisani su yi sallama. Sauka ya
Ζara yi ya kira wayar kakansa wanda ya haifi Mamansa, nan ma ya gaisa sosai da
Ζ΄an Kamaru har da wasu cikin Ζ΄an uwansa. Bai ajiye wayar ba sai da ya kira
Mahaifin Ibb da suke kira Daddy ya yi mishi barka da sallah ya ci sa'a su na
tare da Maama, itama sun gaisa ya kuma jaddada musu zai shigo zuwa anjima ganin
Maama na faΙin ba ta karΙar miΖe ya zo har gida.
Koda ya ajiye wayar sai ya ji wata irin nutsuwa ta
ziyarce shi, wato dai babu abin da ya kai zumunci daΙi. Wayar ya Ζara janyowa,
a hankali yake sarrafata har ya kai kan lambar da babu ranar da ba ya buΙowa.
Kewar muryarta ya ke sosai, kullum cikin sauraron phone record dinsu yake amma
ba su Ζosar da shi ba. So yake ya ji muryarta a zahiri, da kuma yana da dama
ace ya ganta.
"Why all this?" Ya furta a sanyaye yana kallon
lambarta kamar wanda yake jiran jin amsa daga garesu. A hankali ya sauke ajiyar
zuciya, damuwar da yake kwana da tashi cikinsa ita ce ta ke kokarin mamayeshi,
idanunsa suka kaΙa. Kalmar kora da halin da Ibb yake faΙi ba ya so ya kasance
gaskiya. Sai dai kuma ya sani, gaskiyar kenan, mai Ιaci. Amma ya zai yi? Ya
kasa raba zuciyarsa da Humaira. Ya kuma kasa yi mata gangancin tura magabatansa
kai tsaye wajen nata, ba ya son ta kalleshi a mugu mai son kai. Yana da yaΖini
irin su Humaira idan suka faΙa tarkon so su ne masu riΖon alΖawari, zai wahala
su Ιata ran masoyi da gangan.
Idanunsa ya sauka saman alamar faΙowar saΖonnin whatsapp da
ke nuni ta saman screen din.
"Raihana ce Ζanwar Humaira."
Wannan saΖon shi ya Ιauki hankalinsa daga baΖuwar lamba.
Cikin sauri ya buΙo whatsapp din ya shiga. Aikuwa idanunsa suka yi kyakkyawan
gani saman hotunan abar kaunarsa. Ya rasa me zai yi don farin ciki da kuma
dadi, ya ja filo ya yi jifa da shi ya mike tsaye ya shafi sumar kansa yana bin
hotunan da kallo yana murmushi. Wannan zinariyar kuma lu'u-lu'u a cikin mata
ita Ibb ke cewa ya rabu da ita? Inaa! Ba mai yiwuwa ba ne, sai ko idan
Ζaddararsa ce ta zo a haka. Ya kasa hakuri kawai ya dannawa Raihana kira.
***
A lokacin tana tare da su Futuha a Ιakin Anna, ita kuwa Mami
tana falo amsar gaisuwar Ζ΄an barka da sallah yaran makwafta sai wasu a cikin
Ζ΄an uwan Abba da suka zo. Mikewa Raihana ta yi da sauri ganin sunan FH a saman
screen Ιinta, ta san Fadeel ne. Ζ³ar barandar dake a wajen ta nufa ta tsaya gami
da yin sallama. Ya amsa mata suka kara gaisawa kafin ya Ιora da fadin.
"Kin bani kyakkyawan goron sallah Ζanwata, na kuma ji
daΙi sosai. Ki turon acc no dinki nima na ba ki naki goron."
Ta yi Ζ΄ar dariya.
"Aa Yaya Fadeel, ni wallahi don Allah na maka. Ba
abinda ni da Ummita ba mu sani ba game da sharuΙΙan da Humaira ta gindaya maka.
Ni kuma sai na ga wannan hanyar ce kawai zan yi na ragemaka damuwa."
Ya ji dadi kwarai, ya kuma tabbatar da cewa iyalan gidan
abar sonsa su na da kirki kamar ita. Bai yi zaΙen tumun dare ba.
"Nagode sosai Ζanwata, ki gaidamin Ummita. And please
ki turo idan kin bani matsayi Ιaya da Humaira."
Ta amsa da toh sannan ta yi godiya. Koda ta tura ta yi
mamakin ganin dubu ashirin matsayin barka da sallah, ya aiko da text ya ce su
sha sweet. Ta kuwa hau washe baki da murna har su Futuha da Anti Jannat na
neman ba'asi, sai kawai ta mike ta bar su tana dariyar jin su na cewa wai alert
ta ji daga saurayinta. A dakinsu ta iske Ummita, karasawa ta yi a hankali ta ja
hannunta gudun kar su tashi Humaira, Mami ta ce a rabu da ita ta huta. Sai da
suka fito Ummita ta tambayeta.
"Ke wai mene ne?"
Ta nuna mata kuΙin da Fadeel ya turomata, Ummita ido waje
don ba ta ma fahimci sunan ba ta dube ta.
"Wa ya aikomaki wadannan kudaden?"
Ta yi mata alama da yatsu cewa ta yi a hankali. Nan ta
nunamata hotunan da ta aikawa Fadeel da kuma yanda suka yi a waya. Ummita duk
sai ya ba ta tausayi.
"Allah Sarki Fadeel, nikam yana burgeni wallahi.
Humaira ta tsinci dami a akala take wasa da shi."
Raihana ta yi Ζwafa.
"Rabu da ita, in sha Allahu ba ta da miji sai shi.
Itama ai tana sonsa gulma ce kawai."
Girgiza kai Ummita ta yi.
"Bari faΙin haka, kar ki manta jinnu babu abinda ba su
sanyawa, Ya Sayyadi ya ce har raba mata da miji su na yi saboda sanyawa Ιaya
Ζiyayya da kuma hana zaman lafiya."
"Allah ya karemu da sharrinsu. Itama Allah ya yi mata
magani."
Ummita ta amsa da amin.
***
Hajiya Kubra wacce suke kira da Maama, mahaifiya ga Ibrahim
(Ibb) ta dubi Fadeel tana mai faΙaΙa murmushinta har ana ganin haΖorin makkanta
mai sheΖi.
"Ζan Alhajinsa, ganinka sai an yanki tikiti."
Fadeel ya shafi Ζeyarsa yana murmushin jin nauyi, yau gaba Ιayansa
cikin nishaΙi ya ke ji, babu hoton dake yawo a kansa sai hoton Humaira da ya
gani tana murmushin da wushiyarta ta bayyana zahiri.
"Ina nan Maama, ai ko ba ku yanka ba ni fa Ιanku
ne."
Ta yi dariya aka Ζara gaisawa. Suka Ιam taΙa hira bayan an
kawo mishi ruwa da lemu sai snacks ya ci. Ibb ba ya nan sun Ιan fita da Daddy.
Maama ta gyara zama sosai babu alamun wasa a fuskarta ta ce.
"Ζana kamar yanda ka ce ni uwa ce gareka, ina son ba ka
wata shawara kar kuma ka ce na maku katsalandan kai da abokinka."
Duk da cewa tuni ya Ιago zancen, tunda ai tatsuniyar gizo ba
ta wuce ta ΖoΖi sai ya tattaro dukkan hankali gareta ya ajiye kofin dake
hannunsa.
"Maama kin isa da mu Ιin ne, uwa kuma da ta isa, ai Ιa
ba ya taΙa wuce faΙa daga gareta ba ballantana kuma nasiha ko shawara."
Maama ta yi murmushi, hakika kalamansa sun burgeta. Ta
jinjina kai.
"Wannan hakayake Fadeel, maganar ba wata mai tsawo ba
ce sai ta buri da mafarkan iyayenku. Mun yi hakuri mun zuba idanu, daga kai har
Ιan uwanka kamar babu niyyar faranta mana. Kun fi kowa sanin bamu da burin sai na ganin kun fidda matar aure amma
shiru kamar maye ya ci shirwa. Ba mata a garin ne?"
Ta Ζarashe da Ζ΄ar dariya, shi ma murmushin ya yi mai dauke
da damuwa.
"Akwai Maama, ku yi hakuri, in sha Allah zamu yi. A
taya mu neman zaΙin Allah. Mun fi kaunar farin cikinku sama da komai."
"Shikenan, Allah ya yi maku zaΙi mafi alheri da
albarka."
Ya amsa da amin. Yana shirin tafiya sai ga Ibb ya shigo tare
da Daddy. Shi ma fararen kayan ya sanya irin na amininsa. Nan kuma hira ta dawo
sabuwa, Daddy ya hada su ya kara yi musu zancen aure. Ya jima a gidan kafin ya
fito tafiya. Sai da suka karasa har bakin motarsa sannan Ibb ya dube shi.
"Wai lafiya?
Yau kamar wanda aka yi ma albishir da aljanna sai fara'a kake yi. Akwai labari
ne?"
Fadeel ya Ζara fadada murmushinsa. Hotunan Humaira ya
nunamasa, da mamaki Ibb ya dube shi murna fal ciki.
"Dagaske ne abin da nake gani? Ita da kanta ta
turomaka? Ah lallai dole ka yi fara'a, ka ce tsayuwar darenka a azumi Allah ya
karΙa."
Fadeel ya Ιan basar ta hanyar sosa kara hanci.
"No ba ita ce ta aikon ba, Raihana ce Ζanwarta."
Nan fa Ibb murna ta koma ciki, ya ja guntun tsaki.
"Allah ya yayemaka wannan makahon son Fadeel. Ka ture
batun wannan yarinyar ka nemi matar aure ta gaske please. Ni dai dab nake da
kawowa su Daddy matar aure."
Fadeel ya bude mota yana murmushi yana kallom hanya har wasu
Ζ΄anmatan da suka zo giftawa suka maida mishi martani don a zatonsu da su yake.
Ya kauda kai.
"Shikenan, ka ga na huta sai ka yi auren ka samar mana
yara da wuri, su Alhaji idan su na ganin jikokinsu hankalinsu zai kwanta ni
kuma na cigaba da jiran abar Ζaunata."
Ibb ya harareshi.
"Ζan iska, sai aka ce maka daga auren sai haihuwa
ko?"
Fadeel dai dariya ya yi.
"Toh me ya yi saura idan har ba juya ba ne kai?"
Shima Ibb dariyar ya yi. Anan yake faΙawa Fadeel wata ce
Salma, likita ce kwararriya ta mata. Sun jima su na abotar da ta juye ta rikiΙe
zuwa soyayya a yanzun. Ya yi shiru ne don ya gani ko abin zai Ιaure.
"Masha Allah, Allah ya tabbatar mana da alheri."
Cewar Fadeel.
"Ameen, kai ma Allah ya kawomaka mace tagari da za ta
mantar da kai Humaira."
Ya yi murmushi ba tare da ya amsa ba ya shige mota abinsa.
Ibb ya matsa shi kuma ya ja ya tafi. A ransa ya na auna addu'ar Ibb din, ba
kuma ya jin mai tabbatuwa ce.
***
Murja ce zaune gaban Malam wanda tun a waya ta zayyane mishi
komai, batun Fadeel da kuma Humaira wacce ta ke buΖatar a shiga tsakaninsu a
raba su gaba daya, ya kasance son da yake yiwa Humaira kacokam ya dawo kanta.
Malamin bayan ya kammala aikin da duk abin da ya kamata ya mata umarnin ta zo.
Tun da ta zauna take cike da fargaba na tunanin me zai fito a bakinsa, malamin
yayarsu ce tana yawan zuwa karΙomata saΖo wurinsa, ba ta taΙa zuwa don aikin
kanta ba sai a yanzun da soyayyar Fadeel ke neman haukata ta.
"Akwai hatsari a kanki babba idan kika ce za ki raba waΙannan
mutanen."
Ji ta yi cikinta ya kaΙa, ranta idan ya yi dubu ya Ιaci har
wani duhu take gani ya mamaye idanunta.
"Akwai hatsari fa ka ce? Toh wallahi na shirya
tunkararsa nidai, zan aikata ko mene ne duk tsananinsa don Fadeel ya zama
mallakina."
Ya yi shiru yana dubanta gami da auna irin rashin hankalinta
kafin ya jinjina kai.
"Aa Murjanatu, kar ki zo gaba kiyi kuka da ni, jimawar
da muka yi da da yar uwarki da irin alherin da nake samu a wajenta, ba zan yi
abin da zai cutar da ke ba. Ki je nan da kwanaki uku ki kara nazari, idan kin
shirya fuskantar kowane Ζalubale da zai biyo bayan aikin, sai ki dawo."
Murja ta yi jim, a yanda ta ke jin Fadeel gani take babu
wani abu da ba za ta iya jurewa ba. Can ta nisa ta ce.
"Malam, idan har dai ba hauka ba ne ko wata nakasa naji
na gani zan jure."
Ya yi wani murmushi.
"Kina da gaggawa Murjanatu, eh ba nakasa ba ne, amma
rushe maganar wannan yarinya a zuciyar Fadeel ba zai amfaneki da komai ba sai
halaka. Abin nufi, har abada kema ba lallai ki aureshi ba, idan kuwa aurenku ya
tabbata toh fa har ki mutu ba zai kusanceki ba. Ke za ki kasance kare ma ya
fiki daraja a rayuwarsa. Ki yi hakuri, ita gaskiya Ιaci gareta kuma kin fi kowa
sanin ni Malam Tanimu ba na Ιoyewa mutum koda kuwa idan ya aikata abun zai haΙu
da mummunan bala'i sai na sanarmaka idan ka ji ka gani a tafi a haka, sai a
tafi. Kin yarda kin amince?"
Ta ji zufa na karyomata, ita da take burin rayuwa mai kyau
da inganci da shi? Take burin ta mallake shi su ji dadin tarayyar aure? Kai sam
ba ta yi imani da faΙar Malamin nan ba duk kuwa da sanin da ta yi mishi ba na
yau ba don haka kawai sai ta ce ya ba ta lokacin shawara, daga haka ta miΖe ta
bar wajensa da nufin sauya sheΖa. Wannan Malamin ba abokin tafiya ba ne, ba zai
mata yanda take so ba.
***
Sun yi yawo sosai
gidan Ζ΄an uwan Abba, wannan kam ita da Ummita ne sai ko Raihana da ta jera da
su. Si Futuha kuwa daga gidajen Ζawaye sai ko Ζ΄an makarantarsu na sakandire da
suka haΙa reunion aka ci aka sha. Sun je hawan sallah Humaira ta sha kallo,
abin ya yi matukar burgeta. Ta dauki hotuna sosai a wayanta, ita kuwa Raihana
babu kwalliyar Humairar da ba ta Ιaukarwa Fadeel ba, daidai da bidiyonta a
wurin kallon hawa sadda take murmushi da haska bidiyon sarki ta Ιauka ta tura
wa Fadeel. Sosai sallar ta yi mata dadi, ta kuma yaba da kalar wasannin da aka
yi.
***
Zaune take a falo
tana ta kallon yanda a hankali ta soma samun mabiya a shafin Instagram, hakanan
hatta a facebook da Raihana ta budemata ta sanya ta a shafukan tallace-tallace
na sana'o'i nan ma ta samu abokantaka da mutane da dama, sai dai babu wanda
suka taΙa hira a akwatin sirri (inbox). Ita kaΙai tana ta murmushi ganin yanda
hotunan girke-girken da ta yi yake samun likes da kuma comment. Jannat ta shigo
falon da rawar jikinta, dawowarta kenan daga gyaran gashi. Su Futuha sun fice
shoprite sun kai yara, Ummita ta je albarkacin yaran Jannat da suka sa rigimar
su sai an tafi da ita don ba karamin shaΖuwa suka yi ba.
Humaira ta Ιago tana dubanta don har ta tsorata ta, sam ba
ta tunanin ta yi sallama. Su na cikin sati na uku ga sallah, a yanda ta ji daga
Ummita, bai fi kwanaki uku ya rage Jannat ta bar gidan ba wannan yasa take ta
shirye-shirye. Kallo Ιaya Jannat din ta yi mata ba ta ko amsa sannu da zuwan da
take mata ba ta yi gaba, har ta Ιan yi nisa ta dawo baya tana yatsine fuska.
"Ke, ki dafamin abu marar nauyi yanzu."
Humaira ta amsa da toh, daga haka ta watsa mata harara ta
shige. TaΙe baki Humaira ta yi, ko kaΙan ta daina jin ciwon Ζiyayyar da suke
mata, ta lura ba Ζasa suka kwasa ba. Jinin Anna ne dole su kwatanta halinta.
Ban da ma rashin ta ido, ina uwar mace da zuwa gidan surukai ta tare ko tuna
asalinta ba ta yi? Mami ce dai ta sha bamban da su.
Tana wannan saΖe-saΖen zucin wayarta ta Ιauki Ζara. Ganin
baΖuwar lamba ya sanya ta yin jim tana tunani, tana da tabbacin ba shi ba ne.
Mutumin da gaba Ιaya ya sauya bai ko Ζara kiranta ba, ganin wayar na shirin
katsewa ya sa ta Ιauka. Muryar mace ce, ta amsa sallamarta suka gaisa.
"Ina magana da Humaira? Humaira Yusuf mai yin
snacks?"
Ai sai ta miΖe tsaye ta hau washe haΖora. Ta amsa cikin
zaΖuwa.
"Eh, ita
ce."
"Masha Allahu, ina bibiyarki a shafinki na instagram,
na ga tallace-tallacenki. Ina son snacks ne, za'a iya samu nan da kwanaki hudu
haka zuwa biyar?"
Humaira ta Ιan yi tsallen murna sai ta Ιan toshe baki gudun
kar dariyar farin ciki ya suΙuce mata, wannan kusan shi ne order din farko tun
da suka soma talla. Nan ta tambayeta kalolin snacks din da take so, ta yi mata
bayani, a karshe suka yi sallama da zummar Humaira ta lissafa adadin kuΙinta
sannan ta turo acc number. Ai don murna tuni ta mance da batun wata Jannat,
gudu-gudu ta nufi falon Mami tana kwala mata kira. Amma ina! Ba ta nan tana
bangaren Anna, tsabar rufewar idanu kawai sai ta sa kai har cikin dakin Anna
tana kwala kiran Mami. Su na zaune su na hira sai ganinta suka yi. Mamin ta
nemi ba'asi nan ta hau sanar da ita yanda suka yi da mai order. Itama sai murna
da hamdala.
"Kai Alhamdulillah. Dole kiyi murna, maza muje ayi
lissafin sai a turamata."
Da murmushinta mai bayyana kyawunta da tsantsar kamanninta
da Abba ta amsa da toh. Har ta juya za ta fice ta ji tsawar Anna.
"Ke!"
A firgice ta juyo kuwa, har ga Allah sai a sannan idanunta
suka buΙe. Ta tuna inda ta faΙo da kuma kuskuren da ta yi na rashin sallama
ballantana gaisuwa. Kawai sai ta durkushe ta gaida Annar, Jannat ta karasa ta
ja kunnenta har sai da ta saki Ζara.
"Don ubanki
dayake kin raina mutane uwarmu sa'arki ce da har ki faΙo Ιakinta kamar na
uwarki?! Ba aiki na sanyaki a kicin ba? Kema kuma Mami laifinki ne."
Daga nan ta juya harshe zuwa buzanci ta cigaba da sababin faΙa,
Anna itama tana taya ta. Daga yanda Mami ta yi shiru ta haΙe girar sama da ta Ζasa Humaira ta fahimci magana
suke gasamata. Nan da nan jikinta ya yi sanyi, a gefe guda ga na gorin Ιakin
uwa da aka yi mata, ba don darajar Mami dake a idanunta ba sai ta faΙamusu mai
zafin da ba zasu Ζara mararin daΙa kwana ko Ιaya a gidan ba idan har su na da
sauran kunya.
"Humaira, tashi ki je, ki yi aikin da ta sanyaki kafin
na zo." Muryar Mamin ta katse ta. Ta mike tana mai amsawa da toh gami da
share kwallar da ta cika idanunta. Bayan fitarta Anna ta ce.
"Maryama ban san irinki ba, ban san wa kike son ki
burge ba. Wato har wani girki za ta fara na harkar kuΙi? Wannan naki salon
uΖubar ce ko kuwa dai son yarinyar ne fiye da naki yaran ya rufemaki idanu kike
son ta kere su a komai ta yi musu zarra? Idan bacci kike ki farka, kin nemawa
yarinya har ya zama mai arziki, a kuma yanda naji zaΖin miyarta ina mai tabbatar
maki watarana sai ta fi ki kuΙi. Tukunna ma, kuΙaΙen kina nufin ita za ki dinga
damΖawa?"
Mami ta yi shiru na Ζ΄an sakanni har Anna ta Ζara tankawa
yayinda Jannat kuwa ta ja tsaki don tana jin haushin yayarta sosai, tana abu
tamkar a duniya su Humaira ta haifa ba su Futuha ba. Can dai Mamin ta yi
magana.
"Ta asusuna kuΙin za su shigo."
Murmushi Anna ta yi mai tarin ma'ana kafin ta ce.
"Na sanki Maryama, ni na haifeki. Kar ki zo mini da
rainin hankali da wayo kinji ko? Wato ni ga sakara shi ne za ki rufe ni ruf, to
ai koda ta asusunki kuΙaΙen suka shigo a yanda kike nunawa yarinyarnan kamar ki
lashe ta, ke me iya yin hidimar ta ce ba naki ko yaranki ba. Kaiconki Maryama,
lallai idan ba bi a hankali ba yarinyar nan watarana sai ta watsa maki borkono
a idanu. Kina wasa da wuta."
Janant ta kalli Mami, sai kuma ta girgiza kai.
"Anna, zai fi kyau ki bar wahalar da bakinki a kan
wannan saboda Ιiyarki ta yi nisan da ba ta jin kira. Ita mai miji, burinta ta
nunawa duniya ta fi kaunar Ιa wani sama da nata yaran. Idan kin ji yanda
yarannan ke Ζorafin nuna halin ko in kula da take yi musu sai ki rantse ba ita
ce ta yi naΖudar su ba a bola ta tsinto su. Babu ma kamar su Yassar wadanda su
ubansu bai sakarmusu sun ji dadin rayuwa irin na matasa sa'anninsu ba, su ba su
sami wata kyakkyawar kulawa a wurin uwar ba. Ni na rasa irin wannan gidan da
rayuwar cikinsa. Ba haka nake rayuwa a gidan nawa mijin ba, shi koyaushe
burinsa ya wadata mu da abinda za mu huta ni da yaransa, amma tun da na rayu a
gidannan har na yi aure, mijinta bana jin ya kashemin sama da dubu Ιari biyar a
rayuwa."
Mami ta miΖe tsaye tana duban Jannat, zuwa yanzu ranta idan
ya yi dubu to ya Ιaci.
"Ya isheki hakanan! Ke tsabar rashin kunya har kya
kalli kwayar idanuna ki faΙan magana? A gidan dai da kika raina nan kika rayu
sannan ko Yusuf bai kashe maki sama da kuΙaΙen Ζaryar da kika buga lissafinsu
ba, ai kin ci kin sha daga jikinsa. Ke yanzu idan da kina can wannan dajin kina
rayuwa, har kin isa ki ga shi mijin da kike tutiya da shi ki aura? Ni na
isheki! Nan da kike ganina kar nake, na fi ku sanin inda ke mini ciwo. Ba
damuwarki ba ce kuma balle ki sani, idan har ba za ki dauke idanu daga lamuran
gidana ba, ki tattara ki..."
"Maryama!" Tsawar da Annan ta bugamata ne yasa ta
yin shiru tana fesar da huci mai zafi, ta kalli Anna sai kuma ta juya ta fice
daga Ιakin. Jannat nan ta haukacewa Anna wai Mami ta yi musu gorin zama a gidan
don haka su tattara su bar mata gidanta. Anna dai ta dinga lallaΙa Jannat, ta
sani muddin ta bi cewarta ta bar gidan to fa komawa can wani Ζauyensu dake
garin Agadez ya kamata, yanda ta fito ta ΙanΙani rayuwar daula koda ace bai kai
yanda ta ke so ba, ta gwammace ta cigaba da rayuwa a nan. Ta sani babu ta yanda
za'a yi shegiyar surukar zamani irin ta Jannat ta amince da zamanta a gidan Ιanta.
Dakyar dai ta samu Jannat ta janye Ζudurinta, tsana da haushin Humaira ya Ζara
ninkuwa a Ζasan ranta.
***
Humaira kuwa sai ta nemi murnar da take yi na Oda ta rasa,
jiki a saluΙe ta yi mata dahuwar dafadukan macaroni mai busasshen kifi.
Ζamshinsa ya karaΙe kicin Ιin da falo. Koda ta kammala ta haΙa komai a Ζaton
faranti ta kai mata babu godiya ba kallon arziki, itama ba ta sa a ka ba kawai
ta jya da zummar tafiya.
"Ke zo nan!"
Muryar Anna ta ji, ta runtse idanu kirjinta na dukan
tara-tara cike da tunanin da wanne kuma Annar ta zo yanzu ta juya ta koma ta
durkusa ba tare da ta kalleta ba. Ta soma magana a kausashe.
"Ζago ki kalleni nan, ni da kike gani dai na fi
Ζarfinki. Mun ci dubu sai ceto, zuri'ar Mamman Ζan Jika daidai nake da kowane
bafillace mai taΖama da asiri. Har mu za a gayawa asiri? Tun wuri ina gargaΙinki
ki fice a rayuwar Ιiyata, idan ma wani mugun Ζullin aka kawoki da shi don ki
shiga tsakaninta da yaranta toh ahir Ιinku, ni dai na fi Ζarfinku balle kuma
tsatsona. Ki kama kanki tun kafin na Ιau mummunan mataki a kanki. Ζan girkin da
kike taΖama kin iya ni mai iya juya lamarinki da shi ne, idan kuma kina da ja
ki cigaba kar ki fasa. Asir dai ba za ki nunamana ba, mun saka Allah a gaba ne
kawai shiyasa muka watsar. Amma muddin kika ce za ki cigaba da juya Ιiyata
kamar waina da shiga tsakaninta da yaranta da ta haifa da cikinta ni nan zan
nunamaki iyakarki."
Tana kaiwanan ta juyar da kai tana girgiza Ζafa na bala'i.
Humaira ta dubi Anna dakyau, an zo gaΙar da ba za ta jure ba sai ta ba ta amsa
ko yaya ne. Ζazafin sihiri ba za ta jure shi ba don haka ta soma magana da wani
irin Ζunar rai.
"Kiyi hakuri Anna, amma kalamanki laifi ne ko a wurin
Ubangiji, kin yimin mummunan zato kin kuma yimin Ζazafi. Lallai Ubangiji zai yi
mana hisabi a gobe Ζiyama. Na samu kyakkyawan tarbiyya a wurin Dada da Kawuna
irin wanda nake da yaΖinin ko uwar da ta haife ni sai haka. Ban san boka ba
balle mugun malamin da zan je ya yi min wani mugun aiki ba, asalima ban da a
fina-finai da kuma labari ban taΙa karo da su ba. Wanda ya riΖi Allah, ai ba
zai aikata abin da kuke yi ba. Kullum cikin zagi da aibata musulmi Ιan uwanku,
ni Humaira babu wani mahaluΖi a duniyarnan da zan kai ya yimin aiki a kan wasu,
kenan idan nayi hakan ma ban riΖi gaskiya Ιaya ba, ban yi imanin Allah zai iya
amsamin addu'ata ba komai muninta komai kyawunta ba kenan. Ai Ubangiji ya wuce
duk zatonku. Balle ma ban taΙa roΖo mai muni kan kowane Ιan uwana musulmi ba,
kuma ba zan fara akan Mami ko yaranta ba. Tsakanina da Mami sai addu'a, ta
yimin riΖon da ya sa nake jure dukkan wani abu da za ki yimin ke da jikokinki.
Har abada kuma bisa darajar Mami ba zan taΙa daina ganin mutuncinki ba. Kiyi
hakuri idan da abin da na faΙi mai zafi."
Tana kaiwa nan tuni ruwan hawaye sun wamke fuskarta, a bisa
tilas ta kalli idanun babbar da ba ta riΖe girma da tsufanta ba ta gasamata
maganganu. Ita ta fi Anna jin ciwon haka, sai dai haka take, ba ta iya hakuri
idan aka kai ta bango musamman idan abin ya kasance ya haΙu da baΖin Ζazafi.
Juyawarta ya yi daidai da saukar igiyar chaja a gadon bayanta, Jannat ce wacce
a farko ta yi Ιif don gani tayi tamkar a
mafarki wai wata Ζaramar yarinya na gasawa uwarta maganganu, sai da ta motsa da
zummar barin Ιakin sannan ta zabura ta janyo igiyar chazarta. Nan fa ta hau
jibgar Humaira amma kamar ba mutum ake duka ba, ta Ζi tafiya ta kuma Ζi Ζwatar
kanta. Zuciyarta tafarfasa take yi. Kallon Jannat take kawai tsakar idanu
yayinda idanunta suka kaΙa sosai sai ruwan hawaye. Ganin da ta yi Humairar babu
ko gezau sai kawai ta hau wanke ta da mari tana zaginta. Ta yi biyu, za ta Ζara
ta riΖe hannunta gam, ba ta san ya aka yi ba, ba ta kuma jin za ta iya tunanin
mai kyau da marar kyau a lokacin, kawai ta ji yatsun hannunta sun sauka saman
fuskar Jannat da mugun Ζarfi ji kake tas!!! Ya yi daidai da faΙowar su Futuha Ιakin
waΙanda dawowarsu kenan daga shoprite cike da nishadi. Ganin abinda ya faru ne
ya sa Tasleem sakin ihu mai Ζara da ya ja hankalin Abba da Mami dake a sashin
Abban, suka nufo da sauri Abba ya Ιan tsaya daga Ζofa yayinda Mami ta kutsa kai
Ιakin. Alokacin rufewar idanun Humaira har ya kainta shaΖi wuyan Jannat ta
dangana ta da bango, babu sautin kuka sai ruwan hawaye, Jannat ta raina kanta,
ta ji ashe ba ta da Ζarfi don ji tayi kamar ba iyaka Humairar ba ce ta shaΖe ta
ba.
"Wayyo Allahna! Ku taimaka za ta kashemin
yarinya!"
Jin wannan furucin na Anna ya sa Abba danno kai cikin Ιakin.
Tsawa ya dakawa Humaira ba ta ko kalleshi ba. Ya kuwa Ζarasa ya Ιauketa da wani
marin sannan ya fincike hannunta. Mami kuwa mutuwar tsaye ta yi, ita kadai ta
san me take ji a zuciyarta, wannan shi ne lokacin da take gudu, ta juya da
sauri ta bar Ιakin. Su Futuha kuwa suka yi kan Antinsu suka rirriΖe suna kuka
yayinda Anna ma kukan take har da biyu saboda ganin Abban. Shi kuwa rufe
Humaira ya yi da duka sai da ya ga har ba ta motsi kafin ya karasa ga Jannat
yana ba ta hakuri, Jannat kamar jira take kawai sai ta fashe da kuka sosai da
fadin.
"Wannan wane irin cin mutunci da zarafi ne? Da aurena
da darajata da shekaru sa'ar Ζanwar Ζanwata ta shaΖi wuyana? Wannan rayuwar da
me ya yi kama? Kiyi hakuri Humaira, watakila laifina ne da na zo gidannan. Na
saba ganin girmamawa daga mahaifinki, hatta da marigayiya Anti Fati ba ta taΙa
yimin koda kallon banza ba, amma yau ga Ιiyarta nan ta shaΖeni tana ΖoΖarin kai
ni lahira. Aikuwa a yau zan bar maki gidanku."
Ta Ζara fashewa da kuka, Abba ya ji kamar ya Ζara rufe
Humaira da duka, wannan banzan halin a ina ta Ιaukoshi? Tabbas ba halin
mahaifiyarta ba ce.
"Nima yau zan
bar gidanka Isuhu, tun zuwan yarinyarnan naga rashin kunya iri-iri da ban taΙa
gani a wajen yan uwanta ba. Na yi kokarin janta a jiki da nunamata kauna, sai
dai ban sani ba ko tana ji a ranta ni ban kai ta girmamani ba saboda ina zaune
ina cin arzikin gidan mahaifinta ba, tunda abin ya kai ga haka in sha Allahu
zan tattara na koma can Agadez, kiyi hakuri Humaira, wallahi ni ba muguwa ba
ce. Tsakanina da duk abin da ya fito daga jikin Isuhu babu komai sai
girmamawa."
Dakyar Abba yake
magana saboda Ιacin rai ga nauyin Anna da ya dinga ji, wai yau diyar cikinsa ce
ke ci wa tsohuwar mutunci ta hanyar dukan Ιiyarta a gabanta.
"Ki yi hakuri don Allah Anna, wannan gidana ne ba na
Humaira ba. Mallakina ne, kamar yanda uwata mahaifiya da ace tana raye take da
iko kai karfi a kaina da gidannan, haka nake ganinki don haka ina roΖonki kiyi
hakuri ki janye Ζudurinki. In sha Allahu daga yau irin haka ko da wasa ba zai
Ζara afkuwa ba. Ni zan Ιau mataki kwakkwara a kanta."
Ya Ζarashe yana duban
Humaira da sai lokacin take sheshsheΖar kuka, itama shi take kallo, ta sunkuyar
da kai.
"Don ubanki ba za ki buΙi baki ki ba su hakuri
ba?!"
Ya faΙi a tsawace, hakan ya yiwa ran su Tasleem dadi, yau
dai ga wacce suke ganin ta fi su a wurin Abba tana ΙanΙanar kudarta. Abin ya zo
musu a daidai. Ita kuwa mikewa ta yi dakyar ta durkusa sosai, hakuri ta shiga
ba su har Jannat din. Dakyar suka ce ya wuce saboda ganin idanun Abba.
"Muje." Ba musu ta mike jikinta duk ya yi tsami ta
bi bayan Abban zuwa falonsa yanda ya buΖata.
***
Fadeel da murmushi ya
Ιagawa yayartasu hannu alamar jinjina.
Yayar Ibb, Anti RuΖayya wacce ke aure a Kano, sun saba sosai da Fadeel
din tun kafin ma ta yi aure. Ibb ya dube shi.
"Wai ni ban gane ba, toh idan odar ta sauka wa zai karΙa?"
Fadeel ya yi murmushi karo na biyu.
"Nan gidan Antinmu za'a kawo mana, ni kuma sai na zo na
karΙi rabona."
Hajiya RuΖayya ta yi dariya.
"Amma dai wannan ina zaton ita ce zaΙin Ζanin nawa
ko?"
Ya kasa magana sai shafar sumar kai, Ibb ya taΙe baki.
"Ita ce dai yake yiwa son mutuwa ba ta san da zamansa
ba."
Fadeel ya harareshi shi kam dauke kai ya yi ya cigaba da ba
RuΖayya labarin komai. Sosai ta ji ya ba ta tausayi.
"Allah Sarki, yanzu kai zaman jiranta za ka yi
kuma?"
"Um." Shi ne kawai abin da yace yana hararar Ibb
da ya kasa rufamasa asiri. Ibb shima ya rama sannan ya ce.
"Ai wai haka yake nufi, nidai ban san irin wannan abu
ba, ace mutum ya kasa hakura da son wanda ba ka gabansa? Kinsan Allah, mutumin
nan akwai mata da yawa da suke kawo mishi hari, na ce ya runtse ido ya zaΙa ya
darje amma ina. Wai ya hakura da auren har sai Humaira ta yi koda ba shi ta
aura ba sannan zai yi nashi."
Rukayya ta yi salati.
"Fadeel kana cikin hayyacinka kuwa? Wannan wane irin so
ne?"
Nan da nan fuskarsa ta sauya.
"Nawa son da haka ya zo. A sanya ni a addu'a kawai
Anti."
Ta Ιan yi jim tana kallonsa. Sai kuma ta numfasa.
"Shikenan, Allah ya zaΙa abinda ya fi alheri. Zan so
naga wannan yarinyar da ta sace zuciyarka har haka."
Ba musu ya fiddo waya ya buΙe hotunan Humaira wanda hatta a
saman screen dinsa ita ce ya miΖa mata. Ta kalla sosai ta ce.
"Babu Ζarya Humaira kam ta haΙu. Daga kuma yanayin
fuskarta ka san za ta yi haΖuri."
Yabon da ta yi sai ya karawa Fadeel farin ciki, a duniya ya
tsani wanda zai kushe abar sonsa. Ganin har RuΖayya ta yaba sai hankalinsa ya
kwanta. Sun jima suna hirar lamarin Humaira kafin a karshe su yi sallama bayan
Fadeel ya ce mata zai dawo idan an kawo odar snacks ya karΙa.
***
Jannat ce tsaye tana
kallon hanyar waje, har lokacin zafafan hawaye take fitarwa na baΖin cikin
abinda Humaira ta aikata gareta. Fuskarta ya yi jazur, ta juyo ta kalli Anna
wacce ta yi shiru tana kallonta, a duniya Anna ba ta son damuwar yaranta.
"Anna, na yi alΖawari sai na ga bayan Humaira da duk
abin da take taΖama da shi. Ta yimin cin fuskar da ban taΙa tsammata ba, ni zan
nunamata iyakarta koda kuwa zan yi yawo tsirara."
A firgice Anna ke duban Ιiyarta, ta san halin kayanta,
muddin ta furta abu, komai nisan lokacin da za a Ιauka sai ta aiwatar. Wani
lokacin ma, sai ta tabbatar da shafewar abin a kwakwalwarka kwatsam sai dai ka
ga sakamako a aikace. Don haka ta sani ko mene Jannat za ta aikata ba Ζarami ba
ne duba da yanda ta saki fuska lokaci guda har da dariya. A karshe ma hatta da
abincin da Humairar ta kawo sai da ta Ιiba ta yi zaman ci tana santi. Ita dai
Annar ba ta ce mata komai ba, ta fi kowa sanin baΖar zuciya irin na Ιiyarta.
***
Kanta na Ζasa, fiye da mintuna uku shi bai ce mata uffan ba
kamar yanda ita Ιin ma ba ta buΙi baki ta ce komai ba face kukan da take yi
Ζasa-Ζasa. Can dai Abba ya sauke ajiyar zuciya ya soma magana a kausashe.
"Kin bani kunya da mamaki Mamana, ban yi zaton hali na
rashin kunya da Ιa'a daga gareki ba. Me ya hau kanki har haka? Meke yawo a
kwakwalwarki kika aikata abin da yau ace mahaifiyarki na raye za ta yi bakin
ciki?"
Humaira ta ji Ζarfin kukanta ya Ζaru, kewar mahaifiyarta mai
yawa ta ji, ta sani ta aikata ba daidai ba amma ba ta jin Mahaifiyarta za ta
kasa fahimtarta koda kuwa ace ta nunamata kuskurenta. Ta danne abin da ke taso
mata dakyar ta iya magana.
"Nayi laifi Abba, ka yi hakuri ka yafemin."
Ya kuramata idanu duk sai ta ba shi tausayi kuma, sai dai
hakan ba zai sa ya fasa nunamata kuskurenta ba.
"Shikenan, amma ki tabbatar kin samu uwarki kin ba ta
hakuri. Matar da take Ζimanta ki, ai yau ko wani mugun bautar mahaifiyarta da
Ζ΄ar uwarta ke nunamaki ai sa ci albarkacinta ballantana ma babu Ιaya. Amma ki
rasa da me za ki sakamata sai da cin mutuncin yan uwanta? Wannan ba daidai ba
ne Humaira, Maryama ta wuce nan a wajenki idan kina da tunani. Burinta duk a
kanki ya Ζare, kar ki so ki ji yadda koyaushe ba ta da magana sai naki, kullum
cikin yabonki take da burin ki zama hamshaΖiyar Ζ΄ar kasuwa mai siyar da abinci
irin wanda ko Otel sai haka. Ba ina faΙamaki ba ne don wani abu a face
sai na son ki fahimci irin girman da ta ba ki. Daidai da batun bikin yarannan
idan aka Ιauko, sai ta ce ita dai burinta ta ga auren Ζ΄an ukunta (Ummita,
Raihana da Humaira), su ne Ζ΄aΖ΄anta. Toh kiyi takatsantsan, ki kuma kara martaba
wannan girma da soyayyar da take nunamaki. Na san ke Ιin mai jin magana ce kuma
ba na shakku akan tarbiyyar Dada, sai dai ina roΖonki kar ki sake na Ζara jin
makamancin wannan daga gareki. Kin ji ko?"
A sannan kukanta ya tsaya, sai Mami dake yawo a kanta wadda
Abban ya kara sa ta ji kaunarta ta cika zuciyarta ga wani irin nauyi da kunya
da ta ji. Shakka babu ta kai maΖurar da har ta kasa danne a zuciyarta ta aikata
abinda zai sosa ran Mamin da ma Raihana da Ζasim wanda a yanzun suke Ιan
gaisawa sama-sama.
"Na ji Abba, ina neman gafararka, zan samu Mami na ba
ta hakuri. Na kuna yi alkawarin ba zan kara ba"
Murmushi Abban ya yi.
"Masha Allahu, ko ke fa. Maza tashi ki je wajen Mamin
taki."
Itama Ιan murmushin ta yi kafin ta miΖe ta bar falon. Kai
tsaye Ιakin Mami ta nufa, sallama ta yi aka amsa sannan ta faΙa. Mami dake
zaune gefen gado ta yi shiru ta Ιago ta dube ta sai kuma ta sunkuyar da kai.
Gaban Humaira ya faΙi, tabbas Mami kuka ta yi, idanunta sun tasa sun kumbura.
Sai ta ji nata hawaye sun dawo sabbi, ta durkusa gami da Ιan dafa gefen gadon.
Dakyar ta iya tattaro jarumta ta ce.
"Ma..Mami nayi kuskure, nayi babban laifi. Ki yafemin,
ki yi hakuri. Maganganun ne suka yimin nauyi, zuciya ta kwasheni na aikata
haka."
Sai ta kasa kara wani abin a kai, ta yi shiru. Mami ta
kalleta ta Ιan yi wani murmushi mai kama da yaΖe.
"Tabbas kin aikata babban laifi Humaira, kar ki damu,
abinda ya faru ya riga da ya afku. Ni na sani, matsalar ni za ta shafa yanzu.
Uwa ce ya zama wajibi ga duk mai neman dacewa da rahmar Allah ya bi ta sau da
Ζafa, ba zan iya sauya tsanarki a zuciyarta ba kamar yanda ba zan iya jure
Ζiyayyar da ake nunawa jinin Fatima ba don a duniya da ace za'a samu abokiyar
zama ta gari irin mahaifiyarki, shakka babu da an zauna lafiya. Ζ³ar uwata kuwa,
ni da ita mu biyu kaΙai Allah ya mallakawa Anna, zan iya cewa Ζauna da soyayyar
da Anna ke yiwa Jannat ya ninka nawa son a wurinta. Da ace tana da damar zama
tare da ita, da tuni yanzu ba ta tare da ni sai ita. Hakuri nake yi ina
takatsantsan da abin da zai haΙani faΙa da Jannat sabida na sani Ιacin ran Anna
kawai zan fuskanta. A wasu lokutan har nakan yi tunanin Anna ba ta sona
kwata-kwata, sai dai son da naga tana yiwa jikokinta ya shafe zargina. A
hankali kuma na ke gudun zuciyarta, amma faruwar wannan lamarin, Anna ta yimin
maganganu masu zafi wanda ba sani bakinta halaka ce gareni. Har cewa ta yi ba
zan gama da duniya lafiya ba. Wannan shi ne dalilin kukana. Na san kema mutum
ce mai zuciya a kirji, yau da gobe ana maka abu wataran dama dole a kai ka
maΖura. Ina da yaΖinin hakan ce ta kasance yau, amma ina mai baki hakuri a
madadinsu."
Humaira wacce ta gama narkewa sosai a tausayin Mami, ta yi
saurin girgiza kai ta riΖo hannuwanta, cikin muryar kuka ta ce.
"Mami ki daina faΙin haka. In sha Allahu bakin Anna ba
zai kama ki ba saboda mu ma shaida ne akan iyakar biyayyar da kike mata, ni
nayi laifi Mami, ni ce mai bada hakuri ba ke ba. Na kuma yi maki alkawarin jure
dukkan wani abu daga Anna da Anti Jannat albarkacinki. In sha Allahu hakan ba
za ta sake afkuwa ba. Ki yafemin, ina jin kunyarki."
Murmushi Mamin ta yi.
"Kar ki damu, ya wuce. Share hawayenki, kukan ya isa.
Allah ya sa mu dace."
Humaira ta share fuska bisa umarnin Mamin tana mai amsawa da
amin. Itama Mamin ta sauya darasin da yin batun odar da aka ba Humairar. Ita
sai a sannan ma ta tuna da wata oda, nan fa ta kara yiwa Mami bayanin matar da
ta kirata.
"Toh kinga kuwa zama bai ganki ba, anjima ki zo muyi
lissafin komai, idan ya so sai mu ga nawa ya kama sai a sanar da ita ko?"
Zuciyar Humaira tas ta gyaΙa kai tana murmushi. Daga nan ta
miΖe ta fita, Mami ta bita da kallo har ta fice.
Raihana ta fahimci Humaira sai dai ta Ιan nuna rashin
jin dadin marin Anti Jannat a fili, ta dai Ιan basar da Humaira na lokaci sai
kuma aka shirya suka Ιinke. Su Futuha kuwa ta rasa me ya hana su yi mata
maganar sai dai kallon banza kawai da suke watsa mata a duk sadda aka yi katari
suka haΙa ido. Ummita dama ba ta da matsala, wata iriyar yarinya ce mai sanyi
da hakuri, ta nunawa Humaira kawai bata kyauta ba da har ta bari zuciya ta
kwashe ta suka kasa cin albarkacin Mami. Koda ta fadi haka da toh kawai ta
bita, ita kanta ta sani Ummita ta juri abubuwa da yawa wanda ko rabinsa ba za
ta jure ba. Ta taso tun bata san mene ne ma'anar hankali ba, ta rayu cikin duka
da zagin Jannat, ga Anna a gefe wacce a baya Ummitan ke bala'in tsoro kamar
mutuwa. A wurin Mamin kaΙai take samun sa'ida, su Yassar ba su wani damu da
zamanta ba tunda tun kafin ta gama mallakar hankalin kanta take basu girma.
Komai suka ce ta yi ba ta Ζi, koda kuwa ya fi Ζarfinta haka za ka jagula.
Ummita ta ci wahala ta kuma yi hakuri ta jajirce, wannan ne ya sa har gobe Ζ΄an
uwan Mamanta na Bichi ba su taΙa kaunar zamanta a gidan ba.
***
Mami da Humaira sun lissafa komai yadda ya kamata,
hatta da ribar sai da suka fitar sannan ta tura acc number din Mamin ga Hajiya
Rukayya tunda ita Ιin ba ta da account kamar yanda Mamin ta ce. Aikuwa ko
mintuna biyar ba'a yi ba sai ga shi ta aiko kudin. Wannan abu ya yi musu dadi,
washegari kuwa da wuri ta fice siyayya ita Ιaya, sauran sun tafi makaranta.
Koda ta dawo da kaya niΖi-niΖi ga uban rana a garin
haka Ιan sahu ya dinga tayata sauke ledoji. Ta kinkima zuwa ciki. A falo ta yi
karo da Jannat za ta fita tare da yaranta, dama ta ga an wanke motarta tas yana
sheΖi, tun faruwar lamarin sai a ranar suka haΙu, ta gaida ta amma ko kallon
arziki ba ta samu ba sai giftawa da ta yi ta fice yaranta na biye da ita.
Humaira ta yi mamaki don ta yi tsammanin da duka za ta rufe ta ma duk ranar da
suka yi karo. Ba ta wani tsawaita tunanin ba ta maida hankali ga kayanta. Mami
ta fito ta dinga yabon siyayyar. Bayan ta watsa ruwa ta sauya kaya zuwa tshirt
da zani sannan ta fito zaman aiki. Sai wani nishaΙi take yi, ita da Ladidi ne
suka soma, bayan dawowar su Ummita, ita ma ta shiga su ke yi tare.
Aikin da aka ba Humaira kwanaki biyar sau gashinan a
kwanaki uku an kammala komai an haΙa. Hajiya Rukayya ta sha mamaki da ta tsinci
wayar Humaira cewa an gama don babu laifi da Ιan yawa snacks din. Ta yi godiya
ta kuma nemi kwatancen gidan acewarta za ta turo direbanta a karΙa, nan Ummita
ta karΙi waya ta kwatanta mata. Awanni bai fi uku ba sai ga direban ya karΙa ya
tafi. Humaira ta dawo ciki bakinta ya Ζi rufuwa tsabar murna. Futuha ganin
yanda take washe haΖora yasa ta jan tsaki.
"Sana'a ba ilimi shirme kenan, mu dai mun yi
gaba mun bar mutum, hakanan zamu kammala karatu mu zama manyan ma'aikata muna
daga sama kujera muna juya kowa. Ai Tasleem nan gaba wasu na da
kallo."
Tasleem ta tuntsire da dariya. Humaira kuwa hijabinta take
ninkewa da ta sanya ta fita waje ba tare da ta ce musu uffan ba, a yanda take
jin zuciyarta cike da walwala ba ta jin cewa za ta biye musu su Ιata mata rai a
banza. Raihana ce ta yi caraf ta sanya musu baki kuwa.
"Tab, ai wallahi yanzu a zamanin nan dai babu
abin alfahari kamar sana'a, ita fa mace mai sana'a ta huce takaici. Ba ruwanta
da jiran sai an bata ko kuma an yi mata, kawai gani za'a yi a jikinta tana
fitowa Ιas abinta. Muna nan daku in sha Allahu Humaira sai ta zama abin
kwatance, wacce ko mai Masters ba zai nunamata arziki ba. A wannan lokacin kuΙi
kawai, ilimi ba a taΙa yin latti da nemansa, ballantana ma me zai damu mutumin
da yake neman ilimin Muhammadiyya. Ai shi ne maΖurar ilimi, sauran duka bogi
ne."
Jin haka ai sai Futuha ta harzuΖo ta kai wa Raihana bugu,
Raihana ta kauce.
"Shegiya kai! Na sa da ke? Ko kin ji na ambaci sunan
wata? Da ke nake magana ko Tasleem, iskanci kawai. Ina magana kina sanyamin
baki duka zan maki a gidannan. Kin wani raina mu sai kace sa'o'inki. Kema
watarana idan ba mu yi dagaske ba shaΖe mu za ki yi tunda ai zama da maΙaukin
kanwa shi ke kawo farin kai."
Ta karashe tana watsawa Humaira wani banzan kallo ita
kuwa ta kauda kai tana murmushi. Aikin banza, idan rashin kunya ne na nawa kuma
suna gwada yiwa har Mamin balle a junansu, babu kamar Futuha da yanzun kanta ke
bala'in rawa ana lallaΙa ta, hatta da Mami kamar ma tsoron sanya Futuhar aiki
take yi a yanda ta lura, ba ta sani ba ko don Alhajinta mai hidima ne ko kuwa
dai kawai saboda ta kusa aure ne. Tasleem dama ba koyaushe take wuni a gidan
ba, saboda zuwa asibiti.
Ba ta kara bi ta kace-nace da suke yi da Raihana ba ta Ιauki
takarda da bironta ta koma wurin Ummita wacce itama a yanzu ke kokarin koyamata
wasu kalaman na boko irin na yau da kullum da take ji ana Ιan faΙi. Sosai kanta
yana Ιauka.
***
Ya lumshe idanu yana taunar samosa, har ya kammala bai
iya ya buΙe ba, sai can ya buΙe gami da kai hannu zai Ζara, caraf Ibb ya riΖe
tsintsiyar hannun yana dariya.
"Wai kai na tambayeka, ni da na zo wurinka, ni ka
kawowa na ci ko kuwa dai kanka? Tun dazu ka kawomin abu amma ka zage sai ci
kake, oh don ban ce a bani nawa kason ba tunda dai a gabana aka Ζulla
kasuwancin?"
Fadeel ya harareshi.
"Ban da wanda Anti ta cemin ka ci a can? Wannan kuma ni
da kai na kawo wa, idan za ka ci ka ci, ka biyemin kaf zan tashi da shi."
Ibb ya saki hannunsa yana murmushin wannan irin kauna. Shi
kuwa bai ko kalleshi ba ya cigaba da kai girkin Humaira bakinsa. Can a gajiye
ya dubi Ibb.
"Yarinyarnan tana son kashe ni da raina."
Ya kalle shi da kyau kawai ya ji ya ba shi tausayi. A
sanyaye yace.
"Meyasa za ka yarda da hukuncinta? Fadeel ka wartsake
daga baccin da kake, sorry to say, amma yarinyarnan ba ta sonka. Idan kuma ba
za ka hakura ka cire ta a zuciya ba, toh ka yarda mu samu su Alhaji a je nema
maka aurenta."
Fadeel ya girgiza kai yana jin ciwo a kirjinsa idan ya tuna
wai Humaira ba ta sonsa.
"No, ba zan taΙa yi mata dole ba, amma zan Ιaukar maka
alΖawari Ιaya."
"Mene ne shi?" Ibb ya faΙi cike da zaΖuwa.
"Muddin lokacin da ta ban sun cika, zan sanar da Alhaji
a neman aurenta. Idan kuma ba ta amince da ni ba, zan haΖura da ita saboda ta
samu nutsuwar zuci."
Ibb ya sauke ajiyar zuciya, shi fa sam ba haka ya so ji ba.
So ya yi aminin ya furta kalmar rabuwa wanda ya sani sai dai ya yaudari kansa,
ba mai yiwuwa ba ne. Yana kuma ji a ransa, muddin Fadeel ya yi dakon shekara,
toh shakka babu ba abinda zai sa ya iya hakuri da rashin Humaira. Amma sai ya
bar komai a ransa.
"Shikenan, Allah ya yi maka zaΙi nagari."
"Ameen." Ya amsa shi ma.
"Ba za ka ci ba ne?" Cewar Fadeel wanda zuwa
lokacin cikinsa ya Ζoshi amma bakinsa na son ΙanΙanon don haka ya haΖura ya Ιau
gorar ruwa. Harararsa Ibb ya yi.
"Oh, bayan ka cinye kenan ko?"
Murmushi Fadeel ya yi ya cigaba da kora ruwa a cikinsa ba
tare da ya tanka ba.
***
BAYAN WATANNI
BIYAR
Gidan Alhaji
Yusuf wanda aka fi sani da Maiagogo sun wayi gari ranar alhamis da
shirye-shiryen bikin yaransa biyu, Futuhatul-Khair Yusuf da kuma Tasleem Yusuf
wanda kwanaki uku kawai ya rage a fara. An samu sauye-sauye da dama, na farin
cikin ya fi kowanne yawa ga Humaira da duk ma wanda ke tare da ita. A wannan
watannin ta samu alheri mai yawa daga sana'arta. Babbar customer dinta ita ce
Hajiya Rukayya wacce ta hanyarta kaΙai ma ta samu oda na biki da party har ya
zamana tana gwada na abinci bayan snacks sai dai gaba Ιaya sau biyu ta gwada
abincin taro ba laifi kuma masu shi sun yaba hakanan Hajiya Rukayya ta ji dadi
da ba ta ba su kunya ba. Duk abin nan ba su taΙa ganin juna da ita ba sai dai
waya. Mami ta sa an buga leda da stickers mai tambarin DEELSHA'S DELICACIES.
Suna na musamman da Raihana da Ummita suka ba Humaira a sadda Mamin ta ce ta yi
tunanin sunan da za'a sanya a ledar. Sunan ya yiwa Humaira daΙi ko kadan kuma
ba ta tambayesu ma'anarsa ba. Mamin ma ta ji dadin sunan, ganin kalmar turancin
ya sa ta tambayar wacce ta sa, nan Humaira ta sanar da ita su Ummita ne. Daga
haka ba ta kara cewa komai a kai ba.
A yau da ya rage kwanaki uku bikin yan matan Mamin,
gidan nasu ya soma karΙar baΖi Ζ΄an uwan Mami daga Agadez sai ko Ζawayen Futuha
waΙanda suka zo daga nesa kasancewarta mai jama'a fiye da Tasleem. Yan uwan
Abba kuwa ba wanda ya zo gidan da zummar kwana. Mubarak shima ya zo gari, sai
kuwa Anti Jannat. Ya kasance a wannan lokacin gidan ba ya rabo da jama'a, Mami
ta sa Ladidi kawo mataimaka a aiki har su uku saboda yanayin cikar gidan da
zummar bayan biki za ta sallame su.
Anko har kala biyar aka fitar, na Ζawaye daban wanda
zasu sanya ranar kamu da na daurin aure da yini sai ko na ranar dinnerparty. Na
manya su ma kala biyu, na fita kamu sai na ranar daurin aure.
Humaira, Raihana da Ummita daban aka fitar musu da na
sisters wanda zasu saka na yini sai kuma na dinnerparty da Mami ta yiwa su
Futuha jan ido ta karΙar musu katinsu ta riΖe a wajenta don a farko sun nuna su
ko kusa ba su kaunar su halarci dinner din.
Amare sun sha gyara ba na wasa ba daga mai
gyaran jiki na musamman da Mami ta samar musu suke sintirin zuwa. Hajiya Lubna
ita da kanta ta Ιauki nauyin gyara su, gyara irin na mata. Ta kashe kuΙaΙe masu
kauri kuwa wanda hakan ya burge aminiyarta kwarai ta yaba. Ba ma ita Ιaya
ba, Ζawayen Mami da dama manyan mata masu kudi sun ba da gudunmuwa mai yawa na
kudi, kanta ya fasu sosai ta kuna ga fa'idar mu'amala da masu hannu da shuni.
Su Raihana sun karΙi dinkunansu a hannu, sun yo Ζunshi da
kitso abinsu sun fito fes.
A na washegari kamu ne su na zaune suna hira a
daki tare da wasu yan uwan su Raihana sa'anninsu da suka zo daga Nijar, Tasleem
ta shigo. Fatarta har wani Ιaukar ido yake, ba ta da Ζiba irin na Futuha ita
nata jikin daidai misali ne, duban Humaira ta yi fuska ba fara'a.
"Ke Humaira, ke da Ummita ku zo na aike ku."
Humaira ta ji ciwon ke din da tayi kiranta da shi, ita kuwa
Ummita ko a jikinta ta miΖe tana murmushi. Hakanan halittarta yake, tana da
yawan murmushi, abinda zai sanya hawayenta zuba kuwa, toh fa ba Ζaramin abu ba
ne kamar dai akan Humaira ko kuwa wani abun daban. Kamar ba za ta miΖe ba sai
kuma ta yi tunanin ba komai ta yi tunda dai aure ma za su yi su bar gidan sai
ziyara don haka ta taushi zuciyarta ta miΖe itama. SaΖo ta ba su a leda na
ankon Dinner su je su kai can asibitin Malam wajen Ζawayenta kuma abokan
karatunta da suka samu dakyar don har ta Ζare. Ta miΖawa Ummita dubu su yi kuΙin
mota sai kuma lambar wayar Ιaya daga ciki, Sadiya, sun gane ta, takan rako
Tasleem din gida wasu lokutan don ta dauki wani abun ko kuma ta zo takanas
ziyara.
Bayan sun fito waje Humaira ta dubi sararin
samaniya yanda garin ya haΙu da hadari ana cida, lokacin uku da mintoci, ta ja
guntun tsakin takaici.
"Kinsan Allah, sa'ar da ta ci kawai na ganin wannan shi
ne aike kusan na karshe da za ta yi mana kafin ta bar gidannan shiyasa kawai
zan je, amma ban da haka wannan ke Ιin da ta ce wallahi da babu inda zan je
matukar ba Mami ce ta sa baki ba."
Ummita dake kokarin cusa Ζaramar lema a jaka ta Ιago tana
murmushi.
"Humaira ko rigima, rabu da ita lokaci ne ai wataran
sai labari fa. Yanzu kalli, ina Anti Jannat? Ba ta yi aure ba sai dai ta zo
kawai ziyara ta tafi? Toh su din ma hakan ce za ta kasance, mu ma watarana sai
ki ga mun yi namu auren mun tafi mun bar gidan. Sai a dade ma kafin a
ganmu."
Tsaki Humaira ta Ζara ja.
"Ke dai Ummita kina son aure na lura, magana kaΙan za a
yi da ke sai kin yi zancensa."
Da mamaki Ummitan ta kalleta kafin ta amsa.
"Aure ai abin so ne saboda sunnar ma'aiki (s.a.w) ne.
Ke din ma ba sunnar kika tsana ba, mazan ne. Ban kuma san laifi kwakkwara da
suka yi gareki ba."
TaΙe baki Humaira ta yi daidai lokacin da suka fito babban
titi.
"Mu bar wannan magana, nikam ba kya ganin lamarin Anti
Jannat da Ιaure kai?"
Ummita ta yi shiru cikin nazari, tabbas da daure kai, tun
bayan sadda ta zo hutun sallah lamarin nan ya afkuwa tsakaninta da ita, ba ta
kara dawowa gidan ba sai yanzu. Wannan dawowar kuwa, daidai da kallon Humaira
ba ta yi balle har ta jefe ta da kallon banza. Ta lura ko tana wuri Humaira ta
shiga, mikewa take ta bar wurin. Haka dai tana ta kaucewa abinda zai haΙa su a
inuwa guda.Har Humaira ta tarar musu abin hawa suka shiga ba ta amsa mata
tambayarta ba sai da ta Ζara nanatawa kafin ta sauke ajiyar zuciya ta Ιan yi
murmushi.
"Na lura sosai, amma ni abin da tunanina
ya ban ko dai ta sauya ne tana gudun wani abu ya Ζara haΙaku ki maimaita abin
da kika yi. Kin san fa ba zai yiwu ace ta mance ba."
Dariya ta yi.
"Ikon Allah, toh ni ai na mance. Kawai dai sauyin ne ya
Ιan bani mamaki. Babu kyara babu hantara, babu kirana da bare da ta saba yi ba
komai. Sai na ke ganin kamar da walakin goro a miya."
"Ki yi mata kyakkyawan zato, Allah yasa sanadin abin da
ya kasance ta yiwa kanta faΙa. Ni kaina idan kin lura ai ta rage Ιoramin aiki
tunda wannan zuwan ta sa an nemo mata yarinya mai kula da yara. Kawai dai mun
saba da yaranta ba yanda za a yi ta iya raba wannan kaunar."
Humaira ta kalle ta, zuciyar Ummita mai kyau ne, da Allah ya
tashi, sai ya yi haΙa ta da mutumin kirki irinta wato Malam Sahabi. Mutum mai
hakuri da kunya kamar wani mace. Amma abin mamaki duk kunyarsa idan suka ga
saΖonnin soyayyar da yake turowa Ummita sai mamaki ya kusan kashe su ita da
Raihana. Har rantsuwa suke kusan yi su ce ba shi ba ne waninsa ne.
Ummita ta harareta.
"Kallon fa?"
Murmushi Humaira ta yi mai kyau da ya fiddo wushiryarta.
"Kawai kina bani mamaki da kike kokarin kare wadannan
mutanen da ba su taΙa kaunarmu ba koyaushe."
"Uzurin kenan Humaira. Aure fa zasu yi su bar mu yanzu.
Mu ma kuma..."
"Toh naji ya ishe ni hakanan Malama matar Sahabi."
Ummita ta sa dariyar jin abinda ya fito bakinta, ita din ma
taya ta ta yi. Har suka isa Ζofar asibitin su na hira abinsu ana iska kaΙan kaΙan
mai daΙi.
Ibb ne tsaye tare da masoyiyarsa Dr Salma,
yayinda Fadeel ke zaune cikin mota yana jira su yi sallama. Mahaifiyarta ce
kwamce a asibitin inda anan take aiki, suka zo dubiya ta yo musu rakiya har
gaban mota. Bayan sallama da Fadeel ya koma mota yayinda suke hirarsu da Ibb
tamkar kada su rabu, shi kuwa Fadeel kansa ya kwantar jikin kujera yana Ιan
kallonsu yana murmushi. Shakka babu sun dace dari bisa dari. Dogaye ne su duka
biyun don zasu kusan yin kai Ιaya, Dakta Salma baΖa ce, kwayoyin idanunta da
haΖora ne kawai idan ta bude masu haske a fuskarta. Tana da kyau, ba ta da jiki
sosai amma ba za ka kirata da siririya ba. Tana da diri masha Allah, sanya take
da doguwar riga sai coat na likitoci da ta sanya saman kayan, sai kuwa mayafi
Ζarami da ta yi rolling kanta da shi. Hannunta cikin aljihun rigar, gaba daya
hankalinsu ba ya kan Fadeel da ya lula duniyar tunani da jin inama ace shi da
Humaira ke wannan hirar ta nishaΙi. Allah kaΙai yasan yanda zai ji a lokacin.
Ya soma gajiya, hakurinsa ya soma kai wa karshe amma yana dannewa gudun Ιacin
ranta. Ya horu da rashin ganinta ido da ido ba hoto ba, ya sha zuwa ya tsaya a
nesa kaΙan da gidansu ko zai ga wulkawarta sai dai ko mai kama da ita Allah bai
taΙa ba shi ikon gani ba. Tabbas Raihana na kokari gurin aikamasa hotunanta
wasu lokutan ma ba ta san ana Ιaukarta ba. Hatta da karamin video sadda take
aikin snacks sai da ta Ιauka ta aikamasa. Yakan ji inama yana da iko da ita,
inama matarsa ce yana kusa ya riΖo Ζugunta ya sanya ta a jikinsa ya bayyana
mata irin yanda soyayyarta ke cin zuciyarsa sai dai kuma babu hali. Azabar da
bidiyon ke sanya shi ciki ne ya sanya shi dakatar da Raihana daga turo bidiyo
face hotuna.
Ya ja dogon numfashi ya furzar gami da kallon gefe
guda yana mai kauda kai daga kan lovebirds. Hango wata ya yi kamar Humaira, ya Ιan
yi tsai da idanu don so ya tantance abinda yake gani, sai kuma ya kauda kai. Ya
fi tunanin gizo Humaira ta soma yi mishi, sai kuma ya kara kallo. Wannan karon
ita ce tabbas, tana sanye da doguwar riga na material mai mayafi Jajaye.
Yanayin kalar da garin ya yi, sai ya ba wa hasken fuskarta damar sheΖi musamman
da ya kasance tana cikin annashuwa da kwanciyar hankali da alama babu wani abu
dake damunta. Sai hira suke da abokiyar tafiyarta wadda ya gane ta, Ummita ce.
Ya ganta a hoto don ba hoton Humaira kaΙai ba, hatta da Ζ΄an gidan sai da
Raihana ta turamishi hotunansu da kuma bayanin alaΖarsu. Har ya kama murfin
mota zai fito ya tuna alΖawarin shekara da ya Ιaukar mata kawai ya fasa ya
cigaba da kallonta. Dab da motar suka tsaya suna kalle-kalle kasancewar
gilasanta tinted ya sa basu ganshi ba, shi kuwa Ibb shalelan Juliet, bai ma
gansu ba ya lula wata duniyar sai buΙe haΖora yake yi kamar gonar auduga.
Humaira ta Ιan yamutse fuska tana gyara gyalenta da iska ke
kaΙawa.
"Nikam asibitin nan juyar da kai gareshi, don Allah
Ζara kiranta ki ce bamu gane wajen da ta ce ba kinga garin yana kara haΙewa."
Itama Ummita duk ta damu ganin hadari ta fiddo waya ta
dannawa Sadiya. Nan ta ce su tsaya inda suke ta gansu.
Suka ja kuwa suka tsaya, Humaira ta zubawa mutanen dake ta
shawagi a wurin idanu tana godiya ga Allah a ranta idan ta ga an wuce da marasa
lafiya dayake suna daidai Emergency. Ba su wani jima ba sai ga Sadiyar ta iso,
bayan sun gaisa ta karΙa ta yi musu godiya suka juya suka kama hanyar fita.
Fadeel kamar wanda aka tsikarawa allura haka ya zabura ya
fito daga motar ya dubi Ibb.
"Malam ka zo mu tafi ba ka ganin yanda garin ke haΙewa
wai?"
Suka dubeshi, Dakta Salma ta yi murmushi.
"We are sorry Amininmu. Bari na kyale shi haka. Nagode
sosai ku gaida gida."
Bai ko kalleta ba ya amsa da toh don shi gaba daya
hankalinsa na ga su Humaira yana fatan Allah ya sa su amince su sauke su a
gida. Ibb ganin an soma yayyafi ya yi mata sallama ya shiga motar ya tayar.
"Please and please ka yi sauri kada su hau abin hawa,
so nake ko yaya ka yimin kokari ta amince mu kai su gida."
Ya tayar da motar ya soma tafiya sannan ya dubi Fadeel cikin
rashin fahimta ya ce.
"Wa kenan kake magana a kai?"
Fadeel da idanunsa ke kan su Humaira wadanda suka kara Ιaga
Ζafa ganin ruwa ya soma sauka bai ce komai ba face nuni da ya yi mishi da
hannu. Sam bai ga fuskokinsu ba sai baya, kafin ya yi magana Fadeel ya sake
tarar numfashinsa.
"Humaira ce."
"Ohh." Abin da kawai Ibb ya ce kenan.
Yana zuwa daidai saitin inda suke ya tsaya har yana tare
musu hanya, Humaira dake saitin wurin ta kalli motar ranta a Ιace don a ganinta
ko waye yana sane ya sha gabansu. Ta bude baki da zummar magana Ibb ya sauke
gilashi suka kalli juna. A gaggauce ta gaishe shi, itama Ummita haka, ta gane
shi saboda tana ganin hotunansa a wayar Raihana, shi ne dai wanda y taimaki
Raihanar.
"Gida ku ka nufa ne? Ku shiga na sauke ku don yanzu
idan ku ka shiga napep jiΖewa zaku yi."
Ruwan sosai ya Ζara Ζarfi, Humaira ta buΙe baki za ta ja
musu Ummita ta dafe hannun da sauri ta amsa.
"Toh mungode." Ta kalli Humaira, a hankali kuma a
gaggauce ta ce.
"Muje Humaira, yanzu ba lokacin jan musu ba ne, wallahi
nidai ina mura kin sani, ruwannan ya dake ni kuma lafkewa zan yi da bikin
nan."
Jin haka Humaira ta amince suka shiga, ita ta soma shigewa
sai Ummita. Motar sanyi sakamakon Ac dake aiki. Sai a lokacin ta lura da wanda
ke zaune a gefen Ibb din, ji ta yi kirjinta ya buga dam, ta rasa dalilin
bugawar kamar yanda ta kasa dauke idanu a kansa. Shi Ιinma ita yake kallo babu
ΖakΖautawa har bai iya ya amsa gaisuwar Ummita ba. A bangaren Humaira ji ta yi
idan ta cigaba da kallonsa ranta zai iya fita saboda wani irin zafi da take ji
a kirjinta ga kanta dake faman sarawa don haka da sauri ta kauda kai ta matsa
ta maΖure a kujerar bayansa tana jingina da kofar motar. A hankali Ibb ya dan
bubbuga kafaΙar Fadeel, firgigit ya dawo hayyacinsa ya gyara zama, gilashinsa
ya zaro a aljihu ya rufe kwayoyin idanun da so da tsananin kauna ga kewa suka
haΙu suka galabaitar. Dakyar Humaira ta iya gaida Ibb sannan ta gaida Fadeel
din ba tare da ambaton suna ba. Shi ma amsawa ya yi can Ζasa.
Ibb ke tambayar Ummita abin da ya kawo su asibiti.
"Kuna da marar lafiya ne?"
"Aa, aiko mu dai Anti Tasleem ta yi. Ita Ιin Ιaliba ce
a nan. Nursing take karantawa ne."
Dan jinjina kai Ibb ya yi.
"Ok, na fahimta."
Jin motar ta Ιauki shiru sai rediyo dake aiki sai ko ruwa da
ke jiΖa gilasan motar yana sauka a guje saboda karfin da ya yi. Ummita ta dubi
Humaira.
"Wai, da tuni yanzu fa mun jiΖe."
"Uhm." Shi ne amsar da ta ba ta. Fadeel kuwa
lumshe idanun ya yi ya ji sautin Uhm din har tsakar kansa, gaba Ιaya sai da ya
ji tsikar jikinsa ya tashi. Kamar kuma haΙin baki sai ga gidan rediyon sun saki
waΖar Breaker mai taken Kalmar So. Humaira sam hankalinta ba ya jikinta, ji
take kamar ta buΙe motar ta dira a cikinta. Gaba daya koina a jikin rawa yake,
Ac ke kaΙawa a motar amma ita zufa take. Ta tuna da ambaton Allah ba shiri ta
shiga ambata a Ζasan ranta a hankali ta soma dawowa cikin nutsuwarta.
A bangaren Ummita da Ibb, hira suke Ιam taΙawa kaΙan, shi
kuwa Gogan da Humaira ba ka jin komai daga bakinsu, babu kamar Fadeel da yake
jin waΖar ta zo daidai da yanayin da yake ciki. So yake ya tambayi ya take? Ya
lamuran rayuwa? Ba ta hakura ba har yanzu? Ba ta amince ya turo iyayensa ba?
Sai yaushe? Amma ina! Babu ko kalma Ιaya da yake jin zai iya furtawa, ba ya
fatan rabin shekarar da ya kusan cinyewa ya tashi a banza balle ya ga shekarar
ida da rai da lafiya, wannan ya sa yake takatsantsan ya kuma jure bai
Ζara kallonta ba tunda ko ya kalli side mirror ba ya ganin komai face danshin
ruwan dake kwarara sai ko hasken fitilun motocin dake saman titi.
Har suka iso gidan ba ka jin uffan daga Fadeel, shi kansa
Ibb sanin halin mutumin ya sanya bai takale shi da hira ba ko sau Ιaya. Ya dai
san yau Humaira ta fama mishi inda yake mai ΖaiΖaiyi.
"Ko mu karasa da ku har cikin farfajiyar?"
Wannan kalmar ya sa Fadeel cire gilashin idonsa, ya dubi
gidan su Humaira, wato har an iso kenan.
"Aa, mungode sosai. Bari mu karasa ciki."
Cewar Ummita. Humaira kuwa har ta kama Ζofar ta bude, amma
ina, iska mai karfi da ruwan da ya fesomata ya sa dole ta koma ta rufe. Fadeel
ganin haka ya juya bayan, sai a sannan ya kara kallonta ido cikin ido, da sauri
ya dauke idanunsa ya dan kai hannu baya ya dauko lemar dake ajiye a wurin.
Fitowa ya yi ya buΙe lemar, babba ce don ta fi ta Ummita girma, Ummita kam tuni
ta fita itama ta bude nata lemar da ba zai ishe su ba su biyu koda a dazun ne.
Kofar Humaira ya bude gami da miΖamata lemar. A sanyaye take dubansa.
"KarΙa mana Humaira." Ibb ya furta, ta kalleshi.
"Mungode sosai, Allah ya kiyaye hanya." Daga nan
ta fita, sai ya kasance su biyun a Ζasan lemar. Kan Fadeel a Ζasa ba ya son
kallonta gudun Ιarowa kansa aiki, ta sa hannu ta karΙa sannan ta dan ja baya kaΙan.
"Idan na shiga zan aiko a kawo."
Murmushi ya yi mai kyau har a sannan bai kalleta ba ya amsa
da toh. Daga haka ya fice ya koma cikin motar ya rufe. Ita ma ta nufi kofar da
gudu-gudu.
"Muje."
Ba musu Ibb ya yi reverse ya juya kan motar suka bar layin.
Ζ³ar dariya ya yi.
"Fadeel kana son Humaira."
Fadeel bai iya kallonsa ba ballantana ya samu amsa. Ya kara
cewa.
"And you know what? Kun dace sosai."
Nan ma bai kalleshi ba sai dai ya yi murmushi. Ganin ba ya
son magana ne ya sa Ibb rabuwa da shi.
***
A can kuwa Humaira na shiga ta bada lemar a miΖa musu, Ιan
aike ya dawo ya ce babu kowa a wajen, ta karΙa a sanyaye ta shige Ιakinsu da
shi. Madadin ta karasa ciki sai ta ajiyeshi a Ιan gefen don ya sha iska. Suka
sauya kayan jikinsu saboda jiΖewar da suka Ιan yi. Ummita ta Ιauro alwala
sannan itama ta Ιauro, koda ta idar da sallah kwanciya ta yi saman dardumar don
kanta har lokacin sarawa yake yi kamar jijiyoyin kan nata za su tsinke. Tuna
Fadeel kaΙai yana haifar mata da rawar jiki da ciwon kai, daga haka kuma sai ta
ji kamar ana mata ihu a kunne. Kafin ka ce wannan sai ga Humaira ta soma kuka
sosai. Ummita da ke kwashe jiΖaΖΖun kayansu ta juya da sauri ta juyo. Allah ya
taimaka su kaΙai ne a Ιakin ta roΖi yanmatan akan su fita ta gyara don sun yi
kaca-kaca da shi. Tuni ta fahimci matsalar jinnunta ne, ta sha mamaki ma da bai
tashi a mota ta yiwa su Fadeel rashin mutunci ba.
Da sauri ta fice
zuwa kicin, can baya ta zagaya inda ake
dora babban tukunya a icce saboda yawan da aka yi. Garwashi ta zuba cikin kasko
ta dauka da sauri gudu-gudu ta nufi dakinsu. Mami dake kokarin shiga kicin don
ganin kwandunan kayan miyan da Abba ya ce an kawo na girki ta tsaya cak
hankalinta ya yi kan Ummita wacce ke tafiya kamar wani abu ya faru. Da sauri ta
bi bayanta.
Ita kuwa Ummita, tun
cikin babbar sallah da ta je Bichi ta karΙowa Humaira hayaΖi a wurin Ιan uwan
mahaifiyarta hakan yasa Humaira na fara kuka ta yi niyyar turara mata. Abin
mamaki har ta isa yanayin kukan Humairar bai sauya ba. Ta ciro maganin ta barbaΙa
cikin kaskon ta ajiyeshi kusa da Humaira. Nan da nan kanta ya soma juyawa.
Daidai lokacin Mami ta faΙo Ιakin. Abin da ta gani ne ya sanya ta kallon
Ummita,
"Lafiya? Meke faruwa da Humairar? Wannan wane irin
hayaki ne kuma?"
Ummita ta sha jinin jikinta don gaba daya ba ta sanar da
Mami ta karΙowa Humaira hayaΖi ba.
"Ba komai Mami, kukan nan ta soma wanda take yi idan
aljanunta suka tashi shi ne.."
Mami ta daka mata tsawa.
"Shi ne me?! Shi ne kike yi mata hayaΖi ba tare da kin
sanar da ni ba? Haba Ummita, yanzu idan Abbanta ya ji wa zai yiwa faΙa? Maza Ιauke
hayaΖin nan."
Ummita ta dauka ta fitar zuwa bandaki ta kashe, ta sani ta
yi kuskure amma kuma cikin ikon Allah Humaira ta yi shiru sai gumi take haΙawa
da alama kuma bacci ya Ιauketa.
Ummita ta kai duba ga Mami, zuwa lokacin tana zaune gefen
gado.
"Ki yi hakuri Mami."
Girgiza kai Mami ta yi.
"Ba laifi kika aikata ba Ummita, na sani kulawa ce da
yar uwarki, amma ko mene ne ya dace na sani saboda nima ina nawa kokarin a
kanta don har na yiwa Abbanku maganar wani
mai bada magani zan kai ta wurinsa bayan biki ya ga mece ce
matsalarta."
GyaΙa kai Ummita ta yi tana murmushin farin ciki. Ba ta da
fatan da ya wuce ta ga Humaira ta samu lafiya ta amince da auren mai kaunarta
irin Fadeel.
"Toh Mami. Allah ya sa a dace."
Mamin da murmushi ta amsa da amin. Har ta mike ta kai Ζofa
ta juyo.
"Ζaukomin maganin da kike turara mata, idan ya so sai
na yi mishi bayani."
Ba musu Ummita ta Ιauko ta ba ta, murmushi ta yi ta juya ta
fita a dakin.
***
BIKI BUDURI.
Yau ranar ta kama
ranar Kamun Ζ΄anmatan Mami, Futuha da Tasleem. Tun safe Humaira ba ta
zauna ba, tana tsaye akan aikin suyar snacks da aka haΙa tun ana saura kwanaki
biyu aka sanya a firij, sai da aka ci rabin aikin kafin ta bar wurin bisa
umarnin Mami acewarta yanda ta kwashi gajiyarnan gwara ta je ta huta kafin
lokacin da za a tafi event center da aka tanada don Kamun. Haka ta karasa Ιakinnasu
a mugun gajiye tana jan Ζafafunta da suka yi tsami. Hayaniyar Ζ΄anmatan
dake Ιakin ko kaΙan bai mata ba, ji ta yi da ace tana da hali da kaf sai ta sa
an fice an bar ta ta huta. Hakanan dai ta karasa tana amsa sannun da wasu ciki
ke mata tana murmushin yaΖe. Ummita tun safe ta raka Anti Jannat Ζunshi har
lokacin ba su dawo ba. Ita dai daga wannan kwanciyar tana jira ta a fito daga
bandaki ta shiga wanka, ba ta san ya aka yi bacci ya yi awon gaba da ita ba.
Ba ita ta farka ba sai da aka kira sallar la'asar,
nan Ιin ma Raihana ce ta tashe ta.
"Kai, har kin ban tsoro. Kin fa jima kina baccin nan
tun Ιazu nake safa da marwa ba ki tashi ba."
Humaira dake dubanta da manyan idanunta da suka kaΙa suka yi
ja ta ce.
"Har an tafi ne?"
Harararta ta yi.
"Jimin ke Ιinnan, an tafi ne za ki gan ni anan? An dai
soma kwalliya da shirin tafiya. Ki tashi kiyi sallah ki wanka mu tafi lar mu
makara."
"Ina kuma za mu je?" Humaira ta tambaya da mamaki.
Sai kuma don kanta daga yanayin kallon da Raihanar ta jefamata ta tuna.
Ta gyaΙa kai tana hamma da miΖa lokaci guda.
"Oh na tuna, kin ce wajen kwalliya za mu je ashe. Toh
ita Ummitar ta dawo?"
Raihana da tuni ta miΖe ta hau fiddo karamin akwati da
zummar daukar sarΖa ta amsa da eh. Ji tayi kamar ta rufe Humairar da duka, dama
dakyar ta amince za ta yi kwalliyar. Ba ta kara bi ta kan Humaira ba,
itama ganin haka sai kawai ta ja zani ta faΙa banΙakin. Ranta ya Ιaci ganin
yanda aka yi kaca-kaca da shi, ba ta iya wanka ba sai da ta wankeshi tas har
Raihana na kwankwasa kofar tana mitar ta san wankin bandaki take tayi biris da
ita.
A gaggauce ta sanya doguwar riga da mayafinsa ta tayar da
sallah, Ummita na zuwa suka Ιunguma suka fice bayan kowacce ta dauki dukkan
abin bukata. Babu nisa sosai da unguwarsu, Yahaya Gusau sula je gidan wata
yayar Ζawar Raihana ta makaranta, ana kammalawa suka shirya a gaggauce matar ta
yi musu Ιauri. Tsayawa kwatanta irin kyawun da suka yi ma Ιata baki ne. Idan ka
kalli Raihana ka yaba, idanunka na sauka kan Ummita za ka ce ta fi su kyau duk
kuwa da cewar ta fi su duhun fata, amma idan kallonka ya sauka ga Humaira sai
ka yi saranda. Sun fito fes cikin ankonsu na atamfa na kamu. Raihana ce ta biya
kudin kwalliyar ta account dinta, ta dai ce musu Mami ce ta ba su don haka ba
su matsa da tambayar ba. Ta Ιoyemusu daga aljihun Fadeel ya fito, shi ne kuma
ya matsa mata akan sai ta karΙa yana son Humaira ta yi kyau. Hotuna sosai
Raihana ta dauke su, ta tura mishi na Humaira kaΙai.
A gidan suka bar kayansu suka fice. Kai tsaye Manal
Event Center suka nufa. Wurin ya tsaru iyaka, kowa ka gani da irin nasa haΙuwar.
Babu laifi kamu ya yi kyau sosai, Humaira tun da ta nemi guri ta Ζame ba ta ko
motsa ba ballantana ta yi rawa. Ummita dai ta Ιan fita amsa wayar Sahabinta, ta
kuma dawo Anti Jannat ta haΙa ta da Ζ΄an biyu akan ta zauna da su kar su fita,
hakanan ta zauna tare da Humaira da wasu cikin yan uwan Abba, su din ma ba duka
suka zo ba.
A gajiye suka koma gida, kowa ya nemi wuri ya kwanta
bayan idar da sallah. Su Futuha gaba daya sun bar kwana a dakin, daki daban
suka koma tare da kawayensu wanda babu komai ciki, daga shimfiΙaΙΙen kafet sai
katifu sai kuwa fanka dake wulwulawa.
***
Tafe yake zuwa sashin Anti Amarya. Kusan kwanaki sama
da biyar kenan rabonsu da juna, ba don komai ya dauke kafa daga shiga cikin
gidan ba sai Murja da take neman matsawa rayuwarsa da kallo da kuma hirar dole.
Tuni ya taka mata burki da zuwa sashinsa tun bayan da Alhaji ya sanar da shi
saΖonta.
Yau Ιin ma, Alhaji ne ya ritsa shi akan Anti Amaryar
tana tambayarshi wai ko ba ya gari. Nan fa Alhajin ya yi mishi faΙa sosai ya ba
shi hakuri. Don ya wanke kansa ne kuma zai je a yau din. Da sallamarsa a baki
ya tsaya har aka amsa sannan ya shiga. Wacce ba ya kaunar ganin ya ci karo da
ita kuwa a kwance tana chatting, daga ita sai vest da dogon wando. Ya kauda kai
ya juya zai koma, sai ya tsinci muryar Anti Amarya.
"Ah, Fadeel ya za ka juya? Shigo mana. Ke kuma je ki
suturta jikinki." Ta karashe maganar Ζasa-Ζasa tana duban Murja. Ta kuwa
mike da saurinta ta yi Ιaki, yau ji take kamar an mata albishir da gidan
aljanna, ba ta san haka ta yi kewar Fadeel din ba sai da ta gan shi a gabanta
yanzu babu zato. Don haka da sauri-sauri ta zumbulo hijabi ta dawo falon.
Lokacin ya maida hankali suna gaisawa da Anti Amarya.
"Ai ni Fadeel na rasa laifin da na aikata gareka. Na ma
yi zaton ko ka yi tafiya ne ashe kana gidan amma ka Ιuya."
Ya yi murmushi yana Ιan shafar Ζeya.
"Ko Ιaya Anti, babu abin da kika yi. Abubuwa ne suke Ιan
riΖe ni, nakan fita da wuri sannan lokacin da zan shigo dare ya yi shiyasa.
Amma tuba nake, ganinan yau na shigo."
Ta yi Ζ΄ar dariya.
"Toh shikenan ya wuce. Dama Alhaji ne na ga kana kawowa
Meatpie da Samosa mai shegen dadi, har nake tambayarsa inda kake odarsa.
Gaskiya ya yimin sosai, ina so ne a yimin na birthday Ιin autanku (Abdulmaleek)
nan da two weeks, ko zan iya samun lambar waya?"
Fadeel ya yi murmushi, ya na so a duniya ya ji an yaba da
girkin Humairarsa. Kafin ya ce komai sai ga Murja ta tsoma baki.
"Eh wallahi Anti, nima naji dadi. Babu tauri kuma komai
ya ji a ciki sosai. Please ki yi order a wurin."
Ya yi shiru kaΙan, ya sani ba shi da matsala koda ace ya ba
su lambar Humaira tunda dai oda ne zasu yi. Ba ya tunanin kuma Murja ta san
wacece, ba ma ita ba, shi kansa Alhajin bai san daga inda Fadeel ya yi odar ba
don haka hankali kwance ya ce.
"Toh Anti, zan turomaki ta message sai dai zuwa yanzun
suna cikin biki ne ba za a samu ba. Kafin dai zuwa kwanakin da za a yi taron
sun kammala."
Anti Amarya ta jinjina kai. Murja dai Ιif ta yi da ta
fahimci ko ma wace ce dai mace ce yar uwarta. Abin damuwar tana da aure?
Sunanta Humaira? Shi ne ba ta da masaniya. Ita a duniya yanzu mai suna Humaira
take son gani wacce Fadeel ya mato a kanta. Dama kawai take jira ta buΙe
wayarsa ta bincika wanda hakan da kamar wuya.
***
A can gidan Alhaji Isuhu kuwa, yau aka wayi gari da
daurin auren yarannasa wanda ya tara dubban jama'a daga wurare daban daban.
Babu ma kamar jama'ar Alhaji Yakubu kasancewarsa mutum na mutane.
Cikin gidan ko tun
bayan da suka samu labarin an Ιaura auren, nan ya rincaΙe da guΙa da murna. Su
Futuha amaren zamani idanun nan ko Ιigon hawaye babu sai ma murmushi da suke
dokawa. Sun sha kwalliya da farin leshi sun yi kyau har sun gaji. Su Ummita
kuwa shadda ce ruwan madara da aka yiwa kwalliyar stones suka sanya wanda Mami
ta yi musu. Duk inda suka wulΖa sai an kalle su an kuma. Ζ³an uwan Mami gulmar
masu gulmarta suna yi, a cewarsu ta riΖi bare kamar Ζ΄an cikinta, wataran za a
wayi gari sun mata butulci. Yayinda a gefe dangin Abba ke yabon Mami da irin
yanda ta Ιauka ki Humaira da Ummita, sun sani ba ta da laifi ko kaΙan a rashin
zuwansu gidan sai ko na Mahaifiyarta Anna. Shi ma Abban da bai ba su fuskar su
shigo jikinsa ba ya sanya suke ja baya. Sam Abba ba mai sakin aljihu ba ne,
hakan ya sa yake ganin kamar duk wani da zai raΙe shi a yan uwan toh fa buΖata
ce ya zo da ita koda ba hakan ba.
An sha hotuna
sosai, da yamma Amare suka kara shiri cikin atamfarsu mai Ιan karen tsada. Aka
sha yini, sannan bayan Magriba aka hau shirin Dinnerparty.
Nan ma ya yi kyau
sosai, Angwaye da Amare sun sha ado, Amaren sun yi shigar golden lace su kuwa
angwayen golden shadda. Ζawayensu Ζ΄an Ζarya kowacce ji take da kanta. Su ma
Humaira leshi Mami ta yi musu coffee colour mai ratsin golden. Sun yi kyau
kwarai.
Washegari aka
tattara da yammaci aka miΖa Amaren Ιakunansu. Gidan Futuha a rijiyar zaki yake.
DanΖareran gida ne na Alhaji Yakubu mai Ιangare uku, nashi sai uwargidansa
sannan na Futuha a gefe. Yan uwanta sun yaba sosai da gidan, ga kaya na alfarma
da Abba ya yi musu bisa jajircewar Mamin akan ya daure ya fita kunya. Koda suka
nufi sashin Uwargida suka iske shi a garΖame, sun bubbuga ya fi a kirga amma
shiru, dole haka suka juya da ita zuwa nata Ιangaren suna mita. Wasu na fadin
tana nan sun ga sadda aka buΙe labule ana leΖen zuwansu daga wani window a
sama.
Daga nan suka wuce Kuntau inda anan ne gidan Tasleem yake,
babu laifi shi ma ya haΙu. Flat house ne amma an kashe mishi kudi daidai
misali. Ita kadai ce a gidanta sai dai gidan iyayen Hamza na kallon gidan, sai
da aka shigar da ita wajensu suka karΙe ta da hannu bibbiyu aka yi Ζ΄ar nasiha
da addu'a kafin a kai ta gidanta.
***
A sati guda kacal,
gidan gaba daya an watse sai mutan gidan. Mubarak ma wanda bai fi watanni biyu
suka rage ya kammala karatu ba ya tattara ya koma a yayinda a gefe daya Yassar
da Dawud ke shirin tafiya bautar Ζasa. Gidan ya zama gwanin dadi ga Humaira,
babu wani da ke matsa mata yanzu balle kallon banza. Raihana da Ummita sun je
gidajen amare ita kuwa ko leΖe ta Ζi yi. Ta dai yi musu cincin bisa umarnin
Mami, an kai wa kowaccensu gidanta saboda tarbar baΖi.
Raihana da Ummita
suka maida hankali a karatu don sun soma shirin jarrabawar fita aji SS2 zuwa
SS3. Ita kuwa Humaira a sannan ta kammala darussanta na makarantar Anti Laila,
hakan yasa koyaushe tana gida idan har ba wani aikin ta samu ba. Sai ya kasance
ita ke girkin gidan, a cewar Mami, hakan zai Ιebe mata kewa. Ta kuma yarda da
hakan dari bisa dari, ita kanta ba ta son zaman shirun don yana jefa ta tunani
kala-kala.
Ranar ta kama laraba
tana tsaye tana shanyar undies dinta a gefe kuma tana sauraron waΖar Ala mai
suna Shahara. Jin waΖar ya tsaya ne yasa ta fahimci kira ne ya shigo. Ta Ιan
goge hannunta da sauri ta dauka ganin baΖuwar lamba a ranta tana fatan ya
kasance oda ne ta samu don dazu suke magana da Mami take nuna rashin jin dadin
yanda kwanaki biyu shiru ba'a samu ba. Da sallamarta ta Ιaga. Aka amsa daga
can, muryar mace ce. Suka gaisa a mutunce. Nan take shaida mata ta samu lamba
ne daga Ιaya daga cikin kwastamominta, tana son a yi mata snacks na birthday
din yaronta da za ta yi. Nan fa Humaira ta ji dadi sosai, ba ta kawo kowa a
kwanyarta ba sai Hajiya Rukayya, ita ce mai kokarin haΙa ta da mutane. Suka yi
magana ta lissafa mata kalolin snacks din da take yi, ita kuma ta zaΙi kala
uku. Nan ta fadi adadi. Suka yi sallama da zummar za ta turo rabin kuΙin, rabi
kuma idan an kai za ta cika. Ta bukaci Humaira ta turamata acc no ta text.
Da wannan farin
cikin ta karashe shanyar da ta fara, ta dauki bokitin ta shige gidan ta kofar
kicin ta baya. A falo ta hadu da Mami. Ta sanar da ita batun odar da suka samu,
Mami ta ji dadi kwarai.
***
Ita kuwa Anti Amarya
tana ajiye wayar ta dubi Fadeel da murmushi saman fuskarta ta ce.
"Yauwa mun yi
magana. Zan tura mata kudin yanzu idan ta aiko."
Ya Ιan murmusa.
"Ok Anti. Bari na wuce ofis, sai na dawo."
"Toh Allah ya ba da sa'a."
Har ya soma tafiya ta kira sunansa, ya juyo.
"Amma meyasa ka ce kar na ambaci sunanka?"
Ya yi murmushi cikin son nemo abin faΙi can ya ce.
"Saboda ba za ta gane ni ba, ba ni ke yin odar ba.
Sister Rukayya ce ke yi mana. Idan kika ce Haj Rukayya za ta san ta."
Cikin gamsuwa Anti Amarya ta amsa. Daga nan shi kuma ya
fice. Murja dake jin su tana daga dinning table a zaune, ta bishi da kallo.
Yana fita ta yi saurin karbar wayar Anti Amarya, tana tambayarta me za ta yi,
babu amsa. Sai da ta kwafe lambar Humaira fes sannan ta adana a wayarta.
"Me za ki yi da lambar?"
Ta dan sha mur.
"Ina tunanin ita ce budurwan nan tasa da yake mutuwar
so."
Dariya Anti Amarya ta yi.
"Kin samu matsala Murja, me zai yi da ita toh? Nikam
jikina bai ba ni hakan ba. Daga jin muryar wannan Ιin ma kin girme ta. Ba na ji
a gaskiya zai kula yarinya, yaron ba ya son raini tun farko idan kin
lura."
Murja ta dan ji hankalinta ya kwanta, amma hakan ba zai hana
ta bincikawa ba tunda dai ta kasa Ιaukar wayar Fadeel, idan ma ta Ιauka to ya
sanya password ba ka iya shiga.
Tsayuwar mota suka ji a farfajiyar gidan. Murja ta leΖa,
ganin Fu'ad tare da Matarsa Kausar wacce a yanzun take dauke da karamin ciki,
ta ja guntun tsaki.
"Waye ne ya zo?"
Yamutsa fuska ta yi.
"Wannan dogon ne mana mai hankali a gwuiwa tare da
matarsa. Ni na rasa wannan jaraba, mace da
ciki sai shegen yawo."
Ta kara jan tsaki. Anti Amarya ta bude baki ganin wannan
karfin hali na Murja, mutum da gidan ubansa sai a hana shi kawo matarsa? Za ta
yi magana ta fasa ganin Kausar din ta shigo. Ta tarbe ta da fara'a suka gaisa
ta karaso. Shi ma Fu'ad ya biyo bayanta hannunsa rike da jakarta na kaya. Bayan
sun gaisa ne yake cewa Antin tafiya zai yi na kwanaki uku zuwa Abuja zasu yi
meeting da shugaban kamfanin da ya ke aiki shi ne ya kawo ta gidan ta zauna
dayake Ζ΄an gidan su Kausar din sun yi tafiya Saudia. Anti Amarya ta karbe ta
hannu bibbiyu, ta sa Murja kai mata jaka daki. Murja na kumburi haka ta ja
akwatin kayan zuwa Ιakin da babu kowa ciki wanda a baya ya kasance na Hannatu
Ζanwar Fadeel.
Kausar wayayyiya ce
sosai kuma gogaggiyar Ζ΄ar boko da ba ta
daukar raini koda na sakan, tun farkon zuwanta gidan ta ga take-taken rashin
kunyar Murja wannan ne dalilin da yasa ba sa ga maciji. Ba ta shiga harkarta ko
kadan. Murja kuwa ta tsani a duniya ta ga wanda ya fi ta iya kwalliya da komai
ma a wuri, balle kuma kuΙi da uban Kausar ya ninka baban su Murja. Gaba da baya
dai yarinyar Ζ΄ar gata ce kuma gatan da ta samu bai yi sanadin taΙarΙarewar
tarbiyyarta ba. Tana da girmama mutane amma ba ta daukar raini. Hatta da
wayarta sabuwar version ne na Iphone, hakan ya sa Murja ko kallonta ba ta yi
idan tana dannawa tsabar bakin ciki. Wannan ne kuma ya kara mata son ganin ta
mallaki miji irin Fadeel, ta san komai take so za ta same shi cikin sauki.
Koda Fu'ad ya bar
gidan, Anti Amarya da Kausar sun taΙa hira kadan kafin ta mike ta nufi Ιakin da
aka tanadar mata don sosai bacci ne a idanunts. Ciki ya sanya ta zama kamar
wata kaasa. Murja ta bi bayanta da
harara. Anti Amarya kuwa ta kalleta dakyau ta ce.
"Ke banza ce, ba
ki da wayo ko na sakan, yanzu a gaban Fu'ad kike share matarsa? Ke da kike
neman gurbi a zuciyar yayansa, to ta ina zai tayaki yaΖin? Ki cigaba da nunawa
duniya ba ki da kunya, wallahi ina maki kashedi, ba a samun kan mutane sai an haΙa da kissa. Ai koda ace
kina mata Ζin mutuwa bai kyautu ki nuna ba. DaΙina da ke sam babu wayo sai
aukin Ιata rawarki da tsalle."
Murja gaba daya sai jikinta ya yi sanyi.
"Kuma fa hakane Anti. Ni wallahi abin ne ya soma yimin
yawa. Wanda nake so bai san da zamana ba, na rasa ta ina zan soma Anti."
Wani murmushi Antin ta yi.
"Au, kin dawo hanya kenan? Da ba malamai kika Ιaura Ιamarar
bi ba? Ke da ace na bi hanyar malaman za ki ganni a gidannan har i yanzu? Toh
uwar Fu'ad abinda ya kashe ta kenan, ta nuna Ζiyayya da makircinta a fili
karshenta kuma yanzu ga gidannan ya gagareta zama. Malama duk wata Ιabi'a
mummuna watsi da shi za ki yi. Ki sauya salon shigarki zuwa na matan arziki.
Wani matsewa ki fiddo sura ba shi ke burge Fadeel ba, idan kin lura yana son ya
ga mace mai tarbiyya. Sai kin sauya sosai, ki kuma daina rawar Ζafa a kansa, a
hankali nan gaba ko malamin ne sai a bi a shawo kansa. Amma kafin wannan
matakin ke za ki sauya takunki."
Murja ta dinga gyada kai tamkar Ζadangaruwa, sosai darasin
na Anti Amarya ya shige ta, sai dai ta ina za ta fara? Sun jima Anti Amaryar na Ζara wayar mata da
kai tana Ιauka, a karshe dai ta saki ranta sosai ta kuma gane Antin nata ba ta
wasa ba ce.
***
Da taimakon Allah ta
kammala aikin odar da aka bata. Kamar yanda ta saba, wannan karon ma waya ta yi
akan a zo a karΙa. Aka ba ta lokacin zuwa karfe sha biyun rana. Bayan sun yi
sallama ta sauke ajiyar zuciya tana mai jin wani irin nishaΙi. Hamdala ta yi
kamar koyaushe kafin ta fiddo manyan ledojin mai tambarin Deelsha's Delicacies
ta sanya.
***
Murja ta kammala shiri tsaf sai rawar jiki take yi ta
je ta ga Humaira me snacks. Kausar na zaune a falo tana taya Khadija da Hanifa
(Ζiyar Saddika yaya ga Anti Amarya) hura balan-balan su na tarawa. Murjar
ta fito. Kallo ba ta ishe ta ba, ta gefen ido Murja ta watsamata harara. Daidai
lokacin da Anti Amarya ta shigo bayan ta dawo daga farfajiyar gidan inda mai
decoration ke Ζawatawa don anan za a gudanar da birthday din Abdulmaleek na
cika shekaru uku a duniya.
"Ni na shirya zan wuce."
"Toh tsaya na baki cikon kuΙinta. Don Allah ki yi sauri
kina karΙa ki wuce ki karΙo Cake din."
Ta amsa da toh. Anti Amarya na shiga ciki sai ga Fadeel ya
shigo falon riΖe da Abdul yana mishi wasa. Nan da nan Murja ta ji ranta ya yi
wani irin sanyi. Ta kuramasa idanu tamkar ta lashe shi musamman ganin yanda
shigar jan t-shirt da baΖin jeans ya haskaka shi abinka da fari. Ta sauke
ajiyar zuciya tana ji inama kawai ta tsinci kanta a faffaΙan Ζirjinsa. Sai da
ta ji suna gaisawa da Kausar sannan ta dawo hayyacinta. Ajiyar zuciya ta sauke,
ta Ζarasa ta zauna ita mai shirin fita. Murya cike da yanga ta ce.
"Yaya Fadeel barka da rana."
Kallo Ιaya ya yi mata ya kauda kai, shi a yanzu sam ba ta
burgeshi tun sadda Alhaji ya faΙamasa saΖonta.
"Yauwa."
Daga haka ya maida hankalinsa ga Kausar suna hirar aikin
Fu'ad da babu hutu. Ita kuwa Kausar hakan ba karamin dadi ya yi mata ba, ta
gama lura da irin matowar da Murja ta yi a kan Fadeel, ta kuma sani zai wahala
ta same shi tunda sam ba ta gabansa. Murja ta shaΖa, saukowar Anti Amarya daga
saman bene ya sa ta mikewa. Fadeel ya gaisa da ita. Ta miΖawa Murja kudin tana
fadin.
"Ina daΙa roΖonki, na san halinki kar ki je ki zauna
don Allah Murja. Kina karΙar snacks din ki biya ki dauko cake."
Ta amsa da toh, ji take inama direban gidan ba ya nan sai ta
ce Fadeel ya kai ta. Amma tun dazun yana waje ita yake jira. Fadeel kuwa yana
jinsu amma bai sa baki ba. Ba ya son ya zaΖe akan lamarin Humairar har su
shinshino wani abu babu ma kamar Murjar da bai gama yarda da ita ba.
***
Ta tsaya daga Ζofar
gate din gidan tana Ζarewa gidan kallo, yamutse fuska ta yi. Eh ba laifi su na
da rufin asiri amma ko daga waje bai kama Ζafar gidan su Fadeel ba. Ta karasa
ta yiwa Maigadi sallama ta kuma faΙi abin da ya kawo ta, iznin shiga ya yi mata
kai tsaye don dama yana da masaniyar sana'ar Humairar.
A sadda ta karasa
ciki Humaira na zaune tare da su Raihana a falo bayan gama yi mata kwatance a
waya, ta sani ba za a Ιau lokaci ba za ta karaso tunda a sanda suka yi wayar
tana kusa da su.
Sallamarta ya sa
gaba daya suka dube ta. Ba laifi tana da nata tsarin daidai gwargwadod. Abaya
doguwa ce a jikinta sai mayafinsa, sai ko wani Ζaton gilashi da ta rufe
kwayoyin idanunta da shi. Tunda ta shigo falon ya karaΙe da Ζamshin turarenta
mai Ζarfi irin wanda ya zama haramun mace ta fesa ta fita da shi. Suka tarbe ta
da hannu bibbiyu aka gaisa. Humaira har
da kawomata ruwa da ragowar snacks din ta ci. Kasancewarta wayayyiya ta sake da
su aka Ιan taΙa hira har Mami ta fito suka gaisa da ita. Murja ta yaba kwarai
da tarbar da aka yi mata, ta kuma ji a jikinta Fadeel ba zai so Humaira ba, ba
ita ce wacce yake so Ιin ba don dai wannan din ba wata babba ba ce ba za ta
wuce shekaru goma sha biyar ba.
"Kina da page
a instagram ne?"
Humaira ta gyaΙa kai da murmushinta har wushiryarta na
bayyana.
"Eh akwai."
"Mene sunan?"
Nan fa daya, ta sani furtawar ne aiki ba ta iya ba sosai.
Raihana ta karΙe zancen ta fadi. Murja har sai da ta Ιan kalli Humaira sannan
ta kalli Raihanar da murmushi.
"Ok zan yi
following dinki. Na ji dadin ganinki na kuma ji dadin Ιandanon snacks dinki duk
da daman na san Ιandanon. Akwai Ιan uwana Yaya Fadeel yana kawomana sosai. Ta
wajensa muka sanki."
Murjar ta fadi tana mai Ζurawa Humairar idanu don ta ga
yanayinta, so take dai ta samu tabbacin babu komai tsakaninsu. Raihana kuwa Ιan
jim ta yi a ranta tana tunanin wane Fadeel din? Kodai Fadeel wanda ta sani ne,
tabbas ya faΙamata yana odar snacks din Humaira ta hannun wata Antinsa. Ko shi
din wannan ke nufi? Idan kuma hakane ita wace ce a wajensa? Ta maida dubanta ga
Humaira don ta ga yanayinta, sai ta lura ko kadan ba ta sauya daga murmushin da
take yi ba, sai dai jin sunan kamar jikinta ya dan yi sanyi.
"Allah Sarki, na kuwa gode sosai." Abin da ta ce
kenan, wannan ya sa Murja kuma sakin jikinta sosai. Lallai wannan ba ita ce
Humairar da Fadeel ke mutuwar so ba, wannan da alama ba ta ma san da zamansa
ba. Dama ya ce ba shi ke yin odar da kansa ba. Yanzu kam ta yarda. Murja ba ita
ta bar gidan ba tsabar shagala da ta yi suna ta kwasar hira da su musamman
Raihana wacce ta fi su sanin mutane, kusan ma akwai Ζawayen Raihana na
makaranta wadanda duk Murjar ta san su hakan yasa hira ta musu dadi sai da Anti
Amarya ta kira wayarta tana faΙan jimawarta ba
shiri ta mike, su Humaira kuwa har mota suka raka ta da ledojin. Murja ta karΙi lambar Raihana da
zummar a dinga gaisawa duk da ta girme musu don za ta yi sa'ar Tasleem.
***
Sadda ta isa gidan
har yara sun fara zuwa Ζ΄an party. Ta karasa Anti Amarya na mata faΙan dalilin
jimawarta. Hakuri ta ba ta, ganin Fadeel a wurin wanda ke cin abinci a nutse
saman dinning ta ce.
"Wallahi hira muka sha da su Humaira, mutanen gidan
akwai kirki kar ki so kiga kamar kada a rabu."
Fadeel ya ji maganar har ransa, ya kuma ji dadi sosai. Bai
dai ko Ιago ya kalle ta ba. Yana ji dai tana ta ba Anti Amarya labari ita dai
ledojin ta hau buΙewa tana kallon snacks din. Koda ta dandana sun mata dadi
kwarai. Nan aka shiga sanya wa a takeaway ana rufewa, Kausar na nan ana aikin
da ita.
An gudanar da party cikin armashi, yaran Daddy da Mommy ne
suka cika gidan don Anti Amarya sam ba ta barin mara shi ya raΙe ta. Yawanci
duk abokan makarantar Abdul din ne sai ko makwaftansu. Hatta a yaran yan uwanta ba kowa ta gayyata ba.
***
Ζangaren Amare kuwa,
Amarya Futuha an ci amarcin sati daya cif ko Ζofar gida ba ta leΖa ba.
Hotunansu ita da mijinta kala-kala babu wanda ba ta Ιorawa a Instagram, shi
kansa Angon hakan na mishi dadi kwarai bai taΙa hanata ba. Tunda ta zo ba ta taΙa sanya Uwargida a idanunta ba, karshe ma sai
Ango Yakubu ke sanar da ita ta yi tafiya Saudia ita da yaranta. Futuha tun da ta ji haka duk sai ta matsa
mishi akan ita ma ya dace su tafi hutun honeymoon Dubai. Hakan ya yi mishi dari
bisa dari, a lokacin ji yake ko nawa ne zai iya kashewa Futuha saboda dadin
angoncin da yake kwasa. Ba Ιata lokaci aka soma shirin yi mata passport da
sauran abubuwan da ya kamata ma tafiya. Sai bayan kammaluwar komai sannan
washegari ta yi nufin zuwa gidansu ziyara da kuma sallama.
A Ιangaren Tasleem ma, babu laifi Hamza na iyakar kokarin
faranta mata, sun ci soyayyarsu yanda ya kamata, ba ta dora koda ruwan zafi
daga gidan iyayensa ake kawomusu abincin safe zuwa dare. Sai da ta yi sati cif
sannan suka kara shiga ta gaida Mahaifiyarsa da abokan zamanta su uku. Gidan
dai babban gida ne mai tarin yara da jikoki. A ranar har gidajen facalolinta
sai da ta shiga, wasu sun kata tarbar kirki yayinda wasu kallon tara saura suka
dinga yi mata. Haka tattara ta dawo gida.
A ranar da suka yi waya da Futuha take ba ta labarin
tafiyarsu Dubai hankalinta ya yi mugun tashi, ji tayi inama ita ce ta samu
wannan damar. Ciki-ciki ta yi mata murna, dama tana jin haushin hotunan da take
karo da su a media na Futuhar da mijinta yanda kowa ke santin kyawun da suka
yi. Futuha ta ce ta shirya za su zo har gida su yi mata sallama. Ba ta ma iya
amsawa da toh ba ta katse kiran gami da jan tsaki. Ya yi daidai da shigowar
Hamza falon, hannunsa rike da ledoji ya yi mata siyayyar kayan sanyi da kaza.
Har ya karaso kusa da ita ba ta san ya yi ba tsabar ta lula duniyar tunani. Sai
da ya ajiye ne ya dan zunguri kafaΙarta kadan. Ta dubeshi, murmushi tattausa ya
sakar mata, itama ta bishi da na yaΖe. Rungumo kafaΙarta ya yi.
"Tunanin me kike yi ne haka? Har na shigo da favourites
dinki amma ba ki lura ba?"
Ta kai duba ga ledojin dake ajiye, har gumin sanyi Ιaya
yake, sai ta ji ta kasa farin ciki da abin da ya ajiye din duk da cewa a baya
har so take ya kawo su ta dinga tsalle kenan tana rungumeshi. A yanzun kuwa ko Ιigon
annashuwa ba ta yi ba. Sai jikinsa ya yi sanyi, ya kamo yatsun hannunta.
"Wai me ya sauyamin ke haka? Ko bayan fita na kin yi
baΖi ne?"
Dama kiris take jira ai sai ta tunzura ta yakice hannunta.
"Me kake nufi?! Na yi baΖi sun zugani ko sun Ιatan
rai? Yan gidanmu kake nufin sun zo ko
Ζawayena?! Au zargina kake yi akan wani zai iya zuga ni akanka? Ai ba sai an
zuga ni b, ni mai zuga kaina ce!"
Gaba daya ya razana, ya yi jim yana kallonta, a iya saninsa
babu inda maganarsa ta kai nan. Me ya kawo batun zuga kuma ana zaune kalau? A
ina ya ce hakan?
"My Noor, me ya kawo zancen zuga? Ban gane inda
kalamanki suka dosa ba?"
Sai a sannan ta Ιan dawo hayyacinta. Ta ja guntun tsaki ta
zauna. Nan da nan kuma Hamza ya Ιan sauya fuska.
"No please, zan dauki komai amma ban da raini, ina maki
warning na farko da karshe, bana son tsaki. Kar ki kuma."
Ba ta ce komai ba face turo bakin da ta yi, sai ya ji ma
gaba daya ta Ιata masa rai kawai ya mike ya yi daki. Ta bishi da harara, ita ta
sani ko wannan motar tasa zai siyar ba zai ishe su su je Dubai har su kashe
kudade irin wanda Futuha zasu kashe ba. Ta san muddn Futuha ta yi wannan
tafiyar to fa kanta zai fasu, za ta Ζara jin wani girman kai har ma ta dinga yi
mata fi'ili iri-iri. Don haka hankalinta ya tashi, ga babu yadda ta iya, nata
mijin ba ta tunanin ma ya taΙa taka farfajiyar Airport balle ya shiga jirgi. Ta
ja tsaki karo na biyu. Madadin ta kwashe ledojin da ya kawo ta adana komai koda
ba lokacin za ta sha ba, kawai sai itama ta bar su anan ta shige nata dakin ba
ta ko bi ta kansa ba don har sannan zuciyarta zafi take yi, hassada mugun ciwo
ne.
***
Tun karfe goma
Humaira ta je kasuwa yin cefane bisa umarnin Mami wacce ke ta shirin tarbar
Futuha da za ta zo. Tana dawowa kicin kawai ta shiga ta soma shirin girki,
tuwon semovita miyar kuΙewa danya wanda ya ji nama da busassan kifi, shi
Futuhar ta ce tana muradi sai ko lemun kwakwa. Wuraren karfe Ιaya ta kammala
komainta jera a saman tire ta kai falon ta ajiye. Daga nan ta koma dakinsu. Ita
ko kusa ba ta wani zumuΙin ganin Futuhar kamar yanda su Ummita ke yi. Tun
dawowarsu daga makaranta jin ance tana hanyar zuwa suke faman rawar Ζafa. Ai
kuwa ko awa Ιaya cikakka ba su yi da dawowa ba sai ga mota direba ya kawo ta har farfajiyar gidan. Da gudu Raihana
ta fice tarbar yar uwarta, itama Ummita ta mara mata baya a nutse take tafiya.
Humaira sai ta ja guntun tsaki ta cigaba da danna wayarta tana ganin sabbin
likes da comment da sabon hotunan da ta dora na girke-girke suke samu. Ta
shagala sosai sai ji ta yi an warce wayar, ta juya da sauri. Raihana ce. Dariya
ta yi mata.
"Ki taso inji Mami ku gaisa da Futuha. Ashe Dubai za su
wuce da mijinta sati na sama."
Ta Ιan yi murmushi, ba ta fiye son kushe su a gaban Raihana
ba don haka ta taya murna a fili.
"Kai amma na mata murna, Allah ya kai su lafiya. Muje
toh. Bani wayata kuma."
Raihana ta mika mata suka yi dariya. A falon ta iske Futuha
zaune, masha Allah ta Ζara Ζiba da kyau, kumatunnan har wani kyalli suke yi.
Wani arnen leshi ne a jikinta fari da ruwan toka ya sha aikin stones sai faman
baza Ζamshi take yi, hira sosai take yi da Mami. Ζassim ma na zaune banda
Yassar da Dawud wadanda sula tafi Camp a can garin Jigawa. Humaira ta karaso ta
gaida ta, ta amsa mata tana yamutse fuska kaΙan daga nan ta maida hankali ga
uwarta su na cigaba da hira. Humaira wacce dama ta san a rina kawai sai ta mike
ta saci jiki ta koma daki, Ummita ta
mara mata baya.
"Ke kuwa daga gaisuwar sai ki taho?"
Harara ta dan watsa mata.
"Idan na zauna me zan mata? Goyata zan yi? Ai dai kinga
yanayin amsar gaisuwar da ta yimin ko? Toh ni kuwa marar zuciyar ina ce da zan
tsaya?"
Ajiyar zuciya Ummita ta yi.
"Allah ya kyauta, kinsan Allah na yi zaton aure zai
sauya su, amma naga har yanzu da sauransu."
TaΙe baki Humaira ta yi ta ce.
"Toh yaushe ma aka yi daren? Ke ta dai samu duniya ne
kawai shiyasa abinta ya Ζara gaba. Nifa kinsan ba abin da ke ban mamaki face
irin yadda matarnan ba ta yiwa kanta faΙan ta nutsu ba take faman Ιora
hotunanta a media. Shi ma mijinnata soloΙiyo da ya biyemata."
Ummita ta kama baki har da Ιan waigawa ta ga ko babu wani a
kusa da ya ji kalamin Humaira.
"Kinga ki rufamana asiri. Mutum ba shi ya ga zai iya
ba? Kar ki manta har da shi din Ogan nata ake wannan taΙargazar kinga kuwa abu
nasu maganin a kwaΙe su. Wayewar yanzu ce ta shirme ta zo da haka."
Dariya Humaira ta yi.
"Kenan kema haka za ki yi da Sahabinki ko?"
Duka ta kai mata a cinya.
"Allah ya sauwaΖe, mu aurenmu ko party ba zamu yi ba,
walima kawai a cikin gida ta isa. Albarkar auren muke nema. Hum, nifa yanzu duk
ya dameni akan zai turo a sanya rana kafin nan da shekara idan mun kammala nayi
Candy a yi auren. Wallahi kwanakin nan duk akan hakan muke ta rikici. Na rasa
yanda zan Ιullo masa."
Humaira ta mike zaune sosai. A duniya ta tsani ta ga Ummita
cikin damuwa ko na sakan, don haka ta ce.
"To me kike jira? Me zai hana ki ba shi wannan damar?
Kina sonsa yana sonki fa. Kuma sa rana ba shi ne auren ba, don Allah ki yi
shawara da Mami tunda kinga ta san da zamansa, na tabbata za ta goyi da bayan
ya turo."
Ummita ta zubamata idanu ta yi shiru cike da damuwa, ga
mamakin Humaira kuma sai kawai ta ga hawaye sun soma zuba daga kwayar idanunta.
"Lafiya? A maganata akwai wacce ta maki zafi? Kiyi
hakuri don Allah kinji?"
Girgiza kai Ummita ta yi,
"Ko Ιaya Humaira, ke ce dalilin da yasa na kasa ba
Sahabi damar turo iyayensa. Wallahi bana jin dadin mafarkaina a kanki kwanakin
nan. Humaira na damu da rashin bada Ζofa ga kowane saurayi ya nemi aurenki da
kike yi. Ba na so na yi aure na bar ki a wannan halin. Gaba daya na damu."
Shiru Humaira ta yi, toh ita da kamar abin yana damunta
kamar kuma ba ta damu ba. Ta ma kasa fahimtar komai sai kawai ta dubi Ummita a
sanyaye.
"Kin manta ke ce me nusar da ni idan na Ιata? Ke ce me
Ζarfafamin gwuiwa akan imani da Allah a irin wadannan lokutan? Toh ki sani, har
ga Allah ba na jin son kowane namijin ba balle na ji son auren a raina. Hakan
ba yana nufin wata matsalar ba, ki kaddara lokaci ne, duk sadda na ji son wani
a raina, watakila..."
