\
BABI NA 1
Not just the
beginning
Rayuwa cike take da tarin Ζalu-bale, takan zo wa kowanne Ιan'adam
ta mabanbantan fuskoki. Bawa ya karΙi yadda rayuwar ta zo masa ya kuma yi
ΖoΖarin kiyaye dokokin ubangiji shine zai mori rayuwar, akasin haka kuma zai iya
faΙawa ga halaka yayi biyu babu, shi ba da jin daΙin duniyar ba haka kuma
lahirar ma bai same ta ba.
A cikin duhun alaΖa mai cike da ruΙani, soyayya ta fara ne
da kalma Ιaya tak, amma ta Ιarke da tambayoyi dubu. Shin soyayyar za ta iya
tsira cikin sirrin da ke Ιoye tsakanin zukata biyu? Ko kuwa RIKITACCIYAR ALAΖA
zata rusa komai kafin gaskiya ta bayyana?
Pepperdine University Rick J. Caruso School of Law,
Pacific Coast Highway, Malibu, California.
Babu kowa a makeken hall Ιin nasu na Ιaukar karatu sai ita Ιaya
da ke zaune a seat Ιinta, gabanta kuma wani makeken textbook ne sai kuma jotter
da take rubutu a ciki, laptop Ιin da ke gabanta ta Ιaga kai ta kalla sannan
tayi jotting wani part na abun da ta karanto daga laptop Ιin.
Gaba Ιaya hankalinta ya gama tafiya kan karatun da take yi, kyakkyawa ce sosai, a lady in her 25's, sanye da cream veil d tayi rolling saman kanta, wearing a navy blue blazer a x crisp white blouse sai kuma paired tailored black trousers da ya sauΖa ka high heel takalminta, which is also navy blue in color.
Siririn tsaki ta ja jin vibration na wayarta da ke kan desk
alamun kira ne, kamar ba za ta Ιaga ba sai kuma ta miΖa lallausan hannunta ta Ιauko
wayar. With confusion on her face tayi picking call Ιin tare da karawa a
kunnenta. Cikin harshen Hausa da ba za ka taΙa tunanin budurwar na ji ba tace
"Haba Muneebah! Ko sallama ba za ki yi ba sai ki hau Ni da faΙa? Ok, I'll
be coming out right now, mu haΙu a waves cafΓ©
ok" hanging out call Ιin tayi tare da ajiye wayar tana sauΖe ajiyar
zuciya. Gucci brand school bag Ιinta ta ciro daga locker Ιinta ta fara tattare
komai nata, bayan ta gama ta goya jakar sannan ta fito hannunta riΖe da wayarta
cikin takunta irin na Ζasaitattun mutanen nan da suka gaji da wayewa.
Waves cafΓ© ta nufa
kai tsaye dialling Muneebah's digits and luckily Muneebah saw her from where
she's sitting. Hakan yasa ta Ζaraso har wurinta suka Ζarasa tare da zama daidai
lokacin da aka yi delivering drinks Muneebah ordered from DoorDash.
"Fisabilillah Imaan, tunaninki abun da kika yi kin
kyauta? I've been waiting for you since amma kika shige abunki kamar kin fi
kowanne student seriousness huh?"
Imaan, who's absentmindedly looking at Muneebah ba ta ma san
me take faΙi ba.
"Huh! Ya Salam!" Muneebah ta furta tana dafe kanta
tare da Ιaura hands Ιinta kan Imaan's shoulder, making her zone out for a bit.
"Haba friend, when will you let fate decide eh? By now
you have to accept the cards and find peace for yourself mana, you're ending in
stalemate matuΖar ba za ki amshi destiny Ιinki ba." Imaan ta Ιago manyan
Idanuwanta ta dubi Ζawar tata, tabbas abun da Ζawarta ke faΙa is nothing but a
naked truth, me yasa ta gagara coping ne after all that happened?.
"Kin yi shiru Imaan, ba kya ganin hakan da kike yana
affecting health Naki?"
With tears rolling down from her eyes ta fara magana cikin
raunin murya "Muneebah na sani, i know it wollah, na rasa me yasa na
gagara mancewa da komai, ina jin kamar Zuciyata za ta tarwatse Muneebah."
Cike da tausayawa Muneebah ke patting bayan Ζawar tata.
"You have to, friend, dole ki mance da komai, ki yi
abun da ke gabanki, ina tabbatar miki da cewa the day will come when those who
opposed you will return, humbled and willing to mend the bridges they once
burned, and make amends for the damage they caused."
Ajiyar zuciya Imaan ke sauΖewa a jejjere while Muneebah is
wiping the tears da ke fuskar Imaan, with so much concern, Muneebah said
"Let's raise a glass to new beginnings. Sip, savor, and let the past
dissolve. Today, we focus on the present, and craft a future that's brighter
than yesterday." Ta miΖa mata glass cup Ιin da ta zuba drink a ciki. Babu
musu ta karΙa tare da kafa kanta ta fara sha, Muneebah is indeed a blessing to
her, Muneebah is beyond a friend, but a sister from another Mom, Ζ΄ar'uwa ce da
take da gurbi na musamman ciki zuciyarta musamman da tata Ζ΄ar'uwar ta kasance
jarrabawarta.
Shiru suka yi na tsawon wani lokaci, Muneebah trying to erase the pain and bring back her
smile tace "That's My weak friend, sakaliya kawai." Kamar ba ita ke
hawaye ba minutes back ta harari Muneebah without a word from her. "Don
Allah ki daina hararata da wannan Ζwala-Ζwalan idanuwan naki masu ban
tsoro."
"And you now say I'm weak while kina tsorona ke
kuka"
"That's it friend, yaushe za mu Ιan fita ne kam?"
"Mu fita ina ke nan?" Looking utterly bewildered
Muneebah tace "Ina ake zuwa? Beach, bars....."
"Kar ma kiyi wasting saliva Ιinki mentioning non
visitable places to me Muneebah, you know ba na da buΖatar hakan ai."
Muneebah tace "Ni kuwa nasan kina da buΖatar hakan
Imaan, ziyartar wurare zai iya mantar da ke abubuwa da yawa, it can erase your
past Imaan."
Ba wai don ta yadda ba tace "To na ji."
"Ban gane kin ji ba Imaan?"
Kamar Imaan za ta yi kuka saboda Ζosawa da kuma gajiyawa da
surutun Muneebah tace "Ah beg Muneebah, ki taimaka ki yi shiru haka
nan."
A Ιan fusace Muneebah ta miΖe kamar za ta bar wurin tace
"Tun da damunki nake friend, have some space plus peace kin ji!;" za
ta wuce taji Imaan Ιin ta riΖo blouse Ιinta, cikin Muryar roΖo tace "I'm
sorry friend, I don't mean any harm, please dawo, na ji za mu je beach Ιin,
ok?" Dariya Muneebah ta saki sannan tace "Deal?" Tana haΙe index
finger Ιinta da middle finger wuri Ιaya kamar yadda yara ke yi in za su yi
alΖawari. Imaan ta saka index finger Ιinta
tsakiyar yatsun Muneebah tana faΙin "Deal" daga haka ta dawo ta zauna
suka ci gaba da hirarsu wacce rabi da kuma quarter Muneebah ke yin kayarta,
Imaan only smiles, and gives short answers when necessary. Cikin lokaci kaΙan
huge percent na damuwarta faded away. Daga nan kai tsaye apartment Ιin Imaan
suka wuce wanda ke George page residential complex. Dukkansu wanka suka yi,
suka cire wadancan professional attire Ιin suka sauya zuwa abayas wanda duka na
Imaan Ιin ne. Sai daf da Magrib Muneebah Muneebah suka fito saboda ride Ιin da
tayi requesting via Lyft ya iso, sai da ta raka ta suka yi sallama tukun ta
dawo room Ιinta.
Kamar ko yaushe dai haka ta zauna shiru cikin Ιakin nata,
gajiya da zaman da tayi yasa ta janyo school bag Ιinta ta fitar da HP laptop Ιinta,
jotter da kuma textbook Ιinta tana son Ζarasa karatun da ta fara Ιazu Muneebah
ta katse mata. At first she's enjoying every bit of the study amma daga baya
kamar an zuba dusa a brain Ιinta taji ta daina fahimta, hakan ne ma yasa ta
miΖe ganin time Ιin IshΔ ya yi har dare ya fara, sallarta tayi sannan ta dawo
da niyyar karatun ko zai shiga this time around, but to her suprise da ta fara
fahimtar abu making progress sai kuma taji ta daina gane komai.
Ζarar da cikinta yayi yasa ta tuna da tun drinks Ιin da suka
sha a Waves cafΓ© ba ta Ζara saka komai a cikinta ba, sauran abincin da Muneebah
ta girka Ιazu ta Ιauko taci, sannan ta sauya zuwa night dress tare da wanko
bakinta. Tattare takardu da laptop Ιin tayi ta mayar da su study area, sannan
ta dawo ta kaΙe bedsheet Ιin. Kwanciya tayi ta karanto addu'oin baccinta, daga
nan ta lumshe idanuwanta da niyyar bacci ya Ιauke ta sai dai to her suprise,
babu bacci babu alamarsa sai ma saΖa da sincewa da zuciyarta ke yi, at last
baccin ya Ιauke ta without her knowing.
***********************************
Yau ta kasance Safiyar Litinin, misalin Ζarfe bakwai da
mintuna arba'in da biyu, 7:42am, Matashiyar budurwa ce Ζ΄ar kimanin shekaru goma
sha bakwai ke kai kawo cikin Ζaramin gidan nasu wanda ta gama share shi tsaf ga
shatin tsintsinyar ya bada wani sample wanda ya mugun Ζawatar. Tsintsiyar ta
ajiye ta nufi bakin verandar da randunansu irin na Ζasa ke jere su bakwai rus!.
Baho ta cika da ruwa ta nufi bayi da alamar dai wanka zata yi, mintuna kaΙan
kuma sai ga ta ta fito sanye da hijabi tana rawar sanyi.
A haka ta nufi ciki verandar da ke Ιauke da Ζananun Ιakuna
huΙu rus dai-dai rayuwa irin ta talaka. Ζaki na Ιaya, na biyu ta shiga, tsawon
wasu daΖiΖu kuma sai ga ta ta fito sanye da wata koΙaΙΙiyar atamfarta mai ruwan
ganye (green) da Kuma fari, green colour Ιin duk ya koΙe haka farin ma ya koma
milk colour sai dai babu alamar datti jikin kayan.
Hijabinta milk colour mai taushi Ζirar yadin tayebo ta Ιauka
tana shirin sakawa, Muryar mahaifiyarta da ke riΖe da cup a hannunta ta dakatar
da ita.
“Imaan ga kokon ki samu ki sha tunda baki iya jiran Ιumamen
yayi zafi”
Kwantar da kai matashiyar budurwar da aka Ζira da Imaan tayi
tare d juya manyan idanuwanta gare sol sannan tace “Mami!” sai kuma ta tsaya
alamar ta Ζosa da ta fita daga gidan “Mami takwas ta kusa cika kuma kin san
basu son makara”.
Wata tsohuwa ce ta fito ita ma daga cikin Ιaki cikin Ιakunan
d ke jere,, idanunta Ζur akan su ta wani riΖe haΙa tare da yakutsa fuskarta da
ta yamutse, kamar ta ga kashi ta tsartar da yawu tana harare-harare ita kaΙai.
Jin batun da uwa da Ζ΄ar ke tattaunawa akai yasa ta ja dogon tsaki da ya sanar
da su isowarta.
“Kema Rahina akwai ki da shegiyar jaraba, ina ce dai
yarinyar na cewa tayi ba za ta sha ba? yo ki barta haka nan mana, yarinya sai
shegen kafiya ya arnan farko, mtsss”
Sai kuma ta koma Ιakin tana Ζara jan labulenta.
Murmushi Mami tayi tana kallon Imaan da yanayin fuskarta bai
wani sauya da maganar Dadan ba. Cikin ranta kuma tana Ζara fatan shiriya ga
sirikarta akan wannan hali na banbanci da take nunawa tsakin jikokin nata.
“Maza karΙi ki sha Imaan sai ki wuce”
Murmushi kawai Imaan ta saki sannan ta amshi cup Ιin daga
hannun Mami tana mai zama kan wani babban dutse da ke tsakar gidan, tas ta
shanye kokon, ganin Mami na kanta har lokacin yasa ta yi murmushi tace “Na gode
Mami, bari na wuce don har na makara yau ma”
Mami ta ce “To Allah ya tsare Imaan, ki kula da kanki.”
“Ameen Mami” ta amsa mata tare da ficewa daga gidan tana
zuba uban sauri. Allah ya taimake ta da wuri ta samu mai adaidaita ya wuce da
ita.
SOHAAN SNACKS & BEVERAGES
Ζatoton gate Ιin ta nufa cikin ranta tana addu'ar Allah yasa
kada ta haΙu da CEO na wurin aikin nasu.
Da baba Mai gadi wanda ke zaune a bakin veranda na Ιan
tsukukun Ιakinsa ta ta fara cin karo, cike da nutsuwa ta gaida shi, shi kuma ya
amsa mata yana washe baki. Ganin kusan kowa na a bakin aikinsa yasa tayi murna
don tsira da tayi daga punishment sai dai takunta uku zuwa huΙu, a na biyar Ιin
ta ji Muryar MD na kiran sunanta “Imaan”.
Sai da ta zaro idanuwa alamun dai ba ta yi tsammanin Ζiran a
dai-dai lokacin ba, a tsorace ta juyo tare da Ζarasawa inda yake tsaye, kanta
duΖe tace “Ina kwana sir”.
Cikin sakin fuska ya amsa da “Lafiya Ζalau! Imaan jagorar
tawagar makararru ke nan, yanzu ake ganinku kenan” ya Ζarasa in a cool tone
yana dubanta. Ζasa ta Ζara yi da kanta tana murmushi tace “I'm sorry sir”
Dariya MD yayi yana faΙin “Oh ni Isma'il, ina ganin ikon Allah, laifin me kika
yi ne haka?” ya tambaye ta sounding so playful, cikin sanyin murya Imaan tace
“Sir na makara ne amma wallahi ba da son raina ba ne.” Unlike before, In a
serious tone yace “Imaan ya kamata ki rage wannan late coming Ιin naki ba don
komai ba sai don shigowar CEO ba tsammani, kin san ba wani Ζyale ki zai yi ba,
don shi sauya ma'aikata a wurinshi is not something hard.” kai ta langwaΙar
tare dafaΙin “Ayi haΖuri sir, zan gyara da izinin Allah.” murmushi MD yayi yace
“To Allah yasa.”
“Amin” ta amsa masa tana Ιago idanuwanta. Daga haka yace “Ki
je ki kama naki aikin ko?”
Kai kawai ta gyaΙa daga baka ta bar wurin tana Ζara saurin
tafiyarta.
Kai tsaye tafkeken
building Ιin da ke Ιauke da Ιan Ζaramin signboard ta nufa a maΖale jikin ginin
wurin ta sama signboard Ιin yake, a rubuce kuma mai karatu zai ga: SNACKS
CENTRE. Ciki ta nufa tana Ιan sassarfa, da sallama a bakinta ta shiga ciki
sai dai duk cikin mutanen da ke wurin babu wanda ya amsa mata kamar ba su ji
ba. Hakan kuma bai hana ta gaishe su ba a jumlace "Ina kwananku!"
wasu daga ciki ne suka amsa fuska sake wasu kuma na amsawa a daΖile kamar an yi
musu dole. Madam Talatu da ke bin Imaan da harara tace “Sai shegen iya gaisuwa
kamar ita tafi kowa tarbiyya, mtss.” kanta ta sunkuyar ba tare da tace da
ita komai ba alamun dai jiran umarni
take daga Madam Ιin. Harararta ta Ζara yi a karo na ba adadi kafin ta ce “Ku
tashi ku fara aikin ku tun da ta zo.”
A tare sauran ma suka miΖe ganin hakan yasa itama Imaan yin
gaba. Ζakin da suke aiki ta shiga sauran suka biyo bayanta.
Federal University of Health Sciences AZARE
FUHSA, Radiography Department
11:00am
A gaban makeken ginin da ke Ιauke da rubutun
"Radiography complex" wasu kyawawan Ζ΄an mata guda uku ke tsaye suna
riΖe da littafa manya da kuma handouts alamar daga lectures suka fito.
_Untouchable gang_ kenan, Ζ΄an mata masu tashe da ji da kansu
a Radiography Department, ba su fiye shiga sabgar kowa ba saboda yadda suke
tsananin ji da kan su da kuma bayyananniyar Ζyamarsu ga raini a rayuwarsu.
A tare suka wuce har suka kai ga cool down Ιin da ya zama
wurin zamansu, wurin da babu wani mahaluki da ke zama tunda suka fara zama
wurin saboda gudun tashin hankali da rigima duk da cewa a jami'a kowa ji yake
da kansa, kamar yadda kansu yake hayaΖi
haka na wasu ma ke yi amma su nasu hayaΖin daban yake shiyasa kowa ke shakkar
shiga sha'aninsu.
Bayan Ζ΄an matan sun zauna kowa ta zuba takardun dake
hannunta a kan table da ke tsakiyarsu. Ζ³ar farar cikinsu wacce bata cika Ζiba
ba ta kalle su sannan ta ce “Babes! Na gaji wallahi”
“Ba ke kaΙai ba Charity” Mai Ζibar cikinsu kuma gajerar su
ce ta bata amsa yayin da Ιayar kuma ta yi shiru fuskarta babu fara'a. Charity
ta dubi wacce ta bata amsar tana faΙin “Ramcy kin san Allah tun ba yau ba na
lura da Mr. Faruq son Ihsan yake, baki ga yau gabaΙaya idonsa cur kanta ba
kamar wani maye!.” Dariya su biyun suka yi yayin da da Ιayar kuma ke famar
danna wayarta Ζirar iPhone 11 pro max.
Sanye take cikin wata shegiyar ash color blouse wacce aka
mata ado da wani Black flower, sai kuma
wani Black expensive Palazzo trouser da ta saka, takalmin Ζafarta kuma wani
Black hill shoe ne. Kallo Ιaya zaka mata ka tabbatar da cewa kyakkyawa ce, uwa
uba kuma adon da ta caΙa kamar mai halartar wani taro ga kuma wani makeken
Black glasses da ya kusan Ιauke fuskarta, kana iya hango gashin kanta wanda ke
Ζyalli ta bayanta da ta sake shi Ζasa bayan sanya hular malafa (hat) a kanta
wacce ita ma Black colour ce.
Charity ce ta taΙo ta tana faΙin “Ihsan wai baki ji muna
magana akan mutuminki ne?”
Fuska Ιaure Ihsan ta ce “Huh! Dama ina da wani mutumi ne
hala?”
Dukan wasa Charity ta kai mata ita kuma Ramcy sai dariya
take. In da sabo yaci a ce Charity ta Saba da halin Ihsan.
“Banza, Mr. Faruq Nike nufi, wai baki ga yau gaba Ιaya
hankalinsa kanki yake ba?”
“Mtsss” Ihsan ta ja dogon tsaki “Zai yi ya gama ne Charity,
don ba Ni da lokacinsa”
Baki taΙe Charity ta ce “Ban gane zai yi ya gama ba Ihsan,
elaborate!”
Gyara zamanta Ihsan tayi tana duban Charity da Ramcy da suka
ba ta total attention nasu kamar masu Ιaukar karatu. Cinyar Charity da ke
gefenta ta Ιaura hannu tana faΙin “Charity kenan, ba kya ganin sam bai dace da
irin mijin da nake nema ba?, ba irinsa nake so ba Charity, ita Ramcy na san ta
fahimta” tana faΙin haka ta kalli Ramcy sai ta mayar da dubanta ga Charity.
“Tambayarki ta gaba
Charity ” ta idasa tana kannewa Charity ido”
Charity ta ce “Ai kuwa dai i no get you, Kinga Ihsan,
gaskiya guy Ιin yayi, ba kya ganin zai kula da ke ne? Please ki ba shi dama ya
gwada sa'arsa mana”
"Ido waje Ihsan ke bin Charity da kallo sannan ta ce
“Ban gane na bashi dama ya gwada sa'arsa ba Charity, rayuwar tawa kasuwa ce aka
ce masa?” shiru ta yi sannan ta Ιaura da “To bari kiji na Miki filla-filla, na
Miki simplifying equation Ιin da nake ganin kin kasa solving, Charity wannan da
kike gani ko Ιawainiyata bana tunanin zai iya Ιauka da gani, ke fa kin san irin
expensive life da nake so, in banda ma talauci da ke bibiyarmu ai da mijin da
nake hasasowa kaina rayuwa da shi zai kasance na daban ne, the one beyond
measure. Ke ni fa wallahi ina so na auri hamshaΖin mai kuΙi ne wanda zan huta
idan na aure shi, zan yi facala da kuΙi son Raina ba tare da naji zafinsu ba, a
to! Amma see this man, shi kanshi bai ishi kanshi ba, talkless of wata mata da
zai aura, ba ya saka wasu expensive kayayyaki ma, see wani yadi yau da ya saka
ko Babana yana da irinsa, ga wani takalminsa da ya lotse ta gefe ma, To ke
Charity in ban da abunki ma, irin kayan da Babana yake sakawa fa su na gani
jikinsa, wallahi ko ya fi maye maita Ni Khadija na fi Ζarfinsa."
Shirun da tayi ne ya ba wa su Charity damar fahimtar she's
done, Ramcy ce ta Ιan yi murmushi ta ce “Gaskiya ne Ihsan, baki yi kala da
bagidaje irin Mr. Faruq ba, Allah ba wai ina zuzutawa ba Ihsan ke kalar manyan
mutane ne, kalar zama gaban mota ne.” murmushi Ihsan tayi jin an gwaΙa ta ta
wani juya ido tace “Shiyasa kike burge Ni Ramcy, Charity ma na san yanzu ta
fahimci nawa jirgin yadda zai tashi right?” ta faΙa tana kannewa Charity ido.
Dariya kawai Charity tayi tace “Ai dole na fahimce ki irin wannan dogon sharhi
Ζawata. Yanzu dai ba wannan ba, magana ake ta latest iphone nace wai ya za'a yi
ne?” Ramcy tace “Gaskiya kam, ni kinga jiya Babe Ra'up ya tura min kuΙin saboda
Ζin kula shi da nayi jiya da yaje gidanmu.”
Zaro ido Charity tayi tace “Eye Ramcy babe?, kin mugun burge
Ni, Kin ga nima jiya da muka yi waya da Daddy har da kuka na, yanzu dai ya tura
min kuΙin da nake Miki batun."
Wani iri Ihsan taji cikin ranta tana tsinewa talauci da
gangarsa, maganar Charity ce ta sa ta paying attention Ιinta with her eyes
closed.
"Ihsan ki sauΖe apple ID naki yau in mun tashi Kinga
sai mu wuce tare, tund a kuΙin wurin Daddy zai ishe Ni sai na cika su karΙi na
hannunki kema ki fita da taki ko?”
Cike da farin ciki Ihsan “Da gaske Charity?”
“Ζwarai ma kuwa Ζawata” ta bata amsa a taΖaice.
Hannun Charity Ihsan ta riΖo tana kai kallonta ga Ramcy ta
ce “Ramcy ki taya Ni yi wa Ζawata godiya, wollah I'm speechless with this news,
thank you Charity, thanks for always being there for me, I really appreciate..”
Katse ta Charity tayi da faΙin “Kin ga bar wannan godiyar
Ζawata, you're super beyond that!, babes ku tashi mu fita mu ci abinci daga nan
sai mu wuce mu yi abun da zamu yi kowa na miΖa ta."
A tare suka miΖe suna tafe suna rangwaΙa har suka iso wurin
da motar Charity ke ajiye. Ba su Ιata lokaci ba kuma suka shiga ciki nan motar
tasu ta fice daga cikin FUHSA ta harba kan titi.
BABI NA 2
IMAAN
Cike da Ζwarewa take sarrafa kwaΙaΙΙiyar flour, surutun
abokan aikinta kawai kake ji amma ita hankalinta kwacakom na kan aikinta. Sai
wuraren 12:34pm ta samu kammala pancakes da kum cupcakes Ιin saboda haka ta
Ζarasa wurin Madam Salamatu don Ιaukar excuse su yi sallah. Lokacin da ta je ta
tarar da Madam Ιin zaune Ζafarta Ιaya kan Ιaya, kallo Ιaya ta mata ta kau da
kanta gefe cikin ranta kuma tana mamakin
son mulki da nuna isa irin na Madam. Kanta Ζasa ta ce “Madam zamu je mu yi
salla” idan da ginin Ιakin take ta yi tsammanin samun amsa daga gare shi, har
ta cire rai da samun amsar, ta juya za ta fita ta jiyo muryar Madam Ιin “Wannan
Ζ΄a Allah ya yi munafuka”. Ba ta juyo ba bare ta ba ta damar ganin wani sauyi a
fuskar Imaan tata kamar yadda ta so, wucewa can snacks centre ta yi, tare da
musulmai daga cikin ma'aikatan suka yi sallar daga nan suka koma bakin aiki.
Ζarfe 3:00pm dai-dai suka tashi daga aikin, babu Ιata lokaci
suka nufi wurin Madam Ιin don sanar da ita zasu wuce, ganin basu tarar da ita
ba yasa suka koma kowa ya Ιauki cupcakes, pancakes, doughnuts biyu-biyu, nan
kowa ya kama gabansa.
Tafiya take kanta Ζasa kamar wata Ιarauniya yayin da
hankalinta gabaΙaya ya koma kan tuna rayuwarta!, rayuwar da take ciki da kuma
tunanin irin wacce zata faΙa a nan gaba. A haka har ta iso unguwarsu, a layinsu ta haΙu da Mamman wanda ya matuΖar
takurawa rayuwarta da sunan soyayya.
Kanta ta Ιage kamar bata ganshi ba sai dai ganinsa gabanta
yasa zuciyarta yankewa.
“Haba Imaan,me yasa kike son wulaΖanta ni ne, Ni fa mai son
ki ne ko ba komai na cancanci mutuntawa daga gare ki.”
Cike da gundura da tsayuwar ta Ιan daidaita kanta har
lokacin kanta Ζasa tace “Kayi haΖuri Malam Mamman, Ni bana wulakanta mutane,
kowanne Ιan Adam daraja gare shi a wurina, amma zuwa yanzu ya kamata ka fahimci
cewa rayuwata da taka ba za su zo dai-dai ba, don Allah Mamman, ina roΖon ka
don Allah ka bar rayuwa ta haka, bana buΖatar kowa cikinta, na fi buΖatar
Ζarasa ta kamar yadda Ubangiji ya zaΙar min.” daga haka ta Ζetare shi ta wuce
tana goge Ζwallar da ke kwararo mata wacce har ta isa Ζofar gidansu ta gagara
tsaida ta. Wani yawu ta haΙiye tare da sauΖe ajiyar zuciya ta nufi cikin gidan
bakinta Ιauke da sallama.
Kamar dai yadda ta bar gidan tas haka ta tarar da shi,
idanuwanta ne suka sauΖa kan tukunyar da ke kan murhu, hakan ya tabbatar mata
da anyi girki kenan, murmushi tayi ta nufi Ιakunan nasu kamar yadda suke jere.
Ζakin Mami ta shiga, kwance ta tarar da ita kan gadonta, da
sallama ta shiga Mami ta tarbe ta da murmushi akan fuskarta tana mai amsa
sallamar tata.
“Imaan an dawo kenan” kai ta gyaΙa, Mami ta Ζara da faΙin
“Sannu da gajiya, in kin huta ga can abincinki a saman teburi.” murmushi Imaan Ιin
tayi tace “Na gode Mami Allah ya Ζara miki lafiya.” murmushi ne ya kasa barin
fuskar Mami, haka kawai take tsintar kanta cikin yanayi na nishaΙi da jin daΙi
idan tana magana da Ζ΄ar tata. Ajiyar zuciya Mami ta sauΖe sannan ta amsa mata
addu'ar tata “Amin Amin Imaan”.
Shiru ne ya wanzu na wasu daΖiΖu kafin Imaan ta miΖawa Mami
ledar da ke Ιauke da snacks Ιin tace “Ga shi Mami.” baki riΖe Mami take kallon
Imaan Ιin da sauri tace “Ni kam Imaan ban san wace irin zuciya kike da ba, kin
ga yanzu dai ki wuce da abunki can Ιaki ki adana, da safe ai kafin ki tafi aiki
sai kike ci tunda kin ga ba da wuri ake Ιaura Ιumamen ba.”
“Bani nan!” Dada ta shigo Ιakin kamar wacce aka koro ta kuma fizge ledar hannun Imaan Ιin. “Munafukan
Allah ta'ala, yo munafukai mana, ke Rahina anya za ki gama da duniya lafiya
kuwa?” shiru ta Ιan yi tana sa hannu cikin ledar ta Ιauko wani Ζaton doughnut
ta gutsira sai kuma ta mayar da kallonta kan Mami.
“Haba! wallahi kin ji kunya Rahina, wato shine zaku Ιuya a Ιaka
kuna cin daΙi ke da wannan yarinyar taki
mai irin halittarki?" Ζan Ιaga ido Mami tayi ta dubi Dada don tabbatar da
abun da Dada ta faΙa, yaran da suke kamanceceniya da juna yau kuma ita ke
jingina siffarsu da ita? "Mu kun bar mu ko oho, shalele ma da bata cin
wannan girkin namu ai ita ya kamata a ajiyewa. Na san in ta dawo za ta ji daΙi
in na bata.” tana gama faΙar haka ta fice waje tana Ζ΄an surutanta.
Murmushin da yafi kuka ciwo Mami ta yi tana kallon Imaan
wacce kanta ke Ζasa, cike da son Ζarfafa mata guiwa ta kamo hannunta ta haΙa da nata sannan ta Ζira
sunanta a raunace. “Imaan” kasa Ιagowa Imaan Ιin tayi don ko kaΙan ba ta so
take nuna rauninta a idon mahaifiyar tata musamman da ta tabbatar a wannan
lokacin ko shakka babu Mamin kuka take “Haka Ζaddarar rayuwarki ta zo Miki,
kaka da kuma Ζ΄ar uwa su ne ko yaushe ke son Ζuntata Miki, Amma ki Ζara haΖuri
wata rana sai labari, Ni kaina haΖurin nake da Dada tsawon aurena da
Mahaifinku, ki Ζara jurewa kinji?”
Kai Imaan ta gyaΙa, Mami tace “Yauwa Ζ΄ar albarka maza tashi
ki je ki ci abincinki nasan kin gaji sosai”
Imaan ta amsa da "To"
Daga haka Imaan ta miΖe tayi waje, abincin ta Ιauka sannan
ta nufi Ιakinsu, bayan ta ci ta watsa ruwa tare da yin alwala, kan sallayar da
tayi sallar Asr a nan baccin gajiya yayi awon gaba da ita kamar dai koyaushe.
The Untouchables
Suna fita daga school Ιin suka hau hanya, a _Salama
restaurant_ suka tsaya suka ci abinci, daga nan kuma suka wuce _Nour plaza_ don
yin abun da ya fitar da su. Haka dai suka gama siyayyar wayoyinsu, cike da
farin ciki suka fito suka nufi motarsu. G.R.A suka fara nufa aka ajiye Ramcy
daga nan kuma suka yanko hanyar ajiye Ihsan.
Unguwar Odoji suka yi, a bakin titi motar ta yi parking, Kasancewar mota bata shiga
layin yasa Ihsan Ιin ficewa ko sallama ba ta yi wa Charity ba sai famar sakin
tsaki take “Tsiyarka da unguwar talakawa kenan! Ni wallahi na tsani unguwar nan
tamu.” sai yamutsa fuska take tana Ζara lanΖwasa jikinta. Dabar samarin da ke
bakin shagon provision Ιin ta duba ta cikin glasses Ιinta sannan ta saki Ιan
Ζaramin tsaki ta ja tana mai ci gaba da tafiyarta kamar ba za ta taka Ζasar ba.
Mutum uku da ke kan benci a bakin shagon suka dube ta suna
kaΙa kai. Faisal da yaji ba zai iya shiru ba ya dubi Ιaya daga cikinsu yace “Kai kunga me na gani kuwa?”
“Kowa ya gani ai” Mu'azu ya bashi amsa kai tsaye “Ai ni
Faisal wannan yarinyar wallahi ko sadakar aurenta aka ba ni ba na so, yarinya
ba Ζ΄ar uban kowa ba sai mai kasa kayan miya akan tebur amma ta bi ta addabi
jama'a da fitsara kamar wata Ιiyar gwamna!” sai kuma ya taΙe baki yace “Dubi fa
shigar da take don Allah, Allah dai wadaran naka ya lalace!”
Sa'id wanda bai ce komai ba cikinsu shi ya buΙe baki ya ce
“Ku daina irin haka fa! Ku faΙi alkhairi ko kuyi shiru!”
“Haba Sa'id, ai dole mu jajanta wannan al'amari tunda dai a
yankinmu yake faruwa, amma wannan yarinya ai abar a tsinewa ce” Faisal ya bashi
amsa.
“To in dai kuwa haka ne ina ga gara ku sami yarinyar ku mata
nasiha ba wai kuna gulmarta ba.”
“To shikenan Alaramma, ya wuce mun yi shiru.”
"To Allah dai ya kyauta."
A Ιangaren Ihsan haka ta wuce wannan dabar tana yatsina
fuska sai kuma sakin tsaki take a kai a kai, Kamar ba za ta taka ba har ta
karya corner Ιin layinsu, wasu yara da ke kwashe kwatar gidansu ne basu sani ba
suka fatsa mata. Wani uban ashar ta lailayo musu tana kai dubanta gare su,
sanin halinta yasa yaran suka fara zare idanuwansu kowa yana saddaΖarwa yau
kashinsa zai hura wuta.
Glasses Ιinta ta zare ta Ζara dubansu a hasale tace “Ba ku
da hankali ne zaku watsa min wannan Ζazamar kwatar taku mai shegen wari?”
Cikin yaran wani yace “Kiyi haΖuri Aunty Ihsan, ba da sanin
mu bane.” hakurin da yaron ya ba ta yasa ta Ιan sauΖo sai kuma tayi tsaki tare
da wucewa tana yamutsa fuska. “DaΙina kenan da unguwar talakawa, kai talaka bai
yi ba, ace big girl from the untouchables ina rayuwa a wannan trash Ιin,
gaskiya da sakyal.”
Dai-dai wani Ιan Ζaramin gida mai Ζofar Ζarfe wacce fentin
jikinta ya gama koΙewa jikinta duk tsatsa alamar ruwa ya bugi rabonsa ta tsaya,
Ιata fuska tayi tana nufar gidan a zahiri tace “Shit!, how on earth will i
continue living in this trash eh?, Wallahi da mutum na da damar zaΙar familyn
da zai fito da babu abun da zai sa na fito daga wannan tsatson, tsatson
talakawa!" Ta tofar da yawu sannan ta yamutsa fuska wanda hakan kamar ya
zama mata Ιabi'a matsawar ta samu kusanci da wani wanda take ganin bai cancanta
ta kasance kusa da shi ba.
Ko gajiya da tsayuwar da tayi ne oho sai ta furta "I
must find a way out!” ending in so much disgust! ko sallama ba ta yi ba ta
kutsa kai cikin gidan ranta Ιace, da tukunyar aluminium da ke kan murhu ta fara
cin karo ai kuwa ta saki tsaki a bayyane tace, “Murhu, itace, mtsss”.
Tana takawa tana yatsina fuska ta nufi Ιakunan gidan, Ιakin
da ya kasance nata ta nufa tana nishi kamar wacce ta yini tana aiki, ganin
Ζ΄ar'uwarta kwance a kan sallaya yasa ta saki tsaki tana yamutsa fuskarta kamar
ta ga kashi. “Kai talauci!, me nayi maka ne kake bibiyata haka?, in banda
talauci ina Ihsan from the untouchables za ta haΙa Ιaki da wannan trash Ιin mai
bauta a Company?” ganin ba mai ba ta amsa yasa tayi shiru tana cigaba da
yamutsa fuska musamman daya kasance wacce take wa maganar ma ko alamar ta ji ba
ta nuna ba talkless of her saying a word.
Luxury handbag nata ta ajiye a corner nata, sannan ta fara
rage kayan jikint, daga nan ta je ta Ιebi ruwa a bucket ta nufi Toilet Ιin nasu
irin na gargajiya, bayan ta yi wankan ta dawo sannan ta buΙe akwatinta da ke
shaΖe da kaya ta ciro wata light riga ta saka. “Huh!” Ihsan ta furta tana buΙe
jakar ta fito da sabuwar wayarta ta saka charge, daga nan ta koma kan
katifarta. Dada ce ta shigo buguzun-buguzun kamar doki hannunta riΖe da leda ta
nufi katifar Ihsan Ιin sai washe baki take.
Ko da ta isa kusan Ihsan Ιin a Ζasa ta zauna tana miΖa mata
ledar hannunta tare da faΙin
“Shalelena ungo wannan” da sauri Ihsan ta karΙi ledar tana
yamutsa fuska tace “Dada mene ne wannan Ιin?”
Washe baki Dada tayi tana faΙin “BuΙe dai ki gani da kanki,
kayan kamfanin da wannan buzuwar ke aiki ne, ko da ta dawo suka rufe Ιaki da
wannan uwar taki za su cinye, cikin Sa'a sai Allah ya tona asirinsu shi ne na
karΙe don wannan dai da ke ya dace.”
Murmushi tayi a karo na farko wanda ya matuΖar Ζasar fuskar
Tata ya kuma yi mata kyau kafin ta ce “Shiyasa nake Ζara sonki Dadata, yanzu
dai tashi ki je ina son hutawa”
“Ah ai babu komai, to huta abunki, wannan makaranta taku mai
uban nisa ai ko a jirgi kake zuwa sai ka ji jiki”
Haka dai Dada ta fice tana sukuntunta.
4:20pm, Dundas Roncesvalles Peace Garden, Bloordale
village, Toronto, Canada
Iska ce sassanya take kaΙawa wanda iya hakan kan sanya
zuciyar mazauna wurin cikin nishaΙi ga kuma korayen tsirrai da kuma other
ornamental plants da suka Ζara haskaka wurin, irin wannan wuri shi ake
shawartar masu matsalar gani su yawaita ziyarta saboda idanunsu su Ζara Ζarfi.
Ta Ιangare guda kuma wasu kyawawan samari ne guda biyu zaune
kan restchairs Ιin da ke kewaye da table Ιin sai kuma wani yaro da ba zai haura
7years ba a duniya. Daga cikin samarin
ne Ιaya ya ce
“Bloodies!” sai kuma yayi shiru yana kallonsu. Yaron da ke
tare da su ne ya ce “Yea Ya Jahaan, what's up?” ya Ιan Ιage masa gira.
“Guess what Asim!” Wanda aka Ζira da Jahaan ya faΙa yana
tattara hankalinsa ga Asim Ιin.
“Za mu fita Paris Bakery & Pastry tonight, Allah sa haka
ne” ya bashi amsa yana kwaΙe fuska. Ζan harara Jahaan ya aikawa Asim Ιin da ke
washe baki sai kuma ya Ιan kwaΙe fuska saboda hararar da Jahaan ke binsa da
ita.
“To foodie! We're going no where to be frank, Kai in ba
batun ci aka yi ba ba ka dariya ko?, now guess what for the last time, in Ka
kasa kuma...”
Murmushi Asim yayi yana Ιaga kansa sama tare da Ιaura index
finger nasa a gefen goshinsa alamar dai tunani yake. Ba tsammani ya ce “Daddy
ya sanar da kai we're going home abi?” ya idasa yana Ιage gira. Ζan haΙe rai
Jahaan yayi yana faΙin “Ka ci dai-dai amma fa tun da ka Ιage min gira sai nayi
punishing naka”
“I'm sorry Bro Jahan” ya faΙa da sauri yana kama kunnuwansa
da hannayensa biyu.
“Bana Ζarawa, ba da gangan nayi ba, I'm just eager to land
on my fatherland” ya faΙa yana Ιan shagwaΙe fuska alamar a tausaya masa.
Tsaki Ιaya saurayin da tun zamansu bai ce komai ba yayi shi
ya sa Asim Ζim ya rufe bakinsa. Sanin
kansa ne ba'a surutu a wurin wannan miskilin mutumin. Jahaan dai dariya yayi
yana faΙin “Ya Allah!” sai kuma ya dafe kansa kamar wanda ya manta wani abu.
“Ashe dai tare da kai muke, wallahi yanzu gabaΙaya mantawa
nake da muna tare musamman da Asim ya zo, unlike you he's friendly and nice.”
Wani kallo ya cilla masa mai Ιauke da jan kunne alamar ba
buΖatar Ζarin bayani. Dariya Jahaan yayi yana faΙin “Ka ji da kanka dai, Ni
wallahi nasan zanyi mugun missing Asim next dawowarmu, huh! Sai kuma mu Ιaura
da Sarkin miskilai Abuljalaal!”
MiΖewa tsaye AK yayi jin Jahaan na cika masa kunne da
hayaniya, hakan yasa shi ma Asim miΖewa yana riΖe hannun AK Ιin sai kuma ya langwaΙar
da kansa gefe yace “Ya Jalaal Are we good to go?” kai ya gyaΙa masa daga haka
duk su ukun suka miΖe zuwa katafaren Parking lot da ke Ιauke da motoci iri-iri.
Motarsu Ζirar Ferrari SF90 suka nufa, Jahaan a driver's
seat, Asim a back seat sai Arman by Jahaan's side.
Kai tsaye apartment nasu da ke a cikin MLS group of
companies suka nufa. Bai kula kowa ba ya shige abunsa nan su ma suka biyo shi a
baya.
