D’AND’ANO DAGA KUDIRAR ALLAH.
LITTAFIN NAZEEFAH SABO NASHE.
PAID BOOK IDAN KIN SHIRYA
SIYA
TURA KUDIN KAI TSAYE A
ACCOUNT
NUMBERR NAN. 2118666253 UBA
KI TURA
SHAIDAR BIYA TA 08033748387.
Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban
tab’a kusantar wata mace ba?” Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da
sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta “Tabbas
Jaheed jininka don gwajin k’wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne
mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun
tabbatar da Hakan koda Ba’a yi gwajin ba.”
Shiru na tsawon lokaci d’akin ya d’auka kowa da irin tunanin
da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da
k’wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai
tab’a rik’ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d’ansa ne ta yaya
ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai
tab’a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD’i. Mahaifiyar
Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi.
Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K’UDIRAR ALLAH….
K’UDIRAR ALLAH.
Page. 1
NAZEEFAH SABO NASHE.✍π½
08033748387.
******
Idanunsa ya Lumshe a hankali Bayan ya gama kallon fuskarta
da take d’auke da Tsananin farin ciki, da alama sak’on da mahaifinta ya bayar
ta isar masa shine abinda ya saka ta tarin farin ciki da annashuwa.
Bata sani ba shi sak’on yazo masa a hagunce da ta ta
fassarar madadin farin ciki kwatankwacin nata, nasa hankalin tashi ya yi ya
kuma shiga irin wancan yanayin da yake riskar kansa a duk sanda budurwa zata
gaya masa sak’on mahaifinta ya ce ya turo. Ya bu’de tattausan idanunsa masu
tsananin kyau da haiba ya zuba mata su, k’walla ce kwance a saman idanun wanda
k’arfin zuciya da taurin rai yasa ya kasa sakin su su zubo. Namijin gaske ne da
yake iya b’oye rauni da gazawar zuciyarsa a lokuta da dama, duk da matsalar da
yake ciki ya ci
A koka mata koda kuwa kuka ne mai kuwa da kururuwa.
K’addarace mai girman gaske take watangaririya da rayuwarsa, irin k’addarar da
kai tsaye mutum zai ce dama Allah bai haliccesaba matuk’ar bai jajirce akan
doron Imaninsa ba, da sanin cewa Allahn ne dai shine yake jarrabarsa don ya
auna nauyin mizanin sa. Ya gani shin bawansa zai iya yarda da k’addarar har ma
ya rungumeta a yarda ta zo masa. Hawayen da Khairi ta gani cikin idanunsa su
suka k’arya mata gwiwa har nata farin cikin ya zagwanye ya bi iska. Cikin
mabayyanin tashin hankali ta ce “Me ya faru Hubby? Kada dai maganar Abba ce ta
b’ata maka rai baka shirya aurena bane?” Ya girgiza kai yana k’ok’arin togace
tashin hankalinsa ya ce “Na shirya Habibteey, sai dai ke da kan ki tun a farkon
fari na sanar da ke wanene ni? Abinda nake tsoro idan Har ke kin amince kina
tunanin Abba za su amince idan suka yi bincike a kaina suka gano ni ba kowa
bane face d’an mahaukaciya da bata san inda kanta yake ba, balle ta gano waye
ya mata ciki har ta samar dani?” Khairi shiru ta yi zuciyatta itama tana
tsallen tashin hankalin. Tuni ta manta da wannan matsalar ta JAHEED sai yanzu
da ya farkar da ita, tabbas ita ta san waye mahaifinta mutum ne mai zafin gaske
mai kafaffiyar Ak’ida wanda ba’a tab’a tankwara zuciyarsa idan har ya gano
wanene JAHEED ko zata mutu ba zai bari ta aure shi ba, ita kuwa a yarda take
jin soyayyarsa a zuciyarta zata iya aurensa da amincewar mahaifinta ko babu.
Don haka ta saki ajiyar zuciya tana kallon JAHEED cike da
tausayin yanayin k’addararsa da ba laifinsa bane asali ma da za’a tambayeshi
zab’i ba zai yarda yazo duniya ta wannan hanyar ba. Murya cike da rauni ta saki
ajiyar zuciya hawayen da ta kasa b’oyonsu suka fara karakaina a kan k’uncinta
bata san sanda ta kama hannun JAHEED ba ta ce “Ba mai raba
Mu JAHEED ko suna so ko basa so sai na aureka. Da sonka
Allah ya halicceni na tabbata ina jin kai ne maha’din rayuwata, ruwa da iska
ina tare da kai am always your’s.” Ta fa’da tana saka fuskarta a cikin tafin
hannun JAHEED d’in tana sakin kuka mai k’arfin gaske mai saka tausayi a zuciyar
mai sauraro. Shiru JAHEED ya yi yana sauraran kukan nata da yake raunata
zuciyarsa yana jin shima kamar ya saki nasa kukan, sai dai dakiya da k’arfin
zuciyarsa ya hana shi aikata hakan. Madadin hakan wani irin ciwo da bugu
zuciyarsa take yi kamar yarda ta saba a lokuta da dama idan haka ta faru da
shi. Sau hu’du yana neman aure sau hu’dun kuma ana hanasa dalilin rashin asali
da cikakken tushe yana ji yana gani yake rasa abinda zuciyarsa take so da
Muradi. Khairi itace budurwa ta biyar da yaso yana ji kuma a jikinsa wannan
shine zai zama ganin da zai mata na k’arshe. Shikkenan shi haka rayuwarsa ta zo
a juye irin tasa k’addarar kenan mai zafi da wuyar sha’ani. Kalaman Khairin da
take sake kwararo masa mai nuni da tsananin soyayyar da take masa basu k’arfafa
masa gwiwa ba, don suma wa’dancan Matan ba abinda basu ce masa ba k’arshe bisa
tilas suka rabu bai sake jin d’uriyarsu ba.
Ya janye fuskar Khairin daga tafukan hannunsa yana kallon
hawayen da take zubar wa yana jin zafin zubar su kamar dalma a zuciayrsa. “Ki
yi shiru Khairi ni na san tabbas a wannan karan ma banda sa’a, kuma In sha
Allah daga kanki ba zan sake soyayya ba zan yi hak’uri haka Allah ya k’addaro
min.” Kuka ta saka sosai tana sake k’arfafa masa gwiwar ya turo neman aurenta
In sha Allah zata yi addu’a tana ji kuma a jikinta wannan karan Abbanta zai
amince ya ba shi aurenta.” Ya yi shiru yana nazarin idanun Khairin soyayyar
Khairi mai girma ce a zuciyarsa zai iya cewa bai tab’a tsintar kansa a
kwatankwacin soyayya irin ta Khairi ba. So yake mata irin son da ake kira Pure
love, wanda shi da kansa ba zai ce ga dalilin da yasa yake son Khairi ba. Tun
bayan da ya ha’du da ita bai sake samun nutsatstsen barci ba kullum itace a
cikin barcinsa da tunaninsa. Kamar yarda kullum zuciyarsa take cikin fargaba da
rauni akan kada a zo gab’ar da zai rasa Khairi, baya jin a wannan karan zai iya
jurewa. Ya saki ajiyar zuciya yana jan siraran yatsunta ya sake murza zoben sa
da yake hannunta da nata da yake hannunsa wanda suka kira zoben Alk’awari.
Allah yasa mfarkinsu ya zama gaske yau ya gan su a matsayin ma’aurata shi da
Khaireey bai san wace irin godiya zai wa Allah ba, tabbas zai iya yin azimi
sittin don murnar auren Khaireey. “Shikkenan Habibteey ki je gida, zan je na yi
magana da Baffa, za’a turo idan Allah yasa an dace shikkenan idan kuma ba’a
dace ba ina rokonki ki yi hak’uri mu rik’e k’addararmu.” Da sauri Khaireey ta
girgiza kai “No JAHEED I can’t ba zan iya rayuwa ba tare da kai ba JAHEED love.
Idan bai yarda ba mu gudu kawai mu yi auren mu.” JAHEED ya saki murmushi wanda
yake bayyana ciwon da zuciyarsa take masa ya d’aga mata kai kawai ba wai don ya
amince da tunaninta da ya kira shirme ba sai don son ya
Kwantar mata da hankali. Ya ce “Okay maza ki je gida, ki yi
mafarkin JAHEED mafarki mai kyau kin ji Khaireey, ki yi mafarki na ina kissing
those sweetable lips.” Ya fa’da yana k’urawa lab’banta da suke fusgar
hankalinsa ido. Da sauri Khaireey ta runtse idanunta ta fice da Motar da gudu.
JAHEED ya saki raunataccen murmushinsa kafin ya lumshe ido hawayen da yake ta
killacewa suka samu damar silalo masa. Tabbas soyayyar Khaireey daban ce a
zuciyarsa tunda har ya tsiyayar mata da k’walla. Da k’yar ya samu ya ja motarsa
a hankali ya har harabar gidan zuciayrsa na ayyana masa ba mamaki ban kwana ya
yi da Khaireeynsa.
_
Yarda yake tuk’in cikin rashin nutsuwa shi da kansa bai yi
tsammanin zai iya sa gidan da ake rik’onsa lafiya saboda yarda zuciyarsa ta
rasa sukuni ko ka’dan. Mai gadi ya bu’de masa gate ya yi parking a wajen da aka
tanada don ajiye motoci. Nan d’in shine gidansu gidan da tun yana jariri anan
ya taso shi da mahaifiyarsa bai san kowa ba sai mai gidan shi ya ba shi duk
wata kulawa da shi da Uwar gidansa da yake jin ta tamkar mahaifiyarsa tunda ita
ta raineshi har kawo yanzu da ya kai munzalin aure. Ba zai ce baya fuskantar
k’alubale a zamantakewar gidan ba a’a yana samu daga b’angaren Matar gidan ta
biyu dama y’ay’anta gaba d’aya da suka d’au karan tsana suka d’ora masa shi da
mahaifiyarsa da suke tunanin Akwai dalili mai girma da Baffa yasa yake kula da
Mahaukaciyar, duk a zuciyar Baffa bakomai illa son cika umarnin Manzon Allah da
kuma tausayi da jin k’ai irin na duk wani managarcin d’an Adam. Sam Baffa baya
banbanta shi da yaransa na cikinsa k’aunarsa yake kamar y’ay’an da ya tsuguna
ya haifa, idan banda Anty da take kwaza ba Baffan bane ya haifeshi ba wanda zai
gane idan ba fa’da maka aka yi ba.
Ya dad’e cikin motar saboda yarda gabbansa suke cikin rashin
kuzari da raunin zuciya. Kafin ya d’auke kwantacciyar k’walla da take idanunsa
ya saki ajiya zuciya a hankali ya bu’de motar ya fito yana zuro k’afarsa.
Idanunsa suka fa’da cikin na Haidar da ya sakar masa murmushi don nufo motar ya
yi da ya gaji da jiran Jaheed d’in. Haidar tare suka taso shima d’an Umma ne
ita kuma ta rainesu kamar y’an biyu, bata banbanta su ko a wajen kayan sawa har
abada ba zai manta karamci Umma a kansa ba. Haidar ya d’an daki kafa’darsa yana
furta “Mutumin daga ina?” Jaheed ya saki ajiyar zuciya ya ce “Daga wajen
Khaireey.” Murmushi Haidar ya yi yana furta “Na Khaireey ba da kanka a sare,
amma naga mood d’inka is not good me ya faru?” Jaheed ya d’an dube shi kamar ba
zai ce komai ba sai kuma ya tuna yarda suke da Haidar basa iya b’oyewa junansu
damuwa kamar dai y’an biyun zahiri. Ya saki ajiyar zuciya ya ce “Abbanta ya
bani umarnin na fito neman aurenta idan da gaske nake yi.” Haidar shiru ya yi
shima hankalin sa na d’an tashi yana tsoron afkuwar rashin nasara kamar yarda
wa’dancan neman aurarrakin suka dinga lalacewa, an kuma rasa makirin da yake
zuwa dangin Y’an matan ya kwatsa musu asalin Jaheed. Tun lokacin da shi Haidar
ya yi nasa auren Jaheed d’in yake ta walagigin neman aure amma an rasa dacewa
saboda waccan gundumemiyar matsalar. Jaheed ya dubi Haidar da ya lula duniyar
tunani ya ce “Ina ji soyayya ta da Khaireey itama ta zo k’arshe kamar yarda
wa’dancan ma suka wuce
Kamar ba a yi su ba, amma ban tab’a jin haushin rasa budurwa
ba kamar yarda yanzu zuciyata take cike da rauni da k’unci na rasa Khaireey da
zan yi a karo na biyar, Ina son Khaireey Haidar.” Haidar ya ‘dago idanunsa da
suka ka’da suka yi jajir ya zuba akan Jaheed shi d’in zuciyarsa ta raunata
matuk’a ainun saboda tausayin halin da d’an uwansa yake ciki. Tabbas da ace
Najwa ta girma ta isa aure ba abinda zai hana shi aurawa Jaheed, tunda itace
k’anwarsa da suke ciki d’aya da ita yake iko kaf gidan ita ka’dai ce mace a
cikin y’ay’an Umma su biyar, sai dai she is too young shekarunta 14 only. Su
kuma wad’ancan fitsararrun da suke Uba d’aya Nasma Da Najma dama ba a zancensu
don sun raina Jaheed d’in matuk’ar raini sun tsani ko bu’de ido su yi su gan
shi a gidan. Gudun kada ya sake raunata Zuciyar Jaheed d’in sai ya dafa shi. Ya
CE “Kada ka karaya mana Bro, In sha Allah Lokaci yazo da kaima zaka angwance
ina jin hakan a jikina just pray Nima kuma Zan taya ka. Sannan mu samu Baffa mu
sanar masa In sha Allah za’a dace, fatan mu kada Allah ya bawa makirin da yake
zuwa ya rusa maka maganar aure dama a wannan karan.” Jaheed ya d’aga kai yana
furta “Ameen” ba wai don har a zuciyarsa yana saka rai zai samu Khaireey ba sai
dai dole zai bi shawarar Haidar don basu tab’a k’in yiwa juna Biyayya akan
shawara ba.
Daidai lokacin rantsatstisyar motar bak’a wuluk ta shigo
cikin gidan a mugun speed, ga wani ki’da mai k’arfin gaske an ware a cikin
motar. Sauti yake bayarwa sosai. Haidar take ransa ya b’aci don ya san ba kowa
bace sai Najma itace mai wannan banzar d’abi’ar yarinya kamar rainon kafirai,
ba Kuma laifin kowa bane sai na Uwarta data ke d’aure mata k’ugu. Jaheed kuwa
ji ya yi kamar zata tarwatsa kan sa don a rayuwarsa baya son hayaniya shi mutum
ne very cool bai Kuma son shiga shirgin kowa.
Wawan parking ta yi a gefensu, ta fito cikin takun k’asaita
da nuna isa na isassun mata. Idanunta sanye da bak’in shade da ya k’ara mata
rantsatstsen kyan da take alfahari da shi. Ta cikin glass d’in take jifan
Jaheed da wani wulak’antaccen kallo ta isa ta gefensu zata wuce. Murya a ciki
ta ce “Ya Haidar barka da yamma.” A ciki ya amsa tana shirin shigewa ya kira
sunan ta a tsawace, cak ta tsaya ba tare da ta juyo ba duk da suna shakkar Yaya
Haidar ‘din da fa’dansa amma ba zata nuna a gaban mutanen da ta tsana ba. “Ni
ka’dai kika gani a wajen?” Ta juyo a zafafe tana kallon sa kafin ta ce “Kai
ka’dai ne ya wajaba na gaisa da kai.” Mamaki bai bar Haidar ya mata magana ba,
tsananin mamakin gadara da tsaurin idon ta. Kunyar Jaheed ce ma ta kama shi, da
sam bai nuna ya san me suke ba danna wayar sa kawai yake, duk da maganar
yarinyar ta doki dodon kunnensa kuma ta yi masa zafi matuk’a sai dai bisa tilas
ya shanye don ba yau ya fara karb’ar wulak’ancinta da rashin mutuncinta ba ya
Riga ya saba da ita da y’ar uwarta da ma uwarsu gaba d’aya basa ganin k’ima da
mutuncinsa duk da dama shi d’in ya sani a wajen mutane ba shi da wata k’ima
balle daraja irinsu da aka haifa a titi rashin Uba ya kan janyo musu tsana da
wulak’anci daga wajen jama’ar da ba su kai su ba ma balle su taka k’afarsu,
balle ita wannan da yake ganin karanta ya kai tsaiko, a k’ark’ashin Ubanta
yake, cin sa da shansa tun yana zanin goyo Ubanta ne ya d’auke su shi ya samar
masa da nagartaccen ilimin da yake tunk’aho da shi a yanzu. Don haka ba zai damu
ba so samu ne shine zai zama mai gaisheta da nuna ladabi a wajenta abinda suke
so kenan, shi kuma ya kasa musu girman kansa da fa’din ransa da yake jin sa
kamar basarake ya kasa yarda ya amince wa zuciyarsa ya Zauna a taka shi. Ya
yarda shi shege ne mara gata mara galihu amma bai amince shi d’in mara daraja
bane, yana kallon kansa a wani mutum mai daraja ta farko a cikin mutane, don
haka ba zai tab’a k’ask’antar da kan sa ba. Haidar ya saki ajiyar zuciya yana
kallon Jaheed da ko a fuskarsa bai nuna damuwa da abinda Najma ta masa ba,
madadin haka ma wani k’ayataccen murmushi ne kwance a kan kyakykyawar fuskarsa
mai d’auke da zagayyen saje. Cikin sakakkiyar murya ya ce “Yaushe ka ke ganin
ya dace na samu Baffa da maganar?” Haidar ya saki ajiyar zuciya shima ya nuna
bakomai d’in kamar yarda Jaheed ya bagarar ya ce “Ko yau da Magriba sai mu same
shi mu ji abinda zai ce.” Jaheed ya diro daga kan motarsa yana mik’a masa hannu
ya ce “Allah ya kai mu, ka gaisar min da yara na da madam, ace da d’an rigimata
wannan week end Zan zo na kai su park.” Haidar shima murmushin ya yi ya mik’a
masa hannu yana jinjina zuciya irin ta Jaheed mai k’ok’arin nuna komai ba komai
ba duk tsananin b’acin ran da yake ciki ba dai ka gan shi a kan fuskar sa ba,
sau tari har mamakin hakan Haidar yake yi. Ya saki ajiyar zuciya yana fad’awa
motarsa don ya isa gida da wuri don yaga yamma ta yi.
Open this link to
join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/EZyeAwHEGGhJz1pRBmmale
K’UDIRAR ALLAH.
Page. 1
NAZEEFAH SABO NASHE.✍π½
08033748387.
******
Idanunsa ya Lumshe a hankali Bayan ya gama kallon fuskarta
da take d’auke da Tsananin farin ciki, da alama sak’on da mahaifinta ya bayar
ta isar masa shine abinda ya saka ta tarin farin ciki da annashuwa.
Bata sani ba shi sak’on yazo masa a hagunce da ta ta
fassarar madadin farin ciki kwatankwacin nata, nasa hankalin tashi ya yi ya
kuma shiga irin wancan yanayin da yake riskar kansa a duk sanda budurwa zata
gaya masa sak’on mahaifinta ya ce ya turo. Ya bu’de tattausan idanunsa masu
tsananin kyau da haiba ya zuba mata su, k’walla ce kwance a saman idanun wanda
k’arfin zuciya da taurin rai yasa ya kasa sakin su su zubo. Namijin gaske ne da
yake iya b’oye rauni da gazawar zuciyarsa a lokuta da dama, duk da matsalar da
yake ciki ya ci
A koka mata koda kuwa kuka ne mai kuwa da kururuwa.
K’addarace mai girman gaske take watangaririya da rayuwarsa, irin k’addarar da
kai tsaye mutum zai ce dama Allah bai haliccesaba matuk’ar bai jajirce akan
doron Imaninsa ba, da sanin cewa Allahn ne dai shine yake jarrabarsa don ya
auna nauyin mizanin sa. Ya gani shin bawansa zai iya yarda da k’addarar har ma
ya rungumeta a yarda ta zo masa. Hawayen da Khairi ta gani cikin idanunsa su
suka k’arya mata gwiwa har nata farin cikin ya zagwanye ya bi iska. Cikin
mabayyanin tashin hankali ta ce “Me ya faru Hubby? Kada dai maganar Abba ce ta
b’ata maka rai baka shirya aurena bane?” Ya girgiza kai yana k’ok’arin togace
tashin hankalinsa ya ce “Na shirya Habibteey, sai dai ke da kan ki tun a farkon
fari na sanar da ke wanene ni? Abinda nake tsoro idan Har ke kin amince kina
tunanin Abba za su amince idan suka yi bincike a kaina suka gano ni ba kowa
bane face d’an mahaukaciya da bata san inda kanta yake ba, balle ta gano waye
ya mata ciki har ta samar dani?” Khairi shiru ta yi zuciyatta itama tana
tsallen tashin hankalin. Tuni ta manta da wannan matsalar ta JAHEED sai yanzu
da ya farkar da ita, tabbas ita ta san waye mahaifinta mutum ne mai zafin gaske
mai kafaffiyar Ak’ida wanda ba’a tab’a tankwara zuciyarsa idan har ya gano
wanene JAHEED ko zata mutu ba zai bari ta aure shi ba, ita kuwa a yarda take
jin soyayyarsa a zuciyarta zata iya aurensa da amincewar mahaifinta ko babu.
Don haka ta saki ajiyar zuciya tana kallon JAHEED cike da
tausayin yanayin k’addararsa da ba laifinsa bane asali ma da za’a tambayeshi
zab’i ba zai yarda yazo duniya ta wannan hanyar ba. Murya cike da rauni ta saki
ajiyar zuciya hawayen da ta kasa b’oyonsu suka fara karakaina a kan k’uncinta
bata san sanda ta kama hannun JAHEED ba ta ce “Ba mai raba
Mu JAHEED ko suna so ko basa so sai na aureka. Da sonka
Allah ya halicceni na tabbata ina jin kai ne maha’din rayuwata, ruwa da iska
ina tare da kai am always your’s.” Ta fa’da tana saka fuskarta a cikin tafin
hannun JAHEED d’in tana sakin kuka mai k’arfin gaske mai saka tausayi a zuciyar
mai sauraro. Shiru JAHEED ya yi yana sauraran kukan nata da yake raunata
zuciyarsa yana jin shima kamar ya saki nasa kukan, sai dai dakiya da k’arfin
zuciyarsa ya hana shi aikata hakan. Madadin hakan wani irin ciwo da bugu
zuciyarsa take yi kamar yarda ta saba a lokuta da dama idan haka ta faru da
shi. Sau hu’du yana neman aure sau hu’dun kuma ana hanasa dalilin rashin asali
da cikakken tushe yana ji yana gani yake rasa abinda zuciyarsa take so da
Muradi. Khairi itace budurwa ta biyar da yaso yana ji kuma a jikinsa wannan
shine zai zama ganin da zai mata na k’arshe. Shikkenan shi haka rayuwarsa ta zo
a juye irin tasa k’addarar kenan mai zafi da wuyar sha’ani. Kalaman Khairin da
take sake kwararo masa mai nuni da tsananin soyayyar da take masa basu k’arfafa
masa gwiwa ba, don suma wa’dancan Matan ba abinda basu ce masa ba k’arshe bisa
tilas suka rabu bai sake jin d’uriyarsu ba.
Ya janye fuskar Khairin daga tafukan hannunsa yana kallon
hawayen da take zubar wa yana jin zafin zubar su kamar dalma a zuciayrsa. “Ki
yi shiru Khairi ni na san tabbas a wannan karan ma banda sa’a, kuma In sha
Allah daga kanki ba zan sake soyayya ba zan yi hak’uri haka Allah ya k’addaro
min.” Kuka ta saka sosai tana sake k’arfafa masa gwiwar ya turo neman aurenta
In sha Allah zata yi addu’a tana ji kuma a jikinta wannan karan Abbanta zai
amince ya ba shi aurenta.” Ya yi shiru yana nazarin idanun Khairin soyayyar
Khairi mai girma ce a zuciyarsa zai iya cewa bai tab’a tsintar kansa a
kwatankwacin soyayya irin ta Khairi ba. So yake mata irin son da ake kira Pure
love, wanda shi da kansa ba zai ce ga dalilin da yasa yake son Khairi ba. Tun
bayan da ya ha’du da ita bai sake samun nutsatstsen barci ba kullum itace a
cikin barcinsa da tunaninsa. Kamar yarda kullum zuciyarsa take cikin fargaba da
rauni akan kada a zo gab’ar da zai rasa Khairi, baya jin a wannan karan zai iya
jurewa. Ya saki ajiyar zuciya yana jan siraran yatsunta ya sake murza zoben sa
da yake hannunta da nata da yake hannunsa wanda suka kira zoben Alk’awari.
Allah yasa mfarkinsu ya zama gaske yau ya gan su a matsayin ma’aurata shi da
Khaireey bai san wace irin godiya zai wa Allah ba, tabbas zai iya yin azimi
sittin don murnar auren Khaireey. “Shikkenan Habibteey ki je gida, zan je na yi
magana da Baffa, za’a turo idan Allah yasa an dace shikkenan idan kuma ba’a
dace ba ina rokonki ki yi hak’uri mu rik’e k’addararmu.” Da sauri Khaireey ta
girgiza kai “No JAHEED I can’t ba zan iya rayuwa ba tare da kai ba JAHEED love.
Idan bai yarda ba mu gudu kawai mu yi auren mu.” JAHEED ya saki murmushi wanda
yake bayyana ciwon da zuciyarsa take masa ya d’aga mata kai kawai ba wai don ya
amince da tunaninta da ya kira shirme ba sai don son ya
Kwantar mata da hankali. Ya ce “Okay maza ki je gida, ki yi
mafarkin JAHEED mafarki mai kyau kin ji Khaireey, ki yi mafarki na ina kissing
those sweetable lips.” Ya fa’da yana k’urawa lab’banta da suke fusgar
hankalinsa ido. Da sauri Khaireey ta runtse idanunta ta fice da Motar da gudu.
JAHEED ya saki raunataccen murmushinsa kafin ya lumshe ido hawayen da yake ta
killacewa suka samu damar silalo masa. Tabbas soyayyar Khaireey daban ce a
zuciyarsa tunda har ya tsiyayar mata da k’walla. Da k’yar ya samu ya ja motarsa
a hankali ya har harabar gidan zuciayrsa na ayyana masa ba mamaki ban kwana ya
yi da Khaireeynsa.
_
Yarda yake tuk’in cikin rashin nutsuwa shi da kansa bai yi
tsammanin zai iya sa gidan da ake rik’onsa lafiya saboda yarda zuciyarsa ta
rasa sukuni ko ka’dan. Mai gadi ya bu’de masa gate ya yi parking a wajen da aka
tanada don ajiye motoci. Nan d’in shine gidansu gidan da tun yana jariri anan
ya taso shi da mahaifiyarsa bai san kowa ba sai mai gidan shi ya ba shi duk
wata kulawa da shi da Uwar gidansa da yake jin ta tamkar mahaifiyarsa tunda ita
ta raineshi har kawo yanzu da ya kai munzalin aure. Ba zai ce baya fuskantar
k’alubale a zamantakewar gidan ba a’a yana samu daga b’angaren Matar gidan ta
biyu dama y’ay’anta gaba d’aya da suka d’au karan tsana suka d’ora masa shi da
mahaifiyarsa da suke tunanin Akwai dalili mai girma da Baffa yasa yake kula da
Mahaukaciyar, duk a zuciyar Baffa bakomai illa son cika umarnin Manzon Allah da
kuma tausayi da jin k’ai irin na duk wani managarcin d’an Adam. Sam Baffa baya
banbanta shi da yaransa na cikinsa k’aunarsa yake kamar y’ay’an da ya tsuguna
ya haifa, idan banda Anty da take kwaza ba Baffan bane ya haifeshi ba wanda zai
gane idan ba fa’da maka aka yi ba.
Ya dad’e cikin motar saboda yarda gabbansa suke cikin rashin
kuzari da raunin zuciya. Kafin ya d’auke kwantacciyar k’walla da take idanunsa
ya saki ajiya zuciya a hankali ya bu’de motar ya fito yana zuro k’afarsa.
Idanunsa suka fa’da cikin na Haidar da ya sakar masa murmushi don nufo motar ya
yi da ya gaji da jiran Jaheed d’in. Haidar tare suka taso shima d’an Umma ne
ita kuma ta rainesu kamar y’an biyu, bata banbanta su ko a wajen kayan sawa har
abada ba zai manta karamci Umma a kansa ba. Haidar ya d’an daki kafa’darsa yana
furta “Mutumin daga ina?” Jaheed ya saki ajiyar zuciya ya ce “Daga wajen
Khaireey.” Murmushi Haidar ya yi yana furta “Na Khaireey ba da kanka a sare,
amma naga mood d’inka is not good me ya faru?” Jaheed ya d’an dube shi kamar ba
zai ce komai ba sai kuma ya tuna yarda suke da Haidar basa iya b’oyewa junansu
damuwa kamar dai y’an biyun zahiri. Ya saki ajiyar zuciya ya ce “Abbanta ya
bani umarnin na fito neman aurenta idan da gaske nake yi.” Haidar shiru ya yi
shima hankalin sa na d’an tashi yana tsoron afkuwar rashin nasara kamar yarda
wa’dancan neman aurarrakin suka dinga lalacewa, an kuma rasa makirin da yake
zuwa dangin Y’an matan ya kwatsa musu asalin Jaheed. Tun lokacin da shi Haidar
ya yi nasa auren Jaheed d’in yake ta walagigin neman aure amma an rasa dacewa
saboda waccan gundumemiyar matsalar. Jaheed ya dubi Haidar da ya lula duniyar
tunani ya ce “Ina ji soyayya ta da Khaireey itama ta zo k’arshe kamar yarda
wa’dancan ma suka wuce
Kamar ba a yi su ba, amma ban tab’a jin haushin rasa budurwa
ba kamar yarda yanzu zuciyata take cike da rauni da k’unci na rasa Khaireey da
zan yi a karo na biyar, Ina son Khaireey Haidar.” Haidar ya ‘dago idanunsa da
suka ka’da suka yi jajir ya zuba akan Jaheed shi d’in zuciyarsa ta raunata
matuk’a ainun saboda tausayin halin da d’an uwansa yake ciki. Tabbas da ace
Najwa ta girma ta isa aure ba abinda zai hana shi aurawa Jaheed, tunda itace
k’anwarsa da suke ciki d’aya da ita yake iko kaf gidan ita ka’dai ce mace a
cikin y’ay’an Umma su biyar, sai dai she is too young shekarunta 14 only. Su
kuma wad’ancan fitsararrun da suke Uba d’aya Nasma Da Najma dama ba a zancensu
don sun raina Jaheed d’in matuk’ar raini sun tsani ko bu’de ido su yi su gan
shi a gidan. Gudun kada ya sake raunata Zuciyar Jaheed d’in sai ya dafa shi. Ya
CE “Kada ka karaya mana Bro, In sha Allah Lokaci yazo da kaima zaka angwance
ina jin hakan a jikina just pray Nima kuma Zan taya ka. Sannan mu samu Baffa mu
sanar masa In sha Allah za’a dace, fatan mu kada Allah ya bawa makirin da yake
zuwa ya rusa maka maganar aure dama a wannan karan.” Jaheed ya d’aga kai yana
furta “Ameen” ba wai don har a zuciyarsa yana saka rai zai samu Khaireey ba sai
dai dole zai bi shawarar Haidar don basu tab’a k’in yiwa juna Biyayya akan
shawara ba.
Daidai lokacin rantsatstisyar motar bak’a wuluk ta shigo
cikin gidan a mugun speed, ga wani ki’da mai k’arfin gaske an ware a cikin
motar. Sauti yake bayarwa sosai. Haidar take ransa ya b’aci don ya san ba kowa
bace sai Najma itace mai wannan banzar d’abi’ar yarinya kamar rainon kafirai,
ba Kuma laifin kowa bane sai na Uwarta data ke d’aure mata k’ugu. Jaheed kuwa
ji ya yi kamar zata tarwatsa kan sa don a rayuwarsa baya son hayaniya shi mutum
ne very cool bai Kuma son shiga shirgin kowa.
Wawan parking ta yi a gefensu, ta fito cikin takun k’asaita
da nuna isa na isassun mata. Idanunta sanye da bak’in shade da ya k’ara mata
rantsatstsen kyan da take alfahari da shi. Ta cikin glass d’in take jifan
Jaheed da wani wulak’antaccen kallo ta isa ta gefensu zata wuce. Murya a ciki
ta ce “Ya Haidar barka da yamma.” A ciki ya amsa tana shirin shigewa ya kira
sunan ta a tsawace, cak ta tsaya ba tare da ta juyo ba duk da suna shakkar Yaya
Haidar ‘din da fa’dansa amma ba zata nuna a gaban mutanen da ta tsana ba. “Ni
ka’dai kika gani a wajen?” Ta juyo a zafafe tana kallon sa kafin ta ce “Kai
ka’dai ne ya wajaba na gaisa da kai.” Mamaki bai bar Haidar ya mata magana ba,
tsananin mamakin gadara da tsaurin idon ta. Kunyar Jaheed ce ma ta kama shi, da
sam bai nuna ya san me suke ba danna wayar sa kawai yake, duk da maganar
yarinyar ta doki dodon kunnensa kuma ta yi masa zafi matuk’a sai dai bisa tilas
ya shanye don ba yau ya fara karb’ar wulak’ancinta da rashin mutuncinta ba ya
Riga ya saba da ita da y’ar uwarta da ma uwarsu gaba d’aya basa ganin k’ima da
mutuncinsa duk da dama shi d’in ya sani a wajen mutane ba shi da wata k’ima
balle daraja irinsu da aka haifa a titi rashin Uba ya kan janyo musu tsana da
wulak’anci daga wajen jama’ar da ba su kai su ba ma balle su taka k’afarsu,
balle ita wannan da yake ganin karanta ya kai tsaiko, a k’ark’ashin Ubanta
yake, cin sa da shansa tun yana zanin goyo Ubanta ne ya d’auke su shi ya samar
masa da nagartaccen ilimin da yake tunk’aho da shi a yanzu. Don haka ba zai damu
ba so samu ne shine zai zama mai gaisheta da nuna ladabi a wajenta abinda suke
so kenan, shi kuma ya kasa musu girman kansa da fa’din ransa da yake jin sa
kamar basarake ya kasa yarda ya amince wa zuciyarsa ya Zauna a taka shi. Ya
yarda shi shege ne mara gata mara galihu amma bai amince shi d’in mara daraja
bane, yana kallon kansa a wani mutum mai daraja ta farko a cikin mutane, don
haka ba zai tab’a k’ask’antar da kan sa ba. Haidar ya saki ajiyar zuciya yana
kallon Jaheed da ko a fuskarsa bai nuna damuwa da abinda Najma ta masa ba,
madadin haka ma wani k’ayataccen murmushi ne kwance a kan kyakykyawar fuskarsa
mai d’auke da zagayyen saje. Cikin sakakkiyar murya ya ce “Yaushe ka ke ganin
ya dace na samu Baffa da maganar?” Haidar ya saki ajiyar zuciya shima ya nuna
bakomai d’in kamar yarda Jaheed ya bagarar ya ce “Ko yau da Magriba sai mu same
shi mu ji abinda zai ce.” Jaheed ya diro daga kan motarsa yana mik’a masa hannu
ya ce “Allah ya kai mu, ka gaisar min da yara na da madam, ace da d’an rigimata
wannan week end Zan zo na kai su park.” Haidar shima murmushin ya yi ya mik’a
masa hannu yana jinjina zuciya irin ta Jaheed mai k’ok’arin nuna komai ba komai
ba duk tsananin b’acin ran da yake ciki ba dai ka gan shi a kan fuskar sa ba,
sau tari har mamakin hakan Haidar yake yi. Ya saki ajiyar zuciya yana fad’awa
motarsa don ya isa gida da wuri don yaga yamma ta yi.
Open this link to
join my WhatsApp Group: https://
chat.whatsapp.com/.
EZyeAwHEGGhJz1pRBmmale
K’UDIRAR ALLAH
2.
NAZEEFAH SABO NASHE✍π½
08033748387.
Bin motar Haidar ya yi da kallo kafin ya saki sassauk’ar
ajiyar zuciya yana lumshe idonsa wani irin zafi da turiri yake jin zuciyar sa
take yi, duk da k’ok’arin danne b’acin ran da yake yi hakan bai hana bayyanuwar
b’acin ran akan kyakykyawar fuskarsa ba. Tausayin kansa ya sake mama ye shi
kafin ya d’au hanyar da zata sada shi da ainahin cikin Gidan direct.
Faffad’ar haraba ce mai girman gaske fiye da ta wajen da ake
ajiye motoci. Bakomai a harabar sai manyan bishiyu da suka yiwa tsakargidan ado
da inuwa mai k’ayatuwa a idanun mai kallo. Yanayin damuna da ake ciki ya sake
k’awata wajen baka sha’kar komai sai k’amshin tarin bishiyun da suke cikin
harabar lemon tsami guava mango da sauran dangoginsu. Ya sake mai da hankalinsa
kan k’ofar da zata kai shi sashen da Umma take marik’iyarsa inda anan aka
warewa tasa mahaifiyar nata d’akin mai d’auke da parlour da toilet aka kuma
saka mata duk wani abin more rayuwa duk da zamantowarta mara hankali bai hanata
tsaftace d’akin ba idan ka shiga zata zaka yi mai cikakken hankali ce
mamallakin sashen.
Umma da take zaune a babban parlourn da ya raba sashenta da
na Mahaifiyar Jaheed d’in ta bi shi da kallo murmushin kan fuskarta na sake
yalwata ta ce “Ka dawo kenan Mujaheed?” Shi d’in ma murmushin da kai tsaye za’a
kira na k’arfin hali ya saki yana d’aga mata kai kafin ya rusuna ya gaisheta.
Ta amsa masa cike da kulawa saboda yarda take jin Jaheed d’in kamar ita ta
durk’usa ta haifesa bata banbance soyayyar sa da ta nata y’ay’an data tsuguna
ta haifesu abu d’aya ta sani Ba ita ta yi nak’udarsa da shayar da shi amma duk
wata hidima da Uwa take wa d’anta ita ta yiwa Jaheed, shayarwa ce dai a hakan a
haukar Uwarsa ita ta shayar da shi, abin mamaki yarda take ba shi kulawa ba
zaka ce k’wak’walwarta da motsi ba duk da akwai wani keb’antaccen sirri da ita
ka’dai ce ta sani.
Jaheed ya dubi Najwa yana fa’din “Najee samo min ruwa.” Da
sauri ta mik’e don a rayuwarta tana girmama lamarin Jaheed da kuma duk wata
hidima data danganceshi, yarda take son sa bata jin tana son nata jinin haka.
Ruwan mai sanyi ta d’auko a fridge d’in da yake dinning area d’in Umma. Ta kawo
masa a k’aramin tray. Bai bi ta kan cup d’in da take mik’a masa ba ya b’alle
murfin ruwan ya fara kwankwa’da. Sai da ya shanye tas kamar ruwan ne zai tafi
da bak’in cikin da ya masa dafifi a zuciyarsa sannan ya ajiye robar yana sakin
huci a hankali. Umma murmushi ta saki ganin yarda yake wayancewa wajen son
kawar da b’acin ran da ya kasa b’oyuwa a fuskarsa ba duk da k’ok’arin danne shi
da yake. Ta fi kowa sanin Jaheed da halayensa kaf idan yana cikin farin ciki ta
sani kamar yarda idan yana cikin b’acin rai duk k’ok’arin sa da son danne
b’acin ransa hakan baya b’oyuwa gareta a k’wayar idanunsa take banbance halin
da yake ciki, don haka cikin raunin murya ta dubeshi tana furta “Sun ce ka turo
ko?” Da sauri Jaheed ya d’ago yana kallonta cikin mamakin jin abinda ta ce, ya
yi mamaki k’warai da gaske da har ta gano abinda yake ciki, kamar ya ce mata ya
aka yi kika gane sai dai ya ja bakinsa ya tsuke yana duban T.V ha’de da ‘d’aga
kai a hankali muryarsa ta kasa b’oye b’acin ran da yake ciki saboda yarda ta
raunana ya ce “Sun ce Umma.” Sakin ajiyar zuciya ta yi tana furta “Kada ka damu
wannan karan za’a dace In sha Allah, abin buk’ata ka dage da addu’a.” Shiru ya
yi yana jin sauk’in nauyin da k’irjinsa ya yi, kalamin Ummansa ya sauk’ak’a
masa fargabar sa da b’acin ransa. Umma ta dubi Najwa ta ce “Je ki zubo masa
abinci daga ganin wannan idon kana jin yunwa.” Murmushi ya saki a hankali yana
jin dad’in kulawar da Umma take ba shi har yanzu ganinsa take kamar yaro, ko
don bai yi aure bane oho, ko kuma tausayawa irin rayuwar da ya taso a ciki take
shine bai sani ba. “Ka ci abinci ka je ka samu Nene ka gaya mata.” Ya
D’aya kai kawai yana mamakin duk sanda irin wannan zata faru
sai Umman ta umarceshi da ya gayawa mahaifiyarsa ta kan ce “Ko kallonka ta yi
bata maka addu’a ba zai da’da’da maka balle idan ka furta addu’ar itama zata
maimaita Allah kuma Zai amsa In sha Allah.” Jaheed murmushi kawai ya saki yana
amsar Abincin da Najwa ta zubo masa a plate ganin favorite food d’insa ne
Alkubus da miyar taushe yasa ya saki murmushi gefe guda kuma kunun aya ne.
Zamewa ya yi ya zauna a kan carpet don yafi ganewa ya ci abinci k’afar sa a
tank’washe kuma yafi cin abinci da hannu idan ba’a bak’on waje ba shi yasa sau
tari yafi ganewa cin abinci a falon Umma inda zai bararraje ya tsoma hannunsa
ya ci son ransa. Ya wanke hannun A wash hand basin da yake dinning area d’in
sannan ya dawo ya fara cin abincin yana fa’din “Madalla da Umman mu mai da’din
tuwo.” Murmushi Umma ta yi ta ce “Ka hango Alkhbus ba dole Ai ka fara
santi, dama sai kacewa Khairin ta dage ta iya Alkubus
mayensa zata aura.” Murmushi ya saki a zuciyarsa yana fatan Allah ya amsa
addu’ar Umma yau ya gan shi ga shi ga Khairi a gida d’aya matsayin ma’aurata da
yafi kowa murna a duniya don ya tabbata a ranar ba na biyunsa wajen farin ciki,
bai san kuma irin godiyar da zai wa Allah ba gani yake ko kwana ya yi yana
sallah godiyar ta yi ka’dan. Sai da ya cinye abincin tas ya kuma taune
tantak’washin sannan ya yi Hamdala yana duban Najwa da take kallonsa k’asa k’asa, haka kawai Jaheed yake
burgeta duk wani abu da ya yi burgeta yake yi, sau tari tana hasasho Mijin da
zata aura ya zama mai halaye kamanni da komai irin na Jaheed, tun kan ta san ba
d’an uwanta bane da suke ciki d’aya balle yanzu data fara girma sai take auna
Jaheed d’in a matsayin Mijin aurenta tun bayan data san ba maharraminta bane.
Jaheed ya dubeta yana furta “Zo ki kwashe kwanukan nan, kullum
Baki da aiki sai kallo ya kamata Umma ta fara saka ki aiki
Wallahi kada ki tashi baki iya komai ba.” D’an mitsitsin bakinta ta turo kafin
cikin shagwab’a ta ce “Kai Ya Jaheed Wallahi ina aiki yau fa ni na yi alkubus
d’in nan.” Wani irin waro ido ya yi yana kallonta ba Najwa ba hatta Umma sai da
ya sata dariya yana furta “Lie Lie ya mik’e kafin ya kai mata rank’washi a kai
ya ce “Mai k’arya dai d’an wuta.” Ta dubi Umma tana furta “Umma gaya masa don
Allah ba ni na yi ba?” Umma tana murmushi ta ce “Gobe ya tsaya ki yi a gabansa
sai ya tabbatar.” Girgiza kai ya yi yana fa’din “Ah to kin dace tunda kin gado
hannun Umma.” Ya fad’a yana tura k’ofar da zata kai shi Inda parlorn Nenensa
yake. Najwa zata bi shi Umma ta saka baki ta kirata sau tari ita take hanata binsa musamman a irin wannan lokacin
da yake matuk’ar buk’atar d’umin mahaifiyarsa ko dai bata magantu ba idan ya
gaya mata damuwarsa Zai ji sauk’i cikin k’irjinsa, don haka ta hanata bin sa
Najwan ta dawo tana turo bakinta gaba na jin haushin rashin binsa duk da sonta
da hakan don tana son kullum ta dinga ganin Nenen musamman idan suna tare da
Jaheed sai ta dinga jin wani irin farin ciki data kan rasa dalili.
A zaune ya tarar da ita tsaf da ita cikin shigar doguwar
rigar atamfa jikinta sanye da hijab kamar kullum. Ba abinda zai da ka gane tana
hauka sai idanunta idan ta zazzaro maka su sai kuma yanayin yarda take mayar
maka da maganar da duk ka furta sai ta maimaita maka kamar mai karatu. Tana
ganinsa ta d’ago a fisge tana kallonsa fuskarta na d’an sakin murmushi ka’dan
mai bayyana matsayin ta na mahaukaciya. Jaheed murmushi ya saki ya zauna a
gefenta kamar yarda ya saba yana kama hannuwanta ya matsa su ka’dan ya ce “Yau
Nene ba kya kallo?” Sake maimaita masa abinda ya ce ta yi. Jaheed ya saki
ajiyar zuciya yana fatan ranar da Ummansa zata samu waraka ko Zata fa’di inda
asalinta da danginta suke ko da wannan ya tsira zai gode wa Allah idan ma bai
samu dangin mahaifin nasa ba, fiye da yanzu da bai san kowa nasa ba yake
watagangaririya a rayuwa. Idanu ya sauke cikin na Nenen data kafa masa nata
idon kamar mai son gano wani abu a cikin idon nasa. Shiru zuwa wani lokaci suna
kallon kallo kafin Jaheed ya sauke nasa idon yana furta “Ki yi min addu’a Nene
sun ce na turo.” Ta sake maimaita abinda ya ce Jaheed ya d’ago yana kallonta
yana mamakin yanayin damuwa da ya gani tattare da ita kamar yarda ta saba a duk
sanda zai zo mata da makamanciyar magana irin wannan mamakin hakan yake sosai
tunda ya san bata da hankalin da Zata dinga feeling farin ciki ko bak’in ciki a
cikin ranta, bai san me yake janyo mata wannan yanayin ba mai bayyana zallar
damuwar da take ciki. Idan ba idanunsa ne ya gaya masa ba har tarin k’walla ya
gano kwance cikin k’wayar idanunta. Bai ji komai a ransa ba tunda ya san Nenen
ba abinda ta sani irin maimaita magana na ta salon haukan kenan da tun tashinsa
a haka ya santa. “Allah ya baka abinda kake so Jaheed Allah yasa su baka
aurenta Jaheed.” Hakan kuwa da yake so ta furta hakan ta maimaita masa ya saki
murmushi har lotsawar hab’arsa tana sake k’aruwa, itama murmushin ta saki tata
lotsawar hab’ar na sake bayyyana wanda wannan ne kawai abinda suke
kamanceceniya da shi banda haka ba ta inda Jaheed yake kama da ita komansu
mabanbanci ne. Kwanciya ya yi a cinyarta yana sakin ajiyar zuciya a hankali
kafin ya d’au hannun Nenen ya saka a kansa a duk sanda yake cikin damuwa wannan
d’in yana dag cikin abinda yake kawar masa da Rabin damuwarsa. Nenen ta shiga
yamutsa masa Sumar kansa tsawon lokaci kafin ya d’ago yana mayar da k’wallar
idanunsa da suke zuba ba shiri, a gaban Nene kawai yake iya sakar k’wallarsa ta
zuba bai damu ba banda haka ba wanda zai ce ya san k’wallarsa tun bayan
girmansa sai Nenne da yake iya bayyana rauninsa kai tsaye a wajenta. Bai juyo
ya kalleta ba da itama zai ga tata k’wallar da take zuba ba k’akkautawa saka
kansa kawai ya yi ya fice daga d’akin. Sai da ya tsaya a corridor ya kawar da
duk wata fuska ta damuwa sannan ya saka glass d’in idanunsa bak’i wuluk don
bata son Umma taga idanun da suka canja sannan ya fice da sauri ya ji da’di
sosai da bai samu Umman da Najee a babban parlourn ba.
Yana fita Nene ta kifa kanta tana wani irin kuka mai tsuma
zuciya, kukan tausayin Jaheed yake da yarda da sanin ta ta b’oye masa waye shi?
Sannan ta d’auki haukan k’arya ta d’orawa kanta duk don gudun kada a tambayeta
asalinta da na Jaheed d’in. Tana tausayin d’anta kamar yarda sau tari zuciyarta
take son ta bayyana masa asalinsa sai dai tsoron bala’in da sanin asalin nasa
zai haifar yana togaceta daga aikata hakan, zamanta a matsayin mahaukaciya da
rashin sanin asalin Jaheed shi ya fiye musu alheri daga ita har Jaheed d’in
fiye da bayyanar gaskiyar lamarin, tabbas abinda ta b’oye shine alheri garesu
gaba d’aya daga ita har duk wani masoyin ta. Da sauri ta mik’e tana dannawa
k’ofar d’akin mukulli kafin ta juyo ta fa’da toilet da azama ta d’auro alwala.
Tana fitowa sallaya ta shimfi’da ta fuskanci alk’ibla cikin nutsuwa ta tada
sallah. Rako’i da yawa ta yi kafin cikin sujjadar k’arshe ta fashe da kuka tana
furta “Ya Allah ka zama gatanmu ni da Jaheed a rayuwa, Allah ka bashi mata ta
gari ka gajarta masa wahalar rayuwar neman aure.
To fa! Wai me Nenne take b’oyewa ne? Menene asalin Jaheed da
rashin bayyana hakan yafi alheri garesu fiye da bayyana hakan? Daga ji dai kun
san tafiyar mai zafi ce akwai rikita rikita ta gasken gaske yanzu aka fara.
Shin kin biya kuwa 500 kacal dai kada ta gagareki hajiya a yi wannan tafiyar ba
ke. Kai tsaya ki biya ta asusun banki kamar haka 2118666253 UBA
Sai ki tura shaidar biya ta wannan numberr 08033748387.
Vip 1k (Za’a tura musu kai tsaye har gida.)
Nagode sosai
JIKAR NASHE CE✍π½
K’UDIRAR ALLAH.
3.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
___________
Doguwar addu’a Nene ta ja sosai kafin ta d’ago kanta a
hankali idanunta na zubar da k’walla, ta mik’e zuwa gefen gadon. Zuciyarta take
jin tana harba mata da sauri tuno abinda ya wakana a rayuwarta wanda girman
k’addarar zata iya cewa ya wuce duk tunanin mai tunani.