Sai kuma ta ma rasa me za ta ce, kawai sai ta sunkuyar da
kai ta riΖe hannun Ummita cikin nata. Karon farko da ta ji tana hawaye, hawaye
mai dalili ba wanda ta saba yi a irin gaΙar nan babu dalilin ba. Ummita sai ta
ji tausayinta ya lulluΙe ta, Humaira ai itama da zuciya a kirjinta. Dole akwai
abin da ke damunta amma ba ta faΙa, ba ta magana sai dai ta yi shiru idan sun
taso da zance ta maida su wasu cali cali.
"Ki tayani addu'a Ummita, ina da damuwa amma ban gama
gane kan damuwar ba. Ina da abin faΙi, amma zuciyata na kwaΙa ta a koyaushe
akan bai kai abin magana ba nayi shiru kawai. Na rasa meke damuna, idan na ce
zan zurfafa tunani sai jikina ya hau rawa, kaina ya hau sarawa. Watakila iyakar
abin da zan iya faΙa kenan. Nidai ki dinga sanya ni a addu'a."
Ummita ta Ιan rungumeta suna kuka. Kowannensu da kalar
tunaninsa, dakyar suka rarrashi junansu suka share hawayen.
Sai kuma Humaira ta cigaba da karfafa mata gwuiwa akan ta
bari Sahabi ya fito a yi magana. Ta kara da fadin.
"Kinga itama Raihana zan ce ta amince ta bar Imran ya
turo. Shikenan sai ku bar min gida na huta."
Ummita ta harareta, ita kuma ta yi dariya tana kokarin danne
radadin ciwon kan da take ji gudun kar ta kefa Ummita a wata sabuwar damuwar.
Koda Ummita ta fita don amsa kiran Mami wacce ta turo Muhsin, sai ta zame ta
kwanta ta runtse idanu tana tauna maganganun da suka yi da Ummitar, hannuwanta
riΖe da kan da ke faman sara mata. Tana nan kwance har bacci ya sure ta,
Raihana ta zo ta tashe ta akan ta je Mami na kira. Ta ci sa'a zuwa lokacin ya
rage ciwon, don haka dankwalinta da ya zame ta maida ya rufe kan ta fita. Anan
fa Mamin ta mata umarnin ta shirya za ta bi Futuha don ta taimaka mata da girki
abokan mijinta za su je gidan nan zuwa jibi. Kamar ta cewa Mamin a bari mana
sai jibin ta je ta dawo, amma ba ta son jan musu da ita kawai sai ta ce toh.
Ranta na zafi haka ta shirya ta bi Futuha suka tafi. Tana ji Futuhar na yiwa
Tasleem waya wai gatanan a hanyar gidanta, ita dai ba ta ce mata uffan ba sai
kallon window da take yi zuciyarta na zafi, wani sashi na zuciyar na kokarin ce
mata Mami ba ta kyauta mata ba yayinda wani gefen ke kwaΙarta yana nusar da ita
irin kirki da mutuncin Mamin. Bai kyautu ta munana mata zato ba. Da haka suka
karasa gidan Tasleem.
***
A yau Murja ta yi
niyyar zuwa sashin Fadeel don ta rantse ko ta yaya sai ya saurareta ya ba ta
damar amayar da abin da ke ranta ido da ido. Kwanakinnan ko bacci kwakkwara ba
ta iya yi tsabar so da tunaninsa da ke neman zautar da ita, wannan ya sa ta
zuri takalmanta kawai ganin an yi Magrib tana kuma da tabbacin yana nan ta nufi
sashinsa.
Yana zaune ya kafe
manyan frames guda biyu da aka yi mishi na hoton Humaira da idanu yana kallo.
Ta yi kyau matuka, daya tana tsaye ne a farfajiyar Manal Event Centre ranar
bikin su Futuha, dayan kuwa wanda ta dauka da sallah ne ba ta san ma an yi
hoton ba ta rike kafaΙar Ummita tana dariya mai bayyana wushiryarta. Ta yi kyau
ainun, masifar son da yake yiwa hotunan ne ya sanya aka wanko da zummar zai
adana duk radda suka yi aure ya kafe su a Ιakin baccinsa. Uzurin bandaki ya
kama shi, ya mike ya shige Ζuryar dakin don kama ruwa. Daidai lokacin Murja ta
hau kwankwasa Ζofar dakin, tana ji kamar ta tura kanta ciki ko ba izninsa. A
yau ta kai maΖura a so da kauna da begen ganinsa.
Ganin Fadeel ba shi da niyyar buΙewa sai kawai ta murΙa ta
tura kanta falon. Babu kowa, ta Ιaga Ζafa da niyyar bin bayansa zuwa Ιakin, sai
wata zuciyar ta kwaΙe ta. Ba ta son Ιata rawarta da tsalle, har ta juya za ta
bar falon idanunta ya sauka saman hotunan dake ajiye. Jikinta har rawa yake yi
ta karasa ta Ιauka. Ji ta yi kirjinta ya yi wani irin bugu da karfi,
numfashinta kuwa dakyar ta iya jawo shi ta furzar. Ita ce! Humaira mai
Deelsha's Delicacies, ita ce dai masoyiyar da Fadeel ke so. Kafin ka ce me idanuwan
Murja sun soma zubar da hawaye. MaΖoΖon baΖin ciki da tsantsar kishi suka
tokare kirji da maΖoshinta. Ta tuna ko Ιazun sai da suka gaisa ta waya da ita,
ashe ba ta sani ba da rival dinta take mu'amala? Ji ta yi kwakwalwarta na
rayamata kawai ta tarwatsa hoton a Ζasa idan ya so komai ta fanjama fanjam!
Aikuwa ta Ιaga a zuciye da wannan niyyar amma ba zato ta ji tsawar Fadeel a
kanta. Ya Ζaraso ya fisge hoton a hannunta, murya a Ιage ya ce.
"Me ya kawoki Ιakina?! Uban waye ya baki iznin kutsowa
ba tare da sanina ba?"
Kamar ta ce mishi Ubanka ne amma ta danne, kishi dai bala'i
ne. Ta kasa samun nutsuwa, ta kai hannu ta dafe kai har lokacin kuka take, ko
kaΙan tsawar Fadeel bai razanar da ita ba. Wannan kaΙan ne akan yadda take jin
raΙaΙin azabar kishin Humaira a zuciyarta. Dakyar ta iya tattaro kuzarin da ya
yi mata saura ta soma magana.
"Dama akan wannan yarinyar ka ke wulaΖanta soyayyata?
Yaya Fadeel ina sonka ka sani amma ka ke nuna kamar ba ka san da zamana ba.
Meyasa? Da me ta fi ni? Me za ta nunamin? Wallahi Yaya Fadeel muddin ka aureni
zan maka fiye da abin da kake tunanin samu daga wannan yarinyar."
Ransa ya Ιaci ainun.
"Ke a naki tunanin koda ace auren zan yi don kyau ko
suea kin kai na aureki?! Toh ke ba komai ba don ba ki da suffar da zan
gani har naji kwaΙayin aurenki. Daga yau ina maki gargaΙi ki fita harkata, na
rantse maki duk sadda na Ζara ganin Ζafafunki a nan sai na ΙaΙΙallaki. Get
out!!"
Ta razana sosai, ga baΖaΖen maganganun da ya fesamata ga
kuma tsawa, ta kalleshi tana jin ranta na suya sannan ta kara kai duba ga hoton
Humaira kafin ta juya a guje ta fice daga Ιakin. Fadeel ya yi tsaki ya zaune
yana jin zuciyarsa na zugi. Da ace yana da ikon fitar da yarinyar daga gidannan
da tuni ya aiwatar.
***
Tasleem ta buΙe Ζofar kyauren, suka shigo.
Humaira ta bi ta da kallo, ba laifi itama ta yi kyau ta kara haske. Ta
rungume Futuha suna murnar ganin juna, ba ta ko kalli Humaira ba suka shiga
ciki zuwa Ιaki suka bar Humaira a falo zaman jira.
"Shegiya, haka gidanki ya yi kyau?"
Cewar Futuha, Tasleem ta ji zancen kamar zagi hakan ya sa ta
ja tsaki.
"Ba dai baΖa kike faΙamin ba ko? Bayan naki gidan an ce
ya kere nawa nesa ba kusa ba."
Ta yi dariya.
"Abar wannan zancen, ya ne? Kin ji labarin tafiyarmu
ko? Kai Tasleem burina zai cika zan shiga jirgi nayi selfie, na kuma ga wurare
da dama irin yadda su Ζ³ar Snow suke gani su na hoto suna mana yanga."
Baki buΙe Tasleem ke kallonta cike da Ιumbin mamaki.
"Futuha, anya kina cikin hayyacinki kuwa? Ζ³ar Snow dai
da ta yi maki baΖin Ζazafi ita kike farin cikin za ki zarta? Wallahi ina rabaki
da shiga harkar Ζ΄an Tiktok, lallai idan kika sa kanki cikinsu sai kin yi kukan
da na sani fiye da na baya."
Futuha tun da Tasleem ta soma magana take faman doka
murmushi, ta ba wa ranta cewa kawai baΖin ciki ne ke cin Tasleem saboda a
duniya ta fi ta burin hawa jirgi da fita Ζasar waje sai kuma ya kasance ita ce
ta samu wannan damar, ta ba kanta lallai Tasleem dai da biyu take wannan
sabuwar nasihar.
"Ζ³ar uwa kenan, ki bar wanda ya samu duniya ya ci
abinsa da tsinke, ai komai da kike gani lokaci ne. Wasu ma damar da suka jima
su na burinta kenan amma ba su samu ba. Mu kuwa tun da Allah ya kashe ya ba mu
kinga kenan sai mu dama kununmu yadda muka ga dama."
Tasleem ta yi dariyar yaΖe.
"Ai shikenan, Allah dai ya kaiku lafiya. Nidai please
and please ki yo min tsarabar dogayen riguna."
Futuha ta yi farr da idanu tana dariyar itama.
"Kar ki samu damuwa Ζ΄ar uwa, ai ke tawa ce."
A falon kuwa, Humaira na nan zaune tana karewa gidan kallo
aka yi sallama aka shigo. Ta Ιaga kai, wata budurwa ce da ba ta wuce sa'arta ba
ta shigo kai tsaye ta nemi wuri ta zauna suka gaisa fuska a sake.
"Anti Tasleem na nan?"
Humaira ta amsa da eh.
"Ok, bari na jira fitowarta a nan. Kema Ζanwarta ce
ko? Na tuna fuskarku da biki, ku uku cikin shiga iri Ιaya aka ce
sisters dinta ne."
Humaira ta Ιan yi murmushi.
"Eh, Ζanwarta ce."
"Ok, amma ba Uwa Ιaya ba? Naga su kamar buzaye
ne."
Humaira dai ta Ιan yi jim, ta rasa wannan maganganun da ake
mata na babu gaira babu dalili. Sai a nan kuma ba ta amsa ba. Budurwar ganin
haka ta sauya darasin.
"Allah ba Ζaramin so Yaya ke yiwa Anti Tasleem ba.
Akwai wata cousin sister din mu da ke masifar sonsa amma ko kaΙan ya ce shi ba
ya yinta, kuma fa ..."
Sauran zancen ya maΖale a fatar bakinta sakamakon fitowar
Yayannata daga Ιaki. Humaira ta gaida shi, ya gane fuskarta sarai don takan
fito kawo masa abin motsa baki lokacin da yake zuwa zance wajen Tasleem. Ya
amsa gaisuwar fuska a sake, daidai lokacin kuma su Tasleem suka shigo falon.
Nan aka hau sabuwar gaisuwa da Futuha anan take sanar da shi batun tafiyarsu
Dubai da mijinta. Ya yi mata murna kwarai. Daga bisani suka yi sallama har
bakin mota suka raka su, sai bayan sun tafi ne suka koma ciki. Har lokacin
Hamza bai sakarwa Tasleem ba sakamakon haushinta da yake ji na irin kalaman da
ta yaΙa masa. Ita kuwa budurwar Ζanwar tasa mai suna Fauziyya ba wani jimawa ta
yi ba, daman shigowar don ta ganewa Ζ΄ar uwarta Ramlat irin zaman da ke gudana a
gidan Hamza wanda har gobe yana nan daram a ranta. Akwai kuma da yawa cikin yan
uwansa masu taya ta kishin Tasleem. Ciki kuwa har da Fauziyya.
***
Daki guda na saukar
baΖi Futuha ta ba Humaira, nan ta zauna. Madaidaicin gado ne a Ιakin sai kafet
a shimfide da bandaki a ciki. Ya yi Ζ΄ar Ζura kaΙan ba ta damu a haka ta kakkaΙe bayan ta idar da sallah ta
yi kwanciyarta tana danna waya. Tana nan kusan awanni biyu wuraren Ζarfe tara
na dare ta ji shigowar mota. Ba jimawa kuma wayarta ta Ιau Ζara, Futuha ce. Ta Ιaga
da sallama, ba ta ko amsa ba ta ba ta umarnin ta zo falo ta gaida Maigidan.
Kashe kiran ta yi ta mike tana jan guntun tsaki. Mace ko sanin darajar sallama
ba ta yi ba, an yi amma madadin ta amsa sai ta yi share. Hijabi ta sanya ta
fito, su na nan falon dake saman, yana zaune ita kuwa tana saman cinyarsa tana
zuba ruwan shagwaΙa. Sallamar da ta yi har aka amsa bai sa sun sauya a yanayin
da suke ba, Humaira sai ta sunkuyar da kanta domin ba Ζaramin kunya suka ba ta
ba. Wannan wace iriyar fitsara ce? Koda dai dama ta riga da ta san wace ce
Futuha, matar dake tsayuwa gaban waya ta tiΖi rawa ta Ιora a midiya, ai kuwa ba
za ta ji kunyar idanun kowa ba idan tana tare da mijinta. Haka Humaira ta
ayyana a ranta.
"Kika wani tsaya daga Ζofa, Malama ki Ζaraso ki gaida
shi."
Muryar kamar ba ta Futuha ba don gaba Ιaya ta wani ΖanΖantar
da ita irin yadda ta saba idan tana waya da samari a baya. Humaira ta karasa
shigowa ba tare da ta kallesu ba ta gaida Alhaji Yakubu, ya amsa murya a sake.
Daga haka ta miΖe za ta yi ciki, Futuha ta dakatar da ita ta hanyar nuna mata
wata leda akan ta Ιauka ta ci. Ta dauka ba musu ta fice daki. Ita dai mamaki
kawai take yi na irin wannan wayewar zamanin.
Tana shiga ta buΙe,
shawarma ce a naΙe a paper sai ko gashin kaza rabi, ta cinye tas don dama
yunwar take ji ta wanke hannu da baki ta dawo ta nemi makwanci.
***
Kwanakinta a gidan
Futuha babu abin da take yi sai Ιirkar aiki, akwai Ζ΄ar dattijuwar dake zuwan
yini tana tafiya. Takan kama ayyukan gyaran Ζasa, ita kuwa Humaira ta gyara
saman tas, duk wata dauΙa da Futuha ta bari tun zuwanta babu gyara kaca-kaca
sai da ta dawo yana kyalli. Ga girkuna masu dadi da ta ke yi musu safe da
yamma, Futuhar da ba ta Ιan sakarwa Humaira fuska, tsabar jin daΙin yadda ta ke
mata bauta sai ga shi ta soma saki, babban Ζudurinta kuma bai wuce idan sun
dawo daga tafiyar da zasu yi ba ta yi dabarar da Humairar za ta dawo
ΖarΖashinta gaba Ιaya.
Ana gobe su Futuha
za su tafi ne, Humaira ta fito ta zagaye can bayan Ιakunan inda anan ne aka yi
wasu shuke-shuke masu ban sha'awa, a lokacin babu koda a Ιangaren Futuhar, Baba
Furera ta wuce gida, Futuha kuwa an tafi gyaran gashi da jan Ζunshi. Hakan yasa
kaΙaici ya yi mata yawa, ga dai wuta nan daga safe har dare amma ta gaji da
kallon balle kuma danna wayar. Wannan ne dalilin zagayawarta baya tana kallon
shukokin masu burgewa da Ιaukar ido. Tana nan tsaye tana murmushi tana shafar
su gami da shinshinar Ζamshin da ke jikinsu, ta kai duba ga sararin samaniya
yadda hadari ya yiwa garin Ζawanya, a hankali ta lumshe idanu saboda jin daΙin
yanayin. Sai dai kuma lokaci guda kamar wacce aka mintsila ta bude idanuwanta
tarr jin kukan jariri da ke tashi sosai. Ta kai duba ga inda sautin ke fita har
Ζirjinta na bugu da sauri-sauri. Sashin dai da aka ce na uwargida ne, daga nan
ta dinga jin kukan na tashi. Cikin sauri da gudu-gudu ta bar bayan ta dawo
bangaren Futuha, daidai nan suka yi kiciΙus da mai ba shuka ruwa. Ta dube shi,
ganin yadda take faman haki ya sanya shi
tambayar ko lafiya. Da yatsa ta yi mishi nuni da hanyar Ιangaren Uwargidan da
ake kira Hajiya Saratu.
"Me aka yi a
wurin?"
Ta haΙiyi miyau.
"Da mutane a ciki ne?"
Sai tambayar ta ba shi mamaki.
"Hala ke baΖuwa ce? Ai Ιangaren Hajiya ne, tana nan. Ko
wata biyu ba ta yi da haihuwa ba."
Sai hankalin Humaira ya Ιan kwanta amma kuma sai ta hau wani
sabon mamaki da al'ajabin. Don haka ta kuma dubansa ta ce.
"Dama ta dawo daga tafiyar da ta yi ne?"
Ya yi Ζ΄ar dariya.
"Ko kusa, babu inda ta je tana nan. Ai da yake ba ta
fiye fita ta wannan Ζofar ba, akwai Ζofa ta baya, ta fi fita ta can idan ta
tashi zuwa unguwa. Kuma gaskiya dai ni zan iya cewa tun ma da ta haihu ba na
tunanin na ji ance ta fita. Koda dai ba ganewa ake yi ba tunda Hajiya motar
haya take shiga."
Ya Ζarashe da wani irin jimami, har ya buΙe baki zai Ζara
magana sai kuma ya girgiza kai kawai ya fice. Humaira ta bishi da idanu tana
mai cike da al'ajabi. Idan maganganunsa gaskiya ne? Toh me Alhaji Yakubu yake
nufi da Ιoyewa? Ita dai ta ji Futuha ta ce Uwargidansa ba ta nan su na Dubai da
yaranta. Toh idan hakane su ne a gidan, meyasa ko da wasa ba a ganin gilmawar
yaranta tunda dai ai yaro ba zai yarda da rayuwar Ζulle ba?
Amsoshi ne da ba ta da amsar su kawai sai ta ja Ζafafunta da
suka yi wani irin sanyi ya bar wurin.
Humaira ta kama bakinta koda wasa ba ta sanar da Futuha
komai ba, ba ta ga dalilin sanar da ita abin da bai kamata ta ji daga bakinta
ba wannan ya sa ta bar abin a cikinta. Washegari da misalin Ζarfe biyun rana
sai ga su Raihana a gidan sun zo rakiya Airport, daga nan direba zai mayar da
su gida gaba Ιaya.
Jirgin dare ne wannan ya sa sai bayan magriba suka
hau shirin tafiya, Humaira ta tattara kaf kayanta, dama ta gaji da gidan babban
burinta shi ne kawai ta koma cikin Ζ΄an uwanta. Sakewar da Futuha ta yi da ita
bai sa ta iya sakin jikinta ba don ba ta saba da shi ba, ta fi ganewa rayuwarsu
ta baya yadda suke hantararta a abu Ζalilan amma sam zuciyarta ba ta amince da
wannan sauyin ba.
Ζarfe goma jirginsu ya tashi, su kuma aka kai su gida.
Humaira ranar kamar an tsoma ta a aljanna, farin ciki biyu ya haΙe mata, na
farko bai wuce dawowarta gida ba daga zaman uΖuba da bautar da ta ke yi a gidan
Futuha, na biyu kuwa jin daddaΙan labari daga bakin Raihana cewar iyayen Sahabi
nan da kwanaki biyu za su zo tambayar auren Ummita. Ranar dai bacci Ιarawo ne
ya sace su don raba dare suka yi ana hira.
***
Anna ta dubi Mami ranta a tsananin Ιace ta ce.
"Ke kam da a asibiti na haihu zan iya rantsuwa sauyamin
ke a ka yi wannan ba jinina ba ce. Ni dai kaf zuri'armu babu macen da za ta
aikata wanan abi da kike aikatawa na rashin sanin ciwon kai da kuma rashin
zuciya. Wannan rawar Ζafa da murna da kike yi ko kuΙin auren Raihana aka kawo
sai haka."
Tana kai wa nan ta ja tsaki, Mami ta yi Ιan murmushi. Kawo
kuΙin gaisuwar iyaye da sanya rana da aka yi na Ummita a yau ne ya sosa zuciyar
Anna take wannan zantukan. Ita idan irin hakan ma abu na farin ciki ya afku ga
Humaira ko Ummita har ba ta kaunar ya zo kunnen Anna saboda irin waΙannan
bakaken kalaman da ba ta haΖura ta bar wa cikinta sainta furzar. Kamar ko
yaushe a kwanakin nan, wannan karon ma Mamin shiru ta yi ba ta ce uffan ba.
Itama Annar don kanta ta gaji ta bar zancen. Ta sanyo wani batun bayan ta kora
ruwa a cikinta.
"Af, yar uwarki tana nan tafe Ζarshen watan nan."
Cike da mamaki Mamin ta dubi Anna ta ce.
"Jannat kuma? Me zai kawo ta nan kusa alhalin yara ba
hutu suka yi ba?"
"Toh kina baΖin ciki da zuwan nata ne?"
Jin haka da sauri Mami ta ce.
"Ko Ιaya, Allah ya huci zuciyarki. Allah ya kawo ta
lafiya."
Anna ta amsa da amin, ganin tana neman Ιora maganar Ιazu sai
kawai Mami ta miΖe tana mai ba ta uzurin zuwa wurin mijinta. Yamutse fuska
kawai Anna ta yi ba tare da ta ce komai ba.
***
Alhaji ne zaune
saman darduma a barandarsa yana latsa waya, isowar Fadeel ne ya sanya shi ajiye
wayar ya mayar da hankali garesa. Bayan amsa gaisuwarsa ya gangara kan batun da
yake son yi.
"Babban dalilin kiranka bai wuce kan maganar aure ba.
Lokaci ya yi da za ka tsaida hankalinka wuri guda ka nemawa kanka abokiyar
rayuwa. Kana gani dai ga Ιan uwanka nan har an soma batun zuwa gaisuwa da roΖon
iri. Toh an kai lokacin da zubamaka idanun da aka yi ya kamata ace ya zo
Ζarshe, ga baffanninka nan a ganinsu har da laifina a Ζin matsa maka da zancen.
Har cewa suka yi idan babu dama ka je can gida ka zaΙa cikin Ζannenka wacce ku
ka daidaita sai a yi magana. Rashin ba su goyon baya akan haka ba yana nufin na
amince da zaman naka hakanan ba Fadeel. Shekaruna gaba suke Ζara yi ba wai baya
ba, lokacin Ζure mana yake Ζara yi. Alhamdulillah ka fara gini, koda ace bai yi
nisa ba, ina da tabbacin nan da shekara dai ka haΙa komai. Kai yanzu Ιan uwanka
ba abin koyi ne gareka ba? Ka gwammace kana ji kana gani ya yi aure ya bar ka
nan zaune? Har zuwa yanzu babu wacce ka tsayar?"
Fadeel ya Ζara sunkuyar da kansa, ya sani dama tun da har
zancen auren Ibb ya tashi, toh fa Daddy da Alhaji ba za su Ιaga masa Ζafa ba.
Yana kuma da tabbacin yadda Alhai ya yi mishi magana, to fa shi ma Daddy zai Ιora
da nasa bayan kwanaki.
"Ba ka ji
ne?"
Ya Ιago ya Ιan ja numfashi, babu amfanin Ιoye-Ιoye, babu
kuma alfanun faΙin gaskiyar da za ta jaza masa rabuwar da bai shirya ba da
Humaira. Yana tsoron ya kasance idan ya zayyana komai yadda yake tafiya a
yanzu, ran Alhajinsa ya Ιaci ya nemi ya fita a hanyar Humaira, wannan ne
dalilin da ya sanya shi yiwa zancen kwaskwarima.
"Ka yi hakuri Alhaji, ba wai babu wacce na tsayar ba
ne. Akwai, sai dai yarinyar nan da watanni bakwai zuwa takwas za ta kammala
makarantar da take zuwa, ta kuma roΖe ni na ba ta dama har su kammala. Wannan
shi ne dalilin da ya hana ni gabatar da ita a wajenku. Ina neman Ζarin lokaci
zuwa sannan, idan Allah ya yarda ba zan ba ku kunya ba."
Alhaji ya Ιan yi jim, ba haka ya so ji ba, ya so ace kawai
Fadeel din ya ba da damar a nemi auren a haΙa da na Ιan uwansa (Ibb) amma hakan
ma ya ji daΙi tunda dai akwai wacce yake so. Don haka sai ya Ιan saki fuska.
"Shikenan, su
iyayenta sun sani cewa kana neman auren Ιiyarsu?"
Ya ji gabansa ya faΙi, anan kam ba ya jin zai iya Ιoyewa don
haka ya girgiza kai ya furta kalmar a'a.
Murmushin manya Alhaji ya yi.
"Fadeel kenan, to kai ban da ma abinka, yanzu idan aka
tashi mahaifin yarinyar ya aurar da ita ga wani sai ka ce ya yi maka rashin
adalci ko?Idan ba kai ba, ina aka taΙa wannan wautar? Kana son yarinya amma ka
kasa gabatar da kanka wajen iyayenta? A zatonka sun san da zamanka ne kawai
saboda kana zuwa hira wurin Ιiyarsu? Me zai hana mu ka bamu damar tura wa
gidannasu a san da zancenka?"
Ya Ιan sosa Ζeya kaΙan, inama hakan abu ne mai sauki, inama
kuma idan an aikata ba zai ga bore daga Humaira ba wadda yana da tabbacin a
yanda take gudunsa za ta iya cewa ta fasa auren ma baki Ιaya, ai ba don haka ba
da gudu zai yi na'am da shawarar Alhaji. Sai dai kuma ya sani, ba abu ne mai
sauΖi ba.
"Ayi hakuri zuwa lokacin da na faΙa. Ni kuma zan yi
kokarin samun mahaifinta mu gaisa."
Alhaji ya ji abin wani iri, kamar ya yi magana sai dai ya
fasa. Can kuma sai ya Ιige da nasiha akan kar ya biyewa soyayyar shirme da ake
yi yanzu tsakanin matasa na wannan zamani. Abin har ya so ba Fadeel dariya don
shi kam ya lura kamar ma Alhajin tunaninsa wani wuri daban ya tafi. Da wannan
suka rufe babin zancen suka hau tattaunawa akan Hannatu dake shirin zuwa Kano
don ganin mahaifinnasu da ta kwashi lokaci ba su sanya juna a ido ba.
***
Anti Amarya ta shiga
har Ιakin Murja dake kwance tana juyi, tsayawa ta yi gaban gadon tana Ζaremata
kallo rai a kuntace sai kuma ta ja mugun tsaki ta soma magana tana ji tamkar ta
shaΖo ta.
"Aikin wofi kike
yi fa Murja, na faΙamaki ke za ki wahala a banza muddin ki ka ce ba za ki
kokarta ki Ιoye kishinki a kan Humaira ba a gaban Fadeel. Ke ba ma kishin ba,
hatta da son da ace za ki yi hakurin dannewa babu abin da ba za ki iya cimmawa
ba. Ke an faΙamaki koda ace asirin za ki yi masa zai ci shi idan ba ki kasance
gwanar kissa ba? Ai komai Ιan dabara ne. Yanzu kiga, daga ganin hoto gaba Ιaya
kin susuce har abinci sai kin yi dagaske kike iya ci? Yanzu idan kuma ace
zancen auren kika ji ya za ki yi da ranki?"
Murja ta miΖe zaune, gaba Ιaya idanunta sun kumbura. Ta dafe
kirjinta.
"Wallahi Anti ji nake yi kamar kirjina zai fashe, Anti
ban san haka kishi yake da tsananin zafi ba sai akan Fadeel. Na rantse a yadda nake jin zuciyata
zan iya sa wuΖa na tsire Humaira da ranta muddin aka wayi gari ta kasance matar
Fadeel balle kuma har abada hakan ba za ta afku ba idan har ina numfashi a
doron Ζasa."
Kausar dake bakin Ζofa wacce ta yi niyyar shigowa don duba
lafiyar Murjar da ta ji Anti Amarya na cewa ba ta da lafiya, kawai sai ta ja
baya ta juya jin maganganun da suke fitowa daga bakin Murja, iyakar abinda ta
ji kenan, koda ace ma Anti Amarya ta yi magana kafin nan toh ita kam Allah bai
nufe ta da ji ba. Ita gaba Ιaya gidan ma ya ishe ta, Fu'ad wanda ya je Abuja da
niyyar kwanaki uku, sai gashinan har ya cinye satin ya Ζara shiga wani satin.
Burinta kawai ta bar gidan ta koma nasu, ita sam ba ta gane rayuwar da ake
gudanarwa a gidan ba, Anti Amarya dai lamarinta kamar gaske kuma wasu lokutan
takan ji kamar kawai wasan kwaikwayo ne. Ga Murja a gefe wacce kallo dubu idan
za su yi wa juna a rana babu abin da take samu a wajenta sai harara. Su Khadija
ne abokan hirarta sai kuwa wayarta, sannan Fadeel wanda ba kasafai yake shigowa
falon ba. Hakan yasa duk ta ke jin ta a takure.
A daki kuwa, motsin mutum ne ya sa Anti Amarya saurin
fitowa, bayan Kausar ta hango lokacin da take barin wurin, ta dawo ciki ta rufe
Ζofar. A fusace ta kalli Murja.
"Kin gani ko?
Zai wahala idan Kausar ba ta ji abin da muke tattaunawa a kai ba. DaΙina da ke
ba kya iya Ιoye abin da ke ranki ko na sakanni. Kin san ba mu kaΙai ke zaune a
gidan ba amma ki yi ta faman suΙul da baka. Mtsw, don Allah ji yadda kika maida
kanki, babu wanka balle kwalliya, akan Ιa namiji kamar wacce ba ta yi karatu ba
kina son ki zautar da kanki. Ke idan da ace ni ce ke, ai wannan ne lokacin da
zan soma shigewa Humaira da hujja. Ki raΙe su, ki zama tamkar yar uwarsu, ki
yawaita kai musu ziyara daga haka sai ki dinga gano sirrinta. Ke daga haka ma
idan ma wani aikin ne sai kiga mun ci nasarar yi mata a sauΖaΖe mun farraΖa
tsakaninsu. Ζangaren Fadeel ki kwantar da kai ki ba shi haΖuri ki nuna masa
cewa ke fa kin haΖura da shi tunda ba ya kaunarki. Ki yi iyakar ΖoΖarinki wajen
ganin kin danne abin da ke zuciyarki a kansa, ki rage shige masa. Ladabi, rage
kulashi da ma ba shi girma matsayin yayanki shi zai sa ki shawo kansa ya sakar
maki fuska kamar yadda ku ke rayuwa a baya. Ki nuna masa kin fi shi so da
kaunar Humaira, ki koΙa ta a gabansa da ma duk sauran kissa da kisisina na
mata, wannan kaΙai idan ki ka aikata babu mai zarginki koda nan gaba wani mugun
abin da za a yi ya kawo Ζarshen soyayyar Fadeel din da Humairar. Komai fa Ιan
siyasa ne."
Murja wacce a farko taje jingine da gado tana dafe da ciki
tsabar horon yunwar da take yi wa kanta, ba ta san ya aka yi ba ta miΖe zaune
sosai tana Ζara baza kunne ga Antin dake magana Ζasa-Ζasa kamar me raΙa duk
domin tsaro da kuma gudun kar wani ya ji su. Anti Amarya na kawo wa Ζarshe ta
rungume ta su na dariya, har ta Ιan ji Ζwari a jikinta, sai kuma ta Ιan yi
sanyi.
"Amma Anti anya
zan iya danne son Fadeel?"
Harararta Antin ta yi.
"Da ya kike rayuwa babu soyayyar tasa? Hakanan za ki
danne muddin kina son ki cimma manufarki. Ku
yaran yanzu babu kissa ba dabara, sai soyayyar kawai. Toh abinci ma ki
dafa shi zallarsa babu wasu sinadaran da zai Ζamsasa shi ya Ζara mishi ΙanΙano
ai lami za a ci. Balle kuma soyayya, ai idan kana da kyau ka Ζara da wanka. Ba
kashe Humaira ba, ko tsire ta za ki yi da wuΖa a gabansa, wataran ba zai ko
kalla ba balle ya ji abin a ransa. Ki soma wannan ni kuma na san inda zan je a
yi maki aikin da zuciyar Fadeel din zai huce ya soma sanyi a lamarinki. A
hankali za ki mallake shi."
Dariya Murja ta yi cike da jin dadi da annashuwa. Ta lumshe
idanu tana jin wani sanyi a ruhinta, amma fa alΖawari ta Ιaukarwa kanta sai ta ΙanΙanawa
Humaira azabar da sai ta gwammace kiΙi
da karatu. Ba don tsoron kar ta kashe ta da hannunta itama a kashe ta ba, ai da
tun a ranar da ta san Fadeel ita yake so sai ta je har gidansu ta shaΖe wuyanta
har lahira.
Da wannan Ζarfafa
gwuiwa na makirci na Anti Amarya ta samu nutsuwa har ta miΖe ta shige wanka ita
kuwa Anti Amarya ta fice a Ιakin. Koda suka haΙu da Kausar a falon, babu abin
da Kausar Ιin ta nuna koda wasa kuwa wannan ya cirewa Anti Amarya zargin ta ji
tattaunawarsu.
***
MUΖADDARI...
Ummita da Humaira
tsaf cikin shiri, gidan Tasleem suka yi shirin zuwa ba ta jin dadi. Bisa
umarnin Mami, Humaira ta yi mata romon Ιanyen kifi mai Ιan yaji saboda ta ji daΙin
bakinta, ta shirya shi a kwando, suka Ιibarwa Raihana kayanta kala biyu kamar
yadda ta buΖata, tun soma ciwon Tasleem ta je gidan ta Ιan kwana biyu.
A hanya su na tafe
Ummita na amsa wayar Sahabi tana faman doka murmushi, abin da ba ta saba ba
kenan, wato waya a hanya. Asalima ta tsani su fito hanya Raihana ta Ιau waya
tana dannawa ko kuma amsawa, hakan ya ba Humaira mamaki. Ummita na ajiye wayar
ta dube ta.
"Yau ke ce da
kanki kike waya a titi? Lallai an gaida Sahabi, daga ranar da ya aiko aka sa
ranar aure, shikenan sai soyayyarsa ta Ζara girma a zuciyarki har ta sanya kina
karya sharuΙΙan da kika Ιorawa kanki."
Ummita ta yi murmushi karo na barkatai.
"Ke ni kaina yau jin soyayyarsa nake yi har cikin ΖoΖon
raina. Kin san Allah, a yadda nake jin
Sahabi a yau Humaira, da ace a karshen watannan ma a yi bikinmu da.."
Sauran maganar ta maΖale a fatar bakinta sakamakon wata mota
da ta gifta su a guje, idanu waje ta bi motar da idanu. Humaira dake kallon
hanya jin Ummitar ta yi shiru ya sanya ta dubanta don ta gani ko lafiya. Ganin
hankalinta na wani wurin ya sa ta ce.
"Lafiya?"
Cikin alamar ruΙewa kadan ta ce.
"Wallahi wata na gani kamar Anti Jannat a cikin mota ta
wuce."
"Anti Jannat kuma? Ina ce sai jibi Mami ta ce za su
taso?"
Ummita dai da har lokacin matar na mata gizo ta amsa.
"Eh, hakane, amma nidai sai naga kamar ita na gani a
motar."
Cikin rashin ba zancen muhimmanci Humaira ta taΙe baki gami
da Ιaga kafaΙa kaΙan.
"WataΖila kama ce kawai ba wani abu ba."
"Hakane."
Ummita ta amsa, daga nan suka bar zancen.
Kafin su kai ga tarar
abin hawa sai suka ji wani Ιan sahu na magana.
"Siii, ina ku ka yi?"
Suka dube shi, ya sha jallabiyarsa ga wani a gefensa matashi
cikin Ζananun kaya. Ummita ta zubamusu idanu ba tare da ta ce komai ba, sai
Humaira ce ta amsa da cewa Kuntau.
"Ku taho mu tafi."
Har Humaira ta soma tafiya, Ummita ba ta tako ba don haka ta
juyo ta dubeta.
"Ki taho muje mana."
Jiki a sanyaye kamar ta cewa Humaira su sauya wani Ιan sahun
sai ta ji harshen nata ya mata nauyi ga kuma Humaira wacce har ta sanya kai a
ciki wannan ya sa itama ta shiga. Sun soma tafiya hankalin Humaira a kwance
idan ka cire Ummita da ta yi wani irin la'asar, sun yi gaba kaΙan wani namijin
ya tsayar da su ya shiga yana rangaΙa sallama. Sallamar da ya yi ne ya sa
Ummita Ιan samun nutsuwa, ko ba komai ai ba za ka yi tunanin cuta daga wanda ya
nemar maku amincin Allah ba ku ka amsa. Gudu sosai Ιan sahun yake, Humaira na
ta Ιan yiwa Ummita hira jifa-jifa, ita kuwa ta kasa nutsuwa sam, hankalinta
rabi na ga kallon hanya da kuma gilashin Ιan sahun wanda ke kallonsu jifa-jifa
suna hada idanu da shi. Ba ta san ya aka yi ba, ita dai ta kamar na kusa da ita
ya fiddo wani hankicif, kafin ta yi aune ya hura mata a fuska, Humaira ma ta
juyowa kafin ta kai ga wani yunΖurin ya shaΖa mata, ji kake yaraff, sun lafke
bacci mai tsawo ya Ιauke su.
***
Ummita ce ta soma
farkawa, a hankali ta shiga murza idanunta da suke yi mata dishi-dishi kafin ta
buΙe su tarr cikin Ιan tsurkukin Ιakin da babu komai ciki. Daga wata ruΙaΙΙiyar
fanka wacce kallo Ιaya za ka tabbatar da ba ta aiki, sai ko shimfiΙaΙΙiyar
katifa wadda da ita da babu duk Ιaya tsabar yamutsewar da ta yi ta rabe biyu.
Duk dai a Ζokarinta na son tunano abin daya faru ta ci gaba da bin bangon Ιakin
da kallo wanda duk ya yi jirwayen ruwa ga yaana da gizo-gizo da suka cika lungu
da kusurwarsa. Sai ko wata Ζofa wacce daga Ζasanta gaba Ιaya ta rarake har kama
iya hango ruwan jirwayen banΙakin da ya kwanta har ya rine. Ban da tashin zarni
da wari babu abin da ke fitowa daga cikinsa. Ta kuma miΖe tsaye a razane, ta
tuna komai, su na hanyar zuwa gidan Tasleem ne su kai wa Raihana kayanta sai ko
saΖon Tasleem din na girkin da aka yi mata. Toh nan ina ne? Ya aka yi suka Ζare
anan? Fuskokin matasan nan uku ciki har Ιan sahun suka zo mata tarr tarr, da
sauri ta nufi windon dake Ιakin, a buΙe yake sai dai an zagayeshinda wasu irin
Ζarafana masu nauyi, ciyayi ne cike a wurin har ba ka iya hango bangon dake
waje. Ta juya ga Humaira da har lokacin hodar ba ta sake ta ba ta shiga
jijjiga ta tana kukan tashin hankali, ga jikinta da ke rawa ta ko'ina.
A Ιangaren Humaira kuwa, ji ta yi kamar a can wani nisan
wuri Ummita ke kiranta, a hankali ta buΙe idanunta tana kallonta dishi-dishi.
Sannu-sannu kuma har ta dawo hayyacinta ta fahimci dagaske ne dai Ummitar ke
kwala mata kira. Ta miΖe zaune tana ambaton innalillahi. Irin yanayin da Ummita
ta shiga, shi ta tsinci kanta a ciki. Da rawar murya ta ce.
"Na...nn..nan ina ne?"
Ummita dake hawayen itama girgiza mata kai ta yi hankali a
tashe.
"Ban sani ba Humaira, ban san ina muke ba. Mun faΙa
hannun mugaye azzalumai, jikina tunda muka fito yake ba ni cewa babu alheri a
tafiyarnan amma Ζaddara ta riga fata. Na so na ce maki kar mu shiga dan sahun
nan ban yarda da su ba amma.."
Sauran kalaman Ummita suka maΖale a fatar bakinta sakamakon
bankaΙo Ζofar da aka yi da Ζarfi aka sanyo kai cikin Ιakin. Mutum biyu ne cikin
samarin, da matuΖin napep Ιin da kuma wanda ya zauna kusa da Ummita a hanyarsu.
Hannun Ιaya riΖe da leda. Yayinda mai napep din ke shan taba hankalinsa kwance
yana fesar da hayaΖi suna murmushi, matuΖin Ιan sahun ya ce.
"Kun sha bacci, sannunku da tashi."
"Ku dubi Allah da annabinsa s.a.w ku yi hakuri ku
kyalemu mu tafi. Iyayenmu ba su da kudin da za su bayar domin fansarmu. Ku yi
hakuri mun tuba, wallahi komai da ke cikin jakkunanmu ku Ιauka halak malak mun
bar maku."
Ummita ke wannan zancen cikin rawar baki da murya. Ga
kukanta da ta kasa tsaidawa, itama Humaira kukan take yi ta ma kasa cewa komai.
Matashin da ya soma magana tun farko, ya kai duba ga na tsayen wanda ya fi shi
sirantaka da tsawo, tun murmushin farko da ya yi bai Ζara koda buΙe haΖora ba,
shi kuwa na durΖushen ya bi Ummita da kallo sannan ya yi Ζ΄ar dariya. Madadin ya
yi magana sai ya zuΖi sigari ya busamata a fuskar, ta kauda kai tana tari,
Humaira ma ta toshe hancinta. Hannu ya miΖawa na tsayen, ledar ya miΖo mishi ya
karΙa ya buΙe ta. Shinkafa da wake ne sai manja da yaji, ya tura musu ledar ya
Ζara fesar da hayaΖin sigari kana ya ce.
"Ga food ku eat. Kin gane bana son musu,
if you follow za rules here, you will ji dadi sosai. If you break oza, za ku yi
dana sanin haihuwar da uwarku ta yi."
Anan ne Humaira ta samu Ζarfin gwuiwar taso mishi cikin Ιaga
murya ta ce.
"Sai dai taka uwar ta yi nadamar haihuwarka idan tana
raye! Ba dai namu iyayen ba!"
Tana fadin haka a zafafe ya Ιaga hannu ya sauke yatsunsa
saman fuskarta ji kake tas! Ya fizgota ya take Ζafarta kafin ya Ιosana mata
karan sigari inda hayaΖi ke fita a saman fatar wuyanta, ta saki Ζara iyakar
Ζarfinta na azaba, Ummita ta shiga Ζokarin kwace ta tana haΙa shi da Allah da
Annabi kan ya yi haΖuri. Don kansa ya sake ta, wurin kuwa nan da nan ya yi
jazur ya ja ruwa.
"Ke har kin isa na zageki ki rama don ubanki?! Banza
Ζ΄ar iska kawai! Kika Ζara yimin irin wannan kuskuren da shishshigin sai
kin raina wayonki."
Ya Ζara Ζudundumo ashar ya watsa mata, har ya sa kai zai
fice ya dawo da baya ya sanya Ζafa ya murje abincin ledarnan har ya baje a
Ζazantaccen tayils din wurin. Ya dubi wanda suke tare ya soma magana da muryar
Ζ΄an daba.
"Kai Bad boy, koda wasa kar a ba su abinci da
ruwa har sai don kaina na baku iznin haka. Ζ³an wahala kawai."
Daga haka ya sa kai ya fice, wanda aka kira da Bad boy ya
watsamusu mugun kallo sannan ya bi bayansa gami da maida Ζofar ya rufe gam da
muΖulli. Su na tafiya Ummita cikin kuka ta Ιago Humaira tana duba wajen da aka
sanya mata wutar sigari. Humaira hawaye kawai ta ke yi idanunta a runtse ga raΙadin
da ya addabe ta.
"Kiyi hakuri Humaira, don Allah ki kai zuciyarki nesa
har mu samu kuΙuta daga hannun waΙannan azzaluman."
"Toh." Shi ne amsar da Humaira ta iya bayarwa
kawai, daga haka ba ta Ζara ko harafi ba saboda azaba. Ummita ta yi mata tofi a
wurin sannan suka yi zaman shiru sai ambaton Allah da suke faman yi.
***
Mami suna tare a kicin ita da Ladidi, abinci suke ta
hadar-hadar shiryawa na dare tana ta mitar zaman da su Humaira suka je suka yi
a gidan Tasleem alhalin ta ce musu kar su jima.
"Gashinan yanzu har an fara kiraye-kirayen sallar
Magriba, itama gwanar duk da na gargadeta kar ta bari su yi zaman hira da
mutuniyar tasu (Raihana) amma ta yi kunnen uwar shegu."
Ladidi ta yi Ζ΄ar dariya tana goge kwanukan da ta wanke don
yin kwasar tuwo.
"Ai fa kam, Ζ΄anmatannan naki uku idan suka haΙu a wuri
sai haΖuri. Ji suke yi kamar ba su taΙa zaman hira ba a duniya sai a
lokacin."
Mami ta buΙe baki za ta yi magana sai ga Walid ya shigo da
gudu riΖe da wayarta, a bayansa kuwa Muhsin ne.
"Mami Mami! Anti Tasleem tana kira."
Wayar a lokacin har ta katse, Muhsin yana kawo Ζarar Walid
wai game yake ta yi har ana kira yana katsewa. Mami ta Ιan yi musu tsawa akan
suf fice a kicin Ιin su ba ta wuri. Ta na kokarin dannawa Tasleem din kira sai
ga kiran Raihana ya shigo, ta Ιaga ta kara a kunne.
"Raihana, yanzu nake shirin kiranku, maza maza ki cewa
yarannan su dawo. Ku idan ku ka samu hira ba ku san dare ba ya yi ku haΖura
ko?"
"Mami su wa kike magana? Ai kiran ma da Sis ta yi maki
kenan ta ce kodai ta cire rai ne ta sanya Yaya Hamza ya yi mata odar wani abun?
Nidai tun Ιazun ma na kikkira wayoyin su Ummita a kashe."
Mami ta fiddo idanu gami da dafe kirjinta, cikin rawar murya
ta ce.
"Me kike shirin cewa? Kina nufin wai su Humaira ba su
zo gidan ba? Kinsan tun Ζarfe nawa suka bar nan?"
Raihana itama muryarta cikin tsananin ruΙewa da tashin
hankali ta amsa.
"Wallahi Mami ba su zo ba."
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Na shiga uku ni
Maryam."
Hakan da ta faΙi ya sa Ladidi maido hankalinta gareta, itama
gaba Ιaya jikinta ya Ιauki rawa. Mami ta kasa cewa Raihana komai sai kawai ta
katse kiran cikin tsananin tashin hankali ta fito falon inda Ζasim ke kwance
saman kujera yana latsa waya.
"Ζasim! Tashi ka bi sahun su Humaira! Na shiga
uku, tun da rana suka fita a gidannan har yanzu ba su dawo ba."
Gaba Ιaya a ruΙe take maganar, ta kasa nutsuwa balle ta yi
mishi bayani yadda zai fahimta. Ba ta jira cewarsa ba ta yi gaba ta nufi Ιangaren
Abba amma ina, ta iske ya fice zuwa masallaci. Ta dawo falon inda ta tarar
Ζasim tsaye Ladidi na mishi bayanin abin da ya faru. Shi ma nan take ya ji
hankalinsa ya tashi.
"Amma Mami kodai sun biya gidan Ζawayensu
ne?"
Mami wadda gaba Ιaya cikinta ya Ιuri ruwa ga tsananin tashin
hankalin da ya bayyana saman fuskarta ta amsa mishi.
"Kayya Ζasim, ba dai su ba. Ba su da wannan rawar kan,
da ace dai Raihana ka ce shi ne zan yarda. Ni dai jikina yana ba ni akwai
matsala."
Ζasim ya yi shiru, sai ya shiga kiran layukansu amma gaba Ιaya
a kashe.
"In sha Allahu lafiya kalau suke. Ku kyautata
zato."
Fadin Ladidi jiki a sanyaye. Itama ta rasa nutsuwar zuciya,
a wannan lokaci da satar mutum sukutum ba shi da wuya, lallai dole ko rabin awa
suka yi hankali ya tashi, balle kuma kusan awanni uku zuwa huΙu? Abin dai akwai
Ιaga hankali.
"Bari nayi sallah."
Mami ta furta gami da miΖewa ta yi Ιaki. Ladidi ma ficewa ta
yi kicin don kwashe tuwon da har ya soma kamu yayinda Ζasim shi ma ya fice a
sanyaye zuwa masallaci.
***
Tasleem kuwa, Raihanana ajiye waya suka dube ta ita da
Fauziyya da ta maida gidan na Tasleem gidan zuwanta hira da kuma kallo.
"Meyafaru da su Humairar ne?"
Cikin halin tsananin firgici ta faΙamata abin da Mamin ta
ce. Tasleem ta yamutse fuska kaΙan tana ci gaba da taunar tsamiyar da ke
bakinta.
"Ke yanzu kin yarda Ιatan suka yi kenan? Kika
sani ko Ummitan ta yiwa rakiya Ιakin Sahabi?"
Maganar ta dake Raihana, wannan wane irin baΖin Ζazafi ne
marar daΙin ji? Ba ta taΙa tsammanin jin makamancinsa daga bakin Tasleem ba
musamman ma a gaban Ζanwar mijinta. Fauziyya kuwa ta ce.
"Kai Anti Tasleem, wannan Humairar da na gani dai kamar
ba za ta aikata irin haka ba. Ummitar ma ba ta yi kama da Ζ΄an iska ba."
Sai a sannan ita ta tuna ashe ba su kaΙai ba ne. Don haka ta
yi saurin gyara zancenta gami da nuna tarin alhini a saman fuska.
"Hakane, amma kinsan zamanin nan, samarin yanzu Ζ΄an
iska don su hurewa mutum kunne ba komai ba ne. Allah dai ya tsare, ya sa su
koma gidan."
Raihana wacce ta lula tunanin inda ya kamata ta kira don jin
ko su Humairar sun je ta dawo hayyacinta, firgigit ta miΖe tana fadin.
"Nidai wallahi ba zan iya zama ba ana neman Ζ΄an uwana,
gida zan koma."
A fusace Tasleem ta ce.
"An fadamaki nima ban damu ba ne? Ai daren bai yi ba,
kika sani ko napep din da suka shiga ne ya samu matsala? Toh wallahi babu inda
za ki je ki jira har sai mun ji ya ake ciki."
Raihana kamar ta yi magana sai kuma ta fasa, a fusace ta
shige ciki tana jin kuka na taso mata, ta ina za ta iya nutsuwa alhalin ba a ga
Ζ΄an uwanta ba? Fauziyya ganin haka ta miΖe ta bi bayanta, ita kuwa Tasleem da
sauri ta bi hanyar da suka yi da idanu sannan a gaggauce ta fiddo wayarta ta
rubuta text ta tura kamar haka.
*_Aikin har ya kammala ne da wuri haka?_*
Tana aikawa aka maido mata amsa.
*_Tukunna dai, wani abun ya faru?"_*
Ta yi shiru ta kasa maida amsar wannan tambaya, jikinta ya Ιan
yi sanyi. Ita kanta ba ta da tabbacin abin da ke shirin faruwa.
***
Mami tana jin shigowar Abban falo ta miΖe da sauri
har ya dube ta da Ιan mamaki.
"Lafiya Maryama, ya na ganki a rikice?"
Kawai sai ta fashe da kuka. Ya shiga tashin hankalin ganin
haka, wannan ya sa shi saurin riΖo hannuwanta.
"Ki samu nutsuwa ki faΙamin, meke faruwa?"
Muryarta dakyar take fita ta amsa.
"Kasan na aiki yarannan gidan Tasleem amma babu su babu
dalilinsu. Ba su je gidan Tasleem din ba, kuma wayoyinsu gaba Ιaya a rufe.
Hankalina ya tashi."
Tabbas ya san da maganar amma kasancewar ya shiga tsananin
ruΙani ya ce.
"Su wa kenan? Ni ban fahimci komai ba. Wa kika
aika?"
"Humaira da Ummita da na ce maka za su je gidan Tasleem
kai mata saΖo."
Abba jin haka nan da nan ya soma haΙa zufa.
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Kun tabbata ba
sa gidan ita yarinyar?"
Mami ta amsa ta hanyar gyaΙa kai da motsa lebba don sautin
muryar ma ta kasa fita. Jin haka Abba ya zari mukullin mota daga shi sai
jallabiya sai ko wayoyinsa ya fita yana fadin.
"Ina zuwa." Har ya kai Ζofa sai kuma ya juyo ya
dubi Mami.
"Maryama, ki kira dukkan inda kike tunanin za su iya
zuwa ki ji ko can suka tafi, ni bari na je ofishin Ζ΄an sanda na sanar."
Ta kasa magana sai gyaΙa kan da ta yi. Daga haka Abban
ya fice. Kai tsaye babban station Ιin mandawari ya je ya yi report ya ba da
hotunan su Ummita, ba shi da su sai da ya sanya Raihana ta turo masa. Anan ne
itama hankalinta ya kara mugun tashi ta tabbatar dagasken dai an sace su.
***
Raihana ta birkicewa su Tasleem ita lallai a daren take son
komawa gida, kuka take yi ba ta jin koda rarrashi, wannan ya sanya ba shiri
suka miΖe har Tasleem din suka nufi can gidan a motar Hamza.
Su na isa Raihana ta faΙa cinyar Mami ta Ζara Ζarfin
kukanta. Wannan ya Ζara karyar da zuciyar Mamin, ta dafa Raihanar tana Ιan
hawaye. Tasleem ta Ζaraso ta zauna fuskarta Ιauke da damuwar kukan da Mami ke
yi ta ce.
"Kiyi hakuri Mami, in sha Allahu za a gansu. Bana
tunanin an sace su, idan da hali ku kira Sahabi ku ji ko..."
"Malama ya isheki hakanan! Haba! Da wanne kike so a ji?
Da Ιatan su ko kuwa da baΖin Ζazafin da kika Ζokarin yi musu na zuwa wajen
saurayi? Ζazu dama na maki shiru ne darajar Fauziyya, yanzu kuwa daidai nake da
ba ki amsa. Ki faΙi muji, tarbiyyar wa kike shakku a cikin su biyun? Ke da
kanki a bayan idanunsu kin sha yabon nutsuwarsu, ki dai ji da abin da ke
jikinki ba ki zauna zaman Ιaukar haΖΖin mutanen da ba su Ιaukeki yadda ke kika Ιauke
su ba!"
Tasleem wacce ta cika ta gama batsewa da wannan kalar
maganganun da ta ke musu kallon rashin kunyar Raihana gareta tuni ta harzuΖo za
ta soma caccakawa Raihanar zagi sai Mami ta dakamata tsawa.
"Ya ishe ni! Ya isa! Ku marasa tunanin ina ne? Da wanne
zan ji ne? Ashe ba kwa hangomin abin da nake hangarwa kaina?! Ba ku hangen
ire-iren maganganun da zan sha wajen jama'a sanadiyyar Ιatan yaran amana
da nake riΖo? Da ace cikinku ne wa zai ce sakacina ne?!"
Mami na kaiwa nan ta ji kukanta ya Ζaru har da sheshsheΖa,
Ζarshe kawai sai ma ta miΖe ta fice zuwa sashin Anna don tana da tabbacin ba ta
sani ba.
***
Duhun da Ιakin ya yi
ne ya sanya suka matsu a gefe guda suka cure jikinsu ga uban sauro da ke yawo a
kunnuwa yana kuma cizon fatar jikinsu.
"Humaira, ya
zamu yi? Babu ruwan alwala a banΙakin nan da na duba, bamu yi sallolinmu ba.
MaΖogwarona ya bushe Ζishin ruwa nake ji."
Ummita ta yi furucin cikin shaΖaΖΖiyar muryarta da ya dashe
sanadin kukan da suka sha, itama Humairar wacce Ζishin ruwa da kuma yunwa suka
galabaitar gefe guda ga wani fitsari da ya cikamata mara ta ce.
"Ban sani ba Ummita, ban sani ba. Fitsari nake ji amma
tunanin wannan banΙakin da muhallin ya sa na kasa yi. Sun bar mu a duhu kamar
waΙanda ke cikin maΖabarta, ko a maΖabartar muna saka rai da rahmar
Ubangijinmu. Mu cigaba da addu'a, ba zamu rasa mafita daga gareShi ba."
"Toh." Shi ne kawai abin da Ummitan ta iya
furtawa, ta koma ta nannaΙe a jikin bango ta runtse idanunta tsabar tsoron
wurin, cikinta ya Ιuri ruwa sosai, ta cigaba da jan dukkan wasu addu'o'in da
suka zo bakinta.
Suna a haka suka soma jin muryoyin garada daga waje suna
dariya har da kyakyatawa abin babu dadin
sauraro. Kafin su tantance komai
suka ji alamar buΙe Ζofar, gaba daya suka Ζara ruΖunΖume juna don fargaba. Aka
haske musu fuskokinsu da torchlight mai shegen haske, wannan ta sa suka yi
amfani da hannuwansu wurin kare hasken sakamakon Ζarfin da suka ji ya yiwa
idanunsu da suka jima cikin duhu. Wannan karon matasan ne su ukunsu gaba Ιaya
suka shigo.
"Don uwarku ku
saki juna, Ζ΄an iskan banza kawai."
Sun ji ciwon zagin
sai dai tsoro ya sa da azama suka matsa gefe, kowaccensu babu inda jikinta ba
ya rawa. Shi ne dai baΖin azzalumin na Ιazun.
"Wizzy, a ina aka kwana ne?"
Anan suka ji ashe sunansa Wizzy, ya watsawa mai maganar
mugun kallo.
"Kai Babba, don't kawo yaawa mana. Ka yi everything a
muhallinsa mana ok? Here is not good to ce wani abu. Sai mun go out."
Wanda aka kira da Babba ya amsa da.
"Na fahimta Oga."
Daga haka Wizzy ya yo gaba ya dan sa Ζafa ya shuri Humaira.
"Ke gwanar na iya, koda wasa wallahi ki ka kara try din
zagina sai na kasheki na yi killing banza! Kuma a nan za ku zauna har sai mun
gama sanin makomarku! Badboy, a ba su abincin da ruwa, ka ajiye musu fitilar ba
don halinsu ba shegu."
Yana kaiwa nan ya sa kai ya fice yana ba wa Babba umarnin ya
biyo shi su yi magana. Shi kuwa Badboy ya ajiye musu leda da ruwan sha na
purewater sinΖi guda, sai kuwa fitilar daga nan ya fice ya garΖame Ζofar. Da
sauri Ummita ta jawo ruwan hakanan itama Humaira, suka sha suka yi kat, daga
nan haka suka daure suka kama ruwa a banΙakin ba don suna so ba, suka yi
alwala, Ιankwalayensu suka mayar darduma, suka yi sallah.
Humaira ta yi shiru ta zuba uban tagumi tana Ιarin hawaye,
Ummita ta jawo ledar, shinkafa da miya ne garau garau.
"Ke kika ce kina
jin yunwa Ιazu, ki daure ki ci."
Ta Ιan dubi abincin sannan ta dubi Ummita ta girgiza kai.
"Ba zan iya ci
ba Ummita, innalillahi wa inna ilaihir raaji'un, haka za mu yi ta zama tare da
waΙannan azzaluman? Yanzu nan wurin zamu kwana? Su Abba na can hankalinsu a
tashe Ummita. Wayyo Mami."
Kawai sai ta sa kuka hakan ya sa Ummita itama da take danne nata sai kawai ta
sake shi. Wannan karon ma babu mai rarrashinsu, su suka gaji suka yi shiru sai
faman sheshsheΖa.
***
*LITTAFIN NAN NA KUΖI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA
TARE DA SHIGA HAKKI BA.*
*5407827015*
*FCMB*
*Farida Abdullahi*
09034973645
Kamar wasa, Ζaramar magana ta zama babba. Babu su Humaira ba
labarinsu har aka yi kwanaki biyu, wannan ya Ζara tayarda hankalin iyalan gidan
sosai. A ranar ne kuma Jannat ta diro gidan, labarin Ιatan yana risΖarta ta hau
buga salati, cikin sanyin jiki ta ce.
"Koda ace ba na
kaunarsu, bana murnar Ιatan su. Allah ya sa a gansu."
Mami ta amsa da amin, Raihana kuwa ba ta um bare um um a
kwanakin nan sai kallon kowa da idanu. Tasleem itama dai tana gidan ba ta koma
gidanta ba, Abba ne ma ke faΙan zamanta acewarsa zaman ko rashinsa ba shi zai
sa a gansu ba. Wannan yasa a ranar ya ba ta umarnin tattarawa ta tafi. Jannat
ce ta ce za ta kai ta tunda Hamza ya tafi ofis. Anna kuwa nunawa tayi ko a
jikinta, cewa ta yi ba ta yarda ma da batun Ιatan ba, ta fi tunanin dai wani
yawon nasu suka je za su dawo. Babu wanda ya ce mata komai a wannan bahagon
tunanin nata. Zancen dai zuwa lokacin ya yaΙu har gidajen rediyo da social
media inda Raihana ta Ιora hotunansu a dukkan shafuka tana mai tagging shafin Humaira saboda abokan
kasuwancinta su taya ta yaΙawa.
***
*_Tafkeken fili ne
babu gida gaba da baya, tafiya kawai yake yi yana jefa Ζafafunsa yana faman
kwala kiran sunan Humaira ga wani irin baΖin hadari da ya cakuΙe a sararin
samaniya sai walΖiya dake haskawa akai-akai har bai ankara ba ya cimma Ζarshen
hanyar yana shirin afkawa Ζaton ramin dake a gabansa ya ji an riΖo hannunsa da
Ζarfi. Juyawa ya yi yana mai duban mai shi, wata mace ce dattijuwa fara tas,
tana sanye da farin hijabi har da na hannu, komai na tufafinta fari ne Ζal.
Hawaye ne kwance saman fuskarta ta ce. "Ka taimaka ka ceci rayuwar
Humaira, tana cikin hatsari. Ka kularmin da ita. Duk runtsi kar ka rabu da ita.
Alheri ce a gareka." Zuciyarsa ya ji ta tsinke, ya dawo da baya murya a
sama ya ce "Ina Humaira ta ke?" Kawai sai ta nuna masa ramin dake
gabansa, Humaira ya hango saman wani Ζaton dutse a kwance gaba Ιaya gaΙΙanta an
sanya wasu sarΖoΖi an Ιaure ta tamau. Sannan ya maida duba ga Matar shima
lokacin hawaye yake. "Ba ta sona, ba za ta amince na taimake ta ba."
Matar karo na farko ta yi mishi murmushi "Kaf duniya babu matar da za ta
so ka sama da Humaira. Tana sonka, ka bata lokaci ka zama mai hakuri."
Tana kaiwa nan ta saki hannunsa ta soma tafiya da baya tana cewa "Ka ceci
rayuwarta daga hannun azzalumai. Ina roΖonka a matsayina na mahaifiyarta._*
Yana kai wa nan ya soma jin kiraye-kirayen sallar asuba a
kunnensa, firgigit ya farka ya miΖe zaune yana ambaton Allah. Na'urar sanyaya
jikin dake aiki bai hana zufa wanke mishi fuska da jiki ba hakan ya sanya shi
saurin yaye bargon yana ajiyar zuciya kamar wanda ya yi tseran gudu. Kansa ya
ji yana sarawa, wannan wane irin mafarki ne kuma? Wace ce? Meke faruwa da
Humairar? Kwana biyu kenan rabonsa da duk abinda ya shafi social media balle ya
samu damar magana da Raihana ko tambayar lafiyar Humairar, hakan kuma ya faru
ne sanadiyyar ayyukan ofis da suka yi mishi yawa saboda shirye-shiryen tarbar
baΖin Ζasar waje da suke yi a kamfaninnasu. Addu'a ya yi sannan ya miΖe jiki a
saluΙe gabansa har lokacin na bugu da Ζarfi yana jin kamar ya kira wayar
Humairar a sannan ya ji ko za ta amsa. Hakura ya yi ya shiga ya Ιora alwala ya
zura jallabiya ya fice zuwa masallaci. Koda ya dawo wayarsa kawai ya Ιauka, ba
ya jin zai iya haΖuri da kiran Humaira koda ace hakan na nufin rusa tsawon
jiran da ya yi, ya gaji zai tunkareta kawai da batun aure. Zantukan matarnan da
ya gani cikin mafarki da kuma yanayin da ya ga Humairar sun fi komai Ιaga mishi
hankali duk da yana kyautata zaton alheri ne mafarkin.
Ya kira ya fi sau
uku amma amsar Ιaya ce, a kashe. Don haka ya yanke shawarar kiran Raihana, shi
dai babban burinsa jin muryar Humairar.
Ko ringing uku wayar ba ta yi ba ya ji Raihana ta Ιaga a
gaggauce. Sallama ya yi mata ta amsa.
"Ina son jin muryar Humaira, ki haΙa ni da ita
please."
Kawai sai ya ji ta fashe masa da kuka wanda ba Ζaramin
rikita shi ya yi ba.
"Me ya faru?! An yi wani abun ne? Ki faΙamin."
Gaba Ιaya ya ruΙe, nan take sanar da shi ai kwanaki uku
kenan babu Humaira da Ummita balle labarinsu ta
kuma Ζara da cewa.
"Abin damuwar shi ne ba a san su waye ba, idan
kidnappers ne, ai za su kira su ce a ba su kuΙin fansa, waΙannan kuwa babu kira
ba.." Maganarta ma ta kasa fita sakamakon kukan da ya ci Ζarfinta.
"What nonsense! Takardu da za a ce kawai sun Ιata? Kar
ki rainamin hankali mana!"
Daga yanayin yanda yake zancen ma ka san a ruΙe ya ke. Cikin
nutsuwa ta labarta mishi duk yadda komai ya faru har da batun cigiyar da aka
sanya a jiya a gidajen rediyo da ma hotunan Humairar duk da ta Ιora a media. Ta
Ζara da faΙin.
"Ka taimake ni Yaya Fadeel a nemo su, wallahi ba zan
iya rayuwa ba idan babu su. Jinin jikina ne."
Idanunsa suka kaΙa, ya ji wani maΖoΖon abu ya tokare masa a
Ζirji, ga kansa da ya yi mugun sarawa, bai iya cewa komai ba ya datse kiran.
Zama ya yi dabas a Ζasa har lokacin yana riΖe da kansa da yake ciwo tamkar zai
fashe. Ashe dagaske mafarkinsa ne zai tabbata? Humaira na cikin tashin hankali?
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun!" Ya furta a
fili. Kafin wayewar gari tarr jikinsa ya Ιauki tsananin zafi, amma hakanan ya
daure ya Ιaga wayar Ibb wanda shima ya ci karo da hoton Humaira dake yawo a
media. Hankalin Ibb tashe ya ce.
"Fadeel ka ji labarin abin da ya faru da Humaira?"
Shiru ya kasa ba shi amsa sai wasu irin zafafan hawaye da
suka kwaranyo saman fuskarsa. Ya runtse idanu, fatansa bai wuce ace mafarki
yake yi ba, inama duk abin da yake ji yanzun a mafarkin ne.
"Fadeel, are you ok?"
Ibb ya Ζara tambayar jin ya yi shiru. A sannan ne ya soma
magana dakyar haΖoransa har su na bugun juna saboda wani mugun sanyin da yake
ji.
"No Ibrahim, i am not, Humaira rayuwata ce. Ibrahim ka
taimakamin, ina tunanin mutuwa zan yi."
Yana kai wa nan ya ajiye wayar shi bai kashe ba, shi kuma
bai Ζara sauraron abin da Ibb din zai faΙi ba , yana ta faman Hello hello amma
shiru kake ji.
Yana nan kwance ya dai ji shigowar Alhaji dakin amma daga
nan bai Ζara sanin inda kansa yake ba. Alhaji wanda ya samu waya daga Ibb a
gigice ya tallafo shi ya hau kiran sunansa, Anti Amarya itama faΙowa ciki ta yi
sanye da hijabinta har Ζasa.
"Ya kamata a tafi asibiti."
Jin abin da ya fito daga bakin Anti Amarya ya ankarar da shi
abin da ya kamata ace shi ya ya yi wannan hankalin. Ya ba ta umarnin ta sa a
fiddo mota yayinda shi kuwa ya taimaka da kama Fadeel suka fita.
Murja da ta ji hayaniyarsu daga farfajiyar gidan ta fito
daga Ιakinta tana murza idanu daga ita sai riga da wando na bacci ko sallah ba
ta yi ba. Suka yi karo da Anti Amarya da ta shigo sauya sutura don ta bi bayan
su Alhajin a wata motar.
"Anti meke faruwa?"
"Fadeel ne ba lafiya."
Nan da nan ta ji tashin hankali, sai kuma ko me ta tuna
kawai ta danne damuwarta. Wani abu ya tokare kirjinta kawai sai ta ce Allah ya
ba shi lafiya, daga haka ta juya ta koma Ιakinta fuskarnan kamar an aikomata da
saΖon mutuwa. Sai da ta dubi Ζofar shigowa Ιakin ta tabbatar babu mai tahowa
kafin ta Ιauki waya ta danna kira sau uku ba a Ιaga ba, Ζarshe kawai sai ta
aika da saΖo kamar haka.
*_Lokacin aiwatar da
aikin ya yi. An tafi da shi asibiti yana cikin halin rashin lafiya kuma bana
raba Ιayan biyu a sanadinta ne._*
Iyakar abin da ta rubuta kenan a saΖon ta tura zuwa lambar
da ta yi saving da suna BLANK. Ta koma ta zauna gefen gado tana murmushin da
ita kaΙai ta san ma'anarsa kafin ta Ζara fiddo wayarta ta lalubo saΖon da
aminiyarta Saddy ta aikomata na labarin Ιatan Humaira da kuma hotuna. Ajiyar
zuciya ta sauke sannan ta Ιaga yatsunta biyu a kan hoton Humaira gami da
girgiza kai ta ce
"Good bye
Humaira, daga yanzu kin fita daga rayuwar Fadeel, fita na har abada."
***
Ruwan sanyi Ζarara
aka sheΖa musu a fuska wannan ne ya yi sanadiyyar da firgigit suka farka daga
baccin wahalar da ya kwashe su. Idan ka kalle su, ba za ka ce su ne wadannan
Ζ΄anmatan Abban ba masu iya ado da kwalliya uwa uba kuma tsafta. Sun rame sun yi
baΖi a kwanaki huΙu kaΙai da suka yi a wajen, ga fatar jikinsu da ya yi ruΙu-ruΙu
saboda cizon sauro da ma cinnaku. Ummita fama take yi da mugun zazzaΙi, ita
kuwa Humaira a kwanakin amai kawai take kwararawa ga gudawa, gaba Ιaya sun zama
wasu Ζazamai na Ζarfi da yaji. Suka kai duba ga wanda ya yi musu wannan
aika-aikar, wannan dai azzalumin ne mai suna BadBoy. Ya Ζaraso ya ja Ummita
kasancewar babu kuzari a jikinta kawai ta tafi luu, ya dakatar da ita ta hanyar
tura ta da hannu ta faΙi tim a saman busassan aman da Humaira ta yi. Ya fisgo
hannunta ta koma ta zauna kafin ya sa baΖin kyalle ya tamke mata idanu. Humaira
da ta kasa koda Ιaga yatsa sakamakon galabaitar da ta yi na amai da gudawa ya
koma kanta, ya toshe hanci jin Ζarni da warin dake tashi a jikinta, mari ya
kifa mata.
"Don ubanki ke wace iriyar Ζazama ce da ba za ki shiga
banΙaki ba. An faΙamaki nan gidan gyatuminki ne da za ki yi mana kashi a wuri?
Za ku wa ki raina kanki."
Ya fisgota itama ya Ζullemata idanun. Daidai nan Wizzy ya Ιan
leΖo da kai yana mai zuΖar sigari.
"Wai ya ne? Ka tattaro su mu bar nan."
Daga haka ya titsa Ζeyarsu Wizzy na kundumawa Humaira ashar
ganin yadda ta yi kace-kace sai tashin hamami take yi. Ya rantse ba za su shiga
motarsu a haka da ita ba. Wannan ya sa anan suka Ιauki ledar kayan Raihana dake
hannunsu a falon gidan suka damΖamusu a hannu.
"Ku sauya kayan kar ku kuskura ku gwada wani motsi idan
ba haka ba sai na ciremaku kai da wuΖarnan." Daga gargadin da ya fito a
bakin Wizzy, sai Badboy ya tura Humaira banΙakin da ke falon wanda ya fi na Ιakin
da suke ciki kyau shi har da ruwa a Ζaton bokiti. Idanunta ya kunce mata sannan
ya fice ya tura Ζofar. Humaira dakyar ta Ιaga rigar da suka bata, doguwar rigar
Raihana ce na atamfa sai Ιankwali. Kuka ya kufcemata da wani irin kewarta. Ba
ita ta iya saiya kayan ba sai da Badboy ya bugamata Ζofa da Ζarfi ya na zaginta
akan ta yi sauri, wannan dalilin ya sa cikin rawar jiki ta shiga rage kayan
dake jikinta, ta Ιan watsawa kanta ruwa a gaggauce har da Ιora alwala sannan ta
sa kayan ta fito. Itama Ummita hakan ta yi duk kuwa da cewa ga zazzaΙi a
jikinta, amma tana buΖatar tsaftar jikinta ko yaya ko don sallah. Itama dai
kayan Raihanar ce riga da siket Ζ΄an kanti.
Wizzy ya kallesu su
biyun yana mai haΙiyar yawu maΖwat. Shakka babu sun kai a kira su Ζ΄anmatan da
za a nuna, ban da ma baΖar wahalar da suka ci ai ya sani sun haΙu ne Ζarshe
musamman Humaira da ya kasa Ιauke idanu a kanta. SaΖe-saΖen dake ransa, hakan
ne a na Badboy wannan ta sanya shi duban Wizzy.
"Ga nama amma
babu damar ci."
Wizzy ya busar da hayaΖi gami da yin wani shu'umin murmushi.
"Akwai ranar Ζin dillanci. Yanzu dai mu yi haΖuri mu ci
miliyoyin kuΙaΙen nan idan ya so ko mene ne sai a yi."
Badboy ya jinjina kai, ya Ζulle idanun su Humaira wadanda
duk iyakar kalle-kallensu sun kasa gane inda suke. Wizzy ne ya soma fita ya Ιan
duba wuri sannan ya ba Babba dake gaban mota umarnin tayarwa daga haka ya sa
Badboy fitowa da su Humaira suka tura su cikin motar mai baΖaΖen gilasai suka
bar wurin da gudun gaske.
***
Fadeel wanda
likitoci suka duΖufa a kansa dakyar cikin taimakon Allah suka samu ya dawo
hayyacinsa. Sai dai har lokacin zazzaΙinsa bai sauka ba wannan ta sa suka yi
mishi allurai suka Ιora masa ruwan drip ganin gaba Ιaya jikinsa babu kwari
saboda aman da ya yi mai yawa bayan farkawarsa.
Ganin ya kasa
nutsuwa sai kokarin miΖewa yake yi yana cewa zai je neman Humaira hankulan
Alhaji da Ibb wanda tuni ya iso suka tashi, Likita dole ya yi mishi allurar da
zai sanya shi bacci.
Bayan fitarsa Alhaji
ya dubi Ibb.
"Wai meke faruwa ne? Me ya samu Humairar?"
Ibb ya sanar da Alhajin labarin Ιatan su Humaira. Shi kansa
ya jinjina lamarin. Shi tun daga sadda Fadeel ya ce mishi zai yi jiran Humairar
ya fahimci irin zurfin da ya yi a kaunarta.
"Toh ban da abin Fadeel, ai ba sanyawa zuciyarsa damuwa
ya haifar mishi da ciwo ne mafita ba, mafitar ita ce a yi addu'a sannan a Ζara
magana da hukuma don ganin an Ζarfafa bincike."
Ibb ya jinjina kai.
"Hakane."
Suna nan zaune Daddy
ya iso tare da Maman Ibb. Anan suke jin silar ciwon, shi ma dai irin hangen Alhajin ya yi. Daga nan ya ce Ibb
ya yi mishi rakiya zuwa gidan su Humairar. Shi ma Alhajin ya bi su yayinda Mama
da Anti Amarya wacce ta iso lokaci guda da Fu'ad suka zauna anan asibitin.
***
Abba bai yi mamakin
ji daga Ζasim cewa ya yi baΖi ba domin tun faruwar lamarin yake ta samun baΖi
daga kan Ζ΄an uwa har abokan hulΙa. Ζazun ba jimawa Ζ΄an uwan Maman Ummita na
Bichi suka iso su ma.
Falonnasa na saukar
baΖi ya shiga. Daddy da Alhaji suka miΖe aka yi musabaha da Abba sannan duk aka
zauna shima Ibb ya gaida shi. Daga nan kuma Daddy ya gabatar da kansu matsayin
iyayen Fadeel yaron wajensu dake neman auren Humaira. Abba ya ji zancen
banbarakwai, Alhaji kuma sanin da ya yi cewa Fadeel bai bi maganarsa ba na
gabatar da kai ga Abban yasa shi fahimtar komai. Nan ya yiwa Abban bayani cewa
ai yaron nasu bai kai ga zuwa wurinsa ba. Abba ya Ιan saki fuska, watakila dai
shiyasa Humairar aka ce ba ta kula kowa, kenan tana da wanda ta ke so. Nan kuma
aka shiga jajanta batun Ιatan su Humairar, Abba ya Ζara ba su labari daidai
sadda Raihana ta zo kawo ruwa kamar yadda Ζasim ya shaida mata saΖon Abban. Ta
shigo da zumΙulelan hijabi idanunta duk a kumbure, gaishe su ta yi. Abba ya
bita da kallon tausayawa, sai a kwanakin nan ne ta soma magana amma tun bayan
faruwar lamarin ta zama Ζ΄ar kallo. Suka amsa gaisuwarta, jin Ibb ya kira
sunanta gami da jajanta mata ne ya sanya Abba kuma yarda dagaske dai akwai sanayya
tsakanin Humaira da wanda suka kira da Fadeel.
"Ina Yaya
Fadeel?" Ta furta tana duban Ibb don tun wayarsu take ta neman layinsa
yana Ζara ba a Ιagawa. Ya sanar mata da yana asibiti, tausayinsa ya kamata, ta
yi fatan Allah ya ba shi lafiya suka amsa da amin daga haka ta mike ta koma
ciki.
Daddy a take ya yi kiran Commisioner na Ζ΄an sanda wanda ya
kasance abokinsa ya shaida mishi batun Ιatan su Humaira, nan ya ce ya san da
maganar. Ya Ζara roΖonsa akan a tsaurara bincike ko Allah zai sa a dace. Daga
haka suka yi sallama, suka yiwa Abba bankwana da zummar za su dawo, shima Abban
ya tabbatar musu zuwa anjima zai shiga duba
Fadeel.
***
Raihana ta ci karo da
Mami a falo, Mami ta ce.
"Su waye
baΖin?"
Ζan murmushin dole Raihana ta yi.
"Iyayen Yaya Fadeel ne wanda ke son auren Humaira suka
zo jajantawa Abba. Shima yana asibiti ba lafiya."
Daga haka ta yi gaba ta bar Mamin a tsaye shiru. Sai kuma
can ta ankara ta kai duba ga mutanen dake falon, Ζ΄an uwan mahaifiyar Ummita ne
da suka iso daga Bichi sai kuwa yan uwan Abba zaune ana ta jajantawa waΙanda
wasunsu a cikin magana suke watsawa Mami habaici da baΖar magana. A ganinsu
wannan ba tsautsayi bane, akwai lauje cikin naΙi. Juyawa ta yi ta shige Ιakinta
da sauri ta rufe da muΖulli.
***
A wannan daren sai
ga waya daga kidnappers din Humaira kai tsaye Abba suka kira. Ya Ιaga ba tare
da sanin ko su waye ba, lokacin su na tare da makwaftansa da wasu cikin yan
uwansa maza ana zaune.
"Da Alhaji Yusuf
muke magana?"
Abba ya amsa da sauri.
"Eh, ni
ne."
"SharaΙi na farko, idan a cikin mutane ka ke ka tashi
ka bar wajen. Ko da alama kar ka nuna wani abu da zai sa a fahimci wani abu a
saman fuskarka. Ka tashi maza ka koma Ιaki muddin kana son yaranka su tsira da
rai da lafiyarsu."
Jin haka Abba ya miΖe gabansa na dukan tara-tara, wannan
kiran yake addu'ar ji don ya shirya salwantar da duk abin da ya mallaka matuΖar
su Humaira za su dawo gida cikin aminci. Hanyar Ιaki ya nufa ba tare da ya da
kowa komai ba suka bishi da idanu kawai.
Muryarsa har tana rawa ya ce.
"N..a.na..matsa.
Ni kadai ne a Ιaki."
Wata shu'umar dariya aka saki da Ζarfi sannan aka ce.
"Dakyau! Ka buΙe kunnenka ka saurare mu dakyau! Kana da
nan da awanni arba'in da takwas ka kawo kuΙin fansar yaranka miliyan biyar
muddin kana son su Ζara shaΖar numfashi a duniya. Idan kuwa ka yi gangancin
furtawa Ζ΄an sanda wannan zancen toh shakka babu sunan msu matattu. Kar ka manta
muna sane da komai dake gudana a nan. Idan kunne ya ji toh jiki ya tsira."
Abba da tuni hawaye sun wanke mishi fuska yana shirin magana
ya ji sun daka tsawa.
"Don ubanku nace ku yi magana da Babanku! Ku tabbatar
masa kuna hannunmu!"
Sai kuma ji ya yi muryar Ummita ta zabga uban ihu, sai
Humaira mai kiran sunan Abba da iyakar muryarta. Da alama dai wani baΖar
muguntar aka yi musu.
Abba ya miΖe tsaye yana fadin.
"Ummita! Humaira! Ku yi hakuri don Allah kar ku
cutarmin da Ζ΄aΖ΄a, in sha Allah zan ΖoΖarta cika umarninku."
Jin haka sai aka sheΖe da wata iriyar dariya daga Ιaya Ιangaren
sannan aka ce.
"Idan ka yi hakan ka taimaki kanka da kuma su. Ka
kiyaye sharuΙΙanmu ko kuma ka yi dana sanin abin da zai biyo baya!"
Abba kuka yake sosai ya amsa da toh, aka datse layin kiran.
Har lokacin bai bar rawar jiki da kuka ba, muryoyin yaransa na mishi amsa kuwwa
a cikin kunne, ya rasa me zai yi, mene ne mafita? Ga shi nan dai an hana shi
yin furucin ga Ζ΄an sanda dole haka za su yi shiru da iyalinsa su tattauna a haΙa
kudaden a biya kudin fansa.
***
A can kuwa, Wizzy yana kammala magana da Abba ya fidda layin
a wayarsa ya kakkarya ya zubar, lokaci guda kuma ya mayar da layinsa. Suka dubi
juna suka kwashe da muguwar dariya. Humaira da Ummita aka titsa Ζeyarsu zuwa
cikin Ιakin. Babu laifi wajen da suka sauya ya fi wancan kyau, komai tsaf sai
Ζura kuma ga dukkan alamu sabon gida ne da ba a kammala aikinsa ba. BanΙakin
akwai ruwa har da butar alwala. Wajen dai ya fiye musu Ιayan amma kuma
hankulansu ba a kwance suke ba. Ai babu wani gata da za a yi musu alhalin su na
hannun azzalumai abin ya yi musu daΙi su samu kwanciyar hankali. Daga Ummita
har Humaira tun sadda aka garΖame su a Ιakin ba sa aikin komai sai kuka hakan
na da nasaba da jin muryar Abba da suka yi wanda gaba Ιaya sun fitar da ran
Ζara ji ko ganin wani cikin fuskokin da suka sani.
Wizzy kuwa bayan dawowar Badboy daga rufe Ζofar ya dube su
ya ce.
"Aski fa idan ya zo gaban goshi ya fi zafi, wannan
lokaci ne da zamu Ζara zage damtse kuma mu yi takatsantsan don cik umarninta, a
Ζarshe mu ma mu kwashi rabonmu, ta sallame mu."
Babba wanda ke faman hura hanci yana fitar da huci ya soma
magana a kausashe.
"Wai ni fa bana son rainin hankalin da take yi mana!
Matar nan tun da ta bamu aiki ba ta yarda ayi waya da uta sai rubutun saΖo. Ita
ba ta san hatsarin da ke tattare da hakan ba? Idan fa ta yi sakaci har wani ya
yi ya gani to fa akwai matsala. Sannan ta Ζi ta bayyana kanta sai Ιan aiken da
ta ke turowa, ita kenan ko kama mu za a yi ta tsira kenan? Ba mu san wace ce
ba, kuma ba mu san komai a kai ba, namu kawai aiwatarwa idan an cafke mu ta ci
bulus kenan?!"
Wizzy ya Ιaure fuska bai ce komai ba, ganin haka Badboy ya
cafe.
"Kai Babba ka iya kalamanka, ka sani koda wasa idan har
ba mu ne muka so ba, toh fa ba za mu taΙa kamuwa ba. Mun fi ta iya shege ai kai
ka sani. Ni fa duk ba wannan ne damuwata ba, yarannan su na hargitsa lissafina
amma kai Oga ka Ζi bani damar gwangwajewa. Kenan haka muna ji muna kallo za mu
bar su shikenan sun sha?"
Sai a sannan Wizzy ya kalle shi.
"Ba wannan aka umarcemu da yi ba, asalima don
horo ne ya sanya muka kai su tsohon gidan gonar can don kawai su shiha
taitayinsu amma tun farko ba ya daga cikin bajat dinmu. Kai ne ka fiye garaje,
ai na ce maka akwai lokacin da hakan za ta kasance, mu bari mana har mu samu
tabbacin kuΙaΙen nan za su faΙo hannunmu tukunna mana, sai mu yi duk abin da
muka ga zamu iya. Mu dai tabbatar ba mu kashe su ba don ba shi aka sanya mu
ba."
Suka yi shiru babu wanda ya tanka masa musamman Badboy da ke
jin haΖurinsa na dab da Ζarewa akan Ζ΄anmatan musamman Humaira da surarta ke
fisgarta.
***
Hankalin Anti Maijidda (babbar yayar mahaifiyar
Ummita ta Bichi) a tashe ta shigo babban falon na Mami da jama'a ke zaune ana
jajanta wannan lamari na su Humaira. Ba ta Ζasar gaba daya ta je Umarah sai a
jiya ta diro Kanon, ko gida ba ta je ba kai tsaye ta ce a sauke ta a gidan.
Tana shiga ta zube jikin Ζanwar Abba, Baba Amina da suka saba tun a baya
tana kuka sosai ana ba ta haΖuri. A lokacin ne kuma Mami ta shigo daga Ιangaren
Abba cikin dogon hijabinta, ta gama jin yadda aka yi da Abba da kidnappers din
akan kuΙin fansa. Jin muryarta su na gaisawa da makwaftan da ba su jima da
leΖowa gidan ba ya sa Anti Maijidda miΖewa kamar wacce aka tsiΖara ta hau tafi
raf raf har sau uku, wannan ya ja hankulan kowa kanta yayinda wasu suka shiga
tunanin kodai Ιatan Ummita ya girgiza kwakwalwarta har haka? Mami kuwa cak ta
tsaya kawai tana mai zubamata idanu. Maijidda kenan, macen da ba su taΙa raΙar
juna da alheri ba, babu wata jituwa da ta Ζara haΙa su tun bayan rasuwar Fatima
mahaifiyar Humaira.
Maijidda ta soma magana murya a Ιage kuma a kausashe.
"Ki zuba ruwa a Ζasa ki sha Maryam! Ki tara jama'arki
ku yi kiΙa ku yi rawa har da juyi! Yau burinki ya cika! Abin da kika jima kina
Ζullawa akan yarannan yau kin cika shi!"
Jin haka Baba Amina ta miΖe a firgice cikin kaΙuwa ta fisgo
hannun Maijidda.
"Maijidda ki shiga hankalinki mana! Ki yarda da Ζaddara
ki yi imani da ita. Wannan wane irin zantukan banza ki ke yi akan baiwar Allahn
da ta riΖi amanar Ιiyar Ζ΄ar uwarki da amana da kulawa tsawon shekarunnan koda
wasa Ummita ba ta taΙa kokawa da ita ba? Wane irin baΖin Ζazafi kike shirin
yiwa baiwar Allahn nan?!"
Anti Maijidda ta fashe da kuka sosai tana nuna Mami da
yatsa.
"Har abada ni Maijidda ba zan taΙa kaunarta ba, kuma ba
na jin zan yarda da ita koda ace gaba Ιaya mutanen duniyar nan za su taru su yi
mata kyakkyawar shaida! BaΖar azzaluma ce! Amina ni nasan wacece Maryam, ni zan
ba da labarinta! Don haka idan har bincike ake son yi na gaske daga cikin gida,
a soma daga kanta da kuma azzalumar uwarta!"
Wannan Ζazamin furucin ya sa Mami ta fusata sosai.
Hannunta na rawa kamar yadda dukkan gaΙΙan jikinta suke yi ta nuna ta da yatsa,
daΖyar maganarta ke fita saboda zuciyar da ta taso mata da kuma ruwan hawayen
da suka wanke mata fuska lokaci guda.
"Na shanye dukkan baΖaΖen maganganunki na tsawon
shekarunnan ba don komai ba sai domin albarkacin Ζ΄ar uwarki marigayiya Maimuna
da muka yi zaman mutunci da ita! Na kuma cigaba da jure duk wani cin kashinki a
dalilin Ummita jinin Maimuna ce da Naziru. Ban da haka ba ki da wata Ζima ko
daraja a idanuna!"
Baba Amina da mutanen Ιakin dakyar suka tsawatar aka kashe
zancen inda Mami ta fice daga falon cikin Ζunar rai zuwa Ιakinta inda Anna ke
zaune kuma tsaf ta ji dukkan abin da ya faru. Allah ya taΖaita lamarin Jannat
ba ta gidan, ta fita dubiyar wata Ζawarta da aka yiwa aiki a asibiti, da abin
zai fi haka Ιaci.
Anna ta dube ta sai kuma ta yi dariya.
"Maryama kenan, wannan shi ne sakamakon bautar da ki ka
yi na riΖon Ummita ko? Wannan ranar nake jira dama, ban kuma zaci zan gani nan
kusa ba. Shashashar yarinya! Ga shi nan tun ba a je ko'ina ba kin kwashi
kashinki a hannu. Da ace tun a farko kin ji maganata hakan da bai faru ba.
Yanzu sai kiyi kuka da kanki akan duk abin da ya faru."
Mami ba ta ce da Anna komai ba, sai ta fidda hijabin da ta
zumΙula ta Ιauki wayarta kawai ta zauna ta yi shiru tana aikin dannawa, Anna ta
cigaba da zabga ruwan bala'i, da Mami ta ga abin ba na Ζare ba ne, kawai sai ta
fice zuwa Ιakin su Raihana ta bar mata Ιakin.
***
Fadeel ya farka gami da Ζurawa silin idanu, shiru ya yi yana
ΖoΖarin tunano dalilin kwanciyarsa ciwo, a hankali kuma ya juya kansa ya dubi Ιakin.
Ibb ne kaΙai a zaune yana danna waya bai ma lura da farkawarsa ba. Ya lumshe
idanunsa lokaci guda komai ya dawo kwanyar kansa, a firgice ya miΖe zaune.
"Ya Salam!" Ya faΙi da Ζarfi yana mai fisge drip
din da aka sa mishi. Furucinsa ya sa Ibb mikewa da sauri ya nufo shi gami da
riΖe kafaΙunsa.
"Fadeel yi a hankali mana."
Jin haka ya dube shi da rashin kwarin jiki.
"No Ibb, kwana nawa nayi a nan? Humaira na hannun
kidnappers, za su kashemin ita. Ka bar ni na je nemanta."
Daidai nan Alhaji da Daddy suka shigo. Fadeel ya miΖe jiri
na kwasarsa yayinda Ibb ke Ιan riΖe shi, Daddy da sauri ya tarbe shi ganin
kamar zai faΙi ya ce.
"Fadeel kwantar da hankalinka, in sha Allahu za'a ga
Humaira."
Kawai sai ya ji hawaye sun zubomasa, wato za ma a gan ta ba
wai an ganta ba? Ya girgiza kai yana kallon Daddy amma sai ya kasa magana.
Suka taimaka suka mayar da shi mazauninsa. Daddy a nutse ya
karanta masa duk yadda suka yi da Abba ya kuma Ζara da faΙin.
"Yanzu haka ba mu jima da waya da shi ba, ya tabbatar
mana da cewar sun samu kira daga mutanen, sun kuma buΖaci kuΙi. Wannan damuwar
ba zai magance maka kowacce matsalar ba, addu'a da kuma sadaka ita zamu duΖufa
yi. Yanzu idan ka ce za ka fita nemanta, ta ina za ka fara? Ka san a inda suke
ne? Daji, cikin gari, kasuwa, Ζauye, kai ko ma ba a garin suke ba gaba Ιaya
wannan sanin Allah ne kaΙai don haka ka samarwa kanka Ζarfin zuciya ka dage da
kai wa Allah kukanka. Babu abin da ba ya magancewa."
Daddy ya cigaba da kwantar masa da hankali har da cewa koda
ace kudaden da Abban za su haΙa ba za su kai ba, shi ya ji ya gani zai san
yadda za'a yi a cika a bayar don su kuΙuta, balle kuma shi Fadeel din wanda
yake jin zai iya sadaukar da dukkan abin da ya mallaka a doron Ζasa don kuΙutar
rabin jikinsa daga hannun azzaluman nan. Sosai ya ji dadin zantukan Daddy, da
wannan ya lallaΙa ya yi wanka, brush, da alwala, Ibb ya ba shi kaya ya sauya.
Daga nan ya hau ramuwar sallolin dake kansa.
Bai kai ga idarwa ba sai ga Anti Amarya tare da Murja sai ko
Fu'ad da ya kawo su, hannun Murja riΖe da kwandon abinci. Ta gaida su Abban
sannan ta karasa ta ajiye gefen gadon. Gefe ta koma tana satar kallon Fadeel Ιin
da a kwana Ιaya kawai ya zabge. Zuciyarta na wata iriyar tafarfasa.
'Ka yi ka gama Fadeel, na rantse maka koda ace
Humaira ta fito ni Murja sai na kashe ta da hannuna. Ballantana ma ba za ka
Ζara ganinta ba.'
Ta yi maganar a zuci, su Alhaji suka tafi saboda yamma ta
kawo kai yayinda Ibb suka fita don yi musu rakiya. Fadeel na idarwa ya dubi
Anti Amarya ya gaishe ta, ta amsa tana mishi sannu. Ido ta Ιan yiwa Murja hakan
ya sa ta saurin gaida Fadeel, ya amsa ba tare da ya kalleta ba.
Nan suka zauna har sai da Fadeel ya Ιan sha ruwan
shayi dakyar amma sam ya Ζi yarda da cin abinci, tunaninsa ko a wane yanayin
Humaira take? Watakila ma ko abincin ita ba a ba su sun ci ba. Wannan ya
daΖilar da shi daga ci.
***
Sahabi saurayin Ummita kullum sai ya zo gidan ya
gaida Abba da Mami, gaba daya ya komaΙe ya rame tsabar tunanin Ummita. Iyaye da
Ζ΄an uwansa babu wanda bai shigo jajantawa ba. Hakanan Ζ΄an makarantar islamiyyar
su sun zo sun kuma yi saukar Alkur'ani akan Allah ya bayyana su. Hatta da yan
makarantar su Ummita na boko sun zo har da malaman makarantar an jajanta. Aka
yi addu'a suka tafi.
Labarin dai yana ta yaΙuwa don har waΙanda su Abban
ba su ma sani ba sun zo sun taya su jaje, da yawansu a social media suka ci
karo da shi. Mubarak dake Ghana yana jarrabawar Ζarshe hankalinsa gaba daya
yana Kanon, ba don Abba ya ce kar ya zo ba ya zauna har ya kammala da tuni ya
dawo. Hakanan su Yassar ba su zo ba. Amma sosai abin ya taΙa su duk da Ζiyayyar
da suke yi musu.
Ζangaren Futuha kuwa Ζ΄ar Dubai, kasancewarta
mai mu'amala sosai da yanar gizo sai ga abin nema kuma ya samu. Bidiyo sosai ta
yi tana kuka ga hotunan Ummita da Humaira daga Ζasa ta Ιora a shafinta tana
addu'ar Allah ya bayyana su a Ζarshe ma har da sanya muryar shahararren Malamin
nan wato Sudais yana addu'a. Koda ta Ιora hankalinta kwance ta shiga duba yadda
ba a Ιauki dogon lokaci ba bidiyon ya yaΙu, nan fa jama'arta suka fara jajanta
mata su na tambayar dama Humaira mai shafin Deelsha's Delicacies yar uwarta ce?
Da yawa ma wadanda ba su san Humairar ba ko shafinta sai lokacin suka dinga
followinh dinta, lokaci guda shafinta ya yi jama'a fiye da dubu talatin.
Hakanan shafin Ummita ma ya yi jama'a.
Raihana tana kallon duk abin da ke wakana amma ba ta magana,
karshe ma sai ta kashe wayarta gaba daya ta ajiye. Tun da Abba ya shaida
musu da kuΙaΙen da aka ce a bayar na fansar Humaira da Ummita ta ke jin Ζ΄ar
nutsuwa, ko ba komai kenan su na lafiya kuma Abban ma ya tabbatar musu ya ji
muryoyinsu amma bai ce musu ga a yanayin da ya ji ba gudun tayar musu da
hankula.
***
Fadeel da Ibb suka shirya tsaf a washegari zuwa gidan
su Humaira kamar yanda Fadeel din ya nema. Hankalinsa ya kasa kwanciya da
zamansa a asibiti alhalin ba a ga Humaira ba, kuma bai je ga iyayenta ba.
Wannan ne ya sanya su Alhaji goyamishi baya don haka ana ba shi takardar
sallama ya kama hanyar gidan.
Sun samu tarba na mutunci daga Abba, Tasleem tun ganin da ta
yiwa Fadeel matsayin saurayin Humaira ya zo jajantawa ta ji hankalinta ya yi
mummunan tashi. Kishin nan daΙaΙΙe na Humaira ya taso ya soma cin
zuciyarta. Har gobe akwai son Fadeel a Ζirjinta, ta kuma tabbata da ace shi ta
aura da yanzu wani labarin ake ba wannan ba.
Kusan lokaci guda suka shigo gidan da Fadeel anan ta gan
shi, shi kuwa bangaren Abba suka nufa inda Ζasim da ya yi musu iso ya raka su
ciki. Fauziyya ce ta yi mata rakiya gidan, tana kuma lura da sauyin da ya zo
mata lokaci guda sadda Ζasim ya dawo yana shaida mata ai manemin auren Humaira
ne. Ta yi shiru ba ta ce mata komai ba tana Ζara nazarinta.
A falon ta bar Fauziyya ta faΙa Ιangaren Anna tana
huci. Nan ta tarar da ita zaune da Jannat wacce ke zaune tana taunar
gasasshiyar kazar da ta siyo suna hira da Anna kai ka ce babu wani tashin
hankalin da ake yi a gidan. Ganin yanayinta ya sanya su dubanta.
"Toh mai ciki, yau kuma wa ya taΙo ki?"
Ta zauna idanunta suka cicciko da kwalla yayinda zuciyarta
ke faman tafarfasa. Kwafa ta yi kana ta amsa.
"Wai Fadeel na gani ya zo jajantawa Abba fa? Har yanzu
dama yana tare da Humaira? Shi ne don munafunci Humaira ta ci amanar Mami ta Ιoye
zancen?"
Murmushi Jannat ta yi.
"Ke ban da abinki ina Humairar take a yanzu? Kina
tunanin shirin na wasa ne za ta dawo, ai daga can inda take sai wata duniyar
kuma ba wannan da muke ciki ba. Duk fa wanda ya samu dama ya dama. Kuma
da kike wannan maganar ba yanzu gashinan kin auri Hamza ba? Ba kya sonsa kika
bari ciki ya shige ki?"
Tasleem ranta ya Ιan yi sanyi jin yadda Anti Jannat ke fadin
kaddarar Humaira kai ka ce ita ta rubuta hakan. Batun cikinta ya Ζara jefata
damuwa, dama ba da son ranta ta samu ba kuma Hamza ya rantse sai ya yi mugun saΙa
mata idan ta zubar.
"Wallahi Anti idan har zan samu na auri Fadeel zan iya
kashe ko nawa ne a yimin aiki a kan Hamza ya sake ni. Anti wai kin taΙa ganin
Fadeel kuwa da irin yadda ya haΙu? Wallahi ba zan iya zuba idanu wata ta
kwacemin shi ba."
Anna tsohuwar banza ta kwashe da dariya madadin ta yi kwaΙa
akan wannan haramcin da ake aikatawa sai ma ta ce.
"Kina da Jannat Firdausi ai babu ke babu fargaba. Yadda
aka yi wancan haka wannan ma zai kasance labari."
Suka yi dariya. Can kuma Jannat ta Ιan jinjina kai.
"Ko wane ne wanda ya aikata wannan kidnapping din ya yi
matuΖar burgeni, da ace ina da damar ganinsa sai na mishi babbar kyauta. Sai
hakan ya zo mana da nasara kuma akan gaΙa, Boka ya tabbatarmin da cewa Humaira
a can za ta haΙu da ajalinta. Itama Ummita babu tunanin za ta rayu balle har su
samu damar kuΙuta su dawo. Kawai dai zan so dawowar ita Ummita, yarinyar ta iya
bauta."
Tasleem ta yi murmushi.
"Nima dai Ummita ba ta yimin komai ba, ba ni da wani
Ζulli da ita kamar Humaira. Wallahi Anti na tsane ta na kuma tsani duk wani mai
sonta."
"Har da ni kenan!"
Suka juya don ganin mai furucin a razane. Tasleem ce ta
soma kauda kanta gami da jan guntun tsaki ciki-ciki ba tare da ta ce
uffan ba.
Raihana wacce ta gama jin dukkan munanan maganganunsu
ta tako tsakiyar dakin sosai ta cigaba da magana.
"Har da ni kenan! Wannan ba Ummita ko Humaira kaΙai ku
ka tsana ba Anna, har mu jinin Abba. Na yi mamaki dama da Anti ba ki Ιau mataki
akan abin da Humaira ta yi maki a kwanakin baya ba, ashe dama ke tarkon da kika
Ιana babba ne? Ashe wannan damar kike jira? Kai duniya! Mutum ya Ζi mutum har
ta kai yana mishi fatan mutuwa? Me suka tare maku? Ku ji tsoron ranar da haΖΖin
su Humaira zai kama ku!"
"Me kika ji ance da za ki rufe mutane da faΙa tamkar
kina magana da Muhsin ko Waleed?"
Jannat ta furta a ΖoΖarinta na shanye firgicin da ta Ιan
shiga, toh koda ace ba su da hannu a satar Humaira da Ummita, ai wannan Ιarin
zancen da suke yi zai iya jawomusu matsala tunda ana kan bincike ko yau Ιin da
safe sai da D.P.O ya zo wurin Abba.
Raihana ta yi murmushin takaici.
"Kar ku yi tsammanin ban ji mugun Ζullin da ku ke yiwa
bayin Allahn nan ba. Amma ku sani, Allah na tare da bayinSa a duk inda suke
kuma cikin kowane hali. Na rantse muku, duk iya yinku, duk iya ΖoΖarinku, ba za
ku iya kawo sanadin koda karta a fatarsu ba balle a kai ga rasa rayukansu ba
face sai da iznin Allahn da ya halicce su. Ku yi dukkan kokarinku, akwai ranar
Ζin dillaci."
Tana kaiwa nan ba ta ko Ζara kallonsu ba balle ta ji me zasu
ce ta sa kai ta fice daga dakin a guje zuwa nasu Ιakin wanda suka mallaka da su
Humaira a baya. Haka kawai sai ta buΙe sif din kayan Humairar da Ummita ta
fiddo abin da ta san sun fi so cikin kayansu ta yi ta kuka. Lamarin da ya sanya
Mami hana ta kwanan Ιakin sai dai nata Ιakin. Ba za ta iya misalta baΖin cikin
da ta ke ciki ba sanadiyyar Ιatan Ζ΄an uwannata. A gefe guda ga baΖin cikin
kasancewar Jannat yar uwa ga Maminta ballantana a kai kan Tasleem da take ji
kamar ta shaΖe ta. Sai ko Anna da har ba ta kaunar ganin fuskarta a kwanakin
nan tun da ta nuna ba ta wani bakin ciki da Ιatan yan uwanta.
***
Abba ya yiwa su Fadeel tarba na mutunci da dattako, gaba Ιaya
idan ka ga Abba sai ya mugun ba ka tausayi sakamakon yadda ya koΙe ga kuma
rama.
"Ka yi hakuri Fadeel, in sha Allah Ζiris ya rage na
kammala haΙa kuΙaΙen fansar su, lafiya kalau za su dawo hannunmu. Kai dai ka ci
gaba da addu'a."
Fadeel ya Ζara yin Ζasa da kai, Abban da ya ke da burin ya
wayi gari ya gan shi a gabansa da zummar neman auren Humaira, su yi hira da
dariya tsakaninsu sai gashinan ganin da suka yiwa juna na farko ba mai daΙi ba
ne ko kaΙan. Zuciyarsa ta yi rauni nan da nan kuma ya ji idanunsa sun
kawo ruwa daΖyar ya iya daurewa ya amsa.
"Toh Abba, Allah ya kuΙutar da su."
Abban ya amsa da amin, yana son ya ce idan da yadda zai
tallafa, a ba shi dama amma ba ya so Abban ya ga kamar ya mishi katsalandan
wannan ne dalilin da ya sa shi jan bakinsa ya yi shiru. Sun Ιan jima anan har
Abban ke faΙamusu cewa Kawun Humaira suna hanya daga Maine, Ζasar Nijar. Suka
yi musu fatan isowa lafiya a karshe dai Ibb ya soma yiwa Abban sallama kan zasu
wuce ganin Fadeel kamar ma ba shi da niyyar motsawa.
Bayan fitarsu Abba ya yi tagumi cike da tunani, a yanzu
duka-duka dai abin da ya haΙa bai fi miliyan shida ba, ya kuma sani muddin ba
gidansa da suke ciki zai siyar ba bayan motocin da ya sa kasuwa ya siyar, to fa
babu ta inda zai samu cikon miliyan goma na fansar yaransa. Yana wannan halin
ne Mami ta yi sallama ya amsa gami da ba ta damar shigowa. Ta shigo sanye da
hijabinta ta zauna gefensa fuskarta dauke da damuwa ta ce.
"BaΖi ka yi ne?"
Ya numfasa.
"Eh, yaron nan Fadeel ne ya zo da abokinsa, ba su jima
da tafiya ba."
Ta Ιan yi jim sai kuma ta numfasa ta ce.
"Allah Sarki."
Daga haka ba ta Ιora komai ba, shiru ya biyo baya kafin Abba
ya girgiza kai ya ce.
"Maryam, an zo gaΙar da dole sai na siyar da gidannan
na cika kuΙin fansar yarannan. Idan ya so sai mu koma wanda bai fi shi ba,
lokaci na Ζurewa sosai, kaina ya Ζulle gaba Ιaya, dole na tashi na nemi mai
siya ko kaΙan a kuΙin ne aka ba ni zai isa na cika na kaiwa wadannan
mutanen."
Murmushi Mami ta yi.
"Kamar ka san shawarar da na zo na ba ka kenan Abban
yara, sai kuma naji dadi da ka kasance mai yarda da Ζaddara. Siyar da gidan zai
fiye mana alheri matuΖar dai za su bar yaranmu su dawo garemu."
Abba ya jinjina kai.
"Hakane Maryam, dama na riga da na yi magana da
lauyana, na kuma bada damar an sa gidannan a kasuwa, ina ta tunanin ta yadda
zan sanar maki kada ki ji abin daga sama shi..."
"Haba Abban yara, wace irin magana kake yi ne? Mene ne
ciki don ka sadaukar da abin da yake mallakinka don fansar yarana? Idan da ace
yau nima na mallaki wata dukiya kana tunanin ba zan iya sadaukar da ita domin
ceto ransu ba? Don Allah kada ka sa naji kamar kana bambanta Humaira da Ummita
da yan uwansu."
Tun faruwar al'amarin na su Humaira, Abba bai yi koda
murmushi ba sai a yanzun, ya kamo hannun Mami ya riΖe gam cikin nashi.
"Ina kaunarki Maryam, Allah ya yi maki albarka. Nagode
da kika fahimce ni."
Itama murmushinta ta faΙaΙa gami da shafar gefen fuskarsa.
"Nima ina kaunarka. Yanzu ajiye godiyarnan, ka daure ka
sa abu a cikinka sai a je a san ya za'a yi. Ina fatan dai ba ka faΙawa
D.P.O yadda ku ka yi ba ko?"
Abba har ya buΙe baki zai magana sai ya tuna yadda suka yi
da D.P.O da safe. Sun tattauna ya sanar da shi komai bai rufe ba akan batun kuΙaΙen
fansa da aka nema.
*_Koda wasa YallaΙai kar ka nunawa kowa ka faΙamin yadda ake
ciki. Komai kusancinka da mutum, ka Ιoye wannan tattaunawarmu saboda mutane su
na da ban tsoro, koda ace ka faΙawa wanda ka yarda da shi yadda muka yi, to fa
zai iya sanar da wani maΖiyin. Kaf duniya tun da dai daga ni sai Alhaji Bashir
(Daddy) muka san da hakan, to ya tsaya iyakar nan, koda ace sun Ζara kiranka a
waya kar ka bari wani cikin iyalinka ko ma waje ya sani. Mu kuma zamu yi
iyakar yin mu, mu yi kokari mu cafke su duk sadda ka tashi kai musu kuΙin._*
"Ya naji ka yi shiru?"
Mami ta nemi sani tana mai Ζuramasa idanu. Ya numfasa.
"Babu komai Maryam. Ina tsoron na furta masa su ji
labari tunda sun gargaΙe ni. Bana fatan a samu matsalar da yarannan za su rasa
rayukansu."
Ta jinjina kai.
"Ina ji a jikina za su dawo gida cikin aminci."
Daga haka ta jawo kayan abinci ta shiga zubamasa tana mai
lallaΙa shi don ya ci. Dakyar ya tsakuri kaΙan ya miΖe ya yi shiri ya fita don
ganin ya kammala kafin ya kai.
Cikin rashin nasara, aka rasa mai siyan gidan Abba, a karshe
dai tayin da ya Ζi karΙa a farko na iyayen Fadeel hakanan ya karΙi cikon
miliyan huΙu ya haΙa aka tashi kuΙin fansa, babu abin da ya rage sai jiran waya
daga kidnappers don a ji lokaci da kuma wurin da za a miΖa kuΙin. Mami ba ta
san ya aka yi da batun gida ba, Abba dai ya ce mata an samu an haΙa kudade.
Daga nan bai Ζara ko harafin A ba.
***
Humaira da Ummita na rakuΙe a lungu guda na Ιakin sun yi
shiru don zuwa lokacin kukan ma ya Ζi fita, aka banko Ζofar Ιakin aka shigo. Su
ukun dai da suka zame musu tamkar baΖaΖen kumurci su ne suka shigo. Suka Ζura
musu idanu tamkar za su lashe su, Wizzy kamar koyaushe sigari ne a hannunsa, ya
fesar da hayaΖin ya dubi Babba da Badboy cikin murmushi ya ce.
"Ni zan fara, ku kuma sai ku biyo baya."
Ba su ji dadin wannan hukuncin ba amma babu yadda suka iya,
hakanan suka lashi lebbansu suka ja gefe. Shi kuwa kai tsaye ya Ζarasa ya
finciko Ummita wacce ta ΖanΖame jiki guri guda ga jikinta dake masifar rawa.
"Ina za ku kai ta? Ku yiwa girman Allah ku yi
hakuri."
Humaira ke zancen cikin ruΙu da tashin hankali. Suka kwashe
da dariya.
"Haba Baby, kema ai zan zo kanki. Duk inda zan kai Ζ΄ar
uwarki kema za ki je. KuΙin fansarku aka kawo, za a tafi da ku gida."
Humaira sam zancen bai shige ta ba balle Ummita da ba ta san
lokacin da ta shiga kuka sosai ba, su na jan ta tana tirjewa, Humaira na zabga
uban ihu suka dauke ta da mari suka fidda kyalle suka rufemata baki da idanu.
Wizzy haka ya ja Ummita har sai da ya dangana ta da wani Ιakin.
Humaira da suka fita suka rufe kamar ta yi hauka haka ta
dinga bugun Ζofar tana gurnani tamkar wacce ake zarewa rai. Babban
fatanta bai wuce su ceto Ummita da ko ihunta ba a ji ba sakamakon rufemata baki
da aka yi da kyalle.
Ummita na ji tana gani Wizzy ya keta alfarmarta. Tsananin
azaba ya sanya ta sumewa ba tare da sanin inda kanta yake ba. Shi kuwa ya fito
yana sharΙar gumi, ya dubi su Badboy cikin annashuwa ya ce.
"Ku bari shegiyar ta farfaΙo sai ku Ζara farr mata,
suman dadi ta yi."
Suka kwashe da muguwar dariya. Yana kai wa nan ya shige
wurin Humaira.
Tana ji an bude Ζofar ta yi saurin karasawa gami da shaΖe
wuyan rigar Wizzy tana um um saboda bakinta da ke Ζulle ta ma kasa magana. Ya
yi dariya gami da tura Ζofar da Ζafarsa ta baya ya damΖe hannunta.
"Haba my love? Kokawarnan da kike wani sanyamin Ζarfi
ai sai ki jigatar da kanki tun ma ba a je ko'ina ba."
Daga nan ya soma kiciniyar raba ta da kayanta yana taΙa wasu
Ιangare na jikinta, nan da nan ta ji kanta ya soma wani irin sarawa, wani irin
baΖin ciki da ba ta za ta iya kimantawa ba ya tsaya mata cak a Ζahon zuci. A
sadda Wizzy ya yi nasarar keta rigar dake jikinta, a lokacin ne gaba Ιaya
tsikokin jikinta suka mimmiΖe. Idanunta suka Ζara turuwa suka yi ja, ba ta san
lokacin da ta shaΖo wuyansa ba har ya shiga kakarin mutuwa. Duk iya Ζarfin da
ya sa da zummar Ζwatar kansa ya kasa, ga shi ba damar ihu saboda koda ya yi
abokan aikinnasa za su yi zaton na lafiya ne. Haka suka Ζarasa har jikin Ζofar
da ba ta rufe gaba Ιaya ba.
Anan ne Badboy da ke zaune saitin Ζofar ya hangi hannun
Wizzy na lilo, da wani irin gudu-gudu ya tunkari Ζofar, shima Babba ya mara
mishi baya. DaΖyar suka tura Ζofar ta buΙe. Abin da suka gani ya yi mugun
rikita su, Humaira dai ta zame musu tamkar wata ΖaΖΖarfar damisa, daΖyar da suΙin
goshi suka Ζwace Wizzy a hannunta, Babba ya fice da shi daga dakin yayinda
Badboy ya tunkareta da niyyar kifamata mari sai dai yanayin da ya ga ta taso ta
yi kansa ne ya sa shi ficewa babu shiri. Nan ta kife zaune tana rirriΖe kanta
dake azabar sarawa tana huci ga uban gumi kuma ga baki a Ζulle. Kukan nan da ta
saba yi ta shiga rerawa mai mugun tsuma zuciya, ta fi rabin awa a haka har ba
ta san an shigo da Ummita an watsa ta a kusa da ita ba.
Abin da Humaira ta aikata ne ya sanya Wizzy dakatar
da su daga ketawa Ummita haddi, ya ce su kyale su kafin su kashe su labari ya
sauya tunda gobe za su cafki kuΙadensu. Da wannan suka rufe su gam suka bar
gidan su Babba da Badboy na Ιacin ran ganin samu da kuma rashi lokaci guda.
Ganin haka Wizzy ya yi musu alΖawarin zai ba su sabuwar yarinyarsa da ya yi a
wurin mashayarsu kowannensu ya more da ita, sun Ιan ji dadin hakan tunda ko ba
komai ita bariki ke yayi a lokacin. Kowa kuma mararinta yake.
Ummita da har lokacin ba ta da kuzari, kusan ma yanzun suman
zaune ta yi. Ga uban azaba da ta ke ji a Ζasanta, gaba Ιaya hawayenta ya kafe
ta ma kasa koda kukan, tun shigo da ita abu Ιaya ne a bakinta take furtawa
sanadiyyar Ζyallen da aka ciremata, Innalillahi kawai take ambato daga farko
har Ζarshe, wannan daren babu wanda ya runtsa sai Humaira da bayan gama
koke-koken wani bacci marar dalili ya Ιauketa kamar yadda ta saba.
***
A firgice Raihana ta farka daga mummunan mafarkin da ta yi
wai an soka wuΖa a wuyan Ummita, Humaira kuma tana kwance cikin jini. Wani Ζara
ta saki mai firgitarwa ta zabura ta miΖe daga gadon Mami ta nufi hanyar fita
daga Ιakin. A hanyar Ζofa ta ci karo da Mami kasncewae asuba ta kawo kai, Abba
ya fita masallaci. Cikin tsananin ruΙani Mami ta riΖe ta.
"Meyafaru Raihana?"
Ta ruΖunΖume Mamin sai kawai ta fashe da kuka mai tsanani.
Mami ba ta ce mata komai ba ta shiga shafar kanta. Don kanta Raihanar ta
sassauta kukan sannan ta Ιago kai ta ce.
"Mami nayi mafarki marar daΙi akan su Humaira. Har
yanzu ba su kira Abba a waya ba? Mami a kai kuΙaΙennan a dawomin da Ζ΄an uwana
yanzu kafin lokaci ya Ζure. Kar su kashemin su."
Mami ta riΖe hannuwanta.
"Kar ki damu da mafarkin da ba lallai ya kasance
gaskiya ba. Ki yi addu'a da fatan alheri. Ina mai tabbatar maki babu abin da
zai faru da su, lafiya kalau za su dawo gidannan ki gan su."
Raihana ta Ιauki maganganun Mami kawai don ta kwantar mata
da hankali ta faΙi, amma ina da ta ke da tabbacin ganin Ζ΄an uwannata cikin
kwanciyar hankali? Haka dai ta dinga lallaΙa ta Ζarshe ta samu nutsuwa ta fice
ta Ιora alwala ta tayar da sallah amma har sannan kirjinta na dukan tara tara.
Wannan dalilin ne ya sanya ta tsaya ta yi addu'a sosai har ta jawo AlΖur'ani ta
karanta ta roΖarwa yan uwanta tsari daga sharrin dukkan masu sharri.
***
Ζarfe shida na safe daidai sai ga kiran Wizzy ya shigo wayar
Abba. Abba ya Ιaga jiki na rawa. Nan yake tambayar ko kuΙaden sun samu,
ya amsa da eh. Daga nan ya yi mishi kwatancen inda za su haΙu, ya Ζara da faΙin.