Wanka kawai yayi ya sako wasu expensive Armani black shirt
sai kuma wando three-quarter white, sihirtaccen kyansa ne ya bayyana yayinda
wani kwarjini da izza ke bayyana a tattare da shi.
Kyakkyawa ne sosai, yana da hasken fata, kalar fatarsa bata
yi kama da na mutanen Nigeria ba hasali ma fatar tana yanayi ne da fatan
Arabians wato larabawa, bai cika Ζaton mai ba kuma kansa cike yake da baΖar
lallausar suma wacce ke sheΖi saboda tsantsar gyara da kulawa da take samu.
Idanuwansu basu cika girma ba amma suna da kyau sosai musamman ma haskensu da
ya Ζara fidda brown Ζwayoyin idanun nasa, hancinsa dogo ne, bakinsa launin pink
ne sai dai laΙΙansa na da kauri kaΙan. Kyakkyawa kuma lallausan sajen da ya
kewaye fuskar shi ya Ζara fidda ainihin kyau da tsarin halitta da Ubangiji yayi
masa, yanayin zubin halittarsa su ne ake wa laΖabi da athletes and giants, fa
tabΔrakallahu ahsanul khΔliΖin....
Kamilalliyar fuskarsa da ke nuna cikar kamala da kuma haiba
da Ubangiji ya masa baiwa ya Ιan sake jin sanyi na ratsa jikinsa ta kowacce
kusurwa. A haka ya nufi cikin MLS group of companies, bai tsaya ko ina ba sai
office nashi, nan ya fara aiki hankalinsa kwance.
Agogo Sarkin aiki kenan!, Abduljalaal Abubakar KuΙa,, the
one and only son to his parent and the CEO of the great company MLS (Malik
Lustre Sparkles) group of companies.
Babban company da ke da hannayen jari daga mabanbantan mutane. MLS na da
branches a Ζasashe mabanbanta, ciki kuma har da gida Nigeria sai dai wannan da
ke ciki Bloordale village shine Wanda aka fi ji da shi kuma sun fi yin
qualitative jewelleries of different types, sannan sarΖoΖi, awarwaro, Ιan
kunnaye, zobuna da kuma abun hanci da dai sauran kayan Ζawa na mata da wannan
Company ke yi suna da matuΖar inganci kuma babu Algus a cikinsu.
Alhaji Abubakar KuΙa da kuma Ζ΄an uwansa sun gaji wannan
sana'a ne ta sarrafa ma'adanai zuwa kayan Ζawa daga wurin mahaifinsu Alhaji KuΙa,
sai da kuma salonta da ya sauya gaba Ιaya sakamakon ci gaban ilimin kimiyya da
kuma fasaha. Su HuΙu ne a wurin mahaifinsu. Abubakar (Abie) shine babba, Nazif
(Daddy), Nasir (Uncle N) sai kuma Ζaramarsu Aminatu. WaΙannan Ζ΄an uwa guda huΙu
tare da Ζ΄aΖ΄ayensu su ke riΖe da MLS sai dai hannun jarin Abie na Musamman ne,
musamman a wannan reshe na Ζasar Canada, kaso 95 ya kasance mallankinsa. Sannan
akwai Ιan Ιan'uwan mahaifinsu, Alhaji Bashir (Papa) wanda kusan a girme sa'an
Alhaji Abubakar ne. Kuma ba ka taΙa banbancewa cikinsu, kansu haΙe yake a
zahiri.
Alhaji Abubakar KuΙa, kamar yadda ya gabata Ιansa Ιaya,
matansa biyu, Ummah, wato Hajiya Asiya ita ce babba, sai kuma Hajiya A'ishah
wacce ya auro ta daga Ζasashen Larabawa, Ummah
ba ta taΙa haihuwa ba, sai dai kuma hakan bai hana ta ta amsa sunan
mahaifiya ba kasancewar ita za a iya kira kai tsaye da mahaifiyar AK. Nazif KuΙa
na da mata biyu da kuma yara uku, Junaid, Nimra, Sai kuma Sabreen. Alhaji Nasir
KuΙa Wanda Shi kasuwancin bai wani dame shi ba ya fi bawa aikinsa na Shari'a
muhimmanci, matarsa Ιaya Ζwal sai yaransa biyu, Nihal da kuma Ayman. Sannan
Alhaji Bashir ma matansa biyu. yaransa huΙu shi kuma, Jahaan (JK), Safnah,
Manal sai Fauzan autansu.
Cikin wannan ahali akwai tsantsar soyayyar junansu da kuma
haΙin kai, sai dai kuma akwai wata irin Rikitacciyar alaΖa da ke sanya zukatan
wannan dangi cikin duhu da kuma Ζaulani. Wannan kenan!
MΔlik luxurious sparkles (MLS) group of companies,
behind Tavora International Seafood,
Bloordale village, Toronto, Canada.
12:00pm
Yadda mutane ke zirga-zirga a wannan katafaren Company zau
Ζara tabbatar maka da cewa babban wuri ne.
MLS group of companies babban company ne da yake da haΙin
guiwar wasu companies Ιin, Company ne da ake sarrafa ma'adanai da aka haΖo
kamar su Gold, silver, platinum, diamond da makamantansu izuwa kayayyakin ado
masu inganci kamar su sarΖa, awarwaro, zobe, Ιankunne, abun hanci, agogo da dai
sauransu.
Mamallakin wannan Company wanda ya kasance yana da kaso 95
(95%) na jarin Companyn abun mamaki baΖar fata ne, daga jahar Bauchin Nigeria,
wato Alhaji Abubakar KuΙa, the multibillionaire.
Zaune yake akan katafaren gadonsa yana danna system Ιin da
ke gabansa, he's super tensed hakan yasa ya rufe ta ya ajiye ta kan bedside
drawer tare da wucewa bayi ya Ιauro alwala.
Kusan kowacce rana haka take zuwa masa a rayuwarsa, bai rasa
ci, sha ko kuma kwanciyar hankali ba, amma a kowanne dare bacci yana Ζaurace
masa tamkar bawa ya tafi garinsu kaiwa saΖo. Ya daΙe yana jera sallar, daga
Ζarshe ya Ζare da witri, addu'a yayi sosai sannan ya miΖe ya koma kan bed Ιin
nasa. Tabbacin da yake da shi na baccin ba zuwa masa zai yi ba yasa ya rarumo
phone Ιinsa, ganin 12...past yasa ya fara hasashen lokacin a nan gida Najeriya.
Sassanyar ajiyar zuciya ya saki tare da shiga call logs Ιinsa, number
mahaifiyarsa, apple eyes Ιinsa ya Ζira cikin ransa yana fatan ta Ιaga kiran don
shi kansa zuwa yanzu ya Ζosa da irin karar da take nunawa a kansa, yana
buΖatarta, yana buΖatar kasancewa tamkar Ιanta, amma abun ya gagara, yana so
shima yasan irin alaΖar da ke tsakanin Ιa da kuma mahaifiyarsa, the feeling,
yes! The feelings!, He wants to feel it, but Ummie close all the ways.
Kamar dai yadda yayi tsammanin, Ummiensa ba ta Ιaga kiransa
ba, dama sa'arsa ya gwada, ajiyar zuciya ya sauΖe sannan ya ajiye wayar yana
lumshe idanuwansa.
That's how she's, haka nan Ummiensa take, tuj kafin ya
mallaki hankalin kansa yake ΖoΖarin ganin ya fahimci wani abu game da
rayuwarsa, sai dai ALAΖAR ta kasance RIKITACCIYA, babu wani sabo tsakaninsa da
Ummie, amma hakan bai rage ko da Ιigo ne na soyayyarta ba.
Odoji, Nassarawa B, Azare, Bauchi State
Ihsan
Tun da ta gama cin snacks Ιin ta kora da coke Ιin da ta taho
da ita sai ta janyo wayarta tare da kunnata. Few hours ta gama saita komai na
kai, wondering wai yau ita ce riΖe da latest iphone, fatanta dai Allah ya kawo
mata Ζarshen wannan mugun talauci na gidansu, don ita ala dole take ma zaune
gani take abun kunya ne a ce yau ga unguwansu, bare a gangaro izuwa wannan ruΙaΙΙen
gidan a ce a nan ne take rayuwa, “God forbid” ta furta can Ζasan maΖoshi, She's
wishing it not to happen, fatan ta a ce ta bar wannan matsiyacin gidan (as she
says) shiyasa ma ita a tsarin ta babu alaΖa da talakawa, samari ma in ta
saurara to sai rich kids, a taΖaice dai ta zama mai idon Naira.
BABI NA 3
Ringing Ιin da wayarta ke yi yasa ta dakatar da zancen zucin
tare da mayar da dubanta ga screen Ιin wayar. Ganin _SMFM_ yasa tayi picking
tana murmushi.
“Hello my charming prince ” ta faΙa tana gyara kwanciyarta.
A Ιaya Ιangaren ya amsa da
“My charming princess... how's your day?, Ιazu na kira ki
but your phone isn't reachable”
Murya Ζasa tace “Sorry my Man, mun je na sauya wayan ne ban
kuma kai ga charging nata ba hala time Ιin da ka Ζira, how're you doing?”
“Fine babe, ki ce munyi waya, dama kince you're updating
yours to the latest version, anyways dama kuΙin da zan tura Miki ne, I've been
searching for the account details na rasa, perhaps ban san na goge ba Please ki
Ζara texting min kinji?”
“Ok babu damuwa”
Daga haka tayi hanging out call Ιin sannan ta tura kamar
yadda ya faΙa tana murmushi kamar wata mai aljanu.
Slowly tace “Talauci, God forbid! ko sunansa ban son naji an
faΙi, Allah ka aurar da Ni wa mai kuΙi wanda zan yi facali da Naira ba tare da
jin zafi ba”
Imaan
Tun lokacin da wayar Ihsan
tayi Ζara ta farka daga baccinta sai dai tana tsoron tashi ta tarar da
Bala'in Ihsan, ta San halinta sarai, ba mutunci gare ta ba sai ta nemi
wulaΖanta ta a banza. Fitsarin da ya matsa ta yasa ta miΖe don ta je tayi ai
kuwa caraf Ihsan ta dakatar da ita.
“Ke kuma jakar Company ba na hana ki yi min laΙe ba?” Ιauke
da mamaki a fuskar Imaan ta dubi Ihsan Jin ta zo mata da wani sabon batu.
“LaΙen me kenan Ihsan?”
“Kinga Bana son zallar munafurci, Ni na faΙa miki da ki
daina kiran sunana haka with this dirty mouth of yours, Haba shi talaka ko ina
sai ya nuna halinsa, mtsss”.
Jijjiga kai kawai Imaan tayi ta fice ta barta tana
bambaminta ita kaΙai.
Ta dawo zata wuce corner nata Ihsan tace “Ke dalla jakar
Company dakata!” kamar wadda aka yi wa brake Imaan ta tsaya.
“Kin ji wayar da nayi ko?”
Cikin sanyin murya Imaan tace “Ya za a yi naji wayar da kike
yi kuma?”
A hasale Ihsan ta miΖe tayo kan Imaan da USB a hannunta.
“Munafuka wallahi kinji, na faΙa miki tun ba yau ba ki daina
min irin wannan laΙen naki na munafukai amma kin Ζi, wallahi yau mai raba mu
sai Allah” kawai sai ta hau Imaan tana zuba mata USB cable Ιin. Ciki uku tayi
mata kafin ta haΖura saboda Ζarar da wayarta tayi alamar shigowar saΖo, ita dai
Imaan bata ce komai ba duk da cewa a girme ta girmi Ihsan Ιin Amma in da sabo
ta saba da cin kashin da Ihsan Ιin ke mata gashi kuma babu damar ramawa tun da
goyon baya ta samu na yin hakan..
****************
Ganin lokacin salla da yayi yasa ya miΖe tare da fitowa daga
office nashi ya nufi masjid nasu da ke cikin Companyn. Bayan ya yi salla kuma
ya dawo, nan ya tarar da su JK suna ta hayaniya, tsaki kawai yayi ya wuce
bedroom nasa. Yana shiga yayi wanka, fitowar shi sanye da bathrobe da Kuma
farin towel yana goge sumarsa yayin da jikinsa kuma ke fidda daddaΙan Ζamshin
shower gel Ιin da yake amfani da shi, ya fara shafa creams Ιin da ke jere gaban
dressing mirror Ιin da zaka yi tsammanin na wata hamshaΖiyar mace ce mai ji da
kanta sai wayarsa tayi Ζara alamar neman agaji amma yayi ignoring, Ζiran
wayarsa da aka Ζara yi a karo na biyu yasa ya miΖe da sauri ya Ιauko ta sannan
ya dawo ya zauna kan stool Ιin da ke gaban mirror Ιin.
_Ummah_ ya gani rubuce, da sauri ya katse Ζiran don shi haka
Ιabi'arsa take, baya taΙa bari yayi waya da credit Ιin iyayensa. Ζara Ζira
yayi, jin ta shiga yasa ya sauΖe ajiyar zuciya tare da kwantar da kansa yana
lumshe idanuwansa.
Daga can Ιangaren aka yi sallama wanda ta sa ya Ιan buΙe ido
a zabure alamar dai ya Ιan faΙa izuwa duniyar tunani ne.
Cikin daddaΙar muryarsa ya amsa sallamar yana faΙin “Ummah!”
Daga can Ιangaren Muryar matar ta Ζara faΙin
“Sweetheart!” sai kuma tayi murmushi mai sauti tana faΙin
“Ka ga na Ζara Ζiranka though bamu daΙe da gama magana ba ko?”
Shima murmushi yayi wanda ya Ζara bayyana kyau da Allah yayi
masa.
“Kai Ummah, don't tell me you're missing me so madly”
Ζ΄ar dariya ta Ζara yi
ta ce “You guess it right son, I'm so eager to see you home shiyasa kaga na
Ζara Ζira, Abie Ιinka ya ce you're coming home in three days time”
Murya shagwaΙe kamar ba wannan gwarzon ba ya ce “Kai Ummie,
shine ki ka kasa mancewa? So kike ki sama kanki damuwa uhm?”
“No son” ta amsa masa “ just can't wait to see you, tun
yanzu ka faΙa min me da me zan shirya maka!" Shiru tayi tana nazari can
tace "Oh! I remember, your favourite?, zanyi maka snacks da yawa.”
Murmushi yayi ya lumshe idanuwansa sannan yace “You'll
always be my best Ummah, Bari na gama shiri, yanzu na fito daga bathroom”
Da sauri Ummie ta ce “Alright, ka shirya, i love you” sai
kuma ta yi masa kiss ta yadda zai iya jiyowa. Fuska sake shima yace “Love You
too Ummah” sannan ya mayar mata da kiss Ιin.
Ita ta fara hanging call Ιin, ajiyar zuciya ya sauΖe tare da
ajiye wayar kan dressing mirror sannan ya cigaba da rubbing creams Ιin da ke
jere gabansa Ιaya bayan Ιaya har ya kammala. Jallabiya ya sanya sannan ya fesa
turaruka har iri huΙu, _tom ford, kay Ali, coco noir, replica_ da kuma _Henry
rose_ tuni suka bada wani irin sassanyan Ζamshi mai tsayawa a rai, yana gama
fesawa ya Ιauki phone Ιinsa ya fito parlour. A nan ya tarar da su JK har
lokacin suna zaune sai uban surutu yake da Ζaramin yaro.
TaΙe baki yayi wondering why is JK acting immaturely, ya
rasa da wa zai yi surutun ma sai da Asim, 7years old child, Kai!. Haka dai ya
Ζarasa wurinsu fuskarsa babu yabo babu fallasa. Yana zama cike da tsokala JK ya
ce “Asim in munje ai zaka raka mu wurin budurwar tawa ko?” Asim yayi Ζasa da
murya gudun kada ya taΙo AK ya ce “Da wa da wa za mu je?"
Cikin muryar da ya tabbatar AK Ιin zai ji shi ya ce “Da AK” Ιan
zaro ido Asim yayi ya Ιan saci kallon Jalaal Ιin, ganin kamar hankalinsa ba ya
wurin yasa ya sauΖe wata nauyayyar ajiyar zuciya tare da kallon Jahaan sai kuma
ya kama bakinsa da hannayensa biyu yana zaro idanuwansa waje.
Ganin za su Ιata masa rai ne ya sa ya miΖe ya koma bedroom
tare da kiran Ummah, hira suka yi sosai har take sanar da shi akwai suprise Ιin
da za ta masa immediately ya dawo, he's super eager to see what's that thing.
KUΖA ESTATE, BAUCHI, BAUCHI STATE
Estate ne mai Ιauke da tsari gwanin burgewa, ba wani babba
ba ne can kasancewar ba su da yawa sosai, amma tsarinsa kaΙai mutum ya gani zai
so shima ya kasance cikinsu. Gini ne irin na zamani, ga kuma flowers bishiyoyi
iri-iri waΙanda ke tafiyar da damuwa da sanyawa ruhi salama da aminci. A Ιangaren
Alhaji Abubakar KuΙa wanda ke Ιauke da sassa uku, Ummah ce ta fito daga nata
sashen ta nufi sashen Ummie, kan Sallaya ta tarar da ita tana sallar walaha.
Fuska sake ta zauna akan kujera tana faΙin "Tasalla Sarkin salla, Allah
dai yasa muma kina tsunduma mu cikin sallar nan."
Sallama Ummie tayi sannan ta dubi Ummah tana murmushi, sai
dai ba ta ce komai ba don tana son yin wasu zikirorin, itama Ummah ba ta ji
komai da hakan, don in da wanda zai faΙi wace ce Ummie, to bayan ita ce, don
rayuwar da suka yi, babu wani abu na Ummie da ba ta sani ba.
"Ummah!" Ummie ta faΙa tana miΖewa tare da naΙe sallaya ta dawo gefen Ummah ta zauna.
"Kin ji wai Jalaal zai zo nan da kwana biyu?"
Shiru Ummie tayi na Ιan wani lokaci kafin ta saki wani
malalacin murmushi.
"To Ni ina zan sani Ummah Jalaal, nikam ai Ζ΄ar kallo
ce."
"Kamar ya Ζ΄ar kallo kuma ChubaΙo?"
Wani murmushin Ummah ta Ζara yi sannan tace "To mana,
idan ya zo na ganshi ai ko?"
"Hmm" Ummah ta gyara zama sannan tace "Lallai
Fulani dai sai ku, ki haifi abun amma kina juya masa baya?, Ko dan, mu da Allah
bai ba mu ba ai ga shi na kowa ma so muke"
Ajiyar zuciya Ummie tayi tana Ζara tausayawa Ummah bisa
wannan jarrabawar ta rashin haihuwa da Allah ya jarabce ta tare da fatan Allah
ya ba su ikon cinyewa. Cikin son danne rauninta tace "Ki daina faΙin haka
Ummah Jalaal, haihuwa ta Allah ce, yana baiwa wanda ya so ne, bari na tunatar
da ke, ita kanta haihuwar ga wasu ba Alkhairi ba ne, wasu sai ki ga Allah ya ba
su, amma silar Ζ΄aΖ΄an sai su saki hanya, don haka, ki saka a ranki muΖaddari ne
daga Allah hakan ma, ta wani wajen kuma ki Ζara gode masa da ya baki Ιa Ιaya
tamkar da dubu, a kowanne lokaci sannan feelings Ιin ya tasar miki Ummah
Jalaal, ki tuna da Ιanki Jalaal, don haifa miki shi kawai nayi, amma naki ne
halak malak, na san ko bayan raina, zai kula da ke ko ba a matsayin matar uba
ba, a matsayin wacce ta ceci mahaifiyarsa." Cikin cool and weak voice nata
ta kammala maganar tare da goge wasu siraran hawaye da suka zubo mata sannan ta
riΖo hannun Ummah, "Don Allah Ummah Jalaal, ki daina yi wa yaronki kuka,
sai nake ganin kamar ya gaza miki ne"
Jijjiga kai kawai Ummah ke yi tana kuma Ζara jinjina girman
sadaukarwar da ChubaΙo tayi mata, daga bisani ta iya furta "Na daina ChubaΙo,
na daina kuka, tabbas ke Ιin Ζ΄ar halak ce, haka zalika Jalaal, ku Ιin na daban
ne kasancewar ku kyauta ta Musamman daga Ubangiji zuwa gare Ni."
Hannu Ummie ta sa ta gogewa Ummah hawayen da ke kwance kan
fuskarta.
A wannan yanayin maigidan nasu ya shigo, tun daga yanayin da
ya tarar da su ya tabbatarwa kansa cewa labarin gizo ba zai wuce na koΖi ba, same time kuma yana Ζara
jinjina irin soyayyar da ke tsakanin ChubaΙo da Zulaihat tare da fatan ko wacce
kishiya ta rungumi abokiyar zamanta kwatankwacin yadda ChubaΙo da Zulaihat suka
kasance. Ganin kamar ba su lura da shi ba yasa ya koma sashensa.
Bayan Wasu daΖiΖu Ummie ta dubi Ummah, don ganin ta kawar da
damuwar da ke kan fuskar Ummah yasa tace
"Hala yanzu ma tashin ki daga barci Ummah Jalaal"
Ummah ta gyaΙa mata kai
"Za ki karya a nan ko kuma can za a kai miki?"
"Kawo min nan Ιin, bari na je nan wanke baki."
Ummie tace "To" daga haka ta wuce kitchen Ummah
kuma ta wuce sashenta, few minutes later ta dawo. Bayan ta karya kuma a nan ta
shantake, sai lokacin sallar zuhur ta koma nata sashen.
*******************************
AZARE
Imaan ce zaune da wata abokiyar aikin a SOHAAN bayan sun
idar da Sallah a masallaci. Jamilah ta dubi Imaan tace "Imaan kin san me?"
Imaan ta jijjiga kai. Har jamilah za ta ce wani abun sai kuma tayi shiru. Abun
ka da gulmar da ke cin Ιan adam, can ta Ζara duban Imaan Ιin ta ce "Kika
ce wai ba ki san me ake cewa a Companyn nan ba?"
Imaan ta amsa mata da "E, kin san ba kowa nake magana
da shi ba bayan ke."
"Hmm"
"Me yake faruwa?"
"Ke me tunaninki ya kawo miki?"
"Babu komai Jamilah, wani abun ne hala?"
Jamilah ta gyara zamanta tace "Hmm, wai ki san Zuhra ta
wajen beverages?"
"Zuhrah?" Imaan ta maimaita tana Ιan Ιaga kanta
sama trying hard ta gano Zuhrah.
"Ok, wannan Ζ΄ar gayun?"
"Yauwa, ke ce ma ita."
"Me ya same ta?" Imaan ta tambaya tana mai lumshe
Idanuwanta.
"To bari ki ji, an dakatar da ita aiki, MD da kansa
yayi hakan, amma naji Ζishin-Ζishin Ιin cewa wai ta neme shi ne."
Idanuwa Imaan ta ware tana faΙin "What?"
"Abun da kika ji dai Imaan, kuma wallahi Ni na yadda,
don wannan shigar banzar da Zuhrah ke yi in cewa aka yi ta nemi ko uban waye ba
zan yi mamaki ba."
"Allah ya kyauta, tashi mu koma bakin aiki kafin Madam
ta zazzage mu kin ji?"
"Ai kuwa dai, da Ni kadai ne na san babu abun da za ta
yi, amma tun da da ke garanti sai ta tsige mu. Babba da ita amma tana haΙa Ζugu
da yara, mtsss" da haka suka koma bakin aiki, cikin ikon Allah Madam Ιin
mal ba ta nan.
Bayan sun tashi daga aiki, ta Ιebi nata snacks Ιin don
wucewa, har ta Ιaga hannu za ta tsayar da Ιan sahu ta tuna yau babu kuΙi a
hannunta, hakan yasa ta lumshe idanuwanta tare da fara takawa a hankali. Tana
cikin tafiyar ne kuma wani mai mota ya tsayar da motarsa daf da ita, tsorata ma
da farko tayi, a tunaninta ita ta kaucewa hanya, hakan yasa ta koma ta can gefe
sannan ta ci gaba da tafiya with full caution.
Sai da ta kusa shiga layinsu karab ta Ζara ganin motar nan
kusa da ita, da sauri ta dudduba don ganin ko dai ita ce yanzun ma ta kau layi,
ganin dai ba ta hau hanya ba yasa ta Ιago da Idanuwanta, a wannan lokaci, mai
motar ta sauΖe glass Ιin motar, ta ciki ya karaΙo sallama. Ta san hukuncin amsa
sallama a addinance hakan yasa ta amsa daga haka ta ci gaba da tafiya tana
Allah Allah ta shiga layinsu.
Kamar mutumin ya san me take faΙa cikin ranta ya fito daga
motar ya bi bayanta, yana isowa saitinta ya Ζara yi mata sallama. A Ιan tsorace
ta amsa ba tare da ta tsaya ba.
"Yi haΖuri ki ba Ni Ko minti uku ne Ζ΄anmata, na san ba
kima ko mutuncinki ba ne na tsayar da ke kan hanya, ki ba Ni lambar wayarki,
daga nan sai na Ζaraso."
Ba tare da ta tsaya da tafiyar tata ba tace "Ba Ni da
waya"
Mutumin yace "What?" While fuskarsa na nuna
mamakin amsar tata.
"To don Allah ina ne gidanku?"
Da sauri tace "Ba a garin nan nake ba, hutu nazo"
Ζ³ar dariya yayi ganin yadda fuskarta ta sauya Lokaci guda
alamar ba ta yi sabo da karya ba.
"To shi ke nan, gidan da kika zo za ki nuna min."
"Ai gidan malamai ne ba a zuwa, don Allah Yayana ka
juya kar a gan Ni da kai."
The way she talks politely made him stop, sai ya ja ya tsaya
yana mai bin ta da kallo, sai da ta Ιace masa tukun ya koma wurin da yayi
packing motarsa ya ja ta cike da farin ciki.
A lokacin da ta koma gida Mami ta shiga ta gaisar, ba ta bi
ta kan Dada ba kasancewar Dadan da kanta ta mata shamaki da hakan a faΙarta ba
ta buΖatarta a rayuwarta, ta kuma yi wa kanta iyaka da ita don ba ta jin ita Ιin
jininta ce sakamakon RIKITACCIYAR ALAΖAR da ta gifta tsakani.
Wanka tayi bayan ta fito ta Ιauko abincinta, sai da ta ci
tukun ta lallaΙa ta kai wa Mami snacks Ιin, tana ba ta ta fito gudun kar Dada
ta yi musu dirar mikiya. Babu jimawa Ihsan ta dawo, itama wankan tayi, Dada da
kanta ta kawo mata abinci da ruwan leda, don ita ba ta shan ruwan gidan nasu.
Sai da tayi Ζyat tukun ta dubi Dada tace "Wallahi yau
sosai na gaji Dada."
"Sannu Shalele, ki dai dage ki yi karatun nan, ki zama
tauraruwa a zuri'armu don ke ce za ki zamo ta fari da ta fara yin boko."
Yamutsa fuska Ihsan tayi tace "To Dada, yanzu dai ba
wannan ba, kuΙi ake buΖata a makarantar, kuma babu a wurina, Charity da ke
taimaka min itama babu kwanan nan."
"To yanzu ya za a yi, har nawa ne kuΙin?"
"Dubu hamsin ne Dada"
Idanuwa waje Dada tace "dubu hamsin Shalele?"
"E Dada, nawa ne dubu hamsin Ιin wai? Ko albashin watan
nan a karΙa min."
Fuska Dada ta saki tace "Au, ashe dai akwai albashi a
gidan" sai kuma ta marairaice fuska
"Tun da wannan baΖar ashanar ta fara numfashi, daga nan
duk wani farin cikinmu ya kau Shalele, wallahi babu ja in aka ce yar nan taki
ba Ζ΄ar Muhammadu ba ne wallahi zan yadda."
Tura baki Ihsan tayi tana faΙin "Ni ki bar ce mata
Yayata, wannan abar kunyar zan nuna matsayin Yayata? Tirrr"
Tana faΙin haka ta miΖe a fusace, Dada kuma ta fice tana faΙin
"ko kin ce kina yinta ma Shalele ai ba sa'ar ki ba ce. Mutum kamar
annoba?" Daga haka ita ma ta fice suka bar Imaan wacce jikinta ya gama yin
sanyi da al'amarin kaka da kuma Ζ΄ar'uwarta, ba ta taΙa jin sha'awar dalilin
wannan tsana da suke nuna mata ba sai yau, a yau kam ta ji buΖatar hakan domin
ta san wane irin laifi ta aikata musu da ta cancanci irin kyata da tsanar da
suke nuna mata, tana son sanin komai domin samar da daidaito tsakaninta da su.
Jikinta sanyaye ta miΖe itama ta bar Ιakin zuwa tsakar gida,
a gindin bishiya ta zauna tare da lumshe Idanuwanta tana shaΖar iskar. Ba ita
ta koma Ιaki ba sai lokacin sallar Magrib, bayan ta yi sallah ta buΙe
Alqur'aninta tana karantawa a haka har lokacin ya Isha ya Ζarato, tana idar da
ishar kuma ta kwanta tun da yau dai ba girkin dare aka yi a gidan ba, sai dai
ga mamakinta baccin ya Ζi zuwa, har Ihsan ta yi nata baccin Imaan na kwance
tana saΖawa da kwancewa kan zaren Ζullin RIKITACCIYAR ALAΖAR da ke tsakaninta
da Dada da kuma Ihsan, a haka dai bacci Ιarawo ya sace ta.
BABI NA 3
Washegari kamar ko yaushe, da wuri Imaan ta gama gyara
gidan, sanin babu wani abun ci yasa ta shirya don wucewa aikinta, ba ta jira
sun gaisa da Mami ba ta wuce, Ihsan kuwa sai wuraren goma ta tashi, babu sallah
bare salati, haka ta sa Dada da faΙan yunwa take ji, Dada da kanta ta saka
hijabi ta nufi gidan Yaha mai waina ta siyo musu ta jaka Ιaya da rabi ita da
shalelenta.
Imaan kam sai da ta dawo daga wurin aiki sannan ta samu ta
zuba wani abu a cikinta, ta so a yau ta tunkari Mami da tambayarta, amma sai
taji wani rauni a tattare da ita, har take jin kamar ta sauya wannan shawara da
zuciyarta ta ba. Sai kusan Magrib Abba ya dawo daga kasuwa. Jiyowa muryarsa da
Imaan tayi yasa ta fito da sauri, Ihsan kuma ta saki tsaki.
"Sannu da dawowa Abba"
Ta faΙa tare da karΙar ledar hannunsa. Fuska sake kyakkyawan
Dattijon yace
"Yauwa Sannu Uwata, ya aikin naki?"
"Alhamdulillah Abba."
"Ma sha Allah Uwata, a ci gaba da haΖuri dai a yi aiki
tuΖuru komai zai wuce, kin ji Uwata?"
Kai ta gyaΙa sannan ta wuce da kayan veranda tare da
ajiyewa. Da har za ta koma wurin Abban sai ga Mami, kawai sai ta fara haΙa
wuta. Gaba Ιaya murhu biyun ta hura Ιaya na tuwo Ιaya Kuma na miya,
kiraye-kirayen sallar Magrib yasa ta yi talge daga nan ta wuce ta yi sallah ta
dawo.
Imaan na zaune gaban murhu tana iza wuta, bayan tuΖa tuwon
da ta yi sannan ta gauraya miyar kukar da ke fitar da Ζamshin daddawa sannan ta
miΖe za ta bar wurin.
Muryar Dada ce ta tsayar da ita.
"Allah yasa ba wani abun kika zuba a miyar ba."
"A'a Dada, ban saka komai ba"
"A ai ke Ιin ne tsoro kike ba Ni musamman da kika gado
mai sunanki, yo uwarki ce ma misali mai kyau ai."
Kai kawai ta jinjina tana yi wa kakar Tata fatan shiriya
zuwa kan hanya madaidaiciya.
Tas ta gama girkin yayin da Ihsan ke ciki tana danne-dannen
wayarta da ya hana ta fitowa yin sallar Magrib wanda lokacinta har ya wuce.
Haka Hamra ta kwashe tuwon sannan ta kai veranda ta haΙa da
tukunyar miyar za ta kai sai ga Dada.
"Ke don ubanki ina za ki kai tuwon ne?" Sai kuma
ta fashe da kuka ganin Abba zai fita Masallaci
"E, ai dole ki Ιauke ki je ki Ιoye tun da ubanki ne ya
kawo, Ni wallahi na gaji da zama da ke, baΖin cikinki ba zai kashe Ni ba,
saboda haka yau ba gobe ba zan bar muku gidan ku yi abun da kuke so." Tana
kai wa nan ta face hanci.
Kai kawai Abba ya jijjiga sanin halin mahaifiyar tasa, amma
yaya zai yi? Haka Allah ya jarabce shi shi kuma ta Ιangaren uwa, haΖΖinta ne
akansa dole yayi taka-tsan-tsan.
Ζarasawa Wurin da Imaan ke bin Dada da kallo yayi, cikin muryarsa mai Ιauke da nutsuwa
yace
"Lafiya dai Imaan?"
Wani kukan Dada ta Ζara fashewa da shi tana faΙin "Ai
dole ka tambaye ta lafiya tun da ita ka fi Ζauna Ahmadu, ai na san ba haka suka
bar ka ba." Ta Ζarasa cikin Muryar kuka tare da kamo gefen zaninta tana
share Ζwalla.
Cikin sanyin jiki Abba yace "Ki yi haΖuri Dada don
Allah, ke Imaan" ya maida kolinsa ga Imaan wacce ta wani yi gasaΖe tana
tsaye hannunta riΖe da tukunya kanta kuma na Ζasa wanda tsabar yadda Dada ta
Ζulleta da kalamanta ko zafin tukunyar ba ta ji.
"Maza ji ba wa Dada haΖuri"
Ba tare da ta Ιago ba tace "Ki yi haΖuri Dada"
Hanci Dada ta ja sannan tace "To yaya zan yi, Ni dai
duk ranar da aka ga ba na nan wallahi guduwa nayi, don ba zan tsaya yarinyar
nan da uwarta su kashe Ni ba."
Tana faΙin haka ta wuce Ιakinta. Abba ne ya dubi Imaan yace
"Je kayanki Uwata, ki ci gaba da haΖuri kina yi wa Dada Addu'a, komai
lokaci ne, kar ki damu kin ji?" Imaan ta gyaΙa kai tare da wucewa ta ajiye
tukunyar miyar.
Wanka ta samu ta yi ta saka wata doguwar riga mai Ιan taushi
sannan ta gabatar da sallar Isha, sannan ta wuce Ιakin Mami bakinta Ιauke da
sallama. Mami ta amsa mata fuskarta sake. Kusa da Mamin ta zauna sannan tace
"Sannu da hutawa Mami."
"Yauwa Imaan, kin gama tuwon ke nan?"
"Na gama Mami, na zubo miki ne?" Ta faΙa tana shirin
miΖewa.
"A'a kin ga, yi zamanki, ke kin ci ne?"
Ta jijjiga kai alamar a'a. Cike da kulawa Mami tace "Ki
daina wasa da cikinki Imaan, ba na son ulcer ta kama ki."
"In sha Allah Mami zan kula, ulcer kam Allah ma ya
tsare mu da ita."
"Amin, tashi ki Ιebo tuwon ki zo nan ki ci a
gabana." Babu yadda za ta yi ta amsa da "To" sannan ta fice.
Ta gama Ιiban tuwon kenan Dada ta fito ta taras da ita tana
zuba miya. Tsayawa tayi tana aika mata kallon tsana sannan tace "Uban wa
kika zuba wa wannan tuwon? Yarinya shegen ci kamar wata jaka e?" Shiru
Imaan tayi ba tare da ta juyo ta dubi Dada ba, hakan ne ya Ζara hasala Dada ta
fizgo hijabin jikin Imaan take tayi baya har sai da miyar da ta Ιebo zubewa.
Ganin hakan yasa ta sake ta tana faΙin "Don ubanki ajiye tuwon nan za ki
yi, daga kan yau ma na haramta miki cin wani abu wai shi tuwo, in ban da son zuciya
Shalele ba ta Ιiba ba za ki zo ki kwashe?" Kamar Imaan za ta yi kuka tace
"Haba Dada, Ihsan fa kin san ba ta ci, kuma Mami ce tace na zo..."
"Dalla rufe min baki, da ke da uwar taki ai duk gadon
baΖin halin ne, to bari ku ji, na san itama tana ji na daga ciki, wallahi za mu
sa Ζafar wando Ιaya da ku ne matuΖar haka za ta ci gaba da faruwa."
Shirun Dada ya yi daidai ne da shigowar Abba wanda ya dawo
daga masallaci, sanin cewa tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ΖoΖi yasa yayi ΖoΖarin
wucewa Ιakin Mami, sai dai bai kai ga shiga ba ya jiyo Dada na kiransa. Dawowa
yayi yana faΙin "Ga Ni Dada"
"Haba Muhammadu? Yanzu a ganinka ka kyauta ke nan e?
Kana gani yarinyar nan ta saka Ni gaba da faΙa kamar ita ce gaba da Ni shi ne
kuma za ka wuce ko?" Kuka Dada ta fara, ganin haka yasa hankalin Abba
tashi don ba ya son kukan Dadan duk da cewa ya san kuka ne irin wadda ba shi da
ma'ana.
"Ki yi haΖuri Dada, ban ma lura da ku ba ne, don Allah
ki daina kuka, zan hukunta ta kin ji?"
Ya faΙa tare da share mata Ζ΄an shiraran hawaye guda biyu da
suka zubo mata.
Jikinta ta janye tare da faΙin "Rabu da Ni Muhammadu,
Ζ΄arka ta fi Ni daraja, shi ne kawai magana, kai kake goya mata baya ai take
rashin mutuncin" Tana rufe baki ta juya ta nufi Ιakinta ba tare da ta bari
Abban ya mata bayani ko ya lallashe ta ba. Cikin raunin zuciya Abba ya dubi
Imaan wacce kanta ke Ζasa tana share Ζwalla yace "Uwata share hawayen naki
kin ji?"
Da sauri ta share hawayen. Abba yace "Kul kika Ζara ja
in ja da Dada kin ji yarinyar kirki?" Ta gyaΙa kai.
"Yauwa Ζ΄ar albarka, je ki ci tuwonki maza."
Sai da yaga shigarta Ιakinsu tukun ya wuce Ιakin Mami.
Cikin sanyin jiki Imaan ta shiga Ιakinsu hannunta riΖe da
kwanon da ta zubo tuwon a ciki. Sashen da ya kasance nata a Ιakin ta nufa, a
kan tabarmarta ta yi yunΖurin zama bayan ajiye kwanon, ba ta kai ga zama ba
Ihsan da ke danna wayarta miyar kukar da ke Ζamshin daddawa ta bugi hancinta.
Babu shiri ta ajiye wayar kan pillow ta juyo direction Ιin da Imaan ta zauna.
"B**a uba! Wannan uban warin kukar fa?"
Imaan ba ta kalle ta ba sanin yanzu sai Ihsan Ιin ta nemi Ιagawa
mutane hankali.
"Wato ma ga mahaukaciya na magana" Ta tashi a
zabure ta nufi wurin Imaan Ιin tana aika mata wani irin kallo kamar wata
zakanya.
"Wallahi ki fita da wannan kuka mai warin masifar in ba
haka ba kuma jikinki ya faΙa miki, haka kawai ki wani shigowa mutane Ιaki da
ita, wannan warinta ma ai sai ya kumburawa mutum ciki, oh yeah, fice da miyarki
a Ιakin."
Yadda tayi maganar cike da izza da kuma umarni ka yi tunanin
Imaan ba za ta tashi ba kasancewar ita ce gaba da Ihsan Ιin, amma saboda sanyin
hali irin na Imaan Ιin sai ta miΖe hannunta riΖe da kwanon za ta fice. Wani
kallon Ihsan ta Ζara jifanta da shi tana toshe hancinta tare da saurin kaucewa,
murmushi Imaan tayi ta fice tana mamakin hali irin na Ζ΄ar'uwar tata duba da
yadda Ζarfi da yaji take son sauya rayuwarta, ko kaΙan Imaan Ιin ba ta taΙa
hasaso cewa al'amarin Ζanwar Tata zai girmama haka ba, Allah ya ajiye ta a Ιigire
karfi da yaji tana son Nuna cewa bai cance ta ba?
Duk wannan tunani ne da Imaan ke yi tana tsaye, ganin har
lokacin ta Ζi ficewa yasa Ihsan juyowa a hasale ba tare da ta saki hancin nata
ba tace "Ke wai ba za ki fita da wannan miya mai warin ba ne sai kin
lalatawa mutum ciki e?" Rausayar da kai Imaan tayi tare da ficewa, ganin
ta fita yasa Ihsan sakin tsaki tace "Aikin banza aikin wofi, in ban da
lalacewa ina Ιan'adam ina zuba wannan abu a cikinsa? Bullshit!", Daga haka
ta kuma nufi wurinta ta kwanta tare da ci gaba da danna wayarta.
Washe gari da yamma suna zaune a tsakar gida, Imaan da Mami
kan tabarma Ιaya, Dada da Ihsan suma tabarma Ιaya yayin da Ihsan Ιin ke danna
wayarta Dada kuma na mata surutai, ita kuwa ba ma ta Dadan take ba.
Yaro ne yayi sallama yace "Wai ana sallama da Aunty
Ihsan."
Caraf Dada tace "Inji waye?"
Yaron yace "Wani ne a waje."
"Yaya shigarsa, Ιan gayu ne?"
Shi kansa yaron sai da abun ya ba shi dariya ai kuwa yace
"In ta zo za ta gan shi, a ce tana zuwa ko a'a?"
"Tana zuwa." Mami ta faΙa a sanyaye. Wani kallo
Dada ta aika mata sannan ta dubi Ihsan da ba ta san duniyar da suke ciki, Ιan
taΙa ta tayi tace "Shalele, ki tashi ana sallama da ke a waje."