Zugum ta yi a gefen gadon hannayenta dafe da k’uncinta, tana
nazarin yarda rayuwa take gudu kamar yau ta zo gidan da jaririnta Jaheed a
hannu ga shi har ya girma ana maganar aurensa ba tare da Ubansa ya san da
cikinsa ba balle ya san da shi. To ta ina zai san da shi bayan ita kanta ba
zata ce ga fuskar Uban ba, bata tab’a saninsa ba balle ta san sanda ya
kusanceta abu guda ta sani cikin nasa ne kamar yarda ta ji a bakin wasu mutane
da ba zata ce su waye ba. Ta lumshe ido zuciyarta na cigaba da dukan tara-tara
ko sunan Mutumin ta tuna sai ta ji tashin hankalinta ya hauhawa balle kai tsaye
ta danganta shi da Uban Jaheed. Motsin da ta ji yana kusanto d’akinta ne ya
sata saurin mayar da fuskar haukanta ta yarda ba zaka tab’a zaton ita d’in mai
hankali ba ce. Najwa ce ta shigo da kwanon abincinta
Na dare flask mai kyau d’an madaidaici sai dogon jug da aka
zubo mata kunun aya a ciki. Murmushi take sakar mata da alama shak’uwa a
tsakaninsu ta zauna daf da ita tana furta “Allah yasa dai Nene ta yi sallah?”
Maimaita maganar Najwan ta yi ha’de da waftar kwanon hannunta kai tsaye ta fara
cin abincin cikin alamu na rashin nutsuwa. Najwa tana kallonta ta wafce kwanon
Kafin cikin kwanciyar murya ta ce “Baki fa’da ba?” Itama ta
maimaita Najwa ta ce Bismillahirrahmanirraheem.” Itama ta maimaita sannan
Najwan ta mik’a mata kwanon abincin bayan ta saka ta wanke hannunta a y’ar
robar da ta shigo da ita.
Sosai ta ci abincin kafin ta sha kunun ayar. Najwa ta kunna
mata kallo suka zauna suna kallon sau tari a irin wannan lokacin Najwa ce take
zame mata abokiyar hira yarinyar ta d’auko nagarta da kyawun halayen iyayenta.
Bata raina na gaba da ita sam sab’anin su Najma. Suna zaune suna kallon Najwa
na tsefe mata kanta.
π¬π¬~~Kamar yarda Haidar ya yi alk’awari bayan
an idar da Sallahr magriba da kansa ya ja Jaheed zuwa wajen Baffa don gaya masa
ance Jaheed d’in ya turo. Shiru Baffa ya yi bayan jin mai ya kawo su, tashin
hankalin da yake zuciyarsa bai b’uya a kan fuskarsa ba duk da k’ok’arin aikata
hakan da ya yi. Har wata zufa ce take zubo masa. Shiru ya bak’unci wajen kowa
da nazarin da yake a ransa. B’angaren Jaheed tausayin kansa ne ya kama shi
ganin kamar ba zai nasara ba a yarda alamun Baffan Suka nuna. Tsawon mintuna
kafin Baffa ya d’ago yana sakin ajiyar zuciya ya ce “Za’a je In sha Allah, Ina
fatan wannan karan ya zamo na k’arshe da zamu je neman aure idan ba su baka ba
In sha Allah a cikin zuri’ata zan baka Mata.” Gaban Jaheed ya wani irin bugawa
tsoro ya d’an shige shi ba don komai ba sai don ya san tunda Baffa ya ce haka
ba kowa yake nufi a cikin zuri’artasa ba sai Najma ko Nasma su ne y’an mata
Najwa bata isa aure ba idan kuwa haka ne akwai babbar matsala shin Baffa bai
san tsanar da yaran suka masa bane, ba kuma sa ganinsa da gashi sai dai zai ji
kunya k’warai da gaske ba zai iya Ingice kyautar Baffan nasa ba. Mutumin da
shine jigon rayuwarsa, nakamashin dukkan wasu nasarori da ya cimma a rayuwa.
“Zamu je gobe In sha Allah bayan sallahr magriba sai ka bani numberr mahaifin
yarinyar na sanar masa.” D’aga kai kawai Jaheed ya yi yana fatan wannan karan
ya dace da auren Khairi kafin Baffan ya gingimo masa auren Najma ko Nasma da
suke masa kallon wulak’antaccen Bawa mara galihu. Jiki a sanyaye suka mik’e
suka bar wajen Baffan, shima nasa jikin a sanyaye ya bi bayan su da kallo
tausayin Jaheed d’in yana sake mamayar zuciyarsa, tabbas da yana da iko da ya
mayar da Jaheed jininsa d’ansa na halak malak ba d’an rik’o ba.
Sallama Jaheed ya yi da Haidar ya fa’da nasu b’angaren inda
d’akunan samarin gidan suke. Gwiwarsa a salub’e take kamar yarda gangar jikinsa
ta zama salaf ba k’warin ko sisi. Yana karya kwanar lungun da zai sada shi da
B’angarensu suka kusa gabza karo da ita tana ta sauri zata isa wajen
saurayinta. Wani irin banzan tsaki ta ja masa kafin ta zabga masa harara cikin
mayalwatan idanun ta ta kuma tsartar da miyau tana furta “Nonsense.” Cak
Jaheed ya tsaya yana jin kamar ya zabga mata mari sai dai
fuskar Baffa yake ganowa kawai a cikin tata fuskar don haka ya kasa samun
nutsuwar marin nata ya cije leb’ensa kawai ya wuce yana jin sanda ta sake
furucin “D’AN MAHAUKACIYA KAWAI.” Da d’an k’arfi ta yi maganar don haka maganar
ta shiga cikin kunnuwansa direct. Yana jure dukkan wulak’ancinta amma baya bari
ta k’etare iyaka ta tab’a masa mahaifiya don haka bai san sanda ya isa gabanta
ba cikin taku d’aya ya yiwa hannunta wani irin fincika ya ha’data da bango.
Idanunsa tuni suka sauya kala don tsananin tashin hankali k’ok’arin k’wacewa
take amma hakan ya gagara saboda rik’on da ya yi mata mai tsauri ne. Cikin
dakushewar murya ya ce “Repeat your words.” Runtse idanunta ta yi tana jin wani
irin bugu a k’irjinta da gaske ta razana da kalamansa sai dai girman kanta da
tasirin idanunta ya hanata barin ta bayyana hakan akan fuskarta ta jure zafin
rik’on tana kallon cikin idanunsa ta sake furta “K’arya na yi? Ba mahaukaci…..”
kafin ta k’arasa ya kai yatsa ya murje leb’enta da k’arfin gaske har sai da ta
saki fitsari a wando bai
Kuma saki leb’en ba ya furta “Gwara ni tawa Uwar mahaukaciya
ce, taki Uwar kuwa mushirika ce waccece ta fi illa?” Ya wancakalar da ita gefe
yana murza hannunsa ya ce “Kika sake furta kalmar b’atanci ga mahaifyata zaki
ga abinda zan miki Wallahi, I won’t tolerate this kind of nonsense anymore.” Ya
wuce ya barta a tsaye tana bin bayansa da kallo cikin tsananin mamakin tsaurin
idanunsa. Huci ta saki da k’arfin gaske tana jin zuciyarta na sake rub’anya
tsanarsa a fili ta furta “Mu zuba ni da kai.” Ta gyara rolling d’inta tana jin
haushin jam bakin da ya goge mata duk da tsayin lokacin da ta d’auka wajen
shafa shi duk don ta yiwa gwarzon zuciyarta kwalliya sai ga shi mutumin data
tsana yau har da rab’ar jikinta ya kuma
Mutstsike jan bakin. Ga mayen k’amshin turarensa da ya zauna
ra’dam a hancinta.
Ko da ta dawo daga zancen ranta a b’ace ta fa’da sassan su
tana shiga kuma direct d’akinsu ta fa’da ta shige toilet kayan jikinta da suka
mak’ale da k’amshin turarensa ta fara zare wa da sauri tana cillasu cikin
washing machine, kafin ta sakarwa kanta shower da k’arfin gaske. Ta hau
mitstsika jikinta. Takaicinta d’aya yarda jikinta ya ha’du da nasa ji take da
da hali da ta cire fatar bakinta da hannunsa ya tab’a idan ba tunaninta bane ya
gaya mata k’arya sai take ganin kamar k’irjinsa ma ya tab’a nata. Da sauri
Najma ta runtse ido tana furta “Allah ya isa.” Wasu hawaye na bak’in ciki suna
zubowa daga idanunta. Ta dad’e tsaye cikin shower d’in kafin ta hak’ura ta zura
rigar wanka ta fice tana tsane gashinta da yake d’igar da ruwa. Kayan barci
kawai ta zura wando iya gwiwa da y’ar b’ingilar riga da armless ta fice
parlourn dama sam bata saba suturce jikinta ba. A cikin kujerar da ke kallon
Mahmeey ta zauna fuskarta a tsume tana duban Nasma da itama ta zuba mata nata
idanun. Mahmeey ta ce “Wai me ya faru kin fita da walwala kin dawo rai a b’ace?
Ba yau kika ce zaki gaya masa ya turo ba?” Mayar da gashin kanta baya ta yi
tana furta “Na gaya masa Mahmeey ya kuma yi murna.” Mahmeey ta ce “To me ya
b’ata miki rai?” Tsaki ta ja sosai kafin ta ce “Ni da wannan banzan ne, Mahmeey
na tsane shi Wallahi bana son na bu’de ido na gansa a gidan nan, yau don na
kira uwarsa mahaukaciya shine wai ya kalleni yana furta gwara shi Uwarsa
mahaukaciya ba mushirka ba ki ji fa,har ya samu courage d’in gaya min haka?
Wallahi duk Baffa ne ya jawo mana da ya daidaita matsayin sa da namu shi yasa
yake ganin mu kai d’aya da shi, da ya mayar da shi driver Ai da ba haka ba.”
Fuskar Mahmeey a ha’de take dubanta ta ce “Ni ya cewa Mushirika? Cabd’i jam,
amma kuwa wallahi ya d’ebo ruwan dafa kansa, ba kuma mamaki a wannan karan
k’arshen zamansa ne yazo a gidan nan zai san ya shigo gonata, ki yi shirunki
wannan fa’dan ba naki bane nawa ne.” Najma ta saki ajiyar zuciya tana furta
“Wallahi Mahmeey wannan karan kada ki bar shi ya samu nutsuwa ko ka’dan ko
sharri ne ki masa ya bar gidan nan.” Mahmeey ta cije bakinta kawai ba tare da
ta furta komai ba ta ce “Yanzu za’a fara wasan ki bar ni da shi.”
_________
Kashegari kuwa Baffa ya isa k’ofar gidan Alhaji Ahmad Jari.
Mahaifin Khairiyya shi da Aminansa guda biyu da k’annensa guda biya. Jin wanda
yake nemansa yasa Alhaji Ahmad Jari fitowa da wuri don dama ya shiryawa zuwansu
tun kuma da Khairi ta gaya masa d’an Alhaji Ilu Mai fata ne yake sonta ya ji
da’di a ransa don ba wanda bai san Baffa da irin alherinsa a gari ba don haka
dole ka so ha’da zuri’a da shi. Ba wai don arziki ba sai don zamowarsa mutum
Karimi mai nagartattun halaye ababen so da koyi.
A babban sitroom d’insa ya masa masauki, suka zube bisa
faffad’ar daddumar da take parlourn cikin farin ciki da walwala suke amsa
gaisuwar juna fuskarsu d’auke da mad’aukakin murmushi. Aka gaisa sosai kafin a
fara abinda ya tarasu. Baffa ne ya ce “Ka san me yake tafe da mu?” Alhaji Ahmad
ya ce “Sosai kuwa, Khairi ta gaya min d’an wajenka ne yake son ta da aure na yi
matuk’ar farin ciki da jin haka don ha’da zuri’a da kai abin a Ai ne a kuma yi
murna. Don haka babu ja na ba shi auren Khairi.” Baffa ya yi shiru yana sake
d’agowa tsoro da fargaba suna shigarsa lokaci guda baya son ya gayawa mahaifin
Khairi ba shi ya haifi Jaheed ba, yana kuma gudun b’oye masa gudun kada ya ji
labari daga baya ya d’auke shi mutumin banza, yanayin da yaga farin cikin Ahmad
Jari ya san zai karya
Masa gwiwa a lokacin da ya ji ba shine mahaifin Jaheed ba,
asalima ba a san waye mahaifinsa ba. Murya a raunane ya ce “Amma akwai abinda
nake so na gaya maka, ina son Kuma ka saka a ranka k’addararsa ce a haka kuma
bawa ba ya wuce k’addararsa shima da za’a nemi shawararsa ba zai so ya zamo a
haka ba zai zab’i kyakykyawar rayuwa irin ta kowa, maganar aure ba wasa bane
don haka ba’a son k’unbiya k’unbiya a cikinta Ba ni na haifi Jaheed ba……….
(Kin shirya mallakar naki? To hanzarta biya kafin free pages
su k’are 500 ne kacal special kuma 1K (a tura miki har gida)
Tura kai tsaye ta wannan account d’in 2118666253 UBA
Sai ki tura shaidar biya ta wannan numberr 08033748387.
Nagode.
JIKAR NASHE CE✍π½
KUDIRAR ALLAH.
4.
NAZEEFAH SABO NASHE
08033748387.
MIKIYA WRITERS ASSOCIATION.
…….
Baffa ya cigaba da bayani da furta “Tabbas iya gaskiyar
kenan sai dai ina rok’onka ka zama mai adalci kada ka hana shi auren y’arka
dalilin laifin da ba nasa ba… tsintar mahaifiyarsa na yi da shi a hannunta kuma
bata da hankalin da za’a gane shin Jaheed d’in halattacen d’a ne ko wanda
k’addara ta fa’dawa….” Wani irin kallo Alhaji Ahmad yake jifansa da shi, ya
manta da duk wani girma na baffan murya a shak’e ya dakatar da Baffan da furta
“Ba zan ba shi auren y’ata ba Wallahi, ai kai ma kana da y’ay’a ka je ka bashi
mana idan har da gaske Imanin naka ya kai har haka, ta yaya zan d’auki y’ata in
Bawa yaron da ba a san asalinsa ba, bayan rashin asali ma
mahaifiyarsa ma bata da cikakken hankalin da nan gaba za’a gane wanene asalin
Uban yaron idan ma akwai shi?
Mahaukaciya kowa yana iya saduwa da ita a lokacin da yaga
dama kaga kuwa maganar asali babu ita, don haka am sorry to say ba zan ba shi
auren y’a ba.”
Shiru Baffa ya yi hankalinsa a tashe ransa kuma ya jagule
jin abinda Alhaji Ahmad ya ce. Sakin ajiyar zuciya kawai ya yi ba tare da ya
sake furta komai ba ya mik’e a zafafe zuciyarsa na sake k’arfafa masa ya
aiwatar da shawarar da take ba shi. Abokan tafiyarsa ma
Nasu jikin a salub’e suka
Bi bayansa, ba su ga laifin Alhaji Ahmad ba ba kowa ne zai
iya bawa Jaheed auren y’a ba sai mai Imanin gaske, idan kuma ba b’ata suka yi
ba wannan shine karo na biyar da suke zuwa nemawa Jaheed d’in aure ana
Hana shi kuma ko su ne abinda zasu aikata d’in kenan. Tunda
suka fara tafiya a mota Baffa ya kasa furta komai ba abinda zuciyarsa take tuna
masa sai maganar Alhaji Ahmad da ya ce shi mai ya hana ya bashi auren y’arsa.
Wannan ya zauna daram a zuciyarsa yana ganin kuma
Lokaci ya yi da ya kamata ya gwada k’wanjinsa koda kuwa
hakan na nufin abubuwa da
Dama.
Yarda Jaheed da Haidar suka ga jikin Baffa a sanyaye duk da
k’ok’arin b’oye musu da yake hakan ya sanyaya gwiwarsu hankalin Jaheed ya sake
tashi matuk’a ainun fargabar da yake ciki ta sake hauhawa, tun Baffan bai ce
komai ba ya bawa kansa amsa da kansa. BA NASARA. Shine abinda zuciyarsa take
jaddada masa don haka bai buk’aci jin cewar Baffan ba ya mik’e jikinsa a
salub’e zai bar wajen. Baffan bai hana shi ba don shi kansa ba shi da k’warin
gwiwar da zai masa bayani. Haidar ya ha’diye wani abu da ya tsaya masa a wuya
tausayin Jaheed na sake kama shi kafin ya kalli Baffa ya ce “Babu nasara ko
Baffa?” D’aga masa kai ya yi kawai ya kuma yi masa alama da ya wuce kawai baya
son surutu.
A cikin gida Umma ma ta kasa zaune ta kasa tsaye so yake
kawai Baffa ya shigo ya sanar da ita wannan karan an dace. Najwa ma shiga d’ari
fita d’ari sai ta shigo ta ce Umma Baffan ya shigo?” Umma ta girgiza mata kai
tana furta “Bai shigo ba Najee ina ji a jikina wannan karan ma ba nasara.”
Najee ta zauna turus a kujera tana fatan kada Maganar Umma ta tabbata tausayin
Jaheed ne a ranta sosai tana jin da ta isa aure ba abinda zai hana ta ce
Baffanta ya aura mata Jaheed.
Ba gani yake ba don haka duk inda ya samu yake jefar
k’afarsa cikin tashin hankali da rashin nutsuwar zuciya, k’afafunsa sun yi
rauni sosai kamar yarda zuciyarsa ta raunata ji ya yi kawai ya yi karo da abu
da sauri ya ja baya yana runtse idanunsa sanin laifinsa ne yasa ya ce “Am
sorry.” Wani irin tsaki ta sakar masa wanda ya fusata zuciyarsa ba shiri abinka
da wanda zuciyar tasa take a fusace. “Sorry for your self d’an mahaukaciya
kawai ko haukan Uwartaka ya fara shafarka ne don yanayin ka ya nuna mahaukaci
sabon kam….” Kafin ta kai k’arashen zancen ta ji an zabga mata kyakykyawan
marin da ya d’auke ganinta na wani d’an lokaci Jaheed ya d’ago raunatattun
idanunsa yana kallon Wanda ya yi marin Baffa ya gani a tsaye ransa a matuk’ar
b’ace har huci yake ya nuna Najma da yatsa ya ce “Ashe baki da tarbiyya Najma
kalar rashin arzikin da kuke masa kenan? Daman ina jin labari sai ga shi yau na
gani da ido na…” muryarsa har rawa take don b’acin rai kamar yarda k’walla ta
taru a k’asan idanunsa yana mamakin ace wai y’arsa ta cikinsa itace take irin
wannan bak’in halin kamar rainon sabon gari. “Kalleshi ki ba shi hak’uri kuma
ina tabbatar miki zan baki mamaki Wallahi.” Ganin yarda zuciyar Baffan take a
harzik’e yasa ta kalli Jaheed cikin rashin dad’in rai da rashin sukuni ta ce
“Ka yi hak’uri” kalmar da ta fa’deta cikin jin haushi da kuma sake k’ullatar
Jaheed a zuciyarta ta ayyana ko mu da’de ko mu jima sai ta rama marin da yasa
Baffa ya yi mata. Baffa ya zabga mata harara kafin ya ja hannun Jaheed suka
shige daman biyo sahunsa ya yi ganin yarda yake tafiya kamar zai kifa sai ya
tarar da Najma na masa wannan tijarar. Najma ta bi bayan su da mugun kallo
kafin ta datse leb’enta tana furta mu je zuwa shege wulak’antaccen bawa.
Baffa ya zaunar da shi a babban falon su na samari yana
kallonsa cike da tausayawa ya ce “Baba son ka sakawa kanka damuwa Jaheed, in
dai maganr aure ce ina son ka sakawa ranka wannan karan matsalarka ta zo
k’arshe da ikon Allah, ka sani ko wani bawa da irin k’addararsa kuma Allah yana
jarraba bawa ne don ya gwada mizanin Imaninsa In sha Allah nan gaba zaka yi
dariya zaka yi farin ciki ina son ka jure ka daure ba wai don Ubangiji baya
sonka ne ya yi yo ka a haka ba, ba mamaki akwai hikima da aya da Allah yake son
ya nuna da hakan so nake ka jure ka sakawa kanka Jarimta kamar yarda ka saba
kada ka karya zuciyarka ka sawa kanka ciwo a banza a wofi.” Shiru Jaheed ya yi
sai dai wannan karan ya kasa rik’e hawayensa tuni hawayen suka fara zuba ba
kakkautawa jikinsa har rawa yake ga wani zazzafan zazzab’i da ya rufeshi lokaci
guda. Baffa tsoro ya kamashi da sauri ya kira likita yana tsoron kada ciwo mai
girma ya kama Jaheed d’in. Kafin zuwan likitan jikin Jaheed ya sake rikicewa
kakkarwa kawai yake. Baffa ya rufeshi da bargo yana zubar da hawaye yana fatan
Jaheed d’in ya samu lafiya don ya samu damar aiwatar da burinsa da kuma
k’udirin da yake zuciyarsa cikin lokaci k’ank’ani.
Ganin Jaheed d’in yana shirin sume wa yasa ya kalli Sadik ya
ce “Maza shiga gida ka kira Ummanka ka ce tazo ina nan Boys quaters.” Sadik ya
fita a guje don isar da sak’on ya bar Baffa na sake danna kiran likitan don ya
gaya masa ya yi saurin zuwa akwai gagarumar matsala.
Umma hankalinta tashe ta zunduma hijabinta ta fito a guje
Najee na bayanta itama nata hankalin a tashe. Jin abinda Sadik ya ce wai Ya
Jaheed ya suma. Nene na tsaye a bakin k’ofarta ta ji kuma abinda aka ce wannan
karan ta manta da haukan ta ta fita da sauri tana fatan kada wani abu ya samu
Jaheed d’in. Najwa na juyo ta ganta a bayansu don haka ta dawo ta ja hannunta
suka nufi Boys quaters d’in. Tsoron tonuwar asirinta yasa bayan sun isa Boys
quaters d’in ta mayar da asalin fuskarta ta hauka tana dubansu d’aya bayan
d’aya. Kan Jaheed na saman k’afar Baffa yana shafa masa ruwa idanunsa a k’afe
suke. Salati Umma tasa tana furta me ya faru da shi Baffa?” Hannu ya d’aga mata
idanunsa akan na Nenne da take tsaye nata idanun a waje tana addu’a a
zuciyarta. “Matsala aka samu sun hana shi auren da muka je nema masa abinda ya
jawo masa shiga halin da yake ciki kenan.” Umma ta ce Hasbunallah. Ji suka yi
itama Nenne ta ce Hasbunallah ta maimaita abinda Umma ta ce ba kuma tunanin
komai ta dawo ta zauna a kusa da Jaheed d’in idanunta ta zube a kansa ko
kiftawa bata yi. A zahiri fuskar haukace a tare da ita sai dai a ba’dini tsoron
rasa Jaheed shine abinda yake girgiza mata zuciya kada shekarun da ta d’auka
tana hauka don cikar wani burinta ya zama a banza. Ashe ba zata d’au fansar
zaluncin da aka mata ba? Ashe ba zata ga ranar da zata sada Jaheed da
mahaifinsa ba ta kuma sanar da shi jininsa ne kamar yarda ta baro abokin
haihuwarsa wato Hussaininsa a can don ya zame mata shaida ko don nan gaba. Can
ta baro shi bata san a wace rayuwa yake ba bata sani ba Mahaifinsa ya karb’eshi
a matsayin d’a ko kuma ya yi watangaririya da rayuwarsa? Ko kuma ma ya mutu?
Kullum da tunanin da take barci ta tashi da kenan.. tausayin yaranta guda biyu
gwara Jaheed yana tara da ita amma Hussaininsa fa da ta bari a k’ofar Fada
cikin dukan ruwan sama? Ya rayu? Ya mutu? Shine abinda bata sani ba, ta san dai
ta rubuta takarda da zata nuna shi d’in Jinin Sarkin gabas ne ta saka a cikin
kayansa bayan ta gaya musu ta wa d’anta suna da Muhammad Murad! Ta kuma sanar
da su shi d’in Jinin Sarkin Gabas ne ba tare da Mahaifin su ya san da cikinsu
ba ko kuma ya tab’a ganin Uwarsu ko da kuwa a cikin mafarki balle a farke!
Shigowar likita ce yasa ta farka daga wancan tunanin da ta
tafi lokaci guda ta sauke idanunta tana matsawa daga kusa da Jaheed d’in ha’de
da zare idanunta gudun fallasuwar sirrinta a zuciyarta take addu’ar Allah ya
bawa Jaheed lafiya wata rana ta sada shi da danginsa koda hakan na nufin
k’arshen rayuwarta ne.
Aune aunen likita ya tabbatar da raunin Zuciyar Jaheed da
hauhawar jininsa don haka ya masa allurai masu k’arfi da zasu samar masa da
nutsuwa ya kuma buk’aci a bar shi ya samu hutun In sha Allah everything will be
alright. Ya fa’da yana kallon Baffan. Ganin barci mai nauyi ya d’aukeshi yasa
suka fice daga d’akin. Jikinsu a sanyaye da fatan samuwar lafiyar Jaheed d’in.
Ranar Juma’a ne duk hakan ta faru a ranar kuma bayan an
sakko daga babban masallachi Baffan ya buk’aci mutane su tsaya zasu taya shi
d’aura auren d’ansa. Aka kuwa tsaya cikin dandazon jama’ar Baffan ya mik’awa
waliyyin amaryar Jaheed sadakinsa ha’de da bada Umarnin a d’aura auren…….
To fa!
Ko wa Baffa ya aurawa Jaheed a cikin y’ay’ansa Najma? Nasma?
Ko yarinya Najwa?
Ina jiran amsar ku…
JIKAR NASHE✍π½
Don biyan littafin nan kai tsaye danna numberr account d’in
nan
2118666253 UBA don free pages ya kusa k’arewa. Tafiyar dai
mai nisan zango ce kamar yarda rikici da soyayyar da take cikin littafin sun
girmama.
Ina tsoron kada a yi babu ke hanzarta biya ki danno min
shaidar biya ta wannan numberr 08033748387.
JIKAR NASHE TAKU CE!
KUDIRAR ALLAH..
Page 5.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
Tuni mai sanarwa ya fara kwararato a loud speaker yana sanar
da AN DAURA AUREN AISHA ILU MAI FATA WATO NAJMA DA MUHAMMAD MUJAHEED MAI FATA.
Ras gaban Haidar da yake waje ya fa’di yana tunanin anya kuwa Baffa ya san me
ya aikata? Ya san k’iyayyar da ke tsakanin Najma da Jaheed kuwa kiyayyar da
take jin kamar ta soke shi da wuk’a ta huta da ganinsa, da Baffa ya nemi
shawararsa da kai tsaye zai gaya masa ya ba shi Najwa sai ya raineta a gidansa.
Ya ciji yatsa tausayin Jaheed yana kama shi irin tozarci da rashin mutuncin da
Najma zata masa a duk sanda ta ji labarin an aura masa ita. Ya saki ajiyar
zuciya kawai yana fatan Allah yasa hakan ya zama alheri garesu baki d’aya.
Cikin gidan basu san me yake faruwa ba, kamar yarda labari
bai isar musu ba. Jaheed na cikin d’akinsa a kwance duk da jikin da sauk’i sai
dai har yanzu zuciyarsa ba da’di ji yake banda k’arfin Imanin da yake togaceshi
daga aikata kisa da ba abinda zai hana shi kashe kansa ya huta da wannan
takaicin duniyar da yake ciki. A kai a kai yake ganin missed call d’in Khairi
sai dai ya kasa d’agawa a duk sanda kuma zai ga missed call d’inta sai ya ji
hankalinsa ya ninka na baya tashi. Hawaye yake zubar wa sosai kamar yarda
ra’da’din zuciyarsa yake sake rub’anya. Ba zai iya irga adadin kiran ba kamar
yarda itama Khairin bata gaji da kiran nasa ba da tura masa text messages mai
bayyana tashin hankalin da take ciki ba. Bai bu’de message d’in ba saboda ya
san duk abinda message d’in ya k’unsa ba zai wuce bayyana rashin nutsuwa da
tashin hankalin da zuciyarta take ciki ba, kamar yarda tasa ma take ciki.
Gidan tsit sakamakon masallachin juma’a r da jama’ar gidan
da hadiman gidan suka tafi. Don haka zuciyarsa ta sake samun damar zurfafa da
tunanin. Da k’yar ya mik’e ya shiga wanka don ya san a irin wannan lokacin
Baffan baya amsar uzirin kowa na k’in zaman cikin parlournsa. Don haka ya daure
ya fita daga part d’in samarin zuwa na Baffa sanye cikin doguwar rigar
jallabiya fara sol data sake fito da fuskarsa data zama fayau alamun rashin
lafiya kwance cikin kyakykyawar idaniyarsa.
A kuma lokacin Baffa da shi da ahalinsa su Haidar da
k’annensa da ma hadiman gidan suka dawo gidan. Fuskarsu d’auke da murmushi mai
bayyana asalin murnar da zuk’ata suke ciki, idan ka d’auke Haidar da tasa
zuciyar take cike da raunin tausayawa Mujaheed na auren da aka aura masa ba
tare da shirinsa ba, da ace Najma wata mutuniyar kirki ce da sai ya ce abokinsa
ya yi dace k’warai da kyakykyawar mace ta nunawa da kerewa sa’a. Sai dai Najman
Kyawun d’an miciji gareta.
A babban falon gidan Baffa ya zube inda anan duka ahalin
gidan aka saba taruwa duk ranar juma’a a ci abinci a kuma yi wasa da dariya
kasancewar Baffan mutum ne mai barkwanci a wasu lokutan idan yana jin nisha’di.
Aka ta shigo da coolers na abinci masu kyau da inganci wad’anda daga ganinsu ka
san an lashe mak’udan ku’di wajen siyensu.
Bata Abincin Baffa yake ba don haka hankalinsa gaba ‘d’aya
bai kai kan abincin ba balle ya ga yarda Umma ta tsarashi Alkubus ne da Masa
sai aka musu peppe soup na kaza dagargajajjiya sai zob’o da ya sha kayan
k’amshi da fura mai sanyi a gefe da ta sha zuma. Burin Baffa ya tara su ya
sanar da su abin alherin da yake ganin shi ya k’ulla. Don haka da k’yar ya
hak’urcewa zuciyarsa aka gama cin abincin aka kwashe kwanukan tas kafin a yi
addu’a aka shafa sannan Baffan ya yi gyaran murya ya yi sallamar data saka kowa
da yake wajen ya tattaro hankalinsa da nutsuwarsa kan Baffan. Kowa ya ga
yanayin fuskarsa ya san wani abu ne mai mahimmanci zai fa’da don haka suma suka
sanya nutsuwa a zuk’atansu da kan fuskokinsu. Baffa ya kalli Najee ya ce “Maza
ki kira min Nenne don abin ya shafe ta.” Gaban Jaheed ya fa’di jin abinda
Baffan ya ce ya fara addu’ar Allah yasa ba wani lamari mai girma bane yasa
Baffan ya buk’aci ganin Nennen a irin wannan lokacin don ba kasafai Nennen ta
fiye son shiga taron mutane ba.
Nenne a zaune saman sallayar take hannunta d’auke da carbi
tana ja. Sanin cewa ba wanda zai shigo a irin wannan lokacin yasa tana cikin
nutsuwarta. Najee ta tura k’ofar tana sakin sallama, sallamar ta tsaya mata a
mak’oshi ganin Nennen zaune cikin nutsuwa akan Sajjada tana rik’e da carbi.
Nennen ma a firgice ta kalli Najee ta rasa kuma yarda zata yi ta riki’de ta
koma mahaukaciyarta a fuskar zahiri. Najee ta shigo cikin d’akin tana sake
mutstsike idanun ta don tabbatar da zahirin abinda ta gani. Da sauri Nenne ta
aro tunanin dole ta sanyawa zuciyarta da wani irin sauri ta fara jan Carbin
tana nuna alamun hauka a tattare da ita. Najee ta dubeta kafin ta saki ajiyar
zuciya ganin da alama Nenen bata san abinda take ba ba mamaki yanayin haukan
yau da sallah yazo mata. Ta mik’a mata hannu tana furta “Mu je Baffa na son
ganinki.” Nene ta maimaita kafin ta mik’e ta bi bayan Najeen tana sake waro
idonta kamar mahaukaciyar gaske suka nufi Babban parlourn Baffan da yake
harabar gidan sai dai yana da k’ofa ta cikin sashensa da yake cikin gidan.
Baffa cikin nutsuwa ya nunawa Najwa kusa da Umma ya ce
“Zaunar da ita.” Sannan ya gyara zama ya na furta “Dalili ne mai girman gaske
yasa na taraku anan. Albishir d’in da zan muku ina kuma mai farin cikin furta
muku a yau burin da na da’de da shi cikin zuciyata ya cika, zo nan Najma.”
Najma da gabanta ya wani irin fa’duwa ba tare da ta san dalili ba ta mik’e
jikinta na rawa ta isa gaban mahaifinta da ya ke kallonta kamar yau ya fara
ganinta. Hannu yasa ya jata kusa da shi azuciyarsa yana fatan Allah yasa ta
amince da k’addarar auren da ta k’ullu tsakaninta da Jaheed kada ta bujire
masa. Dafa kanta ya yi yana fa’din “D’ago Najma ki gaya min wanene ni?”
Tambayar ce ta mata banbarakwai don haka ta rasa amsar da zata ba shi illa
ha’diye wani kakkauran yawu da ta yi, ta san koma wane lamari abin mai girma ne
kuma ba mamaki ita ya shafa. “Ki yi magana ma.” Muryarta na rawa ta furta “Kai
Babana ne?” “Kin amince da hakan?” Ta d’aga kanta wannan karan cikin rauni. Ya
saki ajiyar zuciya yana furta “Ina da iko da ke ko bani da shi?” Kai tsaye ta
furta “Kana da shi Baffa.” “Alhamdulillah ya fa’da yana sakin kanta ha’de da
zura hannu a aljihunsa ya zaro ku’di bandir biyu yana mik’a mata, hannunta na
rawa ta saka ta amshi ku’din hannu bibbiyu tana tunanin ku’din menene sai ta ji
amsar daga bakin Baffa cikin kakkaurar murya yana furta “Alhamdulillah yau na
cika umarnin Ubangiji na aurar da ke ga Mijin da ya dace wannan shine
sadakinki, ki shirya wani watan In sha Allah zaki tare a gidansa zaki yi azimi
na zab’a miki Jaheed a matsayin Mijin aurenki……” d’if ji da ganin wasu da dama
daga cikin jama’ar parlourn ya d’auke na wuncin gadi. Jaheed ne farko sai Najma
data kasa tantance abinda Baffan ya ce don tuni ta manta a duniyar da take da
alama suman zaune ta yi. Sai Najwa da ta ji jikinta ya fara rawa jin a yau Wai
Jaheed da take mafarki a matsayin Mijin aure shi ya auri Najma ba ita ba.
Mahmeey kuwa tashin hankalinta ya fi k’arfin kwatance kamar yarda na Nene ya
kasa b’oyuwa jin wai mara kunyar yarinyar data mugun tsanarta take kuma mata
rashin kunya son ranta a gidan itace a matsayin Matar Jaheed sam ba irin matar
da take masa Fata ba kenan. Umma kanta wannan ha’din bai mata ba da kuma Baffan
ya yi shawara da ita da ta gaya masa Najee ce ta dace da Jaheed ba Najma ba.
Mahmeey ta mik’e cikin tashin hankali tana kallon Baffa cikin gatsali ta ce
“Amma dai Isma’il a mafarki ka d’aura auren nan ko? Don in dai ni na haifi
Najma to sunan auren nan haramtacce a yanzu ba nan gaba ba wallahi sai ya sakar
min y’a………..
A yi hak’uri ina busy biki ya sa kwana biyu ban yi typing ba
yanzu ma daure wa na yi na muku….
JIKAR NASHE✍π½
KUDIRAR ALLAH.
Page 6.
NAZEEFAH SABO NASHE.
Baffa shiru ya yi duk da yarda yake jin zuciyarsa na
matuk’ar zafafa da jin rad’ad’in furucin Mahmeey idan har ya ce zai yi wata
maganar ba zata zamo mai kyau ba, don haka ya rufe idonsa kawai yana sauraran
kausasan kalaman da suke sake tafasa masa zuciya. Bata fasa fa’dar duk kalmar
da tazo bakinta ba, game da Nene da Jaheed. “Ka rasa wanda zaka aurawa y’ata
sai b’aragurbi wanda baa san asali da tushensa d’an mahaukaciyar da ka tsinto a
hanya, d’an da tabbas ba shi da suna da ya wuce shege to wallahil azeem sai ya
sakar min y’ata koda hakan na nufin komai ma.” Baffa sai a lokacin ya d’ago
yana kallonta idanunsa suna bayyana wutar masifar da zuciyarsa take ciki. “Kika
sake wani abin ya samu auren nan ki k’addara a bakin naki auren….” Daga haka ya
mik’e ya kewayeta ya wuce don idan har ya cigaba da zama zata k’arasa kunyata
shi a gaban jama’ar da suke ganin kima da mutuncinsa. Duk da dai a yanzun ma ba
abinda ya yi saura. Tana ganin ya wuce ta juyo a fusace tana kallon Jaheed “Na
fa’da maka ka sakar min y’a tun kafin ka yi aikin da ka sani don Wallahi ba ta
yarda zan yarda na amince na ha’da jini da d’an mahaukaciya ba.” Runtse
idanunsa Jaheed ya yi yana saurarar dafin kalamanta da suke kamar za su huda
masa zuciya saboda tsananin zafinsu. Ganin lamarin Mahmeeyn k’ara ta’azzara
yasa Umma mik’ewa cikin b’acin rai ta ja hannun Nene da take zaune kamar mutum
mutumi tsananin tafasar da zuciyarta take ciki kuwa Allah ne ka’dai ya sani a
wannan lokacin ji take kamar ta fasa musu sirrin da take aikin kudundunewa shekaru
da shekaru. Umma tana jin sanda ta saki ajiyar zuciya mai nauyin gaske sai dai
bata cikin yanayin da zata gane mai ya janyowa Nenen ajiyar zuciyar. Jaheed ma
ganin sun fita ya mik’e yana jin kamar ya kifa don jirin da yake d’ibarsa. Lura
da haka yasa Haidar saurin mik’ewa ya rungumeshi ta gefe don kada ya fa’di.
Mahmeey ta bi su da wani mugun kallo kafin ta isa wajen Najma da take zaune
kamar mutum mutumi da alama mutuwar zaune ta yi ko nace suman zaune. Don
Mahmeey tana tab’a ta ta yi baya ta fa’di Mahmeey ta saka salati da kuka lokaci
guda tana furta Shikkenan Isma’il Ka kashe min y’a burinka ya cika dama duk
gidan nan y’ay’a na ka sakawa ido.” Bai ma san me take ba don yana can cikin
d’akinsa zuciyarsa da ransa a jagule ji yake kamar ya fito ya zabga mata saki
uku. Ruwa ta d’ebo ta watsa mata sosai a fuska sai a lokacin ta kawo wani
gwauran Numfashi tana kallon Mahmeey ta ce “Allah yasa mafarki nake Mahmeey ba
gaske ba, idan gaske ne wallahi zan iya
kashe kai na…” Mahmeey ta yi saurin rufe mata baki kafin ta ja hannunta
tana furta “Mu je Najwa ki k’addara mafarkin ki ke don wannan auren sunansa
wasa Wallahi ko zan yi yawo tsirara ba zan bar auren nan ba sai na lallata
shi.” Kuka Najma ta fashe da shi sosai sanin cewa ba mafarkin take ba wato ta
tabbata dai an d’aura mata aure da mutumin da tafi tsana tab’ akwai tashin
hankali kenan.
****
Umma kuwa Suna fita direct sashenta ta wuce hannunta rik’e
da Nene da take ta kakkarwa Umman tana jin yarda jikinta yake b’ari bata kawo
komai a ranta ba sai tunanin ko hayaniyar da aka yi ne ya tsorata ta.
Ta shige da ita d’akinta zaunar da ita ta yi gefen gado
kafin ta rufa mata bargo tana furta “Ki yi barci Nenne In sha Allah bakomai.”
Da zata lura Nenne wannan karan bata amsa mata maganar ba ba ta maimaita kamar
yarda ta saba ba lumshe idanunta kawai ta yi don da gaske tana buk’atar hutun
itama ba kuma ta buk’atar a hanata nutsuwa zuciyarta take buk’ata da aiwatar da
shegen tunanin da ya zame mata jiki ta Yaya cikin d’an Sarkin gabas ya shiga
jikinta ba tare da ita ko Sarkin sun tab’a ganin juna a zahiri ba? Me ya faru
ne? Ta fara tunano sanda lamarin ya faru kamar Majigi haka ya fara yawo a
kwakwalwarta……..
************
Shekaru 29 da suka wuce…..
__________________________
Wani d’aki ne mai matuk’ar duhu da rashin wadatacciyar iska, a cikin d’akin Nene ce a zaune da
k’aton cikin haihuwa ko yau ko gobe, tsawon watanninta takwas a cikin d’akin
tun bayan bayyanar cikin jikinta da kai tsaye zata kira shi CIKIN KADDARA KO
CIKIN KUDIRAR ALLAH. Tuni ta saba da zaman d’akin don ta tabbatarwa kanta
zamanta cikin d’akin shine kwanciyar hankalinta fiye da bayyanar ta cikin
mutane. Bata san dalili ba a duk sanda ta kalli cikin sai wani tsoro da firgici
sun shiga zuciyarta, tsoro take ji irin tsoron da yake jijjiga k’wakwalwa gani
take a duk sanda ta haihu a masarautar sunan kanta fillalle don ga duk wanda ya
ji labarin jinin sarki ta haifa D’an Sarki na fari ne a jikinta wanda ita da
kanta tana tsoron bayyana hakan ga mutane duk da ta san Cikinta halastaccen
ciki ne da ko shi kansa Sarkin bai san da shi ba, ta yaya ma zai san da shi
alhali bai san da ita kanta Uwar cikin a doron k’asa ba, bai tab’a ganinta ido
da ido ba a zahiri bata sani ba ko a cikin mafarki, kamar yarda ita ma lamarin yake gareta kamar
almara ko kai tsaye ta kira shi Mafarkin. Da wani baki zata gayawa Sarkin
d’ansa Halastaccen d’a ne ba shege ba kamar yarda ta san mutane da dama za su
yi hasashe. Ta yaya ma zai yarda da halaccinsa tunda ba wanda ya d’aura mata
aure da shi? Me ya kaita? Tabbas ta san idan ta bayyana kanta ,tabbas shi zai zama tsanin tafiyar ta lahira. Duk da
ita kanta dole ce ta saka ta aikata hakan da kuma barazanar d’aukar ranta.
Ta runste ido tana sakin wata zafaffiyar ajiyar zuciya ita
gata k’addara ta kaita ga samun cikin d’an Sarkin bisa tursasawar Mutum guda da
kai tsaye za’a iya kiransa mai son zuciyarsa ko kuma mai son zuciyarta, don
takamaimai ta rasa a wani jinsi zata saka mahaluk’in da ya jefata cikin wannan
sark’ak’iyar da babu mai fitar da ita sai Allah, Mace ce ko Namiji waye kuma a
cikin masarautar? Abinda har kullum take wa kanta tambaya kenan tun bayan
samuwar cikin nata, ba tare da sanin shi Kansa mai martaban ba, ta yaya ma
cikin ya shiga shine abinda ta kasa sani ta hanyar ha’da shimfid’a ma’ana
kusanta tsakanin Miji da Mata ko kuma ta wani lamarin can daban da Allah ne
ka’dai ya barwa kansa sani, bata sani ba ba kuma ta san hanyar da zata bi ta
sani d’in ba.
Abu d’aya ta sani a daren da komai ma ya farun ta tsinci
kanta a wani killataccen d’aki mai kyawun gaske wanda zata iya cewa ba tab’a
ganin irinsa ba ko da a cikin fina finai. Tana kwance ta ji kamar shigowar
mutane suna magana k’asa k’asa da alamar farin ciki a cikin muryar tasu duk da
ta kasa banbance muryar tasu tunda sun bu’da ta sun kuma kaurarata inda duk
masifar ka ba zaka iya shaida mamallakin muryar ba ko da kuwa ka masa farin
sani balle a ce baka san shi ba. Aka haske ta da fitila mai tsananin haske
kafin cikin bu’dewar murya mai sanye da bak’ak’en kayan sink’if ya fara magana,
“Burin mu ya cika mun gama namu aikin, abinda za mu jira yanzu shine bayyanar
cikin a jikinta idan aka dace sai mu jira haihuwarta kafin mu k’wace jaririn
ita kuma mu salwantar da rayuwarta. D’aya daga ciki ya ce “Wannan shine abinda
ya dace da ita, an kuma umarcemu kada mu sake ta gudu kada mu barta a haske ma
balle ta samu damar guduwa da zarar ta haihu kuma sunanta gawa don gudun
tonuwar asirin mu.
Wannan shine abinda ya tayar mata da hankali tunda duk
maganganun nasu sun yi su ne a cukurku’de ba kuma su bata wata k’ofa da zata
gane dalilinsu na aikata hakan ba. Abu d’aya ta sani an tirsasa ta samun cikin
ne aka kuma tsareta aka killace a wannan bak’in d’akin tun bayyanar cikin aka
kuma saka manyan fadawa marasa Imani su tsareta su killaceta ba kuma za’a
saketa ba har sai bayan ta haife abinda ke cikinta sannan a kuma k’wace d’an
ita kuma a koreta bayan an haukatar da ita ko kuma a kasheta kamar yarda ta ji
masu bak’ak’en kayan suna fa’da Hauka zata iya warkewa su Kuma basa son ta samu
sauk’i ta tona musu asiri gwara kawai idan ta cika musu burinsu su kasheta, ta
san za su iya tunda bata da wani gata iyayenta bayi ne da aka siyesu suke bauta
shekara da shekaru bata san asalin su ba
idan ma akwai zuwa yanzu ta san sun k’are tunda yak’i aka yi ya ci garin hakan
yasa Iyayenta suka zama ganimar yak’i mamallakinsu kuma ya zo ya siyar da su a
wannan masarauta mai cike da d’imbin tarihi.
Duk wannan maganganun ta ji su ne a daren da aka gark’ameta
a d’akin. Bayan kwana biyu matar mai bak’in kaya ta kawo ziyara d’akin bata
santa ba don bata bari taga fuskarta ba har ila yau ta kasa tantance muryarta
don muryar tana fita a kaurare ne saboda bata san a san wacece ita, duka tana
ji ta bada umarni. Abu d’aya ta sani koma wacece tana son cikin ne tana kuma
muradinsa ba don ta cutar da shi ba sai don cika wani burinta a kansa, ta
fuskanci haka ne ta hanyar abinci mai kyau da gina jiki da ake bata wanda ake
son duk masu ciki sun ci, a duk kuma bayan satittika akwai likitan da ake sawa
yazo ya duba lafiyarta da abinda yake cikin. D’akin ne dai a duk daren duniya
ake kashe fitilun cikinsa daga waje switch d’in fitilun yake don haka idan suka
gark’ameta bata da ikon sake ganin gaske sai kuma washegari ta inda suke da
tabbacin ko Karen hauka ne ya cijeta ba zata fita da rana ba tunda ta san da
zarar ta aikata hakan kai tsaye zata amsa sunan GAWA a cikin k’urataccen
lokaci. Mutane na biyu kuwa da suke zuwa su ma ta lura suna buk’atar cikin sai
dai ko misk’ala zarratin babu tausayi da imani a tare da su abinda ta lura kowa
da abinda yake so game da ita ba kuma su san suna tarayya wajen son cikin su
dukkansu ba kamar yarda alamu suka nuna Mutanen farko ba su san mutane na biyu
sun san da ita ba kowa bulayi yake cikin duhu da kuma k’wak’war son cikin.
A lissafin su a yanzu cikin nata ya isa haihuwa don haka aka
sake tsaurara matakan tsaro a bakin d’akin, ba wanda ya san da ita a ciki
saboda girman masarautar can a gefen masarautar aka killaceta. Ganin hasken da
ya gauraye d’akin yasa ta san safiya ta yi idan kuma ba safiya ba ce ta yi
tabbas masu kawo mata ziyara ne, gabanta ya fa’di duk da basu kasance masu
cutarwa a gareta ba amma maganar kisan ta girgiza hankalinta shi yasa a duk
sanda ta gansu take tsintar kanta cikin wani yanayi mai bayyana tsagwaron
tashin hankalin da zuciyarta take ciki. Aka turo jibgegiyar k’ofa mai tsawon
gaske wacce aka d’aure ta tamau da jibegegiyar sark’a don ta itace ma da sun
bar kayarsu a bu’de don ta san ko Karen hauka ne ya cijeta bata isa ta tsallake
umarninsu ba idan ba so take su yi gunduwa gunduwa da namanta ba, don kowa ya
san Tarihin masarautar Sarkin Gabas bai fiye Zafafawa rayuwa kamar yarda
wad’anda suke kewaye da shi suka zama
Mugaye na gasken gaske, suka kuma mayar da ran bayi ba a
bakin komai ba su kashe wanda suke so a lokacin da suka ga dama da son ran
Sarkin ko ba son ransa don shi dai kawai zaune yake a kan kujerar mulki amma
don ya ci gadonta kuma a k’aidar garin duk wanda ya ci gadon kujera daga Ubansa
babban d’a shi ake bawa mulki, hakan yasa ake wata irin rayuwa a masarautar
kowa ya zama mugun kansa. Shi yake mulki amma a b’angaren gudanarwa mulki ya
zama d’an kallo don shakulatun b’angaro suke da mulkinnasa su ci zarafi da keta
Haddin duk wanda suke so.
Aka turo k’ofar da k’arfi, hakan yasa da sauri ta yi k’asa
da kanta don basu bata damar kallonsu ba, ko kuma don ta saba a haka dama suke
a gidan sarautar wasu mutane ne su marasa galihu da basu isa su yi iko ko da da
yatsansu ba sai abinda aka zartar a kansu.
Takun suka shiga yi mai cike da firgitarwa da razanarwa
k’amshin turarensu mai k’arfin gaske da ko ba a fa’dawa mutum ya san mai tsada
ne ya cigaba da samun muhalli a cikin d’akin a duk sanda suka shigo sai d’akin
ya yi kwanaki yana zuba wannan mayataccen k’amshin.
Zama suka yi a saman kujera su biyu ne dai kamar yarda suka
saba zuwa, sai wata likita da take sunk’ife cikin nata bak’in kayan baka ganin
komai a jikinta har fuskarta. Cikin tausasawar kalami dkamar ba wad’anda suke
son cutar da ita ba suka bata umarnin kwanciya a kan gado don likitan ta mata
awo, saboda a cikin d’akin har Scanner machine na duba yaro akwai. Likitan ta
fara aikinta su kuma suka kafawa scanner d’in ido ta inda tas suke hango
jaririn a cikin mahaifiyarsa yana ta wutsilniya da alama mai lafiya ne kuma
namijin da suke fata, gefe guda kuma wani dunk’ulallen abu suke gani a cikin
nata da suka kasa gane menene. D’aya daga cikin mutanen suka ce “Abin da aka
fata ya samu, burin Uwargijiya zai cika ga yaro Masha Allah kyakykyawa da shi.”