"Ina Ζara gargaΙinka, kar ka sake ka yi kuskuren zuwa
da jami'an tsaro idan ba haka ba a gabanka zan yanka wuyan Ζ΄aΖ΄anka."
Abba ya hau girgiza kai tamkar Wizzy na gabansa.
"Aa aa, ni kadai zan zo. Ba zan saΙa alΖawarinku
ba."
Daga nan kit aka kashe wayar, ya Ιaga kai ya dubi lokaci,
yanzun shida da mintuna, an kuma ce mishi bakwai daidai ya isa wannan dalilin
ne ya sanya shi miΖewa ba shiri ya janyo jakar kuΙaΙen. Tunanin ya kira D.P.O
ya sanar masa yake amma kuma yana jin tsoron kar su cutar da su Humaira sai dai
ya Ιan yi shahada ya dannawa D.P.O kira, suna cikin magana Mami ta iso, Abba
bai ko lura da ita ba don hankalinsa ya yi gaba. D.P.O ya ce za su fito su ma
cikin kayan gida da kuma motar da ba ta aiki ba, ya kwantarwa da Abban hankali
ya nunamasa kar ya damu su Humaira za su kuΙuta a hannun ko ma su waye.
Mami ta dubi Abban a rikice bayan ya gama wayarsa.
"Abban yara sun kiraka ne naji kana sanar da
D.P.O?"
Bai kalle ta ba ya ja akwatin jiki na tsuma ya ce.
"Eh Maryama mun yi waya da su. Bari naje kar lokacin ya
Ζure mintuna kawai suka ba ni."
Mami ta sha gabansa.
"Meyasa za ka yi ganganci da rayuwar yarana? Mene
dalilin sanar da D.P.O? Ba ka tsoron su cutarmin da su?"
Sai ta fashe da kuka jikinta babu inda ba ya rawa.
Abba bai da lokacin rarrashinta sai kawai ya ce.
"Kiyi hakuri, babu abin da zai faru da su lafiya kalau
zan maidomaki su in sha Allahu. Ku sanya ni addu'a har na dawo dai."
Yana kaiwa nan ya fice riΖe da muΖullin motar Jannat da
Mamin ta aro masa tun jiya an kuma zuba mai dama jiran su kira kawai ake.
Tasleem dake laΙe ta yi baya da sauri zuwa dakin Anna jikinta har tsuma yake.
Abba yana hanya ma sai ga kiran Fadeel, Abban ya kwantar
masa da hankali ya ce sun yi waya yanzun yana hanyar fita amsar su. Ya tambayi
Abban inda suka ce, kamar ba zai faΙi ba sai dai ya faΙamasa. Fadeel ya ce zai
biyo bayansa. Dakyar Abban ya hana shi gudun samun matsala.
***
Bakwai da mintuna uku Abba ya iso dab da kogin da
suka yi masa umarni. Yana tsayuwa ya ji wayarsa na ringing. Jiki na rawa ya
fiddo ya Ιaga.
"Mun ganka, ka fito da jakar ka ajiye gefen wannan
kogin, mu kuma za mu turomaka yaranka. Ba ruwanka da kalle-kalle, ka saukar da
kanka Ζasa har ka ajiye ka bar wurin."
"Toh."
Yana faΙin haka a gaggauce ya ja jakar ya fita. Bisa
bin umarnin nasu kansa yana Ζasa amma fa ta Ζ΄an maza kawai yake sai dai
zuciyarsa na ta harbawa da Ζarfi. Sunayen Allah ya shiga ambato da fatan samun
matsaya.
Wizzy kuwa da suke can gefe Ζasan wata Ζatuwar bishiya, su
na ganin fitar Abban ya sanya Badboy da Babba cicciΙar su Humaira da suka ba su
kwayoyi suke ba a cikin hayyacinsu ba suka nufi motar Abban da nufin sanya su
ciki. Kiran da Wizzy ya samj ne game da batun zuwan Ζ΄an sanda wurin ya sanya
shi fitowa gami da dakawa su Badboy tsawa.
"Ku dawo da su mu bar nan! Shegen ya kira Ζ΄an
sanda!"
Jin haka sai kuwa aka soma harbi, dayake Allah ba azzalumin
bayinSa ba, sai kawai suka yashe su a wurin sakamakon harbin da aka yiwa Badboy
a kafaΙa ya saki Ζara, da gudu suka koma cikin motar kiii suka tayar suka
soma yunkurin barin wajen.
Abba da sai kawai maganganu ya ji da Ζarar harbi bai san
sadda ya juya ba a ruΙe hantar cikinsa na kaΙawa don ya gama saddaΖarwa su
Ummita aka harba. Sai dai ganinsu a yashe a tsakar filin ya sa shi sakin jakar
kuΙin ya nufe su da gudun da a shekarunsa bai san ma zai iya ba. Su Wizzy tuni
sun bar nan su na cizon yatsar wannan babbar asarar da suka yi. Yayinda D.P.O
da mutanensa suka Ζaraso cikin jin zafin kubcewar da suka yi musu.
"YallaΙai ba kuka ya kamata ka yi, kamata ya yi mu miΖa
su asibiti."
Jin haka sai Abban ya ji kamar an masa tuni, ya Ιaga
Humaira, macen Ζ΄ar sandar da ta biyo su ta Ιaga Ummita suka sanya su a mota sai
asibiti. Jakar kuΙaΙen kuma yana cikin motar Ζ΄an sandan suka mara musu baya.
Fadeel da ya kasa haΖuri ya biyo bayan Abban, kafin ya kai ga Ζarasawa ya hango
Abba a mota kawai sai ya yi reverse ya bi bayansu jikinsa babu inda ba ya kaΙawa.
Yana son ya kira Abban don jin ko an same su amma yana tsoron jin akasin haka
daga gareshi wannan ne ya hana shi kiran gaba Ιaya.
***
Murja ta jima tsaye jikin tagar falo tana hangen fitar
Fadeel a gigice. Ranta idan ya yi dubu toh ya Ιaci. Hankalinta kuwa idan akwai
abin da ya fi gaban tashi toh ta ya yi wannan dalilin ne ya sanya ta komawa
cikin daki da sauri-sauri ta Ιauko gyalenta sai ko waya da jaka ta fice daga
gidan a birkice har Anti Amarya wacce ta fito daga nata Ιakin tana tambayar ko
lafiya kuma ina za ta je amma babu amsa.
***
Kasancewar tare suka isa asibitin da Ζ΄an sanda wannan ya sa
a gaggauce aka karΙi Humaira da Ummita zuwa emergency. Abba ya kasa zaune balle
tsaye, ban da hawaye babu abin da ke fita daga idanunsa, ga jiri na kwasarsa
yana ta ambaton sunan Allah kamar zai ciri baki. Daidai lokacin Fadeel ya shigo
a birkice ya Ζarasa ga Abba.
"Abba sun fito? Su na ina? Me ya same su?"
Dukkan waΙannan tambayoyin ba a hayyaci yake yin su ba.
Abban ma da ba a wani nutse yake ba sai ya kasa tanka mishi kawai sai ajiyar
zuciya da kallo ga lebban na motsi amman ko harafi guda ya kasa fitarwa sai
D.P.O ne ya karΙi zancen ya yiwa Fadeel bayani.
"Ka kwantar da hankalinka, in sha Allahu babu abin da
zai faru garesu. Likitan ya tabbatar mana ga dukkan alamu kwayoyi aka Ιura musu
amman in sha Allah za su yi iyakar ΖoΖari a kansu."
Fadeel ya dafe kansa ya yi juyin, ya yi safar ya dawo ya kai
marwar amma wannan kalmar ta ya kwantar da hankalinsa ya kasa samun matsaguni a
zuciyarsa. Kwayoyi? Ya ma rasa inda zai jefa zancen a kwakwalwarsa ballanta ya
samu ya yi aiki da shawarar D.P.O Salahuddeen.
***
A can gida kuwa, Tasleem tun sadda ta kai labarin tafiyar
Abba fanso su Humaira, Jannat ta dauki waya hankali tashe ta kira Bokanta.
Kaca-kaca suka yi sosai tana zaginsa akan ita fa ba su yi haka ba. Wannan ya
sa Boka tun a wayar ya ci alwashin sai ta girbi wannan tozarcin da ta yi
masa. Kasancewar idanunta sun rufe ruf sai kawai ta ja mugun tsaki ta katse
kiran.
Awa bai fi Ιaya tsakani ba, sai ga wayar Abba zuwa ga Mami,
a gaggauce ya sanar da ita kuΙutar su Ummita ya kara shaida mata cewar su na
asibiti. Hankali a mugun tashe suka fice tare da Ζasim da Raihana wacce lokaci
guda wani mugun zazzaΙi ya rufe ta musamman jin cewar su na asibiti. Suka yi
kiciΙus da Kawun Humaira da matarsa Hajjo wadanda isowarsu kenan garin. Ba su
tsaya yi musu dogon bayani ba, Kawu ya bi su yayinda ya ce Hajjo ta tsaya ta
jira dawowarsu a gida.
***
BAYAN AWANNI...
Mummunan labarin da ya iske su Abba na keta alfarmar da aka
yi ga Ummita ya sanya shi sumewa bai ko iya jin Ζarshen ba balle ya san ko har
Humairar ma an taΙa. Nan aka kwashe shi shima don ba shi taimakon gaggawa.
Raihana kuka kamar ranta zai fita yayinda Mami ke taya ta. Kawu da Fadeel kuwa
tashin hankalin da suke ciki ba zai misaltu ba. A gabansu aka fiddo su bayan an
yiwa Ummita Ιinki na mugun raunin da aka ji mata aka sauya musu Ιakunan zuwa na
hutu, daki mai gado biyu. Fadeel ya Ζurawa Humaira idanu kamar kirjinsa zai
fashe haka yake ji, nan take idanunsa suka kaΙa jawur. Gaba Ιaya ta lalace ta
yi rama tamkar wata halittar ce ba ita ba sai ko hancinta da ya Ζara fitowa.
Har aka shige da su bai iya kauda kansa ba. Shi ya yi Ζarfin halin biyan dukkan
abin da aka kashe har da na kama Ιaki.
Cikin ΖanΖanin lokaci labarin kuftowar su Humaira ya
cika gari, mutane da waΙanda suke dangi da ma yan uwa na gari suka dinga
tururuwar zuwa yi wa su Abba barka, babu wanda aka bari shiga wajensu, hakanan
labarin abin da ya afku gare su bai fita ba. Yan jarida kuwa suka dinga yaΙa
rahoto, hakanan social media ta dauka. Futuha mutanen Dubai ta Ζara yin
bidiyo mai nuni da damuwa da kuma farin ciki tana shaida wa jama'a cewa an ga
Ζannenta. Nan aka hau taya ta murna sosai.
Mutanen Bichi da labari ya iske su su ma baa bar su a baya
ba. Anti Maijidda ta yi kuka kamar ranta zai fita jin labarin keta haddin da
aka yi ga Ummita, matsayinta na babbar yaya ga uwarta ya sa Abba sanar da ita a
sirrance.
Sahabi kuwa baki har kunne, sun zo shi da abokansa
yayinda mahaifinsa takanas ya zo ya taya Abba murna da addu'ar Allah ya kiyaye
gaba.
Kwanakin su Humaira biyu suka dawo hayyacinsu. Ummita
ce ta soma farfaΙowa, ranar Allah ya taΖaita Anti Maijidda na zaune tare da
Baba Amina sun yi jugum su na dan hira jefi-jefi hannuwansu riΖe da casbaha.
Wani gigitaccen Ζara Ummita ta saki da ya yi masifar tayar da hankulansu.
"Wayyo Allahna! Kar ka kashe ni! Ka rabu da ni! Na haΙa
ka da Allah ka rabu da ni!! Wayyo Allahna!!!"
Cikin kuka da tashin hankali suka yi kanta su na riΖewa, aka
bankaΙo Ζofar aka shigo, su Abba ne da ihun Ummita ya iske su. Raihana a
guje ta nufi wurin Nurses dake tahowa, kafin ta kai ga magana suka ce sun ji.
An tafi kiran likitan. Su na shiga sai ga Likita, aka fitar da kowa a Ιakin.
Gaba Ιaya matan kuka sosai babu kamar Raihana da take jin
kamar ta shiΙe. A yadda take jin zuciyarta za ta iya fille kan wanda ya aikata
wa yan uwarta wannan tozarcin.
Koda likitan ya Ζarasa gareta flask din ruwan zafin dake
ajiye a gefenta kawai ta Ιauka ta jefa masa. Ba don Allah ya sa shi kaucewa ba
da babu abin da zai hana a same shi.
Tana cikin wannan gigitar Humaira ta farka a matukar
firgice, ta kira sunan Ummita da karfi sannan a guje ta diro ta zo ta rungumeta
tana kallon jama'ar Ιakin kamar wasu sabbin halittun da ba ta taΙa gani ba.
"Su waye ku? Me
za ku yi mana?! Ku fice ku bar nan! Wallahi ku ka yi ΖoΖarin zuwa kusa da mu
zan ji maku ciwo."
Sai kuma ta juya a mugun firgice tana tattaΙa jikin Ummita
dake kuka kamar ranta zai fita.
"Ummita! Yi shiru, Abba zai zo. Naji suna cewa yana
hanya. Yi shiru, sai mun kashe su."
"Kin.."
Likitan ya Ζaraso zai soma magana Humaira ta juya da azama
tana nunashi da yatsa. A sannan su Abba gaba daya sun shigo sun kasa daurewa.
"Kar ka taΙamin Ζ΄ar uwa! Zan kashe ka!!"
"Humaira, Ummita."
Humaira na ganin Abba ba ta ko damu da sauran jama'ar Abba
ta karasa a guje ta rungume Abba tana kuka mai tsuma zuciya.
"Abba za su kashe mu! Abba ka cece mu! Ka Ιauke mu mu
bar nan!"
Irin riΖon da ta yiwa Abban ba na wasa ba ne har maΙallan
wuyar rigarsa sai da suka fita.
Cikin hawaye ya ce.
"Mamana babu abinda za su yi maku, likitoci ne. Kun kuΙuta
daga hannun azzalumai. Ki kalla dakyau, ga Maminki ga yar uwarki Raihana. Kin
gane Kawunki?"
Ta tsaya cak kamar wata sokuwa tana kallonsu Ιaya bayan Ιaya,
Ummita kuwa da nos ta lallaΙa ta yi mata allura tuni bacci ya kwasheta. Kawai
sai ta soma ruwan wasu sabbin hawayen ta ma kasa cewa uffan. Zuciyarta ta
gasΖata eh sun kuΙuta daga hannun azzaluman, amma kuma ta ji tana tantama tana
gani ko mafarki ne. Wannan ya sa Raihana tahowa da sauri ta rungumeta ta kara
sautin kukanta.
A hankali ta Ιaga
hannunta ta Ιaga fuskar Raihana ta na kallo kamar wata baΖuwar halitta ce
gabanta, sai kuma da rawar murya ta ce.
"Raihana ce?"
Raihana saboda Ζarfin kukan ma ta kasa magana sai kawai ta Ιagamata
kai. Humaira ta rungumeta sosai suna kukan tare.
"Amm, don Allah a ragu a Ιakinnan. Alhaji ina son
magana da kai."
Fadin Likita, ganin haka duk aka fice banda Raihana wacce
Humaira ta riΖe hannunta gam tamkar ita kaΙai ta gani.
***
Likita ya dubi Abba
cikin nutsuwa ya soma magana.
"Lamarin ita Ummita na buΖatar rarrashi da ja a jiki.
Kaso casa'in na ire-irenta da hakan ke afkuwa a kansu sukan samu matsala ta
rudani, firgici da kuma rashin yarda ga kowa. Wasu kuma yakan taΙa musu
kwakwalwa. Zamu yi mata gwajin kwakwalwa don a tabbatar da komai na ta lafiya
kalau yake."
Abba ya share fuskarsa.
"Toh Likita, nidai babban burina lafiyarsu. Allah ya sa
komai lafiya."
"Ameen." Ya amsa cikin tausayawa yana mai lallaΙar
Abba.
***
Cikin iko na
Ubangiji an yiwa Ummita gwajin kwakwalwa kuma an tabbatar da komai lafiya.
Wannan ya kwantar da hankulansu. Humaira dai ba ta dogon magana tun farkawarta,
kowa ta gani sai dai ta ambaci sunansa, idan an rungumeta an sa kuka itama ta
soma. Da daddare ba bacci sai razana, ga Ummita haka. Wannan yasa aka raba musu
Ιaki. Fadeel na zuwa, kuma abin mamaki
Humaira na ganinsa ta kira sunansa, abin sosai ya ji dadinsa ya kuma tsaya a
ransa.
Sai da suka kwashe sati biyu a asibiti kafin su tattara su
dawo gida. Babu laifi sosai zuwa lokacin
sun samu nutsuwa ba kamar farko ba. Sai dai daga Ummitan har Humaira duk sadda
tunanin cin zarafin da aka yi musu da kuma keta haddin da aka yiwa Ummitan sai
su yi ta kuka. Har zuwa lokacin babu wanda ya san da mummunan labarin sai ko
Anti Maijidda da Mami wadanda Abban ya faΙawa.
Anti Maijidda nan fa ta dage akan lallai sai a ba ta Ummita
su tafi Bichi, Abba ya Ζi amincewa. A dole ta haΖura ta tafi tana Ζunar rai da
jin tsanar Mami har cikin ΖoΖon ranta.
Jannat ko a fuska sai ka rantse nan jimamin duniya take yi
akan lamarin don ba ta nuna komai wanda zai sa wanda bai sani ba ya fahimci
takun saΖarta da su. Hakanan Anna wacce ta daurewa zuciyarta ta taka har Ιakinsu
ta duba lafiyarsu bayan ta je asibitin a baya har sau uku. Wannan ya wanke ta
daga zargin mutane da rashin nuna kauna ga su Humaira a baya.
***
Sai da su Humaira suka samu sati hudu cif kafin su Ιan maido
da jikinsu, da kuma walwala kaΙan. Sukan zauna cikin jama'a, a taΙa hira da su
idan ka cire Ummita da har lokacin ta tuno aika-aikar da aka yi mata sai kawai
ta fashe da kuka wanda hakan ke tayarwa Humaira hankali itama ta sa nata kukan
sai su haΙu su yi ta yi. Kawun Humaira ya so su koma can Nijar da ita amma nan
ma Abba ya nuna sam bai amince ba dole haka ya tattara matarsa suka koma gida.
Su na zaune a Ιaki, Ummita riΖe da AlΖur'ani tana
karantawa zuciyarta na yin sanyi yayinda Humaira ke kwance saman katifa ta yi
shiru gami da zubamata idanu kusan ma hankalinta ba a kanta yake ba, ta lula
wata duniya ta daban na tunani. Raihana ta shigo ta iske su haka, dawowarta
kenan daga makarantar boko wanda har lokacin Ummita ta Ζi amincewa ta koma
ganin haka babu wanda ya takura mata shi ma mai makarantarsu da ya zo har gida
ya jajanta ya ce a kyale ta zuwa wani lokacin.
"Wash! Wallahi na gaji! Ke kuma kina da baΖo a falon
Abba."
Ta faΙi da murmushi tana duban Humaira duk a Ζokarinta na
son ta ga komai ya dawo daidai a mu'amalarsu. Humaira ta Ιan dube ta gami da Ιan
haΙe gira kaΙan.
"Wa kenan?"
"Fadeel."
Ta yi shiru, ita ba ta ce uffan ba balle ta yi wani yunΖurin
kawai sai ta maida kai ta kwanta ta yi shiru. A karan kanta ba za ta ce ga abin
da take ji game da Fadeel din ba, lamarin dai ba yabo balle kuma fallasa.
Ummita na ji ba ta iya cewa komai ba, Raihanar ma ba ta sake magana ba sai
ta miΖe ta rage kayan jikinta ta shiga wanka, ba ta son duk abin da zai
takurawa rayuwar Ζ΄an uwannata da ta Ζara sanin girman Ζauna da shaΖuwar da ke
tsakaninta da su bayan sun yi mata nisan da ta zaci har abada ba za ta Ζara
sanya su cikin kwayar idanunta ba.
Ummita tana kai wa Ζarshen surar da take karantawa ta
juya ta dubi Humaira.
"Ki je ku gaisa mana."
Humaira ta yi mamakin jin wannan furucin naga bakin Ummita,
tun bayan dawowarsu ba ta wani magana kwakkwara, ko hirar Raihana ke jansu da
shi, sai dai ta basar ta yi shiru. Wannan murmushin da ba ya barin fuskar
Ummita, babu shi babu labarinsa tun dawowarsu. Ita Ιinma Ζarfin hali take yi
don faranta ran Mami da su Raihana ga kuma Ζasim waΙanda gaba Ιaya suke nuna
musu kulawa da ΖoΖarin ganin sun saki jikinsu.
"Kin ji?"
Maganar Ummitan ya Ζara katse mata tunani. Tana so ta
ja musu amma a yanzun duk duniya babu abin da ta ke so irin ta ga Ζ΄ar uwarta ta
dawo tamkar yadda ta ke rayuwa a baya. Abu na biyu kuma ta sani ba ta jin
za ta iya Ιaukar waya ta kira shi da zummar godiya bisa hidimar da ya yi akan
fitowarsu, don ko cikon da suka bayar na kuΙutar da su a hannun Ζ΄an fansa Ζin
karΙa suka yi da Abban ya maida musu, ta sani wannan ita ce damar ta amma
hakanan ba ta son Fadeel din ya cigaba da shigemata shiyasa.
Abban har gidansu ya je ya Ζara godiya sosai shi da Mami
wacce a sannan ne ta ga gidan da ya kere na Aminiyarta Hajiya Lubna.
Ganin Ummitan ta zubamata idanu ya sanya ta miΖewa.
"Toh, na ji Ummita."
Ta faΙi kamar ta fashe da kuka sai ta miΖe ta Ιora hijabi
akan doguwar rigar atamfar da ke jikinta.
Suka ci karo da Mami a falon wannan ya sanya ta tsayawa.
Gidan yanzu duk an watse sai su kadai, Jannat ta tattara ta
koma bayan dogon kiran da mijin ya dinga danno mata har abin ya kusan zame musu
rikici sannan ta tafi ba don ta so ba. Tasleem kuwa tun fitowarsu da kwana biyu
Hamza ya zo suka koma gida.
Cikin sakin fuska Mami ta dubi Humaira.
"Ina zuwa haka?"
Ta sunkuyar da kai sannan ta ce.
"Wai Fadeel ne ya zo za mu gaisa."
Nan da nan fara'ar dake saman fuskar Mamin ya ragu.
"Zuwan me yake ta yi haka ne alhalin jinyar ta Ζare?
Ina ce na muku iyaka da shi tun a baya?"
Humaira ta jinjina kai.
"Hakane Mami, kiyi hakuri. Ai gaisawa kawai zamu yi. Ya
yi abin da ko maΖiyina ne ya cancanci na Ζara yi mishi godiya."
Mami ba Ζaramin mamakin furucin Humairar ta yi ba wanda
daidai da fuskarta ta nuna. Sai kuma ta jinjina kai.
"Shikenan, ki je amma kar ki Ιau lokaci."
Murmushi kaΙan Humaira ta yi sannan ta amsa da toh ta cigaba
da tafiya. Ban da abin Mami, ita ba ta tunanin ma za ta yi auren, wane namijin
ne zai aure ta bayan ta gama wulaΖanta duk masu kaunarta domin Allahn? Ta rasa
dalilin da a Ζ΄an kwanakin nan take jin sauyi a jiki da kuma kwakwalwarta.
Wannan ne ya sa Fadeel samun rangwame daga wurinta.
Ζangaren Mami kuwa ji ta yi kirjinta ya yi wani irin bugu.
Meke shirin faruwa haka? A duniya ba ta kaunar Fadeel ya raΙi Humaira kamar
yanda bai raΙi Tasleem ba. Kai ba ma shi ba... Sai kuma tunaninta ya katse, ta
haΙiyi miyau da ta ji yana mata zafi. Sai kawai ta nufi Ιakinta a gaggauce.
Tabbas ta yi sake a kwanakin da suka shuΙe ba ta bayar an Ιoramata sabon aiki
ba. Wayarta ta fiddo ta shiga zarya a tsakar Ιakin tana jira a Ιauka daga
Ιaya Ιangaren. Doguwar magana suka yi sai kuma ta hau murmushi hankali a kwance
ta katse kiran ta shiga danna wayar karo na biyu inda ta tura kuΙi ga wani
akawun lamba. Daga nan kuma ta ji wata irin nutsuwa ya saukar mata.
***
Ya kwashi mintoci masu yawa a zaune anan,
shigowar su Waleed ne ma ya Ιauki hankalinsa suke hirar makaranta yana
biyemusu. Ya gama fidda rai daga ganinta, gefe guda ga tsoron kada a koma Ζ΄ar
gidan jiya, tunanin da ya sanya gumi tsastsafo masa a goshi duk kuwa da iskar
dake kaΙawa a falon har tana kaΙa labule. Sai dai kuma ba zato ya tsinci
sallamarta, cikin sauri ya kalli hanyar yana mai amsawa da rawar murya.
'Please Fadeel, Control.' Zuciyarsa ta ba shi shawara, ya
sauke nannauyan ajiyar zuciya. Ya zubamata idanu, ta fara dawowa ainahin
Humairarsa, fuskar ta Ιan ciko ba kamar farkon dawowarsu ba. Hakanan ta yi
haske fayau dama can a bayan har da rashin samun wanka ga uban cizon sauron da
tabonsa ya yi ja a jiki da fuskarta.
Ita kuwa kanta a Ζasa ta Ζarasa ta zauna Ιan nesa da
shi, tana ji ya kaΙa su Waleed ciki akan su je su cire uniform dinsu.
"Barka da
rana."
Ya yi furucin yana
dubanta tamkar ya haΙiye ta. Sai a sannn ta Ιan Ιaga kai ta dube shi.
Ganin yanda ya zubamata idanunsa ya sanya ta maida kanta Ζasa ta na jin wani
yaam a jikin da ba ta saba ba a baya.
"Ina wuni, ya wajen su Baba?"
Fadeel da ke jin kamar an tsoma shi a aljanna ya faΙaΙa
murmushin fuskarsa yana hamdala a Ζasan ransa. Dama komai Ιan hakuri ne, idan
ka yi to fa zai wuce. Ya shanye wulakancin da zagin, yanzu ga shi nan ya soma
cin galaba.
"Kowa lafiya kalau Alhamdulillah, Sisterna ma ta zo
daga Adamawa. In sha Allah zuwa gobe za ta zo ku gaisa."
Sai ba ta watsa masa Ζasa a ido ba ta amsa da toh. Shiru ya
biyo baya, a Ιangaren Fadeel ba ya so ya faΙi abin da bai yi daidai da
ra'ayinta ba ta sauya fuska ta miΖe ta bar shi anan, ita kuwa godiya take son
yi mishi don su yi sallama ta koma ciki amma ta rasa ma ta inda za ta fara sai
can da ta ga ba shi da niyyar ce mata uffan sai aikin kallon da ba za ta ce
yana ba ta haushi ko kuma faranta mata ba a lokacin, ta daure ta soma magana.
"Mun gode bisa dukkan Ιawainiyar da ku ka yi mana,
Allah ya Ζara arziki."
"Ban yi abin da za ki godemin ba. Ke kika yi wanda zan godemaki. Nagode sosai
and I..."
Sai kuma ya yi saurin haΙiye zancensa, ya san komai na
tarihin Humaira a sannan daga bakin Raihana, ya san ba ta jin turanci amma kuma
dai kalmar I Love You ko yaro Ζarami da bai je makaranta ba ya sani. Shirun da
ya yi ganin zai yi taΙargaza ne, gaba Ιaya ji yake da ace Humaira za ta ba shi
dama, zancen aurensu kawai za a yi. Ya sani hatta da Abbanta ya buΖaci a ba shi
lokaci kaΙan yaransa su dawo cikin nutsuwa sai a haΙa auren Ummita da na su,
shi ne a karon kansa ya roΖi alfarma a kyale Humaira ta amince da batun aurensa
da kanta. Yana kuma ji a jikinsa hakan ce za ta kasance daga yanayin sauyin da
ya gani tattare da ita.
"Shikenan?"
Ta katse mishi tunani, ya Ιan lumshe idanu sannan ya buΙe su
a cikin nata, ta kauda fuska ta yi shiru.
"Toh, zan koma bakin aiki, dama zuwa nayi na duba
lafiyarku. Ki gaishemin da Ummita da mutan gidan. Allah ya Ζara lafiya."
Ta amsa da amin, cikin sanyin muryar ta ce.
"Zan fadamusu. Nima ka gaidamin Ζ΄ar uwarmu, sai ta zo
goben in sha Allahu."
Ambaton Ζanwarsa Hannatu da Ζ΄ar uwarmu da ta yi ya sanya shi
jin tamkar yana tafiya a iska tsabar mamaki da farin ciki. Ya ji dadin wannan
lamarin sosai.
"Nagode."
Hakan ya furta kawai sannan suka miΖe kusan lokaci guda, sai
da ya ga shigewarta sannan shima ya juya yana murmushin da har haΖoransa suka
bayyana, ga duk wanda ya ga fuskarsa ya san yana cikin farin ciki da annashuwa.
***
Washegari Mami ta
tashi da aikin girki na tarbar Futuha wacce ta yi waya ta sanarmata dawowarsu a
ranar. Daga Dubai sai da suka je Saudia suka yi Umarah kafin su juyo. Humaira
ba ta yi Ζasa a gwuiwa ba wajen shiga kicin Ιin din taimaka mata da aiki, zaman
kaΙaicin babu abin da yake jefa ta ciki sai kogin tunani. Ummita ma ta fito
falo kasancewar akwai wuta ta kunna tashar Saudia tana kallo.
Gaba Ιaya samarin
gidan sun dawo, Mubarak da ya kammala shima yana gida hakanan Yassar da Dawud
wadanda sun fi sati da dawowa daga Camp suna nan tare da su. Anan Kano aka yi
posting Ιinsu inda zasu yi service.
Daga Humairar har
Ummita ba su Ζara samun matsala da su Yassar ba, musamman Humaira wacce a baya
suke Ζi sosai, ita hakan ma har mamaki yake ba ta. Tsakaninsu gaisuwar mutunci,
wasu lokutan har su Ιan tsoma ta a ciki idan suna Ζ΄ar hira. Har a lokacin ba ta
saki jikinta da su ba don ba ta saba da hakan ba.
Suna girkin Ladidi na
taya ta murnar yanda ta soma sakin jikinta tamkar a baya. Raihana ta shigo
kicin din kamar an jefo ta har Mami na mata faΙa.
"Ku yi hakuri. Humaira, Yaya Fadeel ya kira Sister
dinsa Hannatu tana hanyar zuwa."
Gaba Ιaya ta manta da wani batun zuwansu, Mami kuwa haΙe rai
ta yi ba ta ce uffan ba har sai da Raihana ta Ζara magana.
"Ki je ki Ιan sauya kaya don Allah. Kar ta ganki da
Tshirt."
Ladidi ta yi dariya Humaira kuwa ta maka mata harara ta rasa
dalilin kuma da aka yi ta Ιan dawo da jin haushi-haushin Fadeel, sai lokacin
kuma Mami ta yi magana.
"Toh uwarta, ke kuma Humaira meyasa ba ki faΙamin kina
da baΖuwa yau ba?"
Cikin sanyin murya da kuma rashin jin dadin Ιatawa Mamin rai
da ta yi ta ce.
"Kiyi hakuri Mami, gaba daya na manta ma ya faΙamin."
Mami ta sauke ajiyar zuciya, ta sauya yanayinta na farko
sannan a sanyaye ta ce.
"Ai shikenan, ba don girkin da ake na Futuha ba da sai
dai ta zo ba a yi nata tanadin komai ba kenan. Ladidi Ζaro shinkafar nan kafin
ki wanke."
Ladidi dake shirin wanke Ιanyar shinkafa ta zuba a ruwa ta
amsa da toh, sai da ta Ζara ruwan tukunyar sannan ta Ζara awon shinkafar da
ajiye. Raihana dai ta tsaya jiran Humaira ta dage lallai sai ta sauya shigar
jikinta. Mami ba ta sa musu baki ko kadan ba, Humaira har haushin Raihanar ta
dinga ji saboda irin wannan nacin ba ta ko fuskantar yanayin fuskar Mamin.
"Ki rabu da ni
don Allah." FaΙin Humaira cikin haΙe gira. Sai lokacin Mami ta sa baki ta
hanyar bin Humaira da murmushi.
"Aa Humaira, da gaskiyarta. Maza je ki sauya suturar
jikinki. Bai kyautu baΖuwarki ta ganki a hakan ba. Jeki."
Ganin yanayin Mamin har a sannan ba ta gamsu ba, amma ta bi
umarninta suka fice da Raihana zuwa nasu Ιakin. Ta iske Raihanar ta fiddo mata
wata atamfarta purple mai ratsin fara da baΖi, ta kalle ta. Raihana ta murmusa.
"Ya aka yi? Da magana ne? Ko na sauyamaki kayan?"
Guntun tsaki Humaira ta ja.
"Ke dai yadda kika damu da wannan Fadeel din da ma ke
kika aure shi."
Raihana ta ji ba dadi jikinta kuma ya yi sanyi, tana tunanin Humaira ta fara
sauyawa daga lamarin nata da na Fadeel sai ta ga abin ba haka ba.
"Allah ya huci zuciyarki tawan." Ta fadi tana riΖo
hannun Humaira, sai itama ta ji ba dadi.
"Shikenan. Bari na watsa ruwa na sauya ko don ke."
Sosai Raihana ta ji dadin kalamanta. Ta yi dariya.
"Toh."
Daga haka ta fice ta bar Humairar da shiga bandaki.
***
Murja tana zaune
gaban motar ta hakimce yayinda Hannatu
da yarinyarta mai shekaru uku da ta ci suna Husna suke a baya zaune.
Tun da Murjar ta ji
inda Hannatun ta nufa ta kafe akan sai ta bi ta, a farko Hannatu ba ta so ba
don tana da labarin irin son da Murjar ke yiwa Fadeel daga bakin Kausar. Shi
Fadeel dayake bai Ιauki maganar da muhimmanci ba ya sa bai ce mata komai a kai
ba. A karshe dai ganin yadda Anti Amarya ta nuna ta yi na'am Murja ta raka su
ya sa itama Ιoye nata rashin yardar suka tafi tare ba da sanin Fadeel ba.
Karfe biyar na
yamma suka shiga gidan. Raihana ta tare su da fara'arta zuwa ciki. Murja sai
raba idanu ta ke ta ga inda Humaira za ta Ιullo kuma ta ga yanda ta sauya.
Ummita itama ta fito suka gaisa da su, nan suka jajanta musu da addu'ar Allah
ya kiyaye gaba. Ba ta amsa ba sai ta mike sakamakon idanunta da suka cicciko da
kwalla ta nufi daki.
A duniyarta yanzu
babu abin da ta tsani ta tuna kamar abin da ta faru gareta a hannun Kidnappers.
Gani take duk ranar da aka Ιaura mata aure da Sahabi babu abin da zai hana shi
gano komai, Abba ya yi niyyar sanar da shi amma Mami ta nuna kar ya yi hakan.
Ita kuma a karan kanta ta rasa ta ina za ta fara gayamishi. Ga wata sabuwar
kauna da yake nunamata tun bayan fitowarsu duk domin ya kwantar mata da
hankali.
Ganin da ta yi
Humaira na Ιakin, ta yi saurin share fuskarta ta dubeta fuskar a Ιan sake duk
da ba kamar can baya da take Ummitarta ba.
"Sun Ζaraso su na falo. Ki je ku gaisa, mace mai kirki
da ita."
TaΙe baki Humaira ta yi.
"Toh." Shi ne abin da ta iya cewa, daga haka ta sa
kai ta fice. Bayan fitarta Ummita ta tura kai a filo ta yi kuka mai isarta tana
mai tausayawa kanta. Wannan baΖin ciki na keta alfarmarta da aka yi ta kasa
gogeshi daga kirjinta, ta dai san an gogamata baΖin fentin da har abada ba za
ta iya gogewa ba. Amsar da ta kasa ba wa kanta har yau shi ne, wane ne wanda ya
sa a yi kidnapping dinsu.
*_Ba don kar asirinmu
da na Boss Ιinmu ya tonu ba, da sai na nemi aurenki na killaceki saboda kin haΙu
Ζarshe._*
Ta tuna wannan Ζazamin zancen da ya fito daga bakin Wizzy a
sadda yake kam ganiyar raba ta da mutuncinta. Kenan dai akwai wanda ya sanya su
wannan aika-aikar. Waye shi? Kuma a ina yake? Allah ne kaΙai masani. A karshe
dai ta yakice wannan tunanin ta mike ta shiga bandaki.
***
Hannatu ta dubi
Humaira har ta Ζaraso ta zauna tana mata Ιan murmushi. Murja kuwa kallon
Humaira kawai take yi cikin tafarfasar zuciya tana mai kuma cin alwashin ganin
bayanta. Babu wani abu da ya sauya daga kyawunta wannan ne ya Ζara wa Murja
baΖinciki a Ζasan rai. Ta kauda fuska tana amsa gaisuwar da Humaira ke yi mata
a yatsine. Ita kuwa Humaira mamaki take na dama Murjar ta san Fadeel amma sai
ta bar wa cikinta ba ta tambaya ba. Hannatu ta saki jikinta ta yi ta jan
Humaira da hira, kasancewar da Raihana a falon ta samu Ζ΄ar tayi, tun dai
Humaira ba ta saki jiki ba har sai gatanan ta soma murmusawa haΖoranta na
bayyana.
Raihana ta kawomusu abin motsa baki da kuma abinci. Husna ta
maΖalewa Humaira tana mata hira iri iri na yara. Itama ta dinga biyemata. Can
dai Murja ta kasa jurewa ko Mami ba ta
tsaya sun gaisa ba ta amsa wayar Ζarya sannan ta dubi Hannatu.
"Ni zan wuce sai
kun taho. Ζawata ce ta zo."
Suka dube ta har Raihana da ta fahimci sauyin fuskar Murjar
da irin harare-hararen da take wurgawa Humaira jifa-jifa.
"Shikenan, sai mun taho."
Ranta ya Ζara Ιaci, wato dama so take ta tafi Ιin don haka
ta dauki jakarta ko sallama ba ta tsaya yi da su ba ta fice a fusace.
Ba jimawa kuwa da fitarta Mami ta fito cikin shirin fita.
Daga ganin yanayinta sauri take kuma fuskarta ya nuna rashin nutsuwa. Hannatu
ta gaida ta, ta amsa da Ιan sauri. Ganin haka Raihana da Humaira suka tarbi
Mamin da neman ba'asi. Guntun tsaki ta ja fuskarta dauke da tsantsar damuwa.
"Wajen Tasleem
zan je, sun yi dambe da wannan Fauziyar shi ne fa jini ya Ιalle mata amma sun
wuce asibiti."
Hankalinsu su din ma ya tashi. Suka nuna za su bi ta amma
fir ta ce aa su zauna da baΖuwarsu sannan ga Futuha dake hanyar zuwa kada a bar
gidan babu Ζ΄an tarbarta. Dole suka jajanta suka dawo ga Hannatu aka cigaba da
hira. Ba ita ta bar gidan ba sai bayan Magriba. Ta kuwa ajiyewa Humaira leda
babba ta kayan kwalam sai ko turarukan da ta yo mata tsarabarsu. Firr Humaira
ta Ζi karΙa sai daΖyar sannan ta yi godiya. Lokacin itama Ummita ta fito falon,
tare suka yi mata rakiya har gaban motar da suka zo cikinta.
***
Karfe takwas da
mintoci sai ga Futuha a gidan, tun yamma ta sauka a garin tana gidanta, Ζasim
ne ya kai musu girke-girken da aka yi musu. Ta shigo gidan gaba Ιaya jikinta a
mugun sanyaye. Matasan samarin duka suna falo aka tarbe ta da murna, su Humaira
su din ma duka ana zaune ana kallon film din Krissh da ake haskawa a
mbcbollywood. Ganin yanayin yadda take amsa musu hirar ya sanya Yassar dibanta
dakyau.
"Are you
okay?" Ta yi murmushin yaΖe kai ka ce ba Futuhar nan ba ce mai Ιora hotuna
iri-iri da murnar zuwa Dubai a tiktok.
"Yes. Mamin ba ta dawo ba?"
"Ta dawo tana Ιaki."
FaΙin Raihana. Ta kuwa
nufi Ιakin, ban da gaisuwar su Humaira babu wani jimamin da ta yi musu
na abin da ya faru. Ζamshin turarenta da ya cika falon ne ya sanya Ummita jin
kanta na juyawa, ta ji tamkar hanjin cikinta ke kaΙawa. Da sauri ta mike ta yi
dakinsu, kafin ta Ζarasa shigewa banΙakin wani amai ya tahomata wanda sai da ta
amayar da duk abincin da ta ci a ranar. Humaira da Raihana wadanda suka biyo
bayanta ganin irin miΖewar da ta yi ta bar falon suka tsaya cak cike da fargaba
mai tsanani su ke bin ta da kallo. Raihana ta karasa cikin sauri bayan fitowar
Ummita daga banΙakin ta riΖe ta.
"Lafiya? Meke damunki?"
Ummita ta yamutsa fuska kaΙan.
"Ban sani ba, kawai dai na ji zuciyata tana
tashi."
"Allah ya sauwaΖe, ki Ιan kwanta ko za ki ji dadin
jikin." Fadin Humaira cikin dauriya da Ζaryata zuciyarta har da jan
istigfari bisa saΖe-saΖen da ta jefa mata. Ummita kuwa Ιan murmushi ta yi.
"Kar ku damu, kalau nake. Naga duk kun yi wani sukuku
da ku."
Cikin kokarin basarwa Raihana ta zauna gami da jan guntun
tsaki.
"Ai dole, ga Tasleem can kwance asibiti dakyar aka
tsaida jinin. Wai kawai saboda ta kama Fauziyya na waya da tsohuwar budurwar
Yaya Hamza kuma Ζ΄ar uwarta tana ba ta labarin rayuwar ita Tasleem din da Yaya
Hamza shikenan fa daga cacar baki sai cibi ya zama Ζari. Nima Mami naji tana ba
Anna labari. Yanzu dai Maman Hamza ta Ζi zuwa ko duba Tasleem ta ce wai kashe
mata Ιiya ta so yi."
Humaira ba ta ce uffan ba, domin tun dawowarsu ta Ζara jin
Tasleem ta fice a ranta, ta kuma Ζudurta ban da dai gaisuwa ta musulunci to fa
babu abin da zai sa ta cigaba da tura kai ba kwarjini wurin waΙanda ba za su taΙa
kaunarsu ba. Ko kaΙan Tasleem ba ta wani nuna farin cikin dawowarsu ba, ita
kuwa me zai sa ta cigaba da shiga sabgar wacce ba ta yin ta?
"Allah Sarki, Allah ya kawomata da sauki."
Cewar Ummita sannan itama ta ja bakinta ta yi shiru.
***
Yanayin da Futuha ta
shigar wa Mami ne ya sanya ta Ιago kai daga wayar da take amsawa har da
hawayenta. Cikin wani sauri ta sallame wayar ta miΖe, Futuha ba ta kawo komai
ba ta Ζarasa da sauri ta rungumeta ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya.
Mami wacce ta ji
kirjinta ya yi wani irin bugu da Ζarfi ta Ιago kai da azama ta kalle ta har
hannuwanta a rawa.
"Ke mene ne ya
faru ne? Ina Yakubun?"
Gaba Ιaya ta ruΙar da cikin Mami wanda ta ji har wata Ζ΄ar
Ζara ma yake yi.
"Mami Ζarya yake
yimin, ashe matarsa tana gidansa cikin wata irin ΖasΖantacciyar rayuwa?"
"Toh ina ruwanki da ita! Ke ba kanki kika sani
ba?!"
Yadda Mamin ta yi furucin a zafafe ya sa Futuha shiru tana
kallonta da Ιan mamaki saman fuskarta, kamar dai ba Mamin da ta saba karo da
ita ba. Sai kuma ta tuno labarin Ζ΄anmatancin Mamin da Anna ta ba su, mace ce da
a tarihin soyayyarta ba ta taΙa kallon mai mata balle ta ji zuciyarta za ta iya
Ιaukar zaman kishi da ita ba, har tana jinjina mamakin zaman da ta amince suka
yi da Fatima ta kuma Ζaunace ta. A baya dai Mami ba ta san kowa da komai ba sai
kanta da kuma nata. Wannan tunanin da Futuha ta yi ne na tsohon tarihin Mamin
ya sanya ta sauke ajiyar zuciya lokaci guda kuma mamakinta na farko ya gogu tas
daga kwanyarta.
"Nifa ba
wannan Ζaryar ce ta tada hankalina ba, tun kafin mu dawo likita ya bayyanamin
ina da ciki bayan Ζ΄ar rashin lafiya. Na bar abin na Ιoye ban sanar mishi ba
akan zan ba shi labari mai dadi, sai yau da muka dawo ne nake sanar da shi toh
kawai sai ya sauya fuska. Ya kuma rantsemin shi bai aure ni don na haifarmasa,
daga uwargidansa kawai yake da kwaΙayin samun yara. To fa shi ne da faΙa ya
kaure tsakaninmu, ya ce na zubar ni kuma na ce ba zan zubar ba tunda ba shege
ba ne, kawai Mami sai ya ja hannuna ya kai ni Ιangaren Uwargidansa. Nayi
mamakin ganin ashe yaransa takwas har da budurwar da za ta yi sa'ar Raihana.
Komai nata ya ci uwarsa a falon. Goyon Ιa take yi ma, a gabanta da na
yaran ya nunamin yaranta sun ishe shi ba
ya kaunar haihuwa daga kowace mace. Ya kuma aure ni don ya ci duniyarsa ganin
da ya yi ni Ζ΄ar rawa ce wai a Tiktok na kuma san ta kan rayuwa sai ya Ιauka zan
san dabarun family planning kafin aure."
Kawai sai ta fashe da kuka. Mami zuciyarta har wani
tafarfasa yake yi. Ta ji kukan Futuhar tamkar yana Ζara tafarfasa ΖwaΖwalwarta
don haka ta dakamata tsawa.
"Ya isa! Nace
maki ya ishe ni haka! Haba! Da wanne ku ke son na ji? Da mummunan albishir din
da Babandi ya faΙamin ko kuwa da hargitsinku?! Ke ba za ki iya cin uban shege
ba?! Ba za ki iya yadda za ki yi ki ga kin fitar da yar iska daga gidanki ba?!
Shashasha kai marar wayo!"
Tana kaiwa nan ta nemi bakin gado ta zauna kirjinta na dukan
tara-tara tana maida numfashin gajiya. Futuha kuwa ai sai ta Ζara yin mutuwar
tsaye don mamaki. Toh Mamin nan dai ta tabbata ita ce ainahin Mamin can baya
lokutan yanmatancinta, ita ce Mamin da Anna ta yi mugun kewarta. FaΙa, zagi
kuma duk akan kishi? Yau Mami dai da bakinta ta mata iznin daukar kowane mugun
mataki ne akan kishiyarta da mijinta. Futuha ta juya cikin sassarfa tana kukan
har lokacin ta fice zuwa Ιakin Anna.
Mamin kuwa sai bayan da kwanyarta ta Ιan samu nutsuwa,
tashin hankalin dake Ζasan ranta ya Ιan lafa sai ta soma tunano irin maganganun
da ta faΙawa Futuha. Ta lumshe idanu ta ja guntun tsaki. Ta san yarinyar dole
mamaki ya kashe ta, amma ita ta san azabtuwar da take yi ko kuma ta yi a
shekarun baya da suka gushe. Ta tsani kishiya tsana mafi munin gaske.
'Ciki har da Fatima?'
Wani Ιangare na zuciyarta ta watso mata wannan tuni. A fili
ta Ιaure fuska tamau, idanunta nan da nan suka kaΙa tsabar masifa da kuma abin
da ta tuna na daga rayuwar Fatima da Yusuf a baya.
"Har da
Fatima." Ta furta a zahiri, can kuma ta miΖe ta shiga banΙaki ta wanke
fuskarta. Sai bayan ta dawo daidai ne sannan ta fito zuwa Ιangaren Abba. Ta
iske shi zaune yana kallon labarai, itama wuri ta nema ta zauna da wani irin
sanyin jiki.
Abba ya maido hankali
gareta.
"Maryama, na
ganki wani iri, Futuhar ba su dawo ba ne?"
Mami ta girgiza kai.
"Sun dawo, tana wajen Anna ma suna gaisawa."
"To ko jikin Tasleem din ne? Ni me ma ya faru ne da ita
ta yi rauni?"
Ko kusa ba ta sanar da Abban gaskiyar abin da ya yi sanadin
kwanciyar Tasleem din a asibiti ba. Ta sani muddin ya ji to faΙa zai yi wannan
ya sa ta gyara batun.
"Zamewa ta yi ta faΙi a banΙaki. Amma ai da sauki tunda
jinin ya tsaya."
Jinjina kai Abban ya yi.
"Allah ya raba su lafiya. Sai ta Ζara kula."
Ta yi shiru tana kallon gefe guda ta kasa amsa mishi, ya
riΖo hannunta cike da kulawa murya a tausashe ya ce.
"FaΙamin, meke damunki?"
Ζasa ta yi da idanunta sai hawaye, suka zubo saman hannun
Abba da ya Ιora bisa nata. Nan da nan ya Ζara shiga tashin hankali.
"Kinsan bana son kuka ko? Taimaka ki faΙamin damuwarki
Maryam. Zuciyata ba za ta Ιauki wani sabon tashin hankalin ba bayan wanda na
fuskanta kwanakin nan."
Ta jinjina kai ta dube shi.
"Abban yara tunanin yarannan ya kasa barin zuciyata ta
huta. Tun dawowarsu zan iya ce maka Ummita har yau ta Ζi dawowa cikin
nutsuwarta. Yarinya mai fara'a da son jama'a marar hayaniya, ta koma wata
iriya. Babu doguwar magana balle hira, koyaushe zaman tunani da shiru. Wannan
abu yana damuna matuΖa."
Shima Abban hakan da ta faΙi sai ya Ζara taso mishi da nasa
damuwar.
"Hakane Maryama. Toh a shawarce me kike tunanin za'a
yi? Mece ce mafita?"
Mami ta numfasa.
"Mafita a samar mata abin da zai dawo da walwalarta.
Abin nufi, madadin lokacin da aka sa na aurenta da Sahabi, me zai hana a yi
mishi magana idan sun shirya kawai ya kawo lefe a sanya bikin nan da kamar sati
biyu?"
Ζan jim Abba ya yi cikin hali na tunani. Sai kuma ya ce.
"Kina tunanin idan an yi hakan ba a tauye ta ba kuma.
Bana jin yarinyar nan ta samu nutsuwar da za ta karΙi aure a yanzu. Kada ki
manta fa, keta haddinta aka yi ta Ζarfi. Aa Maryama, mu dai yi hakuri tun da
abinda ya rage cikin shekarar bai wuce watanni biyar ba, ki jira mu ga abin da
Allah zai yi a gaba."
Ba haka ta so ba sam, ba kuma ta taΙa tunanin Abban zai
watsamata Ζasa a ido ba. Kai ta mance rabon ma da ta bada shawara irin haka
dangane da abin da ya shafi yaran ya musanta. Ganin sauyin dake saman fuskarta
ne ya sa Abban Ζara riΖo hannunta ya Ιan matsa.
"Kiyi hakuri Maryama, ba fa watsa maki Ζasa a idanu
nayi akan al'amarin yaranki ba. Aa, ki dai daure na sani da zafi ka dinga ganin
Ιanka cikin yanayi mai firgitarwa. Amma a shawarce, me zai hana ta je Bichi ko
sati biyu ta yi kinga za ta samu nutsuwa da kwanciyar hankali."
Daure fuska Mami ta yi.
"Shikenan, Ιauke ta a yau ka kai ta sai Maijidda ta
zuba ruwa a Ζasa ta sha tunda ta ga gazawata a kula da Ummita. Nagode."
Tana kaiwa nan ta zame hannunta cikin na Abban ta soma
kokarin miΖewa tsaye. Ya yi saurin dakatar da ita.
"Haba Maryama, to kiyi hakuri naji na yi laifi a
kalamaina. Ba zan kai Ummita ba face da izninki. Kiyi hakuri, shikenan? Yanzu
me kike tunanin za'a yi don sama mata nutsuwa?"
Ta sauke ajiyar zuciya.
"Tunda har shawarar da na bayar bai yi ba, toh na fi
tunanin ka bayar da kudi muje da su ukun nayi musu Ζ΄ar siyayya sai kuma ita
Humaira da ka riga ka san matsalarta akan maza. Ganin wannan abu da ya afku ga
Ummitan ya Ζara sanyawa ta tsani al'amarinsu. Daidai da Fadeel din da muke
murnar ta soma sakin jiki da shi suna Ζ΄ar hira yanzun ko muryarsa ba ta wani
son ji. Tun wuri gwara a yi mata maganinsa. Na kuma fadamaka labarin wani mai
magani, idan har ka amince sai na kai ta a karΙo a gani ko za'a dace."
Abba ya kurawa Mami idanu, a duniya bai taΙa ganin matar da
ba ta damu da nata ba sai na wasu. Ba ruwanta da damuwar yaranta sai abin ya ci
tura. Matar da Ιiyarta ke kwance a gadon asibiti amma ba ta ko zancenta,
burinta ta samar da farin ciki ga yaran wasu. Kaunarta ya Ζara mamaye
zuciyarsa, ya riΖo hannuwanta ya sumbata sannan ya sakarmata murmushinsa da ya
san yana daga cikin abin da yake Ζara dulmiyar da ita cikin kogin sonsa. Ita
kuwa sai ta Ιan kauda kai tana murmushi.
"Ina kaunarki Maryam, Allah ya yi maki albarka ya bar
mu tare. Kin cikemin gurbin mace hudu a duniya. Babu abin da zan ce maki sai
fatan alheri. Yanda kika ce haka za'a yi, gobe ki shirya zan baku kudi, ku fara
da siyayyar, koda zuwa jibi ne kuma sai
ki kai Ιiyartaki wurin mai maganin. Ina fatan hakan ya yi maki?"
Har lokacin tana murmushi ta gyaΙa mishi kai.
"Ya yi ranka ya daΙe. Fatanmu Allah ya maidowa yaranmu
farin cikinsu."
Cikin jin dadi Abba ya amsa da amin amin.
***
Washegari kuwa hakan
aka yi, tamkar ba Mamin da Tasleem Ιiyarta
ke kwance gadon asibiti ba, tamkar kuma ba wacce Ιiyarta mace ta farko
ba (Futuha) ta kawo mata Ζorafin tashin hankalin da take ciki. Daga fuskarta za
ka fahimci kamar a duniya ba ta da wata aba wai ita matsala ko kuma damuwa. Ta
saki ranta suka zagaye shoprite da su Humaira da Raihana. Ummita sosai kuwa ta
sake Ιin kamar yanda Mamin take buΖata, su kansu sun ji dadin yadda yanayinta
ya sauya. A Ιangaren Ummitan kuwa, ta tabbatar domin ta saki jiki ne aka yi duk
wannan shiri hakan ya sa ba ta watsawa Mamin Ζasa a ido ba, ta daure ta yakice
damuwarta ta saki jiki. A Ιangare guda shima Sahabi na nashi iyakar kokarin
ganin ya faranta ran abar kaunartasa. Wannan ma ya yi tasiri kwarai a zuciyarta
amma har lokacin wannan baΖar ranar ta Ζi Ιacewa a tunaninta da
mafarkanta. Su ne har gidan Hajiya
Lubna, sun Ιan jima tare da yaranta a Ζasa inda Mami ta haye saman kafin daga
bisani ta sauko su wuce.
"Mami ba zamu
leΖa Anti Tasleem ba?" Cewar Raihana. Mamin ta yi shiru. Ganin haka sai
Ummita ta sa baki.
"Mami don Allah
muje a duba ta."
Humaira kuwa uffan ba ta ce ba, asalima kallon shuke-shuken
dake farfajiyar gidan Hajiya Lubna kawai take.
"Shikenan, muje.
Yarinyar ce ta ban takaici, kina da ciki don sakarci ki tsaya wani faΙa akan
kishin banza da wofi."
Su dai babu abin da suka ce. Humaira ta buΙe bayan mota
Ζarama Ζirar KIA da Abba ya tsiya ta shiga. Mami ta Ιan bita da kallo sai kuma
ta murmusa ba ta ce uffan ba. Ta dubi Hajiya Lubna.
"Shikenan
Hajjaju, sai mun yi waya."
Ζ³ar dariya Hajiya Lubna ta yi.
"Toh Hajiya Mamin yara. A gaida Tasleem din ki ce mata
ta sha kuruminta zan zo."
"Ai shikenan. Za ta ji."
Daga haka suka yi sallama.
***
Malamin ya yi shiru
yana duban Ζasa, can kuma ya Ιago ya kalli Murja ya girgiza kai.
"Abin da kike so
ba zai taΙa kasancewa ba."
Wani malolon baΖin ciki ya turnuΖe zuciyarta. DaΖyar ta haΙiyi
miyau mai Ιaci ta ce.
"A yanzu kake
nufi ko har a gaba? Kenan Humaira ba za ta kasu ba?"
Malamin ya yi Ζ΄ar dariya.
"Wane mutum! Inji mutuwar. Ai Hajiya Murja babu wanda
ba zai mutu ba. Kuma ni da na isa na duba mutuwar wani ai da nawa zan fara
dubawa. Abin nufi kina son ta mutu kada ta auri Fadeel din ko? Toh hakan ba zai
taΙa yiwuwa ba."
Ji tayi wani abu mai
nauyi ya tsaya a Ζahon zuciyarta. Malamin ya zubamata idanu, ya lura ba ta
saduda ba don haka ya sauya zancen.
"Amma fa idan kina so za'a iya nakasata rayuwarta. Zamu
iya nakasta ta gaba Ιayanta. Amma da sharaΙi, matukar aikin bai ci ba, zai dawo
kanki. Kin amince?"
Ba tare da dogon tunani ba ta amsa.
"Eh na amince."
"Murja, ko za ki yi shawara?"
Ranta ya Ιaci sosai.
"Wancan karon haka ka ce min, wannan karon ma kana nema
ka tauye ni da faΙin haka ko? Toh yanzu ba shawarar da zan yi, ga kudi nan ka
yi duk abin da ya kamata."
Ta bude jaka ta ciro bandir na dubu ta dire mishi.
Ya yi murmushi.
"Shikenan, ni nawa aiki. Sauran ke za ki yi da kanki.
Dole kina bukatar zuwa inda ita yarinyar take. Ki je ki dawo nan da kwanaki
uku."
Murja ta ji kwanakin tamkar watanni a wurinta. Tana jin
zuciyarta za ta iya bugawa na yanda Fadeel ke rawar Ζafa akan Humaira, kullum
ya zauna da Hannatu a falon Anti to fa hirarta ne kawai.
"Babu wani aiki
da za ka yimin akan Fadeel?"
"Aiki kai, ga wannan layar ki tabbatar kin saka a
ΖarΖashin katifarsa, muddin ya kwana ya tashi ki Ιauke ki binne. Wannan kwallin
kuma ki zizira ki tabbatar kun yi ido hudu."
Ta yi murmushi, duk da cewa ta yi abubuwa da dama ba ta yi
nasara a kan Fadeel ba amma hakan ba zai sa ta karaya ba. Ta karΙa ta sa a jaka
ta mishi sallama ta tafi zuciyarta sol.
***
Misalin Ζarfe bakwai da
mintoci ne, Fadeel ne zaune a falon Alhaji tare da Hannatu da Alhajin.
Wannan damar Murja ta yi amfani da shi wajen kokarin ganin ta Ζaddamar da
shirinta, sai da ta fakaici idanun su Khadija da Abdulmaleek wadanda suke kallo
ta nufi Ιangaren Fadeel. Sai dai ta yi mugun mamakin jinsa a garΖame da
muΖulli. Ta ciji leΙΙa don takaici kamar ta haΙiyi zuciya ta mutu haka ta ke
ji, sai kuma ta tuno duk abinsa da safe yana barin mukullin Ιakin ya fice don a
yi mishi gyara. Wannan ya sa ta yi murmushin mugunta ta juya tana mai kara cin
alwashi.
***
Futuha na zaune tana
faman cika da batsewa kamar ta fashe, Alhaji Yakubu ya shigo fuskarnan a
murtuke ya zauna yana dubanta gami da jefamata ledar dake hannunsa.
"Idan har kina
son mu cigaba da rayuwar farin ciki da ke, to ki gaggauta shan magungunan nan,
an tabbatarmin zasu yi sanadin zubewar cikin dake jikinki. Idan kuwa har ki ka
Ζi, kika dage sai kin haihu da ni, toh shakka babu baΖar rayuwar da za ki
fuskanta sai kin sha mamakinsa. Sannan rashin bin umarnina zai yi sanadin da
zan yi aure."
"Wallahi ba zan sha ba! Idan kuma aure ne ka yi idan ka
isa! Kuma wallahi ka ji na rantse maka matukar ka ce za ka wulakantani ba zan
zauna ba sai dai ka sakeni!"
Ya yi wata muguwar kyakyacewa da dariya. Ya nunata da yatsa.
"Ke Futuha, ba ki da hankali ashe? An fadamaki ni
Yakubu zan saki mace? Ai babu wannan ranar a duniyata. Zaman aure da ni ya
zamar maki dole. Koda bakya so kuwa sai kin zauna da ni. Na dai fadamaki,
muddin rayuwarnan mai dadi da na ΙanΙana maki kina so ya Ιore, to sai kin bi
umarnina. Idan kuwa kin Ζi zan auro..."
Sai kuma ya yi shiru yana jinjina kai duk a kokarinsa na
shanye sirrin dake ransa. Tun su na Dubai ya yi wani irin sabo da Ιinkewa da
Sa'a Ζ³ar Snow, kullum yana shafinta yana jifanta da likes da kuma chatting da
suke yi a Ιoye. Tsantsar kalaman iskanci da ma hotunan tsiraicin da take
turomasa ya yi mugun hargitsa shi, ba ya fatan ya kusanci zina amma ya sha
alwashin aurenta. Ta kuma amince sannan ta ba shi lokaci ya gama cin angoncinsa
kamar yanda ta buΖata. Ya fi kowa sanin Ζ΄ar tsamar dake tsakaninta da Futuha,
ya tabbatar idan zancen ya fasu to fa ba za su kwashe da dadi ba hakan ya sanya
shi zaΙar yin shiru.
"Ka auro wa?! Ka
faΙamata ko ma wacece don ubanta ta yi kaΙan ta shigo gidannan!"
Ya mike ya watsamata harara.
"Saboda ke kika haife ni kenan? Titse ni za ki yi na faΙamaki
ko? Toh sai ki yi da wani."
Yana kaiwa nan ya kama hanyar fita, aikuwa ta yi tsalle ta
dire gabansa idanunta har sun kaΙa tsabar kishi da Ιacin rai, cakumar wuyan
rigarsa ta yi tun ma ba ta kai ga furta Ζala ba ya cire hannu sai ji kake tas a
saman fuskarta.
"Ke! Ashe iskancin naki ya kai haka? Ni kike cakumarwa
wuya?! Wannan ya zama na Ζarshe idan kika Ζara mugun gangancin nan sai na
nunamaki ba ki da wayo! Banza marar tarbiyya Ζ΄ar rawar Tiktok kawai!
Mtsw."
Yana kai wa nan ya fice yana gyara zaman babbar rigarsa,
dama dawowarsa kenan daga wurin Ζ³ar Snow, don dai kalamai da rungume rungume
wadannan ya sha su kamar ba gobe, ita ta yi mishi rakiyar siyan magani kafin ya
maida ta gida da siyayya mai yawa sannan ya dawo gidan.
Futuha ta yi kuka mai isarta tamkar ranta zai fita sai dai
ta Ζudurta a zuciyarta Alhaji Yakubu bai isa ya wulakanta ta ba. Sai ta Ιauki
mummunan mataki a kansa kamar yanda Mami ta ba ta shawarar ta kwaci kanta da
gidanta, to kuwa za ta Ζwata ta Ζarfin tsiya.
Gama tunaninta kawai ta ciri waya ta kira wata tsohuwar aminiyarta
Aneesa Jafar. Matar aure ce amma tantiriyar Ζ΄ar duniya ce domin ko a rayuwarsu
ta makaranta tana cikin masu neman soyayyar Sir Ibb duk kuwa da auren dake
kanta. Ita din shaida ce a yanda take juya mijinta a gida hakan yasa ta yanke
shawarar tuntuΙarta. Tun sadda ta yi aure ba ta Ζara nemanta ba saboda a
ganinta ajinta ya fi nata, sai a yanzun da buΖatarta ta taso.
Kasancewae Aneesa ta
iya barikanci, ko kusa ba ta nunamata komai ba suka gaisa hannu bibbiyu. Sai
kuma Futuha ta warware mata damuwarta. Dariya Aneesa ta yi kafin ta amsa.
"Ai wannan ba
matsala ba ce yar uwa, amma ki yi yanda yace. Ke banda abinki mene ciki don kin
zubar da cikin wanda ya nuna ba ya son haΙa zuri'ar da ke? Kuma wallahi kika
yarda kika haihu da shi to ina mai tabbatar maki nan da nan za ki lalace ki
zama wata daban. Ki daurewa ranki ki zubar da cikin idan ya so ki kawo kudi mu
san hanyar da zamu bi ki mallake shi, yanda ko tsinke bai isa ya tsallake ba
matukar ba ki yi mishi izini ba."
Cikin sanyin jiki da kuma Ιan nutsuwar da Futuha ta samu ta
ce.
"Toh Aneesa. Ni dama tsoron mutuwa nake, kada na sha na
mutu naji ance masu zubar da ciki mutuwa suke yi."
"Mutuwa ai sai lokaci ya yi, nidai ina ba ki shawarar
ki zubar kuma ki je ki yi planning abinki hankali kwance. Matukar dai kina so
mu cimma burinmu."
Ta sauke ajiyar zuciya ta jawo ledar magungunan sannan ta ba
Aneesa amsa.
"Shikenan, yanzun nan zan sha. Nagode Aneesa, zuwa gobe
duk yanda ake ciki zan kiraki mu ji
abinda ya dace a yi."
"Shikenan, sai na ji ki."
Daga nan suka yi sallama. Ta Ζurawa magungunan idanu, a wata
farar takarda suke, ta yi shiru can kuma kamar wacce aka tsikara ta mike ta
dauko gorar ruwa ta bude, ta zazzaga magungunan a hannunta ta shanye su tas sai
jiran sakamako.
***
Tana kwance tana juyi
yayinda yan uwanta duka ke bacci abinsu. Ta mike zaune ta yi shiru, tashin
zuciya take ji sai dai ta rasa yanda za ta yi ba ta kaunar ta yi amai motsin
yunΖurin ya tashe su. Zuwa lokacin ta soma shan jinin jikinta, tsoro da firgici
ya soma shigarta. Bai fi kwanaki uku watan da suke ciki ya mutu ba amma har yau
babu labarin ganin al'adarta. Tsoro iyaka Ummita na cikinsa. Ta kasa jurewa
tashin zuciyar da take ji sai ta bude dakin ta fita da sauri zuwa falon
bandaki, nan fa ta shiga kelaye amai kamar hanjin cikinta za su zubo. Duk wani
kayan kwalam da ta ci a ranar sai da ta dawo da shi. Ta kammala ta wanke fuska
ta gyara wurin, ta kuma Ιauro alwala ta dawo falon ta zauna. Sai kawai ta fashe
da kuka mai tsuma zuciya ga wani irin mugun sanyi da ya lulluΙe ta lokaci Ιaya.
Ba ta son koda tuna kalmar da take tunanin shi ya zama damuwarta balle har ta
furta.
'Idan ya tabbata haka din ne ya za ki yi da Sahabi?'
Zuciyarta ta watso mata tambayar, ta rike kai sai kawai ta
fashe da kuka sosai. Ba ma Sahabin kawai ba, ta ina za ta soma karΙar wannan
Ζaddara na rainon cikin da ta same shi ta hanyar fyaΙe? FyaΙen ma daga Ιan
ta'adda?
Tana wannan kukan mai tsuma zuciya ba tare da sanin irin
Ζarfin buΙe muryar da ta ke yi ba har sai da ta ga hasken fitila a falon an
kunna saboda akwai wuta. Mami ce, kafin Mamin ta ce wani abu sai ga Humaira a
gigice ta fito itama. Kusan lokaci guda suka Ζaraso gareta.
"Mene ne ya faru Ummita?"
Humaira ta tambaya jikinta har yana rawa nan da nan itama ta
soma hawaye ba tare da sanin ainahin dalilin kukan yar uwarta ba.
Ummita ta rungumeta tana kuka sosai.
"Ciki Humaira, Humaira zan haifi shege."
Da karfi kuma cikin daga murya Humaira ke girgizata kamar
zararriya tana fadin.
"Wa ya fadamaki kina da ciki? Karya ne! Karya ne ba ki
da ciki!!"
Mami ta dago Ummita.
"Wa ya fadamaki wannan mummunan labarin? Kin ga wasu
alamomi ne?"
Mamin ta fadi nata hankalin itama a mugun tashe, nan da nan
cikinta ya duri ruwa. Cikin sheshsheka
Ummita ta ce.
"Ma..ma.mi, amai nake ta yi."
Ajiyar zuciya Mamin ta sauke.
"Haba Ummita, amai kuma sai aka ce maki yana nuni da
cewa kina da ciki kenan? Amai ai alamun cutuka ne da dama, ba lallai sai ciki
ba. Lokacin al'adarki ya yi ne?"
"Eh Mami, har ya wuce."
Gaban Mami ya buga da Ζarfi, Humaira sunan Allah ta shiga
ambato sakamakon ji da ta yi tamkar an zare mata wani laka na jiki. A durkushe
take amma kuma jiri ne ke kwasarta. Tana ji tamkar a mafarki ake wannan diramar
ba a farke ba.
"Maryama, meke
faruwa ne?"
Suka juya gaba daya, Abba ne sanye fa jallabiya a tsaye a Ιan
rikice, ya tako ya Ζaraso ganin Ummita na kuka ya sanya shi Ζara jin rashin
nutsuwa sosai.
"Ummita, meyafaru kike kuka?"
Mami ta yi saurin share hawayen da suka zubomata, ta miΖe
tsaye.
"Babu komai, ba ta jin dadi ne. Humaira ku shiga ciki.
Ki kwantar da hankalinki gobe idan Allah ya kaimu zamu yi test a gani."
Bayan wucewarsu Abba wanda ya daskare a tsaye cikin wani
mugun faduwar gaba ya ce.
"Maryama, meye hakan kuma? Na kasa gano bakin zaren wannan tattaunawar da
tsakar dare?! Me kike son ki ce?"
Gaba daya ma Abban ya diririce ko kadan ba ya cikin
nutsuwarsa.
Mami ta dafe hannunsa.
"Babu komai Abban yara, muje zan maka bayani."
Zai Ζara magana ta hana shi ta hanyar roΖonsa akan su tafi
dare ne kar a ji sai kuma ya hadiye maganar ba musu ya yi gaba zuwa Ιaki ta
bishi a baya bayan ta kashe fitilun falon.
Ya ji zancen tamkar
saukar aradu, nan da nan ya dafe kansa.
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Maryama wannan
mummunan labarin da me ya yi kama? Tashi tashi muje asibiti yanzu a dubamin
ita."
Mami cikin hawaye ta yi saurin dakatar da shi ta hanyar dafe
kafarsa gami da girgiza kai.
"Aa Abban yara, kar muyi haka. Yin hakan tamkar tonuwar
asirinmu ne. Duniya sai ta san halin da muke ciki. Ka kwantar da hankali tunda
ana siyar da Pt-strip na awon ciki, gobe da safe mu bayar a siyo a auna
fitsarinta don mu ga halin da take ciki. Mu yi fatan alheri da fatan kar
zatonmu ya tabbata.
Ajiyar zuciya mai karfi Abba ya saki.
"Innalillahi...Ya Ilahi! Wannan ranar dame zan kirata
ni Isuhu? Inama tun farkon fari ban hana Hajiya Maijidda riΖon Ummita ba tun
tana Ζarama, da watakila ba zan ga wannan ranar ba."
Wani irin zuciya ya tasowa Mami, ta ji tamkar ta haΙiyi
zuciya ta mutu. Ranta ya yi mugun Ιaci, wato duk hakuri da dauriyar shanye
damuwa da bakin cikin RIΖON BARE da ta yi, da wannan sakayyar Abban zai bi ta?
Ta so ta furzar da abinda ke ranta sai kuma ta daure kamar koyaushe ta shanye
rabi da kwatan Ιacin ranta ta ce.
"Wane irin rashin tawakkali ne haka Abban yara? Ka isa
ka hana Allah ikonsa ne akan al'amarin Ummita? Ummita ko bangon duniya ta je
idan hakan ya Ζadartu a kanta sai ya afku. Ban da haka ma, kenan kana kaicon
rayuwar da ta yi a hannuna? Kana kaico da irin abin da ya fada mata? Ko a
tunaninka a sanadina ne aka sace su har kaddarar fyaΙe ya faΙa kan
Ummita?"
Ta karasa zancen da wani irin kausasshen murya, ganin ya
kalleta da sauri da alama zancen bai mishi dadi ba kuma bai san fassarar da za
ta ba shi kenan ba ya sanya ta fashewa da kuka mai tsuma zuciya.
"Dama na sani Yusuf, watarana sai ka ga gazawata akan
yarannan duk kuwa da..."
"Haba Maryama, don Allah don Annabi s.a.w ki yi hakuri.
Wallahi zafin bacin rai da damuwa da tashin hankali ne ya sanya ni wannan
maganganun marasa kyawun ji. Ko daidai da kiftawar ido ban taΙa kawowa za ki
cutar da wani a cikin yaran da kika haifa a cikinki ba ma balle a kai ga
Ummita. Yarinyar da kika daukaka ta kika kuma riΖe ta hannu bibbiyu tamkar ke
kika haife ta a cikinki. Wane irin butulu ne ni da zan yi maki haka? Ki yafemin
domin Allah. Na tuba kiyi min uzurin halin rudani da tashin hankalin da na
tsinci kaina ciki."
Mami ta mike ta ja guntun tsaki ya yi saurin tarar gabanta.
"Haba Maryama, da wanne kike so na ji ne? Da tashin
hankalin nan na Ummita ko kuwa da Ιacin ranki? FaΙamin, me kike so nayi ki
huce?"
Jin haka sai kuma ta yi shiru tana goge fuska.
"Kar ka Ζara irin wadannan kalaman naka na rashin
tawakkali."
Ya yi murmushin karfin hali ya rungumeta.
"Idan har wannan ne ba zan kara ba. Na ma yi istigfari
tun sadda kika ankarar da ni kurena. Mu ji da damuwa daya yanzu."
Ta gyada kai, bandaki ta shiga ta Ιora alwala ta sanya
hijabi ta hau saman darduma. Sosai yake jin so da kaunarta a zuciyarsa. Shima
sai ya fasa neman wuri ya kwanta kamar yanda ya so duk kuwa da irin sakensa a
ibada lokuta da dama. Kusan wannan shi ne kadan daga inda ya kuskuro, rashin tsayawa
kai da fata wurin ibada sosai sai idan ya fada matsala babba.
***
Washegari tashin
hankalin da suka riski kansu ciki sai ya mantar da su wani batun zuwa kai
Humaira asibiti.
Gidan ya zama tamkar
gidan makoki. Suna zaune jigum suna jira Mami da Ummita su fita daga bandaki
don sanin matsayar Ummita, akwai cikin ko babu. Abba ya kasa fita kasuwa si
safa da marwa yake a falon balle kuma Raihana wacce tun jin abinda ke faruwa ta
kasa motsawa ballantana ta wuce makaranta. Sai Humaira da ta dau carbi tana jin
tamkar an yi mata mutuwa. Mubarak kuwa wanda shi ya fita ya siyo abin awon
cikin, sai ya jingina jikin bangon falon ya yi shiru cikin bugun zuciya.
A wannan yanayin Mami
ta fito a gigice kuma a guje, gaba daya suka yi kanta har suna rige-rige.
"Meke faruwa?" FaΙin Abba yana jin kamar ya kife
tsabar jiri.
Mami ta fashe da kuka.
"Mun shiga uku! Shikenan Abban yara asirinmu zai tonu.
Ciki ne da Ummita."
Abba ya ja baya da sauri ya zauna saman kujera mafi kusa da
inda yake, yayinda Humaira ta yi mutuwar tsaye. Ita kuwa Raihana kwasa ta yi a
guje zuwa bandakin don ganin halin da Ummitan ke ciki. Aikuwa ta iske ta a kife
tamkar babu numfashi. Ta kuwa Ζwalla ihun kiran sunan Abba. Kusan da rige-rige
suka shiga banΙakin. Mubarak ne ya yi ta maza ya cicciΙe ta bayan ya tabbatar
da bugun zuciyarta ya fiddo ta falon ya shimfiΙe saman kujera sai dai duk wani
kokari na watsa ruwa da ma sauransu anyi amma babu alamun Ummita ta san ana yi.
Ana shirin fita asibiti Mami ta dakatar ta ce gwara a kira makwafciyarsu wata
likita gudun fashewar zancen a duniya. Abba ya yi na'am, Mubarak ne ya fita da
rawar jiki har gidan Dakta Inteesar an ci saa kuwa ta fito cikin shirin tafiya
asibiti. Ganin Mubarak aboki ga babban Ιan ta Najeeb ya sanya ta dakatawa.
RoΖon da ya hau yi mata ya sa ba ta iya yi mishi musu ba sai ta shiga motarta
suka kama hanyar gidan don akwai Ζ΄ar tazara kaΙan ita daga bayansu take. Cikin
ikon Allah ta ba Ummita taimakon gaggawa ta farfado sai kuma ta dube su.
"Ya dace a yi mata gwaji sosai din tabbatar da abin da
ke damunta."
Ta furta hakan ta yi shiru don jin me za su ce, a matsayinta
na likita ta gama tabbatarwa Ummita na da juna biyu. Shiru ta yi musu don ta fi
son ji daga bakinsu sun amince da gwajin. Tana sane da labarin abinda ya afku
ga Ummita. Su kansu mutanen gida ba su da masaniyar cewa duk yadda suka so da Ιoye
labarin fyaΙen Ummitan sai da ya fita ba. A duniyar yanzun ai mutum ake kiwo ba
dabba ba, kana abu kana ganin tamkar duniya ba ta sani ba amma zirr ake
kallonka.
Abba ya yi yaΖe.
"Babu damuwa Dakta, zamu kai ta asibiti."
Ta lura ba su son zancen ya fasu, ita kanta ta tausaya musu
babu kamar Ummita wacce tunda ta farfado uffan ba ta ce ba, kukan ma ta Ζi
yinsa sai sauke ajiyar zuciya akai-akai. Haka Dakta Inteesar ta yi musu sallama
bayan ta rubuta magungunan da ya dace wanda take da tabbacin zai taimaki Ummita
bisa yanayinta na mai juna biyu. Mubarak wanda ke tsaye ya Ζurawa Ummita idanu
yana jin abu mai nauyi na taso mishi wanda ya fi kama da tsabar tausayinta da
kuma kauna ta Ζ΄an uwantaka. Kamar dai yanda yake tunani. Shi ne ya karΙi
takardar magungunan ya fice.
***
Kwance yake idanunsa a lumshe, babu komai a ransa sai
Humaira. Yana ji a jikinsa an soma zuwa gaΙar da yake da tsananin buΖatar
kasancewarsu tare a inuwar aure. Shi din fa ba dutse ba ne, namiji ne kuma
lafiyye da yake buΖatar aure. Soyayya mai Ζarfin da yake yiwa Humaira shi ne
silar da ya danne wannan buΖatuwar ya Ιora shi kacokam a kanta yana jiran
lokacin da mafarkinsa zai tabbata. Sai dai kuma yaushe ne?
Wannan damuwar ce ta hana shi fita ko'ina, hatta da mai
gyara mishi dakuna bai san yana nan ba, shi dai Nura yana falo yana aiki kafin
ya shiga Ιakin. Hatta shi bai dan cewa Fadeel na gidan ba sakamakon motarsa da
ba ta nan tun daren jiya. Ζaci ta yi a hanya ya bar ta can makanikinsa ya
je ya Ιauka.
Daidai lokacin Murja ta faΙo Ιakin da Ζunshin kayan gugan
Fadeel din a hannunta wanda ta karΙa a hannun Sadi mai gugansu, dama ta
jima a yar barandar da zau sada ta da Ιakin Fadeel tana tunanin dabarar da za
ta yi wa Lawal ta shiga. Sai ko ga Sadi ya zo wucewa nan da nan ta karΙa ta ce
za ta karasa da shi.
Suka gaisa da Lawal a falo, ta nuna zai karΙa ya shigar da
su ta ce masa ya bar shi za ta karasa ladanta. Bai ce komai ba, dama a farko
gargadin da Fadeel din ya yi mishi ne ya sanya shi dakatar da ita, ya hana kowa
ya shigo masa sashinsa idan ba ya nan matukar dai ba Fu'ad ko Alhaji da Ibb
bane. Amma ganin kayan wankin ne kawai za ta ajiye ta fito ya sanya shi ba ta
wuri shi kuma ya ci gaba da kakkaΙe kakkaben kujeru da kayan kallo.
A lokacin da ta shiga dakin, Fadeel ya zagaya bandaki, yana
dab da fitowa ya ji motsin mutum a dakinnasa, bai kawo kowa ba sai Lawal. Ya
san ba shi da masaniyar yana gida bai fita ba. Don haka ya fito daga shi sai
singilet da dogon wandon sport.
Daidai lokacin da ta ajiye kayan a gefe ta yi wurgi da filo
ta Ιaga katifar gaba Ιaya da zummar sanya layar. Kasancewar idanunta ya rufe ko
kadan ba ta ga wayoyin Fadeel din dake gefe ba a ajiye. Tana zuci-zucin ta yi
ta Ζare kafin shigowar Lawal ya isketa.
Fadeel ya bude kofar ya fito, hakan ba karamin
razanata ya yi ba ta saki layun dake a hannunta suka zube a Ζasan darduma.
Mamaki mai tsanani ya kama shi har ya bude baki ya kasa magana. Ya karasa sosai
ya kara kallo, tabbas layu ne. Nan da nan ya tamke fuska tamkar bai taΙa wani
abu wai shi dariya ba.
"Zamanki a gidannan ya Ζare. Wallahi kin ji na rantse
maki ko yau Anti Amarya ce ta haifeki dole ki bar gidannan. Ni Fadeel na fi
Ζarfinki, na kuma fi karfin duk wani da zai sanyaki aikata mugun abu don ki ci
galaba a kaina."
Jin haka sai kawai ta hau tsuma da borin kunya.
"Ni..nifa ba.."
"Shut up!"
Tsawar da ya yi ya sanya Lawal faΙowa Ιakin. Nan da nan
hankalinsa ya tashi, shima idanunsa suka sauka kan layar dake ajiye a tsakar
dakin. Fadeel ya hau shi da faΙan don me ya bari ta shigo masa daki alhalin ya
gargaΙeshi.
"Ka yi hakuri YallaΙai, wallahi na yi nayi da ita ta
bani kayan gugar na kawo ta nunan ita za ta kai. Shi ne.."
"Shi ne me?!"
Fadeel a zafafe ya tari numfashinsa jikinsa har Ιari yake yi
ga tsikar jikinsa da ya tashi gaba daya. Abin da ya faru shekarun baya kawai ya
fadomasa a rai, sadda ya kama Mamar Fu'ad tsamo tsamo a Ιakin
Mahaifiyarsa tana barbaΙa magani. Daga ranar ya tsane ta, rashin wayo da wauta
kuma ya sanya bai yi tunanin sharewa ba. Tun daga kuma sadda mahaifiyarsa ta
taka wannan magani ba ta Ζara zaman lafiya ba da Alhajinsu, har dai a karshe
Alhaji ya yi mata sakin wulakanci. Shi kuma ya sha baΖar wahala a hannun Mamar
Fu'ad. Ya ji ya Ζara tsanar Murja ninkin ba ninkin. Kuma yanda ya rantse ba zai
yi kaffara ba sai Murja ta bar masa gida ubansa idan ko Alhaji ya Ζi to fa shi
zai bar gidan gaba Ιaya.
Murja cike da kunyar kamen da aka yi mata ga uwa uba Lawal
dake tsaye ya Ζi fita yana kallon ikon Allah, ta durkusa ta kwashi layun ta
fice tana dakawa Lawal wata uwar harara kamar idanunta zasu zazzago.
Fadeel ya dafe kai yana mai runtse idanu zuciyarsa na
tafarfasa tamkar an kunna ruwan heater.
"Ka yi hakuri in sha Allahu zan kara kiyayewa."
Gyada masa kai kawai ya yi gami da yi mishi alama da hannu
akan ya fita, Lawal ya juya ya fice mamakin wannan hali na Murja da bai taΙa
zato ba. Lallai mutum ba abin yarda bane.
Shi kuwa Fadeel sai da ya samu nutsuwa sannan ya fada wanka,
ba shi da niyyar fita daga gidan amman daga faruwar al'amarin ya ji gaba daya
gidan ya fita a kansa. Kai tsaye wurin Ibb ya tafi, dama tun jiyan yake faman
kiransa akan zancen bikinsa da ya taso yana Ζin zuwa yana ba shi uzurirrika
saboda damuwar Humaira da batun auren Ibb ke taso masa da shi.
Murja kuwa tana zuwa ta shiga haΙa kayanta, ta gwammace ta
bar gidan da ace Fadeel ya fasa zancen nan har Alhaji ya tsane ta ya kuma Ζi
jinin haΙa zuri'ar Ιansa da ita. Anti Amarya kadai ta fadawa, nan da nan
hankalinta ya yi mugun tashi, ta hau ta da faΙa tamkar ta ari baki. Babban
baΖin cikinta ma ba ta yi shawara da ita ba ta yi raΙin kanta.
"Ba ki da wayo ko kaΙan Murja! Wa ya fadamaki samun
Fadeel a hannu abu ne mai sauki? Ke kinsan irin karfin ibadar wannan yaron? Toh
wallahi ko wani Malamin ba zai nuna masa tashin dare da nafilfilu ba ko an
fadamaki baΖin tabon sallar dake goshinsa da goge dutse a goshin ta same shi?
Kai Murja! Toh kuwa ya zama dole ki bar gidannan! Ni zan samu shi Fadeel
din nasan siyasar da zan mishi don kar magana ta je kunnen Babansa."
Murja ta kara jin wani malolon abu ya tsaya a Ζahon
zuciyarta. Dama ta sani Anti Amarya ba za ta taΙa goyamata baya ba. Ta kuma
soma yarda da yayarsu Rabi da ta ce Anti Amaryar kanta kawai ta sani, ba
wani so take yi ta tallafe ta ba shiyasa ta ce ta sauya dabi'u ta nuna
ita wata salihar ce. Ban da haka ai ta san wannan ba abu ne mai sauki ba da
kuma zai yiwu kawai a yi duka Ιaya lokaci daya a wuce wajen.
Ta shareta ta cigaba da hada akwatin kayanta. Kafin wani
lokaci ta kammala ta fice abinta, Anti Amarya ba ta kara cewa uffan ba, ba
karamin Ιata ranta ta yi ba, ita yanzu babban tashin hankalinta yanda za ta
rufe maganar kar ta je kunnuwan Alhaji. Ta tsinewa Murja ya fi a Ζirga. Wannan
ya sa ko kallonta ba ta yi ba da ta fice. Allah ya taΖaita Hannatu ba ta gidan
ta je wurin dangin Alhajinsu.
***
Gidan su Humaira
tamkar gidan makoki, babu walwala a fuskar kowanne, Abba kasuwar ma kasa fita
ya yi. Mami kuwa ta Ζulle a Ιaka ba wanda ya san me take yi. Ummita kuwa tana
kwance shiru kawai har baccin dole ya dauketa sanadin magunguna da ta sha kuma
a daren jiya ko kadan fargaba da damuwa sun hana ta runtsa.
Karatun alkur'ani
Humaira ta kunna a waya ya karaΙe Ιakin don su samu nutsuwar zuciya. Tana
sauraro tana bi a hankali ta hanyar motsa lebΙanta duk cikinsu sun kasa yiwa
Ummita kwakkwarar magana don ba su san ta inda za su fara ba. Raihana kuwa kanta ta cusa karkashin pillow tana kuka a hankali
tana kuma bin karatun. Ji take yi inama komai dake faruwa a mafarki ne. Amma
ina, wannan zahiri ne, shi ne kuma gaskiya mai mugun Ιacin da ke addabarsu.
Hatta da Mubarak ya shiga wani irin hali, komai yake yi
Ummita ce a ransa, bisa umarnin Abban ya bi su Yassar shago amma yana zaune
cikin mugun Ιacin rai. Ya rasa dalilin da ya sa ta tsaya mishi a Ζahon zuci
watakila kuma tsananin tausayi ne da duba da irin kirkin Ummitan yarinya mai
kirki da sanin ya kamata. Bai taΙa ganinta ba face da murmushi saman fuskarta,
tana da hakuri sosai da sanyi. Dabi'unta abin so ne ga kowane namiji.
***
Mami a hargitse take
ta faman danna kiran layin wayar amma abu Ιaya kwamfutar ke nanata mata, a
kashe wayar take. Koda ta gaji ta yi wurgi da ita tana mai jan tsaki. Goshi ta
dafe cikin tsananin ruΙu. Can kuma ta ji wayarta ta Ιauki Ζara. Ta yi azamar
karasawa saman gadon ta Ιauka. Lambar dai da take ta kiciniyar kira ita ce aka
kirata da ita. Ta Ιaga cikin sauri.
"Kai Bala! Ina
ka shiga ne?"
"Kiyi hakuri Hajiya, chaji na bayar sadda kika kira
ba'a Ιaga ba sai mai chajin kawai ya kasheta gudun a yi
ta kira. Ina fatan lafiya?"
Ta girgiza kai idanu a runtse tamkar yana ganinta.
"Ba lafiya ba Bala, aiki ya Ιaci! Duk inda mutanen nan
suke ina buΖatar ganinsu. Wannan karon ni da su zamu tattauna. Sun min ba
daidai ba, na fadamusu dama idan har sakamako bai yi kyau ba to sai sun
maidomin hatta rabin kudin da na ba su. Ba za su ci komai daga dukiyata ba
tunda har kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba."
"Hajiya ban fahimci me kike son cewa ba? Ke ce fa kika
ba su umarnin barin wajen koda kuwa kudaden ba su shiga hannunsu ba? Ta ya ya
kuma za ki Ιora musu laifi kacokam?"
"Bala sun yiwa yarinya fyaΙe, yarinyar da ban so hakan
ta kasance da ita ba. Da ace waccan mayyar aka yiwa ba zai dameni ba. Yanzu dai
mugun abun da suka yi ya bayar da mummunan sakamako, ciki ya shiga."
Bala ya doka salati mai karfi. Can kuma cikin rage murya ya
ce.
"Ciki kuma Hajiya? Toh me ake jira da ba za'a zubar
ba?"
Mami ta sauke huci.
"Zubarwa ai wajibi ne. Dole na zubarmata da shi ko don
gudun tonuwar asirina. Amma yanzu ni ka nemo min su mutanen ko kuma ka aikon
lambar shi Babban nasu sai muyi magana."
"An gama Hajiya, zan kira na sanar da shi sai na hadaku
a waya don dama ina shirin ce maki ba ya garin ya dan yi bulaguro zuwa
Kaduna."
"Shikenan, sai ka turo."
Tana kaiwa nan ta katse wayar tana ji kamar ta zabga ihu,
babu abin da idan ta tuna take takaici kamar rashin cin nasarar mallakar
dukiyar Abba da ta kwallafa a rai. Ga kuma shirin tonuwar asirinta da ke son
afkuwa, matukar cikin Ummita bai fita ba lallai babu shakka watarana abin Ιoye
zai fito fili.
***
Mami ta tabbatarwa Abba lalali sai dai a zubar da cikin
Ummita gudun zubewar mutuncinsu a idanun duniya. Tun Abba ya na nuna bai amince
ba har dai ta ci nasara a kansa ya yarda.
Ranar da zasu je a daren Mami ta shiga wurin Anna don
amsa kiranta. Anna ta dube ta a yamutse.
"Sai wani rawar Ζafa kike yi a cire cikin yarinyar nan,
idan an cire wa kike tunanin zai aure ta? Shi Sahabin ko kuwa dai shi mijin
naki ya ba babban Ιansa aurenta? Ba kya wannan hangen?"
Mami ta ji kirjinta ya buga da Ζarfi. Wannan zance na Anna
ko kusa bai mata dadi ba amma sai ta zaΙi ta Ιoye saboda dalilin da ita kadai
ta bar wa kanta sani.
"Idan har asirinmu zai rufu mene ne ciki Anna?"
DaΖuwa Anna ta wurga mata.
"Ungo nan nace! Ni dai da ace a asibiti nayi naΖudarki
zan iya rantsewa sauyamin ke aka yi ba ke ce jinina ba. Yanzu ke koda wasa idan
mijinki ya ce zai hada auren wannan gantalalliyar da Ιansa abin yarda ne a
wurinki? Babban Ιanki wanda bai taΙa kusantar zina ba a duniya shi ne za ki
yarda a hada shi da ita?"
Kafin Mami ta kai ga cewa komai Anna ta ji an bata amsa.
"Anna, kar ki kara danganta yan uwana da zina, kowa
shaida ne ba zina suka aikata ba, kaddara ce da
za ta iya faΙawa kan kowa. Sannan idan auren ne ma sai me? Ni ina sonta
kuma na rantsemaki a yau Sahabi ya janye da batun aurensa da Ummita to fa ki
rubuta ki ajiye ba ta da miji sai ni nan Mubarak!"
Ba Anna kadai ba, hatta da Mami wanda ganin inuwar mutum a
farko yasa ta Ιoye abinda ke ranta sai da maganar ta yi mata wani irin duka a
kirji. Ta dago tana kallon Mubarak din, sanin da ta yi mishi ba ya taΙa sauya
magana. Mutum ne mai magana daya wannan ya yi matukar Ιaga mata hankali har ta
kasa siyasar data saba na danne abin a zuciyarta. Fuskarta ta nuna tsantsar Ιacin
rai na gaske, idanunta har wani kaΙawa suka yi tsabar bala'i.
"Mubarak! Kar ka kuskura na kara jin makamancin wannan
maganar daga bakinka. Wacce kake faΙawa ka dinga tunawa ita ta haifar maku ni.
Ka kiyayi harshenka!"
Mubarak ya yi shiru kawai yana jin zafin maganganun Anna har
lokacin suna tarfafasa zuciyarsa. Anna kuwa ta hau zagin Mami tana fadin ta yi
mata shiru ai da sa hannunta a rainin da yaran suka yi mata. Shi dai ya dubi
Mamin ya isar da sakon Abba akan ta fito su wuce asibiti sannan ya kaΙa kai ya
bar musu dakin. Mami ta mike ba ta ko biyewa maganganun Anna ba ta bar dakin.
Wannan kalma ta so da Mubarak ya furta yana yiwa Ummita ya tsayamata a Ζahon
zuci, abu ne da har abada ba za ta bari ya afku ba muddin rai.
***
A kokarin zubar da
cikin Ummita aka kusa jaza mata matsala, zubar jini sosai ta shiga yi dakyar
aka samu ya tsaya. Sai dai cikin hukuncin Allah mai kaddarawa cikin yana nan
daram bai fita ba. Haka aka shafe watanni hr biyu ana fama da abu daya amma
cikin bai ko girgiza ba wannan dalili ya sanya Abba cewa a hakura kawai amma
gudun masu shiga da fita na gidan Ummitan ta rage fitowa falon idan ya so duk
abinda take so a kai mata daki.
Ga biki ya matso amma
sun kara neman alfarma an Ιaga bisa hujjar kayan dakin da ba a kammala haΙawa
ba na Ummitan. Wannan abu mai yiwa iyayen Sahabi da shi kansa dadi ba, ga raΙe-raΙin
da aka kawowa uwar Sahabi wai Ummita na da juna biyu, ko kadan ba ta ji ta
amince da zancen ba, da hakan ne ai ta san iyayen Ummitan masu dattako ne ba za
su Ιoye musu ba. Wannan yasa inda ta ji zancen anan wurin ta bar shi kuma a
cewarta ai ciki ba ya Ιuya, idan har akwai to fa zai fito.
Mami ta yi nasarar samun wayar WIZZY. Wayarsu ta farko ya
nuna bai ma san zancen da take yi ba don gaba daya hankalinsa ba a nutse yake
ba gani yake kamar an hada baki ne don a kai musu cafka.
Sai da aka kwashi lokaci mai tsawo sannan ta kara nemansa a
waya ganin dai cikin dake tattare da Ummita ya Ζi fita uwa uba ga wani irin
kulawa da Mubarak ke yiwa Ummita wacce har gobe ba ta da walwala. Wannan abu ya
tashi hankalinta ya kuma jefa ta cikin rudani da tsoro. Ya tabbata kenan idan
ciki bai fita a cikin Ummita ba za ta iya zama rabon Ιanta nan gaba. Ta kuwa
gwammace gwara ta sanar da Wizzy cewa Ummitan na dauke da cikinsa har na
watanni hudu don su ga matakin da za a dauka a kai.
Cikin sa'a ya Ιaga wayar.
"Wai Malama ba mun gama aikin da kika sanya mu ba?
Kiran da kike yimin na mene ne bayan kin jaza mana asarar maΖudai?"
"Kaga Wizzy, kar ka yimin rashin kunyar banza da wofi!
Ni na jazamaku asara ko kuwa ku ne kuka jazamin? Da na ba ku aiki na ce ku
ketawa yarinya haddi ne? Shegen halin akuyancinku ya sanya kun afkamata yanzu
yarinya tana dauke da ciki har tsayin watanni hudu."
Wizzy ya kantamo wata ashariya ya saki.
"Ciki kuma?!! Don uwarta ita din akuya ce daga yi sau
daya sai ciki!"
Mami itama ji tayi tamkar ta sakar masa ashar, da kusa da
ita yake a yadda take ji za ta iya shaΖar wuyansa har lahira.
"Ko mece ce ni ba wannan ne ya sa nayi kiranka ba.
Mafita nake so, idan kuma babu to lallai kuΙina ya dawo. Sadik shi ne sunanka
na gaskiya, kai din haifaffen Katsina ne. Ina da kaf tarihinka na kuma san inda
zan sameka, wallahi muddin ka bani matsala sai na yi maganinka."
Shiru ya Ιan biyo baya tamkar ba zai ce komai ba don ba
karamin dauremasa baki ta yi ba, ita kuwa Mami ta san komai bisa shawarar
Hajiya Lubna, tun ma basu kai ga ba da aiki ba sai da suka sanya aka nemi
dukkan bayanan sirri na wadanda suka ba aikin sannan suka amince.
"Hajiya bai kai ga nan ba. Ni dai yanzu kudi mun ci
ubansu. Kawai dai abin da ya kamata a bar ta ta haihu, ni kuma zan zo na dauke
gudan jinina na kai garinmu."
"Me kake so ka ce?"
"Eh ina so nace maki ni Sadik Wizzy ina son abina. A
bar min ciki ta haihu na karΙi abina."
Mami ta yi shiru tana nazari. Idan har Ummita ta haihu ya
karΙi abin da ta haifa watarana asiri zai tonu, ita kuma ta rantse ta gwammace
gwara abin da za ta haifa din ya mutu da dai wannn gurguwar shawarar ta Wizzy.
"Ya ne wai kika yi shiru Hajiya? Ba ki ji nace maki ina
son abina ba? Toh ina son abina, duk wanda kuma ya yi yunkurin aika shi lahira
nima zan sanya shi dogon bacci. Ina fatan kin fahimta? Idan na karΙe abina ba
sai ta je ko uwar ina za ta je ba mu raba gari?"
Zufa sosai ya rufe Mami, gaba daya kanta ta Ζulle ta kuma
rasa mafita. Dole haka ta amsa da toh suka yi sallama.
***
*LITTAFIN NAN NA KUΖI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA
TARE DA SHIGA HAKKI BA.*
*5407827015*
*FCMB*
*Farida Abdullahi*
09034973645
Ganin lamuran bana Ζare ba ne, ya sanya a dole suka rungumi
Ζaddarar cikin Ummita. Babu yanda suka iya don a gaban idanunsu an yi dukkan
wani kokari don a zubar amma hakan bai yiwu ba. Hankalin su Abba da ma kansu su
Humaira ya Ιan kwanta ganin yadda Ummitan ta samu nutsuwa don sosai take
kokarin Ιoye nata damuwar saboda samarwa Ζ΄an uwannata nutsuwa musamman Mubarak
wanda kullum kokarinsa ya kyautata mata. Shi ne siyo banza siyo wofi, kunna
mata fina-finai a wayarsa da ma bidiyon sanya nishadi da dariya, tun ba ta
dariyar har ta zo ta Ιan soma murmushi. Ranar da abin ya ishi Mami sai da ta
tunkari Abba a siyasance tana ba shi shawarar ya dace Mubarak ya dinga fita
kasuwa kafin lokacin da zai tafi bautar Ζasa. Abban ya nuna hakan daidai ne sai
dai ya kara da fadin.
"Amma na so ace ya hakura da kasuwarnan ya
cigaba da daukewa yar uwarsa hankali ta hanyar hirar da yake taya ta. Naji dadi
kwarai da na ga murmushin fuskarta jiya, na kuma sani hakan yana da alaΖa da
shi. A duniya yanzu bani da burin da ya wuce na ganin farin cikin yarinyarnan.
Ina kuma cike da fargabar yanda yan uwan Mahaifiyarta za su karΙi batun
cikinta."
Wannan magana ta Abba ko a fuska ba ta yiwa Mami ba. Ta
fakaici idanunsa ta watsa mishi harara sai kuma da ta ga ya kalleta ta gyara
fuskar sosai kai ka ce gaba daya damuwar duniyarnan ita aka Ιorawa.
"Ni kaina hakan yana yimin dari bisa dari, sai dai kuma
hakan fa ba mai Ιorewa ba ne tunda wataran din dole ne ya wuce bautar Ζasa. A
yi hakan dai yanzu, na maka alkawarin in sha Allahu zan tsaya tsayin daka wajen
ganin ba ta faΙa cikin Ζuncin baya ba. Ga yar uwarta Humaira ma kullum tana nan
tare da ita."
Sai da ta ambaci Humaira sannan Abba ya ce.
"Af, kinga zan manta, mun yi magana da iyayen Fadeel,
mun kuma yanke nan da watanni shida zuwa sadda shi Fadeel din ya kammala gini
za a tsaida zancen aurensu."
Wani irin jiri ya nemi kwasar Mami daga zaune, ta hadiyi
miyau sannan cikin yaΖe ta ce.
"Wannan abin farin ciki ne sosai Abban yara, amma kuma
ba ka ganin kamar zai zama mun zalunci yarinyarnan? Har wannan lokacin fa
Humaira ba ta kula shi, ba ta kaunarsa."
Abba ya dan daure fuska.
"Bar ja'irar yarinya marar wayo. Ai ba ita ta haife mu
ba. Ni na gaji da wadannan mugayen dabi'unnata na korar samari da wulakantasu.
An kawomin Ζararta ya fi a Ζirga, a yan watannin nan da fitowarsu dalilin da
yasa ban tayar da maganar manemanta ba saboda halin da yar uwarta ke ciki ne,
amma ko sati ba a yi ba akwai wanda ya same ni bayan na fito daga masallaci
cewa Ιansa ya gani kuma yana so. Hakuri dai na bayar. Ni ba zan biye mata ba.
Aure ne dai sai ta yi, idan ba ta son shi Fadeel din ta zo ta kawo wani."
Tsaki Mami ta ja a Ζasan ranta, kamar ta shaΖo wuyan Abba
haka ta ji. Kamar yanda ta saba kuma sai ta shanye bacin ran, fuskarta a Ιan
daure ta ce.
"Aa fa Abban yara, nikam ba wanda zan yarda ya yiwa Ιiyata
dole. A dai bi abin a sannu. Yanzu dai ya muka kwana batun kai ta wurin mai
magani."
Girgiza kai Abban ya yi, wato dai Mami ba ta taΙa ganin
laifin Ζ΄aΖ΄anta.
"Duk sadda ku ka shirya zuwa Mamin Humaira, ni mene
nawa a ciki zan mata dole ta je ne?"
Ya fadi cikin gatse da kuma zolaya hakan sai ya ba Mamin
dariyar da bai kai ciki ba, ta Ιan dara Ιin tana mai farr da idanunta.
"Naji din, ko ma me za ka ce hakan ne kawai. Yau dai
muna da baΖi, yaran Abba zasu kawo mishi ziyara. Zuwa gobe sai muje."
Abba murmushin shima ya yi, ya gane Tasleem da Futuha take
nufi.
"Toh Allah ya kawo su lafiya."
Ta amsa da amin.
Humaira ce ta yi girkin gidan a ranar, ta dawo da aikinta
tuΖuru na shiga kicin ganin hakan yana Ιebemata dukkan damuwa sai dai kuma har
gobe masu neman ta karΙi odar su ta kasa, ko Mami ba ta sanarwa ana neman odar
abinci ba saboda a ganinta ba ta da nutsuwar da za ta yi abin da ya dace.
Bayan ta kammala komai ta zuba a kuloli, ta bar Ladidi da
gyaran kicin din ta koma nasu dakin. Kamar dama jira yake, sai ga waya ta
shigo. Koda ta duba Fadeel ne, wani irin Ιacin rai ta ji ya danne wani sashi da
ke kokarin sanyayamata rai, ta kasa fahimtar yanayin da take ji akan Fadeel
tamkar dai guda biyu ne. Farin ciki da bakin cikin da ya danne wannan farin
cikin. Babu walwala ta amsa da sallama. Shima ya amsa sallamarta.
"Ina fatan ban takuraki ba? Fatan kuna lafiya?"
Ta tsuke baki, tsiwa take son ace ta yi amma sai ta ji
tamkar wani Ιangare na zuciyarta na kwaΙarta. Ta kai duba ga Ummita da ke
kwance idanunta a kan Humairar. Sai ta ji dagaske ta kasa tsiwar a gabanta don
haka murya ciki-ciki ta amsa.
"Lafiya muke. Fatan kaima haka?"
Daga ma muryarsa za ka fahimci ya ji dadin yanda ta amsa ba
kwanaki da take balbale shi da faΙa da bakaken maganganu ba, shi kuwa bai ma
san zafi biyu ne suka hade mata a baya ba, ga na halin da cikin jikin Ummita ya
jefata, ga kuma na wani ciwon kai da bacin rai da muryarsa ke haifar mata marar
dalili.
"Lafiya kalau nake. Ina neman Ιan wata alfarma wajenki
Boddo."
Sarai ta san me yake nufi da wannan sabon sunan da ya raΙa
mata, wato kyakkyawa. Sai ta zaΙi ta basar ta hanyar fadin.
"Ina jinka."
"Zan iya shigowa mu gaisa?"
Ta Ιan yi jim, ba komai take tunawa ba sai zuwansa na karshe
a watannin baya da har Mami ta ji babu dadi. Yanzu idan ta ce ya zo kuma fa? Ta
ji wani abu na tafasa zuciyarta, bakin cikk na saukar mata da ba ta san na mene
ne ba. Wani bangare na jan ta da kokarin ta furta ya zo din, amma wani bangaren
na kwaΙarta da nuna ta tsane shi, ta tsani ganinsa to me zai zo ya yi mata?
"Toh."
Ta ji lebbanta kawai sun ba da wannan amsar. Shi kansa sai a
ya ji wani shock don bai zaci wannan amsar zai ji ba. Ya yi makamancin tambayar
ya fi a Ζirga amma kullum amsar aa, karshe ma ta kashe wayar da hujjar ya dame
ta. Ya yarda addu'a tabbas na tasiri akan Humaira, don duk sadda ya dage
iya dagewa a kan lamarinsu sai ya ga sauyi tattare da ita, ya kuma soma yarda
da hasashen Hannatu kanwarsa da kafin ta koma Yola da ta ji irin yanda Humairar
ke yi da komai ta ce ba yin kanta ba ne a nema mata magani.
"Nagode Boddo, sai na shigo."
Yana fadin haka ya katse kiran, itama Humaira ba ta ce komai
ba ta sauke wayar daga kunnenta. Ta dubi Ummita da ke kallonta cikin murmushin
da ba ta san dalili ba.
"Mene ne?"
Ta tambaya. Ummita ta girgiza kai.
"Ba komai, ina dai ganin wani abin mamaki ne a saman
fuskarki. Idan ban yi karya ba kina mutuwar son Fadeel amma na rasa meke danne
wannan son."
Humaira ta dan harareta da wasa.
"Ni ba sonsa nake ba. Mu bar zancen don Allah kafin
raina ya Ιaci."
Murmushin dai Ummita ta Ζara yi, ba ta ce komai ba ta lumshe
idanu tana ci gaba da jan carbin dake hannunta. Ita kadai ta san tunanin da
take yi, Humaira ta dube ta. Tausayinta sosai ta ji, Sahabi har ya gaji da zuwa
hira don ba fita take ba, hakanan ta daina daukar wayarsa. Kullum zancenta guda
daya ne, ba za ta yaudari Sahabi ba, ta fi kaunar ya san ita din ta haramta
aurensu koda kuwa bayan ta sauke nauyin cikin dake jikinta ne. Ba za ta aure
shi ba sam. Ba ma za ta yi auren a duniya ba kamar yanda ta ke faΙamusu a
yanzu.
Shigowar Raihana Ιakin ne da sallama ya sa Ummita bude
idanun, itama Humaira ta kauda dubanta daga gareta zuwa ga Raihanar. Wannan ne
ya katse tunanin dukkansu.
"Mami ta ce ku fito ku gaisa su Tasleem sun zo."
"To." Shi ne amsar da Humaira ta bayar ba don tana
kaunar ganinsu ba domin ta gama sanyawa a ranta su din ba masoyansu ba ne. Ba
kuma zasu kaunace su ba har gaban abada. Sai da Raihana ta kara maimaitawa
sannan Humaira ta mike, Ummita daman tuni ta yi gaba. Cikinta bai da girma bai
fito ba.
Tasleem wacce daga makaranta ta shigo gidan sanye take cikin
uniform dinta ga tirtsetsan cikinta dan watanni takwas sai faman taunar aya
take yi suna hirar makarantar da Mami, watanni shida kawai ya rage ta kammala
karatun gaba daya. Ba ta yi ko mintuna uku ba sai ga Hajiya Futuha ta shigo
tana ta faman shan Ζamshi. Tasleem ta harareta ta gefen idanu ta kauda kai tana
Ιan huci, fatar Futuha ta kara kyau kamar ka taΙa jini ya fito, kamshin
turarenta kuwa ya buΙaΙe falon gaba daya. Ζasim na rike da jakarta yana take
mata baya, babban burinsa shi dai ta ba shi na kashewa.
Yassar ya dube ta.
"Ka ga manya matar Alhaji naku daban da nasu. Irin
wannan Ζamshi haka? Gaskiya zan zo a sammin turaren."
Ta karaso ta zauna jikin Mami tana dariya.
"Har ka bani kunya Ιan uwa. Idan dai turare ne, ko
direba zan aiko ya kawomaka na siyo su kala-kala a Dubai."
Aka sa dariya Dawud na fadin.
"Inyeee! Ka ga Hajjaju mutan Dubai."
Mami dake murmushin jin alfahari ta ce.
"Ya ishe ku hakanan toh."
Tasleem dai ba ta tanka ba sai dariyar yaΖe kamar bakinta
zai rabe biyu amma Ζasan ranta ji take tamkar ta kurma ihu.
Shigowar Ummita da su Humaira ya sanya hirar ta tsagaita,
suka gaishe su, Futuha ta amsawa Humaira faram-faram don tsakani da Allah so
take ta wuce da ita gidanta ko don girki. Tana da mai aiki amma ko kusa ba ta
iya abincin da Alhaji Yakubu ke so ba kullum sai ya yi mita wannan dalilin ne
ya sanya take son tafiya da Humaira gidan koda na kwanaki ne ta nunawa yar
aikinta yanda take sarrafa tukunya.
"Humaira sannu, bayin Allah har kun dawo hayyacinku
wallahi."
Fadin Futuha, sai kuma Raihana ta sanyo wani zancen gudun
kar a tada abin da zai sosa musu inda ke ΖaiΖayi. Yassar da sun riga sun samu
labarin komai kuma har a zuci ba su yi farin cikin Ζaddarar cikin Ummita ba sai
ya sanyo hirar abinci yana kiran a kawo a ci ya kwaso yunwa daga kasuwa.
Tasleem kuwa Ζuri ta yi da idanunta akan Ummita ba ta ko Ζiftawa musamman ma da
Ummitan ta mike tsaye ta sauya wurin zama. Da ta kammala tabbatar da zarginta
sai ta ga ta nan a tsaye ta miΖe har ayar da take ci na zubewa a saman kafet.
"Kut! Me nake shirin gani Mami?"
Ta yi furucin har a sannan idanunta na kan Ummitan. Gaba
daya suka dube ta, Ummita kuwa ganin idanun Tasleem a kanta ya sanya ta Ιago me
take son fadi, wato dai itama ta gane tana da ciki don haka sai ta mike da
sauri-sauri ta shige daki saboda kukan da ya tahomata na tsantsar damuwa.
"Me aka yi kike mana ihu? Ita kuma wannan me aka yi
mata ta miΖe?"
Futuha ta jero tambayoyinta lokaci guda. Tasleem ta
cafe zancen tana kara hura hancinta da ya buΙe saboda ciki.
"Ciki na gani jikin yarinyar nan."
A razane Futuha ta buΙe idanunta ta dubi Humaira da kuma
Raihana sannan ta maido hankali ga Tasleem.
"Wa kenan?"
"Ummita mana. Mun shiga uku, shikenan yarinyarnan za ta
Ιata sunan gidanmu, image din gidanmu zai lalace a idanun duniya. Meyasa ba a
zubar da cikin ba Mami?"
Humaira wani tururi zuciyarta ke yi na Ιacin rai, wato ita
Tasleem ba ta ko tausayawa halin da Ummitan ke ciki ba balle tayata jimami.
Kamar ta tofa sa kuma albarkacin Mamin dake zaune a wurin ta ja baki ta kuma
zuba idanu ga Mamin don ganin me za ta ce. Mami kuwa ta gefen idanu ta ga irin
duban da Humaira ke mata don haka nan da nan ta daure fuska.
"Idan ita ba ta Ιata mana suna ba, ke gashinan ai kina
ihun da makwafta za su ji su fahimci halin da muke ciki! Wannan wane irin
rashin tunani kike aikata mana? Kina haukar tonawa yar uwarki asiri?"
Jin haka sai Tasleem ta koma ta zauna, ta ja guntun tsaki ba
ta ce uffan ba. Ita wannan duk bai dameta ba kamar yanda kawayenta da dangin
miji da ma abokan hulda da ake kunya za su samu labarin cikin Ummita ya zamar
musu abin habaici da zagi. Futuha kuwa, babu abin da take hangowa sai irin
yanda labarin zai karaΙe social media alhalin ta gama karaΙe ko'ina da nuna
hotunan su Ummita tana shaidawa duniya su din kannenta ne. Yanzu idan zancen
nan ya fita ai ta shiga uku.
Yassar ne ya basu labarin duk fadi tashin da aka yi don
ganin an zubar amma abu ya faskara. Tasleem ta ja tsaki karo na biyu.
"Ba dai abi
hanyar da ta dace ba. Ni wallahi da tun farko an faΙamin da kaina zan zo na yi
mata alluran da na tabbatar sai cikin ya zube. Amma yanzun ma ai ba ta Ιaci ba,
me zai hana a markaΙe shi?"
"Wai Sis Tasleem meyasa ba ki da imani ko ΖanΖani? Kina
magana babu ruwanki idan an yi ko Ummita ta mutu ta rayu."
Tasleem ta harzuΖa da zancen Raihana.
"Da wannan abin kunyar ba gwara ace ma mutuwar ta yi
ba! Ai gwara mu lulluΙe ta cikin sutura a kai ta kabarinta da dai ta haifa mana
shege."
"Sai dai ke ki mutu! Ai dama wanda bai sonka ba zai taΙa
sonka ba. Na kuma gama gasΖatawa ke din azzaluma ce da ba kya kaunar naki. Ciki
kuma Ζaddarar Ummita ce da bai wuce faΙawa kan kowa ba koda kuwa matar auren
ce. Nawa aka yi? Yanda ba kya kaunarmu har abada ba zamu taΙa kaunarki ba,
yanzun ma albarkacin masu albarkar kika ci da ban Ιaga yatsuna na watsa a saman
fuskarki ba."
Humaira ce ke wannan zantukan cikin tsananin rufewar idanu
jikinta har tsuma yake yi. Tasleem ta yi laΖwas, ina za ta mance shaΖar da ta
yiwa Anti Jannat, me ya yi mata zafi da za ta yarda ta yi katoΙarar da itama za
a shaΖe ta ga tsohon ciki. Falon gaba daya aka rasa mai tankawa Humaira, su
Yassar wadanda sun soma hankali sun ragewa zuΖatansu Ζiyayyar Humairar ba wanda
ya goyi bayan zantukan Tasleem din.
Mami kuwa kamar yanda
ta saba danne bakin cikinta da soyayyar yarannata a lokuta barkatai don siye
zuΖatan yaran wannan karon ma haka ta yi.
"Koda wasa kar na Ζara jin makamanciyar wannan magana
daga bakinki. Kina kiran mutuwa ga yar uwar da ke ganin girmanki. Ban san me
yarannan suka tare maki ba. Kina dai kan gaΙar haihuwa ki ji tsoron
Allah."
Mami na kai wa nan ta mike tana Ιata rai ta kama hannun
Humaira suka yi daki wurin Ummita. Itama Raihana ta mara musu baya.
Tasleem ta ja tsaki.
"Ni ban ga amfanin abin da Mami take yi ba. Duk
lalacewar naka, naka ne. Ta guji ranar da wadannan mutanen za su yi mata
butulci."
"Uwar biyu kenan, sai kin zauna da su sosai za ki
fahimci ba su da kowace matsala. Ni kaina a farko rashin ba Humaira dama ya
sanya ni tsanarta amma yanzu da na dan zauna na saki jiki da su na fahimci
kirkinta. Wallahi sosai na tausaya musu sadda suka yi nesa da mu, na kuma gane
ina kaunarsu a jinina, ba zan iya fasalta yanda labarin cikin nan ya jefa ni
ba. Duk da ban kai Yaya Mubarak shiga damuwa ba."
Fitowar wannan zancen daga bakin Dawud ya ba Futuha da
Tasleem mamaki, dama akwai ranar da Dawud zai fadi mai kyau akan su Humaira?
Yassar wanda shima bai jin Ζinsu ko kuma kaunarsu a zuciyarsa, dariya ya yi.
"Kai babban yaya ai ya faΙa, rannan Anna ke fesamin wai
son Ummitan yake yi. Tana ta masifa da tsinewa zancen ta ce ko bayan ranta ba
da yawunta ba."
"Wallahi ba za ta saΙu ba. Tab! Me Yaya Mubarak zai yi
da sauran Ζ΄an ta'adda?"
Futuha ta yi furucin a zafafe. Tasleem kuwa ta ma kasa cewa
komai ji take kamar abin da ke cikinta zai fito idan ta Ζara magana saboda
tsabar takaici da ya yi mata lulluΙi a Ζirji.