A shagwaΙe tace "Ni dai Dada babu yadda zan je, kin fa
san masu sallaman nan Allah na tuba ba wani abun arziki gare su ba."
Cikin sigar Dada tace "Haba Shalele, ke dala kika samu
ma mazan suke zuwa su yi sallamar, wasu fa ba a zuwa musu, kuma Hausawa suka
ce, a rashin tayi, wai akan bar araha, saboda haka ki shirya yanzun nan ki
je."
MiΖewa Ihsan tayi ta koma Ιaki, dama already ta yi wanka,
Ζananan kayan da ke jikinta ta sauya zuwa wata doguwar riga da ta Ιan kamata
sannan ta janyo wani Siririn veil ta yafa, turare ta fesa, ta zaro takalminta
daga ciki ta yo waje hannunta riΖe da wayarta.
A tsaye ta tarar da shi jingine da bishiya ya juya mata
baya, sai dai Ζamahin da ya bugi hancinsa yasa ya juyo babu shiri, tsintar
kansa yayi da faduwar gaba yayin da ΖwaΖwalwarsa kuma ta daga da ayyukanta na
wasu sakanni
Ihsan da ke binsa da kallo ta Ζaraso kusa da shi tace
"Hi"
Gyaran murya yayi sannan yace "Ah Ζ΄an mata kin fito
kenan, shanyar taki har ta kusa bushewa"
Yanayin yadda yayi maganar yasa ta gane cewa kansa ba a
tukunya yake ba, hakan yasa tayi rolling Idanuwanta tace "Sorrie, ba na
jin daΙi ne."
Yayi murmushi yace "Sunana Barr. Junaid, Ni ne mutumin
da na tsayar da ke kwanakin biyu da suka
wuce kika Ζi saurarena, kin kyauta kuwa."
Shiru Ihsan tayi don ita gaskiya ba ta san shi ba, then how
ya san gidansu?, Ta yaya? Ko dai Imaan ya gani ba ita ba. Cikin ranta tace
"possibly, amma tun da gare Ni kazo yanzu, Ni ce da moriyar."
"An yini lafiya sarauniya"
"Lafiya Ζalau"
"Ma sha Allah, sarauniya ba ki tambaye Ni ya aka yi na
gano gidanku ba da sauri ba?"
Malalacin murmushi Ihsan ta saki tare da juya idanuwanta
"Ba dai ka gano Ιin ba?"
Ya ba ta amsa da "E"
"That's ok, ka yi proving cewa, you truly love
me."
Wani irin daΙi ne ga kama Barr. Junaid, sam bai taΙa tunanin
yarinyar da ya haΙu da ita 3days back haka take ba, a lokacin da ya haΙu da
ita, tsantsar kunya ce ta mata lulluΙi, a yanzu kuma ta koma wata wayayyar
yarinya, shigarta ta ranar, compared to shigarta ta yanzu.." saurin kawar
da tunaninsa yayi kafin yace "Ba ki faΙa min sunanki ba Baby."
"Ihsan." Ta ba shi amsa a gajarce
"Nice name, ina fatan za ki amshi tayin da na zo miki
da shi Ihsan, ban zo da yaudara ko wani batu ba, zan ba ki lokaci ki yi tunani
kafin manya su shiga zancen, billah! I'm in love with your from the first sight
Ihsan."
Shiru tayi na tsawon wani lokaci can tace "Ok, zan yi
tunani Barr. Thanks for your love"
"You deserve more Queen"
Lumshe Idanuwanta tayi sannan ta buΙe, ganin yadda ya
tsurawa wayar hannunta kallo yasa tace "Ya dai??"
"Har ma kin manta? Wannan Ιin wayarki ce ko kuwa?"
Yayi wani murmushi yana tuna ranar da ya fara ganinta.
Veil Ιinta ta ja ta rufe idonta, fatanta dai Allah yasa kar
ya gano ba ita yake nema ba, to a yaya mai zai gano bayan ko Ζ΄an unguwarsu ba
kowa ke banbance su in bacin yanayin rayuwa da na kowa ya banbanta ba.
"Kar ki ji kunya Queen, may be kin Ιauka yaudararki zan
yi shi ne kika ce min ba ki da waya ko?"
Sakin veil Ιin tayi da sauri tace "Aa fa, I'm sorry
please."
Fuska sake yace "worry not dear, hakan ya Ζara nuna min
cewa Abba da Umma sun miki horo mai kyau. Ki saka min numberki a nan." Ya
miΖa mata wayarsa, bayan ta saka ta miΖa masa yayi dialling a wurin, bayan ta
shiga ta gama ringing yace "Save my digits, remember na ba ki time ki yi
shawara, take this"
Ya miΖo mata envelope tare da mayar da wayarsa aljihunsa.
Kanta ta sunkuyar kamar mai jin kunya.
"Kar ki ce ba za ki karΙa ba Ihsan, kyauta ce kawai na
miki, please ki karΙa."
Abun da take jira taji ya faΙa ke nan. Ai kuwa ta sa hannu
ta karΙa tana faΙin "thanks"
Daga haka ta koma cikin gida.
Da yake lokacin Magrib ta Ζarato, Mami, Imaan sun bar gindin
bishiyar iya Dada ce ke jira shigowar jikar Tata. Ai kuwa tana shigowa ta Matso
gurin Dadan ta rungumeta.
"Sa'a car, Dada me yasa ba ki sa min suna Sa'adatu ba
da aka haife Ni?"
Janye jikinta Dada tayi daga na Ihsan tare da haΙe fuskarta.
"Lallai Shalele, kema ba kya son sunan nawa ne kamar
yadda ubanki ya ba wa matarsa muhimmanci sama da Ni?"
A shagwaΙe Ihsan tace "Haba Dada, ke kan fassararji ta
yi yawa, mutun in ya ce A, sai kin fassara ta zuwa 1&2, Ni dai kin ga"
"Meye?"
Idanuwa Dada ta Ζwalalo ganin kuΙaΙe masu yawa
"Shalele ina kika samu wadannan uban kuΙaΙen?"
"Shi ya ba Ni, wanda ya zo yanzu, kuma kin san
me?"
"Wallahi ba Ni zai ba wa ba, Imaan yake nema, Ni kuwa
nayi pretending as her, tun da mai kuΙi ne gaskiya sai dai tayi haΖuri, don ba
zan taΙa bari ta samu fiye da abun da Ni zan samu ba, that's over my dead
body."
"Dalla Ni ba na son shegen Yaren nan, tashi ki je ki
adana kuΙin, idan Muhammadu ya dawo babu kuΙin yin wani abun sai ki samar mana
abun da za mu ci mu biyu tun da in sun samu suma Ιoyewa suke su ci a Ιoye."
Ihsan tace
"Shi yasa nake Ζara sonki Dada." Daga haka ta miΖe
ta wuce Ιakinsu.
Ko da ta shiga Ιakin ganin Imaan ta kabbara salla yasa ta ja
tsaki tare da faΙin "Allah yasa sallar dai karΙaΙΙiya ake yi" sai
kuma ta yatsina fuska, "To me yasa ma zan miki addu'a mai kyau?"
Dogon tsaki ta ja sannan itama ta Ιauro alwalar ta dawo tayi sallah. Ζangaren
Imaan ta duba, cikin ikon Allah taga tana nan hakan yasa ta dake tace
"Ke!" A kausashe.
Juyowa Imaan Ιin tayi ta dubi Ζ΄ar uwar Tata sai kuma ta juya
tana jijjiga kai.
A Ιan hasale da yadda Imaan Ιin tayi mata tace
"Ba damuwata ki saka idanuwanki cikin nawa ba, kawai
gargaΙi zan miki, na kuma san kina ji ba ba kya ji ba. Kawai dai abun da zan faΙa
miki shi ne ki kiyaye.". Shiru tayi tana juya Idanuwanta sai kuma tace
"Akwai wani guy da ina kyautata tunanin kun haΙu da shi kwanaki biyu baya,
ba dole sai na fadi exact date ba, amma na san kin sani. GargaΙina gare ki shi
ne, kada ki kuskura ki bari ku Ζara haΙuwa har yasan cewa ba ke ce yau kika
fita ba, idan na kin fara son shi ne, ina so ki fige shi daga zuciyarki ta ko
yaya ne domin yanzu shi Ιin nawa ne, na yaba da shi, na kuma ba shi wuri a
zuciyata, ya zama dole ki manta da cewa ke ya fara furtawa kalmar so. "
"Kina ji na ko?" Ta Ιan Ιaga murya fiye da yadda
take maganar sannan ta ci gaba
"Ba damuwata ki shiga wani hali ba, wallahi Imaan ban
Ζi ki mutu ba a duniyar nan why? Saboda kin kasance abar gasa ta tun muna
Ζanana, kin tauye min samun abubuwa da dama, amma kin san me? Ni nan Ni zan
kasance gaba a ko yaushe. Ina fatan kin ji GargaΙina kuma za ki kiyaye."
Wayarta ta janyo ta fara dannawa ko abun da take ji dangane
da Imaan Ιin zai kau.
A Ιangaren Imaan kuwa hawaye ne suke zarya tun lokacin da
Ihsan ta fara magana zuwa lokacin da ta kai aya, tsananin tausayin kanta ne ya
kama ta, shin ita yaya za ta yi ne da rayuwa? Wace irin Ζaddara ce wannan take Ιamfare
da rayuwarta?
Kowa yana farin cikin kasancewa da ahalinsa ban da ita? Shin
wai ita ta zaΙi Allah ya sanya ta cikin wannan ahalin ne da suke ganin kamar
laifinta ne kasancewarsu da ita?"
Wani hawayen ta Ζara sharewa tana faΙin "Allah ka yafe
mana!" A hankali.
Jin kanta ya fara sarawa yasa ta miΖe tayi sallar Isha,
bayan ta idar ta buΙe Alkur'aninta ta fara karantawa cikin zuciyarta, take wata
nutsuwa da salama suka mamaye Ιargo da jininta yayin da wata iska mai sanyi ta
fara ratsa jikinta.
Kiran da Mami ta Ζwalla mata yasa ta sauΖe ajiyar zuciya
tare da faΙin "Ina zuwa Mami"
Alkur'anin ta rufe sannan ta mayar da shi muhallinsa, wurin
Mami da ke bakin veranda taje sannan ta zauna gefenta. Yanayin yadda Mamin ta
ganta yasa ta tsarguwa har ta gagara shiru ta tambaye ta "Imaan ba ki da
lafiya ne."
Kanta ta gyaΙa tana faΙin "E Mami, kaina ke Ιan
ciwo."
Mami tace "Kuma shi ne ba za ki ce a ba ki magani ba?
Haba Imaan? Sai zuwa yaushe ne za ki saki zuciyarki ki rayu kamar yadda kowanne
Ιan gida yake yi?"
Cikin ranta tace
"Lokacin da Ζ΄ar'uwata, da kuma kakata suka sakar min damar yin hakan"
amma a zahiri sai ta sunkuyar da kanta Ζasa, hakan ya yi daidai da Ιisar
hawayenta kan Ζafar Mami.
Da sauri Mami ta dube ta cike da tsantsar kulawa tace
"Imaan ba iya kanki ke ciwo ba,, kun samu matsala da Ζ΄ar'uwarki ko?"
Da sauri tace "A'a Mami, kan nawa ne kamar zai
cire" ta ba ta amsa tana mai son kare Ζ΄ar'uwar tata tare da gujewa kwandon
tsiyar da za ta iya riska daga Ihsan Ιin idan Mami ta mata faΙa akanta.
Ba tare da Mami ta yarda ba tace "Shi ke nan Imaan,
dama Gari ne Abbanku ya kawo, shi ne zan ce ko za ki kwaΙa shi a ci, amma tun
da ba ki da lafiya ki koma ki kwanta, in na jiΖa zan kawo miki da maganin ciwon
kan."
Cikin sassanyar muryarta da ko yaushe take fita a Nutse tace
"A'a Mami, ki kawo na jiΖa in na shiga ciki shi ke nan." Ba musu Mami
ta miΖa mata ledar Garin sannan tace "Akwai Ζuli a bokitin da nake ajiye
kayan miya sai ki Ιauka ki haΙa da taruhu da magi biyar. In kin gama sai ki
sakawa Dada, Abbanku, Ihsan sai ki saka naki, ki shigo min da nawa da na
Abbanku Ιaki."
"To Mami" daga haka ta wuce ta jiΖa garin, har ya
tsane ya kama jikinsa tukunna ta haΙa shi tas, ta raba kamar Yadda Mamin tace.
Na Dada ta fara Ιaukewa ta nufi Ιakinta bakinta da sallama.
Dada da ke jan carbi daga ciki tace "Waye kuma zai addabe Ni ina neman
kusanci da Arrahamanu?"
Daga waje Imaan tace "Imaan ce" yayin da zuciyarta
ke bugawa da sauri sauri tana fatan kar ta wulaΖanta ta.
"To ki shigo mana"
Jin amsar Dada yasa ta buΙe labulen Ιakin ta shiga, a gaban
Dada da ke watsa mata kallon tsana ta tsugunna ta ajiye kwanon hannunta.
"Dada ga..."
Hannu Dada ta Ιaura kan laΙΙanta tace "Ba sai kin ce
komai ba, Allah yasa ba wani abun kika zo ajiyewa ba, fice min a Ιaki."
Sim sim kamar munafika Imaan ta fito daga Ιakin, kular da ta
zuba na Abba da Mami ta dauka ta miΖa musu, Mami ta haΙo ta da pcm tana mai
mata addu'ar samun sauΖi da wuri sannan ta fito, nata da na Ihsan ta Ιauka ta
nufi nasu Ιakin. Daidai wurin Ihsan ta ajiye mata nata kwanon, ta Ιago za ta wuce unexpected Ihsan
ta sheΖa mata kwaΙon kwakin a fuskarta.
BABI NA 5
Wani irin zafi ne ya ziyarci Imaan kasancewar ya zuba a
idonta, runtse Idanuwanta tayi ta danne da hijabin jikinta. Dariyar mugunta
Ihsan ta saki tare da hankaΙa ta Ιangarenta tana faΙin "Gobe ma ki Ζara
kawo min abincin dabbobin nan, in ban da raini Ni?" Ta nuna Ζirjinta da
yatsa cike da alfahari.
"Ni? The whole me naci garin kwaki, wallahi sai dai ku
can ku Ζarata da ci, kuma bari ki ji ma, aure zan yi na bar muku tsiyarku,
saurayin da yake sonki shi zan aura. Banza kawai."
Ta ja tsaki ta koma ta kaΙo duka garin da ya zube a sashenta
zuwa na Imaan wacce ke zube akan shimfiΙarta Idanuwanta rufe. Abubuwa biyu ne
suka taru mata, ba wai iya zafin yajin da idonta ke yi ba ne kaΙai, wulaΖanci
da maganganun banzan da Ihsan ta mata ne.
Ta share kusan awa biyu a kwance ashe bacci ma ya kwashe ta,
fitsarin da taji shi ya tayar da ita daga baccin har lokacin kuwa idanunta suna
mata zafi, har za ta fice sai kuma karo na farko taji wani kwarin guiwa a tare
da ita hakan yasa ta tsaya kan Ihsan da ke chat da wayarta. Cikin sassanyar
muryarta tace "Ki daina alfahari Ihsan, don ba ki san me gobe za ta kawo
ba." Galala Ihsan take kallonta don mamakin ganin yadda ta wani dake tana
faΙa mata magana kamar ba yayarta Imaan da ta gama sakar mata ba. Ba ta gama
tantance abun da ke faruwa ba sai da taji Imaan Ιin ta ci gaba da maganar ta.
"Dogon buri ba na Ζ΄a mace ba ne, don ba ta san ina aure
zai cilla ta ba."
Tana gama faΙar haka ta wuce waje, Hajiya Ihsan sai da Imaan
ta fice tukunna ΖwaΖwalwarta ta gama fahimtar abun da Imaan Ιin ta faΙa.
Hannayenta biyu ta sa ta tallafi kanta saboda tsantsar Ιacin rai, wani irin
zazzafan huci ta sake tana mai jijjiga kanta har lokacin hannayenta na tallafe
da kan.
"That's impossible!" Ta faΙa da Ζarfi daidai
lokacin da Imaan ta shigo Ιakin, ai kuwa a fusace ta miΖe ta nufe ta kamar
hasalalliyar damisa.
"Har ke waye da za ki faΙa min magana?"
Ihsan ta faΙa tana riΖe wuyan rigar Imaan wacce take bin ta
da kallo.
"Magana nake miki fa! Ke wace ce da za ki faΙa min
magana e?"
Ta Ζara maimaitawa cikin karaji.
Kai kawai Imaan ta jijjiga tana mai yi wa Ζ΄ar uwar tata
fatan shiriya a zahiri kuma ta sa hannunta tana ΖoΖarin ΙanΙare hannun Ihsan da
ke cakwame da wuyan rigarta.
Ζara ΖanΖame rigar Ihsan tayi don zuwa yanzu zuciyarta ta
kai Ζarshe wurin Ιaci, ji take a lokacin mai raba ta da Imaan sai Allah. Ganin
dare ne kuma Imaan Ιin ba ta buΖatar tayar wa iyayensu hankula yasa tace
"Look Ihsan, I'm sorry, dare ya yi ki bar Ni na kwanta."
Wani kallon raini Ihsan ta jefe ta da shi kasancewar akwai
yalwatuwar haske a Ιakin ya ba wa Imaan damar ganin hakan, cikin ranta tace
"Ba za ta taΙa canzawa ba."
"Da ke nake Miss Ihsan, matar future president."
Duk yadda ran Ihsan ya Ιaci yake kalaman Imaan suka sanyaya
ruhinta, a hankali ta saki wuyan Imaan Ιin tana faΙin "Ko da zuciya Ιaya
kika faΙa ko akasin hakan, ina fatan hakan ta kasance."
Imaan ta yi murmushi ta ba ta amsa da faΙin "Da zuciya Ιaya
na faΙa, fatan fatanki ya zama gaske." Tana kai aya ta wuce sashenta.
A Ιangaren Ihsan sosai maganar Imaan Ιin ta mata daΙi,
tsabar ruΙi irin na shaiΙan Kuma zuciyarta ta fara hasaso mata rayuwa a gidan
shugaban Ζasa, hohoho, wani kaso na tsana da ta tashi da ita game da Ζ΄ar'uwar
tata take da disashe, har tana jinta a yanzu a matsayin Ζ΄ar'uwarta. "Ko
dai saboda ta so abun da na so ne a wannan karon?" Ta tambayi kanta da
sauri. Take wani Ιangare na ziciyarta ya ba ta amsa da "Yea! Dalilin haka
ne, dama tsanar da kike mata ai ba haka kawai ba ne, it's because she's always
against you."
"And now she's with me!" Ta furta a saman laΙΙanta
tana murmushi.
Wurin shimfiΙarta ta wuce tana ji a zuciyarta kamar an mata
wata gagarumar kyauta.
KUΖA ESTATE
Ummah ce zaune a katafaren parlournta cikin shiga ta
alfarma, zaune take tana zancen zuci, shigowar kyakkyawan Dattijo ciki yasa ta
miΖe ta nufe shi fuska sake.
"Barka da dawowa Aba Jalaal!"
Shima a sake yace "Barka da gida Rabbatul-bait. Ba ki
kwanta ba ke nan?"
"Ina na isa na kwanta bayan wani sashe na zuciyata ba
ya kusa?"
Murmushi yayi yace "Lallai kam, soyayyarki ba ta tsufa
Rabbatul-bait, kina sanya Zuciyata jinki kusa da Ni."
Itama murmusawa tayi tace "Ina matuΖar godiya
Maigidana, yanzu dai ka samu ka watsa ruwa ko ka ji daΙi, da alama yau ma dai
aiki kayi sosai, ya kamata ka fara hutawa zuwa yanzu Maigida, ka haifa fa, kuma
shekarunka a yanzu sun kai ka samarwa kanka hutu, ka kuma samar mana da mu
iyalinka lokaci na musamman da a baya ba mu samu ba."
Numfashi ga sauΖe tare da faΙin "In sha Allah
Rabbatul-bait. Bari na samu na watsa ruwa na fito" sakinsa tayi ya wuce,
ganin ya shiga ciki yasa ta rufe Idanuwanta kana ta buΙe su. Ζasa-Ζasa ta furta
"Ba zai taΙa canzawa ba, ba zan taΙa samun irin gurbin da ChubaΙo ta samu
a zuciyarsa ba. Huh" ta furzar da iska tana ΖoΖarin ganin ta daidaita
kanta.
Can babu jimawa Abie ya fito cikin wata jallabiya sai Ζamshi
yake zubawa abunsa, Ζamshin da ta jiyo nasa yasa ta yamutsa fuska tana faΙin
"Babu abun da Jalaal ya baro daga mahaifinsa, hatta rashin son
hayaniyar!" Sai kuma ta miΖe ta tarbe shi, dining suka nufa tana ta masa
surutu, sai dai ko A bai ce mata ba, hasali ma da ya zauna lumshe Idanuwansa
yayi yana jiran tayi serving Ιinsa. Bayan sun ci tare suka dawo parlourn,
ΖoΖari take na ganin ya ba ta lokacinsa sun yi wata muhimmiyar magana amma ya
Ζi, sai ma remote da ya Ιauka ya mayar NTA don saurarar labarai, hakan ne ya
hasala ta ma ta miΖe ta nufi Ιaki don ta saddaΖar ba za ta samu lokacin mai
gidan nata ba.
Alhaji Abubakar KuΙa ke nan! Dattijo kyakkyawa mai Kuma ji
da kuΙi, sam ba ya son hayaniya ko wani disturbances a rayuwarsa, hatta Ζarar
da kwano ke yi takan saka shi wani yanayi, sai dai duk da haka yana ΖoΖarin
ganin ya sake da kowa, ba shi da girman kai ko kaΙan ba kuma ya Ζyamar waΙanda
ke Ζasansa, yana ba wa kowa damar fadar ra'ayinsa kowanne lokaci sai dai
kwarjini da haiba irin tasa ta hana mutum sakewa yayi magana da shi.
Alhaji Abubakar KuΙa, wanda ake kira da Abie, Ιa ne na farko
ga Alhaji Abdulmalik KuΙa (Alhaji KuΙa) da kuma Hajja Fatu, Abie ya kasance Ιa
mafi soyuwa ga iyayensa kasancewarsa na daban a cikinsu, lokuta da dama idan
yana tare da mahaifiyarsa Hajja tana yawan faΙin cewa "Babu abun da ya
bari daga mahaifinsa, abu kaza, kamar mahaifinsa!"
Kamar sauran Ζ΄an'uwansa, shi ma zaune yake da iyalinsa a
cikin family estate Ιinsu. Yana da mata biyu, Ummah ita ce uwargida, auren
soyayya suka yi da Abie duk da cewa ita ta fara nuna ra'ayinta akansa. Ummah
mace ce mai son zuciya da kuma sanin makamar zama da mutane, zai yi wahala ko
abun Ιacin rai ka mata ka fahimci wani sauyi a fuskarta, ta san makamar siyasar
rayuwa shi yasa tun da Abie ya aure ta ba a taba samun wata matsala da ita ba a
cikin danginsu duk da cewa haula ce sosai gare su, ba ma wannan ba, babu wani mahaluki da zai
iya ja da maganarta a cikin dangin, hatta Hajja, banda Abie da wasu lokutan
yakan tsawatar mata idan tayi ba daidai ba, Shekararsu goma da aure sai dai ko Ιatan
wata Ummah ba ta taΙa yi ba, babu wanda ya taΙa magana tsawon wannan lokaci sai
da ita da kanta ta magantu, da farko ta tuntuΙi Abie da batun ya Ζara aure shi
kuma ya tubure kasancewar ba ta rage shi da komai ba, ganin hakan yasa ta
tunkari Hajja da maganar, ai kuwa Hajja ta amince da batun da Ummah ta zo mata
da shi, nan ta yi wa Ιan nata magana, da farko Ζi yayi sai da Baba Babba ya sa
baki, amma ya buΖaci su ba shi lokaci don neman matar.
Ummah ce tace masa a'a, ita ta riga ta masa mata wacce take
fata da kuma tabbaci a lokaci guda cewa zai so ta, babu yadda ya iya ta gabatar
masa da Ιiyar mai aikinta ChubaΙo, kyakkyawar bafulatana wacce mahaifiyarta ke
hidimtawa Ummah, ba a samu matsala da shi ba a wanna lokacin a cewarsa duk abun
da Ummah ta zo da shi zai yi na'am da shi don ya san bayan Hajja da Baba Babba
babu wani mahaluki da ke masa irin son da take masa. Ta Ιangaren su Hajja ma ba
a samu matsala ba musamman da uwar yarinyar wacce ke ciwon ajali ta amince da
hakan.
Cikin ΖanΖanin lokaci aka sanya ranar aure, bayan aure kuwa
da kwanaki mahaifiyar ChubaΙo ta rasu. A dai zamantakewarta ta zaman gidan miji
sai dai tace alhamdulillah domin Ummah na ΖoΖarin ganin ta sake da gidan, takan
ja ta a ciki, tana Ζara wayar mata da kai, wannan dalili yasa ChubaΙo (Ummie)
sakewa da Ummah cikin ranta kuma tana jin Ζaunarta Ιari bisa Ιari saboda
halaccin da tayi gare ta na haΙa ta da miji na gari, fatan Ummie Ιaya shi ne,
Ubangiji ya yassare mata wata dama a rayuwa da za ta rama wannan halaccin da
Ummah ta mata.
Ana cikin haka kwatsam ciki ya bayyana a jikin ChubaΙo, kar
ku so ku gurna wurin kowa musamman su Hajja, Baba Babba, uwa uba kuma Abie da
sai lokacin yasan cewa ashe Ιa ma cikon rayuwa ne, Hajiya Ummah ma sosai tayi
farin ciki ganin burinta na rayuwa na gab da cika, haka ta danne kishinta ta
fara ba wa Ummie kulawa ta musamman kamar ba kishiyarta ba, Ιangaren Abie shi
ma yana kwatantawa don kuwa ba kaΙan ba a yanzu yake kaunar ChubaΙo, wannan
dalilin ne ma yasa yake jin son abun da ke cikinta.
Haka rayuwar ta ci gaba da tafiya har cikin Ummie ya kai
watannin haihuwa, ranar wata Litinin kuwa naΖuda ta tashi, suka wuce asibiti, a
nan ta haifi Ιa namiji, tun a asibitin take ganin Ζaunar yaron cikin Ζ΄anuwa da
abokan arziΖi don kuwa wannan na tafiya wannan zai zo, kowa sai faΙin ma sha
Allah yake kasancewar yaron kyakkyawa mai kama da mahaifinsa sak, banbancinsu Ιaya
shi ne kalar fata, don jaririn bai Ιauko duhun fatar mahifinsa ba sai ya Ιauko
hasken uwarsa.
Ganin yadda Ummah ke nan da nan da yaron kamar ta haΙiye shi
yasa ChubaΙo fara wani tunani cikin ranta, bayan sun koma gida Ummah ta ci gaba
da kulawa da ita, ranar suna yaron yaci sunan mahaifin Ummah, Abduljalaal bisa
roΖon da ChubaΙo tayi akan hakan. Ummah ta ji daΙi Ζwarai da hakan ta kuma
tabbatar da cewa ChubaΙo Ζ΄ar halak ne. Haka ta ci gaba da shayar da yaron yayin
da Ummah ke kula da komai nasa, Ummie kuwa ta nuna kara don ko sau Ιaya ba ta
taΙa cewa a ba ta Jalaal ba idan yana hannun Ummah, a lokacin da Jalaal ya kai
shekaru biyu cur a duniya, Ummie ta yaye shi tare da damΖa shi halak malak a
hannun Ummah, a cewar ta wannan ita ce kaΙai abun da za ta iya yi wa Ummah don
rama halaccinta gare ta. Wannan jihadi da ummie ta yi sosai ya Ζara mata Ζima
da martaba wurin mijinta da kuma sirikanta, haka kuma wurin kishiyarta da ta
maye mata wasu gurabe na rayuwa da ta rasa. Daga nan Jalaal ya dawo hannun
Ummah, kulawa sosai take ba shi, tana kuma ΖoΖartawa wurin ganin ya san
Mahaifiyarsa, a lokacin da ya fara magana kuma, da sunan mahaifiyarsa ya fara,
ya kira ta da "Ummie"
Tun daga Jalaal kuma, Ummie ma ba ta Ζara haihuwa ba, kai ko
Ιari ba ta Ζara yi ba.
Duk irin yadda take kawaici da ganin ta Ιoye Ζaunarta gare
shi sai da ta zubar da Ζwalla. Tun daga wannan rana kuma shi da kansa yakan Ιebo
Ζafa ya zo wurin Ummien nasa, sai dai ba ta sake masa ba don komai ba sai don
ganin kada zuciya ta Ιebe ta ta karya alΖawarin da tayi tun ba a je ko'ina ba.
Bayan wani lokaci ma sai ya janye jikinsa daga na Ummien, sai dai kuma time to
time Ummah na kora shi yaje ya gaida Ummien.
Wannan a takaice ita ce rayuwar gidan Alhaji Abubakar KuΙa.
Bayan Ummah ta wuce Ιakinta wayarta ta Ιauko ta kira
Ζ΄ar'uwarta. Bayan ta Ιaga suka gaisa, cikin Muryar da ke nuna tsantsar damuwa
Ummah tace "Yaya Zinatu ban san ya zan yi ba kuma, duk iya ΖoΖarina na
ganin na yi magana da Aba Jalaal ya Ζi ba Ni dama kamar ya san me zan ce."
Ba a jin me ake faΙi a Ιaya Ιangaren, can kuma Ummah tace
"To yanzu Ni ya zan yi? Ko kaΙan ba na son Ζudirirrikana su fara karyewa
bayan na kusan cimma su."
"To, shi ke nan, e, gobe zai sauko garin, to zan
ΖoΖarta."
Katse kiran Ummah tayi tana sakin wani zazzafan huci.
"Har zuwa yaushe ne Ζudirina zai cika Ni Asiya? Na
gaji, na Ζosa komai ya kammala."
"Wane Ζudiri ne naki haka kike so ya kammala Rabbatul-bait?" Muryar Abie ta doki
kunnen Ummah a ba zata.
Kanta ta jijjiga tana fatan dai Allah yasa bai ji wayar da
tayi ba.
"Kin yi shiru?"
Murmushi ta Ιaura akan fuskarta tare da yafa abun da take
lulluΙi da shi a duk lokacin da irin
wannan al'amari ya tunkarota.
"A'a Aba Jalaal! Ba komai ba ne, kawai dai ina da
Ζudirin ganin yaron nan Jalaal shima ya ajiye zuri'a, shekaru talatin da Ιauri
a ce ko zancen mace ba ya yi?"
Ta Ζarashe cikin murya mai nuna tsantsar damuwa.
Janyota jikinsa yayi, cike da kulawa yace "Haba Ummah
Jalaal" (kamar yadda shima yake kiranta wasu lokutan musamman kan
al'amuran Jalaal Ιin.
"Ki kwantar da hankalinki, mu kanmu hakan yana damunmu,
to amma shi aure lokaci ne in kin duba, ko Nima nan in kin duba lokacin da na
aure ki na doshi arba'in. Don haka mu zuba ido mu ci gaba da addu'a har Allah
ya kawo ta gari."
Sam ko kaΙan Ummah ba ta so jin hakan daga Abie ba, amma sai
ta danne abun da take ji tace "Shi ke nan Aba Jalaal, amma dai mata na
gari kan ai sun zo, sai dai fatan sun dawo."
Shiru Abie yayi a wannan lokacin ba tare da ya tankawa Ummah
ba, ganin hakan yasa tace "Yanzu ga Ζ΄ar Yaya Zinatu nan Karimah, yarinyar
nan kamar ta mutu a kan Jalaal, na nuna masa hakan amma yace shi ba ya son
ta."
"To sai a bar shi, in ya fara son ta zai yi magana
ai" Abie ya ba ta amsa a gajarce, shiru tayi da bakinta a wannan karon
sanin cewa hannunka mai sanda ya mata, in ta ci gaba da maganar babu shakka zai
iya cewa ma ya haramta masa auren Karimah, wanda hakan kuma tamkar tsonka
igiyar da mutum ke bi ne a tsakiyar Teku, wannan igiyar kuwa ita ce burinta,
idan har bai cika ba ke nan ta Ιata rabin rayuwarta ne a banza, a bauta, da
kuma sarawa doki ciyawa, sam! Hakan ba zai yiwu ba.
Bloordale village, Toronto.
A yayin da Ζarfen agogon Najeriya Ζarami ya sauΖa akan lamba
ta takwas (8:00pm), a birnin Toronto da ke Ζasar Canada, Ζarfe uku ne na rana
(3pm).
Zaune AK KuΙa yake a ofishinsa yana wasu muhimman ayyuka
kasancewar katafaren kamfanin EL-MUBEEN jeweleries sun buΖaci haΙa hannun jari
da su, wannan tabbas Ζarin nasara ne ga MLS, shi yasa ya maida hankalinsa ga
aikin. Ζarar da wayarsa tayi yasa ya dakata da sannan desktop computer da ke
gabansa sannan ya kai kyakkyawan hannunsa da kallo Ιaya mai karatu zai masa
yasan cewa hutu ya zauna. Wayar ya Ιaga ganin Uncle N, Ζanin mahaifinsa da yake
matuΖar nuna masa soyayya, sallama yayi cikin muryarsa mai daΙin saurara sannan
ya gaida Uncle N Ιin, amsawa yayi a nasa Ιangaren yana faΙin "Lallai son,
wato yanzu dai Ζarfi da yaji so kake ka manta da Ni Ko?" Ya faΙa cikin
sigar zolaya kasancewar dama akwai shaΖuwa ta musamman tsakaninsu, sau tari
idan suna hira sai kayi tunanin sa'annin juna ne don shi Uncle N, mutum ne na
mutane, wayewarsa yasa yake mu'amala da kowa a waye, yana matuΖar ji da Ζaunar
AK, hakan yasa mutane da yawa a familyn sukan ce yana nuna wariya akan AK Ιin.
"Wane yaro ya manta da ubansa share kukansa?" AK
ya ba shi amsa yana sakin fuskarsa kamar yana gabansa, take wani irin
sihirtaccen kyau ya bayyana a tattare da AK Ιin, lumshe Idanuwansa yayi jin
yadda Uncle N Ιin yake dariya
"Lallai wannan yaro ba dai wayo ba, wato dai Ζarfi da
yaji wayo za ka yi babanka ko?"
Shima dariyar yayi mai Ιan sauti kana yace "Kaina Ζasa
Babana, yaya gidan ya iyali?"
Uncle N ya amsa masa da "Lafiya Ζalau sai godiya, kai
kam har yanzu ka Ζi ka ajiye iyalin ma."
Shiru AK yayi jin batun da Uncle N yazo masa, ganin shirun
ya yi yawa yasa Uncle N murmusawa yace "Shirun dai shiru ko Son?"
Bai jira amsarsa ba ya ci gaba "Har yanzu ka gagara
ajiye iyali bayan zuwa yanzu ya kamata a ce ka ajiye Ιin? Jalaal miye kake jira
haka ne? Shekaru sun fara ja, daga kai har Jahaan babu wanda yayi wani yunΖuri
and I don't know why sai dai ina kyautata zaton shi Jahaan ya yi shiru ne
saboda kai."
"Jalaal" Uncle N ya kira sunansa a tausashe.
"Na'am Uncle"
"Kana ji na kuwa?"
ΖasaΖasa yace "E Uncle."
"Ba ka ce komai ba kuma"
Ajiyar zuciya ya sauΖe yace "Uncle ban san me zan ce
ba."
"Ya kamata kuwa ka san me za ka ce, daga kai har Jahaan
ku yi wa kanku Ζiyamullaili ku yi tunani mai kyau, babu abun da kuka rasa bare
a ce rashi ne, idan kyau ne Jalaal, duka family babu ya ku, idan kuΙi ne, shima
kuna da shi, idan nasaba ce ma, Alhamdulillah, babu wata mace da za ta ce kuna
da makusa, ina tunanin kawai shiryawa ne ba ku yi ba, amma ku sani shi lokaci
ba ya jira ai."
Cikin sanyin jiki AK yace "Uncle in sha Allah za mu yi
motsi."
Ζ³ar dariya Uncle yayi yace "Kar ma ku yi Jalaal, ban so
ko Sabreen da Nimra zan ba ku ba."
Dariyar jin kunya AK yayi ya sosa kansa kamar yana gaban
Uncle N Ιin. Shi kam Uncle dariya yayi yace "Dama shirun ne amsar taka ai
na sani, in kuka yi kwantai dai babu ruwana, wallahi sadakarku zan bayar ga
Nimra da Nihal." Ya Ζarasa cikin sigar tsokana.
Shima AK Ιin Ζ΄ar dariya yayi yace "Haba Uncle, ai ba
sai an kai ga haka ba, Ζ΄an yaran nan wa zai aure su yanzu?"
"Ku mana Jalaal" ya ba shi amsa kai tsaye "Ku
Ιin dai, ba dai kuna Ζin Ζ΄anmatan da ke son ku ba?"
A shagwaΙe wanna lokacin yace "Ba haka ba ne Uncle,
matan ne duka babu na gari, babu masu son mutum tsakani da Allah, wollah Uncle
duk mace da ta raΙe mu ba don Allah take son mu ba, abun hannun mu kawai suke
hange, amma a kara mana haΖuri, in sha Allah wanan zuwan da za mu yi za mu ba
ku mamaki."
Ba don Uncle N ya yadda ba yace "To a yi dai mu
gani."
AK ya ba shi amsa da "In sha Allah za ku gani
kuwa"
"Allah ya sa"
Cikin ransa ya amsa da "Amin" yana lumshe
idanuwansa.
"Uhm, kaga gida ma zan shiga Ni kam."
"My regards to Aunty Dr (Uncle's wife) and Nihah, a'a,
i mean baby Ayman"
Dariya Uncle N yayi yace "Hmm, shi ke nan za su ji, sai
goben ko?" AK yace
"In sha Allah." Daga haka suka katse kiran.
Lumshe Idanuwansa yayi yana Ζara tariyo hirarsu da Uncle N,
jinjina kai yayi yana shafa sumarsa da tayi luf-luf take sheΖi. Ajiye wayar
yayi ya shafo sajensa, a hankali ya furta "Allah ka mana zaΙi mafi
Alkhairi a rayuwa, ka haΙa mu da masu Ζaunarmu tsakani da Allah ba don wani abu
da muke da shi ba."
Amsa addu'arsa yayi da kansa yana faΙin "Amin Ya
Rabbi" sai kuma ya ci gaba da aikin da yake yi, so yake daga yanzu zuwa
dare ya samu ya kammala komai, tunda Umar na nan sai ya bar komai a wurinsa, ya
san zai yi abun da ya kamata, Fatansa a yanzu bai wuce ya buΙe idanuwansa ya
ganshi a Ζasarsa ta haihuwa kamar yadda a can ma ake mararin a ganshi Ιin, dama
already Jahaan yayi musu booking flights su ukun zuwa Jos.
Tabbas wannan tafiyar da zai yi ta kasance ta daban domin
jikinsa da kuma zuciyarsa kansu sun fahimci hakan, a wannan hutu da zai yi,
yana fatan samun abokiyar rayuwar da za ta dace da shi, zai bi duk wata hanya
don ganin cewa ya haΙu da mai son shi tsakani da Allah, and he hopefully pray
Allah ya ba shi ita. "Tabbas zan samu" ya ba wa zuciyarsa amsa cike
da Ζarfin guiwa.
BABI NA 6
Tun kafin gari ya gama wayewa Imaan ta fara aikace-aikacen
gida, da misalin bakwai ta wuce wurin aikinta kamar ko yaushe, bayan ta dawo ta
maΖale a corner Ιinta, babu jimawa Ihsan ta shigo alamar dawowarta ke nan.
Imaan Ιin ta kalla kamar za ta ce mata wani abu sai kuma ta dubi screen Ιin
wayarta da ke ruri, ganin sunan Barr. Junaid yasa ta saki wani malalacin
Murmushi tare da Ιagawa ta kara a kunnenta.
"Hello" ta furta tana mai narke murya. Sallamar da
yayi mata yasa ta mayar masa da martani tana faΙin "Oh! Wa'alaikumus
Salam"
Bayan sun gaisa ne yace mata yau yana son zuwa su gaisa,
amma sai dare, babu wani tunani tace masa sai ya zo. Nan suka taΙa Ζ΄at hirarsu
daga bisani suka katse kiran bayan sun yi sallama. Ko kallonta Imaan ba ta yi
ba, infact ita ba ma gabanta Ihsan Ιin take ba.
Da daddare Barr. Junaid ya zo gidan lokacin Abba da Mami na
zaune a tsakar gidan suna hira coz dawowarsa kenan ma daga masjid. Yaro ya aiko
yace yazo yayi sallama da Ihsan, Abba yace wa yaron "Je ka ce inji
waye?"
Caraf Dada da fitowarta kenan tace "Kai yaro tsaya, je
ka ce tana zuwa" sai kuma ta mayar da hankalinta kan Abba.
"Wane irin sakarci ne haka Muhammadu? Kar na kuma ji ka
Ζara magana in an zo neman Shalele, idan ma kishi kake saboda ba takwarar
buzuwa ake nema ba to ka daina, akwai banbanci sosai tsakaninsu duk da cewa a
zahiri ba a ce ba ta sigar kamanni, Shalele matar manya ce." Tana kai wa
nan ta juya ta nufi Ιakin su Imaan tans Ζiran "Shalele! Shalele"
Ganinta cikin kwalliya da shigar riga da skirt da suka kama
ta yasa Dada faΙin "ai har kin shirya kenan?, Dama sallama ake da ke a
waje, Allah sa dai mai maiΖo ne ki samu ki rabu da gidan nan don na ga Ζ΄an
hassadarki ba su da adadi."