Na kusa da shi ya kalli likitan yana furta “Zuwa wani lokaci za’a yi tiyatar a
cire yaron ita kuma daga nan ka san yarda zaki mana da ita Uwargijiya dai ta
gaya miki bata son ko yatsanta a bari so take ana zaro Babyn a aika da ita
barzahu ta yarda ba wani balli da zai tashi daga baya.” Doctor ta saki murmushi
tana fa’din “Ai haka za a aikata kamar yarda ta ce don har na tanadi Allurar da
zan mata da zarar na gama mata theatre d’in, dole ne cika burin Uwargijiya.”
Suka shek’e da dariya ba tare sun damu da ita ba duk da sun san tana ji sanin
cewa baiwa ce ba abinda za ta iya yi yasa suka saki jiki suke fa’dar komai a
gabanta.
Aka umarceta ta mik’e ta zauna sannan aka turo wani kwando
gabanta mai cike da abin sha masu k’ara
jini da kuzari. Tashin hankalin da take ciki bai hanata ci ba don ta san bata
isa ta ce ba zata cin ba, ko da kuwa idan ta ci za tayi amansa bata da wannan
damar. Ta ci sosai aka kuma bata tatacciyar madarar shanu mai d’umi ta sha
kafin su fice su barta a d’akin cikin gigitaccen tashin hankali. A tsorace take
a tsorace da kalaminsu da kai tsaye yake nuna kasheta za suyi bayan sun cire
abinda suke buk’ata. Wani hawaye masu zafin gaske suka zubo mata tausayin kanta
take yi na rashin madafa cikin kuka take furta “Ya Allah ka zama gata na kafin
jibi.” Tunda a jibin aka ce za’a cire cikin ita kuma su kasheta…..
JIkar Nashe✍π½
(Free pages sun kusa k’arewa, Kin biya kuwa? Idan baki biya
ba daure ki biya ta wannan account d’in y’ar uwa. Tsagwaron labarin na gaba
wannan duk tsakure ne. 2118666253 UBA. Sai ki tura shaidar biya ta number kamar
haka: 08033748387.
KUDIRAR ALLAH.
Page 7.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
(Ina barar addu’arku an min mutuwa kada kwana biyu ku ji ni
shiru. Nagode ku cigaba dai da biya In sha Allah nan da kwana biyu za mu
d’ora.)
Ina godiya Aysher Adam (Ayshacool K’anwar maza)
And
Na’ima Sulaiman Sarauta (Nimcyluv)
Bisa k’ok’ari da suke wajen ganin littafin KUDIRAR ALLAH ya
samu karb’uwa nagode sosai really appreciated. π₯°
————————
Tunda kashegari ta yi hankalinta ya sake tashi, tsoro da
firgici ya sake shigarta ta sani sarai kwana d’aya ya rage mata a duniyar gaba
d’aya idan har suka cire cikin za su aiwatar da kisan kamar yarda suka fa’da.
Shiru take zaune a cikin duhun, zuciyarta ma ta kasa aikinta
yarda ya kamata, balle har k’wak’walwa ta karb’i sak’on itama ta yi aikin da
take so. Hawaye ne kwance a idanunta hannunta ta d’ora saman cikin tana jin
yarda yake watsalniya da harbawa da k’arfin gaske kamar mai shirin fitowa
duniyar a lokacin. Wani irin ciwo ta fara ji na tashin hankali tun tana d’aukar
lamarin wasa har ta tabbatar al’amarin ya wuce yarda take zato. Gumi ne ko ta
ina yake zuba a jikinta. Cikin tashin hankali ta durk’ushe a k’asan carpet tana
karanta addu’ar duk da tazo bakinta.
Ko ba a gaya mata ba, ta san nak’uda take ganin yarda wani ruwa yake bin k’afafunta ta
sani da zarar ta haihu a yau ba sai gobe ba za su kasheta tunda abin da suke
buk’ata ya samu.
Motsin da ta ji na bu’de k’ofar shi ya sake razanata ta
dunk’ule waje d’aya ciwon nak’udar ma ta neme shi ta rasa don tsoron ya danne
shi. K’amshin turaren da ta ji wanda ya banbanta da wanda ta saba ji ne ya sake
d’aga mata hankali da tunanin wanene kuma? Taku ake cikin isa da tak’ama ta ji
ana nufota gadan gadan bayan an haska hasken torch light ya hasko inda take.
Duhu bai bata damar ganin kowanene ba sai dai koma waye ya banbanta da
wa’dancan mutanen da suke zuwa. Murya a kaurare ta ji an bada Umarnin kunna
fitila ta hanyar cewa “Kunna haske.” Kafin k’iftawar ido kuwa sai ga hasken ya
gwauraye d’akin. Mai tahowar bai fasa iso wa inda take ba, har ya iso ya zauna
a gefen gado duk da bata banbance mace ce ko namiji saboda yarda kayan da suke
jikinsa suka b’oye duk wata sura da za’a tantance jinsin Namiji ne ko Mace. Ji
ta yi cikin raunin muryar da ta kasa tantance tausayi ne yasa ta fita a
sirrance ko kuma asalin muryar ce ta so fallasa kanta saboda firgicin ganin
halin da take ciki. “Hasbunallah labor take” a ka fa’da a ru’de kafin kace me
ta ga an mik’a hannu wanda yake tsaye daga gefe ya mik’o brief case cikin zafin
nama aka ce “Fita ka tsaya a waje ka tabbatar kuma ba wanda hankalinsa zai yi
yo nan d’in, dama ce muka samu sai mu gode wa Allah.” Aka fa’da cikin murya mai
kauri da bayar da umarni kai tsaye. Da sauri mutumin da aka wa Umarnin ya
fita zaro kayan aiki aka fara a gaggauce
mai kayan basajan ya ko ta fara taimaka mata. Ta sha wuya sosai kafin cikin
k’arfin ikon Allah ta haifo d’a namiji. Hamdala ta ji an yi, aka kuma d’aga
jaririn ana kallonsa murya cike da rauni ta ce “Alhamdulillah Muhammad Murad ya
iso duniya.” Aka fa’da ana sakin ajiyar zuciya had’e da sanya Babyn a k’irji
aka ba shi kyakykyawan runguma. Ba tare da kyankyamin jinin da ke jikinsa ba.
Ciwon ya lafa mata sosai tana kallon yaronta a hannun mutumin da bata san waye
ba? Ko ganinsa bata da ikon yi. Tsaf aka goge shi da turaruka na alfarma kafin
a mik’o mata shi cikin kaurin murya aka ce “Ki masa kallon k’arshe ki kuma
k’addara a zuciyarki ko cikinsa baki tab’a d’auka ba balle ki haifeshi kin gama
aikin ki, ni ba zan d’au ranki ba kamar yarda wad’ancan sakarkarun suke son
d’auka burina samun yaron don haka zan miki sallama a yanzu zan kuma nuna miki
hanyar da kai tsaye zata rabautar da ke daga mummuman kisan da za su miki, ki
nesanta kan ki da masarautar gabas da duk abinda zai danganta ki da masarautar
idan kina son zaman lafiyar ki kenan idan ba haka ba masu farautar ranki zasu
iya yi miki kisan wulak’anci. Ki yi sallama da gidan jininki kisa masa albarka
don ko bakomai ke kika haifeshi duk da ba zaki amsa sunan Uwarsa ba har abada!”
Karb’ar yaron ta yi hannunta na rawa ta sumbaci goshinsa kafin ta furta “Allah
ya yi maka albarka Muraad!” Wasu hawaye na zuba daga kwarmin idonta tana kallo
aka karb’e d’an sannan aka umarceta ta shiga band’aki ta tsaftace kanta. Kaya
masu kyau aka bata ta saka sannan aka bata wasu zinare masu tarin yawa. Daga
haka ta ji an yi fito sai shigowar Basamuden mutumin ta gani. “Ka fita da ita
can bayan gari kafin wayewar garin asuba idan kuma har aka Kamaku kada ka sake
sunana ya fito a bakinka.” D’aga kai ya yi yana kallonta ya nuna mata hanya.
Nene na kuka ta bi bayansa bata da yarda zata yi amma zuciyarta ta yi rauni
ganin zata bar gidan jininta dama iyayenta bari na har abada.
Tunda suka fara tafiya ta fara jin ciwo na sake turnik’e ta sai dai ta daure ta
kasa furtawa drivern ciwon da take ji.
Tafiyar awa guda ya yi kafin ya ajiyeta a wani k’aramin k’auye yana furta “Daga
nan ki k’ara gaba, don nan d’in ma yana cikin yankin masarautar gabas idan kuma
kin k’i ba ruwana.” Ya mik’a mata ku’di masu yawa a enveloped ya fisgi motarsa
da k’arfin gaske.
Nene ta durk’ushe a wajen bayan wata Bishiya tana hawaye
saboda azabar ciwon da yake cin ta mararta kamar zata rabe biyu saboda tsananin
azabar ciwo. Murk’ususu kawai take kamar wata haihuwar zata sake yi. Tsawon
lokaci tana wannan halin kafin Allah ya kawo wasu mata guda uku sun dawo daga
d’ebo itace. Da sauri suka rufa a kanta suna mamakin kasancewarta a wajen don
dai bata yi kama da y’an yankinsu ba tafi kama da k’abilar fulani su kuma
barebari ne. Kamata suka yi suna tambayarta abinda ya sameta? Ko kafin ta basu
amsa sai ji suka yi ta yi wani nishi sai ga yaro ya sumb’ulo da sauri suka cafe
shi. Mamaki ya kama Nene ganin wata haihuwar ta sake yi. Tsoron kada asirinta
ya tonu yasa nan take ta aro haukan dole ta k’ak’aba wa kanta. Tana kallo matan
suka ruga wata bukka sai gasu sun sake fitowa aka yankewa yaro ci iya kafin su
kamata su kai ya cikin gida. Duk da bata so bin su ba sai dai ba yarda zata yi
dole ta bi su tana zaro ido don gudun kada su tambayeta daga inda take. Wanka
suka bata ta yi da ruwa mai zafi kafin su tambayeta kayan jariri a sannan suka
gane mahaukaciya ce. Cikin tausayi suke bin ta da kallo aka samo kaya a cikin
kayan yaran da suke gidan aka zunduma masa aka na’deshi cikin zani. Itama suka
bata kaya ta canja na jikinta. Tambayar duniya da suka mata ta k’i ba su amsa
sai zare ido take har suka hak’ura suka k’yaleta so take kawai su bata
jaririnta ta rungume shi a jikinta ta ji sanyin rad’ad’in da ke zuciyarta. Da
kansu suka fahimci tana son ganin jaririn suka mik’a mata shi ita kuma nan take
ta ba shi Nono tana sakin ajiyar zuciya da Hamdala ga Allah da ya mata wata
kyautar d’an bayan rasa wancan da ta yi.
Cikin dare zuciyarta ta kasa nutsuwa da zama a wannan
k’auyen kasancewar ya mata kusa da garin Gabas hakan yasa ta d’au jaririnta ta
Goya ta sulale ta fice daga cikin gidan ba tare da sanin masu gidan ba.
Har duhun asuba ya washe tana gararamba daga wannan sak’o ta
fa’da wannan sak’o ta yi dabarar zame d’ankwalin kanta wanda hakan ya bayyana
zallar haukanta kamar mahaukaciya sabon kamu.
A bakin titi ta tsaya saboda kukan da yaron ya fara ta zame
shi a daidai kuma lokacin Baffa ya taho da motarsa da gudu saura k’iris ya
bugeta. Da sauri ya ja burki yana mamakin kasancewarta a wajen bakin titin.
Ta’ajibi da tsoro ne suka kama shi ganin mace mahaukaciya da
jariri a hannunta. Cak ya tsaya yana son taimakon ta gefe guda kuma yana tsoron
taimaka mata. Sai dai zuciyar musulunci ta sanya masa tausayinta ya matso kusa
da ita. Tana ganinsa ta rungume jaririn tsam a k’irjinta fuskarsa da nuna
alamun bata son ta rabata da shi. Murmushi ya saki kafin ya furta “Ba yaronki
zan karb’e miki ba, amma zaman ki anan hatsari ne ga sanyi da zai iya yi wa
jaririn illa ki zo na taimaka miki.” Ta nok’e kafa’da sai da ya dinga
lallab’ata sannan ta yarda ta bi shi, bayan ya yi mata wayo da kayan wasa zai
siyawa jaririn a zatonsa da gaske mahaukaciyar ce. Bai san ras take ba kuma ta
ji da’din taimakon da zai yi matan duk da bata san a garin da yake ba. Ta shiga
motar ta bi shi suka tafi. Wannan shine dalilin ha’duwarsu da Alhaji Ilu wanda
ya zame mata majingina ita da d’anta.
Sanda ya isa gidansa matansa kawai ganinsa suka yi sun shigo
da ita. Turus Umma da Mahmeey suka yi a lokacin Umma na da tsohon cikin Haidar.
Murmushi ya saki yana furta kun yi mamakin gani na da bak’uwa ne?” Umma ta
d’aga kai ita kuwa Mahmeey tab’e baki ta yi fuskarta ta nuna zallar b’acin rai.
Ya ce “Tausayi da taimako yasa na d’auko ta daga ganinta ban santa ba ban kuma
tab’a ganinta ba, sai dai yanayinta ka’dai zaka kalla ka san mahaukaciya ce ga
sabon jariri a hannunta sai na ji zuciyata tana son ta taimakawa wannan yaron
saboda nima nan gaba Allah ya taimaki zuri’ata.” Umma ta saki ajiyar zuciya
tana jin ta yarda da duk abinda Mijinta ya gaya mata zuciyarta ta gamsu da son
kyautatawa Baiwar Allahn da zuri’arta don haka ba ko d’ar ta kama hannun Nene data
tsaya ta turje tana nuna alamun hauka. “Zo mu je abincin zan baki ki ci ba
cutar ki zan yi ba.” Umma ta furta tana kallon idanunta cike da tausayawa. Ji
suka yi kawai itama ta maimaita maganar tana sakin y’ar dariya ta bi bayan
Umma. Mahmeey kuwa tsaki ta zabga ta wuce ciki haka kawai ganin farko da ta
yiwa matar ta ji ta tsaneta ba tare da wani dalili ba.
Wannan shine dalilin zamanta gidan Alhaji Ilu a kuma daren
Umma ta haifi Haidar sai ya Zamana Umma ke kula da Haidar da Mujaheed Alhaji
Ilu shi ya saka masa Muhammad Mujaheed.da Haidar ya girma baya iya fa’din
Mujaheed ya masa tsaho saboda rashin iya magana sai ya mayar da shi Jaheed har
bakin kowa ya amsa, Umma ce tasa suke cewa Nene har kuma a lokacin ba su san
sunanta na gaskiya ba. Makaranta guda suka yi. Asibitin duniya ba wanda ba a
kai Nene ba in dai na k’wak’walwa ne kuma a Nigeria sai dai duk inda suka je
ana sanar musu ba wata matsala hakan yasa Alhaji Ilu ya fara tunanin ko asiri
ne yasa Malamai suka fara mata addu’a amma lamarin ba sauk’i sai na Allah. A
wajen Mahmeey kawai suke samun matsala ita da yaranta idan banda haka sai ta ce
zaman gidan Alhaji Ilu bata da wani matsalar komai.
Tana kaiwa nan a tunanin ta ja ajiyar zuciya mai nauyin
gaske idanunta na sake zubar da k’walla tunanin waccen rayuwar tata ya sake
k’arfi a zuciyarta da tunanin ko a wane hali Murad yake?
___________
Kuka sosai Najma take tana jin wani irin zafi da ciwo a
zuciyarta kafin ta mik’e da sauri kamar wacce aka tsikara bata tsaya ko ina ba
sai sashen da d’akunan su Jaheed suke. Da azama ta tura d’akinsa saboda tashin
hankali kanta ko d’ankwali babu. Riga da wando ne a jikinta. Jaheed da yake
zaune gefen gado ya yi nisa cikin tunaninsa ya d’ago yana zuba mata manyan
idanunsa kafin ya lumshe su yana fa’din “Matsala, Baffa ya ha’da ni da wahala.”
Ya furta hakan a zuciyarsa yana watso mata wani kallo da ya kusa yasa mata
tsoronsa a zuciya. Sai dai ta matse tana dubansa cikin k’asan ido kallo mai
nuna zallar bak’in cikin da zuciyarta take ciki. “D’an Mahaukaciya zuwa na yi
ka sake ni….” Ya d’ago yana bata Wani irin kallo kafin ya ciji leb’ensa kawai
yana jin zuciyarsa kamar ta fito daga k’irjinsa don azabar tsanarta da yake ji
a zuciyarsa. Me zai yiwa yarinyar nan ta san shima ba wai sonta yake ba, yana
son a yanzu ya goge rainin da yake tsakaninsu ya dasa mata bak’in ciki ita da
mahaifiyarta a zuciyarsu wanda ba zasu tab’a mantawa da shi ba. Auren ne basa
so suke kuma adawa da shi ya zama dole ya nuna musu shi kuma yanzu yake son
auren. Don haka a zafafe ya fincikota ta fa’da jikinsa yana jin lokaci yazo da
zai keta mata mutuncin ta na y’a mace abinda dai ya san da shi take tak’ama…………
JIKAR NASHE✍π½
Kin biya ko kuwa kina lak’ai lak’ai… haba Hajjaju kada 500
ta hanaki morar littafin nan yanzu fa aka fara.. shin Ina Murad? Su waye mutane
biyun da suke jefar rayuwar Nene cikin tashin hankali kuma kowa da burinsa a
kanta? Mhmmmn lamarin fa mai girma ne…. Ki biya 500 ta wannan account d’in
2118666253 UBA sai ki tura shaidar biya ta wannan numberr 08033748387. Special
1k.
KUDIRAR ALLAH
8.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
—————
Jikinta ne ya fara rawa sosai tsoro mai tsanani ya bayyana
akan fuskarta ganin abinda yake shirin aikatawa. Ta bu’de idonta sosai tana
kallon yarda suka samu kusanci da shi. Runtse idonta ta yi hankali tashe ta ce
“Me kake shirin yi?” Sai a lokacin ya dubeta fuskar mahaifinta ya gani a tata
fuskar hakan yasa ya ji zuciyarsa ta karye har ya kasa aikata abinda ya yi
niyya ya janye jikinsa yana zabga tsaki ya bita da wani wulak’antaccen kallo
kafin ya nuna mata k’ofa yana furta “Get out Malama, ki sake kwatanta min
abinda kika min sai na nuna miki akwai nisan banbanci a tsakaninmu da ke.” Bata
yi magana ba don a lokacin hanyar tsira take nema. Mik’ewa ta yi da sauri tana
gyara gashinta da ya yamutse ya mik’e tsaye kamar mahaukaciya sabon kamu.
Jaheed ya bita da kallo yana datse leb’ensa tsanarta tana sake kunnuwa a
zuciyarsa da gaske ya tsaneta sosai da sosai mutunci da darajar Ubanta zai saka
ya zauna da aurenta idan banda haka da tuni ya saketa tun a lokacin ma. Wayarsa
da take k’ara ce ta dawo da shi cikin hankalinsa ya dubi wayar yana kallon
numberr Khairi da ya haddace a kansa kamar karatu tana yawo akan screen d’in.
Lumshe idonsa ya yi kafin a karo na farko tun bayan afku war abin ya ji yana
son amsa wayar Khairin. Yana kara wayar a kunnensa ta rushe da kukan da dama
shi take yi. Jaheed shiru ya yi yana
sauraran kukan da yake sake karya masa gwiwa gwara ita idan ta yi tana da
madafa ta kuma ji da’di ta tana da Uban da zai share mata hawaye, Shi fa? Ya
saki ajiyar zuciya yana furta “Habibteey, am sorry please.” Kukan ta sake saki
kafin cikin muryar kukan mai bayyana gazawa da rauninta ta ce “Dole na yi kuka
Jaheed, bana son ka gaya min ka rabu da ni zuciyata ba zata d’auka ba.” Shiru
ya yi tunda a zahiri ba shi da amsar bata. “Talk to me Jaheed.” “Me Zan ce miki
Khairi? Abbanki ya datse alak’a mai k’arfin da take tsakaninmu…..” “Bai datse
ba Jaheed zamu iya aure..” Murmushi ya saki irin murmushin da kai tsaye za’a
kira na karayar zuciya ya ce “Ta yaya? Kin tab’a ganin auren da ba yardar iyaye
a cikinsa ya yi inganci am sorry to say Baffa na ya d’aura min aure yau…” Ji ya
yi ta saki wani irin gigitaccen ihu kafin ya ji shiru, maganar duniya kuma bata
amsa ba. Hankalinsa ba k’aramin tashi ya yi ba yana tsoron kada ya rasa Khairin
a duniya gaba d’aya. Ya dinga kiran wayar amma wayar nata ringing ba a d’aga
ba. A hankali ya furta Ya Allah! Yana jin zuciyarsa na sake rauni.
Hankalinta a tashe ta fa’da parlourn Mahmeey jikinta na rawa
ta shiga kiran Mahmeeyn. Da sauri ta fito daga kitchen itama nata hankalin a
tashe ta zuba mata ido. “Me ya faru?” Jikin Mahmeeyn ta fa’da a zafafe tana
sakin kuka. “Ya cuceni Mahmeey.” Mahmeey ta saka hannu tana d’ago ya a razane
ta furta “Me ya miki? Kada ki ce min ya kusanceki?” Girgiza kai ta yi kafin
murya a d’ashe ta ce “Ya kusa dai Mahmeey don Allah ki san yarda kika yi kika
raba auren nan.” Mahmeey ta saki ajiyar zuciya tana jin zuciyarta na d’acin
masifa kafin ta ciji bakinta ta ce “Dole ma ya sake ki Wallahi ko ya k’i ko ya
so.” Najma ta saki ajiyar zuciya a jikin Mahmeeyn tana fatan hakan ya tabbata
da tafi kowa murna a duniya ta ina zata fara nuna Jaheed a matsayin Mijinta a
wajen k’awayenta masu k’aryar tsiya da girman kai, a duk sanda suka san Jaheed
Mijinta ne tabbas ranar duk wani ajinta ya zube.
Baffa kuwa yana gama jin zuciyarsa ta sauka daga fushin da
take ya kira Umma a waya. Umma bata yi k’asa a gwiwa ba ta je sashensa. A zaune
ta gan shi da takarda da biro a hannunsa. Ta yi sallama ya amsa mata ba tare da
ya dawo da annurin fuskarsa da ya yi k’aura tun d’azu ba. Ita dai Umma zama ta
yi a gefensa zuciyarta tana addu’ar Allah ya kawo sassauci a cikin lamarin. Don
kam bata hango ta yarda Najma da Jaheed za su yi zaman auren da har nan gaba
za’a yi alfahari da shi ba. Baffa ya d’ago kai yana kallonta kafin ya mik’a
mata takarda da biron ya ce “Rubuta min duk wani abu da ake buk’ata na kayan
d’akin amarya kitchen da toilet parlour da komai ma.” Umma ta karb’i takardar
tana son ba shi shawara tsoron yanayin fuskarsa yasa ta kasa bayyanawa don haka
ta shiga rubuta duk wani abu da ta san shi zai dace da y’ar gata irin Najma ta
rubuta tas sannan ta mik’a masa tana furta Allah ya tabbatar mana da alheri ya
amsa da Ameen kafin ya sake mik’a mata wata takardar ya ce “Rubuta min list
d’in kayan lefe.” Ta amsa nan ma ta shiga rubutawa yarda aka san ana lefen duk
wata y’ar gata. Baffa ya amsa ya ce “Kin gama na ki je ki Allah miki albarka.”
Umma ta amsa tana ganin wautar Mahmeey da Allah ya bawa d’and’asheshen suriki
amma ta raina kyautar da ya yi mata Saboda wani banzan dalili nata ina ma Najwa
ce ta dace da Miji irin Jaheed da sai ta fi kowa murna.
———MASARAUTAR GABAS….
Duk wanda ya kwana ya wuni a wannan masarautar ya san akwai
wani babban taro da zai faru a masarautar, saboda yanayin yarda ake ta sake
k’awata masarautar da abubuwan ado iriiri masu bayyana ana shirin yin wani
gagarumin taro. Ciki da wajen masarautar an shafe tas da sabon paint fari tas
da ya sake k’awata masarautar. Sarki Mukhtar yana zaune a fadarsa fuskarsa a
washe tas da fara’a yana kallon jama’ar cikin Fadar ya furta “Alhamdulillah
Allah ya kawo mu lokacin da a yau Murad ya gama karatu zai dawo gida, kamar
yarda na d’aukar wa Jama’a alk’awari a duk sanda ya kai munzali ma’ana
shekarunsa sun kai inda zai iya amsar duk k’addarar da ta same shi a lokacin ne
zan sanar da shi wanene shi? To In sha Allah a yau Zan aikata hakan, duk da
zuciyata na jin nauyin sanar da shi amma ya zama dole don sauke nauyin
alk’awarin da na d’auka.” Masarautar ta d’au Kabbara ana kaiwa Sarki jinjina
zuk’atan wasu da dama daga ciki sun zama fari k’al don sun da’de suna jiran
wannan ranar. Ranar da za su san asalin Murad da yarda aka samar da shi, tunda
abu ne sananne har yanzu ba a san Uwar da ta yi cikinsa ta kuma haifeshi ba,
abu d’aya suka sani ranar da aka tsinceshi a bakin fadar cikin shiga ta alfarma
a cikin showel na jarirai sai zabga k’amshin turare mai k’amshin gaske ya ke.
Sai dai ba Uwarsa ba kuma alamunta, lamarin da ya tunzira jama’ar masarautar
suka so yi wa sarki tawaye sai dai Sarkin y nemi alfarma yana rok’onsu su bari
Murad ya girma zai sanar da shi ko shi wanene duk da likita ya tabbatar Murad
d’in jininsa ne ta hanyar gwaji na DNA. Surutai suka fara tashi a fadar kowa
yana fa’dar albarkacin bakinsa jama’a da dama sun d’auki maganar sarki a wani
ma’auni na rainin hankali idan banda haka ta yaya zai ce Murad ba d’ansa ba ne
duk da tsananin kama ta kwabo da kwabo da suka yi. Yaron da ko makaho ya shafa
ya san Jinin sarki ne don ba ta inda ya bar shi. Suna jira dai su ji wannan
karan ko da me Sarkin ya zo. Abu guda da suke so ya faru shine a ce Murad ta
hanyar zina aka samar da shi to tabbas wannan dama ce suka samu ta tsige sarki
don a dokar masarautar su ba su amince da Mulkin Mazainaci ba za’a ciresa daga
sarautar sannan kuma ya bar garin ko da ta k’arfin tuwo ne. To fa!
Shigowar manyan jeeps d’in da ake kira motoci masu numfashi
ne da jini ya yasa ahalin masarautar suka san MURAD ya iso masarautar gabas, bayan shekaru
Ashirin da barinsa masarautar zuwa k’asar England karatu.
Koda motocin suka tsaya bai fito daga motar ba, baya ya yi
da seat d’in ya jingina da kujera yana jin ciwon kai yana dawo masa. Ransa ya
sake b’aci sam bai so dawowa masarautar ba da Bahba ya sani barinsa yai a can
k’asashen jajayen kunnuwa inda ya fi wayo. Ya d’an rik’e kansa yana murzawa a
hankali. Ta cikin tinted glass d’insa yake hango dandazon mutanen da suke
baibaye bakin motocin. Ya d’an saki ajiyar zuciya a hankali kafin ya kalli
driver ya ce “Open.” Iya abinda ya ce kenan ya ja bakinsa ya tsuke bayan ya
cilla wata alawa mai dad’i bakinsa. Ya hau tsotsa a hankali yana fatan
miskilancin kansa ya ragu ko ya ji da’din zama da mutane lafiya kafin a fara
kiransa mai girman kai. Murmushin dole ya dinga lalubo wa a fuskarsa yana jifan
mutanen da shi. Su kuma suna d’aga masa hannu. Kai tsaye Fada aka nufa da shi
duk da baya son hayaniya amma sau tari yana son kasancewa da mahaifinsa da yake
jin k’aunarsa har tsakiyar ransa, Ya sani tun haihuwarsa mahaifiyarsa ta mutu
kamar yarda Bahba ya gaya masa ya sanar da kowa kuma ya gaya masa haka idan ya
tambaya. Sallama k’asa k’asa ya yi kafin ya shiga cikin Fadar Sarki Mukhtar ya
mik’e da sauri yana bu’de masa hannu shi Kuma ya fad’a ciki Sarki ya rungumeshi
yana sakin ajiyar zuciya ha’de da hawaye masu bayyana tsananin Farin cikin
ganin Murad d’insa sanye da kayan sojoji kamar yarda ya jima yana buri.
“Alhamdulillah” ya furta a hankali yana shafa kansa da ya d’an durk’usa
kasancewar ya fi mahaifin nasa tsaho a yanzu. Sha’awa suka bawa jama’a da dama
a wurin wasu kuma tab’e baki suka yi suna jiran cikar alk’awarin sarki da ya
sanar da su a yau zai sanar da Murad waye shi? So suke wani hali Murad zai
shiga idan ya samu labarin don haka suka hau gyara zama suna jiran ji daga
bakin Sarki Mukhtar. Murad ya d’an rusuna a gabansu ya kai gaisuwa kafin ya
koma gefe ya zauna yana rik’e kansa da yake damunsa ciwo. Sarki ya dube shi ya
ga alamar gajiya a tare da shi cikin kulawa da taushin murya ya ce “Ka je ka
samu ka yi wanka ka ware gajiyar da ke jikinka idan ka huta ka fito akwai taron
da aka shirya don kai a waje…” Murad d’aga kansa ya yi kafin ya mik’e da taku
mai nuna k’arfi ya bi ta wata k’ofa da Hadimansa suka nuna masa zuwa cikin
gidan inda anan sashensa yake. Yana dosar hanyar da zata kai shi sashensa ya ji
wata magana da ta fisgi hankalinsa. “Yau dai Ai dole ya sanar da shi wannene
shi da yarda ya samar da cikinsa tunda har yanzu ba wanda ya san Uwar da ta
haifeshi? Asirinsa zai tonu yau tabbas zina ya yi ya samar da shi idan banda
haka wacece Uwar Murad d’in da yake b’oyewa?
Wani irin jiri ne ya fara d’iban Murad da sauri ya juya inda yake jiyo
zancen da azama ya isa wajen…..
JIKAR Nashe ✍π½ Biya naki 500 ko kin huta da jiran
typing kullum…. Saura shafi biyu free pages ya k’are…..
2118666253 UBA ki tura shaidar biya kai tsaye zuwa ga
08033748387
KUDIRAR ALLAH
9.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
Fuskarsa na nuna zallar damuwa ya dinga duban sashen da ya
ji maganar sai dai bai ga kowa ba, kamar wanda Aljannu suka d’ebo zancen suka
saka a kunnuwansa. Hankalinsa a tashe ya juya zuciyarsa na wani irin bugu na
tashin hankali ya koma hanyar da zata mayar da shi Fada a yau yake son sanin ko
shi wanene daga bakin mutumin da yake tunanin shine mahaifinsa. Ashe shi yasa
koda wasa bai tab’a ganin hoton mahaifiyarsa ba a zahiri kamar yarda koda wasa
bai tab’a jin sunanta daga bakin kowa ba, ashe ba a santa ba balle a kwatanta
masa ita. Bai san inda yake takawa ba, saboda raunin da zuciyarsa ta yi ya isa
cikin Fadar. Mamaki ya kama mutanen da suke cikin fadar ganin yarda ya shigo
fuskarsa d’auke da tashin hankali ya zauna a gaban sarkin gwuiyoyinsa a k’asa,
idanunsa da suka yi jajur ya zubawa Sarkin cikin nasa idanun ya ce “Ina son
ganin hoton magaifiyata da kuma sunanta.” Wani irin shiru fadar ta d’auka sarki
kuwa gabansa ne ya fa’di jin abinda ya fito daga bakinsa hankalinsa tashe ya
zubawa Murad ido. Rashin nutsuwa da tashin hankalin da ya gani a idanun Murad
shi ya tabbatar masa da ya ji wata magana da ta dangance shi. Ya d’an d’auke
idanunsa irin wannan ranar yake tsoro yake kuma fargabar zuwanta ga shi tazo
masa a lokacin da bai shirya mata ba. Ya zame masa dole a yau ya sanar da Murad
ta hanyar da ya zo duniya ko da kuwa baya so. Mutanen da suke zube a fadar kuwa
suma jikin su tsuma yake suna son su ji Mai Sarki Mukhtar zai ce da Murad
tabbas ranar wanka ba’a b’oyen cibi. Murad idanun nasa ya cigaba da zubawa
Sarki yana jin tsoron Sarkin ya fito ya sanar da shi ba shine ya haifeshi ba
kamar yarda ya ji a yau. Bai san sanda ya fara datse leb’ensa ba a hankali yana
furta “Ina jin ka, don Allah ka sanar da ni.” Ajiyar zuciya Sarki ya saki kafin
ya dafa kafa’dar Murad d’in ya ce “Yau Zan sanar da kai duk abinda kake son ka
sani Murad sai dai bana son ka min tambaya a kan abinda ba ni da masaniya a
kansa.” Murad ya lumshe idanunsa yana d’aga kai.
Kunnuwansa suka fara jiyo masa labarin da Sarki Mukhtar
Wanda ya d’auka a matsayin Mahaifi duk da kamaninsu sun zamo d’aya amma a yau
zuciyarsa ta yi rauni yana tsoron Sarki ya zama ba shine mahaifinsa ba…..
—————-❤️π₯π«
Wata irin iska mai k’arfin gaske ce ta karad’e harabar gidan
Sarkin, me tafe da wata guduwa da take barazanar d’auke duk wanda yake filin
gidan sarkin. Hankali tashe mutane suka fara neman mafaka ganin yarda gari yake
k’ara duhu kamar ba yanzu hasken alfijie ya Keto ba. Kowa neman inda zai tsira
yake kafin narkakken hadarin ya zubo da ruwa wanda da alama ruwa za’a shek’a ba
na wasa ba.
Cikin mintuna da basu wuce biyu ba ruwan ya kece, ruwa mai
yawan gaske ake kwararawa mai ha’de da tsawa walk’iya ga wani irin mamakon ruwa
da yake shatata a harabar gidan Sarkin, kowa zama ya yi a cikin masallacin don
gudun fita wani abu mummuna ya faru da shi, don idan ana irin wannan ruwan
komai ma yana iya faruwa ga mutum. Lazimin dole suka fara yi, Sarki da yake
zaune a kan daddumarsa daga can gefe shima lazimin yake, duk da wata irin
mummunan fa’duwar gaba da yake mai tsananin gaske bai hana shi yin lazimin ba.
A jikinsa yake jin akwai wani abu na farin ciki ko Bak’in ciki da zai same shi
don a duk sanda ya yi irin wannan fa’duwar gaban ana samun hakan ko dai farin
ciki ko kuma bak’in ciki ko kuma mutuwa mai girma daga ahalinsa jininsa. Ya
‘dan runtse idanunsa yana matsa hannunsa a hankali a zuciya kuma yana jan
Hasbunallah cikin nutsuwa ya dafe k’irjin nasa da ya dameshi da matsanancin
bugu. Zuciyarsa ta raunana kamar yarda idanunsa suka tare hawaye, tsoro yake ji
wani irin tsoro da yake fatattakar dukkan nutsuwar zuciya da gangar jikinsa.
Baya son mafarkinsa ya zama gaskiya, kamar yarda ya saba a duk sanda ya yi irin
wannan mafarkin to ya sai ya rasa d’ansa wanda aka haifa ko wanda yake cikin
mahaifiyarsa. Sau sha bakwai yana irin wannan mafarkin da fa’duwar gaba sau Sha
Bakwai d’in kuma dai yana rasa jininsa. Bai tab’a samun d’an kansa rayayye ba
tsawon shekaru Ashirin da aurensa da matansa hu’du sai dai a haifa masa sati na
zagayowa su mutu wasu ma a ranar da aka haifesun suke mutuwa kamar yarda wasu suke
mutuwa a cikin mahaifiyarsu, yanzu ne yake saka ran samun Tilon d’a daga
Uwargidansa bayan shekaru Goma rabonta da d’aukan cikin, a kuma wannan watan
ake saka ranar haihuwarta, Bayan addu’oi da duk wasu abinda ya kamata yana ji a
jikinsa wannan lokacin zai samu d’an kansa kamar yarda aka nuna masa a mafarki.
Sai dai yanayin da yake ji yanzu a jikinsa ya firgita shi ya kuma sanya masa
tsoron rasa gudan jinin nasa a karo na barkatai.
A hankali Ruwan ya dinga d’aukewa kafin kaji tsit ruwan ya
tsaya cak, Iskar da take ka’dawa ma cikin KUDIRAR ALLAH sai ta d’auke tsaf gari
ya yi Ni’ima ya yi sanyi, daidai lokacin da a masallacin aka yi addu’a aka
shafa. Aka bu’de k’ofa kowa ya yiwa Sarkin Gabas d’in Sallama dafatan saukar
Magajinsa lafiya wannan karan. Ya dinga amsawa cike da farin ciki yana kuma
damk’ar ku’din da baya sanin adadinsu yana rabawa miskinai da talakawan cikin
fadawansa duk wanda aka bawa sai ya fice yana sake jaddada addu’arsa ta saukar
YARIMA mai jiran gado lafiya ya iso duniya lafiya daga cikin mahaifiyarsa.
Cinicirindon jama’a ne suka taru a k’ofar masallacin cikin
tashin hankali ana kallon Jaririn da aka ajiye a gefen Masallacin cikin shigar
kayan sanyi da alama kuma ba’a dad’e da haihuwarsa ba. Salati da Salallamin
jama’a shi ya ja hankalin Sarkin ya kalli wani bafadensa da sauri yana masa
nuni da ya je ya duba masa abinda ke faruwa. Sarkin Fada Yana zuwa taron
jama’ar Suka d’an dare suka bashi wuri. Ya is a wajen Jaririn da aka kwantar
Yana Kallo cike da mamaki shima kafin ya saka hannu biyu ya d’auko shi. Ya zuba
masa ido wani abu yana fusgar hankalinsa game da kamannin Jaririn da kai tsaye
zai iya cewa tabbas jinin gidan sarautar SARKIN GABAS NE. Saboda a tsawon
lokacin da ya d’auka yana aiki a k’ark’ashin masarautar tun lokacin Mahaifin
Sarki Abdallah Mahaifi ne ga Sarki Mukhtar wanda shine Sarkin yanzu ya san
ahalinsu ciki da bai d’in su, kuma a duk lokacin da aka yi haihuwar shi yake
karb’ar yaro ya mik’awa Sarki ya gani ya masa addu’a, to tabbas kamanceceniyar
Jaririn nan da Sarki Mukhtar kai tsaye zai iya cewa babu banbanci! Don kamar
yarda ya d’aukeshi yanzu a hannu haka ya d’au Sarki Mukhtar yana yaro, hoton
Sarki Mukhtar sanda aka haifeshi ya dawowa Sarkin fada a rai yaga tabbas wannan
yaron da yake hannunsa ba shi da banbanci da Sarki Mukhtar hatta zubi da tsarin
shan girarsu. Cire mamakinsa ya yi tunawa da ya yi Uwargidan Sarki tana da ciki
ba mamaki ita ce ta haihu aka yi musu bazata da haka, ba mamaki ta haka zata
sanarwa da Sarkin haihuwarta idan kuwa haka ne ya tabbata Sarki ba zai kyaleta
ba yarda ta yi masa wasa da yaron da aka haifa masa a yau. Ya saki ajiyar
zuciya kafin ya juya cikin sauri tunawa da ya yi sarki ne yake jiransa.
Zubewa ya yi a gabansa yana mik’a masa yaron. Da sauri
Sarkin Gabas ya mik’e bakinsa fal fara’a ya amshi yaron yana masa kallon
k’urilla shima dai nasa kamannin ya hango tattare da yaron, a hankali ya furta
“Alhamdulillah! Allah nagode maka Allah yasa rayayye ne, Ubangiji kasa magajina
ne.” Sai da ya yiwa yaron addu’oi sosai kafin ya d’ago ya kalli Sarkin Fada ya
ce “Yanzu fulanin ta sauka kenan? Dafatan tana cikin k’oshin lafiya mu je na
ganta, Fulani ta samar min da farin cikin da ban tab’a tsintar kaina a cikinsa
ba ta hanyar haifa min yaro mai kama da ni kwabo da kwabo. Wanda tunda ake
haihuwa ba’a tab’a samun mai tsananin kama da ni har haka ba.” Ya mik’e da
yaron a jikinsa ya yi hanyar da zata sada shi da cikin gida wajen Matansa kai
tsaye. Sarkin Fada ma da murmushi ya bi shi yana mamakin yarda yau ‘daya fuskar
Mai martaban ta washe da fara’a har haka kuma yana hira da magana sosai kamar
ba shi ba. Bai yi k’asa a gwiwa ba ya bi shi da sauri, don duk wani masoyin
Sarki tilas ne yau ya taya shi murna.
Harabar wajen Matan nasa shiru sai kai kawon Bayi da suke yi
jefi-jefi. Kowa ya ga Maimartaba Sarkin Gabas da jariri sai a yi saurin kai
gaisuwa su kuma matsa gefe suna magana k’asa-k’asa don dai a kaf masarautar ba
wanda yake da labarin haihuwar Fulanin an san dai tana da tsohon ciki, tun
bayan bayyanuwar cikin nata kuma aka saka matakan tsaro sosai a b’angaren nata.
Kansa tsaye ya nufi sashen Fulanin, fadawansa suka fara
gyaran murya Alamar kowa ya kintsa Mai martaba na nan tafe. Duka bayin Fulanin
suka dare zuciyoyinsu da mamakin halartar Maimartaba sashen Fulanin abinda za
su ce sabon abu a wajensu don dai ba su tab’a gani ba.
A Babban Falon Fulanin Sarkin Gida da Amintattun Fadawansa
biyu suka ja tunga suka tsaya. Shi kuma mai martaba kansa tsaye ya shiga
Parlour na Biyu kafin ya kai Parlour na Uku inda a nan D’akunan Barcin Fulanin
suke. Sassanyan k’amshi da sanyin Ac na ratsa ko ina kamar yarda k’amshin k’asa
ya mamaye hancinan mutanen GARIN GABAS. Gyaran murya ya yi kafin ya mur’da
d’akin hannunsa d’aya d’auke da kyakykyawan jaririn da ya bayyana kamanninsa
tun yana yaro. Shiru d’akin Fulanin ba komai sai k’arar A.c da alama wanka take
don haka kansa tsaye ya zauna a gefen gadon yana sake k’arewa jaririn kallo
wata irin k’auna da soyayyar jaririn na sake fusgar ransa ji yake kamar ya
mayar da shi ciki don tsananin so da begen yaron. Ya saka tattausan leb’ensa ya
ba shi sumba sosai yaron kuwa ya d’an bu’de ido yana kallonsa kamar ya san waye
shi a wajensa ya yi k’uri yana kallonsa. Mai martaba ya sake k’ura masa ido
Kafin a hankali ya furta Allah ya raya min kai Muhammad Murad. Sai kuma ya sake
kai bakinsa ya sumbaci goshinsa. Yana murmushi ya sake cewa “Murad Mukhtar
Abdallah In sha Allah kai ne magajina….” Daidai lokacin Fulani ta fito daga
wanka jikinta sanye da rigar wanka tana tsane gashin kanta da towel d’in da
yake hannunta. Turus ta yi baki bu’de tana kallon Maimartaba da mamakin ganinsa
kai tsaye a cikin d’akin barcinta. Idanunta ya sauka a kan jaririn hannunsa.
Yarda take kallonsa da mamaki shima haka yake kallonta da tsananin mamakin da
yafi nata ganin turtsetsen ciki a jikinta haihuwa ko yau ko gobe…. Ta nuna
jaririn hannunsa tana iso wa bakin gadon ta ce “Ranka ya da’de jaririn wa muka
samu?” Dubansa ya sake kai wa kan jaririn da yake hannunsa kafin ya sake sauke
idanunsa kan cikin da yake jikin Fulani ya ce “Ba ke kika haihu ba?” Cikin
mamaki ta dubi cikin jikinta ta ce “Ni kuma? Ban gane ba ni na haihu ba shi
kuma wannan cikin na jikina fa?” Hannun Maimartaba na rawa ya d’aga yaron yana
mamakin al’amarin ya ce “Kada ki min wasa da hankali Rahina d’an waye?” Ta saki
murmushi ka’dan ta ce “Banda kada ka ce na maka rashin kunya da sai na ce kai
tsaye kai kake min wasa da hankalin, ni dai nan haihu ba kuma idanunka sun gane
Maka hakan, ga cikina nan a jikina don haka kai zan tambaya
d’an waye?” Ya sake d’aga yaron yana nuna mata ya ce “Bari na je wajen Sarkin
Fada na ji a ina aka samo yaron idan ba naki bane?” Da sauri itama ta zura
zundumemen hijabinta ta bi bayansa da yaron a hannunsa. Tuni mutane sun cika
sassan Fulanin da tunanin itace ta haihu ciki kuwa har da kishiyoyinta da kuma
matan k’annen Sarki Mukhtar da mazajensu kowa bakinsa d’auke da fara’a ana
murnar Fulani ta haihu. Mai martaba aka gani hakan yasa aka yi saurin yin shiru
wad’anda kuma basu da hurumi a tsayuwar tuni suka watse. Mai martaba ya zauna
idanunsa cikin na Sarkin Fada da yake tsaye shima bakinsa ya kasa rufuwa. Ya yi
gyaran murya ya ce “Sarkin Fada a ina aka samo yaron nan don Fulani ta tabbatar
min ba ita ta haihu ba, ga kuma cikinta nan a jikinta.” Cike da mamaki Kowa ya
zubawa Fulani ido kafin Sarkin Fada ya fara fa’dar inda ya aka tsinci yaron…
kafin ya gama bada labari kowa ya d’ago a zafafe yana kallonsa Maimartaba ma
cikin mamakin yake kallonsa “A bakin Masallaci ku ka gan shi bayan d’auke ruwa
fa ka ce?” Sarkin Fada ya d’aga kai cike da tabbatarwa. Shiru wajen ya yi kowa
da abinda yake tunani a ransa, kafin Mai martaba ya sake karb’ar yaron yana
sake ganin zahirin kamanninsa da yaron, ya mayar da kallonsa kan k’annensa da
suke Uba d’aya kuma yawanci suna kama da juna. “A matayenku ba wacce take da
ciki?” Da sauri suka girgiza kai suka tabbatar ba Mai ciki. Idanun Mai martaba
ya fa’da kan wata takarda da take jikin showel d’in da aka nad’e jaririn da
shi. Da sauri ya zaro takardar ya mik’awa Sarkin Fada yana umartarsa ya karanta
kowa ya ji. Jiki na rawa Sarkin fada ya bu’de takardar ya fara karantawa.
“K’udirar Allah shi za’a kira samuwar yaron nan, yau aka
haifeshi kuma wallahil azeem d’an sarki ne, Sai dai shi kansa Sarkin bai san
Uwar yaron ba a zahirance bai tab’a ganinta ba Amma kuma tabbas wannan d’ansa
ne jininsa Magajinsa In sha Allah, kuna da damar zuwa asibiti don tabbatar da
hakan. Jinin Sarki Mukhtar Bn Abdallah ne……D’ansa na Halak ba shege ba…..Kuma
ina rok’on ku saka masa Muhammad Murad” Da sauri Sarkin Gabas ya zaro ido cikin
mamaki da jin sunan da irinsa dama ya sanyawa yaron, Wacece wannan ko wanene
wannan da yake hangen irin abinda zuciyarsa take Muradi, kamar zuciyar tasu ma
a tare
Take, A yanzu da ya sakawa yaron sunan Murad sunan ne kawai
ya fa’do masa a zuciya duk da ya da’de yana da burin idan aka haifa masa Namiji
Murad d’in zai saka, amma ba ya jin ya furta hakan ga kowa…
Tun kafin Sarkin Fada ya gama karantawa duk mutanen da suke
wajen suka d’ago suka zubawa Sarkin Gabas ido. Daga kallon da Suke masa ya
tabbatar k’arin bayani suke nema a wajensa, sai dai ya ce musu me? Ko Kur’ani
za’a ba shi bai tab’a kusantar wata mace ba,bayan Matansa guda hu’du ko
k’wark’wara ba shi da ita, amma ga yaro kuma an tabbatar masa nasa ne, alhali a
takardar ma an sanar bai san Uwar Yaron ba… Ba shakka yaron sai dai idan D’an
Aljannu ne… Tashin hankali ya bayyana akan fuskarsa yana kallon Muhammad Murad
da yake hannunsa……
Jikar Nashe ✍π½
(kada 500 kacal ta gagareki baiwar Allah wannan littafin ba
free bane kuma saura 1pg free pages su k’are. Ki biya ku’dinki ta wannan
account kamar haka 2118666253 UBA sai ki turo shaidar biya ta wannan number
kamar haka:08033748387.
Special people 1K kacal. Allah ya baku ikon biya.
JIKAR NASHE CE✍π½
K’UDIRAR ALLAH……..
Page 10.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
MIKIYA WRITERS ASSOCIATION.
_____________
Kowa a parlourn ya yi tsit aka
Zubawa Sarkin Gabas ido ana jiran jin abinda zai fito
bakinsa, Ga shi dai magana ta bayyana jariri jininsa amma ta wace hanya aka
samar da shi? Shine abinda mutanen Fadar suke son sani, tunda dai cikin Matan
Sarkin ba wacce ta haihu balle a ce nasa ne, Ba shi kuma da kuyanga ko
k’wark’wara tunda ba tsarin masarautarsu ba ne. Mata hu’du aka amincewa Sarkin
ya yi shi kuma Matansa Hud’u a idon duniya tunda biyu daga cikinsu su sun san
tsakaninsu da shi ba aure alfarma kawai suke nema ya b’oye hakan saboda wani
gagarumin laifi da suka masa, shima kuma ya rufa musu asiri ne saboda ba ya son
a sake cewa ya yi wani auren ba tsarin sa bane auren Mata da yawa.