"To sai me? Ni wallahi don ya riga ni furtawa ne amma
na Ζudurta ni zan aure ta matukar wancan Sahabi ya guje ta."
Cewar Dawud. Kiran sallar azahar ne ya tashi mazan, Tasleem
ta dubi Futuha.
"Me kike tunani akan maganar cikin nan?"
Futuha ta yamutse fuska.
"To me zamu iya yi tunda an binne zancen ba a sanar da
mu ba sai da ya fito?"
Tasleem ta yi Ζwafa. Ta ciro wayarta ta kira Jannat ta
fesamata abin da ke afkuwa. Jannat ta feshe da muguwar dariya.
"Dakyau! Ki ce abu ya yi dadi? Toh ai wannan maganar ba
abin a Ιoye ba ne. Ke ban da abinki tunda har ya afku ai zai fito. Kawai mu
juya zancen mu yaΙa cewar dama karuwancinsu suka tafi, itama Humaira an keta
mata haddi. Idan har duniya ta yarda ta amince kinga ai shikenan? Ban da
Abbanku da DPO akwai wani da ya san an gan su kafin a kama su sun gudu?"
"Aa." Tasleem ta furta da sauri.
"Toh kinga idan ma an bada wannan hujjar zamu ce a kawo
shaida, wacce kuma babu ita ba za a same ta ba."
Shiru dai Tasleem ta yi, Futuha ta zubawa Tasleem idanu, so
take ta kammala wayar don ta labarta mata abin da Antin ta ce.
"Anti toh dan jira zan kiraki."
Daga nan suka ajiye
waya, ta labartawa Futuha yanda suka yi. Tun ma kan akai aya Futuha ta hau
girgiza kai.
"A'a, a'a, Tasleem kar ku yi haka. Nidai Futuha babu
hannuna ciki. Ba fa sunansu kadai za a Ιata ba kenan har da na gidanmu. Nikam
ba za'a yi haka da ni ba gaskiya, count me out!"
Tasleem ta harareta kawai sai ta yi shiru ba ta ce uffan ba.
Futuha ta zubamata idanu, ta san halin muguntar Tasleem, shirunta na nufin
abubuwa da dama.
"Ina fatan dai ba kina son cemin za ki haΙa kai da Anti
Jannat ku aikata wannan babban kuskuren ba?"
"Sai aka ce maki bani da hankali ko? Mtsw."
Ta ja mata tsaki ta mike ta nufi dakin Anna amma ta gama
Ζudurtawa a ranta babu fashi. Idan har Ζimar ita kanta Ζ΄ar tiktok Futuha zai taΙu
a zage ta a idanun duniya toh wannan daidai ne. Gwara ma su yi hakan kawai.
***
Mami ta taushi Ummita
dakyar ta samu ta yi shiru, ta yi musu Ζ΄ar nasiha sannan ta fito. Kai tsaye
dakinta na nufa ta dauki waya ta kira Hajiya Lubna. Komai dake afkuwa ta
zayyane mata. Ta kara da faΙin.
"Yarannan sun tada hankali lallai sai dai a zubar da
cikin Ummita, kinsan dai yadda muka yi da Sadik Wizzy. Ina tsoron su kwatanta
wani mugun abun."
"Haba Maryam, sai ka ce ba ke kika haife su ba. Ba za
ki yi musu jan ido ba? Wai ni Maryam duk ba wannan ba, ina aka kwana batun kai
Humaira wajen Babandi?"
Mami ta sauke ajiyar zuciya gami da Ζara gyara zaman wayar.
"An kashe wannan zancen, gobe zan kai ta. Na fi so a yi
a Ζare, na gaji ba zan iya ci gaba da wannan
pretending din ba. Idan an hana ta auruwa a tura ta bariki kawai mana ba
shikenan ba? Na tsani wannan Fadeel mai baΖin nacin tsiya, Babandi ya
tabbatarmin muddin dai bai fice a rayuwarta ba to lallai shi zai rusa komai.
Mun kasa jefa mata Ζiyayyarta a zuciyarsa kamar yanda ita muka jefamata,
ba na nasa kaΙai ba har na dukkanin wani
namijin da zai furta mata kalmar so. Kamar kuma yadda muka yi wa FATIMA har ya
zamo silar rabuwarta da Yusuf. A Ζarshe kuma muka zama ajalinta ta hanyar yi
mata turen aljani ya kashe ta."
Wannan zancen ne ya yi dirar mikiya a kunnuwan Futuha wacce
ta nufo Mami don sanar da ita yanda suka yi da Tasleem, ta tsaya cak a Ζofar Ιakin
cikin wani irin kakkarwar jiki da zufa.
Juyowar da Mami za ta yi ta ga mutum tsaye cak a bakin
Ζofa, ba Ζarama razana ta yi ba wannan ya sanya ta ajiye wayar cikin rawar
murya ta ce.
"Ke kuma me ya kawoki nan?"
Futuha ta karasa shigowa dakin sosai har lokacin bakinta a
hangame saboda tsananin mamakin da ya gama baibayeta.
"Mami, duk ke kika aikata waΙannan abubuwan?"
Cikin sauri Mamin ta Ζarasa ta rufe Ζofar Ιakin, ita dai
Futuha bin ta take yi da kallo har lokacin kamar a ranar ta soma ganinta a
duniya. Cikin kausasshiyar murya ta amsa.
"Eh ni ce, na aikata kuma ina kan aikatawar, ina kuma
gargadinki da babbar murya! Bar ganin kin fito daga tsatsona na rantse maki
matukar kika yi gangancin tonan asiri koda a wurin yan uwanki ne sai na manta
da ni na haifeki, zan iya daukar kowane irin mataki muddin dai buΖatana za ta
biya."
Futuha ta jinjina kai ta kasa ma cewa uffan don gani ta yi
tamkar wata Mamin ce daban a gabanta. Sai kuma ta daure ta hadiye fargabanta ta
ce.
"Mami, kenan duk wannan kauna da muke gani kamar kin fi
yiwa su Humaira a kanmu duk ba gaske ba ne? Har fa kidnapping din da aka yi
naji kin ce ke ce."
Ta juya tana wani mugun murmushi ta karasa ga madubi tana
kallon kanta.
"Wawaye, ina ku ka taΙa gani ko ji uwar da ta so Ιan
wani sama da nata? Babu ita kaf faΙin duniyarnan. Idan ma akwai toh ni Maryam
ba na cikinsu."
Sai ta Ζara sakin murmushi mai haΙe da Ζ΄ar dariya.
"Tun auren Yusuf da Fatima, nake Ζunshe da baΖin ciki a
zuciyata, kakkarfan shaidar da aka yimin a garinmu da ma makwaftan da muka
zauna da su a garin nan kafin rasuwar mahaifina na cewa ina da baΖin kishi kuma
har akan kishin ne na taΙa marin (wani Ιan uwana da mahaifina ya so na aura) a
bainar jama'a, na zazzagi uwa da ubansa kawai don ya ambatamin sunan tsohuwar
budurwarsa kuma yar uwata da aurensu bai yiwu ba yana mai yabonta a kan
idanuna. Tun daga wannan ranar ne na fasa aurensa. Ba shi kadai ba, na rabu da
mutane da dama saboda kishi, saboda tsanar da na yiwa kishiya, mahaifina ya taΙa
neman aure na wanki Ζafa har gidan da ya je nema na Ιata sunansa kuma aka fasa
auren. BaΖin shaidar da na samu sanadiyyar zazzafar kishi ya sanya da Yusuf ya
shigo rayuwata matsayin saurayin da bai taΙa aure ba, ya shiga zuciyata sosai.
Na sa a raina ba zan taΙa nunamasa zazzafar kishina ba saboda a lokacin labarin
komai da na aikata a baya ya je kunnensa ta wurin munafukai, wannan ta sanya ya
yimin gwaji kala-kala kamar ya yimin wasan yana da mata auren haΙi, yana da
budurwa da dai sauransu. Ni kuma na danne bana nuna masa Ιacin raina har sai da
ta kai ya Ζaryata zantukan mutane a kaina. Amma fa duk radda ya yimin irin
wannan idan na koma gida ranar ko tsinke ba zan Ιauke da sunan aiki ba, kuka
kuma zan yi shi. Babu wanda ya isa ya taΙa ni a ranar ya sha. Mahaifina ya rasu
dab da aurena da Yusuf. Bayan aurenmu babu irin faΙi tashin da ba mu sha ba
saboda rashin kuΙi. Soyayyar da nake yiwa Yusuf ta sanya ban taΙa gujemasa ba
daidai da kwayar zarra. Kasuwanci iri iri babu wanda bai yi ba har siyar da
kayan miya, gwanjo, da dabino. Kowanne sai an fara rimi-rimi sai lamarin ya Ιaci."
Mami ta haΙe girar sama da ta Ζasa ta juyo tana duban Futuha
dake tsaye tana sauraronta ta cigaba da magana.
"Mahaifin Ummita ya fi mijina rufin asiri sosai, shi
mutum ne mai arziΖi, matarsa duk sabgar dangin miji ta fi kowa gayu da kuma
kyauta saboda mijinta yana da kuΙi. Ba ta da taΖama balle wani abu wai shi
girman kai, wannan kyawawan Ιabi'unta da na tsana, da su ne ta siye zuΖatan
uwar mijina kafin ta rasu, ta yi bake-bake a wurin yan uwan Yusuf, ba a ganina
da mutunci sai ita. Duk yawan kirkina saboda mijina ba shi da kudi sai na zama
tamkar mujiya. Eh uwar mijina tana sona amma soyayyar da take yiwa Jamila ya
wuce gejin nawa. Saboda tsabar yanda tsanar Jamika ya rufemin idanu har gani
nake yi ba a nunawa yarana kauna a lokacin alhalin ita ko haihuwar ba ta samu
ba daga ta samu cikin sai ya Ιare. Haka na jero yara biyar Mubarak,Yassar,
Dawud, Ζassim da kuma Ke. Wannan lokacin ne kuma Yusuf ya zo min da
labarin Ζara aure bayan mutuwar mahaifiyarsa, a sannan kuma ba laifi asirinmu a
Ιan rufe yake. Yusuf har shago yake da shi a kasuwa yana siyar da kayayyakin
agogo wanda Ζaninsa Muntari ya buΙe mishi. Wannan ma ya Ζara tsananta tsanar
Jamila da Muntari a zuciyata ganin wato dai arzikinsu muke ci, da azumi haka
Muntari ke sauke mana kayan abinci, da sallah, Jamila ke zuwa ta kawomana kayan
fitar sallah wannan abu ya tsayamin a Ζahon zuci. Maijidda ita ce macen da ta
soma lura da tarin Ζiyayyar da nake yiwa yar uwarta, akwai sadda ta taΙa ganina
muraran ina yiwa Jamila barbaΙen magani a abinci wanda daga shi ne ta tsane ni
ta kuma ce Jamila ta yi hankali da ni.
Toh zuwan da Yusuf ya yi da batun Ζara aure ya yi
mugun Ιagan hankali amma damuwa ko ta Ιigo ban gwada masa ba, a farko da na Ιata
rai, sai ya rude da rarrashina, sai kawai na fashe da dariyar baΖin ciki na
nunamasa tsokana ce kawai amma nikam bani da matsala da aurensa. Da wannan ya
auro Fatima wacce ya haΙu da ita a kasuwa ta rako Dadarsu siyayyar kayan auren
dan uwanta Umar. Shikenan soyayyar ta kai su ga aure. Anna ba ta tare da ni a
sannan saboda mijina ba shi da kudi babu wurin da zamu ajiye ta, ita kanta a
sannan zagina take yi wai don me zan maΖale nace sai Yusuf da ba shi da ko
keken hawa. Nidai son da nake yi masa ya hana ni karΙar Ζorafe Ζorafenta. Ba ta
damu da zuwa gidana ba a lokacin.
Aka yi auren Fatima da Yusuf, jininta ya hadu da Jamila.
Madadin ni da muke dan shiri da Jamilar a baya, sai suka dinke da Fatima suka
zama tamkar wasu Ζawaye, a sannan ina da cikin Tasleem, na kai zuciyata nesa na
danne da taimakon shawarar sabuwar Ζawata Lubna da muka hadu a wurin wani bikin
tsohon ubangidan Yusuf na kasuwa, mijinta mai arziki ne lokacin yana rike da
matsayin Chairman. Da taimakonta na san Boka Babandi, muka niΖi Ζafa daga nan
har Katsina wajensa ba tare da sanin Yusuf ba. Na samo magungunan hana Fatima
daukar ciki muka dawo.
Cikinta na farko kuwa ya bi rariya, ni ce mai jinyarta da
nuna mata Ζololuwar kulawa. Dadarta koda ta zo ta dinga sanyamin albarka da
yabona. Yusuf kuwa tamkar ya haΙiyeni ganin a lokacin ko arba'in din Tasleem
ban yi ba na haihuwa amma ina fama da kula da Fatima, wannan dalili ya siyomin
sabuwar kauna a zuΖatan yan uwan Yusuf.
Kamar kuma a mafarki ina dauke da karamin cikin
Raihana sai ga Fatima da ciki har watanni biyar ya soma fitowa a jikinta, ba
karamin firgita nayi ba da na gani saboda ko kadan ban ga wasu alamomi ba. Kuma
na rasa yanda aka yi ko a hira ba ta sanar da ni ba. Hankalina ya yi mugun
tashi, sai da na kai zuciyata nesa sosai kafin na iya danne damuwata. Ga wani
irin soyayya da Yusuf ke nunawa Fatima har a gabana wanda nake ji kamar na
shaΖe su duk biyun na huta. Ganin haka ni da Lubna muka Ζara miΖar hanya wurin
Babandi, anan ne na je masa da buΖatar jefa tsanar Yusuf a zuciyar Fatima yanda
ko sunansa aka ambata sai ta ji haushi. Babandi ya ban tabbacin ba ma Yusuf ba,
kowane namiji sai ta tsane shi a rayuwarta muddin ya haΙa ta da wani arnen
aljani. Da wannan na tattaro duka chanjina na ajiyemasa. Muka rabu da zummar
zan ga aiki da cikawa, ya kuma ban wani hayaΖi yace duk sadda ta shiga halin
Ζunci da kuka marar iyaka na yi mata hayaΖin. Wannan zai Ζara tasirin tsanar a
zuciyarta. Da wannan muka rayu, Yusuf ya shiga tashin hankalin sauyin Fatima.
Akwai radda ta taΙa shaΖe masa wuya dakyar aka ΙamΙare ta sai da na nemi
taimako a waje, daga wannan ne kuma ya aikawa Dada saΖo ta zo takanas daga
Nijar aka tafi da Fatima saboda ta rantse muddin aka bar ta ta cigaba da rayuwa
a gidan za ta kashe shi ko kuma ta kashe kanta. Na yi kuka sosai kamar raina zai
fita a gabansu, na ce su kyale ta ayi mata magani a nan idan har larura ce,
Dada ta dinga rarrashina ta ce gwara ta tafi da ita. Daga wannan ranar ne na
rabu da Fatima, rabuwar da har gobe ba ta Ζara tako Nijeriya ba. Wannan abu ya
yimin masifar dadi, cikina nada watanni shida, Jamila ta haifi Ιiyarta mace mai
sunan mahaifiyar Jamila, Rahina suke kiranta da Ummita. Sun yi gagarumin sunan
kashe kudin da naji tamkar na dora hannu a ka nayi ihu da kuka ina ji
inama Yusuf keda kudin Muntari. Da wannan na soma tunanin duk runtsi sai
dukiyar Muntari ta zama rabon Yusuf watarana."
Mami ta numfasa ta karasa ta zauna gefen gado, ganin haka
Futuha itama ta nemi wuri ta zauna, wasu abubuwan za ta iya tunawa wasu kuwa ba
ta da wayo. Ta dai san Mubarak na yawan yabon mahaifiyar Humaira da kaunar da
ta nunamasa, yayinda su Yassar suka tsaneta saboda tsanar da ta yiwa Abbansu.
Maganar Mami ya katse tunaninta.
"Haka rayuwar ta cigaba har na kusa haihuwa, Yusuf gaba
daya ya rame ya tashi hankalinsa saboa Fatima, ya kai mata ziyara har sau biyu
daga nan ne hankalina ya yi mugun tashi, wato soyayyar da Yusuf ke yiwa Fatima
ya ninka nawa kenan? Ban yi Ζasa a gwuiwa ba, ban kuma damu da cewar tsohon
ciki gareni ba, na bi shawarar Lubna na niΖi Ζafa na koma wurin Babandi. Nan na
nemi a yimin aikin da zai sa a raba Fatima da abinda ke cikinta da duniyar ma
baki daya. Ya nunamin yanzu haka da muke magana Fatima naΖuda take yi, ya
tabbatarmin zaa turamata baΖaΖen aljanun da za su yi sanadin rayuwarta. Na yi
murna kwarai, amma abin baΖin ciki ya cemin abin da za ta haifa dole zai rayu a
doron Ζasa, nidai ban wani damu sosai ba. Koda ya gama dubansa ya ce aikin zai
yiwu haka na tattara na tafi da farin cikin Fatima za ta bar duniyar baki Ιaya.
Za ta bar mijina. Sati uku da haihuwar Fatima, labari ya zo mana na rasuwarta.
Zo ki ga kuka a wurina kamar zan shiΙe. Na nuna zan je gaisuwa, amma Yusuf ya
hana ni saboda cikina ya shiga watan haihuwa, da wannan hujjar ya tafi har ina
ce masa Ζafarsa Ζafar jaririyar Fatima ya kawomin ita zan riΖe. Wannan ya sa
Yusuf ya ji dadi sosai ya dinga yimin godiya bisa kaunarsa da nake. Har a
zuciyata addua nake kada a ba shi Humaira ya kawomin. Aikuwa haka ya dawo babu
ita ya cemin wai Dadar ta daukarwa Fatima alΖawarin kula da Humaira, ya yi
hakuri. Daga nan fa rayuwa ta dawomin sabuwa fil a gidan mijina. Daga ni sai
yarana, na haifi Raihana bayan Jamila ta haihu da kusan watanni shida, Humaira na
da watanni hudu itama lokacin. Shekaru suka tafi har aka shekara biyar, zuwa
lokacin rayuwar kunci da talaucin ya ishe ni, samun Yusuf ya ja baya sosai.
Gaba daya ya zamana hatta kudin makarantar yara daga aljihun Muntari yake fita,
wannan ya kara sanyamin Ζiyayya mai tsanani na Muntari da Jamila. Ban samu
sukuni ba har sai da na biya wasu yara suka haΙa gobarar da ba a fitar da komai
a gidan Muntari ba sai Ummita."
Idanu waje Futuha take duban Maminta wannan karon.
"Ma..ma.." Ta ma kasa magana taabar firgicin da ta
shiga da tsananin ruΙani. Tana kara tabbatar da nisan da mahaifiyarta ta yi a
fannin da suke ganin sun fi ta. Mamin ta yi yar dariyar mugunta.
"Yes, ni na sanya aka Ζona iyayenta, aka kashe
jaririyar da Jamila ta haifa da Jamilar ma. Ban san ya aka yi shegiyar yarinyar
ta tsira ba. Haka labarin gobarar ta zo mana, hankalin kowa ya tashi ciki har
da ni da na nuna ban san komai ba. Shegiya Maijidda tun a sannan ta nuna ita
wallahi ba ta amince gobarar gaske ce ta kashe Jamila ba. Ta ce a bincika amma
kowa ya yi burus da ita ga tunaninsu kawai zafin mutuwar Jamila ne saboda irin
shaΖuwar da suka yi da juna. Da nayi wani tunani akan dukiyar Muntari sai na
shawarci Yusuf akan ya Ιau riΖon Ummita kar a raba ta da dangin
mahaifinta. Nan fa ya amince, ya kuwa dage akan lallai shi sai an ba shi
Ummita. Sun so yin fada da Maijidda wacce ta dage lallai ita za ta dauketa, a
karshe dai da Kawunnansu suka sanya baki dole ta hakura ta kuma kalleni ta bini
da Allah ya isa. Na fashe da kuka ina nunawa jama'a Maijidda ta tsane ni, nan
aka hau rarrashina har yan uwan Jamila ana ganin baΖin Maijidda. Yusuf har
kusan faΙa ya yi da Maijidda a kaina dakyar dai komai ya lafa. Wannan shi ne
silar dawowar Ummita hannuna, daga baya kuma Humaira ta zo wannan kin
sani."
Futuha ta ja dogon numfashi.
"Tab! Mami kina da abubuwan mamaki sosai. Wallahi ba
don ke da bakinki kike fadamin ba, da ace a wani wurin na ji dukkan wadannan
zan Ζaryata ko waye ya faΙi."
Murmushi Mami ta yi.
"Ku ne ba ku san rayuwa ba, yanzu da ace wani mugun
halin na nuna a zahiri, kuna zaton Abbanku zamu kai yanzu da shi ba tare da mun
rabu ba? Ko kuwa kuna tsammanin a baya ida kishi ya kwashe ni na kashe
Fatima da hannuna yanzun zan cigaba da rayuwa a duniya? Ai hakan ba zai taΙa
afkuwa ba, komai Ιan hakuri ne da bi sannu-sannu. Ka yi siyasa a komai, ka
shanye komai ka danne sai ka ci riba. Ina dab da cin ribar kwace dukiyar Yusuf
saboda na faranta maku, na ba yarana maza jari su huta daga maΖon da Yusuf ke
yi musu, na kuma nunawa Anna ba Firdausi Jannat ce kaΙai Ιiya ba, nima na san
yanda zan iya kwatar kaina a wurin miji, wannan ne dalilin daya sa na sanya aka
sace yarannan, sai dai kuma kuΙaΙen su na dab da samuwa, komai ya rushe saboda
zuwan Ζ΄an sanda. Amma ban saduda ba, ban kuma karaya ba, har gobe ba zan fasa
yunΖurin Ζwatarwa yarana haΖΖi ba tunda ubansa marowaci ne mai shegen
maΖo."
Fuska a sake Futuha ta rungume Mami kafin ta saketa ta ce.
"Wai Mami ashe daman kina kaunarmu?"
Harararta ta yi.
"Wa ye ba ya kaunar nasa? Na fadamaki ai duk duniya
wanda za ki ga ya nuna ba ya son nasa ya fi kaunar wasu toh Ζarya yake yi,
munafuki ne."
Jinjina kai Futuha ta yi tana washe baki.
"Hakane, Mami na kara sonki wallahi. Kin wanke tunanin
dake zuciyata na ganin bakya kaunarmu. Ni fa lallaΙa Humaira nake yi so nake ta
zo gidana ta koyawa yar aikina girke-girke. Shiyasa kika ga ina ta janta a jiki
da kissa."
Mamin ma dariya ta ce.
"Sai ki bada himma."
Sai kuma ta daure fuska sosai.
"Ina kara jaddada maki, koda wasa kika yi yunkurin
sanar da wani ko wata labarinnan wallahi zan iya kashe ki."
Sosai furucin ya tsoratar da Futuha, ta yi saurin rike
hannunta.
"Aa Mami, wallahi na rantsemaki babu wanda zai ji. Ai
ina sonki, ba zan so hukuncin shari'a ko yaya ya hau kanki ba."
Sai anan ta saki fuska ta shafa kan Futuha. Daga haka suka
bar zancen suka koma falo inda Tasleem suke zaune da su Mubarak ana cin abinci.
Ko kallon Futuha ba ta yi ba, tsanarta take ji a zuciya, wato saboda tana da
kudi shiyasa har wani shiga daki suke su rufe su na kwasar hira ita da Mami. A
duniyarta ko a mafarki aka ce Futuha za ta samu miji wanda ya fi nata za ta
Ζaryata. Ga Hamza yanzu ya sauya mata, zamansu gaba daya babu dadi hatta a
bangarenta da uwar mijinta da ma yan uwansa. Albarkacin cikin jikinta kawai
take ci ta san da wannan. Don ma dai Anti Jannat ta ce ta kwantar da hankalinta
har ta haihu sannan su san yanda za su Ιullowa lamuran. Wannan ne kadai ya sa
ake ganinta cikin nutsuwa, kuma ita dinma ba ta ragawa Hamzan.
***
Da yammacin ranar daidai lokacin da su Futuha suka
fito da zummar tafiya gida har da Tasleem wacce za ta sauke nata gidan
sanadiyyar Hamza da ba zai samu zuwa daukarta ba, sai ko Humaira wacce a
dole ba don ranta ya so ba bisa umarnin Mami za ta bi Futuha gidanta ta yi
zaman sati biyu kawai don ta koyawa yar aikinta girke-girke, su Raihana sun yo
musu rakiya farfajiyar gidan. Humaira tana tuno Fadeel wanda ya ce yana hanya,
tana son ta dakata ta jira shi amma wata zuciyar na kwaΙarta da nuna mata babu
amfanin sauraronsa tunda ba aurensa za ta yi ba. Suna nan tsaye, tana sanye da
yadi mai taushi maroon colour wanda ya fiddo tsantsar kyawunta da hasken
fatarta, ta Ιora karamin mayafi a kanta golden colour. Babu kwalliya ko na Ιigo
a fuskarta amma kuma sosai kalar ta karΙe ta, zama wuri Ιaya babu fita ya sanya
har wani sheΖi fatarta ke yi. Daidai sadda Futuha ta bude Ζofa tana shirin
shiga, daidai lokacin maigadi ya wangalewa Fadeel Ζofa ya turo da hancin
motarsa ciki. Bisa umarnin Abba, Fadeel ya zama Ιan gida, duk sadda ya zo yana
da damar da zai yi parking a farfajiyar gidan. Ya kuma shiga idan an mishi izni
su gaisa da mutane. Shi din ne dai ya zaΙi rashin zuwan akai-akai saboda gudun
kada ya baΖantawa Humaira ta ga kamar yana neman shigarmata hanci da Ζudundune
alhalin gidansu ne.
"Wannan motar kuma fa?"
Fadin Futuha tana karewa motar kallo, lexus Ls blue black
sai sheΖi take yi, daga gani ba a moreta sosai ba don ba ta nuna alamun tsufa
ba.
"Wannan motar Fadeel ne. Na gane, ya taΙa zuwa da ita
sau Ιaya wurin Abba."
"Fadeel?" Tasleem da Futuha suka nanata sunan a
zahiri. Aikuwa kafin su rufe bakunansu haΙaΙΙen matashin nan mai sa numfashin
yan mata tsayuwa na wucin gadi ya fito daga cikinsa. Sanye yake cikin maroon
tshirt da baΖin wandon jeans kamar da hadin baki shi da masoyiyartasa. Ya rufe
idanunsa da baΖin gilashi yana wani murmushi mai ruΙar da zuΖata. Duhun kayan
da ma motar da yake jingine a jikinta sai suka kara fiddo da tsantsar farinsa
na usulin bafalutani Ιan asalin garin Yola.
Gaba daya Tasleem ta yi wani shock, suka yi mutuwar tsaye.
Idanunta har wani ruwa-ruwa yake yi saboda tsabar kallonsa da ta shagala yi ga
wani irin so da kauna dake fisgarta har ta mance da wasu igiyoyi masu Ζarfi da
suke nannaΙe da ita suka yi mata shamaki da dukkan wani Ιa namiji da ba
muharraminta ba. Shi kuwa Fadeel idanunsa a saman na Humaira har dai su Yassar
suka karaso aka yi musabaha.
Humaira kuwa ta yi wani irin dauke kai daga kallo daya ba ta
Ζara ba.
"Wajenki ya zo ne?" Futuha ta wurga mata tambayar
tana Ιan murmushin yaΖe, a ranta kuwa jinjinawa Mami ta yi, tabbas ba karamin
kokari tayi wurin danne abin da ke Ζasan ranta ba, akwai masifar wahala. Sosai
itama ta ji kishin ace Humaira ce ta samu wannan kyakkyawan matashin kuma mai
rufin asiri.
"Ban sani ba." Amsar da Humaira ta bayar kenan
tana Ζara tamke fuska. Tasleem kamar ta shaΖe ta, yarinyar ta samu dama amma
tana nuna girman kai. Ita da ace itace da wannan damar ai sai inda Ζarfinta ya
Ζare.
"Assalamu alaikum."
Sallamarsa ta katse musu tunani, Raihana ta jingina jikin
Humaira dab da kunnenta ta ce.
"Ki riΖe wannan bawan Allahn sosai idan kuwa ba haka ba
ni zan maye gurbinki."
Ba ta san ya aka yi ba sai tsintar idanwanta ta yi da
wurgawa Raihana wata muguwar harara mai nuni da tsantsar kishi, Raihana ta sa
dariya tana riΖe kunnuwa gami da Ιan jujjuya kai alamun ta tuba. Tana kuma kara
gasΖatawa Humaira na son Fadeel, ba kuma ta san abin da ya danne wannan
soyayyar ba.
Tasleem ta amsa
sallamarsa ciki ciki yayinda Futuha ta saki fuska sosai aka gaisa sannan ya
dubi Humaira da shanyayyun idanunsa bayan ya cire gilashin.
"Boddo, barka da yamma."
Ya fadi yana mai Ιan dunΖule hannu da Ιan ranΖwafar da kai
kaΙan tamkar wani basarake. Nan fa gaba Ιaya idanun ya koma kansu ana ganin
ikon Allah.
*LITTAFIN NAN NA KUΖI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA
TARE DA SHIGA HAKKI BA.*
*5407827015*
*FCMB*
*Farida Abdullahi*
09034973645
Ba ta ce uffan ba sai idanuwanta da ta sauke a cikin nasa.
Ya ji kallon har a Ζasan ransa.
"Sauri fa muke yi." Tasleem ta furta cikin Ιaure
fuska, gaba Ιaya wani irin mugun kishi ke cin zuciyarta. Fadeel bai ko kalle ta
ba ya dubi Futuha.
"My sis, ko za ki ban aron Ζanwartaki for just
5mins?"
Murmushin da bai kai zuci ba Futuha ta yi.
"Ba ka da damuwa. Humaira jeki."
Humaira da ke jin kamar ta shaΖo wuyan Fadeel amma sai ta
kasa yi mishi musu ta bi bayansa sadda ya yi gaba zuwa inda ya ajiye motarsa. A
jikin motar suka tsaya su na hangen su Futuha da ke hira sai ko Tasleem da ta
zubamusu idanu tamkar makauniyar da ta samu ido.
"Ka kirani kuma sauri muke za mu tafi."
Ya ji babu dadi daga yanayin muryar da ta yi mishi magana,
ya dai daure ya haΙiye kamar koyaushe.
"Humaira kina addu'a sosai kuwa? Kina nafilfiloli da
sallar dare? Kina mayar da hankali wajen yawan karatun Alkur'ani?"
Ta yi shiru kamar ruwa ya cinye ta, ta sani tana sallolinta
biyar akan lokaci, tana kuma addu'a daidai gwargwadon yinta, amma yawan karatun
Alkur'ani da kuma sallolin dare da ma nafila ba za ta iya buΙe baki ta ce mishi
aa a kansu ba, kawai sai ta ji hakan ya yi mata nauyi a saman harshenta.
Ya tsinci amsoshin tambayarsa daga shirunta, don haka ya cigaba da magana a nutse ba tare da ya
dauke idanu daga saman fuskarta ba.
"Salollin farillah wajibi ne Humaira, amma su Nafiloli
neman Ζarin lada ne da kusanci ga Ubangiji. Za su buΙemaki Ζofofin rahma
wadanda ba ki taΙa zato ba. Hakanan shi kansa karatun Alkur'ani, yawan
tilawarsa da yin azkar safe da yamma zai ba ki kariya daga shaiΙanu da ma
jinnu. Babu wani ko wata ko kuma wani abun da zai cutar da ke. Ina roΖonki ki
yawaita addu'a, ina kuma ba ki shawarar yawan hailala, istigfari da salatin
Annabinmu s.a.w. Ki Ιauka tamkar wani Ιan uwa ne gareki na jini yake ba ki
wannan shawarar. Kin yarda kin amince za ki amfani da ita?"
Ba ta taΙa jin wani irin sanyi da nutsuwa tattare da
kasancewarta da Fadeel ba sai a yau kuma a yanzun da yake kwararo mata waΙannan
shawarwarin. Sai gaba daya ya tuno mata da Kawunta da ma Dada, ta tuna da kalar
rayuwarta a Nijar, koda wasa idan ta idar da sallah, Dada ba ta barinta ta bar
saman darduma sai ta yi nafila ta kuma tsaya ta ga ba ta yi wasa da addu'a ba,
hakanan tilawar Alkur'ani, duk juma'a Kawunsu na tattara su har yaransa su yi
tilawa, kowacce ta biya inda ta iya. ShaiΙan kwarai ya yi tasiri a zuciyarta da
har ya sanya ta yi watsi da dukkan wannan, ta zama daga ta idar da sallar asuba
sai bacci ba kamar a farkon zuwanta Kano ba da ma rayuwarta a Nijar inda koda
wasa ba ta isa ta koma shimfaΙarta ba har sai rana ta fito bisa koyarwar Dada.
A farko tana yi daga baya duk ta watsar. Ummita duk ta fi wannan kokarin. Ita
kuwa kasala ya mata yawa.
"Kinji? Please."
Ya kara nanatawa. Ta dube shi sai ta yi murmushin da rabon
da ya gan shi saman fuskarta har ya mance. Ta gyada mishi kai.
"Naji, nagode sosai da tunatarwa kuma zan kiyaye in sha
Allah."
Ai sai ya ji tamkar an jefa shi wata duniyar ta nishadi da
farin ciki, sai kawai ya rasa me zai ce ban da leΙe da ya Ιan lasa yana maida
mata martanin murmushin. Ζarar hon da aka danna da Ζarfi ya sanya suka dubi
wajen, har ga Allah shi Fadeel ya ma mance adadin mintocin da aka yi mishi
alfarmarsa, balle kuma Humaira da ta lula tunanin sakancin da take yi da addu'a
tun zuwanta garin. Tasleem ce da wannan aikin ranta a mugun Ιace.
"Nagode, kije suna jiranki. Sai mun yi waya ko?"
Ta ji tamkar ta ce eh, sai kuma ta fasa ta juya kawai ta
kama tafiya, ya bita da kallo sai kuma ya buΙe motarsa ya shiga, ya sani Abba
ba ya nan balle ya shiga su gaisa. Don haka ya yi ribas aka buΙe gate ya fice.
Itama tana shiga gaban motar kusa da direba, direban ya ja suna Ιagawa juna
hannu ita da Raihana.
Tasleem da Futuha a bayan motar zaune sai yare suke yi. Ita
kuwa duk ta tsargu amma ta haΙiye Ιacin ranta.
Tasleem ke mitar dole ne ma Humaira ta rabu da Fadeel tunda
har ita ba ta same shi ba to kowa ma ya rasa. Yayinda Futuha ta ce ta kwantar
da hankalinta soyayyar babu inda za ta kai. Haka suka yi ta gulmar Humaira ba
tare da ta tsinci ko harafi ba. Ba ta da haΙi da buzaye balle ta fahimci akan
abin da suke tattaunawarsu.
Har aka sauke Tasleem, ba ta da walwala, ganin haka itama
Humaira ta ja jikinta ko ki gaida gida ba ta ce mata ba.
A gidan Futuha, Ιakin dai da ta taΙa sauka wannan karon ma
shi ne ya kasance masaukinta. Ta ajiye jakar kayanta ta faΙa ta Ιauro alwala
ganin ana dab da kiran sallar magriba, sai a lokacin ta jawo waya ta kira yar
uwarta Ummita. Suka Ιan taΙa hira don ta Ζara kwantar mata da hankali, cikin
ikon Allah ma sai ta ga ko a muryarta babu wata damuwa. Koda ta ajiye ta kara
tsunduma da tunanin Fadeel, wai me ya yi mata ne ma da har ta tsaneshi hakan?
Oho, ta ba kanta amsa, sai kuma ta ja tsaki cikin jin zafin rai, to meye nata
ma na tsayawa tunaninsa? Don haka sai ta miΖe ta shimfiΙa darduma jin an soma
kiraye-kirayen sallah. Koda ta idar sai da ta yi nafila sannan ta yi salati da
istigfari. A karshe ta yi addu'a sosai. Sai kuma ta tsinci zuciyarta da yin
wani sanyi tamkar an yayemata wata damuwar. Sabuwar wayarta Ζirar Huawei da Abba
ya damΖa musu bayan fitowarsu daga hannun Ζ΄an ta'adda ta yi Ζara sauti mai dadi
shaidar shigowar saΖo. Ta Ιauka ta duba.
*_Babu wata damuwa ko baΖin ciki da Allah ba zai iya
magancewa Ιan adam ita ba. Ki miΖa dukkan lamuranki gareshi, ki kusanceshi, zai
kusanceki. Allah yana son masu ambatonsa safe, rana da kuma dare. Ina miki
fatan alheri koyaushe._*
Ta karanta fiye da sau uku, ya yi mata dadi sosai, ta kuma
kasa barin murmushi. Fadeel ne, koda babu suna a lambar tana da haddarta saboda
kira na yau da gobe da yake yi kuma duk da ita ne. Ta sauke ajiyar zuciya,
kwankwasa Ζofar da Futuha ta yi da shigowarta da sallama ya sanya ta ajiye
wayar ta dube ta. Murmushi Futuha ta yi mata.
"Yauwa Humaira idan kin huta ki fito ki Ιebi abinci a
kicin. Daga gobe za ki soma gwadawa Hafsatu yanda kike tsara abinci da komai,
yau kinga sai ki huta ko? Ni zan shiga ciki ba lallai kuma mu haΙu ba sai da
safe."
Ita dai ta amsa da toh kawai, bayan fitar Futuhar ta girgiza
kai. Mamakin wannan rayuwa ta yaran Mami take, tabbas albasa ba ta yi halin
ruwa ba, da ace sun biyo Mami hatta da girkin ba su da matsalarsa. Ta rasa
menene ribar Ιiya mace idan ta zauna har ta yi aure ba ta iya girki ba. Banda
shiriritar Futuha, ta gwammace a koyawa Hafsatu girki ta cigaba da yi mata
bauta ita kuwa ta zauna ta miΖe Ζafa. A
Ζarshe dai ta watsar da tunane-tunanen da ta tabbatar ba za su yi mata wani
amfani ba ta cigaba da ambaton sunayen Allah har aka kira sallar isha'i ta
gabatar ta kuma haΙa da nafila ta yi addu'a anan ma sannan ta ninke dardumar ta
fita, abincin sam bai yi mata ba. Shinkafa ce dafaduka ta dai ji kaji wadanda
daga ka kai saman hancinka sai Ζarni ya bugeka, da sauri ta mayar ta ajiye.
Sanin da ta yi idan ta zauna sai ta kwana da yunwa ne ya sanya ta daukar
indomie kanana biyu ta dafa ta ci ta sha ruwa.
Saita alarm ta yi ya
tashe ta karfe uku, dakyar ta tashi saboda ba ta saba ba ga bacci dake neman
fin Ζarfinta, sai da har uku da rabi ta buga sannan ta iya miΖewa firgigit tana
ambaton sunan Allah. Hakan ya ba ta wani Ζarfi ta kuwa Ιauro alwala ta dawo ta
yi nafiloli ta karanta alΖur'ani bacci na Ιaukarta, dakyar ta daure ta yi
sallar asuba sannan ta kwanta anan bacci mai karfi ya kwashe ta.
Sai wuraren takwas
na safe ta tashi ta yi wanka ta shirya tsaf ta dora hijabinta ta nufi kicin. Ta
sani mutanen gidan ba sa tashi da wuri, maigidan kansa sai ya kai goma bai fita
ba. A kicin ta tarar da Hafsatu na zaman jiranta har ta yi gyara ta wanke
kwanuka. Suka gaisa fuska a sake, nan suka shiga haΙa kayan kari, kasancewarta
babbar mace kuma mai basira tana hankalta kwarai da yanda Humaira ke sarrafa
girkinta. Suyar dankali da agada suka yi sai ko sauce da ta haΙa, sai ruwan
shayi da ya ji citta da kanumfari. Sai ko farfesun nama da ta yi da ya ji kayan
lambu. Kicin din ban da Ζamshi ba abinda ke tashi, komai ta yi daidai gwargwado
yanda ta tabbatar ba za'a yi almubazzarancinsa ba. Hafsatu ta fita da shi zuwa
dinningtable na Futuha, ita kuwa Humaira bayan ta zuba wa Hafsatu ta Ιebi nata
ta yi Ιaki don ba za ta iya jurar har sai su Futuha sun tashi ta karya ba
saboda yunwar da ya addabe ta, a ranar kuma ta tashi da wani irin karfin jiki
da walwala. Ta Ζara gasΖata cewar Fadeel, babu abin da ibada ba ta Ιaukewa na
daga damuwa da ma Ζuncin zuciya. Hamdala kawai ta ke yi bisa yanayin da ta
tsinci kanta a ciki.
***
A Ιangaren Fadeel
kuwa, sosai suke shirin bikin Ibb da Dakta Salma wanda bai fi sati ya rage a yi
ba. Abokansu duk wanda ya ji zancen auren Ibb sai ya tambaya ko an yi na
Fadeel? Amsar dai bai wuce nan kusa shima zai yi ba. Kamar koyaushe a kwanakin
nan, yau ma su na tare bayan ya raka Ibb wurin Dakta Salma jin tsarin events
din da za ta gudanar, Ibb sai faman mita yake yi mishi akan kawai ya kai kudi a
sanya aurensu lokaci guda shi kuwa murmushi kawai ya ke yi. Girgiza kai Ibb ya
yi.
"Fadeel na sanka, kana da ΖoΖari sosai gun Ιoye damuwa,
ba ka fiye son Ιorawa mutane nauyin damuwarka ba, amma ba yanda ka iya, mun
taso tare kuma kai Ιin aminina ne dan uwana na maka sanin da wani mafi kusa da
kai Ιin bai yi ba. Yanzu a ture zancen wasa, please and please ka yi abin da
muke da tabbacin yiwuwarsa, idan yin a yi, idan barin a bari."
TuΖi yake yi amma sai da ya Ιan juyo ya dube shi.
"Ban fahimceka ba. Me za a bari?"
Ibb ya kauda fuska yana Ιan shan Ζamshi.
"Auren mana, ko dole ne sai ita? Lamarinta ya fara kai
ni bango, ita ba Ζ΄ar kowa ba a Ζasarnan sai ji da kai da taΖama. Matan da suka
fi ta sun nuna su na yi da kai sun kuma nuna sun ji sun gani kowane yanayi ma a
tafi da su amma ka nace mata, ka maΖale sai ita. Haba Fadeel, yaushe duk wannan
zai wuce? Har yanzu kana da hope din cewa za ta amince da aurenka da
bakinta?"
Fadeel bai ce komai ba, amma zuciyarsa zafi take. A duniya
bai taΙa yin so ba sai akan Humaira, kuma da son ya tashi kama shi, sai ya yi
mishi wani irin kamun dabaibayi wanda ko ya Ζi ko ya so, hakanan zai rayu da
shi. Bai dai san abin da gaba za ta haifar ba.
"Ban iya Ζiyayya ba, kamar yanda ban iya soyayya ba ka
san da haka ko? Meyasa ka ke tunanin akwai ranar da zan iya haΖura da Humaira
alhalin ba ta yimin laifin da zan Ζi ta ba har yau? Ko ka yi zaton ta taΙa
wulaΖantani ko zagina? Toh Humaira ba ni ta wulaΖanta ba, soyayyar da na furta
ina yi mata ta wulaΖanta, amma na yi mata uzurin kasancewarta daga jinsin Dan
Adam wanda muka riga muka san ajizancinsa. Ka yi hakuri, na sani kana jin babu
dadi yadda ake maka Ζorafi akan aurena har da masu nemana da sharri. Please ina
son ka toshe kunnuwanka daga garesu. Duk radda ni Fadeel na furta maka cewa na
bar Humaira, toh ka sani ina nufin rabuwa ta har abada, amma yanzu bana jin ko ΙurΙushin
hakan a zuciyata. Ba na jin kuma wannan mafarki naka mai tabbatuwa ne saboda ba
ta yimin kamun wasa ba. Ka bi wannan Ιan uwannaka da addu'a Ya Sheikh, komai
zai zamo tarihi fa in sha Allahu."
Harara Ibb ya wurga masa jin ya ambace shi da sunan zolaya,
Fadeel kuwa murmushi ya yi mishi yana Ζara yi mishi kirari da Angon Salma. Nan
kuma ya saki fuska aka bar maganar gaba Ιaya.
***
Cikin hukuncin Allah,
a kwana a tashi har tsawon lokacin da su Abba suka Ζara roΖar alfarma a yi
bikin Ummita da Sahabi ya kusa cika, a sannan Humaira ta tattara ta bar gidan
Futuha adalilin mijin Futuhar da ko kallo suke sai ya dinga kiran Humaira wai
ta fito su yi kar ta Ζumshe a Ιaka. Ko kuma ya yi ta santin girki yana fadin ai
kaf gidan su Futuha ta fi su iya girki, Futuha tun tana yaΖe har ta zo ta kasa
jure Ιacin ranta ganin tashi guda ya siyo wani rantsetsen leshi dan dubu
arba'in ya kawo wa Humaira matsayin ladan girki da take yi musu. Anan ne gaba
daya ta sauya fuskarta ta ce Humaira ta tattara ta koma gida, ta sa direba ya
kai ta bayan ta karΙe leshin. Ba tare da sanin cewa ita Humaira hakan ya fiye
mata komai dadi ba don dama ta gaji da zaman gidan, dadinta daya bai wuce na
ibadar da take yawan yi yanzu ba sosai, kuma abin mamaki koda Fadeel ya kira ta
ta rage jin wannan tsanar da Ιacin ran sai dai ba yabo ba fallasa.
Tashin hankalin daake
gudu dai shi ne ya afku, Abba ya zaunar da Sahabi da wani Kawunsa a dakin baΖi
ya sanar da su abin da ke faruwa. Sahabi da yake jin wai wai a gari bai yarda
ba ji ya yi har wani jiri na neman kwashe shi daga zaune. Kawunsa kuwa ya
jinjina lamarin, ya kuma yi addu'ar Allah ya sauki Ummitan lafiya a karshe ya
ce idan ta haihu ta yi aure ban da Sahabi don tuni dama sun yi mishi mata ganin
ana ta yawo da hankalinsu akan Ummita. Sahabi ya kasa cewa uffan, idanunsa sun
kaΙa. Tsakani da Allah yake son Ummita, ya kuma so aurenta, amma bisa gargadi
iyayensa ga Kawu, matukar idan sun je ta tabbata ciki ne a jikin Ummita toh
lallai su faΙi hakan. Sun kuma yi barazanar saΙawa Sahabi muddin ya musa
zancen. Da wannan aka Ζulle mishi baki ya kasa cewa komai. Sai ma da zai tafi
ne ya roΖi arziΖin ganin Ummita, nan Abba ya ba shi hakuri gami da nunamasa ba
za ta iya jure ganinsa ba. Ya yi hakuri dai ya bi umarnin iyayensa. Daga wannan
Sahabi ya ja jikinsa suka bar gidan bayan Abba ya damΖa musu dukkan wani abu da
suka kawo da sunan aure.
Ummita na Ιaki ban da
kuka babu abin da take yi, Humaira wannan karon ta ma kasa rarrashinta, ga ciki
ya fito ras ana gani kasancewar bai fi watanni biyu ya yi mata saura ta haihu
ba. Ta shiga watanni bakwai cif. Ita kanta Humairar hawayen take yi tana
gogewa. Ta dai tabbata shikenan Sahabi ya rabu da Ummita duk kuwa da irin dogon
wayar da suke yi da soyayyar da suke nunawa juna.
"Kaddararki ce
Ummita, kiyi hakuri mu rungumeta da hannu bibbiyu. Watarana komai zai zama
tarihi."
Ta girgiza kai.
"Humaira na sani Ζaddarata ce, amma wallahi Humaira na
tsani cikin jikina da abin da ke cikin. Ba zan taΙa sonsa ba. Humaira duk sadda
cikina ya yi motsi ji nake kamar na Ιauki wuΖa na caka a cikin abin da ke cikin
ya mutu gaba daya koda ace nima nawa ajalin kenan. Allah ya isa, Humaira ba zan
taΙa yafewa azzaluman nan ba. Har gobe mummunan fuskokinsu na nan a
kwakwalwata, wallahi yau idan Allah zai nunamin su, sai na raba su da
numfashinsu."
Hawaye sosai itama Humaira take yi, balle kuma Raihana wacce
shigowarta kenan dakin sanye da Uniform ta dawo daga makaranta ta tsinci
labarin fasa auren Sahabi da Ummita kwata kwata a bakin Mami, kuka sosai take
yi sanin irin kaunar da suke yiwa juna. Ta karaso ta rungume kafadar Ummita
tana kuka tamkar ranta zai fita ta ma kasa magana. Sai Humaira ke aikin
rarrashinsu cikin Ζarfin hali duk da itama hawayen ne ke zubomata.
"Humaira!
Raihana!! Kuna ina?!"
Jin muryar Mubarak yana kiran sunansu murya a sama ya sanya
su duban juna kafin su fito zuwa falon gaba daya ban da Ummita da ko motsi ta
kasa. Kirjinta ne kawai ke dukan tara-tara, zai wahala ta yi mafarki bai afku
ba, tana tsoron kuma yanzun ace mafarkin nata ne ya tabbata. Sai ta hau ambaton
Innalillahi a Ζasan ranta.
Ba Mubarak ne kaΙai a falon ba, har da Mami da Abba wanda
bai je kasuwa ba saboda lamarin fasa auren Ummita sosai ya taΙa ransa, dama
kuma ya san da zuwan ranar, amma babu yanda iya.
"Kai Mubarak, mene ne haka kake ihu a gida?"
Mubarak da idanunsa suka kaΙa gaba daya ba cikin nutsuwarsa
yake ba, daga shi sai singilet da wando three quarter, fuskarsa ta yi jazur
abinka da farin mutum. Waya kawai ya miΖawa Abba, Mami da su Humaira har su na
rige rigen zuwa leΖa saman wayar. Rubutu ne a ka yi dogo, headline din rubutun
mai jan hankali sai ko rubutun.
GASKIYA TA YI HALINTA...
Rahina Sani da
Humaira Yusuf wadanda kwanakin baya ake tunanin sace su aka yi, a yanzu gaskiya
ta yi halinta. Yan matan sun bi samarinsu ne yawon sharholiya inda a karshe har
Ιaya ta zubar da cikin da ta yi yayinda Ιayar kuwa Allah ya tona asirinta cikin
ya Ζi zubewa tana nan yanzu haihuwa yau ko gobe. Bincikenmu ya tabbatar da cewa
ba sace su aka yi ba, dama Ζ΄an hannu ne suka bi abokan watsewarsu ganin
asirinsu zai tonu ne ya yi sanadin da suka haΙa baki suka yi Ζaryar an sace su.
Tabbas inda ranka ka sha kallo da mamaki!
Sakin wayar Abba ya yi har yana taga-taga zai fadi, da
taimakon su Mami dake kusa da shi ya samu ya zauna a kujera mafi kusa saboda
rawar jiki. Humaira kuwa zuciyarta ke wani irin tafarfasa ranta idan ya yi dubu
ya Ιaci, waye wannan ke kokarin Ιata musu suna a idon duniya? Mene ne ribarsa?
"Wannan wace irin rayuwa ce? Daga wannan sai wannan?
Waye da wannan aikin? Kai Mubarak a ina ka samo mummunan labari haka?"
Duka wannan zantukan Abba ke yinsu lokaci guda cikin rawar
murya mai nuni da zallar Ιacin rai. Mubarak da ya dauki wayarsa ya amsa.
"Abba ina zaune naga an turo group din da nake har da
masu bibiyata ta inbox su na tambayar ko dagaske ne. Da na duba naga an yi
forwarding sama da sau hamsin. Wannan ya sa na fahimci koda ace ba a jima da
baza labarin ba, toh ya samu karΙuwa ainun."
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! A duniya ba ka
sanin cewa kana da maΖiya sai irin hakan ta kasance. Ina so maganar nan ta
tsaya iya mu da wadanda suka sani a gidan, koda wasa kar a faΙawa yarinyarnan
ko don yanayin da take ciki. Mu rufe duk wata Ζofa da za ta tsinci labarin. A
karΙe wayarta, ku kuma ku kiyayi tayar da zancen a gabanta. Ni kuma in sha
Allahu sai inda Ζarfina ya Ζare wajen ganin an bi maku hakkinku, koda ace abin
da na mallaka zai Ζare sai na sanya an bincikomin me wannan aika-aikar an
hukuntashi ya kuma faΙi dalilinsa na aikata wannan abu."
Kowa a wurin ya gamsu da batun Abban, Mami kuwa tunani kawai
take yi na waye wannan da ya fi ta nuna Ζiyayya ga yaran? Fatanta kar ya
kasance wacce take zargi. Ta sani tunda har Abba ya ci akwashin Ιaukar mataki
akan al'amarin to fa babu fashi.
Da wannan aka kashe zancen amma fa ran kowa a Ιace, koda su
Humaira suka koma Ιaki, sun tarar Ummita ta shiga bandaki wannan ya sanya da
sauri ta Ιauke wayarta ta kashe ta jefa a sif, da Ummitan ta fito ma babu wani
a cikinsu da ya nuna mata komai. Ita Ιin ma ba ta lura da yanayinsu ba balle ta
mayar da hankali, damuwar rashin Sahabi ya rinjayi komai. Tana buΖatar ganin ta
samu nutsuwa ko ya ya ne, tana tsoron ciwon da damuwa za ta haifar mata. Wannan
dalilin ne ya sanya ta jin tsoron tambayarsu dalilin kiran da Mubarak din ya yi
musu, sai ta zaΙi yin shiru gami da kwanciya ta hau jan carbi.
***
Wasa-wasa sai ga zance ya yaΙu a duniya. Abinka da soshal
midiya masu jran Ζiris sai ga labari salo-salo ana juyawa har da masu fitowa su
na Ζara nasu gishirin su na Ζara yaΙawa. Abin mamaki da tsoron shi ne har
asalin su Humaira da Ummita na kasancewarsu yaran riΖo a gidan da suke haka aka
dinga yaΙawa ana faΙin watakila musguna musu ake yi ya yi sanadin shigarsu
karuwanci yayinda a wani gefen wasu ke cewa mai yiwuwa son duniya ne ya kai su
ga faΙawa halin da suka tsinci kansu. Har da kuma wadanda suka ce koda ace ba
karuwancin suka fita da zummar yi ba, zai iya yiwuwa sun yi ne domin su samu
maΖudan kuΙaΙe amm a Ζarshe abokan ta'addar nasu suka cutar da su ta hanyar yi
musu fyaΙe. Labaru dai iri-iri akan bayin Allahn nan biyu Humaira da Ummita
babu irin wanda bai yaΙu ba. Mafi rinjaye sun fi aminta da cewar da haΙin
bakinsu aka sace su hakan ta kasance. Ζalilan ne masu tsoron Allah wadanda ba
su yarda da wannan labaran Ζanzon kurege da ake ta fafutukar yaΙawa ba.
Tsintar wannan labari a wurin dangin Ummita da ma
Humaira sam bai zo musu ta daΙi ba. Hankali tashe Anti Maijidda ta diro Kano,
ko kaΙan ba su da labarin wai Ummita na da ciki, a hakan ma ba ta amince ba sai
da ta zo don kanta ta ga Ummita da tulelan ciki, wannan baΖin ciki yasa har
suma ta yi ta kuma tiΖe lallai sai dai Abba ya ba ta Ummita su tafi. Mami kuwa
tashin hankalinta bai wuce na wayar da Wizzy ya Ζara yi mata bayan bayyanar
labarun da ake ta yayatawa ba akan lallai Ummita na haihuwa ta ba shi Ιansa
yana so zai kai wa gyatumarsa idan kuwa ta saΙa zai iya tona asirinta. Wannan
dalilin ne yasa itama ta kafe akan Ummita ba za ta tafi ba.
Anti Maijidda ta fusata ainun ta dubi Mami da hawaye
jage-jage saman fuskarta tana kai nunata da yatsa.
"Ke Maryam! Ni ba sakara ba ce ki dube ni dakyau! Idan
idanun kowa ya rufe ba a ganin aibunki ni kuwa Maijidda ko ruwan teku za ki
shiga ki wanke jikinki ki fito ba za ki taΙa sauyawa daga yanda nake kallonki
ba. Don haka tun wuri ki fita idanuna na runtse, idan kuma ke kika yi naΖudar
Ummita a yau sai ki hana ni tafiya da ita mu gani!"
Jin haka sai kawai Mami ta sa kuka sosai, Abba ransa ya Ιaci
yayinda Ummita ta kwantar da kai a kafaΙar Humaira tana nata kukan.
"Hajiya Maijidda ina ganin Ζimarki kuma albarkacin
Jamila da abin da ta haifa ya sa ban taΙa Ιaga idanu na faΙamaki maganganu ba.
Ko ba komai kina ganina da wannan girman, amma fa ba zai yiwu ace koyaushe ki
zauna kina kushe Maryama ba. Haba, duk ΖoΖarin da take yi akan Ummita bakya
gani? Meyasa kike nema ki yanke zumuncin da ke tsakanina da Ιiyar Ιan uwana? Ke
a ganinki idan ace yau Maryama na cutar da ita zan zuba idanu ne nayi shiru? Ni
ga sakarai?"
Mami ta Ιan dube shi ta gefen idanu kawai, yayinda Maijidda
ta ji zafin maganganunsa.
"Alhaji Yusuf, na ji Maryam ba ta cutar da Ummita, amma
yau idan har ni na isa da Ummita matsayin yaya ga mahaifiyarta ina neman
alfarma a wurinka ka bar ni na tafi da ita Bichi. Ka ga dai yadda abubuwa suka
rincaΙe, sunanmu gaba daya ya gama Ιaci, ba naku ba, ba kuma ga namu ba Ζ΄an
uwan mahaifiyarta. Don haka ina roΖon arziki ka bar ni na wuce da
ita."
Ummita ko kusa ba ta gane Ιacin sunan da Antinta ke magana a
kai ba, sai ta yi tunanin ko don cikin dake jikinta ne kuma ga shi nan an soma
sani a gari. Abba kuwa, ya yi shiru yana nazarin maganganunta, da alama sun yi
tasiri a zuciyarsa. Ganin haka da sauri Mami ta dube shi.
"Yau kenan kana ΖoΖari ka nuna ba ni na haifi Ummita
ba? Kokari ka ke yi ka sallamawa Maijidda Ummita ta wuce da ita ko? Kana son
nunamin ba ni na haifeta ba, ashe Raihana idan ace ita hakan ya faru a kanta ba
zamu yi hakurin duk abin da zai je ya zo ba mu bar ta karkashin kulawarmu ba?
Lallai ka sani Yusuf, a yau idan ka amince da dauke Ummita daga hannuna toh ka
sani cewa ta tafi kenan har abada ba za ta dawo wurina ba. Na kuma gode da
nunamin iyakata da ku ka yi."
Tana kai wanan ta juya ta soma tafiya cikin zubar hawaye,
wannan ya tashi hankalin Abba da ma su Ummitan. Abban na kiran sunanta ta
yi banza da shi, ita dai Anti Maijidda na tsaye riΖe da hannuwa a kirji tana
kallon irin salon makirci na Mami mai ban mamaki. Ummita cikin sauri ta miΖe ta
riΖo hannun Mami tana kuka kamar ranta zai fita lokaci guda tana girgiza
kai amma kalma Ιaya ta kasa fita daga bakinta. Mami ta dube ta cikin hawayen
sai kuma ta shafi gefen fuskarta ta yi murmushin yaudara. Cikin karyar da murya
ta ce.
"Kar ki damu Ummita. Da nan din da can duk Ιaya
ne."
Sai a sannan Ummitan ta magantu.
"Aa Mami, kiyi hakuri. Wallahi babu inda zan je, ke din
tamkar uwa kike a gareni. Idan har a duniya za iya barin mahaifiyata toh kuwa
zan iya rabuwa da ke. Kin rungumeni a sadda na buΙi idanuna babu iyaye, kin
maida ni tamkar Ιiyar cikinki, kin kaunace ni ta kowace fuska. Ni kuwa me zai
sa na zama mai butulci a gareki? Kiyi hakuri da kalaman Anti Maijidda, ta yi su
ne saboda tsantsar tausayi da kuma ganin kamar zan fi samun kwanciyar hankali a
can, amma na tabbata ita kanta ta sani kina nunamin kaunar da ba don kar nayi
wauta ba, zan ce ta fi na Raihana da su Anti Tasleem."
Anti Maijidda ta kasa cewa komai tayi gum sai kallo, Abba
kuwa sai kalaman Ummita suka kashe mishi jiki, shakka babu gaskiya ta fadi kuma
ba zai so a yiwa Mami butulcin nan ba. Ya dai so a farko ya amince da batun
Anti Maijidda idan har sauya wurin zai dawo da walwala da farin cikin Ummita.
Humaira sosai ta ji dadin kalaman da Ummita ta yi ga Mami, ta tabbata hakan ne
kawai zai sanyaya zuciyar Mamin, sai kawai ta ji Anti Maijidda ta sire a ranta.
Ita a duniya yanzu ba ta da maΖiyi irin mutumin da zai kushe Mami da ΖoΖarinta
a kansu, abin da dai ta fahimta shi ne, ba a iyawa DAN ADAM, wannan sai
mahaliccinsa. Ba ta san mene ne ribarta na aibata Mami ba.
Murmushi Mami ta yi tana dubanta kafin ta dubi Anti Maijidda
da ta yi mutuwar tsaye. Sai a lokacin Anti Maijidda zuciya ta tunzurota ta soma
magana tana duban Ummita.
"Yau kin watsamin Ζasa a ido ko Ummita? Ni kika nuna
bani da wani matsayi ko Ζarfin iko a wajenki? Wa.."
"Anti please. Ki duba yanayin da take ciki mana ki rabu
da zancen nan haka. Ina haΙa ki da Allah ki bar komai har ta rabu da abin da ke
jikinta lafiya idan har dagaske farin cikin kike nema mata."
Mubarak ke wannan tun soma zancen ya shigo yana kuma
sauraronsu. Ransa ya Ιaci ba kaΙan ba da yanda Anti Maijidda ke kushe masa uwa
kuma mahaifiya amma ya fi jin zafin yadda take neman haifarwa da Ummita wai
sabon Ιacin ran na daban. Jinjina kai Anti Maijidda ta yi, ta hadiye Ιacin ran
nata kamar yanda ya nema. Dagaske ta fi kaunar samun lafiyar Ummita a yanzun da
kuma kwanciyar hankalinta wannan yasa ta taka zuwa ga Ummita ta janyota ta
rungume. Yadda Ummitan ke kuka hakanan itama take yi.
"Kiyi hakuri ya isa hakanan, shikenan magana ta wuce.
Kiyi zamanki anan zamu dinga waya kin ji?"
Ummita ta gyada mata kai, daga haka kuma aka kashe zancen.
Abba da Mubarak suka fita don haΙuwa da D.P.O don tsaurara bincike akan wanda
ya yi wannan aika-aikar da ma neman
alfarma gurin D.P.O akan ya fito gidajen yaΙa labarai ya faΙi abin da ya sani
kan satar su Ummitan zuwa yanda aka kaya sadda aka je kwato su.
Mami kuwa ta Ζara jifan Anti Maijidda da murmushin cin
nasara sannan ta juya ta bar falon zuciyarta fari Ζal yayinda ta bar Anti
Maijidda da Ιumbin takaici da cizon yatsa. Ta sani addu'a babu abin da ba ya
magani, za kuma ta dage da kai kukanta ga Allah, watarana halin Mami zai
bayyana Ζarara a idon duniya.
***
Anti Amarya ta dubi
Alhaji bayan gama nuna masa jita-jitar da ake yaΙawa akan su Humaira ta ce.
"Yanzu Alhaji wannan magana ko Ζarya ne a yanda sunan
gidannan ya Ιaci fisabilillahi sai ka aminta da auren Fadeel da Humaira?"
Nan da nan Alhaji ya Ιaure fuska ya ajiye wayar.
"Me kike son ki cemin? Sai na tauyewa Ιana farin
cikinsa akan Ζaryar da maΖaryata suke yamuΙiΙi da shi?"
Ta tari numfashinsa.
"Saboda farin cikin Ιanka mu kuma za ka zubar da namu
Ζimar gidan a idon duniya? Ka san wannan Ιacin sunan kuwa ba iyaka Nijeriya ya
zagaye ba? Allah kaΙai ya san inda lamarin ya tsaya. Alhaji ya kamata ka buΙe
idanunka sarai ka dubi lamarin da idanun basira, ni ban taΙa Ζin Humaira ba
saboda ban ga abin Ζi tattare da ita ba kamar yanda babu wani aibu da ta taΙa
yi gareni ba. Amma ana magana ne na haΙa zuri'a, idan ya kasance sai bayan mai
afkuwa ya afku maganar duniya ta tabbata gaskiya sai ka sa hannu a kumatu ka ce
za ka yi tagumi da nadama?"
Shiru Alhaji ya yi, maganganun Anti Amarya suka shiga tasiri
a zuciyarsa. Dagaske yanzu idan har zancen duniya ya tabbata shikenan ya haΙa
iri da Ιata gari?
Anti Amarya ganin ya yi shiru sai ta yi Ιan murmushin
mugunta, ko babu komai dai alamu sun nuna kwalliya za ta biya kuΙin sabulu,
alΖawari ne ta Ιaukarwa kanta yanda Fadeel bai auri Murja ba ya yi sanadin
barinta gidan, toh shima har abada sai ta raba shi da Humaira. Sai ta ga iya
gudun ruwansa.
"Shikenan Antin yara, zan dai duba zancen. Mu yi addu'a
mu kuma jira mu ga ta inda gaskiya za ta yi halinta."
Ta sauke ajiyar zuciya ganin ta yi nasara.
"Hakane, Allah ya bayyana gaskiyar."
Ya amsa da amin.
Ζangaren Fadeel kuwa har tsawon kwanaki uku da al'amarin ya
fasu yake cikin wani irin tashin hankali da baΖin ciki. Soyayyar da yake yiwa
Humaira ta yi Ζarfin da ko daidai da Ζiftawar idanu ba ya zarginta da fasiΖanci
balle kuma ya aminta da jita-jitar da ake yaΙawa. Wannan ya sanya a Ιangarensa
shima ya sanya aka soma bincike akan al'amarin don a gano bakin zarensa. Ga
bikin babban amininsa nan da kwanaki uku amma hakanan damuwar yanayinnan ya
gusar da murnar bikin a zuciyarsa. Ta yaya mutanen da aka ceto su cikin wani
hali na maye da kuma muguwar rama da baΖi ace yawon duniya suka shiga? Har
abada ba zai yarda da wannan ba. Da taimakon wani abokinsu na makaranta wanda
yake babban ma'aikacin sirri na SS, bincikensu ya dinga zurfi. Ibb dai ya zuba
idanu kawai yana Ζara mamakin wannan irin zazzafar kaunar ta Fadeel akan
Humaira. Har shakka yake yi kada bayan aure ya zame mata mijin tace saboda shi
kam abin ma ya shallake tunaninsa.
***
Tasleem tsaye tana
safa da marwa a Ζuryar Ιakinta daga ita sai vest wacce ta Ιage mata saboda
girman da cikinta ya yi sai ko Ζaramin short, waya ne a kunnenta, burinta kawai
Antinta ta Ιaga domin ta Ζagu ta ji labari. Har sai da ta kusan katsewa sannan
Jannat ta Ιaga muryarta a sake. Ko gaisawa ba su yi ba ta gangara inda yake ci
mata tuwo a Ζwarya.
"Anti, ina ta neman wayarki a kashe na Ζagu naji daga
bakinki. Kin ji labarin da ke yawo a media akan su Humaira ko? Anti hala
aikinki ne?"
Wata dariya Jannat ta yi daga Ιangarenta tun ma kafin ta ce
komai Tasleem ta samu amsar tambayarta, sai kuma ta magantu.
"Ni ce nan my daughter, ai ban fanshi marin da
munafukar Ζanwarki ta yimin ba. Idan sunansu ya Ιaci a idanun duniya wa kike
tunanin zai aminta da auren Ιaya a cikinsu? Ko a zatonki wancan sakaran Fadeel Ιin
zai Ζara kallonta? Tasleem ki kwantar da hankalinki, yanzu na san na gama Ιaukar
fansa akan Humaira don uwarta. Ita kuwa Ummita kinga cikin dake jikinta ya
taimaka wurin da jama'a za su yi saurin aminta. Ke tun sadda al'amarin ya faru
nake bibiyar kalaman jama'a ina dariya. Huumm muje zuwa."
Tasleem ta yi murmushi sosai.
"Na ji dadin rabuwar Fadeel da Humaira, na sani ko ya
nace akan sonta zai wahala iyayen da suka san mutuncin kansu su yarda Ιansu ya aure ta. Amma Anti naji fa wai
Abba zai sa ayi binciken wanda ya fara yaΙawa don a gano gaskiyar magana. Bakya
tunanin idan aka kama shi asiri ba zai tonu ba?"
Tsaki Jannat ta ja.
"Nawa aka yi irin haka Tasleem, kin taΙa ganin waΙanda
aka yi nasarar cafkewa?"
"A'a."
"Toh ki sa ranki a inuwa tawan, babu abin da za su iya.
Yanzu ai na kira Abbannaku na jajanta masa har da kukan shegantaka, shi kuwa
sai faman godiya da ban hakuri yake."
Suka yi dariya Tasleem har tana riΖe cikinta da ya Ιan motsa
saboda dariya.
"Ina yinki sosai Antina."
"Nima haka yar uwa. Maminki ce dai ta matsamin da
tambayoyi tun ranar farko shiyasa nake ta kashe waya, wai ita ga mai wayo,
bugar cikina take yi don ta gane ko ni ce na sanya a yi amma na nunamata ban
san komai ba sai ma da ta faΙamin. Kema ina jan kunnenki koda wasa kar ki
kuskura kiyi maganar da kowa."
Tasleem ta amsa cikin jin dadi da walwala.
"Kar ki samu damuwa Anti. Ba ki da matsala da ni."
Daga haka suka yi sallama zuΖatansu cike fal da annashuwar
Ζuntatawa bayin Allah.
***
A kwana a tashi babu wuya cikin Ζudurar Allah, har dai
jita-jitar da ake ga su Humaira ya kai watanni biyu, a wannan lokacin Ζura ta
lafa sosai sakamakon shaidu daga D.P.O har ma da shi kansa Abba da ma waΙanda
Abban ya yiwa tayin gidansa don ceto yaran nasa, likitocin da suka taimaki
rayuwarsu da ikon Allah, da dai sauransu sun bayyanawa manyan gidajen
jaridu abin da suka sani akan zancen har ma da irin gudunmuwar da suka bayar a
lokacin. Wannan ya sanya jama'a suka gasΖata hakanan waΙanda suka aminta sai
suka rinjayi masu kushe da Ζaryata zancen. Da wannan aka rufe babin Ummita da
Humaira aka shiga kuma wani labarin daban ya zama abin tattaunawa a sosha
midiya. Amma a Ιangaren Fadeel, magana ba ta mutu ba don yana nan a kan bakansa
na sanya wa a binciko mai wannan aikin duniya ta san shi kuma ya ΙanΙani
yadda ake ji idan aka Ιata wa mutum suna.
A Ζarshe ma da ya ga ba a samu haΙin kai daga jama'a ba, sai
ya sanya kuΙi har dubu dari biyar ta hanyar tsohon abokin karatunsa ma'aikaci a
SS, ga duk wanda ya kawo labari ko kuma ya ke da sanayya da wanda ya
aikata laifin. Nan fa jama'a kowa ya yi ca, burinsu kawai su samu wadannan kuΙaΙe,
a yanda rayuwar ta yi zafi sun san ba Ζaramin taimako zai musu ba.
Lokacin da Mami ta ci karo da wannan sanarwar a wani group
dinsu na hamshaΖan mata wanda Hajiya Lubna ta buΙe, sosai ta ji hankalinta ya
tashi. Ta ji ta Ζara tsanar Fadeel musamman da ya kasance zuwa lokacin Jannat
ta gaji da Ζaryata cewa ita ta aikata a wajenta ta fito fili ta faΙamata cewar
ita ce kuma fansa ta Ιauka. Ta sani, muddin ya kasance Fadeel sun ci galabar
gano mai laifi to fa sunan Jannat zai Ιaci kamar yadda Ζimarta zai zube a wurin
Abba.
Wannan ne yasa ta fita a whatsapp ta kira Jannat, ringing
bai fi sau uku ba ta Ιaga. Mami ba ta jira komai ba ta hau magana.
"Kin karanta labarin dake yawo?"
Cikin rashin ba abin muhimmanci ta amsawa yar uwar.
"Yes, na gani na karanta. Sai me?"
Mami ta danne jin zafin ire-iren magana gatsal da Jannat ke
yawan yi mata a lokuta mabambanta ta ce.
"Sai ki girbi abin da kika shuka tun da ke ba kya
shawara da uban kowa idan kika tashi Ιarna. Shi dai Fadeel da kike yiwa
kallon tara saura gashinan yana shirin ba ki mamaki. Ko kina zaton Ζarfin
kusancinmu ya kai ya hana shi daukar fansa a kanki?"
Tsaki Jannat ta ja.
"Ni babu wanda ya isa ya kama ni balle kuma ya ce zai
yimin hukunci. ki ga kwantar fa hankalinki kawai, ni abin ya shafa kuma
nawa hankalin a kwance yake don haka ba abin da zai faru."
Ζwafa Mami ta yi.
"Shikenan, kiyi kuka da kanki duk abin da ya je ya
zo."
Daga haka ta katse wayar tana sauke numfashi cike da Ιacin
rai. Ta rasa yaushe Jannat za ta yi hankali. Ita komai ba ta iya bin sa da
sauki ba sai ta yi garaje? Ai sai ta je ta ji da kunyatar da za ta yi a idon
duniya da ma su Abba.
***
Yakubu ya dubi Futuha da murmushin yaudara bayan ta nutsu
tana sauraron abin da zai ce ya soma magana.
"Na lura sam zamanki da Uwargida tun farko ba ra'ayinki
ba ne, nawa ra'ayin ne. Hakan yasa na siya maki gida daban a can kusa da yar
uwarki Tasleem. Kinga ke kadai abinki babu takura. Hakan ina fatan ya yi
maki?"
Wani dadi ya kashe Futuha har ta kasa Ιoyewa ya bayyana
saman fuskarta, dagaske aikin da ta sa aka yi ta hanyar abokiyar karatunsu Anti
ba karamin ci yake yi ba tunda har gashinan ya soma tunanin kawo mata sauyi
cikin rayuwa ta hanyar keΙance ta da abokiyar zamanta da nuna bambanci. Ta yi
farr da idanu bayan ta rungumeshi ta sakar masa sumba a lebba.
"Hakan ya yimin sosai fiye ma da zatonka. Yaushe zan
koma?"
Wani dadi da sanyi suka lulluΙe zuciyar Yakubu ganin ya
shawo kanta cikin mugun sauki. Ya san da ace ta san dalilinsa na tashin wannan
zancen sauya muhallin da ba ta fara aminta da hakan ba.
"Nan da sati Ιaya an kammala komai sai tariya. Yanzu
ana aikin Ζarasa haΙa kayan wutar solar ne."
Dadi ya Ζara Ζume ta. Ta ji sosai kaunar Yakubu na Ζara
mamayarta. Ζacin ranta na hotunan auren Ibb da matarsa Dakta Salma da aka turo
group din makarantarsu ya wanku a zuciyarta. Batun karatu dama tun tafiyarta
Dubai da dawowarta ta watsar, Yakubu ya nuna ba ya so zai wadatar da ita da
komai da take so, hakan ya sa ko a kanta ba ta damu ba balle kuma Abba da dama
shima ya fi kaunarsu da zaman auren sai dai ya so ace ta kammala. Mami kuwa
itama ganin Ιiyarta na samun dukkan abin da ya dace na jin dadin duniya sai ta
share zancen karatun.
"Allah ya kaimu lokacin."
Ya amsa da amin, daga haka ta miΖe ta na fadin bari ta kawo
mishi abu mai sanyi, shi kuwa ransa Ζal ganin nan da sati biyu Ζ³ar Snow za ta
zama mallakinsa matsayin matar aure.
***
_Sosai Ummita ke ihun daya cika kunnuwanta tana ambaton
sunan Allah iyakar Ζarfinta, wannan ya sanya ta nufarta a guje ba ta damu da
jinin da ke yawo a tsakar Ιakin ba tamkar ruwan famfo ta damΖo kafaΙunta tana
jijjigawa tana fadin._
_"A'a Ummita kar ki mutu ki bar ni, zasu kashe mu idan
suka riske mu a nan. Kinga ki tashi mu gudu!"_
_Rigarta Ummita ta damΖa da Ζarfi tana hawaye take fadin._
_"Innalillahi..Kai...Kai..Humaira anya zan rayu?
Humaira ko na mutu kar ki bari a jefarmin da gudan jinina. Kar ki bari su yi
nasarar rabaki da Ιana._ _Ki kira shi da suna Ahmad sannan ki kularmin da shi
tamkar ina raye._ _Wayyo Humaira ga Wizzy nan!"_
_Wai sai ta juya ta dubi Wizzy, riΖe yake da Ζaton adda a
hannu yana kiran sai fa ya raba Ummita da jaririn. Kawai sai kuma ta ga jariri
a hannunta, Wizzy zai karΙe ta shige gabansa kawai sai ta ga Mami ta zo
ta tureta ta fisge jaririn a hannun Ummita ta damΖawa Wizzy._
"Humaira! Humaira!!"
Sunanta da Raihana ke faman kira tana jijjigata iyakar
Ζarfinta ne ya sanya ba shiri ta miΖe daga nannauyen baccin da ya kwashe ta a
saman darduma. Gaba Ιaya ta haΙa zufa sharkaf duk kuwa da iskar fankar dake kaΙawa
a Ιakin. Ta damΖe hannun Raihana manyan idanunta suka Ζara girma har hakan ya
yi mugun kaΙa Ζ΄an hanjin Raihana, tsoronta kada dai aljanun Humairar ne suka
tashi, cikin rawar murya ta ce.
"Lafiyarki kuwa?"
"Ina Ummita?"
Ta nuna mata Ζofar banΙaki.
"Wanka ta shiga."
Sai a lokacin ta sauke doguwar ajiyar zuciya cike da tunanin
irin wannan mafarkin, me kuma ya haΙa Wizzy da Mami? Ta yi Ιan nisa a tunani
muryar Raihana ta Ζara katse ta.
"Mami ta ce ki shirya ku yi abin kari sannan ki Ιorawa
Sis Tasleem farfesu ta haifi Ιiyarta mace suna asibiti. Yanzu zamu wuce da
Mamin, idan an kammala tace ki ba Yaya Ζassim ya kawo."
Humaira ta gyaΙa kai.
"Toh, Allah ya raya. Ki gaidamin ita."
Raihana ta amsa ta fita a Ιakin, daidai lokacin Ummita ta
fito daga banΙakin. Baiwar Allah duk ta rame sai ciki da ya Ζara fitowa, bai fi
sauran sati biyu ta shiga watan haihuwarta. Hancinta duk ya buΙe. Ta dubi
Humaira tana Ιigar da ruwan wanka.
"Anti Tasleem ta haihu? Naji kamar haka Raihana ta
ce."
GyaΙa kai Humaira ta yi jikinta a sanyaye cikin tunanin
mafarkinta, Ummitar cikin mafarkinta tana so da kaunar abin da za ta haifa har
tana ba da amanarsa, amma kuma wannan ta tsani ma a yi mata batun abin da za ta
haifi duk kuwa da rayuwar da take gudanarwa maΖale da shi a jikinta.
Ummita dake tsane jikinta tana kallon Humaira ta madubi
wacce ta zubamata idanu ta yi Ιan murmushin yaΖe.
"Kallona kike kamar irin kina bankwana da ni zan mutu
wajen haihuwa ko?"
Maganarta ta girgiza zuciyar Humaira sosai, ta ji nan da nan
hawaye sun cicciko mata ta kauda kai daga dubanta.
"Allah ya kiyaye, hakan ma ba zai faru ba da yardar
Allah. Don Allah ki daina yawan irin waΙannan kalaman basu da dadi. Ke dai ki
yi addu'ar rabuwa lafiya da abin da ke cikinki."
Murmushi kawai Ummitan ta yi wanda hausawa ke kiransa da
yaΖe daga nan ba ta ce uffan ba, itama Humaira ba ta son zancen don haka ta
miΖe ta dauki zani da brush ta yi banΙaki.
***
Yarinyar Tasleem sak mahaifinta har duhun fatar, haka dangin
mijinta suka dinga zarya a gidanta don tuni aka sallameta a yammacin ranar da
ta haihu wato Asabar domin lafiya lau ta haifi Ιiyarta. Ta so kwarai ta je gida
wanka amma Mami tana sanar da Abba ya ce sam aa, babban dalilinsa kuma kada a
je a yi ta zuwa ana ganin Ummita ana Ζara mata wata damuwar ta daban. Wannan ya
sanya hakanan ba don ta so ba ta zauna sai Ladidi ce ta je mata zaman wanka don
dama bazawara ce mijinta ya rasu sai ko marayun yaranta da ta bari wajen
tsohuwarta.
Humaira ba ta leΖa ta ba sai da aka yi kwanaki uku, kullum
dai ita ke girki ana kai wa. Sai da Mami ta yi magana sannan ta shirya ta je.
Raihana na makaranta su na rubuta jarrabawar mock daga nan kuma ba jimawa za ta
soma WAEC.
Fuska a yatsine Tasleem ta amsa gaisuwar Humaira gami da
fadin.
"Sai yau kika ga damar zuwa kenan? Ai da ma kin bar shi
gaba daya."
Ta kuwa ji zafin maganar ta ji dama sam ba ta zo ba. Wato ba
ta ga bautar girkin da take yo mata ba ana kawo wa ba sai kawai Ζorafin ba ta
zo ba. Don haka ta Ζi tankawa ta miΖawa Ladidi jaririyar don a yi mata wanka.
Ba ta wani jima ba ta fice abin ta. Tare suka wuce da Ζasim a mashin Ιinsa don
yanzu sam Abba ba ya kaunar shigarsu Ζan sahu. Adalilin haka ne ma yake ΖoΖarin
siyar Ζaramar motar fita unguwa bayan tasa ta amfaninsa dake gidan.
Wannan haihuwa ta Tasleem ita ce ta yi sanadiyyar zuwan
Jannat garin Kano da kyakkyawan albishir na dawowar da zasu yi Kano ita da
mijinta da ma yaransu a dalilin sauyin aiki da ya samu ta zo wa Tasleem. Ta
kuwa ji dadi don har tsalle ta yi ta rungumeta har sai da ta yi mata tsawa akan
ta bi a hankali. Futuha ma ranar da Jannat ta zo itama ranar ta Ζara zuwa
na biyu, nan take ba su labarin gidan da Yakubu ya gina mata a sama kaΙan da su
Tasleem. Ko kusa Tasleem ba ta yi wani murna ba sai murmushin yaΖe saboda baΖin
cikin cigaban da Futuhar ke ta samu a rayuwa, ita kuwa Anti Jannat sosai ta ji
dadi ta taya ta murna.
***
Fadeel ya Ζurawa matashin da ya ci suna Joshua idanu, siriri
kuma dogo baΖi wuluk. Kallo Ιaya za ka yi mishi ka san ya Ζare saboda tsabar
shan sigari da kuma kayan maye. SarΖa mai tambarin cross ce a wuyansa. Ya dubi
Ridwan ya ce.
"Wannan dai shi ne wanda ya yaΙa rumours akan su
Humaira?"
Ridwan ciki da tabbaci ya gyaΙa kai.
"Shakka babu shi ne, komai na shaidun da muka samu daga
abokansa ya nuna hakan kuma shi da bakinsa ya gasΖata ya kuma ce sanya
shi aka yi amma a yi hakuri."
Mamaki ya Ζara kama Fadeel.
"Amma kuma YallaΙai alamunsa sun nuna tamkar bai ma jin
Hausa gaba daya."
Ζ³ar dariya Ridwan ya yi.
"Haka kowa zai yi zato, amma shegen ko wani Bahaushen
ba zai nuna masa Hausa ba. Hatta karatunsa a kwalejin ilimi na Kano abinda ya
karanta kenan Hausa da English. Ko ba haka ba?"
Ya watsa tambayar ga Joshua da ya yi tsuru da idanu yana
jinsu. Jiki a sanyaye ya amsa.
"Hakane Sir."
Fadeel ya daure fuska. Ya ji tamksr ya shaΖe wuyan Joshua ya
huta, ba iyaka haushinsa kawai yake ji ba akan abin da ya aikata aa, har ma da Ιatancin
sunan da ya kusan haddasawa ya rasa Humaira gaba Ιaya a wurin Alhajinsa domin
ya tabbatar masa idan zargin da ake yi ya tabbata to fa sai dai ya haΖura da
Humaira. Ba shi kuma ya samu nutsuwa ba sai da shaidun da suka tabbatar da
satar suka rinjayi masu Ζaryatawa. Wannan dalili kuma ya sanya Alhaji ya sauko
akan bakansa ya kuma ce nan da wata Ιaya za a yi aurensa da Humairar
muddin dagaske iyayenta suke za su ba shi ita. Shima ya aminta da hakan,
hakanan Abba ya san da zancen amma ko kadan bai sanar da wani a gidan ba.
"Yanzun ka shirya faΙa mana wacce ta sanyaka aikata
hakan?"
Tambayar da Ridwan ya watsa masa kenan. Ya sunkuyar da kai
kirjinsa na dukan tara tara amma gwara ya tona asirin ya huta don bai ga hanyar
tsira a hannunsa ba. Miyau ya haΙiye maΖwat sannan ya ce.
"Wata ce ta haΙa ni da wata mata mazauniyar Ζasan Egypt
ta ce tana da wani zazzafan aiki wanda idan har nayi mata komai ya tafi yanda
take so za ta yimin kyautar dubu dari biyu."
Ridwan da Fadeel suka dubi juna sannan suka maida hankula
gareshi.
"Ya sunanta? Ka ba mu labari tiryan-tiryan don mu san
abin da ya faru."
Joshua ya kasa cewa komai sai zufa.
"Look Joshua, ba wani abu muka ce zamu yi maka ba, muna
son mu je root din matsalar ne don mu magance ta. Ka fito ka faΙamana su waye
ke da hannu a ciki."
Ya jinjina kai cikin aminta da zancen Ridwan ya soma magana.
"Nidai ina tare da Babana ne a nan Kano, Mamana
asalinta Ζ΄ar Ζasar Ghana ce. Toh tana aiki a Misra ne gidan wasu larabawa ne
kamar ban dai sani ba. Toh matar ce
ta ba wa Mamana aiki kan ta nemo mata wanda ta san zai iya yaΙa labarin
Ζarya akan case din Ummita da Humaira kuma itama ba aikinta bane sanya ta aka
yi ta nemo wanda zai yi a biyashi.
Wannan dalili ne ya sa Mamana kirana ta yimin bayanin komai, nan da nan
batare da dogon tunani ba na aminta zan karΙi aikin nan. Tun daga nan magana ta
koma tsakanina da ainihin matar da zan yiwa aikin ba Madam din da Mama ke aiki
a gidanta ba, ta instagram oage dinta muka soma magana na lura sabon buΙewa ne
shafin nata, anan ne ta ke yimin bayani sosai na aikin har ma da Ζara
jaddadamin wadannan kudaden da za ta
bani. Toh shi ne na shirya labarin na aikamata ta lambar da ta turon na can
Egypt ta ce da zarar na kammala na aikamata ta whatsapp, hakan kuwa aka yi
nantura mata, sai da ta tabbatar komai ya yi kafin ta yimin umarnin samun
lambar da ba a san ni da ita ba na yaΙa. Ta sanya na buΙe shafukan media
sababbi da ba a sanni da su ba, har sai da labarin ya yaΙa yanda take so sannan
ta bani umarnin rufe dukkan akawun din.
Kuskuren da nayi sai na sanar da abokaina su huΙun nan da ku ke gani,
suka goyamin baya amma suka ce sai na ba su kasonsu a kuΙin da za'a ban, akan
kuΙin mun samu matsala da su. Sai kuma da aka sa kuΙin da ya ninka na aikin da
aka bani cewar ana neman wanda ya aikata laifin shi ne suka ci amanata suka
fallasa. Kun ji yanda abin ya kasance. Ita kuma matar tun bayan lamarin ta yi
blocking dina bayan ta sallame ni. Mamana ta ce kada na Ζara tayar da zancen
bisa umarnin Madam dinta, kuma kada na bari Babana ya sani. Sannan ni ko sunan
wacce ta sanya ni bansani ba, Maman ba ta taΙa ambatonta da sunanta ba. Wannan
shi ne abin da ya faru YallaΙai. Ku
gafarceni."
Fadeel ya dunΖule hannunsa bai ce komai ba, Ridwan ya yi
umarni aka mayar da Joshua ma'ajiyarsa sannan ya dubi Fadeel.
"Ita kuwa wannan mene ne dalilinta ko ribarta na aikata
hakan? Abu Ιaya dai da na fahimta, ko wace ce tana da relation da su biyun nan.
Hakanan kawai ba za ta sanya a yaΙa rumours akan su ba."
Fadeel ya jinjina kai, tabbas hakane amma kuma shi a iya
tunaninsa kamar dai ba su da wani dangi a Ζetare.
"Hakane YallaΙai. Yanzu mene ne abin yi?"
"Abin yi Ιaya zuwa biyu, zamu karΙi lambar ita Matar da
ma Mamansa idan ta kama. Idan binciken zai kaimu har can gidan su Humairar toh
sai a je."
"Shikenan hakan yayi. Zan yi waya da Abbansu na sanar
da shi komai."
"Ok ba damuwa. Nima nan zamu yi kokarinmu."
Daga haka suka yi sallama Fadeel ya bar ofishin.
***
Ranar sunan Ιiyar
Tasleem yarinya ta ci sunan mahaifiyar Hamza wato Asma'u suke kiranta da Husna.
Sunan da kusan rigima aka yi tsakanin Tasleem da Hamza don ta rantse sai dai ya
sanya sunan nata uwar shi kuwa ya rantse ba zai fasa sanya Husna ba. Hakanan
aka ci suna idanun Mai jego duk a kumbure saboda kukan baΖin cikin da ta yi,
uwa uba sai ga tsohuwar budurwar Hamzan kuma yar uwarsa ta kawo mata kayan
barka. Ta ci uban kyau da rantsetsan
leshinta ruwan Ζwai an mata adon stones. Black beauty da ita fuskarnan ta sha
make up sai Ζamshi take yi. Bisa shawarar Jannat ne Tasleem ta danne Ιacin
ranta sai yaΖe. Tana ji dangin Hamzan na tsokanar budurwa da sunan Amarya
amarya amma sam ba su kawo komai ba. Jannat na dariya ta ce.
"Toh kin gani ma ashe ta kusa aure kike wani tada
hankalinki."
Sai a lokacin itama Tasleeem din ta Ιan saki ranta. Gwara ta
tattara ta yi auren ko ta huta da jarabar bibiyar mijinta da take yi. Futuha
kuwa a tsaisaye ta leΖa sunan ta kuma wuce da Humaira da Raihana don su taimaka
mata da tattara kaya saboda kaurar da zata yi sai wani rawar kai da Ζafa take
yi.
Hakanan suka tattara sannan ta ce su yi gaba a mota a kai
kayan tare da su don tuni an kai dukkan kayan katakonta an kuma jera, sai na
sanyawarta a jiki suka rage. Wannan duk budurin da ake yi ba ta ga gida ba.
Humaira da Raihana suka bi umarninta zuwa gidan, yayinda ita kuwa ta wuce
gyaran gashi don ta ce gwara mutan unguwar su ganta tsaf ba raini don Yakubu ya
ce mata unguwar Ζ΄an gayu ne.
***
Ummita zaune ita Ιaya a falo tana biyawa su Muhsin karatun
hadda da aka yi musu a islamiyya, haka Mubarak ya shigo ya risΖeta. Kallo Ιaya
kawai ta yi mishi ta maida kanta Ζasa tana gaida shi don a yanzun kwata kwata
ba ta kaunar ganinsa ba don komai ba sai irin kallon da yake bin ta da shi da
kuma manufarsa na soyayyar da yake nuna mata, koda bai furta ba alamominsa sun
nuna. Madadin ya wuce sashin Anna wurin Mami kamar yanda Waleed ya sanar mishi
cewa tana can, kawai sai ya Ιige da zama a falon yana duban Ummita cike da wani
irin kauna mai tsafta ga kuma tausayi.
"Beauty."
Ko kusa ba ta gane da ita yake ba sai bayan ya Ζara
maimaitawa. Ta Ιago idanunta fuska ba walwala ta dube shi. Ya yi mata sanyayyar
murmushinsa, kamanninsa da Abbansa ya Ζara fitowa.
"Gobe fa zan tafi Camp, baki da labari?"
Ta girgiza kai tana maida hankalinta kan littafi mai tsarki.
"Ban sani ba. Allah ya kaika lafiya ya sa a kammala
lafiya."
Ya lumshe idanunsa ya bude da murmushi saman fuskarsa.
"Amin beauty, nagode. Sai dai zan yi kewarki."
Fadin hakan da ya yi hatta Waleed sai da ya dube shi, nan da
nan ya daure fuska ya ce su je su cewa Mami ya zo. Suka kuwa mike har su na
rige-rige suka bar falon. Ita kuwa Ummita ta kasa cewa komai sai faduwar gaba
fat fat.
"Sun watse sun barki ke Ιaya ko?"
GyaΙa kai ta yi.
"Beauty ba magana?"
Ta dago ta dube shi da idanunta wadanda suka cicciko da
hawaye. Ba ta son har abada abin da zai tuna nata da Sahabi wanda tuni aka Ιaura
aurensa da yar uwarsa.
"Yaya Mubarak, don Allah ka kirani da Ummita. Bana jin
dadin sunan da ka sauyamin."
Ya taso ya Ιan yi durΖuso a gabanta.
"Ba zan iya dainawa ba Beauty. Sai dai zan yi kokarin
danne abin da ke zuciyata har Allah ya rabaki da cikin jikinki lafiya. Bana son
na furta yanzu amma yana nema ya rinjaye ni. Kiyi hakuri da ni zan Ζara danne
zuciyata har zuwa lokacin da ya kamata komai ya bayyana a zahiri. I am so
sorry."
Wannan karon da hawaye saman fuskarta take dubansa cike da
tausayinsa. Bai san masifar da yake shirin jefa rayuwarsa ciki ba. Ban da abin
Mubarak me zai yi da ita, Ummitan da sunanta ya gama Ιaci a idanun jama'a?
"Mubarak!"
Tsawar da Mami ta dakamasa ya sanya gaba daya suka dube ta,
ranta a tsananin Ιace take dubansu. Ta Ιan jima kaΙan da shigowa falon amma sam
ba su lura ba. Kaf kalaman Mubarak din na karshe a kan kunnuwanta ya yi su.
Ummita ta sha jinin jikinta da irin duban da Mamin ke watsa musu.
*LITTAFIN NAN NA KUΖI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA
TARE DA SHIGA HAKKI BA.*
*5407827015*
*FCMB*
*Farida Abdullahi*
09034973645
Duk iyaka kokarin Mami ta kasa danne zuciyarta saboda abu Ιayannan
ba za ta iya Ιaukarsa ba, haΙa zuri'a da Ιiyar Jamila wato Ummita. Mubarak ya
miΖe yana dubanta hakanan Ummita tun duban farko sai ta yi Ζasa da kanta
kirjinta na dukan uku uku don gani tayi ma kamar Mamin cetonta ta yi daga
kalaman Mubarak wadanda suke shiga kai tsaye cikin zuciyarta tamkar mashi. Ko
kusa ba ta kawo komai ba face kyakkyawan zato ga Mamin.
"Mene ne haka ne? Kar ka kara yimin wannan sakarcin. Ka
riΖe abin da ke ranka kuma ka kauda shi don ba zai taΙa yuwuwa ba."
Mamaki ya cika Mubarak, itama Ummita ta Ιan ji maganar a
ranta amma kuma ta basar. To me zai dame ta ma tunda dama ita ba soyayya ce
gabanta ba? Ita ta fi kaunar ma ta mutu yayin haihuwa ko ta samu shahada ta
huta da baΖΖan cikin duniyarta. Mubarak har ya buΙe baki zai Ζara magana Mami
ta dakatar da shi ta hanyar Ιaga mishi hannu.
"Kar ka cemin komai. Fice harkar gabanka, kai da kake
da tafiya a gaba mene ne za ka tsaya kana Ιatawa kanka lokaci kana Ιatawa
yarinya itama?"
"Ma.."
"Nace maka bana son jin uffan daga gareka ko? Don haka
ficemin a nan."
Ya jinjina kai kawai bayan ya kara duban Ummita da aka yi
sa'a itama ta Ιago kai suka haΙa idanu ta mayar, sannan ya fice yana Ζara
Ζudurtawa a Ζasan ransa in sha Allahu mallakinsa ce muddin dai ta amince da
aurensa.
Bayan fitarsa Mamin ta karaso ta zauna sosai a saman kujera
har lokacin fuskarta ba walwala ta soma magana.
"Ke yanzu idan ma wani yace maki ki yi soyayya sai ki
dube shi? Yanzu ai babu abin da ya fi maki alheri face ki kula da kanki da abin
da ke jikinki har Allah ya rabaki da shi lafiya. Ummita na fi kaunar farin
cikinki sama da na Mubarak, yau kika biyewa yaron nan sai ya kaiki ya baro. Ni
na haife shi na kuma san ra'ayinsa da ma Ιabi'unsa, ba shi da ra'ayin auren
bazawa.."
Sai kuma ta yi Ιif jin hasalalliyar zuciyarta za ta sa ta yi
katoΙara. Ummita kuwa ta fahimci tsaf abin da Mamin ke ΖoΖarin faΙi, sai ta
shiga kokwanto akan anya dagaske Mamin da kanta ke wannan batun ko kuwa dai,
don haka ta Ιago ta dube ta ita kuma ta kauda kai karshe ma ta miΖe ta
bar falon. Shakka babu ita Ιin ce da kanta, maganar ta tsayawa Ummita a
rai. Bazawara fa take kokarin kiranta? Mami da kanta? Sai kawai ta ji wasu
sabbin hawayen sun kwaranyo. Zuciyarta na ce mata eh ga kuma zahiri na idanunta
na kara tabbatarmata da haka Ιin ne amma wani Ιangaren na zuciyar na kokarin
kare Mamin da tunanin ajizanci na kowane Ιan adam, mai yiwuwa itama suΙutar
baki ne saboda Ιacin rai ba hakan ta so faΙi ba. Wannan dalilin ya sanya ta
share hawayenta ta tattara kur'anan su Muhsin ta maida kowanne a jakarsa sannan
ta kwashi jakunkuna zuwa Ιakinsu.
***
Ζaramin gida ne wanda ya ji fenti daga waje ya sha kyau,
ciki kuwa kana shiga, babu batun farfajiyar gidan saboda wani tsukakken wuri ne
sai famfo a gefe ga bishiyu Ζananu an mishi ado da su. Daga ciki kuwa kai tsaye
falo za ka faΙa, ba shi da girman da zai cinye manyan kujerun Futuha sai raba
su aka yi wasu aka kai safayar Ιaki falle guda dake a Ζ΄ar tsakar gidan.
Ζaki Ιaya ne a ciki sai store da kicin Ιinta Ζarami wanda hatta da freezer
dinta bai shiga ba sai a zagayen baya gefen kicin aka sanya shi. Hakanan babu
matsugunin kayayyaki da yawa na wuta na amfani kicin dole hakanan suka cuccusa
su da taimakon ma'aikata tsohon gidan da suka kawo kaya. Gado dai ya shiga Ιaki
amma fa ya cinye kusan rabin Ιakin. Raihana da Humaira sai kallon kallo da
mamaki, ita dai Humaira ba ta tanka ba sai Raihanan da ke ta jajen lamarin da
hango rikicin da zai faru idan Futuha ta ga gidan da take ta yiwa rawar Ζafa
har Tiktok ta yi na bidiyo tana a tayata da addua za ta tare a sabon gidan da
mijinta ya gina mata, har da alΖawarin za ta yiwa followers dinta bidiyon gida
kamar yanda suka buΖata su na Ιokin su gani.
Ana kammala jeran komai wadanda ba su samu wuri ba aka sanya
su a store, bayan fitar masu kawo kaya Humaira ta dubi Raihana.
"Nifa gaskiya binsu zan yi a sauke ni a gida ba zan
zauna har ta zo ba."
Ganin haka wuf Raihana ta dauki mayafinta.
"Balle kuma ni, ta ina zan zauna a yi borin nan a
gabana? Wallahi ba da ni ba. Mu ba su muΖulli idan ya so su yi mata waya ta faΙi
inda za su kai mata ko kuma ai za ta koma tsohon gidan ta yiwa Uwargidanta
sallama, kinga sai ta karΙa a can."
Murmushi Humaira ta yi, har ta tausayawa Futuha ganin yanda
ta ke rawar Ζafar shiga gidan da a yanzu ko na Tasleem ya fi shi tsari da
wadatuwa. Tana ji koda suka kama hanyar tafiya gida bayan sun bada muΖulli sai
da ta Ζara kiran Raihana ta gama masifar dalilin da yasa ba su jirata a gidan
ba salon ace ta shiga babu Ιan rakiya kafin ta hau tambayar yanda girman
parking space din gidan yake wai ko zai iya cin mota biyu. Raihana ta amsa da
ita dai idan ta dawo ta shiga ta ganewa idanunta daga hakanta kashe wayar baki
daya. Duk yanda Humaira ta kai ga son riΖe dariyarta sai da ta kufce mata,
Raihana ta taya ta.
"Allah kuwa ta ban tausayi kuma ta ban dariya idan na
tuna yanda take ta wani jijji da kai da Ιora bidiyo wai a taya ta murnar tariya
a sabon gidanta."
Humaira cikin faΙaΙΙan murmushi ta amsa.
"Kin ga illar son a sanin da ta ke yi a idanun duniya
kenan, yanzu da ace asirinta a rufe yake ba ta sanar da kowa ba shikenan babu
mai ji balle gani. Ba ki ji ta ce washegari za ta yi walimar tariya ba har fa
abinci kina dai ji a gabanmu ta ba da odarsa tana cewa akwai sabuwar mai
abincin da ake yayinta a bukukuwa."
Takaici sosai ya kama Raihana.
"Ai shikenan, sai ta shirya naΙe tabarmar kunya da
hauka."
Haka suka yi ta hirarsu har suka Ιullo gidan Tasleem inda
anan za su wuce tare da Jannat wacce ta maida gidan wajen yininta. Wannan karon
ba ta zo da yaranta ba saboda makaranta ta bar su can hannun kanwar babansu
dake aure a Misra. Gargadin Abba ne bai aminta su kara shiga Ιan sahu ba idan
har ba wasu kwakkwaran dalilai ba ne da ya yi zafin da sai an nema an shiga.
Wannan ya sa suka yanke hakuri da zaman jiran Jannat ta gama ta wuce da su a
motarta gudun kar su je Abban ya yi musu faΙa. Su kansu tsoron shigar suke yi
yanzu musamman Humaira.
Sun zo dab da gidan Tasleem har su na hangowa ne wayar
Humaira ta dauki Ζara.
"Idan ita ce please ki ce mata muna abin hawa mun ma yi
nisa."
Humaira dai murmushi take don ita abin ma dariya yake
ba ta, gyaΙawa Raihana kai kawai ta yi kafin ta fiddo wayar a jaka ta duba.
Fadeel ne. Madadin Ιacin rai ko baΖin ciki da haushi, sai ta ji ranta ya yi
wani irin sanyin da ba ta yi zatonsa ba. Raihana da ta leΖa ta ga waye ta kuma
ga yanayin dake kwance a fuskar Humaira sai ta ji tamkar da daka tsalle tsabar
farin ciki, amma sai ta Ζarawa murnar armashi da ambaton sunan Allah gami da
yin hamdala.
"To sai ya katse? Ki Ιauka mana please."
Ta kuwa amsa sannan ta kara a kunnenta da sallama. Fadeel
daga Ιarinsa ya amsa. Ji ta yi muryarsa na sanyamata wata irin nutsuwa da
sanyin ruhi, ta kasa hasko meke shirin faruwa da ita har sai da maganarsa ta
katse tunaninta.
"Boddona, nayi kewarki sosai. Kin ji bawan Allahn nan
shiru a waya kwanaki biyu amma ba ki nemi ki san ko lafiya ba ko?"
Sunan Boddona ya sanya ta dan lumshe idanu ta buΙe su da
wani Ιan guntun murmushi a saman leΙΙanta, Raihana dai kallon ikon Allah kawai
take yi tana washe bakin jin dadi na wannan sauyi da aka soma samu daga
Humaira.
"Ka yi hakuri, nima ban samu nutsuwar zama ba ne balle
har na kira na ji ko lafiya. Fatan komai lafiya? Ya mutanen gidan ya wajen
Maman Husna?"
Sai da Fadeel ya yi wani irin dauke wutan da har ta yi
tsammanin yankewa wayar ta yi, Raihana ma mutuwar tsaye ta yi domin cak ta
tsaya daga tafiyar da suke yi baki a buΙe sai kuma ta sa hannu ta rufe. Ganin
haka Humaira ta fidda wayar a kunnenta ta kalla, sannan ta Ιan juya kadan tana
kallon Raihana. Wayar ta maida kunnenta tana murmushin yanayin mamakin fuskar
Raihana ta kara magana.
"Ba ka ji ba?"
Wata doguwar ajiyar zuciya ta ji ya sauke da Ζararta sai da
ta ji a kunnenta.
"I am with you Boddo, na ji komai. Dukkansu lafiya
kalau, nagode sosai da wannan."
Ta yi Ιan murmushi ba ta ce uffan ba har suka tsaya cak a
Ζofar gidan Tasleem, Raihana sai ba ta kwankwasa ba tana jiran su kammala wayar
bayan ta yi mata raΙa akan ta taimaka ta sa a loudspeaker don ta ji. Ba musu
Humaira ta yi hakan.
"Kin yimin iznin shigowa yau? Kiyi hakuri, ina kewarki
a idanuna. Na jure Boddo, amma hakurina na neman gazawa da aski ya zo gaban
goshi. Please kin min izni na shigo yau mu gaisa koda na mintuna biyar
ne?"
Ta ji wani tausayinsa da ba ta taΙa tsintar kanta a ciki ba
ya kama ta. Meyasa wai ta ke ba shi wahala har haka? Me ya taΙa yi mata don ya
baΖanta ranta? Ta ba kanta da kuma zuciyarta da amsar a'a, wato babu shi. Ta Ιaga
kai ta dubi Raihana, da hannu yake roΖonta akan ta ba shi damar. Lumshe idanu
ta yi sannan ta amsa.
"Ba damuwa. Ka shigo ka Ιebi lokacin da ya yi maka
sannan ka tafi."
Nan ma Fadeel sai da ya Ιauke wuta har ya ba su dariya suka
gimtse.
"Kamar a mafarki. Alhamdulillah. Ki yi hakuri da shirun
da nake yi Boddo, in sha Allah ana yin Magrib za ki gan ni. Nagode."
"Nima na gode. Allah ya kawo ka lafiya. Sai
anjima."
"Ba ki ji ba."
"Me?"
"Ba zan gaji da ce maki ina sonki ba."
Yana fadin haka ya katse kiran. Kalaman sun shige ta kwarai,
ta ji ta tamkar an yaye mata kaso tamanin na damuwarta. Ba ta sani ba ko tana
son Fadeel ba, amma tana matuΖar tausayinsa idan ma tana tunano wulakancin da
ta yi mishi a rayuwa da ma wadanda ba su ji ba su gani ba sai ta ji tamkar ta
tsire kanta don Ιacin rai. A kwanakin nan dai ta sani tana nadamar abubuwa da
dama data aikata a baya, babban tunanin dake cin zuciyarta bai wuce na dalilin
aikatawar ba amma ta kasa tuna koda guda Ιaya.
Dariya da rungumar da Raihana ta kai mata ne ya farkar da
ita daga zurfin tunanin da ta faΙa.
"Son so yar uwata. Allah ya nunamana aurenku da Yaya
Fadeel. Ya sauki yar uwarmu lafiya ya ba ta dukkan farin ciki itama."
Ta kasa amsawa sai dan murmushi kawai, tuna Ummita duk sai
jikinta ya yi sanyi a kasan ranta ta ce amin din.
"Malama mu shiga ciki kar mu zama abin kallo."
Tana fadin haka ta ture ta ta yi gaba tana kwankwasa Ζofar
itama ta bi bayanta tana dariya. Koda suka shiga da nishaΙinsu, tana ji Jannat
na hirar Ιatancin sunan da aka yi musu amma ta yi banza da ita musamman ganin
har da rainin hankali a zancen don tana yi tana dariya har da cewa wai wa ya
sani ma ko dagaske ne tunda abu a duhu babu wanda ya san gaskiya sai su biyun
da abin ya faru da wadanda aka kira da suna kidnappers din. Duk yanda ta shiga
da walwala sai da Jannat ta rushe wannan farin cikin, shiyasa ta dinga kaucewa
haduwarsu tun da aka ce ta zo amma yau gashinan zamansu inuwa guda ya janyo
tana gasa mata zantuka marasa kan gado. Haka ta kai zuciyarta nesa ta danne.
Tana ji su na hirar gidan Futuha inda Raihana ke ta labarta musu yanayin gidan,
Tasleem me za ta yi ban da dariya? Ta dinga kyakyacewa son ranta har sai da
Jannat ta yi mata magana. Raihana kuwa duk yanda ta kai da yiwa Futuha dariyar
gidan sai da ta ji haushin farin cikin da Tasleem ta hau yi har da ambaton
Allah ya Ζara. Jannat ba ita ta tashi tafiya ba sai dab da magriba, Humaira da
Raihana har suka gaji ga tunanin Fadeel da zai zo bayan Magriba. TuΖin ma yinsa
ta dinga yi da gadara da yanga kamar ba ta so sai ka ce ta san da zuwan Fadeel
din amma ko kusa ba su sanar mata ba. Don kanta kuma daga baya ta ware hannun
sitiyari ta shiga gudu har suka isa gidan. A gurguje Raihana ta sanya Humaira
shiryawa. Ummita na daga kwance tana kallonsu sai murmushi kaΙan a fatar
bakinta. Inda ta ga da buΖatar gyara za ta yi magana. Duk da halin da take ciki
ta yi farin ciki kwarai da wannan sauyi na Humaira akan al'amarin Fadeel.
Humaira ta kammala shiri cikin wani rantsetsan yadinta mai
adon maroon da yellow ta yi kyau sosai musamman da ta yafa mayafi yellow sai
tashin Ζamshi take yi. Raihana ta so ta yi mata kwalliya amma ta nuna ba ta
ra'ayi, ita duk kaffa kaffar da take yi kada ta motsawa Ummita wani lamarin
akan Sahabi, ba ta san cewa Ummita kwarai take jin dadin yanda ta sauya ba.
"Masha Allah kin yi kyau sosai."
Fadin Ummita tana dubanta. Ta maida mata martanin murmushin
amma ba ta ce uffan ba can kuma ta dubi Raihana.
"Kinga ban sanar da Mami ba, na rasa ta yanda zan faΙamata."
Cikin basarwa Raihana ta ce.
"Kar ki wani damu, tana wajen Abba, ke idan ma ta
tambaya zan fadamata."
"Toh." Shi ne kawai amsar Humaira ta ba.
***
Wannan karon madadin ta gan shi tsaye a farfajiyar gidan,
sai ta same shi a Ιakin saukar baΖi na Abba. Ashe Mubarak ne ya kai shi can,
shi suka yi karo ya sanar mata inda yake. A kunyace ta sunkuyar da kai ta nufi Ιakin
kai tsaye.
Da sallamarta ta
sanya kai ciki bayan ya amsa. Suka Ιan dubi juna ta kauda kanta, ya sha adonsa
cikin yadinsa mai tsada fari Ζal ga kuma hula ya Ιora wanda ya yi matuΖar hawa
da kayansa. Kallonta kawai yake yi ba Ζaramin kyau ta yi mishi ba. Ta Ζaraso ta
nemi wuri ta zauna can nesa da shi kaΙan tana gaishe shi. Ya amsa mata
zuciyarsa tamkar ΖanΖara. Sai kuma ya rasa ta inda zai fara, sai ya ji kamar an
Ιaure mishi bakin saboda tsabar shauΖi, ita kuwa ta baza kunnuwanta don son ta
ji me zai ce. Can ta tsinkayi muryarsa a tausashe.
"Kin yi
kyau."
Ta kasa cewa komai sai murmushin da ta Ιan yi. Jin lamarin
ta ke banbarakwai, wai ita ce ke yin zance. Abin dai kamar a mafarki.
"Boddo." Ya kira sunan da take matukar jin dadinsa
amma koda wasa ba ta taΙa gwada mishi ba. Sai da ya Ζara maimaicin kira kafin
ta amsa a hankali. Fadeel ya yi hamdala a ransa, tabbas babu wani abu mai
girman da ya fi Ζarfin addu'a. Komai idan ka sanya Allah ciki kuma ka dage da
addu'a to fa zai zo ya zama tarihi. Hakan kuma yake fata, wannan Ζiyayyar ta
Humaira gareshi ta koma tamkar ba ta taΙa yinta ba.
"Nasan za ki ce Fadeel ya fiye naci da takura. Kiyi
hakuri, haka Allah ya yi ni, yadda ban iya Ζin abu ba haka nake idan na so ba,
ba na mishi son da nake jin zan iya haΖura da shi yau, gobe ko jibi. Kina daga
cikin abu mafi girma da tsada da na taΙa samu a rayuwa, a zatonki zan bari ki
suΙucemin?"
Ta kasa tankawa, jikinta ya yi la'asar, sai ta ji ya yi
matuΖar ba ta tausayi kwarai har ta Ιago idanu kaΙan ta dube shi, kwayoyin
idanunsu suka sarΖe, ya harΙe tafukan hannuwansa guri guda ya tallafa haΙansa
gami da Ιan karkata kai kawai yana dubanta. Ta janye Ζwayoyin idanunta gami da
sadda kai tana wasa da zoben azurfar yatsarta. So ta ke ta ce ka yi hakuri
Fadeel, na sani ban kyautata maka ba ka yafemin. Amma ta ji ta kasa, da wane
idanun ma za ta dube shi har ta iya bayan shafi-shafin rashin mutuncin da ta
sauke a kansa.
"Aa Boddona, in sha Allahu sai mun kasance a inuwar
aure. Sai kin zama mallakina nan ma ba da jimawa ba."
Ya Ζarashe zancen da murya Ζasa-Ζasa. Abin mamaki idanunsa a
saman fuskarta, ko kallonsa ba ta yi ba balle ya tsammaci kallon hararar da ya
riga ya yi sabo a shi. Wannan sauyin da take yi sai ya ji zuciyarsa n kasa Ιauka,
ba kuma wai rashin aminci da shi ba. Ko kusa, sai dai kawai ya kasa sakin jiki
yana ganin kamar na Ιan lokaci ne. Duk da haka yana kokarin tunasar da kansa
cewa addu'a ce ta kai su ga wannan munzalin ba kuma ya tunanin akwai abin da
zai sauke su a kanta. Ya miΖe ya Ιan matso kujerar da take kai ya zauna, tana
can Ζarshe kujerar kasancewar mai zaman mutum uku ce, shi kuwa yana gefe ya ba
da tazara tsakaninsu. Magana mai muhimmancin da ya kasa sanar da ita ne ya ke
ganin ya dace ta sani yanzu. Kirjinsa na bugu saboda fargabar kada ta tada bori
kan tsarin bai mata ba. Amma da ya ambaci sunan Allah sai ya samu Ζwarin gwuiwa
don haka ya karya bille ya soma magana.
"Humaira, iyayenmu sun yi magana sun kuma tsayar da
ranar aurenmu."
Ta ji tsiΖar jikinta ya tashi, ita da aure? Babu wani yanayi
da ta ji da ya wuce na sanyin jiki kamar wacce aka yi wa duka. Har wani zufa ne
ya yankomata, sai ta shiga maimaita sunan Allah a Ζasan ranta.
Shirunta ya haifarwa da Fadeel wata irin fargaba har sai da
ya ji inama bai ce uffan a kai ba. Har ya fidda ran za ta tanka sai ta Ζaryata
tunaninsa ta hanyar magana tana dubansa fuskarta na nuni da damuwa.
"Amma ta ya ya zan yi aure na bar Ummita cikin wannan
halin?"
Ya sauke ajiyar zuciya jin abin da ta ce, cikin Ζarfafa
gwuiwa ya ce.
"Kar ki damu Boddo, idan har wata Ιayan da su Abba suka
sanya ya cika, matuΖar aka Ιaura babu wanda zai takuraki da zancen tariya har
sai lokacin da kika aminta don kanki. Hakan ya yi maki?"
Ga mamakinsa sai ta gyaΙa kai da Ιan murmushi kaΙan a fatar
bakinta. Ai sai ya ji inama yana da damar haΙa jikinsa da nata. Hakan ma da ta
aminta da aurennasa ya yi mishi sosai, muddin dai ta zama mallakinsa to sauran
duka mai sauki ne. Hakan ya ayyana a ransa. Bai ja ta da hira ba gudun kada
kuma a zancen ta yi wani tunanin ta sauya ra'ayi don haka ya zaΙi su yi sallama a wannan gaΙar, yana da
tambayoyin da zai so ace ya yi mata na dalilin Ζin shigar ta makaranta ta zaΙi
girki da ma dai son jin duk wani abu da ya shafe ta amma ba ya son kwaΙarsa ta
yi ruwa sai ya haΙiye kwaΙayinsa ta hanyar yi mata sallama ya miΖe, itama ta
miΖe suka fito tare ta ja Ζofar ta rufe. Hannuwansa cikin aljihu ya ke dubanta
kamar ya haΙiye.
"Sai mun yi waya. A gaidamin yan uwana."
Ta gyada kai. Har ta soma tafiya sai ta juyo, yana tsaye cak
kawai yana kallonta da shanyayyun idanunsa so na fisgarsa. Ta Ιan kauda kai
daga dubansa ta ce.
"A gaidamin su Baba, idan kun yi waya da Maman Husna
ace ina gaida ta."
"Ko na turo maki lambarta? SaΖonnin sun min yawa kada
na manta."
Ta Ιan murmusa.
"Shikenan sai ka turo."
Ta juya za ta tafi ya dakatar da ita.
"Boddo."
Tsayawa ta yi ta juyo, murmushinsa ya yi har gefen kumatunsa
na lotsawa.
"Ina ji da ke."
Ta yi saurin juyawa ta nufi ciki, sai da ya ga shigewarta
kafin ya fice zuwa inda ya adana motarsa yana shafar sumar kansa duniyar na
mishi dadi.
***
Mami kuwa ta cika ta
yi fam, abu biyu ne suka haΙe mata, ga hotunan gidan da Futuha ta aikomata da
kuma wayar da suka yi tana rusa uban ihun kuka tana cewa gida za ta taho yanzun
a daren, ga kuma labarin auren Humaira da Fadeel da take ji a wurin Abba sai
aka yi katari a ranar kuma Humaira ta fita hira wajensa. Wannan ranar ta fi
kowacce baΖin ciki a wajenta. Suna falo zaune har Anna da ta fito saboda tashin
hankalin akurkin gidan da ta ga Futuha ta koma da kuma batun yajin da ta dako
har ana batun tana hanyar dawowa gida, sai yare suke bugawa a falon Jannat tana
yi itama Annar na yi, Raihana da su Mubarak dai sai tausarsu suke yi inda
Mubarak ya dage akan lallai idan Futuha ta tako yau sai ta juya ta koma gidanta
acewarsa ba za ta tayarwa Abba hankali ba ga shi yana fama da hawan jini. Anna
kuwa ta dage lallai sai Futuha ta dawo gidan tunda ba haka aka yi da
Yakubun ba, a wannan yanayin Humaira ta
shigo falon fuskarta dauke da murmushi sai baza uban Ζamshi take yi mai sanyi.