"Yanzu zan fito ma Ni kam."
"Yauwa, ki dai hanzarta."
Ba tare da Dadan ta ji amsar Ihsan Ιin ba ta wuce.
Turare Ihsan ta fesa wanda tun kafin ta fito Ζamshin yayi wa
su Mami da ke waje maraba.
Tana fitowa ko kallonsu ba tayi ba take ΖoΖarin ficewa, Abba
ya dube ta cike da takaici yace "Zo nan Ihsan"
Ζan Turo bakinta tayi sannan ta dawo daidai wurin da yake ta
tsaya.
"Ba ki san babu kyau mace take bayyana afonta ga wanda
ba muharraminta ba? Ga ki kin wani buΙo turare kamar mai zuwa gasar Ζamshi.
Anya Ihsan? Anya?"
Yayi shiru yana jijjiga kansa
"Ki koma ki sauya kayan nan kafin ki kwaso
zunubai."
ShagwaΙe murya tayi tace "Kai Abba, yanzu dai zan dawo
kuma na riga na sa kayan"
A Ιan zafafe Mami tace "Za ki wuce ki je ki cire ne ko
kuwa?"
"Ta cire me?" In ji Dada da ta fito daga bayi
hannunta riΖe da buta, dungurar da butar tayi ta Ζaraso wurin da suke,
sassanyar ajiyar zuciya Ihsan ta saki don dama ba ta jin za ta iya ma cire
kayan nan.
"Wuce ki je abun ki" Dadan ta faΙa tana nunawa
Ihsan Ζofa.
"Amma Dada..."
"Ya isa haka Muhammadu, wallahi daga kai har Buzuwar
matarka zan Ιata muku rai akan Shalele, ya za a yi yarinya ana jiranta waje ku
tsare ta da wasu maganganu marasa tushe?"
Cike da takaici Abba yace "Amma Dada ai haramun ne mace
ta fita waje tana Ζamshin da wani namiji zai iya..."
"Rufe min baki a nan Muhammadu, kema Rahina ki kiyaye
Ni, ba na son halinkin nan na sari ka noΖe, don haka mu fita sabgar yarinyar
nan ku daina takura mata, in Allah ya yadda ma ta kusa bar muku gidan don
jikina ya ba Ni ta samu mijin aure, ku kuma kwa yi ta zama da waccar takwarar
Buzuwar maras farin jini, aikin Banza!"
Imaan tana jinta daga Ιaki sai dai ko kaΙan ba ta ji haushin
Dada ba tun da dai ta san ba hakan ba ne, hasali ma ita ce ba ta da burin yin
auren da yanzu wata maganar ake ba wannan ba.
Ganin ta bar wurin yasa Mani faΙin "Yanzu Malam haka za
mu ci gaba da zubawa Ihsan ido sai yadda tayi?"
Abba ya dubi Mami fuskarsa na nuna zallar Ιacin rai da
rashin jin DaΙi
"Wallahi Maminsu nima na gaji da halin yarinyar nan, a
ce duk abun da take so shi za ta yi? Ina ga lokaci ya yi da kawai za ta fitar
da miji a aurar da ita kamar yadda Dada ta faΙa don wallahi Zuciyata ta gama
ganiya da munanan Ιabi'u irin na Ihsan da ta koya saboda rashin gwaΙa, idan ta
bar gabanmu ta je ta ci gaba, rayuwa ai sai ta koya mata darasi."
"A'a Abbansu, aure ba shi ne mafita ba ga Ihsan, kana
tunanin ko ta yi auren ma za ta iya zama ne? Wane namijin ne zai juri munanan Ιabi'unta?
Yarinyar da ko girki ba ta iya ba buwa uba kuma rashin tarbiyyar zama da
mutane."
Abba ya haΙiye wani abu mai Ιaci da ya tsaya masa a wuya ya
dubi Mami yace "Haba Maminsu, na gaji wallahi, Imaan ko sau Ιaya ba ta
Ζona min rai, wallahi wata rana ina ga Zuciyata fashewa za ta yi da baΖin cikin
Ihsan."
Cikin sigar lallashi Mami tace "HaΖuri za ka yi Abbansu
sannan mu Ζara yi mata addu'a, Allah ya Ζara shiryata ya kuma kare ta daga
sharrin duniya."
"Amin" kawai Abba ya iya furtawa daga haka ya miΖe
ya wuce Ιaki, itama Mami ta bi bayansa cike da takaici.
A Ιangaren Ihsan tun kafin ta fita Ζamshinta ya sanar da
Barr. Junaid isowarta, gyara tsayuwa yayi tsawon daΖiΖu biyu ta iso wurin da
yake tsaye jingine da motarsa. Shagala yayi da kallonta yana sakin murmushin da
bai san dalilinsa ba cikin ransa yana Ζara yabawa da kyau da kuma tsari irin na
Ihssn Ιin har yana jin cikin ransa babu wani Ιa namiji da ya kai shi sa'ar
samun mace.
"Ya dai?" Ihsan ta faΙa ganin yadda ya tsare ta da
ido. Ζan zabura yayi yace "I was gone with your body structure, behaviorr,
the scent and everything, I'm indeed the luckiest man ever in the world,
Ubangiji ya mallaka min ke a matsayin matata Ihsan, you're super adorable and
charming queen."
Jin yadda yake goΙa ta yasa ta wani narke tana lumshe eyes Ιinta,
ba Ζarya, ita kyakkyawa ce ajin farko don a ganinta babu wani abu da ta rasa da
wani Ιa namiji zai so game da matar aurensa da yadda zai so ta kasance
forgetting about behaviors and values wanda su ne kaΙai abun da za a ce ta yi
lacking Ιin.
"Barka da fitowa sarauniyar kyawawa."
"Barka, ya hanya?" Ta tambaye shi tana Ιan nuna
concern Ιinta gare shi.
"Lafiya Ζalau na zo, ya lafiyarki, kin bar Ni da
kewarki Ihsan"
"I'm sorry" ta faΙa a hankali "I'm also
missing you here, missing you badly Barr. You've taken something precious and
valuable from me." Cute smile ne tayi escaping kan kyakkyawar fuskarta da
ta Ζara mata kyau, kasa Ιauke idanunsa yayi daga gare ta, ji yake ina ma su
kasance tare, kasancewa irin ta har abada, Ζamshinta kaΙai ya birkita masa
lissafi har yana jin ina ma a ce mallankinsa ce a wannan lokaci, da kuwa tabbas
babu wani abu da zai masa shamaki da samun kusanci sosai da ita ta yadda zai ta
shaΖar wannan daddaΙan Ζamshi babu ΖaΖΖautawa.
"It seems like you're taken away from me Barr. Ka yi
shiru."
Dawowa cikin hankalinsa yayi yana mai kau da kansa gefe
cikin ransa yana furta astagfirullah! A zahiri kuma yace "Ke Ιin ce
princess, za ki haukata Ni, Ζamahin nan naki ya yi yawa, ki daina fitowa waje a
irin wannan yanayin saboda Ιata gari ki kuma gaggauta neman yafiyar
Ubangiji."
KwaΙe fuska tayi kamar za ta yi kuka sannan tace "Haba
Barr. Ba fa wani wuri zan je ba, just wurinka na zo, the only person I want to
spend my life with"
Ganin yadda jikinsa ya gama mutuwa yada yace "Uhm, ba
na jin daΙin jikina princess, ki koma ciki, za mu yi waya in na koma, ok?"
Ba don ta so ba tace "Ok, speedy recovery Barr. Allah
ya tsare hanya."
Da "Amin" ya amsa mata sannan ya zuba idanuwansa
cikin nata, ganin babu wani expression na Ιacin rai tattare da ita yasa yace
"Oh, sorry princess, excuse me"
Da sauri ya juya ya buΙe motarsa can ya dawo hannunsa riΖe
da wata leda babba.
"Take this, ki gaida Mama please, za mu yi waya"
Ranta ya Ιan sosu of course da yadda yayi treating nata,
amma ledar da ya miΖa yasa ta kawar da komai tana murmushi tace "Thanks
Barr. Kafin ka koma Please ka tsaya nearby pharmacy store ka sayi magani, and
don't hesitate to call me after reaching home, bye" tayi waving masa hand
shima yayi mata yana mai juyawa, da ido ta bi shi har ya shiga motarsa ya tayar
ya wuce ta baya, don ta iya nan ne mota ke iya shigowa layin. Idanuwanta ta
lumshe ta ma rasa wane tunanin za ta yi, hakan yasa ta wuce gida kai tsaye.
Tana shiga ba ta tarar da kowa a tsakar gidan ba kawai ta
shige nasu Ιakin by the time Imaan ta jima da bacci abunta, ajiye kayan tayi
sannan ta sauya zuwa kayan baccinta. Ledar ta janyo ta buΙe, babu komai a ciki
sai mayuka masu matuΖar tsada, turaruka, kayan ado, ga wani expensive agogon
hannu sai sheΖi yake, tana fitarwa taci karo da wani card mai shegen kyau. Da
sauri ta buΙe card Ιin tana karanta abun da ke ciki, bayan ta gama ta saki wani
cool smile tana faΙin "proposal card?" Sai kuma ta ajiye shi gefe,
envelope ta gani hakan yasa ta buΙe, ganin kuΙi yasa ta lumshe idanuwanta.
Lallai ita Ιin mai Sa'a ce, in da ba don sa'arta ba da yanzu
duka waΙannan na Imaan ne, "Ta yaya ma zan bar Imaan ta mallaki irin waΙannan?
Over my dead body!" Ta faΙa cikin zuciyarta, mayar da kayan tayi ta Ιauko
wani cookies da ta taho da shi daga school da kuma nutri-milk, har ta gama
cinyewa Barr. Bai kira ta ba, fita tayi ta wanke bakinta ta dawo, kwantawa tayi
ta Ιan lulluΙa blanket zuwa saman cikinta, a lokacin ne kuma kiran Barr. Ya
shigo, ba ta san lokacin da wani murmushi ya suΙuce mata ba, Ιaga kiran tayi ta
kara a kunnenta tana amsa sallamar da yayi mata.
Ta Ιangarenshi yace "I'm home Princess, na sayi drugs
kamar yadda kika ce, na kuma sha and I'm feeling better."
"Good! Yanzu dai zan bar ka kawai ka huta, da safe sai
mu yi magana ko?"
"Ba komi son magana da Ni ne yanzun?" Yayi
questioning nata.
"A'a, ai na ga ba ka da lafiya ne, You need some rest,
but if you insist mu yi hirar, I'm glad"
Dariya mai Ιan sauti yayi a nashi Ιangaren yace "You
know mu maza rashin lafiyarmu ba ta kwantar da mu, na na ji sauΖi kuma but your
voice will serve as special therapy to me."
Murmusawa Ihsan tayi sannan tace "I'm here for you
ai."
"Yauwah my princess, na gode Ζwarai, ki isar da saΖona
ga Mama ai ko?"
Yamutsa fuska tayi kana tace "Ta yi bacci ai"
"Ok, kin san ina so kowa ya san da Ni a gidanku, ina so
mu kasance tare ne soon, I promise to care for you, zan mayar da ke ne tamkar
sarauniya Ihsan, ina ji a jikina kamar na samu matar aure, Mom Ιina, sisters Ιina
will all love you I'm sure saboda suna son abun da nake so, I'll get you
everything you like princess, ni yanzun aji nawa kike ne ma kin san ba a nan
nake aiki ba, familyna duka suna Abuja."
Shiru Ihsan tayi tana wani tunanin cikin ranta, tambayarsa
da yayi mata yasa tace "200level nake"
"Ok, amma kina jin za ki iya aurena kuwa Ihsan?"
Tambaye ta zo mata a ba zata, of course she's feeling
something about him amma hakan ba yana nufin za ta amince da shi ne kai tsaye
ba, she needs to know who's he, tana son tabbatar da cewa ya mallaki duk
qualities Ιin da take buΖata a wurin mijin da za ta aura, ta fara ganin wasu,
amma ba za ta yi saurin yadda ba kada taje deceiving nata yake.
"Kin yi shiru Ihsan" ya faΙa cike da damuwa.
"Yea, why not?" Ta ba shi amsar a gajarce.
"Kar da ki ce na fiye kauΙi, ina dai jin tsoron rasa ki
ne, zan ba ki lokaci ki Ζara tunani kafin na Turo magabatana, idan iyayen ki
sun yi bincike a kaina sun kuma tabbatar na cancanci su ba Ni ke good, daga nan
sai na nema miki transfer zuwa wata private university a can Abuja Ιin in mun
yi aure, Are You pleased with what I say?"
Murmushi tayi mai Ιan sauti kana tace "Yea, thanks
Barr. Allah ya zaΙar mana abun da yafi Alkhairi."
Ya amsa mata da "Amin, na ji kamar bacci kike ji ma,
nima maganin da na sha yasa ina jin baccin, Sleep tight my queen, but always
remember one thing, you've a lover who's love can never be derailed! Ihsan I do
love you with every bit of my heart, I love you with every flow of blood in me,
you're not only my love, you're the heart in me, that heart that keeps me
living, that heat that pump blood to the whole body, idan kika ce ba ki so na,
i don't know what will actually happen, ban san ma taya sonki yayi min irin
wannan kamun ba tun ganinmu na farko, but ina fatan ki zama abokiyar rayuwata
ta har abada, i love you Ihsan"
Lumshe idanuwanta tayi, hoping that he'll have all the
qualities she need from a man saboda ya gama tafiya da imaninta, je knows how
to love, how to care and...his last sentence make her feel herself! Ta ji kamar
ta fi kowa a duniyar.
A sanyaye tace "I love you also Barr. I'm wishing you a
night full of special and sweetest dreams, good night"
Wata irin ajiyar zuciya ya sauke har tana iya jiyowa,
"Bye princess "
"Bye" daga haka kuma ta katse kiran ba tare da
jiran komai ba.
Bacci take son yi sai dai kuma tunani ba zai bar ta ba, tana
jin wani irin yanayi game da Barr amma she'll not give up so early, za ta yi
magana da Charity da Ramcy, when all went ok about Barr. Za ta yi accepting
nasa as her husband matukar yana da waΙannan qualities, tana so tayi wa sauran
mata fintinkau shi yasa take neman mijin da ya dace da ita da rayuwarta, tana
buΖatar mijin da ta tabbatar har abada Ζ΄ar'uwarta ba za ta samu ya shi ba, ya
kasance Ιan babban gida, kyakkyawa, mai tarin dukiya ta yadda ita ma zai jiΖata
da ita ta yadda za ta fito daban cikin mata, tana buΖatar mijin da ya iya
soyayya, mijin da zai kula da ita kamar sarauniya, mijin da ya gama macewa a
soyayyarta, she needs someone unique, special and best husband ever.
Gare ku Ζ΄anmata Ζ΄an Ζwalisa, tabbas an san mace da ado da
kwalliya, addini ya ba ki lasisin yinsu amma bai ce ki bayyanawa wanda ba
muharram Ιinki ba, e, babu wanda yace kada ki saka turare, turare ni'ma ne,
amma ba a ce ki saka wanda zai fita har wani namiji ya ji ba, point of view,
idan har a gida za ki saka, Ζ΄anmata ki sheΖa kwalba guda ma ko ki yi wanka da
shi ma fi mishkila, amma kuma muddin za ki fita waje,to dole ki kiyaye saka
turaren da Ζamahinsa zai fitahar wani Ιa namiji ya iya ji, in kin san turarenki
na da Ζarfi advisibly ya kamata ki saka kaΙan kaΙan gudun kada wani namijin
yaji. Kin san illar namijin da ba muharram Ιinki ba yaji Ζamshinki? Kin san
tarin zunubin da za ki kwasarwa kanki? HaΖiΖa da kin sani da ba za ki kwatanta
hakan ba.
***********
Haka a Ιangaren Barr. Ta kasance, ya gana faΙawa a soyayyar
Ihsan tabbas, he's hoping for mallakar Ihsan, tana da qualities Ιin da yake so
wurin mace, kyau, ilimi da kuma wayewa, only one thing she lacks, a iya haΙuwarsu
ya lura kamar dai addini bai wani dame ta ba, amma to him hakan ba wata matsala
ba ce duba da cewa Ιan'adam tara yake bai cika goma ba, yana fatan bayan
aurensu za ta sauya, zai tabbatar da ta samu cikakkiyar wayewar addini daga
wurinsa, not only him, his Mom and his only sister.
A can Ιangaren su AK, kasancewar bai gama da aikin da yake
ba yasa suka Ζara kwana Ιaya kan yadda da suka saka don komawa gida, sai washe
gari suka riga suka yi booking flight, shi, JK, da kuma Asim, tabbas hausawa
sun yi gaskiya da suka ce kowanne tsuntsu kalar kukan gidansu yake yi, gaba Ιayansu
ba su da wani fata a yanzu da ya wuce su gansu a Ζasarsu ta haihuwa, suga
dangi, dangi su gansu suma, a Ιangaren AK abubuwa biyu ne suka taru suka masa
yawa idan ya tuna da yunΖurin da yayi wa kansa alkawarin yi bayan ya dira a
Ζasarsa ta haihuwa, bai san ta ina zai fara ba, amma ya Ζudurta zai bi duk wata
process da ta dace don samun true love shima, a partner that'll love his
wholeheartedly not because of what he has, wacce za ta so Jalaal yake so ba
wacce za ta so Multimillionaire Abduljalaal Abubakar KuΙa ba.
**************************
Asussubar fari Imaan ta tashi ta gama aikace-aikacen gida ta
yi wanka tayi shirin tafiya wurin aiki, lokacin Ihsan ta tashi daga nata
baccin, kallon Imaan Ιin tayi tana kwaΙe fuska, abubuwan da suka faru da ita
jiya ta fara tunanowa, all that happened is because of her, Ζ΄ar'uwar da ta gama
tsana wacce a halin yanzu kuma kaso mai tsoka na tsanarta gare ta ya fara
raguwa, ita ta kawo mata Barr. Junaid tabbas, dole ta san yadda za ta yi ta ga
ta hana haΙuwar su biyun gudun kada wata matsala ta Ιullo. Da wannan tunanin
tayi shirinta na tafiya school itama.
Bayan sun fito daga lectures kai tsaye gidan Charity suka
wuce, sai da suka dafa noodles suka ci tukun suka zauna zaman hira.
Nan Ihsan ta kawo musu zancen cikin hikima tace "Babes,
let's say ni Ιin nan ba dai ina da burin kasancewa marar hamshaΖi ba, to sai
misali a ce Imaan ta gidanmu ta samu Ni ban samu ba, sai na yi amfani da
kamannin da muke na samu soyayyarsa, a ganin ku zan iya hakan?"
Dariya Charity tayi tace "Lallai duk yadda aka yi Ihsan
kin faΙa, amma dai na ji haushi da ya kasance ta hannun Imaan ya zo, amma duk
da haka ai ba damuwa ba ce, ke dai kawai ki samu daular in ya so ita ta jira
daidai ita ko ya kika ce Ramcy?"
"Ζwarai kuwa, maganar Charity gaskiya be who's that
lucky guy Ihsan?"
Idanuwanta ta lumshe tana hasaso shi a gabanta sai kuma tayi
smiling tace "Ba wani wani ba, just a Barr. Ban san ta yaya aka yi nayi
falling masa ba, amma ina son yi bincike sosai akansa, I want to know so many
things about him, ba na son ba shi dama while bai cancanta ba."
Cike da mamaki Charity tace "Ta yaya bai cancanta ba,
ai na san duk namijin da Ihsan ta kware masa wallahi ya cancanta, Ramcy me kika
ce?"
"Haka ne kam, ina fatan dai Ιan Abuja ne kin ga sai mu
yi aurenmu kusan lokaci guda ko?"
Murmusawa Ihsan tayi tace "Me kike ci ne haka Ramcy?
Idan har ba Ιan nan ba kin san babu inda zan zauna a Nigeria, ke nifa ban Ζi in
mun yi aure ba ya bar Ζasar, ya samu aiki abroad mu tafi abunmu kada Ζ΄an sa ido
su mana yawa."
"Ai kuwa dai, wallahi Ni Ko danginsa ba na so su raΙe
mu Ihsan, ina so mu kasance daga Ni sai shi, sai kuma Ζ³aΖ΄anmu."
Haka dai suke ci gaba da hirarsu, daga nan suka yi bacci,
sai wuraren uku na rana suka tashi, ba su damu da yin salla ba suka yi wanka
Ihsan ta saka kayan Charity kasancewar tsahonsu kusan Ιaya, daga nan tayi
dropping kowannensu.
Who are the
untouchables????
(Su wane ne untouchables)
Su uku ne Ζawaye kuma aninan junansu suka yi wa kansu take
da Untouchables, sun kuma amsa sunan nasu na untouchables saboda sun gagari
kowa babu kuma wani mahaluki da zai taΙa Ιaya daga cikinsu ya kwana lafiya.
Khadija Muhammad Nadada (Ihsan), Rahama Uba Mairiga (Ramcy)
sai kuma Nusaiba Bala JiΖamshi (Charity).
Abotarsu ta fara ne da mutum biyu, Ihsan da kuma Charity,
abotar ta fara ne a ranar da suka fara Ιaukar karatu kasancewar sun zauna wuri
guda, daga yanayin sutura, kayan Ζawa da kuma ado da Ihsan ta gani jikin
Charity yasa taji cewa ta kai matsayin Ζawar da za ta iya kulawa, ta rasa ta
ina za ta fara mata maganar kwatsam sai Lecturer nasu yayi tambaya ya kuma fara
cankar waΙanda za su amsa, fatan Ihsan bai wuce a canko Charity ba kuma a ce ba
ta san amsar ba, kamar Lecturer ya san me ke zuciyar Ihsan kawai ya canko
Charity ya kuma maka mata tambayar da ba ta san amsarta ba, wannan abu ya
matuΖar yi wa Ihsan daΙi kasancewar ta samu damar kula Ζ΄ar masu kuΙi ai kuwa
tayi sauri ta rubuta a paper ta turawa Charity gabanta, a lokacin da Lecturer
ya maimaita mata tambayar kuwa ta karanta abun da Ihsan Ιin ta rubuta mata, ai
kuwa Lecturer ya ce daidai ne a mata tafi. Daga nan Charity ta zauna ta yi wa
Ihsan godiya ta kuka buΖaci da su zama Ζawaye, babu musu Ihsan ta amince don
dama abun da ke ranta kenan kuma ta Ζudiri cewa ko ta halin ΖaΖa sai ta yi
abota da Charity Ιin sai kuma Ubangiji ya sauΖaΖa mata aikin.
Tun daga wannan rana suka Ιinke suka zama abokan juna, sannu
a hankali kuma Charity kan ba wa Ihsan kayayyakinta idan sun je gidanta,
Charity Ζ΄ar masu hannu da shuni ne, mahaifinta Shahararren Ιan siyasa ne a
jahar Kaduna, Alhaji Honourable Bala JiΖamshi, ta kuma kasance Ζ΄a Ιaya tilo ga
iyayenta, hakan yasa take da gata sosai, duk abun da take so in dai kuΙi na
mallakarsu to ba ta rasawa, Charity kyakkyawa ce ita ma, sannan kuma mace ce da
abun hannunta bai rufe Mata ido ba, yadda take kyautatawa mutane yasa Ζ΄an
ajinsu suka mata laΖani da Charity Don in ta so tana iya siyawa gaba Ιaya Ζ΄an
ajin handout.
A wani Ιangaren Ihsan kuma Ιiyar talakawa ce da Ζ΄ar'uwarta
ke Ιawainiya da karatunta sai dai a yanzu Ιawainiyar school fees kaΙai ke a kan
Ζ΄ar'uwar, sauran abubuwa kamar su kayan karatu, abun hawa, da sauransu suna kan
Ζawarta ne Charity da suka kasance tamkar wasu Ζ΄an'uwa saboda aminci. Ihsan na
amfanuwa da dukiyar Charity yayin da ita kuma Charity ke amfanuwa da ilimin
Ihsan Ιin.
Haka suka ci gaba da rayuwarsu har Allah ya haΙa su da
Ramcy, Ιiyar wani Barr ne wanda ake matuΖar ji da shi a garin Azare kuma babu
laifi yana da hali da kuma rufin asiri. Ramcy, wacce ita nata jiji da kan na
daban ne, da faΙa abun nasu ya fara lokacin da ta so taka Ihsan, sai kuma reshe
ya juye da mujiya, tun daga nan kuma sai aka Ιinke. Su ukun komai nasu ya sha
bambam da sauran mutane kama daga shigarsu, suturar da suke sawa, mindset Ιin
su da dai sauransu. Za mu iya cewa kai tsaye Ihsan da Ramcy sun yi gamayya ne a
halin dogon buri da son zuciya, in dai har za su samu to su fa kada kowa ya
samu, sun kuma yadda cewa za su iya komai don su su samu ko ta kan wa ta faΙo
yayin da Charity kuma ta ciri tuta domin ita macece da abun duniya bai wani
dame ta.
A takaice waΙannan su ne untouchables.
BABI NA 7
KUDA ESTATE, BAUCHI BAUCHI STATE.
Tun bayan sallar la'asar a part Ιin Ummah ake shirye-shiryen
tarbar mutanen Bloordale village, girki iri-iri aka yi kasancewar Flight Ιin
1pm zai biyo wanda a Nigeria kuma zai yi daidai da Ζarfe 6pm na yamma, sosai
aka gama komai akan lokaci sannan Ummah ta sa aka gyarawa AK room Ιinsa aka
saka turare. A daidai lokacin da jirginsu yayi landing aka gama clearing komai
suka Ιungumo gaba Ιayansu, Asim, JK and AK, dialling number Sulaiman yayi, a
friend of him wanda yazo aiki Jos kuma da yiyuwar zai tafi a ranar, hakan yasa
ya biyo su tafi tare. Ana wasa ana dariya suka nufi motar ban da AK da
tunaninsa ya tafi wani wuri na daban, bayan sun shiga Mota Sulaiman ya ja
motar, a hanya suka tsaya suka yi sallar Magrib tukun suka wuce, ana kiran Isha
suka isa Bauchi, kai tsaye estate Ιinsu suka wuce.
Kasancewar babu wanda ya san da dawowarsu in ka cire Ummah,
Ummie Abbie, Uncle N, Abba da kuma Mammah. Part Ιin Abbie kai tsaye suka nufa,
tun lokacin da motarsu ta gama parking ma'aikatan sashen suka nufo motar don
sun san waye Sulaiman ga AK Ιin. Suna fitowa ma'aikatan suka biyo su da
kayayyakinsu ciki. Ummah wacce ke zaune a parlour ta ci kwalliya tana zaman
jiransu miΖewa tayi kai tsaye ta nufe su fuskarta sake.
Mutanen Bloordale village sai yanzu kuka iso?"
Cikin sakin fuska JK yace "Wallahi Ummah."
Ba tare da mayar masa da amsa ba ta mayar da kaklonta ga AK
wanda ya saki fuskarsa kaΙan.
"It seems like you're exhausted, ku samu ku watsa ruwa
sai ku ci abinci. Asim mutanen Bloordale." Ta Ζarasa tare da riΖo hannun
Asim Ιin. "Ba magana ne? Ko dai Jalaal ya hana ka magana ne?"
Dariya Asim yayi yace "A'a, ina wuni Ummah"
"Lafiya Ζalau, yau dai sai wurin Mom ko?"
Asim yayi dariya yace "in dai ba ta zo ta Ιauke Ni ba
ba zan je ba. Zan zauna tare da Ya Jahaan."
Ummah tayi dariya tace "To ka samu ka watsa ruwa kaima,
he's your own room here" ta nuna masa da yatsa
"Thank you." Daga nan ya nufi Ιakin da gudu.
Shigowar Ζ΄anmata da kuma yaran gidan daga sassa daban-daban yasa Ummah
Ζarasawa wurinsu tana musu sannu da shigowa. Wurin suka samu suka zauna tare da
gaida Ummah, amsarsa tayi cikin fara'a tana faΙin "Sun iso yanzu, wanka
suka shiga."
Tana kai aya ta zauna itama kusa da Ζ΄anmatan tare da
nazartarsu Ιaya bayan Ιaya tana son gano Ζudirirrikan kowannensu.
Tsawon wasu mintuna JK da kuma Asim suka fara fitowa, cike
da girmamawa Ζ΄anmatan suka gaishe da JK Ιin shi kuma Asim ya gaida su.
Suna gaisawar AK ya fito, ji yayi kamar ya koma ganin yadda
Safnah, Manal da kuma Nimra ke bin sa da kallo without minding that Ummah na
zaune a parlourn. Siririn tsaki ya ja ciki-ciki sannan ya Ζaraso, fara gaishe
shi suka yi Ιaya bayan Ιaya kowa da irin nasa salon na jan hankali, a daΖile ya
amsa musu kai tsaye ya wuce dining, murmushi Ummah ta saki don zuwa yanzu ta
gama fahimtar kowaccensu ta kuma ta matuΖar jin daΙin yadda AK Ιin bai sake
musu fuska ba, itama miΖewa tayi tana faΙin "Ku tashi ku ci abinci
Ζ΄anmata." Ba musu suka miΖe kowacce tayi Tata hanyar zuwa dining, Nimrah,
Safnah da Manal da kowacce ta ji dadin yadda AK bai ba wa Ζ΄ar'uwarta amsa cikin
kulawa ba, that means duk cikinsu babu wanda yake da muhalli cikin ransa. Hakan
yasa suka bi Ummah kowacce na saΖa ta yadda za ta mallaki AK Ιin ya zamo nata
bisa huΙubar iyayensu.
A Ιangaren AK gaba-daya ba a sake yake da su ba, hakan yasa
bai wani ci da yawa ba ya miΖe, Ummah ce ta dube shi tace "Ya dai
Son?"
Shafa cikinsa yayi yace "I'm satisfied."
Cike da kulawa tace "Har yanzu Ιabi'arka tana nan
Jalaal, Allah ya shirya ka"
Cikin ransa ya amsa da "Amin" sannan ya fice,
garden ya nufa kai tsaye, Ιaya bayan Ιaya Ζ΄anmatan suka yi wa Ummah sallama
suka wuce wanda hakan ya matuΖar ba wa Ummah dariya sai ta bi su da kallo.
A can garden Jahaan ya tarar da Jalaal suka wuce sauran
parts Ιin gidan suka yi gaisuwa, sun samu tarba wurin Mammahn Jahaan da kuma Aunty Salaha abokiyar
zaman Mammah wato Maman Manal. Bayan gaisuwa shi kam Papa cewa yayi su haΙu da
safe don a gajiye shi ma yake. Daga nan suka nufi part Ιin uncle N, shi kam ba
su tarar da shi ba, Aunty Dr. Ta tarbe su sosai haka suka yi Ζ΄ar raharsu kamar
dai yadda suke yi da mijinta. Part Ιin Daddy ma ba laifi Nenne mahaifiyar Nimra
ta tarbe su akasin Mamah uwargidan Daddy wacce bayan gaisuwa babu wata magana
ma da ta Ζara haΙa su, ko da suka tambaye ta Daddy ce musu tayi ba ya gari. Ba
tare da saka hakan a ransu ba suka yi sallama, Jahaan ya wuce sashensu, shima
Jalaal ya wuce wurin Ummie yana fatan Allah ya sa ya samu sauyi a wurinta.
Da sallama a bakinsa ya shiga parlourn nata wanda ke fitar
da wani sassanyan Ζamshi, idanuwansa ya lumshe saboda yadda Ζamshin ke ratsa
ko'ina na jikinsa, jin babu wanda ya amsa yasa ya tabbatar da cewa Ummien na
ciki. Ajiyar zuciya ya sauΖe tare da nufar bedroom Ιin nata, knocking ya fara
yi kafin ya murΙa handle Ιin a hankali bakinsa Ιauke da sallama, amsa masa
Ummie tayi ba tare da ta juyo ba, bai yi mamaki ba don tsawon rayuwarsa ba zai
ce yau Ummien ta saka idonta a nasa ba in za ta masa magana, hasali ma ba ta
yin doguwar magana da shi. Ζarasawa yayi kusa da sallayar da Ummien ke zaune a
kai ya Ιan tsugunna yana mamakin irin kwarjinin da kullum mahaifiyarsa ke
Ζarawa gare sa. Cikin sanyin murya yace "Sannu da gida Ummie, mun same ku
lafiya."
A taΖaice tace "Lafiya Ζalau, kun iso lafiya?"
Yace "lafiya Ζalau"
Ummie tace "To ma sha Allah, ya aikin?"
"Alhamdulillah Ummie"
Tace "haka ake so, a dai kula a kuma yi aiki da
adalci."
"In sha Allah " daga haka ya ja bakinsa yayi shiru
yana fatan a yau ta kawo masa wani zancen har ya samu damar yin doguwar zance
da ita, sai dai jiya iyau, itama shirun ta masa. Ya jima a zaune sai da ya gaji
ya miΖe tsaye yana faΙin "To Ummie, idan Abbie ya shigo ki sanar masa mun
dawo lafiya, Allah ya tashe mu lafiya."
Da "Amin" ta amsa masa, cikin sanyin jiki da ruhi
ya fito daga Ιakin.
Fitowarsa ya ga wulgawar mutum, amma sai ya basar kasancewar
babu wani mahaluki a gidan bayan shi, Ummie da kuma Ummah, sau tari yakan ga
irin waΙannan
Sashen Ummah ya nufa kai tsaye, kamar yadda yayi tsammani
kuwa Ummahn tana zaune a parlourn kuma ya tabbatar da cewa shi take jira, tun
yana yaro ΖanΖani yake matuΖar so da Ζaunar Ummah, halacci da kuma kararta gare
shi ba ta da iyaka, abun da ya rasa a wurin mahaifiyarsa shi ya samu wurinta,
tana nuna kulawarta gare shi, ta Ιauki damuwarsa a matsayin tata, ta kuma
sadaukar masa da abubuwa da dama saboda farin cikinsa. Anya akwai irin waΙannan
matan a duniya? Akwai matan uba irin Ummah kuwa? Da a ce matan uba za su riΖi
Ζ΄aΖ΄an abokan zamansu irin yadda ta riΖe shi, to babu shakka da babu wani
mahaluki da zai yi kukan maraicin uwa a duniya wai don tasa ta gusa a gefensa.
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauΖe tare da daidaita kansa ya
shiga ciki yana sallama. Ummah ta amsa tana faΙin "Na Ιauka ba za ka jima
ba son, ina ta jiranka. Asim har ya yi bacci Abunsa."
Cike da kulawa yace "Ayya Ummahta, mun Ιan zagaya gidan
ne."
Wani abu ne ya tsaya mata a maΖoshi, da Ζyar ta haΙiye tare
da ΖirΖirar murmushi tace "Ai ka kyauta, Allah ya saka da Alkhairi."
"Amiin Ummahta."
Kuncinsa ta Ιan ja tace "Yau dai na san ka gaji, duk
irin kewarka da nake dole na bari ka huta sai mu samu lokaci, yanzu na san kana
buΖatar hutawa, da safe sai mu yi hirar."
"To Ummahta, zan shiga ciki" ya Ζarasa kusa da ita
ya riΖo hannunta yayi kissing sannan yace "Ubangiji ya tashe mu
lafiya."
"Amiin my son, bari na biyo ka da wani abun don na ga
ba ka sake ka ci abinci ba, je ka ina zuwa " babu musu Jalaal ya wuce nasa
Ιakinsa, yana toilet ya jiyo Muryar Ummah jikin Ζofar tana faΙin "Make
sure You eat son, sai da safe." Daga haka ta fice daga Ιakin tare da rufe
entrance door ta wuce nata Ιakin.
Samun kanta tayi da kiran wayar Yaya Zinatu. Cikin Sa'a kuwa
wayar ta shiga, bayan ringing Ιin da ta fara Yaya Zinatu ta Ιaga. Ajiyar zuciya
Ummah ta sauΖe suka gaisa. Yaya Zinatu tace "A'a, Asiya lafiya dai in ce
don ban yi tsammanin kiranki ba."
Ummah ta marairaice fuska tace "Haba Yaya Zinatu, kin
san dai ke nake tunkara da duk wata damuwata, ko so kike na tunkari Yaya Babba
da zancen ta haΙa da Ni da ke ta zazzage mu?"
"A'a, yanzu dai faΙa min me ya faru."
Ummah ta sauΖe numfashi tace "Ai ba abun da bai faru ba
Yaya Zinatu, ya kamata mu yi abun da ya dace kawai, yau Jalaal ya dawo, tun
safe nake kiran layinki zan ce miki Karimah ta haΙo kayanta ta zo amma shiru
Layinki ba ya tafiya."
Yaya Zinatu tace "Ayya, kin san wayar tawa ce ta samu
matsala sai Ιazu na samu Alqasim ya gyaro ta."
"Kai Yaya, wai ke wayar ma ba za ki sayi ta arziΖi ba?,
Shi ke nan dai, zan tura Miki kuΙi ki sayi wata, don a kwanakin nan zan yi ta
nemanki."
Yaya Zinatu tace "Tooo, to na gode Ζanwata, yanzu dai
faΙa min me yake faruwa na ji hankalinki a tashe."
Ummah ta furzar da wata zazzafar iska sannan tace "Ai
ina faΙa miki Yaya, muna nan muna shiri ashe dangin uban yaron nan ma nasu
shirin suke yi?"
"Kamar yaya kenan Asiya?" Yaya Zinatu ta tambaya
cikin son sanin me yake faruwa.
"Hmm" Ummah ta faΙa "Ina faΙa miki ai yaron
ya dawo Ιazu, babu tsammani kawai sai ga Ζ΄anmatan gidan Ιaya bayan Ιaya kamar
haΙin baki, wallahi duk ina lura da su akwai abu a zukatansu. Wallahi yaron yan
tashi suka suka fice simi-simi suka bar Ιakin, shi yasa kawai nake so Karimah
ta dawo gaba Ιaya zuwa hutun nasa ya Ζare, Ni kuma zan tunkare shi da maganar
na san ta Ιangarensa ba za a samu matsala ba, kin ga idan haka ta faru duk na
wurin dangin uban za a watsar da su, daga nan uban zai bayar da goyon bayan yin
auren. Daga nan kuma sai mu yi abun da ya kamata."
"Gaskiya Gara da kika sanar da Ni da wuri, gobe-gobe
Karimah za ta taho, Ni kuka zan je wurin Malam na masa bayanin komai in da
taimakon da zai bayar to, kin san aikinsa kamar yankan wuΖa haka yake."
"To shi ke nan, zan haΙa Miki da kuΙin wayar da na
malam Ιin na tura Miki. Ki yi abun da ya kamata kawai. Fatana dai burinmu ya
cika, ba wai mu sarawa doki ciyawa ba."
Cikin Ζarfafa guiwa Yaya Zinatu tace "Haba dai Asiya,
ki ma bar batun sarawa doki ciyawa, bautar da kika yi ta shekaru ba za ta tafi
a banza ba, na san ki kuma na yadda da ke, za ki yi nasara, burinki zai cika
babu wani mahaluki da zai hana hakan, idan kuwa wani ya kutso doke mu yi
maganinsa. Wannan shi ne."
Ummah tace "Yauwa Yaya Zinatu na gode sosai, Allah ya
bar Ζauna."
Daga haka suka yanke kiran. Umma ta sauΖe ajiyar zuciya a
nata Ιangaren tana fatan burinta ya cika, tana da kyakkyawan tabbacin cewa da
zarar Jalaal ya auri Karimah, burinta ya gama cika, a wannan lokacin ta
tabbatar babu wani mahaluki da zai iya Ζwace shi daga gare ta, daga nan za ta
fara aiwatar da Plans Ιin ta over him and his father, da zarar ta gama mallakar
komai kuma, za ta yanke duk wata alaΖa da ke tsakaninsu bayan tabbatar da cewa
su Ιin ba za su Ζara moruwa ba, wanan shi ne sakamakon da za ta yi wa Ιiyar Ζ΄ar
aikinta da ta aurawa mijinta don ta haifa mata yaro ko yarinya daga nan kuma ta
kashe ta, sai dai gashi yanzu ita ba ta tsira da komai ba sai yaron gaba-daya
ta kwace mata mijin nata a hannunta ta kuma kwace duk wani so da kulawa da take
samu a ce a wurinsa.
Zaria, Kaduna state.
Suna kashe kiran Yaya
Zinatu ta sakin wani makirin murmushi tana Ζwalawa Ζ΄arta kira. "Karimah,
Karimah"
"Yes Mommy, ina zuwa."
Daga wurin da take tace "Yi maza ki zo, abun nema ya
samu." Jin abun da Mommy tace yasa ta yi saurin zaro wayarta ta fito daga Ιakinta
zuwa parlourn tana faΙin "Mommy me aka samu?"
Mommy ta nuna mata gefenta tace "Samu wuri dai ki zauna
tukun" zama Karimah tayi tare da mayar da hankalinta kan mahaifiyar tata.
"Mommy ina jinki?"
Nutsuwa Mommy tayi tace "Kina ji na ko?" Karimah
ta gyaΙa kai
"Yanzu na samu kira daga Asiya, kuma kiran saboda ke
ne, don haka tun kafin na faΙa miki saina kafa Miki sharruΙa"
Shagwabe fuska Karimah tayi tace "Kai Mommy, nikam in
za ki faΙa min kawai ki faΙa ba wai kina ja min rai ba."
"Ke matsalata da ke kenan, anya za ki min abun da ya
kamata ma kuwa?"
"Zan yi mana" Karimah ta ba ta amsa tana Turo
baki.