Da k’yar ya saki ajiyar zuciya ya sake d’agowa yana zubawa
Murad da yake hannunsa ido, kamanninsa da yaron yana sake k’arfafa irin
kamannin nan da Hausawa sukewa Lak’abi da kwabo da kwabo. Idanunsa a raunane ya
d’ago ya kalli jama’ar Falon wanda duk jininsa ne da suke Uba d’aya, shi ka’dai
ne bare a cikinsu y’ar uwarsa d’aya ce Mace kuma ta rasu shekara d’aya da ta
wuce a hatsarin Mota. Ya yi gyaran murya yana so ya fa’di abinda yake ransa
Amma yana nazarin fuskar y’an uwansa da kai tsaye dama burinsu kenan su samu
mummunan abu da zai zama bak’in tabo gareshi su ya’da shi a duniya don mutane
su yi Allah wadarai da shi, so suke a dole sai mutane sun k’i shi, Haushinsa
suke ji sosai da ya zamo shine Sarkin gabas ba d’aya daga cikinsu ba, duk da
girman da ya bawa Yayansu bai wuce kwana ashirin da takwas ba, amma a tsari na
Masarautar Gabas ko da kwana d’aya ya girme shi shi zai gaji sarautar Ubansa
don haka sarautar kai tsaye ta fa’da kansa. Duk da Uwarsa itace ta uku a matan
Sarkin Gabas Mai rasuwa Amma ita ta fara haihuwa don haka dole shine ya zama
Sarki wannan ya d’arsa tsana mai girma a zuk’atan zuriyar Mahaifinsa Sarkin
Gabas Abdallah.
Ya d’inke fuskarsa tsaf ba ragowar d’igon rahma so yake sai
ya cirewa zuciyarsa Shakkarsu da tsoron cutarwarsa gare su. “Ba ni da wani abu
da zance, sai dai ina ji a jikina koma daga ina wannan yaron yake na amince
Jini na ne, zan kuma kira likitoci su zo su tabbatar da hakan, idan komai ya
kasance kuma kuna da ikon zartar da hukuncin duk da ya dace gane da Mulki na,
abu d’aya na sani Ina son sa! So mai tsanani da zan iya rasa komai da kowa a
duniya ciki kuwa har da Sarautar da ku kan ku, zan zab’i kasancewata da shi na
rabu da kowa saboda shi.” Daga haka ya ja bakinsa ya tsuke yana jin hukuncin da
ya zartar a zuciyarsa shine daidai su suka damu da Mulki suke kuma d’okinsa.
Shi a yanzu Son da yake wa jaririn hannunsa ya fatattaki son da ya kewa Mulki
dama shi ba ma’abocin son Mulkin ba ne don dai jama’ar Gabas sun nace sai
shine, Business d’in da yake yi a k’asashe daban-daban ya ishe shi rayuwa don
yana da ku’di ba na wasa ba.
Gunguni da k’ananan surutai ne suka dinga tashi a Babban
Falon Fulanin kowa yana furta abinda yaga dama akan wannan maganar, Abu d’aya
fuskokinsu suke nunawa duk da basa son bayyanuwar hakan sai dai kallo d’aya
Sarki Mukhtar yake musu ya tabbatar da Burinsu ya cika! Haka dama suke so idan
Jama’a suka ji abin kunyar da ya aikata su masa tawaye su kuma yi tur da Allah
wadarai da Mulkin nasa. Don zina A masarautar Gabas Babban laifi ne a zamanin
da yake sawa har su jefe mutum ko kuma a masa d’aurin talala. Balle Sarki da
kansa? Da d’an da suke tunanin d’an shege ne a hannunsa. Fulani dai tana zaune
tana jin zuciyarta ta yi wani irin nauyi sam maganar da Mijin nata ya yi bata
mata da da’di ba, sai dai ta san ko giyar wake ta sha ba yarda za’a yi ta
fuskanci Mukhtar da wannan zancen, duk da yake mutum mai sauk’in hali gefe guda
kuma yana da zafin zuciya a lokuta da dama kuma mutum ne shi Mai zurfin ciki.
Ta ja bakinta ta tsuke ga wani irin ciwon baya da na mara da ya zo mata lokaci
guda.
Da k’yar k’ananan maganganun suka lafa kafin kowa ya mik’e
suka fice d’aya bayan d’aya zuk’atansu d’auke da madaukakin farin ciki da ya
kasa b’oyuwa a saman fuskokin su, duk da k’ok’arin da suka yi wajen b’oye
hakan.
Shiru parlourn ya d’auka, ba kowa daga Sarki sai Matansa
guda hu’du biyu ba gaske biyu kuma daga ciki sun san Matan Jabu ne, tunda ba
aure a tsakaninsu. Sarki Mukhtar ya d’ago a hankali yana nazarin fuskokin Matan
nasa da kai tsaye zai iya hango matsananciyar damuwa da take kwance akan
fuskokinsu musamman biyun Fulani Rahina da Fulani Saddik’a su fi nuna
matsanancin tashin hankali duk da na Rahina ka’dan akan na Saddik’a da bata ma
da cikin ba kuma ta da alamar sa, gwara Rahina zata iya haihuwa nan kusa. Su
kuwa sauran idan ya yi nazarin fuskokinsu zai iya d’orasu a mizanin Kadaran
kadahan duk inda ta kwana sha ce, tunda su da kansu sun san igiyoyin auren nasa
a wajen Sarki Mukhtar sun mutu murus ba ko d’aya. Ya saki sauk’akkar a zuciya
kafin murya a dake mai sautin Amon rashin tsoro ta daki dodon kunnensu. “Ku
saka a ranku Murad d’ana ne Jinina ne, kuma ina son kowa ta masa kallon hakan
bana son wata magana bayan hakan, kuma ban ce kowa ta tambayeni dalili ba abu
d’aya na sani da Kuma shi zan gaya muku ba wata mu’amalar banza da ta tab’a
ha’da ni da wata Mace, ban san ta yarda aka samar da cikin ba kamar yarda ban
san a yaushe na kusanci wata Macen na mata ciki ba, wanda ya aikata shi ya san
ya ya samar da cikin ko shi ko Uwar yarinya, abu d’aya da zan fa’da idan likita
ya tabbatar da Murad Jinina ne, zan rungumeshi zan nuna masa So ba Kuma zan
laminci a nuna masa k’yama ba zan iya rabuwa da kowa saboda Murad, dafatan kun
fahimta?” Ya fa’da yana ware idanunsa masu tsananin kyau da kwarjini a kansu.
D’aga kai suka yi alamar sun gane sun kuma Fahimta. Ya dubi Fulani Saddik’a
Mace mai hak’uri kawaici mara son tashin hankali sab’anin Fulani Rahina da ta
zama Mace mai fa’da da masifa ga saurin fushi ya ce “Saddik’a zo nan.” Ta mik’e
jikinta a sanyaye ta isa wajensa. “Daga yau na baki Amanar Murad, Ina son ki
saka a ransa ke ce Uwarsa ke kuma kika haifesa kada ki bar wani abin cutarwa ya
rab’esa zaki iya?” Cikin wani irin tsananin farin ciki Fulani Saddik’a ta d’aga
kai tana jin duk wani bak’in cikinta ya yaye. Ta saka hannu biyu ta amshi Murad
tana saka shi a jikinta ta rungume wata irin zazzafar k’aunarsa tana bin sassan
duka jikinta. Da gaske Sarki Mukhtar ya gama mata komai. Fulani Rahina kuwa
hankalinta ne ya tashi jin hukuncin da Sarki ya zartar lokaci guda, idan har
tana fahimta daidai shikkenan Fulani Saddik’a ce zata zama Uwar Sarki mai jiran
gado, duk da ta san Al’ummar Garin Gabas ba za su amince D’an Shege ya Mulkesu
ba, duk da Haka bata so ba, bata so a bawa Saddika ba, me Yasa SARKI bai bata
ba duk da Kowa a Gabas ya san itace MOWAR SARKI, ita Sarki ya fi so kamar yarda
kowa ya shaida itace mai fa’da a ji a Fadar Garin Gabas. Cikin fushi mabayyani
ta kalli Sarkin da ya d’auke fuskarsa tamau “Me yasa za’a bawa Saddika alhali
ni ce Uwargida?” Sarki Mukhatr ya zuba mata ido kafin shima nasa ran a b’ace
cikin zafin murya ya ce “Haka na yi niyya.” Ya juya ga Saddika da ta sake
rungume shi tsam a jikinta ya ce “Ki je da shi Sassana a can na amince ki yi
rainonsa saboda bana son a yi wasa da lafiyarsa idan komai ya kammala ma barin
k’asar za ku yi ke da shi za ku koma England har sai Ya girma sannan zaku dawo
ni da kai na Zan dinga zuwa muku ziyara, abu d’aya nake son sani yanzu likitoci
su tabbatar Murad Jini na ne. Za’a siyo Madara da duk abinda yake buk’ata.” Fulani
Saddik’a ta sake d’aga kai kafin ta mik’e rungume da Mukhtar a jikinta ta bi
wata hanya da kai tsaye zata kai ta sassan Sarkin. Fulani Rahina ta bita da
wani wulak’antaccen kallo tsanarta da kishinta yana sake kambaba a zuciyarta ji
take kamar ta je
Ta mak’ureta da ita da Shegen jaririn su Mutu gaba d’aya ko
ta huta da ciwo da ra’da’din zuciya. Sarki da yake hankalce da ita bai mata
magana ba, har sai da su Fulani Maimuna da Fulani Habiba suka fice sannan ya
dawo da kallonsa gareta cikin muryar garga’di ya ce “Ki aikata abinda yake
ranki, tabbas kina son ki bi sahun su Maimunatu don zan iya aikata komai game
da tsare rayuwar Murad.”
Daga haka ya Mik’e cike da taku mai nuna nagarta da k’arfin
Mulki ya bi bayan Fulani Saddika. Wannan furucin nasa shi ya sake gigita Rahina
ta rasa natsuwarta gaba d’aya ta san tunda ya furta tabbas yana nufin abinda
yake cikin zuciyarsa ne kai tsaye.
Ta ciji yatsa a hankali tana sake jin azababben ciwon na
sake dawo mata k’ugunta kamar zai b’alle.
(Ku cigaba da biya masoyana da’din
Littafin na gaba wannan duk shimfi’da ne. Kamar yarda na
fa’da In sha Allah. 500 zuwa asusun banki kamar haka 2118666253 UBA. Sai a tura
shaidar biya ta numberr waya 08033748387.
JIKAR NASHE.✍π½
K’UDIRAR ALLAH.
11.
NAZEEFAH SABO NASHE.✍π½
08033748387.
Yarda gumi ya jik’a Fulani Saddik’a zai tabbatar maka da
nak’uda ce take yi mai azabar gaske. Runtse ido take yi kawai tana cije bakinta
kukan ma ya k’i zuwa sai cizon leb’enta take. Hakan ya janyo hankalin Barorinta
ba shiri suka yi yo kanta da sauri da k’ok’arin son su taimaka mata. Zafin
ciwon da take ji ne yasa tana ji tana gani suka kamata zuwa cikin d’akin.
Kafin su juya sanar da Jakadiya ta yi wani irin k’akkarfan
nishin da yasa kan Babyn ya danno da
K’arfin gaske. Ta saki hucin wahala a hankali tana duban
abinda ta haifa, zuciyarta ce ta kusan bugawa ganin jaririyar yarinyar a
gabanta. Da k’yar ta ha’diye yawun da ya tokare mata a mak’oshi ta janye
hannunta ta d’au jaririyar a hannunta kamarsu guda da y’ar ba abinda ta d’auko
na Ubanta. Hawaye ne ya so ya kece a idanunta sai dai ta yi k’ok’ari sosai ta
danne abin a ranta ganin yardaddun barorinta a wajen.
Labari ya kara’de masarautar gabas aka fara sanar da
haihuwar Fulani Saddika kowa ya cika da al’ajabi gefe guda kuma ana tunanin a
ina aka samo wancan jaririn da aka tsinta? Sanda Sarki ya samu labarin bai ji
komai a ransa ba kamar yarda ya samu farin ciki da aka kawo masa Murad a
matsayin d’ansa bai sani ba ko don Macece. Da kansa ya taso zuwa b’angaren
Fulani Saddik’an don ganin lafiyar ta da ta jaririyar da ta haifa. Ido Fulani
ta zuba masa lokaci guda kuma abinda yake ranta ya kasa b’oyuwa a zuciyarta sai
da ta bayyana kuka ta saka sosai kukan da ya raunata zuciyar Sarkin gabas bai
san sanda ya k’arasa wajenta ba da sauri ya fara tambayar ta lafiya?” Hawayen
ne ya fara zubo mata ba kakkautawa kafin ta sanar masa damuwarta na rashin
samun muradinta Magajin Sarkin Gabas. Shiru ya yi yana zuba mata idanunsa masu
cike da kyau da Haiba kafin ya saki ajiyar zuciya ya ce “Ki k’addara haka Allah
ya so ki ma gode masa da ya baki d’iya macen ki kuma yi fatan ta rayu…” Ta
ha’diye kukanta ta yi tunawa da budulcin da taso ta yiwa Allah da sauri ta ce
“Astagfirullah.” Ta kuma sake rungume jaririyar a
Jikinta cikin nutsuwa take sauke ajiyar zuciya. Sarkin
Mukhtar ya saki murmushi a
Hankali shima. Yana cigaba da nazarin Saddik’ar da bata iya
b’oye abinda yake ranta. Da kansa ya amshi yarinyar ya kuma yi mata hu’duba Da
Fateema.
Daga lokacin da visar su ta fito ya ha’da Murad da Uwar
rainonsa zuwa k’asar England inda a can ya fara karatu ba kuma ya zuwa ko ina
sai idan an yi hutu yake zuwa Nigeria, don haka mutane da yawa ba su san shi ba
saboda rashin son hayaniyar sa da shiga mutane.
Sanda Sarki ya gama ba shi labarin tuni jijiyar kansa ta
tashi ta yi ra’da ra’da, idanunsa sun sake girma kamar yarda suke kasancewa
idan yana cikin b’acin rai. Hannu kawai ya saka yana murza goshinsa da yake
sara masa kamar zai dare. Ya
Lumshe idanunsa so yake
Hawayen su zuba sai dai juriyarsa da izzar sarauta ga
allurar sojojinsa mai saka zuciyarsu dakiya sun hana shi zubar da hawayen.
Ya mik’e yana furzar da huci a hankali, Sarki yana ji yana
gani ya fice daga fadar duk da yanayin da yake ya ci a dakatar da shi sai dai
ya san a wannan lokacin ba wanda ya isa ya dakatar da Murad. Nutsuwa yake so ya
samarwa kansa kafin zafin zuciya ya saka shi ya Jirge fushinsa a kan duk wanda
ya yi nufin shiga gonarsa.
Har ya isa b’angarensa hucin yake furzarwa, jin alamun
Hadimansa suna binsa ba tare da ya juyo ba ya dakatar da
Su ta hanyar d’aga musu hannu. Yana shiga ya rufe k’ofar da
saurin gaske hannayensa duka biyun ya dinga dukan bangon d’akin da su, tunani
ne fal ya cika zuciyarsa so yake ya hango wacece mahaifiyarsa shin shi d’in
d’an Sunna ne ko d’an haram, dole ba zai zama d’an Sunna ba tunda dai sarki da
kansa ya san bai tab’a kusantar wata mace ba sai Matansa hu’du idan haka ne ya
zama dole ya gano ta hanyar da aka samar da shi wacece kuma Uwarsa?
______________________
A gefen Baffa Jaheed yake zaune kansa a k’asa zuciyarsa a
raunace take sosai jin zantukan da Baffan yake yi. “Gobe zata tare a gidanta ba
wata bidi’a da za’a yi don na ga Uwarta bata neman zaman lafiya da ni.” Zuciyar
Jaheed ta shiga wani irin bugu da da hali da kansa zai dakatar da Baffa daga
wannan zancen don bai hango ta yarda zamansu da Najma zai yi tsawo ba. Amma
kima da martabar Baffan ta hana shi furta komai illa ha’diyar yawu mai kauri da
ya yi ya d’agawa Baffan kai murya can k’asa Kuma ya yi furucin godiyar da ya
san tabbas ba ta kai har zuciyarsa ba. Baffa ya d’aga kai ya ce “Ni zan gode
maka Mujaheed da aka amince da auren mara kunyar yarinya irin Najma sai dai ina
son ka yi hak’uri da duk abinda zai faru wata rana sai labari wata rana kuma da
Kan ka zaka gode min.” Jaheed ya d’aga kai duk da bai hango
sanda ranar zata zo ba in dai har da Najma yake tare yarinyar da ta tashi da
tsanarsa a zuciyarta tun k’uriuciyatta. Jaheed yana fita Baffa ya mik’e zuwa
cikin gidan. Fuskarsa a d’aure ya shiga sashen Mahmeey a parlour ya zauna kafin
ya saka Nasma ta kira masa Najma. Fuskarta a ko’de ta fito daga d’akin da alama
ranar ma yini ta yi tana kukan. A gaban Baffan ta zube idanunta suka cigaba da
zubar hawayen da suke. Baffa ya bita da kallo mai cike da nuni da zallar jin
haushi kafin cikin takaici ya kira sunanta murya a kaurare. Najma da sauri ta
d’ago kafin ta rusunar da k’wayar idanunta tana jin ko kasheta Baffa zai yi ba
zata amince ta zauna da d’an mahaukaciya ba, da ta zauna da shi gwara ta gudu ta
bar gidan. “Dole ne ki zauna da Jaheed in dai kina amsa sunana a matsayin
mahaifi idan kuwa kin shirya goge sunana daga matsayin mahaifin Ki sai na ce
Bissalam.” Ya furta mata kai tsaye kamar ya san abinda yake ranta. K’irjinta ne
ya buga sosai murya a sark’e ta ce “Baffa bana son shi na tsane shi kamar yarda
na tsani mutuwata Wallahi zan iya kashe shi na kashe kai na a duk sanda ya amsa
sunan Mijina…” wani irin Mari Baffa ya bata, kamar an cillo Mahmeey cikin
tashin hankali ta janye ta tana furta “Kada ka sake dukar min y’a akan wancan
banzan shashashan…” Baffa ya d’ago ransa a b’ace yana kallonta ya furta “Idan
kin ga bata amsa sunan Matar Jaheed ba sai dai idan na daina amsa sunan
Ubanta……” wani irin jan burki Mahmeey ta yi kafin ta ce “Akan d’an mahaukaciyar?”
Baffa ya d’aga mata kai cike da tabbatarwa. Mahmeey ta saki dariya kafin ta ce
“Ai dama ni na san ba banza ka ke zaune da matar nan ba akwai wata a k’asa…”
wani kallo Baffan ya mata wanda ya sata shiru ba shiri shi kuma ya mik’e yana
nuna Najma ya ce “Ki shirya gobe kamar yanzu Mijinki zai d’auke ki zuwa
gidansa.” Ba Najma ba harta Mahmeey sai da k’afafunta suka kasa d’aukarta suka
zauna a k’asa cikin tashin hankali Baffa kuwa bai bi ta kan su ba ya fice daga
sashen yana jin hakan da ya yi shine daidai idan har ya bar Najma bai aurar da
ita ba tabbas Mahmeey zata iya b’ata masa tarbiyyarta. Mahmeey shiru ta yi
kafin ta jawo wayarta ta fara kiran waya tana magana cikin tashin hankali. “A
yi koma me ye akan lamarin nan, bana son a yi tariyar nan Don Allah Malam.”
Shiru daga d’aya gefen kafin Mahmeey ta ce “Na yarda Malam koma me ye a yi masa
idan ma haukata shi za’a yi a yi, ko kuma a birkita shi ya saketa dole.” Ta
kashe wayar tana kallon Najma da ta kwanta a jikinta tana kuka. “Ki rufe min
baki komai Malam ya ce zai zo da sauk’i abu guda muke so ki ba mu ha’din kai.”
Najma ta d’aga kanta tana sakin ajiyar zuciya a hankali.
Jaheed kuwa da jan k’afa ya shiga sashen Umma. Umma tana
ganinsa ta san ba lafiya ba. Ajiyar zuciya ta saki a fili ta furta “Ka yi
hak’uri Jaheed taka k’addarar kenan.” Ya saki ajiyar zuciya a hankali kafin ya
d’aga kai ya kalli Najee da ta yi zuru zuru idan ba kallon tsoro ya mata ba sai
yaga kamar har rama ta yi. Ya lumshe idonsa kawai kafin ya ce “Najwa kawo min
Lipton tea, amma Honey zaki yi using ba Sugar ba.” Najwa da sauri ta mik’e don
cika umarninsa. Tea d’in ya sha mai zafin gaske kafin ya sauke cup d’in yana
sakin ajiyar zuciya yarda tea d’in yake da zafi haka yake jin zafi a zuciyarsa.
Tsawon mintuna kafin a hankali idanunsa a lumshe ya ce “Baffa ya ce zata tare
gobe.” Umma ta d’aga kai ta ce “Allah ya nuna mana yasa a ce gara da aka yi.”
Bai amsa ba don ya san da k’yar hakan zata faru. Tsawon 1 hour ba mai iya
magana a cikinsu kafin ya mik’e cikin rashin sukuni ya yi hanyar sashen
mahaifiyarsa. Can yake so ya je ya yi kuka a jikinta ko ya ji sanyi a
zuciyarsa. Jin motsi yasa Nene komawa ainahin suffarta ta mahaukaciya duk da
rashin sukunin zuciya da ta tashi da shi hakan yasa idanunta suke cike jingim
da hawaye. Jaheed ya zauna a gabanta jikinsa a sanyaye ganin kamar bata jin
da’di ya d’ora hannunsa akan goshinta ya ji ba d’umi, sai sannan hankalinsa ya
kwanta. Hannunsa cikin nata ya ce “Nene gobe zata tare.” Idanu kawai ta bi shi
da shi, bai damu ba don sau tari tana kasancewa cikin wannan yanayin. Ya d’auke
idanunsa a kanta. Suka zauna jigum jigum Nenne a
Lokacin zuciyarta ta tafi tunanin irin rayuwar auren da
Jaheed zai yi da matar da bata son sa bata k’aunarta. Ya da’de a zaune kansa a
kan cinyarta yana zubar da hawaye addu’a yake Allah ya dawo da ita cikin
hankalinta ta sanar da shi ko shi waye. Tsawon lokaci yana kwance kafin ya
mik’e yana d’auke hawayen idanunsa ya fice daga d’akin. Kuka Nene ta saki sosai
tana furta “YA Allah ka kai mu lokacin da zan sanar da Jaheed asalinsa….” Turo
k’ofar aka yi idanunta ya fa’da cikin na Najwa da take kallonta cikin mamakin
jin abinda ta fa’da don duk abinda ta fa’da a cikin kunnuwanta………
JIKAR NASHE CE. ✍π½
Kin biya ko kuwa? Book 1 ne free Book 2&3 paid ne akan
500 kacal via 2118666253 UBA
Sai a tura shaidar biya ta wannan numberr 08033748387.
Na gode masu min waya min yi biki lafiya mun gama lafiya sai
fatan Allah ya basu zaman lafiya. Na gode sosai
K’UDIRAR ALLAH
12.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
Runtse idanunta ta yi gam sanin cewa Najwa ta gama jin
abinda ta fa’da d’in, ga shi bata da ikon mayar da maganar cikinta da ta mayar.
Najwa kuwa cikin mabayyanin mamaki ta k’arasa
Wajenta jikinta a kasalance ta zauna daf da ita tana jan
hannayenta ta ce “Nene na ji kin yi magana kada ki min pretending da gaske kin
san asalin Jaheed duk shekarun nan ki ke walagigi da rayuwarsa sannan kika
d’orawa kan ki cutar hauka na k’arya, me yasa kika aikata haka Nene?” Idanunta
ta bu’de cikin na Najwa da itama ta kafe ta da nata idanun ko k’iftawa bata yi.
Hawaye ne kawai yake sauka daga idanun Nene ta rasa yarda zata yi ta mayar da
su a yanzu dai kam ta san ba zata iya k’arya ta Najwa ba don yarinyar tana da
kaifin tunani da k’wak’walwa irin ta manya. Najwa ta sake jan hannunta tana
matsawa a hankali ta ce “Ki sanar da ni Nene.” Nenen ta saki ajiyar zuciya a
karo na farko bayan shekaru da dama ta yi magana da wani cikin hankali ba cikin
pretending d’in hauka ba. “Ki yi alk’awari idan na gaya miki zai zama sirri
tsakanin ni da ke ko Jaheed ba zaki fa’dawa ba?” Najee shiru ta yi tana tunanin
d’aukan alk’awarin tana tunanin girmansa da raunin da zuciyarta take da shi
wajen b’oyewa Ummanta abu don itace aminiyarta don haka ta tafi tunani. Son jin
labarin yasa ta d’ago tana kallon Nenen ta ce “Zan d’aukar miki alk’awarin ba
zan gaywa kowa ba sai dai bani da juriyar da zan iya d’aukar miki alk’awarin ba
zan gaywa Umma ba.” Nene ta yi shiru don bata son Umman ma ta ji maganar sai
dai kuma tana tunanin sanin Umman ba zai zama Aibu ba idan har ba Jaheed za su
gaywa ba ita
Kuwa bata son Jaheed ya san maganar har sai ta san sanadin
yarda ta samu Mijinta. “Na
Amince ki gayawa Umma.”
Ta fa’da cikin sanyin murya da taruwar k’walla a k’asan
idonta tsoro take ji sosai idan abu ya fasu a duniya har ya isa inda bata son
ya je ta tabbata wad’ancan mutanen da suke harin rayuwarta za su iya kasheta.
Gefe guda kuma nauyi da kunyar idanun Abba ne yake shirin mama ye tunaninta, da
wani ido zata kare kanta da tsawon lokacin da ta d’auka tana jinginawa kanta
hauka lamarin da girma da kuma
Kunya. Najwa cike da zakwa’din son jin labarin ta dafata
tana furta “Bari na kira Umma ki bamu labarin nan a gabanta.” Kasa hanata ta yi
duk da k’ok’arin hakan da ta yi tana kallo ta fice cike da karsashi. Nene ta
lumshe idonta a ranta tana furta shikkenan yau dai ta faru ta k’are komai zai
bayyana kansa sai fatan Allah yasa su fahimceni su fahimci abinda yasa na
aikata hakan.
Daga yanayin fuskarta Umma
Ta gane tana cikin wani tsananin farin ciki da har ya kasa
b’oyuwa a cikin idanunta. Hannun Umman kawai ta kama tana furta “Umma zo ki
ga.” Umman tana tambayar ta amma ba amsa jan ta kawai take zuwa sashen Nenen.
A zaune suka samu Nenen, idanunta na zubar da k’walla. Najwa
ta ce “Nene ga Umman yi magana.” Nene ta kasa magana illa ha’diyar zuciya kawai
da take yi tana danne zuciyarta da take jin b’acin rai kamar yanzu komai ma ya
faru. Umma kuwa cike da al’ajabi take kallon Najwa ta ce “Wai me ya faru kin
bar ni a cikin duhu?” Najee ta saki ajiyar zuciya tana furta “Umma Nene tana
cikin hankalinta yanzu zata miki magana.” Umma ta ware ido tana furta
“Alhamdulillah bari na kira Baffanku na gaya masa da Mujaheed.” Da sauri Najee
ta ja hannunta tana girgiza mata kai “Ki zauna Umma bana son ki kira kowa Nene
bata son a san tana cikin hankalinta,
duk tsawon shekarun nan Ashe ba hauka take ba….” Kallon da Umma ta yiwa Najwa
ne ya sata ha’diye sauran abinda ta yi niyyar fa’da don idanun Umma sun nuna
zallar mamaki da
Jin abinda ta ce d’in. “Najwa bana son shirmen banza ta yaya
zata jinginawa kanta hauka….”
Da gaske ne Umman Jaheed ba mahaukaciya ba ce ni, amma ina
son ki min afuwa ki kuma rufa min asiri a yau Zan sanar da ku asalina da abinda
ya baro ni daga gida Amma don Allah ya zama sirri bana son ko Jaheed ya sani…”
Turus Umma ta zauna a gefen gadon k’irjinta yana matsanancin bugu Baffa kawai
take tsoron ya san labarin nan don idan har ya sani ba zai yafewa Nenne ba, ya
tsani mutum mak’aryaci balle ita abin nata ya yi yawa ma sosai ta yarda ta
yaudaresu tsawon shekaru ta musu wasa da hankali a zuwan mahaukaciya ce ya
dinga kashe ku’dinsa a kanta a banza tabbas ba zai sake yarda da lamarinta ba.
“Ki yi hak’uri ki yafe min dalili mai k’arfi ne ya saka ni aikata haka ba son
raina ba.” Umma ta ja ajiyar zuciya tana ha’diyar yawun da bata shirya
wucewarsa ba. “Shikkenan ina jin ki, me ya rabo ki da gida kuma wacece ke?
sannan Ina son ki gaya min gaskiyar zance bana son k’umbiya k’umbiya..” Umma ta
fa’da zuciyatta na sake rauni tana fatan Allah yasa Jaheed ba shege bane ta yi
cikinsa ta gudu daga gida ta jinginawa kanta haukan dole.
Nene shiru ta yi zuciyarta rawa take da matsanancin bugu,
duk da a ranta tana son furta abinda yake ran nata wanda ya hanata sukuni
shekara da shekaru sai dai wata zuciyar tana kwab’arta ga barin aikata hakan.
“Yi magana mana.” Umma ta fa’da idanunta akan Nenen da ta ga hannunta yana rawa
kamar ma jikinta b’ari yake. Don ta kwantar mata da hankali sai ta kama
hannayenta “Ki yi magana In sha Allah Zan rufa miki asiri in dai Baffa ne ba
kya so ya sani ko wani nasa ba zan bari ya sani ba balle shi, yanzu dai abinda
na fi buk’ata sanin asalinki da yarda kika samu cikin Jaheed saboda ina jin
tsoro a zuciyata ina fatan Jaheed ya zamo tsarkakken d’a ba kamar yarda
zuciyata take tararrabi ba.” Sai sannan Nene ta saki ajiyar zuciya ta d’ago
raunannun idanunta da suke zubar da k’walla ta zubawa Umman kafin ta lumshe su
cikin muryarta mai sanyi ta fara ba su labarin rayuwarta……
___________
Sunana Fatima wacce aka fi kira da Fatu a can garin mu na
Gabas. A cikin masarautar aka haifeni a ciki kuma na taso na girma tunda
iyayena bayi ne a masarautar. Tun bayan taso wa ta ban tab’a ganin sanda
Iyayena suka zauna suka huta ba kullum a cikin wahala suke da har ta bayyana a
jikkunansu ta hanyar rashin wadatuwar lafiya tattare da su. Sunan Mahaifiyata
Inno mahaifina Kuma Babani, mutanene da suka nuna mana asalin soyayya da kulawa
musamman ni da na zamo mace a cikin yaransu maza guda biyar.
__________________
~SHEKARU TALATIN DA SUKA WUCE.~
MASARAUTAR GABAS…
Masarauta ce mai tsohon tarihi da girman gaske ha’de da
k’arfin mulki da kuma gamammen arziki. Duk wanda ya san Masarautar gabas ya
santa da wadatar arziki game da k’ak’karfan ikon mulki da ake gudanar da shi
bisa son rai da zallar mugunta. Duk da Sarkin sarki ne mai adalci da kuma son
kyautatawa al’ummar sa, sai aka yi rashin dace da wa’danda suke kewaye da shi
su kuma mutane ne Mugaye da ba abinda suka sani sai zalunci da son bak’antawa
talakawa kamar yarda tarihi ya nuna. Mahaifinsu Sarki Abdallah kafin rasuwar sa
mutum ne shi mai nagartattun halaye wanda ya sanya mutane suke son sa musamman
talakawa da ya zamo Katanga abin jinginarsu, basu tab’a kuka da shi ba kamar
yarda a zamanin sa aka samu wadatuwar arziki aka rabauta daga talauci don kuwa
ya d’agawa talakawa k’afa sosai ya kuma bu’de musu hanyoyin samun ku’di a
sauk’ak’e ta yarda kowa yake washshalawa cikin farin ciki da ginuwar arziki.
Y’ay’ansa Ashirin da takwas sai dai Babban d’ansa su biyu
kacal mahaifiyarsu da ake kira Fulani ta haifa da shi da y’ar uwarsa mace guda
Fatume, Shi Kuma sunansa Mukhtar da mahaifinsa yake kira abin zab’i. Soyayyar
mahaifinsu ga Mukhtar soyayya ce mai girman gaske da baya iya b’oyeta a
idanunsa kowa ya sani yana son Mukhtar ne saboda rauninsa da tsananin son
addininsa da mahaifiyarsa ta d’ora shi a kai. Ya yi farin ciki sosai da samun
Mukhtar a matsayin Babban d’ansa da zai gaji sarautar gabas saboda yarda halaye
da d’abiunsa suka barranta da na y’an uwansa. Su
Mutane ne masu zuciya mara alheri a cikinta sai gungumen
Sharri burinsu kullum cusgunawa talaka da Kuma bak’anta musu
kamar yarda suke d’aukan duk wani talaka wulak’antacce kuma k’ask’antacce.
Sosai yake jan Mukhtar a jikinsa tun bayan da ta fara rashin lafiya da yake ji
a jikinsa kamar cutar ajali ce ta kama shi ya dinga nuna masa dabarun Mulki da
yarda zai dinga samun nasara akan Mak’iya koda sun nufoshi da Sharri ba abinda
zai same shi da izinin Allah da kuma kariyarsa.
Tun kafin rasuwar Mahaifinsu bak’in cikinsu a kan Mukhtar ya
bayyana muraran ta yarda suke son ganin bayansa. Sun kuma sha kai masa Farmaki
Amma Allah yana kareshi. Kafin mutuwar mahaifinsa Mukhtar ya yi aure da d’aya
daga cikin y’ay’an Sarkin Yamma wacce ya yaba da hankalinta. Watanninta bakwai
Allah ya yiwa Sarki Abdallah rasuwa. A ranar da kuma ya rasun Mukhtar ya haye
kujerarsa ta Mulki inda aka na’da shi SARKIN GABAS. Nan y’an uwansa suka shiga
Hassada da bak’in ciki iri iri ta yarda Mukhtar d’in ya dinga tsallake
sharrinsu da Makircinsu har ma da k’ok’arin kashe shi da suke son yi duk da
komai suna aikata shi ne a b’oye a kuma sirrance.
BAYAN SHEKARU DA HAWANSA KAN MULKI.
Bai tab’a samun haihuwa ba hakan ya ‘daga hankalinsa da duk
wani mai k’aunarsa duk kuma inda ya je za’a sanar da shi lafiya yake ko da yake
tabbas da gaske lafiya yake tunda Sau kusan biyar matarsa tana haihuwa d’an
yana rasuwa ko kuma tun cikin bai girma ba sai ta yi b’arinsa. Bisa tilas
Mukhtar ya Amince da shawarar y’an uwansa akan ya k’ara aure. Aka aura masa
mata Uku lokaci guda suma dai sun d’an jima babu haihuwar hakan yasa Mukhtar ya
tattara lamarin haihuwa ya jingineshi a gefe, musamman da aka wayi gari
k’anwarsa ta yi hatsari ta rasu motar ta k’one k’urmus ko gawarta ba a cire ba,
sai d’anta da ta bar musu a wajen Mukhtar ta tafi ashe sallamar kenan shikkenan
Mukhtar sai ya tattara duk soyayyar sa da kulawarsa ta koma kan Abdallah
k’arami da ake kira Halifa. Ya saka a zuciyarsa tabbas ba shi da rabon ganin
d’ansa ne a rayuwa don haka ko Abdallah ka’dai Allah ya bar masa ya gode masa.
Wata irin guguwar tashin hankali ta fara faruwa a Masarautar
ta yarda akewa y’an mata fya’de bisa son rai dana zuciya wanda kowa ya shaida
ba wanda yake aikata musu hakan sai jinin Sarautar da suke gidan musamman yarda
samarin y’ay’an y’an uwan Sarkin suka girma suka balaga to fa a duk sanda suka
k’yallara ido suka ga budurwa basu da buri irin suga sun keta budurcinta ko da
da k’arfin tuwo ne.
Sarki Mukhtar bai san da wannan labari ba, ranar da ya ji
kuma hankalinsa ba k’aramin tashi ya yi ba. Ba shiri ya saka aka tara masa
taron Mata da Bayi da y’an matan da suke cikin masarautar. Aka cika a filin da
yake harabar masarautar zuwa lokacin a k’idaye an ketawa y’an mata hamsin
mutuncinsu wasu sun samu ciki wasu kuma sanadiyyar haka sun rasa ransu, wasu
kuma sun samu motsuwar kwanya. Sarki Mukhtar Bn Abdallah, ya dinga sakin ajiyar
zuciya ana iya juyo sautin ta ta cikin loud speaker da take hannunsa, kafin ya
yi sallama cikin sakakkiyar muryarsa mai bayyana tarin nutsuwarsa da kamalarsa.
“Mun yi tur mun yi Allah wadarai da wannan abin da yake faruwa a masarautar
Gabas, bisa zalunci da son zuciya an wayi gari ana keta
Mutuncin y’an mata, don haka mun zauna da mahukunta
masarauta ta yarda zamu saka ido sosai a cikin masarauta duk wanda aka sake
samu da laifi irin wannan tabbas hukuncin sa kisa ne, ba zamu yarda da zalunci
da keta haddin d’iyoyin mu mata ba, abu na gaba Mata mun sabunta musu suturarsu
ina nufin y’an mata da suke yawo ba mayafi daga cikin bayin mu, a yanzu
masarauta Zata raba su kayan da zai rufe jikinsu sink’if ba tare da an ga ko da
yatsan k’afarsu ba madadin wancan kayan da suke sakawa da yake bayyana surar
jikinsu yake kuma banbanta su da iyayensu, a yanzu masarauta zata mayar da
suturarsu irin ta iyayensu don gujewa ya’duwar Fasadi a cikin Masarautar Gabas.
Duk Macen da aka sake samu an mata fyad’e kai tsaye zamu jingina laifin ne kan
Iyayenta akwai kuma mummunan hukunci da zai biyo kanta da iyayenta gaba ‘daya,
don haka ya zama dole gareku Iyaye ku saka ido akan d’iyoyin ku mata, ba mu
amince da sake ganin Mace bayan sallar Magriba ba ko cikin dare a waje dafatan
zaku kiyaye.” Hukuncin sosai ya yiwa iyayen da’di don duk masu y’ay’a mata a
masarautar zuk’atansu a cikin fargaba da taraddadi suke, don haka suka dinga
godewa Sarki Mukhtar dafatan gamawarsa lafiya tare da samun Magaji mai albarka.
Wannan addu’ar ita ta bak’anta ran wasu daga cikin mutanen wajen musamman y’an
Uwansa da suke Uba d’aya a zuciya suka dinga amsa Ba Ameen ba, In sha Allah har
gaban Abada Sarkin Gabas ba shi da Magaji. Haka taro ya tashi zuk’atan Iyayen
yara cike da farin ciki a gefe guda kuma masu aikata laifin suka k’ullaci Sarki
tare da ji a zuciyarsu ba ta yarda za’ayi su fasa aikata hakan tunda shima yana
daga cikin shara’din da Bokansu ya gindaya musu in dai suna son wani daga
cikinsu ya zama sarki ko shi ko ahalinsa to dole sai sun bi wannan hanyar ta
keta wa y’an Mata mutuncin su, sun kuma ji suka bi kuma suka sakankance da
maganar Boka GAKSIYA ce!
_______\____
Wannan shine ya d’aga hankalin iyayena.
Tunda suka koma gida Inno da Babani suka fito da ni da suka
b’oye a d’aki can bayan Gadonsu na k’arfe, Inno ta saki ajiyar zuciya tana
dubana hankalinta a tashe,Tun bayan hauhawar lamarin fya’den suke killaceni a
‘daki basa barina na je ko ina. Tsoro suke ji sosai basa son wani abu ya same
ni. Inno ta shafa kaina tana fa’din “Ya Allah ka kare min Fatu daga wa’dannan
Azzaluman.” “Idan kin tsaya tsayin daka akan tarbiyyarta tabbas Allah zai kare
miki ita.” Babani ya fa’da Idanunsa a cikin na matarsa Inno “Ban amince da
fitar Bayan Magariba kamar yarda Sarkin Gabas ya ce kin ji ko Fatu? Don ya
rantse duk wanda aka sake samun an yi wa y’arsa fya’de to hukuncin kisa ne a
kansa da y’ar tasa.” Wani irin bugu k’irjina
ya yi na d’ago a tsorace ina
kallon su da suma suke kallona. Inno ta d’ebo bak’ak’en kayan da aka
basu a fadar ta ce “Daga yau wad’annan su ne kayan sawarki Umarnin Sarkin Gabas
akan duk wata Mace data balaga a cikin masarautar nan, ba a amince da cire koda
nik’ab d’in fuskarta ba ne.” da sauri na karb’i kayan ina jin da’di jin tsorona
na yawaita ta yarda har hakan ya kasa b’oyuwa a cikin idanuwana da fuskata. Tun
bayan da aka wa k’awata fya’de da ya yi sanadiyyar rasa raina nake cikin wannan yanayin na tsoro da firgicin, ko
muryar namiji na ji na y’an gidanmu samun kaina nake da rawar jiki da na
zuciya, saboda ni Yarinya ce da ban wuce
shekaru sha bakwai ba ina da kamala da
nagartacciyar Tarbiyya da Inno bata min wasa da ita, nutsuwata ta samo asali ne
ta yarda Inno take Jana a jiki take nuna min abu mai kyau da marar
kyau, tun kuma a k’ananun shekaru na Inno ta tsoratar da zuciyata ta hanyar
nuna min kada na yarda namiji ya rik’e min hannu da zarar na amince ciki zan
samu na haihuwa duk wacce kuma ta sake ta yi cikin shege a Masarautar Gabas hukuncinta
kisa ne ta hanyar d’aurin rai da rai. Don haka da wad’annan abubuwa suka faru
na fi kowa shiga tashin hankali.
Sai dai kana taka Allah na tasa wata rana na dawo daga wajen
matar sarki da ake kira Fulani Saddik’a kasancewar ni nake kula da kitchen
d’inta don kam Inno ta min horo na girki ba na wasa ba babu girkin da ban iya
ba. Cikin duhun Magriba nake tafe sanye sunk’uf da irin shigar da aka amince mu
yi a masarautar, Da Suwaiba muke tafiya ranar kuma Suwaiba bata jin da’di bata
zo ba daidai wajen duhuwar bishiya na ji an yi sama da ni, ina k’ok’arin kurma
ihu na ji an shak’a min wani abu a hancina wanda daga nan ban sake sanin inda
kai na yake ba, sai farka wa na yi na gan ni a wani d’aki mai tsananin duhu, a
kuma lokacin na dinga jin maganganu k’asa k’asa da dariya mutane suna fa’din
mun gama aikin mu saura jira da bayyanuwar cikin idan komai ya kankama zamu
kasheta mu d’auki d’an da zai zama Sarkin Gabas ba tare da shi Sarkin ya san
shine Ubansa ba mu za mu yi rainonsa zai kuma zama abin tunk’ahon mu! Suka saki
shewa a tare.
Ba su sake bari na na sake lek’a waje ba, tun bayan da suka
fahimci ina da shigar cikin da yake duk bayan wata guda suke aunani. A daren da
za su min theatre su cire cikin ni Kuma su kasheni a daren na haihu bisa
jagorancin wasu mutane da ban san ko su waye ba na haifi d’a namiji su kuma
Abinda na lura d’an suke buk’ata fiye da wad’ancan
mutanen,su suka taimaka min suka fito da ni cikin gari suka umarceni da na gudu
na ceci raina kafin mugayen su cimmani. Sai dai wani ikon Allah ina zuwa wani
k’auye sai na fara wata nak’udar inda anan na haifi Jariri Mujaheed bisa
taimakon wasu mutane a k’auye. Cikin
dare kuma na gudu inda anan na ha’du da Baffa ya taimaka min.. wannan shine
abinda na sani Wallahi ban san ya aka yi na samu cikin yaran nan ba…” Ta fa’da
wani kuka na sake kece mata. Zuwa lokacin Umma da Najwa ma kukan suke suna
tunanin girman lamarin da ya zarce tunaninsu. Sun da’de a haka kafin Umma ta
d’ago ya share hawayenta ta ce “Yanzu Nenne ta yaya kike tunanin za’a gane Uban
cikin nan?”
JIKAR NASHE✍π½
Book 1 ne free Book 2 is 500 via 2118666253 UBA sai a tura
shaidar biya ta wannan numberr 08033748387.
Tafiyar mai zurfi ce kuma an kusa gama na bati ki biya ki
huta da takaici.
KUDIRAR ALLAH
13.
NAZEEFAH SABO NASHE.
Nene ajiyar zuciya kawai ta saki idanunta cikin na Umma tana
sake share hawayen da yake zubo mata ba kakkautawa ta ce “Allahu a’alamu Umma
Wallahi ba zan ce ba, abu d’aya nake so ku min ku rufa min asiri kada Baffa ko
Jaheed ya san wannan maganar.” Umma ta girgiza kai tana fa’din “Ai hakan ba zai
yiwu ba Nene ta yaya kike tunanin za’a samu mafita idan su Baffan ba su sani
ba? Saninsu Ai ina ga shine abinda ya dace.” Nene kuka ta saka sosai hankalinta
ya tashi ba ka’dan ba don ta san idan har Baffa ya sani to kai tsaye za’a tafi
masarautar wanda hakan yake nufin da kai tsaye magautan za su iya k’aryata
abinda ta ce kuma kisa shine makomarta. Ganin tashin hankalin da ta shiga ne
yasa Najwa sakin ajiyar zuciya tana kallon Umma ta ce “Umma mu rufa mata asirin
zuwa sanda Allah zai yi hukuncinsa.” Umma ta yi shiru a zuciyarta tana son rufa
wa Nenen asiri sai dai wata zuciyar tana tunanin tona asirin shine abinda ya
dace. Ta jijjiga kai tana kallon Najwa yarinyar da ta gasgata da lamarinta tun
yarintarta ta san tana da wata baiwa mai girman gaske wanda Allah ne ka’dai ya
barwa kansa sani a ranta ta dinga tunanin da ace Najwan wata k’atuwar budurwa
ce da kai tsaye zata turata masarautar wajen binciken asalin yarda aka samar da
cikin sai dai a yanzu ta yi yarinta ta saki ajiyar zuciya tana furta “Zan
amince da abinda kika ce, sai dai daga yau Najwa ina son ki saka a ranki kina
gama secondary zaki tafi Garin gabas yin karatun Jami’arki a can daga nan ne
zamu san yarda kika yi kika shiga masarautar gabas kai tsaye koda da niyyar
aikatau ne ba don komai ba sai don ki binciko mana asalin lamarin ta hanyar
baiwar da Allah ya baki, na san zaki iya In sha Allahu, a yanzu dai zan rufa
asirin zuwa lokacin da zan banka’da shi da kai na.” Gaba d’ayansu suka amince
da shawarar Umma a wajen Nene shekaru uku kamar yau ne ta shafe shekaru sama da
ashirin da biyar saka ye da sirrin a ranta balle wannan y’an shekarun ita kanta
a zuciyarta tana jin Najwa zata iya tana da yak’i ni da fata a kanta. Umma ce
ta mik’e ta fara fita kafin Najee ta bi bayanta suka bar Nene a zaune tana jin
wani sanyi a zuciyarta duk nauyin da zuciyarta ta yi ya tafi kamar d’auke war
iska, fitar sirrin ya jawo mata samun nutsuwar zuciya da sauk’in ciwon kan da
yake addabarta kullum. Sai dai zuciyarta ta koma tunanin yaronta Murad ko a
wani hali yake yanzu ina suka kai shi shine abinda ya tsaya mata a cikin ranta.
Ta d’an lumshe ido hawayenta na zuba tana tunanin ranar da ta d’au Murad a
cikin showel kamaninsa har a lokacin ba su b’ace mata ba Suna nan zaune ra’dam
a k’wak’walwarta kamar ma yanzu abubuwan suke faruwa. Mutane na biyu da take
son gani sune Mahaifinta Inno da Babani suna raye ko basa raye suma bata sani
ba, abu d’aya ta sani ta san suna cikin tashin hankali da rashin nutsuwar
zuciya tun bayan b’atanta, tunda ba su sake ganinta ba tun sanda mutanen suka
d’auketa.
__________________
Baffa da Magribar fari ya shiga gidan, b’angaren Umma ya
fara shiga tana zaune da ita da Nene da ta kasa sakewa balle ta bayyana a yanzu
bata cikin haukan, duk da shi Baffan bai sani ba, sai dai gaba d’aya siffofinta
sun canja zuwa sanyin hali k’warai da gaske. Gefe kuma Najee ce take ta gyara
dinning inda suka ci abinci. Baffan ya amsa gaisuwar da suka masa kafin ya zaro
waya a aljihnsa ya kira Inna Sa’a k’anwarsa da take bin sa tana d’agawa ya ce
“Sa’a kin zo ne?” Sa’a ta sanar masa tana harabar gidan. Ya kalli Umma yana
furta “Tashi ki je ga Sa’a can tazo za ku kai Najma gidan aurenta.” Umma ta
d’ago da sauri tana kallonsa sai dai bata hango alamar wasa a tattare da shi
ba, asali ma fuskar tasa a ha’de take sosai alamar baya son musu ko gaddama a
cikin abinda ya ce. Umma ta saki ajiyar zuciya tana mik’ewa idanunta akan Nene
da itama tashin hankalin da take ciki ya
kasa b’oyuwa akan ta ta fuskar. Baffa yana fita Umma ta kalli Nene ta ce
“Addu’a zaki musu Nenne da fatan alheri tunda dai Baffa a wannan gab’ar ba zai
ji bari ba, idan banda haka sam ban hango ta inda lamarin nan ya dace ba
Wallahi.” Nene ta saki ajiyar rai a fili ta furta “Allah ya ka’de fitina Umma
sai dai ki jawa d’an naki kunne duk abinda zata yi don Allah kada ya kulata ta
ci darajar Baffa.” Umma ta ‘d’aga kai kawai tana ficewa sanye da hijabinta.
Najee ta bi bayanta don son ganin artavun da za’a yi wajen fita da Najma daga
gidan don tsanar da ta yiwa Jaheed abu ne da kowa ya sani.
Umma cikin sakakkiyar murya ta yi sallama, suka amsa mata a
ciki idanunsu a kanta don jin abinda ya kawota. Mamaki ya kama Umma ganin
Najman zaune ba alamun ma ta san za’a kai ta gidan Mijin don kaya ne na barci a
jikinta gashinta ko gyaran arziki bai samu ba. Ganin ba zasu tanka ta ba don
Mahmeey sai cika take tana batsewa yasa Umman zama tana furta “Ashe amaryar
bata shirya ba? Amma Baffa ya jajib’o ni nazo na tafi da ita?” Da sauri suka
d’ago suna kallonta Mahmeey data kasa hak’urin turirin sa zuciyatta ke yi ta ce
“Ki tafi da ita gidan Uwar wa?” Umma ta d’ago cikin mamaki tana kallonta sai
dai ta kawar da b’acin ranta ta ce “A tafi da ita gidan Mijinta mana.” Mahmeey
ta zabga mata harara tana sakin tsaki ta ce “Ki je ki gayawa Mijin naki ba inda
zata je wallahi, na shiryawa duk abinda ya shiryawa amma y’ata ba zata gidan
wani matsiyaci d’an mahaukaciya ba.” Umma ta ha’diye yawu mai d’acin da ya
tarar mata ta ce “Sai dai ki d’aga waya ki sanar masa.” “Yanzu kuwa” Mahmeey ta
furta tana zaro wayar ta “Idan banda munafunci me yasa baki aura masa taki y’ar
ba?” Umma ta saki murmushi a zuciyarta tana tausaya musu wannan fa shine abinda
hausawa ke kira rashin sani ya fi dare duhu. Da sun san waye Jaheed ta tabbata
sai sun fi kowa Farin ciki da auren. Baffa na d’agawa Mahmeey ta fara masifar
da ta saka shi katse wayar ya kuma nufo sashen ransa a b’ace. Yana jin a wannan gab’ar zai iya sakin
Mahmeey idan bata bi umarninsa ba.