Ganin yanayin mutan gida sai da ta ji dam saboda ta yi zaton ko wani abun ne ya
kuma faruwa. Idanunsu a kanta, ga Anna da Jannat harara ne, Mami kuwa ba za ka
tantance ba sai dai fa fuskar a haΙe take tamau. Humaira ta dake ta Ζarasa ta
gaida Anna. Ba ta ko kalle ta ba balle ta amsa, ganin haka ta mike za ta nufi Ιaki
Mami ta yi mata tsawar da kowa a falon sai da ya dube ta.
"Ke! Da iznin uban wa ki ka fita wajen Fadeel?!"
Kamar an Ιinke mata baki sai ta kasa cewa uffan yayinda
Raihana ta yi caraf ta amsa.
"Mami na fadamaki fa kuma Abba yace Yaya Fadeel ya zama
Ιan gida tunda zai auri Ζ΄ar gida. Kiyi hakuri please ki daina jin haushinsa
yanzu tunda har Sis Tasleem ma ta yi aurenta ta manta da shi."
Wani kallon banza Mamin ta watsamata, Anna da Jannat dai
idaunsu kawai suka zuba ga Mamin saboda sun kasa yarda ita ce, a zuΖatansu basu
taΙa jin sanyi cikinsa ba kamar yanzun musamman Anna da take ganin fuskar
tsohuwar Mamin da ta sani a Agadez a na wannan. Mami kuwa kamar ta yi shiru sai
ta yi tunanin watakila shirun nata ya tona ainahin abin da ke ranta musamman ma
ga su Jannat ga Mubarak da suka zubamata idanu cikin hankalta. Don haka ta
sauke ajiyar zuciya.
"Shikenan wuce ki shiga ciki ki sauya kaya. Anjima zamu
yi magana."
Humaira wacce idanunta suka cicciko da hawaye ta gyaΙa kai
gami da miΖewa ta bar falon tana ji kamar an muzanta ta. Haka ta koma Ιakinsu
cikin mutuwar jiki.
"Ke da Mami ko?"
Ummita ta wurga mata tambayar da ya sanya ta dubanta, tana
daga zaune saman darduma bayan ta idar da salatin Annabi s.a.w. Kaf abin da ya
faru tana ji daga inda take. Ζan murmushin yaΖe ta yi mata.
"Ban san kuskuren dake cikin nagartar Fadeel ba,
watakila kuma sai yanzu da idanuna suka soma ganinsa da Ζima wata silar za ta
raba mu ta nisanta mu da juna idan har hakan zai faranta ran Mami."
Girgiza kai Ummita ta yi.
"Ban ce ki bijirewa dukkan wani umarni na Mami ba, amma
ki sani, ba Mami ce kaΙai me iko a kanmu ba. Abba shi ne mafi Ζarfin ikon
zartarwa. Idan har Allah ya Ζaddara aure tsakaninku babu wani mahaluΖi da zai
iya dakatar da faruwar hakan. Mami hujjarta ba karΙaΙΙiya ba ce, akan wane
dalili don bai auri wata ba wacce dama tun farkon fari ba dominta ya Ζulla
zumunta da gidannan ba, ace za a haramtawa wacce ba ta ji ba kuma ba ta gani ba
abin da Allah bai haranta ma ta ba? Anan dai na raba fahimta da Mami."
Humaira ta sauke nannauyan ajiyar zuciya har a lokacin ba ta
dauke idanu cikin na Ummita ba ta ce.
"Bana son saΖe-saΖen da zuciyata ta soma yimin akan
Mami, iyakar Ζarfina nake ΖoΖarin Ζaryata tunanina Ummita sai dai hakan na nema
ya faskara."
Ζan murmushi mai ciwo Ummita ta yi mata.
"Na fahimceki, ba kuma na son saka Mami a jerin masu
son zuciya idan nayi haka kamar ban mata adalci ba duba da yanayin riΖon da ta
yi mana na nuna fifiko akan yaranta na ciki. Sai dai a wannan gaΙar bana goyon
bayan hakan, ki toshe kunnuwanki Humaira. Fadeel mutumin kirki ne, a duniya ban
da soyayyar iyayenki, zan iya rantse maki Fadeel ne masoyinki na gaske bayansu
don ko mu ba lallai mu nuna mishi sonki ba. Ya sadaukar da lokacinsa duk a
kanki, shekara da kusan watanni ya jure dukkan wulakanci da baΖaΖen maganganun
da sauran mazan da suke sonki da aure suka kasa jura suka kama hanyar gabansu,
Fadeel ya cancanci ki aureshi. Ba fata nake maki ba amma muddin kika zama mai
juya baya a gareshi da Ζin yarda da shi, wallahi Humaira haΖΖinsa ba zai bar ki
ba."
Daidai wannan gaΙar hawaye suka wanke fuskar Humaira, ta
sani gaskiya Ιaya ita ce Ummita ta faΙamata. Har haushin kanta take ji idan ta
tuna yanda ya dinga ya bibiyarta a bainar jama'a tana yanΖwana shi. Ya jure
dukkan wannan ya kuma sadaukar da lokacinsa don kawai ya ga ta sauko don kanta
ta aminta da shi, ita kuwa me zai sa ta butulce masa?
Daga haka Ummita ba ta Ζara ce mata uffan ba, ai ruwa cikin
cokali ya ishi mai hankali, don haka ta bar ta da tunani iri-iri a Ζasan ranta.
***
A falon kuwa da fitar
Humaira sai Jannat ta kwashe da dariya.
"Mamin yara kenan, yau kuma marainiyar Allahn Ζ΄ar gaban
goshinki da ba ta laifi ita kike yiwa wannan Ιibar albarkar?"
Mami ba ta ce uffan ba don har lokacin zuciyarta a zafafe
take musamman da Jannat ta alaΖanta Humaira da sunan Ζ΄ar gaban goshinta. Wannan
ko a mafarki ba ta hangen haka.
"Mami, don Allah ki bar Humaira da Fadeel haka, idan
har yanda Raihana ta ce sanadiyyar Tasleem ne. Yanzu Tasleem igiyoyi uku ne a
kanta har da Ζaruwar Baby da ta samu. Ni ban san dalilinki na hana ta kula
matashi mai kirkinsa ba."
WaΙannan zantukan su na fitowa kai tsaye daga bakin Mubarak,
kafin ta tattaro amsar da za ta ba shi sai ga Futuha ta bankaΙo labulen falon
ta shigo a haukace tana wani irin kuka da sheshsheΖa, ta ci uban ado an shafe
fuska da Foundation amma sanadin kukan da ta sha duk sai ta koma kamar wata
aljana. Ganin Mubarak a zaune bai sa ta bar ihu da kukan da ta fasa ba, gaba
daya suka miΖe ita kuwa kai tsaye jikin Antinta Jannat ta faΙa gami da Ζara
sautin kuka da ihu. Wannan ya yi sanadin shigowar Abba falon don tun Ιazun yake
tsinkayar muryoyi a sama amma na yanzu ya fi duk na baya shiga kunnuwansa don
haka ya shigo falon a hargitse. Ganinsa sai Anna ta Ιan ja jiki ta koma ladabin
Ζarya kamar yanda ta saba yi a gabansa. Tsawa ya dakawa Futuha ba shiri ta kame
bakinta ta yi shiru, Mami sam ba ta so zuwan Abban ba don zai iya lalata
shirinta ya sa Futuha komawa dakin mijinta a yau. Ya kuwa jefowa Mamin tambayar
abin da ke faruwa idanunsa ma ko kan Anna bai kai ba saboda tsoro da fargabar
da ihun Futuha ya haifar masa. Mami ta Ιan gyara murya ta ce.
"Ke Futuha sai kiyi masa bayani, waΖa a bakin mai ita
ta fi dadi ai."
Futuha ta dubi Mami sannan ta maida kai ga Abba amma ta kasa
cewa komai tsabar fargaba. Jannat ta yi kundunbala ta soma magana muryarta
dauke da salon makirci, nan ta labartawa Abban Ζarya da gaskiya akan ginin da
Yakubu ya yiwa Futibar ya maida ta. Abba ya tamke fuska tamau, Jannat ba ta taΙa
ganin ya dube ta da tsantsar Ιacin rai da rashin walwala ba sai a ranar.
"Shi ne me?"
Tambayar ta sa Jannat kasa cewa uffan, sai Mubarak ne ya yi
caraf ya amsawa Abban.
"Shi ne ita kuma ta dawo gida ta ce ba za ta rayu a
cikinsa ba."
Abba ya nuna Futuha da yatsa.
"Ke, ki saurare ni dakyau, ni dai ubanki Isuhu ina raye
a kan idanuna ba za ki maida ni mutumin banza ba da bai san me yake yi ba. Kai
Mubarak ka dauki mota ka maida ta ka kuma tabbatar ta shiga gidan aurenta kafin
ka dawo gida. Ba zan Ιauki wannan sakarcin wofin ba."
Anna tana so ta yi magana amma tana gudun zubewar girmanta a
idanun Abba, girman da ta Ιoye ainahin zuciyarta ta danne komai ta shekara da
shekaru wajen gina shi a idanun Abban don haka ta ja bakinta ta yi shiru,
Jannat kuwa ta Ζulu iyakar Ζuluwa. Balle kuma Mami da take jira Abban ya koma Ιangarensa
ta je su buga wacce za su buga don bai isa ba sai ya Ζwatarwa diyarta Ζ΄anci.
Hakanan Futuha tana kuka ta bi bayan Mubarak suka tafi, a mota ganin ta cika
shi da ihu ya dakamata tsawar da ta hargitsa ta, ya koma Mubarak Ιinsa sak da
suke shakka, dole ta haΙiye sauran kukan ta koma yinsa a ciki ciki yanda ba zai
ji ba.
***
Ya kammala shirin
baccinsa tsaf zuciyarsa duk a Ιace saboda takaicin Futuha, haka Mami ta shigo
tana Ιaure masa fuska, ya dube ta kadan kuma ya ba kansa cewa damuwar ce itama
ke cinta wannan ya sa bai ce mata uffan ba. Sai da ta mula don kanta sannan ta
magantu.
"Abban yara wane irin hukunci ne ka zartar akan
al'amarin da ba ka ganewa idanunka zahiri ba?"
Da Ιan mamaki ya juyo daga barin chajin da yake Ζokarin sanyawa a wayar ya dube ta.
"Kika ce me?"
Ta kauda kai har lokacin fuskarta a daure ta amsa.
"Ai ka ji abin da nace. Fisabilillahi ta yaya
yarinya za ta tashi cikin gida babba
kamar haka, miji ya yaudareta ya soma kai ta wuri mai kyau daga baya kuma ya
sauya mata muhalli zuwa ΖasΖantaccan wuri sannan ta dawo da kokenta ta sanar da
mu amma mu kasa magance mata mu Ζwatar mata haΖΖinta? Wannan yanzu daidai ne a
wurinka?"
Abba ya dan yi jim yana duban Mami, ya lura tun lokacin da
suka tattauna a Ιazun dangane da batun tsaida ranar auren Humaira da Fadeel
take tattare da rashin walwala ya kuma fi kyautata zaton rashin sanar da ita
kan lokaci ne ya jawo hakan amma kuma sabon zancen da ta yi a yanzun shi ya sa
shi tunanin damuwarta kala biyu ne. Wato har da lamarin Futuha. Uzuri ya yi
mata ganin bai taΙa samun matsalar ja in ja da ita ba har kuwa a shekarun baya
da ya je mata da batun Ζarin aure. Can dai ya nisa ya ce
"Idan dai
muhallin da diyarki take ciki shi ya zama dalilin Ιacin ranki shikenan, gobe
zan je naga gidan bisa adalcin da kika nema."
Duk da haka ba walwala ta dora Ζorafinta na gaba.
"Sai na biyu, idan har ni Maryam kana yimin kallo na
matsayin Uwa a wajen Humaira ba mariΖiyarta ba, ka janye batun auren Fadeel da
ita saboda ina da wanda na zaΙa mata ya kasance abokin rayuwarta."
Maganar ta shiga kunnuwan Abba a bazata, sai da ya yi Ιan
shiru na lokaci kaΙan yana jin muryar Mamin na masa amsa kuwwa cikin dodon
kunne.
"Maryama, kinsan abin da kike faΙi kuwa?"
Ta dube shi tsakar idanu, ta koma Maryam dinta ta Agadez sak
wacce ba ta ragawa kowa balle kuma ganin kowa da Ζima ta ba shi amsa kanta
tsaye.
"Yes Isuhu, ni Maryam na faΙi na yiwa Humaira mijin
aure. Idan kuma kana son nunamin ni ban isa da ita ba saboda ba ni ce uwarta ba
toh bismillah."
*_Aikinki akan yarinyar ya Ιaci gaba Ιaya kuma ba komai ya
jaza hakan ba face samun tsayayyen matashin da yake tsananin sonta kuma ya jajirce wajen yi mata
addu'a da ma koyamata yanda za ta Ζarfafa ibadunta.*_ *_Ina mai tabbatar maki
Hajiya Maryam matukar kika bari auren Fadeel da Humaira ya afku toh ki tabbata
rushewar dukkan tubalin ginin da kika dauki tsawon lokaci kina ginawa zai
afku._*
WaΙannan maganganun na Babandi su ne suka Ζara assasa wutar
Ζiyayyar Fadeel a zuciyarta, har shi din waye? Me ya taka da zai iya Ιata mata Ιoyayyen
shirinta? Yau dai gashinan a sanadiyyar baΖin nacinsa ya soma maida mata hannun
agogo baya, ta soma fiddowa Abba ainahin kalar Maryam din da bai taΙa sani ba.
Daga sama ta ji muryar Abba.
"Ki faΙi Ζwakkwarar hujjarki koda kuwa guda Ιaya ne
tak, ni kuma idan na duba Ζarfinta na maki alΖawarin zan yi yanda kika ce koda
kuwa zan ji kunyar mutanen da bani da tamkarsu a yanzu wato iyayensa."
Kai tsaye ta ce.
"Saboda na yi mata miji, sannan ita kanta Humaira ba ta
sonsa."
Cikin Ιan haΙe gira Abba ya ce.
"Wannan biyun da kika lissafo ba su da matsuguni
Maryam, eh tabbas ke kike riΖe da Humaira kuma kin yi abin a jinjina maki kuma
a Ζara sonki dominsa kamar yanda wannan ya Ζara siya maki daraja da Ζima da ma
kauna a zuciyata, amma fa ki sani, ni ke da haΖΖin yiwa yarana zaΙin miji kaf
dinsu, soyayya kuma ina da tabbacin soyayyar da yaron ke yi gareta zai isa su
rayu cikin aminci da kyautatawa. Ina kuma da tabbacin in sha Allahu koda a baya
ta furta ba ta sonsa, a yanzun ko don irin halaccin da yake kan nuna mana shi
da iyayensa, ta sauko daga dokin..."
"Ka ga Yusuf ya ishe ni hakanan! Na rantse maka muddin
ba ka janye kudurin aurawa Fadeel Humaira ba ni Maryam ba zan Ζara kallonta da
idanun rahama ba saboda ka nunamin ba ni na haife ta ba kuma ban isa na zartar
da hukunci a kanta ba."
Ran Abba ya Ιaci, yau duniyar gaba daya ta yi masa Ζunci.
Wannan wane irin tashin hankali ne haka kuma daga wajen wacce bai taΙa zato ba,
wacce koyaushe sai dai ta kwantar masa da hankali idan ya shiga irin wannan
yanayin. Meke faruwa ne haka?
"Wace irin Ζiyayya kike yiwa Fadeel haka Maryama da har
kika kasa tankwara zuciyarki ki san da wanda kike magana?"
Mami ta kasa tankawa saboda Ιacin zuciya, ji take yi kamar
ta shaΖo wuyansa ta kashe shi ko ta huta da wannan zazzafar Ζiyayyar da ta
kwashi shekaru tana dannewa a ruhinta har sai da tura ta kai bango. Amma sai ta
zaΙi ta miΖe kawai ta fice ta bar masa dakin. Ranar dai haka suka kwana
kowannensu a Ιangarensa rai a Ιace. Ga Abba mamaki da al'ajabi ne suka lulluΙe
shi, to ma waye mijin da take ikrarin ta yiwa Humairar? Shi Ιacin rai ma bai sa
ya tambaya ba saboda bai ga amfanin tambayar da amsarta ba lallai ya aiwatar
ba. Ga Mami kuwa haka ta yi ta zarya a daki ga dare ya tsala babu damar kiran
Hajiya Lubna don kai mata kokenta balle kuma Babandi da take shakkar kira kar
ya Ζara sanar da ita wani abin shiga ruΙanin da fargaba. Don haka sai ta ci
alwashin sauyawa Humaira ko a fuska, a ganinta ko don kaunar da ta nuna mata a
baya zai sa zuciyar yarinyar ta russuna ta hakura da Fadeel ita kuma za ta yi
tunanin wanda ya dace ya yi daidai da Humairar su haΙa kafaΙa a wurin aure amma
ba tsara ko fiye ma da mazajen da yaranta ke aure ba.
***
Abba kuwa ya cika
alkawari domin duk da irin bacin ran da Mami ta Ζunsa mishi a daren jiya sai da
washegari ya wanki Ζafa bayan sanar da Yakubu mijin Futuha (wanda ya cilla
Abuja saboda yasan za a rina) ya yiwa gidan diyartasa tsinke tare da Mubarak da
ya yi masa jagoranci. Ya tarar da mata kusan su biyar cikin shiga ta alfarma
sai baza Ζamshi suke su na ta bugu amma ko gezau kamar babu rai a gidan. Ganin
dattijon mutum bai sa sun damu da gaida shi ba, gogaggun Ζ΄an duniya ne daga
kallo daya sai faman yatsina fuska suke ana taunar cingam har Ιaya na fadin
kodai ba nan ne gidan Futuhar Tiktok ba? Sunan da Abba ya ji sun fadi ya yi
matuΖar ba shi mamaki, wato dai Futuha har yanzu tana sharafinta a sosha midiya
kenan duk da ya hana? Mubarak kuwa da yake tun sadda zai yi jarrabawar karshe
ya raba kansa da soshal midiya ya sa ko bayan dawowarsa bai damu da leka Tiktok
ba kamar yanda bude buden status ba Ιabi'arsa ba ce hakan ya Ζara dalilin da
bai san me Futuhar ke shukawa ba.
Kai tsaye Abba ya kira ta a waya, ta amsa da murya ciki-ciki
don sosai Abban ke ba ta haushi. Ya ba ta umarnin lallai ta zo ta bude masa
Ζofa yana tsaye a bakin kyaurenta. Jin
haka hankalinta ya tashi, ga kuma matan Tiktok da suka yi cirko-cirko a gaban
gidanta su na jira ta bude, ta rasa uban wa ya ba su adireshin gidanta kuma
cikinsu har da Ζ³ar Snow don ta dauki muryarta ta kuma ji an ambaci sunanta.
Babu yanda ta iya hakanan ta bude kyauren cikin rawar jiki.
"Don ubanki shi ne kika shanya mu muna ta buga maki
Ζyauren gida? Lallai ai dole ki kasa buΙe mana Ζyauren saboda kin gama cika
shegen baki kin yi mana kurin gida. Toh bari mu shiga mu ga uwar dake cikin
gidan mu yiwa jama'a bidiyo."
Duk wannan zantukan na fitowa daga bakin Ζ³ar Snow kuma
kishiyarta mai zuwa, da kissa da kisisina ta samu Yakubu ya ba ta kwatancen
gidan da zummar za ta je taya ta murna.
Abba ya yi shiru ya kasa magana kamsa har wani sarawa yake
yi, wannan tashin hankalin har ina? Ζ³arka ta jawo an zageka a gaban idanunka?
Mubarak kuwa da ya zo wuya ya daka musu tsawa da ba su umarnin barin wajen tun suna shaida juna. Kasancewarsu tsageru
suka hau duramasa ashariya yayinda Ζ³ar Snow ta bude motarta ta shiga tana masa
zagi na uwa da uba, Abba ne ya dakatar da shi daga tankawa har suka ja motarsu
suka bar wajen. Futuha kuwa kuka sosai take yi, duk rashin kirki da mutuncinta
ba za ta so a zagi iyayenta ba. Yau gashinan sanadiyyarta an zage Abbanta tas a
kan idanunsa. Abba ya dago ya dubeta da idanunsa da suka kaΙa, sai kuma ya kada
kai ya juya ya nufi mota bayan ya ba Mubarak umarnin ya zo su wuce kar yace
mata komai saboda makwafta da kuma masu wucewa duk sun fito gulma har da matan
aure. Tun a hanya kirjin Abba ya yi wani irin nauyi da zafi, nan da nan kuwa idanunsa
suka soma kakkafewa hakan ya yi mugun tashin hankalin Mubarak kai tsaye ya nufi
asibiti da shi. Sai da aka shawo kansa ya dawo hayyacinsa kafin ya kira gida ya
sanar da Mami. Hankalinta ya tashi, ko babu komai duk da irin guma mata da ya
yi tana son abinta, dalilinsa ne ta aikata duk abin da ta aikata a rayuwa
hankali tashe ta sanar da mutan gidan ta yi shirin tafiya.
"Mami ina iya binku?"
Wani banzan kallo Humaira ta samu daga Mamin wanda ya kara
sanyata shan jinin jikinta amma tana ji a ranta duk runtsi duk wuya ba za ta
iya rayuwa babu Fadeel ba. Ta kara jinsa a rai musamman da ta yi istihara a kan
lamarinsa bisa shawarar shi kansa Fadeel din da ya kirata a daren ta kara jin ta samu nutsuwa da lamarinsa.
Wannan ya sa ta nufi dakinsu ta a hawayen ciwon Abba da addu'ar Allah ya tashi
kafaΙunsa.
A Ιaki kuma ta iske wani tashin hankalin, wato Ummita ce
cikin halin naΖuda, duk da ba ta san ya
ake haihuwa ba amma daga yanda ta ganta tana ta juyi da rike riken baya tana
kirarin mutuwa ya sa hankalinta ya yi mugun tashi. Babu wani abu da ya zo mata
a lokacin sai mafarkinta. Ta shiga kwala ihun kira amma ina! Gidan an watse an
tafi ga Abba don haka a guje ta fito zuwa sashen Anna neman Ιauki cikin rufewar
idanu saboda tsabar tashin hankali.
Tana shiga ta iske Annan tare da Jannat su na ta hirarsu
cikin yare. Ganin yanda ta faΙomusu sai da ta tsorata su. Cikin tsawa Jannat ta
ce.
"Baki da hankali ne za ki faΙo mana Ιaki ba sallama
babu komai?!"
Humaira ta durkusa a gabanta tana kuka.
"Don Allah ki taimaka mu kai Ummita asibiti, haihuwa
zata yi kar ta mutu."
Maganar ta Ιan shigi Jannat, ko babu komai Ummitar ta yi
mata bautar da wani a yaran Mamin bai mata ba, ta kuma fi Humaira yin biyayya a
gareta. Anna ta yatsine fuska.
"Ke har kin gane haihuwa ce za ta yi? A ina kika san
wata naΖuda? Watakila ma juyi ne."
Jannat ta dubi Anna cikin yare take ce mata ai Ummita
cikinta ya haura takwas, daga nan ta bi bayan Humaira bayan ta yafa mayafi
saman kanta da ko dankwali babu, Humaira dai da ta gaji da maganganunsu ne ta
kuma fitowa don tunanin kiran wayar Mamk da ya faΙo ranta.
"Ke! Ina za ki je? Muje ki taimaka mata ta fito, bari
na sanya a nemo mana abin hawa."
Tana kai wa nan ta fita farfajiyar gidan, motarta su Mami
sun wuce asibiti wurin Abba da ita. Dawud ta yi karo da shi wanda shigowarsa
kenan gidan bai ma san wainar da ake toyawa ba don wayarsa na kashe babu chaji.
"Yauwa maza nemo abin hawa Dawud, Ummita ke naΖuda yi
sauri."
Ai jin haka a gaggauce ya juya, can kuwa Humaira na kukan
halin ciwon da ta ga Ummita ciki ya zo ya kuma lafa mata kaΙan a haka ta daure
ta zuramata hijabi ta taimaka mata ta miΖe suka fito ko takalmi Ummita ta kasa
sanyawa sai salati take yi da kiran ta tuba a yafemata, Humaira ta nema mata
gafarar kowa da ta ke mu'amala da shi. Wannan ba Ζaramin tada hankalin Humaira ya
Ζara yi ba. Har sun shiga abin hawa Jannat ta maida ta tace ta dauko kayan da
aka haΙa na tarbar haihuwa, itama sai lokacin ta tuna. Mami ce ta haΙa komai ta
ajiye a Ιakinta saboda ba a son Ummita ta gani balle har damuwarta ya Ζara
ninkuwa. Da saurinta kuwa ta fita ta koma Ιakin Mamin tana lalube saboda tsabar
ruΙewa ba ta ma gan shi a gefen madubi ba a ajiye cikin karamin akwati,
dole sai Jannat ce ta je ta dauko bayan ta balbale Humaira da masifar ruΙewar
banzar da ta yi, acewarta.
A cikin Ιan sahun ma haka Ummita ta dinga salati da nanata
kalmar a nema mata yafiya har Jannat ta gaji ta ja tsaki wai ta fiye raki da
yawa. Dawud na gefe kusa da Ιan sahun shi kansa sai dai Ummita ta ba shi
tausayi ya ji dama haka haihuwar take? Tun su na tafe Jannat ta yi waya ta
sanar da Mami nan da nan ta ce su taho da ita asibitin da Abba yake don shima
ya warware kawai dai maganin bacci ne bai sake shi ba acewar likita yana
buΖatar hutu.
***
Gadan-gadan aka karΙi Ummita don har ta soma zubar da
ruwan naΖuda, gaba daya ahalin gidan hankalinsu tashe idan ka jira Jannat dake
ta chatting abinta. Tashin hankalin Mami bai wuce na fatan Allah yasa abin da
za a haifa ya mutu ko don ta huta da bibiyar da Wizzy yake mata musamman yanzu
da Ummita ta shiga watan haihuwar kusan koyaushe sai ya yi mata wani shegen
gajeran saΖo a whatsapp cewar KAR KI MANTA. Wannan kalaman su kadai yake ce
mata daga su ba ya Ζara koda harafi Ιaya. Ga Mubarak kuwa, babban burinsa
Ummita ta rayu kar ya rasa ta. Gaba daya ya kasa sukuni sai safa da marwa yake
yi, Raihana dai na gefe tana danna counter tana jan salati yayinda Humaira take
zaune shiru.
Kafin a kai ga fitowa a sanar musu ta haihu suka ji
kukan jariri ya karaΙe inda suke, nan da nan duk suka nufi Ζofar suka yi
cirko-cirko. Jimawa kaΙan Ιaya a cikin Nurses din dake ciki ta fito fuskarta a
sake tana kallonsu ta ce.
"Alhamdulillah, ta sauka lafiya an samu Ιa
namiji."
"Nos ya Ummitan?" Tambayar da Mubarak ya cilla
kenan.
"Tana cikin Ζoshin lafiya sai dai da alama Ζ΄ar shagwaΙa
ce sai kuka take mana tun bayan da ta haifo santalelan saurayin."
Wani guntun tsaki Jannat ta ja, su kuwa babu wanda ya ce
uffan kowa da kalar tunaninsa. Humaira dai ko ma mene ne, ko wane irin tabo ne
da yaron ita ta godewa Allah da har Ummita ta sauka lafiya ta kuma rabu da
cikin da ta tsana lafiya. Hakanan ma tunanin Raihana. Babban burinta na
kasancewar lafiya yar uwarta ta sauka.
Ga Mami kuwa ba su iya sun fahimci halin da ta ke ciki ba
sai dai ga dukkan alamu akwai wata damuwar da take ciki don gaba Ιaya fuskarta
ta nuna. Sun fi kyautata zaton kuma saboda lamarin haihuwar Ummita ne. Wa zai
yi murna da haihuwar Ιan da aka same shi ta fyaΙe? Babu shi kam, amma kaddara
ce babu yanda suka iya.
"Ku je gida zan zauna a wurinta. Ke Humaira ki yo mata
abu mai Ιan ruwa da zafi wanda za ta ci ki kawo."
Ba ta so tafiya ba tare da ta ga fuskar Ummita da ba amma
sai ta daure ta amsa da toh ganin kamar har a lokacin fushi sosai Mamin ke yi
da ita ba ta huce ba.
Bayan tafiyarsu idan ka dauke Mubarak da Mami ta kora don
dubo ko Abba ya farka, babu kowa a asibitin sai ita (Mamin). Tana zaune ta yi
shiru cikin tunani, toh yanzu idan ta kasance za ta kai wa Wizzy jaririn nan wa
za ta sanya wannan aiki? Kuma ma a ina za su haΙu? Ta dai san ba za ta taΙa iya
raba Ummita da abin da ta haifa a asibitin nan ba saboda babban asibiti ne kuma
mai tsaro sosai ga kyamarori (CCTV) ta ko'ina don haka sai ta zaΙi neman
shawarar abokiyar shawararta a ire-iren waΙannan gaΙoΙin. Wato Hajiya Lubna.
MiΖewa ta yi ta fice can farfajiyar asibitin ta danna mata kira, ringing hudu
ta Ιaga ana biyar. Ko sallamar da dama ba ta wani ΙaΙa su da Ζasa basu yi ba
Mami ta tare ta da sauri.
"Lubna ina cikin tashin hankali, ga dai yarinya ta
haihu an sami namiji amma kaina ya Ζulle. Yanda yarannan suka sanya idanu a kan
jaririn nan ta ina kuma ta wace hanya zan soma dauke shi na kai wa wancan Ιan
shegiyar?"
"Kai Maryam, wannan ai abu ne mai sauki duk kin bi kin
wani sanya ni fargaba. Kar ki yarda ki sanar da shi an haihu ki bari har sai an
kwana biyu yanda idanu ba zai dawo kanki ba. Duk lokacin da kika samu wata
wawakekiyar damar ba sai ki fiddo da shi ba ko da haΙin bakin wani amintaccen
ma'aikacinku ba? A Ιoye dai aka fitar da shi ni na tabbatar ba za a zargeki ba,
toh ke wa ma kike tunanin zai zargeki bayan wannan halin iya wuyar da kika
gwada musu a rayuwa tsawon zama?"
Sauke ajiyar zuciya Mamin ta yi na samun Ιan sauΖi daga
damuwarta.
"Shikenan, zan yi iyakar kokari na ganin bai samu
labarin ba zuwa lokacin da zan aiwatar da shirina."
Daga haka suka yi sallama bayan Hajiya Lubna ta Ζara jaddada
mata lallai ta yi kokarin aikata hakan ko ba komai Ζimar gidan nasu zai dawo
idan ya so sai su san me za su yi a gaba don cimma sauran manufofinsu wadanda
babu Ιigon alheri.
***
Dakyar Ummita ta iya tsaida kukanta, sun gyarata tas an kuma
yi mata sauyin Ιaki amman ko Ιaga kai ta kalli abin da ta haifa da ya
kwaso kamanninta tamkar an tsaga kara an karya ba ta yi ba. Ya yi kukan
har ya haΖura ya tura yatsa baki yana tsotsa a haka ya yi bacci.
Itama gajiya ta sanya bacci mai nauyi Ιaukarta. Koda
Mubarak ya shigo haka ya iske su, ita bacci jaririn ma haka. Fuskarta ta yi
wani fayau kuma ta Ιan sauka ba kamar Ιan kumburin da ta yi a fuskar ba kafin
ta haihu. Ya kai duba ga jaririn, kamannin da yaron ya yi da Ummitan sai ya ji
ya shiga ransa sosai. Tausayinsa kuma ya mamaye shi, ire-irensa su na nan
birjik a faΙin duniya waΙanda Ζaddarar samuwarsu ta hanyar da ba ta sunna ba ta
faΙamusu musamman ma a yanayi irin na Ummita ta hanyar fyaΙe. Amma hakan ba ya
wanke tabon da suka riga suka goga daga ubansu, sai a dauki tsangwamar duniya a
Ιora a kansu alhakin da ace son ransu ne su ma za su fi kwadayin a haifesu ta
hanyar aure. Ya Ζara kai duba ga Ummita, ya tabbata ko ganin jaririn ba ta son
yi saboda tsana, fatansa Allah yasa watarana zuciyar wannan Uwa ta russuna har
hakan ya jawo mata kaunar Ιanta. A hankali ya sa hannu ya Ιauki yaron ya yi
mishi addu'a har ma da yi mishi huΙuba bisa umarnin Abba wanda ya samu lafiya
bayan Mubarak din ya shaida masa abin da ke faruwa ya sanya shi yiwa yaron huΙuba
da suna Ahmad. Abba kuwa ya tsaya domin rama sallar da ta kubce masa.
Yana nan tsaye bayan ya shimfiΙa jaririn haka Mami ta shigo,
ganinsa a nan sai ta haΙe girar sama da ta Ζasa, ba ta son abin da zai sanya
Mubarak Ιin raΙar Ummita da ma abin da ya shafe ta gaba daya. So take kawai ya
tattata ya bar garin zuwa Camp kafin ya Ιallo mata wani abin da ba za ta iya Ιauka
ba.
"Kai kuma me kake yi anan?"
Ya dubi Ummita gudun kar Mami ta Ιaro wani batun har ta yi
sanadin tashinta daga bacci sai bai ce uffan ba ya juya ya fita, Mami ta Ιan
dubi inda suke kwance sannan ta juya ta rufe Ζofar ta bi bayansa. Ya sanar da
ita saΖon Abban da ma huΙubar da aka yiwa yaron da suna Ahmad.
"Sai kuma a rasa wanda zai yi sai kai? Meyasa zai yimin
haka? Ina ruwanka da sabgar yaron da ba a san asalinsa ba?"
Mamaki ya Ζume Mubarak.
"Mami, wai lafiya kwanaki biyun nan ranki duk a Ιace?
Haba Mami, don Allah ki bar faΙin hakan kada ki faΙa gaban Ummita abin babu
dadi."
Kamar ta kifa masa mari haka ya ji, shi kuwa sosai ransa ya Ιaci.
Ga damuwar da Futuha ta jefa Abbansu ciki ga kuma wannan haihuwa da ya tabbatar
za a sha daga da Ummita akan duk abin da ya shafi Ιan.
"Toh ubana, sai ka faΙamin abin da ya kamata da wanda
bai ma dace ba ka ga ai zan ji tunda kai ka haife ni. Mubarak tun muna mu biyu
ina mai Ζara gargadinka akan ka fita hanyar yarinyar nan ka kuma gaggauta cire
ta a zuciyarka don na rantse ni dai Maryam muddin ni na haifeka kai ma ba
shegen bane ba za ka taΙa aurenta ba."
Ya ji kansa ya yi wani irin sarawa, a duniya ko misΖala bai
taΙa fuskantar zai samu matsala daga Mami ba akan Ummita, ya fi tunanin
zantukan su Anna da Jannat ne ya sanya ta zama haka amma ba wani abu daban ba.
Madadin ya yi magana sai kawai ya ba ta hakuri ya bar wajen don ba ya so su haΙa
wata diramar a asibiti.
Da ficewarsa sai ga wayarta ta dauki Ζara, dubawar da za ta
yi ba kowa ba ne face Wizzy. Sai da ta yi taga-taga za ta fadi da sauri kuma ta
dafa Ζofar Ιakin. Ganin mutane a wajen sai ta yi tunanin shigewa dakin da
Ummita take, ta ji Nos ta ce za ta jima tana bacci wannan ya sa kanta tsaye
babu shakkar komai ta shiga amsa wayarta.
"Mene ne? Kiran na meye ka ke yimin? Ba nace maka kar
ka kuskura ka kirani har sai ta haihu ba?"
Ya yi Ζ΄ar dariya.
"Hajjaju kenan, kina tunanin za ki yanke alaΖa da ni da
wuri alhalin kina tare da abu mafi soyuwa a rayuwata? Ina! Ai ba zai yiwu ba,
koda ace yau gudan jinina ya fito a duniyarnan ki sani kin samu jikan da zai
kiraki da kaka ko da kuwa daga bangon duniya ne. Ni kiran da nayi shi ne, ya
ake ciki? Ina magana a whatsapp sai wani you no care kike nunamin, to idan ba
so kike nayi eh yane ba wato na yi dirar mikiya a gidan ki gaggauta sanar da ni
halin da ake ciki. Ta fesar da cikin ko kuwa ya na nan a dunΖule?"
Wani irin zufa ya karyowa Mami. Ta ji hatta da jikinta ya Ιau
rawa, ta juya inda Ummita ke kwance ganin ta Ιan motsa ya sanya da sauri ta
bude Ζofar ta fita ba ta ce masa uffan ba har sai da ta Ζarasa ficewa zuwa
farfajiyar asibitin.
A Ιangare Ummita kuwa, tsaf ta ji muryar Mami tana yiwa
abokin wayarta magana akan me zai kirata, sai dai ko alama ba ta tsinkayi abin
da ya ce ba. Motsin da ta yi na farkawa tana kokarin tashi ya sanya Mamin
ficewa a dakin, ta buΙe idanunta tarr ga wani jiri dake kwasarta daga kwance
tsabar yunwa. Tunanin maganganun Mamin take son yi amma lokaci guda kukan da
jaririn dake gefenta ya tsala ya sanya ta dan karkata kai ta kalleshi. Kallo na
Ζurillah, burinta ta hango kamannin Ubansa ko ta samu shaidar da za ta nuna
domin a binciko inda yake a cafke shi, sai dai kuma ban da su din waye ya taΙa
ganinsa? Kukan yake yi tana jin wani iri a zuciyarta, yanayin da ba ta taΙa
hangensa akan yaron ba yana zuwar mata a sannu sannu. Ta kasa miΖewa zaune
balle ta samu damar kai masa tallafi a haka su Humaira suka shigo Ιakin suka
risΖeta. Ganinsu sai ya sanya ta komawa ta kwanta sai kawai ta soma kuka a
hankali, da sauri Raihana ta Ζarasa ta Ι an rungume ta tana kokarin maida
Ζwallar da ta cika mata idanu.
"Ya isa hakanan don Allah. Kiyi hakuri tunda Allah ya
raba lafiya yar uwa."
Humaira kuwa sai ta ajiye kwandon kayayyakin da suka taho da
su ta shiga haΙa mata bisa umarnin Mami da suka yi karo da ita za ta fice da
waya a kunne, ta dai katse kiran ta musu magana kusan ba a nutse ba sannan ta
sa kai ta karasa ficewa zuwa farfajiyar, su kuwa suka yo ciki. Raihana ta saki
Ummita ta karasa ga Bebin da ya Ιan jinkirta da kukan ta Ιauke shi ta zuba masa
idanu. Can kuma ta kalli Ummita, kamar ta ce kun yi kama sai kuma ta ji tsoron
kar ta ji haushinta. A haka aka kwankwasa kofar dakin da sallama suka amsa aka
shigo, Baba Amina ce Ζanwar Abba sai ko Abban da kansa a bayansa kuma
Mubarak. Abban da kansa ya yi kiranta ya sanar da ita zancen haihuwar wannan ya
yi silar zuwanta. Ita ta taimakawa Ummita ta sha shayin ta ci abinci kadan, anan
kuma Abban da ita suka hadu wajen yiwa Ummita nasiha da nunamata muhimmancin
yarda da Ζaddara. Sosai kuma maganganunsu suka shige ta, sai anan ma take ji
Mamin ta je gida ta dawo a bakin Abba. Bayan fitar su Abban da Mubarak ne kuma
Baba Amina ta zage wajen taimaka mata ta yi wanka ta shirya tsaf, shima yaron
ta wanke shi ta sanya mishi sabbin sutura, wankewar da ya sanya kamannin
mahaifiyarsa ya Ζara bayyana muraran a fuskarsa hatta da Ιan baΖin tabon da
Ummita keda ahi a gefen kumatunta haka jariri Ahmad ma. Ta yi ta satar kallonsa
cike da sha'awa ga wata iriyar Ζauna da ta yiwa zuciyarta Ζawanya. Ba zato ta
ji Baba Amina ta miΖa mata shi har ya kusan faΙuwa ba don Allah ya sa ta tarba
da hannunta ba.
"Daure kiyi hakuri ki ba shi ya sha Ummi, in sha Allahu
wataran zai zamo maki abin alfahari. Kar ki duba hanyar da kika same shi, kiyi
hakuri ki yarda wannan wata jarrabawarki ce da ba ki isa kin kufce mata ba.
Watarana sai labari da yardar Allah."
Kwalla suka cicciko mata, nan Baba Amina ta taimaka mata
yaron kuwa ya cafka ya soma tsotso kamar zai tsige mata fata, haka yana sha
tana jin wani irin ciwo a mara ga zafin fisgar da yake yi har hawaye ta soma
tana jujjuya kai. Humaira da ta zuba musu idanu sai Ζarar wayarta ta katse ta.
Ganin sunan Fadeel na yawo saman screen ya sanya ta fita a dakin fuskar dauke
da Ζaramin murmushi. Da sallama ta Ιaga wayar, ya amsa mata a sake.
"Boddona wato idan Fadeel ayyuka suka hana shi kiranki,
ba za ki dauki waya ki kirashi ba ko?"
Ζ³ar dariya ta yi kaΙan da har ya tsinkayo sautinta, ita sau
da dama yanayin shagwaΙar da muryar da Fadeel kan yi mata na ba ta mamaki da
kuma dariya, shi dai a lallai ta ji tausayinsa koyaushe.
"Oh, dariya ma na baki? Toh aikuwa yanzu zan bar dukkan
abin da nake yi ki gan ni da yammacin nan."
Ta dan rausaya idanu kaΙan tana murmushi.
"Ka yi hakuri toh, ni ba na ma gida, Ummita ta sauka
lafiya muna asibiti."
"Allah Sarki, me aka samu?"
Da sanyin jikin tausayawa yaro Ahmad ta amsa.
"Namiji ne, an masa huΙuba da Ahmad."
Ya yi addu'ar fatan alheri gareshi kafin kuma ya Ζara
kwantar mata da hankali da nunamata su ne suke kusa da ita, su kasance masu jarumta su dinga
Ζarfafa mata gwuiwa. Kamar dai sun haΙa baki da Baba Amina, haka ya yi ta yiwa
Humaira nasiha. Hakan ya sanya tsantsar so da kaunarsa wadanda ba ta san
mafarinsu ba suka shiga ratsa ta sosai. Ya karashe zancen da fadin.
"Yauwa, kuma bana son kina yin asarar hawayenki
musamman da yake bana kusa."
Ta Ιan russunar da idanun kamar yana kallonta saboda jin
nauyin maganarsa.
"Bari na kyaleki ma yi magana anjima in sha
Allah."
"Toh, na gode a gaida mutan gidan."
"Zasu ji, nace ba?"
"Naam?" Ta amsa gami da tattara nutsuwarta don a
sautinsa ya nuna ko ma mene zai fadi nada matukar muhimmanci.
"Ina matuΖar kaunarki."
Sai ta sauke ajiyar zuciya har tana jin tsikar jikinta na
miΖewa, tana son furta masa ita din ma hakan ce a wajenta amma wani kunya ya
hanata aikatawa. Sai kawai ta ji Ιif ya yanke kiran. Ta numfasa kafin ta ja
Ζafafunta zuwa ciki duniyar na mata wani irin dadi ga kaunar Fadeel dake Ζara
tsuma ta.
***
A Ιangaren Fadeel kuwa, ajiye wayar ya yi jikinsa duk a
mace saboda shauki da kewar Humaira da
ya mamaye shi lokaci guda, har yanzun yana
shakkar kada wani abu ya sauya zuciyarta daga gareshi, sati ukun da
kwanakin da suka yi saura jinsu yake tamkar shekaru duk kuwa da cewar a zahiri
ga Ibb na ta faman tashi faΙi wurin ganin an haΙa dukkan abin da ya dace
dangane da lefe da ma kuma list na wadanda zasu gayyata. Fadeel din shima sosai
ya maida hankali ga ginin gidansa wanda an kammala komai sai kayayyakin furniture
da yake sanyawa don alΖawari ne ya daukarwa kansa da yardar Allah sai dai
Humaira kawai ta shigo gidansa amma ba ya bukatar a yi mishi hidimar da babu
wanda zai mora sai shi sai kuma matarsa. Ita din yake so da kauna ba komai ba.
A wannan lokacin ma zaune yake a falon Ibb din wanda yake
amsa wayar Daddy, ya yi shiru cikin tunanin Humaira yana mai murmushi idanun a
rufe ruf. Ba zato ya ji an wurgo mishi filo, ba kowa ba ne sai Ibb.
"Allah ya sauwaΖe maka kai kam Romeo. Ina ce shirin
aurenka ake yi da yarinyar nan? Toh mene ne kuma na wannan dogon tunanin kamar
ba yanzu ku ka gama waya da junanku ba?"
Fadeel wanda tun jifa da filon ya wartsake, Ιan harara ya
wurga masa.
"Toh sannu, kai me za a kiraka idan ka kira ni da
Romeo? Mutumin da hatta da gabatar da lakca ba ta hana shi amsa wayar Madam
kamar ba daga gidan ka fito ba."
Murmushi Ibb ya yi kaΙan.
"Ni yanzu ba wannan ba, ya ake ciki kai da mutuniyar
taka?"
Shi din ma Fadeel martanin murmushin ya maida masa gami da
kwantar da kai jikin kujera.
"Alhamdulillah, akwai cigaba kwarai ba kamar baya ba.
Kai ba ka ga alamu ba?"
Jinjina kai Ibb ya yi.
"Na gani tabbas. Amma ba anan gizo ke saΖar ba, mu dai
fatan Allah yasa ba Ιangare guda ke so ba."
"Ina da yaΖini da tabbacin yanzu tana sona, sai dai ta
kasa furtawa ne saboda dalilinta. Kai ni koda babu son daga fanninta, zan koyar
da ita na tarbiyyantar da ita soyayyata. Har yanzu kana tantamar irin kaunar da
nake yi mata wai?"
Ibb na Ζ΄ar dariya ya girgiza kai.
"Ko kusa, na san ai kai tuni ta shafe babin kowace mace
a zuciyarka. Hakan nada kyau. Allah dai ya sanya alheri."
Fadeel ya amsa yana sannan ya sanar da shi haihuwar Ummita.
Sosai Ibb ya tausaya mata.
"Ya ake ciki batun binciken can?"
Ζan yarfa hannu ya yi.
"I dnt know, ban yi waya da shi ba, kuma bai kirani ba.
Amma a satin da ya wuce ya bani tabbacin da alamun nasara don suna bincike akan
accounts din da aka bude na whatsapp da instagram har da facebook da sunan
Feedy Baby. Ya kuma ce an soma samun bayanai akan ta don ba ta rufe akawun din
ba na instagram ta cigaba da amfani da shi a Ιoye, hakanan whatsapp, yanzu dai
su na monitoring kowane motsinta."
Ibb ya yi fatan nasara, haka suka yi ta tattaunawa har dai
Salma ta shigo ta sanar musu abinci ya kammala wannan ya katse su suka miΖe.
***
Mami gaba daya ba a
nutse take ba, Wizzy ya jaddada mata cewar sai ya dauki fansa a kanta ko kuma
ya tona mata asiri matuΖar ta hana shi gudan jininsa saboda yana tambayarta ko
an haihu ko aa ta yi mishi ihun ya rabi da ita babu ruwansa. Wannan ne shima ya
fusata shi har ya kaifafa harshe a kanta ya yi mata munanan kalamai. A karshe
dai dole haka ta bar asibitin ta kkma gida don samun damar yin tufka da
warwara.
***
Ummita kuwa kwanansu Ιaya aka sallamo ta. Ko ta ya ya? Oho,
sai ga makwafta na Ιullowa ganin jariri, aka rasa wanda ya sanar da su. Jannat
kuwa ko dakin su Ummitan ba ta shiga. Tasleem zuwanta daya ta koma, dalilin
jego ne ya sanya Abba bai yi mata faΙan rashin nuna kulawa ga Ζ΄ar uwarta ba.
Ita kuwa Futuha Abba ya yi rantsuwar kada ta sake a nan kusa ya ga Ζafafunta a
gidansa, kuma ya tabbatar mata muddin ba ta goge dukkanin shafukanta na kan
yanar gizo ba zai saΙa mata. Dolenta babu yanda ta iya duk da irin tara jama'ar
da ta yi a kafafen musamman Tiktok hakanan ta shafe su don Mubarak na lurar wa
Abba ko ta aiwatar ko a'a.
Anti Maijidda ta zo bayan Ummita ta cika sati da haihuwa, ta
Ιan ji dadi ganin yanda ta kwantar da hankalinta ta ke kuma ba yaron kulawa,
idan an ce mata kafin haihuwar za ta yi haka ba za ta yarda ba. A ranar Anti
Maijidda ta tattara ta bar gidan domin ta rantse ba za ta kwana a gidan da Mami
ke cikinsa ba.
***
Mami ce zaune a falon Abba cikin amsa kiran da ya yi mata
don su yi magana mai muhimmanci.
"Ina sauraronka." Ta yi furucin ciki-ciki, tun
sadda Abban ya ce ba zai taΙa hana Fadeel auren Humaira ba ta ke jin haushinsa
ga uwa uba takurar da ya soma yiwa yaranta. Babu dama Yassar ya kai sha biyu a
waje sai ya bude masa wuta kamar ya ari baki, wai ina yake samun kudaden da har
yake shigar tsadaddun kaya yake yawon fita taΙi? Ga Futuha da gaba daya ya yi
mata geji da gidansa, hakanan Dawud shi ma ya hana shi mu'amala da wasu
abokansa Ιata gari. Ζassim kuwa koyaushe yana gidan makwafta wurin abokansa yaran
gidan, haka zasu ja shi yawo wuraren shaΖatawa iri iri na masu kudi a yi ta
kashe masa kudade yana shigar kece raini, a yau din ma ganinsu da Abban ya yi
da matasan gidan uku wadanda aka yiwa tambari marar kyau har ana zarginsu da
shaye shaye da abubuwa barkatai, Abban har marinsa ya yi a gaban Mamin, wannan
ma ya taΙa zuciyarta kaca-kaca don haka take cika da batsewa Ζiris ya rage ta
fashe.
Ga Abba kuwa bai damu da yanayin dake saman fuskarta ba ya
soma magana.
"Sanin kanki ne auren Mamana ya zo sai dai yanayin da
muke ciki ya hana a yi abin da ya kamata na shirye-shirye, ita dai a satinnan
za ta je Nijar ta yi musu sallamar aure, iyayen yaron da shi kansa sun jaddada
min ba sa buΖatar koda tsinke daga wajenmu, za su yi mata komai na gidan aure
iyaka a kai musu ita amma matsayinmu na masu mutunci ba zamu naΙe hannuwa hakan
ta kasance ba, ko ya ya mu yi mata wasu kayayyakin kamar daga na kicin da dai
sauransu. Ku ne mata, kun fi sanin abin da ya kamata a yi. Abu na gaba kuma
Ζarshen satin nan mai kamawa za su kawo lefe."
Zantukan suka shiga tafarfasa zuciyar Mami, ji take yi
tamkar ta yi fiffike ta dira a jikin Abba ta shaΖe wuyansa har lahira. Daukaka
dai Ιaukaka wanda ta sani shi ne abin da ya iso rayuwar Humaira? Toh wai tana
mene ne haka? Kai jama'a.
"Da sake!"
Ta furta a fili tana wani irin tsuma kamar na zakanyar da ta
wuni ta kwana ba ta ci ba. Abba cikin rashin fahimta da yi mata uzurin Ιacin
ran da take tattare da shi a yinin ranar ya sanya shi kai zuciya nesa ya
jefamata tambaya.
"Ban fahimceki ba."
Ta dube shi tsakar ido, fuskarta muraran ta bayyana abin da
ke cin zuciyarta murya a sama ta ce.
"Eh nace da sake! Ba za ta saΙu ba wallahi! Muddin ina
raye ba zan bari Humaira ta auri dan iskan yaron nan ba mazinaci!"
Kalmar mazinaci ta yi matukar girgiza Abba har sai da ya ji
wata iriyar faΙuwar gaba. Salati ya yi da karfi yana nuna Mami da yatsa dake
kakkarwa.
"Maryama ki tsoraci Allah, kar tsanar yaron nan ya kai
ki da daukar hakkinsa? A ina kika gani da idanunki yana aikata zina? Wai
Maryama meke damunki? Wannan sauyin da kike nunawa na menene?"
Ta Ιan yi jim tana girgiza Ζafafa kamar ta karya ta, so take
ta ce masa sauyin na ubanka da uwarka ne amma kuma tana tanΖwasar kanta gudun
lalacewar aikin shekara da shekaru, don haka sai ta rasa mafita, bakinta kuma
ya Ιinke, kawai sai ta fashe masa da kuma.
Humaira dake tsaye a Ζofa riΖe da jug wanda ta yiwa Abba
lemun cittar da ya sanya ta, tun sadda Mami ta soma ambaton kalmar Da Sake!
Take tsaye kamar an Ιaure mata Ζafafunta ta kasa motsawa. Komai ya shiga
kunnuwanta hatta da kiran Fadeel mazinaci da Mami ta yi. A yau Ιaya kuma karo
na farko da ta ji a ranta Mami ta ba ta haushi dagasken gaske.
'Mami lokacin da aka nunawa abu tsana, lokacin zuciyata take
tafarfasa saboda kaunarsa. Kiyi hakuri, Fadeel koda mazinaci ne zan jure
tarayya da shi, ballantana kuma zuciya da ruhina su na karyata kalamanki
gareshi.'
Wannan duk zantukan zuci ne da Humaira ke yi lokacin da ta
juya ta soma tafiya da nufin maida haΙin firij har zuwa sadda za su kammala
tattaunawa. Haka ta koma Ιakinsu zuciyarta a Ιace, Raihana da Ummita da kuma
Sa'ade bazawarar Ιiyar Baba Amina dake kula da Ummita suka zubamata idanu.
"Lafiya Humaira?" Har su na haΙa baki wajen
tambayar, sai kawa ta girgiza musu kai da murmushin yaΖe bayan ta yi dabarar
dauke ruwan hawayen da ke kokarin zubomata.
"Ba komai."
"Haba Amarsu, tun ma ba'a yi komai ba?"
Fadin Raihana cikin son kawar mata da damuwa da bagarar da
zancen. Su Ummita suka Ιan dara. Ita dai ban da murmushin dole babu abin da ke
saman fuskarta.
***
Mami kuwa sosai suka fafata da Abba don ta rantse ita dai ba
zaa yi auren ba, wannan ya sa Abba ransa Ιaci suka samu mummunan saΙanin da har
sai da ya kira Baba Amina a waya da zummar ta zo ya sanya ta hidimar auren
Humaira. A cewarsa shima yana da Ζ΄ar uwa.
Mami ta wuce dakinta a fusace ta rufe ruf, kanta take duba
ta madubi ta yi kwafa.
"Lokacin da za ka mutu yarana su mallaki arzikinka ya
yi Yusuf. Idan har tsafi gaskiya ne sai na kashe ka."
Ta furta a kaifafe.
***
Mami ta ga abin na Abba dagaske ne, a gefe ga Humaira dake
shirye-shiryen tafiya Nijar sai Ιoki take yi saboda tsabar jimawar da ta yi ba
ta je ba. Abba kuwa kamar yanda ya ce ne, Baba Amina ya kira suka yi magana ya
ba ta ragamar siyayyar kayan kicin wanda a farko ta nuna sam ita ba za'a yi
haka ba idan an yi ba'a yiwa Mami adalci ba. Sai da Abban ya Ιata rai ya
zayyane mata yanda suka yi, da kanta ta samu Mamin da zancen amma Mami ta buΙe
mata wuta da zummar babu abin da ya shafe ta da auren Humaira da Fadeel. Jiki a
mace da kuma Ιumbin mamaki Baba Amina ta dawo a dole ta karΙi wannan ragamar ta
kuma taushi Abban akan ya yi mata uzuri tunda hakan ba ta taΙa faruwa
tsakaninta da yaran riΖonnata ba.
Humaira kuwa sosai Mami ta dauke mata wuta, gaisuwarta ciki
ciki take amsawa, hakanan ko tsinke ta bar sa Humaira dauke mata balle ta sanya
ta aiki. Raihana da Ummita lamarin duka ya dame su. Humaira ma tana jin zafin
hakan, duk ta bi ta rame amma ba ta jin za ta iya yiwa Mami alfarmar rabuwa da
Fadeel alhalin ba ta da kwakkwarar dalili ba. Idan har a yau ta yi yanda Mamin
ke so tana da tabbacin alhakin Fadeel sai ya kama ta. Ba kuma za ta taΙa samun
rayuwar jin dadi da walwala ba a duniyarta.
A yau ma tana zaune tana gyara kayanta cikin jaka tana
yi tana sauraron Raihana da Ummita dake faman zantawa akan lefen da za'a kawo
washegari wanda ita kuwa ana kawowa da kwana Ιaya za ta wuce Nijar. Ba ta ce
musu uffan ba, sai bayan fitar Raihana ne Ummita ta dube ta.
"Ya kamata ki je ki sami Mami kuyi magana Humaira. Haka
za ki tafi tana fushi da ke?"
Ta ajiye set din kayan da take shirin sakawa a akwati a
saman cinyarta bayan ta zauna gefen gadon jiki a sanyaye.
"Toh ya zan yi Ummita? Kina gani fa Mami ko gaisuwata
ba ta amsawa."
Ummita ta girgiza kai.
"Hakanan za ki mayar da komai ba komai ba ki je ki kara
ba ta hakuri ki lallaΙa ta. Mun yi mata uzuri saboda sanin da muka yi cewar
kowane DAN ADAM ajizi ne. Mu kara yi mata mu gani."
Sauke nannauyan ajiyar zuciya ta yi.
*"Shikenan, bari na je na gani ko za ta saurare
ni."
Ζan murmushi Ummita ta sakar mata na karfafa gwuiwa. Wannan
ya sanya ta mikewa ta nufi dakin Mami. Ta shiga da sallama a bakinta amma babu
amsa, don ta tabbatar ko ba ta dakin ne ya sanya ta Ιaga labule ta shiga. Mamin
hankali kwance tana zaune gefen gado sai faman danna wayar hannunta take. Abin
bai ba Humaira mamaki ba, ko ba komai zuwa yanzu dama ya ci ace ta saba da
hakan. Don haka ta daure ta karasa ta durkusa a gefe, Mami kuwa tun shigowarta
ba ta ko kalleta ba sai ma fuskarta da ta tamke tamkar hadari ya haΙo.
"Mami ina sane da cewa har yanzu kina fushi da ni, na
zo ne domin na Ζara ba ki haΖuri akand laifin da ban san na aikata ba."
Wani kallo ta Ιago ta watsa mata wanda ya sa Humaira
sunkuyar da kai gami da yin shiru.
"Kin zo ne don ki nunamin ke din ba ki da mutunci kuma
butulu ce?"
Jin haka sai abin ya daure mata kai.
"Mami har ga Allah ban san taΖamaiman laifin da nayi
ba."
"Dakyau! Ai idan ba ki yimin wannan butulcin ba, ba ki
cika Ιiyar Fatima ba."
Maganar ta daki zuciyar Humaira da har sai da ta Ζara buΙe
idanunta wurin kallonta sosai. Mami me yawan yabon halayen Mahaifiyarta, yau
kuma ita ce saboda son zuciya irin nata ta ke kushe ta?
"Kiyi hakuri Mami, kiyi hakuri idan har da abin da na
maki mai zafi amma domin Allah kada laifina ya ture kyawawan yabon da
Mahaifiyata ta samu a wurinki. Babu abin da take buΖata a wurinmu face fatan
alheri."
Muguwar harara ta watsa mata, kamar ta ce fatan alherin
uwarki sai kuma ta danne zuciyarta dakyar.
"_Kar ki yi saurin rushe komai don ba alheri ne gareki
ba._ _Nace maki mu bi komai sannu har mu cimma gaci._ _Aure dai ki kwantar da
hankalinki ba zai faru ba kamar yadda Babandi ya tabbatar mana._"
Maganganun Hajiya Lubna ke yawo a ΖoΖon ranta, don haka sai
ta yiwa Humaira nuni da Ζofa.
"Ficemin a Ιaki tun ban kwaΙa maki mari ba. Ke har kin
kai ki faΙamin abin da ya dace da ma wanda bai kamata ba? Ko kin ga ni Maryam
na shiga shirgin aurenki da wancan lalataccen? Toh kamar yanda ban shiga ba ki
je can ku Ζarata ke da shi, ai kowa ya san abin da za ku aura daga ke har
shi."
Ζan shiru Humaira ta yi tana nanata kalaman Ζarshe na Mamin
a zuciyarta idanunta kuwa Ζurr a kanta, to me take nufi? Gaba daya ta kasa
fahimtar manufarta da kuma inda ta dosa. Sai da Mamin ta yi mata wata tsawa kan
ta fice mata a Ιaki sannan ta miΖe gwuiwa a matukar sanyaye ta fita tana fidda
hawayen bakin ciki. Tunanin ba Ummita kadai ce a Ιakin ba saboda lokacin yi
mata wanka ya yi sai kawai ta shige kicin ta zauna tana kuka sosai. Tana kara
gasΖata cewa dai wasu sabbin halayyar Mamin da ba ta sani bane suke bayyana a
muraran. Lallai ta fara shaΖar Ζamshin gaskiya a kalaman Anti Maijidda, za kuma
ta so tasan ko menene ta sani akan Mamin har ta kasa aminta da zuciya Ιaya take
zaune da Ummita da ma ita kanta. Sai da ta kammala kukanta ta share hawaye ta
koma sashinsa bayan ta wanke fuska amma ina, duk da haka Ummita da Raihana dake
zaune riΖe da Ahmad a hannu wanda ya sha wanka suka fahimci akwai ta yi kuka
sakamakon sauyin da fuskarta ta yi.
"Lafiya Humaira?
Me aka yi? Kin bar waya tun Ιazu angonnaki ke faman kira."
Ta yi murmushin yaΖe kafin ta amsawa Raihana.
"Babu komai, ina wayar?"
Ta miΖa mata tana mai Ζara jefamata tambaya don ita sam ba
ta yarda ba, a Ζarshe ta ce.
"Mami ce ko? Don nasan ba kya shiga sashin Anna balle
nayi tunanin ko..af ko kin haΙu da Anti Jannat ne? Ba ta jima da fita a
dakinnan ba ko kun haΙu?"
"Ke dai Raihana ko ma wacece kuma ko mene ne tunda dai
ya faru ba shikenan ba?"
Ta Ιan yatsine fuska.
"Allah ya kyauta dai." Ummita ta amsa da amin. Sai
da Raihana ta bar wurin ne ta kwashe duka yadda suka yi da Mamin ta sanar mata.
Ummita yarinya mai kaifin basira da kwakwalwa tsaf ta fahimci manufar zantukan
Mami amma sai ta Ιoye ga Humaira duk kuwa tana tunanin watakila itama ta
fahimta kawai dai ba ta son fassara zancen yanda zai yi mata Ζuna a zuciya ne.
***
Washegari kuwa ya kama ranar
da za'a kawo lefen Humaira, tun safe Baba Amina ta iso sai shiri take yi
don ma dai an ce maza ne za su kawo. Mami kuwa sai cin magani take yi ta Ζi
kula koda gaisuwar Baba Amina balle ta sa ran samun maganar arziki. Raihana ya
je makaranta don sun soma zane jarrabawa, su Muhsin ma duka ba sa nan. Mami ce
zaune a galo sai Baba Amina a gefe ita da Jannat wacce duka ranta a Ιace yake
sakamakon wayar da ta kammala da mijinta da ya rufe ta da faΙan lallai ta dawo
kda ta Ζara koda kwana Ιaya don tare zasu yo Ζaura zuwa Nijeriya baki daya amma
firr ta Ζi saboda bikin Humaira da ya tsaya mata a rai, burinta ta ga tsiyar da
za a kawomata ga aikin da bokanta ya bayar take son aiwatarwa akan Humairar
wanda zai sa ko bayan aurenta da Fadeel ta kasa samun kwanciyar hankali a
gidansa, an tabbatar mata auren babu fashi hakan ya sa ta Ιullo da wata hanya
daban na musguna mata duka don ta faranta ran Tasleem dake haukar son Fadeel
amma ba ta samu aurensa ba. Kayan Humaira kawai za ta dauko saiti Ιaya ta kawo
masa ya yi aikin da idan har ta sake ta yi amfani da kayan za ta tsani zaman
gida kullum tana hanyar gantali koda kuwa ba za ta aikata wani shirme na banza
ba. Tana da tabbacin muddin aikin ya ci toh fa Fadeel da ma yan uwansa za su
tsane ta kuma ya rabu da ita.
Suna nan zaune Mami da Jannat sun cika sun yi fam saboda
Baba Amina dake kiran wayar sauran yan uwan Abban da ba su Ζaraso gidan ba akan
su yi da jiki an kusa. A haka wayar Mami ta dauki Ζara, dubawar da za ta yi ba
kowa ba ne sai Wizzy, ta dan saci kallon Jannat dake gefenta, ganin hankalinta
na ga waya tana dannawa ya sanya da sauri ta mike ta shige Ιaki ta rufe kafin
ta sa wayar a kunne. Cikin kwantar da murya kamar ba Mami ba take magana.
"Haba Wizzy, meyasa kake son yimin azarΙaΙi a lamura
ne? Ban fadamaka ka kwantar da hankalinka a soma sabgar biki ba idan ya so sai
na sato maka shi na kawomaka?"
A kausashe ya ce.
"Ke Hajiya kina fa kawomin rainin hankali iri-iri, sai
wani hankadomin hotunan yaro kike yi kina sanya soyayyarsa samun matsuguni a
zuciyata toh kuma don me za ki wani ja min lokaci don za'a yi bikin Ζ΄ar dabar
da ta kusa kashe ni?"
Ta dan goge zufar goshin da ya karyo mata tana mai sauke
ajiyar zuciya.
"Ka dai yi hakuri, ni ai Maryam ba na daukarwa mutum
alΖawarin da na san cewa ba zan iya cika shi ba. Ka kara hakuri zuwa lokacin
komai zai tafi yadda kake so."
"Shikenan! Kin ci darajar jikanki da na nunamaki ko ni Ιin
waye. Zan ba ki daga nan har sati uku."
"Babu damuwa. Amma don Allah ka bar kokarin kira koda
ta whatsapp din ne, ka dinga hakurin na yi maka magana."
Ya yi wata shegiyar dariyar shaΖiyanci.
"Shikenan amma dai yanzu ki je ki daukarmin sabon hoton
yarona ki turo na gani. Kar ki turon kala Ιaya."
Ta ja guntun tsakin da take da tabbacin ba zai shiga
kunnuwansa ba sannan ta amsa da ta ji. Bayan sun ajiye wayar ta soma jin
haushin kanta, ko ta yaya za ta shiga yiwa yaron hoto, wannan yawan hoton da
take yi har Ummitan kan iya gano wani abin muddin dai ba ta yi da gaske ba.
Yarinyar akwai kaifin tunanin. Ta dai yi shahada ta fito zuwa dakin. Ba ta ko
dubi Jannat ba da ma wasu baΖin da suka shigo ta nufi wurin Ummita.
Ummita ta tarar ita
Ιaya adalilin fitar da Humaira ta yi bisa rakiyar Raihana zuwa kasuwa siyayyar
tsarabar da za ta kai Nijar, motar Abba ta kai su. Ganinta sai Ummita ta Ιan
saki fuska. Kuka yake ta yi tana tsaye tana faman jijjiga shi ya Ζi yin shiru.
"Ya aka yi me
ya same shi haka yake kuka?"
"Nima ban sani ba Mami, tun Ιazu ya Ζi ya yi
shiru."
Mami ta sa hannu ta karΙe shi.
"Ina madararsa?"
Kasancewar Abba ya siyo madarar gwangwani biaa shawarar Baba
Amina tun a farko don ta ce nonon ba ya isar sa. Ta Ζarasa wajen feeder da ta
haΙa madarar ciki saboda zafi sai ta sanya a kofi mai dauke da ruwan sanyi ta
bar shi ta miΖawa Mamin haΙe da bif na sanyawa a wuya gudun Ιata jiki. Mamin ta
shiga ba shi tana dan murmushin da bai kai zuci ba, can a Ζasan ranta ban da
tsinuwa babu abin da take jifan Wizzy da shi. A cewarta duk shi ne ya cuce ta.
Ummita ko ta yi shiru kawai amma jikinta ya yi sanyi, hakanan ta ji ba ta
aminta da wannan kulawar daga Mami ba, Mamin da ko kallon arziki ba ta fiye bin
Ahmad din da shi ba duka saboda ganin da ta yi tamkar Ιanta na soyayya da ita
Ummitan. Wannan sabon sauyi da kuma hoton da ta ke dagewa wurin yiwa yaron sai
yake Ζulle mata kai. Na farko dai Mamin ko status ba ta taΙa Ιorawa ba na yaron
hakanan ba ta ga wani ko wata da Mamin za ta aikawa hoton ba balle har a kai ga
Ιauka.
Haka ta yi ta saΖe-saΖen zuci, can dai ta miΖe zuwa bandaki
sanadin fitsarin da ya matso ta, koda ta fito hoton dai ta tarar Mamin na Ιaukar
Ahmad, tana ganinta kuma sai ta wayance ta hanyar nunamata hoton.
"Kinga wannan Ιa wato ya san Camera, ya yi Ζuri yana
kallo kai kace ya san hoton za'a yi."
Ta dan yi Ζ΄ar dariyar yaΖe amma ba ta ce uffan ba. Can kuma
kamar an mintsili Mamin ta miΖe tsaye sannan ta miΖawa Ummita yaron.
"Maza sanya shi a kafaΙa ya yi gyatsa. Ni bari naje
daki naga wadannan Ζ΄an karΙar lefen sun soma cika gida."
Da sauri Ummita ga magantu.
"Mami don Allah kiyi hakuri hakanan ki sanya hannu a
auren Humaira."
Ta tamke fuska.
"Humaira ta nunamin ni ban isa da ita ba, ba ni ce
uwarta ba. Me kike so kuma na ce mata? Ai shikenan, ni dai idan a tunaninta
baΖin ciki nake yi don ba nawa aka aura ba to tabbas ta cutar da ni ta kuma
dauki alhakin riΖon da nayi mata a Ιan shekarun nan. Ta je, aure dai ta yi shi
ga tanan ga Fadeel din."
Daga haka ta sa kai ta bar dakin. Ummita ta bi bayanta da
kallo, sai take Ιan jin kalaman Mamin na shigarta, kodai dagaske akwai wani
aibun na Fadeel wanda ba su da masaniya da shi? Haka ta yi ta saΖe-saΖen zuci
akan Ζ΄ar uwarta da wanda za ta aura, wannan ya yi sanadin da ko zancen hoto ba
ta Ζara tunawa ba balle ta yi.
***
"Nifa ina ji a jikina ba wani abin arziki zai samyo wa
yarinyar nan ba, ita da ake zargin ma ba
cikakkiyar mace ba ce? Ki kwantar da hankalinki ai sun zo kayan su na can
sashin Abbanku yanzu za a yo nan da su. Zamu ganewa kwarkwatar idanunmu."
Jannat ke rarrashin Tasleem a waya da wadannan kalaman. Gaba
daya ta hargitse wai ita dai Antin ta san yanda za ta yi Hamza ya rabu da ita
ta zo ta auri Fadeel.
"Hum, Anti kenan, bana jin a yadda yake mutuwar so da
kaunarta zai iya yin karamin lefe."
"Mtsw, ke kam akwai wauta wallahi. Toh an faΙamaki shi
son daga lefe ake ganewa? Ke dai ki bari na aiwatar da abin da zan yi, koda ta
shiga gidan na rantsemaki sai dai ta gaji ta nemi saki."
Haka suka yi ta tufka da warwara akan baiwar Allahr da ba ta
ji kuma ba ta gani ba. GuΙar da Jannat ta ji yo daga can falo ana rangaΙawa ne
ya sanya ta fitowa daga dakin Anna da ta shige zuwa falon wanda tuni Annan ke
zaune itama tana jiran ta sha kallo. Sai dai kuma nan da nan kallo ya kuma sama
ganin yanda aka shiga shigo da akwatina daga daya biyu har sai da aka sauke set
uku reras na kaya! Toh fa!! Zo ka ga idanun Mami wacce ba da son ranta ba ta
fito sai domin Annan da ta yi mata magana kan ko yaya ta danne abin a ke ranta,
ga kuma Jannat wacce tsabar bakin ciki da hassada sai da ta ji kwalla sun
cicciko a idanunta. Ga Anna kuwa, jikinta har wani irin tsuma yake yi balle
kuma a je kan uwa uba Mami wacce ta mike a mugun razane ta dakawa matar dake guΙa
wata irin tsawa wanda sai da wuri ya yi tsit aka zubamata idanu. Da sauri kuma
cikin yare Anna ta yiwa Mami magana. Nan da nan ta saita kanta. Ta juya zancen.
"Ni na fada, yaron nan mugu ne, wannan kayan bai yi
kama da na yaron arziki ba. Duka-duka nawa yake da har zai ci ace ya tara
wannan uban dukiyar? Toh idan ku idanunku sun rufe ni Maryam babu tsiyarsa da
za ta burgeni!"
Wata mai kaudin bakin ta tare ta.
"Haba Hajiya Maryam, babu kyau shaidar abin da ba ki da
tabbacinsa. Ni wallahi ban taΙa jin an kushe wannan yaron ba sai daga
wajenki."
Mami ta dubi mai magana, wata abokiyar tsokanar Abban ce ana
kiranta da Larai.
"Ke Larai! Ki tsaya iyaka matsayinki. Dama irinki mai
kwadayin abin duniya mai jiran Ζiris ai babu ta yadda za'a yi Fadeel ya taΙa
laifi a wurinki. Inace har da ke ya kai wa ziyara a satin can ya sauke maki
buhun shinkafa da mai? Toh bari ki ji na fadamaki, wallahi matukar ina raye ina
wannan gidan babu mai aurawa Humaira Ιan yankan kai! Ashe kenan son da nake
mata na banza ne matukar ba zan yi mata yaΖin abin da nake da tabbacin gaskiya
ne ba. Yadda zan tsayawa Raihana hakanan zan tsaya tsayin daka akan ganin
rayuwarta ta inganta."
Jikin da yawa a wurin ya yi sanyi, wasu na tauna maganganun
Mami su na shinshino Ζamshin gaskiya a ciki, idan ba gaskiyar ba ne, akan wane
dalili ne zai sa yaron da aka ce bai ko haura arba'in ba zai mallaki maΖudan
kudaΙen da zai haΙo gagarumin lefe akwati har saiti biyu. Wasu kuwa suka tafi
akan zargin ba komai Mami ke gwadawa ba sai abin da ke ranta Ζarara wato
hassada da baΖin ciki. Ai tun da take babu wata Ιiyarta da ta more irin wannan
miji ga kyau ga kudi uwa uba kuma Ζuruciya.
Baba Amina ce ta tari numfashin Mami gudun kada ta kawo musu
abin da ba shi ba don da alama har zatukanta sun samu matsuguni a zuΖatan wasu.
"Kiji tsoron Allah Maman Mubarak (Kamar yanda take
kiranta), tun farkon soma munanan kalamai a kan Fadeel da kike yi, sai da Yaya
ya sanya aka yi bincike sosai kuma aka tabbatar da komai nashi daidai da wurin
aikinsa sai da ya tura aka kara tabbatar da shi din managarcin mutum ne mai
kokarin kyautatawa na Ζasa da shi. Don Allah ko mene ne a ranki kada ki kawo
mana shi anan, kar ki sanya a zargi abin da ba shi ba. Yadda aka fara komai
lafiya a Ζare lafiya."
Maganganun Baba Amina sai suka shafe zargin da wasu suka
fara a zuΖatansu, suka kuma haskaka ko mene manufar Mami, wato dai ba komai ba
ne face hassada.
Mami za ta Ζara magana cikin azama Jannat ta rike hannunta
gami da yi mata raΙa cikin yare a kunne.
"Kar ki sake ki bada kanki a gabansu, za a tafi ana zunΙenki.
Ki bar komai za mu samu mafitarsa."
Ita kuwa Anna sai ta hau yiwa Mamin faΙan gangan, karshe ta
goyawa Baba Amina baya, ita dai Baba Amina jinta kawai ta ke yi don ta san Anna
ba kaunar Humaira take yi ba. Ta sha jin yanda yanayin mu'amalarsu take a bakin
yaranta da kuma Ummita. Amma a yau matar ke cewa wai Humaira ba ta da miji sai
Fadeel.
Idanun Mami ba su raina fata ba sai da aka shiga fiddo
tsadaddun lesuka da atamfofi har ma da mayafai, komai da komai da ake so a lefe
babu ne kawai babu a ciki. Kayayyaki masu mugun tsada dai gashinan a gabanta
tana gani kuma ba na kowa ba sai Humaira, yarinyar da ba ta taΙa jin ΙurΙushin
kaunarta a ruhi ba. GuΙar Larai da ta cika wajen kusan ma da gayya take yi tana
ambaton Allah ya sanya alheri, Humaira ta yi goshi.
Mami fuu ta mike ta bar wajen, duk dauriya irin ta Jannat
kasa daurewar ta yi, tun tana yaΖe har fuskarta ta koma ta Ιauru tamau kamar
Ζullin goro. Ba don Anna ta dakatar da ita daga tashi cikin yare ba, da tuni
itama ta bi sahun Mami. Sai bidiyon dole da ta dinga yi, koda aka kammala gani
sai ta tura wa Tasleem da Futuha domin su sha kallo.
***
Habawa! Ai wannan bidiyo ba karamin kaΙa Ζ΄an hanjin Tasleem
ya yi ba. Kuka da sheshsheka haka ta dinga yi tana kururuwar wallahi Humaira ba
ta isa ta auri Fadeel ba. Cikin wannan yanayin Hamza ya risΖeta a Ιaki.
"Tasleem lafiyarki kuwa? Anyi wani abu?" Gaba daya
yana tambayar ne kirjinsa na dukan tara-tara, tsoronsa kada dai har wani ya yi
masa shigar sauri ya fesa mata labarin aurensa. Dama da niyyar da ya shigo
dakin da ita kenan, Hajiyarsa ta ce lallai ya sanarmata kafin wani magulmacin
ya fesa mata. Ta fisge hannunta daga rikon da ya yi mata ta miΖe tsaye idanunta
gaba daya sun rufe ta hau bambamin faΙa.
"Kai Hamza! Kai ne silar rushewar mafarkaina, ka yi
sanadin da na kasa samun cikar burina don haka na rantse maka ba za ka Ζara ΙanΙanar
farin ciki daga gareni ba muddin ba ka sauwaΖemin igiyar aurenka ba!"
Hantar cikin Hamza ta kaΙa , ya rasa meyasa yake Ιan shakkar
Tasleem a wasu lokutan, ya dai aminta cewa duk inda masifaffen mutum yake ana Ιan
shayinsa. Daga kalamanta ya Ζara tabbatar da zarginsa, wato wani munafukin ya
kawo mata tsegumi. Zufa ta karyo mishi, ya mike a rude ya hau zuba kamar famfo.
"Kiyi hakuri Tasleem, wallahi auren da zan yi ba don na
ci amanarki zan yi shi ba. Ramlat ta jima tana zaman jiran..."
"Dakata Hamza! Dakata! Wai wane yare kake yi? Na kasa
gane komai! Yi yaren da zan ji na fahimta sosai! Uban waye zai yi aure sannan
wace Ramlat ka ke magana akai?!"
Ta yi maganar cikin fita hayyaci, ko kaΙan ta kasa fahimtar
komai. A farko sai da razana ta sanya ta dauke wutar dole, ta ji wani dumm a
kunnenta, ta dinga kallon Hamzan tamkar wani sabon halitta a gabanta. Kai
tamkar a ranar ne ta soma ganinsa a duniya. Shi kuwa ya rasa me zai ce, ya
aminta da cewar dai ya yi katoΙara, wato dai ba batun auren take yi ba. Sai ya
sauke ajiyar zuciya.
"Shikenan, abar zancen, meke faruwa ne kika..."
"AnΖi a bar zancen! Wallahi sai an yi shi!!! Waye zai
yi aure! Ka fadamin nace!!"
Yanda take maganar cikin ihu da Ζarfi ya sa Ιiyarsu farkawa
daga bacci a razane tana kuka, ko kallon inda take Tasleem ba ta yi ba balle ta
kai mata agaji, shi ko Hamza da ya yunΖura da nufin zuwa ya Ιauke ta, ta yi
sauri ta shiga gabansa ta cakumi wuyan rigarsa har necktie dinsa na zugewa ya
fadi a Ζas don shigowarsa kenan ba jimawa daga asibiti, wurin Hajiyarsa kawai
ya shiga kafin ya yo nan. Ya sa hannu ya fisge ta ya wancakalar.
"Kina hauka ne Tasleem? Don nace aure shi ne kike yimin
wannan borin? Ki tsaya fa ki ji, umarnin Hajiya ne wannan auren kin fi kowa
sanin dai ni ba ni da ra'ayin mata biyu."
Ai kuwa wani tsautsayi za a ce ko suΙutar baki da ya kwashi
Tasleem, sai ga ta nan ta narko wata ashariya ta narka ga Hajiyar Hamza, shi
kuwa da ya ke yunkurin nufar Bebinsu dake kuka sai ya tsaya cak yana mai jin
wani gingirim a kai. Tasleem dai ke zagin uwarsa mahaifiya da ta haifeshi? Da
wata wawuyar zuciya ta kwashe shi bai san lokacin da ya nufe ta ba gadan-gadan
ya hau jibga, tun tana ihu tana Ζunduma masa ruwan ashar har dai ta rasa bakin
magana saboda kumbura mata baki da ya yi har yana fidda jini. Cikin sa'a sai ga
wata goggwonsa ta shigo da zummar a gaisa ta ci karo da wannan mummunan abu,
dakyar ta samu ya bar jibgar Tasleem. Amma ina da wata zuciyar ta kwashi Hamza
sai ga bakinsa na furta kalmar saki ga Tasleem. Ta yi matukar razana don ba ta
shiryawa hakan ba bagatatan! Duk irin ban baki da hakurin da Gwaggo Ζanwa ga
Hajiyarsa ke bayarwa bai ko saurare ta ba, itama ta ji laifin na Tasleem ya
girmama amma ba ta so sam ya kai ga saki ba musamman ma kasancewar a gabanta
ne. Sai da ta ji dama ba ta shigo ba.
***
Sai yamma likis Humaira da Raihana suka shigo gidan, wadanda
suka yi saura ba su wuce gida ba su na ganinta aka hau guΙa. Ita kuwa sai
ta Ιoye fuskarta a kafadar Raihana suka Ζarasa Ιakin. Kuka sosai take yi, babu
abin da ya fado mata a rai irin Ummita, irn hakan ce ta kusa faruwa tsakaninta
da Sahabi amma al'amura suka rincaΙe. Koda suka karasa, Ummita ta rungume ta
cikin wani irin murna na taya Ζ΄ar uwarta farin ciki.
"Toh wai meye abin kuka don Allah?"
Ta furta tana rarrashinta. Raihana ta yi dariya.
"Ke kuwa na murna ne mana."
Ita dai ba ta tanka musu ba, a karshe ma ta shige bandaki
bayan ta ajiye ledar dake hannunta don ta kama ruwa.
Wannan daren raba shi ta yi suna hira da Fadeel da ke faman
zayyane mata irin kewarta da zai yi ba kadan ba.
"Boddona, ba za ki iya Ιaga tafiyar har bayan aurenmu
ba sannan muje tare?"
Ta yi murmushi tana dan lumshe idanu domin dagaske ta soma
jin bacci, sai hirar da shi ta Ιan kawar mata da damuwar maganganun Mami akan
matukar ta auri Fadeel toh ta tabbata ta yi asarar ingantacciyar rayuwar farin
ciki. Ita kuwa yanda take jin kaunar Fadeel ta amince da duk kalubalen da za ta
fuskanta a dalilinsa.
"Kin yi shiru."
Ya furta cikin son jin abin da zai fito daga bakinta.
"Ka yi hakuri, na faΙamaka ba jimawa zan yi ba, sati
kawai Abba ya Ιibarmin."
Sauke ajiyar zuciya ya yi.
"Shikenan Boddo, amma lallai fa zan yi kewarki."
"Kwana nawa ne zan zama mallakinka?"
"Me kika ce?"
Sai da ya faΙi hakan ne ta ankarar da suΙul da bakan da ta
yi. Kawai sai ta rufe ido da tafin hannunta na hagu tana dariya Ζasa-Ζasa, ashe
dai za ta iya mayar masa da martanin magana mai dadi? Shi kuwa a bangarensa
fasalta irin farin cikin da kalamanta ya jefa shi ciki ba zai yiwu ba, koyaushe
shi ne mai amayar da abin da ke Ζasan ransa ita kuwa ko oho sai dai ta bi shi
da Hum, um, eh ko aa. Sai hakurin da take yawan ba shi idan ya yi wata Ζ΄ar
Ζorafin ko ya ya. Haka suka raba dare su na hira a karshe ya dinga magana ya ji
shiru sai hucin numfashinta da ke amsa kuwwa ta cikin wayar, anan ne kuma ya
fahimci bacci ya yi awon gaba da ita. Dole hakanan ya hakura shima ya
katse kiran.
***
Bisa shawarar Mami, Tasleem ta Ζi zuwa gidan saboda tsoron
haΙuwa da Abba sai kawai ta sauka a gida Futuha. Tun zuwanta babu abin da suke
zantawa sai lefen Humaira da ya bi ya tsone musu idanu. Futuha ta yi kwafa.
"Ki rabu da yar iska, yanzu za ta soma yiwa
mutane fiffika tana ganin duka ta fi mu. Ni fa wallahi zan so ace yanda kika
fito daga gidankin nan ke kika aure Fadeel din ko ba komai mu ga ta
tsiya."
Fadin haka ran Tasleem ya Ιan yi sanyi. Ta ji ashe Futuhar
na kaunarta da alheri ba kamar ya da ta zata ba a baya.
"Hum, bari ke dai yar uwa. Nima dai zan so hakan ta
kasance amma Abba kinsan shi zai toshe dukkan wata kafa da mutum zai yi
wancakalarsa a rayuwa. Ni wallahi a baya Mami nake zargin ba ta sonmu amma
yanda ta hakikance akan ba ta son auren Fadeel da Humaira yasa na Ζaryata
zargi. Abba shi ne mugun."
Futuha cikin yanayi na suΙutar baki da kuma dadin zance ta
taso.
"Ke! Inji wa? Wallahi toh kf duniyarnan ba mu da
masoyiyar da ta wuce Maminmu. Kinsan irin sadaukarwar da ta yi duk don mu samu
rayuwa ingantacciya?"
Ba ta jira jin ta bakin Tasleem ba ta shiga Ιaro zance babu
ΖaΖΖautawa. Sai da ta ba Tasleem labari kaf na irin abubuwan da Mami ta yi a
rayuwa sannan ta yi shiru. Dama zancen ya jima yana cinta a rai, ita ta tsani
ka ba ta sirri don sai da ta yi dagaske ta ke iya riΖeshi. Tasleem ta ji
zantukan tamkar a mafarki har dai sai da ta Ζara matsawa kusa da Futuha.
"Idan wasa kike yi kinsan Allah bana son irin
wannan."
Tsaki Futuha ta ja kafin ta rantsewa Tasleem cewa dagaske ne
kuma Mami da bakinta ta faΙa mata. Wani ihun murna mai cike da al'ajabi Tasleem
ta yi, tana mai ji a ranta cewa dole ta fesawa Anna da Jannat ko don su bar
ganin laifin Mami sannan Anna ta Ζara samun tabbaci akan babu abin da ya sauya
daga Maminta. Jin Futuha kawai take yi tana jaddada mata kada ta sanar da kowa
komai ta rike sirrin Mami, ita dai ta bi ta da toh, tana kuma da yaΖini akan ai
Jannat da Anna masoya ne ga Mamin, lamarin sosai zai yi musu dadi.
***
Washegari tun da asuba Humaira ta yi wankanta tsaf ta shirya
cikin wata atamfar super da Mami ta Ιinka mata. Sai da ta kammala shiri tsaf su
Ummita na zaune da Raihana cikin jimamin tafiyarta ta bar su, ta karasa ta
dauki inda Ahmad ke shimfide ta ta sumbaci goshinsa sannan ta gyara masa lulluΙi.
Suka kara yin sallama da su Ummita, daga bisani suka yo mata rakiya. Mami na
sashin Abba, Abban yana falon Mami yana jiran Humaira ta fito ya je ya sanya ta
a mota. Sai da suka gaisa sannan ya ba ta umarnin su tafi.
"Abba zan yiwa Mami sallama."
Ya girgiza kai.
"Bacci take yi kwa yi a waya."
Ko kadan ba ta so haka ba, tana da tabbacin akwai abin da ke
faruwa. Maganar Abba karo na biyu akam ta kama hanya su tafi ya sanya dole ta
bi umarninsa ta yi gaba bayan sun kara yin sallama da su Ummita tamkar kada a
rabu.
***
Mami dake kallonsu ta windon Abba ta saki labule cikin huci
ta furzar. Wayarta ta fiddo ta dannawa Wizzy kira.
"Kana buΖatar Ιanka, ni kuma ina buΖatar ka cikamin
wannan aiki da na sanyaka ya kasance na Ζarshe."
Ya yi wata muguwar dariya yana hangen motar Abba da aka buΙewa
Ζyaure ta fito.
"Ai ki sha kuruminki Hajjaju, a yau babu su babu kwanan
duniya."
Ta jinjina kai tana murmushin mugunta.
"Dakyau! Sai na samu kyakkyawan labari."
Daga haka ta katse kiran, Raihana dake yunΖurin shigowa ta
ja baya tana mai riΖe kirjinta da ya tsananta bugu, kalmar innalillahi shi ta
shiga ambato domin kunnuwanta sun kasa gasΖata abin da ta ji na fita a bakin
Mami. A cikin sakanni kadan ta dawo hayyacinta, da wani irin azama da gudu ta
bar wurin zuwa dakinsu hannunta har kakkarwa yake yi wajen danna waya. Ummita
na tambayarta ko lafiya sai dai ina! Babu baka sai kunni. Wayar Abba ta kira,
ringing biyu ya Ιaga da sallama. Yana tafe tana tuΖi lokacin har ya fita zuwa
babban titi.
"Ab..ba..ba.."
"Lafiya Raihana? Meyafaru?"
"Abba za a kashemin ku, ka tsaya ka juyo gida."
Madadin ta ji razani a muryar Abban sai ta ji kamar ko a
jikinsa.
"Kar ki damu Raihana, babu mai tsallakewa kaddararsa.
Amma ki sani, ina da labarin da kika tsinta ko kuma kika ji a yanzu tun a daren
jiya ya risΖi kunnuwana. Na sanar da D.P.O tun a daren jiya ya kuma bani
shawarar da ta dace. Ina tare da rakiyarsu. Kin ji ko?"
Humaira dake gefe ta kasa gane zantukan da Abba ke yi,
kirjinta sai duka yake. Abba kuwa bai jira cewar Raihana ba ya katse kiran. Tun
daren jiya ya tsinci wayarbda Mami ke yi da wani inda take ba shi umarnin kashe
shi da Humaira gaba daya. Har gari ya waye ya kasa tufka da warwara, ga mamaki
mai tsanani da ya kewaye zuciyarsa. Ya ka sa gasΖata cewa Maryam ce da wannan
yunΖurin.
***
Can Ιangaren Wizzy
kuwa, yana tafe a bayan su Abba sannu da sannu don ya cimma su a inda ya gama
dukkan wani tanadi da shiri, har a lokacin duhun asubahi bai gama washewa
ba. Kallon da zai yi ta mirrow ya hangi
motar dake biye da shi a baya, ganin da ya yi duk inda su Abba suka kurΙa a
mota shima ya kurΙa ana biye da su ya sanya shi buga sitiyari, ya tabbata ko
wace motar ce ba zai wuce na masu tsaro ba, zarginsa bai gama tabbata ba sai da
ya ga yana shan wata wawuyar U turn an bude gilashi an bishi da harbi sai da
aka fasa gilashin motarsa ta baya.
***
Mami ta fito
afujajan daga bandaki daure da zani jiki duk kumfa da azama ta nufi wayarta
dake faman Ζara, ganin Wizzy ya sanya ta murmusa don ta san haΖanta ya cimma
ruwa. Sai dai me? Wani wawan ashariya ya jefa mata.
"Kin janyo an kusa kashe ni a madadin na kashe?! A
gidan uban wa Ζ΄an sanda suka sami labarin nan?"
"Me kake nufi? Ban fahimta ba?" Ta jefa masa
tambayar a rikice, ya yi mata bayani yanda za ta gane. Ya kara da fadin.
"Ke Madam, na baki nan da gobe ki gaggauta kawomin
ajiyata idan kuwa ki ka yi wasa da hankalina zan zo har cikin gidan na ga uban
da zai hana ni Ιaukarsa! Useless kawai!!"
Daga haka ya katse mata wayar, Mami kuwa ai sai ta ji
kafafunta sun dauki rawa, toh waye ya san da zancen da har maganar ta isa
kunnuwan Ζ΄an sanda? Ta ya ya hakan ta kasance? Duk iyaka tunani da zarginta ta
kasa fahimta, a iyaka saninta sadda take waya a falon Abba yana dakinsa yana
bacci, koda ta kammala ta shiga yanda ta bar shi hakan ta tarar da shi. Toh waye wannan da ya ji sirrinta? Sai ta zaΙi
shigewa banΙakin don ta Ζarasa wanke jiki a gaggauce ta je ta duba mutanen
gidan ko za ta samu wata shaidar.
***
Fadeel ya Ζurawa hoton da Ridwan ya aikomasa idanu, hoto ne
na wacce ake zargi da yin Ιatanci ga Ummita da Humaira, kamar ya san fuskarnan
sai dai ya kasa tuna inda ya santa. Sai ya zaΙi buΙe Ιayan hoton na bayanin da
Ridwan ya turo masa. Sunan ya sanya shi miΖewa tsaye babu shiri. JANNAT
MOHAMMAD AGADEZ.
Tabbas idan idanunsa ba su gane mishi Ζarya ba, ita ce dai
Ζanwar Mami daya taΙa gani a gidan su Humaira har ta ke jajanta masa lamarin Ιatan
su Humaira. Kai ya sha ganinta ma ba sau daya ba ba biyu ba. Wannan shi ne ana
zaton wuta a maΖera...
***
"Abba lafiya?" Tambayar da Humaira ta yi mishi
hankali tashe jin Ζarar bindiga ga kuma juyin da motar dake bayansu tayi babu
shiri.
"Kwantar da
hankalinki. Babu komai."
Yana fadin hakan ya gangara gefen titi ya tsaya, motar su
D.P.O su dinma fakawar suka yi don sun tabbatar ba za su samu damar cafke
mutumin ba.
"Ina zuwa." Abin da Abban ya ce kenan kafin ya
bude motar ya fita. Humaira dai har wata zufa ke karyowa a goshinta, kirjinta
kuwa bugu yake yi ba ΖaΖΖautawa, babu abin da ya faΙo ranta sai waΙancan
mugayen masu garkuwar da suka kama su. Waigen Abba kawai take yi tsaye da wanda
ta tabbatar Ιan sanda ne don ta gan shi ba sau Ιaya ba kuma ba biyu ba a
gidannasu duk da cewar bai sanya kakin
aikinsu ba. Hakanan sauran mutane biyar da ke tare da shi babu kayan aiki a
jikinsu.
D.P.O Alhussain ya dubi Abba dakyau.
"Kar ka damu Alhaji, in sha Allahu zai zo hannu. Mun
kwafi lambar motar zamu tsaurara bincike ta yadda komai za ya bayyana a zahiri.
Amma Alhaji a shawarce ina so ka Ιoye batun kawo maku harin nan da aka yi koda
kuwa ga iyalinka ne sannan abin da ka fito da niyyar yi kada a fasa shi yin
hakan zai bada wata Ζofar da za a Ζara yin wani shirin nan gaba. Zamu yi
bincike sosai har mu gano waye."
Abba ya jinjina kai har a sannan cike yake da Ιumbin mamakin
Maryam wanda ko a mafarki ya ga za ya aikata makamancin hakan zai Ζaryata a
yayin da ya farka. Dakyar ya daurewa zuciyarsa suka yi sallama da D.P.O sannan
ya koma ga motarsa ya shiga. Murmushin Ζarfin hali ya sakarwa Humaira wacce
wayarta ke ta Ζarar shigowar kira daga
Fadeel amma tsabar ruΙani ya sanya ba ta ko fiddo ta a jaka ba ballantana ta
kai ga Ιagawa.
"Abba mu koma gida don Allah. Na fasa tafiyar."
Kallonta ya yi, sosai sai ta ba shi tausayi, ko ya za ta yi
idan ta ji abin da ke faruwa ko kuma ya yi nufin afkuwa garesu kuma daga wacce
suka yi amannar har abada ba za ta taΙa cutar da su ba? Sai ya girgiza mata kai
cikin murmushi na Ζarfin hali ya amsa.
"Aa Mamana, babu inda za mu juya. Muje na sanyaki a
mota, kada ki damu nasan direban kamar yanda na faΙamaki Ιa ne ga tsohon
Maigadin Ιan uwana. Yana da amana, na kuma sani sai dai abin da Allah ya riga
da Ζaddarawa zai afku toh wannan babu wani mahaluΖin da ya isa ya tsallake. Ki
kwantar da hankalinki in sha Allahu lafiya kalau za ki je ki dawo kinji
ko?"
Da kalaman Abba masu Ζarfafa gwuiwa kuma lokaci guda masu
karya zuciya ta Ιan samu sassauci, ko ba komai ya tunasar da ita abin da ruΙani
ya so ya mantar, wato ambaton Allah. Abba kuwa tuΖi kawai yake yi amma gaba Ιaya
yanayinsa ya nuna yana cikin damuwa mai Ιumbin yawa. Humaira dai hankalinta ya
rabu kaso barkatai, abin da ya faru yanzu da kuma yanayin Abba sai ko kirjinta
dake faman bugu tun faruwar al'amarin.
Abba kuwa ya damΖa ta
a hannu na amanan, Rabe. Mazaunin gaba ya zaΙar mata ita Ιaya yadda ba za ta
takura ba, duk kuma yadda ya so Raben ya karΙi kudin motar Ζi ya yi saboda
karamci da kuma albarkacin Marigayin da ma shi kansa Abban wanda zai wahala su
kai mishi wani kuka nasu ya Ζi yi ba idan da halin yin.
Sosai Humaira ta yi kuka da suke sallama da Abban domin sai
da ta ji tamkar kada su rabu. Sai dakyar Abba ya samu ta nutsu ya yi mata Ζ΄ar
nasiha har da zolaya kafin ta saki ranta.
Bayan tafiyar Abban ta fiddo wayarta don ta kira su Raihana
sai ta tarar da missedcalls har goma sha, wasu daga Raihanar wasu kuwa Fadeel
ne. Kafin ta kai ga wani yunkurin sai ga Fadeel ya Ζara kira. Tana Ιagawa da
sallama ya rufe ta da faΙa.
"Meyasa Boddo!
Meyasa za ki tsoratar da ni wai?! Raihana ta kirani a ruΙe ko na yi waya da ke
nace aa, mun gwada kiran wayoyin Abba a kashe. Ina kike yanzu ganinan a
hanya."
Ta tuna dagaske wayar Abban a kashe take tun amsa wayar
Raihana da ya yi tana ganin sadda ya kashe ta gaba daya. Ko kusa faΙan Fadeel
din bai yi mata zafi ba, ta sani damuwa da lamarinta ne ya yi silar hakan.
"Ka yi hakuri, wayar tana cikin jaka, ina tasha har na
shiga abin hawa."
"No ki jira, ni zan zo na kaiki."
Cikin sauri ta girgiza kai tamkar yana gabanta.
"Aa wallahi, ka yi hakuri dai tunda har Abba ya san
direban kuma sun gama magana."
"Wace tashar ce?" Abin da ya nemi sani kenan
kawai, ta faΙamasa sunanta daga nan ya katse kiran sai lokacin ne kuma ta samu
damar kiran Raihana. Jin muryar Raihanar a shaΖe ya sanya ta tabbatar da ta san
komai.
"Raiha, kiyi hakuri wayar tana jaka."
"Babu komai, Abba ina ta kiran wayarsa a kashe. Lafiya
ku ke?"
Ta yi tambayar cikin kokarin kwantar da murya da Ιoye damuwa
bisa shawarar Ummita.
"Ba mu jima da rabuwa ba, ya juyo ya taho gida."
"Toh, Allah ya tsare ya kiyaye hanya. Zamu yi kewarki
ko ince har mun fara."
Ta dan yi murmushin Ζarfin hali.
"Nima haka Raiha, a gaidamin Ummita da Ahmad. A sanya
mu cikin addu'a."
Daga bisani suka yi sallama, tana nan zaune har ya yi saura
bai fi mutum biyu motar ta cika ba sai idanunta ya sauka kan Fadeel dake tsaye
ya yi shigar tshirt fara Ζal da maroon wando na Adidas. Sumar kansa idan ka
Ζura idanu za ka fahimci ko tsayawa taza bai yi ba. Sai rarraba idanu ya ke yi
a tashar, sai ya ba ta tausayi da kuma murmushi lokaci guda. Ta dan yunkura da
zummar buΙe Ζofa ta fito idanunsa suka shiga cikin nata, da azama ya Ζarasa ita
kuwa tuni ta bude murfin Ζofar. Ya sa hannu ya riΖe murfin gami da durΖusawa su
na fuskantar juna, ta kauda idanunta ta maida ga kallon gaban motar.
"Barka da asuba."
Abinda ya fito daga bakinta kenan. Madadin ya amsa sai ya yi
shiru yana Ζaremata kallo. Can dai ta juyo, daidai lokacin Rabe ya karaso.
"Ranki ya dade kin san shi ne?"
Fadeel ya kalle shi sai kuma ya miΖa hannu suka yi musabaha.
"Eh na san shi." Sai a lokacin ya dan murmusa.
"Waye shi?" Ya tambaya, Rabe dai na tsaye kallon
ikon Allah, ya dai fahimci ko waye daga yanayin kallonsa da nata, ita din cike
da jin nauyi da kunya, yayinda shi kuwa kallonta yake morewa, ga duk wanda ya
kalle shi kuwa zai gane ba Ζaramin nisa ya yi a kaunarta ba.
Ta Ιan bishi da hararar wasa, Rabe kuwa ya yi Ζ΄ar dariya.
Fadeel ya dube shi.
"Aurenmu nan da sati biyu in sha Allahu. Ina
gayyatarka."
Nan da nan ya Ζara washe haΖoransa wadanda yawan yin asuwaki
ya sanya ba su dafe ba.
"Sai Oga, ina taya murna. Allah ya nunamana
lokacin."
Daga haka ya yi gaba ya bar su. Fadeel ya harareta kadan, ta
yi mishi kyau, fatarta ta Ζara gogewa sakamakon mayukan gyara fata marasa haske
da Baba Amina ta kawomata har ma da na wanka da take amfani da su.
"Kin yi kyau. Sai dai meke faruwa ne naji kamar Raihana
na cewa an yi attacking Ιinku? Ban fahimci komai ba."
Sai a lokacin ta tuna tashin hankalin da suka tsallake cikin
ikon Allah. Tunaninta kuma ya tafi ga son gano yanda aka yi Raihana da ke zaune
a gida ta san da wannan magana, toh waye? Ko dai na gida ne?
Ζan Ζas da ya yi da yatsunsa saitin fuskarta ya maido ta
hayyacinta.
"Kin wani
zubamin idanu ina tambayarki. Kwana nawa ne zan zama mallakinki?"
Ya karashe da wani kalar kallo da ma murmushi. Ita sam ba ta
ma san cewa idanunta a kansa ta tsayar ba. Sai ta Ιan yi wuri wuri da idanunta tana kallon mazauna bayan motar,
macen ma hankalinta na ga wanda ta ke da tabbacin mijinta ne su na kwasar
hirarsu.
"Ki bani labari idan wani abin ya faru da ku a
hanya."
Nan da nan ta labarta masa komai da ta ji kuma ta gani, ya
dan yi shiru yana nazarin zantukan, akwai dai alamar tambaya babba.
"Antinku Jannat na gida ko ta tafi?"
Tambayar da ya watsa mata kenan, shi gaba daya yanzun bai
yarda da Jannat din ba, matar da son zuciyarta zai sa ta yi yunkurin munana
sunan wadanda ba su yi mata laifin komai ba, toh za ta aikata abin da ya fi
hakan. Ga Humaira kuwa jin tambayar ta
yi wani bambarakwai, da ace ma Fadeel din nada labarin takun saΖar da ke
tsakaninta da Jannat toh za ta kawo dalilin da yasa ya ambace ta a wannan gaΙar
kenan, amma sanin da ta yi koda wasa ba ta taΙa buΙa masa sirrikan cikin
gidansu ba ya sanya ba ta kawo wani abu a ranta ba sai dai ta yi mamakin
tambayar.
"Eh tana nan sai bayan biki za ta koma."
Ya jinjina kai.
"Alright, hakan ya yi daidai. Ba don Abba ba, ni da
kaina zan kai ki wurin su Kawu. Amma babu komai, wannan ne tafiya ta Ζarshe da
za ki yi ke Ιaya ba tare da ni ba a rayuwarki in sha Allahu."
Ta Ιan yi Ζasa da kanta tana wasa da zoben hannunta.
Zuciyarta ban da soyayyar Fadeel babu abin da ke yawo cikinsa.
"Inda muke bai dace mu cigaba da hira a haka ba. Zan
dinga kiranki har zuwa lokacin da wayarki za ta daina shiga sai dai please kina
isa ki sanya layin can ni ki yimin koda flashing ni kuma zan kiraki.
Kinji?"
Ya Ζarashe a raunane, ta Ιan kalle shi, rabuwa ko yaya take
ba ta da dadi. Ta kawar da kai.
"In sha Allah."
Abin da ta ce kenan kawai, ya miΖe gami da fiddo Ζaramar
envelop a aljihin wandonsa ya Ιora saman Ζaramar jakarta dake kan cinyoyinta.
"Bon Voyage."
Daga nan bai ba ta damar cewa komai ba ya rufemata Ζofar ya
yi gaba. Ta bishi da idanunta da suka cicciko da kwalla, kamar ta ce masa tana
sonsa ko hakan zai saukaka masa dumbin
kewarta da take da tabbacin zai ji, sai kuma ta ji harshenta ya yi
nauyi, a hankali kuma cikin zuciyarta ta furta 'Ina sonka sosai Fadeel.' Amma a
fili juwa envelop din kawai ta Ιauka ta sanya a jaka ba tare da ta duba abin da
ke ciki ba. Mintuna bai fi uku ba fasinjojin suka cika motarsu ta tashi bakinta
dauke da addu'a.
***
Ummita ta fito daga
banΙaki idanunta sun Ιan tasa sai dai ba su kai ga na Raihana ba wacce har
lokacin kuka take yi tamkar ranta zai fita duk kuwa da wayar da ta amsa na
Humaira ya ci ace ta samu sassauci amma ina abin ya fi Ζarfinta ya shallake
dukkan tunani. Ta Ζarasa gefenta ta zauna.
"Ya isa haka Raihana, kinga Ιazu kin daure da Mami ta
shigo ba ki yi wani abun da zai Ιagamata hankali ba asalima baccin gangan kika
yi. Yanzun kuma kin kasa nutsuwa, tambayar duniya nayi maki akan ki faΙamin
wanda ke kokarin kashe su Abba kuma a ina kika ji amma kin Ζi. Lafiya lau muka
yiwa Humaira rakiya amma yanzu kin hargitse. Kin tayarmin da hankali, daure ki
faΙamin ko ma me ake ciki please."
Raihana sai ta ji kamar Ummitan ta Ζara mata giyar kukanta,
ta ina? Kuma da wane bakin? Kai wane hankalin ne ma zai dauka alhalin nata
hankalin ma ya kasa, sosai take faman Ζaryata kanta amma wata zuciyar na kwaΙarta
da Ζara haska mata al'amarin sakamakon kunnuwanta dake mata amsa kuwwa da
muryar Mami wacce ke Ζara jaddada cewa a kashe Abba da Humaira. Toh idan ita ta
kasa Ιauka, ta ya ya za ta fara yiwa Ummitan bayani ta gasΖata ta? Ta ya za ta
ce mata ai Mamin da ta riΖe su matsayin Ζ΄aΖ΄a na cikinta ita ke barazanar kashe
musu uba da kuma Ζ΄ar uwa?
"Shikenan Raihana, tunda ba za ki yi magana ba. Kuma ba
za ki bar kukannan ba zan je na sanar da Mami, ba za ki bar ni cikin tashin
hankali da canki canka ba."
Ummita tayi maganar cikin fidda tsammani da kuma yunΖurin
miΖewa don aiwatar da abin da ta ce. Cikin sauri Raihana ta riΖo hannunta tana
mai girgiza mata kai. Ummita ta fahimci ko mene ne ba Ζarami bane, za ta iya
rantsewa rabon da ta ga Raihanar cikin wannan yanayin tun sadda suka kuΙuta
daga hannun Ζ΄an garkuwa. Kai ba ta jin ma tashin hankalin ya yi kamar wannan.
Gaba daya fuskarta ta yi ja ga kuma jijiyoyin goshinta da suka fito raΙau, kuka
sosai da majina. Cikin dusasshiyar murya ta ce.
"Kiyi hakuri zan fadamaki komai amma sai da iznin Abba.
Ko kuma ki bari kya ji daga bakinsa. Kar ki faΙawa kowa komai."
Ta karashe tana Ζara fashewa da kuka, Ummita cikin hawayen
ta ce.
"Shikenan, amma na rantse idan ba ki bar kukannan ba
zan je yanzu na kira Mami."
Raihana jin zafin sunan Mami da Ummitan ke faman ambata ya
sanya ta mikewa tsaye cike da jin wani Ζarfin da ta nema ta rasa a mintocin
baya.
"Na daina, nace ki bar ambaton sunan kowa, kiyi hakuri
Abba yace kada zancen ya fita. Bari na wanko fuskata."
Daga haka ta yi hanyar bandaki, ita kuwa Ummita bin ta da
idanu ta yi baki a hangame, yanayin yanda ta bada amsa a fusace ne ya sanya ta
kallonta. Ta sauke ajiyar zuciya gami da share nata fuskar. Za ta yi hakurin ji
daga bakin Abban ko mene ne.
***
Anna da Jannat su na
kwance su na bacci jin an bankaΙo kofa da Ζarfi ya yi sanadin farkawarsu a Ιan
razane. Tsaki Jannat ta ja ganin Mami tsaye sannan ta juya kai ta Ζara lulluba
da Ζaton bargo.
"Maryama lafiyarki kuwa? Anyi wani abu ne za ki shigo a
haukace?"
Mami wacce ke bin su da kallo cike da nazari gaba daya ta
fita hayyacinta, ita dai hankalinta ya kasa kwanciya. Toh uban waye ya sanar da
Ζ΄an sanda Ζudurinta idan aka ce duk jama'ar gidan bacci suke yi?
Ta sauke ajiyar zuciya na wahala.
"Babu komai." Daga nan ta sa kai ta fice ta maida
musu Ζofar ta rufe, kafin ta bar wajen sai da ta tsaya jikin Ζofar ta kasa
kunne shiru tana son ji kodai za su ce wani abu amma ba ta ji komai ba wannan
ne ya sanya ta nufar dakin samarin yarannata don nan din ne kadai ba ta leka
ba.
Kwankwasa kofar ta yi niyyar yi sai ta fasa gudun kada wanda
ya yi wani yunkurin ya ji motsinta, ta bude ta leΖa kadan, bacci suke yi daga
Yassar har Dawud, hankalinta ya kai ga Kassim wanda ya juyawa Ζofar baya, ta Ιan
yi Ζuri da idanu don son tantance abin da ya dauke masa hankali a waya yake
kallo. Muraran ta hango mummunan abu na yawo a kan wayar, bidiyo dai na
haramtacciyar zina na jinsi shi yake kallo, hankalinsa sosai yana ga abin da
yake yi har sai da gigitaciyar Ζarar da ta saki ya farkar da Dawud da Yassar,
Ζassim kuwa da wani irin firgici da rawar jiki ya yi cilli da wayar.
Ya yi daidai da shigowar Abba gidan, yana tsaye da jami'an
tsaro na SS da suka zo tafiya da Jannat su na magana ta fahimta, Abban na cikin
muguwar kaΙuwa na jin wannan sabon al'amarin, suka tsinci ihu da kururuwar
Mamin. Gaba Ιaya suka nufi ciki da gudu-gudu har Abban don ganewa idanunsu abin
da ya faru kasancewar Ιakin samarin dab da waje yake.
Yassar ne ya yi kan
wayar da Ζasim ya yi cilla da ita ya dauka, shi kuwa Ζasim da gudu ya tafi don Ιuya
a bandaki jikinsa na mugun kaΙawa tsabar firgici cikin sauri Mami ta karasa ta
rike shi gami da watsamasa mari hagu da dama.
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Kassim mene haka
nake gani?"
Yassar ke ambato hannunsa da yake rike da wayar har rawa
yake yi, Dawud ya karasa ya karΙa ai kamar wanda aka jonawa wutar lantarki sai
ya yi jifa wayar. Ya yi daida da fadowar su Abba Ιakin. Mami idanunta sun rufe
ruf ta cakumi vest din dake jikin Ζassim tana girgiza shi tana kuka take fadin.
"Don ubanka sai ka faΙamin inda ka koyi kallon banzan
nan?! Kana neman jinsi ne? A gidan uban wa ka ke yi?!!"
Maganar ta saukarwa Abba kamar wata kibiya a Ζahon zuciya.
"Ke Maryam, me kike magana a kai ne?"
Sai a sannan ta san ma da Abba a Ιakin, ta dube shi cikin
rufewar isanu har ma ba ta tuna tare ya ke da wani balle ta tuna tashin
hankalin da take ciki na rashin cikar muradinta ta soma magana.
"Ka cuce ni Yusuf! Tsaurin daka yiwa yarannan na hana
su abin kashewa shi ya janyo Kassim kalla-kallacen bidiyoyin luwaΙi. Ni dama na
jima ina zarginsa da matasan yaran gidan Alhaji Tsalha! Ance yaran ba su ji
kuma abin da suke aikatawa kenan amma nayi magana ya Ζaryata ni, kuma ka hana
shi mu'amala da su ya
."
"Ke! Ya isa hakanan!"
Abba ya tsawatar ganin kamar ba a hayyacinta ma take
zantukan ba ga Ridwan da ya tsaya cike da jinjina wannan lamari. Sai kuma ya Ιan
kalli Ridwan din sannan cikin karfin hali ya ce.
"Ki bar zancen zan san ta yanda zan Ιullo masa, yanzu
dai ki shiga ki kira Jannat ina son ganinta."
Mami ta ji wani malolon bakin ciki, wato yana nufin dai ba
zai matse bakin Ζassim din ba ta Ζarfi a ji ko me kenan da har ra'ayinsa ya
tafi ga kallon zina? Sai kawai ta sa kai ta bar Ιakin, Abba ya bi ta da kallon
kin ban mamaki kafin ya mayar da hankali ga Ridwan wanda cikin nutsuwa yake
yiwa Ζassim tambayoyi kai ka ce don shi ya zo. Nan Kassim cikin zubar hawaye ya
soma magana bayan ya yi rantsuwar bai taΙa aikatawa ba ya Ζara da fadin.
"Sosai suke
kashemin kudade don son na saki jiki da su na bi sahunsu, ni kuma na nunamusu
ba zan aikata hakan ba shi ne ni kuma bisa zugar su Usha na soma kallon
bidiyoyin don na ga abin da suke aikatawa. Abba don Allah ka yafemin, wallahi
tallahi ban taΙa aikata kowace kalar zina ba balle kuma ta jinsi."
Kuka sosai ya sanya a Ζarshe dukkan gaΙoΙin jikinsa babu
inda ba ya kakkarwa. Abba dai ya kasa magana saboda tsananin kunyar Ridwan da
kuma baΖin cikin gurΙacewar zuri'arsa da ya rasa ta inda aka haihu a ragaya. Ya
dai san cewa jarrabawarsa kenan. Ridwan ne ya dinga yiwa Ζassim nasihohi masu
ratsa jiki. Kassim sai da a karan kansa ya yi nadama ya kuma yi alΖawarin fita
a hanyar su Usha da yan uwansa. Da wannan Abba ya ce Ridwan su Ζarasa ciki
aiwatar da abin da ya kawoshi.
***
Jannat ko a kanta ba
ta taΙa zaton wani abu ne ba don Abba ya yi kiranta, saboda Mami ranta a Ιace
yake ne da batun Ζassim da kuma rashin nasarar da ta yi sai ta ma kasa tsayawa
yi mata wani bayani dogo, tana isar da saΖon ta fice Ιakinta don tunanin
mafita.
***
Ta karaso falon, Abba dai kallonta kawai yake. Ga ta dai
mutum har mutum a fuska, matar da yake yiwa kallon kanwarsa Amina, koda alama
babu wani abu wai wasan Ζanwar mata tsakaninsu face girmamawa da nuna damuwa ga
dukkan wani abu daya shafi al'amarin iyalinsa. Bai manta ba, faruwar lamarin na
Ιacin sunan su Ummita takanas ta kira shi a waya tun daga Misra ta jajanta masa
har da yin Allah ya isa ga duk wanda ya aikata laifin.
Ita kuwa Jannat ta bi mutanen da kallo sannan ta mayar kan
Abba, gaba daya sai kuma ta Ιan sha jinin jikinta. Da murmushin yaΖe ta gaida
Abba. Madadin ya amsa sai ya ce.
"Ga baΖinki nan."
Ta gaishe su, ta kara da fadin.
"Toh, sannunku. Sai dai ban gane fuskokin ba."
Ridwan ya murmusa yana mai fiddo Id card dinsa na aiki ya
nunamata.
"Sunana Ridwan Bello Jafar, ma'aikacin SS ne. Mun zo
tafiya da ke bisa kama ki da laifin Ιata suna."
Ai sai ta ji kamar ta saki fitsari a wando, iyakar dakiya ta
dake wajen Ιoyo razanarta. Ta dubi Abba wanda idanunsa ke tsaye Ζurr a cikin
nata sannan ta dubi Ridwan da yanayin basarwa ta ce.
"Ζata suna kuma? Me kake nufi? Sunan wa na Ιata? Sannan
waye ya baku iznin kama ni?"
Ya nunamata shaidar izinin kafin ya amsa.
"Ga shaidar iznin tafiya da ke Madam, Ιatancin sunan da
nake nufi ba kowanne ba ne sai wanda kika yi ga Ummita da kuma Humaira. Muna da
evidences da muke da tabbacin komai da kika aikata, sauran bayanin idan mun je
can za ki ji. Ki bamu hadin kai kawai ki bi mu mu tafi."
Shikenan! Ta faru ta Ζare wai an yiwa mai dami Ιaya sata.
Zufa ya shiga yankowa Jannat ta ko'ina a fuskarta, ta hau girgiza kai cikin
tsananin ruΙewa da tashin hankali bisa kokarin ta ga ta kare kanta amma banda
kalmar Ζarya ne babu abin da bakinta ke iya furtawa. Ga Abba da ya yi mata Ζuri
da idanu yana dubanta, har lokacin jikinsa a mugun mace yake. Wannan wane irin
zuri'a ne ya yi aure a ciki? Daga Maryam har Jannat sun jefa shi cikin Ιumbin
mamaki da kuma tsoron halayyar DAN ADAM. Ban da kalmar Innalillahi...babu abin
da yake ambato a can kasan ransa.