"Yauwa, ko nutsu ki saurare Ni Karimah, wannan dama ce
da ta zo mana bagatatan duk da mun daΙe muna jiranta, wallahi kika kuskura
wannan dama ta suΙuce mana sai na ba ki mamaki. Kina ji na?"
Ta gyaΙa kai tare da mayar da hankalinta ga Mommy ganin
she's damn serious.
"Lokaci ya yi da za mu yi amfani da damar mu mu cika
namu muradan, na farko, gobe za ki wuce Bauchi gidan Asiya akan batun yaron
mijin nan nata Jalaal, kin san yaron an ce a Ζiyasi ya fi kowa kuΙi a gidan in
ka cire mahaifinsa wanda shima kuΙin mahaifin nasa kinga kamar nasa ne tun da
shi Ιaya ya haifa."
Mommy ta saurara sannan ta ci gaba "To, ita Asiya so
take ki aure shi dama ai kin sani, amma fa ba don Allah take so ya aure ki ba
sai don nata burin ya cika wanda ba zan
faΙa Miki ba a yanzu sai zuwa lokacin da kika fahimta da kanki. Ki tuna kema
kina da naki burin haka nima mahaifiyarki, za mu yi amfani da damar nan ne mu
taimaka mata ya aure ki kamar yadda take so sai dai muma a namu Ιangaren ta
taimake mu ne, idan har auren nan ya tabbata mu kuma daga nan za mu fara buga
namu wasan kin gane?"
Wani irin murmushi Karimah tayi tana lashe baki "Kai
Mommy wallahi kanki yana ja da yawa, Ni dai damuwata na aure shi kawai,
kyakkyawa ne, da kika yi batun kuΙin nan sai naji kamar in na aure shi ma na
raba shi da kowa nasa don na mora da yawa, amma Mommy ya zan yi da Nasir?"
"Nasir Ιin banza! Ke fa Karimah matsalata da ke sai ana
zancen hankali ki fara mana shirme."
"Yi haΖuri Mommy kin san Nas yana kashe min kuΙi kuma
shima aurensa zan yi don kuwa samun Namiji irin Nas a shimfiΙa..."
Ζaka mata duka Mommy tayi tare da buge bakinta cike da
takaici tace "Sakarya kawai, wallahi ki ma rabu da Nasir Ιin nan don
ubanki, ina ΖoΖarin rufa Miki asiri kina ΖoΖarin tona min ko? To wallahi
Karimah in kika rasa yaron nan Jalaal kin baΙe a Ζasa, yaro ga kyau ga kuΙi? To
wallahi ki nutsu, yanzun nan ina sallamarki ko haΙa kayanki. Sannan in kin je
za mu ke waya amma ban yadda Asiya ta san cewa muna magana ba, ko ta tambaye ki
kice mata ba ma waya don ina so komai ya tafi yadda ya kamata. Kin gane?"
Karimah ta gyaΙa kai tana faΙin "Ba ki da matsala Inna
Uwata, ai ki ma rubuta cewa Jalaal ko? Yauwah ki rubuta cewa mun yi aure, duk
yadda zan yi na jawo hankalinsa gare Ni zan yi, ke kin san Ni ba wasa ba ce
amma ina so ki Ζara Ζaimi wurin malaman nan naki da suna maka aiki yake ci. A
yi auren kawai da wuri, ke kuma ki yi naki aikin ko?"
Murmusawa Mommy tayi tace "Yauwah Baby, ki je ki haΙa
kayan, kafin ki tafi goben kya biya ki siyo min waya don Asiya ta Turo min kuΙi,
duk yadda aka yi akwai abun da take Ιoye min tun da har ts Turo min uban kuΙin
nan duk son zuciya irin na Asiya, amma dai zan tabbatar da cewa ta banbance
tsakanin aya da tsakuwa, dole!"
MiΖewa Karimah tayi tana yauΖi kana ta nufi Ιakinta da sauri
ta fara haΙa kayanta
BABI NA 8
Asubar fari AK ya farka bakinsa Ιauke da addu'ar tashi daga
bacci, Ζara lumshe Idanuwansa yayi kamar mai shirin komawa baccin yana ΖoΖarin
tuna fuskar da ya gani a cikin mafarkinsa na yau, fuskar mace! Abun da bai taΙa
mafarki da shi ba bayan Ummiensa. Me ke shirin faruwa da shi? Je asked himself
"dreaming of a lady? Who's she and
what's her intention towards me?" Ya furta cikin muryarsa da take dishe
sakamakon baccin da yayi. Jin alamun shiga salla yasa ya mike da sauri ya diro
daga kan bed Ιin nasa tare da nufar bayi, a gurguje ya watsa ruwa ya Ιauro
alwala sannan ya fito ya sanya jallabiya ya Ιan fesa turare. Lokacin da ya isa
ya tarar har an yi raka'a Ιaya, bayan an idar ya rama wacce ta kuΙuce masa
sannan yayi azkar Ιinsa a cikin
masallacin sai da ya gama ya fito, ganin shi kadai ne ya rage yasa ya
wuce part Ιinsu kai tsaye, ko da ya koma bedroom nasa ya so ya koma bacci but
baccin ya Ζi zuwa masa, gaba Ιaya yarinyar da yayi mafarki yau da ita ya gagara
manta fuskarta, da ya rufe idanuwansa sai ya ga fuskarta cikin damuwa.
Ganin ya kasa cire ta cikin ransa yasa yayi tsaki ya miΖe ya
Ιauko Alqur'ani ya fara karantawa, few minutes after ya fara jin bacci, hakan
yasa ya ajiye Qur'anin akan bedside drawer, nan wani daddaΙan bacci ya kwashe
shi shi ne har wuraren 10 bai fito ba, Ummah takan kewayo ta duba shi ganin
bacci yake yasa take fitowa ba tare da tashinsa ba.
Wuraren 10:34am Jahaan ya shigo part Ιin nasu ganin shiru
Jalaal Ιin bai fito ba tun da ya san cewa suna da appointment da Papa, not only
papa, Daddy Abbie duka ba su haΙu ba bare su gaisa jiya.
Da Ummah ya ci karo a parlour, ya risina ya gaishe ta, ta
amsa masa a daΖile, bai damu da hakan ba saboda ya saba da hakan, abu Ιaya shi
ne bai san dalilin da yasa Ummah ke masa hakan ba, idan tare da Jalaal suka
shigo za ta karΙe su hannu biyu tayi ta tarairayarsu har da wasa da dariya amma
in shi Ιaya ya shigo to fa da Ζyar yake samu ta amsa gaisuwarsa ma, tun suna
yara ya lura da hakan sai dai kasancewarsa mutum dai bai iya saka damuwar kowa
a ransa ba yasa bai taΙa ko da baiyanawa wani ba, amma kuma tabbas akwai abun
da yake hasashe tattare da hakan.
Kai tsaye Ιakin AK ya nufa, ya murΙa handle Ιin tare da
shigewa ciki yana sallama, yadda ya tarar da shi hankali kwance yana bacci ga
wani cool smile kan fuskarsa yasa ya zaro idamuwbsa with full excitement ya
Ζarasa bakin gadon. Mutumin da in har aka taΙa handle Ιin Ζofa duk baccin da
yake yake farkawa abun mamaki yau ga shi har sallama an yi amma shiru. Fatan
Jahaan Ιaya, Allah ya sa hasashensa ya zamo gaskiya. A bakin gadon ya zauna
tare da Ιago hannun AK ya saka hannunsa, sai kuma yayi amfani da Ιaya hannun
nasa wuri tapping bayan AK Ιin yana faΙin "Wake up dude! Wake up!"
Kamar wanda aka zabura AK ya ce "Don't worry, I'm with
you"
Mamaki Ζarara ne ya bayyana kan fuskar Jahaan Ιin jin abun
da AK ya faΙa,take ΖwaΖwalwarsa ta hasaso masa abun da yake fata, ganin eyes Ιinsa
a rufe yasa JK Ζara tapping bayansa yace "Oh yea, wake up dude! Papa na
jiranmu fa." Wannan karon a zabure AK ya tashi ya zauna yana murza eyes Ιinsa.
Instead of seeing his dream girl sai yaga JK, wani dogon
tsaki ya sake yana bin JK da mugun kallo wanda sosai ya ba shi dariya, kasa
riΖe dariyar yayi ai kuwa ya fashe da ita har yana riΖe cikinsa. Ζuluwa sosai
AK yayi don haushin JK Ιin yake ji haka kawai, not only because ya katse masa
mafarkinsa, but yadda yake wani masa dariya. Sai da JK yayi dariyarsa har ta
ishe shi tukun ya dubi AK yace "tell me who's she, Who's that luckiest
girl da tayi taking mind Ιin Mr. Perfect Ιinmu?"
Wannan karon iya Ζuluwa AK ya yi, hakan yasa ya ja tsaki
tare da direwa daga kan bed Ιin ya shige toilet, dariya JK yayi yace "Za
ka fito ka same Ni ne, amma na riga na gano ka kuma sai ka faΙa min who's she,
yauwah."
Ko da AK ya shiga bayin maimakon yayi abun da ya kai shi sai
ya samu wuri ya tsaya ya naΙe hannayhensa a Ζirji tare da lumshe Idanuwansa don
son tariyo mafarkin yarinyar da ya Ζara yi da safe kuma, bai ga komai ba sai
duhu, hakan ya sa ya Ζara jan wani tsaki yana faΙin "Why should I even
mind about her?"
"Ki fita daga heart Ιina please,I'm not man of women
ok?" Duk maganar da yake yi cikin zuciyarsa yake, haka kawai kuma bayan ya
yi zancen zucin sai yake ganin kamar bai kyauta ba, da sauri zuciyarsa tace
masa "Duk Jahaan ne ya jawo maka, You should have now asked her who's she
amma ya katse maka baccinka." Tsaki ya ja tare da nufar heater, ya danna
switch, sannan ya tara ruwa mai Ιan zafi cikin Jacuzzi. Bayan shafe lokaci can
ya fito sanye da milk bathroom yana goge sumarsa da wani Ζaramin towel fari.
Kansa ya kawar gefe ganin har lokacin Jahaan na nan, dariya
Jahaan ya kwashe da ita, take ransa ya Ιaci sai dai yayi controlling temper Ιin
nasa ne ta hayan nufar mirror, mazauni yayi wa kansa da mirror stool Ιin tare
da ci gaba da goge sunar tasa.
"Ko ma dai me za ka yi today you must tell me who's
she" Jahaan ya faΙa sounding so naughty.
Bai kalle shi ba AK kam ya miΖe ya janyo trolley Ιin da ya
zo da ita, kaya ne kala biyu a ciki sai gayyar turaruks da kuma mayukansa na
shafawa. A hankali ya fito da su Ιaya bayan Ιaya ya jera kan dressing mirror Ιin
har lokacin JK na nan ya kwanta kan bed.
Bayan ya gama fitar da komai na cikin trolley Ιin ya Ιaga ta
tsaye sannan ya dawo gaban mirror, mayukansa ya shafa a Nutse sannan ya saka
wata white soft t-shirt mai kyan gaske, bayanta an rubuta The young shall grow
sai wani baΖin jeans da ya Ιan Ζama shi. Turarukansa ya fesa haka kawai ya
tsinci kansa da kallon mirror, murmushi ya sake tare da shafa lallausar sumar
kansa. Bai bi ta kan JK Ιin ba ya nufi hanyar fita, hakan ya sa JK dirowa daga
kan gadon babu shiri ya yi tsalle ya cafko shi "Haba dude!"
Kallonsa AK ya tsaya yi ba tare da ya ce komai ba
"Kawai daga faΙan gaskiya?" Sau kuma ya sake shi,
bai ko Ζara juyowa ya kalle shi ba ya fice, bayansa Jahaan Ιin ya biyo suka
wuce dining. Ζauke da mutmushi kan fuskarsa ya Ζarasa ganin Ummah na zaune tana
karyawa.
"Yau dai kam an huce gajiya son, irin wannan bacci
haka?"
Kansa ya kawar gefe tare da faΙin "Wallahi na gaji ne
sosai, good morning Ummah"
"Morning my son, ka tashi lafiya?"
A taΖaice yace "Lafiya Ζala"
jajaanbne ya dube ta a mutunce yace "Ina kwana
Ummah" Jahaan Ιin ta duba har tana jin kamar ta shaΖe shi sai dai yaya za
ta yi? Murmushi ta yafa akan fuskarta tace "Lafiya Ζalau, Ya gidan
naku"
"Lafiya lau" shi ma ya ba ta amsar fuskarsa babu
yabo ba fallasa cikin ransa yana tunanin irin alternation na Ummah. Zuba musu
girkin suka ci, bayan sun gama ta dube su ganin sun nufi hanyar waje tace
"Ba dai fita za ku yi ba ko yarona?"
Dalatawa dukkansu suka yi, Jahaan ya sauΖe ajiyar zuciya don
dama can jikinsa ya ba shi za a rina, ya rasa why Ummah ba ta don alaΖarsa da Ιan'uwansa,
is it because of her selfish interest or something else Allah kaΙai ya san
mata, shi dai zai ci gaba da haΖuri don ba ya jin zai wani ba ta damar tasiri
cikin Ζ΄an'uwantakarsu.
Amsar da Jalaal Ιin ya ba wa Ummah ne yasa ya Jahaan saurin
ficewa don jiransa a waje.
"Yanzu Son ba za a huta ba? To shi ke nan, ka samu ka
je ka dawo za mu yi magana ne."
"To Ummah"
"Kar ka daΙe ka ji?"
Ya gyaΙ mata kai sannan ya fice. A waje ya tarar da Jahaan,
kai tsaye part Ιin Papa suka nufa Jahaan sai tsokanar AK yake shi kuma ya Ζi
tanka masa.
Mammah suka fara gani a parlourn tana kallo, gaishe ta
Jalaal yayi a mutunce ita kuma ta amsa masa fuska sake sannan tace "Ai
dama na san can ka yi, to ga can breakfast ku je kuyi ko?"
Da sauri Jahaan yace "Mammah ai mun yi a wurin
Ummah" fuskarta ta Ιan sauya kaΙan don har ga Allah ba ta wani son yarin
nata yake cin abinci a sashen Ummahn. Ganin yadda fuskarta ya sauya yasa yayi
saurin faΙin "Mammah don Allah ki ce wa Papa ga mu nan"
Ya yi hakan ne gudun kada AK ya fahimci wani abun. Ζan
murmushi tayi tace "Ai da ya fice abun sa, ya yi ta jiranku har ya gaji ya
koma Ιakinsa bari na masa magana."
Tana faΙin haka ta wuce bedroom Ιin Papa babu jimawa sai ga
shi ya fito cikin manyan kaya, tun da ya hangi yaran nasa ya saki fuska, da
sauri Jalaal ya Ζarasa kusa da shi ya ba shi side hug yana faΙin "Good
morning"
"Morning... Ka tashi lafiya"
Jalaal yace "Lafiya lau."
Zama suka yi a parlourn yayin da Jalaal ke zaune akan carpet
daidai Ζafar Papa. Sake gaida shi Jahaan yayi ya amsa masa. Daga nan ya tambaye
su ya aikin? Suka amsa da "Alhamdulillahil" Papa yace "Ai kun
kusa ma Ku dawo Nigeria gaba Ιaya, we're about to relocate to our motherland,
hakan zai Ζara Ιaukaka darajar Ζasarmu, masu son kayanmu kuma to, a yi abun da
ya dace"
Mutmushi kawai suka yi gaba Ιayansu, Papa ya dube su yace
"Ku dai har yanzu shiru, me kuke nufi ne?"
Kallon juna suka yi sannan suka sunkuyar da kayuwansu Ζasa.
"Magana nake fa, Jalaal, Jahaan, kun yi shiru"
Da Ζyar Jalaak yace "Papa a yi haΖuri"
"Ai ba zancen a yi haΖuri ba ne Jalaal, ku ba kwa
tunanin rayuwa ne? Haka kuke so ku Ζare taku rayuwar babu iyali ne?" Shiru suka yi ba tare da sun
ce komai ba "Duk sa'anninku sun yi aure wasu har da yara ma amma kullum
aka muku zancen sai ku yi shiru kuna sunkuyar da kai, to yau ku faΙa min meye
matsalar, matan ne ba sa son ku ko kuwa dai dama w neman matan auren?"
Kunya ce ta kama Jalaal wanda yaji kamar Ζasa ta tsage ya
shige ciki.
"Da ku nake fa kun sunkuyar da kai kamar kuna gaban
sirikanku, to wallahi kafin ku tafi hutu ku tabbatar ko wannenku ya gabatar min
da wacce yake so, don in za a biye ta Abbie Ιinku a haka za ku zauna, Gara a faΙa
muku tun da ku ba ku san me ya dace ba."
"a yi hakuri Papa" suka faΙa cikin haΙin baki.
Papa yace "Na dai faΙa muku, in kuka Ιata min lokaci
kuma duk wacce na samo muku Dole ku karΙa."
"In sha Allah za gabatar da matan kafin mu tafi Ιin"
"Kar ma ku gabatar ku ga abun da zan muku." Yana
faΙin haka ya miΖe ya gota gefe ya wuce Ιakinsa ya bar su a zaune suna karanta
wasiΖar jaki, suna wurin zaune babu wanda ya ce uffan har Papa ya fito, suka bi
shi suka fita tare, wurin da motarsa ke fake suka raka shi ya hau sannan suka
masa Allah ya kiyaye.
Sai da ya wuce Jahaan ya dubi Jalaal yace "Ka ga irin
abun da ka jawo mana ko?"
Harararsa AK yayi yace "Na jawo mana kamar yaya? Kowa
ya jawo wa kansa dai"
"Oh haka ma kace?" AK ya Ιage kafaΙa "Shi ke
nan, wallahi Ni ka ga dama ina da wacce nake so, tun da ka ce kowa wa kansa ya
jawowa wallahi Ni zan gabatar da ita kawai a yi abun da ya kamata, kai kuma in
aka nemo maka wacce ba ta dace da kai ba kai ka sani."
"Mtss" AK ya ja tsaki "To sai me? An faΙa
maka Ni ina da matsala ne? My dream girl is coming"
Jahaan ya zaro ido waje yace "Ba shakka, shi yasa yanzu
kake dogon bacci ke nan, shi ke nan in Papa ya dawo sai na ce masa mu biyu duka
mun shirya."
Jawo rigar Jahaan AK yayi yana jin kamar ya kai masa naushi
"Ba na son shirmenka fa Jahaan"
"To Papa, yi haΖuri mana" ya ba shi amsa yana wani
narke murya kamar yana magana da Papa, lokaci Ιaya kuma yace "Wai kai
Jalaal da me kake nufi ne? Ni ne babban amma kai kake ji da girman? To Allah ya
shirya."
"Ni zan wuce wurin Abbie, I no get your time"
KafaΙarsa Jahaan ya buga yana faΙin "Ζan rainin
hankali, sai shegen faΙin rai kamar yafi kowa." AK bai kula shi ba suka
nufi part Ιin Ummie, kamar kullum daga gauduwa da jin ya yake ba ta Ζara ce da
shi komai ba, sun dai yi barkwancinsu da Jahaan, daga nan ya tambaye ta ko
Abbie na nan, ta sanar da su ya wuce office. Hakan yasa suka mata sallama, da
Nimrah suka ci karo wacce ta ci uwar kwalliya kamar mai fita biki. Murmushi
tayi ta dubi Jahaan ta gaida shi sannan ta dubi AK tana wani narke murya tace
"Ya Jalaal good morning."
A taΖaice yace "Morning " daga haka suka raba ta
suka wuce. Haushi ne ya kama ta, but babu yadda zata yi tun da ita ke neme,
kuma dama an ce mai nema shi ke samu, hakan yasa ta bi bayansu. Ganin sun nufi
part Ιin Ummah yasa ta Ιan ja tsaki, ita fa wannan Ummahr wallahi ji take kamar
ta shaΖe ta, in banda mugunta taba ganin yadda su ukun suke son auren AK Ιin
amma ko kaΙan ba ta taΙa ΖoΖarin nuna masa hakan ba bayan kuma ta san ba zai
ketare umarninta ba.
Babu jimawa sai ga su sun fito bayan Dramar da suka buga da
Ummahta, parking lot suka nufa kai tsaye, da sauri Nimrah ta Ζarasa ta Ιan
tsaya ta side Ιin da AK yake ta yi knocking glass, zugewa yayi yana bin ta da
kallo, take ta diririce tace "Uhm Yaya Allah ya tsare hanya"
"Amin" kawai yace can Ζasan maΖoshi sannan ya
mayar da glass Ιin hakan yasa ta sauΖe numfashi, tana gani suka fice har ta
daina hango su. Ajiyar zuciya ta sauΖe tare da faΙin "Ya Allah ka ba Ni
Yaya Jalaal, I alone Ya Rabb" sai kuma ta dafe saitin zuciyarta. A duniya
babu wani Ιa namiji da take so irin ya Jalaal, tun suna yara lokacin ba su san kansu ba suke faΙa a kansa,
fatanta dai Allah ya sa ta cinye wannan wasa tare da mallakarsa matsayin mijin
aurenta.
Juyawa tayi don ta koma part Ιin su taci karo da Manal wacce
itama ta sheΖa kwalliya sai Ζamshi take. Kallon banza suka aikawa juna, Nimrah
ta wuce sashensu ta bar Manal Ιin da ta nufi part Ιin Ummah. Tana zuwa sashensu
Nenne ta tare ta da faΙin "Kin samu kun yi magana dai ko?"
Bakinta ta tura tace "Kema Nenne kin sani ai, kin san halinsa, wallahi Ni tsoro ma yake ba
Ni"
"Tsoro ko?" Nenne ta tambaye ta tana tsare ta da
ido "A lokacin da kika rasa shi kika jin an Ιaura aurensa da Manal ko
Safnah, lokacin za ki yi bayanin tsoronsa kike ji."
Wani Ιan Siririn hawaye ne ya zubo daga idonta ta share
sannan tace "Nenne ke dai ki ci gaba da min addu'a, in Sha Allah Ya Jalaal
nawa ne, nawa har abada."
Nenne tace "To Allah yasa, ba dai kin Ζi bin abubuwan
da nace ba, ai da tuni an wuce gurin" Ιata fuska Nimra tayi kana tace
"Ni dai ba zan yi abun da zai sa na rasa Ζima da mutunci ha, ba kuma zan
yi abinda zai kaucewa hanya ba, Yes Nenne, I love ya Jalaal, ba wai don kuΙinsa
ba, don Allah nake sonsa, idan har ba za ki min addu'ar na mallakesa ba shi ke
nan, idan na mutu kema za ki yi rashi."
Tsaki Nenne tayi tare da faΙin "Ai in dai ba za ki yi
abun da nace miki ba kina tare da wahala don masu farautar tasa suma ba haka
suka bar shi ba." Takaicin halin mahaifiyar tata ne ga kama ta, hakan ya
sa ta wuce Ιakinta ba tare da furta komai ba. Tsaki Nenne ta kara ja ganin
yadda Nimra ta banko Ζofa sannan tace "Don ubanki idan ma ke ba ki yi ba
Ni zan yi, wallahi dole a ci arziΖi da ke, dole na yi abun da ya kamata, ko don
Haj. Asiya da ke wani nuna isa a kansa kamar ita ta haife shi, mtsss, sai na
nuna mata cewa nawa salon ya wuce nata."
Hajiya Manal ko da ta shiga part Ιin Ummah a tunaninta
Jalaal Ιin yana nan, ba ta samu fuska ba hakan yasa ta fito tana cin magani,
karo ta ci da Karimah wacce saurayinta ya sauΖe ta yana ΖoΖarin fitar mata da
kayanta daga Boot. Kallon banza ta aikawa Karimah ganin wata irin shiga da ta
yi, ba ta san ta ba amma sam shigar ta yi baΙalanci da yawa.
"Yan mata ya dai? Irin wannan kallon kamar ba Mrs.
Jalaal KuΙa to be kike kallo ba?"
"What?" Manal ta tambaya cikin kaΙuwa.
Mutmushi irin na Ζ΄an bariki Karimah ta yi tare da faΙin
"Yesso! Yadda naga kin yi reacting prove me right that Kema son sa
kike"
Kasa magana Manal tayi sakamakon wani abu da ya tsaya mata a
maΖoshi hakan ya ba Karimah damar faΙin "I guess it right abi? To ki ma
cire ranki kan mijina don AK ba shi da wata mata sama da Ni, ban wuri."
Tana gama faΙar haka ta banke Manal da takaici ya gama kashe ta sannan ta shige
ciki, Nas ya shigo mata da trolleynta.
Da ido Manal ta bi su tana jin haushin kanta na rashin cin
mutuncin Karimah Ιin, sai dai rashin sanin takamaimai wace ce yasa ta wuce part
Ιin su zuciyarta babu daΙi, jikinta ne yayi sanyi kaΙan ganin sun Ζara yawa,
hakan yasa ta ji cewa dole ta yi aiki tuΖuru in ba haka ba tana gani za su
Ζwace shi daga gare ta musamman wannan mai zubin karuwan da ba ta ma san wace
ce ita ba da har take wani jin kanta fiye da su jininsa. Tana shiga Aunty Salaha
da ke kallo ta ce "Ya dai Manal?"
"Babu komai Maamah, kawai dai na je ne ban samu Ya
Jalaal Ιin ba sai takaicin da na kwaso "
Mammah ta bi ta da kallon takaici kana tace "Ba dai na
ce miki ki haΖura da Jalaal Ιin nan ba Aminatu kin Ζi ji? Kar ki ga tsakaninsa
da Yayanki akwai alaΖa mai kyau, wallahi hakan ba zai sa ya karta miki rashin
mutunci ba, uwa uba kuma Haj. Asiya da ke nuna tata isar a kansa, dama dai a ce
uwar ce ke Ζafafa da shi na san Fulani ba za ta bari soyayyar Ιanta ya kashe
jinina ba, she's been my favorite a familyn nan, amma Haj. Asiya hmm"
"Maamah ba ma Ummah ba ce damuwar, kin san me?"
Aunty Salaha ta jijjiga kai ba tare da ta kalli Manal Ιin ba
don har ga Allah ita ba son wannan alaΖar ma take ba.
Kamar Manal za ta yi kuka tace "Maamah wata ce ta ci
min mutunci wai na ma cire raina, Ya Jalaal nata ne" sai ga hawaye sun
fara bin fuskarta. "Haba Manal! Wai akan namiji kike kuka haka? Haba
Manal? Kin ga in ma za ki cire shi a ranki kamar yadda ta ce duk da ba san wace
ce ba ki cire, ga samari nan a duniya da suka fi Jalaal kyau da dukiya, ko nan
Sajid yana son ki kika ce a'a saboda jdanunki sun rufe akan Jalaal Ιin da ba
lallai ki aure shi ba, shi fa bai ma san kuna haukarku ba daga ke har Safnahr
da kuke faΙa da juna akansa kuma kin dai san ko auren zai yi Ιaya a cikinku zai
aura, ga Nimrah ma ga kuma ita wacce kika ce ta miki kashedi. Ina jiye miki
tafiyar dare ba mariki, don haka ki nutsu ki cire shi a ranki."
Ajiyar zuciya Manal ta saki tare da faΙin "Amma Maamah
Ni ba don kuΙinsa ko kyansa nake sonsa ba you know."
"Sai ki same shi ki faΙa masa cewa kina sonsa daga nan
kika idan ko amsa gaisuwarki zai yi" Aunty Salaha ta ba ta amsa a zafafe
tana ture ta gefe ganin duk bayanin da ta gama yi mata ba ta gamsu da shi ba.
Itama miΖewa tayi ta nufi bedroom Ιinta tana jin kamar ta cire zuciyarta ma
gaba Ιaya ta huta, ita dai ta san cewa da so yana yin shawara da ba za ta bari
na ta fara son Ya Jalaal ba, ta san ya fi Ζarfinta ta ko"ina to amma
jarrabawa ce daga Allah, tana fatan cinta don zuwa yanzu itama so take ta Ιauki
shawarar mahaifiyar tata da ke kan layi na gaskiya, idan kuma ta mutu silar
ΖoΖarinta na fitar da son sa a zuciyarta ta shi ke nan."
BABI NA 9
A Ιangaren su AK kai tsaye MLS suka wuce, sun daΙe a wurin
Abbie kafin su wuce office Ιin Daddy da shia ba su haΙu da shi ba. Sai da suka
yi zuhr prayer tukun suka wuce gida, AK ne ya fara sauΖa saboda shi Jahaan ya
ce akwai abun da zai, ba don komai ya fadi hakan ba kuma sai saboda ba ya son
yawan zuwa part Ιin Ummah , ko da AK ya shiga bai tarar da kowa a parlour ba,
Ummah na kitchen tana ΖoΖarin haΙa masa nasa abincin ranan yayin da Karimah ta
baje tana bacci a Ιakin da Ummah ta nuna mata a matsayin nata tsawon lokacin da
za ta shafe.
Wanka yayi sannan ya saka wasu tsadaddiyar jallabiya kalar
ruwan madara, this prove that jallabiya is his favorite dress. Turare ya shafa
sannan ya samu wuri ya kwanta yana lumshe idamuwansa, ba komai yake son tunawa
ba sama da fuskar dream girl Ιinsa, he's hoping now to see the face, yana so ya
gane fuskar kafin ya Ιunguma kan abun da ya Ζudurta a ransa. Siririn tsaki yaja
cikin ransa yace "me yake damuna ne?, Who the hell is she da za ta shiga
Zuciyata ta zauna?, I'm related to her?"
Zuciyarsa ce ta fara ba shi amsa da "No! You
ain't!" Ζaya sashen na zuciyarsa yayi saurin faΙin "Then why should I
mind about her?"
The other side said "Because you are in love with
her" Da sauri ya tallafi kansa with both hands Ιinsa yace "Nooo! Is
that how love is?"
Tashi yayi ya zauna har lokacin hannayensa na tallafe da
kansa. BuΙe Ζofar da aka yi yasa ya Ιago a hankali, a hankali ya furta
"Ummah"
Fuska sake tace "Ka dawo ke nan?" Ya gyaΙa mata
kai, nazartar yanayinsa tayi musamman yadda jijiyoyin kansa suka yi ruΙu-ruΙu
hakan ya tabbatar mata da cewa something went wrong
Cike da kulawa tace "Son, are you really ok?" Ya
gyaΙa mata kai, jijjiga nata kan tayi tace "No son, something must have
went wrong, feel free, tell your Mom what's wrong"
Numfashi ya sauΖe kana yace "Nothing much Ummah, kawai
yunwa nake ji"
"When did you start hiding things from me e? Remember
I'm your mom, your caregiver also your friend, in ba ka faΙa min damuwarka ba
shi else will you approach?" Ta Ζarashe cikin yanayin da ke nuna tsantsar
kulawa, a wannan lokaci babu abun da Ummah ke buΖatar sani fiye da damuwar
Jalaal Ιin and deep down she's hoping Allah ya sa ba batun aure wani ya mΓ sa ba
cikin uncles Ιinsa.
Yanayin yadda Ummah ta nuna kulawarta gare shi yasa ya yi
wani tunani kawai sai ya tsinci kansa da faΙin "I was called few minutes
from MLS Ιazu, it's an issue of an important contact sun kuma ce they'll only
communicate with the CEO physically don ba sa son a samu matsala, Ummah I was
here yesterday, in na ce zan tafi you'll feel bad so also Abbie and I don't
want to miss this opportunity Because in ya wuce mu shi ke nan." Yana kai
aya ya wani narke fuska kamar hakan ne a ransa, mamaki shi kansa yayi na yadda
ya sunΖumo Ζarya while ba Ιabi'arsa ba ne.
Ji Ummah ta yi kamar ta shaΖe shi saboda takaici, ga shi ta
riga ta sa Karimah zuwa don su samu kusanci a samu a yi auren kowa ya huta shi
kuma ya zo da wani batu, abun da ma ya shigo da ita Ιakinsa shi ne don ta masa
maganar aure amma ya zo mata da wani zance. Ko me ta tuna sai ta ji hakan ai ba
komai ba ne musamman da ya kasance al'amari ne na kuΙi, to shima dai kusan
aikinta ne tun da za ta iya cewa a ita yake nema wa, komai ya tara nata ne,
mallankinta. Wani irin makirin murmushi Ummah ta yi tare da jan kuncinsa
"Ba za ka sauya ba Jalaal, shi ne za ka sanya damuwa cikin ranka e? So
kake ka kamu da wani ciwon ne?"
AK ya Ζara narke fuska tare da lumshe Idanuwansa, Ummah kam
gefen lips Ιinta ta cije cikin ranta tana faΙin "in ka san wata ba ka san
wata ba ai."
A zahiri kuma tace "Kar ka wani damu, zan yi wa Abbie
da Ummienka bayani, sai ka fara shirin tafiya." Babu shiri ya miΖe tare da
hugging Ummah yace "Thank you so much Ummatah, thanks for always being
there for your child, thank you"
Jikinta ta raba da nasa tare da tallafo shoulders Ιinsa tana
mai kallonsa "You deserve more than that son, Kai dai kawai ka fara shiri,
your Ummah will always stand by your side, shi ke nan?"
Ya gyaΙa mata kai tace "Good, now smile " murmushi
yayi har sai da jerarrun fararen haΖwarensa bayyana. Ummah ta zaunar da shi
bakin bed tace "Ka zauna, bari a kawo maka Lunch Ιin ciki."
Babu musu ya zauna tare da faΙin "Thanks Ummah."
Bayan ficewar Ummah wata nauyayyar ajiyar zuciya ya sauΖe
yana dafe chest Ιinsa da hannunsa, he's wondering why yayi irin wannan Ζarya,
ta yaya ma aka yi wannan plan Ιin ya zo mishi kai tsaye? Zuciyarsa ce tayi
saurin ce masa "Kana tsoron wa'adinka ya cika ba ka gabatar da ko wacce
mace a matsayin abokiyar rayuwa ba and you're afraid of Papa ya aura maka wacce
ba ka shirya ba, uwa-uba kuma, You're now super eager to know your dream girl,
ka taimaka mata saboda ka ganta a yanayi na bukatar taimako.'
Hannunsa ya dunΖule tare da naushij iska yace "Yes!
That's it"
A Ιangaren Ummah ko da ta fita parlour tunanin abun yi ta
fara, haka kawai wani sashe na zuciyarta ke Ζaryata zancen Jalaal amma da ta
tuna cewa bai taΙa yi mata Ζarya ba tun yana yaro sai taji wani iri, so take a
yi a yi maganar aurensa da Karimah, hakan wani mataki ne na nasara da kuma
cikar burinta, amma ta san me za ta yi, za ta Ιullo masa ne ta yadda bai yi
tunani ba daga shi har iyayen nasa, za ta gwada musu cewa ita Ιin jar wuya ce,
akan burinta babu abun da ba za ta yi ba.
Samun kanta ta yi da shiga Ιakin da Karimah take, ganin tana
bacci yasa ta tashe ta, bayan ta tashi ta ce mata "Ki yi ki watsa ruwa ki
yi kwalliya mai kyau, akwai abincin Jalaal za ki gan shi jere kan tray, idan ba
ki gani ba ki tambayi su Sa'ade za su nuna miki, ki Ιauka ki kai masa, and mind
you ki yi abun da ya kamata, ki yi ΖoΖarin ganin kin ja hankalinsa a kallonsa
na farko gare ki, behave well Karimah, kar ki nuna masa halinki na shirme
ok?"
Cikin rawar jiki Karimah da ba ta Ζarasa jin me Ummah ke faΙi
ba ta banka Ζofar toilet ta shiga, jijjiga kai Ummah ta yi bayan shigewar
Karimah sannan ta cije lips Ιinta, yamutsa fuska tayi tace "Ki gama rawar
Ζafarki Karimah, daga ke har mahaifiyarki ina amfani da ku ne don cikar
muradina. Da zarar na gama da ku including he himself Jalaal Ιin da iyayensa
duk zan zubar da ku ne na kafa sabuwar rayuwa. That's all I'll do." Daga
haka ta juya ta fice zuwa nata Ιakin.
Su Karimah manya wankan ma a hanzarce aka yi ana ta Allah
Allah a je wurin AK, wasu English wears ta sanya, riga da wando da suka kama
jikinta, kitson attachment Ιinta ta gyara ta bazo shi har tsakiyar bayanta, ba
tare da ta saka hula ko wani veil akanta ba ta fesa turarukanta itama masu
matsakaicin Ζamshi sannan ta saka takalminta ta fito, abincin da Ummah ta ce
mata an jera akan tray ta Ιauko sai wani kwarkwasa take tana yauΖi kamar kuΙaiwa.
Kai tsaye Ιakinsa ta nufa, babu knocking babu komai ta murΙa
handle Ιin Ζofar tare da shigewa abun ta, he's taken away that time, yana wata
duniyar da shi kansa bai san wacce ba ce ko a ina take ba bare ya san da
wanzuwar bil'adama a tare da shi, Karimah kuwa tun da ta shiga ta tsira masa
idanuwa coz kansa yana facing Ζofar ne, kamar za ta haΙiye shi haka take
kallonsa, jin sauyawar iskar Ιakin daga daddaΙan Ζamshinsa da ma freshener Ιin
da ake masa amfani da ita a Ιakij zuwa wani irin Ζamshi ko ya ce wari na daban,
hakan ne ya sa ya buΙe idanuwansa da ke lumshe.
Da farko ya Ιauka idanuwansa ne ke masa gizo ganin akan
halittar da ya sauΖe su, sai dai ya
murtsuke idanuwansa sannan ya mayar da duk wani focus na kallonsa ga daidai
wurin da ya ga mutum, tabbas, ba gizo Idanuwansa ke masa ba, zahiri ya gani,
take ya ci wani irin amai ya taso masa, a rayuwarsa idan akwai abun da ya tsana
ko ya Ζi bai wuce arna ba, arnan ma masu Ζara gashin doki, babu shiri ya nufi
bayi da Ιan sauri. Ita kam Karimah wucewarsa bayi ne ya dawo da ita daga tata
duniyar tunanin. Da kallo ta bi shi har ya shige ciki tana mamakin yadda ko
nuna ya san da wanzuwarta da bai yi ba.
Fuskarta Ιauke da mutmushi take bin Ζofar bayin da kallo
bayan ajiye abincin da ta yi a kan bedside drawer tana jiran fitowarsa.
Mintuna kadan ya fito fuskarsa da jikinsa a jiΖe alamun dai
har wanka yayi, kasancewar bai yi tsammanin zai tarar da ita ba don ya yi
tunanin ko cikin sabbin maids Ιin Ummah ne sai dai ga mamakinsa she's still
there, sitting on his own bed and staring her owl looking eyes on him, wani
irin takaici da Ιacin rai ne suka dira masa lokaci Ιaya, pointing Ιinta yayi da
yatsa daga bakin Ζofar bayin sannan yace "You?? Put of sight before I
loose my temper on you!" Ya faΙa a tsawace yayin da eyes Ιinsa suka fara
sauya yanayi.
Wani irin murmushi ta yi don ita har ga Allah ko dukanta zai
yi babu abun da zai sa ta fice daga Ιakin saboda har yanzu ba gajiya tayi da
kallonsa ba, ba ta ma Ζi ta kasance da shi ba a wannan lokaci. Ganin yadda ta
yi kunnen uwar shegu da shi yasa ya fito ya nufi charger Ιin sa da ke jikin
socket ya Ciro ta ya nufe ta a hasale, ganin ΖoΖarinsa na nufo ta da cable yasa
ta zaro idanuwanta cike da tsoro ta miΖe daga bakin gadon jikinta na Ιan rawa.
Abincin da ta ajiye ya nuna mata tare da
faΙin "Ζauki wannan ki fice da shi dallah, don't let me set my eyes with
you ever in ba haka ba zan iya kakkarya ki"
Idan akwai abun da ake cewa tsoro, to tsoron nan ya gama
mamaye jikin Karimah, jikinta na rawa ta Ιauko tray Ιin ba tare da ta yi masa
bayanin wanda ya aiko ta ba da kuma matsayinta gare shi ba ta fice da sauri,
duk da cewa wando ne a jikinta amma harΙewa take da Ζyar ta Ζarasa dining ta
dire tray Ιin a Ζasa ta nufi Ιakinta da sauri tana zazzare idanuwa.
Mamaki take wai yau ita Karimah ta ci karo da namijin da ya
motsa mata Ζ΄aΖ΄an hanjinta saboda tsoratarwa. The whole she? Anya kuwa wannan za
ta iya cin nasara akansa? Wani irin Ζarfin guiwa ne ya zamo mata sakamakon
tunawa da cewa hakan burin mahaifiyarta ne, wannan dalili yasa ta ji ba za ta
iya sarewa ba. Wayarta ta Ιauko tare da tsintar kanta da kiran number Mommynta,
babu wanda a yanzu take buΖatar shawararsa irin ta Mommyn nata, gani take a
yanzu babban burinta shi ne mallakar wannan haΙaΙΙe kuma kyakkyawan saurayi mai
cika da zati mai kyau.
Ajiyar zuciya ta sauΖe jin Mommyn nata ta Ιaga kiran
"Hello" a Ιangaren Mommy aka ce "Babyna kin isa Ζalau ya
baΖunta, sai yanzu kika tuna da Mommynki wato kin samu daΙi ko?"
"Ba wannan ba ne ya sa na Ζira ki ba Mommy, akwai
gagarumar matsala sosai, Jalaal ko? Yauwah wallahi Mommy sai mun yi masa
kyakkyawan shiri, Mommy ba wai don cikar burinki kaΙai ba, nima don nawa cikar
burin dole sai kin yi abun da ya dace, kin ga yau abun da yayi min daga kai
masa abinci? Wallahi Mommy ko kyakkyawan kallo ban samu daga gare shi ba kin
san me?"