Daga yanayin fuskarsa Mahmeey ta san ba shi da niyyyar
saurara mata kamar yarda itama bata da niyyar sarara masa. Ya kalli Najma a
zafafe ya ce “Ke! Mik’e Ki wuce mu je, idan kuma kin k’i a bakin auren uwarki.”
Najma ta d’ora hannu a kai zata zunduma ihu Mahmeey ta dakatar da ita “Tashi ki
je Najma, amma ba wai na amince da hakan bane Saboda ina tsoron saki akwai
dalili na Wallahi ka saka a ranka sai ka yi kuka da idonka a kan wannan auren
kuma ban amince ki ragwa d’an mahaukaciya ba kin ji na gaya miki?” Ina Najma ta
saurara kuka kawai take cikin tashin hankali tana jin zata iya aikatawa Jaheed
komai a cikin daren nan ciki kuwa har da kisa idan ta kama. Don haka ba abinda
take sai aikin ajiyar rai saboda yarda zuciyarta ta cunkushe da bak’in ciki
matsananci.
Ta shige gaba ko mayafi babu a jikinta sai hular kayan da
suke jikinta na barci. Nasma ce ta yi saurin binta da hijab ta zura mata itama
kukan take taya y’ar uwarta.
Baffa ya bi bayanta da kallo yana fatan abinda ya k’ulla
d’in ya zama alheri gareta da su ma
Gaba d’aya a rayuwa, so yake ya nuna mata shi d’an Adam ko
yaya yake ba abin wulak’anta wa da tozarta wa ba ne, mutum
Yana da kima da mutuncin da Ubangiji da kansa ya ce ya
karrama shi idan banda haka shi da kansa bai hango dacewar Najma da Jaheed ba.
A zuciyarsa ya bita da addu’ar saka albarka da samun hak’uri da juriya a
zuciyarsa yana ji a ransa gatan da zai mata kenan na aura mata nagartaccen
mutum irin Jaheed.
Motar tsit daga Umma har Inna Sa’an babu mai magana sai
kukan Najma da ya cika musu kai. Aka tsaye a babban gidan Jaheed da ya gina don
zaman aurensa da Khaireey ashe ba ita ce zab’in da Allah ya masa ba. Najma da
k’yar ta fito daga cikin motar idanunta akan gidan duk da kyansa da tsaruwar sa
ya burgeta matuk’a ainun sai dai k’iyayyar mamallakin gidan ta shafi gidan ta
inda shima ta ji tana masa k’iyayyar. Ta runtse idonta tana sake damk’e
hannunta da k’arfin gaske kafin ta sake runtuma ihu.
Su Umma suka yi yo kanta da sauri suna tambayar lafiya? Bata
amsa ba illa bin su da ta yi da kallo mai cike da nuni da zallar raini. Ba su
bi ta kanta ba suka shige parlourn suna yaba kyau da tsaruwarsa komai a kam
male tsaf da shi ba wani tarin hayaniya kamar yarda Jaheed d’in ma ya zama
mutum mara hayaniya. Suka gama zage gidan kafin su saka k’afa su fice suna mata
fatan alheri. Harara ta bi su da ita a zuciyarta tana jinjina lamarin gulma da
kinibibinsu. Kamar wacce aka tsikara ta mik’e ta shige kitchen wuk’a ta fito da
ita k’arama mai kaifin gaske ta soke a jikin aljihun wandonta sannan ta koma ta
zauna tana sake risgar kuka tana ji a zuciyarta abinda zata aikata shine
daidai.
Jaheed kuwa tun bayan da ya fito daga wanka ya rasa nutsuwar
zuciyarsa. Zama ya yi kawai a gefen gado jikinsa bakomai sai rigar wanka wani
irin alhini ne a ransa na rabuwa da gida ya je ya komawa rayuwar da bai san
makomarta ba. A idanun Najma yake hango muguwar tsanar da ta masa. Ya saki
ajiyar zuciya yana tuno Khaireey da burin da suka ci a duk sanda daren aurensu
ya zo, ashe ba zai tabbata ba ashe duk abinda suke mafarki zai zama shafe
labari shuni. Ya lumshe idonsa sai ga saukar zazzafan hawaye akan fuskar sa.
Knocking d’in da Faruk ya yi ne ya dawo da shi cikin nutsuwa da hankalinsa
murya a raunane ya ce “Am coming Faruk.” Faruk daga waje ya amsa “Okay ka yi
azama dare yana yi ga friends duk suna jiranka.” To kawai ya ce ya cigaba da
shafa mai a jikinsa kamar baya so. Kafin ya samu sassauk’an yadi ya saka ya
fice da d’an sauri. Faruk ya shigo ya ja masa akwatinsa zuwa waje. Sai dai suna
isa harabar da yaga dandazon abokansu bai san sanda ya ja hannun Faruk da sauri
ba suka yi baya. Kallo guda Faruk ya masa ya gane akwai matsala. “Wad’annan
mutanen Faruk bai kamata mu tafi da su ba, ka san dai yanayin amarayar tawa sai
a hankali so ina ga har kai ma na sawwak’e maka zan je da kai na kawai.” Faruk
ya d’aga kai shi da kansa ya gamsu da abinda Jaheed ya ce don haka ya juya suka
isa gurin abokan cikin azancin harshe suka sallamesu, sannan Faruk ya ja
hannunsa wajen Baffa da yake zaune a gefen gidan wajen garden yana ganinsu ya
saki murmushin dole ha’de da nuna musu gefensa suka zauna. Jaheed zai fara
magana Baffa ya d’aga masa hannu. “Kada ka ce komai Jaheed, nima na zan ce ba
Allah ya yi miki albarka ya ka’de dukkan fitina.” Jaheed ya amsa a hankali
zuciyarsa na sake k’arfafa mutunci da girman Baffan a idanunsa. Jikinsa a
sanyaye ya yiwa Faruk sallama sai dai bai iya ya shiga cikin gidan ba yarda
zuciyarsa ta yi rauni baya jin zai iya ganin mahaifiyarsa da Umma ya san k’ara
masa wani nauyin za su yi. Suka yi sallama da Faruk ya shiga motarsa zuwa gidan
da kai tsaye zai kira gidan Khaireey don komai na cikinsa ita ta tsara ashe ba
zai zama mallakinta ba.
Yana parking zuciyarsa na sake k’arfafa bugu mai k’arfin
gaske, da k’yar ya sarrafa kansa zuwa cikin gidan. Bakinsa d’auke da addu’a ya
murd’a key d’in babbar k’ofar da zata sada shi da cikin gidan. A yarda su Umma
suka barta ya sameta fuskarta jik’a da hawaye. Tana ganinsa ta mik’e a zafafe
tana masa wani kallo da kai tsaye zai kira na raini. “Kai d’an mahaukaciya idan
ka cika kai d’an ta ne na gaske ka sake ni yanzu.” Ya juya ransa a b’ace yana
sauke idanunsa a kanta da suka canja colour saboda tsananin b’acin rai.
“Kalleni da kyau k’arya na yi ba d’an mahaukaciyar ba ne?” Wani irin taku ya yi
ya isa gabanta cikin b’acin rai ya jawota da k’arfin gaske ya cillata saman
kujera kafin ya bita a zafafe ya danne a hakan yake son keta mata mutuncinta
don ya nuna mata ba kowa ba ce ita, ji ta yi kawai ya ja rigarta da k’arfin
gaske hakan ya bata damar zaro wuk’ar da ta tana da a jikinta ta d’agata ta
maka masa a wuya…..
JIKAR NASHE✍π½
KUDIRAR ALLAH..
14.
NAZEEFAH SABO NASHE…
Wani irin runtse ido ya yi saboda zafin kartar wuk’ar, sai
dai hakan bai saka ya fasa abinda ya yi niyya ba, ta wannan hanyar ka’dai zai
hukuntata ya mata saduwar wulak’anci sai ta san akwai banbanci mai girman gaske
tsakanin Mace da Namiji. A zafafe ya yaga ragowar sutirar da take jikinta bai
bi ta kan albarkatun jikinta ba don ba so ne a gabansa ba. Da wani irin k’arfi
ya shigeta ba tausayi bakomai. Duk da ihun da take bai sarara mata ba saboda
idan tausayinta ma ya bijiro masa sai wa’dancan munanan maganganun su danne
tausayinta a ransa.Son ransa ya yi mata duk da ya sameta a budurwa bai hanashi
yi mata kusanta mugunta ba. Tun tana ihu har ta sume masa. Ya mik’e yana gyara
jikinsa kafin ya d’ebo ruwa ya shek’a mata. Idanunta na bu’dewa suka sauka
cikin nasa da yake mata kallon k’urilla tsanarsa mai girman gaske ta sake
bijiro mata sai dai bakinta a wannan karan ya mutu murus ba zata iya masa
rashin kunya ba. Jaheed ya saki murmushi yana murza yatsun hannunsa ya ce “Gobe
ma ki sake maimaita raininki a kai na Wallahi sai na miki abinda ya fi wannan.”
Daga haka ya wuce ya barta a kwance cikin azabar zafi da ra’dad’i mai shiga
kwanya, kukan ma ta kasa yi ga shi ta kasa tashi saboda yarda take jin jikinta
kamar ana zuba borkono da wani irin azabar zafi mai shiga kwanya. Kukan da take
tuni ya d’auke wata irin tsanarsa ce take sake cin zuciyarta. Tsawon mintuna
tana kwance ta kasa mik’ewa sai da k’yar ta dafa kujerar ta mik’e cikin tafiyar
tata tata ta nufi wata k’ofa da take kyautata zaton bedroom ce. Sai da ta shiga
ruwan zafin da ta tara sannan wani kuka ya zo mata mai k’arfin gaske da ta tuna
shikkenan Jaheed ya amshi abinda take tak’ama da shi, abu guda da yake ci mata
rai yarda ya mata saduwar rashin mutunci kamar wata dabba. Ga shi ya gama gane
jikinta don fatafata ya yiwa kayan ta. Ji ta yi ba abinda ba zata iya aikata
masa ba, yau dai ya yi escaping amma next target d’inta ba zata yi loosing ba
In sha Allah.
Sai da ya shiga toilet sannan ya dinga jin jiri na d’ibarsa
da sauri ya kalli gefen wuyansa a mudubi tsoro ne ya kama shi ganin yarda jini
yake malala a wuyansa, idanunsa suka fara lumshewa da sauri ya fito tun kafin
ya kai ga sumewa ya kira Faruk a waya. Faruk yana d’agawa ya sanar da shi yazo
gida yanzu ba shi da lafiya. Gaban Faruk ya fa’di sosai da sauri ya fito daga
gidan da yake ba su da nisa sosai ya shiga motarsa zuwa gidan Jaheed d’in. Ko
kafin zuwan sa Jaheed ya galabaita iya galabaita ya dai samu ya d’aure wajen da
yake zubar jinin. Yana ganin missed calls d’in Faruk ya d’aga murya da k’yar
take fita ya ce “Faruk shigo ciki ba zan iya tafiya ba jiri nake ji.” Wani irin
shock da fa’duwar gaba suka samu Faruk ko kashe wayar bai yi ba ya danna kansa
cikin gidan. Direct Master bedroom ya shiga inda tun daga bakin k’ofar ya fara
ganin jini. Zuciyarsa na bugu ya k’arasa cikin d’akin yana k’wala kiran “Jaheed
Hasbunallah me ya faru?” Numfashinsa sama sama yake fita don haka ba zai iya
amsa shi ba. Faruk ya kama shi da sauri ya Goya a bayansa suka fita bai bi ta
kan Najma ba da bata san ma sun fita ba tana can cikin tafasa da d’acin zuciya
ji take kamar ta kashe kanta don tsananin bak’in ciki da takaicin irin saduwar
da Jaheed ya yi mata ga gane mata albarkatun jiki da ya yi.
Kai tsaye asibitin wani amininsu da suka yi makaranta tare
ya kai shi bayan ya masa waya ya sanar da shi. Don ya san idan har ya kai shi
wani asibitin sai an buk’aci hukuma ta shigo ciki shi Kuma baya son lamarin ya
kai ga hukuma har sai ya san silar afkuwar abin tukun. Doctor Saif ya d’ago kai
yana kallon Faruk “Wuk’ar fa ta shiga sosai Allah ne ya kiyaye Amma sai an masa
d’inki, ko waye ya masa wannan aikin gaskiya ransa ya so karb’a.” Faruk ya ja
ajiyar zuciya ya ce “Matsala aka samu zan maka bayani daga baya, ba kowa ba ce
illa matarsa illar auren dole kenan.” Doctor Saif ya jinjina lamarin yana saka
masa drip ya ce “Ya zama wajibi ka fa’da a gida gaskiya a raba auren nan don
duk wanda zai nemi kasheka da gaske mak’iyinka ne na gaske.” Hankalinsu ya kwanta
ganin Jaheed ya samu barci bayan ya sha allurai na kashe zafi da ra’dad’in
ciwo. Sai a lokacin Faruk ya kira Umma a wayarsa ya sanar mata don bai san ta
inda zai fara yi wa Baffa bayani ba. Jikin Umma na b’ari ta juya tana kallon
Baffa da ya kafa mata ido yana neman k’arin bayani. Ba ta da dalilin b’oye masa
tunda fuskarsa ta nuna ya ji komai. “Kashe shi ta yi?” Ya fa’da cikin rashin
nutsuwa. Umma ta girgiza kai “Bata kai ga kisan ba amma an kusa suna asibitin
Saif clinic.” Baffa ya mik’e yana zura doguwar rigar jallabiyarsa hankalinsa a
tashe da jin mummunan labarin nan, ashe rashin Imanin Najwa har ya kai nan.”
Umma ma hankalinta a tashe ta bi Bayansa tana sake hijab d’inta.
A asibiti fuskarsa Cikin b’acin rai ya Zubawa Jaheed ido.
Faruq sai k’ok’arin Kwantar masa da hankali Yake amma ina Baffa kamar tura
lamarinsa ake burinsa kawai ganin Najma ya sauke mata b’acin ran da zuciyarsa
take ciki.
Har safiya Jaheed bai farka ba, kamar yarda suma su Baffan
ba su samu sun rintsaba. Sai shidda na safe sannan ya motsa ya bu’de idanunsa
da suka masa nauyi. Ganin Baffa da Umma a zaune yasa shi saurin bu’de idanunsa
ya yi k’ok’arin mik’ewa da sauri Faruk ya taimaka masa. Ya d’an harari Faruk
yana furta “Shine sai da ka gaya musu me yasa Faruk?” Shi d’inma gintse fuska
ya yi ya ce “Saboda ya kamata su sani, kai a tunaninka wannan maganar abin a
barta ne?” Baffa kuwa wani yawun b’acin rai ya ha’diye kafin ya ce “Maza Faruk
kama shi ya shiga toilet ya yi alwala.” Faruk ya aikata abinda Baffan ya ce.
Sai da ya idar da sallah da Azkar sannan Baffa ya amsa gaisuwarsa yana furta
“Ya aka yi wannan abin ya faru Mujaheed? Kuma bana son ka min k’arya.” Jaheed
ya d’an saki ajiyar zuciya bai son gayawa Baffan ta’asar da y’arsa ta masa, sai dai Baffan ya Riga ya
d’aure shi da jijiyoyin jikinsa don haka murya a raunane ya ce “Tsautsayi ne
Baffa da kuma sharrin yarinta” Baffa ya yi tsit cikin tsananin b’acin rai
jijjiga kansa kawai yake. Ba tare da ya furta komai ba har zuwa sanda Doctor
Saif ya shigo duk sun kasa katab’us a d’akin kowa da tunanin da yake cikin
ransa. Jikin da sauk’i” Doctor ya fa’da a hankali yana kallon Baffa. “Ko yanzu
zai iya tafiya gida idan har zai iya kula da kansa baa son ruwa dai ya tab’a
ciwon.” Baffa ya d’aga kai yana yiwa Saif godiya Faruk ne ya kama shi suka
mik’e suka fita.
Baffa umarni ya bawa Faruk akan su fara zuwa gidan Jaheed.
Jaheed bai so haka ba amma haka ya yi shiru yana ji yana gani aka isa gidan
nasa.
Tana zaune a parlourn zuciyarta a dugunzume da b’acin rai da
ciwon jiki da ma na zuciya. Bata ji d’uriyarsa ba don haka ta kasa ta tsare a parlourn tana
jiran fitowarsa su d’ora daga inda suka tsaya. Sai ta ji alamar mota ta tsaya
ta gyara zamanta sosai tana kallon kwalbar acid d’in da ke hannunta. Ta windown
parlourn ta lek’a sai ta ga Baffanta da Yaya Faruq. Da sauri ta b’oye kwalbar
tana ji suka shigo ganin Jaheed da bandage a wuya ya d’aga hankalinta don ba
mamaki Baffa ya ji labari kenan shine abinda ya kawo su da sassafe. Fuskar
Baffa kawai ta kalla hankalinta ya ninka na baya tashi. Ta zauna a tsorace tana
gaida Baffan da Umma da suka zuba mata ido cikin takaicinta da tarin jin
haushinta. Ba wanda ya amsa gaisuwar a cikinsu. Baffa ya kalli Jaheed ya ce “In
dai ina da iko da kai Mujaheed kuma kana kallo na a matsayin mahaifi ina so ka
saki yarinyar nan yanzun nan.” Jaheed cikin sanyin jiki ba na komai ba sai na
tausayin Baffan ya d’ago yana kallonsa murya a raunane ya ce “Ka yi hak’…..” Da
sauri Baffa ya dakatar da shi murya ba wasa ya ce “Just obey my commands.”
Jaheed ya d’ago yana kallon Najma da ta yi k’asa da kanta ya ce “Na saketa
Baffa.” Baffa ya saki ajiyar zuciya ya ce “Hankalinki ya kwanta ko? Sai dai ina
so ki sani daga rana irin ta yau na zare ki daga sahun y’ay’ana kai kuma Jaheed
Allah ya yi maka albarka ya baka mata ta gari, albishir d’in da zan maka Na
baka Najwa nan da shekara biyu idan ta gama makaranta za’a yi bikinku, abinda
ta maka kuma ina mai baka hak’uri ni na jawo maka.” Jaheed ya lumshe ido wasu
hawaye masu d’umi suna saukar masa bai san wace irin soyayya Baffa yake masa
ba. Umma tana kallon Najma ta mik’e “Burinki ya cika sai ki fito na mayar da ke
gida.” Jikinta a salub’e ta mik’e tana kallon Jaheed d’in gabanta na wani irin fa’duwa
haka kawai sai ta samu kanta da ganin tsananin kyan Jaheed d’in a wajen. Kamar
ba zata tafi ba sai kuma ta juya ta bi Umma cikin mutuwar jiki. Suka bar Jaheed
da Faruk a zaune Faruk yana ta lallashinsa akan ya hak’ura ya koma Gida. Jaheed
ya girgiza kai “Faruk ba na k’i ta taka bane, amma bana son na koma gida hijira
zan yi daga Nigeria gaba d’aya ko zuciyatta da ruhina za su huta.”
Ya fa’da yana lumshe idonsa
Wasu hawaye na zubo masa, haka kawai yake jin ransa ba
da’di.
Yana zama kiran Khairi na shigowa cikin wayarsa runtse ido
ya yi yana tuno da kyautar da Baffa ya masa duk da bai tab’a kwatanta Najwa a
matsayin matar aure ba sai ya ji abin ya masa banbarakwai da yanzu yake
tunaninta a matsayin matar da aka wa alk’awarin aurenta. Ya lumshe ido Najee
fa! Najee da yake mata kallon k’anwa ta ina zai fara rayuwar aure da ita?
Jikinsa ba karsashi ya d’aga wayar duk da baya so don ya san kukan da ta saba
dai zata saka masa. Wannan karan madadin kukan ajiyar zuciya ya ji ta saki mai
k’arfin gaske. “Habibi shikkenan ka rabu da ni? Na ji ance matarka ta tare
jiya.” Shiru ya mata tausayinta na sake rub’anya a zuciyarsa “Yes ta tare amma
mun rabu yau da safe.” Da sauri Khaireey ta saka Uban ihu tana furta
“Alhamdulillah Habibi na gaya maka kai nawa ne ni ka’dai In sha Allah, ka zo mu
gudu mu yi aure.” Shiru ya mata yana jin ta tana fa’dar duk abinda yazo bakinta
ya yi k’asa da wayar ya sab’uleta daga kunnensa yana lumshe idonsa tunanin
dramar jiya na sake zuwa ransa. Da k’yar ya ya kice tunanin ya rasa me yasa ya
kasa mantawa da
Lamarin ko don sabon shiga ne a waccan harkar bai sani ba.
Da k’yar ya yakice tunanin ta hanyar jan wayarsa ya shiga binciken k’asar da ya
kamata ya gudu ya bar Nigeria da tashin hankalin da yake cikinta. QATAR ya ji
hankalinsa ya tsaya a kanta don haka ya shiga binciken yanayin k’asar da ma
makarantunsu gaba d’aya.
Baffa kuwa yana isa gidansa ya shige sashensa baya buk’atar
hayaniya kamar yarda baya son a sake masa wata magana da ta danganci lamarin
Najma tabbas ya yarda Y’ay’an yau daf suke da fin k’arfin iyayensu ya yi mamaki
k’warai da gaske da Najma ta zama mai kunnen k’ashi ta kasa yin biyayya ga
abinda yake so, duk da k’ok’arin sa k’warai da gaske wajen ganin ya kyautata
rayuwarsu da abubuwan jin da’di ya inganta iliminsu bai san ta inda ya kuskure
ba da har take tunanin ta saka masa ta hanyar bijirewa muradinsa. Bai k’i yiwa
iyayensa biyayya ba ga yarda y’arsa ta masa ina ga wad’anda suka bijirewa
iyayensu? Allah yasa mu dace kawai.
Umma da b’acin ran ta shiga b’angarenta inda ta samu Najee
da Nene suna ta gyaran babban parlourn ta, tun d’azu suke zancen rashin ganinta
a kitchen da sassafe kamar yarda suka saba, nan suka dinga addu’a da taraddadin
Allah yasa lafiya. Nene na ganinta ta san ba k’alau ba don haka bata san sanda
tray d’in hannunta ya fa’di ba, mummunan mafarkin da ta yi da Jaheed take ya
dawo mata a sukwane cikin tashin hankali ta ce “Umman su Jaheed Allah yasa
lafiya me ya faru?” Daidai lokacin da Baffa ya tura k’ofar parlourn ya shiga
idanunsa akan Nene da take furucin……..
JIKAR NASHE. ✍π½
KUDIRAR ALLAH.
15.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
________________
Cak numfashin jama’ar parlourn ya d’auke na wani d’an lokaci
ganin yarda idanun Baffan suka nuna ya ji abinda Nene take cewa. Magana ce mai
bayyana wanda ya fa’deta yana cikin nutsuwa da hankali ba alamun rashin hankali
tattare da ita. Don haka Nene bata da ikon mayar da maganar cikinta. Baffa ya
cigaba da taku zuwa cikin parlourn duk takun da zai yi kamar yana taku ne da
bugun zuciyar Umma, Nene da Najee. Saboda tsoro da fargaba da zuciyarsu take
ciki. Bai d’auke idanunsa daga kan su ba cigaba yayi da kallonsu d’aya bayan
d’aya yana nazarin yarda fuskokinsu suke bayyana tsantsar rashin nutsuwa da
zuk’atansu ke ciki. “Yaushe hankalinta ya dawo?” Ya furta idanunsa akan na Umma
ba alamun wasa tattare da shi. Umma ji ta yi k’afafunta suna neman gagarar
d’aukarta. Ta waske cikin son b’atar da tunaninsa ta ce “Ni kaina yanzu
tambayar da nake shirin yi mata kenan ka shigo, maganarta kawai na ji a sama
cikin nutsuwa da kamala mai nuni da cikar hankalin kwanyar d’an Adam.” Ta fa’da
da k’yar tana k’ok’arin kawar da waccan fuskar firgicin zuwa fuskar kamala da
zata bayyana ainahin gaskiyar da zuciyarta ke ciki. Kallo ya mata irin dogon
kallon nan da yake ratsa cikin ido mai sanya mutum ko yana da gaskiya ya
daburce. “Ke Nene wacece ke? Zuwa yanzu na tabbatar da kina cikin hankalinki.”
Bakinta ne ya fara rawa kafin ta dafe kanta da take jin yana sara mata tana
tsoron zuwan wannan ranar ga shi tazo mata a lokacin da bata shirya ba, me zata
cewa mutumin da ya mata halacci a rayuwa? Sam bai kamata ta sake k’irk’irar
k’arya ta gaya masa a wannan lokacin ba da tasirin idanunsa ka’dai zai iya
jijjiga zuk’ata. Umma ce ta dafa ta cike da k’arfin hali ta ce “Baffa kamar
bata gama dawowa daidai ba, ka bari idan ta samu nutsuwar zuciyarta na san da
kanta zata maka bayani.” Baffa ya yi shiru maganar Umma na masa yawo a kai ya
yarda da kaso tamanin cikin zancenta sai dai wata zuciyar na k’aryata duk
abinda ta ce. Sai kawai ya saki ajiyar zuciya ba tare da ya furta komai ba ya
fice daga sashen gaba d’aya yana ji a ransa ko ba yau ba zai yi bincike da
kansa. Umma ta saki ajiyar zuciya tana bin bayansa da kallo kafin ta nunawa
Najee k’ofar d’akin Nene ta mata alamar su wuce don ita kanta yanzu hutun take
buk’ata hutun zuciya da na kwanya gaba d’aya. Najee ta ja hannun Nenen da sauri
suka shige sashenta.
****
Najma kuwa jikinta a sanyaye ta shiga d’akin Mahmeey da take
kwance tana barci hankalinta kwance. Najma ta ja k’afafunta da suke Mata ciwo
ta zauna da k’yar a gefen gadon tana kiran Sunan Mahmeey a hankali. Mahmeey ta
bu’de idonta da kyar jin an kira sunanta daga sama. Da sauri ta tashi idanunta
a bu’de tana kallon Najma cikin mamaki “Ke kuma daga ina haka da sassafe?”
Najma ta sauke idanunta a hankali tana ji k’una da rad’ad’in zuciyarta na sake
hauhawa da gaske lamarin ya mata ciwo ga keta mutunci ga sakin aure da ma bai
karb’e budurcinta bane da sauk’i amma yanzu duk wanda zata aura a matsayin
bazawara zai aureta. Ta runtse ido tana sake jin haushin kanta da Jaheed duk
lokaci guda. “Ki min magan Malama kin tasa ni gaba kina kuka.” Mahmeey ta fa’da
cikin b’acin rai. Najma ta saki ajiyar zuciya ta ce “Ya sakeni Mahmeey bayan ya
cuceni ya k’wace budurcina.” What! Mahmeey ta fa’da tana ware ido “Wani banzan
zance nake ji daga bakin ki? Yanzu zuwa kika yi ya yaudareki ya k’wace budurcin
sannan don rashin mutunci ya sako min ke.” Najma kuka ta saka mai k’arfin gaske
tana fa’dawa jikin Mahmeeyn. Kukanta ya
sake harzik’a zuciyar Mahmeey ta dinga jin itama kamar ta saka kukan saboda
tsananin bak’in cikin da zuciyarta take ciki. Tsanar Jaheed ta sake k’arfi a
zuciyarta. Mik’ewa ta yi da azama tana zura hijabinta wajen Baffa zata je ta
gaya masa rashin mutuncin da d’an gaban goshinsa ya aikata, bata san tuni Baffa
ya san zancen ba.
Tana murza k’ofar bedroom d’in ta sameta a bu’de don haka
kai tsaye ta danna kanta cikin d’akin, ba sabon abu bane wajen Baffa tuni ya
banbance halayyar matansa ya san halin kowacce don haka ko da ya ji an danno
d’akin bai bu’de idonsa ba don ya san Mahmeey ce. Tsaye ta yi a gaban gadon
tana k’arewa fuskarsa mai bayyana kasala da tashin hankali kallo. “Sai ka tashi
ai, ka ji tozarcin da d’an gaban goshin naka ya maka, bayan ya kusanci y’ar ka
sannan da safe ya aikota da saki.” Wani irin murmushi na gefen baki Baffa ya
saki idanunsa a lumshe ba tare da ya bu’de su ba ya fara magana “Ni na saka ya
saketa.” Da sauri Mahmeey ta waro ido jin abinda Baffan ya ce “Kai fa kace ka
saka ya saketa? To saboda me?” “Saboda sakin shi ya dace da mara tarbiyyar y’ar
ki wacce zata iya saka wuk’a a wuyan mutum da niyyar hallaka shi, kin ci sa’a
ma da baki tai Cesar a police station ba.” Gaban Mahmeey ya fa’di bata san
sanda ta zauna a gefen gadon ba tana dafe k’irji ta ce “Kisa fa ka ce? Me zai
saka ta kashe shi? Sai dai idan hawan k’awara ya mata ta ji zafi zata hallaka
shi, amma ni ban yi mata hu’dubar ta kashe shi ba.” “Kin bata acid Ai ta watsa
masa idan ba ki ce ta kashe shi ba kin ce ta nakastashi Wallahi Zainabu ki bi
duniya a hankali.” K’irjinta ne ya shiga bugu ta mik’e jikinta a kasalance ta
fice daga bedroom d’in tana jinjina k’arfin hali irin na Najma idan ta kashe
shi bata san itama kasheta za’a yi ba? Hakanan ta koma b’angarenta ta tasa
Najma a gaba da masifa, har sai da Najman ta fa’da jikinta cikin tashin hankali
ta furta “To na tsane shi ne Mahmeey shi yasa.” “Hakan ne ya baki Lasisin kashe
shi saboda wauta, kin san idan da ya mutu kema mutuwa za ki yi ko?” Rungume
Mahmeeyn ta yi kawai don dole ta ja bakinta ta yi shiru jin jikin Najman ya
d’au zafi sosai.
______
Najee jikinta a sanyaye ta fito daga kitchen ta koma bedroom
d’in Umma. Haka kawai yau take jin wata irin fa’duwar gaba. Umma da take zaune
d’auke da waya a hannunta tana neman wayar Faruk ta ji ko ya koma wajen Jaheed
ta d’ago tana kallonta. Jikinta a sanyaye ta zauna gefen Umman ta zauna a bakin
resting chair da take kujerar Umma ta d’ora hannunta akan goshinta tana furta
“Me ya samu autata na ganki haka?” Murmushi Najee ta yi tana lumshe idonta ta
ce “My heart beats faster Umma.” Shiru Umma ta yi sai yanzu maganar da Baffa ya
yi ta fa’do mata na aurawa Jaheed Najee da sauri ta d’an janye Najee daga
jikinta tana furta “Tashi Auta mu yi magana.” Bugun zuciyar Najee ya sake
k’arfafa jin abinda Umma ta ce, a idanunta kuma ta hango ba wasa a duk abinda
zai fito daga bakin ta. “Baffanki ya bada aurenki da zarar kin gama makaranta
don haka ba ke ba kula kowane Namiji.” Najee ji ta yi zuciyarta ta daina aiki
na wuncin gadi, zufa ta fara karyo mata da k’yar ta ce “Umma wa aka bawa aure
na?” “Jaheed” Umman ta fa’da idanunta na zagaye fuskar Najee ta hango wani
tsantsar farin ciki da ya kasa b’oyuwa a idanunta sai kuma ta ga ta runtse ido
tana warasu a cikin na Umman ta ce “Me zai saka Yaya Jaheed ya aure ni bayan
yana aurar Yayata.” “Allah ne ya halatta masa aurenki in dai basa tare da Yayar
taki, abin buk’ata ki yi addu’a Allah yasa hakan shine alheri a rayuwarki.”
Mamaki ne ya kashe Umma ganin Najee ba tayi wani bak’in ciki ba sai ma tarin
walwala da jin da’di da ta gani tattare da ita, kamar dama jiran irin wannan ranar
take. Umma murmushi kawai ta saki don ko da Najee bata fito ta fayyace sirrin
zuciyarta ba a yanzu ta san da soyayyar Jaheed a zuciyarta a hankali ta furta
“Allah yasa ku zamewa junanku Alheri.” Najee idanunta a lumshe kawai ta amsa a
zuciyarta da ameen tana sakin ajiyar zuciya wanda Umman ta ji shi har cikin
ranta.
Daga haka Umma zameta ta yi a jikinta ta nufi b’angaren Nene
da take zaune cikin tunani da firgicin zuciya bata san wani kallo Baffa zai
yiwa abin ba, shin zai mata uziri ko kuma zai k’ullaceta akan b’oye masa da ta
yi. Turo k’ofar ya sake razanata a firgice ta d’ago da kanta da idanunta da
Suka jigata take kallon Idanun Umma.
A k’asan leb’enta ta amsa sallamar wanda hakan yasa Umma
bata ji ba. Ta zauna a gefen gadon tana kallon Nenen ta fara fa’din “Kada ki ce
zaki nunawa Baffa gaskiyar lamari a yanzu, b’oye masa shine abu mafi alheri a
wajena da ke baki d’aya. A yanzu ki nuna masa kin dawo cikin hayyacinki amma ba
zaki iya tuna rayuwarki ta baya ba, duk rintsi ki nuna masa kin manta komai,
idan ba haka ba komai ma zai iya faruwa, musamman a yanzu da yake cikin bak’in
cikin abinda Najma ta yiwa Jaheed….” Da sauri Nenne cikin fa’duwar gaba ta
d’ago tana duban Umma. Umman ta d’aga kai “Allah ya kiyaye amma da yanzu wani
labarin ake ba wannan ba, ta yi attempting soka masa wuk’a shine dalilin fitar
mu cikin dare afujajan amma dai da sauk’i kuma Baffa a take ya d’au hukunci ya
raba auren don idan aka bar su nan gaba ba a san ne zata yi ba….” Da Umma ta
san a wani yanayi Nene take da bata cigaba da bayani ba, idanunta ne a waje ta
dafe k’irjinta da yake mata matsanancin bugu, tana kallon Umman. Umma ta dafata
tana furta “Bakomai fa ya samu lafiya cikin hukuncin Ubangiji bari na kira miki
shi ki ji muryarsa bai san kuma kin dawo hankalinki ba ban san ya za’a yi ba
yanzu.” Nene ta ha’diye yawu da k’yar tana furta tunda dai ya samu lafiya bar
shi ba sai kin kira shi ba Umman Jaheed ina son in ga wani farin ciki zai yi
idan ya fuskanci a yanzu ina cikin hankali na.”
Umma ta d’aga kai tana furta “Shikkenan.”
————
Bayan kwana biyu Jaheed ya ji jikinsa da sauk’i duk wata
azaba da yake ji ta kau daga zuciya da k’irjinsa. A yanzu abu guda ke damunsa
masifaffiyar sha’awar da ya jangalowa kansa, bai sani ba ko don farin shiga a
lamarin abinda bai tab’a aikatawa bane. Da zarar ya rufe ido ba abinda yake
gani sai surar Najma shi dai ya san ba sonta yake ba sai dai ya ta’allak’a abin
da sha’awa. Yau ma da sassafe ya yi wanka yana zaune ya dinga ganin kiran
Khaireey a wayarsa a hankali ya kai hannu kan wayar ya d’aga muryar Khaireey a
d’ashe sai dai ta nuna zallar farin cikin da take ciki ta ce “Jaheed ka zo
Babana ya amince da auren mu, ka zo za ku yi magana da shi…….”
JIKAR NASHE✍π½
KUDIRAR ALLAH
16.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
Talla! Talla!! Talla!!!
https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk
Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da
kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan
mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin
haΙin mu na Arabian sabaya powder wanda
babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin
dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman
wadannan kayan.
*************
Wani irin duuuum Jaheed ya ji a kunnensa ya kuma kasa
gasgata abinda Khairyn ta ce da shi har sai da ta sake maimaitawa. “Kana ji na?
Nace Abba ya amince mu auri juna Yayyansa sun shiga cikin lamarin.” Sakin
ajiyar zuciya ya yi ba tare da ya amsa mata ba saboda maganar zai iya cewa ta
masa dirar mikiya ta ina zai fara sanar da Khairi abinda Baffa ya ce zai ha’da
shi aure da y’arsa? Ta ina kuma a yanzu zai fara sanar da Baffa maganar auren
Khairyn? Me Baffan zai d’auka akan hakan? Baya son y’arsa shi yasa ya kafe zai
auri Khairi. Tabbas yana cikin TSAKA MAI WUYA LITTAFIN JANAFTY. Rashin amsar da
zai bawa Khairi yasa ya zame wayar daga kunnensa bayan ya furta “Okay” cikin
sanyin muryar da Khairi bata gasgata ta Jaheed ba ce,a irin soyayyar da suke wa
Juna ta zata Jaheed da zarar ya ji
amincewar Abbanta zai k’walla ihu da murna na tsananin farin ciki madadin haka
Jaheed katse kiran ya yi yama kashe wayar gaba d’aya yana sakin ajiyar zuciya.
Zuciyarsa hutu take buk’ata da dogon tunanin yarda zai rabu da kowa lafiya ba
tare da ya sab’a musu ba.
Tsawon mintuna yana kwnace ya kasa aiwatar da komai kowace
shawara ya yi sai yaga bata dace a wannan gab’ar ba. Don haka ba shiri ya kira
wayar Faruk don shine abokinsa abokin shawararsa kuma wanda baya iya b’oyewa
damuwarsa a yanzu d’in ma yana ganin duk shawarar da Faruk ya bashi da ita zai
yi aiki tunda dai tasa zuciyar ta kasa aikin da ya kamata.
Ringing biyu ta yi Faruk ya d’aga wayar kamar dama jiran
kiran yake. Jaheed ya saki ajiyar zuciya ya ce “Kana ji na Faruk?” Faruk ya
amsa da “Yes ina jin ka.” Jaheed rasa ta inda zai fara ya yi saboda shi kansa
Faruk d’in bai san fassarar da zai yiwa lamarin ba. Don haka kawai sai ya ce
“Idan ba abinda kake don Allah ina son ganinka.” Faruk ya amsa da “Ba abinda
nake, on my way to your house dama right now.” Daga haka ya kashe wayar.
Mintuna biyar ne suka kawo shi gidan Jaheed d’in. A zaune ya
same shi ya zuba hannayensa biyu a k’ucninsa cikin dogon tunanin da yasa ko
bu’de k’ofarsa bai ji ba balle shigowarsa, har sai da ya dafa kafa’darsa sannan
ya d’ago da sauri yana sakin ajiyar zuciya. Faruk ya saki tsaki yana furta “Ban
san sau nawa zan gaya maka dogon tunani illa ne ga lafiyar zuciyar ka ba.”
Jaheed murmushi ya sakar masa yana furta “Tunani dole ne Faruk ga wanda tunanin
ya kama, ni sai na dinga ganin kamar ni ka’dai duniya yake juyin waina da ni,
kamar na fi kowa matsala a rayuwa.” Faruk ya zauna cike da tausayin Jaheed yana
furta “Kai kake ganin haka, wani yana can gefe yana sha’awar taka rayuwar
dafatan cewa dama shine kai. Yanzu kuma me ya faru?” Wayarsa Jaheed ya d’aga
yana dialling numberr Khaireey. Bugu biyu ta d’aga muryarta na nuna kamar fushi
take da shi. Ya saka wayar a hands free yana fa’din “D’azu Khaireey kaina na
ciwo ban ji abinda kike cewa ba, kin san na samu minor accident me kika ce?”
Sakin ajiyar zuciya ta yi sai yanzu zuciyarta ta yi sanyi daga zafin data
d’auka d’azu muryarta cike da k’warin gwiwa ta ce “Abba na ya ce ka turo jibi a
d’aura mana aure, ya yarda bayan Yayyensa da na Umma sun nuna masa rashin
kyautatawar abinda aka yi da kuma tuna masa idan shine wannan k’addarar ta
fa’da a kansa ya zai yi, a yanzu jikinsa ya yi sanyi ya kuma yi nadamar wancan
hukuncin da ya yanke, da kansa ma ya ce zai zo wajen Baffa neman afuwa.” Jaheed
ya juya yana kallon Faruk da shima kallonsa yake yana kuma sauraran duk abinda Khaireey
take fa’da a cikin wayar. Jaheed ya zame wayar a kunnensa bayan ya ce da
Khaireeyn “Za mu yi waya later In sha Allah, na yi bak’o.” Khaireey bata kawo
komai a ranta ba ta ce “Okay Habibi sai na ji ka.” Da shi da Faruk d’in a tare
suka saki ajiyar zuciya, Faruk ya ce “Wannan fa shine ana wata ga wata, ni ba
ta maganar ka da Najee nake ji ba, maganar Baffa da yarda zai zo ya amince ka
auri Khairey yake yarda ya d’au fushi da mahaifin yarinyar nan, amma dai tunda
ya ce zai je ya same shi da kansa sai ka bari mu ga yarda zata kaya, kai dai
kada ka tofa taka, Allah ya zab’a maka abinda ya fi alheri, ni ko d’aya bana
ganin laifin Khairy don yarinyar ta cancanci a jinjina mata yarda ta tsaya
tsayin da ka wajen nuna maka soyayya duk da maganganu marasa da’di da ta ji a
kanka. Idan har ka sameta tabbas zan maka murna.” Jaheed girgiza kai ya yi don
ya yarda da duk abinda Faruk ya fa’da, abu guda ne ba zai iya ba watsa wa Baffa
k’asa a ido, ko da kuwa son Khairy zai illata masa zuciya zai rungumi k’addara
matuk’ar Baffan bai amince ba, abu na biyu zai amince ko bayan auren Khairy ya
ha’da da Najee ko don martaba da girman Baffan duk da a ido kallon k’anwa yake
wa Najee bai tab’a kawar da matsayin hakan a zuciyarsa ba, bai kuma tab’a yi
mata wani kallo da ya wuce wannan kallon ba na Yaya da k’anwa ba. A haka suka
tsayar da shawarar da niyyar sai abinda Baffan ya ce su ba za su yanke shawara
da kan su ba, ba kuma za su je su tari Baffan da maganar ba har sai idan shine
ya tare su da maganar.
A yammacin ranar ya yi wanka tunda ya d’an ji dama dama a
jikinsa. Farar t.shirt ya saka da wando black da yake akwai sanyi a garin sai
ya kawo bak’ar rigar sanyi mai d’an girma ya saka a jikinsa inda ya rufe kansa
da hular rigar. K’amshin turaren Rasasi kawai yake zabgawa. Ya fito sanye da
black slippers a k’afarsa, fuskarsa ta bayyana yanayin da zuciyarsa take ciki
na rashin sukuni da farin ciki, duk da k’ok’arin sa na kawar da hakan. A
motarsa k’irar Benz fara tas ya fita. Gidan su yake son zuwa su gaisa tunda
kwanansa uku bai je gidan ba.
In dai zaka gan shi a lokacin sai ya burgeka don kai tsaye
zaka hango kamanceceniyarsu da shahararren d’an film d’in India Sharuk khan sai
dai haske da Sharukh d’in ya fi shi.
Tunda ya hango Baffa zaune a harabar gidan kan babbar
daddumar da ake shimfi’da masa duk Bayan sallahr Isha’i, sai ya ji gabansa ya
fa’di. Kwarjinin Baffan ya sake girmama a idaniyarsa. Bai san sanda ya cusa
hannunsa cikin tarin sumar kansa ba. Ya k’arasa saman daddumar Baffan jikinsa a
sanyaye ya durk’ushe a gabansa. Ido Baffan ya zuba masa yana amsa gaisuwar sa,
kamar dama Jaheed d’in ya san shi yake jira.
Amsa gaisuwar sa ya yi yana sake nazarin fuskarsa sosai,
kallon da ya sake girgiza hanjin Jaheed sai ya dinga fassara kallon Baffan a
mazaunin Butulu mara kirki balle adalci. “Ya jikin naka?” Ya samu muryar Baffan
a sama yana tambayarsa. Cikin rawar baki Jaheed ya amsa da “Alhamdulillah!” “Ma
sha Allah.” Baffan ya furta yana cigaba da danna casbahan hannunsa. “Surikin ka
ya zo jiya.” Wani irin dum kan Jaheed ya yi jin abinda Baffan ya ce, hakan na
nufi da Baffan ya ji haushi kenan ko me? Bai dawo daga tunani da fargabar da ya
shiga ba ya ji Baffan ya cigaba da fa’din “Na bashi ku’din sadakinka na aurar
y’arsa bayan na gama yarda da nadamar da ya yi, ina fatan ta zame maka mata ta
gari In sha Allah. Magana ta biyu maganar Najwa tunda na Riga na maka alk’awarin
aurenta ba zan janye ba In sha Allah, idan ta gama makaranta zan aura maka ita
idan kana sonta.” Da sauri Jaheed ya d’ago ba tare da ya shirya fa’dar abinda
ya zo bakinsa ba ya ce “Ba abinda zai hana ni auren Najee Baffa in dai ina
raye, nagode da karamcinka gareni, idan kuma har wannan auren bai maka ba, kana
da iko a kai na zan iya janye maganar auren In dai baka so.” “Bana hana aure
Mujaheed, kuma na yaba da hankalin yarinyar don haka har a zuciyata na amince
maka aurenta, gobe idan an sakko daga masallaci za’a d’aura maka aure da ita,
ka san tsari na bana son bidi’a saboda haka na sanar da mahaifin ta Walima
kawai za’a yi ta tare a gidanka.” Jaheed shiru ya yi kansa a k’asa bai zata
abubuwa za su zo masa da sauk’i haka ba. Ya saki ajiyar zuciya kafin ya d’ago
ya ce “Sai dai Baffa ka min hak’uri na Riga na nemi Visa a k’asar QATAR zan je
k’arin karatu In sha Allah, ko za’a bari sai na dawo sai ta tare.” Baffa ya
d’au tsawon lokaci yana kallon Jaheed d’in har Jaheed d’in ya d’an tsargu bai
sare da lamarin ba sai da ya ce “Yanzu Mujaheed har zaka iya yanke shawarar
abinda ya dace da kai ba tare da sani na ba? Ko duk laifin Najma ne ya shafe
ni?” Da sauri Jaheed ya hau girgiza kai “Wallahi Allah Baffa bakomai a raina,
dama na da’de ina nema sai yanzu suka bani amma idan baka so zan bar shi
Wallahi.” Baffa sai sannan hankalinsa ya kwanta “Ba zan ce kada ka je neman
ilimi ba, kamar yarda ba zan amince ka tsallaka wata k’asar ba matar aure ba,
idan kaga na amince ka bar k’asar nan sai dai idan ka tafi tare da matar ka don
haka ka shirya sama mata visa ku ranka ya ku tafi gaba d’aya.” Wani irin sanyi
ne ya shiga zuciyar Mujaheed yana jin girma da kimar Baffa na sake girmama a
zuciyarsa, Da gaske Baffa d’abi’u da halayensa kwatankwacin irin halayyar
sahabbai ne. Burinsa kenan tafiya da Khaireey sai ga shi komai ya zo masa da
sauk’i. Godiya ya yiwa Baffan sosai dafatan gama da duniya lafiya kafin Baffa
ya dakatar da shi da fa’din “Ameen, ta shi maza ka je wajen iyaye ka mata,
Allah ya yi maka albarka.” Jaheed ya amsa da ameen, ya mik’e don shiga cikin
gidan.
A balcony ya hangota zaune a saman kujerar da ke wajen. Suka
ha’da ido ya yi sauri kawar da kansa. Ita kuma da sauri ta bi shi da kallo
zuciyarta na cigaba da wani irin k’akkarfan bugu. K’amshin turaren sa da ya
kasa barin hancinta ta cigaba da shak’a tana jin zuciyatta na sake k’unci da
tunano mata Jaheed a daren farkonsa gidan aurenta. Ta lumshe idanunta tana jin
saukar hawayen da bata san dalilin su ba, haka kawai yake tsintar kanta a
wannan yanayin tun bayan da aka tabbatar mata Jaheed ya saketa.
Da sallama ya shiga b’angaren Umma. Najee ce ka’dai a
parlourn tana aikin bulbula turaren wuta. Saura k’iris abin turaren wutan ya
sub’uce a hannunta Sabo da jin muryarsa da ta yi ta doki dodon kunnenta.
Muryarta na rawa ta ce “Ya. Jaheed sannu da zuwa.” Cikin idanunta ya kalla yana
nazarin yarda ta kasa sakewa da shi da alama ta samu labarin abinda Baffa yake
shirin k’ulla wa tsakaninsu. Ta k’i yarda sam su ha’da ido don wata irin
kunyarsa take ji. Lumshe ido ya yi yana furta “Amaryar Jaheed ya da kunya tun
yanzu?” Ai kafin kace me? Ya nemeta ya rasa don da mugun gudu ta b’ace daga
wajen b’at. Jaheed ya saki murmushi yana sosa kansa a zuciyarsa yake tunanin
duk sanda ya auri Najee zai yi fama da yarintarta, musamman kasancewarta Auta
da bata san komai ba sai shagwab’a. Autar ma wacce ta tashi a tsakiyar maza.
Fitowar Umma ce ta saka shi dawo da hankalinsa kanta. Ya
gaisheta irin gaisuwar da suka saba yi. Ta masa ya jiki sannan ta masa fatan
alheri akan auren da aka ce zai yi gobe, duk da ba wanda ya sani Baffan ita
ka’dai kawai ya sanarwa, ita kuma ko Najee bata gayawa ba ta bar abin a ranta,
kamar yarda Baffan ya ce so yake ya bawa kowa mamaki. Jaheed ya amsa yana d’an
jin kunyarta, bata bi ta tasa ba don ta san me ya saka shi jin kunyar Sabo da
zai yiwa y’arta kishiya, ita kuwa ina ita ina shiga hurumin Ubangiji fatan
alheri kawai zata bi su da shi. Don haka ta ce “Tashi ka shiga wajen Nene,
tunda ta san ka ji ciwon nan hankalinta yake kanka na san kawaici kawai take.”
Jaheed ya amsa yana mamakin Umma da tace wai kawaici Nene take ko ina taga
hankalin da zata san wani abu kawaici? Tunda bai san ta dawo cikin hankalinta
ba.
A zaune ya sameta cikin kamalalliyar shigarta. Hannunta
d’auke da alk’ur’ani Mai girma. Jaheed ya shiga cikin d’akin yana mamakin ganin
Nenensa da Alkur’ani, kamar wata mai cikakken hankali. Idonta ta d’ago ta zuba
masa tana kallon yarda ya zube a gabanta. “Nene Ina wuni?” Ya fa’da kamar yarda
ya saba. So yake ya ji ta maimaita masa abinda ya ce kamar yarda ta saba sai ya
ji ta ce “Lafiya lau Mujaheed d’an Albarka ya jikin naka?”