Ummita dake tsaye riΖe da Ιan Ζaramin kofi mai murfi da ta
haΙowa Raihana shayi ta tsaya cak cikin razani da jin abin dake fitowa daga
bakin wanda ya kira kansa ma'aikacin SS kuma mai suna Ridwan. Ban da Allah ya
taimaka tana dab da bangon shiga kicin Ιin babu abin da zai hana a yanda jiri
ya kwashe ta ta zube a nan. Sai da ta ga Ridwan ya miΖe tsaye cikin ba wa
Jannat umarnin ta ba su haΙin kai su tafi da kuma ihun da Jannat din ta fasa
akan Abba ya taimake ta sharri ne aka yi mata ya sanya ta jin wani mugun Ζarfin
zuciya ya taho mata. Ummita mai haΖuri da kawaici, mai yawan murmushi da tausar
wanda aka Ιatawa, nan da nan ta rikiΙe ta juye ta koma wata kalar Ummitan mai
ban mamaki a inda ta yi fatali da kofin hannunta wanda Ζararsa ya dauki
hankalinsu suka dube ta, ba ta damu da radadin zafin da ya tsirga saman fatar
Ζafarta ba ta tsallake ta yo gaba jikinta har wani mugun rawa yake yi na Ιacin
rai. Babu abin da take tunawa sai muggan kalaman da aka yi amfani da su wajen Ιata
musu kyakkyawar tarbiyyar da Abba ya gina su akai shekara da shekaru. Ta tuna
sanadin dukkan haka ne ya sa gaba daya aka janye aurenta da Sahabi da a yanzu
ya koma ainahin garin iyayensa wato Zamfara da matarsa.
Kallon Abba ta yi ya kauda kansa daga dubanta zuciyarsa cike
da tsantsar tausayawa sannan ta maida kai ga Ridwan.
"Domin Allah abin da kake fadi akan wannan (ta nuna
Jannat) gaskiya ne?"
Ridwan ya gane ta kwarai, ita ce Ummita don ba ta sauya ba,
ya dai ga ta ma fi yarinta a fili sosai fiye da yadda aka yawo da hotunanta.
Kawa sai ya ji ta burgeshi ta kuma ba shi tausayi kwarai. Madadin ya amsa da
baki sai kawai ya Ιan gyaΙamata kai. Ta juya ga Jannat daidai lokacin da su
Yassar suka shigo har Mami da Anna da ma Raihana wacce dama can a gigice take
sakamakon Ζarar da Jannat din ta yi ba na wasa ba ne.
"Anti Jannat, ke da kanki? Ke ce kika Ιata mana suna?
Me muka yi maki? Wace kalar bautar ce bamu yi ba da har kika zaΙi yi mana
mummunan Ζazafin da duniya za ta bar ganinmu da Ζima?"
"Ummita kin yarda zan aikata wannan?"
Ta fadi tana kokarin riΖo kafadun Ummitan, kamar wacce za a
jonawa wutar lantarki cikin mugun sauri ta ja baya. Za ta Ζara gangancin
matsawa domin ta taΙa ta aikuwa ga mamakin kowa Ummita Ιaga yatsunta biyar ta
yi ta sauke saman fuskar Jannat hagi da dama. Za ta Ζara ne da sauri Abba ya
riΖeta, kuka sosai take yi kamar ranta zai fita.
"Ya isa, ya isa, kiyi hakuri hukuma za ta yi maganinta
da ma dukkan wani azzalumi."
Ya Ζarashe yana duban Mami wacce ta yi mutuwar tsaye jin
abin da Ζanwarta ta shuka ya fito muraran. Ta kuma dan sha jinin jikinta bisa
kallon da Abban ya watsa mata sai ta yi saurin wayancewa da matsowa ta dubi
Jannat.
"Kin bani mamaki, ban yi zaton za ki aikata hakan ba.
Me suka tare maki a rayuwarki?"
Jannat dake kuka sosai ta ji kamar Mamin ta sokamata mashi a
Ζahon zuciya, ba kuma domin akwai su Ridwan a wurin ba za ta shaΖe wuyan Ummita
ne ta aika ta lahira saboda marin da ta yi mata. Ba don jirginta da ya kasance
na dare ba da tuni a safiyar yau Ιin ta tashi zuwa Misra inda za su tattaro su
dawo Nijeriya gaba daya.
"YallaΙai zamu wuce lokaci ya ja. Kiyi hakuri Ummita,
za ta girbi abin data shuka maki kinji ko?"
Ya Ζarashe yana yiwa Ummita kallon da shi kadai ya san
ma'anarsa. Daga haka wani ma'aikacinsu ya matso ya ba Jannat umarni akan ta yi
gaba su je, nan fa Anna ta hau bori da ashariya duk cikin hausarta da bai irin
na Bahaushe sak. Hatta da Abba sai da ta zage wai ya bari za'a tafi da autarta
saboda ya nuna son kai. Abba dai mamaki bai bar shi ba, kenan duk wannan son da
kaunar da suke nuna mishi da yarannan a fatar baki ne? Ya lura Mami sai kokarin
janye Anna take yi tana mata yare akan ta yi shiru amma ina idanunta ya rufe
ita za a tsfi da gudar jininta kuma mafi soyuwa a ruhinta.
Raihana ba ta ce uffan ba, zuwa yanzu lamarin na su Jannat
ba ya girgiza ta, ko babu komai ta ga wacce ta fi su iya tsari da kuma makirci.
Na su ba komai bane. Ana wannan abu kallon Mami kawai ta ke yi yadda ta dage
har da jan Ummita a jiki tana rarrashi. Ba ta sani ba akan Ummitan ko abin nata
ya kai zuci ko aa, kawai sai ta kasa aminta da hakan sai ta juya ta koma Ιaki
saboda wani sabon kukan da ya yunΖuro mata.
Haka aka wuce da Jannat tana kuka da ihun a yafe mata don
gaba daya kuma da ta ga al'amarin dagasken gaske ne sai ta shiga tashin
hankali. Abba kuwa ana ficewa da ita ya fice zuwa dakinsa, tun a falon ya sanya
mukulli ya kulle don ba ya buΖatar ji ko ganin Mami a wannan yanayin. Yana
buΖatar samun hutun da zai yi tunanin da ya dace.
***
Duk wannan budurin da
ya faru su Futuha ba su da masaniya a kai sai washegari labarin ya riskesu daga
Dawud da ya yi waya ya zayyane musu komai da komai. Zo ka ga kuka da sheshsheka
wurinsu musamman Tasleem da ta ji tamkar an tafiyar mata da wani sashe na
jikinta don za ta rantse shaΖuwa da kaunar dake tsakaninta da Jannat ta
shallake nata da na Mami. Ita mai shirin fita zuwa makaranta inda suke
shirye-shiryen zana jarrabawar Ζarshe sai ta fasa suka Ιunguma har Futuha zuwa
gidan. Ba su iske Mami ba don tun ranar da aka tafi da Jannat suke asibiti
sakamakon faduwar da Anna ta yi, ita ta kwana a wurinta bisa iznin Abba don shi
dama ba shi da buΖatarta yanzun. Ta riga da ta gama sirewa a ransa. Raihana
suka soma cin karo da ita kwance a falon da casbaha a hannunta tana ja.
"Ke ina suka kai Anti Jannat?"
Tambayar da Tasleem ta soma jifanta da shi cikin zubar
hawaye ko zama ba ta yi ba. Guntun tsaki Raihana ta ja a Ζasan ranta a fili
kuwa dakyar ta ce.
"Nima ban sani ba."
"Uhum, nikam tun farko dama sai da na nuna rashin goyon
bayana ga wannan.."
Idon da Futuha ta yiwa Tasleem ne ya sanya ta yin shiru,
dagaske dai suΙutar baki ta so yi, sai ta ji tsoron kada Raihanar ta fahimci
komai. Ita kuwa Raihana koda ta fahimtar ma ba ta nunamusu komai ba, ta fi
damuwa akan al'amarin kashe ran da uwarta ta so a yi. Har yanzu ta kasa kwantar
da hankalinta, abin ya jefa ta cikin matsanancin damuwa da tunane-tunane.
"Kin je asibitin wajen Anna ne?"
Cewar Futuha, girgiza mata kai kawai ta yi. Futuha ta ja
tsaki.
"Duk dai abinki duk wani guje-gujenki ba ki da sama da
Annar da kuma mu, aikin banza kawai. Wato wai ke an taΙa Ζ΄an uwanki shi ne kika
dauki gaba da uwar uwarki. Dakyau."
"Rabu da ita dai Futuha, duk dai lalacewar naka naka
ne. Tashi mu wuce asibitin don ni ko wajen Abban ba zan shiga ba. Ai yana ji
yana gani aka titsa Ζeyar Antin amma ya Ζi hanawa saboda ya nuna son kai da
fifiko tsakanin wasu can da mu."
Tasleem ya fadi tana huci gami da gyara goyon da ke kokarin
kunce mata.
Sai a lokacin Raihana ta mike zaune a zafafe ta shiga ba su
amsa.
"Su din dai jininmu ne koda kun Ζi ko kun so. Kuma
wallahi da ace ni ce ku zan ji da rayuwata ne ba na tsaya kallo da kushe ta
wasu ba. Ke kuma da kike kiransu da wai Ζ΄an uwana, to ki goge kalmar wai din,
yes jinina ne su kuma wallahi sun fiyemin ku nesa ba kusa ba. Kin tsaya ganin
kuskure a rayukan wasu, kina nan mijinki har lefe ya kai na Ζ³ar Snow zai aure
ta. Mtsw! Nonsense!"
Tana kaiwa nan ta juya a fusace ta bar su a tsaye kamar an
wawushe musu Ζ΄aΖ΄an hanji. Ba zagin da ta yi musu ne ya taΙa su ba don dama
batun raini to fa Raihana ta yi musu shi, ko kadan ba ta wani ba su girma tun a
baya, yanzun ma da ya ragu sun sani ko sun Ζi gaskiyar hakan ne albarkacin zama
da su Ummita ne. Batun kai lefen Ζ³ar Snow da Yakubu ya yi shi ne ya fi komai sanya
su cikin razana. Lefe gagarumin da suka gani yana yawo yau kusan sati kenan aka
ce na Ζ³ar Snow ne, shi dai?
"Tasleem wai kodai ni ce ban ji daidai ba?"
Futuha ta fadi da wani irin ruΙani, ita kuwa Tasleem ta Ιan
ji sanyi a ranta, kl babu komai idan har hakan ya tabbata ga Futuha zai kasance
ba wai ita Ιaya ba ce ke shaΖar bakin cikin Ιa namiji ba.
"Kai ta ya za ki biyewa wannan mahaukaciyar? Kema kin
sani dai don ta shaΖa maki baΖin ciki ne ta tayar da hankalinki."
Sai Futuha ta hau girgiza kai cikin mugun tashin hankali,
Tasleem ganin haka ta ja hannunta suka fice tana fadin.
"Dallah Malama kar abin da ta fada ki bari ya yi wani
tasiri a zuciyarki. Yakubun da ke Dubai yau kusan sati uku kike wani tunani na
daban? Toh ina ce Ιazun ma ya kiraki kun sha hira?"
Jin haka sai Futuha ta dan samu nutsuwa, sai kuma ta yi
kwafa.
"Shegiyar yarinya kai, wallahi ta jefa ni cikin ruΙani
na Ιan lokaci. Zan yi maganinta ne bari mu dawo."
"Atoh, ko kefa. Ni so nake Anti Jannat ta fito, don ba
ma za'a kwaso kayana ba sai ta fito idan ya so na siyar mu haΙa kuΙin ta kai wa
Teacher dinta ya karkatomin hankalin Fadeel."
Ta fadi Teacher gudun kar wani ya ji. Futuha dai jinta kawai
take amma har a Ζasan ranta ta san da wuya aikin ya ci. Yaudarar kai dai
Tasleem ta ke yi, amma da aiki na cin Fadeel da Ibb da tuni wani labarin ake ba
wannan ba.
***
Mami zaune a gefen
gado bayan ta gama ba Anna abinci dakyar ta yi loma biyar ba ta Ζara marmarin
ci ba. Sai kuka take yi tana tsinewa Abba kai ka ce shi ne ya sanya a kama
Jannat. A wannan yanayin su Tasleem suka shigo dakin, haΙa su tayi gaba daya ta
rungume tana kuka wai an tafi da shalelenta. Mami kuwa sai ta mike ta bar musu
gadon ta koma saman kujerar dakin cike da dumbin tunani. Toh wai waye ya sanya
aka cigaba da bin Ζwakkwafi har aka binciko gaskiyar al'amarin? Ta san dai Abba
tuntuni ya bar maganar. Sai ta Ιan ja tsaki, ita ba ma wannan ba, ta kasa gane
wanda ya sanar da Ζ΄an sanda har aka kai wa su Abba Ιauki, ga kuma wani sauyin
da take fuskanta daga Abban, wannan kuma ta fi danganta shi da Jannat wacce
asirinta ya tonu. Watakila fushin da ya yi da jin zancen ne ya shafe ta.
"Saki kuwa ni Hansatu?! Shi Hamzan ne ya sake
ki?!"
Furucin da Anna ta yi ne cikin dafe kirji ya sanya Mami
maido hankalinta ga hirarsu. Ta mike tsaye cikin mugun firgita tana duban
Tasleem wacce ko a jikinta, haka ma mikewar Mamin ba ta wani razanata ba, Ιan
shakkar Mamin da take ji a baya yanzu duka ya kau adalilin jin wacece ainahin
Mamin da ta yi daga bakin Futuha sai ta gane cewa ashe ita da ma su Jannat ba
su yi komai ba kuma ba za su taΙa shuka irin abin da ta shuka ba a rayuwa.
"Wa aka saki?"
Mamin ta Ζara tambaya don gani ta yi tamkar ba ta ji daidai
ba. Tiryan-tiryan Tasleem ta ba su labarin abin da ya faru ta Ζara da fadin.
"Nifa Mami wannan abun ya yimin daidai kuma ya zo kan
gaΙar da nake da buΖata. Ya je ya auri uwar Ramlatun ma ina ruwana. Ni yanzu
Fadeel nake so na aura."
"Za kuwa ki mutu ba aure! Ke shashashar ina ce?! Waye
ya faΙamami akwai ranar da tsinannen yaron can zai aureki?! Wallahi na rantse
maki har abada ba za ki taΙa aurensa ba! Tun muna shaidar juna ki tashi ki koma
Ιakinki ko kuma yanzu na saΙa maki!"
Ta turo baki.
"Nidai Mami bana son aurensa. Dama wallahi da nasan
matsiyaci ne babu abin da zai kai ni ga aurensa. Ai kowa yana auren ne don ya
samu gida hutun da zai ci karensa babu babbaka, idan ma mutum bai samu ba sai
ya Ιullo hanyoyin da ya san hakansa zai cimma ruwa. Toh ni dai ba zan iya
aikata abubuwan da kika aikata ba amma zan iya yaΖi da namiji har ya sauwaΖemin
na fito na samu cikar burina."
Maganganunta sun sa Mami ta yi Ιif na wucin gadi, ta kuma
kalli Anna wacce ke kallonta itama cikin rashin fahimtar komai sannan ta maida
duba ga Futuha da alamar tambaya. Futuha kuwa ta kauda kanta tana Ιan taka
yatsun Ζafar Tasleem, tana bin ta da kallon ya za ta yi mata haka? Ita kuwa
Tasleem kafaΙunta kawai ta Ιaga kaΙan gami da kauda idanunta don ta rantse ta
shirya yaΖi da duk wanda ya ce sai ta koma gidan Hamza. Yanzu dai Mami ce za ta
yi mata yaΖin da za ta wanku a idanun Abba ko kuma ta yi barazanar tonamata
asiri a wajensa. Wannan shi ne Ζudurinta.
"Ke! Ni sa'arki ce? Ni kike yiwa wannan
maganganun?"
Mamin ta fadi cikin zafi da kuma son sanin ainahin manufar
Tasleem din.
"Nasan komai Mami, na san wace ce ke da abubuwan da
kika aikata. Wallahi samun da za ki yi na rufamaki sirrikanki nayi shiru da
bakina guda daya ne, ki wanke ni a wurin Abba ya amince na zauna a gidan ba
tare da kwaΙa ko wata tuhuma ba. Wannan kaΙai za ki yimin ni kuma na maki alΖawarin zan Ιoye
komai."
Gumi ne ya tsirfowa Mami a goshi, kirjinta har wani tagwayen
lugude ya shiga yi. Wane irin suΙul da baka ta yi har ta zayyanewa Futuha komai
da komai ba tare da tunanin hakan kan iya haifar mata matsaloli a gaba ba?
Yanzu gashinan wa gari ya waya? Kai! Wai Tasleem dai Ιiyar cikinta ke yi mata
barazana ko kuma ta tona mata asiri? Ta kara Ιaga idanu ta kalli Tasleem din
wacce Anna ta damu da tambayar mene ne shi din da Mamin ta aikata amma ba ta ce
uffan ba itama idanunta a kan Mamin tarr babu shakkar komai. Wannan ya Ζara
firgitar da Mamin, sai kawai ta sanya kai ta bar Ιakin ta fice ba ya ko tsaya
amsa kiran da Anna ke kwala mata ba.
"Kai bana son iskanci kun ji ko? Ku faΙamin abin da
Maryam ta aikata na san matakin dauka kafin itama wannan mugun uban naku ya sa
a ficemin da ita."
"Haba Anna, duk fa lalacewar uba uba ne."
Futuha ce ta fadi don har ga Allah ta ji sosuwar rai bisa
kiran Ubansu mugu da aka yi. Tsaki Tasleem ta ja.
"Sai ki yi ai, uban da bai damu da namu farin cikin ba
za ki shigarwa don an fadi aibu a kansa? Anna bari kiji abubuwan ban mamakin da
Ιiyarki ta aikata."
Tana fadin haka ta kwashe dukkan wasu labaran da Futuha ta
ba ta ta fesarwa Tasleem, inda ta yi kuskue Futuha ta gyara, idan ma mantuwa ce
ta yi sai ta tuna mata. Anna wani irin murmushi take yi sosai. Sai da suka kai
aya sannan ta girgiza kai.
"Ban yi mamaki ba. Maryama dai da na baku labari akan
zafin kishi za ta iya aikata komai, ban yi mamaki ba. Sai dai na cika da
al'ajabin yanda har ni ta Ιoyewa wadannan labaran. Kai an gaida Maryama. Muna
mata kallon biri tana mana kallon ayaba."
"Uhum, ai ni kaina Anna na sha mamaki. Farko na yi
zaton duk don soyayyarmu ce ta sanya amma kuma zuwa yanzu na fahimci son
zuciyar Mami ne. Kanta kaΙai ta sani ba ta damu da mu ba."
Tasleem ta furta a zafafe. Futuha ta girgiza kai ta bude
baki za ta yi magana Anna ta tari numfashinta.
"Shashasha kawai, ke ba ki san Maryama ba. Son kanta ai
ku din ne kan nata. Ni na sani tabbas dagaske domin ku samu jin dadi da
walwalar ta aikata hakan, amma shi ne don ranki a Ιace yake kike neman kwaye
mata zani a kasuwa ko?"
Tasleem dai turo baki tayi kawai tana kokarin fiddo nono ta
ba bebinta. Sai kuma aka koma jimamin Anti Jannat, Futuha ta kira Yakubu ta
sanar masa komai saboda sanin da ta yi yana da manyan mutane watakila su shiga
rigar alfarma a saki Jannat.
***
NIJAR.
Humaira cikin Ζ΄an uwanta da abokan arziki a garin na Maine.
Gaba daya a kwanaki uku da ta yi ba ta da wata damuwa sai farin ciki da
annashuwa. Kawunta sosai yake hidimar kawo mata dukkan wani abu da take so.
Matarsa Tanti Hafsatu da suke kira da Hajjo kuwa ita da wasu cikin yan uwan
Mamanta tun zuwanta aka soma yi mata gyare-gyaren aure. Ci wancan sha wannan,
wasu kuwa tana ji sai dai su ce ba yanzu ba sai a ranar da za a kai ta. Wannan
gatan da take samu ya sanya har hawaye takan yi, ta sani ba don Mami ta dauki
fushi da ita kan lamarin Fadeel ba, babu abu daya da ba za ta samu daga gareta
ba. Amma fushin ya kore komai. Sun gaisa da Abba a wayar Kawu amma koda wasa
bai yi mata wani bayanin game da abubuwan da ke faruwa ba. Hakanan Fadeel da su
Ummita, su din ma babu wanda ya ce komai. Shi Fadeel batu ne na Jannat, koda
wasa bai bari ta ji ba don ba ya son abin da zai Ιaga hankalinta.
A rana ta hudu Kawu ya kawo mata magungunan tsarin jiki sai
rubutuka da ya yi mata. Tun soma shan da ta yi ta soma jin sauyi daga gangar
jikinta. Ya ba ta addu'o'i masu Ζarfi ya ce ta dinga yi kullum safe da yamma
sai kuma tashin dare da ya lura tana yi har ya zame mata jiki, nan ma ya bata
wasu addu'o'in. Ya kuma ce ta dinga karanta la'ilaha illa anta subhanaka inni
kuntu minazzalimin Ζafa arba'in duk sadda ta shiga wata damuwa.
A kwanakin da ta yi
ta ga soyayya da kauna matuka, har ta cika sati cif bata da wata damuwa ko na Ιigo.
Ana gobe za ta wuce su na zaune su na shan hira da Kawu yana mata nasiha akan
zaman aure da kuma irin kyawawan halayyar mahaifiyarta sak ta dube shi cikin
nutsuwa.
"Kawu, don Allah mene ne maΖasudin rabuwar Mamana da
Abba?"
Ya Ιan yi shiru, toh meye amfanin Ιoyon tunda har Fatima a
yau babu ita? Shi kansa akwai al'amarin da ya Ιaure masa kai a labarin wanda
har yanzu bai fahimta ba sai dai ya yi karfin halin ba Humaira dukkan labari.
Daga na irin soyayya da kaunar da Abba suka yi da Fatima, da ma kuma yanda a
karshe ta zo ta tsane shi mugun tsana wanda sun sha tambayarta ta ce musu ita
dai ba ta sani ba kawai ta tsane shi. Ya Ζara da fadin.
"Wannan tsanar har Fatima ta mutu ba mu gano silarta
ba, idan ya taso mata sai ta dinga riΖe kanta tana ji yana mata ciwo tamkar ya
fashe, wani lokacin kuma ta yi kuka mai yawa daga bisani bacci ya Ιauke ta. Mun
bar shi akan iskokai ne. Sadda za ta rasu kuwa, lafiya lau ta haifeki sai bayan
ma har Ζanwar Dada, Inna ta mata wanka ta shirya ta tsaf kawai aka shiga aka ga
fuskarta da dukkan jikinta ya yi baΖiΖirin kamar wacce aka Ζona. Aka tattaΙa
aka ji babu rai, gaba daya lokaci guda ta komaΙe ta koma tamkar babu jini a
jikinta."
Humaira da tun soma labarin take kuka sosai ga wani irin
fargaba da ya shigeta da kuma tausayin Mahaifiyarta ta ce.
"Kawu kenan nima idan na haihu zan mutu ne irin yanda
Mammana ta rasu?"
"Haba Humaira, wa ya ce maki haihuwa mutuwa ce?"
Ta girgiza kai.
"Kawu nima na yi fama da makamancin wannan halayyar na
Mamma akan Fadeel. Ni tsana ce na yiwa kowane Ιa namiji da zai ce yana
sona."
Ya yi shiru yana kallonta da mamaki, ta cigaba da koramasa
bayanin duk yanayin da ta tsinci kanta a ciki da ma hayaΖe-hayaΖen da Mami ke
yi mata don taimakonta. Sai wani tunani ya zo masa, tabbas Fatima ta ce itama a
lokacin Mami ta taimaka mata da hayaΖi wanda nan da nan ta ke jin kanta na
juyawa bacci mai nauyi ya dauketa kuma idan ta farka muddin ba Abban ta gani ba
to fa tsanar ba ta Ζara dawowa. Ya tuna har hayaΖin ta ba su akan su cigaba da
yi mata.
"Ya aka yi kika daina jin tsanar?"
Ya yi mata tambayar cikin sauri. Nan ta kwararo masa bayani,
ita dai tun maida hankali sosai da ta yi ga ibada shikenan kuma sai komai ya
sauya. Ta ba shi labarin abin da ke damunta wato tsanar Fadeel din da Mami ta
yi. Hatta da farkon zuwan Fadeel din gidan wanda Tasleem ta yi zaton wajenta ya
zo ta shirya sai da ta ba shi labari. Kawu ya yi shiru yana sauraronta cikin
wata irin fargaba da tunani. Kada dai a baya sun tafka kuskuren yarda da
Maryam? Ya tuna tabbas Fatima mai yawan ibada da nafilfilu tun sadda ta dawo
gida Nijar suka lura gaba daya ta bar yin ibadunta yanda ya kamata. Hatta da
sallah sai Dada ta yi magana take tashi ta yi. Idan ma ta idar babu wata
doguwar addu'a take miΖewa.
Ya ambaci kalmar Innalillahi zuwa karshenta a zuciya, bai
mance ba akwai sadda wani Malami tun lokacin Fatiman ya ce asiri ne aka yi mata
kuma da sanya hannun abokiyar zamanta amma sai suka yi biris suka ji haushi
suka Ζaryata shi, a tunaninsu ta ya ya za'ayi matar da take zaune da su da
zuciya daya ta aikata wani mummunan abu ga Fatiman?
Jikinsa sai ya yi mugun la'asar.
"Kawu akwai wani abu ne naji ka yi shiru?"
Sai ya yi mata murmushin yaΖe.
"Babu komai Humaira, maza je ki kwanta dare ya yi kinga
gobe sammako za ku yi."
Ya fadi hakan ne saboda tare za ta wuce da su Hajjo sai
budurwar Ιiyarsa sa'ar Humairar, wato Safina. Sauran masu zuwa Ιiyoyin Inna
Ζanwar Dada sai ana bai fi sauran kwana biyu biki ba za su taho da Kawun.
MiΖewa ta yi ba don ta gamsu da yanayin fuskar Kawun ba ta
yi mishi sai da safe ta bar wurin. Hajjo dake gefe tana damawa Kawun fura tana
jinsu ta mike bayan ta gama damawa Kawun fura ta ajiye masa da ludayi, cikin
harshen fillanci ta ce.
"Komai da ya
faru ya riga ya faru sai dai a kiyaye gaba. Yanzu tunda har ka gano bakin zaren
sai a yiwa abin tufka ta hanyar cigaba da kula da yarinyar da dora ta bisa
turbar addu'a da kuma nema mata abubuwa tsarin jiki duk da cewa babu tsarin da
ya fi addu'ar."
Kawu ya numfasa cike da jimami da taraddadi.
"Mamaki da tsoron halayyar DAN ADAM ya Ζara shiga ta
Hafsatu, yanzu ke kya ce wannan baiwar Allahr za ta iya cutar da ko mage ne
balle kuma mutum?"
Murmushi Hajjo ta Ιan yi.
"Meye abin mamaki anan? An fa yi wanda ya fi haka. Kuma
kar k manta zargi ne.."
"Ko kusa bana kokwanto ko zargi a kan haka, wannan
gaskiya ce da na jima da ji kuma na Ζi yarda sai yanzu da komai ya bayyana a
zahirance. Ba zai yiwu ace hayaΖin da Maryama ta ba Fatima shekarun baya ba
irinsa take hayaΖawa Humaira kuma yanayin da Fatima ke shiga dalilin
hayaΖe-hayaΖen ace iri guda ne da na Ιiyarta. Wannan ai ko akwai ban mamaki,
ban da kuma toshewar basira irin tamu a lokacin, mun kasa tunanin akwai cutarwa
a ciki ba? Kowannenmu ya shaida da irin kaunar da Fatima da Isuhu ke yiwa
junansu ba amma rana Ιaya ta yi masa tsana wadda da bakinta ta furta mana ba ta
san dalilinsa ba? Kai Hafsatu, nikam ba zargi nake yi ba, na riga da na
tabbatar da sa hannu wannan makirar."
Hajjo ta jinjina kai yayinda kwalla suka cicciko mata na
tuna yanda Adda Fatima (kasancewar yaya take a wurinta koda babu aure
tsakaninta Kawu, don yar uwarsu ce ta fannin Baffansu) ta sha fama kafin
rasuwarta.
"Amma idan har hakan ne toh wallahi matarnan ta jira
sakayyar Ubangiji don ta dauki alhakin wacce ba ta ji ba kuma ba ta gani ba.
Matar da ta yarda da ita tsakani da Allah mu ma haka. Ni babu abin da ya ban
tsoro sai wannan bori da tada jijiyoyin wuyan da Humaira ta ce tana yi akan ba
ta kaunar aurenta da Fadeel. Toh a zatonta yarinyar za ta yi ta zama babu aure?
Ai ni tun da naji cewar wai Humaira ba a sanyata a makarantar boko ba sai da na
yi maka magana idan ba ka manta ba, nace maka ko Ζ΄ar gidan Iyagana da ta girmi
Humaira da suka koma can Katsina da zama an maida ta boko kuma yanzu gashinan
har ta kusa kammala kwalejinsu. Ka hau ni da faΙan ai wannan ma gata ne za ta
yi mata. Eh gatan ne, amma yanzu wa aka cutar? Za ta shiga rayuwar miji Ιan
boko fisabilillahi daga shi har danginsa na san sun ci sun tada kai da biro da
takarda yarinya babu faransancin babu turanci."
"Hafsatu don Allah abar maganar tunda dai mai afkuwa ya
riga da ya afku. Ki yafemin faΙan da nayi maki a lokacin, amma ki sani ko
Humaira ba ta yi wata aba boko ba, mu godewa Allah tunda ta tsira a hanyar
tsirar, wato na islama da ba a hanata ba. Sannan karki manta duk fa yanda Allah
ya tsarawa bawa a rayuwa hakan ne zai tabbata. Yanzun ba gashinan ba nan da ta
yi mana girki kamar kunnuwanmu za su tsinke don dadi? Ai DUKAN RUWA BA ZAI HANA
GWARJE AMO BA! Mu je zuwa muna nan dake wataran yarinyar nan sai ta zama tamkar
farin wata mai haska darare a cikin yan uwanta. Babu abin da zai hana zakaran
da Allah ya so ya yi cara."
Ta ji karfin gwuiwa bisa maganganunsa har sai da ta murmusa.
"Allahu ya nunamana wannan ranar."
Kawu ya amsa da amin yana jawo Ζwaryar furarsa.
***
Mami sosai ta cika da mamakin ganin Abba bai ce uffan ba
game da dawowar Tasleem gidansa matsayin bazawara. Koda ta kalallameshi banda
Allah ya kyauta babu abin da ya ce. Tunanin shirye-shiryen bikin da ya sa a
gaba shi ya dauke hankalinsa ne ya sanya ba ta kawo komai ba amma a kaifin
basira irin nata ta sani akwai dai abinda ya sauya Abban, ko fara'arsa ta daina
gani.
Ζangaren jannat kuwa ranar da ta kama na dawowar Humaira, a
ranar ne aka gurfanar da ita gaban alΖali, a Ζ΄an kwanakin da ta yi gaba daya ta
fita hayyacinta duk kuwa da cewar babu duka balle zagi amma fa wahalar zama a
inda ba ta sama ba ya sauya ta. Tasleem koda ta ganta fashewa tayi da kuka, sai
kuma a lokacin ne suka san Fadeel ne ya Ζarfafa binciken har mai afkuwa ta
afku. Wannan ya Ζarawa Mamin tsanar Fadeel, itama Tasleem sai da ya yi mugun Ιata
ranta.
Mami tana ganin an shige ciki domin shari'ar ta koma da
baya ta fidda waya ta kira Wizzy. Tuni ta shiryamasa cewar ya aika mace gidan
ta daukar masa Ahmad tunda babu kowa sai Anna da Ummita.
"Ka gaggauta wanzar da shirin don bana son a samu wata matsala, ka kuma tabbatar da komai
ya tafi daidai."
Daga haka ta katse kiran ta shiga dakin shari'ar.
A gabansu alΖali ya yankewa Jannat hukuncin biyan tara na Ιata
sunan da ta yiwa su Ummita, miliyan biyar ga kowaccensu. Sai kuma Ζaryata kanta
a gidan jaridu da ma rediyo da kuma soshal midiya kan cewar ita ce ta sa aka yi
wannan mummunan aikin da kuma ba da hakuri. Hakanan shi ma Joshua. Tun daga
lokacin ya hau kuja da roΖon gafara don ya sani ba shi da maΖudan kuΙaΙen da
zai biya don wake kansa a gaban alΖali. Ya shiga tsinuwa ga Jannat wacce ita ce
ummul-aba'isin na shigarsa wannan hali. Shi da ya yi aikin akan kuΙaΙe Ζalilan
sai ga shi ya jawowa kansa, ga mahaifinsa da ya ce babu shi babu hannunsa a
ciki.
Daga haka aka Ζara titsa Ζeyarta aka tafi da ita har sai
lokacin da aka biya tara sannan.
Haka suka fito bakin kotun su Tasleem da Mami na kuka, ga
Anna can a gida ta baza idanu tana jiran ta gansu tare da ita.
Mami kuwa zuciyarta cike take da zullumin ko Wizzy ya
aiwatar ko kuwa an samu akasi. Ta duba ta ga dukkan yaranta idan ka cire
Mubarak da ke can Sokoto a camp babu wani da ba ya tare da su. A iyakar saninta
babu wata matsala da za a samu da shigar mace cikin gidan tunda dai babu kowa.
***
A daidai wannan
lokacin motar su Humaira ta tsaya a tasha, suka fito ita da Hajjo a take aka
samar musu abin hawa da zai kai su har gida sakamakon lodin kayan da suka taho
da su. Suna hanya zuciyarta cike taf da farin ciki, ba ta kira kowa ba da
zummar sai dai kawai su ganta.
***
Wizzy ya bude motar gami da duban matarnan, matashiyar
budurwarsa da yake ji da ita a lokacin, sai da suka kai ruwa rana kafin ta
aminta da buΖatarsa har sai da ya yi nata alΖawarin da ta jima tana son ji, wai
aure. Ta sha zabgegen hijabi da niΖaf.
"Nusy, kar ki bari a samu wata matsala. Ki bi komai
daki-daki yanda muka tsara."
Ta yi mishi farr da idanu bayan ta Ιage nikaf din.
"Wannan ba damuwa ba ne Guy, komai zan yi
dominka."
Ya jawo fuskarta ya sumbaci goshin sannan ta sauke nikaf din
ta dauki jakarta ta fita. Yana daga can tsallaken ya ga shigarta gidan ba tare
da dogon zance da maigadin ba. Sai ya sauke ajiyar zuciyar, ribas ya yi da
motar ya koma daga can bayan gidan ya tsaya gudun kada a gan shi duk kuwa da
cewa motar tinted ce amma ita ce dai motar da ya kai wa su Abba hari.
***
Ummita dake zaune a falo ga Ahmad a gefenta yana bacci cikin
net dinsa. Hankalinta gaba daya ya yi zurfi a tunanin yanda aka kaya a wurin
shari'ar amma ta kasa kiran koda Raihana ce don ta ji meke faruwa. Sallamar
budurwar ta katse tunaninta, ta dubi Ζofa gami da amsawa. Ganin mace da nikaf
ba ka ganin komai sai idanunta ta dan yi jim, ba don ba ta saba ganin mai irin
shigar ba sai don kasancewar abu ne mai wahala su yi baΖuwa da irin shigarnan.
Kamar Nusy ta san zargin da take yi, sai ta Ιage nikaf din, kyakkyawar fuskarta
ta bayyana da murmushi mai bayyana haΖorinta na makkah.
"Sannu, nan ne gidan su Futuha Yusuf?"
Ganinta har da haΖorin makkah da kuma yanayi na kamala sai
ta Ιan saki jiki, itama cikin Ιan murmushin ta amsa.
"Yauwa, eh nan ne. Ζaraso ciki mana."
Nusy cikin tabbacin samun nasara ta Ζarasa ta zauna idanunta
ya sauka kan wanda ta zo dominsa, wato Ahmad. Yaron tubarakAllah, da alama goyo
mai kyau yake samu don yana da kumari sosai fatarsa kuma ta Ζara gogewa.
"Ba ki sanni ba ko? Ni makwafciyarta ce ta Kuntau ana
cemin Maman Suhail, mun yi da ita dama zan yi mata rakiya wata unguwa shi ne ta
yimin kwatancen gidan nan ta ce na zo mu hadu anan mu tafi."
Ba wani sanin gidan na su Futuha na yanzu ta yi ba balle ta
fahimci gaskiyar lamarin, ta ba da gaskiya sosai akan zancen Nusy.
"Allah Sarki, eh sun dan fita ne amma na tabbatar sun
kusa dawowa yanzu. Bari na kawomaki ruwa."
Tana fadin haka ta miΖe, an zo daidai wajen da Nusy take so,
tana ganin shigar Ummita kicin ta yi saurin miΖewa ta bude net din Ahmad ta
daukeshi. Ta Ιago suka yi ido hudu da Waleed da ya shigo daga bangaren Anna
rike da ball a hannunsa. Ya gaida ta don bai mance sadda Ummita ta yi baΖuwa ba
ya Ζi gaishe ta Antinsa Humaira ta yi mishi tsawa. Ta amsa tana dan wayancewa
da jijjiga Ahmad kai kace kuka ne yake yi. Waleed kuwa dama ruwa ya fito sha
sai kawai a guje ya yi kicin yana wasanninsa na yara. Ta sauke ajiyar zuciya da
sauri ta Ιaga zumΙulelan hijabinta ta sanya Ahmad a ciki ta rufe, ta kama hanya
ta fice bayan ta sauke nikaf din ya rufe fuskarta.
Har ta fice daga farfajiyar gidan, Allah ya taimaka Maigadi
ya Ιan mike wannan ya sa ta Ζara Ιaga kafafunta ta fice a gate din.
Daidai lokacin motar su Humaira ta tsaya suka fito, idanunta
akan matar dake ta baza sauri ga kukan jariri na tashi cikin hijabinta. Kafin
ta yi wani tunanin sai ga Ummita a haukace ta banko kyauren gate din ta fito.
"Ahmad! Wayyo
jama'a ku taimakamin Ιana!!"
Jin haka ai sai wasu samari da ma ita kanta Humaira dake
tsaye suka nufi matar a guje, daidai sadda Wizzy ya yo gaba da zummar kawai ta
bude motar ta shiga daga ta iso, sai dai ina, wata irin raruma da wani ya kai
mata sai ga ta nan yiff a Ζasa, yaro kuwa ya ji buguwa ya fasa ihun da ya fi
kukan da yake yi a baya. Da rawar jiki kuma a haukace Ummita ta hau Ιage
hijabinta sai ga Ahmad, Wizzy kuwa tuni ya yi wata muguwar ribas ya bar wurin a
miliyan, duk iyaka kokarinsu na ganin sun damΖeshi abin ya ci tura. Nusy dai ta
zo hannu tana kuma ji da gani wanda ta aikata dominsa ya juya ya bar wurin.
Nan da nan Ummita ta
damΖe Ahmad tana kuka har lokacin jikinta na kakkarwa. Samarin nan kuwa suka
shiga kokarin bugun Nusy wani dattijo ya hana ya bada umarnin a damΖa ta a
hannun Ζ΄an sanda.
Ana nan ba a kai ga tafiya da ita ba sai ga motar su Abba ta
sanyo kai. Mami tun daga nesa ta hangi cincirindo ai sai da ta ji wani mugun
jiri daga zaune yana son kwantar da ita.
"Meke faruwa haka kuma? Waccan ba Mamana ba ce?"
Fadin Abba yana Ιan Ζara Ζurawa wurin idanunsa. Mami dai ta
kasa ce masa uffan sai Raihana daga baya ta amsa da su ne har da Ummita. Sai
kawai ya ja burki ya tsaya ya fito, Mami dai ta kasa motsi balle ta fito daga
motar. Suna fita wayarta ta hau Ζara. Ganin sunan Wizzy sai da ta ji wani
guntun fitsari ya kufce mata ya zubo, ta Ιaga ba tare da cewa uffan ba.
"Ke tsohuwar kilaki! Ki saurare ni dakyau! Na rantse
maki tunda har aka kama min farin cikin rayuwata sai na salwantar da rayuwarki!
Sai na kasheki da hannuna muddin asiri ya tonu! Kuma yanzu na gaji da bibiyar Ιana
ta hanyarki! Zan tunkari ita banzar gyatumarsa ta ba ni Ιana ko ta halin ΖaΖa
ne! Ke kuma ki saurari abin da zai biyo baya! Ba ki san waye ni ba! Labarina
kawai kike ji!"
Yana kai wa nan ya datse kiran, wasu hawaye masu Ιumi na
bakin ciki ya zubo saman fuskar Mami, ta yi saurin kauda su ta bude murfin
mitar ta fito. Duk wannn abu da take yi akan idanun Hajjo wacce tun fitowar su
Abba ta lura da Mamin da kuma yanayinta, tana ganin wayar da ta amsa. Mamin na
fitowa itama idanunta ya sauka cikin na Hajjon, ta gane fuskarta sarai, matar
Kawun Humaira sai ta kauda fuska ta daure ta tamau.
Abba ya dubi Ummita
da neman ba'asin yanda lamarin ya faru. Cikin kuka ta labartamasa komai, Futuha
tunda ta ji an ambace ta da ma sunan unguwar da take sai ta zaro manyan
idanunta waje gami da dafe kirji a mugun firgice. Kafin ma Ummita ta kai aya ta
hau rantse rantse.
"Na rantse da Allah karya take yi, ke a ina kika san
ni? Wallahi Abba karya ne ni tunda naje wannan unguwar ma ban taba shiga kowane
gida ba don ba class dina ba ne su. Wallahi sharri take yimin."
Nusy kuwa dai ba ta tanka ba sai jin ciwon gudun da
masoyinta ya yi ya kyale ta a nan, idan wani ya ce mata zai aikata hakan gareta
za ta Ζaryata. Mami kuwa tana gefe ta yi gum ba ta ce uffan ba.
Hajjo dai ba ta bar
kallonta ba har sai da Abba ya ba su umarnin duk su shige ciki shi zai juya a
miΖa Nusy hannun hukuma. Da wannan gaba daya suka yi cikin gidan, Raihana ta
rungume Humaira ta fashe da kukan da Humairar ta ba kanta ko don abinda ya
kusan faruwa ne. Tun tana rarrashinta har dai kukan ya soma karyar da nata
zuciyar. Dama ta lura da irin muguwar ramar da Raihana ta yi. Tasleem ta
tsallake su gami da jan tsaki ta shige ciki don yanzu ta koma ainahin dakinsu
kuma tsohon gadonta. Futuha kuwa Ιangaren Anna ta yi don ta kwantar mata da
hankali bisa hukuncin da aka yiwa Jannat.
***
Ta fakaici idanun jama'ar dake falon ta shige Ιakinta ta
sanya muΖulli. Waya ta fitar ta dannawa Hajiya Lubna kira. Ζara uku ana hudu ta
Ιaga.
"Lubna ki taimakamin, komai ya lalace."
Tana maganar ne cike da tashin hankali.
"Kwantar da hankali ki sanar da ni a nutse. Meke faruwa
ne?"
Nan da nan ta zayyane mata komai ta Ζara da fadin.
"Muddin waccan yarinyar ta buΙe baki ta yi wata maganar
toh ki sani akwai babbar matsala. Nikam ban san kuma me zan yi ba."
"Wannan ba damuwa ba ce Maryam, yanzu dai abin da nake
so ki yi kokarin sanin station din da aka miΖa ta ni kuma zan nemi Alhaji don
ya yi magana su sake ta. Ai harka ce ta kuΙi kwantar da hankalinki komai zai
tafi daidai."
Ta dan ji sassauci kaΙan.
"Shikenan, bari Abban yaran ya shigo. Amma lallai
muddin wannan yarinya ta fito zan dauki mummunan mataki akan Ιan iskan yaron
nan."
"Ko kefa, ki kwantar da hankalinki komai zai tafi yanda
muke so. Ai ko ba ko faΙa ba dole Wizzy ya ci ubansa. Ya batun can kuma na
baya, kin gano wanda ya sanar da Ζ΄an sanda? Na fadamaki Maryam koda yaranki kar
ki sake ki aminta da su."
Wannan ya tunasar da Mami tashin hankalin da ke gabanta.
"Uhm, bari kawai Lubna. Ai yanzu an yanka ta tashi
domin babu wani abu cikin sirrina da Ζ΄ar banzar nan Tasleem ba ta ji daga bakin
Futuha ba wai har ni ta ke yiwa barazana akan maganar? Wancan batu kuwa har
gobe na kasa fahimtar komai, karshe na zargi Abbansu ko shi ya sanar toh idan
haka ne kuma meyasa har yanzu bai dau mataki ba? Nidai na ga y sauyamin, babu
hira da ni balle a sakarmin fuska."
"Toh kuwa lallai ki zauna ku yi magana da shi sosai ki
fashe da kukan kissa ki nuna sauyin nan da ya yi maki sam bai maki dadi koda
dai duka wadannan ba sai na koyamaki ba ke dinma Malamata ce a wannan fannin.
Yaranki ko zan yi waya da Babandi mu sanya a Ζulle musu baki ta yanda babu inda
maganar za ta Ζara fita."
Sanin da Mami tayi Anna ba matsala ba ce ya sanya ba ta ma
kawo ta a rai ba, ita idan ta sani ba wani abun bane. Tun kuma safiyar yau din
sai yanzu ta yi wani murmushin da har zuciyarta ta ji daΙin wannan zantuka na
aminiyarta.
"Ina yinki sosai Aminiya, Allah ya kara doraki kan
Alhaji da maΖiyanki."
Suka yi dariya, nan kuma suka koma batun Jannat wanda tuni
ya baza gari, Hajiya Lubna ta jajanta mata da tambayar yanda za su yi da batun
kudaden. Ta taΙe baki.
"Motarta dai ta ce a siyar sai sarΖoΖinta da mijinta
zai taho da su. Ya ce dai babu hannunsa a ciki don haka ko sisin kwabo nasa ba
zai yi kuka ba."
"Shegen sama, shiyasani, ko me ake ciki dai sai ta
fito. Sai kuma ta kiyayi gaba tunda yanzu idanun duniya duk a kanta suke."
Mami ta numfasa.
"Atoh, kinga bari naje ga waccan kafaffan mijin nawa ko
zan iya tankwara zuciyarsa na gano dalilin sauyamin da ya yi."
Suka yi dariya ransu Ζal kafin su yi sallama.
***
Hajjo ta yi wanka ta fito ta dubi Ummita baki buΙe.
"Wai har yanzu ba ki bar wannan kukan ba? To maganin me
zai maki?"
"Kema dai kya faΙa Tanti, ni wallahi ban ga amfanin
kukanki ba. Mu godewa Allah ma tunda ya yi mana maganin komai."
Cewar Humaira dake kokarin kauda nata hawayen, Raihana ko
tana zaune shiru ba ta ce musu uffan kwakwalwarta cike da tunani iri iri.
Tasleem ba ta dakin suna can bangaren Anna ana maida zance.
"Don Allah ki bar tunanin komai ki godewa Allah. Ai
babu babban makami a yanzu irin addu'a kuma Alhamdulillah gashinan ta yi
maganin komai."
Da wannan Ummita ta hakura da kukan ta share hawayenta, ita
babban tashin hankalinta bai wuce kuma abin da zai Ζara faruwa a gaba ba. Ko ba
a fada ba ta san azzalumin mahaifinsa ne ke biΙarsa. Ita kuma idan duniyarnan
za ta haΙe babu mai raba ta da Ahmad.
"Wayarki tana ta Ζara tun Ιazu, Yaya Mubarak ne ke kira
amma kin Ζi ki Ιaga." Fadin Humaira tana mai miΖa mata wayar, ta sa hannu
ta karΙa ba ita kuwa ta faΙa bandakin don gyara nata jikin.
***
Bayan dawowar Abba daga miΖa Nusy hannun hukuma inda akai
akai ta faΙi wanda ya sanya ta ta Ζi, yana zaune yana amsa wayar Alhaji
mahaifin Fadeel dake jajanta al'amarin Jannat da kuma kwantarwa da Abban
hankali ganin dole ya shiga damuwa tunda kanwar matarsa ce, kasantuwar hakan
kuma ya jawo kananun magana iri-iri a kafafun yada labarai kowa na cewa
watakila ma ita ta sa aka sace su. Abba ya yaba sosai da samun surukin da ya
rikiΙe ya zame masa abokin kuka a rayuwa ya dinga godiya. A haka Mami ta shigo
falon ta iske shi. Ganinta bai sa Abba fasa wayar ba, tana ji yana bada labarin
abin da ya faru bayan dawowarsu daga kotu amma sam ba ta fahimci da wanda suke
wayar ba sai daga baya. Ta matsu sosai ta ji ya kai gaΙar da take so wato sanin
hannun da Nusy take, ba Ζaramin girgiza ta yi da jin wai tana hannun Ridwan ba.
Wata irin zufa ta karyo mata. Ridwan dai da Jannat ta zama karkashinsa a can
ofishin SS, kai kai kai, ita kuwa ta san zai wahala Hajiya Lubna ta iya wani
abin a kai amma dai za su gwada sa'arsu. Har Abba ya kammala wayar ba ta sani
ba sai da ta ji ya yi magana.
"Hajiya Maryam lafiya?"
Ta Ιan yi firgigit gami da dan muskutawa da tattaro dukkan
damuwar duniyarnan ta Ιora saman fuskarta. Dama ya lafiyar kura?
"Ina fa lafiya Abban yara, kana tunanin zan zauna cikin
nutsuwar ruhi bayan abubuwan da suke biyowa baya? Wallahi idan aka ce wani nawa
zai cutar da jininka zan Ζaryata hakan. Wai Jannat dai da kanta ta aikata
wannan mummunan abu ga yarannan? Haba Abban yara, ni gaba daya kunyarka nake
ji. Don Allah ka yafemin kar ka hukuntani da laifinta. Tabbas ta aikata
wauta."
Sai ga Mami ta soma kuka da hawaye, Abba ya Ιan yi shiru
kawai yana kallonta. Ba don da kunnuwansa da kuma idanunsa ya ji ya gani tana
bada umarnin a aiwatar da kisa a kansa da gudan jininsa ba, zai iya dafa
Alkur'ani dukkan abin da take faΙi kuma take nunawa a zahirance da zuciyarta Ιaya
ta ke yinsa. Sai dai ina, Maryam ta gama sirewa a ransa, kullum kuma kodayaushe
cikin addu'a yake akan Allah ya kara buΙa idanunsa ya nunamasa gaskiyar matar
da yake rayuwa da ita kuma ya rayu da ita tsawon shekarunnan cikin rufewar
idanu da rashin sanin haΖiΖaninta.
Mami ta Ιan yi turus jin babu wani sauyi ko kuma yanayin da
zai nuna maganganunta ya shige shi a saman fuskarsa, ta dube shi da dan mamaki
kirjinta na Ιan dukan tara-tara, kada dai zarginta yake yi?
"Abban yara kodai kana tunanin da sanya hannuna cikin
abin da Jannat ta aikata?"
Ya numfasa gami da girgiza kai da riΖo yatsun hannunta.
"Ko kusa Maryama, ni ba na zarginki da komai. Idan na
zargeki na ce na zargi wa? Matar da muka rayuwa tsawon shekaru sama da ashirin
cikin so da kauna ta gaskiya? Ko kuwa wacce ta riΖemin amanar gida da na yara
har ma da wadanda ba ita ta haifa ba cikin kauna da aminci? Har abada ke ba
abar zargina ba ce."
Mami ta Ιan yi yaΖe, a karan kanta sai ta ji tsarguwa, ba ta
gamsu da zantukan Abban ba. Shi kuwa idanunsa Ζurr cikin nata, danne zuciyarsa
yake yi sosai don ya fi kaunar tafiyarsu a hakan har zuwa sadda zai kama ta
dumu-dumu.
"Kawai dai lamuran ke dauremin kai, waye ya aiko a sace
Ahmad? Idan kuma ba aike bane, ita din wace ce da ta zo tafiya da shi? Akwai
dai lauje cikin naΙi wanda na tabbata Ridwan zai tsaya tsayin daka wajen ganin
ya warware wannan Ζulli."
Kirjinta ya ba da dam! Bayan sunan Fadeel, a yanzu Ridwan
shi ne suna na biyu da kaf duniya ta ji ta tsana. Wato shi ga Ιan iska, ya
shigo rayuwarta don ya wargaza ta, toh kuwa bai isa ba. A fili kuwa jinjina kai
ta yi cikin nuna damuwa Ζarara da mamaki.
"Tabbas nima abin ya Ιauremin kai Abban yara, koma wace
ce wannan yarinyar da ta kira kanta da Nusy, akwai wani sirri tattare da
zuwanta da bincike kadai zai tona shi. Ka kwantar da hankalinka gaskiya za ta
bayyana."
Murmushi ya yi sosai.
"Nima gaskiyar na fi son ta bayyana. Zan so abin da
yake Ιoye ya fito fili. Na dai yanke shawara da zarar an kammala bikin Ζ΄ar
uwarta zan maida ta hannun Hajiya Maijidda na Ιan wani lokaci mu gani. Ba don
saboda bikin ba ma tun yanzun za ta wuce, toh amma ba na son na yanke mata
wannan farin ciki."
Mami ta daure fuska tamau.
"Wace irin magana ce wannan kake yi? Wato ka raina
dukkan kulawar da Ummita ke samu a wurina?"
Shima nan da nan ya Ιaure nasa fuskar.
"Nayi zaton ke ce farkon wacce za ta yi amanna da
wannan shawarar Maryama, idan har dagaske kwanciya da nutsuwar hankalin Ummita
ki ke buri, toh fa babu abin da ya fi wannan samar mata nutsuwa."
Sai ta gane tana shirin kwafsawa da sauri kuma ta gyara
zancen ta hanyar raunana murya da fuska.
"Na sani Abban yara, amma kewarta na fi tunani da zan
yi. Shikenan dai Allah ya kawo karshen komai."
Abba ya amsa da amin, ba shi da tabbacin ko dagasken take yi
akan lamarin Ummita, ya dai bi ta da hakan ne kawai.
Sai da Abban ya fice zuwa masallaci don gabatar da sallar
la'asar sannan ta samu damar kiran Hajiya Lubna ta sanar da ita. Hajiya Lubna
ta tambayi cikakke sunan Ridwan din, nan ta sanar da ita, sai kawai ta ja
tsaki.
"Aikin banza kai, ai wannan Ιan Hajiya Fa'iza ne, matar
Late General Mukhtar AbdurRashid. Sai dai yaron a yanda na san shi yana da wani
irin kafiya akan ra'ayi da taurin kai. Za dai mu gwada sa'ar mu. Kar ki samu
damuwa. Idan ma ya Ζi bada haΙin kai ai sai mu biyo mishi ta sama."
A farko zantukan Hajiya Lubna sun Ιan sa jikinta mutuwa,
amma jin Ζarashen sai ta samu kwarin gwuiwa. Suka rabu akan duk yadda ake ciki
za su yi waya.
Daga nan Babandi ta dannawa kira ta labarta masa komai, ya
ce kada ta samu damuwa zai yiwa abin tufka. Sunan Ridwan kawai ya tambaya
cikakke daga nan ya ce zai mata aiki a kansa.
Haka ta sallame wayar zuciyarta fari Ζal.
***
Matashin ma'aikacin
dogo mai Ζira, baΖi ne, irin baΖin da hutu ya ratsa. Yana da cikar sumar kai,
ya na sanye cikin Ζananan kaya ya tsaya gaban tebur gami da Ζurawa Nusy idanu
babu wasa ko kaΙan a cikinsu. Ita kuwa tana binsa da kallo tamkar ta lashe shi,
a baya tana yiwa Wizzy kallon wani haΙaΙΙe kuma jarumi musamman a fagen bariki,
amma a yanzun da Ridwan Mukhtar AbdulRashid ke tsaye a gabanta sai ta nemi
sauran ruwa a jikinta ta rasa. Sai dai ta sani wannan ba sa'anta ba ne, ko za
ta mutu ba zai auri Ζ³AR BARIKI irinta ba da ba ta san adadin wadanda suka ci
moriyarta ba.
"Idan za ki yiwa
kanki adalci, ki faΙi gaskiya ki huta kuma hukuna ta huta. Ke din wace ce kuma
mene ne dalilinki na shiga gidan Alhaji Yusuf da niyyar satar Ιan mutum?"
Ta ji idanunta sun cicciko da Ζwalla amma ta yi shiru babu
amsa. Idan ta fadi ba amanar Wizzy kadai ta ci ba, har da na kanta don ta
tabbatar za ta yi biyu babu, wato dai babu auren Wizzy balle kuma samun wani
Ζ΄anci na rayuwa.
Ridwan ya Ιan kwankwasa tebur, ta Ιago idanunta ta kara
dubansa. Fuskarsa kaΙai ta isa sanya matarsa samun nutsuwa da bacci mai dadi.
Ko wace ce ta same shi ta huta.
"Ba ki shirya magana ba kenan? Ki sani Nusaiba akwai
hanyoyi da dama da zamu sanya ki magantuwa, idan kin zaΙi ta hanyar tsananin
hakan ce za ta faru. Idan kuwa kin shirya sanar da mu ba tare da Ιata lokaci
ba, wannan ma kin kyautawa kanki."
Wani tunani ya faΙomata sai ta yi saurin magana ba tare da
hango matsalar abin da take shirin faΙi zai jawo ba.
"Nidai ba satar Ιanta na je da niyyar yi ba. Babansa ne
ya ke da buΖatar ganinsa ya nemi alfarma na kawomasa shi Ζofar gidan koda kuwa
na mintoci ne sai na maida musu shi."
Ya ji zuciyarsa ta yi wani irin tuΖuΖi. Babansa? Shi dai da
ya ke da alhakin keta alfarmar macen da a yau yake jin babu ya ita a zuciyarsa?
Shi din dai da ya yi garkuwa da ita? Nan da nan jijiyoyin kansa suka fito raΙau,
idanunsa suka kaΙa. Ya murza yatsun hannunsa suka yi Ζara Ζas Ζas.
"A ina zamu same shi domin mu tabbatar da abin da kike
magana a kai?"
Sai kuma ta hangi wautarta, nan da nan ta soma zufa. Ya
dakamata tsawar da sai da ta miΖe tsaye tsabar firgici.
"Ki sanar da ni!"
Wayarsa dake gefe ce ta katse shi, ganin mahaifiyarsa ce ya
sanya shi saurin Ιauka ba tare da ya Ιaga ba ya fita a dakin da sauri, a
duniyar Ridwan ba shi da abin girmamawa sama da ita. Mutum ne mai matukar gudun
zuciyarta. Ya samu kyakkyawar shaida ta girmama uwa a wurin mutane. An kuma ci
sa'ar da ya kasance ba ta fiye yi mishi katsalandan kan aikinsa ba.
A wannan karon da Hajiya Lubna ta shaida mata alfarmar da
take nema na sakin Nusy bayan ta roΖi alfarmar ta sirranta sunanta. Sai ta yi
kiran Ιan nata don jin taΖamaiman wace ce Nusy din.
Ridwan jin tambayarta ya yi mamaki, koda wasa bai sanar da
ita komai game da Nusy ba amma lamari an Jannat da ma su Ummita babu wanda ba
ta sani ba. Kasancewar ba su yi zaman hira ba ne ya sa koda wasa zancen Nusy
bai haΙa su ba. Bai nata tambaya kan tambaya ba, sai ya zaΙi labarta mata
dukkan komai. Hajiya Fa'iza ta amsa masa bayan gana sauraro.
"Ka cigaba da bincikenka, ina fatan Allah ya baka
nasarar magance komai. Allah ya yi maka albarka. Ya nunamin cikar burina kafin
mutuwata. "
Ya yi murmushin jin dadin wannan addu'a, ya sani ba ta da
buri sai na son ganin aurensa, shi kuma ya sani kukanta ya zo karshe da yardar
Allah don ya riga da ya gama samun wacce yake jin zai iya Ζare rayuwarsa da
ita.
***
Labarin Jannat ya
karaΙe ko'ina, mijinta ya samu zuwa ya kuma kawo sarΖoΖinta da aka nemi ya
kawo, an siyar an haΙa da motarta amma duk da haka su na buΖatar cikon wurin
miliyan hudu da rabi. Anna ta tattara nata ajiyar da bai cike miliyan ba ta bayar, Mami kuwa dakyar ta sanya dubu dari
takwas inda ta rantsewa Anna su kadai gareta, duk da haka dai da sauran rina a
kaba. Futuha ta bada dubu dari uku, Tasleem ko ba ajiye ba balle ta bayar,
sarΖarta Ιaya ta gwal da ta mallaka ta yi shiru don ta san ba lallai ta samu ta
mayar ba. Akan haka har Futuha sai da ta yada mata magana, wai duk tsananin
kusancinta da Jannat ta kasa bada ko biyar da za'a haΙa a biya don a samu ta
fito. Ita dai ba ta biyemata ba ta banzatar. Anna da kanta ta taka har zuwa
gaban Abba da ya yi burus da batun Jannat sai shirin bikin Humaira da yake
gudanarwa, roΖonsa ta shiga yi da kuka sosai akan ya taimaka ya sa hannu ko
iyaka hakan a bayar don Jannat ta fito. Abba ya bata hakuri ya nunamata babu
abin da zai iya yi a kai tunda dai magana ba a hannunsa take ba. A hannun
hukuma da kuma yaran da aka Ιatawa yake. Wannan al'amari ya yi mugun dasa
haushin Abban a zuciyar Anna. Ta kuma daΙa roΖonsa toh ya taimaka ya cika koda
bashi ne idan ya so bayan fitowar Jannat din sai ta biya shi.
"Kiyi hakuri Hajiya, a yanzu dai ba zan ce akwai su ba,
na tattara abinda ke hannuna na bada odar kaya na shaguna na, abin da ya rage
kuma shi nake amfani da shi wajen fita kunyar jikarki da bikinta ke tafe."
Ina wuta Anna a jefa Abba don kiran Humaira da sunan
surukarta da ya yi. Kamar ta dura masa ashariya haka ta ji sai dai ta daure ta
haΙiye Ιacin ranta. Shi kuwa Abba miΖewa ya yi yana gyara zaman babbar rigarsa
don ya kammala shirin fita kasuwa a ladabce cikin danne Ιacin rai ya ce.
"Ni na fita Hajiya, lokaci na tafiya. A yi hakuri za a
samu mafita in sha Allahu."
Yana kaiwa nan ya sa kai ya bar falon sai Ζamshin
turarukansa da suka bi bayanshi suka shige kofofin hancinta.
"Kai wannan Isuhu an yi Ιan duniyan Ζarshe, yanzu a
dubi tsabar idanuna ya shirgan uban Ζarya duk don kar ya taimaki auta? Oh ni,
yau naga abin da ya fi karfina. Aikuwa duk muguntarka sai yarinyarnan na fito
tunda kai azzalumin mutum ne, sai baΖin mugunta kamar wani arne a cikinsa."
Ita kaΙai dai ta dinga bambamin nan har ta kai aya babu wani
a falon da zai taya ta daga karshe ta yi kwafa ta miΖe ta bar falon.
***
A yau Raihana ta
Ζudurta sai ta bincika wayar Maminta, duk irin kwaΙar da zuciyarta ke yi mata
ta kasa hakura. So take ta ga da wanda Mamin ke waya har ta kai ga ba shi
umarnin kashe Abbansu. Idan har ta yi nasarar samun lambar mai shi, toh kuwa ta
yanke Abban za ta kai wa don ya bayar a kamo mutumin. Wannan ya sa a yammacin
yau ranar Talata tana dawowa daga jarrabawar da suka soma na WAEC ta dinga
fakar idanun su Tasleem da Yassar dake zaune a falo ana hira ta mike ta bi
bayan Mamin zuwa dakinta da ta shiga. Ta kudurce idan har suka yi kiciΙus za ta
wayance da tambayarta maganin ciwon kai wanda gajiya da kuma damuwa suka
haifarmata, idan ko ba su hadu ba to wayarta za ta durfafa. Cikin iko na
Ubangiji kuwa ko kyallin Mamin babu sai motsin ruwa da ta ji a banΙakin.
Hamdala ta yi jiki da hannu na rawa ta dauki wayarta dake saman gado ta bude
don ta san lock din. Kai tsaye ta shiga Call log ta hau dubawa har ta kai kan
na kwanan watan da Humaira ta tafi, tana yi tana kallon Ζofar bandakin, har
idanunta ya kai ga lambar da aka yi saving da WZY wanda lokacin kiran hya
kasance da asubahi. BuΙewa ta yi ta karanta lambar har sau uku nan da nan ta ji
ya zauna a kanta don babu laifi tana da hadda, da sauri ta fita ta kashe wayar
ta bar dakin tana maimaita lambar a Ζasan ranta, Allah ya taimake ta su Tasleem
ba su ankara da ita ba, kai tsaye dakinsu ta shiga su Humaira na mata magana ba
ta amsa ba don kar ta mance lamba sai da zare wayarta daga chaji ta shigar da
lambar ta yi saving sannan ta dago ta dubi Humaira.
"Yi hakuri kina magana hankalin yana nan, kaina ke ciwo
kinga har yanzu bai bar sarawa ba."
Humaira wacce Hajjo ba ta jima da yi mata gyaran jiki ba
fatarta sai kyalli take yi don tun a Nijar aka soma ta ce.
"Wayyo sannu, bari na samo maki magani wurin
Mami."
Daga nan Humaira ta mike ta fice, dama tana son ganin Mamin
su gaisa sosai, tun zuwanta har yanzun ba su wani gaisa ba. Sun dai gaisa da
Hajjo itama sama-sama, ko me Mamin za ta yi a ganinta uwa ce a gareta. Tunda
dai aure za ta yi gwara a rabu lafiya.
A falon Ζamshinta ne ya bayar da zuwanta, Tasleem ta
kuramata idanu kamar ta shaΖo wuyanta ta mutu, cikin dogon hijabi take amma sai
wani kamshi da kyalli jikinta ke yi. Ta gaishe da su Yassar waΙanda a yanzu
babu komai tsakaninsu face mutunci. Kai ka ce ba su taΙa tsangwamarta a
rayuwarsu ba.
"Ina kike tunanin za ki je?"
Ta ji muryar Tasleem a kanta, ta juya ta dubeta. Wani irin
duba na ke a wa? Tasleem ta bude baki don mamakin hararar da Humaira ke yi
mata, kafin ta samu abin faΙi sai kawai gani ta yi yarinyar ta sa kai a Ιakin.
"Amma wannan yarinyar ta mugun rainamin wayo. Don
uwarta har ina ma ta magana ta harare ni ta yi gaba?"
"Ke dai za ki ji tsoron Allah ki bar takura rayuwar Ζ΄ar
mutane. Haba Tasleem, kina girma kina cin Ζasa. Nifa dama can kawai taya Ιera Ιari
ne amma idan za a titse ni ba zan nuna laifi guda da yarinyarnan ta aikata
gareni ba."
Cewar Yassar kenan. Tasleem ta kara kufula.
"Ai ba za ka gani ba saboda kai babu abin da ka
sani."
"Sanar da mu."
FaΙin Dawud. Ita kuwa sai ta basar, ai da kunya ta ce musu
wai kwacen saurayi Humairar ta yi mata, ita a karan kanta ta san zance ne kawai
ba hakan yake ba. Su ma kuma sun san komai. Sai ta zaΙi waskewa ta hanyar
nunamusu irin fifikon da Abbansu ke nunamata a kansu amma tamkar dai
maganganunta ba su samu wani matsuguni ba. Shi Yassar idan dai bushasha da
arziki ne, babu irin wacce ba ya yi a dukiyar Abba. Ya zama Ιan karya da
kashewa mata kudi. Dawud ma yakan yafici rabonsa amma ya fi Yassar tsoro wannan
ya sanya na sa bai fito fili ba. Toh idan dama don kudin ne suke jin haushi da
ganin kamar an fi kyautatawa Humaira, ai dai yanzun su ma suna yagar na su.
Wannan ya sanya ko a jikinsu.
***
Humaira da sallama a bakinta ta tura kai dakin Mami, ta iske
ta tsaye riΖe da wayarta tana dannawa amma ganinta sai ta yi saurin juyowa
tamkar wata marar gaskiya can kuma ta basar ta hanyar saita kanta ta ajiye
wayar ta nufi gaban madubi don goge jiki.
"Mami ina wuni."
Ciki-ciki ta amsa.
"Lafiya."
Shiru ya Ιan biyo baya, ita ba ta ce uffan ba hakanan Mami
dake shafa mai a jiki. Wayar Mamin ce ta yi Ζara Humaira ta mike da zummar Ιauka
ta miΖa mata, amma kafin ta kai ga wayar ta ji Mami ta dakamata tsawa.
"Kar ki kuskura!"
Tana fadin haka ta taso da wani mugun sauri ta kai hannu ta
dauki wayar, WZY ne ya kira. Humaira dai tana tsaye kamar an shuka icce tana
kallon Mamin har lokacin kirjinta duka yake don ba kaΙan tsawar da Mamin ta yi
ta tsorata ta ba. Mami ta Ιan saci kallonta sannan ta katse kiran, a karshe ma
ta danna Airplane mode yadda ba zai kara kira har ya same ta ba.
"Ina ruwanki da wayata? Bana son iskancin wofi, kin
wani shigo kin min tsaye a ka, toh kin gaishe ni ba ina ce shikenan ba sai ki
juya ki tafi?!"
Ta numfasa.
"Kiyi hakuri Mami, Raihana na zo karΙarwa maganin ciwon
kai ya matsa mata kuma daga nan na..."
"Kiyi me?! Raihana ni baΖuwarta ce da ba za ta iya zuwa
ta karΙa da kanta ba? Har akwai wani shamaki tsakaninmu ina uwarta
mahaifiya?!"
Kalaman sun daki Humaira da har ba ta iya Ιoye mamakinta ba
ta dubi Mami dakyau amma sai ta ji miyan bakinta ya kafe ta kasa cewa uffan.
Tsakin da ta ji Mami ta yi ne ya maido ta cikin tunaninta.
"Kiyi hakuri nayi zaton da kai da kaya duk mallakar
wuya ne, ban Ιauka akwai bambanci tsakani ba. Amma zan kiyaye tunda an
ankarar."
Tana kaiwa nan ba ta jira me Mamin za ta ce ba ta yi gaba da
sauri ta fice ta bar kofofin hancin Mamin da shaΖar Ζamshin da ta bari. Bayan
fitarta Mami ta Ιan dafe goshi, meyasa? Meyasa ta ke kasa sarrafa kanta a
kwanakin nan, gaba daya ta kasa hakurin Ιoye abin da ke ranta. Amma ta sani
adalilin wannan daukakar da ta zo ga Humairar ce alhalin nata yaran na
watangalili a gidan mazajensu sun kasa samun jin dadi da walwalar da ta so
musu.
"Ya zama dole na kula kada taΙarΙarewar abubuwa su fi
wanda nake fuskanta a yanzu."
Ta yi furucin a fili, ta kalli wayarta ta Ζi fitar da ita
daga plane mode ba don komai ba sai gudun abin da Wizzy zai fesar mata. Ta san
ba za ta ji mai kyau da kuma dadi ba don haka ta yi watsi da lamarinsa.
***
Futuha ce kwance a falonta tana danne-danne a waya kamar
yanda ta saba, sai ta wuni gida a Ζazance idan har ba yarinyar da ke mata aiki
ce ta zo ba. Ba ta kauda ko tsinke, girki ma hakanan take hakuri da yanda
yarinyar ke jagwalgwalawa ta kawomata.
Kira ne ya shigo wayarta, sunan Ζawarta Aina'u da ta gani ya
sanya ta Ιagawa.
"Marar mutunci, sai yau kika tuna da ni?" Cewar
Futuha cikin walwala.
Tsaki Aina'u ta ja.
"Ba dole ba, ke yanzu don wulakanci da daukata da kika
yi Ζ΄ar iska kika kasa sanar da ni abin bakin cikin da ya sameki, koda dai na ji
muryarki ma babu wata alama na Ιacin rai."
Sai tunanin Futuha ya ba ta ko batun Anti Jannat take yi,
kasancewar Aina'un ta san Jannat sadda suke gida.
"Toh banda abinki wannan ai ba abin yayatawa ba ne, don
ma dai kudaden da aka buΖata babu wani yawa, just 10millions fa."
Wani uban ashariya Aina'u ta saki ta wayar kafin ta ce.
"Kada dai ki cemin ba ki da labarin auren da Yakubu
mijinki zai yi da Ζ³ar Snow?"
Ai sai ga Futuha a tsaye kirr saman Ζafafunta. Kirjinta wani
dukan tara-tara ya shiga yi.
"Wannan zancen banza ne kike yi, Yakubu fa yana Dubai.
Wace Ζ³ar Snow din kike maganar zai aura?"
Wata dariya Aina'u ta saki.
"Lallai Futuha wayonki ya tashi a banza. Toh ita Ζ³ar
Snow din kika san ina take? Wallahi tana tare da shi a can ma suka hade lefen
nan da kika ga hotunansu, ina maki magana ba cikin satin nan ya ce maki zai
dawo ba? Toh tare za su taho da ita kuma yana zuwa aure za'a daura. Gidan da ya
fidda ki a ciki, nan zai ajiye ta har an Ζara yi mata wani mahaukacin gyara ya
yi kyau."
Ihu mai karfi Futuha ta saki har sai da ta razana Aina'u.
"Ζarya kike yi! Ba dai mijina ba! Ke uban wa ya
fadamaki duka wannan?! Aina kar ki kashe ni, kirjina zafi yake ina ganin
dishi-dishi."
Aina'u ta hau rantsuwa da Allah akan dagaske take yi, kuma
ta ce tunda har ba ta aminta ba za ta hankaΙo mata hotuna ta sha kallo. Ko
sakanni biyar ba su yi ba da ajiye wayar Aina'u ta aikomata hotunan da Ζ³ar Snow
ke Ιorawa tana rufe fuskar Angonta. Gaba daya Yakubunta ne a hoton. Ta kuwa
buga wayar jikin talabijin dinta gami da fasa uban Ζara. A haukace ta shiga
daki ta dauki mayafi sai gida.
***
Raihana bayan da ta lura hankalin kowa ya tafi akan Humaira
da Hajjo ke yiwa gyaran jiki kasancewar yaran Baba Amina sun zo itama tana
dakin, sai ta mike ta nufi bangaren Abba. Mami ta fita unguwa, cikin sa'a ta
iskeshi zaune shi Ιaya ya kammala shan fura. Ganinta ya sanya shi Ιan zubamata
idanu da amsa sallamarta.
Ta Ζaraso ta zauna a gefe.
"Rahane (sunan da ya ke kiranta a wasu lokutan), ba ki
da lafiya ne kwana biyun nan?"
Ta sunkuyar da kai gami da bude baki cikin sanyin jiki ta
amsa.
"A'a Abba, lafiyata kalau."
"Kin kasa cire maganar can a ranki ko? Meyasa ba kya
jin nasiha? Nace maki ki bar komai a hannuna tun da na riga da na ankara toh da
yardar Allah hakan ba zai Ζara kasancewa ba. Ai wataran za a kuma kwatawa,
kinga sai ya kasance muna da shaidu ba kamar yanzu ba."
Raihana da tuni hawaye sun jiΖa fuskarta ta gyaΙa kai da Ιan
jan majina.
"Toh Abba, dama na dauki lambar wanda Mami ta kira a
ranar ne shi ne nace bari na kawomaka nasan zai taimaka wajen bincike."
"Ya aka yi ta bari kika taΙa wayarta? Na sha gwada yin
hakan amma ban samu nasara ba."
Ya fadi cike da jin dadin wannan nasara, ko ba komai za'a
bincika a kamo shi yaron da aka sanya ya aikata laifin. Ta ba shi labarin yanda
aka yi ta dauka sannan ya fiddo wayarsa ta sanya masa lambar.
"Kiyi hakuri Raihana, na sani daga ni har ke mun kasa
yarda da abin da yake a zahiri saboda inda ake zatonsa ba anan aka iske shi ba.
Abin ya zo da daure kai da al'ajabi, ina fatan wannan ba zai hana ki cigaba da
yin biyayya gareta ba, kema kuma ina fatan da zarar kin kammala jarrabawa ki
yiwa shi yaron can magana ya fito a yi magana."
Gyada kai kawai Raihana ta yi, ita yanzu komai ma na duniyar
ji take ya sire mata, har kullum fargabarta bai wuce da idanun da za ta dubi
Humaira idan wannan Ιanyen aikin na Maminta ya fito ba.
Daga haka suka rabu da Abban. Shi ko Abba kai tsaye ya tura
lambar zuwa ga D.P.O sannan ya kirashi suka yi magana. D.P.O ya tabbatar masa
da yardar Allah za su bincika har su cafke mai wayar. Da haka suka yi sallama.
***
Babandi kenan, baΖin
kuma gabjejan Ζato mai tumbi zaune saman kujera ya ci uban rawanin da ko zafi
bai yi masa. Mami na daga gefensa a zaune, falon tsaf sai iskar fanka ta ko'ina
domin gidan Malam Babandi solar ce ke aiki. Tsohon Malami ne kuma babba da ya
ci ya hantse da haram. Ya dubi Mami dakyau.
"Gaskiya Hajiya Maryam akwai matsaloli sosai. Na farko
kin yi saken da yaranki suka san komai dangane da abin da kika shuka, wannan
idan ba ki manta ba yana daga cikin sharuΙΙan da na taΙa gindaya maki a baya,
wato kar ki kuskura a yanda kika faro mu'amalarki da kowa, ki bada Ζofar da
wani ko wata zai ji. Idan ban manta ba kwanaki can kin faΙamin kin sanar da ita
babbar yarinyarki, koda muka bincika muka ga ba zai haifar da matsala ba amma
duk da hakan ai na kwaΙe ki. Yanzu dai ita wannan yarinya taki ta biyu, Yasmeen
take ko?"
"Tasleem." Mami ta gyara masa da muryar da ta fito
daga can Ζasan maΖoshinta, a duniya ba ta son rashin nasara a kan komai ma ba
wai iyalinta ba.
Babandi ya cigaba da zancensa.
"Yauwa Tasleem, yarinya ce mai taurin kai da kafiya a
yanda na gani, zai wahala ta iya bar wa cikinta komai."
"Nidai don Allah Babandi a yi dukkan abin da ya dace
idan har kwalliya za ta biya kudin sabulu, sannan batun auren ita Humaira da
yaron can, kiyi hakuri, ban hango wani katanga da zai yi sanadin rushewarsa ba.
Sai dai abu Ιaya, ki zaΙi ta Ιangaren da kike son a musgunawa rayuwarta mu gani
ko zai yiwu. Abu na gaba kuma wato mijinki Isuhu, ba zan ce maki ga abin da na
gani ba, amma wacece Maijidda? A zuri'arsu akwai wata mai suna hakan ne?"
Gaba daya abubuwan da yake faΙi tana jinsa ba don tana
fahimtar komai ba, ba ta tashi dawowa hayyacinta ba a gigice sai da ya ambaci
Maijidda. Ta ji dam! Wata iriyar faΙuwar gaba. Idanu waje take dubansa.
"Me..me kake son ka ce?"
Babandi ya girgiza kai.
"Tambayarki nayi ko akwai Maijidda? Ai ban ce ba
tukunna."
"Babu, ba mu da wata Maijidda hakanan shi kansa
Alhajin."
Babandi ya yi wani irin murmushi gami da girgiza kai.
"Toh ai shikenan."
Ta dube shi cikin fitar hayyaci.
"Me zai faru da shi Isuhun da Maijiddar?"
Ya Ιan zubamata idanu sai kuma ya numfasa.
"Duhu na hanga, ban gane komai ba. Na dai ga wata an
kuma cemin Maijidda ce. Ban san manufar hakan ba."
Gumi ne ya shiga kwaranyo mata. Maijidda dai? Toh don uwar
Maijiddan me za ta yi a rayuwar mijinta? Kada dai waccan tsohuwar kilakin da
duk mijin da ta aura mutuwa yake yi ita ce Maijidda da Babandin ke nufi? Toh ma
da take tunanin aure ne zai faru tsakanin shi Isuhun da Maijidda?
"Ina!! Wallahi na rantse maka idan ni Maryama ina raye
Babandi ba ka isa ba! Ashe dama kai macucin banza ne?! Wato aure ka hanga
tsakanin baΖar annobar can da mijina shi ne za ka yimin na Ζ΄an bariki?! Lallai
kai cikakken marar hankali ne da tunani! Ni Maryam kake tunanin ina raye san
bari Isuhu ya auri wata bayan ni?!"
Babandi ya ji zafin maganganunta.
"Hajiya Maryam kar ki sake ki zage ni. Ni nace maki na
hangi aure ko zama tsakani? Har yau duk da irin shekarun da muka kwashe da ke
ki iya kallon cikin idanuna ki kira ni da marar hankali kuma macuci?!"
Idanun Mami sun rufe ruf akan baΖin kishin da ya tasar mata,
ji ta yi kamar Abban take gani zaune a gabanta. Babu abin da take haskowa sai
tabbatuwar aure tsakanin Maijiddan da Abba. Jikinta kuwa har rawa yake yi don
haka a harzuΖe kuma cikin kururuwa ta daka masa tsawa.
"An kiraka Ιin! Nace ka yi uwar da za ka yi Isuhu! Ni
ce ma banzar da na zauna sauraron tatsuniyoyinka marasa kan gado. Yo mutumin da
yake da mata har huΙu hakan bai isheka ba kana neman almajiranka maza kai zan
tsaya ka magancemin matsalolina alhalin kodayaushe lalacewa yake! Ni nan na
ishi kaina! Zan yiwa kaina komai! Daga yau idan ka kara ganin Ζafata a inda ka
ke kirani da wani sunan ba Maryam ba!"
Tana kaiwa nan ta yi gaba tana ji yana fadin sai ta yi
muguwar nadamar zageshin da ta yi amma ba ta ko juyo ba balle ta ji nadamar
kalaman da ta yi mishi.
***
Kamar tare suka isa cikin gida da Futuha wacce ke faman
kwara ihu tana kiran wayyo. Mami duk da yanayin tashin hankalin da take ciki
sai da ta ji cikin ya yi mugun Ιurar ruwa, idan akwai wani abu da ta tsana a
rayuwarta bai wuce ta ji ko ta ga wata masifar ta afkawa yaranta ba. Yaran da
ta ci kwakwa wajen ganin rayuwarsu ta inganta. Ta Ιoye ainahinta ga duniya
domin ta samu kyakkyawar shaidar yaudarar mutanen da take tare da su duk don
ingancin da ta ke son rayuwar yaranta su yi.
"Ke! Meye haka? Wannan wane irin hauka kike yi kina
neman tara mana jama'a?"
Futuha cikin kuka take sanar da Mami labarin auren Ζ³ar Snow
da Yakubu. Ta Ζara da faΙin.
"Ni wallahi Mami ba zan zauna da ita ba, na fasa
aurensa dama ai bakin cikin abin da ta aikata min na Ιata sunana a soshal
midiya ne ya sanya na aureshi. Toh wallahi na gama aurensa!"
Jiri sosai ta ji yana nema ya kayar da ita, daidai lokacin
kuma aka buΙewa Fadeel katon Ζyauren gidan ya shigo ya yi parking, ganin Mami
ya sanya shi fitowa sai baza Ζamshi yake har wata Ζ΄ar Ζiba ya Ζara saboda
kwanciyar hankali da murnar samun farin cikinsa. Ya ci ado cikin shaddarsa
coffee da hula kalarta.
Mami kallonsa take yi, kallon kai ne silar rugujewar rayuwar
Ιiyata Tasleem, kai ne kuma silar da aka kama Ζ΄ar uwata Jannat. Shi kuwa a
kunyace da kuma ban girma ya Ιan russuna ya gaisheta. Madadin ta amsa sai ta buΙe
baki da zummar gasa masa baΖaΖen magana amma ta fasa hango Yassar da ta yi ta
baya yana mata alama da hannu, alamar roΖon ta yi hakuri ta bar wa cikinta.
Yana jin duk yanda suka yi da Futuha, ta harari Fadeel kawai ta ja hannun
Futuha da ta Ιan danne kukan ganin Fadeel din zuwa ciki. Bai yi mamakin hakan
da ya gani tattare da Mamin ba don ya lura tun a kotu take shaΖe da shi saboda
kama Jannat, amma a zatonsa tunda har dai kauna ta don Allah ta ke yiwa su
Humaira ai ya ci ace ta ji dadin tonuwar asirin wanda ya Ιata musu suna. Sai
Yassar ne ya ja shi zuwa masaukin baΖi.
***
Suna shiga falon suka
yi karo da Humaira ta yi kyau shar da ita cikin lemon green din leshi ta yafa
baΖin mayafi. Ba ta yi kwalliyar a zo a gani ba amma fa fatarta ta gogu tas.
Ganinsu ya sanya ta gaida Mami gami da yi mata barka da zuwa bayan ta Ιan kula
da yanayin tashin hankalin dake saman fuskokinsu har ita Futuhar.
Mami ba ta amsa mata ba sai ta yi gaba, itama Humaira ganin
hakan sai ta soma tafiya domin ta fita.
"Ke!"
Ta tsaya gami da juyowa ga kallon Mamin.
"Ki yimin farfesun nama yanzu ina jin yunwa."
Humaira ta Ιan yi turus, ta mance rabon da Mamin ta sanya ta
koda tafasa ruwan zafi ne. Sai yanzun da Fadeel ya zo sannan za ta kirkiro
aiki?
"Ko ba za ki yi ba?"
Tambayar Mamin ya katse tunaninta, jiki a sanyaye ta ce.
"Zan yi."
"Toh wuce ki je."
Daga nan Humaira ta kama hanya ta nufi kicin. Wannan ya
faranta zuciyar Tasleem dake zaune har da kyakyacewa da dariya.
***
A can kuwa Fadeel da ke zaman jira shiru, yana kokarin kiran
wayar Humaira sai ga Abba ya shigo. Bayan sun gaisa ya ce
"Ba ta fito ba ne?"
Fadeel yana Ιan sosa Ζeya amma bai ce komai ba.
"Shikenan." Abin da Abban ya furta kenan ya nufi
ciki.
*DUKAN RUWA*
_Ba zai hana gwarje amo ba._
Da Raihana ya soma kiciΙus ta fito daga kicin inda ta tarar
Humaira ta kama aiki ranta duk a Ιace don ta yi duk iyaka yinta ta bar mata
aikin ta tafi amma ta ce sam tunda Mamin ta sanya ta za ta iya yi ta je ta ba
wa Fadeel hakuri ya tafi kawai. Ganin Abban itama sai ta ji sanyi ba ta ko
gaida shi ba ta tafi kai tsaye kan abin da ke cin ranta.
"Abba ga
Humaira ta bar Yaya Fadeel ya.."
"Ya isa, kiramin ita."
Abban ya katse ta, ya yi daidai da fitowar Mami daga
dakinta. Ganinsa sai ta haΙe girar sama da ta Ζas, kallo daya ya yi mata ya
kauda kai shima ta sa fuskar a Ιaure sakamakon fitar da ta yi ba da izninsa ba
a yau, wani abu da ya zame masa baΖon abu wanda ba ya jin ta taΙa yi masa
hakan. Humaira ta shigo falon tare da Raihana, hawaye kwance saman fuskarta
kafin ma ta kai ga cewa wani abu Abba ya tari numfashinta.
"Shirya ki je kin bar mutum zaune yana ta
jiranki."
Jiki a sanyaye ta dauki mayafinta dake saman kujera, Mami
itama zuciya a sama ta ce.
"Ni kuma ban miki iznin fita ba! Aiki na sanya ta ai,
don me shi ba zai iya jiran ta kammala ba tunda ganinta a yau din ya zame masa
tamkar rubutu a saman dutse?"
Humaira sai ta yi turus, Mami dai ba za ta daina shayar da
ita mamaki ba. Ζiyayyarta a fili na wannan auren ta ke nunawa ba ta ko iya Ιoyewa.
"Duk ikonki akan ta bai kai ya ni ba, daga ita din har
ke din karkashina ku ke, babu dalilin da zai sa na zuba idanu a mayar da ni
sakarai a gidana. Don haka Humaira kar ki yarda na Ζara ba ki umarni na biyu,
ki wuce yanzu."
Ambatonta da Humaira da Abban ya yi wanda bai taΙa kwata
hakan ba ya sa ta fahimci abin ba mai sauki bane don haka sum sum ta sa kai ta
bar falon tana jin Mami na bambamin faΙan wai Abban ya nuna dagaske ba ita ta
haifi Humaira ba kuma ba ta ita ta ce mata ta yi, ta yi din ba. Ita dai ta fice
da sauri tana share fuskarta.
Abba ya dubi Mami dakyau, kamar zai ce wani abu sai kuma
ganin Raihana a wurin. Juyawa ya yi zuwa bangarensa can din ma bin bayansa ta
yi.
"Diyarka ta dawo gida saboda maci amanan mijinta zai
auri abokiyar faΙanta. Nima kuma ina goyon bayanta don ban ga wani dalilin da
zai sa ya yi mata wannan tozarcin ba a idon duniya."
Cikin al'ajabin wannan sabon labari da ma rashin fahimtar
inda aka dosa Abba ya kalleta kallon tsanaki.
"Wane tozarcin? Wa kuma kike magana a kai?"
Ta harareshi kamar
idanunta za su zazzago.
"Matan da ka aurar har su nawa ne? Ina magana ne kan Ιiyarka
Futuha. Shi Yakubun ko sanar da ita batun Ζara auren bai yi ba saboda ya san
auren cin amana ne. Kuma ni dai Maryam yanda ba zan dauka a yimin ba hakanan ba
zan zuba idanu a halakar da kuruciyar yarana ba a hana su walwala da jin dadin
zaman gidajen mazajensu. Tana nan gida na kuma hana mata komawa, ta yi zamanta
har sai ya zo ya janye batun auren can da zai yi. Ya rasa wacce ma zai aura sai
yar iskar Tiktok da ta yi mata Ζazafin zina a baya?"
Tsananin Ιacin rai da baΖin cikin da ma nadamar kyawawan
shaidun halayyar da ya yiwa Mami a baya suka bi suka lulluΙe shi, ga kuma zafin
da maganganunta suka haifar a cikin Ζirjinsa. Ya miΖe tsaye jijiyoyin kansa sun
fito raΙau tsabar Ιacin rai. Wayarsa kawai ya fiddo ya danna lambobin Futuha,
umarnin ta zo ya yi mata, ba jimawa ta shigo tana Ιari-Ιari ta zauna can gefe
kusa da Mami. Shi kuwa Abba har lokacin yana daga tsaye yana safa da marwa, sai
bayan zaman Futuhar ya soma magana murya a kausashe.
"Maryam! Idan har na isa da ke da kuma Ιiyar da kike
tutiya taki ce, ni Isuhu ba zan lamunci zamanta a gidana ba alhalin da igiyar
aure a kanta. Ke kuma na rantse maki
kika yi gangancin kwana a gidannan sai na nunamaki ni Isuhu na haifu kuma babu
wata Ιiya ko Ιan da zan haifa a cikina ya yi tunanin zan biyewa son zuciyarsa
na banza!"
Mami dama a Ζule take don babu abin da ke yawo a
kwakwalwarta sai maganganun Babandi, wani mugun haushi Abban ke ba ta. Ta kuwa
miΖe itama a zafafe ta ce.
"Ni kuma nace babu inda za ta je! Ba zan yarda da auren
cin amana ba! Idan kai ba ka san darajar abin da ka haifa ba har ka nema mishi
Ζ΄anci, ni nan Maryam ban haifar yarana ga wasu Ζattin banza don su tozartamin
su ba! Ai ba su tashi sun ga uwarsu da kishiya ba!"
"Ba zan yi mamakin kalamanki ba Maryam saboda a yanzu
ne nake sanin ainahinki ba lulluΙin da kika yimin ba a baya, yanzun kike
nunamin ke wace ce. Toh ki sani, ni dai gida nawa ne, ban ginashi da kwandalar
kowa a cikinku ke da yaranki ba. Wallahi a yau sai Futuha ta koma gidan mijinta
ba za ta kwana a gidana ba, idan kuma kika taka umarnina sai dai ki sa Ζafa ki
bita duk inda za ta je amma na yi rantsuwa babu kaffara yarinyarnan ba za ta
kwana a gidana ba. Ba kuma tsoronki nake ba da kike tutiya da fankamar wai ba
su buΙi idanu sun ganki da kishiya ba! Amma ki sa a ranki zan nunamaki ni din
namiji ne ba MIJIN MACE DAYA ba."
Kirjin Mami ya buga dam! Maijidda ita ta faΙo ranta.
"Me kake nufi?"
Ta tambaya a rude, madadin ya ba ta amsa sai ya sa kai ya
shige dakinsa. Futuha kuwa kuka sosai take yi jin irin yanda iyayen ke musayar
yawu. Ta miΖe tsaye ta kama hanya.
"Ke, na fa ce babu inda za ki je. Ki shiga cikin dakina
kiyi kwanciyarki."
Za ta so hakan amma fa ba za ta iya ba don ta tsorata da
yanayin Abban. Ta sani mutum ne dama tun can mai zafi idan an taΙo shi sai dai
kalar Ιacin ran yau da ta gani ba irin wanda ta saba ganinsa ciki ba ne a
ire-iren lokutan da aka taΙo shi ba. Wannan ne dalilin da ya sa cikin
sheshsheka ta ce.
"Aa Mami, zan koma amma na rantse idan Yakubu ya dawo
sai ya bani takardata ba zan iya cigaba da rayuwa da shi ba."
"Don ubanki ni za ki watsawa Ζasa a ido?"
Futuha ba ta amsa ba sai kawai ta yi gaba ta fice da gudu
gudu. Mami kam zama ta yi ta fidda dankwalinta tana yiwa kanta firfita saboda
ji take ma iskar dake wulwulawa a dakin kamar feshin iskar wuta ce ba ta yi
mata yanda ya kamata. Yau dai Abba da kansa ya iya kallonta ya faΙamata
maganganun cin fuska son ranshi? Wato rigar mutuncin da ta ara ta yafa ya fiye
mata alheri akan zahirin ita a idanunsa? Dama ba mallakarsa ce ta yi ba yake
shakkarta kawai albarkacin wancan kyawawan halayyar da ta ke nunawa ta ci? Toh
wai ita ba ta ma fahimta ba, aure yake nufin zai yi?
"Wallahi Isuhu ba ka isa ba! Ka yi kaΙan!!"
Ta yi furucin cike da hargagi da Ιaga murya, babu wani da
zai ba ta amsa don haka ta kwashi jiki ta yi bangaren uwarta, yau ce ranar
farko tun bayan aurenta da ta ji tana buΖatar shawararta wajen waΙannan
Ζullace-Ζullacen da take yi. Shakka babu idan gininta na tsawon shekaru ya
rushe ko kuma ya karasa rushewa za ta kwashi kashinta a hannu.
***
Fadeel ya yiwa
Humaira duba na tsanaki, tana cikin wata damuwar da duk iyaka kokarinta na yin
murmushin yaΖe sai da ya Ιago ta.
"Ka yi shiru." Ta furta a sanyaye ganin sun kwashi
mintoci cikinsu babu alamun wani zai ce uffan. Ita tunanin sabuwar Mami da
manufofinta ke dukan zuciyarta shi kuwa damuwarta ce ta haifar da ta sa. Tun da
ya ga yanayin da Mami ta tarbe shi ya san akwai wata a Ζasa, ya kuma fi
tunanin rashin nutsuwar Humaira saboda
ganin Mamin cikin wani yanayi ne. Bai kawo komai bayan wannan ba.
"So nake ki gama tunaninki."
Ta girgiza kai.
"Ni ba tunani nake yi ba fa."
"Boddo please. Ko meke damunki kiyi hakuri ki cire shi
a rai idan ba haka ba zan samu Abba da Alhajina yanzu kawai a daura auren na
wuce da ke gidana."
Ya ba ta dariya dagaske, ta Ιan bishi da hararar wasa. Shi
ma murmushin ya yi mata gami da Ιan Ιaga gira kaΙan. A Ζarshe suka sha hirarsu sosai da ta mantar
da ita Mami da sabgarta. Sun Ιan jima kafin su yi sallama ya fice.
***
Anna ta muskuta tana kara tamke fuska, ai ita yanzu kam a
duniyarta babu abin da ta tsana sama da Abba da wadancan yarannasa biyu da suka
yi sanadiyyar kama autarta. Ta sanya gonarta Ιaya babba ta can Agadez a kasuwa
yanzu haka an samu mai siya duk da akwai faΙuwa sosai a yanda aka taya amma ita
dai burinta a samu abin cikawa a fiddo Jannat wacce mijinta ya yi Ζememe ya
kuma rantse ba zai ba da ko biyar ba tunda ba shi ne ya sanya ta aikata ba.
Dama yana cike da jin haushin yawon da ta ke yi bini-bini idan abu ya tashi sai
ta matsa mishi za ta zo Nijeriya. Ga rashin Ιaukar yan uwansa da daraja,
ganinsu take Ζ΄an Ζauye futuk.
"Ke Maryam, idan za ki buΙe zuciyarki ki fito ki nunawa
wancan sokon mijinnaki Maryam ce da ba a nunamata Ιan yatsa ba ta karya ba. Ai
ni da ace tun farko ma nasan wautar da kika yi kenan na wannan makircij da bai
kai ki ko'ina ba da ba zan bari ba. Ai gwara mutum ya sanka da halinka amma
yanzu zai dinga yi maki wani kallo saboda ba haka kika nunamasa a farko ba.
Yanzu dai ki jira Ζ΄ar uwarki mu samu ta biya wadancan karnukan kuΙinsu sai a
san me za a yi."
"Yanzu Anna sai Jannat ta fito za ki duba
matsalata?"
Mamin ta furta cike da takaici.
"Ke ba kya tausayinta ashe? Ita tana can a garΖame
cikin yanayin a tausayawa ke kuwa ai naki mai sauki ne. Ki tashi tsaye ki
Ζwatarwa yaranki Ζ΄ancinsu ta Ζarfin tuwo idan ba haka ba dama na fadamaki tun
ba yau ba, Isuhu zai iya tattara rabi da kwata na dukiyarsa da sunan na Ummita
ne yake juyamata."
Annar ta yi mata wani tuni mai Ζarfi da muhimmanci, tabbas
akwai dukiyar Ummita a hannun Abba, duk kuwa da cewa shima Abban ya samu
gadonsa a dukiyar Ζanin nasa. Tana tsoron Ummitar ta tashi aure ya ce zai
tattara komai ya damΖa mata abinta da mijinta, idan kuwa hakane ita ya dace ta
samarwa Ummita miji ba kowa ba. Mijin da za ta iya juyashi son ranta ba wanda
zai gagareta sarrafawa ba. Mijin da ba zai zama Ιan da ta haifa da cikinta ba.
Toh wa za ta samu haka?
"Ina magana kin yi shiru."
Kalaman Anna suka katse tunaninta. MiΖewa tsaye tana wani
murmushi mai tarin ma'anoni.
"Zan san abin yi."
Daga haka ta fice ba tare da ta Ζara ba Anna amsar
tambayarta na me za ta yi ba.
***
A kwana a tashi cikin
hukuncin Allah har ranar sanya Humaira a lalle ya gabato. Ana gobe za a soma
shagalin bikin sai ga yan uwanta daga Nijar sun dira a gidan. Mami duk shige da
ficen da Baba Amina ke yi da ma wasu a Ζ΄an uwan Abba da kuma Hajjo babu ko Ιaya
da ta sanya hannunta ciki. Ita kuwa Humaira ta tattara batun Mami ta ajiye gefe
bisa shawarar Hajjo da Baba Amina. Ta bi Mamin bi bana wasa ba amma Mamin ba ta
ko sauraronta. Ga Tasleem a dakin da babu damar a yi wani abin sai ta tanka ta
faΙi baΖa, a Ζarshe ma ta tattara ta koma Ιakin Anna da kwana. Hankalin Tasleem ya yi masifar tashi ganin
dagaske dai bikin Humaira da Fadeel za'a yi, wannan na nufin za ta tashi a
tutar babu kenan? Ta iske Mami hankali a mugun tashe tana kuka kamar ranta zai
fita ita fa lallai Mamin ta san abin yi don zuciyarta ba za ta iya zama ta yi
haΖurin ganin hakan ya kasance ba. Mami ta dafe kanta dake tsananin sarawa,
kwana biyunnan ba ta iya bacci saboda damuwa.
"Don Allah Tasleem ki rabu da ni da wannan koke-koken
naki. Na samu tabbaci daga Babandi aurennan fa sai an yi babu makawa. Wannan
borin naki zai tashi a banza."
Tasleem ta dora hannu a kai wani sabon kukan na kwace mata
har da majina. Ashe haka baΖin ciki yake? Haka radadin kishi yake? Toh ita yau
duk biyun take ΙanΙana, ganin Humaira kamar wata sarauniya ya sanya ta ji inama
ta kashe kanta ta huta saboda baΖin ciki da azabar kishi. Har ji ta yi wasu Ζ΄an
uwan Abba na ce mata ranki ya daΙe don hauka, acewarta.
Mami da ta Ζuramata
idanu gaba daya sai ta ba ta tausayi, Fatima ta haifa mata baΖin ciki ta kuma
bar duniyar ta bar ta da shi, gashinan tana Ζunsa. Can ta nisa ta ce.
"Toh ko za ki je wajen Babandi, dama ya ce ko bayan
auren na fadi abin da nake son a yi musu amma saboda takaicin abin da naji gami
da Abbanki da Maijidda sai idanuna ya rufe na ci mishi mutunci. Ki je ki ce
nace ya yi hakuri ya dubi lamarinki ya samar maki da mafitar da ta dace. Zan
biyashi ko nawa ne."
"Mami ki kirashi a waya toh."
Harararta ta yi ta ja tsaki.
"Kiran me zan mishi bayan na ce maki ga yanda muka yi
da shi? Ke dai zan ba ki lambar da kwatance ki je."
Ta amsa da toh, a take kuwa Mami ta dauki waya ta turanmata
lambar ta whatsapp dinta ita kuwa ta yi mata sallama ta fice bayan ta bi
umarninta na shiga banΙaki ta wanke fuskarta.
A wajen Anna ta bar Ιiyarta ta fice bayan ta sa facemask ta
rufe hanci da bakinta yanda babu wani da zai gane ta a hanya.
***
Babandi ya kalle ta
tsaf, ya buga wani murmushi mai tarin ma'ana bayan gama sauraronta da kuma jin
daga inda ta zo wajensa.
'Kin tafka kuskure babba Hajiya Maryam. Kin kashe Ιiyarki da
hannunki.' Ya yi furucin a Ζasan ransa.Ya nisa kafin ya ce.
"HaΖiΖanin gaskiya ba don ina ganin mutuncin Hajiya
Lubna da ta zama silar haΙuwata da Mahaifiyarki ba, da babu abin da zai sa na
Ζara karΙar wani aikin da ya shafe ta da ma wani nata. Amma tunda har ta
fahimci ni Babandi ba za ta iya gudanar da rayuwa yanda take so ba tare da
taimakona ba (Waiyazubillah) toh shikenan zan taimaka maki albarkacin
hakan."
Tasleem ta saki wata doguwar ajiyar zuciya tana Ιan
murmushin da ya Ζara kwaΙaitawa Babandi ita. Ya lashi leΙΙansa gami da mayar
mata da martanin murmushi kafin ya hau buge-bugen Ζasarsa sannan ya Ιago ya
dubeta
"Gaskiya Malama Tasleem yau dai kin zo a sa'a domin
kuwa koda na Ζara bincikawa na tabbatar za a iya fasa auren Humaira da Fadeel,
akwai kuma gagarumin sa'a da ke nuni da cewar za ki zama mallakinsa nan gaba.
Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba, aikin da za ki yi hakan ya faru ba mai
sauki ba ne.""
Da sauri ta tari numfashinsa.
"Na rantse kowane iri ne aikin zan iya yinsa muddin zan
auri Fadeel."
Ya jinjina kai yana shafa gemunsa.
"Sai mu'amala ta shiga tsakaninmu har na tsawon wata Ιaya
kafin aurenki da Fadeel. Ita ko Humaira a yau zan fara aiki a kanta zuwa ranar
da ki ka ce za'a Ιaura auren ina mai tabbatar maki ba zai yiwu ba. Idan dai
kika ba da haΙin kai yanda ya dace kuma kika yi gum da bakinki ma'ana kika Ιoye
cikinki hatta ga wacce ta turoki nan, toh shakka babu za'a dace. Za ki yi
mamakin irin mahaukacin son da Fadeel zai soma yi maki har sai kin ce ya yi
yawa."
Tasleem ta Ιan yi dum, ga Ζoshi ga kwanan yunwa. Tsaf ta
karanci me yake nufi da mu'amala amma sai ta ji kamar dai hausarta akwai gyara
a jikk wannan ya sanya ta Ζara neman ya yi mata Ζarin bayani. Nan fa Babandi ya
buΙe mata komai ta tabbatar dai saduwar ita yake magana a kai ba komai ba. Ta
Ζare mishi kallo, jibgegen Ζato mai mummunan fuska daidai gwargwado. Sai dai ga
dukkan alamu yana amfani da manyan turaruka masu Ζarfi marasa dadin kamshi. Ba
dai za ka ce yana tashin hamami ba.
'Kar ki sake ki cuci kanki, mene ne a ciki don kawai dai
saduwa? Fadeel fa ne za ki aura ya zama a ΖarΖashin ikonki.'
Wani sashi na zuciyarta ke mata tuni, nan da nan ta ji ta yi
na'am musamman da ta Ζara hasko kanta cikin wannan katafaren gidan da ta samu
labarin ya danΖara na Humaira. Ga kuma kayan alfarma na lefe wanda zai dawo
mallakinta. Duniya ta yiwa idanunta rumfa ruf, ba ta hangen komai sai Ιaukaka
da shaharar da ke gabato ta. Wannan ya sa ta dubansa a tsanake.
"Na amince amma da sharaΙin sai na yi tsarin iyali
gudun daukar ciki."
Ya yi wani murmushi na mugunta, a ransa faΙi yake.
'Ashe ba ma fansar nayi niyyar Ιauka akan Hajiya Maryam ba.
Ai sai kin haifa mata Ζaramar bokanya ko kuma boka.'
A fili kuwa sai cewa ya yi.
"Ke da kike gaban Babandi, ai ba ki da matsala akan
tsarin iyali. Akwai layar da zan ba ki, muddin kika sanya a bakinki yayin
komai, ina mai tabbatar maki babu ke babu samun ciki. Ba ma a kaina kawai ba,
ko tsakaninki da sabon Angonki Fadeel idan har ba ki shirya ki haihu da shi da
wuri ba wannan laΖanin zai maki aiki da ma wasu na sirri. Mallakarsa kuwa kin
yi kan gama."
Wani dadi ya ratsa zuciyar Tasleem, ta kara samun Ζwarin
gwuiwar da ta ji ko rai aka ce ta kashe akan ta samu cikar burinta za ta iya
saboda kwaΙayin duniyar da kuma daukakr da ta ke hasasowa kanta muddin ya
kasance Fadeel ya zama mijinta.
"Shikenan, Malam nidai na shirya komai ma a yi tunda
za'a dace. Sannan nidai koda ace Humaira an raba ta da Fadeel, bana son ta auri
mijin da ya fi shi ko nan gaba. Na fi kaunar ta auri ΖasΖantaccen da za ta
dinga zuwa wurina da ΖoΖon bararta na neman taimako."
Babandi ya jinjina kai, ai barewa ba za ta yi gudu ba Ιanta
ya yi rarrafe. Ya san ba a Ζas ta tsinci wannan muguntar ba.
"Burinki zai cika. Ina zuwa."
Ya miΖe ya shiga Ιakinsa kafin ya fito ya miΖa mata laya da
umarnin ta tura bakinta. Ta bi umarninsa sannan ta mike suka nufi dakin
kirjinta na harbawa amma hakanan ta daure, ba ita ta bar gidansa ba sai kusan
goma da mintoci na dare. Babandi ya bi ta da kallo bayan ta fice ya kyakyace da
dariyar nishadi, wa ya Ζi banza a rayuwa? Ai wannan lamarin karΙaΙΙe ne ba kuma
ya jin zai bar rayuwarta ta sarara. Hakika Tasleem ta faΙi hannunsa. Daga nan
ya mike ya gyara jiki ya bada umarnin kada hadiminsa ya bar wani ko wata su
shigo ganinsa a sanar da kowa ba ya nan. Aiki sosai ya zauna yi na mallake
Tasleem da kuma sa mata tsoronsa ta yanda ba za ta taΙa iya tsallake umarninsa
ba saboda ba kadan ba ya ji ya kamu da matsanancin buΖatarta kuma yana son
hakan ya Ιore ko don ya gwadawa Maryam ita ba komai ba ce.
***
Hankali tashe Mami ta ja Tasleem zuwa dakinta ta rufe.
Dubanta take yi a tsanake. Jikinta banda Ζamshin turarukan da Babandi ke amfani
da su babu abin da ke tashi. Ta kara shinshinarta sosai, Tasleem ji ta yi kamar
ta saki fitsari a wando.
"Me ya yi maki?"
Ta tambaya cikin tsananin ruΙani. Girgiza kai Tasleem
ta yi. Ta tuna gargaΙin Babandi cewa muddin ta sake bakinta ya furta abin da ya
faru ga kowa wane ne toh ta sa a ranta aikin ya lalace har abada kuma ba za ta
samu koda rabin mutum irin Fadeel ba balle a kai ga shi da kansa. Wannan
ya sanya ta samarwa kanta nutsuwar dole ta fisge hannun Mami daga jikinta.
"Mami mene haka wai? Me kike tunanin ya yimin? Babu fa
abinda ya yimin, kawai dai ya ban wasu turaruka na shafa ya ce na zauna ya
dinga yimin wasu karatuka bayan ya kammala kuma ya ce naje na jira zan soma
ganin sakamako. Gobe ma yace na koma zai ban wani garin magani da zan barbaΙa a
makwancin Humaira."
Ajiyar zuciya mai karfi Mami ta yi har da kama jikin madubi.
Sai bayan tafiyar Tasleem ta dinga tunanin anya ba ta aikata kuskure da ta tura
ta wajensa ba musamman da ta tuno yanda suka kwashe. Ta kira wayar Tasleem din
ya fi a Ζirga amma ba ta ko Ιaga ba hakanan na Babandi ma sai a ce mata a
kashe. Tana niyyar zuwa da zummar kai mata yarinyarta dake faman kuka sai ga
Tasleem din ta shigo gidan.
"Shikenan, ki wuce ki je kin bar yarinya tana ta
kuka."
Itama ajiyar zuciyar ta sauke ganin Mamin ta yarda da
zantukanta na bogi. Har ta kai Ζofa Mamin ta dakatar da ita hakan yasa ta
waigo.
"Ki kula sosai da duk wani abu da Babandi zai sanya ki
yi, idan har kanki ya Ζulle a kai ki sanar da ni kafin ki aikata."
Gyadamata kai kawai ta yi kafin ta juya ta nufi dakin Anna
don gaba daya ma ta tattara kayanta daga ainahin dakinsu, ba za ta juri ganin
wannan rawar Ζafar da ake yi akan auren Humaira da Fadeel ba.
***
Ζangaren Humaira ba
ta da ko Ιigon damuwa game da komai. Idan ka ga yanda ta yi kyau za ka
rantse ba ta taΙa sanin wata aba wai
wahalar rayuwa ba. Ummita ita kanta ta bar damuwa da yanayin kaddararta, gaba
daya ma babu mai yi mata tuni a kai, yanda Ζ΄an uwan Humaira ke haba-haba da ita
da nunawa Ahmad kauna sai ta Ζara sakewa da su. A yanzu babu abin da ke damunta
dangane da abin da ya faru da ita na baya sai ko yanzun da Ridwan ke neman
takurawa rayuwarta da kira da Ζara fallasa mata zahirin zuciyarsa. Ga kuma
Mubarak a gefe wanda ya ce babu gudu ba ja da baya don ya samu labarin Ridwan
daga bakin Ζ΄an uwansa. Ita kam gaba dayansu babu wanda ta ke jin ma kaunarsa a
ranta sai tausayi da suke ba ta ganin su matasa su na neman daukarwa kansu abin
da bai dace da rayukansu ba. A cewarta.
Safiyar ranar Juma'a su na zaune a daki, Humaira sai yatsine
fuska take tana kallon kwanon da Baba Amina ta dire a gabanta na kazar da aka
dafa da sinadaran gyaran mata.
"Ki kalla dakyau Humaira, hakanan za ki ci shi ko bakya
so."
Fadin Baba Amina kenan, yanmatan dake dakin aka kwashe da
dariya har Ummita da Raihana wacce ta saki ranta saboda murna da farin cikin
ganin auren Fadeel da Humaira na niyyar tabbatuwa, abin da ta jima tana son
gani.
"Nikam Baba idan ta Ζi ci a miΖomin yanzun nan na tashi
da shi."
Cewar Raihana tana Ζ΄ar dariya.
"Aa Raihana, wannan kam na matan aure ne. Ki jira zai
zo kanki ke da Ummita nan ba da jimawa ba kuwa sai mu gani ko cika baki ne ko
kuwa dagasken za ki iya ci."
Aka yi dariya, Ummita ko murmusawa ta yi, ita ba ta fiye son
ana sanya ta a layin waΙanda za'a aurar ba.
"Allah kuwa Baba cikina ya cika, dazunnan fa na gama
shan wani..."
"Toh marar sirri, a gaban Ζ΄an uwan naki za ki tona
abinda aka baki?"
Hajjo ta katse zancen Humaira, anan kuma sai Baba Amina duk
ta sa aka fice a dakin aka bar Humairar sai ko Ummita da Hajjo.
"Kinga Humaira, wadannan abubuwan da nake sanyaki sha
da ci, suna daga cikin abin da za su Ζara siyamaki daraja a wurin mijinki. Ba
ki da wanda ya wuce mu da zamu tsaya don ganin rayuwar aurenki ta inganta da
taimakon Allah. Abu kuma na gaba da nake son faΙamaki, bai wuce akan Maminki
ba. Kar ki ga don ta sauko kamar ta sauya fuska ta shiga cikin sha'anin
bikinnan na jiya ki yi zaton babu sauran ΙurΙushin hassada da bakin ciki a
Ζasan ranta. Ta riga ta fiddomaki da kuma mu da zahirin wace ce ita wannan kadai
ya isa ki kula koda bayan aurenki ki yi kokari kada ki bada wata Ζofar da za'a
ji kanki keda mijinki. Ki godewa Allah, samun miji irin Fadeel a zamanin nan
sai a tona. Mutumin da tun kina gwada masa tsana da kyara yake bibiyarki da
nuna maki kauna ta gaskiya, wallahi Humaira koda wasa kika cutar da shi a
zamantakewarku sai Allah ya yi masa sakayya. Kar ki yi amfani da wannan dumbin
kaunar da yake gwadamaki wanda hatta a dangin Mahaifinki akwai wadanda suke
nuna adawarsu da shi ki yi tunanin cutar da rayuwarsa. Ki yiwa kanki karatun ta
nutsu, ki yi hakurin zama da mijinki kar ki yaΙa matsalar da za ki fuskanta da
shi ga kowa ba ma fatan matsalar ake maki ba, amma ki kula ki san me kike
yi."
Haka Baba Amina ta yi ta yi mata maganganu masu ratsa zuciya
har sai da jikinta ya yi sanyi. A karshe ta soma cin kazar su na zolayarta.
Hajjo ta mike ta fice zuwa wurin yan uwansu da suke Ιakin baΖi. Itama Baba
Amina ta fita wannan ya ba Raihana damar dawowa ta zauna gefen Humaira tana
yamutsa fuska.
"Wai kun ji labarin an yiwa Sis Futuha kishiya
kuwa?"
Dagaske ba su da wannan labarin, Humaira dai ta ganta tana
kuka ranar da Fadeel ya zo amma ba ta samu damar cewa uffan ba saboda umarnin
da Mami ta ba ta a lokacin.
"Kai Raihana, dagaske kike?" Fadin Ummita.
TaΙe baki ta yi.
"Allah ko dagaske, Ζ³ar Snow mijinta ya aura."
"Ζ³ar Snow fa kike ce?!"
Fadin Ummita idanunta waje. Humaira ko sai da ta Ιan yi jim
don ta na tunani kamar ta san sunan kamar kuma ba ta sani ba. Can ta tuna wace
ce, wacce dai ta yiwa Futuhar mummunan Ζazafin da ya yi sanadin aurenta da
Yakubu ba Ibb da take mutuwar so ba.
"Ita dai, yau ma za ta tare kuma a gidan da Futuha ta
fito. An mata gyara sosai. Hum, ta tashi hankalinta ita kuma, dazu har rotse ta
yi mishi a goshi dakyar ya kwaci kansa ya bar gidanta. Abba ma ya je ya yi mata
kaca-kaca da barazanar saΙa mata muddin ta Ζara gangancin kashe rai. Ba don
Abban da abokin Yakubun ba ai da tuni itama ta dawo gida zawarci."
Raihana ta karashe zuciyarta a karye har kwalla sai da ta
cika idanunta. Rashin sa'ar Ζ΄an uwa mata da ma rashin sa'ar uwa ta gari yana
mata zafi a ranta. Me suka Ιauki duniya ne haka? Kowanne cikinsu dogon buri ya
ke ci mata kai ka ce shi ke da alhakin Ζayyadewa kansa lokacin da zai mutu.
Futuha a zahiri ta nuna kwadayin abin hannun Yakubu, yau gashinan ya nuna mata
halin maza ire-irensa. Tasleem ko ba ta ma san a layin da za ta jera ta ba.
"Allah ya kyauta. Ya tsare. Amma ta bani tausayi
gaskiya. Ai ko ni duk hakurin ba na jin zan iya zama da wacce ta yimin Ζazafi
ba a rayuwa."
Fadin Ummita kenan da ya katse tunanin Raihana.
"Amma a ganinki tun farko laifin waye? Laifinta ne da
ta zaΙi duniyar Tiktok akan zahirinta, Allah dai ya tsare."
Suka amsa da amin.
***
Misalin karfe biyar
na yamma aka shirya Humaira cikin wani arnen leshi mai daukar idanu kalar
yellow ochre, ta yi wani irin kyau da ta fito tamkar a matar wani hamshaΖin.
Ummita kanta ta ci ado sosai cikin wani leshi golden da suka yi ankonsa da
Raihana. Su biyu kacal suka yi shi, Ahmad kuwa Hajjo ta karΙe ta ce wajenta zai
zauna ita ce mai rainonsa. Duk kuwa ta
yi hakan ne don kar ya hana Ummita sakewa a wurin biki, tana fatan itama
Allah ya fiddo mata da miji ta yi aure.
Gidan gaba daya aka
fice har Mami wacce Hajiya Lubna ta yi ta yiwa famfon kar ta bari a kwace mata
ragamar gida. Wato ta zuba idanu Baba Amina ta yi mulki a gidan mijinta alhalin
ita ya dace komai ya Ιulla ta hannunta. Anti Laila kuwa Ζanwa ga Hajiya Lubna,
wato matar da ta koyawa Humaira girke-girke. Takanas ta zo har da Ζatuwar
ledarta na taya murnar aure da ta tahowa da Humairar. Ita kam da zuciya Ιaya ta
ke sonta. Ta kuma iso da Ζaramin akwati mai dauke da agogo mai dankaren kyau
daga Kabir dan Hajiya Lubna ya ce a ba Humaira. Humaira duka ta amsa ta damΖawa
Raihana. Ita ko ta je ga Baba Amina dake zaune ta nunamata. Mami na kallon
wannan diramar, haushin Raihana tamkar ya kashe ta, wato ba ta ma dauketa komai
ba don tun zuwansu wurin yinin komai aka bada na Humairar wajen Baba Amina take
kai shi. Ko inda Mamin take ba ta kalla, Mamin dai ta haΙe itama cikin wata
shaddarta sabuwa da ta sa aka yi aikinta daga can Mali amma ba ta taΙa sanya ta
ba sai a yau ta yi mata rana.