"A'a" in ji Mommy
"To wallahi har amai yayi saboda ya ganni"
Salati Mommy ta hau yi tana Ζara jin girman al'amarin
"amma dai wannan Allah ya yi Ιan iska, to in bai yi haka ba wa ma zai yi?
Jikin Alhaji Habu KuΙa ne fa, lallai Gara da kika kira Ni, akwai aiki ja a
gabanmu, yau yau zan je wurin Malam Rilwanu na san zai yi abun da ya dace, gobe
kuma zan je Birnin Gwari wurin wannan bokan da ya riΖe Miki Nasir, idan na dawo
zan saka miki saΖon a mota sai na miki bayani in sun iso, amma ko da wasa kada
ki bari Asiya ta san cewa ya wulaΖanta ki za ta iya sauya ki da Juwairiyya
saboda tana neman wacce za ta yi mata aiki yadda ya kamata ne ba tare da an
samu matsala ba."
"Wace Juwairiyya kuma Mommy? Ba dai ta wurin Yaya Babba
ba?"
"Ita dai Karimah, saboda haka ki manta da abun da ya
faru yau kin ji?"
"To Mommy amma ai Ummah ba ta shiri da Yaya Babba ta ya
za ta saka ta cikin muradanta? Ke ma kin san Yaya Babba da wa'azim tsiya kamar
ta fi kowa tsoron Allah."
"Kin ga Babyna, ki bar Asiya yadda kika ganta, kawai
dai ki bi ta a hankali don ta wuce tunaninki."
Karimah tace "To Mommy, kar ki manta ki yi abun da ya
kamata kawai."
"To babyna, sai anjima"
Daga nan suka katse kiran, Hajiya Karimah ta saki wani irin
murmushi don yanzu ji take kamar an Ιaura aurenta da AK ne saboda ta san
Mommynta duk abun da ta mata alΖawari sai ta samar mata. Fitowa tayi ta Ιauke
tray Ιin ta nufi kitchen da shi kai tsaye tana mai cije lips Ιinta.
A Ιangaren AK tun da ta fice ya dawo gefe yana mayar da
numfashi, why Ummah za ta Ιauki Christian aiki, shi ba wai wani abu ba ne kawai
ba ya son masu Ζara gashi ne, ga shi ita wannan bayan Ζarin gashi har da salon
bariki a tattare da ita. Tsaki ya ja tare da mayar da cable Ιin sannan ya ja
bedsheet Ιin da ta zauna kai ya wuce laundry da shi kamar ya riΖo kashi, dawowa
yayi ya duba freshener ya buΙe ta gaba Ιaya don har yanzu warin turaren wannan
maid Ιin bai daina tashi ba a Ζofofin hancinsa ba, haka ya Ζara Ιauko turarensa
ya feshe shi kana ya Ζara sanyin Ιakin take Ζamshin Ιakin ya sauya. Kayan
jikinsa ya cire ya sauya sannan ya fito daga Ιakin nasa, bai tsaya bi ta kan
kowa ba ya nufi sashen Ummie fatansa dai ya samu abun zubawa a cikinsa.
Bai tarar da ita a parlour ba hakan yasa ya nufi dining ya
fara buΙe flasks Ιin da ke jere, serving kansa white rice with veggies yayi
tare da egg sauce sannan ya zauna Ιauke da Bismillah a bakinsa ya fara cin
abincin yana lumshe idanuwansa, the best and unique test na girkin Ummie ya
banbanta da na kowa, ba wai ya saba da cin girkinta ba ne, no, sai ta kama yake
ci, amma ya ba wa ΙanΙanon girkinta maki na musamman a wannan fage, zai iya
cewa iya rayuwarsa babu wani abinci da ya saka a bakinsa da zai kwatanta ΙanΙanonsa
da na Ummiensa. Tsintar kansa yayi da tuna dream girl Ιinsa, "ko ita ma ta
iya girki?" He asked himself. Ruwan lemun da ya kurΙa ya sauΖe yana juya
hannunsa alamar bai sani ba.
Wayarsa da ke vibrating kan table ya Ιago, ganin Jahaan yasa
ya daidaita kansa sannan ya Ιaga. Daga can Ιangaren Jahaan yace "Ya, man
wai ina ka shiga ne? Na je part Ιin Ummah but you were no where to be
found"
Ajiyar zuciya ya sauΖe sannan yace "Ina part Ιin Ummie,
amma ka jira Ni yanzu zan fito"
"Me kake a can, ko dai Ummie ta cire karar da take yi
ne akan Ιanta na fari?"
Siririn tsaki AK Ιin ya ja sai dai hakan bai hana Jahaan
jiyo wa ba "Ka yi tsaki da kyau ai, ga Ni nan zuwa ka jira Ni a can"
"Noo" AK ya dakatar da shi.
"Ko me kake Ιoyewa dole na zo na gani, kawai ka jira
Ni".daga haka ya katse kiran.
"Aikin banza" AK ya faΙa cikin ransa yana mamakin
irin yarinyar Jahaan, wai kuma a hakan da an taΙa shi sai ya ce ai shi ne
babba. Mtsss, ya wani ja tsaki.
Shigowar Jahaan yasa ya Ζara kane fuskarsa wai shi ba zai
karΙi raini daga JK ba. Hannun Jahaan na kan haΙarsa yana mamakin me AK yake a
dining Ιin Ummie, a haka ya Ζaraso yaba faΙin "Sata ka fara ne AK?"
"Duk yadda ka Ιauka" ya ba shi amsa a gajarce yana
mai Ιaukar wayarsa ya mike tsaye zai wuce, riΖe shi Jahaan yayi kana yace
"Man ina kuka za ka je, ai sai ka jira Ummie ta fito na tambaye ta ko da
saninta kake cinye mata abinci, idan ba ta sani ba kuma sai a san matakin Ιauka
a kanka."
Wani kallo AK ya aikawa Jahaan, kau da kai Jahaan Ιin yayi
yana dariya kana yace "Duk abun da za ka yi ba zai sa na sake ka ba har
sai Ummie ta fito ta ga mai sace Mata abinci in ta ajiye, don ka san ba za a
ha'inci Ummie ina gani ba."
Ζwace rigarsa daga hannun JK yayi yana jin kamar ya kai masa
duka, daga haka ya nufi hanyar waje yana wani muzurai shi Ιaya, bin bayansa
Jahaan yayi yana kwasar dariyarsa har ya iso shi.
Wani kallon AK ya Ζara aikawa Jahaan yana faΙin "Malam
ka dame Ni da dariya, idan ba za ka iya shiri ba Ni ka tafi abunka"
"Na tafi ina? Ai Ζafata Ζafarka Jalaal, ka yi abun a yi
dariya kuma sai ka ce ba za a yi ba. Mutum sai shegen son girma, wannan ba mu
san ya za a yi da kai ba idan ka samu wacce kake so, na rantse maka ko kallonka
ba za ta yi ba in dai kana wannan muzuran don sai ta yi tsammanin ma mugun soja
ne."
Yana kaiwa nan ya kwashe da wata dariyar.
Ran AK ne ya Ιaci kawai sai ya nufi hanyar garden, jin Ζiran
sallar la'asar yasa kawai ya sauya ya nufi mosque shima Jahaan ya bi bayansa.
Bayan an idar da Sallah AK ya ja Jahaan zuwa sashensu don shi da gaske fa har
yanzu Ζyamar Ιakin yake ji, idan ya tuna da koΙaΙΙiyar arniyar Maid Ιin nasu
sai yaji wani iri. A haka suka wuce part Ιin Mammah, da Manal suka ci karo
wacce take karatu a parlourn ta baje littattafa, she's nursing student, tana
karatu ne a Adamu Adamu College of Nursing sciences, hutu yanzu suke kuma da
sun koma za su yi hospital final exams Ιinsu, jiki na rawa ta miΖe ganin su AK,
gaisge su tayi AK ya amsa a gajarce, shi kuwa Jahaan bai bi ta kanta ba. Sai da
suka shiga AK ya baje kan bed Ιin Jahaan.
Ya daΙe a kwancen idamuwansa lumshe amma bai ce komai ba.
Can kamar wanda aka tsikara ya miΖe ya zauna "Are you interested in going
back?"
"Back to where?" jahaan asked with view of needing
more elaborations
"Bloordale"
"Ba mu gabatar da matan auren namu ba? And kwana Ιaya
fa muka yi."
"Kawai amsa za ka bani ha dogon bayani ba."
"Ina son komawa mana AK, wallahi Ni tsorona Ιaya
maganar Papa, shi yasa nake so gobe mu fara fita ko Allah zai haΙa mu da
rabonmu waΙanda za mu daidaita da su."
Lumshe Idanuwansa AK yayi kana yace "I don't even know
how to start, amma zan koma gobe Ni kam, time Ιin da Papa ya bayar ya yi kaΙan
ka samu yarinyar da za ku daidaita beside Ni ba na son yara ma, na fi son full
grown up woman wacce ba za ta sa min ciwon kai ba."
"Eyeee?" JK
ya tambaya yana taye baki "Lallai ne manya, ba ka tunanin ran Papa
ya Ιaci da tafiyarmu ya zaΙa mana waΙanda ya ga dama kamar yadda ya faΙa?"
"Ba zai yi ba" ya ba shi amsa a gajarce
"Kana da tabbacin hakan?"
AK ya gyaΙa kai "We've an important contract and, sun
ce physical contact suke buΖata."
MiΖewa JK yayi ya fara takawa jin mafita ta zo musu cikin
sauΖi, ko Ζara bi ta kan AK bai yi ba ya fara haΙa trolley Ιinsa, sai da ya
gama ya dubi AK da ke bin sa da kallo "Sannu zumuΙi, to ko Flight ban yi
booking ba."
"Shi ne kuma za ka sa na haΙa kayana?"
"Ai Ni nace ka haΙa ko?" Dawowa Jahaan yayi gefen
AK ya zauna yana sauΖe numfashi.
"Amma dai ka cuce Ni Man"
Bai kula shi ba sai ma Ζara lumshe Idanuwansa shi kuma
Jahaan sai surutu yake, ganin AK ya Ζi kulasa yasa ya bar masa Ιakin ya dawo
parlour kusa da Manal da ke karatu.
https://www.facebook.com/profile.php?id=100094397072466
BABI NA 10
A Ιangaren Ummah sai da Yamma ta fito, ta shiga kitchen don
faΙawa masu aiki abincin da za a girka ta ci karo da tray Ιin abincin AK,
tsintar kanta tayi da buΙe su, ganin ko taΙawa ba a yi ba yasa ta juya zuwa Ιakun
Karimah don jin ko ba ta kai masa ba ne.
Karimah wacce ke chat Ummah ta duba tace "Karimah kin
kai wa Jalaal abincin kuwa?"
Ta buΙe baki za ta faΙa mata abun da ya faru ta tuno da
maganganun Mommynta bakan yasa ta narke fuska tace "Na kai masa Ummah, ya
ce duk babu wanda ya masa a ciki, na ce ya faΙi me zan dafa masa ma ya ce na
bar shi zai sha cornflakes."
"Shi ne ba za ki zo ki faΙa min ba kuma?"
"Kina bacci lokacin ai Ummah"
"Ke kuma ba ki san me ya kamata ki yi ba? Idan kika
girka wani abun ai zai karΙa ya ci amma kika yi burus, kina tunanin hakan zai
samar miki soyayyarsa ne?"
Shiru Karimah tayi tana nazaratar maganar Ummah ta kuma
fahimci cewa tana kan layi sai dai me? Ita fa ba ta iya girka komai ba apart
from Indomie, suna da mai musu abinci, wanke wanke da kuma shara, hatta gyaran Ιaki
ita ba ma iyawa tayi ba.
Maganar Ummah ne ta
dawo da ita daga duniyar da ta leΖa "Ki kula da kyau, ki yi amfani
da dabarunki a matsayinki na mace ki tabbatar kin samu gurbi a zuciyarsa daga
yanzu zuwa dare don gobe zai bar garin ma."
Karimah ta Ζwalalo ido tace "Ina zai ce Ummah?"
"Zai koma yadda ya fito mana, don haka ki yi yadda za
ki yi na faΙa Miki, idan kin yi Sa'a to, zan ba ki numbersa ko Bayan tafiyarsa
kike kiransa ki tabbatar kin samu kusanci da shi kin ji"
"To Ummah, I'll do all that's necessary."
"Da ya fi Miki".
Ζakin AK ummah ta nufa kai tsaye sai dai ba ta same shi ba,
hakan yasa ta fito parlour ta zauna tana jiran shigowarsa. Ganin har Magrib bai
dawo ba yasa hankalinta ya Ιan tashi, fatanta dai kar yaje ya ci abinci a
sashen mahaifiyarsa don kuwa in hakan ta faru zai iya daina cin abincin
sashenta kamar dai mahaifinsa, shima tun da ya fara cin gurkin Ummie ya yi wa
nata Ζaura sai yace wai sai dai ta girka masa da kanta ba wai masu aiki ba. Ita
kuma Ummah, maganar gaskiya, ko lokacin da tana amarya ba ta girki, da mai aiki
tazo tun lokacin da ta san cewa Ιan babban gida za ta aura. Tsaki Ummah ta ja tace "Wawuyar yarinya
tana son lalata min plan, amma ba zan taΙa yin sake shekarun da na Ιata a baya
ina aiki su ruguje ba, dole, dole ne Jalaal ka kasance ΖarΖashin iko da
umarnina." Daga haka ta koma parlour ta zauna zaman jiran dawowarsa.
AK kam A nan part Ιin su Jahaan suka Ζarasa yininsu har
dare, a nan ma suka ci abincin dare tukunna JK ya wuce part Ιinsu. Yana shiga
Ummah ta tare shi fuskarta na nuna tashin hankali. "My son, where have you
being, ina nan ina ta jiranka, Karimah ta ce ba yi Lunch ba, ga shi wayarka ba
ta tafiya."
Cikin son kwantar mata da hankali yace "I'm sorry
Ummah, wata Ζazamar Maid ce ta kawo and you know ba na son mata irinsu, why
kika Ιauki irin wannan Ζ΄an aikin?"
Janyo shi tayi ta zaunar da shi sannan tace "Son mace
Ζ΄ar aiki?"
Ya gyaΙa mata kai yana wani yamutsa fuska don ko kaΙan ba ya
Ζara ganin fuskar wannan Ζ΄ar aikin.
Shiru Ummah tayi tana tunani can dai tace may be Karimah
Ζarya ta mata ta tura masa Ζ΄ar aiki, amma ya ce arniya ai, me hakan yake nufi?
Kaf cikin masu aikin sashenta babu wata Christian bare yace wani abu. Ganin
babu mai ba ta amsa yasa ta Ζudiri aniyar tambayar Karimah Ιin.
Kallonsa tayi cike da kulawa tace "yanzu dai mu je na
ba ka abincin ka ci to"
Fuska ya yamutsa sannan yace "I'm already satisfied, na
ci abinci babu jimawa."
"Is ok, ka yi haΖuri ka ji son"
Mutmushi yayi yace "Ki daina ba Ni haΖuri Ummahta, just
tell who the so called Karimah is ta
kula ko ma ki daina sa ta aiki tun da ba ta yin abun da kika sa ta."
"Shi ke nan my son"
Ζakinta ta wuce ta bar shi a parlourn, tana shiga ta janyo
wsyarta ta makawa Yaya Zinatu kira, bugun fari ta Ιaga bayan sun gaisa tace
"Yaya akwai matsala fa"
"Matsalar me kuma Asiya?"
"Yaron nan zai koma Canada gobe Yaya kuma ga shi ba a
tsayar da magana ba"
"To yanzu me ye abun yi?"
"Shi ne ma dalilin kiran naki ai"
"To gaskiya Asiya dole wannan karon ki zo nan Kaduna
duk lokacin da ya kusa dawowa ko kuma ki zo nan babu jimawa, akwai wani boka da
yake min aiki Asiya a birnin Gwari kuma gaskiya aikinsa na mugun ci, za a yi
aiki kawai a kansa a yi a wuce wurin ko ba haka ba?"
Ajiyar zuciya Ummah ta sauΖe don ba ta son tonawa kanta
asiri, amma bokaye babu irin wanda aminyarta ba ta raka ta ba har na Ζasashen
kewaye amma amsa Ιaya suke ba ta na cewar "Ko an yi aiki a kansa ba zai yi
tasiri ba, akwai garkuwa ta musamman a jikinsa"
"Kin yi shiru Asiya?"
"Shi ke nan Yaya, hakan kawai za a yi. Ki sa mana
lokaci sai mu je"
"To shi ke nan, yanzu ita Karimah Ιin gobe ke nan za ta
dawo?"
"Yadda dai ta ce, idan tana son zama a nan Ιin ai shi
ke nan"
"To shi ke nan, sai an jima"
Suna katse kiran Ummah ta fito parlour, har lokacin AK na
zaune yana kallon sport. Kujera ta samu ta zauna sannan ta kira sunansa. Ζagowa
yayi giving her his total attention.
"Jalaal yaushe ne za ka kawo min sirika ne?"
Tsintar kansa yayi da kumshe fararen idanuwansa trying hard
to remember her face, that's his dream girl."
"Ka yi shiru son."
"Ummah ki Ιan Ζara jira kaΙan, in Sha Allah nan ba da
jimawa ba ma."
Wani irin bugawa chest Ιin Ummah yayi jin amsar da ba ta yi
tsammani ba, hakan yasa ta Ζago murmushi don kar ya gano wani abun tace
"Ma sha Allah, amma dai kafin nan ina maka albishir da cewa na maka
kyautar mata."
Babu shiri AK ya miΖe tsaye sai dai bai iya cewa komai ba
sai kuma ya koma
"Shi ke nan, na fahimta ba ka so, kar ka damu mu bar
zancen" ajiyar zuciya kawai ya sauΖe sannan yayi excusing kansa ya wuce Ιakinsa,
available flights ya duba sai da babu na gobe sai jibi babu yadda zai yi kawai yayi booking seat
biyu shi da Jahaan, bayan ya kammala ya fito parlourn, Abbie ya dawo lokacin
hakan ya sa ya zauna suka yi hirarsu nan ya samar da shi cewa jibi za su koma,
hakan bai yi wa Abbie daΙi ba saboda bai samu wani lokaci sosai da Ιan nasa ba
saboda ayyukan da suka sha kansa amma yayi masa fatan Alkhairi daga nan ya fito
ganin dare bai yi ba yaje ya gaida Ummie, a nan yake sanar da ita cewa zai wuce
jibi, tace
"Ya kamata ka je Azare, ka gaida Baffa Malam, rabonka
da shi tun yaushe?"
Kansa ya sosa cike da jin kunya yace "Kusan five years
ke nan"
Ba tare da Ummie ta kalle shi ba tace "Ya rage naka
kaje ko a'a, don na san kana ziyartar wadanda kake ganin sun dace a duk lokacin
da ka zo, daga yau zuwa gida Baffa Malam wajibi ne a kanka duk lokacin da ka
zo."
Cikin sanyin jiki yace "To Ummie" daga nan ta bi
shi da fatan Alkhairi tana faΙin "Allah ya kai mu goben," ya amsa
mata da "Amin" daga nan ya
dawo Ιakinsa, wanka yayi kamar ko yaushe ya sauya kaya ya fesa turare sannan ya
kwanta.
Tun daga ranar da Imaan ta yi shawara da su Ramcy daga nan
ta rabu da saurayinta Uzair wanda ke mutuwar sonta kuma yake e, Allah sarki
Uzair duk da haka bai kawo komai a ransa ba sai yayi tunanin ko hacking
accounts Ιin nata aka yi, daga Ζarshe sai ya yanke shawarar zuwa gidansu su yi
magana.
Imaan na zaune a tsakar gida yaro yayi sallama yace wai ana
sallama da Ihsan, ba ta ba da amsa ba sai da ta nufi Ιakinsu ta dubi Ihsan Ιin
da yanzu ba ta fiye zaginta ba tace "Ana sallama da ke a waje"
"Waye?"
Imaan tace "Ban sani ba"
A gadarance tace "Ki dubo min mai Mashin ne ko mota, in
mai Mashin ne ma ki sallame shi in kuma mai mota ne ki tambaye shi waye."
Kamar wacce ake ba wa control Imaan ta fita waje, kyakkyawan
saurayi ne jingine da motarsa, hakan yasa ta Ζarason don cika aikan nata. Tana
isa Uzair ya miΖe tsaye y Ζaraso inda take "Haba Babe, why kike wahalar da
Ni these days? I've been..."
Ba ta bari ya Ζarasa ba tace "I'm sorry, ba Ihsan ba
ce, in ji waye za a ce mata?"
Kallon kin raina min hankali ya aika mata, shi dai iya
saninsa Ihsan ita Ιaya ce a gidansu in fact ba ta taΙa ba shi labarin wani a
gidansu ba hasali ma ce masa take yi ita kaΙai ce a gidansu. Marairaice fuska
yayi kamar zai yi kuka yace "Haba Babe, don Allah in wani laifi na
miki..."
"Ka ga malam, I'm not your babe, ka faΙi waye kai za ta
fito ai"
Yanayin kalamanta ne yasa ya Ιan sha jinin jikinsa sai yace
"Ok, ki ce mata Uzair ne" ya faΙa ba don ya gama yadda ba.
Ko da Imaan ta faΙawa Ihsan sunan mai kiranta ce mata tayi
tace "Ba ta da lokacinsa"
Kasa tafiya tayi sai ta tsinci kanta da jin kunyar zuwa ta
ce masa Ζ΄aruwarta ba ta da lokacinsa, a dai yadda ta fahimta saurayinta ne kuma
da alamu saboda sabon saurayin da tayi yasa ta daina sonsa, to amma meye
laifinsa? Wai su samari me yasa ba sa gane mata mayaudara masu son abun
hannunsu irin Ζ΄aruwarta Ihsan ne?
Jiki sanyaye ta fita, cike da tausayawa ta Ζarasa wurin da
yake tace "Bawan Allah ka yi haΖuri da Ihsan, mahaifinta ya hana ta
tsayawa da kowanne namiji sannan kuma ya riga da ya yi mata miji ya ce kada ta
Ζara tsayawa da wani. Don Allah ka yi haΖuri kar ka Ζara zuwa gudun fuskantar
wulaΖanci."
Tana kai wa nan ta juya ciki abun ta.
Allah sarki Uzair, wani irin zafi sosai kalaman Imaan suka
masa, ganin har ta shige gida ba tare da ya yi mata tambayoyin da yake buΖatar
amsoshinsa ba yasa ya dafe kansa, da Ζarfi yace "Why Ihsan? Why me?"
Naushi ya aikawa iska sannan ya wuce cikin motarsa kai tsaye.
BAUCHI, BAUCHI STATE
Washe gari da safe bayan ya karya direct part Ιin Mammah ya
wuce, cikin Sa'a kuwa ya tarar da Papa bai fita ba, bayan sun gaisa ya sanar da
shi cewa za su wuce ya kuma faΙa masa dalili. Murmusawa Papa kawai yayi yace
"Duk tsallake-tsallakenku ku yi ku gama Abduljalaal, daga kai har Jahaan
shekarar nan ba za ta wuce ba zan Ιaura muku aure, wannan shi ne magana."
Sosa kansa AK yayi yace "Afwan Papa, ba sai an kai
wannan mataki na, in Sha Allah kwanan nan za mu yi magana, Ku dai yi mana
addu'ar Allah yasa Alkhairi a ciki."
"To ameen Jalaal, ba lallai ina nan dawo ba lokacin
tafiyarku da na miΖa ku airport"
"Laa babu komai Papa, Junaid zai miΖa mu ai"
Papa yace "To shi ke nan, Allah ya tsare ya ba da Sa'a
kan abun da ake yi, ku kula da kanku, ina shi Jahaan Ιin?"
"Ga Ni nan Papa" ya faΙa yana Ζarasowa yadda suke,
gaisge da Papa yayi bayan ya amsa Papa ya dube shi yace "Jahaan, ka kula
da Ζanin nan naka, ka tabbatar next zuwan da za ku yi kun shirya wa aure da
gaske" kansa ya shafa yace "In Sha Allah Papa"
"To Allah ya muku albarka, ya Ζara muku son junanku ya
kuma kai ku lafiya."
"Amiin Papa" suka amsa bakinsu haΙe, daga nan yace
"Za su iya wucewa" babu musu suka fice tare, dag bakin apartment Ιinsu
suka tsaya, AK yace da JK ya shirya su Ιan zaga gari yau kam, hakan aka yi kuwa
ya koma shi kuma ya wuce part Ιin su. Wanka yayi ya shirya cikin wani expensive
boyel mai sheΖi da taushi white color wanda Ummmie ce da kanta ta Ιinka musu
shi da Abbie shi yasa ma yake iya saka shi don shi ba ma'abocin shigar hausawa
ba ne. Sosai kayan suka amshe shi, hular da aka sayi kayan da jta ya Ιaura kan
baΖar lalllausar sumar kansa sannan ya Ιaura agogonsa silver color Ζirar
MLS mai shegen kyau, daga nan ya feshe
jikinsa da turarukansa masu bayar da Ζamshi mai sanyaya zuciya.
Akwai takalmin da aka haΙa kayan da shi shima dai launin
fari ne, sakawa yayi take ya fito kamar wani Basarake, har ya nufi Ζofa ya tuna
da wayarsa, komawa yayi ya Ιauko ta sannan yayi dialling numbern Jahaan tare da
fitowa. Karimah ce zaune a parlourn tana latsa wayarta, daddaΙan Ζamshin da ya
ziyarci hancinta yasa ta dakata tana jiran taga ta ina ne. Baki ta sake tana
kallonsa shi kam bai ma san tana parlourn ba saboda wayar da yake da JK. Ji
tayi kamar ta je ta rungume shi amma da ta tuna tsiyar da ya tsula mata jiya
babu shiri ta kama kanta. Har bayan ficewarsa Ζamshinsa na nan a parlourn wanda
ya sauΖarwa Karimah da kasala, take wata irin buΖata ta bijiro mata gashi kuma
babu wani wanda ta sani a nan Bauchi, ganin dai ta kasa daurewa yasa ta yi
wanka itama ta fice zuwa wani wurin da za ta shaΖata la'alla ko ta samu abokin
harka.
AK na fita suka haΙu da Jahaan a bakin part Ιinsu, wata
farar mota mai Shegen tsada suka nufa wacce jiya Abbie ya fita da ita. Daga nan
kuma suka fice daga gidan. Jahan ne ya dubi AK da hankalinsa ke kwance
idamuwansa lumshe yace "Ina muka nufa ne?"
Murya Ζasa AK yace "Ziyara, za mu gaida Ummieta (kakar
JK) daga nan sai mu wuce Azare gidan Baffa Malam, Ummie ta fara sauΖowa Jahaan,
har ta ce nake zuwa gidan Baffa Malam, ke nan da yiyuwar nan gaba ta sake da Ni
Ko?"
Cike da tausayawa jahaan Ιin yace "Of course yes, Ni ka
ga da ban yi tunanin ma zuwa gidan Ummieta ba saboda tafiyarmu jibi. Za kuwa ta
ji daΙi na sani."
Kai tsaye wani katafaren sabon mall AK yace ya raka shi, AK
ne da kansa yayi mata siyayyar atamfofi kusan goma, turaren jiki, turaren Ιaki
da na banΙaki zuwa man shafawa, shi kam Jahaan kawai bin sa da kallo yake, AK
mutum ne ba gama gari ba of course, shi ne gaba da shi amma ya fi shi hangen
nesa, samun kansa yayi da shafa kansa daga nan ya koma mota ya jira shi, babu
jimawa sai ga shi ya dawo bayan ya zuba kayan a back seat. Daga nan unguwar Ummieta suka nufa da ke Zongo, a
bakin gate suka yi parking sannan AK ya Ιauko Babbar Jakar da ke shaΖe da kaya
ya damΖawa Jahaan.
Kallonsa Jahaan yayi ba tare da ya karΙa alamun yana buΖatar
Ζarin bayani.
"Take it mana."
JK yace "I'm not taking it, Kai da ka siya kai za ka
bayar, mu je kawai."
Ganin ya Ζi karΙa yasa ya riΖe sannan suka shiga, tun kafin
su isa ciki yara suka kaiwa Ummieta saΖon zuwan Yaya Jahaan da abokinsa
balarabe. Ai kuwa Ummieta ta fito daga Ιakinta tana zaman jiran isowarsu bayan
saka jikarta Shahada ta Ιauko musu ruwa da lemo a kitchen.
Da sallama suka shigo parlourn, Jahaan a gaba sai AK a
bayansa. "Maraba Lale baΖin Canada, sai yau kuka tuna da Ζ΄ar kakar
taku?"
AK da yake jin matar kamar kakarsa kasancewar shi ba shi da
ko Ιaya yace "Haba Ummieta, ai kullum kina ranmu, gidanki ne gida na farko
da muka ziyarta..."
"Ai shi yasa nake sonka Auduljalal, ka fi Jahaan
hankali wallahi, wai hakan suna shi ne babba."
Takaici ne ya kama Jahaan yace "to shi ke nan, Ni bari
na koma kayana"
Da sauri Ummieta tace "Haba Jahaan, ai kaima kana da
hankalin, ku zauna maza, ke shahadah yi maza ki kawo musu ruwa"
Nan suka fara gaisawa a mutunce, Shahada ta kawo musu ruwa
suka sha, Jahaan kam da kallo ya bi shahada yana tunanin ko Ζ΄ar waye ita Kuma
don bai santa ba."
Suna cikin hirar Jahaan ya dubi Ummieta yace "Ni
Ummieta wannan yarinyar shahada kam ban gane ta ba"
Ummieta tace "Ina kuwa za ka gane ta Jahaan kai da ba
ka da zumunci, iyayensu ma da wuya ka gane su ai saboda zaman Turai"
Wani iri Jahaan yaji sai lokacin yake ganin rashin
kyautawarsa cikin sanyin jiki AK yace "Allah sarki, Ummieta sai an haΙa da
haΖuri, kin san yanayin aikin ne sai a hankali, amma in sha Allah za mu
gyara."
Murmusawa Ummieta tayi tace "Kai dai na yarda da kai
Auduljalal, na san ka da hankali don haka na yi haΖuri amma kuma yin zumunci
Allah"
"In sha Allah" AK ya amsa mata "To ba ki faΙa
masa Shahada Ιin waye ba ce Ummieta"
"Rabu da shi Auduljalal"
"Yi hakuri dai Ummieta ki faΙa masa kika san ko Ζ΄ar
gida za a yi da ita?"
Ai ba shiri fara'ar Ummieta ta Ζaru da sauri tace "Ai
kuwa da na yi farin ciki Auduljalal, watakila albarkacinta Jahaan zai ke yin
zumunci da Ζ΄an'uwan uwarsa."
AK yace "In Sha Allah" harararsa Jahaan yayi duk
da cewa cikin ransa daΙi yaji da abun da AK Ιin yayi. Ummieta tace "Sai
Shahada Ιiyar Ζanwar uwarsa Asma'u ce, wacce ke aure a Kaduna, yanzu ma hutu ta
zo har Allah ya haΙa su, ke shahadah" Ummieta ta Ζwala mata kira, amsawa
tayi ta zo tana faΙin "Ga Ni"
Ummieta tace "Ba ki sansu ba ko? Yayyenki ne" cike
da jin kunya tace "Ummieta ai ban san su ba, ina yinin ku"
AK ya amsa mata da "Lafiya" a gajarce, yayin da
Jahaan ya washe baki yace "Lafiya Ζalau Shahada"
Cikin jin daΙi Ummita tace "To madalla, wannan shi ne
Jahaan" ta nuna JK da hannu "Wannan kuma Auduljalal" dariya
Shahada tayi babu tsammani tace
"Kai Ummieta Auduljalal kuma ai kin Ιata masa suna" shi kansa AK sai
da ya murmusa, yanayin yarinyar ya burge shi, daga gani ba ta da rawar kai irin
ta Ζ΄anmatan yanzu kuma da alama tana da kunya kuma ta samu tarbiyya. Jahaan kam
dariya yayi yace "Rabu da ita Ζanwata, Matso ta nan mu yi zumunci kafin mu
kawo muku ziyararku daban."
Shahada ta dawo ta Ιangaren da suke tana faΙin "Allah
ya ba ku iko" ya amsa da "Amin"
"To ya karatu kuma?"
"Alhamdulillah Yaya."
"A ina kike naki karatun?" Tace "KASU,
shekara ta biyu, ina karantar microbiology"
"Wow, ma sha Allah, Allah ya taimaka ya sa
albarka." Ta amsa masa da "Amin Yaya"
"Sai kuma maganar aure ke nan?"
Hannunta ta saka ta rufe fuskarta tare da faΙin "Kai
Yaya" shima dariyar yayi yace "E mana, ko ba yanzu ba?"
Shiru ta yi masa har lokacin fuskarta na rufe da hannayenta.
Sosai AK yake kallonsu, sun matuΖar ba shi sha'awa, how he
wish shima Ummiensa na da Ζ΄an'uwan da suke da yara, da zai yi ΖoΖarin yin
zumunci da su tun da bai samu kusanci da tasa mahaifiyar ba.
Yana gani Jahaan ya miΖa mata wayarsa ta saka mata numbersa,
ya matuΖar jin daΙi haka kawai yana fatan wata alaΖar apart from Ζ΄an'uwantaka
ta Ζullu tsakanin Ιan'uwan nasa da kuma yarinya mai kunyar nan shi kuma yayi
addu'ar Allah ya ba shi mai irin halayenta don ya gama nazartar yarinyar.
Ko da za su tafi Ζ΄an sauran cash Ιin hannun AK ya damΖawa
Shahada wacce ta karba a kunyace tana godiya, da kansa ya janyo yakar da ya
ajiye a bayan kujera ya dire ta gaban Ummieta tare da "A yi haΖuri Ummieta
babu yawa"
"Har da wahala haka?" In ji Ummieta "To
Madalla Auduljalal Allah ya yi albarka ya Ζara buΙi, na gode sosai, ku gaida
iyayen naku, don Allah kar ka manta ka gaida Fulani, ita kam ba ta zumunci irin
naku."
AK ya amsa da "To za ta ji Ummieta, sai mun kwan biyu
kuma"
Jahaan yace "Sai mun dawo kuma karo na gaba."
Ummita tace "Ke Shahada ki raka su mana"
Shahada tace "To" sannan ta raka su har Ζofar gida
wurin da suka yi parking, sai da suka tafi ta dawo gida tana murmushi.
Ta rasa dalilin murmushin amma wannan ziyarar ta Ya Jahaan
ta matuΖar burge ta. Da haka ta koma
gida.
Daga gidan Ummieta Azare suka nufa gidan Baffa Malam kamar
yadda suka tsara, a can ma sai da suka tsaya suka yi siyayya mai yawa wacce
kusan duka kayan abinci ne ma sai kuma shaddodi kala goma da AK Ιin ya siyawa
Baffa Malam Ιin. Shi kadai ne wani dangi na mahaifiyarsa da ya rage a dai yadda
take faΙi don shi zai iya cewa bai san komai akan Ummien nasa ba sai Ζ΄an
abubuwa kaΙan da yake tsinta daga wurin Ummah.
Manta sunan unguwar yayi don rabonsa da gidan an jima, hakan
yasa ya kira Ummie ya tambayeta, tana faΙa masa yayi tambaya aka nuna musu,
daga nan kuma suka wuce, tun da Baffa Malam yaga ana shigo da buhuhunan
shinkafa da katankatan Ιin taliya ya tabbatar da zuwan Abduljalaal, wasu hawaye
ne suka zubo daga idon tsohon. Shigowar su AK kai tsaye Ιakin Baffa Malam Ιin
yake aka kai su kai tsaye. Bayan sun gaisa haka suka yi ta hira abunsu. Jin
sha'awar sanin wasu abubuwa game da Ummiensa yasa ya tambayi Baffa Malam Ιin.
Sai dai ba wani abu da ya samu hakan yasa ya Ζara gaskata zancen zuciyarsa na
cewa akwai wani Ιoyayyen abu da ba a so ya sani game da Ummien nasa, ba ma
wannan ba, something fishy and twisted happened.
BABI NA 11
Ba su ne suka bar gidan ba sai yamma bayan kuΙin da AK ya
cika Baffa Malam da shi ya kuma karΙi
lambar tsohon da yake matsayin kakansa sannan ya musu sallama, har za su bar
Azare Jahaan yace "Ba za mu Ζarasa mu gaida Mommyn Sulaiman ba?" AK
yace "Mu je mana" nan suka juya akalar motarsu zuwa Annoor Cosmetics
suka sayi turarukan jiki, na Ιaki da na bayi daga nan suka nufi Sani Abatcha street AK na Ζara nanata abun da
ya gani, bayan sun isa sosai Mommyn Sulaiman ta ji daΙin ziyarar tasu har ba ta
so su tafi ba sai sun kwana amma da ta ji uzurinsu sai ta musu fatan Alkhairi
da addu'ar Allah ya kai su lafiya. Daga nan suka niΖi hanya zuwa Bauchi.
A gajiye suka isa Bauchi hakan yasa suka yi sallama da juna,
AK yana komawa wanka yayi ya saka kayan baccinsa, daga nan baccin wahala ya
kwashe shi.
AZARE, BAUCHI STATE
La'asar sakaliya Ihsan suka fita tare da Barr. Junaid za ta
yi shopping, kasancewar ta fi buΖatar kayan kwalliya da kuma turaruka yasa suka
nufi Annoor Cosmetics. Bayan ta gama siyan abun da za ta saya ne ta ci karo da
abun da ya Ιaga mata hankali ainun, a hanyarta ta fita ita da Barr. Junaid ta
ci karo da kyakkyawan saurayin da ya gama gajiya da haΙuwa wanda kallo Ιaya da
ta masa ta tabbatar da cewa ba na wasa ba ne, cikar haiba da zati da Ubangiji
ya masa yasa Ihsan kasa Ιauke idanuwanta, daga sama har Ζasa ta kalle shi,
tufafin jikinsa, agogonsa da komai da ya sanya yayi suiting Ιinsa kamar dai don
shi aka yi su. Ba ta san lokacin da kalmar "Ma sha Allah" ta suΙuce
daga bakinta ba, unexpected kawai ta neme shi ta rasa, ta waiga ko ina amma
he's no where to be seen, sai da Barr. Ya lura da yadda hankalinta ya bar
wurinsa ya mata magana tukun ta dawo saiti. Wata irin nauyayyar ajiyar zuciya
ta sauΖe sannan ta bi shi suka bar wurin sai dai har ta isa gida ta kasa barin
tunanin guy Ιin da ta gani, she's gone with him, gaba Ιaya ya tafi da imaninta
sai dai me? Ba ta san shi ba ba kuma ta san ina za ta samu mai kama da shi ba
bare ya haΙa ta shi. A haka suka wuce Check 'N' Buy, daga nan ya mayar da ita
gida. Ko da ta shiga gida yau gaba Ιaya
ta sauya, babu Wanda ta yi wa mummunar magana hasali ma duk wanda ya kula ta ko
kallonsa ba ta yi bare ta yi maganar, jikinta gaba Ιaya ya yi sanyi feeling very weak.
Daren yau ma sai da Uzair yazo, amma sai ya ce inji Sajid
ne, ba ta wani jima ba kuma ta kimtsa ta fito abunta, a lokacin da ta ci karo
da Uzair babu shiri ta juya za ta koma, da sauri ya sha gabanta tare da zubewa
kan knees Ιinsa yace "Don Allah Ihsan, listen to me ko da iya na yau ne ki
ba Ni damar magana da ke"
"Me kuma za ka ce min?"
"I've so many questions to you that require answers,
don Allah" ya haΙe hannayensa biyu alamar roΖo.
Kanta ta langwaΙar tace "Ni ka tashi a gabana kar wani
yayi zaton wani abun ina jin ka"
Zubur ya miΖe jin ta amince yace "Thank you babe,
thanks"
"Ka ga Uzair, ka faΙi abun da za ka faΙa ka ji"
"To, don Allah relax mana babe, it's me, that specially
made for you, ki nutsu mu yi magana in ma laifi na miki kika toshe duk wata
source of communication da ke tsakaninmu, I'm ready to die for you Ihsan,
you're the love of my life."
"Shi ne abun da za ka faΙa?"
Ya jijjiga kai "Noo, I'm only speaking my mind, Ranar
har da zuwa ki ce min an bayar da ke ko? To na ji Ihsan, In ma bayar da ke aka
yi bai kamata ki yi cutting off relationship Ιinmu haka ba unexpected kuma ki
toshe hanyar maganarmu, You know ba zan iya jurewa ba."
"Ka ga Uzair, don Allah in abun da za ka faΙa ke nan
zan wuce Ni kam"
Da sauri yace "Yi haΖuri mana, son ki jarrabawata ce
Ihsan, ke kanki kin sani, to me yasa za ki so raba Ni da rayuwata a lokacin da
nake daf da fara jin daΙinta, jiya Daddyna ma ya ce na faΙa masa gidanku za su
zo a fara maganar auren mu" sai da ta jira ya gama faΙar abun da zai ce
tuΖin ta dube shi tace "Shi ne abun da za ka faΙa?" Ya gyaΙa kai
"To ka buΙe kunnenka Uzair na faΙa maka, Ni Khadijah
Muhammad Nadada ba zan taΙa aurenka ba, idan ka fahimta fine, in kuma har yanzu
ba ka fahimta ba to ka ci gaba da zuwa, na fita hakkinka dai"
Tsintar kansa yayi da zuba mata idanuwansa wondering if
Ihsan ce ke maganar nan, anya ita ce kuwa? Kamar ta san me yake cewa a ransa
tace "Ζwarai dai Ni ce, tsohuwar budurwarka yanzu kuma na ce ba na
yi"
"Amma Ihsan kina tunanin kin min adalci ke nan?"