JIKAR NASHE CE✍π½
K’UDIRAR ALLAH
17.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
(Allah ya baki lafiya Na’ima Sulaiman sarauta. (Nimcyluv).
Wani irin d’agowa Jaheed ya yi kamar a firgice ya zubawa
Nene da Itama take kallonsa ido. Da gaske kallon da Yake mata na tsananin
mamakin jin amsawar da ta masa ne. Bai tsammaci hakan ba a irin wannan lokacin,
Nene murmushi ta sakar masa tana kallon tsakiyar idanunsa ganin yarda mamakinsa
ya kasa b’uya da alama ko yana tunanin mafarkin da ya saba ne. Don haka ta kai
hannunta na kama na hannunsa da ya dunk’ule waje d’aya, idanunsa a lumshe yana
fatan ko mafarkin yake kada ya farka nan kusa. Nenensa a cikin hankalinta tana
amsa masa maganarsa cikin nutsuwa ba irin harigidon da ta saba ba. Yau shi kuwa
wace irin godiya zai yi wa rabbul izzati. Bai dawo daga mamakin ba ya ji
muryarta mai taushi ta amsa masa tambayoyin da bai bayyana su ba. “Ni ce dai
Nenen ka Jaheed, ba mafarki kake ba Allah ya dawo min da hankalina.” Ta fa’da
tana jan istigfari a zuciyarta. Jaheed ya saki ajiyar zuciya mai k’arfin gaske
yana furta “Alhamdulillah!” Cikin muryar da ta bayyana rauninsa gurin Rabbil
Izzati, don tuni hawaye suka gauraye idanunsa sauka suke da zafinsu cikin
sark’ewar harshe ya ce “Nene sanar da ni, wacece ke? Daga wani gari ki ke? Idan
kuma nan ne garin ku wanene mahaifina? Ya Ubangiji Allah yasa kada zargin
mutane na cewa ni shege ne ya tabbata.” Ya fa’da yana duban Nenen da ta lula
cikin duniyar tunani. Banda tana tsoron makomarta da ta Jaheed d’in gaba d’aya
da a yau zata sanar da shi shi wanene? Sai dai tsoro da fargaba ba zai barta
ba, bata son abinda zai nesanta da Jaheed ba kuma ta son ya je inda za’a wulak’anta
shi tunda bata da wata shaida da zata bayyana mahaifinsa kai tsaye a garin
Gabas, dole ne sai ya yi bincike kafin ta gano ainahin wanda ya jefata a cikin
wannan sark’ak’iyar mai wuyar warwara.
K’irjin Jaheed ya cigaba da wani irin bugu da k’arfin gaske,
ya ayyana shikkenan ta faru ta k’are ba sai Nene ta bu’de baki ta yi magana ba
ya san shi d’in shege ne mara asali wanda ba’a san ubansa ba, ba mamaki ma
hakan ne sanadiyyar d’auke war hankali da tunanin Nene. Hucin numfashi Nene ta
furzar kafin a hankali ta furta “Ba zan iya tuna komai nawa ba Jaheed! Harta
sunana da sunan garin dana fito ba zan iya tuna su ba sai dai mu yi ta addu’a
har zuwa lokacin da zan tuna komai d’in….” Murnar Jaheed ta koma ciki ya zuba
mata ido cike da tausaya mata, wace irin k’addara ce wannan mai girman gaske
yake bibiyar Nene da shima kansa, yana rok’on Ubangiji Allah yasa su amsa
jarrabawar nan daidai. Hannu yasa ya d’auke k’wallar data tarar masa, kafin ya
mayar da hannu ya share k’wallar da take idanun Nenen yana sakar mata murmushin
da kai tsaye za’a kira na dole ko na yak’e. Nene ta sakar masa murmushin itama,
don k’ok’arin kawar mata da damuwa sai ya soko zancen aurensa. “Gobe za’a
d’aura min aure da Khaireey Nene.” Take annurin da Nene take tare da shi ya
d’auke tsaf daga fuskarta. Cikin b’acin rai ta ce “Aure kuma? Ina maganar Najwa
da Baffa ya baka?” A idanunta ya hango tsananin son aurensa da Najee ya sani
dole dama zata yi farin ciki da zamowar Najee surikarta, amma bai san wannan
dalilin zai saka ta k’i Khaireey ba.
Murmushi ya sakar mata yana furta “Nene a yanzu Najeenki ta yi k’arama
da aure, so ki ajiye min ita sai na da 2 to 3 yrs kamar yarda Baffa ya ce, ni
kuma na miki alk’awarin rik’e miki Najee da soyayya mai girma a zuciyata.” Sai
sannan ta saki murmushi ta na furta “Mujaheed bana son ka yi wa Baffanku
butulci duk duniya baka da wanda ya fi shi, ina son ka jajircewa zuciyarka
wajen ganin ka kyautata masa duk runtsi kada ka bijirewa auren Najwa ka min
wannan alk’awarin?” Jaheed ba tare da jin komai a zuciyarsa ba ya damk’e
hannunta yana d’aga mata kai “Na miki Nene duk runtsi duk wahala ba zan k’i
auren Najee ba.” Ta saki ajiyar zuciya tana furta “Allah maka albarka, amma
tabbas da Baffa ya yi shawara da ni, da ba’a fara waccan maganar ba har sai an
d’aura aurenka da Najwa idan ya so nan gaba ta tare Amma dai itace Uwargida.”
Dariya sosai Jaheed ya yi ya ce “Kai Nene banda son kai.” Itama dariyar ta yi
tana furta “Son kai ko gaskiya duk duniya ba wanda nakewa son da nakewa Najwa a
cikin raina nake jin yarinyar kamar ni na haifeta.” Jaheed ya jinjina kai ba
tun yanzu ya fuskanci hakan ba, tun Nenen na cikin hauka ko tana ciwo Najee
kawai taka bata abinci ta karb’a. Ya ce “Burinki zai cika In sha Allah, Najee
zata haifa miki jikoki masu yawa.” Ta bu’de ido tana kallonsa kafin ta furta
“Mujaheed baka da kunya dama?” Dariya ya yi sosai kafin ya mik’e ya fice da
sauri yana jin wani farin ciki da nutsuwa a zuciyarsa ba don komai ba sai don
dawowar Nene cikin hankalinta.
A parlour ya samu Umma tana zaune idanunta akan T.V tana
kallon tashar da ta fi so wato Sunna t.v. Ta gefe ta kalleshi ganin yarda yake
zabga fara’a ta tabbatar ya gano Nenensa ta samu lafiya. “Akwai labari a
bakinka Mujaheed.” Ta fa’da tana d’auke idanunta daga saman T.Vn. Murmushi ya
saki ya na zama a gefenta ya ce “Akwai Umma, ashe Nene ta dawo cikin
hayyacinta.” Ta d’aga kai tana murmushi “Ta dawo Mujaheed, ina sane na k’i
sanar maka na fi so ka gani da idonka, Alhamdulilah Abu d’aya ya rage ta tuno
rayuwarta ta baya wannan kuma sai a hankali In sha Allah.” Mujaheed ya d’aga
kai yana cewa “Allah yasa Umma, bari na wuce sai da safe.” Yana shirin mik’ewa
ta ce “Ya maganar lefe Mujaheed?” Ya d’an sosa kansa ya ce “Za’a yi Umma, a min
list a kuma fa’da min ku’din da za su isa sai na bayar.” Umma ta d’aga kai tana
kallonsa “Ashe kuwa Baffa baya raye?” Da sauri ya waro idonsa don rashin gane
inda zancen Umma ya nufa. Ta d’aga kai cike da tabbatarwa “Ka san dai shi yake
muku lefe ko? Tambayar da na maka maganar sizes d’in yarinya nake maka ba na
ku’di ba Alhaji Mujaheed.” Dariya Mujaheed ya yi sosai yana furta “Tuba nake
Umman mu zan tambayeta In sha Allah, ko kuma na bawa Najee numberr wayarta sai
ta tambayeta.”
Umma ta watsa masa wani kallo ta ce “Saboda me zaka saka
kishiya ta tambayi kishiya sizes don ha’din fa’da?” Jaheed ya waro ido shi har
ga Allah ya ma manta bai gayawa Khaireey maganar Najee ba, kamar yarda itama
Najeen bai sanar da ita gobe za’a d’aura masa aure ba. Umma dariya ta masa
sosai ganin yarda tsoronsa ya bayyana ta ce “Kada ka zama matsoracin namiji
mana ko an gaya maka zama da mace fiye da d’aya na rago ne, ka sanar da ita
maganar Najwan ne? Ita kuma Najwa ka sanar da ita maganar auren da zaka d’aura
gobe? Tun yanzu ya kamata ka fara daidaita tunaninsu…” K’arar abinda ya fa’di a
hannun Najee ne ya saka su juyawa da sauri. Suka zuba mata ido da glass cup
d’in da ta d’ebo kunun aya zata sha a ciki. Idanunta a waje take kallonsu bata
damu da b’arnar da ta yi ba, k’ok’arin ma taka glasses d’in take da sauri Umma
Cikin tsawa ta dakatar da ita. “Kina hauka ne Najee? Ba ki
ga abinda ke gabanki bane sai kin taka kin ji ciwo?” Da sauri ta ja baya sai
dai tuni kwalba ta nutse a k’afarta, bata damu ba ta ce “Aure zai yi gobe
Umma?” Umma ta zuba mata harara da ta saka ta yin shiru da sauran zancen da
yake bakinta.
“Wuce ka tafi Mujaheed dare ya yi.” Ta yi saurin fa’da ba
don komai ba sai don bata son Mujaheed d’in ya hango lagon Najeen. Yana fita ta
mik’e a zafafe ta isa gaban Najeen ji kake tasss ta wanketa da mari. “Aure zai
yi ko zaki hana shi ne uwarsa? Shin wai ma nawa kike da har kika san maganar
aure? Na sake jin zancen aurenki Da Jaheed a bakin ki sai na yi k’asa k’asa da
ke, ni ba banzar uwa ba ce da zan d’auki rashin kunyar yaran Zamani. Wuce ki
bani waje, ki cika min ciki ki ga idan ban hanaki aurensa ba, dama ina lura da
ke tunda aka yi maganar nan kike wani rawar kai, sai kin zubar da ajinki tun
kafin ya so ki ke kin nuna maitarki a fili, na sake gani zaki ga abinda zan
miki, bayan gaisuwa ban amince wata magana ta sake shiga tsakaninku ba.” Shiru
Najee ta yi hawaye na sauka a idanunta bata tab’a ganin b’acin ran Umma irin na
wannan lokacin ba. Jikinta a sanyaye ta ce “Ki yi hak’uri Umma don Allah.”
Umman ta d’aga mata kai tana furta “Hak’uri na d’aya ki cire wannan makauniyar
soyayyar daga ranki, mazan yanzu sun aureki suna tsananin son ki ma ya aka cika
balle ke ce kika nuna mai tar son sa a fili, ki zama mai aji na gaya miki.”
Najee ta d’aga kai, tana sake jaddada kalmar hak’urinta. Ta kuma k’udirta a
ranta daga ranar zata dage da addu’a Allah ya bata ikon rage son Jaheed a
zuciyarta.
________
Kashegari an idar da Sallahr Juma’a su Najma da Nasma na
zaune a falon Mahmeey ta babbar loud speaker da ke cikin gidan suka dinga jin
sanarwar d’aurin aure basu damu ba. Saboda girman masallacin duk sati yawanci
ana d’aura aure a masallacin don haka ba su mayar da hankali wajen saurarar su
wa za’a d’aurawa aure ba. Sai da Najma ta ji ance an d’aura auren Muhammad
Mujaheed da amaryarsa Ummul Khaieey.” Zan iya cewa wata irin wuta Najma ta
dinga gani a idanunta kunnuwanta suka d’auke na wuncin gadi. Ta mik’e da sauri
idanu waje tana kallon Nasma ta ce “Ba dai Jaheed aka d’aurawa aure ba?” Cikin
Mamaki Nasma ta ce “Idan ma shine ina ruwanki Najma? Da kike
neman sakawa kan ki damuwa?” Ta girgiza kanta tana furta “Ba zaki gane ba
Nasma, taimaka min ki je cikin gida ki jiyo min gaskiyar zance.” Nasma tsaki ta
ja tana mik’ewa ta shige d’akin Mahmeey tana furta “Da alama wani abu ya shiga
kan ki, bari na sanar da Mahmeey.” Mahmeey ta d’ago tana kallon Nasma bayan jin
abinda ta ce ta yi tsaki kafin ta mik’e ta fita parlourn. A zaune suka tarar da
Najma duk ta hargitse gashin kanta. Mahmeey tsaki ta zabga mata ta ce “Kina
hauka ne Najma? Wani irin abu ne wannan? Jaheed d’in da aka d’aurawa aure shine
kika sakawa kanki damuwa? Son sa kika fara yi? To idan ma son sa kika fara yi
ki zare maza maza don ba zan tab’a bari ki koma gidan matsiyacin can ba, balle
ma y’ar uwarki Ubanki ya basa sai ki d’auke hankalinki daga kansa.” Wani irin
bugu zuciyarta ta buga da k’arfin gaske a fili ta furta “Najee kuma?” Sai ta
hau yamutsa gashin kanta. Mahmeey baki ta bu’de tana kallonta da mamakinta
kamar wacce Jaheed ya yiwa asiri me take shirin gani haka? Ta zauna tana dafata
a hankali ta ce “Najma juyo ki gaya min menene a ranki game da wancan banzan
d’an mahaukaciyar?” Najma ta runtse idonta da k’arfin gaske tana furta “Son sa
nake Mahmeey son sa zai illata min zuciya tun bayan rabuwar mu kullum da
matsanancin tunaninsa da kewarsa nake kwana, wallahi ina son sa..” kafin ta
rufe bakinta Mahmeey ta zabga mata wasu irin maruka masu zafin gaske tana huci
ta furta “Ashe kuwa lokacin mutuwarki ya zo, don ko zaki mutu ba zaki komawa
auren wancan banzan yaron ba d’an mahaukaciya mara asali da tushe……” Najma ta
runtse idonta a fili ta furta “Wallahi Ina son sa Mahmeey I love him so
much…..”
JIKAR NASHE✍π½
Saura 3pages shafukan bati su k’are hanzarta biyan naki, don
jin wace waina za’a toya a masarautar gabas idan Najee ta je shin zata samo
silar cikin Jaheed da Hassan d’in sa? Ko kuma tata k’addarar zata gamu da ita?
Duka yana cikin wancan tafiyar biya 500 kacal a asusun banki kamar haka.
2118666253 UBA. Sai ki tura shaidar biya 08033748387.
Special people 1k kacal. Sai na ji ku.
KUDIRAR ALLAH
18.
NAZEEFAH SABO NASHE.
08033748387.
________________
Wani irin kallo Mahmeey ta zuba mata, mai cike da nuna
zallar takaici kafin ta zabga tsaki ta ce “Tunda kina son sa Ai sai ki bi sa,
shashashar yarinya kawai.” Daga haka ta wuce ta bar ta anan zaune hannunta
cikin tulin sumar kanta tana ja a hankali kamar wata mahaukaciya sabon kamu. Da
gaske ita kanta gani take kamar sihiri aka mata, ta yaya mutumin da ta tsana a
rayuwa zai koma mata masoyin da take jin ba zata iya rayuwa ba idan ba shi?
Hawaye ne suka cigaba da mata sintiri a fuska. Cikin rashin nutsuwar jiki da ta
ruhi ta mik’e a hankali zuwa cikin d’akinta. Windown d’akin ta yaye tana hango
tarin Mutanen da Jaheed ya kasa b’oyuwa a cikinsu. Gaba d’aya ya fi so kyau da
cikar zati. Yanzu shikkenan ta rasa shi? Murmushinsa kawai take hangowa ta
windown da alama yana cikin tsananin farin cikin da ya kasa b’oyuwa. Haushi da
tsananin kishin sa ne suka shiga kama mata zuciya ta kife kanta a saman windown
tana sakin ajiyar zuciya a hankali take furta “Why? Me yasa zuciyata? Me yasa ?
Baki min adalci ba. Ta share hawayen ha’de da jan wayarta kai tsaye ta shiga
Instagram searching sunansa ta yi abinda bata tab’a kwatanta yi ba. Mamaki ya
kamata ganin yarda yake da tarin followers fin million d’aya. Ashe Jaheed
celebrity ne bata sani ba? Ta shiga comments d’insa inda ya yi posting wani pic
d’insa da ya yi masifar kyau ba zata manta ba pic d’in da sallah ya yi shi don
ta tuna sanda ya saka shaddar, gani ta yi y’an mata suna ta furta wow! Wow! A
comment majority sun kasa hak’uri har da masu cewa check your dm sir. Da sauri
ta wurgar da wayar ta kifa kanta a pillow ta saki kuka mai ratsa zuciya.
******
Jaheed kuwa zan iya cewa farin ciki da yake ciki a ranar ji
yake ba na biyunsa, don haka cikin fara’a da yalwar murmushi yake amsa gaisuwar
abokansa. Haka aka gama hotuna abokan su ka watse bayan Faruk ya sanar musu
gobe akwai kai amarya Suna buk’atar su zo su musu kara. Sai sannan suka samu
damar shiga cikin gida shi da Faruk. Najwa da take tsaye a parlourn ta k’i
d’ago da kanta balle ta kalleshi don wani irin haushinsa take ji da kishi mai
zafin gaske. Nene kanta ba wani fara’a take ba don ta ita da ba’a fara d’aura
wannan auren ba. Umma ce kawai ta tareshi da fara’a tana fa’din “Ma sha Allah
Jaheed ango.” Ya d’an sunne kai yana murmushi, ta gefen ido ya ke hangen Najee
da ta k’i juyowa ta kalleshi. Bai mata magana ba, Umma ta masa fatan alheri
kafin ta kalli Nene ta ce “Saura ke Nene ban ji kin ce komai ba?” “Allah ya yi
albarka shine kawai abidna zan ce.” Umma ta saki murmushi tana fa’din “A haka
ma mu ne da godiya.” “Najee” Jaheed ya fa’da a hankali ta d’ago da k’yar tana
kallonsa kafin ta ha’diye abinda take ji a ranta da k’yar ta furta
“Congratulations Ya. Jaheed.” Ya lumshe idonsa yana furta “Thanks Najee, Allah
ya nuna mana namu.” Ta d’auke kanta ba tare da ta amsa ba, sai Nene ce ta masa
da saurinta tana fa’din “Ameen, ranar kuwa da na yi rawa da juyi.” Dariya sosai
Umma da Jaheed har ma da Faruk suka yi. Haka suka zauna ana ta hira har Baffa
ma ya shigo aka cigaba da hirar da shi. Yana sake jaddadawa Jaheed hakkokin da
suka rataya a kansa a matsayin sa na Miji, idan kuma ya zalunci matarsa ya sani
tabbas sai Allah ya saka mata. Jaheed ya amsa kansa a k’asa idan bai manta ba
irin waccan nasihar da Baffa ya masa ce wancan satin da za’a kai masa Najma sai
ga shi still yana maimaita masa tabbas Baffa ya ci ya amsa sunan Nagartaccen
Mutum dattijon k’warai.
******
Bayan sati guda…..
Jaheed da amaryar sa suka d’aga Qatar bayan sun yiwa y’an
uwa sallama cike da kewar juna suka bar ahalinsu zuwa wata k’asar. Najma
hankalinta ya tashi sosai da sosai ta rasa nutsuwarta sosai take son Jaheed a
yanzu da ta tabbatar ya mata nasiha.
Lokacin ana saura sati guda azimi. Baffa ya fara shirin
tafiya Umara da yake duk shekara yawanci a can yake aziminsa, kowace shekara
kuma akwai matar da yake tafiya da ita. Wannan zuwan sai ya fa’da kan Mahmeey.
Don haka a daren da zai yi tafiya ya tara duka ahalinsa kamar yarda ya saba. Ya
musu nasiha da su ji tsoron Allah musamman idan baya nan, su tuna duk abidna za
su yi Allah na kallonsu. Kowa ya amsa a lokacin wata dabara ta fa’dowa Umma a
zuciya da sauri ta kalli Baffan yana shirin raba musu ku’di kamar yarda ya
saba, ta ce “Baffa ina neman alfarma don Allah.” Ya juyo yana maida hankalinsa
gareta “Ina jin ki.” Ta gyara zamanta tana furta “Dama cewa zan yi tunda ana
hutun makaranta don Allah Najma zata Bauchi wajen Hajiya Inna hutu ita da Nene
zan aika saboda su d’ebe mata kewa ka san jikin tsufa.” Ya juya yana nazarinta
baya jin shakkar tura Najma wajen Hajiya Inna don ya san Macece mai nagarta da
sanin ya kamata, Yayar Umman ce amma kallon Uwa yake mata don ita ta rik’e
Umman har ta ba shi aurenta. Har ta fitar da rai zai yarda sai kuma ta ji ya ce
“Kwana nawa za su yi? Kin san ban fiye son y’a mace da barin gida ba, don Ma
dai Hajja Inna ce da kai tsaye zan ce a’a” Cikin fara’a Umma ta ce “Ko ana gobe
Sallah sai su dawo.” Ya girgiza kai yana furta “Kada su wuce haka, idan sun
shirya sai Habu Driver ya kai su.” Umma ta shiga godiya cikin farin ciki.
Kashegari kuwa da sassafe Baffa da Mahmeey suka wuce Makka,
Bayan Baffan yasa su Najma da Nasma sun ha’de kayansu kaf sun koma b’angaren
Umma don kula da tarbiyyarsu.
Sai da ta gama komai sannan ta shiga d’akin Nenen. A saman
sallaya ta sameta na azkar bayan ta idar da Sallahr walaha. Ta zauna a gefen
gadon tana fa’din Allah ya amsa mana dai Nene.” Ameen” Nene ta ce tana nazarin
fuskar Umman da alama akwai abinda yake tafe da ita. “Yaushe za mu tafi Bauchin
da na ji kina gayawa Baffa?” Umma tana murmushi ta ce “Ba bauchi za ku ba Nene,
GARIN GABAS za ku ke da Najee…” wani irin waro ido Nene ta yi tana kallonta
murya na rawa ta ce “GARIN GABAS kuma?”
Umma ta d’aga kai cike da gasgata wa ta ce “Yanzu nake son
mu fara wannan yak’in na gano silar samuwar cikin Jaheed da d’an uwansa, Najee
ba zata iya ita ka’dai ba, ni kuma shekaru Uku ina tunanin sun yi nisa don haka
zaku tafi tare ki taimaka mata bayan kun yi Basajan Kamanninku.” Nene
hankalinta tashe take kallon Umma Sam bata gano wasa a icon Umman ba, da gaske
abinda yake zuciyarta kenan. Ta saki ajiyar zuciya a hankali muryarta a raunane
ta ce “Ina jin tsoron Umman Yara, wallahi ina tsoron shiga masarautar nan.”
Umma ta dubeta duk da tana jin tausayin yanayin da ta ganta bai hanata murtiske
tsoron nata ba ta ce “Wannan shine lokacin da ya dace ku je Nene, zamanki anan
d’in ba tare da kin san me can yake ciki ba ina ga sam ba mafita ba ce, ki je
can ku yi fito na fito da koma waye ya yi silar shigar Ki cikin matsalar nan.
Najwa tana da wayo kuma tana da kaifin basira da hankali fiye da ta wani babban
don haka na tabbata zata taimaka miki, zan nuna muku abubuwan da zaku yi Basaja
da su a jikin ku da fatarku ta yarda duk bala’in mutum ba zai gane ku ba In sha
Allah har sai mun cimma mafita.” Nene ta saki ajiyar zuciya tana d’aga kanta a
hankali duk da tana jin tsoron har a lokacin sai maganar Umma ta k’arfafa mata
gwiwa, ita da kanta ta san zamanta a nan d’in bai da wata ma’ana zuwa can d’in
ta fuskanci k’alubalen shine abinda ya kamaceta, don haka ta amince da shawarar
Umma d’ari bisa d’ari ta kuma samu k’warin gwiwa a tattare da ita. “Yaushe za
mu tafi?” Ta ce tana kallon Umma. Umma ta saki ajiyar zuciya tana jin murnar
nasarar da ta samu a kan Nene ta amincewarta ta ce “Jibi In sha Allah, sai dai
ina so ki kiyaye kin san dai ban gayawa Baffa inda za ku ba, ita kanta Hajja
yanzu sai na kirata na rok’eta kada ta sanar da Baffa inda kuka je, Nene bana
son a samu matsala don ke da kan ki kin san Baffa mutum ne mai kafaffen ra’ayi
don haka ki kiyaye.” Nene ta d’aga kai tana furta “In sha Allah.” Umma ta mik’e
ta fice daga d’akin.
A d’akinta ta zaunar da Najee ta gaya mata dukkan shirinsu.
Haka kawai sai Najee ta ji gabanta na matsanancin bugu. Da sauri ta kalli Umma
ta ce “Umma da ni kuma za’a?” Umma ta d’aga kai tana nazarin y’ar tata da ta
bayyana dukkan tsoronta ga lamarin. Don son ta k’arfafeta sai ta ce “Da ke za’a
je Najwa ina ji a jikina zaki iya don kina da kaifin basira da hangen nesa, In
sha Allah kuma ba abinda zai faru.” Najwa ta d’an lumshe idonta tana amsawa a
hankali. Tana kallon Umman ta fice daga d’akinta ta barta cikin yanayi na bugun
zuciya da ma rauninta gaba d’aya da ba zata iya cewa ga sababinsu ba.
Shirye shirye suka kankama Umma ta musu duk wani tanadi da
za su buk’ata a can. Kafin ta samo wani abu da za su shafa a jikinsu kalar
jikinsu ta dawo bak’a na lokaci ka’dan idan kuma suka wanke shikkenan. Hak’oran
roba aka sakawa Najwa da zai b’oye duk wani kamanninta sai ta zama irin mutanen
nan masu Gatso yanayin shigarsu ya yi kama da na mutanen nan da ake kira
bararoji. Sun dai nuna alamun suna cikin wahala matuk’a ainun. Da Asussuba suka
yi wannan shirin Umma ta kira Faruk ta sanar da shi komai. Ta kuma umarceshi ya
kai su har cikin garin Gabas d’in ya tabbata sun shiga cikin masarautar kafin
barowarsa garin. Duk da Faruk ya ji tsoro shima a farko amma da Umma ta bayyana
masa dalilinta sai ya ji tsoron ya kau, ya samu k’warin gwiwa suka tafi ya saka
location na sunan garin a wayarsa abinka da Zamani nan da nan waya ta nuna masa
hanyar da zata sada shi da Babban garin Gabas d’in. Umma ta musu fatan alheri
ta juya gida don bata amince Driver ya kai su ba, zuciyatta ta fi aminta da
Faruk ta san idan Faruk ne bata yarda za’a yi Baffa ya san inda suka je
sab’anin Driver da zai iya gayawa wani k’arshe har sirrin da ba sa so ya
bayyana a zo a sani ta shiga uku wajen Baffa.
_________MASARAUTAR GABAS……
Tunda suka iso cikin garin gaban Nene da na Najwa bai daina
fa’duwa ba. Shi kansa Faruk haka kawai ya ji nasa gaban yana fa’duwa. Ya dai yi
addu’a ya bar abin a ransa. Yana kallon Nene ta mudubi ya ce “Yanzu ya za’ayi
ku samu shiga gidan Sarautar nan, don daga gani akwai matakan tsaro a gidan.”
Nene ta bi gidan da kallo gaba d’aya fasalin da ta san shi ya canja, banda ma
an rubuta Masarautar Gabas bai zama lallai ta amince shi ba ne. Saboda yarda
ginin ya zama na Zamani mai matuk’ar kyau da burge mai kallonsa. Ta saki ajiyar
zuciya tana furta “Shine abin tambaya Faruk, ni kai na ban san ta yarda za mu
shiga gidan sarautar nan ba, asalima Wallahi tsoro nake ji…”
JIKAR NASHE✍π½ To fa! ko wa ya san ta inda za su
shiga gidan sarautar nan? Ga dai bikin zuwa babu zani.
KUDIRAR ALLAH..
19.
NAZEEFAH SABO NASHE
08033748387.
Faruk ya saki ajiyar zuciya a hankali Kafin ya furta Ina
zuwa. Ya fita daga motar cikin takun nutsuwarsa ya isa bakin babbar k’ofar mai
tambarin sarauta. Babban gate ne mai girman gaske kalar ruwan gold. Tun daga
nesa zaka hango tsaruwarsa da girmansa kamar Anan aka dasa shi. Daga ganinsa
mutanen da suke bakin gate d’in suka taso suna masa wani duba. Faruk ya samo
nutsuwar dole ya sakawa fuskarsa duk da k’ok’arin zuciyarsa na son tona masa
asiri. Hannu ya mik’a wa wanda ya fara zuwa wajensa d’in. Bak’in mutum ne dogo
sosai mai siffar samudawa. Sai da ya ‘dan yi Jim kafin ya mik’awa Faruk hannu
yana furta “Bawan Allah me ke tafe da kai? In dai Sarki kake son gani gwara ma
ka juya yau bai sanar mana zai ga kowa ba, don shirye shirye na’din Yarima
wanda zai gaji sarki bayan mutuwar sa ake saboda haka bai da damar ganin kowa.”
Faruk ya saki ajiyar zuciya yana furta “Kamar ka san abinda ya kawo ni kenan,
yanzu idan zan ga Sarkin ta ya Zan samu appointment.” Basamuden ya sake masa
wani kallo kafin ya ce “Yaushe kuke tunanin Sarkin Gabas ya zama sarki mai
araha da za’a iya ganinsa a koda wani lokaci, bana jin duk Nigeria akwai Sarki
mai martabarsa don haka ganinsa yake da matuk’ar wahala.” “Ko da wa’dannan?”
Faruk ya fa’da yana nuna masa damin ku’din da ke hannunsa da shi kansa bai san
yawansu ba. Da sauri Bafaden ya ware ido yana kallonsa kafin ya furta “Afuwa
Yallaba’ai Ai tun farko sai ka min bayani. In dai haka ne zan baka appointment
zuwa Nan da jibi kazo zaka ga Sarki.” Murmushi Faruk ya yi, yana jinjina lamarin
mutanen k’asar mu inda basa abu don Allah sai don Naira yanzu dubi yanda ya
mayar da shi Yallab’ai don kawai ya ga Naira.
Ganin ya samu kansa yarda yake so sai kawai ya saki murmushi yana furta
“To godiya nake, sai dai ba Sarkin nake buk’atar gani ba, ina son ka bani
numberrka nima zan baka tawa a duk sanda aka shirya taron ka sanar da ni.” Ya
fa’da yana mik’a masa ku’din da suka doshi Naira dubu d’ari biyu abinda Bafaden
nan bai tab’a rik’ewa ba kenan, don koda Sarkin Gabas zai bada Zakkar kamarsu
to fa kafin tazo kansu an zabtare kaso mafi tsoka. Jikinsa na rawa ya dinga
hangen mutanen da suke gefe ya yi saurin tura ku’din cikin Babbar rigarsa yana
furta “An gama ranka ya da’de saka min numberr.” Faruk ya karb’i wayar tasa mai
k’irar Nokia ya saka masa numberrsa shi kuma ya kira layinsa inda kiran ya
shigo wayarsa sai ya yi saving yana murmushi ya kalli Bafaden ya masa godiya
yana furta “A duk sanda na shirya ganin Sarkin ina fatan zaka shige min gaba.”
Da sauri ya d’aga kai yana futta “Mai zai hana, ko kai abokin Yarima ne?” Faruk
ya ‘d’aga masa kai kawai yana tafiya da sauri. Ya tsallaka can gefen titi inda
ya yi parking motarsa. Sai da ya mata key sannan murya a hankali ya ce “Ba ta
hanyar da zaku samu shiga gidan Sarkin nan a yanzu, sai dai mai gadin ya sanar
da ni akwai taron da za’a yi zai kira ni ya gaya min to ina ga ta hanyar nan ne
ka’dai zaku iya shiga gidan, don haka yanzu sai dai na kai ku hotel idan ranar
taron ta yi zan sanar da ku ta waya sai ku shiga kafin nan mun samo dabarar da
zata sadaku da shiga cikin ahalin Sarkin sosai, amma fa dole ku yi takatsantsan
Nene.” Ya fa’da idanunsa akan Nene. Ta saki ajiyar zuciya tana d’aga kai. Shi
Kuma ya je ya samar musu masauk’i mai kyau inda zasu zauna kafin ranar taron ta
zo, tunda dai Nene bata da wasu y’an uwa da ta sani duk rayuwarsu a gidan
Sarkin yake anan ta girma anan ta tashi. Kuma ba halin zuwa wajen iyayenta bata
sani ba suna raye ko sun mutu ma? Wannan ka’dai idan ta tuna yana d’aga mata
hankali sosai.
__________________
A zafafe Fulani Raheena ta zubawa Jakadiya ido bayan ta gama
isar mata da sak’on Sarkin Gabas. “Me kike fa’da min Jakadiya?” Jakadiya ta
rusunar da kanta ka’dan tana sake maimaita abinda ta ce “Sarki ya ce a sanar da
ku ku fara shirin gangamin taron bikin na’din Yareema kamar yarda shari’a ta
tanadar za’a yi nan da kwana bakwai.” Fulani Raheena ta sake ware idonta akanta
ta ce “Bayan shi fa? Akwai abinda kika fa’da bayan wannan.” Jakadiya shiru ta
yi bata so aka ji mutuwar sarki a bakin ta ba, shaf ta manta da Raheena take
magana ba da Saddik’a Uwar goyon Murad ba shi yasa da farko ta ambaci Murad a
matsayin wanda za’a na’da Yareema. “Ba zaki maimaita bane Jakadiya?” K’wayar
idanunta a k’asa ta furta “Allah ya huci ran Gimbeeya Sarki ya zartar da
Umarnin na’da Yareema Murad a matsayin Magajin…..” Kallon da ta wurga mata ne
yasa ta datse zancenta tana ha’diyar yawu da k’yar. Tsoron idanun Fulani
Raheena ya kamata. Sai ta ga Fulanin ta saki dariya ta ce “Shine ya zartar da
na’da Murad d’in ko mutanen gari?” Jakadiya turus ta yi ta kasa amsa mata. “Ki
koma ki sanar da shi yana buk’atar ganinsa yanzu ina neman iso.” Jikin Jakadiya
na rawa ta juya da sauri don isar da sak’on Fulani Raheenan, ta sani sarai ba a
b’ata mata rai bata k’i ta ci mutuncin mutum komai girmansa ba inda suka sha
banban da sauran matan sarki kenan, musamman Fulani Saddik’a.
Jakadiya na isar da sak’on Mai martaba ya saki murmushi shi
da kansa ya san an zo wajen Raheena rigima zata yi ta gasken gaske shi kuma ya
shiryawa duk abinda tazo da shi. “Aje a ce muna mata maraba.” Ya fa’da murya a
nutse. Da sauri Jakadiya ta koma ta k’ofar da zata sadaka b’angaren Raheenan.
Tun kafin ta gama isar mata da sak’on ta mik’e a fusace ta bu’de wata k’ofa da
zata sadaka da b’angaren Sarkin ta sashenta kenan su matansa ka’dai suke da
alhakin bi ta wannan k’ofar. A ciki ta yi sallama. Shi kuma ya yi gyaran murya
yana amsa mata sallamar cikin kamalalliyar muryarsa mai kwarjini. Ta zauna
idanunta akan hoton Yareema Murad da yake kafe a jikin bangon d’akin kamar ka
kira shi ya amsa maka. Da k’yar ta ha’diye wani yawu da ya tsaya mata a
mak’oshi tana jin haushin Murad da tsanar masa ma gaba d’aya wato ita baya ta
nata y’ay’an sai ta Murad d’an gold duk nata ma a yanzu sun kai munzali banda
ma ta farkon macece itace sa’ar Murad shi kuma na biyun shekarunsa ashirin da
uku, don bayan haihuwar macen shikkenan sai haihuwa ta bu’de mata, y’ay’anta
hu’du biyu maza biyu mata. “Sak’o ya isar min.” Ta furta muryarta a cunkushe.
Kamar ba zai yi magana ba sai kuma ta ji ya ce “Alhamdulillah, haka ake so
dafatan zaku nutsu ku shirya abinda ya dace, ki k’addara Muraad d’an cikin ki
ne don haka yarda zaki tsyaa akan harkar y’ay’an cikin ki haka nake nema ki
tsaya akan na Murad.” “Me yasa za’a na’dashi Yareema alhali kowa ya san ba
halastaccen d’anka bane?” Wata irin d’au kewar wuta SARKI ya yi yana mamakin
jin furucinta. Murya a sark’e ya ce “Ke
kika haramta shi?” A zafafe ta d’ago tana kallonsa “Wacece Uwarsa a cikin mu
matanka hu’du da musulunci ya halatta maka ka kusance mu? Ko kuma kana da
k’wark’wara ne?” Zuwa lokacin zuciyar Maimartaba ta fara hassala wani irin
tarnak’i yake ji a zuciyarsa sai dai ya daure abinda yake ji d’in ya bita da
kallo kawai. “Don haka Murad ko mutuwa ya yi ba shi da gadon ka in dai duka
babu d’aya a cikinmu da aka yiwa cikinsa ya haife kuma kowa ya san a tsari irin
ta sarautar Yankin Gabas basu amince da k’wark’wara ba don haka Muraad ba shi
da ikon gadar mulkinka koda baka da wasu y’ay’an balle kana da su. Abdulhakeem
shine yake da wannan damar.” Murmushi Sarki ya sakar mata ya ce “Idan kuma ba
haka ba fa? Tashi Raheena ki fice min daga d’aki mara tsoron Allah kawai, idan
baki yi wasa ba….” Ya fa’da yana cizon leb’ensa kawai ba tare da ya k’arasa
abinda yake son fa’da d’in ba. Ta mik’e a fusace ta fice daga d’akin tana jin
zuciyarta na sake fusata da wani irin bugu mai k’arfin gaske, ta yaya komai
yake shirin Kwab’e mata ne? Duk shekarun da ta kwashe tana jiran amsa sunan MAI
BABBAN D’AKI yana shirin tafiya a banza kenan?
Tunda ta shiga d’akinta zagaye d’akin kawai take cike da
neman mafita tunani iri-iri ya shiga zuwan mata sai dai ta rasa tudun dafawa.
Da tsauri kamar wacce aka tsikara ta d’au wayarta ta shiga danna wasu numbers
bugu uku wayar ta shiga. Daga can gefe cikin murya mai kaushi aka amsa mata.
“Komai yana shirin kwab’ewa ya kamata mu san abin yi, idan ba haka ba duk
shirin mu ya zama a banza, kuna da labarin MURAD yake shirin nad’awa a matsayin
magajinsa?” Daga can gefen aka tuntsire da wata bahaguwar dariya kafin cikin
kaurara murya a ce “Lokaci ya zo kenan? Lokacin bankad’uwar sirrika da dama?
Ciki kuwa har da lokacin bayyanuwar naki sirrin da kika da’de kina
k’udundunewa, ko kin zata bamu son komai ba akan naki sirrin?” K’it ta kashe
wayar jikinta na mak’yark’yata jin abinda mutumin ya ce, ta ware ido tana sake
kallo da nazarin numberr ko ta yi wani kuskure ne wajen saka numberr tunda ta
san number biyu ce banbancin numberr da ta wancan wanda ya san d’ayan sirrin
nata. Abin mamaki numberr dai da take nema ce, amma me yasa? Ya aka yi ya san
abinda bata son ya sani… wannan karan tsoron da take ciki ya fi na gaya mata da
aka yi Murad ne Magajin sarki. Ta yaya zata yi maganin Matsalolin da suke
tunkarota. K’arar da wayarta ta yi ne ya sake razanata a tsoroce jikinta na
b’ari ta kai dubanta kan wayar tsoronta ya sake bayyana ganin sune dai suka
sake kiranta. Bata damar k’in d’agawa don ita da kanta ta san bata isa ba. Duk
mulkinta da isarta a idanun wa’dannan mutanen banza suke, don sun san abin da
duk take k’ullawa. A zuciyatta ta shiga tsinewa wanda ya samar da cikin Murad
duk da bata shiga cikin wa’dannan matsalolinba. Hannunta na rawa ta sake
dank’ar wayar ta kara a kunnenta. “Ki nutsu ki saurari abinda za mu ce miki,
idan kina son komai ya tafi cikin sa’a da nasara sai kin san yarda aka yi kika
ha’da auren Murad da k’anwarki, ta haka ne zamu samu cimma burinmu a kansa, za
mu kashe shi ba tare da an san mu ne sila ba, abu na gaba daga yanzu zuwa ko
yaushe kada ki sake ki sake nunawa Mijinki ba kya son na’da Murad da zai yi a
matsayin magajinsa.” Jikinta na rawa ta amsa musu bayan nan kafin ta ce komai
sun kashe wayar. Itama ta zare layin da sauri ta mayar da shi inda take
adanashi don bata amfani da shi sai matsala irin haka ta taso. Daga ranar ta
k’udirce a ranta ba zata sake magana akan na’din da za’a yiwa Murad ba, duk da
ta san mawuyacin
Abu ne al’ummar garin mahakuntan sarautar su yarda da na’din
wanda ba a san ta yarda aka samar da cikinsa ba. Da ita aka fara shirin duk
wani abu da za’a buk’ata a gidan sarautar Sarki ya ji da’din abinda ta yi don
haka ba jin fargabar komai ya sakar mata dukka ragama duk da wani gefe na
zuciyarsa na son nuna masa kuskurensa a cikin aikata hakan.
_________ Ranar Na’din Sarauta…….
Tun safiyar ranar yake jin zuciyarsa ba da’di, har hakan ya
bayyana akan fuskarsa, duk da dama Miskili ne bai fiye sakin fuska ba, sai dai
na yau ya bayyana matuk’a ainun. Da k’yar ya mik’e ya fara shirin wanka, shima
hakan bai samu ba har sai bayan da Fulani Raheena da yake kira Mamma ta shigo
sashen nasa har sau biyu tana sanar da shi mutane sun fara hallara kada a zo
ana jiransa.
Da Rangaji ya isa tafkeken toilet d’in nasa yana kallon
ruwan wankan da hadiminsa ya cika masa. Kamar koda yaushe kuma an jera komai
yarda ya kamata. A kasalance ya fara wankan. Kafin ya fito ya fara shiri duk da
k’ok’arin sa na son aikata sauri sai dai kasalar da zuciayrsa take ciki ya kasa
aikata hakan sosai yake jin rauni a zuciayrsa da gangar jikinsa. Sam mai
martaba ya kasa ganewa ne amma baya son sarautar nan ko ka’dan balle har a ce
wai an na’dashi Yareema mai jiran gado. Himilin kayan da aka ajiye akan gado da
ake son duk ya saka su a jikinsa ya dinga bi da kallo yana yamutse fuksa. Sam
baya son saka kayan sarauta nauyi suke masa sosai su hana shi sakat, ai kuwa
yana sakawa yana mita don ya san idan bai saka bama Mamma ba k’yaleshi zata yi
ba. Rawanin ne dai bai na’da ba don bai iya ba ma kuma ya san ko ya na’da idan
ya je wajen kunce shi za’a yi a sake na’da masa wani. Don haka yana mita ya
zira jibgegiyar Alkyabbar a jikinsa. Wani irin kyau da cikar zati ya yi ba d’an
ka’dan ba. Shi da kansa sai da ya tsaya a mudubi yana k’arewa kansa kallo.
Kafin ya yamutsa sumar kansa ka’dan. Ya zura takalminsa irin na sarauta ya yi
gyaran murya. Nan da nan Fadawansa suka gyara tsayuwarsu ya fito suka rufa masa
baya suna kirari da fa’din “An gaida Yareema mai jiran gado, sarautar Sarkin
gabas da kai ta dace.” Haushi abin yake ba shi sai dai bai isa ya hana su ba
haka suka isa har babbar fadar sarki ta sirrantacciyar hanyar da take sashensa.
Wayarsa ce ta shiga ringing kafin shigarsu Fadar. Ya bi wayar da kallo yana mamki
ganin bak’uwar number a wayarsa da ba wanda ya san numberr sai Ahalinsa
Familynsa, don ba business line d’insa bane. Har zai kashe sai kuma ya ji yana
sha’awar ya amsa kiran ya ji waye da kuma dalilin kiran? Tun kafin ya yi magana
ya ji an saki ajiyar zuciya ana furta
“Yauwa Murad kana ji na?” Ajiyar zuciya ya saki jin Mamma ce, ya ce “Ina
ji Mamma.” “Yauwa kana ina ne na zo sashenka baka nan.” Ya amsa da cewa “Gani
nan shiga Fada yanzun nan…” “Maza ka juyo Muraad kada ka shiga fadar nan, akwai
inda za mu, akwai Babban Malamin da ya buk’aci ganinka zai maka addu’a kafin a
maka na’din nan, aminin Baffa na ne.” Murad ya saki ajiyar zuciya yana futrta
“To Mamma, a ina Zan sameki?” Ka zo sashena ina nan cikin mota ina jiranka.” Ta
katse wayar shi kuma ya juya yana kallon fadawansa biyu ya furta “Mu je sashen
Mamma, tana buk’atar gani na, kafin isata wajen na’din.” Suka juya da sauri don
cika umarninsa. A Motar ya sameta ya zauna a gefenta, fadawansa kuma suka shiga
Motar fadawanta da ke bayan ta Momma. Drivernta ya ja da sauri don isa gidan
Babban Malami, Malam Jazuli.
Addu’a ya masa sosai, kafin ya ba shi ruwan Zam zam ya sha
sosai ya ce “To da ikon Allah ba abinda zai sameka ba dai mutum da muguntarsa
ba.” Murad ya saki murmushi yana amsa masa da ameen suka masa sallama d’an
tsohon malamin da baya iya tafiya sosai ya rakasu bakin k’ofa cike da addu’oin
samun nasara.
A hanyar su ta dawowa gudu kawai suke don haka ba su lura da
su Najwa da ke gabansu ba ba su yi aune ba suka buge Nene Ai kuwa ta fa’di jini
na zuba ta gefen Hancinta Najwa ta zunduma ihu sosai hannunta a kai tana furta
Na shiga uku. Fulani Saddik’a ta ware ido tana kallon Murad ta furta
Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna! Lumshe idonsa Murad ya yi yana jin yarda
zuciyarsa take bugu da k’arfin gaske kamar zata yi tsalle ta fito daga
k’irjinsa, bai san me yasa ba, bai fito daga motar ba, sai dai salatin da ya ji
drivern ya yi yasa shi shima fitowa ba shiri. Idanunsa akan na Nene da take
kwance gefen titi kamar matacciya suttirun jikinta da kamanninta sun bayyana a
wahale suke matuk’a da gaske daga ita har Najee da suka yi kama da bararoji!
JIKAR NASHE✍π½
KUDIRAR ALLAH….
20.
NAZEEFAH SABO NASHE.
______________
Numfashin Najwa ne ya kusa d’aukewa saboda abinda idanunta
suka nuna mata. Tsananin kamannin Jaheed da wannan bawan Allahn da Yake tsaye a
gabanta. Ko baa fa’da mata ba ta san shine d’an Uwan Jaheed da Nene ta basu
labarin shi ta fara haihuwa. Kamar amsa da tunaninta sai ta ji Matar da ke
tsaye ta ce “Murad duba baiwar Allahn nan mana kamar fa bata numfashi.” Sai
sannan ya lura da abinda yake kawai samun kansa ya yi da tsurawa Nene ido
gabansa na fa’duwar da bai san dalili ba. Ya d’ago yana kallon Mamma da take ba
shi umarni, muryarsa a shak’e kamar wanda aka wa dole ya ce “She is alive but
tana buk’atar ganin likita da wuri Mamma.” Ya fa’da a hankali cikin muryar da
ta bayyana rashin son maganarsa a zahiri. Mammah ta saki ajiyar zuciya kafin ta
kama hannun Nene don da tsoro da fargaba sun hanata gane Nenen tana numfashi.
“Ku kamata mu kai ta asibitin cikin Fada, a bata duk wata kula da ta dace ni
zan raka Murad wajen taron can da zarar an tashi zan taho nan na duba ta Ya
Allah ka dubemu ka bata lafiya.” Ta fa’da tana sauke idanunta kan Najee da ta
bi duk ta tsorata da lamarin, ga shi duk motsin da Murad ya yi idanunta na
kansa har abin ya fara ba shi haushi. Ya juya a fusace yana kallonta. “Ke
d’auke idanunki a kai na haba.” Da sauri kuwa ta d’auke idanun nata a kansa
tana mamakin yarda yake masifa banbancin da yake nuna su kenan tsakaninsa da
Jaheed shi Salihi ne bai fiya masifa sosai ba, ga yawan fara’a shi kuwa wannan
bata hango hakan tare da shi ba, tsabar ha’de rai girarsa har kusan ha’deta
take. Tana kallo suka shiga mota aka saka Nenenta a wata Motar daban da sauri
ta bi bayansu da d’an k’ullin kayansu da suke cikin buhu. Wani kallo Murad ya
mata ganin ta nufi motar gadan-gadan “Hey you ina zaki?” Ya fa’da a tsawace
sosai cikin muryar da ke bayyana zamowarsa Soja. Ta ja ta tsaya turus gabanta
na fad’uwa. Mamma ce ta ja tsaki tana harararsa “Ban gane ina zata ba? Mu buge
nata Uwa sannan ka dinga tambayar ina zata? So kake mu barta anan don rashin
tausayi? Je ki ki shiga can motar kin ji.” Da sauri Najee ta shiga motar da aka
saka Nenen Muraad ya bi bayanta da harara har da d’an guntun tsaki bai san me
yasa ba haka kawai sai ya ji yarinyar bata kwanta masa a rai ba, bai sani ba ko
don tsananin muninta ne da rashin tsafta Oho? Ya d’an tab’e baki yana sakin ajiyar
zuciya ka’dan bai furta komai ba don ya san idan ya furta d’in ma Mammah wannan
karan zata iya kai masa duka a yarda ya hango tsananin b’acin ranta.
Harabar gidan Sarkin Gabas d’in ta cika mak’il da jama’a,
abin har ya fara bawa Murad tsoro ganin yarda wajen ya zama ba matsaka tsinke
kamar wani taron sallahr idi. Daga cikin motar ya saki ajiyar zuciya yana d’an
murza goshinsa ka’dan saboda wannan abin ne fa sam baya son sarauta ga shi
Bahbah ya kafe sai ya na’da shi. Mamma da ta lura da yanayinsa ta saki tsaki a
fili ta furta “Gwara ma ka sakawa kanka son jama’a na dole in gaya maka, don
Jama’a yanzu ka fara ganinsu tunda ka zo a jinin sarauta nan gaba ma kai ne
Sarki da yardar Allah.” A fili ya furta “Ba ameen ba Mamma, ni fa bana son
maganar sarautar nan wallahi da Bahbah zai bi ta tawa da Abdul ya na’da wa abin
nan, haka kawai a d’orawa mutum abinda zai hana shi nutsuwa a bar ni da jidali,
ni kayan sarautar ma ba son saka su nake ba na fi son Normal English wears.”