"Hajiya Maryam wallahi sai mun tashi tsaye, nikam ina
tsoron kar wannan abu ya tabbata. Kiga yarinya duk ta fi yaranki more aure?
Duba kiga yan uwan mijinta babu na raini a cikinsu. Suturarsu masu tsada ne na
Ζarshe ina faΙamaki."
Hajiya Lubna ke wannan bayanin tana karewa su Anti Amarya da
su Hannatu Ζanwar Fadeel kallo. Mami ta cika ta yi fam, ta ji kwallar baΖin
ciki sun cika idanunta.
"Bar ni haka Hajiya Lubna, wallahi kuka nake son
fashewa da shi. Wannan ranar baΖa ce a gareni kuma ba don kin matsa akan zuwan
ba da babu inda zan tako don ban ga wani abu cikinsa bayan baΖin ciki ba.
Yarana su na can cike da tashin hankali, amma wadannan hotihon banzan ba su
kishin yan uwansu sam, ji yanda ita waccan ke zirga-zirga ke kya ce bikin kanin
ubanta ake yi, ji don Allah yanda wancan soloΙiyon ya wage baki yana zubawa
Humaira kudi."
Ta karashe tana duban Yassar da ya ke tiΖar rawa yana yi wa
Humaira karin kudi da take tsaye a fili.
"Sai hakuri, farin cikinnan zamu san yanda zamu yi daga
baya ya koma baΖin ciki."
Kallo bai tashi komawa sama ba, sai da aka yi kiran uwar
Amarya ta fito, Mami da Baba Amina suka fita a lokaci guda. Wannan abu ya yiwa
Mamin ciwo amma hakanan ta danne ta dinga zuba murmushin da bai je zuci ba.
Humaira kuwa har hawaye ne suka zubomata, babu wanda ya fado a ranta sai Dada
da mahaifiyarta. Baba Amina ta dan ja ta a jiki ta a goge mata fuskar da
handkerchief sai hoto da liΖin ya koma kansu wannan ne dalilin barin Mami hall
din gaba daya don hatta da MC din idan ya ambaci sunanta sai ya ambaci na Baba
Amina.
Raihana ta fito don
kai wa wasu Ζawayensu na makaranta kati dake waje, ta ji wayar Ummita dake
jakarta na Ζara. Kafin ta ciro ya zama missedcall, ta ga ba ma kira daya ba ne,
kira ne wurin goma sha wani abu daga Mubarak, Ridwan da kuma wata lambar da ta
dauki hankalinta matuΖa kuma ta girgizata. Tana nan tsaye bayan ta ba da katin
sun shige ta rasa abin yi sai kakkarwar hannu da jiki, wayar ta Ζara ringing.
Lambar ce dai dagaske, lambar da ta gani a wayar Mamin har ta tura wa Abba. Ta
yi saurin Ιagawa kirjinta na harbawa. Kafin ta yi magana ya riga ta.
"Blackbeauty, ina fatan kin dauki muryata? I am the
Wizzy the father of Ahmad."
Ai ba ta san lokacin da ta durΖushe a cikin fararen duwatsun
dake wurin ba, Wizzy da ya yiwa Ummita fyaΙe? Shi ne Wizzy da Mami ke waya da
shi? Ta kara fiddo wayar a kunne ta duba dakyau, tabbas lambar ce ba Ζarya ba
ne. Ta katse kiran ta ciro wayarta tuni hawaye sun gama wanke fuskarta ga wayar
har tana faΙuwa a kan duwatsun ta buΙe ta fiddo lambar Wizzy dake wayarta, ta
Ζura idanu tabbas ita ce dai lambar.
Mami wacce ke tsaye tare da Hajiya Lubna su na jiran direban
Hajiya Lubnan da aka nema aka rasa ya kaΙa yawo, ta hango Raihana cikin halin
ruΙani. Ta dubi Hajiya Lubna.
"Raihana kuma? Meyafaru da ita?"
Hajiya Lubna ita dinma sai lokacin ta ankara da ita, cikin
sauri suka hau tafiya zuwa inda take.
Kafin Raihana ta kai ga daukar kowane mataki, wayar Ummita
dake hannunta ya Ζara ringing, Mami daidai lokacin suka karaso ita kuma ta Ιaga
wayar tana fadin.
"Waye Wizzy? Mene dalilinka na kiran Ummita?"
Kirjin Mami ya bada dam, suka dubi juna da Hajiya Lubna
cikin tsananin kiΙima. Wizzy kuma? Kiran Ummita? Ai sai kafafun Mami suka hau
rawa, dakyar ta karasa ta zagaya gaban Raihana, ita kuwa Raihana ganin Mami ya
sanya ta Ζara nanata tambayar da ta yiwa Wizzy don ta ga yanayin da za ta
shiga. Ai kuwa zaro idanu ta yi waje, hannu ta kai ta fisgi wayar.
"Bani mu ji waye?"
Haka kawai ta fadi ta sa wayar a kunne ta dan yi gaba
acewarta wai Ζarar sautin da aka sanya a cikin hall ya sa ba ta jin abin da
yake fadi. Hajiya Lubna cike da dabara ta riΖe hannun Raihana.
"Ki kwantar da hankalinki, ko waye za mu sani. Me ya ce
maki ne naga duk kin shiga ruΙani har da su kuka?"
Raihana ta bi matar da kallon munafuka mai Ζara tunzura
uwarta. Ai dama sai hali ya zo Ιaya ake Ζawance. Ta sani sarai don kada ta bi
bayan Mamin ne ya sa ta ke siyasance ta. Sai ta kauda kai ba tare da ta ce mata
uffan ba. Hankalinta na kan Mamin da ta ba su baya ta kuma yi can nesa da su.
Mami kuwa ta saurari kalaman dake fitowa a bakin Wizzy.
"Ke wace ce? Ki ba wayar ga mai wayar uwa ga yarona ita
nake son magana da ita kar ki bari na wulakanta rayuwarki kema."
"Wizzy." Ya ji muryar Mamin cikin kunnuwansa, sai
kuma ya kyakyace da dariya.
"Oh, ki ce wayar fasin fasin ake da ita, daga hannun
wannan sai na waccan, Hajjaju kenan. Kin yi mamakin jin na kira lambar Uwar
yarona ko? Ki. Yi zaton zan zuba idanu na biyewa shirme da shiriritarki? Kin
kasa cika umarnina ma fiddo Nusy har jami'ai sun fara farauta ta saboda ta ba
da kwatancen inda nake, ta ci amanata. Yanzu haka na yi nesa da Kano da ma duk
inda aka san za a gan ni na koma ainahin Ζauyenmu. Toh ki sani, a duk radda na
tashi dawowa zan yi zuwan a mutu ko a rayu, ba Ahmad kadai ba har uwar Ahmad
zan dauke ke kuma haΙuwarmu dama na faΙamaki ai ba za ta yi kyau ba. Ki shirya
tonan asirikanki."
Gumi ya shiga tsirfowa Mami, ta dan juya ta dubi su
Raihana, ta kuwa kuramata idanu babu ko kiftawa. Ta kauda kai ta ce.
"Shikenan, ka yiwa Allah kar ka kara kiran wayar
Ummita. Zan maka yanda kake so kafin a kammala bikin auren nan."
Ta dinga magiya har sai da ya ce ya ji. Da haka suka yi
sallama ta goge lambar bayan ta yi blocking dinta. Kasancewar wayar Ummita babu
wani lock da ta sanya hakan ne ya ba ta damar yin yanda ta so kafin kuma ta
koma ta ba Raihana wayar. Har lokacin kallonta kawai take yi hawaye na zuba a
saman kuncinta. Wai wannan matar da Allah bai raga da komai na kyawun fuska ba
sai ko munanan Ιabi'unta ita din mahaifiya ce gareta babu yanda kuma za ta yi
ta sauyawa tuwo suna.
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Raihana kin ji
masifar dake shirin tunkaro mu? Wai uban Ahmad ne yake son karΙar Ιansa? Lallai
ki kiyaye furta wannan zancen ga Ummita, mun samu ta dawo cikin nutsuwarta
yanzu, idan wannan magana ta fito bamu san halin da za ta shiga ba kuma."
Mami duk ke wannan zantukan har da fidda hawaye itama ta a
share su. Hajiya Lubna ko sai Ζara jinjinawa irin salon kisisinar Mami
take. Gaba Ιaya ta rikiΙe zuwa ta Allah, wanda bai santa ba ma zai ce har
zuciyarta dagaske ta ke. Raihana ta kauda kai tayi murmushi mai ciwo lokaci
guda tana sa yatsunta ta share fuskarta. Allah ya taimaka ba ta yi kwalliyar
hodar foundation ba, babu kuma irin nacin da Ummita ba ta yi mata akan ta yi
din ba ta ce ba ta ra'ayi hakan ya ba su mamaki kwarai game da ita don ta fi su
ma son kwalliyar sosai.
"Shikenan, ba zan fadamata ba. Ni bari na koma ciki kar
a neme ni."
Daga haka ta juya ta bar su a tsaye, suka bita da ido.
"Hajiya Maryam, jikina yana bani akwai wani abu da
diyarki ke Ιoyewa."
Cewar Hajiya Lubna. Mami ta girgiza kai tana wani murmushi.
"Ko kusa Lubna, ban gan shi ba. Na san Raihana sarai,
da ace akwai abu a ranta ba za ta iya yin shiru ba. Haka take, ba ta Ιoyon abin
da ke ranta."
Hajiya Lubna dai ta ji ta amma ba ta yi na'am ba. Daga nan
suka rankaya zuwa wurin motar inda direban tuni ya dawo yana jiransu. Hakuri ya
dinga bayarwa da Hajiya Lubna ke mishi fada kafin su shiga ta ba shi umarnin ya
jira a waje sai ta mishi iznin shiga motar. Dole haka ya bi umarninta ya samu
can gefe ya tsaya yana kallon masu shige da fice Ζ΄an biki. Sai lokacin Mami ta
labarta mata yanda suka yi da Wizzy, ta kara da fadin.
"Na riga na yanke zan sa Bala (wanda ya haΙa ta da
Wizzy tun farko) ya yi amfani da damarsa wayar yaron nan ta shiga hannunsa ya
kai wurin masana kwamfuta a yi resetting ta dawo kamar sabuwa. Wannan damar zai
sa ya rasa komai da muka yi tsakaninmu. Kinga koda asirinshi ya tonu wanda nake
ji a jikina zai tonun tunda dai an kama budurwarsa an kuma fara harinsa, babu
wata shaidar da zai nuna gaban kotu da za'a ce har da ni a ciki. Abin godiyar
ma, bai taΙa yin ido hudu da ni ba ballantana ya ce ya san ni. Nima a bangarena
zan fidda komai nasa daga wayata."
Murmushi sosai Hajiya Lubna ke yi.
"Tabbas wannan babbar dabara ce. Nima dai akan ta wa
matsalar na auren da Honarabul ke shirin Ιaukowa na waccan shuwa arab din dole
na je na ga Babandi. A baya ya yi aikin kamar za a fasa amma kinga ashe magana
tana nan kuma yan banzan danginsa sun nuna goyon bayansu. Kinsan duk yanda ka
kai ga kyautatawa dangin miji tsinannu sai sun ga aibunka. Koda dai bana
tsinana musu hatta uwarsa bai isa ya yi mata ba sai da iznina. Watakila wannan
Ζarfin da ya bani na iko a gidansa da kuma kaunar da ya nunamin ce ta yi
sanadiyyar da suke nunamin hassada da bakin cikinsu."
Fuska Mami ta yamutse.
"Hum, ba ki ga waccan balbelar ba?"
"Wa kenan?"
"Wace ban da yar iskar bazawarar can Maijidda? Nifa ko
zan yi yawo tsirara ba zan aminta da aurenta da mijina ba."
Dariya Hajiya Lubna ta yi.
"Kai kai kai Maryam, yanzu ke da bakinki kin ce Babandi
bai tabbatar maki da aure tsakaninsu ba. Toh na meye za ki yi wannan irin yanke
hukuncin da gaggawa haka?"
Girgiza kai Mami ta yi.
"Uhm uhm Hajiya Lubna. Babandi shegen kansa ne. Ni
jikina yana bani zai wahala idan ba dangantaka ta auren yake nufi ba. Sai yanzu
ma nake ganin wautarmu na tsayawa kan mutum daya don yi mana aiki. Yanzu
gashinan abubuwa ba sa tafiya yanda muke so, ya kamata dai ki lalubo mana wani
gwarzo kuma babban malamin da ya shahara da zai iya yi mana aiki."
"Nima nayi wannan tunanin Hajiya Maryam, lallai mu
tsaya mu nemi wata mafitar, akwai masu taimakon jibgi guda suna nan. Shi kuma
Bala ki yi maza ki kirashi yanzu, ai da zafi akan bugi karfe, gwara ki ba shi
wannan aikin da alkawarin manyan kudade idan ya aiwatar kada lokaci ya
kure."
Bisa wannan shawarar Mami ta fiddo waya ta kira Bala, ta ci
sa'a ba ta sha wuyar samunsa ba. Suka yi magana ya kuma ji daΙin kudaden da aka
yi mishi alΖawari ya ce zai yi yanda ta ce. Da haka suka yi sallama.
Sai da suka gama Ζulla-Ζullarsu kafin Hajiya Lubna ta kira
direbanta ya zo ya ja suka bar farfajiyar wajen taron.
***
Tasleem kuwa tun da aka sa Ζafa aka tafi wajen biki, ta zari
mayafinta jikinta har rawa yake ta wuce gidan Babandi. Ta rasa meke janta zuwa
gareshi. Kiranta kawai ya yi ya sanar da ita ta zo yana jiranta ta ji nan
duniya idan ba ta je ba akwai matsala, ko makaranta ta kasa mayar da hankali
kan jarrabawar karshe da take yi. Haka Babandi ya more ta sannan ya ba ta wani
Ζullin magani akan ta yi yanda za ta yi ta sanya a abin ci ko shan Humaira, sai
ko wani turare da za ta shafe a kayan da ta tabbatar shi Humairar za ta sanya
ranar daurin aure. Da wannan murnar ta dawo gidan. Koda Mami ta tambayeta
daliin jimawarta, cewa ta yi layi ta tarar.
***
Washegari ya kama ranar Ιaurin aure da kuma yinin cikin gida
sai ko kai Amarya duka. Tun safe jikin Humaira a sanyaye yake, kewar yan uwanta
da tunanin sabuwar rayuwar da za ta shiga na aure sun tsaya a ΖoΖon ranta. Tana
gani ana ta shige da fice ana shiri, masu wanka nayi masu karyawa suna yi, ita
ko ta kasa sa komai a bakinta balle ta samu ta ji faΙan Hajjo ta miΖe ta shiga
wanka. Da ta kalli Ummita sai ta ji hawaye na Ζara zuba kamar famfo a fuskarta.
Ummitan ma daurewa kawai ta ke yi, ita ko Raihana ma gaba daya ta dunkuke cikin
bargo tana kuka. So take ta je ga Abba ta fayyace masa komai amma kuma ba ta
son raba masa hankali gida biyu. Ta san yana ta hada-hadar fita zuwa daurin
aure. Wannan dalili ne ya sanya ta bar komai a cikinta.
Ζangaren Anna kuwa, murna har da su rawa saboda kudaden da
aka turo mata ya yi daidai da wadanda aka suka rage ta cika wajen fiddo
autarta. Ta yiwa Mami magana, suka dunguma har Futuha da ta shigo gidan da
safe zuwa inda Jannat din take. Tasleem ko ba ta bi su ba sai tunanin ta
inda za ta shiga dakin ta shafa turare a kayan Humaira alhalin babu ko
tsinkenta a dakin. Ga mutane an cika a ciki, gaba daya kanta ya Ζulle. Ta fito
falon goye da Ιiyarta a baya wacce ko wanka ba ta yi mata ba ga famfas ya cika
sai tashin zarni take yi. Ζazanta na Ιaya daga cikin halayyarta. Ζazamar gaske
ce har ma fiye da Futuha kai ka ce ba Nos ba.
"Ladidi don Allah yi da jiki ki miΖawa Amarya wannan
shayin yarinyar ta Ζi cin komai, ni bari naje na ga ko masu kai kayan can
gidanta sun tafi."
Baba Amina ke maganar ba ta ko lura da Tasleem ba, ta fice
da sauri Ladidi na amsa mata da toh. Wani irin sauke ajiyar zuciya ta yi tana
jin wani sanyi a ranta. Ta yi sauri ta fada kicin din. Suka gaisa da Ladidi. Ta
dubi tire din mai dauke da filas da kuma kofi sai kayan shayi da plate wanda
aka soya kwai aka rufe.
"Ladidi don Allah dubamin akwai ragowar fulawa."
Ta amsa da toh sannan ta shige store din dake jingine da
kicin din tana fadin ba za a rasa ba bari ta duba. Tasleem a gaggauce ta fiddo
Ζullin maganinta cikin zanin goyon, ta kunce ta bude kwan ta barbaΙa kadan a
sama, ta rufe ta kara bude murfin filas din shayin ta zuba ciki kadan ta rufe
ta jijjiga ta ajiye, ganin Ladidi na shirin fitowa ta yi saurin tura maganin
cikin zani ta saita tsayuwarta.
Ladidi ta fito rike da karamin buhun fulawa ta ce.
"An ci sa'a kin samu ba yawa, haka mutumin naki kike
son ci?" Tana nufin danwake. Tasleem ta dan yi dariya ranta fari sol ganin
a saukake ta aiwatar da guda daya saura Ιaya.
"Kamar kin sani, don Allah taimaka ki yimin idan kin
miΖa saΖon Humairar."
"Ya akai kika san an Humaira ne?"
Tambayar da Ladidi ta jefomata kenan, ta dan ji faduwar gaba
kadan, ashe fa ba ta riga da ta shigo kicin din ba sai kuma ta basar.
"Ah, na ji Baba Amina na baki saΖo tana fita."
Sai a sannan Ladidi ta saki fuska.
"Auho, toh bari na kai sai na zo na Ιoramaki."
Daga haka ta dauka ta fice zuwa dakin su Humaira. Ajiyar
zuciya mai karfi Tasleem ta saki, murmushin jin dadi ta yi har da Ιan buga
tsalle. Lallai idan Humaira ta ci a yanda Babandi ya ce za ta ji nan duniya ba
ta son auren Fadeel. Shi kuwa turaren da za ta fesa a kayan da Humairar za ta
sa, zai yi sanadin da za ta haukace ta bi duniya.
Da wannan farin cikin ta fice a kicin din. Sai dai me? Bayan
awa guda ta shiga dakin don ta ga irin sauyuwar fuskar da Humaira za ta yi da
borin ba ta son auren Fadeel, amma ta tarar ma waya take yi da Fadeel din tana
doka murmushi yanmatan dakin na tsokanarta. Wani zafi da jiri ta ji a kirjinta
da kuma jikinta. Jiri har yana so ya kayar da ita. Tana da tabbacin Humaira ce
ta ci ta sha shayi da kwai, don har shigowa ta yi da zummar neman wani
mayafinta a sif din Raihana ta tarar Humairar ta a yagar kwai tana loma a baki
amma ya akai bai yi tasiri a jikinta ba?
"Ke Tasleem lafiyarki kuwa?"
Ta dubi mai tambayar, Sauda ce diyar Baba Amina dake aure a
Zaria.
"Babu komai, kaina ke ciwo tun safe da shi na
kwana."
"Ayya, ai sai ki nemi magani. Sannu."
Ta amsa da yauwa tana murmushin yake da kallon Humaira. Ta
sa kai ta fice za ta nufi dakin Anna. Sai ta hangi kaya a hannun Raihana za ta
shiga falon Abba da su wanda ba ya nan ya fice zuwa wajen daurin aure.
"Kayan waye wannan?"
Tasleem ta tambaya da dan sauri. Raihana ba ta ko kalleta ba
don haushinsu take ji su duka ta amsa.
"Na Mrs Fadeel in sha Allah."
Wannan Mrs Fadeel din ya baΖanta ranta sosai, ta ja tsaki,
Raihana ta fice tana waΖar. "Ko anΖi ko an so, aure zai Ιauru.."
Ta sani da ita take, ba ma haka waΖar take ba amma don ta Ζo a ranta ya sanya
ta juya shi, wallahi ban da da wayonta aka haifi Raihana za ta rantse ba
jininsu ba ce yanda ta fifita Humaira sama da su.
Wata Ζwafa ta yi, tana gani Raihana ta shige bangaren Abba
ta ajiye kayan ta fito bayan ta jawo kofar, key kawai ta murΙa amma ba ta zare
shi ba ta wuce dakinsu da zummar taso Humaira da ta yi wanka ta je ta shirya a
can saboda mutane sun yawaita a dakinnasu. Cikin sa'a kuwa ta yi sauri ta afka
ciki ta daga kayan ta fiddo kwalbar turaren ta fesa a jikinsu sosai ta mayar yanda
ta gansu ta ajiye. Ta bude kofar ta fita ta rufe ta fada sashin Anna tana
dariya.
"Ai idan kinsan wata ba ki san wata ba. Babandi ya
cemin sai kin haukace kin bi duniya, wannan ranar nake jira. Maza jeki Mrs
Fadeel ki sanya kayanki. Uniform dinki na asibitin dawanau."
Tana kaiwa nan ta feshe da dariya. Sai a lokacin ne ta samu
nutsuwar shiga wanka, yarinyarta can ta jefa ta wajen Ladidi don a yi mata
wanka. Zuciyarta fari Ζal za ta zama matar Fadeel.
***
Gama wayarsa da Humaira ya shiga wanka, bayan ya fito ya
kammala shirinsa tsaf cikin shadda ruwan goro da ta sha aiki, kyau iyaka kyau
ya yi. Dogo mijin doguwa, ga cikar zati ga kyau da haiba. Fadeel kenan. Ya fito
falonsa inda Ibb da su Idris abokansu ke jiransa. Nan suka sanya mishi ihu da
zuzuta haduwar da ya yi a yau.
"Ka ga angon Humaira."
Ya yi wani murmushinsa haΙadΙe.
"Ku tashi muje dama shi muke jira, yana so amma yana Ιatawa
mutane lokaci."
Ibb ya fadi yana harararsa don tun dazu suke zaman jiransa
sai da ya shiga kawai ya ganshi ya yi daiΙai a kan gado yana waya da Humaira.
Fadeel ya yi dariyar da fararen hakoransa da dimple suka
fito.
"Sorry, muje toh."
Daga nan suka fito gaba daya, ba su ko shiga bangaren Anti
Amarya ba saboda cunkoson jama'a suka bari akan sai sun dawo.
A kan idanunta ya shiga mota suka fice daga gidan, ta ji
saukar hawaye a kuncinta. Ta saki labulen dakin Antinn nata ta juya zuwa ciki.
Zama ta yi ta shiga kuka kamar ranta zai fita. Wato Fadeel ya rantse ba zai
aure ta ba, Humaira ya zaΙa sama da ita?
A wannan halin Rabi yayarsu ta iske ta.
"Haba Murja, wai sai yaushe za ki sa wa zuciyarki
dangana?"
Ta dago fuskar tana dubanta, gaba daya tayi wata iriyar rama
da baΖi, dama rabin farin na mayuka ne, har wani ja take yi kamar na soyayyen
Ζosai.
"Anti wallahi ina son Fadeel."
Rabi ta zauna a gefenta.
"Amma shi kuma ba ya sonki. Wannan bai isa sanya ki
hakuri da shi ki rungumi mai sonki ba? Anas Ζanin mijina sai binki yake kina
wulaΖantashi."
"Anti shaye-shaye yake fa."
"Sai me? Kar ki manta ya fi mijina kudi sosai. Kedai ba
burinki ki yi auren kudi ki hutawa ranki ba? Mu din ma ai fatan da muke yi maki
kenan. Ki rungumi kaddara ki aminta kawai a daura maku aure. Kina haifar namiji
shikenan mu burinmu zai cika kin zama matar gida. Wallahi a yanda halittar
fatarki ta kara munana Fadeel ba zai taΙa kallonki ya ji sonki na aure ba balle
sha'awa. Ki yi hakuri ki lallaba rayuwarki da auren Anas kar ki yi saki na
dafe. Watakila ma sai kiga sanadin soyayyar da yake yi maki Allah ya shirya
shi. Sai kiga ya sauya daga yanda kika san shi. Mu dai ki zama Matar Gida, ki
haifar masa Ιa namiji dukiyarsa ta zama ikonki."
Rabi ta dinga yi mata famfo, har a karshe ta ji ta saduda ta
amince da hakan. Da wannan murnar da farin ciki ta kira Anas ta yi mishi
albishir cewa ai Murja ta aminta da batun aurensa. Shima ya yi farin ciki sosai
ya kuma ce a ba shi Murjar ya ji ta bakinta. Nan ta sanar da shi eh hakane ta
yi na'am har feeto ya yi mata a kunne ta cikin wayar tsabar farin ciki. Ita dai
ta yamutsa fuska. Ai gwara ma ta yi kudin ta nunawa Fadeel ba shi kadai ke da
arziki ba.
***
Ta shirya tsaf cikin leshin da Raihana ta tanadar mata.
Raihana na kokarin miΖa mata sarΖa ta ga Humaira ta yi wani dumm, lokaci guda
kuma idanunta suka kaΙa. Ta rike kanta ta shiga tari.
"Lafiya
Humaira?" Ta tambaya hankali tashe.
"Masha Allah, ga nan Ango da tawagarsa nan
shigowa."
FaΙin wata mata, nan aka hau gyara hanya, suka shigo da
sallama dauke a bakunansu kowannensu cikin gayu. Matasa masu jini a jika ga
ruwan arziΖi.
Ummita ta kauda kai daga kan Ridwan tun ganin da ya yi mata
ya zubamata mayatattun idanunsa kamar ya haΙiyeta.
"Wancan guy din fa ke yake ta kallo, ke kuwa kin Ζi ba
shi dama."
Raihana ta faΙi Ζasa-Ζasa, tuni ta gyara fuskarta ta fito,
baΖin cikin halayyar yan uwanta ba zai sa ta kasa nunawa Humaira murnarta da
samun miji Ιaya tamkar da dubu ba.
Harararta kadan Ummita ta yi.
Humaira ko tun da wata abokiyar tsoΖanarta ta sanya hannunta
cikin na Fadeel ta yi Ιif ta kasa magana, duk iyakar kokarinta na ganin ta zare
amma gogan sai ya tamke su tam a cikin nasa. Nan fa aka shiga hotuna bayan
kammala gaishe-gaishe. Fadeel ya matsu ko kallonsa ne Humaira ta yi amma ina,
kunya ba ta bar ta ba. Zuciyoyinsu sai wani zillo yake yi na farin ciki.
Wizzy na tsaye daga baya yana Ζarewa gidan kallo da mutanen
dake ciki, bai san Mami ba a fuska hakanan ita din ma balle ya yi tunanin za ta
gan shi ko kuma shi din ya gan ta. Yana kuma da tabbacin zai wahala wani cikin
su Humaira da Ummita su iya gane shi, a ganinsa abu har an shekara zai wahala
su gane shi.
"Ke Ummita, yaron nan dai Ιuminki yake son ji." FaΙin
Hajjo tana mai miΖo mata shi bayan ta je sun kammala hotuna da su Fadeel an
gaisa. Hankalin Wizzy gaba daya ya yi kansu, Ummitan ta ci wani irin kwalliya
da blue lace ta yi kyau tsaf. Ahmad din ma shigar Ζananun kaya aka yi masa, ya
yi ΙulΙul abinsa. Yana kallonsu cike da wani irin kauna da bai san daga sadda
ta faro ba. Ya bi Ummita da kallon sama har Ζasa, ta Ζara zama wata yarinya
sharr da ita.
Daidai sadda wani ya karasa kafin Humaira ta kai ga sa hannu
ta karΙi Ahmed, ya ce Hajjo ta miΖa masa shi. Wani Ζululun bakin ciki ya tokare
a wuyan Wizzy, wannan wane Ιan iskan ne haka? Dama ya kula da irin shishshigin
da yake yiwa Ummitan, toh kuwa bai isa shiga tsakaninsa da Ιansa ba. A yau zai
raba su da wannan farin ciki ya Ιauke jininsa idan ya so daga baya ko Ummitan
ya dawo ya sace. Shi ya ji ma zai iya aurenta su rayu tare.
Ummita ta dubi Ridwan. Ya kashe ta da wani sassanyan
murmushi, ta yi Ζasa da kanta. Ganin haka Hajjo da murmushi ta juya ta bar musu
wurin tana mai fatan alheri a can Ζasan ranta. Ta tabbatar idan har wannan aure
ya tabbata toh shakka babu Ummita ma tana cikin layin masu dace a rayuwa. Tana
da labarinsa a bakin su Raihana da Humaira a sadda suke koΙa shi duk don su
nemi kafa shi a zuciyarta.
"Ni ake ta yiwa yanga? Ζan nawa ma rowar ganinsa ake
yimin?"
Duk sadda ya kira Ahmed da Ιansa wani daΙi take ji amma ta
ke kannewa. Yanzun ma ba ta ce komai ba sai kauda kai gefe.
Ya taka zuwa inda ta mayar da fuskarta. Idanunsa ya kai ga
Wizzy, ganin haka Wizzy ya kauda kai da sauri yana kallon wani Ιangaren, shima
sai ya Ιan share amma tun sadda aka shigo yake lura da shi, gaba Ιaya zuciyarsa
ba ta yarda da shi ba.
"Mama tana tambayar yaushe za ki je ta ganki? Kinsan fa
na ce mata sa ranar kawai ya yi saura. Kin amince."
Ya karashe da Ιan Ιaga gira, ta zaro ido gami da Ιan dafe
kirjinta.
"Ni da bakina na ce maka na amince?"
Ya Ιan bi bakin da kallo yana murmusawa kafin ya maida
idanunsa kanta. Ta kauda kai, ta rasa dalilin da idanunsa ke mata wani irin
kwarjini.
"Ko ba ki furta ba ai idanunki sun fallasa sirrin dake
cikin zuciyarki."
Ta kasa cewa komai sai giftashi da ta yi ta wuce murmushi
dauke a fuskarta. Shi dinma bin bayanta da kallo ya yi cikin murmushin har sai
da Idris ya Ιan buga kafaΙarsa. Ya basar gami ga miΖa Ahmed ga Ζ΄ar yarinya kuma
jika ga Baba Amina dake ta faman miΖa hannu wai ya ba ta shi. Ta karΙe shi kuwa
ta yi gaba tana masa wasa. Dukkan wannan abu akan idanun Wizzy suka faru.
Ya gama shaΖar baΖin cikin wannan soyayyar da Ummita ta samu, ya kuma ji kwarin
gwuiwar ganin wata Ζ΄ar albarkar ta rage masa aiki ta hanyar karΙar Ahmed da
kuma nufar hanyar Ζofa da shi inda Ζawayenta yara suke tsaye ana wasa.
Ya faΖaici idanun jama'ar dake wurin ya yi saurin yin baya.
A wannan fakar idanun Ummita idanunta suka kai kansa, har abada ba za ta taΙa
mance wannan mummunan fuskar ba duk kuwa da irin shigar manyan kaya na kamala
da ya yi ba a can da yake shigar Ζananan kaya, kayan ma na Ζ΄an duniya irinsa.
Kirjinta ya hau bugu, ta ga ya juya zai fita, ta kasa sukuni ta bi bayansa, ta
kasa magana saboda ta fi buΖatar tantance komai da idanunta kan ta yanke
hukuncin ihu za ta yi ko kuwa gudu za ta yi. A yayinda hankalinta ke kan Wizzy,
shi ko Ridwan nashi hankalin ya koma kanta ganin ta zo ta tsakiyarsu inda za'a
yi hoto ta wuce ba a hayyaci ba. Ya juya da sauri ya bi bayanta daidai sadda
Wizzy ya sa hannu ya karΙi Ahmed da yaudararriyar murmushi da ya sakarwa
yarinyar gami da fadin ta ba da shi ya ga wannan fine boy din. Daga haka ta ga
ya nufi wajen falon da shi yana Ιan yi mishi wasa. Ihun da ke maΖale a fatar
bakinta shi ta saki gaba Ιaya iyaka Ζarfinta. Wannan ya ankarar da Wizzy, da
wani irin sauri ya zura Ahmed cikin babbar riga ya soma gudu zai fice. Ai
cikin wani irin zafin nama Ridwan ya bi shi da sauran mazan dake a wurin. WaΙanda
ke waje kuwa suka yi nasarar cafke shi, Ummita kam tuni ta fita hayyacinta kira
take "Shi ne! Wallahi shi ne! Ya zo ya Ιaukemin Ιa!"
Humaira da Fadeel da sauran jama'a hankalinsu ya tashi,
Fadeel ya riΖe Humaira gam ganin yanda jikinta ya hau wani irin mazara, aka
fita gaba daya zuwa farfajiyar gidan inda Ridwan ke riΖe da Wizzy gam! Ahmed ko
yana hannun Dawud. Ummita na zuwa ta karΙi Ahmed ta rungume tana ja baya sosai
daga Wizzy, kallonsa take yi a mugun tsorace jikinta na Ιari, Anti Maijidda da
Hajjo suka riΖe ta sosai. Wizzy kuwa idanunsa sun raina fata, Humaira ta bishi
da kallon tsaf. Tabbas shi ne. Ta hau nuna shi da yatsa itama.
"Fadeel wallahi shi ne ya ketawa Ζ΄ar uwata haddi! Shi
ne baΖin azzalumin da ya cuci rayuwarmu!"
Sai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya, Fadeel ya rungumeta
sosai cikin alamun rarrashi. Nan dai Ridwan ya yi waya ga abokan aikinsa akan
su iso da gaggawa.
Abba da jama'arsa dake zaune a falonsa na saukar baΖi jin
wannan labari suka fito, ya nufi Wizzy ya bishi da maruka hagu da dama.
"Yanda ka shigo hannu da yardar Allah Ζarshenka ya zo.
Muje ni da kai shari'a yanzu aka fara. Azzalumi!"
Wizzy dake cika da batsewa yana hura hanci kamar tsohon
salansa sanadiyyar marin da ya sha na Abba ya tari Abban da sauri.
"Ka dinga yin jam'u ai YallaΙai! Azzaluman ai biyu ne
ba Ιaya ba! Akwai azzaluma irin matar mai wannan gidan?! Ita ce ta sanya muka
aikata wannan mummunan aikin don ta samu ta mallaki dukiyarka!"
Ana ga wata ga wata! Nan fa kallo ya koma sama! Jama'a suka
yi caa ana maganganu, kowanne da abin da yake faΙi. Abba kuwa ai sai da ya ji
duniyar na juyamasa, yana ji abokan Fadeel suka yi caa a kansa akan ya Ζara
shirga wata Ζaryar sai sun fasa bakinsa. Shi kuwa Wizzy ya dinga
rantse-rantsensa cewar har da hannun matar Abba. Daidai lokacin motar ta iso
aka titsa Ζeyarsa aka tafi. Su Fadeel ma babu jinkiri suka tafi, shi kam a son
ransa ya so a ba shi matarsa kawai su fice tare don ya tabbatar wannan lamarin
sai ta dinga kuka a kansa. Ibb ne ya nunamasa ba a haka tunda dai su na cikin
rashin nutsuwa ya Ζyale su samu hankula su kwanta.
Magana dai har yamma ana ta yi, kallo sai ya koma sama.
Madadin hirar da ta shafi biki da kuma sabga ta mata sai gulmar Mami. Da yawa
sun cika da al'ajabi sun kuma yi rantsuwa kan cewar za ta aikata. Wasu kuwa sun
ce sam! Mami ta riΖi yaran da zuciya daya, kawai dai akan auren Humaira ne aka
yi yaΖi da ita don a fili ta nuna ba ta ra'ayin Fadeel, zai kuma iya zamtowa
akwai dalilinta. Anti Maijidda kuwa kuka sosai ta shiga yi tana hamdala da
Allah ya nunamata ranar da kusan kowa ya gane wace ce Mami.
***
Wai ina Mamin?
Tun shigowar su Fadeel tana Ιaki, ta yi wanka sai dai ta
kasa fiddo kaya balle ta sanya. BaΖin cikin wannan gidan arzikin da Humaira za
ta shiga shi ya tsaya a ΖoΖon ranta, Ζarshe ma kuka ta shiga yi. Abin mamaki,
kuka na baΖin ciki da jin inama ta mutu kafin wannan rana. Wai Ιiyar Fatima ce
kishiyarta, ita ce dai ta samu wannan Ιaukaka ta ko'ina. Ita kuwa nata yaran
daga bazawara mai Ζananun shekaru sai ko wata can da aurenta ke gantali, su
kansu mazan sun Ζare karatunsu babu aiki. Kasuwar ma Abba ya dakatar da su daga
zuwa saboda irin Ιarnar da ya ce suna yi masa. Yassar da Abban yace zai samar
masa koyarwa ya rantse ba zai yi ba, shi kam Allah ya kiyaye a ganshi yana
koyarwa. Wannan ya hasala Abban har ya fita hanyarsa ya ce ya yi duk yanda ya
so.
Tana nan kwance ta ji ihun Ummita da ya karaΙe gidan. Ta
mike har zaninta na faΙuwa tana ja tana Ιorawa. Jiki na rawa ta Ιauki dogon
hijabi ta zura. SaΙaf saΙaf ta bude Ζofar ta fita lokacin hankulan jama'a duka
ya yi waje an fita an bi Wizzy. Ba ta fahimci wa Ridwan ya riΖe ba sai da
kunnuwanta suka ji muryar Humaira na sanar da Fadeel wai shi ne mutumin
da ya keta haddin yar uwarta. Ai cikin Mami sai da ya yi wani irin kaΙawa. Jiki
na rawa ta nemi hanya ta koma Ιakinta ta datse gam! Gumi fa ko ta ina ya shiga
tsastsafo mata. Tana nan ta dauki waya amma rawar da hannunta ke yi ya sanya ta
kasa koda bude wayar balle kuma ta kira. Ta yi wurgi da wayar sakamakon cikinta
da ya shiga murΙawa ai sai ta nufi bandaki ta hau gudawa. Can ta Ζara fitowa ta
yi jim a jikin Ζofar Ιakinta don jin me ke gudana, wani sabon al'amari ta ji,
Anti Maijidda ke kuka da hamdala wai Allah ya toni asirinta. Yau gashinan Wizzy
ya ce tare da ita ce suka haΙa baki suka yi garkuwa da su Ummita.
Ai Mami sai ta sulale a wurin ta zauna daΙas! Wannan tashin
hankalin da me ya yi kama? Duk da ta sani babu wata hujja da Wizzy zai nuna ya
ce har da ita ciki amma wannan furucin nasa babban barazana ce a gareta. Haka
ta wuni ta Ζi fitowa a Ιakin, duk irin bugun duniya da kiran wayarta da aka
dinga yi amma ta yi biris ko kallon wayar ta kasa balle ta ga mai kiran. Tana
ji wasu na rantsuwar tana ciki wasu kuwa cewa suke yi ga dukkan alamu dai ta
fice a gidan tunda akwai wadanda suka ce sun ga fitowarta sanye da hijabi.
Raihana kuwa a ranar asibiti ta kwana saboda tsananin ciwon
kai da zazzaΙin da ya yi mata dirar mikiya.
Hakanan a wannan daren Abba yace babu abin da zai sa a
jinkirta kai Humaira Ιakin mijintaz da wannan tashin hankalin suna kuka suka
rungume juna ita da Ummita tamkar kar su rabu. Ga Ζ΄ar uwarsu can a asibiti
kwance, haka aka tsitsa Ζeyar Humaira bayan sun yi sallama da Abba ya yi mata
nasiha zuwa gidanta na aure.
***
Washegari kuwa tun asuba Mami ta shiga wurin Abba, yana
dawowa daga masallaci sai ganin mace ya yi a zaune tana faman kuka. Ya kalle ta
bai ce uffan ba ya kama hanyar shiga Ιakinsa. Ta tare shi da sauri ta rike
kafafunsa tana kuka kamar ranta zai fita.
"Abban yara, kada dai ace ka yarda da wannan baΖin
Ζazafin da aka shiryamin? Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Wallahi Abban
yara muddin aka ce kai ma ka mara wa masu zargina baya nikam ban ga wanda zan
kama ba. Ni Maryam me marayun Allah suka yimin da zan cutar da rayuwarsu?"
Abba kallonta kawai ya ke yi da idanunsa da suka tasa ga
dukkan alamu bai samu wani baccin kirki ba. Murmushin yaΖe ya bita da shi.
"Ni kin ji na ce maki ina zarginki ne Maryama? Kin ji
wani abu daga bakina?"
Sai ta mike tsaye suna duban juna.
"Ba ka faΙi ba, amma shirunka ya nuna ka aminta da
zargin masu zargi."
Ya kauda kai don wallahi ji yake yi a duniya a yanzu babu
abin da ke mishi muni ya kall sama da fuskarta.
"Maryama, abar zancen. Tunda shi wannan baΖin azzalumin
ya shiga hannu, gaskiya za ta yi halinta ai yanzu. Ki kwantar da hankalinki
masu zarginki za su bari muddin komai ya bayyana."
Yanayin da ya yi zancen sai ba ta gamsu babu komai a
zuciyarsa ba dangane da ita. Ta dai matsa mishi kamar yanda ya buΖata ya faΙa Ιakinsa.
***
Ina labarin Humaira da Fadeel?
Kukan Humaira ya Ζi ci ya Ζi cinyewa. Abubuwa da dama ne ke
Ζara mata Ζarfin kukan. Wannan tashin hankalin na jin wai da sanya hannun Mami
a garkuwa da su ya tsaya a ranta. Ta dinga tunano kalar rayuwar da suka yi da
ita a gidan tsawon shekarun da ba su da yawan da za a kasa Ζirgawa, irin kulawa
da nuna kaunar da ta dinga yi mata. Ita kuwa komai da Mamin ta ke mata ta Ιauke
shi da zuciya Ιaya, ba ta taΙa kawo wani abu na mugun zato a kanta ba idan aka
cire sanin da ta yi Mami ba ta farin ciki da aurenta da Fadeel. Sai yanzun
abubuwa da dama suke mata yawo a kwakwalwa, wai dama ya za'a yi macen da ta
haifi yara da kanta ace ta fi kaunarsu akan abin da ta haifa? Kenan ta tabbata
batun Hajjo da ta ce da biyu Mamin ta dakile ta daga karatun boko? Toh idan ita
din ta kasance Ιiya ga tsohuwar kishiyarta da ta rasu, me Ummita ta tare mata?
Me ta yi mata a rayuwa da har sa ta nakasta rayuwarta har haka? Ta maida ita
Ζaramar budurwa kuma bazawara? Tayi sanadin da aka keta alfarmarta har wannan
masifa ke bibiyarta wato Wizzy. Ta yi sanadin da aka fasa aurenta da masoyinta
Sahabi. Mene ne ribar Mami da ta shuka dukkan waΙannan munanan ayyukan. Shin
kodai Raihana ta sani ne? Tambayar da ya shiga kwakwalwar Humaira kenan. Ta Ιan
muskuta ta share fuskata. Anya Raihana ba ta da wani labarin dangane da Mami?
Yarinyar a yan kwanakin nan ta sauya gaba daya ba ta rabo da kuma da damuwa?
Sai an matsa da tambaya sannan ta ke saita kanta ta shiga harkokinta? Kai
gaskiya tana da tabbacin akwai abin da Raihanar ke Ιoyewa. Sai tausayin
Ζanwarta ta ya mamaye zuciyarta, ita Ιin ba ta da wani aibu a yanzu, ta
tsarkake zuciyarta daga dattin Ζiyayya da hassada irin wanda yan uwanta Tasleem
da Futuha suka Ιorawa kansu. Tana kaunarsu tana kuma zaune da su da zuciya Ιaya
babu wani abu bayan hakan.
Turo Ζofar da aka yi gami da sallama cikin tausassan murya
ya katse tunanin Humaira, ta Ζara sunkuyar da kanta tana Ιan sakin numfashi
irin na wacce ta ci kuka kuma take kan yinsa. A can Ζasan zuciyarta ta amsa
sallamartasa.
Ya Ζaraso cikin dakin sosai, ya yi wanka ya sauya sutura
zuwa jallabiya fara Ζal wacce ba ta Ιoye kyakkyawan tsarin halittar da Allah ya
yi mishi ba. Sai baza Ζamshi yake yi ta ko'ina. Ya Ιan bi Ιakin da kallo kaΙan
yana murmushi da alfahari da zaΙin da ya yiwa Humairar na kalar da ta fiso wato
kore. Sai adon Ιakin ya kasance farin da kore. Zama ya yi a gefenta har kafaΙunsa
na gugar nata. Fadeel kenan, shigowarsa babu aboki ballantana Ιan rakiya.
Hannu ya sa ya yaye rufin fuskarta. Ganin hawaye kwance ya
sanya shi saurin riΖo haΙarta da Ιago kan suka dubi juna, ai yanda ya ga
idanunta sun kumbure sun yi ja sai ya ji wani sabon tashin hankalin na daban.
"Boddo, kukan kike ta yi? Ya Salam, sai ki janyowa
kanki wani ciwon?"
Ya shiga taΙa goshinta da gefen wuyanta don ya ji ko jikinta
da zafi, ita kuwa sai noΖewa take shi ko zuciyarsa daya yake yi. Gaba daya
ganinta cikin wannan halin bai masa dadi ba ko kaΙan.
"Please ya isa hakanan. Kinga yanzu babu zafi jikinki.
Kiyi hakuri tunda komai yanzu yana hannun hukuma. Idan kuma don kin ji ya
ambaci Maminki ne kar ki bari wannan ya yi tasiri a zuciyarki. Tunda har ya gan
shi a hannun hukuma to zai iya ΖirΖirar kowane sharri ya faΙi. Ki kwantar da
hankalinki koma mene ne bincike zai bayyana."
Ta gyaΙa kai, ya lalubo tafukan hannunta ya sanya cikinnasa.
Rashin sabo da hakan daga shi din har ita sai da suka ji wani yarr.
"Kina da alwala?"
Shi ne tambayar da ya yi mata, nan din ma kan ta gyaΙa ta a
kokarin zare hannunta. A hankali ya saki sannan ya faΙa banΙakinta. Can kuma ya
fito ya yi mata umarnin zuwa su yi nafila. Ba musu ta miΖe ta gyara zaman
laffayarta. Bayan sun idar ya dafa kanta ya yi mata addu'o'i. Daga nan ya kama
hannunta ya miΖar suka fita suwa falo. Ta Ιaga kanta a hankali tana kallon
falon, hamdala ta shiga ui a zuciyarta, yau ita dai Humaira ita ce ta mallaki
wannan irin falon da sai dai ta gani a soshal midiya su na yawo don ko gidan
Futuha da ake ta santinsa bai kai rabin nata tsaruwa da kyau ba. Komai a falon
adon skyblue ne da fari, iyakar kyau da tsari ya yi.
Jan hannunta da Fadeel ya Ζara yi ne ya maido ta hayyacinta,
ta Ιan yi saurin janyewa tana Ιan tura baki. Da alama ita ba ta son wannan
baΖon halin nasa na riΖe mata hannu. Ya yi murmushi ya matso dab da ita gami da
sa hannunsa saman Ζugunta ya matse ta gam har fuskokinsu na haΙuwa wuri guda.
Idanunsu a lumshe ba ka jin komai sai bugun da kirjin
kowannensu ke yi. DaddaΙan kamshi babu ko digon wari shi ke fita daga
bakunansu.
"Kin zamo mallakina Humaira, babu sauran wata Ζofa da
ke buΙe tsakaninmu. Babu kuma sauran sharaΙin da ya yi saura. Ki taimake ni ki
bar kokarin yimin iyaka da dukkan inda hannuna ya sauka a jikinki."
Ya yi maganar da muryar da ta rasa na Fadeel ne ko kuwa, har
sai da ta buΙe idanunta, aka yi sa'a shi Ιinma kallonta yake yi a lokacin, sai
dai ga mamakinta, hawaye ne kwance saman kumatunsa. Ta yi kokarin ja baya a Ιan
ruΙe, ya yi saurin Ζara riΖe ta sosai.
"No Humaira, bar ni na ji Ιuminki, na Ζara samun
tabbacin Fadeel ba mafarkin da zai iya farkawa yake yi ba. Alhamdulillah Ya
Rahman."
Ya furta zuciyarsa da wani irin nauyi ga farin cikin da yake
lulluΙe shi. Sabuwar soyayyar Humaira na Ζara huda dukkan wata Ζofa ta jikinsa
tana shiga tana mamayarsa. A Ιangaren Humaira kuwa ba ta san sadda yatsunta
suka sauka a kuncinsa ba, dauke masa hawayen ta yi yayinda itama nata su ke
zuba. Ita ya kamata ta koka ba shi ba, ta wahalar da shi iyaka, ta kuma yi
mishi cin fuska kala-kala, sai dai dukkan wadannan bai sa ya juya baya ya
haΖura da ita ba. Sanadinsa za ta iya cewa ta samu warakar zuci da gangar jiki
daga cutar da ake tunanin iskokai ne masu sanya ta tsanar dukkan wani Ιa namiji
a rayuwa. Ya riΖe yatsunta idanunsa a cikin nata gami da kai su baki ya
sumbata. Ta runtse idanun tana jin kamar ta kwace yatsunta amma kuma roΖon da
ya gama yi mata na kar ta yi mishi kowane iyaka ne ya sanya ta daurewa. Tana
jinsa ya dinga yin yanda ya so har sai da suka nemi faΙuwa sannan ya bar ta. Ta
yi saurin zama a kujera mafi kusa da ita. Shi kuwa durΖuso ya yi a gabanta gami
da riΖo dukkan yatsun hannayenta yana dubanta kai ka ce ranar ya soma ganinta a
rayuwa. Murmushi sosai yake yi yana kallonta yayinda ita kuma ta kauda kai zuwa
gefe guda, kallonsa na haifar mata da yanayi mai kashe kuzarin jiki.
"Nagode, nagode da kika aminta da aurena. Ina mai miki
albishir da cewa kin dace in sha Allahu, kamar yanda dama ni tun tuni na sa a
raina samunki a rayuwa shi ne dacewar da zan yi. Alhamdulillah. Yau ga Fadeel
ga Humaira. Kin ga ranar haΖuri ko?"
Ta Ιan yi murmushi. Ya kai hannu ya shafi leΙΙanta.
"Soyayyata kaΙai ta isa mu rayu cikin farin ciki da
aminci. Nidai na san koda ace har yau ba a wani sona, toh ana ji da ni."
Ta yi Ζasa da kanta, shiru ya biyo baya, shi bai bar wasa da
yatsunta da kuma bin ta da kallo ba, ita kuma ta kasa furta abin da ke yawo a
zuciya da saman leΙΙanta. So ta ke ta ba shi tabbacin cewa itama fa tana so da
kaunarsa wanda ta san ya sani kawai so yake yi ya ji daga bakinta.
MiΖewa ya yi ta bishi da idanu har ya je fa ledojin da ya
shigo da su yana fadin shi yunwa yake ji saboda tun safe bai ci komai ba murnar
an Ιaura aurensu.
Suka ci har ta miΖe ta bar shi, yana jinta tana masa sai da
safe ya gyaΙa kai kawai yana bin ta da murmushin da shi kaΙai ya san ma'anarsa.
Ζakinta ta shiga ta Ιan tura Ζofar, laffayar jikinta ta warware ta ninke ta buΙe
sif dake manne jikin bango ta sanya. Rigar da ta ji Hajjo ta ce mata ta
sanya shi ta fiddo, warware shi ta yi, doguwar riga ce mai hawa biyu kalar
maroon. Gefenta wani gashi ne mai laushi. Ta shiga bandaki ta sauya shiga
sannan ta fito ta nemi wuri ta kwanta bayan ta kashe fitila. Ba ta fi mintoci
da kwanciyar ba ta ji shigowar Fadeel, kirjinta ya hau bugu tara-tara, wai yana
nufin anan zai kwana? Shi ne tambayar da ta yiwa kanta, ta runtse idanunta
tamau alokacin da ya hau gadon sosai, fitilar ya kunna haske ya karaΙe Ιakin,
da kallo ya bi fuskarta, ya sani ba bacci take yi ba, runtse idanun na dole ne.
Ba ta yi aune ba ta ji ya yaye gaba Ιaya bargon, da sauri ta dora hannuwa saman
fuskarta. Ya yi murmushi ya kashe fitilar kafin ya maida bargon ya rufa musu.
Janyo ta jikinsa ya yi sosai, ya fidda hannuwanta saman fuskarta, duk kuwa da
cewar dakin da duhu ba ganin idanunta zai yi ba.
"Please faΙamin koda sau Ιaya ne naji. Kinji?"
Ya na maganar tamkar mai raΙa. Ta yi shiru sai bugun
kirjinta da yake ji, yanayin maganarsa sai ya ba ta tausayi, ta tuna dukkan
gwagwarmayar da ya sha a kanta. A hankali ta bude baki ta ce.
"Ina matuΖar so da Ζaunarka Fadeel."
Ya yi Ιif na lokaci Ζalilan, ita kuwa ta samu wani irin
kuzarin da sai da ta Ζara maimaitawa, kaunar tasa take ji yana fisgarta sosai.
Ai ba ta yi aune ba ta ji sauran kalaman bakin nata sun maΖale adalilin toshe
nata bakin da ya yi da gurbin nasa.
Daren dai sun raya shi tamkar ba za su yi bacci ba.
Washegari suka tashi zuciyoyinsu cike da walwala da soyayya mai tsafta. Humaira
kuwa jikinta ya yi mugun sanyi don tuna Ζ΄ar uwarta Ummita. Wannan abun shi
Wizzy ya kwatar mata da Ζarfin tuwo. Wannan dai Ζ΄ancin da Fadeel ke ta cin
alwashi da alΖawarin kyautata mata saboda shi? Dakyar ta samu lamarin ya fice a
ranta sakamakon kulawar da Fadeel ya dinga ba ta tamkar ya haΙiye ta. Sun kira
waya ta gaisa da Raihana ta kuma tabbatar da samun saukinta, hakanan da su
Hajjo suka zo yi mata sallama sun ba ta tabbacin Ummita ta Ιan saki ranta har
Abba na fadin zai haΙa ta da Anti Maijidda su wuce Bichi.
Hakan ya yiwa Humaira dadi kwarai domin ita kanta ba ta
kaunar ganin Mami a wannan gaΙar, zuciyarta ba ta amince da ita ba kamar a
baya.
***
Kafin su Hajjo su kai ga dawowa gidan Mami, sai ga Jannat
sun dawo gidan har da Futuha gaba Ιaya. Sun samu labarin komai dangane da
zargin da ake yiwa Mami na satar su Ummita. Futuha da Tasleem waΙanda suka san
da zancen hankalinsu ya tashi ainun domin sun san komai ba kuma zargi ba ne.
Jannat kuwa ashariya ta dinga zundumawa gami da yiwa Mamin Allah ya Ζara.
"Kin fifita su akan yaranki na cikinki ai ga sakamakon
abin da kika yi nan kina gani."
Ita dai Mami ba ta ce uffan ba, Tasleem ko da tun a gidan
Futuha take fama da lemun tsami a baka saboda tashin zuciya, wani amai ne ya
taho mata da ya yi sanadin miΖewarta a guje ta faΙa banΙakin Anna. Gaba Ιaya
suka bi ta da kallo. Mami kirjinta ya yi wani irin duka da Ζarfi.
"Wannan tashin zuciyar da kike ta yi dama tun a can ai
nasan ba a banza ba. Sai ki tattara ki koma gidan Hamza tunda akwai sauran rabo
tsakani."
Mami ta juyo a ruΙe ta Ζara bin Anna da kallo mai maganar
hankalinta kwance. Futuha da Jannat babu wanda ya dara don gaba Ιayansu
zuciyoyin ba dadi, ga Futuha, baΖaΖen maganganun da ake yi mata da habaici a
Tiktok ya fi Ζarfin kanta. Ga kuma Yakubu da ya Ιauki Ζ³ar Snow zuwa Saudiya
inda daga nan za su wuce Dubai sai ko London. KuΙin da ya bar mata a wannan
tafiyar shi ne rabin abin da yake ba ta kyauta a wata, gaba Ιaya ya rufe bakin
aljihunsa sai dan abin da bai taka ya karya ba yake ba ta. Ta kuma fahimci
azabar da yake son gana mata muddin ta yi sake za ta dame ta shanye irin kalar
na uwargidansa. Jannat ma dai rigima ce ake ta yi da nata mijin, inda
mahaifiyarsa da danginsa suka dage akan lallai sai ya rabu da ita ko kuma ya yi
aure. Zafi biyu ya haΙe mata ga tunanin inda za ta fara samu ta tattaro kan
kudadenta da ta yi asararsu.
MiΖewar Mami ce ya sa duk suka dube ta, kai tsaye banΙaki ta
je ga Tasleem, suka yi kiciΙus sadda take fitowa tana share baki.
"Ke, yaushe rabonki da al'ada?"
Tasleem ta Ιan yi shiru, ita dai ta san koda ta dawo daga
gidan Hamza tana jego ne ba ta yi wanka ba, tun da ta yi wankan kuma ba
ta Ζara ganin jini ba.
"Ina magana kin mayar da ni sakara! Nace yaushe rabonki
da al'ada?!"
A firgice Tasleem ta amsa.
"Tun farkon dawowata da na yi wankan biΖi. Amma Mami ai
shayarwa nake yi, shi ne dalilin rashin ganin al'adata."
Mami ta Ιan yi jim tana lissafawa, kai ba za ta taΙa yarda
ba, hankalinta ba zai kwanta ba idan har ba bincikawar ta yi don kanta ba.
Wannan yasa ta yi kiran Ζassim a waya ba shiri ya zo. Su Jannat dai sun yiwa
Mami caa wai akan me take zarginta ita dai shiru kawai ta yi. Har Ζassim ya
shigo ta ba shi kudi ya amso mata Pt-strip ba ta ko sauraron zantukan su, Anna
har da su zaginta wai tana zargin Ιiyarta da bin maza alhalin tana idda? Ita
dai ba ta tanka ba, Tasleem kuwa shiru ta yi ba ta ce uffan ba. Suna nan hira
na gudana tsakanin Anna, Jannat da Futuha har Ζassim ya kawo aiken. Mami ta karΙa
ta ce ya fice, da kanta ta titsa Ζeyar Tasleem har bandaki. Tasleem a dole ta
bi umarnin Mamin don itama tana son tabbatarwa, ana yi kuwa sai ga ranΖwalelan
shaidar positive ya nuna a jiki. Mami ta kusan sakin ihu a bandaki, ciki dai
ciki? Toh uban waye ya yiwa Tasleem din ciki?
A haukace ta Ζara tambayarta cikin fita hayyaci.
"Don ubanki wani abu ya shiga tsakaninki da Babandi
ne?"
Ta kasa magana, jikin Tasleem ya hau rawa, dama ta soma
zargin cikin ne ashe ko ya tabbata. Wannan ruΙewar ta Mami ya sa tsoronta ya daΙu.
Ita kam ta shiga uku idan ciki ne ya shiga jikinta. Shirunta kuwa ya tabbatarwa
Mami cewa eh, wani abu ya gifta tsakaninta da Babandi. Ai sai ta shiga duka
Tasleem kamar an aiko ta, Tasleem har ta fito daga bandakin a guje Mamin na
biye da ita har cikin Ιakin. Tana dukan tana tsinewa Babandi. Sai da su Jannat
suka riΖe ta gami da yi mata inkiya kar mutane su dawo su ji.
"Wai waye Babandi? Me kike magana a kai? Ciki
kuma?"
Anna ta nemi ba'asi a ruΙe. Nan Mami ta kora musu bayanin
bokannata da yanda suka yi kaca-kaca akan aikin Humaira da Fadeel da ma yanda
ta tura Tasleem wajensa har mai afkuwa ta afku.
"Maryama baki da hankali! Ke mahaukaciya ce ashe ina
maki kallon mutum mai hankali? Ta ya ya za ki samu saΙani da mutum ki yi mishi
zagin uwaka ubaka kuma ki tura Ιiyarki wajensa?! Shikenan! Yanzu dai ta tabbata
Ιan Bokanki ne a cikin Ζiyarki."
Wannan kalma ta Ζarshe na Anna ya mugun jijjiga zuciyar
Mami. Ai sai ta fashe da wani irin kuka, Jannat masoyiya ga Tasleem itama kukan
ta sanya gami da zuwa ta Ιago Tasleem tana rantsuwar ita dai wallahi sai ta kai
ta an zubar da cikin. Nan da nan Tasleem ta ture ta.
"Aa wallahi! Ba wanda ya isa ya zubarmin da ciki,
Babandi ya ce idan na tabbatar ciki ne da ni toh yana son abinsa idan na haihu
na kai masa!"
Tana maganar kamar ba Tasleem ba cike da faΙa idanunta tsaye
kai ka ce ba ita ta gama kuka yanzu ba. Gaba daya suka bi ta da kallon mamaki.
Kiran da Dawud ke kwalawa Mami iyakar Ζarfinsa ya yi sanadin da suka Ιunguma
cikin tashin hankali zuwa waje. A falo suka yi kiciΙus da shi, lokacin su Hajjo
sun dawo ba su kai ga shigewa masaukinsu ba. Wasu kuwa sun fice zuwa kasuwa
Ζarasa siyayya.
"Meyafaru Dawud?" Ta tambaya jikinta a mugun mace.
Kan ya kai ga cewa komai sai ga Ridwan cikin kayan aikinsa da abokan aikinnasa
su uku, biyu mata sai Ιaya namiji. Fuskarnan tamkar ba shi ne mai fara'a ranar
bikin Fadeel ba. Ya Ιaure ta tamau, ya fito a jami'in aikin na gaske marar son
wasa. Arrest warrant ya buΙe ya nunawa Mami.
"Hajiya mun zo tafiya dake bisa zargin da ake yi maki
na garkuwa da yaran maigidanki. Hukuma ta bamu damar shigar da Ζara kotu."
Wani razanannen ihu Futuha ta saki tana Ζunduma uban ashar
wai Ζarya ne. Shi kuwa Dawud hawaye kawai yake fitarwa don dama labarin da ya
zo kawo wa Mamin kenan. Su Hajjo suka yi cirko-cirko suna kallon ikon Allah har
matan nan suka nufi Mami da zummar tisa Ζeyarta a tafi.
"Me kuke nufi? Ina ku ke zaton za ku kai ni?! Yanzu a
ganinku zan cutar da yaran da nake yiwa so fiye da yara a da na haifa?"
"Hajiya wannan duka shari'a ce za ta bayyana. Yanzu dai
ki bamu haΙin kai mu yi aikin da ke gabanmu."
Wannan ranar ta zo musu da tashin hankula iri-iri. Futuha ta
Ιauki waya ta yi kiran Abba, koda ta sanar masa ban da Allah ya kyauta gami da
kashe wayar babu abin da ya ce. Nan Futuha ta hau fadin wai dama Abba ba sonsu
yake ba, ya fi so ya ga sun watse sun bi duniya! Mami kadai ke son su tsawon
shekarun nan komai da take yi don su take yi.
Ganin Futuha na kokarin yin suΙul da baka ne ya sanya Mami
dakamata wata tsawar.
"Ke! Ya isa hakanan! Nace ki bari haka! Ai Ζarya fure
take ba ta Ζ΄aΖ΄a. Idan ma an yi hakan don a Ιatawa uwarku suna ki kwantar da
hankalinki babu inda Ζarya za ta je. Duk inda za su kai ni zan fito."
Abin da Mamin ta ce kenan sannan ta yi gaba ma'aikatan suka
mara mata baya. Ridwan sai da ya tsaya ya Ιan waiga, rashin ganin Ummita a
wurin sai ya ji hakan bai masa dadi ba. Kawai sai ya sa kai ya fice.
Nan fa yaran Mami kamar su yi hauka. Suka kira Mubarak suka
labarta masa, hankalinsa ya tashi. Ya kira Abba, Abba ya kwantar da hankalinsa
ya ce ya yi hakuri ya nutsu tunda satika ya rage ya kammala ya dawo, ya bari
zai kula da komai.
***
Kamar da wasa sai ga Mami har tsawon sati a hannu hukuma,
babu duka balle zagi, ta kafe akan ita ba ta san Wizzy ba kuma ba ta san ma a
inda ya santa ba. Wizzy ma an tambaye shi yace shi bai taΙa ganin wacce suke
waya ba, amma ya riΖe muryar. Ya kuma sani matar uban su Humairar ce.
Sai da Mami ta cika sati aka shiga kotu, duka wannan Abba
yana asibiti adalilin ciwonsa da ya tashi. Raihana ko ta dawo gida amma Abba ya
bata umarnin tattarawa ta koma gidan Baba Amina don ta Ζarasa jarrabawarta.
Ummita kuwa tana Bichi amma sanadin shari'ar sai da ta dawo.
Ita da Humaira aka nemi su bada bayanin komai da ya faru da
su, haka kowaccensu ta yi magana zuciyoyin cike da rauni babu kamar Ummita dake
Ζara jin tsanar Sadik Wizzy da su Baaba wadanda duk aka titso Ζeyarsu ta
hanyar Wizzy din, kowannensu ya amsa eh ya aikata laifin idan ka cire Mami da
ta dage akan ita sharri da Ζage akai mata. Lauyar da Hajiya Lubna ta Ιaukar
mata ta tsaya tsayin daka wurin yi mata wannan yaΖin. Aka yankewa su Wizzy
hukunci daidai da laifukansu yayin da kotu ta wanke Mami daga zargi bisa duba
da rashin hujja koda Ζwaya Ιaya da za'a kama ta dominsa.
***
Ta dawo gidanta hankali kwance, yaranta gaba daya su na cike
da farin cikin kuΙutar mahaifiyarsu da kuma wanke ta da kotu ta yi idan ka cire
Raihana da ba ta gidan kuma ko labarin ma ba ta kaunar ta ji. Ummita da Humaira
kuwa har abada ba su jin za su Ζara aminta da Mami. Ballantana kuma Abba
da yake ji a jikinsa lallai da saka hannunta. Ya kuma kara yarda da kalar
zalunci na matar da yake aure.
Ta iske Abban a falonsa zaune yana kallon labarai, ga dukkan
alamu hankalinsa ma ba ya kan talabijin din, ya zurfafa cikin tunani. Gaba daya
ya rame kamar wanda ya yi cutar watanni. Ita kanta Mami ta rame saboda tashin
hankulan da ta gani a wannan Ζ΄an watannin. Zama ta yi gefensa. Ya ji zuwannata
amma bai ko kalle ta ba. Kafin ta kai ga magana ya riga ta cikin shaΖaΖΖiyar
murya.
"Maryam, zaman me Jannat take yi a gidana?"
Ta yi turus, ta yi zaton zai ce wani abu a kanta amma sai ta
ji ba ma ta itan yake ba. Cikin Ζ΄ar borin kunya ta ce.
"Ina za ta iya tafiya gidanta alhalin yar uwarta na
garΖame a wajen jami'an tsaro? Adalilina ne ya sanya ta ke zaune."
Ya miΖe zaune sosai daga kishingiΙar da ya yi.
"Ta tattara ta bar min gidana, ba na buΖatar ganinta.
Abin nufi, koda wasa kada ta Ζara gangancin takowa cikin gidannan! Gida dai
nawa ne, ni ke da iko da shi! Toh daga yau ba na buΖatar ta Ζara zuwa."
Sulhu take nema, tana so ta shawo kansa don ta san meke tafe
a ransa a kanta don haka sai ta yi saurin amsawa.
"An gama Abban yara. Zan sanar da ita ba za ta Ζara
takowa ba."
Bai ce uffan ba ya na ta tufka da warwara har sai da ya ji
ta kwantar da kai saman kafaΙarsa.
"Abban yara kana kaunata, naji ance har kwanciya
asibiti ka yi sadda aka tafi da ni. Nayi mamakin wannan Ζazafin da wannan baΖin
azzalumin ya so ya yimin, ya kusa raba ni da rigar mutuncina."
Abba ya yi wani murmushi mai ciwo.
"Kika ce rigar mutunci Maryama? Ina rigar mutuncin naki
yake? Ai a yanzun ma da nake tare da ke, DARAJA ΖAYA kawai kike ci. Ban da
wannan kusan zan iya cewa babu komai da ya rage a tsakanina da ke."
Yana kai wa nan ya zame kanta daga kafaΙarsa, ta yi wani
irin zama tana kallonsa satoto.
"Bangane nufinka ba? Daraja Ιaya kamar ya? Igiyar auren
fa?"
Ta yi tambayar zuciyarta na duka da karfi, kallonsa take yi
kawai tana lissafo ire-iren tashin hankulan da ta jefa kanta ciki duk a
sanadiyyarsa da yaranta. Toh me Yusuf ke shirin ce mata?
Abba ya yi Ιan murmushin takaici.
"Aure? Ai ba ki Ιauke ni miji ba. Nima rashin sani ne
ya kai ni ga Ιaukar mace irinki a matsayin matar aure, uwa ga yarana. A iyakar
zaman da nayi da ke, ki faΙamin abu guda da na tauye maki na haΖΖoΖinki dake
rataye a wuyana Maryama. Abin da ban taΙa zato ba, ashe wayona da hankalina bai
min rana ba tunda har na rayu da mace irinki mai fuska biyu har na tsawon
shekarunnan ba tare da na ankara ba. Kura da fatar akuya, kin cutar da ni kin
cutar da ahalina. Na riΖe ki da zuciya daya, na kula da ke da kuma naki. Wannan
wane kalar sakayya kika yimin? Ni dai Yusuf kika so a kashe? Kika gurΙata
rayuwar yarana? Da me na rage ki? Wace buΖatar ce da ta zame min wajibi ba na
kokari wajen sauke shi?"
Mami sauraronsa take yi amma fa gaba Ιaya ya gama kashe mata
dukkan wani kuzari. Kirjinta ya hau bugu fat! fat! Wato ta tabbata dai Abba da
kansa ya sani ta yi yunΖurin kashe shi da Humaira? Ashe dama kurum ya yi yake
bin ta da kallon shashasha? Dama rigar mutuncinta ya jima da kecewa a idanunsa?
Wani gumi ya shiga tsirfo mata, tana sauraronsa amma ba ta iya fadin ko harafin
A ba har ya kammala ya mike ya fice zuwa Ιaki ya bar ta da nanata zantukan
Ζarshe da ya yi.
"Ki nesanta kanki daga zuwa Ιakina Maryama. Ki zauna a
naki Ιakin har zuwa sadda mai yiwuwa ko zaman ya Ζare ko wani abun daban saΙanin
tunaninmu ni da ke."
Mikewa tsaye ta yi gwuiwoyinta a sake, ashe dai har yanzu
akwai sauran rina a kaba, a tunaninta ta gama rufe bakin tsanyar tunda har
shari'a ta wanke ta ba tare da kawo hujja ko daya zai nuna akwai sa hannunta
ba. Lallai kafin Abba ya ankare da abubuwan da ta shuka na baya, ya kamata ta
san mafitarta. Da wannan ta miΖe ta koma
Ιakinta.
***
Kwanaki uku, abu dai
kamar wasa ta ga dagaske ne, tsakaninta da Abba sai idan ta gaida shi ya amsa,
babu sakin fuska balle har ta samu damar wata maganar. Zai shirya ya yi
ficewarsa ko abincinta ba ya saurara. Jannat kuwa ta tattara nata ya nata ta
bar gidan. Anna abin ya taΙa ranta ta kuma rantse sai ta yiwa Abba magana akai.
Mami dai ta hana ta amma ina! A rana ta huΙu ne da tafiyar Jannat, ta tsaya a
hanyar da ta san cewa dole ta nan din yake zuwa ya fice. Yana fitowa kuwa ya
gan ta. Ζan durΖusawa yanda ya saba ya gaishe ta a mutunce. Ta amsa tana cin
magani gami da gyara tsayuwa sakamakon Ζafa da ta matsa mata.
"Isuhu, na yi shiru ne saboda ban sani ba ko Maryama za
ta iya kokarinta wajen ganin ta sa ka janye dokar da ka kafawa Auta na zuwa
gidannan sai na ga hakan ya faskara. Wannan ne ya sanya ni zuwa da kaina domin
na ji ba'asi. Haba Isuhu, duk wani abu da yarinyar nan ta aikata sharrin shaiΙan
ne, ta ba da haΖuri ta kuma nemi gafarar yarannan (acewar Annar kenan), toh na
mene ne za ka hana ta zuwa inda uwarta take fisabilillah idan dai ba ni Ιin ka
yi shirin kora ba?"
Abba sosai ya yi mamakin son zuciya irin na wannan matar,
wato don ba nata aka yiwa ba? Kai shi yanzu dukkanin dangin Maryama ma tsoronsu
yake domin su na shayar da shi mamaki. Yanzun ne ya Ζara fahimtar cewa ashe dai
ba tsanarsu wasu a danginsa suka yi ba, ashe Hajiya Maijidda ba a banza ta
tsani ganin Maryama ba. Ita din ta jima da sanin ainahin fuskar Maryama.
"Isuhu ka yi shiru ina magana?"
Anna ta buΖata a Ιan zafafe, abin da bai taΙa gani kenan a
tare da ita ba. Koda dai ya sani cewa duk tafiyarsu guda.
"Kiyi hakuri Hajiya, ni dai Isuhu idan har wannan gida
ikona ne, toh Jannat ba za ta Ζara shigarsa ba. Ban raba maku zumunci da ita ba
tunda taku ce, amma idan dai a wannan gidan ne toh sai dai ku yi hakuri. Duk
sadda kike da buΖatar zuwa wajenta in sha Allahu mota da direba ba zai gagareni
samar maki ba."
Anna ta saki baki galala, yau Isuhu da kansa ke yi mata
musu? Wato dai ba a shaidar Ιan kuturu sai ya girma da yatsa.
"Ai shikenan, tunda dai hakanan ka ce nima yanzu dole
zan haΖura da zaman gidanka. Allah ya bamu alherinsa."
Abba ko a jikinsa ya miΖe.
"A gafarceni Hajiya, amma ni dai na gama yanke magana.
Ban ce ki bar gidana ba saboda ba ki yimin komai ba.."
"Aa, wannan dai kora da hali ne. Ba Auta kaΙai ka kora
ba, nima dama watakila kana da niyyar kora ta tunda iyakar saninka ai ba zan
rayu a gidan nan babu Auta ba. Nima dai watakila kana Ζullace da ni, babu yanda
ka iya ne shiyasa."
Abba ya Ιan yi murmushi mai ciwo jin abin da ke fita daga
bakin ΖAN ADAM mai mance halacci, mai son kai da son zuciya. A yau dai Anna ita
ke korar kanta daga gidansa saboda son rai irin nata.
"Ni dai Allah ya sani, ban kore ki daga gidannan ba
saboda na dauke ki tamkar uwa a gareni. Ina mai baki hakuri bisa abin da na yi
idan bai maki dadi ba. Ki yi hakuri hakan ba zai sauya komai ba."
Daga haka ya sa kai ya fice, yana jin Anna na salati da
kiran wai dama can ya gaji da ciyar da ita amma bai ko juyo ba sai murmushin
baΖin ciki da tausayin kansa da ya ke ji na zaΙen tumun daren da ya yi tun a
farko. Kewar iyayensa ya ji na mamayarsa, ashe dai iyaye ba za a rabu da
kewarsu ba musamman ma irin nasa nagari masu halayyar dattako. Ya yi musu
addu'ar samun rahmar Ubangiji kana ya shiga mota. Madadin zuwa kasuwa sai kawai
ya fice zuwa gidan Ζanwarsa Baba Amina.
***
Ya iske ta zaune,
Raihana ba ta nan ta fice jarrabawa, hakanan sauran Ζ΄anmatan yarannata su biyu
su ma sun fice. Ita daya ya iske. Tana ganin da yanayin da ya shigo nan da nan
hankalinta ya tashi, ta kira sunan Allah a zuci da kuma fili.
Bayan ya zauna ta gaidashi. Kawai daga tambayarsa ko lafiya,
ya soma zubar da hawaye. Baba Amina mace mai saurin kuka don har Abba na cewa
su Humaira ita suka biyo, nan da nan ta soma kukan itama.
"Yaya lafiya? Ko mene ya yi zafi maganinsa Allah."
Ya jinjina kai. Ya ba ta labarin dukkan abin da ya sani a
yanzu game da Mami har da yanda suka yi da Anna. Ya kara da fadin.
"Amina na yi zaΙen tumun dare."
Baba Amina zuwa lokacin kuka take yi sosai. Tausayin Abba da
kuma tashin hankalin da ta ji na wai Mami na neman rayuwarsa ya sanya ta wannan
kukan. Abban da ya zo don ya samu a rarrashe shi, sai shi ne ya koma rarrashin.
Ta mike ta hado masa kayan shayi da abinci, ta yi mamakin yanda ya zage ya ci
kuwa, tausayinsa kwarai ta ji, har ta kasa hakuri Ζarshe ta dube shi.
"Toh yanzu Yaya hakanan za ka yi zaman rayuwa da ita?
Nikam hankalina sam bai kwanta ba, shikenan ka haramtawa kanka cimar gidanka
saboda Maryam?"
Ya dan yi murmushin yaΖe bayan ya kora ruwan shayi mai dumi
a cikinsa.
"Amina kenan, wallahi ganinta ma bana son yi. "
Takaici ya kama Baba Amina.
"Toh Yaya ka yi aure mana."
Ya Ιan yi jim sannan ya jinjina kai.
"Tsoron matan nake Amina, ba zan iya auren kowa ba a
yanzu."
"Ba duka aka taru aka zama Ιaya ba Yaya, ni wallahi
dama na jima ina yi maka sha'awar auren wata baiwar Allah, da ace za ka bani
dama ni zan san yanda zan shawo maka kanta ta amince."
Ya yi murmushi.
"Wato dama kin dade kina so na yi auren kenan."
Ta yi murmushin itama.
"Eh toh, gaskiya kusan hakan ne. Tun da na soma gane
wace ce ainahin Maryam na ji haka kawai ina son zamanka tare da wata bayan
ita."
Abba ya girgiza kai.
"Mutum abin tsoro ne Amina. Kedai kawai Allah yasa mu
dace."
Ta amsa da amin tana mai kara tausayawa rayuwar Yayannata.
Haka ya yi mata sallama ya tafi bai ko damu da sanin ko sunan wacce ta zaΙar
masa ba. Kusan ma bai dauki lamarin da muhimmanci ba. Ita kuwa ta dauke shi da
matukar girma, ta kuma dauki Ιamarar dagewa da addu'a har kafin ta tunkari Ιan
uwan mahaifinsu Baffa Tukur da zancen, tana son ta ga tabbatuwar lamarin ko don
samar da farin ciki ga yayanta da kuma ganin yanda Maryam za ta Ζara bayyana
munanan Ιabi'unta kowa ya ankara da shi. Ai tunda har Raihana da kanta ta bude
baki ta ce dama Abbanta ya kara aure, ta san cewa lamarin babba ne.
***
Tafiya ta yi tafiya
har aka kwashi watanni biyu, Humaira cikin ikon Allah ta samu juna biyu, wani
irin tarairaya na musamman ta ke samu daga Fadeel, a wannan watanni Abba ya
hana ta taka koda harabar gidansa da sunan ziyara, acewarsa ta yi hakuri da
zuwa gidan zuwa wani lokaci. Ita kuwa zuwa lokacin Ζarshen damuwa ta shige shi
domin so take yi ta ga Abbannata saboda ta sani tabbas yana cikin damuwa. Ta ji
komai daga bakin Raihana.
Ganin wannan ne yasa Abba amincewa da zuwanta, ranar ko da
ya kasance na zuwannata bai fita kasuwa ba, zamansa ya yi a gida. Yana zaune a
falonsa Tasleem ta shigo gaishe shi, ya mance rabon ma da ya ganta don har
mantawa yake yi ta a gidan, ya bita da kallo sosai ta sha zumΙulelan hijabi
tana ta kare cikinta wanda bai kai ga fitowa ba amma hakanan take tsarguwar
kada Abban ya ankare da shi. Shi kuwa ramar da ta yi yake bi da ido. Ya amsa
gaisuwarta a daΖile ya kauda kai.
"Abba don Allah ina son Ιan wani abu zan siya kayan
sanyawa na ciki."
Ya Ιan yi jim, tabbas yanzun ya sani tana da hakki a kansa,
idan bai mata ba yana tsoron Ιacin zamanin nan. Ya dan kara dubanta, sai ta ba
shi tausayi. Yarinya Ζarama ta haΙu da zawarci saboda kishin banza da ta Ιorawa
zuciyarta har ya kai ta ga marin uwar mijinta.
Hannu ya sa a aljihu ya fiddo kudi ya Ζirga dubu goma ya
miΖa mata. Ta yi mamaki sosai don ba ta ma zaci za ta samu kamar hakan ba. Ta
yi godiya, har za ta tashi sai ya kira ta, dawowa ta yi ta zauna jiki a mace.
Zuwa yanzu ta gaji da zuwa wajen Babandi sai dai ta rasa dalili idan har ya
dauki waya ya kirata toh ko me take yi ba ta kammalawa tana rawar jiki za ta je
wajensa. Nasiha mai ratsa jiki Abba ya yi mata game da rayuwa da kuma faΙa akan
rashin alfanun zaman mace babu aure. Ya nuna mata hakan ba zai Ζare ta da komai
ba, yanzu idan babu shi a duniyar wa za ta tambaya? Abba dai sosai ya yi mata
faΙa akan ta tsoraci Allah a lamuranta, kada ta bari son duniya da abin da ke
ciki ya rufe idanunta. Tasleem jikinta ya Ζara mutuwa, ita fa dama yanzu ta
gane dama kyau ba ya kawowa mace miji mai arziki balle kuma surar jiki. Kawai
ta gane kaddarar mutum ce komai dake faruwa, yanzu ta bar yiwa kanta hangen
miji irin na Humaira don ta san ba za ta samu ba, ita babban abin da ke ramar
da ita bai wuce cikin Babandi dake jikinta ba wanda ta Ζi ta zubar saboda
tsananin tsoron abin da zai biyo baya tsakaninsu idan ta zubar.
"Ζ³ar uwarki tana nan shigowa yau za ta kawomana ziyara.
Ki sa Ladidi ta samar mata wani abin."
"Abba wa?"
Ya dube ta.
"Humaira."
Ta ji kwalla sun cicciko mata, ta sani Humaira ta zama
hajiya, ko ba ta ganta ba ta san za a ganta cikin kwanciyar hankali da nutsuwa
ba kamar ita ba da ta rasa hakan. Gatanan ba wan ba Ζanin, Ζarfi da yaji ta
zama kwartuwar Boka. Kullum cikin aikata zina take yi babu ji babu gani.
"Toh." Abin da ta firta kenan ta mike ta tafi.
***
Tun fakawarsu a harabar gidan take ta zumuΙin fita, ya yi
sauri ya danna lock. Ta juyo tana marairaice fuska.
"Kai don Allah Habeebee."
Ta faΙi a shagwaΙe. Ya yi murmushi gami da lakuce mata karan
hanci.
"Ba wani Habeebee, mun zo tare amma sai rawar Ζafa kike
ki yi gaba ki kyale ni?"
Ta Ιan turo baki kaΙan, ya kai yatsunsa zai buge ta yi
saurin riΖe yatsun ta sumbace su kasancewar gilasan motar masu duhu ne sosai
(Tinted).
"Kai Boddo, kar ki sa fa a fasa shigar nan mu juya
gida."
Ya faΙi da murya mai cike da bege. Ta yi saurin sakin
hannun.
"Toh yi hakuri na bari."
Ya Ιan lumshe idanunsa kafin ya buΙe su yana murmushi daga
nan ya buΙe motar suka fito tare.
Tana leΖensu ta window, tun da ta ji tsayuwar mota ta yi
azamar zuwa jikin tagar Ιakinnasu ta tsaya. Koda suka fito ma a kan idanunta
ne. Kallon tsaf ta yi musu da ya Ζara haifarmata da tausayin kanta da baΖin
cikin yanda rayuwarta ta Ζare.
Sun yi kyau abinsu, Humaira ta Ζara haske da jiki, ta ci ado
cikin wani tsadadden leshi ruwan toka mai adon baΖi ko daga idanu an san zai yi
laushi, baΖin mayafi da jaka da takalminta kuwa, ai sun Ζara fiddota a matar
manya ballantana idan aka je ga sarΖar da ta sanya silver colour da abin hannu.
Ga wani arnen agogo shima. Hakanan shi ma Fadeel ya yi kyau cikin farar
shaddarsa.
Tasleem dake tsaye jikin window sai ta ga tafiyar da suke yi
ma da murmushi da Ζ΄ar hirar da ta ga suna yi tamkar da gayya suke yi don su
Ζara turamata haushi. Sai ta yi saurin sakin labule ta nemi wuri ta zauna, kuka
sosai ta shiga yi, ita kam babu wa balle Ζanin. Ta samu labarin Hamza ma yana
shirin tafiya Ζasar waje don wani course da aka tura shi na aikinsa. Ita kam ba
ta da rabo sai na wahala. Ta shafi cikin Babandi dake jikinta, sai kawai ta sa
hannu a kai.
"Na shiga uku na kashe kaina ni Tasleem!"
Ta faΙi da murya a Ιage, kusan ma babu wanda ya ji, Mami na Ιakinta
yayinda su Walid suke can suna murnar ganin Humaira sun kaΙa sashin Abba.
Wannan ne ya sa ta yi kiΙanta da rawarta. Ζarshe ta miΖe ta
zura hijabi ta Ιauki fos Ιinta, gwara ta je wajen Jannat don ta nemawa kanta
mafita. Ciki dai ba zai zube ba, Babandi ya rantse idan ta zubar to fa sai ya Ιauki
mummunan mataki a kanta. Wannan ne abin da take shakka. Saboda ba ta son ya
kirata a waya ne yasa ta kashe wayar gaba Ιaya ba ta ko marmarin buΙewa gudun
kada ya nemi ta zo.
***
Mami kuwa ko kadan ba ta da labarin zuwan Humaira, tana
dakinta saboda abin duniya da ya yi mata zafi. Sauyin da Abba ya yi mata, ga
waya da ta yi da Anna inda ta fesa zagi na uwa da uba ga Abba a wayar sakamakon
ta bar gidan Jannat tana hanya za ta koma Agadez. Ba birninta ba, Ζauye bisa
rakiyar Jannat. Ita dai Mami ba ya iya cewa komai ba.
***
Humaira da Fadeel zaune a gaban Abba, hira suke yi har da
Fadeel wanda yake yiwa kallon Ιa a yanzu sama da suruki. Su Walid da Muhsin ko
na gefen Fadeel su na cin cakulet din da ya ba su.
"Toh Mamana ba za ki kawo wa mijin naki ruwa ba?"
Sai kuma kunya ya kama ta, ta miΖe tana murmushi.
"Ki shiga can an yi maku girki sai ki taho da
shi."
Ta amsa da toh sannan ta fice su Walid suka bi bayanta,
Fadeel ya bi ta da kallo tamkar ya maida ta ciki, Allah ya sani, bai san adadin
son da yake yiwa baiwar Allahn nan ba. Hakanan Allah ya sanya masa, ba ya fatan
ya so wata bayan ta. Ya fi kaunar Ζare rayuwarsa tare da ita.
"Ζana Fadeel."
Maganar Abba ya katse tunaninsa. Shi yana can kallon Ιiyarsa
shi kuwa idanunsa na kansa yana murmushi da kokarin auna irin kaunar da ya gani
a idanunsa da yake nunawa Ζiyartasa. Ya yi saurin amsawa gami da Ιan shafa
Ζeyarsa don ya Ιan ji nauyin Abba, ban da iyayen nasa maza babu wani ko wata da
ya ke jin nauyin nuna soyayyar Humaira a gabansa, hatta Anti Amarya ba nauyinta
yake ba don sun je gidan sau daya da daddare bayan aure. Alhaji ya musu nasiha.
"Ka ce kana da magana kuma na ji ka shiru."
Sai yanzu ya tuna ma ya kira Abban a waya tun kafin zuwansu
akan zasu yi wata maganar. Ya jinjina kai.
"Eh Abba, na Ιan sha'afa ne. Dama akan zancen abokina
ne, Ridwan game da Ummita.."
Abba ya tari numfashinsa yana murmushi.
"Nasan da maganar, yaron da kansa ya zo ya same ni ya
nemi iznin zuwa wurinta a can Bichi don su Ζara daidaita kansu. Ban kuma amince
masa ba sai da na nemi yardarta ta waya, ta kuma amince. Bayan wannan ne ban
dai san ko akwai wani abu ba."
Fadeel ya sha mamaki, shi fa sati guda kenan da Ridwan ya
nemi alfarmar ya je masa wurin Abba, shi ko ya na mance domin idan ya
gama wasu uzurorinsa babu abin da ke yawo a kwakwalwarsa face Humaira da
tunaninta. Cike da kunya da Ιan murmushi ya ce.
"Oh, Abba ai sati guda ma kenan da muka yi maganar da
shi, ni ne dai ban samu zuwa ba sai yau.
Dariya Abban ya Ιan yi.
"Toh ai shi tuni ma inaga dai ya je."
"Allah ya tabbatar mana da alheri."
Abba ya amsa da amin. Suka cigaba da hirarrakin duniya.
***
Ita ko Humaira shigar ta babban falon tana jin hirar da su
Waleed ke mata wai Anti Tasleem tana nan, Anna kuma ta bar gidan sun yi faΙa da
Abba. Ita dai ba ta ce komai ba amma ta cika da mamaki, sam ba ta da labarin
tafiyar Anna, wato dai saboda Jannat itama ta bar gidan? TaΙe baki Humaira
kawai ta yi. Ita kam tana tausayawa Abbanta, da ganin yanda ya rame ma za ka
fahimci cewa akwai wata damuwar dake cin ransa wanda ta sani ba zai wuce
sharrin Mami da a yanzun suka san da shi ba. Ganin sun kasa barin hirar
gulmammakin da suke tsinta ya sanya ta tsawatar musu.
"Toh ya ishe ni hakanan, Mami tana gidan?"
Suka amsa da eh, ko don Abba ita kam za ta shiga su gaisa,
ko ba komai ta haifi Raihana, ta haifi mutum irin Yaya Mubarak mai kirki,
sannan su Yassar wadanda yanzu tsakaninsu babu laifi an samu sauyi.
Da sallama a bakinta ta sa kai a Ιakin. Ta shiga, Mami ta Ιago daga kallon wayar da
take yi ta dube ta don ba ta gama tantance cewa ita din ce ba ko aa. Babu shiri
fuskarnan ta koma tamkar an aiko mata da saΖon mutuwa. Kallonta take yi tana
Ζara nazartar tsadadden leshin dake jikinta da ma mayafin, mayafi ne na masu kuΙi.
Fatarta kuwa tamkar ka taΙa jini ya fito ga wani cikowa da ta Ζara yi. Wallahi
da ace za ta iya yanzun za ta tsire Humaira da wuΖa ko ta huta da wannan azabar
baΖin cikin da ta ke ji game da ci gaban da ta samu. A Ιangaren Humaira ko tana
nufarta tana Ζara hankalta da yanda ta rame sosai.
"Mami ina wuni."
Ta gaishe ta a mutunce, madadin ta amsa sai ta kawar da kai
ta miΖe tsaye ta juya mata baya. Hawaye ne suka zubo mata, hawayen baΖin ciki
wannan daukakar da ba ta fito daga jikin tsatsonta ba, sai ma ya kasance
yaranta sun Ζare a wahale.
"Me ya kawo ki Ιakina? Ki tashi ki ficemin bana
buΖatarki balle gaisuwarki!"
Humaira ta shanye zafin maganar da ta jefa mata, wato dai
ita Mami ba za ta taΙa saukowa ba.
"Kiyi hakuri." A zafafe ta juyo
"Hakurin uwarki zan yi?!"
Ta yi mamakin ganin hawaye jage-jage kwance samam fuskar
Mamin. Ta kuma cika da al'ajabin wannan zagi da ta bi marigayiyar uwarta da
shi.
"Mami me ya yi zafi?"
Wani banzan kallo ta yi mata, itama Humaira ranta ya gama Ιaci
sai tafarfasa yake yi.
"Har abada ke dai Humaira na tsane ki, ban taΙa
kaunarki ba ballantana kuma ita uwarki Fatima, ki gaggauta cirewa a ranki wai
Maryam za ta taΙa yi maki kallon wata aba da za ta kalla da mutunci a rayuwa.
Ke dai annoba ce domin tun shigowarki cikin rayuwata nake fama da abubuwa
iri-iri a rayuwa! Ki ficemin a Ιaki."
Murmushin baΖin ciki ta yi ta miΖe tsaye, ji ta yi babu wani
sauran gurbi na daraja da ta ba wa Mami a zuciyarta. Dama ta jima tana hasashen
wannan rashin kauna, a yau kuma ta tabbatar mata da hakan da bakinta.
"Ko ba ki furta ba zan fice Mami, na jima dama da
fahimtar ba kya kaunata, fuska biyu kike nuna min. Sai dai ki sani Mami, ni dai
Humaira Ιiya ce ga Abba, ta jini da tsoka. Babu mai sauyawa tuwo suna, ai DUKAN
RUWA ba zai hana gwarje amo ba, kin so ganin rayuwata ta lalace, kin so ki gan
ni a lalace sai dai kuma ba alfahari ba, Alhamdulillah Ιiyar Fatima ta samu
abin da ba ki taΙa zato ba. Rayuwarta ta inganta, ta kuma samu miji Ιaya tamkar
da dubu. Bana alfaharin kasancewar na samu abinda wasu ba su samu ba, amma ina
alfahari da mijin da Allah ya mallaka min. Da ke da babu a rayuwata ba zai
amfane ni da komai ba, a baya ina maki kallon uwa kuma mai sharen hawaye a
yanzu kuwa ina maki kallon MATAR UBA marar kirki mai son zuciyarta, ki sa a
ranki in sha Allahu yanzu ki ka soma ganin cigabana a rayuwa ba dai ci baya ba.
Na bar ki lafiya."
Tana kai wa nan ta juya ta fice jikinta har rawa yake yi
saboda tsabar Ιacin rai da tsananin fushi, idanunta sun kaΙa jazur amma hawayen
ya Ζi zuwa sai sauke numfashi take yi akai-akai, gaba daya ta mance ma da wani
batu na Ladidi da ruwan da za ta kai, sai kawai ta koma falon Abban cikin
wannan yanayi.
Mami kuwa baki sake take kallon hanyar da Humaira ta bi,
wani irin shock ne ya shige ta ba kaΙan ba, Humaira dai yarinyar da ta ke
rainawa ita ce ta budi baki ta yi mata Ιiban albarka da maganganu masu zafi da
soya zuciya? Ita fa Humaira da a baya ta ke mata biyayya tamkar ta kwanta ta
taka gadon bayanta ta wuce?
Sai ta dube dirshan tana auna maganganun da ta yarfa mata,
wani irin ashariya ta Ζudunduma ta watsar a iska don babu kowa a Ιakin. MiΖewa
ta yi a karshe ta yafici gyalenta da kudin da za ta shiga abin hawa. An kai gaΙar
da za ta kai kanta gaban Babandi, ta ji ta yarda za ta haΙa shi da dukkan abin
da ya cancanta ta roΖe shi akan ya yafemata ya fice a rayuwar Tasleem Ιiyarta
sannan ya nema mata mafita akan wannan masifar da ke damunta. Daga wannan sai
wannan?
***
Humaira ko su Abba da Fadeel na cigaba da taΙa hirarsu,
kawai sai ganinta suka yi. Fadeel da ke kallon Ζofa shi ne ya soma ganinta,
daga yanayinta ya san babu lafiya, tsaye ya miΖe har ya mance da Abba cikin
sauri ya nufi matarsa. Abba ma tuni ya miΖe ganin halin da Humairar ke ciki.
"Boddo, lafiya?" Ya tambaya a rude yana riΖo kafaΙunta.
Babu baki sai kawai ta shiga girgiza kai, sai a sannan
hawayen suka zubo amma fa ba ta ce komai ba. Abba ma ya Ζaraso.
"Mamana ya aka yi na ganki haka? Meyafaru?"
Kalmar mamana da Abban ya furta ya sanya ta jin wani sabon
rauni ya taho mata, gaba daya gaΙoΙin jikinta suka mutu tuna cin mutuncin da
Mami ta yiwa Mahaifiyarta a yanzu. Sai kawai ta shiga kuka sosai har kafaΙunta
na girgiza.
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Na tabbata aikin
Maryam ne, ina zuwa." Daga haka Abba
ya yi gaba, da wani irin zafin nama Fadeel ya haΙa ta da jikinta ya
rungume tsam, nan da nan nashi idanun suka kaΙa, a duniya ya tsani abin da zai
taΙa Humaira tun a baya ballantana yanzun da ya Ζara sanin wace ce ita.
"Please ya isa, ya isa kiyi hakuri Boddo, so kike ki
kashe ni? Ζirjina zafi yake yi idan kina kuka."
Jin haka sai ta Ιan soma rage Ζarfin kukan, ya Ιago ta ya
shiga share mata fuskar yana lallaΙa ta, ya sumbaci saman leΙbanta, ya koma ga
dukkan kuncinta biyu da saman idanu zuwa goshi. Gaba daya ya rikice neman abin
da zai haifar mata da nutsuwa kawai yake, don haka sai ya Ζara sanya ta a
jikinsa yana Ιan shafa gadon bayanta. A hankali ta zame jikinta tana Ζara goge
hawayen da suka zubomata gami da bin shi da murmushin yaΖe don ta kwantar masa
da hankali.
"Habeebee a falon Abba muke fa."
Ya Ιan lumshe idanu ya buΙe, har lokacin bai ga abin da zai
sakar masa da zuciya ya yi murmushi ba, sosai Ιacin ran Humaira ke sauya mishi
yanayinsa, kusan zai iya cewa yana fin ta jin zafin duk wani abu da zai rusa
farin cikinta.
"Gida zamu tafi, shiga ki yiwa Abba sallama."
Ta Ιan yi narai-narai da fuska, abin mamaki, abin da bai taΙa
faruwa ba ta gani haΙe rai sosai ya yi tamkar ba Fadeel ba.
"Kar ki yimin magiya Boddo, na riga na faΙa, gida zamu
tafi. Ki shiga ki bi umarnina kawai."
***
Shi kuwa Abba yana
isa falon da shirin shiga wajen Mami sai ga ta nan buguzum-buguzum ta fito rike
mayafi da ta kasa yafawa, ya yi daidai da fitowar Tasleem don ta je wurin
Mamin. Ganin Abba da Mamin sun tsaya kallon-kallo sai ta yi turus. Abba ya dan
dubi su Waleed gami da ba su umarnin su je wasansu, bayan sun fice ya maida
duba ga Mamin.
"Maryam me kika yiwa Humaira?"
Ya fadi hakan saboda wasu lokutan yakan kira sunan Humairar
musamman a irin lamari haka mai muhimmanci. Ta bishi da kallon tara saura domin
a yanda zuciyarta ke tafarfasa ba shi ba, ko ma waye ya nemi faΙa mata baΖa
akan wata Humaira toh ba za ta bar shi ba.
"Ita Ιin banza! Kai yanzu Isuhu saboda ka kasance
butulu har za ka iya duban fuskata ka ce wai me na yiwa Humaira! Toh uwarta
Fatima na zaga ko za ka rama mata?!"
Ta na maganar kai ka ce duka za ta hau Abban da shi. Ya Ιan
runtse idanu sannan ya buΙe.
"Kin zagi uwarta ba zan rama mata ba, amma zan dauki
mataki a kanki. Nan dai gidana.."
"Kora ta za ka yi? Nace kora ta za ka yi butulu?!"
Ta tari numfashinsa tana hayagaga har da turo kirji da Ιan
Ζara tsawo don Abba ya fi ta tsawo sai ta Ιaga kai ta ke iya kallonsa.
"Ba zan kore ki ba, idan ma korar ce akwai lokacinsa.
Sai dai ki sani ba zan lamunci ki dinga zagin Ιiyata ba. Ki kiyayi harshenki a
kanta Maryam don ba za ta Ζare maki ta daΙi ba. Zan iya ture wancan maganar da
na faΙamaki na aiwatar da abin da ba za ki taΙa zato ba."
Mami ta daka wani tsalle ta yi wurgi da mayafi da
dankwalinta ga wayarta na faΙuwa ta buga tafi kamar wacce matsalar kwakwalwa ya
sama.
"Ka sakenin mana Isuhu sai me? Nace ka sakenin! Butulu kawai wanda ke mance halacci! Ba don ni
Maryam ba kana tunanin za ka samu wannan ni'imar da ka samu? Wallahi ba don ni
ba da yanzu kana yawo da tsumma! Amma saboda kai ba ka san halacci ba har yau
ni Maryam kake batun sakina akan wata shashashar banza ragowar maza Hu..."
Wani wawan mari ya sauke a saman Ζucninta, da wani irin gudu
Tasleem ta taho ta riΖe kafar Abba tana kuka.
"Abba don girman Allah ka rufamana asiri, ba don halin
Mami ba ka yi hakuri ka yafemata."
Mami kuwa tun daga marin ta yi Ιif saboda ba ta yi zatonsa
ba, ita kokari ma take yi jinta da ya Ιauke na wucin gadi ya dawo ga wani
hazo-hazo da take gani. Abba ko maganar da ya yi niyyar yi har yana Ιaga yatsa,
ya fasa sakamakon riΖo da magiyar da Tasleem ke ta yi babu ΖaΖΖautawa, sai
kawai ya dan bugi Tasleem da Ζafa don ta sake shi aikuwa da sauri ta saki Ζafar
saboda cikinta da ya Ιan taΙa ta kuma ji zafi, ta yi baya da sauri ta a rike
cikin. Ya juya ya fice zuwa dakinsa. Mami kuwa sai ta hau bugun Tasleem.
"Don ubanki wa yace ki rike shi?! Yar iska kawai! Ki
bar shi ya sake ni."
Tasleem na kuka kira take yi
"Mami cikina fa." Ladidi ce dake daga kicin tun
dazu tana jin abin da ke faruwa ta shigo da sauri ta hau roΖon Mamin. Ta dai ji
Mamin na batun wai Tasleem ba za ta haife mata Ιan boka ba dole a san yanda
za'a yi ta koma wa Hamza, sam idanunta ma ya rufe ba ta san me take firzarwa
ba. Mamak da tsananin tsoro ya cika zuciyar Ladidi, wai kuwa Mami Ζalau take?
Tabbas a lura da ciki a jikin Tasleem amma maganar da Mamin ta yi wai ciki na
Boka ne ya fi komai girgiza ta. Tsabar kaduwa sai ta tsaya cak rike da hannu a
haΙa tana kallonsu yayinda Mami ta kwashi tarkacenta ta fice sai dai wannan
karon gidan Hajiya Lubna ta nufa. Tasleem ko Ιaki ta shige dakyar tana jan
Ζafar borin kunya don ta sani Mami ta gama kwaye mata zani a kasuwa, Ladidi ta
san komai yanzu.
"Jar uban can!" Abin da Ladidi ta ce kenan kawai
ta juya gwuiwa a sake don kwaso kulolin girkin da ta yi zuwa falo.
***
Daidai lokacin da
Humaira ta juya da zummar zuwa kiran Abba don ta ce masa zasu tafi, sai ga
Abban ya shigo. Ganin yanayinsa ta sani yana cikin damuwa. Shima bai ko zauna
ba ya dubi Fadeel.
"Ζauki matarka ku tafi Fadeel."
Ya fahimci yanayin Abban kwarai, ya amsa da toh ya fice rike
da jakar Humaira itama ta durkusa ta yiwa Abban sallama tana hawayen wannan
kwantaccen damuwar da ta gani tattare da Abban. Mami ta zame musu bala'i.
"Abba ka yi hakuri."
Ya dan yi murmushin yaΖe.
"Bakomai Mamana, jeki, Allah ya yi maku albarka."
Ta amsa da amin ta fice, wannan zuwa dai bai musu dadi ba
sam.
Suna tafe tana
satar kallonsa, hannunsa sarΖe a nata amma ba ya ko kallon inda take sai ma
fuskarsa da har lokacin babu Ιigon walwala. Har suka je gida bai fasa yanda
yake mata ba, ya fita a mota tana kallo ya zagaya ya buΙe mata murfin ta fito
sannan ya maida ya rufe motar.
Ζakinsa ya wuce kai tsaye tana kallonsa, tana kuma lura da
shi. Sai ta kasa jure wannan fushin da ya shiga sanadin kukanta da Ιacin ranta,
ta ji kamar an Ζara ninka mata kaunar Fadeel, ita fa a yanzun ma gani take yi
son da ya ke mata wasa ne, shafar mai ne akan wanda take masa. Ta kasa wucewa Ιakinta
kamar yanda ta yi niyya kawai sai ta bi bayanshi. Ta iske shi ya fidda riga
daga shi sai farar singiletinsa, suffar kyakkyawar halittarsa ta fito Ζal,
wanda bayan ita ba ta fatan a samu wata da idanunta za su dinga tozali da shi.
Ya ji shigowarta, ya daure iya daurewa bai Ιago ya kalle ta ba amma fa kokawa
yake yi da zuciyarsa, ta karaso ganin kansa a Ζasa sai kokari cire agogo yake,
ta sa hannu a saman haΙanta ta Ιago kansa idanunsu ya sarΖe a na juna. Hawaye
take fitarwa sosai tsabar ganin kamar a yau ta rushe dukkanin wasu
alΖawarurruka da ta Ιaukarwa kanta na ba za ta Ιata ran mijinta abin kauna da
sonta ba har abada, amma tun ma ba su je ko'ina ba ta hassasa mishi bacin rai.
"Habeebee ka yafemin don Allah." Shi kuwa ba ta
san cewa kukan ne ba ya so ba. Ya yi saurin goge mata su zuciyarsa na Ιan
sassauta Ιacin ran.
"No Boddo, please ya isa kar ki yimin illah, ni
damuwarki ce na tsana, bana son abin da zai Ζara sanyamin ke kuka. Ba za ki
gane zafin da zuciyata ke yi idan kin shiga damuwa ba. Wallahi nakan daina
ganin girma da mutunci wanda ya haddasa damuwar dole gareki. Ke ce bana son na
ga kin shiga damuwa, duba ki gani, mun fita da farin ciki mun dawo da abin Ιacin
rai. Wannan Mamin taki ni..."
Sai kuma ya haΙiye abin da ya yi niyyar faΙi, kawai sai ji
ya yi ta kai bakinta saman nasa, nan da nan ya ji ya dauke wuta, ta sa hannuwa
tana shafar wuyansa. Bai san lokacin da ya riΖo ta gaba Ιaya ba jikinsa har
wani rawa yake. Yau dai Boddo da kanta ke sarrafa shi, wannan al'amari ne da ya
jima yana son ganin ranar zuwansa. Ita da sau da yawa ke kasa yi mishi sumba
sai ya yi kamar zai yi me don roΖo. Nan ma ana yi ake saurin juya baya a rufe idanu.
Abin da ya biyo kuwa ba zai rubutu ba, shikenan suka mance
da dukkan wani Ιacin rai da damuwa sai wacce ta zama dole.
***
A can Bichi kuwa Anti
Maijidda ce ta yi shiru kawai ta zuba wa Baba Amina ido wacce tun safe ta yo
sammako ta zo garin ita da Raihana da tuni ta kammala jarrabawa.
"Hakan mai yiwuwa ne kuwa Amina? Ke fa kin san komai
tsakanina da Maryam. Kina ganin yaranta za su karΙe ni?"
Baba Amina ta yi murmushi.
"Wannan fa duka mai sauki ne Maijidda, ai shi aure
nufin Allah ne. A baya daga ni har shi Yayan ba mu taΙa kawowa akwai ranar da
zance makamancin haka zai gifta tsakaninku ba. Kar ki ga na riga shi zuwa ki
zaci wani abu, kawai dai ya wakilta ni ne saboda ba ya son ya fara zuwa da
kansa a samu rashin goyon baya. Nidai ki cire tunanin wata Maryam da yaranta a
zuciyarki, Raihana ma ai Ιiyarta ce amma ba ki ga yanda take murna da wannan haΙin
ba. Maijidda ki sa a ranki rayuwar Ιan uwanki musulmi za ki taimakawa, ke din
mace tagari ce da muka yi amanna da tarbiyyarki da kyawawan Ιabi'unki, mun kuma
sani za ki riΖe Yaya da amana. Ba sai mun tsaya Ιata baki wurin labarin wacece
Maryam ba, kusan ma kin fi mu saninta akan kowa. Amincewarki kawai muke da
buΖata a yanzu. Don Allah kar ki tuna kowa ki daure wannan zuciyarki ta ki,
ki samarwa Yayana gurbi a cikinta."
Dariya Anti Maijidda ta yi.
"Amina kenan, shikenan, na ji saga gareki, sai ya zo
din. Allah ya zaΙa mana abin da ya fi alheri."
"Yeee Amin Anti Amaryarmu. Godiya godiya."
Suka juya gaba Ιaya, Raihana ce ta rungume Anti Maijidda ta
baya tana murna da wannan sambatun. Itama Ummita ta fito tana dariya, ashe akan
kunnuwansu aka yi komai.
"Ja'iran yara, dama laΙe kuka yi mana? Oh ni
Amina."
Anti Maijidda kuwa murmushi kawai take yi ba ta ce komai ba
duk rashin shirunta a magana.
Raihana ta zagayo ta zauna tana dariya.
"Ni dai Baba ba laΙe na yi maku ba. Ummita ce fa ta yi
baΖo shi ne muka fito tarbarsa."
Jin haka suka kara duban Ummita, ta sunkuyar da kai tana
murmushi a kunyace, ta shirya tsaf kuwa abinta cikin wata koriyar atamfa sai
mayafi ta yi kyau shar da ita.
"Ridwan din har ya iso?"
FaΙin Anti Maijidda, ta gyada kai tana murmushi.
"Ki je toh kar a bar shi da zaman jira."
Suka fice har Raihana tana cewa bari ta je sai ya ba ta
tukwuicin kwalliyar da ta yi mata. Suka bisu da kallo su na murmushi.
"Af wai ina Ahmad tun zuwana ban gan shi ba?"
"Yana gidan Ιanki (wato dan Anti Maijidda babba,
Bashir) a can ya kwana."
"Ai naji Yaya na cewa a karshen satin nan shi Ridwan
din zai turo ko? Shima dai Al'amin din mai neman auren diyarki (Raihana) a
satin nan zai zo a yi magana. Ba dogon lokaci za'a sanya ba, wata daya kawai
Yaya yace idan har ba su ne suka zo da wasu uzurirrikan ba."
Sosai Anti Maijidda ta ji dadi. Ta yi addu'a akan Allah ya
amince. Su Baba Amina da Raihana ba su suka bar garin ba sai yamma cike da
tsarabar da Anti Maijidda ta haΙa musu.
Bayan tafiyarsu ta yi waya da yan uwanta akan bukatar da
Baba Amina ta zo da ita, babu wanda ya kawo kushen abin sai ma fatan Allah ya
tabbatar da alheri.
***
Mami zaune a falon
aminiyarta tana kuka kishirΙan. Hajiya Lubna ko sai afkin girgiza Ζafafu take
yi. Can dai ta ja tsaki.
"Maryam kukan nan fa ba zai mana wani magani ba. Ni
yanzu kin kara dagula lissafina, da wannan auren na Daddyn Kabeer (mijinta) zan
ji, ko kuwa da wannan rigimar da ta Ιallo maki. Nifa a ganina kawai ki je ga
Babandi ki ba shi hakuri, ita kuwa Tasleem ki mayar da ita can kauye wajen Anna
ta haihu kafin wannan baragurbin labarin ya fashe a gari kowa ya ji
warinsa."
"Nayi tunanin haka Lubna, sai dai kuma Anna ta rantse
min muddin na turo mata tsatson Isuhu wajenta sai ta tsinemin. Kina gani yanzu
fama suke yi na yanda auren Jannat zai koma, daga zuwa raka Annar da ta yi sai
saΖon saki ta samu daga Baban Ζ΄an biyu. Dama danginsa a wuya suke da ita, yanzu
batun da nake maki fa har sun aura masa wata yar uwarsa. Wannan tashin hankalin
ma ni ya yimin yawa Lubna, ta ko'ina babu sauki, aikin Babandi ya kwaΙe, kissar
ma ta daina aiki. Ga Futuha cikin matsala, ga Ζassim da shaye-shaye. Na shiga
uku nikam." Sai ta kara fashewa da kuka, amincinsu babu yaudara, aminci ne
irin wanda hali ne ya zo daya tun farko aka kulla, sai Lubna itama ta ji hawaye
sun zubomata. Su dai masu wuni da yini cike da farin ciki, matsala ba wata aba
ce a wurinsu ba nan da nan da sun dau waya sun kira Babandi ko sun kulla wani
makircin shikenan suke magance ta, yau kuma su ne cikinta birjik amma babu wani
sauki. Ita dai idan Honarabul ya auri Hajiya Fareeda Mai Daham ta ta ta Ζare,
mace mai tarin dukiya da usuli mai kyau. Yar gidan Malamai da maza da yawa suke
kai mata hari, tana da bala'in nutsuwa da kamun kai uwa uba aji da girmama
mutane. A yanda ita ko ba ta kallon dangin Honarabul da gashi ai ta san rayuwa
dai ta jin dadi babu ita babu shi a gidannan.
"Ki bari Maryam, yanzu kin dai ji Babandi na kirashi a
gabanki ba ya gari ya je ganin gida, idan ya dawo sai muje mu same shi."
"Yanzu a tunaninki ba Ζarya yake yi ba?"
Hajiya Lubna ta girgiza kai.
"Kayya, bana tunanin haka ko kaΙan, kinsan ai ban ce
masa da ke zan zo ba, ban ma nunamasa muna tare ba ballanta ace don saboda ke
zai min Ζarya. Ki dai bari zamu je din, zan kuma tuntuΙi Hajiya Zainab batun
zuwa Kamaru da zamu yi, ya kamata muje a kwanannan"
Da wannan suka rarrashi juna Mami ta wuce gidanta.
***
Cikin satin aka sanya
ranar auren Raihana da Ummita lokaci guda, a sannan Ummita ta dawo Kano wurin
Baba Amina inda ta bar Ahmad a can gidan Anti Maijidda don yaron sosai ya yi
wayo ya saba da su. Tafiyar Ummitan sai ya kasance ko a jikinsa.
Suka yiwa gidan
Humaira tsinke, sun mata bazata domin ko kadan ba ta da labarin zuwansu. Zo ka
ga murna da farin ciki har da su hawaye a wajensu. An kwana biyu ba a ga juna
ba don Raihana ma sau daya ta taΙa leΖa mata ta kafa hujja da jarrabawa. Sun
sha hirar duniya tamkar kada su rabu, babu inda ba su taΙa ba. Har zancen auren
Abba da Anti Maijidda da ita Humaira ba ta da labari sai a lokacin, kwatanta
irin farin cikin da ta yi da ji ba zai misaltu ba.
Sai bayan sati da saka ranar su Raihana sannan Abba ya je
wajen Anti Maijidda kuma Alhamdulillah sun kara fahimtar juna. Kasancewar abu
na manya nan aka tsaida sati guda kacal domin daurin aure. Haka Abba ya dawo
gida zuciyarsa tamkar bai san wata abu mai suna bakin ciki ba saboda kyakkyawar
tarba da shimfidar fuskar da ya samu daga Anti Maijidda da iyayenta.
***
Mami duk abin da ake
ciki ba ta da labari, na sanya ranar Raihana kawai Abba ya fadi mata shima sai
bayan dawowarsa daga Bichin da ba ta san ya je ba.
Wani malolon abu ya tsaya a maΖoshinta.
"Yanzu Isuhu har a sanya ranar Ιiyata ka kasa faΙamin?
Ai ba Amina ce ta haifamin ita ba! Toh na rantse maka sai Raihana ta dawo
gidannan tunda dai ni ce uwarta babu banzar da ta haifamin ita!"
Ta fadi cike da bori tana jijjiga hancinnan duka ya buΙe
tsabar masifa. Abba ba ya tunanin wani hargaginta zai Ιata masa rai, shi fa har
ya soma jinsa a angon ma tun kan a Ιaura aurennan. Wani murmushi ma ya saki.
"Ba Amina ce ta haifi Raihana ba ke ce, amma kuma ni
Isuhu tunda har Raihana ta nuna ta fi ra'ayin zama a gidan yar uwata ba ki isa
ki juya ni ki sa na maido ta nan ba. Idan kin ga Raihana da Ummita a gidannan
toh ki sani aurensu ne ya gabato."
Ta wurga masa harara kamar idanunta za su tsinko su fado.
"Kai ka san wannan Isuhu. Ni dai nasan ni na raini
cikin Raihana na kuma haife aba ta, babu wanda ya isa ya yimin iko da ita. Mu
zuba mu gani!"
Tana kai wa nan ta yi gaba. Yassar da tun soma zancen nasu
yake durkushe gaban Abba sakamakon kiransa da ya yi su tattauna batun kasuwa ya
ji babu dadi ko kadan, wai yaushe Mami ta sauya ne? Ko dai dama haka take? A
yanzu rayuwa ta ladabtar da shi, ko kuma ace soyayyar da yake yiwa wata budurwa
da lokaci guda ta nuna ba ta kaunarsa, abu ne da bai taΙa faruwa gareshi ba.
Sanadin yarinyar ya nutsu ya kuma rame don tunani. Ya kara shiga cikin
hayyacinsa, ya bar dukkan wata fankama da karya da yake yi don koda ya soma
nunamata facakar kudi nunamasa ta yi ba su ne a gabanta ba.
"Kai ina magana ka yi shiru? Ina tunaninka ya
tafi?"
Da wannan ya ba tunane-tunanensa da mamakin yanda maganganun
Mami ba su yi wani tasiri sun Ιata wa Abban rai a wannan karon ba.
***
RANA BA TA ΖARYA...
Yan uwa da kuma abokan arziki ne suka shaida daurin auren
Hajiya Maijidda Bukhari da mijinta Alhaji Isuhu Mai Agogo a garin Bichi. A
ranar kuma Abba ya juyo inda aka tsaida kwanaki uku na zuwan Anti Maijidda
kamar yanda ta buΖata.
Ranar da ta kama na kawo kayan Ιakin Anti Maijidda wanda
Abba da kansa bada aka yi, cikin iko na Ubangiji a ranar Mami ta fice zuwa
gidan Babandi ita da Hajiya Lubna. Ita kuwa Tasleem ta kaΙa yawonta gidan
Futuha don a yanzu gaba daya komai na duniya ya yi mata Ζunci.
Baba Amina ta iso, aka sanya komai a Ιangaren Anna. Babban
falo ne sai Ιakuna biyu kowanne da bandaki a ciki sai kuwa kofar kicin da ke a
garΖame. Tun farkon ginin gidan dama Abba wuri biyu ya yi, Mami ba ta ko
firgita ba don a sannan tana ganin ko giyar wake Abban ya sha ba zai kara
gangancin yi mata kishiya ba. Karshe ma zuwan Anna sai wurin ya koma nata.