"Adalcin me kuma? Tun farko na ce ka fara so na
ne?"
Kansa yake jijjigawa sannan yace "No Ihsan, ba ke ba
ce, don Allah ki faΙa min laifin da na yi miki wallahi zan durΖusa gabanki ki
yafe min"
"Uzair babu laifin da ka min, dama can kai ba sa'an
aurena ba ne, ka dube Ni da kyau ka gani"
Ta faΙa tana bin mijinta da kallo
"I'm not your type ka sani, rashin hangen nesa yasa ka
afko wurin da bai dace da kai ba, now kuma mai wurin ya zo shi yasa na yanke
alaΖata da kai, zuwa yanzu na san ka gane, sai da safe."
Daga haka ta wuce gida abunta ta bar shi tsaye yana bin ta
da kallo, wai yau shi? Shi Uzair Ihsan ke cewa ba za ta aure shi ba? Yarinyar
da ya gama tsara rayuwarsa da ita? Yarinya da ke ce masa ba za ta iya rayuwa in
babu shi ba? Shin dama Ζarya take masa tun da? Dama yaudararsa take da
kalamamta ashe? Lallai yau ya tabbatar da kalmar yaudara tana existing, a da in
an ce yaudara yakan ce a'a, amma yanzu da aka masa ya yarda da cewa akwai ta.
Cikin wani irin yanayi ya juyaya nufi motarsa daga nan ya fice ta babban layi
zuciyarsa na masa Ζuna amma ya Ζudurta cewa ba zai Ζara neman soyayyar wata Ζ΄a
mace ba bare har ta samu damar yaudararsa kamar yadda aka masa, ita kuma Ihsan
ya bar ta, idan akan a'a ta fara to Allah ya shirya ta, idan kuma halinta ne
dama to ya bar ta da duniya, za ta koya mata hankali wata rana. Haka ya tafi
don yin jinyar karyayyar zuciyarsa.
Tun daga wannan rana Ihsan ta samu full concise, daga nan
suka Ιinke ita da Barr. Junaid, sosai suke nunawa junansu soyayya, kashe kuΙi
kuwa ba a magana, duk abun da tace tana so jikinsa na Ιari zai saya mata, kuΙi
a account Ιinta ba ya fashin saka mata, Mom Ιinsa already knew about her, har
pictures Ιin ta ya nuna mata, ganin yarinyar wayayya kuma kamar Ζ΄ar babban gida
yasa Mom ta amince da ita har suke gaisawa, haka sisters Ιinsa all like her,
hatta Aunty Na'ima da Aunty Amani all ya nuna musu ita sun kuma yi masa Allah
ya sa Alkhairi.
A Ιangaren Ak Washe gari babu yadda suka je daga shi har
Jahaan har wuraren Ζarfe sha biyu na rana, sai da suka yi Lunch then suka yi
sallah. Daga nan kuma suka fita suka yi siyayyar duk wani abu da za su buΖata a
can da babu shi sai a nan sannan suka dawo gida. Sai wuraren biyu da rabi tukunna Junaid ya zo ya wuce da su airport
bayan sallamar da suka yi da iyayensu daga nan kuma jirginsu ya Ιaga zuwa
Canada. A babban filin jirgin drivernsu wanda ya kasance mai jan kunne ya zo ya
Ζarasa da su muhallinsu. Suna dira Abbie suka fara kira, then papa, Ummie,
Ummah, Mammah suka sanar da shi cewa sun sauka lafiya, nan dai suka musu addu'a
da kuma fatan nasara. Dukansu ba su fita aiki ba sai washe gari bayan AK ya
sanar da JK cewa batun contract babu shi, kawai yana buΖatar dawowa ne.
JK yace "To me yasa?"
"Saboda haka na yi ra'ayi."
"Ζarya kake Man"
"Dama na saba ai" ya ba shi amsar a gajarce.
Da sauri JK Ιin yace "Haba Man, don Allah ka faΙa min
na san ba za ka yi abu irin haka ba babu wani dalili, ka daure ka faΙa min
please"
Ganin yadda ya marairaice fuska yasa AK faΙin "Jahaan
hakan shi ne kaΙai mafita gare mu baki Ιaya, ka ga yanzu batun kafin tafiyarmu
Da Papa ke yi akan mu fitar da matan aure ka cancelled sai kuma mu yi ΖoΖarin
neman kamar yadda yace next zuwa Naija da za mu yi dole mu tsayar da magana
though kai yanzu ka riga ka fita daga sahuna na searching"
Dariya JK yayi yace "Na fita sahunka kamar yaya?"
"Kada ka raina min hankali mana Bro, that your ehn Meye
ma sunan Shahida ne ko shahada? You've fallen for her"
"Who told you?"
Yace "my conscious mind"
"Then it tells you wrong, kawai dai ina so na gyara
rashin zumuncin da ke tsakaninmu ne, bari na kira ta ma."
Harara AK ya cilla masa shi kuma ya kwashe da dariya yana faΙin
"To in ma na faΙa sai me? Haram ne?"
AK yace "Noooo, not haram at all but a Capital
halal!"
"Kuma shi ne za ka wani fara min iya shegenka saboda ka
raina Ni Ko?"
Kunnuwansa ya kama tare da faΙin "I'm sorry Yaya
Jahaan"
"You better apologize" ya faΙa yana wani kame
fuska sai dai rashin sabo yasa ya kwashe da dariya, shima AK Ιin dariya yayi
wacce ta Ζawata fuskarsa kafin yace "Now tell me more about how you feel
about her, da gaske ne love exist? If yes, elaborate the feelings to me."
Tsare AK da ido Jahaan yayi yana faΙin "Ko dai ko
dai?"
"Ko dai what?" AK asked trying to calm his face
"Kaima ka samu wacce ta dace da kai?"
AK ya yamutsa fuska kafin yace "Yet! But still
searching, the fact is even complicated"
Jahaan yace "Complicated as in?"
AK yace "You know ba Ni da wani wanda zan iya tattauna
irin matsalar nan da shi apart from you, Kai kuma na san halinka, You can even
laught at me and you know am allergic to that"
Kame fuskarsa Jahaan yayi ganin Ιan'uwan nasa is like he's
in need of him, hakan yasa yace "No, yi haΖuri my bloody, ka san dai ina
dariya ne kawai in useless matters not irin wannan, feel free and talk with
your bro, that only bro you have oh! Please"
Ganin yadda Jahaan Ιin yayi sounding serious yasa AK faΙin
"Mutane da yawa suna tunanin am hard and difficult while I'm not, and
that's because I do only things peculiar to me alone, amma sun kasa fahimtata,
wasu say I'm arrogant, this and that bla bla, amma na san I'm a kinda little
bit soft in a other ways, yanzu a tunaninka ma zan samu matar da za ta so Ni
Bro?"
Jahaan da jikinsa yayi sanyi yace "Da yawa ma
dude"
"Amma saboda abun da na tara ba don Allah ba."
Jahaan yayi shiru don kuwa maganar AK na kan layi
"And kwanaki mun tattauna da kai cewa ina so na auri
macen da ke so na ne saboda Allah ba don abun da na tara ba, ina so na gina
rayuwa mai kyau da iyalina ba wai rayuwar da su suke Allah Allah na gusa na bar
musu dukiya ba."
Dafa kafaΙar AK jahaan yayi saying "maganganunka na kan
layi dude, I can say duk matan da ke bibiyarka da sunan suna son ka yanzu kawai
a baki ne, it's not you they love actually, suna dai ganin tarin abun da
Ubangiji ya ba ka ne, ka ga ni Ιin nan da kake gani ban tara abun da ya kai
naka ba ma?"
AK ya zuba masa ido yana sauraransa jikinsa duk ya yi sanyi
"Wallahi akwai mata da yawa da ke so na, not me I mean,
what I have, wallahi AK wasu har da faΙa min kai tsaye that suna sona saboda
abun da nake da, do you know what?"
AK ya jijjiga kai "Duk yawancinsu sukan ce kai suka so
amma rashin samun wannan damar yasa suke so na, ke nan, you're their target har
yanzu."
AK yace "But why all these? Duka haka matan suke? Idan
har haka ne zan Ζarasa rayuwata Ni Ιaya ne."
Trying to calm AK down, Jahaan yace "Calm down my
partner, ba duka aka zama Ιaya ba duk da cewa zamanin yanzu kuΙin mata suka fi
hange fiye da kuΙin, amma akwai waΙanda Ubangiji ya riga ya tseratar daga son
zuciya ta hanyar tsarkake zukatansu daga son abun duniya, akwai na Ζwarai
AK."
"Amma ina na Ζwarai Ιin suke Jahaan? Kullum haka ake faΙi amma Ni har yau ban samu
ba, ban samu mai so na don Allah ba sai don abun hannuna, to wai su ba sa gudun
abun hannun nawa ya Ζare ne?"
"They'll definitely leave you da zarar babu, tun da
dama can abun da yayi attracting nasu gare ka ke nan."
Dafe Kai AK yayi sannan yace "Then I'll end my life
alone, ba zan taΙa aure..." Hannu Jahaan ya saka a bakin AK ya toshe masa
yana jijjiga kansa "Don't say that dude, ina tabbatar maka da cewa you'll
find your truelove, may be today, tomorrow, or one day, just keep on praying,
you'll get her soon."
Ajiyar zuciya AK ya sauΖe yana son sanar da Jahaan wani
sirri na zuciyarsa amma yana tunanin Kada yayi, daga Ζarshe dai zuciyarsa ta
yanke barin Sirrin nan zuwa wani lokaci.
Maganar da Ummah ta masa ne ta faΙo masa a rai, hakan yasa
yayi tsaki yace "Dole na gaggauta nemawa kaina mafita JK, dole ne?"
Still dafe da kafaΙarsa har lokacin JK yace "Kada ka yi
gaggawa AK domin ba ta cika zuwa da Alkhairi ba, a cikin duk wani abu da aka yi
da nustuwa, akan samu dacewa amma a gaggawa akan riski nadama a gaba."
"To ya zan yi JK? Idan har ban samarwa kaina stand ba
zan saka kaina a damuwa, you know what?"
JK yace "No" yana jijjiga kansa
"Wai Ummah, ta samar min mata, ka ji fa?"
"Alhamdulillah, happy for you, sai ka amince
kawai"
Harararsa AK yayi yace "Ba na jin zan iya Ζetare
umarnin Ummah JK, you know, she's the
mother I can say I have, a lokacin da Ummie ta yasar da Ni, Ummah stood
for me, she deserves to be respected, ba zan Ζi zaΙinta ba JK, amma before, ina
so na bayyanar da nawa zaΙin."
"Lallai Man, kana Ιoye min wani abu ne, da alama you've
fallen for someone I don't know, kana tsoron rasa ta ko?"
"Noo" AK ya ba shi amsa da sauri "I don't
know what's love in ka cire wadda nake ma Ummie, Ummah, Abbie, Your and my
family as whole, I've never been in love you know, ta yaya ma zan san wani abu
soyayya bayan ban taΙa yi ba?"
"Your actions already say that"
AK yace "I'm not in love, but ina ji a jikina cewa,
idan na same ta she'll have all the qualities I want."
Cikin zumuΙi JK yace "Tell me please, tell me who's
she?"
"I don't know JK, I know nothing about her, not even
her face, amma dai I've saw someone like her jiya da muka je Azare."
"Ke nan dai yar can ce? Where do you people first meet
I mean your first sight?" Ya faΙa cikin raha
HaΙe fuska AK yayi yana faΙin "I don't know, but I'll
find her where ever she is JK, she'll be my perfect partner I guess"
"To Allah ya tabbatar da Alkhairi, in fa yi tsami dai
za mu ji"
AK bai kula shi ba sai ma miΖewa da yayi ya nufi fridge ya Ιauko
drink ya dawo.
A nan Ιangaren Ummah kuwa ba yya ji daΙin tafiyar tasu ba
saboda an yi lengthening cikar burinta, amma me? Ko ba komai ta tsira da karin
kima da mutunci a wurin AK Ιin, da ta tambayi Karimah ko tana son komawa can KD
ce mata tayi za ta Ιan huta kafin nan, domin Mommynta ta ce mata ta zauna za ta
aiko mata saΖo za su yi wani Ιan aiki akan Ummahn.
AK mai masoya da yawa ke nan, ita dai Manal tun ranar da
Mammah ta mata wannan Ιan Ζaramin jan hankalin ta fara ΖoΖarin cire soyayyar ya
Jalaal a cikin ranta don ta tabbatar ba za ta taΙa mallakarsa ba musamman da ba
ta ma san adadin masu son nasa ba, wacce shi yake so a ciki duk ba ta sani ba.
Safnah on the other hand
Nimrah kuwa Nennenta ta mata alΖawarin samun AK ko ta halin
ΖaΖa, duk da ta san illar abun da Nenne za ta aikata amma sai ta yi shiru don
ita kanta ta gaji da yi mata nasiha.
Kasancewar ba su da wata masaniya kan tafiyar AK Ιin yasa
Nenne yin tafiya zuwa wani Ζauye a jaharsu ta Edo don samarwa Ιiyarta farin
ciki da daula.
Abun da ta gagara sani shi ne AK kam ya bar Ζasar ga shi
kuma an haΙo ta da magunguna iri iri wanda za a yi amfani da su ma shi, wasun a
abinci wasu kuma shafawa Nimrah za ta yi ya shaΖi Ζamshin a jikinta. Ita fa
Nenne ba ta da wata matsala da ko me zai faru, don ta shirya ta yadda za ta
tabbatar ta ciyar da AK Ιin maganin, sai da ta dawo ta kira Nimrah ta baje mata
komai gabanta tana mata bayani, wani kallon takaici Nimra ke bin uwar da shi
kafin tace "To meye amfanin wadannan Ιin Nenne?"
Nenne ta dubi Ζ΄ar Tata ta ce "Sirrin mallakar
Abduljalaal ne a matsayin mijinki Ζ΄ata, already na riga na Miki wannan
alΖawarin don haka dole na cika miki shi don kuwa farin cikinki shi ne na
Nennenki"
Bayanin yadda za a yi
da dukkan kayan ta mata, Hawaye na zuba daga idanuwanta tace "Nenne ai ya
riga ya tafi, ya tafi kayansa."
"Wa Ιin?" Nenne ta faΙa a Ιan firgice
Nimrah tace "Shi Ya Jalaal Ιin, rana Ιaya kuka tafi, ba
ki jima da tafiya ba Ya Junaid ya kai su Airport suka tafi."
"What? Ke nan asarar kuΙi nayi Nimrah?"
Nimrah ta dubu mahaifiyarta tace "Ni kam ban sani
ba"
"Shi ke nan, amma yaron nan ba Ζaramin taΖadiri ba ne,
ya kashe Ni Nimrah " Ζafafuwan ta ta miΖe yayin da kayan ke tsakoyarsu
sannan ta dubi kayan tace "Chineke oo! Ya gama da Ni yarin nan, na gama
kashe kuΙina akan wannan maganin a ce ya tafi, to ko ina yake Allah ya isana,
anya wannan kuwa mutum ne?"
"To Nenne a ajiye sai ya dawo mana"
"Kin ci ubanki da sai ya dawo, maganin yana da time
limit na in ba a yi amfani da shi ba shi ke nan ya zama asara, Ni dai tsakanina
da yarin nan sai Allah ya isa, don kuwa ya gama kassara Ni, amma kuma ya zan
yi, duk tunanina kuΙina za su dawo daga ranar da ya dawo ΖarΖashin ikonmu, ashe
shi kam mugu ne, kau Allah ya tsinewa jinin Fulato (FULANI) kamar yadda suke
kiran Fulani a can yankinsu.
BABI NA 12
Washe gari da safe Imaan ta wuce wurin aikinta da wuri,
kamar kullum ba ta shiga sabgar kowa ba in ka cire Ζawarta Jamilah da take
replying zancenta time to time wasun kuma sai dai tayi murmushi. Bayan sun fita
breakfast ne wata young lady ady da ke
aiki a sashen beverages ta zo wurinsu Imaan tace "Among you people from
snacks centre, The CEO is looking for is it Fatima Nadada ko me?"
Gaban Imaan ne ya buga tana fatan Allah ya sa ba laifi tayi
ba. Jamilah ce ta amsa mata da faΙin "Ki ce tana zuwa" juyawa matar
tayi, Jamilah ta dubi Imaan tace "Imaan me yake faruwa CEO yake
nemanki?"
"Wallahi ban sani ba Nima, Allah dai yasa ba wani abun
ne ya faru ba."
Jamila tace "Amin fa, ki samu ki je akan lokaci kada ki
yi laifi."
Jiki a sanyaye Imaan ta miΖe sai dai ta kasa tafiyar,
marairaice murya tayi tace "Please Jamilah ki raka Ni"
"Ni??" Jamilah ta tambaya tana zare ido
"Ke fa yake nema not me, ba ki ja min laifi ba ba ki
jawowa kanki ba Gara ma ki wuce"
"Don Allah kawai rakiya za ki min"
"Geji zuwa bakin Ζofar office Ιin, daga nan zan
tsaya"
Da sauri Imaan tace "E na yadda"
Jamilah ta miΖe suka tafi har bakin office Ιin CEO da ba
kullum yake zuwa ba sai ya shafe dogon lokaci tukun, birki Jamilah ta ci, Imaan
tayi knockong sannan ta saka kunnenta jikin Ζofar, daga ciki taji an ce
"Yes"
Hakan yasa ta tura ta shiga a hankali, lumshe idanuwanta
tayi jin wani sassanyan Ζamshi ya buge ta.
Gabansa ta tsaya kanta Ζasa sannan ta gaishe shi, da hannu
ya nuna mata seat sannan yace "You can seat down miss" zama tayi duk
ba a sake ba while kanta na Ζasa sai wasa take da yatsunta. Kalllonta CEO yayi
yace "Are You Miss Fatima?" Ta gyaΙa kai yace "Talk to me, ba na
son maganar kurame ok?"
Shiru yayi sai kuma yace "Are You?"
Tace "Yes sir?"
Envelope ya miΖo mata ta saka hannu ta karΙa, "bayan
taro da wannan Company ya haΙa wanda ya Ζunshi executives Ιinsa an kawo wata
muhimmiyar shawara na ba wa haziΖan ma'aikata damar Ζaro karatu ko don saboda
ci gaban Companyn, gaba Ιaya executives na Company sun yi duba akan kowanne
ma'aikaci da daga Ζarshe kuma sun yi matsaya akan cewa ke ce kika fi kowa Ζwazo
da yin aiki me kyau. Da wannan nake taya ki murnar samun wannan dama, za ki
sanar da iyayenki idan suka amince to in kuma a'a sai a ba wa wani damar."
Yana kai wa Aya ya mayar da kalkonsa ga Imaan wacce ta
rungume envelope Ιin a Ζirjinta hawaye da rige-rigen sauΖa daga idanunta. Haka
kawai ya tsinci kansa da faΙin "Ya kike kuka Miss Fatima?"
Goge hawayen kan fuskarta tayi sannan ta miΖa masa takardar
tare da faΙin "Wannan takardar ba ta cancance Ni ba, a ba wa wani
kawai" daga haka ta dire ta akan table Ιinsa ganin ya Ζi karΙa sannan ta
fara takawa za ta fice. Har ta buΙe Ζofa taji ya ce "Miss Fatima"
Dakatawa tayi ba tare da ta juya ba
"Dawo ki zauna" sam ba ta so hakan ba sai dai babu
yadda za ta yi, amma ta Ζudiri aniyar cewa ba za ma ta kai takardar gida ba
gudun kada wani rikicin ya Ιarke, me ma ya kai ta in ba so take Dada ta nuna
mata iyakarta ba?
Nazartarta CEO yayi kana yace "Miss Fatima, abun da
kika yi bai kamata ba, you're making a mistake for your life because
opportunity comes ones, idan har kika bar wannan damar ta kuΙuce Miki fa za ki
yi nadama nan gaba musamman idan wasu daga cikin Companyn suka amfana da damar,
za a Ζara musu matsayi, so also the pay, she ma za a Ζara musu. Ki yi tunani
sannan ki kai takardar gidan, idan har iyayenki na su amince ba sai a ba wa wani
slot Ιin."
Ajiyar zuciya Imaan ta sauΖe sannan tace "Na fi kowa
farin ciki da wannan dama Sir amma ta fi karfina, ko na je da ita gida haka zan
dawo da ita don ba abu ne da zai yiwu ba, saboda haka maganin a yi ma kar a
fara."
"To Miss Fatima, ban katse miki hanzati ba, amma a
rashin tayi akan bar araha, ba ki san ko iyayen naki su amince ba"
"Ba za su amince ba fa" ta maimaita cikin sigar da
ke tabbatar da abun da aka faΙa.
CEO yace "na san ba hurumina ba ne hakan, amma ko za ki
faΙa min dalili?"
Tace "Haka kawai" yace "To ki ba Ni dama Ni
zan zo har gidan naku na yi magana da iyayen naki, I'm sure za su amince."
Numfashi ta sauΖe ganin CEO ya kasa fahimtarta, sai dai kuma
ba za ta taΙa bari takardar nan ta isa gidansu ballantana a shiga wata wutar
masifar. Trying hard to understand her
CEO Sulaiman yace "Is ok, za ki iya tafiya miss" jiki sanyaye Imaan
ta fice a office Ιin, ko da Jamilah tace ta tambaye ta dalilin kiran ce mata
tayi babu komai, kawai CEO ya tambaye ta shawarwari ne kan yadda za su Ζara
gyara kayansu and that's all, ba don Jamilah ta yadda ba ta yi shiru sanin
halin Ζawar Tata na zurfin ciki.
Bayan sun tashi daga aiki Imaan ta koma gida tana ta roΖon
Allah ya sa kada CEO yace zai zo gidan nan ya jaza mata bala'i, jiki sanyaye ta
Ζarasa ranar, jin babu wanda yayi sallama a gidan har lokacin baccinta yasa ta
ji daΙi maras misaltawa tana addu'ar Allah ya mantar da shi ma gaba Ιaya.
Bloordale village.
AK ne zaune a katafaren office Ιinsa yana ta aiki a system Ιin
da ke gabansa, lokaci guda ya takawa kansa birki da danna keyboard Ιin tare da
jinginar da kansa da jikin lalllausar kujerar da yake zaune, lumshe Idanuwansa
yayi yana furta sunan Allah a saman laΙΙansa.
Sumar kansa ya shafa zuwa kwantaccen sajen fuskarsa. Gaba Ιaya ya gagara
aikin da yake son yi tun kwanaki biyu baya, tunanin da yayi wa zuciyarsa
Ζawanya yasa yayi saving abun da yake yayi switching system Ιin off.
Wannan wanne irin yanayi ne yake tsintar kansa tun bayan
fara mafarkin yarinyar nan? Who's she actually? Me ya shigo da ita rayuwarsa?
Me yasa yake shiga cikin tunaninsa da mafarkinsa while bai ma santa ba, yana
jin kamar su yi maganar da JK amma zuciyarsa na hana sa, he want that to be
confidential, yana so alaΖarsa da dream girl ya zama sirri tsakaninsa da
zuciyarsa har sai ya samarwa kansa mafita. Shigowar JK da ya zauna a Ιaya daga
jikin kujerun da ke gabansa yasa ya dawo da hankalinsa gare shi.
"Are You not Alright bro?"
Jijjiga Kai AK yayi yace "No at all"
"You must not be alright I can see, me yake damunka
ne?"
AK ya ba shi amsa a gajarce da fadin "Babu komai"
Cike da kulawa JK ya riΖo hannun AK yana faΙin "Idan
har zan iya kasa gane walwalada kuma damuwarka ban ga amfanin alaΖarmu da kai
ba AK, na san batun auren nan nan, don Allah kada ka saka komai a ranka, keep
on praying, muma muna yi maka, so also Ummje I know, tana maka addu'a dude, why
za ka damu kanka bayan zaΙin Allah kake nema? Look, in ma batun yarinyar wurin
Ummah ne kada ka wani damu, she'll not do something that'll harm you, na san in
ta fahimci you're not interested za ta janye because she truly love you and
your happiness."
Kalaman JK sun yi matukar tasiri a zuciyarsa har yake jin
kamar an rage masa damuwarsa, amma kuma still akwai matsala, sai dai yana
hoping ta zo da sauΖi."
JK ne ya dube shi yace "yanzu muka gaisa da Ummieta da
Shahada, sun ce a gaishe ka kuma a maka godiya Allah ya Ζara buΙi."
Kallon JK AK yayi yana faΙin "Wai har ka fara kiranta a
waya?"
JK ya Ιage masa gira "Ko akwai matsala ne?"
AK yace "Akwai mana, akwai matsala mana za ka fara
takurawa yarinya da halinka."
"To ya za ta yi tun da tana so na?"
"Did she propose?"
Jahaan ya Ιage gira "Da zarar Ni na yi na san za ta
amince?"
AK yace "Will you?" jahaan ya gyaΙa masa kai yana
murmushi.
AK ya harare shi yace "Girma dai ya faΙi"
Da sauri JK yace "Abi?, AK ya gyaΙa masa kai
"Lallai kana ruwa kuwa Jalaal, to in ban faΙa mata ba
so kake ita ta faΙa min?"
"Yesso"
"Lallai ba ka da lafiya AK, wallah I'm eager to see
lokacin da za ka yi felling ma wata, crying in front of her, pleading her to
love you yuh! Kaiii" Ya wani yi shewa kamar mace. Wani mugun kallo AK ya
aika masa yana faΙin "Over my dead body"
"Kar dai ka cika baki"
Tsaki AK yayi zai miΖa JK ya riΖo shi "Haba my man,
daga Ζ΄ar Ζaramar magana sai ka yi fushi? To shi ke nan, a bar zancen, bari na
ba ka wuri ka ci gaba da aikinka."
Daga haka ya zaunar da shi shi kuma ya fice Abunsa yana
murmushi tare da fatan Allah sanyaya zuciyar Ιan'uwan nasa don kuwa irinsu
soyayya ta fi ba su wahala.
Ganin JK ya fice yasa AK sauΖe ajiyar zuciya, wayarsa ya Ιauko
ya fara dannawa jin hr lokacin mood Ιinsa bai sauya ba yasa ya ja dogon tsaki
tare da ajiye wayar ya miΖe daga mazauninsa ya nufi jikin window, tsgwa yayi
yana Ζarewa sararin samaniya kallo, ya jima yana karanta wasiΖar jaki don shi
kansa ba zai iya cewa ga tunanin da yake yi ba, gaba Ιaya duniyar ta tsaya masa
ba ya jin daΙinta.
Rashin maslaha da mafita yasa ya baro office tun ba a je
ko'ina ba. Ko da lokacin tashinsu yayi jahaan da ya biyo masa don jin ko zai
wuce ne ko kuma zai tsaya kamar yadda ya saba ya tarar da office Ιinsa locked,
"ikon Allah" ya faΙa a ransa yana mamakin kasancewar hakan, zuciyarsa
ce tayi saurin ba shi amsa da "May be ba ya jin daΙi ne"
Da wanna tunanin ya wuce zuwa apartment Ιinsu, bedroom Ιinsa
ya nufa kai tsaye, turus ya tsaya yana bin Ιakin da kallo ganin yadda duka
mayuka da turarukan da ke kan mirror a baje a Ζasa alamar zubar da su aka yi ga
kuma pillows a zube a Ζasa haka bedsheet shima ya samu sabon matsuguni a Ζasa
ga kuma flower vases da suka tarwatse a Ζasa so also the bedside lamp.
Cikin kaΙuwa Jahaan ke bin ko'ina da kallo yana mamakin abun
da ya faru da Ιakin, kamar wadda aka tsikara ya shiga ciki tare da wawwaigawa,
"Then wure is he?" Ya tambaya yana dudduba ko wane sashe na Ιakin.
Ζofar bayin da ya gani yasa ya nufe ta da sauri tare da murΙawa,
da sauri ya shiga ciki yana Ζwala kiran sunan AK Ιin cikin murya mai nuna
tsantsar damuwa, "Ina kake ne? Kana ji na?" Jin shiri yasa ya Ζara faΙin
"Idan wani abun kake lemme know, are you ok?"
Shiru a wannan karon ma yaji hakan yasa ya yanke shawarar
Ζarasawa ciki. Birki ya taka a lokacin da ya shiga ciki ganin AK Ιin tsaye yana
kallon mirror. Ζan tsoro ne ya Ιarsu a ran Jahaan, cikin Wata murya mai yankewa
yace "Dude"
AK kam bai juyo ba bai kuma masa ba, hakan yasa JK Ζarasawa
Wurin da yake yana mai shirin kai hannunsa jikinsa. Da sauri ya janye hannun
jin wata irin tsawa da AK Ιin ya buga masa yayin da jikinsa ya Ιau mazari.
Cikin ransa yake ambaton sunan Allah tare da faΙin
"What's wrong Jalaal?" Kamar gunki haka AK ke tsaye. "Please AK
tell me what's wrong"
Ganin ya Ζi amsa masa yasa ya lallaΙa a hankali ya tsaya a
saitinsa tare da miΖa kansa ta gefen hannun AK Ιin don samun ganinsa cikin
madubin kasancewar AK ya kere masa a tsaye.
Abun da idanuwansa ga gani yasa yayi saurin rungume AK Ιin
ta baya yana faΙin "Na shiga uku, me ya faru da kai Bro"
Duk yadda AK yaso Ζwace jikinsa daga jikin Jahaan ya gagara
coz yana buΖatar hakan, yana buΖatar jinsa a jikin wani don samun nutsuwa, sun
jima a hakan daga bisani JK ya raba jikinsa da na AK Ιin ya tsagayo gabansa,
cikin tashin hankali ya riΖo hannunsa yace "Your hand is bleeding AK, mu
je clinic a tsayar da jinin"
AK bai ce komai ba kamar wawa haka yake bin JK da ido, ganin
hakan yasa JK Ιin jansa suka fice daga toilet Ιin sannan ya nufi hanyar fita daga Ιakin, dakewa
AK yayi ya hana damar hakan, cike da kulawa Jahaan yace "Mu je mana, kana
zubar da jini fa"
Kai ya kauda gefen kafin ya iya furta "I'm going no
where, ka bar Ni duka jinin ya zube"
"Why AK, wani abu ya faru ne? Don Allah mu je mana"
AK yace "Babu yadda zan je"
Rausayar da kai JK yayi sanin halin Ιan'uwan nasa na kaifi Ιaya,
da sauri ya nufi closet ya janyo wani Siririn towel ya fito sannan ya riΖo
hannun AK ya naΙa masa ya Ιaure. Jawosa yayi ya zaunar da shi bakin bed kana ya
fara tattare abubuwan da ke zube a tsakar Ιakin, abubuwan da suka tashi daga
aiki kuma fita yayi ya shigo da bin, yana tsaye ya kwashe su sannan ya fitar da
su, bayan mintuna ya shigo hannunsa riΖe da glass cup mai Ιauke da lemu mai
sanyi. Kai tsaye wurin da AK Ιin ke zaune ya Ζarasa tare da miΖa masa cup Ιin
yace "Have this" karΙa yayi bayan ya sauΖe ajiyar zuciya sannan ya
kafa kansa, tas ya shanye shi JK yayi saurin amsar cup Ιin gudun kada shi ma ya yasar, a gefensa ya ajiye sannan ya
zauna kusa da AK Ιin.
Shiru ne ya wanzu na wani lokaci daga Ζarshe JK ya katse
shirjn da kiran sunansa.
Bai Ιago ba bare ya sa ran zai amsa, amma dai ya tabbatar da
ya ji, hakan yasa ya dafa shoulder dinsa yace "Dude, me yake faruwa
ne?" Shiru yayi bai amsa masa ba har lokacin bugun zuciyarsa na fita da
wani mugun sauri ga wani irin zazzafar iska da yake fitarwa. Wannan dalilin
yasa Jahaan tsorata don zai iya cewa a zamansa ko kuma dai rayuwarsu da Ιan'uwan
nasa a taΖaice bai taΙa ganinsa cikin yanayi kwatankwacin wannan ba, duk da
cewa a baya ya yi jinya sosai akan yadda Ummie ta banzatar da shi har yana tunanin
ko wani laifi ne ya aikata gare ta amma tun bayan da ya fahimci rayuwa ya
watsar da komai ya samu lafiya duk da cewa dai har yanzu akwai burbushin wannan
damuwa, Jahaan ya Ιauki hakan kuma a matsayin abun da zai iya faruwa da kowanne
Ιa da uwarsa ta saddakar da shi ga wata uwar a wani babi wai shi na kara.
Matsawa kusa da shi sosai Jahaan yayi don ba ya manta
lokutan baya da yayi ta fama da jinya, likitan da ke lura da shi yakan ce a
yawaita samar da skin-to-skin contact da shi, hakan ka iya rage masa raΙaΙi da
damuwar da yake ji.
A wannan yanayi sun shafe kimanin awa Ιaya kafin daga bisani
Jahaan yaji jikin AK Ιin ya saki alamar bacci, tallafarsa yayi gudun kada ya faΙi
sannan ya kwantar da shi kan bed Ιin shi kuma ya zauna yana kalkonsa tare da
tausaya masa, yana kuma roΖon Ubangiji da ya azurta shi da mace ta Ζwarai wacce
za ta maye masa wasu muhimman gurabu da yake da giΙinsu a rayuwa.
Tsawon awanni uku AK ya farka, ko da ya gana farkawa da
tunanin me yake ya fara, ganin shi kwance yasa ya miΖe zaune yana bin Ιakin da
kallo kafin daga bisani ya tsaida kallon nasa ga Jahaan da ke jingine da fuskar
bed Ιin yana gyangyaΙi.
Idamuwansa ya lumshe tare da fara tariyo abubuwan da suka
faru, tun daga lokacin da tunanin yarinyar da yayi wa laΖabi da dream girl Ιinsa
ya addabe shi, zuwa tunanin gizon da ta masa a ranar da suka kai wa Baffa Malam
ziyara, zuwa tunanin yadda zai Ζara tozali da ita ya kuma yi mata tambayoyin da
yake da su tattare da ita tun daga kan dalilinta na shiga rayuwarsa ta kuma
liΖewa tunaninsa da kuma rayuwarsa ga shi har yakan iya ajiye ayyukan da ke
gabansa a dalilin tunaninta da ya addabj zuciya da ΖwaΖwalwarsa. Yana iya tuna
lokacin da ya mike tsaye yana tunanin me zai aikata ya daina tunaninta ne ya
fara jin kansa na sarawa, takamaimai ba zai iya tuna lokacin da ya bar office
har ya dawo apartment ba, zuwa kuma yanzu.
A hankali ya ci gaba da bin Ιakin da kallo yana bin komai da
komai na cikinsa, bedside lamp bai ga ba so also flowers Ιin da ke jere kan
mirror Ιinsa, "what really happened?" Ya tambayi kansa, "ke nan
dai ba mafarki ba ne? This girl is making me crazy and I don't know why"
ya faΙa cikin zuciyarsa tare da ziraro Ζafafuwansa Ζasa, toilet ya shiga ya
watsa ruwa, a nan ma ya ga sauyi sosai bayan ya fito ya sanya jallabiya ya yi
ΖoΖarin tayar da Jahaan da baccin ya fara cin idonsa, a matuΖar firgice ya
tashi hakan yasa ya dire Ζasa tare da tsayawa sannan ya dafo kafaΙar AK Ιin
cikin kulawa yace "Man! Ka tashi, I'm worried about you, what all made you
behave strange e?"
"Me kuma nayi?" He asked in his soft voice
Kallonsa Jahaan yayi yana Ζara nazartarsa, tabbas ya lura
bai san abun da yayi ba, hakan yasa ya sauΖe hannunsa da ya Ιaura a shoulders Ιin
AK ya ja hannunsa suka fita, kai tsaye bin ya nuna masa, broken pieces of
bedside lamp, flower bases and kwalaben creams Ιinsa kusan bakwai.
Ζauke da ayar tambaya ya dubi Jahaan ba tare da ya ce komai
ba. Jahaan yace "Sit down first" babu musu kuwa ya zauna shima ya
zauna next to him
"Ka Ιauke Ni a matsayin Ιan uwa?"
AK ya tsira masa ido ba tare da ya ce komai ba.
"Ka yi shiru?"
A hankali AK yace "Ban gane ba"
Jahaan yace "Ina nufin ina da matsayin Ιan'uwa a
wurinka?" AK ya gyaΙa kai
"Babban aboki fa?" Ya Ζara gyaΙa masa kai
"Don Allah AK, Abduljalaal! Don Allah, idan har ina da
waΙannan matsayin da ka ce Kada ka Ιoye min damuwarka"
AK yace "Tell me what happened first and I promised to
tell you what's wrong with me"
"Deal?"
AK ya gyaΙa kai tare da faΙin "Deal"
Jahaan yace "na biya ta office naka to know if you're
leaving sai mu tafi tare, sai na tarar closed, i was surprised saboda na san ba
ka barin office before time hasali ma har da daddare kana iya zama ka yi wasu
muhimman ayyukan, I rushed home to see if all is ok shi ne na..."
Nan ya labarta masa komai sannan yace "now you're
promise"
Kamar AK ba zai ce komai ba can kuma yace "I'll ask you
first, In ka amsa min zan yi amfani da amsoshin da ka bani domin na maka
bayanin what's actually going"
Tsananin son sanin me ke damun AK Ιin yasa jahaan amincewa
da batun AK.
Shiru suka yi can AK yace "Yaya ake gane feeling na so?
Ina nufin ba irin wadda ke existing tsakani Ιa da kuma iyaye ba ko na
Ζ΄an'uwantaka?"
Juya idanuwa Jahaan yayi sannan yace "Are You too in
love?"
Harararsa AK yayi sannan yace "Ba ka shirya jin damuwar tawa ba ke
nan?"
Jahaan yayi saurin faΙin "Nooo" tare da jan
Ζarshen "amma tambayar taka ce tayi confusing Ιina, tana da alaΖa da
damuwar taka ne?"
"I don't know"
"Ok, keep on going ina jinka?"
"Should I?" AK ya tambaya "Ka amsa tawa
tambayar ne?"
"Jahaan ya dafe Kai yana fatan shiriya ga Ιan'uwan nasa
don ba kaΙan ba tun suna yara ma haka yake wahalar da Jahaan Ιin duk da shi ne
babba sai dai sassanyan hali da yake da shi yana danne girman da yake da shi
har wasu kan yi tunanin AK Ιin ne gaba da Jahaan.
AK "I'm all ears" cikin halin ko in kula
"To kaima dai ka san nima ban sani ba tun da I've never
been in love"
"Ke nan i should tell Shahida or shahada the naked
truth that you don't love her?"
Jahaan ya zaro ido tare da faΙin "Haba AK, ina ΖoΖarin
in taimaka maka kana shirin ruguza Ni?"
"Then give me my amswey"
"Na faΙa maka nima ban sani ba, but we can Sulaiman to find out sai mu duka biyun mu
samu ilimi"
Da sauri AK yace "You can call him alone, ni Kai na
tambaya in ba ka sani ba fine sai a bar magabar
ai ba dole ba ce.
Jahaan ya dafe kai yace "To ai shi ke nan"
Tunawa da illar rashin amsa tambayar yasa Jahaan faΙin zan
kira shi idan ya so sai mu ji ilimin tare.
AK bai ce masa komai ba har ya Ciro phone Ιinsa yayi
dialling numbern Sulaiman.
BABI NA 13
Suna zaune tare Jahaan ya kira Sulaiman, da farko bai Ιaga
ba sai a kira na biyu don dama bai tsammanin hakan ba tun da dai dare ya yi.
Ζara jarrabawa Yayi a karo na biyu, cikin ikon Allah Sulaiman ya Ιaga, gaisawa
suka yi har yana tsokanar Jahaan Ιin wai yau ya tuna da shi, ya tambaye shi ina
AK yace ga shi a kusansa, sanin hali yasa bai ce ma a ba shi su gaisa ba, ai
kuwa ko an bayar Ιin ba magana zai yi ba musamman yadda ya wani hakimce ya Ιaura
Ζafarsa akan Ιaya.
Gyaran murya Jahaan yayi kana yace "Ka ga Sulaiman Ζ΄ar
tambaya gare Ni"
"To ba damuwa ina jin ka"
Jahaan yace "Don Allah idam mutum ya kamu da soyayya ta
yaya zai gane, wato yaya feeling Ιin soyayya yake?"
Dariya Sulaiman yayi a Ιangarensa kana yace "Ko dai ka
zurma ne mutumina?"
Jahaan ya Ιago ya kalli AK shi kuma ya zabga masa harara.
Dariya yayi Ζara-Ζasa sannan yace "Ni dai kawai ka faΙa min in ka
sani"
Dariya Sulaiman yayi yace "Ai dole na fada maka kaji,
idan ta tabbata mu samu mu aurar da ku, Ζawaye kowa ya yi aure amma banda ku,
Allah dai ya kawo matan da za su kwashe mu kafin..."
"Ka ga Sulaiman, ba surutu nace ka min ba"
Jahaan ya faΙa saboda kallon da AK Ιin ya masa
"Tooo" shima ya ba shi amsa "Lallai na yarda
zama da maΙaukakin kanwa shi ke kawo farin kai don kuwa ga shi kaima ka fara
koyon halin Abduljalaal "
Tsaki Jahaan yayi don so yake AK yaji amsarsa shima ya faΙa
masa damuwarsa
"Please ka ba Ni amsa in ka sani"
"Me ye ma tambayar taka?"
Jahaan yace "Nace ta yaya ake sanin an kamu da soyayya
sannan ya feeling Ιin soyayya yake?"
Gyaran murya Sulaiman yayi yace "wato in na fahimce ka
alamun kamuwa da so kafin an furtawa juna?"