Mamma bata sake tanka shi ba, don ba k’aramin haushi yake bata ba idan ta ji ya
ce baya son sarautar nan ita kuwa burinta kenan ko dai ba a kira ta Uwar sarki
ba, za’a kirarta marik’iyar Sarki tunda dai Murad ba shi da wata Uwar bayan
ita. Ta fita daga motar tana furta “Addu’a at first place yallab’ai.” Daga haka
ta bi tsakiyar fadawanta zuwa inda aka tana da mata don zama. A kuma lokacin ne
masu tafiya da Murad d’in suka iso bakin motar suka yi saurin bu’de masa ana
rufe shi ta gefe da gefe. Murad ji yake kamar ya saka ihu ya runtse idonsa da
ke cikin black shades d’insa ta yarda duk bala’inka ba zaka hango k’waya idonsa
ba. A haka fuskarsa a ha’de ya dinga tafiya ta tsakiyar mutane don wannan shine
karo na farko da mutane za su san Sarkin su mai jiran gado. Idanun da suke
kansa sun yawaita don haka ya dinga jin matsanancin fa’duwar gaba, mutane kuwa
kallonsa suke sosai suna yaba kyawu da zatinsa mai bayyana cikar mazantakar d’a
namiji. Mata da yawa furta Ma sha Allah suke, sun san daga yau ba za su sake
samun damar yi masa wannan kallon na k’urilla ba. Haka al’ada garin take ga duk
wanda za’a wa na’din sarauta mai jiran gado sai ya bi ta cikin jama’a sun masa
kallon tsaf don duk sanda ya zama sarki ba su da ikon sake ganinsa sai dai a
cikin rawani. Sai da ya gama zaga jama’ar tas ya gama gaishe da manya sannan ya
isa inda aka tanadar masa don ya zauna. Daga inda yake yana hango fuskar
Maimartaba da take bayyana tsananin farin cikin da yake ciki. A zuciyarsa ya ce
“Don kai ka’dai zan amince da wannan sarautar Bahbah, banda haka da nemata za’a
yi a rasa.”
Lokaci guda aka turo amintattun fAdawa biyu suka isa da shi
gaban takawa. Inda anan ne za’a na’da masa rawani a kuma ba shi Sandar Yareema
mai jiran gado. A gaban manyan Fada ya gurfana yana kai gaisuwa. Wasu da dama
suka amsa cikin farin ciki yayin da fuskokin wasu yak’e kawai suke wasu kuma
bak’in cikinsu ya kasa b’oyuwa akan fuskarsu duk da k’ok’arin da suke na son
aikata hakan.
Sarkin na’din fada ya mik’e ya isa gabansa bayan ya amshi
rawani a wajen Maimartaba da ya yi dakonsa da kansa. Ya karb’a ya fara nad’a
masa ana sakin ganguna masu wak’a na furta sai ka yi. Ana na’din Gaban Murad na
wani irin matsanancin bugu zufa na keto masa ko ta ina. Addu’ar Malam Jaluzi ya
dinga karantawa a kan harshensa kafin ya samu nutsuwa a tattare da shi. Sarki
na shirin mik’a masa Sanda mai tambarin masarauta a jiki d’aya daga cikin
mutanen Fadar ya mik’e yana kallon Sarki cikin idanunsa ya ce “Ba mu amince da
na’din wanda ba a san asalinsa ba, idan ana so mu yarda sai ka sanar da mu
yarda ka samar da cikinsa da kuma Uwarsa..” Cak Sarki ya yi da sandar a
hannunsa yana kallon mutumin da ya yi maganar cikin b’acin rai ya furta “Ba ni
da wata magana bayan wacce na fa’da tuntuni kuma a shari’ance babu dalilin da
zai saka na kasa na’da shi a matsayin Magaji na.” Wani ma ya mik’e yana cin
magani wanda k’anin Uba ne ga shi sarki Mukhtar ya ce “Ko da za mu bayyana wa
jama’a yarda ka samar da cikin sa?”
JIKAR NASHE.✍π½
A yi hak’uri da wannan ciwon kai ya saka ni a gaba na gode.
KUDIRAR ALLAH
21.
08033748387.
NAZEEFAH SABO NASHE.
Tuni wajen ya kaure da hayaniya jin abinda tsohon ya ce.
Sarkin Gabas kuwa wani kallon cikin ido ya bi Baffan nasa da shi, kafin ya
jijjiga kansa a hankali cikin sark’ewar murya ta cikin loud speaker ya fa’da
yarda kowa zai ji. “Ina buk’atar sani nima, kamar yarda kowa zai so sanin yarda
aka samar da cikin Murad ba mamki daga yanzu mutane su daina zargi na a
matsayin mutum banza su amince bani da hannu cikin abinda Allah ya zartar,
fa’dar taka na nufin k’arshen duk wani azzalimi ya zo don na rantse da Allah a
yau a yanzu kuma ba sai gobe ba zan fille kan duk wanda aka samu da cin amana
da tozarta masarautar Gabas….” Hannun Baffan Gwandu ne ya fara rawa tsoro ya
bayyana k’arara a fuskarsa duk da k’ok’arinsa na son yakice haka, ashe bai sani
ba kansa yake son k’ullewa dumu dumu, burinsa tozarta Sarki shi yasa ya yi
wannan maganar amma shi da kansa ba zai ce ga ta yarda aka samar da cikin ba,
kwa’dayin bawa d’ansa Sarautar Waziri na uku shi yasa shi aikata haka, da
alk’awarin da aka masa na da zarar an samu kujerar ga shi nan yanzu ya jefa
kansa cikin zargin Sarki k’iri da muzu, don daga ganin Kallon da maimartaba
yake masa yana tuhumarsa da abubuwa da dama ba kuma ya k’yaleshi ba ne, idan
kuwa haka ne ya shiga uku, ya kuma zama dole ya nemi wa’dancan mutanen da suka
d’ora shi akan keken b’era duk da bai san su ba bai kuma san su waye ba
sakamakon basaja da suka yi a kamanninsu, muryarsu da shigarsu. Ko za’a
kasheshi a yanzu dai ko yatsansu bai sani ba, bai san kuma kalar jikinsu ba. A
yarda suka yi da shi da zarar ya fa’di wannan maganar za su mik’e su mara masa
baya da shi da wanda ya fara maganar sai dai wayam ba su ga kowa ba, abin abin
al’ajabi da almara sai ka ce wani aikin Jinnu, ko dai ma ba mutane ba ne?
Hayaniyar ta cigaba da wanzuwa a wajen taron kowa burinsa ya
san yarda aka samar da cikin Yareema Murad sarki ya ciga da kallon Baffan
Gwandu yana furta “Jama’a na saurararka kai da wanda ya fara magana.” A cikin
muryar Maimartaba suka jiyo rashin sassautawa ga duk wanda aka kama da laifin.
Baffa k’asa ya yi da kansa ta idanun mai martaba ya hango dukkan wata nagarta
da martabarsa ta zube a idanun Maimartaba yaron da suka raina aka haifeshi a
gabansu. Ya share zufar da ta fara zubo
masa a goshi hannunsa har rawa yake don tsoro da razani, Sarki kuma ya kafa ya
tsare akan dole sai ya fitar da shi da jama’arsa a duhu. Muryarsa na rawa kamar
wanda aka shak’e ya fara magana “A yi hak’uri,wallahi sharrin shai’dan ne da
ru’din duniya, wallahi nima ban san su ba su suka umarceni dana aikata haka
idan na fa’da za su tashi su mara min baya, ko fuskarsu ban sani ba balle
kamanninsu a min afuwa.” Waje ya sake kaure da hayaniya masu zagin Baffan
Gwandu na yi shi dai ya yi k’asa da kansa. Sarki kuwa ido ya kafa musu yana nazarinsu
a yanzu shi kansa burinsa sanin wancan kwamacalar ya kuma so a ce sun sani
d’in. Ya girgiza kai yana kallon fadawansa ya nuna musu su. “Ku killacesu har
zuwa sanda za su fa’di gaskiya.” Haka kuwa aka yi aka tisa k’eyarsu zuwa gidan
Yarin masarautar. Sarki ya saki ajiyar zuciya kafin ya umarci Sarkin NAD’i akan
ya cigaba da na’dawa Murad rawanin da yake yi. Surutun mutanen ya ‘dan ragu a
wajen kowa yana cigaba da al’ajabin lamarin. Gefe guda Fulani Raheena ma a
cikin tsananin mamaki take da tsoro game da ru’dani da ya haifar mata da wata
irin fa’duwar gaba, kada dai wad’ancan mutanen da itama suke zuwa mata a wata
siffa jikinsu sunk’uf duk kuma
k’wak’warka baka isa ka gano su waye ba muryarsu ma bata kama da ta wa’danda
aka sani, kada dai kamar yarda Baffa Gwandu ya ce Aljannu ne su tabbatar
Aljannun sune suke tsorata kamar yarda suke tsorata su Baffan. Ta runtse ido a
fili ta furta “Ya salam!” Tana jin wani matsanancin tsoro yana sake damalmala
zuciyatta. Allah Allah take a tashi daga taron ta je ta kira wayar da suka saba
magana da mutanen don ta tabbatar da zarginta.
Aka na’dawa Murad rawanin da ya zauna tsaf akan sa ya kuma
masa kyau sosai ya k’ara masa kwarjini da Haiba. Da gaske sarauta ta amshe shi
duk da shi yana nesanta kansa da ita da gudun fanfalak’i. Ya d’an damk’e
hannunsa kunnuwansa suna cigaba da jiyo masa maganganun mutanen masu yaba
kyawun sa da nagartarsa gefe guda kuma ta’ajjabi da mamakin yarda aka samar da
cikinsa shine yake harzik’a kwanyarsa ya dinga sakin ajiyar numfashi a hankali
kamar ko wani lokaci da idan tunanin ya masa yawa ya kan haifar masa da ciwon
kai mai tsananin gaske yanzun ma hakan ce ta faru ya runtse idonsa yana jan
Hasbunallah a hankali. Lura da kamar hayaniyar tana damunsa ne yasa Maimartaba
bawa amintattun fadawansa damar matsar da shi zuwa cikin sashensa ko ya samu
nutsuwa. Haka kuwa aka yi Murad ya ji da’din hakan da suka masa ya mik’e da
d’an hanzari Fadawa Suna fa’din gyara kintsi suka yi saurin shigar da shi cikin
motarsa da kuma sauri aka ja motar saboda yarda jama’a suka fara dafifi a wajen
motar da burin d’aukar sa a hoto. Murad yana jin sanyin a’cn motar ya lumshe
idonsa a hankali yana sakin ajiyar zuciya kafin ya cigaba da tunanin da yake.
Tafiya mik’akkiya aka yi kafin isa Babban sashensa da aka masa gini na Zamani
mai kyawun gaske inda Sarkin yake so ya masa aure ya kuma tare a wajen saboda
hayaniyar da masarautar ta d’auka yasa Sarkin ya ce a kawo shi nan d’in, kuma
daf yake da Babban clinic d’in da yake cikin masarautar.
Ya bi wajen da kallo haka kawai sai ya samu kansa da son
zuwa yaga halin da matar da suka buge take ciki, duk da shi mutum ne da bai
damu da sabgar mutane ba sai ya ji lamarin Matar ya tsaya masa a rai yana kuma
don yaga halin da take ciki. Fadawan ya kalla a hankali yana furta “Let check
on her.” Suka bi shi da kallo ba tare da sun san me yake nufi ba, tunda ba da
su aka bugeta ba balle su san wa yake magana a kai. Idanu suka zuba masa kafin
suka ya wuce da d’an hanzari cikin irin tafiyar sojoji. Suma bin sa suka yi da
sauri tunda ba su san wacece ba. A reception d’in asibitin nurses suka dinga
kawo masa gaisuwa cike da mamakin wanzuwarsa a asibitin don haka sabon abu ne a
wajen su da basu tab’a gani ba musamman yau da suka san babbar rana ce a
wajensa. Ya tsaya daga jikin Babban counter d’in da ke wajen yana kallonsu
d’aya bayan d’aya cikin jin haushin kallon da suke masa ya ce “Where is she?
Hope she is alive.” Ba tare da gane abinda yake nufi ba suka bi shi da kallo su
ba abin su ce masa Who ba? Ba su isa ba ba su da wannan ikon. Cikin takaici ya
sake zuba musu manyan idanunsa yana fa’din “Can’t talk?” Rusunar da kai
receptionist d’in ta yi tana furta “Am sorry Sir, but I didn’t understand what
you mean.” Sai sannan ya san laifinsa ne da bai sanar da su wacce yake nufi ba,
ya ‘dan murza goshinsa yana furta “The old woman da ta samu accident d’azu.”
Sai sannan suka gane abinda yake nufi. Suka d’aga kai Suna fa’din “Yes she is
alive, Allah ya kiyaye ta dai samu rauni a kanta apart from that ba wani abu.” Ya
saki ajiyar zuciya har zai fita sai kuma ya juya yana furta “Bari na ganta.” Ba
su yi wata wata ba suka tafi da sauri don nuna masa d’akin da aka kwantar da
ita. Yana tura d’akin idanunsa da na Najwa suka sark’e waje d’aya, a fili ya ja
tsaki yana furta “A witch.” Ya d’auke kansa da sauri yana kallon Nene da ke
kwance idanunta a rufe kamar mai Barci sai dai ba barcin take ba, tsabar tunani
ne ya cunkushe mata zuciya na rashin tudun dafawa idan har ta bayyana kanta a
matsayin uwarsu Murad ta ya zata sanar da mutane yarda cikin ya shiga alhali
ita kanta bata sani ba. Masifaffen k’amshin da ta ji ne yasa ta bu’de idanunta
da sauri sai kuwa idanun suka sark’e da na Murad da yake tsaye yana kallonta.
Wata irin fa’duwar gaba suka shiga duka su biyun suka kuma kasa d’auke idanunsu
daga kan juna da suke wa junansu kallon k’urilla. Murad bai san dalilin kallon
ba ita kuwa Nene ta sani, cikin wani irin yanayi take kallonsa k’walla na neman zuba daga idanunta,
ba na komai ba sai don tsananin farin cikin ganin Murad a gabanta, cikakken
mutum managarci mai nutsuwa da duka suka bayyana akan fuskarsa, da gaske Murad
ne don ko ka’dan babu banbanci a kamanninsu da Jaheed, illa Murad da ya fishi
yawan saje da cikar gashin gira da na ido da suke kwance sun wa idanunsa rumfa,
ita ka’dai ce da take matsayin Uwa zata gane wannan banbancin, wani irin
maganad’isu ya dinga jan hannunta ji take kamar ta janyo Murad ‘din ta saka shi
a jikinta ta sanar da shi itace Mahaifiyar da ta reneshi a cikinta cikin duhu
war d’aki, itace mAhaifiyar da ta yi nak’udarsa ta haifeshi, sai dai me idan ta
sanar da shi hakan wace amsa zata ba shi idan ya tambayeta ta yaya ta samu
cikinsa da kuma dalilin da yasa ta tafi ta bar shi? Bata da amsa amma haka nan
ta ji zuciyarta ta yi rauni kuka ya kufce mata kukan da tun lokacin da abubuwan
suka faru bata samu ta yi shi ba sai yanzu da taga Murad a gabanta cikakken
namiji, hannu na rawa leb’enta na rawa cikin wata irin murya ta furta
“MURAAAAAAD!”
JIKAR NASHE✍π½
Kin siya kuwa ko har yanzu? Book 1 ya kusa k’arewa idan kina
son Book 2 ki biya 500 kacal ta wannan asusun 2118666253 UBA. Kai tsaye sai ki
tura shaidar biya ta wannan numberr 08033748387. Kada a yi babu ke yanzu aka
fara badak’alar da dukkan da’din littafin na gaba. Baa fara komai ba akwai
rantsatstsiyar soyayya mai gigita kwanya bayan zafaffiyar k’iyayya. Ki siya ki
karanta ina tabbatar miki ba zaki yi nadama ba.
KUDIRAR ALLAH
22.
08033748387.
NAZEEFAH SABO NASHE ✍π½
________________
Sunan da ta ambata na Murad sai ya tsaya mata a mak’oshi
sakamakon dakushewar da muryarta ta yi, sai kuma a lokacin ta ankara da wautar
da ta so tafkawa. Da sauri ta runtse idonta bugun zuciyarta na sake hauhawa
kamar yarda na Murad yake yi ba tare da ya san na menene ba. Bai ji sautin
sunan ba don haka bai san ta kira shi ba ba ma shiba duk wanda yake d’akin bai
jin ba illa Najwa da ta gane abinda Nenen ta furta idanu ta fito da su waje
tana fatan Allah yasa Murad d’in bai fahimci abinda Nenen take nufi da bata san
me za su ce su wanke kan su ba. Addu’arta ta karb’u ganin yarda fuskar Murad
d’in ta nuna bai san abinda Nenen ta ce ba. Ta saki ajiyar zuciya mai k’arfin
gaske wanda ya ja hankalin jama’ar wajen kanta. Da sauri ta gyara zamanta tana
k’ok’arin daidaita hak’oran roban da suke bakinta wanda ta kasa sabawa da su
har yanzu dalilin girman da suka yi wa bakinta ga gatson dole da suka sakata ga
bak’in da aka shafa mata mai kamar shuni don haka ta yi muni ba na wasa ba dole
Murad ya tsani kallonta. Idanu ya zuba mata jin ajiyar zuciyar da ta yi mai
nauyin gaske harara ya zuba mata ka’dan kafin ya mayar da kallonsa kan Nene
yana karantar yanayinta ya d’an furzar da hucin numfashi yana furta “Dafatan
dai ba matsala?” Nene ta lumshe idonta tana jin d’igar hawaye akan k’uncinta
kasa amsa masa ta yi da bakinta don ta san idan ta ce eeh ma k’arya take don
haka ta d’aga kai. Ya d’an yi luuu da idanunsa alamun gajiya na sake bayyana a
cikin idanun nasa ya d’aga mata hannu yana furta “Allah ya bada lafiya.” Sannan
ya fara tafiya da baya da baya still idanunsa cikin na Nene da ta kasa janye
idanun akan sa. Murmushi kawai ya sakar mata ya juya da sauri don ficewa daga
d’akin bayan ya sake furta Witch! Ganin kallon da ta bi shi da shi, Allah sarki
Najwa bai san ita ba kallon komai take masa sai na mamakin yarda yake kama da
Jaheed.
Karo Suka kusa yi da Mammansa Fulani Saddika data shigo
d’akin ita da fadawanta da ma’aikatan jinyar da suka rakota. Ko ba’a fa’da ba
dama ta san yana asibitin tun shigowarta jin yarda k’amshinsa ya kara’de asibitin, mamaki ya kamata ganin Murad da
kansa yau ya zo dubiya asibitin ta bi shi da kallo. “Kai kuma fa? Me ka zo yi
ko ciwon kan ne ya matsa maka?” Duk da ta san da wuya yazo asibitin ganin
likita saboda yana da special Doctor d’insa da yake gani a Nigeria in dai ciwon
bai yi zafi ba, idan kuwa ya yi zafi ya gwammace ya tsallaka k’asar masu
jajayen kunnuwa a duba shi tunda dama a can ya fi kauri. Lumshe idanunsa ya yi
kafin ya girgiza kai a hankali yarda ita ka’dai zata ji ya ce “Na zo ne kawai
na duba patient d’in ki.” Mamma ta ware ido tana furta “Are you sure?” Ya d’aga
kai yana murmushi kafin ya fice da sassarfa yana d’aga mata hannu. Mamma ta bi
bayansa da kallo tana mamakin abinda ya ce Lallai patient d’inta ta ci a kirata
mai sa’a tunda har Murad ya tako ya zo dubata. Ta jinjina lamarin kafin ta saki
ajiyar zuciya itama ta shiga d’akin don duba patient d’in. Idanunta a lumshe ta
tarar da ita duk ba barci take ba sai son bawa zuciya nutsuwa daga zuzzurfan
tunanin da yake damalmala kwanyarta. Sallamar da ta ji ne yasa ta ta bu’de
idanunta tana kallon Fulani Saddik’a gabanta ya fa’di don ko a maye take
kamannin Fulanin ba zai b’ace mata ba, Mace Adala kenan mai nagartattun halaye
da ake kira ta fisu kaf ta fi matan sarki. Da ace bata b’atar da nata kamannin
ba ta hanyar Basaja da tsaf Fulanin zata shaida ta don sun yi zaman mutunci da
ita kusan itace nagartacciyar baiwarta wacce ta amince ta san duk wani
sirrinta. Sai dai a yanzu kam ba zata shaida ta ba ba don nata kamannin sun
canja ba sai don canjin da aka musu na dole don gudun kada a ganesu. Fulani ta
zuba mata ido kafin murya da sanyi ta ce “Sannu da jiki baiwar Allah, dafatan
dai kina samun sauk’i.” Nene ta d’aga kai tana k’ak’alo nata murmushin da kai
tsaye za’a kira na dole. “Yi magana mana baiwar Allah ba dai matsala ko?” Murya
a sanyaye ta furta “Alhamdulillah na samu sauk’i.” Fulani ta saki murmushi tana
furta “Ma sha Allah, haka ake so. Sai magana ta gaba a ina za’a samu danginku a
sanar musu don naga kamar k’aramar y’ar taki ba zata iya jinyarki ba, tunda an
ce jininki ya hau kina buk’atar hutu sosai.” Najwa gabanta ne ya fa’di su ka
ha’da ido da Nene da itama take kallonta
da sauri ta d’an girgizawa Nene kai. Murya a sanyaye Nene ta ce “Garin mu da
nisa Hajiya, Kuma ko Anje can d’in ba mu da kowa bamu da wanda zai iya jinyata
ki bar ni da yarinyata zata iya komai.” Fulani ta juya tana kallon Najwa kafin
ta jijjiga kai ta ce “Ya sunanki?” Da sauri Najee ta furta “Sunana Ladidi.”
Fulani ta ‘d’aga kai tana furta “Ladidi Ai ba sunan gaskiya bane, sunanki na
gaskiya nake son ji.” Najwa ta ja ajiyar numfashi kafin ta ce “Hadiza nake.”
Fulani ta d’aga kai tana furta “Ai kuwa sunanki yafi k’arfin furtawa ga duk
wani mazaunin Fadar nan sai dai mu dinga kiranki Ladidin. Sabida sunan mai
Babban d’aki ne Mahaifiyar Sarkin Gabas.” Najwa ta saki murmushi kawai wanda
gatsonta ya sake bayyana. A zuciyar Fulani ta jaddada munin Najwa ga bak’i
kamar mutanen South Africa. “Shikkenan ko mu zamu tafi, zan saka a dinga kawo
muku abinci idan an kawo muku abincin sai ku dinga fa’da musu idan kuna son
wani abu kafin a sallameku mu ga abinda Allah zai yi.” Nene ta d’aga kai tana
furta “Mun gode Allah ya k’ara girma da d’aukaka ya tsare gabanki da bayanki.”
“Ameen” Fulani ta fa’da a hankali ta juya tana kallon Najwa ta ce “Ladidi Zan
aiko da kaya don Allah ki cire na jikinki ki yi wanka ko kya yi kyan gani.”
Najwa ta d’aga kai tana sakin murmushin da ko ka’dan bai mata kyau ba, sai ma
muni da ya k’ara mata. Sai da suka fita sannan ta kalli Nene Suka saki dariya a
tare. Najwa ta ce “Wai Nenne muni na yi ne sosai?” Nene dariya ta yi sosai ta
ce “Ai Najwa don baki ga yarda kika koma ba ki je ki ga mudubi a toilet.” Da
sauri Najwa ta mik’e ta shiga toilet d’in. Ware ido ta yi kafin ta saki dariya
ganin yarda fuskarta ta yi dole duk wanda ya kalleta ya ji bata burge shi ba ashe
shi yasa Murad ya ce mata Witch. Ta ha’diye yawu da k’yar saboda haushin Sunan
da ya kirata da shi sai yanzu ta tuna ma’anar Witch Mayya! Haushin Murad ta ji
sosai a ranta kafin ta fito daga toilet d’in tana sakin dariya tace “Cab Nene
haka na koma Blacky!” Nene ta saki murmushi tana furta “Kamar ba Kyakykyawar
Najee d’in Jaheed ba.” Kunya ce ta kama Najee tana hasasota matsayin matar
Jaheed sai kuma nan da nan kishi da jin haushin matarsa ya rufeta, ko sai
yaushe za’a kirata da Matar Jaheed? Ta tambayi kanta, sam bata san maganar ta
fito fili ba Nene ta saki dariya tana furta “In sha Allah shekara I war haka
kin amsa wannan sunan haka za’a yi auren ko baki gama makaranta ba.” Da sauri
Najwa ta rufe fuskarta fahimtar da ta yi Nene ta ji zancen da take da
zuciyarta. Nene ta saki murmushi kawai tana jin a ranta kamar itama ta janyo
wannan lokacin tana burin ha’da jini da Baffa da Umma salihar mace mai
nagartuwar halayya.
_____________
Cikin toilet d’in take tsaye tana aman da ya k’i tsaya mata,
ya zame mata jiki duk safiya sai ta yi shi kamar masifa ga shi kore sharr. Jiri
ne yake d’iban ta da k’yar ta fara k’ok’arin dafa bango don fitowa daga
bathroom d’in. Sai ga Umman Najee nan ta shigo da d’an hanzari idanunta akan
Najma da ta wani d’ashe ta yi fari tas ga rama ta yi ba ta wasa ba. Bata mata
magana ba ta kamata suka fita zuwa d’aki, a bakin gadon ta zaunar da ita tana
furta “Yau kam duk kafiyarki sai mun je asibiti, wannan ciwon ya isheni ina
dalili? Kin ga yarda kika dawo kuwa kamar mai yaron ciki?” Daga ita har Umma
sai da zuciyarsu ta buga da k’arfin gaske suka zubawa juna ido kowa da tunanin
da yake cin ransa. Umma nata fargabar kada dai magana Najma ta d’auko musu, don
ita bata san Jaheed ya kusanceta ba, ita kuwa Najma addu’a take dafatan Allah
yasa cikin Jaheed ne a jikin ta ko wannan ya yi dalilin da zai saka ya dawo ya
saurareta. Ido Umma ta zuba mata duk da ba likita bace ita amma yawan shekarun
da ta yi tana rainon ciki da haifeshi ya ci ace ta fuskanci ciki. Ta sake
ajiyar zuciya kafin ta mik’e ta zaro hijab tana mik’a mata “Tashi mu tafi tun
yanzu.” Najma ba yarda ta iya ta mik’e jikinta ba k’wari ta bi bayan Umman suka
fita falo Umman na rik’e da hannunta zuciyarta na bugun jin tsoron tabbatuwar
tunaninta.
____
Fulani Raheena kuwa tun bayan komawarta gida zuciyarta ta
kasa nutsuwa da maganganun Baffan Gwandu da suke hasasho mata fallasuwar nata
sirrin data tone ta zuba shi a cikin k’asa sai dai a yau tana tunanin akwai
wanda ya kusa tono shi. Ya aka yi matsalar da take ciki ta yi kamanceceniya da
ta Baffan Gwandu? Su waye wa’dannan mutanen da suke wasa da hankalinsu a da ta
zata nata hankalin ita ka’dai ake watangaririya da shi ashe har da na jama’a da
yawa a cikin a masarautar nan? Ya zama dole ta gano su waye idan ma Jinnu ne su
dole su bayyana don wannan karan komai zai faru sai dai ya faru akan tonuwar
b’aragurbin k’wan da zai addabi jama’ar da ke ciki da wajen masarautar Gabas.
Bata da hannu a cikin samuwar cikin Murad tata matsalar ta daban ce ta kuma zarce matsalar da Sarki yake ciki ta
samuwar cikin Murad da rashin sanin wacece mahaifiyarsa duka wannan mai sauk’i
ce akan tata. Ta zauna a gefen gado dab’as bayan ta lalubo sirrintaccen layin
wayarta ta saka a wata k’aramar waya ta daban. Bugu biyu numberr ya shiga kamar
yarda ta tsammata waccan kaurararriyar muryarce ta yi magana bayan sakin
dariyar da ta kusa saka Fulani yin fitsari a wando. “Tunanin ki ya baki daidai
mowar sarki, b’aragurbin k’wanki ya kusa fashewa idan kuma ya fashe zai addabi
masarautar gabas, hanya d’aya ce ki gaggauta saka Murad ya auri y’arki kamar
yarda muka gaya miki itace zata mana ajalinsa shi kuma Mukhtar ki bar mu da shi
ya kusa barin duniya ma gaba d’aya.” “Me yasa zaku ce sai ya auri k’anwata
alhali kun san sarai a matsayin y kuma ina son na san ko ku su waye? Me yasa
kuka saka ni a cikin wancan gagarumar matsalar?” “Saboda kin cancanci shiga
matsalar sakamakon zalamarki da kika nuna na son haihuwar Magajin sarki wannan
shine hujja mun baki abinda kike so kema ya zama dole ki mana abinda muke so
daga gobe muke so ki fara aiwatar da k’udirinki na ha’da Murad aure da
k’anwarki sanin ko mu su waye Kuma ba zai amfaneki da komai ba, idan lokacin
sani ya yi da kan ki zaki sani.” Daga haka suka kashe wayar. Fulani ta bi wayar
da kallo kafin ta saki ajiyar zuciya hawayen nadama na sauka a idanunta da
alama dai ta kusa tashi a tutar babu idan kuwa haka ne ya zama dole ta saka
Murad ya auri K’anwarta in dai hakan shi zai saka ta samu cikar burinta.
———————-
Nene ta mik’e tana kallon Najwa har zata ambaci sunanta sai
kuma ta yi murmushi ta furta “Ladidi burin mu ya cika na shigowa masarautar
Gabas abu guda ya rage mana samun hanyar da zamu shiga ainahin cikin masarautar
don samo wancan rufaffen sirrin, ina jin tsoro Najwa bana son a sheganta min
y’ay’a banda haka da tuni na bayyana kai na a matsayin Mahaifiyar Muraad…….”
Turo k’ofar da aka yi da k’arfi ne yasa Nene yin shiru da
zancen tana d’aga idonta tana kallon mai tahowar k’amshin turaren sa yana dukar
hancinsu idanunsa ya zube a kan Nene fuskarsa na nuna alamun duk ya gama jin
abinda suka ce, hantar cikin Najwa ta juya har kana iya juyo k’ararta ita kuwa
Nene suman zaune ta yi tana k’ok’arin saita numfashinta da ya kusa d’aukewa……..
ya cigaba da shiga cikin d’akin cikin takun isa Fulani Saddik’a na bayansa……..
Ku min afuwa ciwon kai ne ya tasa ni gaba kwana biyu amma
dai da sauk’i sosai Alhamdulillah
KUDIRAR ALLAH.
23.
08033748387.
NAZEEFAH SABO NASHE.✍π½
_________________
Alhamdulillah na ji sauk’i ina godiya Anty Hadiza Sodangi
abisa kulawarki gareni, na yi addu’a kuma an dace, Rabbi ya saka miki da
mafificiyar Aljanna ya raya miki zuri’a akan tafarkin shiriya.
______________
Nene wani irin ha’diyar yawu take wanda bata shiryawa
zuwansa a wannan lokacin ba, zufa ta gama jik’a ta ta ko ina duk da sanyin a.c
d’in da take cikin d’akin. Kallo d’aya zaka musu ka tabbatar da rashin gaskiya
a tare da su musamman Najwa da ta kasa kallonsu. Fulani Saddik’a wani murmushi
ta saki bayan ta kalli Murad ta tabbatar shi bai ji abinda ta ji ba saboda
airpods d’in da ke kunnensa yana amsa waya. Ta juya tana kallon Nene kallo mai
bayyana tuhuma sai dai ta danne abin a ranta ta ce “Ya jikin naki?” Nene da ta
kusa sakin fitsari a wando ta d’aga mata kai cikin raunin murya ta ce
“Alhamdulillah” Fulanin ta ce “Ma sha Allah Ai daga gani jiki ya yi kyau shi
yasa ma likitocin suka sanar min sun baki sallama, to sakamakon maganar da na
ji kuna yi jiya na rashin wajen zama sai na yanke shawarar tafiya da ku can
wajena kafin a samu mahallin saka ku.” Murad ya bu’de ido yana kallonta
“Wajenki Mamma?” Ta d’aga kai cike da gamsarwa ta ce “Ba su da inda ya kamata
su zauna fiye da wajen nawa, zan saka a cigita gida idan komai ya lafa sai su
koma can a yanzu dai kam can ne ya kama ce su.” Shiru ya yi banda yana tausayin
Uwar ba yarda za’a yi ya yarda Mamma ta d’auki wannan mummunar yarinyar ta kai
gidanta, amma haka kawai yake da feeling na tausayi akan Babarta don haka sai
ya share ya d’an tab’e baki ha’de da ware hannu yana furta “As you wished Mamma
Allah ya bada lada.” Daga haka ya juya ya bar d’akin dama sam bai san me yasa
ya biyo Mamman ma. Suka bi bayansa da kallo har Mamman kafin ta juyo da kanta
tana kallon Nene irin kallon k’urilla mai cike da son tabbatar da zarginta, sai
dai a ilimi irin nata ta yi k’ok’ari k’warai da gaske ta b’oye mamakin jin
maganar ta nuna musu gaba d’aya ma bata ji abinda suka ce ba. “Ku taso mu tafi
amma bana buk’atar komai kawai ku taho zallar ku ka’dai nake buk’ata.” Nene ta
saki ajiyar zuciya tana mik’ewa jikinta cike da kasala zuciyarta na sake sanar
da ita tabbas Fulani ta ji maganar nan kawai sharewa ta yi ta nuna bata ji, sai
itama ta daure kawai ta ha’diye nata k’udirin. Suka bi Fulanin inda hadimanta
suke bakin k’ofa suna jiranta.
A sashen Fulanin motoci biyun Suka yi Parkin Fulani ta fita
kafin ta umarcesu su ma su fito. Jikinsu na rawa suka fito Nene tana bin wajen
da kallo, wajen dai fulanin ne dai da ta sani sai dai an yi renovating d’insa
ya zama wani irin gini mai kyawun gaske. Ta dinga bin wajen da kallo tana
tunano zamanin baya Lokacin k’uruciyarta kafin k’addara mai girma ta yi facali
da wancan farin cikin da take ciki. Hanyar sassan bayi take bi da ido zuciyarsa
na bugu da k’arfi tsoro take ji sosai bata son a ce ta rasa iyayenta kamar
yarda zuciyarta take hasasho mata. Fulani Saddik’a ta juyo idanunta cikin na
Nene tana sake nazarin fuskarta duk zarginta yana son tabbata daga ganin
yanayin idanuwan Nenen ta san abinda duk take tunani zai iya zama gaskiya. Bata
mata magana ba illa wucewa da ta yi tana nawa hadimanta umarnin su kai su Nenen
wani keb’antaccen d’aki inda take ajiye manyan bak’in da bata son su yi nisa da
ita. A sashenta d’akin yake cikin babban parlourn ta. Hadimanta suka bita da
kallo suna mamakin abinda ta ce don ko su suna iya k’irga sau nawa k’afafunsu
suka shiga cikin d’akin balle a kai wa’dannan yamutsatstsun mutanen da ko kyan
kama ba su da ita. Sai dai basu da hurumi ba kuma su isa su tambayi Fulanin
dalilinta ba don haka suka ja baki suka shiru tare da bin umarnin Fulanin kai
tsaye, bayan sun wurgi su Nenen da wani kallon banza na raini. Nene ta saki
murmushi kawai don ta san hassada ce irin ta d’an Adam da ba ya iya b’oyewa.
Babban d’aki ne mai girman gaske mai d’auke da wani
faffa’dan gado da ya sha filillika irin dai shimfi’da gidan sarauta. Sai zabga
wani irin k’amshi yake na turaren wuta da na Humrar d’aki. K’asansa malale yake
da carpet mai taushin gaske. “Nan ne d’akin sai a kiyaye banda k’auyanci, ni
Wallahi ban san me ya sa Fulani tayi shawarar kawo ku nan ba.” “Me yasa ba zaki
je ki tambayi Fulanin dalili ba?” Najwa ta fa’da fuskarta a ha’de cikin jin
haushi da tsanar halayyar wasu mutanen masu wulak’anta mutum tun basu san irin
girman da Allah ya masa ba, ji fa a rashin sani bata san Nene b’ace Uwar Murad
amma ji abinda take gaya mata. “Kada ki min rashin kunya yarinya ji da munin da
Allah ya baki da Uban hak’oranki.” Ta fa’da tana hararar Najwan. Najwa ta bu’de
baki zata yi magana Nene ta dakatar da ita. “Barta Najwa akwai ranar mayar da
magana ba yanzu ba.” Sai da ta harari Nenen sannan suka yi tsaki suka fita
bak’in cikinsu guda basa son Fulanin ta kawo wanda zai maye gurbinsu tunda sun
saba yi mata almundahana da hainci akan duk wasu abubuwanta. Suna fita Najwa ta
ce “Amma Nene me yasa kika dakatar da ni baki bar ni na ci Ubansu ba.” Nene ta
saki murmushi tana furta ba yanzu ba Najee akwai lokaci.” Suka mayar da kansu
kan sake kallon d’akin duk da arziki ba bak’on su bane amma d’akin nan ya tafi
da duk hankalinsu. Najee ta ‘Dane gadon har da tsalle tana murmushi ta ce “Na
d’ane gadon Uwar Sarkin Gabas, Nene Allah ya nuna mana ranar da zasu san ke ce
Mahaifiyar Sarkin Gabas daga kan wad’annan barorin zan fara rashin mutunci,
Nene har shi fa Murad d’in ba zan k’yaleshi ba sai na rama kallon hadarin kajin
da yake min.” Nene murmushi kawai ta saki kafin ta furta “Ai dole Najeen Nene
ni kaina sai na tayaki rama wa don ina kallon idanunsa da hararar da yake zabga
miki, don yaga an canja miki kamanni Bai san Najee na ko larabawa albarka ba
wajen kyau sai dai a nuna mata hasken fata don ko gashi ba su fiki ba, tun
yanzu ma kenan ina ga nan gaba mak’erin y’an mata ya k’ere min ke za’a ga
cikakkiyar mace mai cikakkiyar sura ta nunawa a jarida.” Najee murmushi ta saki
tana sunkuyar da kai. Kafin ta ce “Da gaske Nene ni kyakykyawa ce? Amma ana
cewa su Yaya Nasma sun fi ni kyau.” Nene ta girgiza kai “Ko ka’dan sun dai fi
ki hasken fata amma zallar kyau da dirin jiki Ai Najee na ba baya bace•” farin
ciki ya lullub’e Najwa kafin ta mik’e ta shiga toilet don yin wanka sai kuma
gata ta fito a guje Nene ta kalleta tace “Lafiya?” A hankali don kada kowa ya
ji ta ce “Nene idan na yi wankan abinda zan shafa kamar fa mun bar shi a
asibiti.” Nene ta saka hannu a aljihunta ta zaro robar mai d’auke da bak’in
abin ta mik’a mata “Ban manta ba Najee, ta ya zan manta da abinda shine rufin
asirin mu.”
Suka saka dariya gaba d’aya.
Najee ta ce “Wallahi Nene d’azu na tsorata na fa zata Sun ji
abinda muke fa’da.” Nene ta saki murmushi kawai ba tare da ta ce komai ba.
Najee ta sake cewa “Yanzu da sun je abinda muka ce me za mu ce da su?” “Ba
abinda za ku ce sai dai Zan yi murna sosai idan har ya tabbata hasashen da nake
haka yake.” Suka tsinkayi muryarta daga sama tana shigowa cikin k’asaitacciyar
shigar da take bayyana kasancewarta Fulanin Sarki ta yi kyau sosai kamar ba
yanzu suka rabu da ita ba har ta sake fesa wani wankan sai zabga k’amshi take.
Fuskarta d’auke da murmushi ta shigo cikin taku d’aid’aya. Ita ka’dai ce ba
hadiman nata, hannunta janye da wata babbar trolley. Sak suka yi suna kallonta
fusakrsu d’auke da tsoro da razani har ma da firgita gaba d’aya. Murmushin bai
bar saman fuskarta ba ta samu waje daf da Nene a bakin gadon ta zauna. “Tun
asibiti na ji duk abinda kuke fa’da.” Ta sake tsunduma su cikin mamaki “Mafarki
na ya tabbatar na bayyanuwar Mahaifiyar Murad burin da na da’de ina son cika
shi a rayuwata sai ga shi yazo min a lokacin da ban tsammata ba, wata zuciyar
na ce min k’arya kuke amma wata zuciyar na k’arfafa ni akan tabbas ke d’in ke
ce Mahaifiyar Murad da ta d’au cikinsa ta kuma haife shi.” Ta fa’da tana nuna
Nene da ta yi mutuwar zaune don yanzu lamarin ya zarce suman zaune gaba d’aya
bata fahimtar komai, razanar da zuciyarta take ciki ta zarce dukkan tunanin mai
karatu, bata san a wata fuska Fulani zata dubeta ba, shin zata taimaketa ne ko
kuwa itama da nata burin? Idan har taimakonta zata yi me yasa tun a lokacin
bata sanar da Murad abinda kunnuwanta suka jiye mata ba? Me yasa ta zab’i ta
b’oye masa? Alhali abin murna ne da farin ciki yau a ce yaga mahaifiyarsa?
“Na san zaki yi mamakin dalilin da yasa na b’oyewa Murad
kasantuwarki mahaifiyarsa, Ina da nawa Burin da kuma shara’din da sai kin min
alk’awarin zaki cika shi sannan zan taimaka miki cika naki burin, kafin nan ina
so ku yi wanka ku ci abinci ku huta sosai zan zo mu yi magana, idan kin fahimci
ki d’ora kan ki akan turbar zaman lafiya, rashin fahimta ta kuwa yana nufin
abubuwa da dama…” Daga haka ta mik’e har a lokacin dai idanunta akan Nene tana
sakar mata murmushin da Nenen ta kasa fassara shi, bata san a matsayin da zata
ajiye k’ayataccen murmushin nata ba, Me fulani take nufi? Shine tambayar da ta
cika zuciyarta har ta hanata katab’us tana kallo Fulanin ta fice daga d’akin
bayan ta d’aga mata hannu tana furta “Na baku Awanni hu’du zan dawo, kafin nan
ina son na jaddada miki bana son k’arya a duk zancen da zaki gaya min, sannan
kuma bana son mutum mai sab’a alk’awari idan na sameki da d’aya daga cikin
wa’dannan akwai hukunci mai tsananin gaske ciki kuwa har da b’atar da ke daga
sararin duniyar nan……..” Daga haka ta fice da sauri bayan ta ja musu k’ofar da
k’arfin gaske. Bugun k’ofar ya yi daidai da bugun zuciyar Nene da k’arfin
gaske. Ta dafe wajen tana jan Hasbunallah a hankali, Ba abinda ta fahimta a
zancen fulanin da ya zarce itama akwai nata b’oyayyen k’udirin… Ta kalli Najee
da take tsaye itama kamar statue ta kafawa Nenen ido cike da nata tsoron da
fargabar. “Zama bai gan mu ba Najee na lura itama da tata manufar ya zama dole
mu bar gidan nan a yau d’in nan kafin komai ma ya faru.” Najee ta ware ido ita
da kanta ta amince da abinda Nenen ta ce don haka ta fasa shiga wankan da ta yi
niyya suka fara tunanin ta hanyar da zasu bi su tsere daga gidan nan ba tare da
Fulani ta gan su ba. “Ki lek’a Parlour idan kin ga wa’dannan marasa mutuncin
bayin ki kira min su.” Najee ta d’aga kai tana lek’a parlourn cikin sa’a kuwa
sai ta gansu. Murya k’asa k’asa ta ce su je in ji Nene don Allah. Da dai kamar
ba za su je ba, sai suka tuna mahimmancin su a wajen Fulani don haka suka bi
bayanta. A tsaye suka ga Nenen tana ganinsu ta saki ajiyar zuciya. “Yauwa don
Allah taimako zaku mana, ku nuna mana hanyar da zata fitar da mu mu kan mu bama
son zaman gidan nan.” Kallon kallo Suka shiga yi wa juna kafin su saki murmushi
su girgiza kai “Fulani ta ce ko Parlour kada a bar ku ku fita har sai idan ita
ta bada izini.” Nene da Najee suka zaro ido…..
Mhmmmmmmn! Baki biya ba ko har yanzu? Book one ya kusa zuwa
k’arshe ki biya d’ari biyar kacal don samun kashi na biyu. Tura ta asusu kamar
haka 2118666253 UBA sai ki tura shaidar biya ta number kamar haka 08033748387.
Gundarin zak’in labarin cike da zazzafar k’iyayya da soyayya suna gaba. π₯°
JIKAR NASHE✍π½
KUDIRAR ALLAH
24.
08033748387.
NAZEEFAH SABO NASHE.
______________
Fargabar Nene ta sake k’aruwa jin abinda Hadiman Suka furta,
da alama kuma ko mai za su ce musu ba zasu bar su su fita ba, umarnin
mahaifiyarsu za su bi. Don haka ma bata rok’esu ba ta ja hannun Najwa kawai
suka zauna suna kallo Hadiman Suka fita suna dariya k’asa k’asa, da alama sun
hango mugunta Fulanin ta shirya musu. Najwa ta kalli Nene tana sakin ajiyar
zuciya ta furta “Mun ga ta kan mu Nene wai me matar nan take shirya mana ne?”
“Alheri In sha Allah.” Nene ta furta duk da zuciyarta tana taraddadi akan amsar
da ta bawa Najeen. Tsawon sa’oi suna zaune a haka suka daure suka yi wanka suka
kuma samu kaya a kayan da Fulanin ta kawo musu cike da akwati duka dogayen
riguna ne free sizes don haka duk suka musu daidai. Fuskarsu suka sake shafa
mata shuni. Abinci ka’dan suka tsakura saboda fargabar da zuciyarsu take ciki.
Suna zaune shiru cikin taraddadi Fulani ta sake danno kai cikin d’akin,
k’amshin dadda’adan turarenta ne ya sa suka san itace. A hankali ta sauke
idanunta cikin nasu, wannan karan ba wannan yalwataccen murmushin, fuskarta a
ha’de take sosai kamar bata tab’a dariya ba. Ta bi kwanukan da kallo kafin ta
furta “Dafatan kun ci abinci? Don maganar da za mu yi tana buk’atar nutsuwa.”
Da sauri Nene ta d’aga kai. Ta dubi Najee da idanunta duk suka duba ru’dewa
dariya ta so saki sai dai ta yi k’ok’ari k’warai da gaske wajen ganin ta danne
dariyar. “Wannan y’ar ki ce?” Ta fa’da tana duban Fulani “Bana son amsar k’arya
a duk tambayar da zan yi.” Da sauri Nene ta girgiza kai “Ba y’ata ba ce, amma
bata banbanci da y’ar tawa.” “Amsa guda cal na fi buk’ata.” Fulani ta fa’da
tana d’aga yatsunta guda “Bana buk’atar kwan gaba kwan baya.” Nene ta saki
ajiyar zuciya kafin murya a k’asa ta ce “Ba y’ata ba ce.” “Na sani” Fulani ta
fa’da tana sake tamke fuskarta kafin ta saki wani guntun murmushi da ya tsaya
iya kan leb’enta kawai. “Sunanta Na gaskiya Najwa y’ar ga Alhaji Mai fata.”
Wannan karan gaba d’aya sai da cikinsu ya hautsina da k’arfin gaske suka dubi
Fulanin da kyau da tunanin ko ba ita bace wani Aljannun ne ya yi Basaja da
kamanninta. “Kuna mamakin yarda aka yi na sani ne?” Shiru ba amsa illa ha’diyar
yawu da suka yi da saurin gaske. “Na san komai, tun bayan da na ji abinda kuka
fa’da a asibiti na yi duk wani bincike na sirri a kan ku, aka kuma gaya min ko
ku su waye, da gaske ke ce Mahaifiyar Murad da d’an uwansa Mujaheed da kika
sake haifa bayan barinki gidan nan, abu guda da ban sani ba akan ki aka kuma
k’i sanar da ni shine ta yarda aka yi y’ay’an Sarki suka wanzu a cikin ki? Ina
so na sani shin Murad da ‘dan uwansa y’an halak ne kamar yarda aka rubuta a
takardar da aka tsinci Murad d’in da ita idan d’an halak ne ya ya aka yi ya
zama halastaccen alhali ba a d’aura muku aure da Sarki ba, baya ga haka ta yaya
kika tara da Sarki har kika samu cikinsu da mu Matan Sarkin muka kasa samu?
shine abinda nake son na sani, Bana son k’arya kin san yana daga cikin shara’di
na.” Nene ta sunkuyar da kanta tsoron Fulani ya gama mama ye dukka zuciyarta
wace irin mace ce ita? Ko dai tana aiki da Jinnu? “Yi min magana bamu da lokacin
b’atawa.” Fulani ta fa’da idanunta na kallon can wani gefe. “Wallahi ban san ta
yarda aka yi cikinsu ya shiga jikina ba abu guda na sani wata rana…….
Nan Nene ta shiga bata labarin abinda ta sani. Kafin ta gama
Fulanin ta ware ido tana kallonta cikin al’ajabi, wannan wani irin abu ne? Ta
yaya za’a fahimci wanene wanda ya shirya dukka wannan kitimurmurar? Bata nuna
komai akan fuskarta ba ta bar tashin hankalin a cikin zuciyarta ta dawo da
kallonta kan Nene tana furta. “Ni na raini Murad tun daga jarirantaka har
yanzu, ni na san halinsa ciki da bai ina son sa fiye da son da nakewa duk wata
halitta abayan k’asa ciki kuwa har da Ubansa, ina son ki min alfarma kada ki
sanar da kowa wannan zancen zan kuma tayaki bincike a hankali har zuwa sanda
zamu cimma burinmu, zaki iya tantance k’amshin turaren da kika ce shi ka’dai ne
abinda zaki shaida daga wa’dancan mutanen?” Nene ta d’aga kai ko a yanzu na ji
turaren nan ba abinda zai saka na kasa gane shi saboda sanin da na masa.”
“Alhamdulillah” Fulani ta fa’da cikin kwanciyar hankali “In sha Allah asirin
duk wanda ya ha’da wannan kitimurmurar ya kusa tonuwa. Ki kwantar da hankalinki
ba Zan cuceki ba wallahi zan daraja ki a matsayin wacce ta haifa min sanyin
idaniya a duniya zan baki dukka kulawa amma idan kin bani ha’din kai.” Nene ta
d’aga kai cike da gamsuwa Fulani ta dubi Najwa tana dariya “Ladidi ko Najwa?”
Najee itama dariyar ta yi tana furta “Duk wanda kika kira Ranki ya da’de.”