Koda aka kammala, Baba Amina ba ta bar gidan ba domin a
ranar ne Anti Maijidda za ta shigo Ιakinta. Har yamma tana kicin suna aikin
tarbar baΖi ita da Ladidi da ta ji labarin auren da Abba ya yi a bakin Baba
Amina. Sosai lamarin ya ba ta mamaki, tana kuma da tabbacin uwar Ιakinta ba ta
da masaniya. Ta sani dai akwai babbar matsala idan ta dawo gidan.
Toh hatta su Yassar da suka dawo daga kasuwa tare da Abba,
sai a lokacin Abban ke sanar da su. Ba su ce komai ba sai fatan alheri. Sun dai
kame bakinsu daga sanar da wani cikin yan uwansu bisa umarnin Abba akan shi da
kansa zai faΙawa Mamin. Abin dai bai musu dadi ba musamman jin wacce Abban ya
auro, matar da ba sa ga maciji tsakaninta da uwarsu.
***
A gidan Babandi kuwa,
Mami da Hajiya Lubna suna ta kai ruwa rana da shi inda ya ce shi sam daidai da
fuskar Mami ba ya kaunar gani a yanzu. Ya kara da faΙin.
"Idan har za ta mance alaΖar shekara da shekaru ta ci
mutuncina, ki faΙamin ta yadda ni kuma zan kasa Ιaukar fansa akan Ιiyarta? Ke
dai Hajiya Lubna ai kinsan irin baΖar wahalar aikin da na ci akan kishiyarta
mai rasuwa Fatima wanda a Ζarshe muka ci galaba kuma aka aika da ita lahira.
Amma duk wannan bai hana Hajiya Maryam runtse idanu ta zazzageni ba?"
Mami dai ta ma hakura da ban bakin ta yi shiru kawai, ranta
zafi yake don ita haushi ma yake bata, toh mutum dai tunda an ba shi hakuri ai
shikenan mene ne kuma na jan magana ta yi tsawo har yana tone-tone?
"Hakuri dai za ka yi Babandi tunda mai afkuwa ya riga
da ya afku sai komai ya shige. Ita kanta Hajiya Maryam yanzu ta fahimci komai
na rayuwarta ba zai tafi daidai ba sai da sanya hannunka (Wa'iyazubillah),
yanzu dai a sulhunta ka yi mana maganin kokenmu."
Ya yi wata bahaguwar dariya.
"Shikenan, yanzu naji komai ya wuce. Ku fadi buΖatunku
don sauri nake zan shiga kasuwa, gobe sammakon tafiya Kamaru zan yi a ta mota,
akwai wani sirri da zan je karΙowa wurin kakana."
Ganin haka Hajiya Lubna ta gyara zama ta karanto mishi nata
damuwar, fin Ζarfin da surukarta matar Ιanta Kabir ke kokarin nunamata a kansa
kai kace ita ta haifamata shi, taΖamarta kuma don ubanta ya fi Kabir din da ma
uban Kabir din kudi, sai kuwa batun auren da mijinta ya yi ta kara da fadin.
"Ni wallahi ko irin aikin da aka yiwa Fatima ne shi
nake buΖatar ka yi mata matuΖar za a dace."
"Ai inaa, Hajjaju ba za ki iya irin kissar da Hajiya
Maryam ta yi ba. Hatta da ni ina yabawa wannan kokarin da ta yi na tsawon
shekarun nan. Ke kuwa kina da saurin fushi da zuciya, ba za ki Ιoye abin da ke
ranki ba irinta. Ki dai bar komai a hannuna. Ke kuma Hajiya faΙi muji
naki."
Mami ta dan muskuta ta soma magana.
"Babandi ka riga da ka san nawa. Na tsani na budi idanu
na ga Humaira cikin gidan daula alhalin nawa yaran su na terere. So nake ko
haukata ta ne ayi idan na ba za ta rabu da tsinannen can, to don Allah a yi
abin da itama ba ta mori rayuwar ba. Sai
abu na gaba, Alhaji fa kawai kallona yake yana kuma zaune da ni ne amma bai
yarda da ni ba kwata kwata, yana zargina sosai. Ina buΖatar na mallakeshi ko ta
wane hali, wallahi wannan karon na shirya Babandi, ko mene zan iya aikatawa
muddin zan mallaki Abban yara. Sai kuma na Ζarshe, ka taimakamin da wani aiki
da zai yi sanadin cikin Tasleem, kar ta haifarmin abin da zai jawo na ji
kun..."
"Aa, a'a Hajiya Maryam, kar ma ki fara! Koda wasa kar a
yi gangancin taΙa halittar dake cikin Tasleem, ina son abina. Ta haifa ta
kawomin, na samu gagarumin albishir daga cewa wannan abin da za ta haifa shi
zai Ζara daukaka darajata kuma zan yi mahaukacin arziΖi. Ki bar ta ta
haifarmin, idan da rabo ma bayan ta haihu sai ki ga na aure ta mun rayu cikin
daula. Sauran maganganun naki kuma ki barmin wuka da nama. Komai zai tafi
daidai da zarar na dawo. Na fadamaku wani sirri zan karΙo, wannan sirrin kuwa
na kai shekaru takwas ina nemansa, sai yanzu na samu Kakana ya aminta zai bani,
na rantse maku ba mazajenku ba, ku hatta da abokansu da ma danginsu sai kun
dinga yi musu kwarjini kun Ζara zama abin so a wajensu."
Suka ji wani sanyi na ratsa zuΖatansu, suka dubi juna da
murmushi a saman fuskokinsu.
"Lallai kuwa idan har wannan aiki ya kammalu na maka
alkawarin tafkeken gidan da ya fi wannan Babandi."
Hajiya Lubna ta furta da wani zumudi don har ta hasko tana
juya Baban Kabir da ma mutan gidan. Ita kuwa Mami ta tuna da akwai sauran zance
a bakinta don haka ta tari numfashin Babandi dake shirin magana.
"Toh amma ya zancen Maijidda da ka taΙa yimin? Kar ka
manta sanadinsa muka samu matsala, nidai ka taimaka idan wani abin ka hango
tsakaninta da Alhaji ka sanar da ni a yiwa abin tufka tun yanzu."
Babandi ya girgiza kai.
"Aa Hajiya Maryam, ai ko wancan karon ban ce maki aure
ba. Ke ce dai guguwar kishi ta kwashe ki kika aikata abin da kika yi. Na dai ce
ki kula don kuwa na hangi akwai wani abu da shi mijinnaki zai iya samu
sanadinta, kodai ta aura masa diyarta ko kuwa dai ta nemo masa matar aure.
Nidai ban ga wani aure tsakaninsu ba."
Mami duk da ta ji tashin hankali na cewa wai Abba zai iya
kara aure bayan ita kuma ta hannun Anti Maijidda hakan bai san ya ta firgita
kamar a farko da tunaninta ya bata cewa ai Maijiddar za'a aura ba.
"Kar ka damu Babandi, don dai ta wata diyar Maijidda ko
wata can abu ne mai sauki wanda na tabbata ba zai gagare mu ba. Dama ita
Maijiddar ce ba na kaunarta har abada, na tsane ta fiye da irin tsanar da ta
yimin kuma har da ganin ba ta da tsoro shiyasa amma ko wace ce zan cin ubanta
matukar ta rabi inuwar mijina."
Suka dara gaba daya yayinda Babandi ke yiwa Mamin kirari na
musamman. Sun Ιan jima suna tattaunawa akan Tasleem inda Babandi ya Ζara
tabbatar mata bai aminta da zubar da ciki ba, karshe ta yanke tura Tasleem din
can Agadez wajen Anna ko ta Ζi ko ta so kuwa. Babandi dai ko a jikinsa, shi dai
yace cikin ne bai ga wanda ya isa ya zubar ba.
***
Tasleem ta yiwa
Futuha kallon tsaf, gaba daya ta rame ta Ιan yi duhu don dai ita din farar
gaske ce ma da ba ta san yanda za ta ganta ba.
"Wai Futuha ke kukan dadi ma kike yi. Da aurenki da
mutuncinki, kawai ke dai sauyin yanayi da Yakubu ya yi maki da kuma auren cin
amanar da ya yi su kadai ne matsalolinki. Ni kuwa me zan ce? Na rabu da mijin
dake sona tsakani da Allah saboda hangen dala, na zo nayi biyu babu karshe ma
sai ga ni da cikin Boka Babandi a jikina. Wallahi Futuha ina ji kamar na kashe
kaina ko na huta da wannan azababbiyar rayuwar da nake yi marar Ζ΄anci."
Futuha ta share nata hawayen, tabbas gaskiya Tasleem ta
fadi, duk lalacewar nata rayuwar ai aure ya mata sutura. Ita ko ga babu aure ga
kuma ciki wanda tun ma kafin ta kai ga cika iddarta ta same shi.
"Hum, na sani Tasleem, na san kin fi ni. Amma ba kya
ganin irin yaudarar da Yakubu ya yimin? Yanzu fa zancen da nake maki har sabon
bidiyo Yar Snow ta dora a shafinta na Tiktok wai ya shirya mata haΙaΙΙen
birthday party kuma har tana ba shi kyakkyawan albishir na cewar tana da juna
biyu amma wallahi mutumin nan ko a fuska bai nuna Ιacin rai ba sai ma rungumota
da ya yi jamaa na musu tafi. Ni shegen ya hana ni daukar ciki ya yimin dadin
baki, nayi zaton haihuwar ce ba ya so, kenan da ni ce ba ya kauna? Mutumin nan
idan ya shigo gidannan tamkar akan Ζaya yake, ga raba dare yana hira da ita ta
whatsapp, hum."
Ta kasa cigaba da magana sai kawai ta hau sharar kwalla,
Tasleem ta dan bai gidan da kallo.
"Toh ba dole ya dinga jinsa a kan Ζaya ba, duk fa yanda
na kai ga rashin tsafta wallahi kin fi ni kazanta Futuha. Ji don Allah wannan
farantin gar ya bushe ban san tun yaushe kike ajiyarsa anan ba. Shikenan don
Ζ΄ar aiki ta bar zuwa sai ki zauna ko ya ya ba za ki Ιan gwada tattara gida ba?
Zanin gadonki kuwa inaga ya fi wata a shimfide, ai ina ji tun kafin Anti Jannat
ta wuce Agadez."
Tsaki Futuha ta dan ja.
"Naji zan gyara. Zan sa a bincikamin wata Ζ΄ar
aikin."
"Kuma kina da kudin biyanta?"
Shi ne tambayar da ta watsa mata kawai. Sai ta kara yin gum,
ina ta ga kudin? Dama ai da bazar Yakubu take rawa amma yanzu ya maida ta bola,
hatta da na cefane sai ya ga dama yake ba ta abin kirki. Haka suka yi ta tufka
da warwararsu, suka zage Raihana akan yanda ta guje su kafin kuma su hau
jajantawa kansu na irin daular da Humaira ke ciki wanda a tunaninsu su suka fi
cancantarsa ba ita ba. Wannan shi ya yi sanadin da Tasleem ba ta bar gidan ba
sai magriba bayan Futuha ta dafamusu Indomie sun ci. Sai da ta yi dakyar ma ta
lallaΙa Tasleem din ta taimaka suka dan rage Ζazantar gidan da sunan ranar
girkin Futuhar ne Yakubun zai zo. Ba ta damu da yin girki da shi ba domin ba ci
yake ba, watara ya zo da filas na abincin da Ζ³ar Snow ta girka masa wasu
lokutan kuma Takeaway.
***
Ta dawo gidanta cike
da kwarin gwuiwa da kuma wata irin nutsuwar da ba ta taΙa tsintar kanta ciki ba
tun bayan cafke Wizzy. Hankalinta ya kai ga wata baΖuwar mota a ajiye, ta Ιan
bita da kallo sai kuma ta yi tunanin watakila cikin abokan Yassar ne wani ya
kawo mishi ziyara don haka ta karasa shigewa ciki inda su Waleed da Muhsin suka
tarbe ta da murnar oyoyo. Mami ta yi murmushi tana Ιan rungumesu. Yau daban
take jinta.
"Oyoyo Ζ΄aΖ΄an Mami, ku bar ni haka toh kar ku kayar da
ni."
"Mami! Mami! An sanya gado mai kyau da kujera da kafet
har da labule a dakin Anna."
Jin maganar Muhsin ta yi kamar saukar aradu a tsakar kanta.
Ta ji faduwar gaba. Ta dube shi.
"Kai Muhsin, bana son karya wane irin gyara kuma?"
"Lah, Allah kuwa Mami dagaske ne. Baba Amina ma tana
can da wasu mutane suna cin abinci."
Ai sai ta ji kirjinta ya buga da karfi, Amina dai? Tare da
wa toh? Dakyar ta iya jan Ζafarta ta nufi tsohon Ιangaren Anna a baya,
kunnuwanta na dauko mata muryar Waleed na ihun fadin "Amarya ce wai dakin
Amarya ce inji Baba Amina."
Ba ta iya juyowa ba dai wani sabon himma da ta ji da wani ja
da ta ji tamkar ana mata da lantarki ta daΙa sauri har sai da ta sadu da sashin
Anna. Wani Ζamshi ya soma bugar hancinta na turaren wuta mai Ιankaran sanyinda
dadi, babu wacce tuna da ta ji Ζamshin face Fatima sai ko Jamila uwa ga Ummita
waΙanda ba su rabo da turarukan wuta haka.
Ta bankaΙa labulen ta shiga, idanunta kuwa suka soma shiga
na Amarya Hajiya Maijidda Mrs Isuhu Maiagogo. Ta yi kyau iya kyau cikin wani
leshi uban ubansu kalar kore. An mishi aiki wanda ya yi kyau ya fiddo ta,
fuskarta kuwa kwalliya ce sosai da ta fiddo fuskarta kai kace wata Ζ΄ar budurwa
ce mai Ζananan shekaru. Koda dai dama Maijidda idan ka ganta ka kuma ga yaranta
ba za ka ce ita ta haife su ba don jikinta bai nuna ba sai dai abin da ba za'a
rasa na girma ba wanda ya zama dole.
"Maijidda! Uban
me kike yi a gidana?!"
Ta fadi cikin mugun kaduwa da fita hayyaci don Ζafafunta har
kakkarwa suke yi. Baba Amina da yan uwan Anti Maijidda hudu dake zaune suka
mike tsaye ganin ikon Allah, dama sun shiryawa hakan sun san za ta kaya tunda
dai Abban bai sanar da ita komai ba.
Wani murmushi Anti Maijidda ta yi.
"Idan kin nutsu kin kwantar da hankalinki, shi wanda ya
ajiyeki ya kuma ajiyeni a yanzu, zai sanar dake."
"Kina nufin ki cemin Yusuf ne ya ajiyeki? Aurarki ya yi
ko kuwa me?"
Mami ke wannan tambayar domin jinta ta yi tamkar an zare
mata dukkan wani laka na jiki. So take Maijidda ta ce a'a, duk da iskar fankar
dake kaΙawa bai hana gumi lulluΙe ta ba.
Wayar Mamin ce ta yi Ζara, ba ta ko damu ba ballantana ta
daga, Abba ne domin Baba Amina ta mishi text cewar ga Mamin a sashin Maijidda.
Har ya katse ba ta Ιaga ba, ita kuwa Maijidda dariya ta yi kawai ta wuce zuwa
daki.
"Ke Maijidda! Amina ku fadamin meke faruwa?! Yusuf
wannan karuwar ya aura ko kuwa me?!!"
"Maryam!"
Suka juya gaba daya ga Abba dake tsaye ya shigo, dama tunda
ya ga ba ta amsa wayarsa ya san wata taΙargazar za ta yi.
Ta juya ta watsa masa wani kallo kamar idanunta za su faΙo,
fuskarnan ta da a Ιaure, ba ya so su raba halin a gaban baΖi don haka ya yi
mata nuni fa hanyar waje.
"Muje falona, ko me ake ciki zan sanar da ke."
Ta yi Ιan jim kawai har lokacin ba ta Ιauke idanu a kansa
ba. Sai da ya Ζara maimaitawa kafin ta kauda kai ta bi falon da kallon tsaf
sannan ta kalli Baba Amina dakyau kallon zan dawo kanki kafin ta wurgawa sauran
matan harara ta yi gaba.
***
"Kin je za ki
tayar da hankalin gida kin manta da yaranki, kefa ba yarinya ba ce."
Abba ya fadi yana cin magani bayan shigarsu Ιakin, ita kuwa
Mami tsaye ta yi masa a kai, hannunta a saman Ζugu ta Ιan juya kai idanunta a
rufe sannan ta bude su.
"Kaga Yusuf, idan ma tarwatsa hankali zan yi wannan bai
shafeni ba, ka fito a mutum sak! Ka fadamin dalilin wannan gyara na munafunci,
wanda ba a tashi yinsa ba sai bayan ba na nan, kuma ka sanar da ni zaman da
waccan annobar ke yi a cikin gidana!"
Abba ya ji zafin maganganunta, kai tsaye yana kallonta ya
amsa.
"Zaman aure take yi kamar ke. Auro ta nayi, matata
ce!"
Ai da jin haka sai ga Mami ta daka wani wawan tsalle ta
shaΖe wuyan rigar Abba gami da sakin wani irin kururuwa tana kiran wayyo!!!
"Ba ka isa ba! Wallahi ba ka isa ba ka yi kaΙan! Ni za
ka wulaΖanta? Ni za ka ci ma mutunci? Ζan iska Ιan tasha! Yusuf na fika iya
tashanci! Daga kai har Maijidda kashe ku zan yi! Munafukan banza mu...!"
Wani wawan mari Abba ya Ιauketa da shi kafin ya ΙanΙareta
daga wuyansa ya hankaΙa ta. Ta kuma yunΖurowa daidai da shigowar Baba Amina a
rude da ma su Yassar wadanda ke zaman jiran wannan lokaci da Maminsu za ta san
da batun auren Abbansu, sun sani dama abin ba zai kyau ba.
Wannan karon ba ta yi gigin riΖe wuya rigarsa ba sai ihu da
magana cikin Ζarfi da ta cigaba da yi.
"Na fada na kara, kai da Maijidda munafukai ne! Ni za
ka yaudara? Dama ai tunda naga take-taken wannan Ζaramar yar barikin na san
cewa sai ta yi yanda ta yi ta shigomin gida! Ta zo ga ka nan ta ga idan wata
uwar kake tsinanamin a gado da ma
tukunyar girkina! Wayyo ni Maryam na shiga uku na lalace! Maijidda? Maijidda
baΖar karuwa?!"
Sai ta tafi a guje ta rarumi tv dake saman tv stand za ta
kai shi kasa da sauri Yassar da Dawud suka riΖe ta kuwa haΙa da su da shi din
ta hankaΙa suka kife. Wani mugun Ζarfi ne ya zo wa Mamin na kishin fita hayyaci
da hauka.
Abba gaba daya idanunsa sun kaΙa tsabar baΖin ciki da wannan
abin tirr da Mamin ke yi a gaban yaranta. Bai dauka haukarta ya kai nan ba. Ga
zaninta kuwa ya kunce yana terere a tsakiyar falon don ma Allah ya taimaka tana
sa dogon wando a Ζasan kayanta.
Zagi ta uwa ta uba haka ta dinga kwaranyowa Abba da Maijida
har ma da Baba Amina dake tsaye. An kira ta da munafukar da ta Ζulla komai, har
da gorin suturu da ma tallafin abinci da tayi mata a baya kafin mijinta ya samu
arziΖin kansa.
Dakyar Yassar da Dawud suka fitar da Mami suka sada ta da
dakinta, ta tsine musu ya fi cikin kwando akan idan ba su rabu da ita ba za ta Ιaga
musu nono. Sai da suka rufe ta sannan suka hau maida numfashi, Dawud goshinsa
har ya kumbure saboda wani duka da ta kai mishi da gwangwanin maganin feshi na
sauro dake ajiye saman wani Ζaramin katako dake jikin bango hanyar dakin Abban.
Daidai lokacin Tasleem ta shigo gidan goye da Ιiyarta Anisa
dake bacci. Lokacin ana kiraye-kirayen sallar Magriba. Muhsin da Waleed kuwa
sun tsaya cirko-cirko a tsorace sai kuka suke yi ganin Maminsu tana wasu
abubuwan da ba zasu ce gashinan ba. Abin dai bai kai hankulansu su dauka ba.
Kirjin Tasleem na bugu da sauri-sauri ta ke duban su Yassar
da kuma Mami dake bugun Ζofa tana tsinuwa garesu akan su buΙe mata yau sai ta
kashe Abba da Maijidda.
"Yaya Yassar meke faruwa? Anyi wani abu?"
"Aure Abba ya yi, ya auro Aunt dinnan ta Ummita shi ne
fa."
Zaro idanu Tasleem ta yi waje.
"Anti Maijidda? Kut! Abba wannan ai cin amanar Mami ya
yi? Duk irin yanda suke takun saΖa? Ya mance da wannan?!"
"Tasleem buΙemin kofa wallahi ko na haΙa har ke na
tsinewa na kwashemuku albarka!"
Suka tsinci muryar Mami wannan karon ma har da kuka ta kara
da fadin.
"Ku ka bari waccan karuwar ta shiga dakin Abbanku sai
na tsinemuku. Shegu wadanda ba su kishin uwarsu! Ku budemin Ζofa na je na kashe
su kamar yanda na kashe Sani da Jamila!"
A mugun firgice suka dubi juna, Tasleem wacce ta jima da
sanin wannan Ιanyen aikin da uwarta ta yi sai ta yi saurin duba hanya ko akwai
wani bayan su da ya ji. Yassar da Dawud kuwa suka yi saurin buΙe Ζofar.
"Mami, kika ce me? Su wa kika ce kin kashe?"
Ta banka masa harara.
"Uwarka da ubanka na kashe! Matsa ku bani hanya!"
Ta hankaΙe su za ta fice, Tasleem ta tari hanya.
"Mami ki yiwa girman Allah kar ki je yanzu. Ki bari sai
dare ya ratsa sai muke mu kashe su. Yanzu idan kika je za'a kama ki!"
Mamin ta yi shiru jikinta sai mazari yake tana tsuma, ita fa
ba ta gane komai, Maijidda da Yusuf kawai take so ta ga sun bar mata sararin
duniyar. Tasleem ganin kamar ta dan nutsu tana sauraronta dai ta cigaba da yi
mata kulla kulla na Ζarya duka dai don ta samu ta nutsu, kawai Mamin sai ta
dora hannu a kanta. Ita ba za ta ce me take ji ba, ashe dai a can baya kishin
banza ta yi wannan na yanzun shi ne ainahin kishi?
Sai kuma ta juya ta shige Ιakinta tana kururuwar kuka mai
sauti. Yassar da Dawud dai sun yi jigum don sun ji abin da ya girmi kunnuwansu
sai kowannensu ya kasa cewa komai suka soma taku domin zuwa gabatar da sallar Magriba wanda
tuni har wasu masallatan sun idar. Tasleem da sauri ta dakatar da Dawud.
Takarda ta yaga a littafin da Muhsin ya barbaza yana aikin makaranta sai biro
da ta gani a saman tv, sunan allura ta rubutawa Dawud din ta ba sa.
"Ka taho da shi don Allah, a chemist din Tj, zai ba ka
idan kace inji ni, na Mami ne."
Ya karΙa ba musu ya tura cikin aljihu ya fice, ita kuwa tana
hawaye ta ja su Muhsin dake faman kuka zuwa dakinta. Yau dai idan har ba
allurar baccin aka yiwa Mami ba akwai babbar matsala a gidan.
***
Kallonta kawai yake yi tun daga sama har Ζasa cikin shigarta
na Ζaramar riga da wando iya Ζauri yana buga murmushi lokaci guda yana jefa
gurgurun dake ajiye saman centertable a baki. Ita kuwa Humaira ta haΙe girar
sama da ta Ζasa ta cika ta yi fum yayinda kumatunta suka kumburo. Sanadin
wannan fushin bai wuce na amsa wayar abokiyar aikinsa da ya yi ba har yana
dariya. Shi kuwa wannan kishi na Humaira masifar burgeshi yake, ba da son ransa
yake motsa mata shi ba, kawai dai yana Ζara tabbatarwa kansa da irin son da
take masa yanzu ya shallake tunaninsa.
Ita kuwa Humaira ganin da ta yi ya maida ta kamar ma
wata cartoon bai dauki lamarin da muhimmanci ba don haka sai ta miΖe fuu za ta
wuce zuwa Ιaki, ya sa hannu ya riΖo nata hannun, ta juyo ta dube shi, shima ya
narkar da nasa kwayoyin idanun cikin nata kafin ya fisgota ta faΙo saman
kafafunsa.
"Allah ya huci zuciyarki, kinji?"
Ta kauda kai tana huci ba ta ce uffan ba. Fadeel ya sanya
hannunsa saman haΙarta ya juyo da fuskarta suna kallon juna. Ta runtse idanu
gami da tsuke baki ita a dole ya mata laifi. Murmushi ya yi ya dubi leΙΙan
kafin ya sa yatsa ya bi samansu.
"Please bana son fushinki. Ki yi hakuri kaina a Ζasa.
Yanzu ke a tunaninki wannan kirjinnawa akwai gurbin wata bayan ke?"
Ta Ιan ji sanyin kalamansa, ta buΙe idanun tana duban
hannunta da ya Ιora saman kirjinsa sai kuma ta dubeshi tana Ιan harararsa.
"Toh naji amma ni meyasa ka ke yi mata dariya
haka? Har fa nan sai da ya lotsa."
Ta faΙi tana kai yatsa saitin kumatunsa gami da dannawa da
Ζarfi. Ya Ιan saki Ζara yana riΖe yatsun gami da sumbata.
"Boddo wannan da biyu fa."
Ta yi murmushi. Ya riΖota sosai.
"Idan na rantse za ki yarda?"
Ta girgiza kai.
"Bana buΖatar sai ka rantse, ban taΙa kama ka da laifin
Ζarya ba, na kuma sani ba da gangan ka yi ba. Amma ai ni kadai ya fi cancanta a
yiwa ko? Ba wata Jennifer ba."
Ta Ζarashe da turo baki. Ya sumbaci kuncinta.
"Naji na karΙi laifina, a yimin gafara." Ya
Ζarashe yana mai kai hannayensa dukkan inda kwakwalwarsa ta ayyana masa.
Lamarin da ya fi karfin daukar kwakwalwa da zuciyar Humaira har sai da ta shiga
mayar da martani kafin ta tureshi ta miΖe tsaye tana dariya dalilin wayarsa da
ta yi Ζara. Ya shafi sumarsa gami da bin ta da kallo wanda babu wani mahaluΖi
da ke ganinsa a wannan yanayin idan ba ita ba. Wayar ta miΖa masa ganin sunan
Alhajinsa a jiki. Babu shiri ya yi kokari wurin saita kansa gani da daukar
gorar ruwa ya kwankwaΙa sannan ya bi kiran Alhaji don tuni har ya katse. Ita
kuwa ta dauki gurgurun da yake ci ta zauna can gefe tana ci hankalinta kwance.
Ba ta yi aune ba sai ji ta yi ya sunkuce ta har gurgurun na zubewa tayi dariya
bai tsaya a ko'ina ba sai Ιakinsu.
Rayuwar tasu gwanin sha'awa, kusan basu da wata matsala ko
damuwa. Sai da ya nutsa yake sanar da ita haihuwar da Hannatu ta yi, an samu Ιa
namiji. Ta kuwa har murna za ta je Yola kafin bikin su Raihana ta dawo. Ya ji
ta amma bai yi na'am ba, shi dai ya sani ba zai iya jure ta yi masa nisa koda
kuwa na kwana Ιaya ba ne balle wasu kwanaki.
***
Firgigit ta tashi
daga baccin dolen da Tasleem ta sanya ta. Ta hau murza idanu gami da duban
gari, garin ya waye tarr, ta mike a razane ta buΙe window. Rana ce sosai, ta
dubi lokacin ta ha Ζarfe tara da rabi na safe. Abba da Maijidda ta tuna ba ta
ko yi tunanin wata aba wai sallah ba, ta yi wuf ta fice ba ta bi koda ta kan
wayarta dake faman ruri ba.
A falon ta iske Tasleem da su Yassar a zaune suna
tattaunawa, Futuha itama tana nan ta zo dalilin labarin bazata na auren Abba da
ya same ta daga bakin Tasleem a waya. Suna ganin Mamin gaba daya suka miΖe
tsaye.
Ta banka musu uwar harara. Ta dubi Tasleem.
"Don ubanki ni za ki yaudara ki yimin allurar bacci? Ni
da na haifeki da ke za'a haΙa baki wajen cutar da ni? Kuna ji kuna ganin abin
da ubanku ya yimin ko?! Ya auri wata banzar karuwa yau har ya tare a Ιakinta
amma ku kasa Ιaukarmin mataki? Kai yau nidai Maryam na haifi Ζ΄an iskan yara
tsinannu!"
"Haba Mami! Haba don Allah, ki bar tsine mana hakanan.
Idan fa muka lalace ke ce za ki soma kuka kafin wani ya yi. Aure ai Ζaddarar
Ubangiji ne, ya muka iya tunda mai afkuwa ta afku?"
Yassar ke wannan zantukan don shi ya gama kai wa bango, ya
gaji da wannan tsine-tsinen da Mamin ke musu, ba kuma ya so ta je gaban su
Abba ta yi Ιaran Ιaramar da za ta tona
asirin kanta ta jaza musu wani sabon bala'i don sun riga da sun gama jin
labarin duk abin da ta aikata a bakin Tasleem da suka ga alamar ta san wani
abun.
"Yimin shiru! Shashashan wofi kawai da ba ya kishin
uwarsa mahaifiya! Wallahi da ace ba a gida na haifeka ba Yassar da yau zan ce
kai din shege ne ba jinina ba!"
"Ya isheki Maryam!"
Suka dubi mai magana, Abba ne wanda ya shigo tare da Anti
Maijidda don ta nace akan lallai ya kamata Abban ya hada su ya kuma ba Mami
hakurin rashin sanar da ita, duk ta fadi ne don a samu maslaha a zauna lafiya
wanda ba ta da tabbas a kai. Ta ci ado cikin atamfarta Holland mai golden da Ιan
ratsin ja, ta yafa mayafi ja a kafada sai baza Ζamshi take hakanan shima Abban
da ya yi shirin fita aiki. Ina wuta Mami ta tsoma wadannan bayin Allahn biyu?
Haka ta ji a zuciyarta, sai ga wasu zafafan hawayen baΖin ciki wanda ba ta
shirya musu ba sun zubo saman kuncinta. Kai Yusuf an yi dattijon banza, wannan
cin amana da ya yi mata ba ta jin an taΙa yi nata irinta ko zamanin budurcinta.
Shi kuwa Abba Ζarasowa ciki suka yi, ya dubi su Yassar
fuskarsa a Ιaure. Su kuwa gaba daya suka nutsu, Futuha dai kallon da take yiwa
kowane maza na marasa alΖawari da amana irin mijinta, a yau da ta ga Abban da
Anti Maijidda a tare, irin kallon da ta yi musu kenan. Ta ji mugun tsanar Anti
Maijidda a ruhinta, ta kasa ma kallon Abban tsabar taya Mami kishi. Wannan ai
yaudara ce, a cewarta.
"Me ya hanaku shirin fita kasuwa?"
Yassar ya Ιan sosa Ζeya.
"Yanzu zamu yi Abba. Dama saboda Mami.."
"Babu ruwanku a cikin wannan lamarin, ku fice ku
shirya. Shi kuma Ζassim yana ina?"
Suka rasa ta yanda za su ce da Abban akan Ζassim, ko kadan
bai kwana a gidan ba.
"Yassar an tashi lafiya?"
FaΙin Anti Maijidda tana dubansu dakyau. Mami ta watsa mata
banzan kallo. Shi kuwa Abba ya kara dubansu.
"Don ubanku ba ku iya ku gaishe da ita ba?"
Ba musu suka gaida ta ta amsa da murmushi, Futuha kuwa ta Ζi
ko magana sai Tasleem ce da gaisuwar don ita yanzu ta fi damuwa da matsalar
kanta akan ta wasu. Nata ma ya ishe ta.
Su Yassar suka fice har sannan Mami ta kasa koda tari, ta ma
rasa me za ta ce ga Abban na wannan rainin hankalin da yake yi a gabanta.
"Kai ku bar nan zan yi magana da mahaifiyarku."
Ba musu Tasleem ta dauki Anisa dake kwance saman kujera ita
ko Futuha ta rarumi jakar hannunta suka wuce daki.
"Maryam zauna ina son magana da ke."
Mami sai a lokacin ta saki wata dariya gami da tafa hannuwa.
Gashinta kamar na sabuwar mahaukaciya kasancewar babu kitso duk ya miΖe tsaye,
daga ita sai kayan jiya wanda har a sannan ba ta cire ba.
"Ni dai Yusuf? Ni Maryam ka ke son magana da ita? Ai
babu sauran abin da za ka cemin, azzalumi maci amana."
Ya maida duba ga Maijidda dake tsaye tana kallon ikon Allah.
"Kin gani ko? Ai na faΙamaki ba za ta saurare ni ba.
Muje kawai."
Cikin salon kissa Anti Maijidda ta ce.
"Ranka ya daΙe, daga ni har Maryam karkashin ikonka
muke. Idan ka zartar dole mu bi umarninka. Don Allah kada wannan shirmen da
take yi ya sanya ka fasa abin da ka zo da niyyarsa. Ke kuma Hajiya Maryam ina
ke ina faΙa da abin da Allah ya riga ya zartar? Ki samarwa zuciyarki nutsuwa mu
zama Ζoramu masu sanyi wajen hutawar mijinmu, mu samar da farin ciki a
rayuwarsa da na iyalinsa."
"Uban uwar farin ciki! Nace maki uban uwar farin ciki
Maijidda! Makirar banza makirar wofi! Kedai wallahi ban taΙa sanin baΖar mayya
ba ce sai yanzu. Dama ni nasan tun kafin ki kashe tsohon mijinki Babayo kike
bibiyar mijina. Ai da biyu kike zuwa gidan Jamila! Tsohuwar kwartuwa, ina maki
albishir da kin sanyo Ζafarki a gidan masifa da bala'i. Na rantse sai kin gwammace
zaman cikin kabarinki akan wannan gidan nawa da kike ciki. Mu zuba daga ke har
shi daidai nake da ku!"
Daga haka buguzum-buguzum ta nufi hanyar daki sai kuma ta
dawo a guje ta daka tsalle ta sanya hannu a bakinta kira take.
"Hooo kun ji kunya! Hoo kun ji kunya wallahi! Kwartayen
banza! Tirrr!"
Daga haka ta yi dakinta ta rufe Ζofa ta bar Maijidda da buΙe
baki shi kuma Abba na aikin girgiza kai kawai.
"YallaΙai, anya Ζalau take? Gaskiya ya kamata a kira
likita ya duba ta. Kada fa wannan abu ya zautar da ita."
Abba ya dan yi murmushi mai ciwo.
"Kar ki damu Jidda, Maryam ce, za ta aikata fin haka.
Ζan kiramin yarannaki ina son magana da su."
Ta amsa da toh sannan ta nufi dakin su Tasleem kanta tsaye.
Kunnuwanta ya yi mata kyakkyawan ji inda Tasleem ke ikrarin ba don cikin dake
jikinta ba tsaf za ta haΙa kaya ta shiga duniya. Wannan kalma ta ciki ya sanya
Maijidda cikin fargaba, ta kuwa shiga kai tsaye.
"Ciki Tasleem? Ciki kike da shi?"
A firgice Tasleem ta dube ta, ta kasa magana. Matar tun can
taba da mugun kwarjini da ba'a iya yi nata fitsara komai ΖanΖantarta balle kuma
yanzun da take matsayin amaryar babanta ta jiya jiya.
"Ba maganarki muke yi ba."
Futuha ta bata amsa a fusace don ji take inama ta yi mata
dukan tsiya. Daga dai wannan ba ta jin akwai wata tsiwar da za ta iya yi. Anti Maijidda ta
sauke ajiyar zuciya, tabbas ciki ne da Tasleem, sai yanzun da ta tsura mata
idanu ta hankalta. Ta bar zancen tunda yanzu ba hurumin yinsa bane.
"Ku fito mahaifinku na son ganinku."
"Toh." Tasleem ta amsa da sauri, ita yanzu gaba
daya jikinta ya yi sanyi, tsoronta kar ta sanar da Abba batun wannan ciki, ta
mayar da zumΙulelan hijabin da ya zama na yawonta na dole, sai ta ji dama ace
da ta shigo dakin ba ta cire ba. Futuha kuwa ta bi bayan Anti Maijidda da
harara da tsaki.
Koda suka je, sosai Abban ya ja kunnuwansu akan kar wacce ta
sake ta kawo raini ga Anti Maijidda, a yanzu uwa take a wurinsu. Ya kuma yi
musu nasiha na rayuwa irin yanda ya saba lokaci lokaci. A karshe ya dubi Futuha
ya tambayi mijinta, ta amsa da fadin yana lafiya amma ciki-ciki. Daga nan ya
mike suka kama hanyar falonsa da Anti Maijidda dake salon tafiya, ko me ta faΙawa
Abban har wata Ζ΄ar dariya ya yi wacce t Ζara shaΖawa Futuha. Sai kawai ta fashe
da kukan taya uwarta kishi.
"Wallahi Tasleem duka maza halinsu Ιaya."
Ita dai Tasleem ba ta ce komai ba, hankalinta a tashe yake
da wannan gamon da Anti Maijidda ta yi, ta ji gwara ta bi shawarar Antinta
Jannat ta koma wajensu a can Agadez ta haihu tun kafin Anti Maijidda ta tona
mata asiri. Ta yanke za ta sanar da Mami haka wannan dalilin yasa kamar an
tsikareta ta mike ta shiga dakin Mami. Sai dai me, waya ta ga Mami ta saki a
kasa tana kurma uban ihu, a guje Futuha ta shigo. Abba da Anti Majjidda wadanda
su ma ihun ya shiga kunnuwansu suka dawo da sauri zuwa dakinnata.
Mami a gigice take magana idanunta rufe.
"Shikenan! Shikenan Babandi ya mutu! Ya ce zai kawomin
sirrin da zan mallake Abbanku! Wayyo na shiga uku! Babandi ka dawo! Shikenan ka
mutu ba ka bani asirin ba! Ka bar min Ιiya da ciki! Wallahi ba za ta saΙu ba
sai an zubar da cikin nan!"
Ζakin ya yi tsit, Tasleem sai kokarin rufewa Mami baki take
yi amma ina! Kusan zaucewa za'a ce Mamin ta yi, sosai take bori tana tone-tone!
Futuha ta yi kan Mamin tana girgiza ta da karfi.
"Mami ya isa! Kiyi shiru haka don Allah!"
Abba kuwa baki ya saki yana ambaton sunan Allah, ya ji kamar
jiri na kokarin kayar da shi Allah ya taimaka Anti Maijidda dake bayansa ta yi
saurin riΖo shi.
A can falo kuwa Raihana da su Baba Amina dake doka sallama
suka ji hayaniya a dakin Mamin da gudu Raihana ta soma yin gaba Ummita na biye
da ita sai ko Baba Amina. Suka shiga daidai sadda Mami ta fincike daga rikon da
Futuha ta yi mata tana nuna Maijidda.
"Wallahi Maijidda sai na kasheki yanda nayi sanadin
mutuwar Sani da Jamila! Kema sai kin bar duniya! Kin yi kaΙan rayuwata ta Ζare
sanadinki!"
Nan fa idanun kowa ya kuma sauka ga Mamin, Anti Maijidda
Ζarfin da yunΖurin da take na ture Mamin sai ta ji gaba daya jikinta ya saki,
Maryam ta yi sanadin mutuwar Jamila Ζanwarta? Raihana kuwa ta toshe kunnuwanta
ta runtse idanu lokaci guda tana mai durΖushewa a Ζasa, so take ya kasance
mafarki ne ba gaskiya ba abinda kunnuwanta suka tsinkaya. Ummita kuwa ta ma
rasa halin da take ciki balle kuma Abba da ya hau furta kalmar innalillahi har
karshensa a fili da kuma Ζarfi.
"Ke ce kika
kashe Jamila?"
Anti Maijidda ta samu damar yaΖar harshenta da lebbanta
dakyar ta jefawa Mamin wannan tambayar idanunta gaba daya sun kaΙa, ba ma na
azabar shaΖar da Mamin tayi mata kawai ba, aa har da baΖin ciki da mugun
firgici na jin wannan sabon labarin. Mami ta Ζyakyace da dariya hakan yasa
jikinta Ιan saki da har Baba Amina ta yi nasarar ture ta daga jikin Anti
Maijidda.
"Eh ni ce nan na sanya kananzir na cinnawa gidan Sani
wuta don na tsane su, na tsani duk wani wanda ya fi mijina dukiya. Kuma
kwalliya ta biya kudin sabulu tunda yanzu da bazar Sani mijina Yusuf ke rawa!
Sai dai shima fa Yusuf akwai shegen maΖo da rashin sakin kudi."
Ta Ιan dakata tana riΖe Ζugu gaminda jujjuya kai, abubuwa
dai na wacce kwakwalwarta ta samu taΙuwa. Sai kuma ta Ζara tuntsirewa da dariya
har da tafi da shewa sannan ta dora tana nuni da Ummita.
"Wannan yasa na yanke shawara na sanya a sace wadannan
shegun yaran don na samu arzikin Yusuf gaba daya yarana su ci moriyarta. Haba!
Ya hana su sukuni, yara sai da kudi ai, amma dan banzan rowarsa abinka da wanda
ya tsinta a Ζasa ya sanya yarana shiga damuwa."
Ta hau juya kai tana buga kan da hannayenta.
"Ni, ni, ni Maryam na tsani damuwar yarana! Sai dai su
zauna a keΙe a yi ta zagin Yusuf, ni kuma nasan saboda rashin sakar musu dukiya
su yi facaka ne sai ka ce gadon ubansa!"
Ta zare ido tana kallon Abban gami da danna masa harara. Shi
dai hawaye kawai yake fitarwa hannunsa Ιaya dafe da kirjinsa dake zafi. Ashe
sauran mamaki da tsoratarwa na gaba sadda Mami ta dora daga inda ta tsaya bayan
ta je gaban Ummita ta tsaya.
"Ina Ιaya baΖar ashanar? Humaira! Ζiyar baΖar annobar
Fatima?! Na rantse da Allah na so na kasheta kamar yanda nasa Babandi yiwa
Fatima turen aljanu su aikata lahira! Kash! Babandi ka mutu ba a kan lokaci
ba (waiyazubillah), ka mutu ka bar Tasleem da cikinka, ga shi ban mallaki
Yusuf ba, ban kashe Humaira ba! Ke kuma Maijidda sai na sanya kin tsani Yusuf
fiye da tsanar da na jefa a zuciyar Fatima wanda har ta mutu ba ta son ganinsa.
Fiye da tsanar da Humaira ta soma gwadawa wancan la'anannen shegen! Kai Babandi
ba ka kyautamin ba!"
Sai ta kurma uban ihu. Baba Amina kuwa salati take yi ga
kuka sosai, Futuha da Tasleem su dinma kukan suke yi, sun tabbatar shikenan
Maminsu fa ta haukace kuma nata ya Ζare don irin wannan taΙargazar da ta yi ba
zai hana su maka ta gaban kuliya ba. Sai abin da AlΖali ya yanke. Abba dake
shirin zubewa suka yi saurin yin kansa har Raihana, aka fita gaba daya inda nan
Mami ta yi yunΖurin bin bayansu da hauka, wani hankaΙa da Anti Maijidda ta yi
mata ta kuma Ιauke fuskarta da mari hagu da dama ya ba su Futuha mamaki. Futuha
ta ji kamar ta shaΖo Anti Maijidda, ita dai duk lalacewar uwarta tana son
abarta, ita kuwa Tasleem Ζarfin kukanta ne ya Ζaru, ai koma mene Mamin ce ta ja
wa kanta kuma ta jaza musu. Akan idanunsu Anti Maijidda ta rufe Ιakin da
mukulli ta kuma riΖe mukullin a hannu ta bi bayan su Baba Amina sashin Abba.
Nan da nan Raihana ta fiddo waya ta kira lambar likitan Abban, amma bai shiga
ba, sai ta kira Fadeel wanda shi ne ya haΙa su da shi don idan irin haka
ta tashi ya zo har gida duba Abban.
Fadeel cikin sauri ya kira Likitan Abban, Dr Mansur, bai
kuma sanar da Humaira ba amma ya ga dacewar zuwanta duba jikin Abban wannan
dalilin ne ya sanya shi dakatar da fitar dda mota daga gate din gidansa da ya
yi niyya don har sun yi sallama. Ita kuwa lokacin har ta dauki waya don dama
jira take ya fita ta kira Raihana su dora daga inda suka tsaya jiya batun biki
da fidda anko. Ganin an bude Ζofar ya sanya ta Ιan tsorata ta juyo, ya dube ta
da murmushin yaΖe kuma a sanyaye.
"Lafiya? Mantuwa ka yi?"
Ta fadi tana binsa da kallon rashin gamsuwa da yanayinsa sai
ya yi kokari sosai wurin saita kansa.
"Lafiya Boddo, ji nayi ban kyauta ba har Abba ya yi
aure amma ba ki je ba. Oya shirya ki zo muje na kaiki."
Ta ji dadi sosai, sai da ta rungumeshi tana murna da godiya
kafin ta sake shi ta yi saurin ficewa zuwa dakinta. Dama ta yi wanka abinta ta
shirha cikin atamfa. Mayafi kawai ta dauko sai Ιoki take wannan yasa koda ta ga
Raihana ba ta biyo bayan kiranta ba bai dame ta ba. Shi kuwa Fadeel taimaka
mata ya yi da kashe fitilu da sauran kayan wuta na gidan bayan ta fita ya Ζulle
suka fice.
***
Alhamdulillah tun ma kafin zuwan Dakta Mansur, Abba ya Ιan
samu ya dawo hayyacinsa kawai dai sai gumi da ya dinga haΙawa akai-akai. Koda
Daktan ya iso, ya dai duba shi ya kuma ba shi taimakon da ya dace sannan ya
roΖi su kula da abin da zai sosa zuciyarsa daga nan ya tafi. Su na nan
jugum-jugum, ba ka jin komai sai sautin kuka da jan majina, ba daga su Anti
Maijiddan ba kuma ba ga su Ummita ba musamman ita da take jin wani irin yanayin
da ba ta taΙa riskar kanta cikinsa ba, inama sadda su Wizzy suka kama su sun
kashe ta tun a lokacin ta huta, da ba ta ga wannan ranar ba, da kunnuwanta ba
su jiyemata cewa wai Mamin da ta riΖa matsayin uwa ta rayu ΖarΖashin ikonta
tsawon shekaru ashirin da Ιoriya ita ce ta yi sanadin yanke mata farin cikin
rayuwa gaban uwa da uba ba.
"Raihana miΖon wayata."
Maganar Abba ta katse tunaninsu. Ba musu ta miΖe jikinta har
wani rawa yake yi tsabar tashin hankali da kuma kukan da ta ci, ga muryar Mami
dake ihu da kururuwar sai ta kashe su duka ya cika kunnuwansu. Ta dauko saman
kujera kusa carbi da kuma hankicif dinsa na shirin fita kasuwa ta miΖa masa.
Kai tsaye lambar Ridwan ya kira. Bayan sun gaisa ya ce ya zo gidansa yanzu yana
son ganinsa. Koda ya ajiye wayar sai kawai Futuha ta rarrafo gaban Abba cikin
kuka ta ce.
"Abba don Allah ka yi hakuri kar ka sa a kama Mami. Ku
yafemata wallahi sharrin shaiΙan ne."
Abba kallonta kawai ya yi sai ya girgiza kai yana murmushin
yaΖe. Wato dai Futuha ba za ta taΙa yin hankali ba.
"Abba kar ka saurareta, Mami ta cancanci a yi mata
kowane kalar hukunci. Abin da ta aikata ba ya buΖatar a yafemata. Da ace ana
sauya uwa wallahi yau ni Raihana sai na sauya."
Sai ta Ζara fashewa da kuka mai tsuma zuciya, tausayinta
sosai suka ji, Anti Maijidda ta rungumo ta jikinta tana rarrashi nata hawayen
na zuba. Shi dai Abba har sannan bai ce uffan ba.
Sallamar Humaira ne ya sanya suka dubi hanyar falon. Dama
ita kam kai tsaye Ιangaren Abbanta take soma shiga kafin ko'ina tun bayan
aurenta. Ganin yanayinsu ya sanya annurin da ta shigo da shi ya Ιauke Ιif. Ta
ji kirjinta na bugu, sai ta shigo falon da sanyayyar gwuiwa, ga dai Abbanta
zaune ballantana ta ce ko ciwonsa ne ya tashi. Ta durΖusa a gabansu ta kasa
cewa uffan sai dai ta bi wannan da kallo sannan ta koma kan wancan. Sautin
muryar Mami da ya karaΙe gidan ya shiga kunnuwanta, ihu take tana a bude mata
Ζofa sai ta raba kowa da numfashinsa. Anan ta gano inda matsalar take, wato
kishin auren da Abban ya yi ne ya ke cin Mami har ta tada hankalin mutan gidan.
Amma kuma kai, kamar dai wani abun ne babba ya faru. Yanda ta ga Ummita da
Raihana su na kuma sai itama ta ji nata zuciyar ta karye, ba ta son ganin babba
yana kuka kawai sai ta shiga nata hawayen.
"Don Allah meyafaru? Meke faruwa da Mami take ihu babu
wanda ya je taimakonta?"
Ummita ta girgiza kai.
"Wa zai je? Babu wanda zai je. Humaira Mami ta cuci
rayukanmu, ta kashemana iyayenmu saboda son zuciyarta. Mami ce silar mutuwar
iyayena a gobara, ta kuma yi silar mutuwar mahaifiyarki."
Sai Humaira ta Ιauke wuta, har wani jiri ta ji na son kama
ta.
"Wannan wace iriyar banzar magana ce kike yi?"
"Ba maganar banza ba ce Humaira. Dagaske Mami ta
aikata."
Fadin Raihana tana sheshssheka. Ita Humaira kasa magana ma
ta yi don Ζasan mararta har wani irin Ιaurewa ta yi ta riΖe shi tamau tana
salati da girgiza kai, hawayen kawai kwaranya suke yayinda kwakwalwar ke tuna
tarin alkhairan da Mami ta nuna mata a farkon zuwanta. Ashe duk na banza ne ita
ta kashe uwarta?
Zuwan Ridwan ne ya katse wannan zaman jimami, suka shigo
tare da Fadeel wanda ya ke tsaye jikin motarsa yana neman layin Humaira.
Su kansu sun sha jinin jikinsu na yadda suka tarar da mutan
gidan, zuwa lokacin Mami ta bar maganganun sun dai ji ta shiru. Fadeel gaba
daya hankalinsa na ga matarsa da ke cikin wani hali na tashin hankali, ga dai
Abba da alamun sauki a tattare da shi. Sai da aka gaisa sannan Abba ya korawa
Ridwan bayanin dukkan laifukan da Mami ta fadi da bakinta ta aikata su. Sun
girgiza matuΖa. Babu Ιata lokaci Ridwan ya yi waya don a zo a tafi da ita bisa
umarnin Abba, koda dama ko Abban bai ce a kama ta ba, ya halatta a hukunta a
shari'ance. Futuha da Tasleem sai faman kuka za'a tafi da Maminsu. Futuha har
da miΖewa ta yi falon Mami ta kira Mubarak hankali tashe ta sanar da shi dukkan
abin da ke faruwa, dama yana shirin tahowa Kanon. Ba ta tsaya anan ba sai da ta
kira su Yassar ta ce su dawo gida don Abba ya sa a kama Maminsu a tafi da ita.
Jim kaΙan kuwa sai ga jami'an tsaro mata da maza, koda aka
buΙe tana zaune tana ta surutai ita kaΙai sai kuma can ta kwashe da dariya. A
kan idanunsu aka sanya mata ankwa ta a fisge-fisge ita dai a bar ta ta kashe
Maijidda da Abba da su Humaira haka aka titsa Ζeyarta aka tafi. Humaira kuwa
wani sabon ciwo da ya murΙo mata sai ga ta a durΖushe a kasa. Da azama Fadeel
da ma jama'ar wurin suka yi kanta, kan kace me kuma sai ga jini ya Ιalle mata.
Aka kwashe ta zuwa asibiti, sai dai ina, tuni sun yi asarar cikin da ke jikinta
Ιan watanni biyu wanda ko Fadeel ba ta kai ga sanarwa ba a cewarta za ta ba shi
mamaki ne. Wannan zubewar cikin ya Ζara jefa Fadeel cikin tsananin damuwa, da
ace yasan ma tana da cikin ai ba zai ko bari ta zo gidan ba duba jikin Abba
ballantana wani abun ya taso. Sai kuma can ya ja istigfari tunawar fa ya yi ba
fa ikonsa bane.
Kan ka ce me, labarin kama Hajiya Maryam ya karaΙe unguwa da
ma wasu mutanen. Alhajin Fadeel da su Ibb da Daddynsa har gida suka zo
jajantawa Abba. Hakanan Ζ΄an uwan Abba haka aka dinga zuwa masu kuka nayi masu
zagin Mami su na yi. Sai ya kasance kamar yanzu ne aka yi rasuwar Jamila da
Sani da kuma Fatima.
Kawu takanas Humaira ta kira ta labartamasa komai, haka ya
biyo hanya shi da Hajjo zuwa Nijeriya don ya tabbatarwa kansa.
A dai sati da fitar wannan zance, babu inda bai shiga ba.
Yanar gizo, kafafen talabijin da gidajen rediyo duka.
Mubarak koda ya zo sai ya tarar da tashin hankali biyu, ga
na batun auren Ummita da Ridwan ga kuma na Mami. Yana kuma ji a jikinsa koda
babu Ridwan, abinda mahaifiyarsa ta aikata ga Ummita ba ya jin za ta aminta ta
auri jininta. Kai shi kam kunya ma yake ji na wannan abin da ya faru.
***
Yankewa Mamin hukunci ya Ζi yiwuwa dalilin taΙin kwakwalwar
da likita ya tabbatar bayan bincike cewa tana da shi, hakanan akantura ta zuwa
gidan mahaukata da zummar sai ta warke sannan za'a yanke mata hukunci.
Gidan gaba daya babu dadi, Abba koyaushe cikin hawaye da
kuma dana sanin auren Mami. Sai ko Ummita da ta Ζi kwantar da nata hankalin
kullum cikin kuka. Kasa zaman gidan ma ta yi ita da Raihana suka tattara suka
Ζara komawa wajen Baba Amina. Humaira kuwa daga asibiti ma bayan an sallame ta
Fadeel gidansa ya yi da ita inda Hajjo ta ke kula da ita da yi mata duk abin da
ya dace don jikinta ya dawo daidai gami da kwantarmata da hankali.
Abba sam ya Ζi a Ιaga bikin su Ummita, hakanan aka Ιaura
auren don ma na Raihana ne aka kusan fasawa dalilin Ζananun magana daga dangin
Al'ameen inda kai ya rarrabu, mahaifiyarsa da wasu a yayyunsa nata na cewa ba
zai auri jinin azzaluma Mami ba, wasu kuwa musamman mahaifinsa sun ce babu gudu
ba fashi tunda dai Ιiya ce wacce ta samu kyawawan shaidu daga jama'a to shi kam
ba zai fasa ba kuma Ιansa ya ji ya gani yana so. Haka aka Ιaura auren ba da son
ran mahaifiyarsa ba.
Sati guda kawai suka Ζara a gida sannan suka tare. Baba
Amina ta yi iyakar kokarinta wajen gyara su da ma yi musu dukkan abin da ya
dace. Ta kuma samu yaran sun Ιan dawo nutsuwarsu, hakanan Humaira ma an samu
kanta ta fawwalawa Ubangiji komai. Balle kuma da Anti Maijidda ta zama mai Ιebe
masa kewa ko kadan ba ta bari ta bar shi zaune jugum a halin tunani. Tasleem
dai Abba ko kallonta ba ya yi, gaba daya ta koma wata abar tausayi, ga Hamza ya
zo har gida ya karΙi Ιiyarsa Aneesa, Abba ko kadan bai hana shi ba sai ma
goyamishi baya da ya yi. Wannan ya Ζara sanyawa ta yiwa kanta karatun ta nutsu.
***
BAYAN SHEKARU BAKWAI...
Katafaren falon gidan Alhaji Yusuf Maiagogo cike yake da
yara dake faman hayaniya wanda ya cika kunnuwansa har ba ya jin abin da ake faΙi
a tashar CRTV da ya Ζurawa idanu. Shigowar matarsa Hajiya Maijidda ne ya sanya
shi saurin yin hamdala a fili bayan ya amsa sallamarta.
"Madallah da Ζ΄ar aljanna, kin shigo a daidai, tattara
jikokin nan naki su ficemin na ji halin da duniya take ciki."
Ta yi murmushi ta dube su. Ahmed wanda shi ne shugaban sanya
su tsalle da ihun Ιa ga Ummita, sai Ζ΄an
biyun Humaira, Fareeda da Fadeela, sai ko Afnan da Yazid Ζ΄aΖ΄an Raihana da kuma
Yusra Ιiyar Ummita, su shida amma kamar goma sha shida ne ajiye a falon.
"Ahmed, maza ja tawagarka ku je can Ζasa falona ga
Innarku Amina ta zo."
Jin haka yaran suka Ιunguma da ihunsu da komai wanda ya fi
na baya zuwa babban falon Hajiya Maijidda dake Ζasa. Idan ka ga gidan na Abba a
yanzu ba za ka ce shi ne aka taΙa rayuwa a cikinsa can baya ba, babu wani abu
da ba'a sauya tsarinsa a ciki ba. Ta karasa ta zauna, daidai lokacin da mai
labaran ya soma magana akan Hajiya Maryam, matar da shekaru bakwai a baya aka
fasa yanke nata hukunci sanadin hauka.
"Cikin iko na Ubangiji, ta samu lafiya ta warke ras
bisa tabbacin da aka samu daga wurin kwararren likitan kwakwalwa Dakta Yusha'u
Rano. Sai dai kuma ba anan gizo ke saΖar ba..."
Abba ya katse yana mai jin wani irin Ιaci a ransa. Anti
Maijidda ta dube shi gami da Ιan dafe hannunsa.
"Naga alama ba ka kaunar wannan labarin, tun jiya da
aka yi zaman shari'arnan ka ke matsawa kanka da tunani."
Abba ya yi murmushin yaΖe.
"Haba Jidda, kin san dole na ji zafin wannan al'amari,
na sani alΖalan gwamnati sun yi iyaka kokarinsa na ganin an samu kwakkwarar
shaidar da za'a yankewa matar sn hukunci da shi a gaban alΖali amma kuma babu
koda Ιigo, sai dai ta ina kike tsammanin hukuncin zai min daΙi bayan ta yanke
kauna tsakanina da Ιan uwana? Kai bana jin a duniyarnan zan iya yafewa Maryam.
Ta cutar da ni Ζarshe."
Ajiyar zuciya ta saki ta jinjina kai.
"Tabbas hakane, ba kai kaΙai ba, ta yiwa kowannenmu
tabon da har abada ba zamu mance da shi ba. Amma babu yanda muka iya tunda mai
afkuwa ya riga fa ya afku. Don Allah ka cire komai a ranka, ina mai tabbatar
maka cewa duk inda Maryam za ta shiga a duniyarnan alhaki ba zai bari ta runtsa
ba. Ai haΖΖokin da ta ci yawa ne da su. Wallahi tun ba ta mutu ba za ta soma
girbar abin da ta shuka."
"Allahu ya sa hakan."
Sallamar Ζassim ce ta katse Anti Maijidda, gaba daya ya
tsome ya yi wata iriyar rama saboda masifar shaye-shaye da ya yi a baya wanda a
yanzun ya haΙu da ciwon hanta da ya yi sanadiyyar ba shi tsoro har ya yiwa
kansa faΙa da kuma taimakon addu'a da nasihohi daga Abba da ma Anti Maijidda da
ta ja shi a jiki, aka samu ya rabu da sha.
DurΖusawa ya yi ya gaishe su. Suka amsa da kulawa.
"Abba, dama Mami ce ta zo gidannan, tana falon
Ζasa."
Har ga Allah shi bai ma kawo wace Mamin ba.
"Wacece Mami?"
Ya tambaya da zuciya daya, Anti Maijidda kuwa tuni ta je
gano. Wato dai Hajiya Maryam ba ta da kunya, kenan tana nufin ta biyo igiyar
aurenta tunda har yanzu da aure tsakaninta da Abba? Bai tsinka igiyar ba. Sai ta yi shiru kawai tana jin Ζassim na yi
mishi bayanin wace Mamin. A Ζarshe ta ga ya fusata ya a faΙan me ya kawo ta
gidansa? Kafin ma su kai ga wani yunkurin sai ga sallamarta a falon. Gaba Ιaya
suka dube ta. Hajiya Maryam sarkin gayu da Ζamshi, ita ce cikin wani tsohon
atamfar shekara fa shekaru sai ko hijabi koΙaΙΙen dake jikinta. Ta rame kwarai
kuma ta yi duhu hakan ya Ζara bayyana gajartarta. Ta karaso tana Ζarewa falon
kallo, ko ba a faΙa ba an narka uban dukiya. Ganin Maijidda ya sa wani abu ya
soki zuciyarta, ta kauda idanu daga kanta ta maida saman na Abba. Kan ta kai ga
magana ya riga ta bayan fitar Ζassim.
"Me ya kawo ki gidana?"
Da Ιumbin mamaki ta dube shi.
"Yusuf, ni kake tambaya me ya kawo ni gidanka? Kai fa
mijina ne, uban Ζ΄aΖ΄ana ai duk lalacewata bai kamata ka wulakanta ni ba."
Ya Ιan Ιagamata hannu.
"Dakata, ke Maryam ai ba ki da darajar da za'a
wulakantaki dominsa, dama can kura ce da fatar akuya. Ni dai babu wani ja in ja
da zan tsaya yi da ke, aure kuma da kike maganarsa ki je babu shi tsakaninmu,
na sake ki. Har abada ba na jin zan Ζara rayuwa dake Maryam. Abinda kika
aikatamin da zuri'ata ke da Allah wannan, ga ki ga duniyar, ta isheki. Ki
tattara ki ficemin daga gida wallahi daidai da dakika ba kaunar ganinki nake
ba."
Mami ta ji wata kaΙuwa sosai, a tarihin rayuwarta ai ba ta
taΙa kawo saki tsakaninta da shi ba. Yau kuma ya sake ta a gaban maΖiyiyarta.
Ta yi kwafa.
"Dama nasan a rina tunda ka auri Maijidda! Ke kuma sai
ki zuba ruwa a Ζasa ki sha. Yusuf kai kuma wallahi sai ka san ka yi da Ζ΄ar
halak. Allah ya isa tsakanina da ku."
Tana kaiwa nan ta juya fuu ta bar falon tana kuka. Shikenan
ita kam ta shiga uku, abubuwa goma da ashirin sun bi sun haΙe mata.
***
Maigadin ya bita da kallon tsaf yana mai nazartar yanayin
halittarta. Ya kai ta maΖura don haka a tunzure ta ce.
"Wai Bello ba ka shaida ni ba? Hajiya Maryam ce
aminiyar Hajiya Lubna uwargidan Honarabul."
Sai a sannan ya dauki murya da ma kamanni amma abin dai da Ιaure
kai yanda duk ta lalace ta yi muguwar rama. Kamar ba ita ce wannan Hajiyar mai
taΖama ba da take zuwa tana amsa gaisuwarsu dakyar. Dama can ya tsane ta
ballantana da wannan Ιanyen aikin da ta yi na rashin imani ya cika ko'ina duk
da a yanzu ya zama cikin tsoffin labarai amma jin ta fito ya Ζara tada
cece-kucen jama'a a kai.
"Ina magana Bello ka yi min banza kuma ka tare
hanya?"
Ya Ιaure fuska tamau yana zabga mata harara.
"Wacce kika zo wajenta ai tuni ta jima da barin wannan
gidan. Can garin bin yawon bokayenta ta kama hanyar Chadi a mota tayi mummunan
hatsarin aka yanke mata Ζafa guda. Yanzu dai ta koma garinsu can Ζauyen Auyo
cikin Jigawa, domin Alhaji tuni ya sallama mata, maganar nan da nake maki
shekaru biyar kenan da afkuwarsa. Sai ki bita can."
Ya Ζarashe yana juyamata Ζeya. Mami sai ta ji wani irin yaam
tsikar jikinta ya tashi, an yankewa Hajiya Lubna Ζafa kuma ta koma Ζauye? Ita
kuwa ta shiga uku, da Hajiya Lubna ta dogara, wurinta take tunanin za ta ji
samu kuΙaΙenta da ta biyo bashi wanda ta aikamata ta akawun don ta tura ga
Babandi, ba ta kai ga tura masa ba ne alikacin suka samu labarin mutuwarsa ta
hanyar yaronsa na Ζut-Ζut. Ga babu komai a akawun din nata kaf ta haΙa don ayi
nata aiki mai kyau akan Abba da Maijidda da kuma Humaira.
Kuka sosai ta fashe da shi, gefe guda ta tausayawa
aminiyarta, a wani gefen kuma na takaici da tunanin inda za ta nufa. Ζassim ya
ce nata Mubarak ya yi aure kuma yana zaune ne a can kudu da matarsa kuma
bayarabiya ya aura musulma. Ta dai karΙi lambarsa da zummar za ta kirashi.
Hakanan ta juya saboda mitar da Bello ke yi akan ta bar Ζofar gidan kar ta yi
masa sanadin aikinsa.
Kai tsaye gidan Futuha wanda dama tun farko ita ce ta je ta
taho da ita, amma firr Mamin ta Ζi zaman koda mintuna biyar ne tace ita dai sai
ta je ga Abba ta koma Ιakin aurenta. Duk yanda Futuha ta so nuna mata hakan ba
mai yiwuwa bane ta yi kunnen uwar shegu da ita.
Ta iske Futuhar zaune tana cin fara da mai sai ko salad da
ta yanka a kai, tana ganinta ta yi saurin miΖewa tsaye.
"Mami kin je? Ya ku ka yi da Abban?"
Sai ta zauna ta fashe da kuka, cikin kukan ta ba Futuha
labarin komai hsr na zuwanta gidan Hajiya Lubna. Futuha ta koma ta zauna
jikinta a mace tana sharce nata hawayen.
"Mami kin gani ko? Ni nasan Abba har abada ba zai mayar
da ke Ιakinki ba. Kin ma yi kuskuren tunkararsu. Mami komai fa dake faruwa ke
ce silarsa. Kin jefa rayukanmu cikin masifu iri-iri tsabar don zuciya irin
naki. Ni yanzu ki dube ni Mami da abin da nake Ζarewa koyaushe, cimar da nake
ci kawai lokutan da nake kwadayinsa shi ya zame min cin safe da dare. ArziΖin
da Yakubu ke taΖama da shi babu, ya saki Ζ΄ar snow ni kuma da uwar gidansa ya
rantse ko za'a kashe shi ba zai sake mu ba. Koda dai ni ke son sakin saboda cin
mutunci da wulakanci da gorin da yake yimin tun faruwar lamarinki. Abba ya mara
masa baya akan idan har na kashe aurena to ba dai gidansa ba. Shi kuwa ya hau
ya zauna, Ιan abin da zan samu na kudi daga yayyuna, haka zai zo ya amshe su ta
hanyar yimin dadin baki, wataran har da duka. Mami kina kallo dai ya ganki a
gidannan amma kasancewar girma ya fadi bai ko kalle ki ba ballantana akai ga
gaisuwa. Kiyi hakuri Mami, amma bayan fitarki ya cemin bai yarda ba kuma bai
amince da zamanki a gidansa ba. Akan haka har faΙa muka yi ya kira Abba ya
sanar da shi, shima kuma Abba ya ce koda wasa kika zauna sai ya Ιauki mataki a
kaina. Ni dai na shiga uku wallahi, rayuwar duka babu dadi a tsawon shekarun
aurena da Yakubu, ga haihuwa da nake so amma an tabbatarmin ba zan haihu ba
saboda mahaifar ta samu matsala. Mami ke ce silar gurΙacewar tarbiyyarmu. Ke
kika ja mana."
Sai ta fashe da kuka sosai fiye da na baya, Mamin itama
kukan ta soma iyakar Ζarfinta, tausayin kanta da na Ιiyarta na Ζara mamayarta.
"Aa Futuha, ni ban cutar da ku ba asalima na fi kaunar
na ga rayuwarku ta inganta. Akwai uwar da ke son ganin ta gurΙatar da rayuwar
Ζ΄aΖ΄anta? Nayi komai don na samar da dauwamammen farin ciki a duniyarku sai dai
abin ya juye. Kuyi hakuri zan gyara komai."
Futuha ta dago rinannun idanunta da suka ci kuka, fuskarnan
har ta yi jazur.
"Me za ki yi ki gyara Mami? Wani mummunar za ki Ζara
aikatawa da sunan gyara?"
Ajiyar zuciya Mamin ta sauke tana jan hanci.
"Babu wanda zan Ζara kashewa, amma ai ina da haΖΖi akan
Ιana Mubarak? Zan kirashi, shi zai nema min muhallin zama ba zan kashe maki
aure ba. Ita kuwa Tasleem duk radda ta Ζara kiranki da wata Ιoyayyar lambar ki
yi mata albishir da fitowata. Ki kuma roΖe ta akan ta dawo gida ta bar duk inda
take ta zo Maminta ta tuba."
Futuha ta Ζara fashewa da kuka tunowa da ta yi da Tasleem,
tun bayan kamun da aka yiwa Mami, cikinta ya bayyana aka soma maganganu wanda
ya yi silar shigarta duniya bayan ta ajiyewa wasiΖar neman gafarar Abbansu.
Haka Mami ta tashi babu kuzari da tunanin inda za ta je
kwana, Futuha ta tsaida ta ta kira layin Yassar, nan ta roΖi ya aiko kudi a ba
Mamin tasu, Yassar da Dawud wadanda ke aiki a kamfanin Alhajin Fadeel wanda yau
shekaru hudu kenan da buΙe shi a garin Abuja, a can suke zaune tare da matansu,
babu musu ya ce ta turo akawun lambarta. Amma koda ta zo masa da batun Mamin ta
zo gidana ya nuna shi sam bai aminta da hakan ba. Gwara dai a san yanda za'a yi
kawai, amma ba zai amince ta Ιata rayuwar gidansa ba. Hakanan Dawud shima da
aka kira, yace dai zai taimaka amma babu batun masaukinta a gidansa. A cewarsa
Matarsa ba za ta ji dadi ba. Duka a loudspeaker na wayar Futuha da ta bude,
komai yana shiga kunnuwan Mamin. Na karshe kuwa da aka kira Mubarak ne, ya Ιaga
bayan sun gaisa Futuha ke ba shi labarin Mami da halin da take ciki na neman
taimako.
"Zan aiko da abin da ya samu, kin san Hafsatu ta kusa
haihuwa akwai hidima a gabana. Daga baya za ga abin da zan iya yi. Ki turo
account number."
"Toh, ga Mamin za ku gaisa."
"No please, meeting zan shiga sauri nake. Later."
Daga haka ya katse wayar.
Mami ta Ζara sautin kukanta sosai, Futuha dai sai kallonta
take tana Ιan matsar kwalla.
"Yau ni dai Maryam ni ke ganin wannan ranar? Na ci
kashin yarannan na ci fitsarinsu amma ni suke yiwa wannan tofin Allah tsinen?
Ni ni Maryam yau ni ce yarana ke gudun raΙa?"
Futuha dai lallashinta ta cigaba da yi da ban baki, ba
jimawa sai ga alert ya shigo daga Yassar, dubu goma ce kacal ya turo sai ko can
Dawud ya turo dubu biyar. Futuha ta zari hijabi suka fita tare da Mamin, P.O.S
suka karasa ta zaro mata kudaden ta ba ta sannan ta fidda layin da ba ta amfani
da shi sosai ta ba Mamin akan ta nemi ko Ζaramar waya ta sanya sai ta yi
kiranta. Mami ta dube ta da hawaye.
"Yanzu shikenan kema rabuwa zan yi da ke Futuha?"
Futuha ta girgiza kai wannan karon ta ma kasa tsaida ruwan
hawayenta sai kwaranya kawai suke.
"Aa Mami, ai muna tare. Kiyi hakuri, yanzu bani da wani
abu da ya fiyemin face na cigaba da rayuwata a Ιakin mijina, idan ma na fito ba
wani dadi zan ji a gidan Abba ba duk da Anti Maijidda tana kawomin ziyara wasu
lokutan har ta yimin alkhairai bani da matsala da ita, amma Abba ba zai lamunta
da kashe aurena ba. Har jari fa ya bani amma Yakubu ya karΙe ya cinye. Duk
sana'ar da zan gwada a aljihunsa yake tafiya. Kiyi hakuri duk inda kike zan
dinga zuwa, ni da ace za ki bi shawarara da kin yi kudin mota kin tafi wajen su
Anna."
Ta girgiza kai da sauri.
"Allah ya sauwake, idan na koma kauyenmu a haka abin
kunya ne garemu baki daya. Ni kuma na fi karfin wani Ιan kauye ya wulakanta ni.
Kar ki damu zan yi kudi kwanan nan. Komai zai warware. Ba zan iya rayuwar kauye
ba. Ni nasan me na baro don haka ba zai yiwu na koma cikinsa ba."
Futuha ta kasa magana kawai sai kallon Mamin, ita wato duk
wannan abu bai sa ta shiga taitayinta ba? Hakanan suka yi sallama Mamin ta kaΙa.
Futuha ta kasa hakuri sai da ta kira Abba ta sanar da shi
duk abinda su Mubarak suka yi tana kuka. Abin bai masa dadi ba, ai duk yanda ya
kai ga son kada su raΙi mahaifiyarsu biyayya gareta wajibi ne a kansu musamman
ma su maza. Sai da ya kira su a waya daya bayan daya ya bude musu wuta sosai
karshe ya rufe da nasiha. Wannan ta sa suka ba shi hakuri suka kuma ci alwashin
kiran Futuha don ta kara hada su da Mamin amma fushi da zafin zuciya ya hana ta
Ιagawa.
***
Idanunta bai raina fata ba sai da ta kasa samun gidan da
take buΖata, a iyaka lissafinta ta fi kaunar gida mai Ιakuna koda falle biyu ne
sai falo da kuma kicin. Ta fi kaunar kuma ya kasance muhalli ne mai kyau mai
tayil ba wai suminti ba. Sai dai ta kasa samun koda mai simintin ne da kudaden
hannunta balle ta shiga, ga yamma ta yi. Hankalinta ya yi mugun tashi, duk inda
ta san za ta samu alfarma wurin Ζawayenta Ζ΄an Ζarya da fafa duk ba ta samu ba.
Gidaje har uku ta je amma guda daya kawai ta samu ganawa da matar gidan kuma
surukar Hajiya Lubna, itama a wulakance ta tarbe ta. Ko gama sauraronta ba ta
yi ba ta ce ta tashi ita kam sisinta ba zai shiga tsakaninta da ita ba. Da ace
dai za ta aminta da yi musu aikace-aikacen gida ne sai a dinga biyanta albashi.
Wannan cin zarafin da Hajiya Zulaihat ta yi mata ya mugun Ζona ranta, ita dai
Maryam ita ake nufi ta yi wanke-wanke? Ai ko giwa ta mutu, gawarta ta fi karfin
kiyashi ya ja.
Da wannan baΖin cikin ta fito fuuu ta yi titi ba a hayyaci
ba. Ta rasa ina za ta shiga, sai kawai ta dora hannu a kai ta kurma ihun kuka
ta durkushe tana yi ba ΖaΖΖautawa har mutanen da suka shiga sallar Magriba suka
fito aka taru ana bin ta da kallon mahaukaciya. Ζarshe ta yanke komawa gidan
Futuha don ba za ta yarda ta kwana a titi ba.
***
Zaune take da tulelan cikinta haihuwa yau ko gobe tana
kallon Age Is Just A Number a tashar ZeeWorld, hankalinta kwance take cin tuffa
daidai sadda ta ji hayaniyar yaran a kunnenta. Ta dube su, girgiza kai ta yi,
wato Fadeel ba ya jin nauyin kowa a kan yaransa, akan ya bar su su cika sati
gidan Abba ya gwammace ya tattaro su ya maido mata su ko kwanaki uku ba su kai
ga cikawa ba. Bakinta ta kama kawai gami da hangamewa, sai ta ji ita ke kunyar
su Abban ma ba shi ba. Suka taho a guje suka rungume ta su na kiranta da Ummee.
Gogan ya shigo janye da akwatin kayansu. Wayarta ta yi Ζara daidai lokacin,
Anti Maijidda ce. Ta san zancen bai wuce na su Twins ba don haka ta daga ba ta
ko jira sun gaisa ba ta hau yi mata kashedi akan kar ta Ζara aiko mata twins
hutu tunda su kam babansu bai bari. Gwara ta ji da su Afnan. Hakuri ta dinga ba
ta ita kuwa jin muryar yaran yasa ta katse wai ashe babansu ya shigo. Humaira
ta ajiye wayar gami da kallon Fadeel da ke faman bude musu robar ice cream.
"Habeebee, haka muka yi da kai? Fisabilillah ka kyauta
da ka kawomin su? Kai ko tausayina ma ba ka ji a yanayin nan?"
TaΙe baki ya yi.
"Ni gaida Abba na shiga yi yara suka maΖale za su biyo
ni, toh meye nawa a ciki? Kuma su da ga Nannynsu a gida kuma ga ni nan me zai
dameki? Kedai Allah ya sauke ki lafiya."
Ta sauke ajiyar zuciya kawai da firta ai shikenan daga haka
ba ta ce komai ba ta kwashi akwatinan yaran ta nufi dakinsu da shi. Sai da suka
ci abinci da Daddynnasu sannan ta titsa Ζeyarsu wajen Yadikko, dattijuwar da ke
kula da su, ita ta yi musu wanka suka sauya kaya suka bi lafiyar gado.
Ita ko Ιangaren mijinta ta shiga ta taimaka masa wajen rage
suturar dake jikinsa domin shiga wanka. Ya tallafo ta gaba Ιaya har cikin dake
jikinta yana shinshina Ζamshin turarukan da ba ta rabo da su har sun zame mata
ma jiki.
"Ke kam bakya tsufa, kullum wata Ζ΄ar budurwa kike koma
min."
Ta Ιan ja karan hancinsa da Ζarfi har ya Ιan yi Ζaramin
Ζara.
"Ko? Ka Ζara kallon kanka a madubi dai ka ga yanda kake
Ζara zama wani handsome guy."
Murmushi ya yi.
"Ni fa na ga alama nan gaba sai na dinga thinking twice
kafin na furta wata kalmar ta English a gabanki."
Ta yi dariya gami da rungume shi.
"Kai ne malamin ai, ba don kai ba ko zo na kashe ki da
turanci ban iyaba. Thanks to you da ka daukarmin malamar karatu ka kuma yi
kokarin ganin na goge sosai ina mu'amala da Ιalibaina na girki na kabilu iri
daban daban."
Shima rungume ta ya yi. Ta lumshe idanu cike da shauΖi,
Fadeel ya yi mata komai, bai bar ta da wahalar karΙar odar girki ba sai da ya
tabbatar ya samar mata wuri na musamman a bangaren gidan an gina mata katafaren
kicin da ma aji wanda za ta dinga koyar da dalibai masu son koyon girki a ciki.
Tana da yara Ζ΄an aiki wadanda aka yiwa tshirt ruwan hoda a bayansu an rubuta
Deelsha's Delicacies. Komai na su akwai tambarin wannan sunan a jiki, sunan
Humaira ya karaΙe ba ma iyaka Kano, kusan wurare da dama a faΙin Nijeriya an
san da ita.
Daren dai haka suka raya shi tamkar wasu sabbin ma'aurata,
koyaushe Fadeel ji yake kamar ana Ζara rura wutar Ζaunarta a zuciyarsa. Har Ibb
da Dakta Salma sun saka musu sunan Laila da Majnun sun gaji da kira sun haΖura.
***
Bugun Ζofar take yi da ya firgita Futuha. Yakubu ya dube ta.
"Waye haka? Dama kina yin baΖi ne idan bana nan?"
Ta yi saurin girgiza kai a tsorace.
"Wallahi aa, nima ban san waye ba." Ta fadi
Ζirjinta na bugu da sauri-sauri. Ya yi kwafa ya miΖe daga kwanciyar da ya yi
saman doguwar kujera ya shuri takalmansa ya nufi kyauren ya bude, ba don ya ja
gefe ba saura Ζiris Mami ta faΙa kansa. Ganinta ya sanya shi sauya fuska sosai.
"Sannu Yakubu, ashe kana gidan." Futuha jin murya
kamar ta Mami ya sa ta fitowa daga falon da sauri. Ita din ce kuwa. Ta dubi
Yakubu dake watsawa Mamin kallo kai ka ce wani abin Ζyamar ya gani. Ta maida
idanunta kan Mami bakinta har rawa yake wurin tambaya.
"Mami, lafiya kuwa kika dawo?"
Sai ta soma kuka.
"Na rasa muhalli Futuha, na rasa wurin kwana don Allah
Yakubu ka amince yau kaΙai na kwana anan idan ya so gobe sai na yi sammako na
fita neman gidan haya."
"Ba zai yiwu ba gaskiya Hajiya, gidan nan na gina shi
ne domin ni da matata, ban yi gurbin kowa a ciki ba har ke da kike mahaifiyarta
don haka ki yi hakuri ki bar nan kar ki Ιatan rai a daren nan."
Cike da takaici Futuha ta dube shi.
"Haba Yakubu, mahaifiyata ce fa. Don ta roΖi alfarmar
kwana guda a gidannan ba za ka iya yi mata ba?"
Ya kalle ta a wulakance.
"Ai ni bani da karfin zuciya irin na Abbanki da zan bar
uwar matata ta rayu da mu tsawon shekaru. Wato na ciyar da ita kuma na ci da
Babarta? Toh ba zan yarda ba wallahi, daga ke har ita yanzu sai na tattaraku ku
bar gidannan."
Ran Futuha ya kai karshe wurin Ιaci, wato Yakubu ya kai
matakin Ζarshe a fagen rashin mutunci. Uwa uwa ce ai duk lalacewarta, sai kawai
ta ji ta tunzura ta mance da duk wani gargadin Abba.
"Toh matukar Mami ba za ta kwana a gidannan ba nima ba
zan zauna ba zan bi ta mu tafi."
"Ni kuma muddin kika taka Ζafa kika fita a gidannan kin
fita kenan a bakin aurenki!"
Daga haka ya koma ciki bayan ya watsawa Mami kallon banza,
ita kuwa kuka kawai take yi tana girgiza kai cike da tunano alkhairan Abba.
Ashe ba Ζaramin namijin ΖoΖari ya yi mata a baya da ya aminta ta rayu gida daya
da Annarta ba, ko sau daya bai taΙa nuna wani bacin rai ba balle Ζyamar
al'amarin? Har Futuha ta juya ta koma ciki ba ta ma ankara ba, can ta dawo yafe
da mayafi sai jaka. Mami ta girgiza kai.
"Babu inda za ki je. Nima yanzu idan na fita ban san
gidan da zan shiga na kwana ba. Ki yi zamanki tunda ya Ζi aminta na kwana a
gidannan, zan nemi wani wurin."
Haka suka tsaya jayayya, a karshe dabara ta faΙowa Futuha,
nan da nan ta fiddo wayarta ta kira Baba Amina. Cikin kuka ta shiga roΖon
alfarma a gareta a kan Mami. Ta bata labarin yanda mijinta ya dage akan kwanan
Mamin, ga kuma dare ya tsala babu inda Mamin za ta je. Zuciya ta musulunci ya
sanya Baba Amina ta duba girman Allah da Futuha ta haΙa ta da shi ta aminta, ta
ce Futuha kar ta sake ta fito, ta dai saka Mamin shiga koda makwaftansu ne za
ta aiko babban Ιanta ya dauke ta a mota. Godiya sosai Futuha ta yi, tana sane
ta fasa kiran Anti Maijidda da ta yi niyya da farko, ta san ko giyar wake Mamin
ta sha, ba za ta lamunci wata alfarma daga Anti Maijidda ba. Batun Baba Aminar
ma ta so nuna ba za ta je ba, sai da Futuha ta nuna bacin rai sannan ta
sassauta. Tana nan makwaftan har dai Wasilu Ιan mijin Baba Amina ya zo, ta sha
jinin jikinta ganin dalleliyar motar da aka turo a dauke ta cikinsa. Haka ta yi
lamo sanyin AC na bugata da tunanin ina mijin Baba Amina ya samu kuΙaΙe haka
har ya mallaki motar nan? Ba ta Ζara shan mamaki ba sai da ta ga madadin a nufi
unguwar Jakara sun karya kwana sun shiga rijiyar zaki gaban wani danΖareran
gida, gaba daya unguwar shiru babu ko Ζarar inji sai hasken fitilun solar daga
kowane gida. Haka aka wawake Ζaton gate suka shiga.
Baba Amina ta karΙe ta babu yabo ba fallasa, ta bada umarni
ga babbar jikarta Yusra akan a nunamata masaukin baΖi. Daga haka ta wuce wajen
mijinta. Hatta abinci sai da aka kai mata ta kuwa ci hannu baka hannu kwarya.
Sai kuma ta mike ta shiga ta wanke jikinta ta mayar da kayanta. Ta kwanta babu
tunanin ko ramuwar salla tana kallon fankar dake wulwulawa a dakin, wai yau ita
Maryam ita ce ta ke cin alfarmar waΙanda ta raina take Ζyamata? Yau dai Baba
Aminar da ta saba yi mata kyautar kwancen kayanta da kuma tsoffin kujeru idan
ta tashi sauyawa, ita ce a wannan daular? Toh ita kuwa Baba Amina sana'ar me
mijinta ya samu haka? Yaushe ma ya bar koyarwar da ta san yana yi a baya?
Sai kuma ta hau tunanin inda za ta nufa daga nan, ita har ga
Allah abin kunya ne ta je kauyensu a haka. Toh amma kuma ai da wannan kunyanda
tozarcin da take fuskanta gwara ta koma Ζauyen. Wata zuciyar ta shawarce ta,
sai kuma ta girgiza kai.
"Allah ya yimin tsari." Ta bayyana a fili. Ita dai
gwara ta samu koda na mota ne ta je can Auyo wajen Hajiya Lubna ta karΙi kuΙaΙenta.
***
Da sassafe ta ji an banko Ζofar an shigo, ta miΖe firgigit,
Baba Amina ce fuskarnan tamkar an aikomata saΖon mutuwa. Mami ta miΖe zaune
tana mutsistsuka idanu.
"Maryam, gari ya waye, ki tashi ki tattara ki bar min
gidana. Jiya albarkacin Futuha ki ka ci saboda mu mutanen arziki ne mun san
darajar aure da ma Ιan adam, ba za mu lamunta ki je ki kashe auren Ζ΄armu ba
saboda tsabar rashin hankali irin naki. Ki gaggauta shiri don dai abin kari ba
zan hanaki ba, za'a kawo ki ci ki gaggauta tafiya."
Tana kaiwa nan ta fice ta banka Ζofar, Mami ta mike tana haΙiyar
yawu maΖwat, wani abu ne tokare a maΖogwaronta, wannan cin kashin da take
fuskanta da me ya yi kama? Tana nan zaune tana tufka da warwara gami da sharce
hawaye Yusra ta shigo da sallamarta ta gaisheta sannan ta ajiye tiren dake
hannunta ta dauki na na jiyan da ta shigo da shi, har za ta fice Mami
cikin sauri ta dakatar da ita da cewa ke. Ta dawo ta tsaya.
"Sunana Yusra."
"Ok Yusra, dan taimakamin da kwatancen gidan
Raihana."
Yusra babu abin da ta sani akan Mamin, amma daga yanayin
yanda Baba Amina ke nuna rashin son baΖuncinta sai ta ji shakkar sanar da ita.
Lura da hakan sai Mami ta murmusa kadan.
"Ni mahaifiyarta ce."
Ta sha mamakin jin wannan furuci, wato ita ce Mami? Maman
Anti Raihana da take da labarinta? Tabbas ta san labarin komai amma a fuska ba
ta san wace Mamin ba. Girgiza kai Yusra ta yi.
"Kiyi hakuri sai na tambayi Baba idan ta amince
shikenan."
Sauke ajiyar zuciya ta yi. Ta san Amina ba za ta wani aminta
ba sai ta sauya dabara ta ce ta bar shi kawai. Gwara ta yi amfani da lambar
wayar Raihanar da ta karΙa hannun Futuha.
***
Hakanan ta fito daga gidan Baba Amina, mijin Baba Amina har
dubu ashirin ya Ιauka ya ba ta, ta karΙa ta yi godiya tana tuna sadda mijinta
Ke musu idan sun shiga matsalar da ta fi Ζarfin aljihunsu.
Wurin masu siyar da waya ta nufa ta samu waya Ζarama
secondhand ta sanya layin da Futuha ta ba ta sannan ta shiga neman layin
Raihana.
Sau uku ta yi Ζara aka Ιaga, muryar Raihana ta doki dodon
kunnenta.
"Raiha, ni ce Maminki."
Ta ji Ιif na Ιan lokaci an dauke wuta ta ma yi zaton ko ta
tsinke can sai ta ji Raihana cikin muryar kuka ta amsa.
"Mami."
Ko ya uwa ta kai ga lalacewa uwa ce, kaunar Mamin da kewarta
da take kwana da tashi da shi wannan karon ma shi ya cika mata zuciya. Koyaushe
cikin addu'a take akan Allah ya shirya mahaifiyarta kar ya dauki ranta ba tare
da ta tuba ta nemi yafiyar wadanda ta cutar ba.
Itama Mamin cikin hawayen ta amsa.
"Naam Raihana. A ina zan sameki ina so zamu yi
magana."
Nan da nan Raihana ta yi mata kwatancen gidanta cikin
rufewar idanu. Ta manta dakyar ta samo soyayyar uwar mijinta da ma danginsa
wanda kyautatawarta garesu da ma kyawawan dabi'un da suka ga ya sha bamban da
na mahaifiyarta bayan sun mata gwaji iri-iri yasa suka yada makaman, suka
kuma riΖe ta da mutunci.
Mintoci kalilan sai ga ta a gidan. Raihana ta fito ta buΙemata
suka shiga ciki tana danna hawayenta ganin yanda Mamin gaba daya ta sauya kamar
ba ma'abociyar Ζamshin nan da saka manyan suturu ba. Allah ya taimaka mijinta
ba ya gidan ya ma yi tafiya Abuja. Ζanwar mijinta da suke tare kuwa tana
makaranta. Dama Afnan da Yazid suna can gidan Abba ba su dawo ba. Bayan sun
zauna sai da ta fara kawomata abinci da ruwa ta kara ci don a gidan Baba Amina
ba ta ci a nutse ba sannan ta soma magana.
"Mami, kece kika zama haka?"
Ajiyar zuciya Mami ta yi gami da girgiza kai tana bin gidan
Raihana da kallo, babu laifi ya tsaru sai dai har yau a yaranta ba ta ga wanda
ya samu gida irin na Humaira ba, yanzu kuwa ko ya ya gidan yake? A can baya ma
ba za'a haΙa shi da wannan ba ballantana kuma yanzu da ta ji wai yaranta a
kamfanin mahaifin Fadeel suke aiki. Ta sani arziki kam zai ci uban na baya.
Shirun da ta yi ya sanya Raihana Ιora zancenta.
"Mami don Allah wannan hali da kika tsinci kanki ciki
ya ci ace zuwa yanzu ya isheki ishara. Kin yi komai don ganin rayuwar yaranki
ta inganta, amma ki sani yaranki kaf babu wanda bai ci arzikin Humaira ba.
Humaira ita ce silar da Fadeel ya nemawa su Yaya Yassar aiki a kamfanin
babansa. Humaira ta kasance mai kyautata mana, koyaushe cikin kawowa yaran
tsarabe-tsarabe take a duk sadda ta je Umarah ta dawo."
"Har Umarah ta je?" Fadin Mami idanu waje, Raihana
ta yi murmushi.
"Yes Mami, ta je kuma ta kai su Abba, ya kuma kai
Kawunta. A yanzu da nake maki magana Humaira sai ta siyar dake da harshen
turanci, ta zama babbar mace kuma majingina ga Ζ΄an uwanta. Ta na da babban ajin
koyar da girke-girke a gidanta wanda Fadeel ya gina mata hakanan tana cigaba da
karΙar oda. Batun da nake maki da yanzu a wannan satin za'a yi hira da ita a
babban kamfanin gidan rediyon BBC dake Abuja amma yanayin laulayin cikin da
take fama da shi kuma ta kusa haihuwa shi ne dalilin da aka Ιaga. Mami babu
riba Ιaya da kika ci, Ummita dai ta kammala karatunta aiki ne kawai Ridwan bai
aminta da shi ba hakan yasa ni da ita muka kafa kasuwanci don nima kakar su
Yazid ta ce ba ta amince nayi aiki ba. Yanzu ki duba ki gani, da bazarsu
yaranki suke taka rawa, ban yi niyyar faΙawa Futuha yanzu ba amma ke dai zan
fadamaki ko hakan zai sa ki kara gane kuskurenki Mami, ki kuma sani cewa
dagaske Humaira da Ummita masoya ne a garemu. So suke su taimakawa Futuha ta
kafa kasuwanci, kuma a yi magana da Abba akan ya gargadi mijinta shima a nema
mata gafararsa don ya huce daga zafin da ya dauka da ita kuma duk saboda ke.
Har gobe ina bakin cikin abinda kika aikata Mami wanda ya yi silar rasa
Tasleem, an neme ta sama ko ka Ζasa an rasa. Babu wanda ya ji ko kuma ya kara
ganinta, ba mu san duniyar da ta ke ciki ba, ba wanda ya san rayuwar da ta jefa
kanta ciki. Mami ko domin lahirarki ina roΖonki akan ki nemi afuwar wadannan
bayin Allahn. Ki sauya sabuwar rayuwa ki zauna lafiya da kowa."
Mami hawaye take fitarwa sosai, ta ji za ta gyara, ta yarda
wanda ya fika ya fika har abada, wannan daukaka ta Humaira ba karamin taΙa
ranta ya yi ba, wato duk haukar da ta yi ta Ζare babu abin da hakan ya sauya.
Zuciyarta ta cika da tunanin Tasleem, ko ina ta ke? Wace kalar rayuwa ta faΙa?
"Shikenan, zan gyara komai amma yanzu ki bani wani abu
zan je Jigawa ganin Hajiya Lubna, akwai kuΙaΙena a hannunta, su zan karΙo sai
na dawo na kama gida na fara sana'a."
Mamaki ya cika Raihana.
"Mami ba ki yi maganar neman gafarar su Abba da Humaira
ba."
Ta dan runtse idanu tana dan jin zafi da radadi, kamar ta ta
je ta durkusa wajen wadanda ta raina a baya neman gafararsu? Ba ta jin dai a
yanzu za ta iya sai dai ko nan gaba. Don ta kwantarwa da Raihana hankali sai ta
gyada kai.
"Zan yi hakan, yanzu dai ina bukatar kudi daga wajenki
zan je ga Hajiya Lubna."
Raihana ta dan ji sanyi, za ta so dai Mamin ta aiwatar akan
kari ba wai ta ja lokaci ba.
"Toh, amma kinsan inda gidansu yake a can?"
Sai a nan ta tuna wautarta ma.
"Aa, sai dai nasan sunan Babanta, Lawal Mai Ashana
kinga za'a iya samun wanda ya san shi."
"Wannan ba dabara ba ce Mami, bari na kira Anti Laila,
ai muna zumunci da ita tun ba Humaira ba da ba ta yarda Malamarta ba ta
girki."
Ita dai uhm kawai ta ce amma bayan haka ba ta ce komai ba,
ta yarda tsanar da ta yiwa Humaira a baya ba Ιan kaΙan ba ne don har
yanzun idan ana maganarta ita dai jin ta take babu yabo ba fallasa a zuciyarta.
Ta dai yarda kuma ta aminta sun fi karfinta har abada.
Raihana sai da ta ba ta kaya ta sauya, kasancewar ta fi ta
tsawo ma sai da kayan suka yi Ιan shari Ζasa musamman dayake Mamin ta
rame. Ta haΙamata da sabbin atamfofi har biyar da mayafai cikin na
siyarwar su daga nan ta bata dubu hamsin. Koda ta raka ta har gate sai da ta
ksra rungumeta tana kuka kamar kar su rabu, ta roΖi Mamin gafarar duk wani
bacin rai da ta taΙa shiga sanadinta, Mami ta girgiza kai tana nata hawayen.
"Ba ki yimin komai ba Raihana, idan kin ma yi na yafe.
Nima ki yafemin."
Ta ce itama babu abinda Mamin ta yi mata, ta kuma bi ta da
roΖo akan ta nemi gafarar da ta ce ta yi kar lokacin ya Ζure. Ta amsa da toh
suka rabu akan zasu yi waya.
***
Da kwatance ta isa gidan su Hajiya Lubna. Ginin sumunti
fentin duka ya goge, kana gani dai ka san ya kwana biyu a duniya. Cikin gidan
ma ta soma karo da awakai da matan Ζannan Hajiya Lubna ke kiwo, mutanen da a
baya Hajiya Lubna idan sun je wurinta take nuna musu taΖama da isa, ko
gaisuwarsu a wulakance take amsawa. Bukatunsu kuwa hakanan za su yi ta shelar
zuwa ana jeromata su sai sun ci sa'a dakyar take taimakawar. Haka Mami ta daure
zuciyarta tana toshe hanci saboda ruwan da ya cakuΙe da kashin awakan yana
tashin samami. Ta shiga da sallama, matan gidan duka su na tsakar gida, mai
tankaΙen tuwo tana yi, mai daka daddawa tana yi sai kuwa wasu a gefe suna
kitso. Can kuma yara na wasa da kasa sun yi dama-dama da jikinsu. Suka amsa
sallamarta su na mata kallon baΖuwar fuska.
"Wajen Hajiya Lubna na zo."
Suka kalli juna suka yi wata iriyar shewa gami da fadin
warr! Ita abin ma sai ya ba ta haushi.
"Lafiya? Ko ba nan ne gidan ba?"
"Aa, maida wukar meye na fusata? Nan ne mana. Amma ai
mun ji kin ce Hajiya, koda dai ba a sauyawa tuwo suna ko?"
Wacce ta fadi hakan ta karashe cikin shakiyanci.
"Kema dai Sa'ade akwai ki da wata magana, toh ai yanzu
ko hanyar jirgi bana jin Luba za ta tuna, ke kam dadin ya kare an dawo asali an
zauna babu cas ba as!"
Mami ta bude baki za ta tarewa aminiyarta ta ji muryarta
tana sallama. Ta juya da sauri ta dube ta. Sanduna ne guda biyu take dogaraws
ta shigo, ta yi mugun rama da duhu. Wata Ζ΄ar leda ce a hannunta baΖa. Ganin
wata kamar fuskar da ta sani ya sanya ta yin shiru tana nazari.
"Ga nan Hajjaju ta dawo, sannu da zuwa."
Fadin Sa'ade. Suka kwashe da dariya, Mami kuwa karasawa ta
yi da sauri ta rike hannunta daya.
"Hajiya Lubna! Ke ce kika zama haka?"
Sai ta fashe da kuka, itama Lubna nan da nan ta shaida
muryar.
"Maryam! Dama akwai sauran shan ruwa a gaba? Ashe zamu
kara haduwa?"
Sai kuka, ganin an musu ca da idanu ya sanya Lubna jan ta
zuwa wani daki dake can kusa da garken awakai. Dakin da ko Maigadin gidan
Hajiya Lubna ba zai rayu cikinsa ba. Babu komai sai katifa mai kama da gado
wanda ta siya tun farkon dawowarta gidan sai ko akwatunan kayanta a can gefe.
Nan suka shiga maida yanda aka yi bayan sun sha koke-kokensu.
"Uhm, Maryam naga rayuwa, saura kiris na rasa raina a
garin yawon bin Bokaye. Allah ya tsaga da rabon dai zan shiryu. Sanadin haka
Daddyn Kabeer ya sake ni, nan shi ne muhallina a gidannan. Matan Ζannena ne
amma gasunan sun raina ni wulakanci iri-iri, ban isa su dafa su bani ba sai dai
na yi yanda zan yi na ci abinci. Sai nayi dakyar nake samu Kabeeru ke yimin
aike. Maryam mun yi kura-kurai da dama wanda sai yanzu nake Ζara nadamarsu. Mun
yi imani da abin da shima din halittar Allah ne, ba zai iya yiwa kansa ba
ballantana ya yi mana. Lokaci bai Ζure ba Maryam, kamar yanda na samu na nemi
gafarar mijina ya yafemin duk da ya rantse ba zan kima gidansa ba, da ma
danginsa wadanda na cutar, har yau kuma nake cigaba da neman gafarar
Ubangijina, kema ya kamata ki nemi gafarar mutanen da kika zalunta a rayuwa.
Rayuwarnan na Ζara ganewa ba komai ba ce, yanzu ji inda nake rayuwa tamkar ban
taΙa Ιandana wata rayuwa ta daula ba."
Mami kuka take sosai, tabbas koda a baya ba ta karaya ba da
al'amarin duniyarnan, yanzu ta Ζara tsorata. Ta kuma ji dagaske za ta iya
durΖusawa koda a gaban Maijidda ce ta nemi yafiyarta. Haka Lubna ta dinga yi
mata nasiha iri-iri akan rayuwa.
"Idan da za ki bi shawarata, ki koma gaban Anna ki
zauna."
Ta numfasa, Futuha ta sanar da ita irin baΖar wahalar da
Anna da Jannat suke ciki, Jannat ta Ζara yin wani auren tuntuni, mijin ya
yaudare su da Ζaryar arziki ashe bai mallaki komai ba. Lefen burga da karyar da
ya haΙa mata ma a washegari aka zo aka kwashe su kaf. Daga karshe ake ganewa
shi ya sanya, Anna da Jannat suka turje akan sai ya sake ta ya ce shi kuma
yanzu ya fara aure. Shekara guda gidan da yace nasa ne ashe na haya ne, aka zo
aka kawo notis, karshe dai mutumin sai ainahin gidansa ya kai ta wurin matansa
biyu wadanda kansu yake a haΙe ga uban Ζ΄aΖ΄a. Jannat yanzu haka yaranta uku da
shi, yan biyunta kuwa ko Ζeyarsu ba ta gani sun koma zaman Saudia, inda tsohon
mijinta ya Ζara samun aiki. Sai dai sukan yi waya da ita da begen son ganinta
wanda Babansu ya nuna ba yanzu ba. Anna kuwa girma ya ja kwarai, hakanan take
rayuwar babu yabo ba fallasa.
Mami ta kwashe labarin yanda su Anna ke fama a can ta faΙawa
Lubna.
"To ke ba gwara kin je kin Ζarasa neman ladanki ba can?
Kin kula da dattijuwarnan itama ki nema mata gafarar bayin Allahn nan?"
"Hakane Lubna, wallahi rashin sanin inda Tasleem yake
yanzu shi ke cimin tuwo a kwarya. Hankalina yana kanta."
Ta fadi cikin sharce hawaye.
"Babu yanda muka iya sai addu'a, muddin dai tana raye
in sha Allahu sai kiga Allah ya bayyana ta."
Haka suka yi ta tattaunawa akan matsaloli, a karshe Lubna ta
aika aka siyomusu alala a makwafta suka ci suka sha ruwa. Mami dai haka ta
hakura suka kwana washegari bayan sun karya ta kama hanyar Kano bayan ta raba
kayayyakin da Raihana ta ba ta gida biyu ta bar wa Lubna rabi. Batun kudadenta
babu su, duka sun tafi a maganin Lubna kamar yanda ta ce mata, haka ta hakura
da su saboda da gaske suke kaunar junansu. Haka suka rabu da kuka kamar
shikenan sun yi bankwana.
***
Ba ta san hawa ba ballantana sauka, ta dai ji motarsu ta yi
wata irin wulwulawa saboda bugun da aka yi mata daga baya ta bugi wani Ζarfen
wutar lantarki kafin ka ce me ta kama da wuta. DaΖyar aka ceto rayukan wasunsu
yayinda wasu suka ce ga garinku ba a tseratar da komai nasu ba sai toka. Mami
gaba daya fuskarta ta babbake hakanan hannayenta sai ko kafafunta.
Tana ihu tsabar azaba da fadin.
"Na shiga uku! Wayyo Allahna! Ashe haka azabar wuta
take! Wayyo ni Maryam, na shiga uku ku taimaka ku raba ni da wannan
radadin!"
Ta suma ya fi a kirga har dai aka sadar da su zuwa asibitin
Murtala dake birnin Kano.
***
Anti Maijidda hankalinta ya tashi da jin labarin Ζonewar
Mami a bakin Futuha, dakyar da suΙin goshi Abba ya aminta da batunta, ya kura
kaf yaran Mamin a waya ya sanar da su maza su dawo Mahaifiyarsu na asibiti rai
a hannun Allah. Kafin sati dukkansu sun halarta, babu kuma wanda bai je duba ta
ba, fuskarnan babu kyan gani hakanan Ζafafunta da likita ya tabbatar musu zai
wahala ta Ζara taka su don ba iyaka Ζunar ba kawai, sun bugu da Ζarfe wanda
dakyar aka Ιanbarota daga jiki.
Matan kuka suke yi kwarai, duk rashin imanin mutum idan ya
ga Mamin sai ta ba shi tausayi yanda take ihu da fadin abubuwan da ta aikata a
rayuwa tana kuma neman gafara.
"Wallahi ba zan iyaba! Ba zan iya jure azabar kabari ba
ni Maryam! Wayyo Futuha baku san ya nake ji ba! Haka wuta take?! Wallahi na
tuba ku yafemin, ku yiwa girma na Allah ku kiramin Humaira da Ummita na nemi
gafararsu. Ina Maijidda ina Abbanku?!"
Haka ta yi ta sumbatu iri-iri, dalilin Anti Maijidda,
Humaira da Ummita suka zo hakanan shima Abba da Baba Amina, babu wanda bai
zubar da hawaye ba, rayuwar Mami ta ishi bawa ishara musamman masu hali irin
nata. Abin duniya ba ya Ιuya, mutane musamman na cikin asibitin aka dinga yaΙa
zantuka game da abubuwan da Mamin ta ce ta aikata. Sai da aka hana shiga
wajenta saboda yanda masu son kashe kwarkwatar idanunsu ke yunkurin zuwa.
***
MURFI...
Gidan cike yake da jama'a Ζ΄an suna ana taya Humaira murnar
sauka lafiya inda ta haifi Ιanta namiji Ζosasshe mai kama da ita sak! Su Ummita
gaba daya sun hadu har Futuha wacce a yanzu ko kusa ba sa ware ta a cikinsu.
Sun hada kansu gwanin sha'awa. Haka suka dinga shige da fice wurin ba abinci
baΖi, Humaira wacce a yanzu take da jama'a ta ko'ina, gidan sai ya kasance
tamkar haihuwar fari.
Fadeel da su Ibb suna can falonsa inda aka kai musu abinci
kala-kala suna ci. Kowa ka gani zuciyarsa fari Ζal. Anti Majjidda da nata
tawagar su ma su na gefe ana hira da raha.
Abinda zai ba ka mamaki bai wuce yanda Murja a yanzun ta
yada dukkan makamanta ba suke zumunci da Humaira. Ba dai can ba amma duk sadda
wata sabgar junansu ya tashi mai muhimmanci zasu taya kansu murna. Ta gama
amanna cewa wutsiyar rakumi ta yi nesa da kasa, ta rungumi mijinta da hannu
bibbiyu tana kuma yaba abinda yake mata. Bangaren Anti Amarya itama ta sanyawa
zuciyarta salama, ta saduda saboda Allah Abban Fadeel da Fu'ad ke zaune da ita,
wannan ne silar da itama ta yiwa kanta karatun ta nutsu tunda ba ta rasa komai
daga gareshi ba ta ke zaune da su da zuciya daya ba kamar a farko ba.
Ta shigo gidan tana raΙe-raΙe, yaran da ta soma cin karo da
su da ma matan dake farfajiyar gidan a zaune duka babu fuskar da ta gane ciki.
Ta cigaba da taku har zuwa cikin falon gidan, tana ji wata na fadin ia kuma
wannan wacece haka sanye da nikabi?
"Ke baiwar Allah, wa kike nema ne?"
Ta juyo tana kallon mai tambayar, Futuha ce riΖe da
muΖullayen kicin bayan ta adanawa Humaira abinci na musamman na baΖin da tace
za ta yi, ta ci adon ta cikin leshi pink wanda suka yi su uku, ita da Raihana
da kuma Ummita. Ta dan yi Ζibarta ta kuma washe abinta. Daidai nan Ummita ta
karaso tana goye da yaronta Ιan watanni takwas Affan.
"Sister ina mukulli...wace wannan kuma?"
Maganarta ta yanke ganin mace da nikabi, sai kuma aka soma
taruwa, a hankali ta sa hannu ta Ιaga nikabinta da ruwan hawaye ya yiwa
kaca-kaca. Duk lalacewarta, ko a tandun kwalli za a tsoma ta a fito da ita ai
ba za ta Ιace musu ba.
"Tasleem!" Fadin Futuha da Ζarfi, itama Ummita sai
ta zaro nata idanun. Sai kawai Futuha ta rungumeta suka shiga kuka mai sosa
rai. Labari ya kai ga su Maijidda da su Humaira da Raihana, nan fa aka firfito
don ganewa idanu, tabbas ita ce. Humaira ta sa Futuha ta kai ta Ιakin baΖi, sai
da ta yi wanka ta sauya kayanta da suka ci ubansu suka koΙe sannan ta dubi
Raihana da Futuha sai ko Anti Maijidda da Baba Amina wadanda ke zaune sai ta
kara fashewa da kuka.
"Ina kika je?" Shi ne tambayar da Anti Maijidda ta
jefomata.
"Duniya na shiga, bariki na yi, na aikata zina da mazan
da ban san adadinsu ba, na bi shawarar da gurΙatacciyar zuciyata ta bani akan
tunda har babu mai sona kuma an tsane ni na fada duniya. A daren da na bar gida
naΖuda ta kama ni, bayan na haifi Ιan namiji sai na kai shi gaban gidan marayu
na ajiye. Dama na fita da shirina na dukkan abinda zan buΖata na haihuwa. Ina
kuka haka na bar yaron bayan na bar wasiΖa akan shi din maraya ne a taimaka a
kulamin da shi. Daga nan na nemi wani tsohon abokina da muka hadu a fesbuk,
akan ina bukatar taimakonsa. Ya cemin shi yana Kaduna sai dai ko idan zan zo.
Nace naji. Ba shiri na wuce tasha na nemi motar Kaduna. Zuwan da nayi na iske
shi kadai ke rayuwa a gidan da aka ba shi na ma'aikata. Na koramasa bayanin da
na tabbatar zai tausayamin ya bar ni na kwana, cewa an saki mahaifiyata kuma
mahaifina ya kore ni. Da wannan bai kara neman ba'asin komai ba don da alama ba
shi ne a gabansa ba. Bobby shi ya soma dora ni a hanyar bariki, ya maishe ni
tamkar katifarsa bayan mun yi tsarin iyali, da ya gaji da ni ya yi wata sabuwa
sai ya kore ni, koda na Ζi tafiya ya yimin dukan kawo wuΖa, babu wanda ya zo
cetona. Na kama gida na soma fita yawon club ina neman abokan banza idan sun yi
amfani da ni su ban kudi, da wannan nake cin abinci nake kuma biyan kudin
haya. A karshe da nayi sabbin Ζawaye suka zuga ni kan yanda nake da kyau zai fi
ace Abuja nake harkokina. Da wannan na bisu zuwa Abuja. Anan ne har na samu
wani inyamuri musulmi ya aure ni, amma kullum ya sha giya sai ya dake ni. Kun
gani." Ta daga rigarta ta nuna musu shacin tafka iri-iri a fatarta. Ta
dora da fadin.
"Sai da na shekara hudu cikin uΖubar mutumin nan, sai
ya ga dama yake bani na cefane, zai shigo da mata wanda duk ya so, bani da
damar da zan hana sai cibi ya zama kari, ni zan girka musu abinci idan kuma na
Ζi sai ya hora ni da yunwa har na tsawon kwanaki. Rana tsaka na wayi gari ya
tattara kayansa ya bar gidan zuwa Lagos ya barmin wasika na amanar gidansa kan
zai je wani aiki ya samu bai dawomin ba sai bayan shekara guda, ya dawo kuma da
ciwo mai karya garkuwar jiki. Ban ankara yana da ita ba sai bayan ya shafamin,
na yi kukan bakin ciki da danasanin shiga bariki, sai kuma a sannan naji ina
son dawowa gida amma tsoron abinda zan tarar ya hana ni. Shi ne na soma kiran
Futuha da lambobin mutane don naji ya kuke, kiran karshe ne take sanar da ni
dawowar Mami. Nayi kuka sosai da murna, daga baya kuma labarin Ζunar da ta yi
da kuma na komawarta Nijar ya same ni daga bakin matar da na ari wayarta a
karshe na yi kiran Futuha, ita kuma lokacin saΖo ta bayar tunda matar ta Ζi
aminta ta sanar da ita daga inda nake kiran. Wannan ne ya yi sanadin dawowata,
sai da naje can gidan Abba ban iske kowa ba, sabon Maigadinku ya tabbatarmin
kuna gidan Humaira. Shi ya yimin kwatance na zo. Kuyi hakuri don Allah ku
yafemin, na cutar da rayuwata, na cutar da ku. Me zan yi na wanke kaina daga
wannan zunuban?"
Ta fashe da kuka, su dinma kukan ta sanya su. Anti Maijidda
da Baba Amina suka yi mata kaca-kaca da nuna mata tsantsar wautarta. A karshe
dai saboda kar jama'a su ankara sai suka fita aka kyale ta daga ita sai Futuha.
Nan ta ba ta labarin dukkan abinda ya faru bayan rabuwa.
"Mami yanzu kam tana Nijar, a dole ta hakura ta ce a
maida ta koda mutuwar ce ta mutu a asalinta. Tasleem, zuciyoyin wadannan bayin
Allahn mai kyau ne, ba su duba komai ba suka yafewa Mami. Suke kuma bada kudade
ana mata aike. Humaira ita ta dauki nauyin komai na asibiti sadda Mamin ta rayu
a asibitin. Ummita kuwa kullum cikin hidimar sanya direba kawo abinci take.
Hakana Anti Maijidda da Baba Amina. Mami an yanke mata kafafu, ta yi nadamar
komai ko kuma nace dukkanmu mun yi nadama. Rayuwar su Humaira ta inganta, namu
rayukan ne bai tafi yanda muka daukake shi nuka ci buri ba. Yanzu mene amfanin
badi ba rai? Ki godewa Allah da ba ki mutu ba Tasleem, Allah ya ara maki damar
da za ki nemi gafarar Abba da su Humaira kema. Nikam yanzu babu komai tsakanina
da su sai sam barka."
Tasleem ta hau jinjina kai cikin zubar hawaye zuciyarta cike
da tsantsar nadama.
***
AGADEZ, NIJAR...
"Ta dawo? Alhamdulillah, Alhamdulillah!"
Mami ke wannan hamdalar cikin muryar kuka jin bayanin da
Futuha ke mata ta whatsapp. Ta turo kekenta zuwa kusa da gadon Ζarfe na Anna
dake kwance sai abin da aka yi mata sakamakon shanyewar da Ιarin jikinta ya yi.
Cikin yare take sanar da Anna cewa Taslee ta dawo gida. Anna har da
hawaye suka shiga fita babu baki sai gwalagwalanci dakyar Mamin ta fahimci
hamdala ce Annar ke yi.
Ta bude voice na biyu da Futuhar ta turo. Nan ta shiga
salati da kuka sosai, cutar kanjamau ce da Tasleem?
Sallamar da Jannat goye da yaronta karami bai sa Mami daina
kukan ba. Mace mai diri da kyawu, ta koma wata siririya sai Ζashin wuya. Kirjin
nan a shafe babu tudun nono duk fatar ta yamutse. Har tana tuntube ta karaso,
duk karnin nono take yi. Wani kazamin goyo take da babu ko turaren jiki.
Daki ne ginin Ζasa, gadon karfen Anna shi ya cinye dakin sai
ko tabsrmar kabar dake malale a kasa, can gefe kuwa tsohuwar sif na kayan
Jannat ne da ta ajiye sadda ta dawo gidan cikin tsoffin kayanta na gidan tsohon
mijinta, gadon da madubi yana can gidanta, wannan din ma Ζin shiga ya yi
dakinta yasa ta bar wa Anna.
"Maryam lafiya? Ko Anna ta mutu ne?"
Ta girgiza kai ta miΖa mata wayar, ita kadai ce waya babba
da suke amfani da ita don kira da samun sakonni daga can. Raihana ce ta mata
kyautarta sadda za ta taho Nijar. Kuka itama Jannat ta shiga yi. Tasleem
mutuniyarta ce, jininsu ya hadu, duk a yaran Mami ba ta da kamarta. K aunar da
take nata na musamman ne. Haka suka hadu zuciyoyinsu cike da tsantsar nadama.
Sai ga karuwancin da take kira ga bayin Allahn da ba su ji ba ba su gani ba ya
fada kan wacce ta fi kauna da so cikin yaran Ζ΄ar uwarta.
***
Tasleem sai da aka kai ruwa rana kafin Abba ya yafemata,
karshe sai da ya sa aka bincika duk inda ta ce ta je da kuma auren, ya samu
tabbacin abin da ta fadi. Ya zubar da hawaye jin wai yarinyarsa ta ciki ta yi
karuwanci. Har sai da ya kwanta rashin lafiya sanadin damuwa. Hakanan dai ya
rungume ta, itama ta zauna ta yiwa kanta karatun ta nutsu. Ta soma zuwa asibiti
karΙar magani kuma da taimakon Allah jikinta ya soma yin kyau idan ka ganta ba
kamar sadda ta zo ba. Abba da kansa ya sa aka je aka dauko yaron da ta kai
gidan marayu, wani irin hatsabibin yaro ne da ba ya jin magana kuma ba ya
shakkar kowa. Idan ya kai Tasleem bango ta sa hannu ta dake shi sai ya duramata
ashariya ta ban mamaki. Illoli iri-iri sun gani a wajen yaron ga ba ya shakkar
kowa a cikinsu. Ganin haka yasa Abba kai shi makarantar allo ta kwana da zummar
ya je can a hora shi.
Bayan watanni uku da dawowarta labarin mutuwar Anna ya riske
su, wannan ne ya yi silar zuwan yaranta kaf Nijar har mazan bisa umarnin Abba.
Shi dai bai je ba amma ya kira Mami ta waya ya yi mata gaisuwa. A wayar ma sai
kuka take da nemarwa mahaifiyarta gafararsa. Ya ce babu komai. Hakanan Humaira
da ta yi kiranta ta dinga kuka tana neman yafiyarta.
***
Zuwan su Nijar ne yasa koda suka tashi dawowa sai da mazan
suka hada karfi da karfe suka gyarawa Mamin muhalli gami da nema mata Ζ΄ar aikin
da za ta dinga taya ta hidimar girki da ma abinda ba za ta iya ba. Jannat ma
sai da su Mubarak suka yi mata gima sha tara ta arziki. A karshe Raihana ta
fidda sakon da su Anti Maijidda da Humaira suka bayar a ba Mamin na kudade suka
ba ta. Mami ta daga kudaden tana kuka hawayenta na jika takardun. Lallai
ka so naka duniya ta Ζi shi, ka kuma Ζi naka duniya ta so shi. Yau ta ci
arzikin wadanda ta raina a duniyarta. Wannan kadai ya ishe ta ishara. Gani ga
wane ya ishi wane tsoron Allah.
Tammat Bi Hamdulillah!