Murmushi ta yi tana dafata ta furta “Ki zauna a Ladidinki bana son kuma ki goge
wannan bak’in painting da yake fuskarki Don Allah har zuwa sanda zan cimma buri
na.” Najee ta d’aga kai tana sakin murmushi a hankali. Fulani ta mik’e tana duba
agogonta “Bari na bar ku ku huta zuciyarku ta samu nutsuwwa don na san d’azu na
tsorata ku.” Ta fa’da tana dariya suma dariyar suka yi suna tunanin yanayin da
suka kasance a d’azun don tsabar firgita da razana ba inda baya rawa a jikinsu.
________***
Su Umma da Najma kuwa suna zuwa wajen likitan bayan duk wasu
gwaje gwaje likita ya tabbatar da shigar ciki sati hu’du cif. A tsorace Umma ta
dinga kallon Najma tana furta “Ciki kuma?” Sai ta ha’diye maganarta ta mik’e
tana yi wa Doctorn godiya kafin ta ja Hannun Najma suka fice daga asibitin.
“Jaheed ya kusanceki ne?” Umma ta fa’da a motar bayan ta tayar da niyyar fara
driving. Kunya ce ta rufafwa Najma ta sunkuyar da kanta kawai tana wasa da
yatsun hannunta. Umma kallo guda ta mata ta tabbatar da amsar tambayar ta sai
ta saki ajiyar zuciya tana fa’din “Alhamdulillah! Hakan yanzu zai nuna miki
girman k’addarar Ubangiji ga Bawa, na san k’addarar cikin nan ce ta kai Jaheed
ga kusantarki ga shi nan kina d’auke da jikan mahaukaciya a cikin ki, Ya zaki
yi da wancan k’iyayyar da kike masa, tunda Allah ya nuna miki ikonsa. Shi yasa
ba’a son bawa ya zurfafa k’iyayyarsa ga abu don wata rana mak’iyi kan zama
masoyi.” Shiru Najma ta yi ba tun yanzu ba ta yi nadama
Ga duk abinda ta aikata sai dai ta san ba mai amincewa da
nadamar tata. “Sai ki masa takatsantsan da cikinsa idan mun yi waya da shi zan
sanar da shi kina da cikinsa kin san dai aurensa na nan a kan ki har sai kin
haife cikin nan sannan iddarki ta cika ko?” Najma ta ‘d’aga kai tana jin wani
sanyi a ranta jin abinda Umma ta ce wai da auren Jaheed a kanta, auren da ta
Riga ta fitar da dai da shi ta zata ya mutu murus, idan kuwa haka ne zata yi
duk mai yiwuwa ganin ta dawo da Jaheed cikin rayuwarta, zata bi duk hanyar da
zata bi ta karkato da soyayyarsa gareta. Umma ta ce “Allah ya raba lafiya.” Ta
cigaba da tuk’inta zuciyarta na ayyana mata abubuwa da da dama.
_______________
K’arfe ukun dare daidai lokacin da agogon d’akin Fulani
Raheenan ya buga. Ta bu’de idonta da ya fara mata nauyi sosai saboda
matsanancin barcin da yake cikinsu. Bata samu barci ba a daren ko ta ce ma
tsawon kwana uku da suka shige bata samun barci Saboda halin firgicin da take
ciki. K’afafunta ta ziro k’asa ta taka tattausan carpet d’in dake bakin gadon
ta. Ta mik’e tana tattare gashinta ta tufke waje guda. Tana mik’ewa ta shiga
toilet fitsari ta yi kafin ta fito ta zura wani zundumemen hijabinta da ya rufe
duk jikinta ruf ta jawo nik’ab ta saka ta rufe fuskarta da shi. Sannan ta ‘d’au
y’ae jakar ta fata ta fita a hankali yarda ba wanda zai ji motsinta. Ta k’ofar
baya ta fita kamar yarda ta saba irin wannan fitar ta sirri. Shiru wajen baka
jin kukan ko tsuntsu a wajen. Bata jin tsoro don zuciyarta ta bushe mafita
kawai take nufi da rufin asirin ta. A hankali take taku zuwa inda suka yi za su
ha’du da mutanen.
Banda duhuwa ba abinda kake gani a wajen sai hasken farin
wata da ya mama ye wajen, don hanya ce da sam mutane basa binta da rana ma
balle da daddare. Haskota aka yi da torchlight hakan ne ya nuna mata inda suke.
Ta isa wajen a hankali tana sakin ajiyar zuciya. Kamar koda wani lokaci Suna
sanye cikin bak’ak’aen kaya baka ganin komai a tatttare da su suka mik’a mata
wani k’ulli a leda “Dukka bayani yana ciki, abin buk’ata ki yi takatsantsan baa
son kuskure ko guda. A satin nan muke son ki kai buk’atar ha’da auren Murad da
k’anwarki gaban sarki.” Ta karb’i k’ullin tana sakin ajiyar zuciya kafin ta ce
“Kuna tunanin Sarki zai amince da buk’atar auren Murad da k’anwata?” Dariya
suka yi sosai suna furta “Da zarar kin saka wannan layar a k’ark’ashin
harshenki kika furta masa k’udirinki zai amince.” Ta gyad’a kai kafin ta furta
“Ba zaku nuna min kan ku ba? Shekara nawa muna tare ban tab’a ganin fuskarku
ba? Tambaya ta gaba kune kuka samar da cikin Murad? Kuma wacece mahaifiyarsa?
Kuma
Me yasa cikin bai zama tare da ni ba sai wata can?” Dariya
suka yi sosai kafin su ce “Lokaci na zuwa da zaki samu amsar duka wa’dannan
tambayoyin naki, ki je ki aikata abinda muka umarceki!”
Suka fa’da cikin daka tsawa
Kafin su umarceta ta bar wajen. Ta juya a hankali ta bar
wajen zuciyarta cike da jin haushin rashin amsa mata tambayoyinta da ba su yi
ba, su waye wa’dan nan d’in? Shine abinda bata sani ba.
Kashegari kuwa da k’udirin hakan ta tashi a ranta. Ta yi duk
abinda zata yi kafin isa turakar Sarki bisa jagorancin Jakadiya. Sai da ta gama
hilace shi tas kafin ta bijiro masa da zancen ha’da Murad da k’anwarta. Abin
mamaki ko ka’dan Sarkin bai musa mata ba ya amince take ya kuma ce mata ta
sanar da Murad d’in shima kuma zai sanar masa ranar Sallah za’a d’aura auren da
zarar an sakko daga Sallahr Idi shi kansa zaman Murad d’in ba aure ya fara
isarsa. Zallar farin
Ciki ya bayyana akan fuskarta ta fice daga d’akin cikin
farin
Ciki ta isa sashenta kafin ta dannawa mahaifiyarta kira ta
bata kyakykyawan albishir. Ta Kuma ce ta turo mata Amran a yau akwai abinda
zata bata ta je da shi har b’angaren Murad da zarar ya sha’ka zai ji duk duniya
ba matar da yake son ya aura sama da ita.
_______
Da k’ananan kayansa da ya je training da su ya yi hanyar da
zata sadashi da b’angaren matan Sarkin. Kai tsaye sashen Mammansa ya nufa. Bata
d’akinta kamar yarda ya saba ganinta a duk safiya don haka ya fito yana kallon
su Mardiyya masu aikin b’angaren nata. “Ina Mamma?” Ya furta cikin murya mara
sautin amo don a gajiye yake lik’is. Mardiyya ta nuna masa kitchen. Har zai
zauna ya ce ta kira masa Mammahn sai kuma ya fasa ya nufi kitchen d’in da
kansa. A tsaye ya samu Mamman da y’ar bak’ar yarinyar suna aiki tare don Mamman
ta saba ko me take yi ita take masa abinci shi da Maimartaba a duk ranar
girkinta. Ya ware ido ganin yarda yarinyar take aikin fere dankali. “Mammah me
wannan take yi?” Mamma ta juyo fuskarta a ha’de ta ce abinda idanunka suka gane
maka.” Ta juya ta cigaba da aikinta Harara ya zubawa Najwa kafin ya fice daga
kitchen d’in duk yunwar da yake ji ba yarda zai yarda ya ci abincin da waccan
yarinyar ta saka hannu.
Yana zaune a parlourn sa Hannunsa cushe cikin sumar kansa
yana murzawa a hankali ransa ne a b’ace ga yunwa da yake matuk’ar ji ya ji an
turo k’ofar an shigo. Azababben k’amshin da ya ji ne yasa shi bu’de ido a
hankali. Kyakykyawar budurwar da ta sha kwalliya sosai tana tsaye tana sakar
masa murmushi ta zauna a gefensa ha’de da d’aukan pillow tana saka shi a
cinyarta ta d’ora hannayenta a kai, cikin murya mai cike da yanga ta ce “Barka
da hutawa.” Murad kasa d’auke idanunsa ya yi a kanta wata irin soyayyarta mai
zafi tana harbawa a zuciyarta ya lumshe ido a hankali yana furta “Barka dai
Beauty!
JIKAR NASHE✍π½
KUDIRAR ALLAH
25.
NAZEEFAH SABO NASHE✍π½
08033748387.
Shi kansa da ya yi furucin sai da ya ji abin wani
banbarakwai, abinda bai tab’a yi ba a rayuwarsa son wata mace ko ya bawa
halittarta. Ya d’an furzar da hucin numfashi yana cigaba da kallon fuskarta da
ta sha makeup. Da gaske kyakykyawa shi da kansa ya shaida haka. Yanayinta ya
nuna gogewa da wayewa yarda take kallon cikin k’wayar idanunsa tana jifansa da
wani sihirtaccen murmushi mai sanya maza kasala. Layar hannunta ta cigaba da
matsawa kafin ta sake jifansa da wani murmushin ta mik’e tana taku ta nufi hanyar
fita “Am sorry na for disturbing you Amrah by Name.” Ta fice cikin takun yanga
da take sarrafa jikinta yarda ta so duk da ba wata kyan sura ba ce da ita ta
azo a gani. Murad ya lumshe idonsa yana jin wata irin kasala gaba d’aya ta
mamaye gabbansa abinda bai saba da shi bai kuma d’aukeshi da mahimmanci ba
tunanin aure da sha’awa ma gaba d’ayanta.
Amra na fita ta saki ajiyar zuciya ganin da gaske tarkonta
ya kama Murad ita da kanta ta san ya yi mata kuma shine ya dace da zama Mijin
Amra. Ta fa’da tana murmushi ha’de da fa’din “Nagode Yaya Raheena kin biya ni.”
Daga haka ta nufi b’angaren Fulani Raheenan tana tafe tana sauraran wak’ok’in
da suke sanyata nisha’di. Ta fuskarta Fulani Raheena ta hango alamun nasara.
Murmushi ta sakar mata kafin ta furta “Bani Layar nan don itace makaman yak’in,
da alamu mun yi nasara.” Amra ta saki murmushi tana furta “K’warai kuwa,
wallahi tarkon da kika d’ana masa ya kama shi, Alllah ya nuna mana ranar auren
Yaya, Murad ya yi ta ko ina ba shi da makusa shi ya dace da zama Miji na har na
k’agu lokacin ya zo ban san wani irin y’ay’a zan haifa masa……” “Ke!” Fulani
Raheena ta dakatar da ita a tsawace tana wurga mata wani irin kallo. “Wace irin
banza ce ke? Daga ganin Sarkin fawa sai miya ta yi zak’i? Ce miki aka yi nufina
ki aure shi ki haifa masa yara? Ba don wannan na shiga na fita na samo miki
zuciyarsa ba saboda nawa burin ne, ran Murad nake so so nake ki zame min tsani
na shek’a shi lahira, bana son ganinsa Abdul nake so ya mulki mutanen Gabas…”
waro ido Amra ta yi tana kallonta cikin tsananin mamaki ta furta “Kisa kuma
yaya?” “Kisa Amra, ya kuma zama dole ki bi umarnina tunda kika ji sirrina idan
ba haka ba kuma ki shirya tafiya lahira kema, zan iya kawar da ko waye don
cikar burina.” Ta fa’da idanunta suna k’afa fitowa suna nuna alamun b’acin
ranta da gaske. Amra tsorata ta yi da yanayin Yayarta ta ta kuma bata mamaki matuk’a
da gaske, bata yi tsammanin rashin Imanin nata har ya kai haka ba. “Zaki iya ko
kuwa?” Ta fa’da tana sake tsareta da ido. Amra ta ha’diye kakkauran yawun da ya
taru a bakinta kafin cikin mutuwar jiki ta d’aga kai “Zan iya.” “Ashe kina son
rayuwarki, banda abin ki ke Ai abin jin da’dinki ne ace kece matar Yareeman
gabas ko bakomai kema kin shiga tarihi, za kuma ki samu dukiya mai tarin yawa
ta tumunin takaba, ki bu’de kunne da kyau ki ji ni, duk abinda na umarceki shi
zaki yi bana son musu.” Ta sake d’aga kanta a hankali. Tashi ki tafi ki bani
waje.” Tana tafiya Fulani Raheena ta bi bayanta da wani watsattstsen kallo
kafin ta ciji leb’enta tana furta da alamu kema sai an min aiki a kan ki
yarinya, dole sai an min yarda zan dinga juya Ki son raina ki dinga bin
umarnina ko ba kya so. Daga haka ta mik’e zuwa cikin d’akinta tana jin kamar
duk wani burinta ya gama cika.
Da Magriba Murad na zaune a parlournsa hankalinsa duk yana
kan kallon football sai ga Sak’o daga sarki akan yana nemansa a Fada. Ba b’ata
lokaci ya mik’e suka fita da bafaden zuwa ainahin k’aramar Fadar gidan sarkin.
A zaune ya samu Sarkin gabas d’in Fulani Raheena na zaune a
gefensa hannunta d’auke da plate d’in apples tana yanka masa. Da murmushi fal
fuskarta ta tari Murad ‘Din. Ya zauna a gefen kujerar Sarkin kansa a k’asa yana
matsa hannunsa. Maimartaba ya dubeshi yana murmushi bayan ya amsa sannu da shan
ruwan da yake masa. “Mun sha ruwa lafiya Murad gwauro.” Murmushi ya saki yana
sosa kansa a hankali cikin nutsuwa ya furta “Lafiya k’alau.” Maimartaba ya
mik’a masa tray d’in da yake d’auke da peppe soup na cowtail.
Duk da a k’oshe yake haka ya amshi peppe soup d’in yana sha
a hankali don ya san bai isa ya ce Ya k’oshi ba Sarki ba ya kyauta ace ba’a so,
yana daga cikin abubuwan da baya so, kuma kowa ya sani. Sipping yake a hankali
yana jin bugun zuciyarsa na k’aruwa haka kawai tun yammacin ranar yake fama da
bugun zuciya mai k’arfin gaske. “Lokacin da ya kamata ka yi aure ya zo Murad!”
Ya jiyo maganar Sarki daga sama yana fa’da a hankali cikin nitsatstsiyar murya.
Da sauri ya d’ago yana kallon Sarki. Shima dubansa yake yana murmushin da
alamun rashin wasa a maganarsa. “Da gaske ya kamata ka yi aure Murad shekarunka
sun tura, kana da wacce kake so ko mu maka zab’i?” Haka kawai sai hoton
yarinyar d’azu ya dinga fa’do masa yana jin ita ya dace ya aura sai dai haka
kawai ya dinga jin nauyin bakin furta hakan ga Sarki. “Na baka zab’i.” Ya fa’da
a hankali. Sai a lokacin Fulani Raheena ta saki ajiyar zuciya farin ciki ya
cika ta, ta tabbata aikin Malamin ne ya ci. “Alhamdulillah! Tunda ka bamu zab’i
ba za mu maka zab’in tumun dare ba, Dama yanzu Mamanka take ce min ta maka Mata
ta baka k’anwarta don haka In sha Allah ranar idi zata zama ranar aurenka ba
don komai ba sai don kafa tarihi, shi yasa na zab’i ranar idin k’aramar sallah,
ina fatan hakan ya maka?” D’aga kansa ya yi kawai yana ajiye plate d’in
hannunsa, sai ya ji yana fatan dama yarinyar da ya gani a d’azu ita zata zama
matarsa. Jikinsa a sanyaye ya mik’e ya fita daga fadar, yana jin kamar bai yiwa
kansa adalci ba da ya bada damar a zab’a masa matar da zata zama maha’din
rayuwarsa, me yasa bai tsaya ya tantance da kansa ba duk da burin da ya ci na
zab’ar mata ta kerewa sa’a da kowa zai jinjina masa. Tunda yake bai tab’a ganin
matar da take burgeshi ba shi yasa ba agenderr hakan a cikin ransa banda
yarinyar da ya gani d’azu bai tab’a d’arsa wata mata a ransa ba.
Haka ya dinga tafiya yana rangaji zuwa sashen Mammansa da
yaji haka kawai k’afafunsa na jansa zuwa can ba tare da ya san dalili ba. Ba
kowa a Babban parlourn sai Hadimanta ya bi su da ido kawai kafin ya saka kansa
d’akin Mamman tana zaune idanunta akan t.v sai dai ba kallon take ba tunani ne
ya cika mata zuciya. Shigowar Murad yasa ta d’aga kai da sauri tana kallonsa.
Damuwar da ta gani a idanunsa ya sata mayar da hankalinta kansa. Ta nuna masa
gefen gadon tare da kashe t.vn tana furta “Me ya sameka haka? You looked
worried.” Ya sunkuyar da kansa kawai ya kasa magana. Mamma ta ja hannunsa tana
kallonsa “Oya talk to me me ya sameka na ce?” Ajiyar zuciya ya saki kafin ya
furta “Na yanke hukunci without you Mamma shine abin ya dameni.” Fa’duwa
gabanta ya yi sosai ta gyara zamanta ta ce “Hukuncin me ka yanke Murad?”
“Aure!” Ya fa’da idanunsa suna raunacewa cikin nata. Hannunta na rawa ta ce
“Aure kuma? Wa zaka aura?” Ya saki ajiyar zuciya yana fa’din “Sisterr Umma.”
“What?” Fulani ta fa’da da sauri hannunta na saki gaba d’aya ta zauna a hankali
gefen gadon tana furta “Wa ka gayawa zaka aureta? Kuma me yasa baka nemi
shawarata ba me yasa hakan ta faru ba tare da sani na ba?” Ta fa’da hankalinta
a tashe duk ta d’imauce. “Mai martaba na gayawa” Ta sake zare ido hankalinta na
sake tashi ta furta “Shikkenan ba ni da ta cewa, Murad me yasa kake son saka
kanka a matsala? Ka san abinda ka aikata kuwa? Zaka saka kanka a matsala? Tashi
mu je wajen mai martabar.” Bin bayanta ya yi a hankali ta fice zuwa k’ofar da
Zata sadata da Parlourn Maimartabar. Fulani Raheena ta gani a zaune da
maimartabar bayan Jakadiya ta yi mata umarni ta shiga. Yanayinta kawai Raheena
ta gani ta saki murmushin mugunta don ta san abinda ya kawota. Kallo Saddik’a
ta watsa mata kafin ta gaishe da Sarkin da yake kallonta cikin mamakin yanayin
da take ciki. “Wata magana Murad ya je min da ita, wacce zai yi wuya na amince
da ita.” Mai martaba ya gyara zamansa ganin da gaske maganar mai mahimmanci ce
maganar da zata sa Saddik’a ta taso da daddare ta zo turakarsa ba ranar
girkinta ba. “Ina jin ki!” Ta zauna tana fitar da hucin numfashi na alamar
b’acin rai. “Auren Murad da ake neman k’aga masa ba Zan amince da shi ba!” Mai
martaba ya dinga kallonta cikin mamaki yana son karanto abinda yake ranta.
Fulani Raheena kuwa gyara zama tayi tana sake matsa Layar hannunta cikin
murmushin mugunta tace “Auren Murad da Amra kamar an yi an gama, ko da ke kika
haifi Murad balle ba ke ce uwarsa ba!” “Idan kuma ni d’in ce Uwarsa fa? Ko kin
gwada jininsa da nawa kin ga ba d’ana bane? Shin kin gwada k’wayoyin halittarsa
da nawa kin ga ba nice Uwarsa ba?” Ta fa’da cikin furzar da numfashi tana jin
kamar ta rufe Raheena da duka…….. “Aure da k’anwarki da Murad ba zai yiyu ba in
dai ina numfashi!”
JIKAR NASHE✍π½
A yi hak’uri wayata
ce ta lalace da ta aro na yi. π«£
KUDIRAR ALLAH..
26.
NAZEEFAH SABO NASHE✍π½
08033748387.
Fulani Raheena ta sake dubanta sosai tana mamakin furucinta
da tunanin yarda aka yi idanun Fulani Saddikan suka soye har suka daina
tsoronta. Saddik’a kuwa idanunta ta mayar cikin na sarki tana jiran jin abinda
zai ce, ga mamakinta ba wani b’acin rai a fuskarsa ya ce “Me yasa Saddik’a ba
kya son ha’da auren? Ina ga ba wani aibu bane tunda har shi Murad d’in ya
amince…” “Aibu ne mai martaba, aibu ne mai girman gaske da tasirinsa zai iya
jefa Murad a cikin masifa don haka ni dai da yawuna ban amince ba…” ta furta
idanunta kamar su zubar da k’walla. Mai martaba ya saki ajiyar yana furta “Ko
da shi Murad d’in yana so?” Kasa magana ta yi ganin kamar Maimartaban ba zai bi
bayanta ba, wato yana nufin ita bata isa ta zartar da hukunci akan Murad ba
kenan? Lallai akwai abin mamaki nan gaba randa gaskiya ta yi halinta. Ta
ha’diye yawu mai d’acin gaske na rashin tasiruwantuwar zancenta a wajen
Maimartaba, sai kawai ta mik’e bayan ta jefe su da kallo mai nuni da zallar
takaici ta fice a d’akin zuciyarta tana jin kamar ta fasa b’aragurbin k’wan da
warinsa zai yi sanadiyyar rugujewar farin ciki a wajen Al’ummar Gabas! Sai dai
ta san bata isa ba bata da wannan ikon ba a bata wannan damar, tunda duk wani
abu da take kamar umarni ne ake bata, ta fice daga d’akin cikin mutuwar jiki.
Sarkin ma kallonta yake tausayinta mai girma yana son ya mamaye zuciyarsa sai
dai tasirin asirin Raheena ya kasa barinsa ya yi katab’us sai zallar bin
dokarta da cika umarninta kamar dai Uwar da ta kawo shi duniya. Raheena ta
sauke ajiyar zuciya tana sakin murmushi da kai tsaye mai kallonta zai
fassarashi a matsayin na mugunta ko na cikar muradanta. “Kada damuwar da ta
shiga ta sanyaka a damuwa nan gaba ka’dan zata yi alfahari da auren nan, zaku
ma ta ce gwara da aka yi don hakan alheri ne ga masarautar gabas.” Ta furta
idanunta da suka sha sihirtaccen kallo suna kallon cikin nasa maganan, yana jin
furucinta na fisgarsa kamar magana’disu haka ya d’aga mata kai alamar ya yi
na’am da dukkan umarninta. “Ranar idi itace zata zamo rana mafi mahimmanci ga
mutanen gabas!” Ta juyo waccen muryar da tayi mafarki da ita a daren jiya, ko
tace abin da ake kira Imagination don dai zahiran tana ganin duhuwar inuwar mai
furucin a cikin barcinta, kuma muryar ta kara’de duk wani lungu da sak’o na
d’akinta, kamar dai a cikin mafarki mai tasiri a kwanya da zuk’ata. Sai dai ko
kafin k’iftawar ido waccen maganar ta d’auke da kuma ta bu’de ido bata ga kowa
ba, sai iska mai k’arfin gaske data kara’de d’akin. Da gaske ta firgita saboda
yanayin da aka isar mata da sak’on ya sha banban da inda ta saba karb’ar sak’o
a kowane lokaci. Ta ja baki ta yi shiru ta kuma manta da maganar sai yanzu da
take gaban Sarki maganar ta fa’do mata, bata ji komai a ranta ba illa wannan
auren da za’a yi shine ake mata ishara da shi a cikin mafarkinta, me hakan yake
nufi? Idan banda haka me yasa ranar idi zata kasance rana
Mafi mahimmanci ga al’ummar gabas! Ta d’auke numfashi tana
gujewa dukkan wasu tunani da suke sanya ru’dani a zuciyarta ta ayyana waccan
ranar ta idi da za’a d’aura auren Murad da Amra shine abu mai mahimmancin. To
za dai mu gani! Mai martaba ya gyara zamansa yana kallonta “Sai a je a fara
shirin duk abinda ya kamata don sati uku kamar yau ne.” Fulani Raheena ta saki
murmushin jin da’di da cikar burinta ta ce “In Sha Allah komai zai tafi
successfully cikin nasara.” Mai martaba ya jinjina kai yana furta “Haka muke
fata!” Daga haka ya mik’e don isa makwancinta ita kuma ta fice daga d’akin
zuciyarta wasai tana jin kamar yau ne za’a na’da Abdu d’inta a matsayin Sarkin
gabas.
Fulani Saddik’a kuwa koda ta koma d’aki kasa nutsuwa ta yi
duk ranta ya gama b’aci ga wani irin bugu da zuciyarta take yi mai k’arfin
gaske. Da gaske ta sare da duk al’amarin Raheena, a komai ita take zama mai
nasara me yasa koda yaushe ita take zama koma baya? Har mutane suke mata kallon
itace BORAR SARKI! Ta zauna turus a gefen gado idanunta na tsiyayar da k’walla
da yake nuna gazawar zuciyarta a fannoni da dama. Me yasa idanun Mai martaba
kullum a runtse suke ba ya hango aibu ko bak’in halin Raheena? Ko da yaushe
sune masu laifi har gwara ita akan wad’ancan sauran matan nasa da ba’a san meye
matsayin su a gidan ba, don ba ma ya shiga sabgarsu baa san Kuma wani laifi
Suka aikata masa ba. Tana wannan halin su Nene suka fa’do mata sai dai ta ji ta
samu sauk’in fargabar ta tana jin komai ma zai zo mata da sauk’i, tabbas zata
b’ullowa Raheena ta inda zatonta ba zai tab’a zata ba. Haka kawai sai ta samu
kanta da sakin k’ayataccen murmushi ha’de da sakin ajiyar zuciyar da ta tafiyar
mata da duk wani b’acin ranta. A hankali ta dinga jin sanyi na shiga kafofin
jikinta zuciyarta na hucewa daga turirin da take. TABBAS IDAN RAHINA TA SAN
WATA BATA SAN WATA BA! Ta fa’da murya a fili cike da karsashi. Ta zame a wajen
tana mayar da kai ta kwanta. Da a ce dama tana da tsarki kwana zata yi ta na
fil fili tana kaiwa Allah kukanta. A hakan ma cikin rashin tsarki ta dinga
tasbihi ga Jalla ha’de da tsarkake sunansa. Sai ta ji ta sake samun k’warin
gwiwar tunkarar duk Matsalolin RAHEENA da suke fuskantota, tana jin kamar burinta
ya cika, kamar wancan burin da ya dad’e zaune daram a zuciyarta daf yake da
cika, burin ranar da Raheena zata tozarta a idanun mutanen Gabas….
A d’akinsu Nene kuwa zaune suke bayan sun gama
Cin abinci suna tattauna duk ta inda bincikensu zai kama,
duk da Saddik’a ta ce su bar komai a wajenta, sai zuciyar Nene ta kasa amincewa
da hakan ta fara tunanin hanyar da zata kai su ga b’ullewa ba tare da sanin
Saddik’an ba, don sam bata hango sanayyar Saddik’an a cikin wad’annan
caku’daddun al’amuran masu kama da almara ba. Ta saki ajiyar zuciya tana duban
Najwa. “Je ki parlour kiga Fulani tana nan? So nake mu zame na fita na duba
ainahin tsohon gidan mu ko iyayena suna nan daga nan zan fara.” Najee ta d’aga
kai. Ta mik’e tana gyara k’ullin zanin da ta yi shi mai suna d’age gwanjo. Ta
mudubin d’akin ta kalli kanta haka kawai ita da kanta sai ta bawa kanta dariya
har hak’oran gatson na shirin cirewa, ta yi saurin mayar da su. Nene ma dariya
ta yi tana fa’din “Ladidi Uwar muni, maza je ki ki dawo ki kira mana Umma mu
gaisa jiya da yau duk ba mu gaisa ba.” Najwa ta fice tana fa’din “Yanzu kuwa.”
Ba kowa a parlourn da alama duk sun yi barci kasancewr dare ne lokacin goman
dare ta yi kuma gajiyar azimi yasa duk sun kwanta. Najee ta juyo da sauri ta
sanar da Nene ba kowa. Nene ta saki ajiyar zuciya ta mik’a mata bak’ar doguwar
rigar tana furta “Mu je to. Ta k’ofar kitchen da nasa kika sato mukullin za mu
bi. Ko da Fulani ta kama mu Kuma a take a wajen ki fara murk’ususun ciwon cikin
k’arya sai na ce magani na je samo miki, ai kin gane ko?” Najee ta d’aga kai,
tana cigaba da saka doguwar zulumbuwar rigar wacce ta Hadiman Fulani ce suka
sato. Tas suka fito kamar Hadiman b’angaren fulanin, don haka da wuya ka gane su.
Suka fita parlourn a hankali bayan sun gark’amawa nasu d’akin
D’an mukulli. Shiru harabar gidan ba kowa sai fadawa da suke
wucewa jefi jefi. Ba ka jin komai sai kukan tsintsaye. Wajen duk ya canja don
haka Nene taso ta rikice, sai dai cikin hikima da buwayar Allah sai ga shi ta
je hanyar gidajen Fadawan. Kamar wasa kuma sai ta gane gidansu duk da an d’an
canja fasalin ginin amma hakan bai hanata gane k’ofar zaurensu ba. Ta saki
ajiyar zuciya hawaye na shirin zubo mata tunanin waccen rayuwar ya dinga dawo
mata, rayuwa ce mai cike da jin da’di da k’uruciya ba komai a cikin zuciyarta a
lokacin banda shirme da wasa sai ga shi
Lokaci guda an jirkita tunaninta aka kuma aza mata babban
tunani irin na manya a lokacin aka mayar da ita cikakkar mace mai juna biyu a
cikin shekara sha shidda kacal! Ta d’auke k’wallar idonta tana fatan ta je taga
iyayenta da rai cikin k’oshin lafiya da kwanciyar hankali, ba kamar yarda
zuciyarta take d’imauta ta da cewa iyayen nata tuni sun da’de cikin kushewarsu
tsoron hakan
Yasa ta tsayawa a zauren gidan tana ajiyar zuciya. Bata son
shiga ta tarar da wasu sab’anin iyayenta. Najee ta dafata cike da rarrashi ta
ce “Mu shiga Nene, in sha Allah alheri za
Mu tarar.”
Nene ta ce “Allah yasa Najee Allah yasa na tarar da su cikin
lafiya, Allah Yasa ina da rabon ganawa da su.” Najee ta amsa da ameen cike da
tausayi.
Kafin ta saka hannu
ta k’wank’wasa gidan, sai dai alamu sun nuna saya gidan ma aka yi.
Don haka tana saka hannunta sai k’ofar ta bu’de, nan suka
Hango filin tsakargidan da hasken fitila ya haske shi
tarwai. K’asa ce malale a tsakargidan a share tas! Suka fara sallama daga cikin
d’akin aka amsa musu kafin a fito ana furta Maraba lale wa muka samu da
daddare?” Nene ta yi cak zuciyarta na bugu da k’arfin gaske ganin matar ba
mahaifiyarta ba ce, wannan da take tsaye ba zata zarta sa’arta ba. Shikkenan ta
faru ta k’are ta furta a hankali don in dai su Babi suna nan ba abinda zai saka
a canja musu gida anan zasu rayu har su mutu matsayin su na gadaddun bayi.
Matar ta dallaresu da fitila mai charging tana furta “Bayin Allah ban waye da
ku ba?” Nene ta saki ajiyar zuciya kafin ta sake rufe fuskarta suka gaisa da
matar sannan ta ce “Ainahin mutanen gidan muke nema” wani kallo matar ta bita
da shi, duk da bata ganin fuskarta ta ce “Wane irin ainahin mutanen gidan sai
dai idan b’atan kai kuka yi, ai nice a gidan nan tun bayan b’acewar mutanen
gidan bayan b’atar y’arsu suma aka nemesu sama ko k’asa aka rasa, baa sani ba
sace su aka yi ko guduwa suka yi oho! Sarki dai ya bada Umarnin ni da Mijina
Sarkin Aska mu dawo nan shekaru talatin kenan kuma ba wanda yazo nemansu sai
ku? Ku ‘din su waye?” Nene ta saki ajiyar zuciya kafin ta girgiza kai cike da
k’arfin hali ta juya tana furta “Yi hak’uri baiwar Allah ina ji b’atan kai muka
yi.” Ta ja hannun Najee da sauri suka bar gidan. Ko a hanya zuciyarta bugu take
da tunanin ina iyayenta suke, a ina zata fara nemansu idan ma suna raye? Kuka
sosai take sai dai mara sauti ba mai ji sai Najee da take jin yarda jikin Nenen
yake rawa.Daidai k’erarren gidan nasa suka zo wucewa shi kuma ya fito kenan don
shiga cikin gidan nasa ya ce karo da Najee da jikinsu ya ha’du, take ya ji wani
irin shock ga shi ta buga masa kanta a k’irjinsa, cak numfashin Najee yaso
tsayawa ta dinga kokawa da muryarta wajen ba shi hak’uri, sai dai yanayin
tsoron da take ciki bai bar shi ya ji abinda ta ce ba. Ya zaro wayarsa cikin
b’acin rai yana dallareta da fitila. A fili ya furta “What? You? Uban me kike
da daddaren nan har kika zo kika bugeni kina ha’da wannan k’azamin jikin naki
da nawa?” Yanayin yarda yake furucin a tsawace a kyamace ne yasa Najee zuba
masa wani kallo ta cikin hasken fitilar ba tare da shirinta ba ta zabga masa
harara ha’de da murgu’da baki…. Murad ya dinga jin wata wutar masifa tana juya
rayuwarsa a zafafe ya fisgota da k’arfin gaske yama manta da batun k’azanta
yasa hannu ya murje bakinta inda hak’oran roban suka tusge gaba d’aya…….
JIKAR NASHE✍π½
Da alama dai daf ake da barinki a baya, don kuwa part one ne
free kuma daf yake da k’arewa ga shi kin tsaya son ku’di kin kasa biyan d’ari
biyar kacal ko dubu d’aya ana jiran na bati! π«£π€£ bana JIKAR
Nashe ta murd’a kambunta book two ko kyallinsa ba zaku gani a whatsapp ba. Tura
ku’dinki kai tsaye don gujewa barci kina tunanin ya aka yi aka samar da cikin
y’an biyun? Kuma shin Nenen da Sarkin su ne iyayensu a gaske ko y’ay’an aljannu
ne? 2118666253 UBA. Sai a tura shaidar biya ta wannan numberr 08033748387.
JIKAR NASHE✍π½ mai tak’ama da ikon subhanaπ€
KUDIRAR ALLAH…
27.
NAZEEFAH SABO NASHE.✍π½
08033748387. (π€ Wanda ya gane ya gane.)
_________________
Cikin azama don gudun fallasuwar sirrinsu Nene ta janyeta ta
tura a bayanta, tana kallon Murad d’in da b’acin ransa ya gama bayyana akan
fuskarsa saura k’iris ya saukewa Najeen yatsunsa a kan fuskarta. Sai kawai ya
saki guntsun tsaki yana furzar da wani huci ya cije leb’en k’asansa. Banda yana
ganin girma da mutuncin Uwar yarinyar nan da yau ba abinda zai hana shi
b’allata, idan kuma ya b’allata ya b’alla banza. Idanu Nene ta sauke masa hakan
ya saka shi rusunar da nasa k’wayar idanun yana jin wani sanyi yana ratsa jiki
da zuciyarsa wanda bai san dalilinsa ba. Ya dai samu kansa da dunk’ule hannu
waje d’aya sai kuma ya juya da sauri cikin takunsu na sojoji ya bar wajen a
zafafe kamar walk’iya. Nene ta saki ajiyar zuciya tana janyo Najwa da ta b’uya
a bayanta jikinta na b’ari sosai al’amarin Murad ya bata tsoro, wato banda Nene
ta janyeta so ya yi ya kifa mata mari. Nene dariya ce ta k’wace mata duk da
bata cikin yanayin dariyar amma ganin yarda Najee ta tsorata idanunta suka
firfito waje shi ya sata sakin murmushin da bata shirya ba. Najee ta lumshe ido
tana fa’din “Wallahi Nene na fa zata mari na zai yi. Ga hak’oran bogin sun cire
yau da asirin mu ya tonu.” “Banda na janyeki tabbas da marinki zai yi, ban san
me yasa sam kurwarku bata jituwa ba, wuce mu je ki kira min Umman yara ina son
magana da ita.” Najee ta bi bayanta da sauri suka koma cikin gidan Fulanin,
cikin ikon Allah ba wanda ya fito don haka ba’a san har sun koma d’aki ba. A
bakin gado suka zauna suna sakin ajiyar zuciya. Nene ta ce “Allah ya rufa mana
asiri har muka je muka dawo ba wanda ya san mun fita.” “Ai kuwa da ba mu san ke
za muce wa Fulani ba” “Yanzun ma ba abinda zaku ce min, tunda har kuna da wani
sirri da zaku iya b’oye min.” Fulani ta fa’da tana. Fitowa daga wata k’ofa inda
balconyn d’akin take. Jikinsu ne ta fara rawa a tsorace suka fara kallonta da
mamakin furucin ta. Tana tsaye idanunta a kansu tana sakin murmushi ta ce “Ba
ku same su ba ko? Baa san kuma inda suke ba?” Hantar cikin Nene da Najee ce ta
ka’da suka dinga kallon Fulani a tsorace jin furucin ta daga sama, sai kace mai
aiki da jinnu, wa ke sanar da ita sirrinsu ne?” Nene ta tambayi kanta sai dai
kamar amsa da furucinta Fulani ta ce “Na san inda kuka je, kuma da kin gaya min
can d’in zaku je zan sanar da ke ba zaki samu abinda kika je nema ba.” Shiru
Nene ta yi idanunta Suka kawo ruwa tana duban Fulani ta ce “Kin san sun mutu
ko? Don Allah sanar da ni labarin rasuwar iyayena.” “Ban san sun mutu ba, ba
kuma zan ce miki suna raye ba. Addu’a ce kawai tsakaninki da su.” Nene ta sunkuyar
da kanta tana jin harbawar zuciyatta yana tsananta. Fulani ta d’an bubbuga
bayanta kafin ta fice daga d’akin cikin tafiyar rangaji tana furta “Asuba ta
gari, just pray for them, Khairan In sha Allah.” Kukan Nene ta ha’diye tana bin
bayan Fulani da kallo, kamanninta da yanayinta yana bata tsoro tabbas Fulani na
aiki da jinnu ko wani k’asurgumin Bokan, idan banda haka ta yaya aka yi ta san
sun fita tunda ba bin bayan su ta yi ba, sannan yanzu ta zo tana mata wasu
zantattuka masu kama da harshen damo. Kuka sosai suka sha ita da Najee, kafin
su kira Umma. Bugu d’aya ta d’auka kamar dama jiransu take. “Kuna lafiya ko?”
Suka d’aga kai da yake vedio call su ke. Umma ta jinjina kai “Hope kun fara
samun abinda muke nema?” Nene ta girgiza kai “Ba abinda muka samu Umma, komai a
rufe yake ban san ta inda zan fara ba wallahi.” Umma ta d’an yi jim kafin ta
saki ajiyar zuciya “Alright, idan baku samu ba zuwa Ranar Sallah sai ku dawo,
as you all know ranar d’aya Ga Sallah Baffa yake dawowa daga Umara bana son ya
dawo yaga ba kwa nan.” Nene ta d’aga kai haka suka cigaba da hira cikin nutsuwa
Umma tana sake ba su shawarwarin da za su bi don a samu a cimma manufa.
*************
Tuni shirye shiryen biki ya fara kankama a cikin masarautar
zancen Auren Murad ya kara’de lungu da sak’o, kowa burinsa da fatansa ganin
wannan ranar mai d’imbin tarihi a masarautar Gabas auren Yareema d’an Sarkin da
baa san ta yarda aka samar da cikinsa ba. Fulani Raheena fitar da ku’di take
kamar bata so, ta kuma rufe bakin Sarkin ruf ta yarda yake sakar mata dukiya
kamar baya so burinsa kawai a fita kunyar jama’a duka k’asa ma ba iya yankinsa
kawai ba. Akwatin lefe da wasu irin gwalagwalai ba a magana akwatinan kansu a
bin kallo ne. Shi dai ango Murad bai san ma wainar da ake Toyawa ba, bai san
wacece amaryar ba sai dai waccan yarinyar da suka ha’du rana guda ta tsaya
masa. A k’ahon zuciya, sau tari sai ya nufi cewa a fasa auren sai ya ji kamar
an nanna’de harshensa ya kasa magana, haka yana ji yana gani ya zubawa sarautar
Allah ido. Fulani Raheena bata damu su ha’du da amaryar tasa ba, don an
umarceta kada su sake su ha’du har sai an gama sihirtaccen aikin da akewa
amaryar don haka ta dage tuk’uru wajen ganin tasa Amra ta aikata duk wani
tsubbu da aka saka ta ta yi.
Gefen Fulani Saddik’a ma, tsaye ta tashi da nata shirin
kamar dai ba ita ke adawa da auren ba ta dinga shirya k’ayataccen biki da nata
aljihun da na y’an uwanta aka fara shirin gagarumin bikin da ba’a tab’a yi ba a
masarautar Gabas.
Ranar da aka umarceta ta ha’da amarya da angon don saka
soyayya mai zafi a zuciyarta. A ranar ta bata wasu magunguna ta yi wanka da su,
sannan aka tsumata sa sihirtaccen turaren da ya kama jikinta sosai. Idanunta ya
sha sihirtaccen kwalli. A d’akinta ta zaunar da ita kafin ta kira Murad a waya
ta ce ya zo sashenta yanzun nan zai ga matar da zai aura. Ji ya yi kansa ya yi
wata irin sarawar da bai tab’a yi ba ya zauna a gefen gado yana rik’e kan nasa
har a lokacin wayar na kare a kunnensa murya can k’asa kamar mai mura Fulani
Raheena ta ce “Dafatan Murad ya ji mu, kuma zai bi umarnin mu.” Da sauri ya
mik’e yana ha’da murya wajen fa’din “Yanzu kuwa.” Ta kashe wayar tana shek’a
dariyar da sai da Uwarta ta d’ago tana kallonta, itama da tata dariyar a
fuskarta ita da kanta da ta haifi Raheena sau tari tana tsoron shu’umancinta.
“Da alamu aiki ya ci d’an banzan kenan?” Uwar ta fa’da tana kallonta. Raheena
ta sake dariyar sosai tana tura kuttun hannunta k’ark’ashin gado ta ce “Tun
yaushe, yanzu zaki ga d’an banzan, ko nace gawar wata guda na bashi Zan shek’a
shi lahira. Ko ciki ba zan bari ta samu ba, ko da yake ko ta samun d’an ba zai
gaji Sarautar gabas ba tunda Ubansa ba ya raye kuma Abdul yana raye.” Uwarta ta
saki murmushi tana fa’din “Allah ya ida mana nufi, ace Jikana ne yake sarautar
Gabas da na fi kowa sa’a.” “Ki k’addara hakan a matsayin an gama.” Ta fa’da
cike da tabbatarwa. Daidai lokacin da amintacciyar baiwarta ta shigo don isar
da sak’on zuwan Murad. Ta amsa mata tana kallon Amra ta ce “Zo nan.” Amra ta bita
suka shiga wani d’aki wani powder ta sake fesa mata a fuska sannan ta ce “Wuce
ki je.” Amra ta juya jikinta a sanyaye suka fita da hadimar da take tsaye tana
jiran ta, ita ta kama k’asan doguwar alkyabbar da take jikinta. Suka fita zuwa
babban parlourn da Fulanin take saukar bak’i. Tun daga corrodor suke jiyo
k’amshin turarensa da ya mamaye wajen. Amra ta lumshe ido a hankali tana jin
wani farin ciki na ratsata da gaske Murad ya kusa zama mallakinta, ha’dadden
namijin da duk garin gabas ake zancen ha’duwarsa, ga ku’di ga mulki ga kuma
jarumtaka ta Soja. Idanunsa a k’asa suke don haka bai san da zuwanta ba. Har
sai da ta yi sallama. Ya amsa a ciki sai kuma haka kawai ya samu kansa da ‘dago
idanunsa take idanunsa suka sark’e cikin nata, wata nauyayyiyar ajiyar zuciya
ya sauke kafin ya murza idonsa sosai don tabbatar da cewa itace ba gizon da
idanunsa suka saba masa ba ne. Murmushi ta sakar masa tana tafiya a hankali
zuwa inda yake ta zauna daf da shi cikin tausashshiyar murya ta ce “Ina yini?”
Ido kawai ya zuba mata ya kasa amsa gaisuwar tata. Har ta gaji da kallon ta
d’ago tana kallonsa, ajiyar zuciya ya sauke ya ce “Ke ce?” Dariya ta yi tana
d’aga mata kai ciki son tabbatar masa da itace. Ya saki ajiyar zuciya ha’de da
lumshe ido yana jin duk wata damuwa da ta tattare ya cushe a k’irjinsa ta kau.
Farin ciki ya maye gurbin wancan bak’in ciki. Murna yake sosai da ya zamo itace
zata zama mallakinsa matarsa nan da lokaci ka’dan, hak’ik’a shi mutum ne mai
sa’a tunda ya auri matar da ta dace da rayuwarsa irin matar da yake buri da
muradin aure mai shekaru da hankali wacce ta san kanta ba k’waila ba. A hankali
ya furta Alhamdulillah. Shikkenan sai hira ta kaure tsakaninsu ya saki jiki
suka fara tsara yarda rayuwar auren su zata kasance da ma shirin bikin gaba d’aya. Wannan shine babin da ya bu’de zafaffiyar
soyayya a tsakaninsu yana jin itace maha’din rayuwarsa a yarda yake jin zafin
soyayyarta a zuciya baya jin akwai wani abu da zai saka ya rabu da ita.
_____\
Yarda Azimi yake gudu haka kwanaki suke tafiya kamar
k’iftawar ido, da gaske rayuwar duniya k’arewa take, ba tare da bawa ya sani
ba. A kullum kwanan duniya tafiya suke da ajalinka wasu su mutu wasu su rayu
rayuwa mai kyau, wasu su rayu cikin cuta da rashin jin da’din rayuwar haka
Allah yake so ba wai don baya son bawa ba sai don jarraba Imanin sa. Haka ne ya
faru ga ahalin Masarautar gabas Sallah na k’aratowa ana sake shirye shiryen
bikin Murad, har ya rage saura kwana d’aya kacal Sallah inda a ranar idine za’a
d’aura auren Murad Mukhtar Mai gabas! Da amaryar sa Amra. Duk da azimi ne hakan
bai hana bayyanar bak’i a ciki da wajen masarautar, duk wani hotel da ke garin
Gabas na ya cika da mutane mak’il kowa burinsa a ce da shi aka d’aura auren
d’an Sarkin gabas na farko. Tsananin yarda ake sanar da d’aurin auren ne yasa
duka mutane da ake arewacin k’asar nan Suka samu labarin auren. Hidima ake kala
kala ana yanka dabbobi iri iri da danginsu kaji da ma d’awisu. Fadar masarautar
gabas a kacame take haka duk wani mai fa’da aji ya halarci wannan gagarumin
d’aurin aure.
Filin idi ya cika mak’il da jama’a ko ina motoci ne, da yake
wajen Sallahr idin a cikin masarautar yake, mata manya da yara duk sun fito
sallahr don haka Najee da Nene ma suna cikin tawagar Fulani da b’atacciyar
shigarsu sun sha kyau cikin atamfa mai kyan gaske da Fulani ta d’inka musu.
Suka kuma sake narka bak’in da ke saka su muni a fuska. Haka kawai Nene ta
dinga jin wata irin fa’duwar gaba, don haka ta kalli Najee ta ce maza ki d’auko
min waya a cikin gida. Sai dai kafin ta mik’e ta fara jin sanarwar za’a d’aura
auren Yareema Murad da amaryarsa Amra. Itama Najeen nata gaban ne ya fa’di ta
runtse idonta tana jan Hasbunallah! Kamar daga sama aka dinga jin magana a loud
speaker “Kada a d’aura auren nan a matsayina na Uwar yaron na d’aura masa aure!
D’if masarautar ta d’auka aka fara neman mai maganar don maganar zuwa tayi
kamar daga iska. Can zuwa wani lokaci kowa yana cikin al’ajabi sai ga wasu irin
manyan motoci suna bayyana a cikin masarautar. Kowa ya zuba ido gani wani
babban bak’o ne wannan da yake tafe da jiniya ga motoci bak’ak’e wuluk da su.
Tsawon mintuna biyu kafin mutane su fara fitowa daga cikin motocin suka kewaye
mota d’aya suka zagaye ta kafin a bu’de tsaleliyar matar mai kama da larabawa
saboda tsabagen kyau ya fito daga zabgegiyar motar. Idanunta sanye da wani
bak’in glass. Da nik’ab. Kai tsaye babbar runfar da Sarkin Gabas yake zaune ta
isa. Duk mutane suka zuba mata ido. Shi kansa Sarkin kallonta yake da mamakin
wace mai k’arfin halin ce da har take kiran kanta da Uwar Murad! Gefe guda ma
Nene mamakin take ta yarda tana zaune wata can daban take kiran kanta matsayin
Uwar d’anta?
A gaban Sarkin ta tsaya bata cire nik’ab d’in ba ta ce “Da
gaske Ni ce Uwar Murad! Ko yanzu ka tsaga jikina zaka tarar da jininsa don haka
na d’aura masa aure da zab’i na, ban amince ya auri yarinyar da kuke son ku
aura masa ba. Yau ce ranar da ya kamata na bayyana kai na. Ta fa’da tana yaye
fuskarta. Wani irin shock mutanen wajen suka shiga, musamman Nene da take zaune
kusa da Fulani tsananin kamannin matar da su Murad ya bayyana Muraran ba mai
sai ta furta ba, ko yanzu ta saka saje da gemu za’a iya cewa Murad ce ko
Jaheed! Mutane da dama bayyanar fuskar
matar ya girgiza tunaninsu hatta Sarki sai da ya yi suman zaune idanun sa cikin
na matar da kai tsaye za’a kira Murad carbon copy…….
K’arshen Book 1. Book 2 is not free π₯°
Kash nima mutuwar zaune na yi biro na ya kub’uce daga
hannuna idan ya tabbata wannan ce Uwar su Murad ita kuma Nene wacece? Tabbas
akwai cakwakiya kuma duk warwarar na cikin littafi na biyu, wace mata aka
aurawa Murad?
Don huce takaici biya 500 kai tsaye cikin asusun banki kamar
haka 2118666253. UBA. Sai ki tura shaidar biya a 08033748387. Sai na ji ku!
Special 1k. Mutanen
amana da basa gajiya da yi min kara. ππ₯³
JIKAR NASHE. Akwai