Cike da takaicin yadda Sulaiman ke jan maganar yace "E
haka"
Sulaiman yace "To Kamar yadda masu iya magana suka ce
so ba ya boyuwa tabbas haka ne domin da
zarar so yafara shiga zuciya sai kuma gangar jiki ta fara nuna wasu Ιabi'u da
alamomin na so ko na amincewa, wasu daga cikin alamomin kamuwa da so kamar
Burgewa, wato da zarar kaga budurwa tana burge ka haka kawai ko dan wani abu
kamar ΖoΖarinta ,kyanta kwalliyarta, ko
wani abu da ya shafe ta,.To hakan alama ce dake nuna cewa zuciyarka za ta iya amsar soyayyarta."
Jahaan yace "Ina jin ka"
Sulaiman ya ci gaba "Abu na biyu da ke nuna alamun cewa
ka kamu da so akwai kallo, yawaita kallon abun da ka kamu da soyayar tasa ko da
kuwa ba za ka iya hakan ba, da zarar so ya fara processing a zuciyar saurayi ko
za ka ga ka fara jin kunyarta koda ba a furtawa juna kalmar so ba musamman ma
idan ba ka taΙa soyayar ba, idan ka kalleta sai ma ji ka masa sakewa a kusa da
ita har ka kasa iya haΙa ido da ita, idan kuma cikin rashin Sa'a ka kalleta Ιin
kuka yi four eyes sai kaga ka kauda kai da wuri kana jin wani irin yanayi na
fusgarka."
"Wata alama mai nuna tabbas akwai so ita ce jin fargaba idan an samu kusanci ko an ambaci ko
da sunan abar Ζaunar ce ko kuma sauyin bugun zuciya idan an samu wani kusanci
duk ΖanΖantarsa. Masu raunin zuciya a irin wannan yanayin suka rasa control
musamman waΙanda kaΙaici ke Ιawainiya da su, hakan kuma zai iya sa su yi
mummunan aiki kamar dukan wanda ke kusa da su saboda rashin gano ainihin me ke
damunsu ko kuma su yi fa yin abu kamar masu taΙin hankali".
Shiru Sulaiman yayi tare da haΙiyar yawu. Cikin zaΖuwa
Jahaan da ke jin kamar da shi ake yace "E ina jin ka"
Sulaiman yace "Na gaba, yawan tunaninta a ranka, Kaji
kana so ake labari akanta ko kuma kai kanka kana son bayar da labarinta
musamman ga makusantanka.."
"Da zarar so ya Ζullu yakan haifar wa da zuciya tunani
sosai, wani lokacin tunanin ya haifar da farinciki domin zai raya ma ai waccce
yake son za ta so shi don yana da kaza da kaza
har sai ka gamsar da kanka zata soka sai kaji farinciki, a wani lokacin
kuma so sai yasa ma tunani me zafi da shakkum anya kuwa za ta so ka? Anya wani
bai dace zuciyarta ba this and that..."
"Daga nan fa?" jahaan ya tambaya cike da zaΖuwa
"Daga nan sai ka fara jin kana son Ζulla alaΖa da ita
ko mutunci. Daga alaΖar ta Ζullu sai ka
ji kana so. Kasancewa tare da ita a kowanne lokaci, yawan tunaninta, tausayi da kuma kyautatawa za su biyo baya,
za ka ji cewa za ka iya kasancewa da ita a kowanne irin yanayi.
Rashin bayyanar da wannan saΖo saboda wani dalili na kunya
ko wani abu kan iya haifar wa da mutum tunani maras yankewa a kowanne lokaci
har mutum ya fara ji ya Ζosa da rayuwar in aka kai wani lokaci kuma wani ciwon
ya kama mutum musamman na zuciya saboda rashin samar mata da nutsuwa da aka yi
ba tare da an farga ba."
Wata irin ajiyar zuciya AK da ke sauraronsu yayi shi kuwa
Jahaan gaba Ιaya ji yake ma kamar da shi ake, cikin ransa yace "Ke nan dai
son Shahada nake?"
Maganar da Sulaiman yayi yasa ya tuna cewa bai yi
disconnecting call Ιin ba
"Ya dai JK?"
Jahaan yace "Na gode Ζwarai Sulaiman."
Sulaiman yace "Allah yasa wata ce ta sace zuciyarka
jahaan" dafe saitin chest Ιin sa yayi tare da kallo AK da fuskarsa ba ta
wani bayyana wata alamar da za ka fahimci yanayin da yake ciki ba sannan yace
"Ka saka Ni a addu'a kawai Allah ya ba Ni ita, sai da safe" Ζit ya
katse kiran saboda sabon halin Sulaiman Ιin na yawan magana, ko shi kansa at
times in suna tare da Sulaiman uzuri kawai yake masa bare kuma AK.
Kusa da AK Ιin Jahaan ya matsa sannan yace "To Man, ka
cika alkawarinka"
"Wane alkawarin kuma?" Ya faΙa with his innocent
face and look
"Wallahi ba ka isa ba Jalaal, dole ka faΙa min abun da
ke damunka ko kuma na sanar da Abbie"
Da sauri AK yace "Behave maturedly mana, So kake ka
daga masa hankali for no reason?"
jahaan yace "e! Haka nake so, ai gara ya san yanayin da
kake ciki tunda Ni da nake kusa da kai ka Ζi fadamin after all ni tawa damuwar
ba na iya Ιoye maka don Ni ina gudun abu ya wuce tunani a ga laifina"
Jikin AK ne yayi sanyi, ko ba a faΙa masa ba ya san Jahaan
na daban ne gare shi kuma kyauta da Ubangiji ya ba shi mai tsananin daraja, tun
yarinta suke tare, yake sadaukar masa da abubuwa da yawa ciki har da farin
cikinsa domin nasa, je deserved to be treated well of course.
Sanyaya murya AK yayi yace "Zan faΙa maka, amma not
now"
Jahaan bai ce masa komai ba ya fice daga Ιakin sannan ya
nufi nasa Ιakin.
AK na ganin fitar Jahaan ya sauΖe ajiyar zuciya sannan ya
miΖe ruwa ya watsa daga nan ya sauya kaya. Ji yayi kawai babu abun da yake
buΖata fiye da Muryar mahaifiyarsa duk da ya riga ya san cewa ba wata maganar
za ta yi da shi ba, amma duk da haka he still needs it.
Kiran fari Ummie ta daga, daga gaisuwa kuma babu wani abu da
ta Ζara faΙi, haka suka share kusan mintuna sai ita ta kashe kiran. Numfashi ya
sauΖe sannan ya kira Ummah, sosai suka gaisa tana ta ce masa tayi kewarsa this
and that.
Sun sake suna hira abun su ta kawo masa zancen Karimah, da
haka ya mata sallama da faΙin dare ya yi, babu yadda Ummah ta iya suka katse
kiran tana sakin zazzafan huci. Bai bi ta kan Jahaan ba don ya riga ya san cewa
zai ne shi, hakan yasa ya fice garden don shan iska da kuma Ιebe kewa.
AZARE, BAUCHI STATE
A Ιangaren Imaan tun da taga kwanaki biyu sun shuΙe wata
wutar masifar ba ta Ιullo a gidan nasu ba ta tabbatar da cewa CEO Sulaiman ya
riga ya janye batun tafiyarta Ζarin karatu, sosai kuma hakan ya mata daΙi yayin
da Ihsan kuma komai ya Ζaru, ji da kai ya Ζaru haka ma dogon Buri sai abun da
ba a ce komai ba, yanzu fantamawa take abunta don yanzu suturun da take
ta'ammali da su, gyalalluka, Cosmetics da dai sauran kayan amfani duk sun fita
daban don kusan duk tsoffin kayanta ta bar wa Imaan su duk da cewa dai English
wears ne amma ta karΙa tun da dai hijabi ita take sakawa ba mayafi ba. Kayan
maΖulashe kuwa kamar su buΙe baki su yi magana don yadda Barr. Junaid ke ajiye
mata su niΖi niΖi wanda hakan ya mata matuΖar daΙi har tana jinta daban cikin
duniyar baki Ιaya, ji take ta fi kowacce mace Sa'a a duniyar nan, abu mafi jin
daΙi gare ta ma bai wuce yadda take juya Barr. Ζin ba don kuwa duk abun da ta
ce ba ya tsallakewa.
Shi dai ya gama kamuwa da soyayyar Ihsan fiye da kuma kuma
har yanzu bai san cewa ba ita ce wannan yarinyar da zuciyarsa ta fara harbuwa
da Ζaunarta ba kasancewarta ba, a yanzu ba shi da wani burin da ya wuce ya
kyautatawa Ihsan tun da har a gidansu babu wanda ya nuna Ζinsa a kanta, sai dai
abu Ιaya da yake Ιaga mas hankali shi ne duk yadda Ihsan ke nuna masa so da
Ζauna ta Ζi ba shi damar isowarsa gida, a cewar ta ita sai ta kammala
karatunta, to yaya zai yi tunda duk abun da take so shi ma yana so? Dole ya
zubawa sarautar Allah ido har zuwa lokacin da Allah ya tsara musu zai yi.
Abu Ιaya da bai sani ba shine, Ihsan ba wai shi take so ba,
kuΙin hannunsa kawai take Ζauna don ita a nata tsarin ko yau ta haΙu da wanda ya fi shi, babu jiran da za ta
yi za ta rabu da shi ta auri wanda za ta zama abar nuni, ta zama ta musamman
cikin mata ta yadda ko wacce mace za ta so irin daular da take ciki. To tun da
ta rabu da Uzair gani take babu wani namijin da ba za ta iya barinsa ba idan ta
samu wanda ya fi shi. Abu Ιaya kuma ya tsaya mata a rai da kuma ruhinta, ta
kuma gagara cire shi, takan tsinci kanta cikin kewa da kuma tunanin halittar da
ta yi wa kallo Ιaya tak a rayuwarta tare da fatan ina ma a ce wannan kyakkyawar
fuskar Tata ita ce kwance a kan fuskar Junaid, to babu shakka ita mai amince
masa ne su yi aure, sai dai fuskar nan ta gagara barin ruhi da ΖwaΖwalwarta,
gani take kamar wannan fuska ita ce abokiyar rayuwarta, amma ta yaya? Ta yaya
za ta Ζara ganin fuskar bayan ba ta san ta yadda za ta fara ba?
Ihsan ke nan, wannan dalili yasa ta fara tunanin ta yaya za
ta samu wannan fuska ko kuma makamanciyarta? "dandalin sada zumunta!"
Ta ba wa kanta amsa.
Tun daga yau kuma ta fara buΙe hajojinta a social media
fatanta dai Allah ya sa ta dace, a yanzu dai facebook ne kawai Ihsan ta Ζi
aminta da buΙe account a can don su Ramcy sun ce mata masu facebook faΖirai ne.
Washegari Imaan ta tashi da kewar Hajiya, kasancewar weekend
nr yasa taji tana muradin zuwa gaida Hajiya Ιin. Misalin Ζarfe goma na safe ta
shirya cikin wani Navy blue palazzo trouser da Ihsan ta ba ta, ta haΙa da
rigarsa sannan ta shafa Ζ΄ar powder da kuma wet lips, sosai tayi kyau kamar me,
abun ka da wadda bai saba ba dama an ce in ya yi ta fi yi masa kyau.
BaΖin takalminta ta saka da kuma baΖin Hijab sannan ta yi wa
Mami sallama ta fice. Mai adaidaita ta tsayar, ta ce masa ya kai ta Filin
pastor, bayan ya kai ta ta ba shi kuΙinsa sannan ta nufi gidan Hajiya. Gaishe
da Baba Bala mai gadi ta yi ya amsa yana tsokanarta wai yau ta tuna da su, Ιauke
da murmushi kan fuskarta tace "Haba Baba Bala, dama ban mance ku ba,
yanayin aiki ne yasa ba na ziyartarku amma ai Hajiya tawa ce akwai amana'
"Allah Imani (kamar yadda yake kiranta)"
"Ta gyaΙa kai tare da faΙin "Bari na shiga wurin
Hajiyar tawa "
"To shi ke nan, ki fito lafiya"
Kanta ta saka ta nufi sashen Hajiya, Ιauke da sallama a
bakinta ta shiga, babu kowa a parlourn sai Yar matashiyar da ke goge-goge.
Gaishe da ita Imaan tayi itama ta mayar mata da gaisuwar tun
da kusan a girme Imaan Ιin ta girme mata.
Kujera ta nunawa Imaan tace "Ki zauna, bari na yi wa
Hajiyar Magana."
Imaan ta zauna tare da fadin "Na gode"
Free minutes sai ga mai aiki Hajiya na biye da ita, da
saurin Imaan ta miΖe ta nufi Hajiyan tare da rungumeta tana jhun murna.
Itama Hajiyar dariya take tunda Imaan Ιin ta nufo ta. Cike
da farin ciki Hajiya tace "irin wannan Oyoyo haka Imaan ai sai ki karya
Ni"
Imaan ta janye jikinta tana Ιan tura baki
Hajiya tace "Yau ke ce a nan? To mu koma cikin kawai,.
Sa'ade ki kawo mata wani abun"
Daga haka ta riΖo hannun imaan suka nufi Ιakinta.
A bakin gadi ta zaunar da Imaan tare da fadin "Ni fushi
ma nake da ke Daughter, yanzu kin fara mantawa da Ni"
Imaan tace "Wane Ni in manta da Hajiyata? Wai haka Baba
Bala ma yace na manta da ke bayan kuma ya san yanayin aikinmu "
Hajiya ta taΙe baki tace "E, aiki aiki kamar ke ce
shugabar aiki, rabin ki da nan Imaan tun yaushe?'
Imaan tayi rolling Idanuwanta tace "Hajiya wata biyu ne
fa kawai"
Hararar wasa Hajiyar ta aika mata tare da faΙin "Kawai
ko? To ina ce dai yau Ιin kwanaki za ki mana?"
Zaro idanuwa Imaan tayi tare da faΙin "Kai Hajiya, iya
kayan jikina ma nazo da shi, zan dai yini da yamma sai na tafi"
Hajiya ta zauna grfenta tace "Ban fa yarda ba Imaan,
Mami ta rike min ke a gidanta ta hana Ni ke, gaskiya dai, to shi ke nan."
Imaan tace "Hmm, Hajiya ko gaisawa fa ba mu yi ba kike
ta nemo mana magana"
"Oh? Maganar ma nemota nake?"
Imaan ta toshe bakinta da hannayenta kana tace "Ni dai
Ina kwana, kin tashi lafiya?"
"Lafiya Ζalau Imaan, ya su Dada, Mami, Abba da
ihsan?"
"Lafiyarsu Ζalau, Mami ta ce a gaida ki ma"
Fuska sake Hajiya tace "To ina amsawa kuwa, ya aikin
naki? Ina fata dai kina jin dadinsa"
Imaan ta gyaΙa kai, Hajiya ta ce "BuΙe baki za ki yi ki
faΙa min Imaan ba ki gyaΙa min kai ba,
Jiki sanyaye Imaan tace "Alhamdulillah, ina jin dadinsa
sosai"
Nazartarta Hajiya ta yi kafin ta ce "Ma sha Allah"
sai kuma ta yi shiru tana bin Imaan Ιin da kallo har sai da ta tsargu, can tace
"Lallai Ikaan, to ya batun samari kuma? Ina ce yanzu dai akwai
tsayayye"
Ζan tura baki Imaan tayi tana faΙin "Ni fa babu kowa,
na fi so ma na yi rayuwata a haka Hajiya"
Sakaka Hajiya tayi tana kallon Imaan har ta gama maganar
kana tace "E lallai kam, biri ya yi kama da mutum, samarin ma kora su kike
yi ke nan?"
Bakinta gaba tace "To Ni Hajiya ba zan yi aure ba, ko
kina tunanin ma Dada za ta bari na yi aure ne bayan Ihsan tana gidan?"
"Ke da Ihsan Ιin waye gaba ne e? Wai har yanzu Dada ba
ta sauya hali ba ne?"
Imaan kam ba ta amsa mata ba sai ajiyar zuciyar da ta sauΖe.
Hajiya tace "Shi ke nan, na fahimta Imaan, amma dai ki
cire batun wata Ihsan a ranki duk da cewa na san ba iyawar za ki ba, ki fahimci
rayuwa kuma ki sani, yanzu ne lokacin da tauraron yake haskawa, babu wata
magana ta sai kin jira Ihsan, idan har kika yi wasa da damarki zuwa gaba ba
lallai ne samarin ma suna kallonki ba sai an haΙa da addu'a."
"Don haka ki nutsu ki ji Ni ma, idan har don wannan ne
kike korar samari to ki daina, idan har akwai Wanda ya zo kuma kika ji ya
kwanta Miki sannan kika yi istikhara kika ji dai kika son hakan ki sanar da Ni
first, don na ga in ta Maminki za a biye haka za ta Ζunshe baki ta ki magana,
saboda haka ki fara faΙa min kin ji?"
Imaan ta gyaΙa kai yayin da hawaye ke zubo mata, share mata
Hajiya tayi sannan tace "Yauwa, ki nutsu ki ki abun da na faΙa Miki kin ji
yarinyata?" Still imaan didn't t say anything bayan gyaΙa kai da ta yi.
Ganin yadda ta suΖure saboda maganar da suka yi yasa Hajiya
kawo mata wani zancen, ba a wani jima ba kuwa imaan ta sake suna hira abun su,
abun mamaki kuma yadda suke hirar suna dariya tana wani shagwaΙa abun ta, hakan
ya tabbatar da cewa ko wace ce wannan Hajiya tana da girma mai tsoka da muhalli
babba cikin zuciyar Imaan tun da har ta iya sakewa suke hira, wannan
suΖurarriyar Imaan Ιin kuma ta sauya zuwa wata daban.
Haka suka yini abun su, Hajiya sai Ιauko abubuwan motsa baki
da ba ta gajiya da su take tana ba wa imaan Ιin ita kuma na sha, salla ce kawai
take tayar da su, sai kuma gama abincin rana da aka yi suka ci. Wuraren Ζarfe
biyar Hajiya ta yi baΖo wanda yayi silar tafiyar Imaan Ιin babu shiri bayan
atamfofi kusan huΙu da Hajiyar ta haΙa ta da su da kuma kuΙin da ba ta san nawa
ba ne sannan tace da ita kar tana jimawa da yawa ba tazo mata ba, sosai ta kuma ba wa imaan Ιin sakon gaisuwa
ga Abba da Mami kana tace a gaida Dada ma. Bakkn nan kuwa ba kowa ba ne wannan baΖo sai CEO Sulaiman..
Tun da Imaan ta tafi take ta saΖawa da kwancewa cikin ranta
tana mamakin me yazo yi gidan Hajiya? Sai dai kuma daΙin da ta ji shi ne shi
bai ganta ba, fatanta Allah ya sa kar ya kawo batun karin karatun da company ya
ba ta dama ta yi rejecting don abu mai sauΖi ne Hajiya tace za ta tsaya har
Imaan Ιin ta tafi.
Bayan Imaan ta koma ta isar da saΖon gaisuwar Hajiya ga kowa
sannan ta budewa Mami kayan da Hajiyar ta ba ta, ta ba wa Mami Ιaya ta kuma
miΖa mata kudin tace ta biya kuΙin Ιinki sannan ta ajiye mata sauran, babu
tsammani Dada ta shigo kamar aljana ta fizge kuΙin da Imaan ke mikawa Mami.
"Munafukan Allah ta'ala, wai Ni Rahanatu sai zuwa yashe
ne za ki daina koyawa Ζ΄ar nan munafurci? Anya kuwa za ku shiga aljanna?"
Imaan da takaicin Dada ya cika ta tace "Dada Hajiyata
ce fa ta ba Ni shi ne na ba wa Mamin..."
"Ungo nan munafuka!"
"Don ubanki Hajiyar taki sai tace ki ba wa uawarki
kawai? Ko don dama can bakinku Ιaya itama ai munafukar ce, aikin banza da
wofi" ta sa hannu ta tattaro atamfofi kana ta nufi hanyar waje tana faΙin
"Na ga Ni da ku wai zai gaji ya bar wa wani don wallahi har abada ba zan
mance da ku ba munafukai kawai"
Ajiyar zuciya suka sake a tare Mami kam haΖuri kawai take ba
wa Imaan wacce ko kaΙan hakan bai wani dame ta ba sai ma mikewa tayi sannan ta
nufi Ιakins
BABI NA 15
A hankali soyayya ta mai Ζarfi ta fara shiga tsakanin
Muhammad da Rahanatou, a Ιangaren guda kuma ginin da yake yi ya yi nisa sosai, Dada
kuwa a yanzu ba ta da burin da ya wuce taga ta ruguza batun auren Muhammad da
Rahanatou sai dai duk yadda tayi ba ta cin nasara. Ana haka Ba ya buΖaci
Muhammad da ya turo magabatansa don a nasa tsarin ba ya so auren ya daΙe ba a
yi ba saboda yana so su koma Ζasarsu bayan auren Rahanatou.
Duk da cewa Dada ta riga ta yanke duk wani zumunci da ke
tsakaninsa da dangin mahaifiyarsa wanda dama ba wani yawa gare su ba, ta
ΖoΖarta sosai ta raba zumuncinsa da Ιan'uwansa Ιaya Abdullahi wanda shi ma tasa
uwar ta goya masa bayan yanke alaΖarsa da Muhammad Ιin. Karo na farko da jikin
Muhammad yayi sanyi don kuwa ba shi da wani na kusa da zai ce zai tura, wannan
dalilin yasa ya fara bincike don nemo lambar wayar da zai samu Ιan'uwan nasa,
bayan wahalar da ya sha daga Ζarshe dai ya samu, bayan sun gaisa ya buΖaci
adreshinsu don kai musu ziyara, Yaya Abdullahi yasa aka tura masa ta message.
Cikin satin Ya shirya ya je har Lagos gurin Ιan'uwansa wanda ya ji daΙi ziyarar
shi na, ai jini ba wasa ba ne, haka suka yi sato a can, ranar da zai dawo har
da kukansu tukun Yaya Abdullahi ya nema masa motar da za ta kai shi gida sannan
suka yi wa juna sallama.
Sati guda da komawar Muhammad gida ya kira Ιan'uwan nasa ya
sanar da shi batun neman auren nasa sannan ya roΖi Alfarmar ya shiga ciki a yi
da shi, sosai Yaya Abdullahi yayi farin ciki da hakan, ya kuma yi masa
alkawarin shiga cikin hidimar tasa, daga nan ya nufi wurin wani malami da
gidansa ke kasuwar Kaji, almajirin mahaifinsa ne hakan yasa kai tsaye ya faΙa
masa abun da ke tafe da shi, daga nan ya buΖaci Muhammad Ιin da ya sanar da
iyayen yarinyar ranar Litinin za su je su haΙu da magabatan nata.
Cikin ikon Allah kuwa ba a ja auren ba aka yi shi a cikin
abun da bai wuce watanni uku ba, daga nan iyayen amarya suka buΖaci tafiya da
ita can Nijar don ta ga gida saboda su ba dawowa nan Ιin za su yi ba sun koma
can kenan. Dada wacce ko kaΙan ba ta so aka yi auren nan ba amma tun da an fi
Ζarfinta haka ta haΖura ta shiga aka yi hidima da ita, abun da ma ya taka
muhimmiyar rawa wurin haΖurin Dadan shi ne gidan da Muhammad Ιin ya gina kuma
nata Ιangaren ma ya fi nasa Ζayatuwa.
Bayan su Rahanatou da Muhammad sun dawo daga Nijar, aka miΖa
ta gidan Mijinta, hamdala ta yi wa Ubangijinta don kuwa dai ita kam ta dace, ga
miji na gari ga kuma rayuwar jin daΙi, sai dai ashe hasashenta ne wannan Ιin
don kuwa Dada ta Ζudiri aniyar bin kowacce hanya don ganin ta raba auren
Rahanatou da Muhammad.
Kasancewar Rahanatou mace wacce ba ta da tashin hankali yasa
duk ΖoΖarin Dada na ganin ta takalo ta ta mata rashin kunya hakan bai faru ba,
tsawon shekara guda da auren ne kuma Rahanatou ta fara Ζosawa da al'amarin Dada
amma in ta tuna nasihar da mahaifinta da kuma Mahaifiyarta haΙi da dangi suka
mata sai ta watsar da komai ta ci gaba da rayuwarta.
Ana haka kuma ciki ya bayyana jikin Rahanatou, bayan watanni
kuma ta haifi Ιa namiji, mafarin raguwar Ζiyayyar Dada ga Rahanatou ke nan, don
sosai take son yaron wanda ya ci sunan marigayi Malam na Dada, wato Muhammad
Ashir, sosai yaron yake ganin gata daga kowanne fanni kama daga kan Dada zuwa
Mahifinsa, uwar ma ba a bar ta a baya ba don yadda take jin sa cikin ranta ba a
magana.
Bayan ta yi arba'in ne suka shirya ita da Muhammad suka nufi
Nijar, yaro kam tabarakallah ya shiga ran dangin mahaifiyarsa ma, daga nan suka
dawo bayan sun yi kwana biyu a can tare da goma sha tara ta arziΖi.
Tun da Muhammad Ashir (wanda Dada ke Ζira da BabaΖarami) ya
kai watanni huΙu ta fara Ιauke sa daga wurin mahaifiyarsa, in ta dawo da shi to
kukan yunwa yake yi. Bayan an yaye shi kuwa kwacakom Dada ta sa aka tattara
mata kayansa ya koma wurinta da zama.
Soyayar Dada ga BabaΖarami ba a magana musamman da ya
kasance takwaran mijinta, a yanzu dai fatanta shi ne idan Rahanatou ta haifo
mace ita ma a mata mai suna, haka BabaΖarami yayi ta wayo har ya kai shekaru
biyar, bakinsa yasa mahaifinsa sanya shi a makarantar boko da Islamiyya sai dai
har zuwa lokacin Rahanatou wacce BabaΖarami ke kira da Mami ba ta Ζara samun
ciki ba ga shi kuma kullum Dada cikin faΙa take wai ta daina haihuwa in ta saka
wasa Muhammadu zai Ζara aure.
BabaΖarami na aji biyu na nursery Allah ya ba wa Rahanatou
ciki, ita kanta ta yi farin ciki da hakan ko don Ζwarzabar da Dada ke mata,
kulawa sosai take samu daga mijin nata wanda tun cikin yana da watanni ya Ιebe
mata wasu ayyukan. Hajiya Dada sai murna take tana addu'ar Allah yasa a haifi
mace don a yi mata takwara ita ma, wahala sosai Mami ke sha don ko a cikinta na
fari ba ta sha irin wannan ba, bayan wasu watanni ranar wata Alhamis Mani ta
fara naΖuda, haka Dada ta yunΖura don
taimaka mata ta haifi jaririn ko jaririya amma ina, haihuwar ta Ζi zuwa
ga kuma uwar wahalar da Mami Ιin ke sha, a taΖaice dai kwanaki uku ta kwashe
tana fama sai a na huΙun ta haifi yarinyarta kyakkyawar gaske fara Ζal da ita
don kuwa ta ma fi Muhammad kyau, kar ku so ku ga Yadda Dada ke Ιaukin yarinyar,
a lokacin da Abba ya samu damar magana da Mami yake tambayarta "wani suna
za a saka wa yarinya?"
Cike da maΙaukakin mamaki tace "Ni za ka tambaya kuma
Abba?"
Ya gyaΙa kai yace "E mana, wannan karon kin sha wahala
sosai a haihuwa shi yasa ko kaΙan ba na so na tauye Miki haΖΖi, ina so ki zaΙi
sunan da kike so a saka wa yarinyar"
Da sauri tace "Amma Dada ta ce a mata mai suna ai, idan
aka saka sunan da ba nata ba za ta ji babu daΙi"
"Kada ki damu, zan yi mata bayani ai, idan kin Ζara
haihuwa sai a mata, na san Kema a irin wahalar da kika sha dole kina da zaΙi
and ba na son na tauye Miki"
Shiru Mami tayi can tace, "Haka ne ina da zaΙi amma ina
tsoron Dada kada ta ji haushi"
"Hmm, na faΙa Miki zan mata bayani, ki faΙa min
kawai"
A sanyayr tace "Ina so a saka mata sunan mahaifiyata
Amma (Fadimatou)"
Murmushi Abba yayi kana ya karbi jaririyar da ke kwance kana
ya mata huΙuba da suna Fadimatou kamar yadda Mahaifiyarta ta buΖata."
Tsabar yadda Mami ta ji daΙi har da hawayenta, bai wani jima
ba ya fito daga Ιakin, karo suka ci da Dada wacce ke ΖoΖarin shigowa da dahuwar
da ta yi wa Mami.
Ja da baya yayi yace "Yi haΖuri Dada, ban san kina
tahowa ba ne"
"Ba komai wai dama ina ta sauri na na kaiwa Rahanatou
dahuwar nan, ka ga fa har yanzu ruwan Nonon bai zo ba, any ba za a je asibiti
ba?"
Duniyar Tunani ya faΙa sai da Dada ta Ζara kiran sunansa
kana ya zabura yace "E, Dada ina ga za a je asibitin ma"
"Yauwa ai ya kamata, don ina son takwarar tawa ta yi
kuzari sosai amma rashin abincin nan yasa take Shegen kuka sai dai bacci in ya
sace ta uwar ke samu ta huta"
Yau ake wata ga wata, kun ji Dada fa, wai takwararta? Shiru
Abba yayi Dada tace "Gyara ka ga in miΖa mata"
Ba tare da ya ce komai ba ya kauce Dada ta shige, ajiyar
zuciya ya sauke daga nan ya wuce Abunsa yana tunanin ta yadda zai sanar da Dada
cewa ya riga ya yi wa jaririyar huΙuba.
Har yarinya ta cika kwana shida babu wanda ya san an mata huΙuba
ban da mahaifiyarta da kuma mahifinta wadanda ke tunanin ta yaya za su yi wa
Dadar bayani. A Ιangaren Dada jin shiru har zuwa lokacin Abba bai yi magana ba
yasa ta Ζudiri aniyar yi masa tuni don a nata tunanin ko mantawa yayi.
Da daddare bayan ya dawo gida yana cin abincin dare Dada ta
zo don su yi magana, bayan sun gaisa ta yi shiru can tace "Dama mace zan
maka tuni ne har yau da ba ka yi wa yarinyar nan huΙuba ba ga shi gobe sati
cur"
Ba tare da Abba ya dube ta ba yace "An riga an mata huΙuba"
Cikin farin ciki Dada tace "Ai ina ce mantawa ka yi,
ashe an riga an mata, dama na sani ai"
A ba zata ta ji Abba ya ce "Sunan yarinyar Fatima"
Tsaye Dada ta yi tana kallon Abban fuskarta na nuna yanayin
mamaki "Fatima kuma,?"
Abba da ya gama cin abincin ya ture tray gefe yace "E
Dada, ki yi haΖuri na san kin so a ce mai sunanki ne, ki yi haΖuri karo na gaba
sai a Miki takwarar"
Nuna Abba Dada ta yi da yatsa tace "Lallai Muhammadu,
wallahi za a sauya sunan ne Yanzu tun da babu wanda ya sani, Hadizatu za a yi
wa yarinyar huΙuba a karo na biyu"
Ganin yadda Dadan lokaci guda ta Ιau Ιumi yasa Abba matsowa
kusa da ita sannan ya saisaita muryarsa kana yace "Dada ai ba a yi huΙuba
biyu tun da sunan da aka riga aka yi huΙubar ba shi da wani kushe, sunan Ιiyar
ma'aiki ne mafi soyu..."
"Dakata Muhammadu!" Dada ta katse shi a fusace
"Ya zai ka ce haka? Shi ma Hadiza ai suna ne kuma sunan matar ma'aiki
meyasa ba za a saka shi ba"
Runtse idanuwa Abba yayi can yace "yanzu kam an riga an
saka ki yi haΖuri Dada"
Ζara saisaita muryarsa yayi sannan ya ci gaba "Itama
Rahanatou ba za ta ji daΙi ba idan taji kina faΙin ba ki son sunan."
"Ban gane ba" Dada ta tambaya tana tsare Abba da
ido, sunkuyar da kai Abba yayi yace "ki yi haΖuri Dada"
"Ba wannan na tambaye ka ba, ban gane Rahanatou ba za
ta ji daΙi ba"
"E Dada, eh, ai dama sunan mahaifiyarta ne"
Tafa hannu Dada ta fara tana salallami
"Lallai kam, ba shakka biri ya yi kama da mutum, yanzu
ke nan ka zaΙi bin umarnin matarka akan nawa Muhammadu?"
"A'a Dada, ki yi..."
"Ba zan yi ba, nace ba zan yi haΖurin ba Muhammadu, Ni
za ka tozarta ina?"
Abba ya jijjiga kansa yana sunkuyar da kansa Ζasa
"Ko dan ma shi ke nan, fice min a Ιaki to, je ka ba Ni
wuri kafin raina ya gama Ιaci kuma"
Babu musu Abba ya fice ya bar Dada wacce ke surfa masifa ita
Ιaya, ya fice ne kawai ya bar ta saboda ya ba ta lokaci ta sauΖa tukun yadda za
ta fahimce shi, a sukwane ya Ζarasa sashen Mami.
Washegari suna, abun
ka da mace mai sanyi da daΙin zama irin Mami, duk da dai dangi dai na kusa kam
babu amma maΖota da abokan arziΖi tun da safe suka fara shigowa gidan kowa sai
tambayar sunan yarinya yake, kowa da ya ji an ce Fadimatul Imaan sai ya yi
mamaki saboda yadda in an shigo Barka Dada kowa ya zo sau ta ce masa takwararta
ce Hadiza, ganin Dada shiru ba ta fito ba kuma babu wanda ya ga gilmawarta yasa
mutane fara tambayar ina take, A sanyaye Mami ke ce musu tana sashenta. Haka
dai aka fara Ιaura girki shiru babu Dada babu labarinta, wasa-wasa har taron
suna ya watse ba ta fito ba. Wannan dalili yasa Mami lallaΙawa ta nufi sashen
Dadan don dubawa ko lafiya.
Tana shiga kai tsaye ta shige parlourn Dada tana mai
sallama. Daga uwar Ιaka Dada ta fito tace "Me kuma ya kawo ki?"
Jikin Mami ne yayi sanyi don ta riga ta fahimci dalilin Ζin
shigowar Dadan saboda an yi wa Amma mai suna ne, a sanyayr tace "Ki yi
haΖuri..."
"Rufe min baki munafukar Allah ta'ala " Dada ta
katse ta tana nuna ta da Yatsa, "dama an riga an ce min buzaye akwai su da
iya mallaka, a fuska kamar ba za ki yi komai ba ashe Kema ba Ζaramar Ζyalle ba
ce turmin Zami ne"
Wasu siraran hawaye Mami ta Ιan goge jin kalmar da Dada ta
jefe su wai mallaka.
A hankali ta kuma cewa "Don Allah Dada"
Ζara katse ta Dada ta yi tana faΙin "Ba zan ji komai
daga bakinki ba Rahanatou, ai walΖiya aka yi ta haska, da Muhammadu ya bi
shawarata da bai aure ki ba tun farko"
Goge Ζwalla Dada ta fara yi da gefen zaninta sannan tace
"Tun bayan haihuwar Babakarami kika ji ina cewa in Allah ya Ζara kawo
Ζaruwa sunana za a saka kuma Muhammadu bai taΙa ce min wani abu ba haka ke ma,
ashe ke kin riga kin Ζulla komai, a dare Ιaya kawai sai ki sauya ra'ayinsa ya
saka sunan uwaki?"
Sunkuyar da kai Mami tayi jikina ya gama sanyi ba tare da ta
ce komai ba.
"Na tsane ki Rahanatou saboda ke ba Alkhairi ba ce ga
ahalina, tun daga kan aurenki Muhammadu ya fara ja da Ni, yanzu ga shi in na
yanke hukunci ma saka shi kike ya take, daga ke har jaririyar taki da kika raΙa
mata sunan uwaki babu Ni babu ku, na tsane ku gaba Ιaya kuma ba zan taΙa son ku
ba, Muhammadu kuma da kika mallake Allah ya fi ki don ki shirya kwanan nan zan
je a karya asirin da kika masa a gun Malam daga nan kuma aure zai Ζara, matar
da za ta mutunta zaΙina ta kuma haifa min takwara nima."
Dada na gama faΙin haka ta Ζule Ιakinta tana huci yayin da
ta bar Mami na goge hawaye, da kyar Mami ta iya Ιaga Ζafarta ta koma nata
sashen.
Sai wuraren Ζarfe 11pm na dare Abba ya shigo gida fuskarsa
na nuna tsantsar damuwa. Though itama Mami Ιin na cikin damuwa kuma ta yi
shirin sanar da shi in za a iya sauya sunan Imaan a mayar da shi na Dada ta
amince amma ganin yanayin fuskarsa yasa ta fasa.
Cikin kulawa ta tambaye shi ko me ya faru? Don a tunaninta
ma ko akan batun Imaan Ιin ne sai dai takardar da ya miΖo mata tasa hannu ta
amsa tare da duba ta, karantawa tayi saboda ba ta fahimci ta Meye ba ta Ιago
tare da sanya idanuwanta cikin nasa don buΖatar Ζarin bayani.
Cikin yanayi na Ζunci da damuwa yace "Takardar tsayarwa
ne daga aiki"
A tsorace tace "Me?"
Ya maimaita mata kamar yadda ya faΙa a baya
"Innalillahi wainna ilaihy rajiuna" ta furta kana
tace "Dakatarwa kake nufi Abba?"
Ya jinjina mata kai alamar tabbatarwa.
HaΙe jikinsu tayi sannan ta fara magana cikin murya mai nuna
damuwa da kulawa tace "Ubangiji ya sa hakan shi ne mafi Alkhairi, dama
haka Allah yake in ya so, a wasu lokutan yakan hana mu abu ne idan har ba
Alkhairi ba ne ya kuma ba mu abun da ba ma jin sonsa idan har Alkhairi ne. Kada
ka saka Ζunci da damuwa cikin ranka, in sha Allah taskokin ubangiji za su Ζara
buΙuwa kuma babban rabo na zuwa nan gaba."
Ajiyar zuciya Abba ya sauΖe jin kalaman matar tasa kuma abar
Ζaunarsa, shi yasa yake Ζara son ta don kuwa idan ta masa kalamanta masu tsada
yakan ji damuwarsa ta ragu kamar dai yadda ta faru yanzu.
Hannunta ya haΙa cikin nasa sannan yace "Allah ya gyara
mana Ζasar nan kawai, daga yunkurin tabbatar da gaskiya sai a dakatar da
mutum?"
Mami tace "Na san da wahala ka iya mantawa, amma ina
roΖonka da ka rage damuwar nan, ba na so wani abu ya same ka, ka tuna akwai
Dada, Ni, Babakarami da kuma Imaan, ka kula mana da lafiyarka don garemu
garkuwa ce, batun aikin nan kuma in sha Allah wata damar za ta zo"
A sanyaye Abba yace "Allah ya amince"
Tace "Amin"
MiΖewa yayi da shirin fita, Mami tace "Ina kuma za ka
je?"
Yace "Zan sanar da Dada ne"
Ta jijjiga kai tare da miΖewa ta tsaya kusansa "A'a ba
yanzu ba, na san yanzu ma tana da damuwarta musamman ta rashin yi mata takwarar
nan wanda yanzu nike ji kamar a sauya a saka natan, idan ka Ζara faΙa mata
wannan magana hankalinta zai tashi azimun, kada mu je abubuw sau haΙu su mata
yawa ta shiga damuwa. Mu Ιan jinkirta zuwa gobe haka"
Na'am da shawar Mami Abba yayi hakan yasa bai sanar da Dada
ba sai washe gari.
Bayan ya sanar da Dadan abun da ya faru ne ta wani miΖe a
zafafe tana bin both Mami da Abba da mugun kallo
"Ai dama na sani" ta faΙa tana mai tafa hannayenta
"Dama na san za a rina! Mu kam yau mun shiga uku an haifi mana tsiya a
gida, ayo tsiya mana"
Cikin son kwantar mata da Hankali da dakatar da ita daga faΙin
munanan maganganunta Abba yace. "Haba Dada, Ζaddara ce kawai ba komai ba,
mu amshe..."
"Ka ci uwaka da Ζaddara Muhammadu" Dada ta katse
shi tana yi masa danΖwalo.
"Alqur'ani babu wani Ζaddara a nan, an dai haifi
jaraba, Gara ma dai da ba a saka mata sunana ba ashe, don kuwa wannan Ζ΄a sam ba
ta da albarka, a ce a ranar sunanki ubanki ya rasa aikinsa? Ku fice min a falo
kafin wani abun ya kuma faruwa, Na dai nanata muku ku ji Ni raΙau, babu Ni babu
wannan yarinya da kuka haifa don ko sunanta ba zan fadi ba naje wani bala'in
nima ya bi Ni" tana kai wa nan ta wani gyara zaninta ta shige uwar Ιaka,
Hannun Mami Abba ya kama suka fice daga sashen Dadan duka zukatansu babu daΙi
musamman kalaman da Dada ta saki don kuwa dai sun munana a mahangae rayuwa,
hankali da kuma tunani kai kyau.
A taΖaice wannan shi ne mafarin Ζiyayyar da Dada ke yi wa
Imaan wacce a halin yanzu ba ta san me ake ba infact ko duniyar ma ba ta sani
ba. Shawara Abba yayi da Mami akan sana'ar da zai fara da kuΙaΙen da suke
hannunsa saboda zaman banza dai ba zai kai su ga ci ba sakamakon Ιawainiyoyin
iyali daga Ζarshe dai suka yanke shawarar ya buΙe shagon kayan masarufi tun da
unguwar dai babu shaguna ma a kusa. Bayan ya sanar da Dada shawarar da ya yanke
ta amince da hakan duk da cewa har lokacin haushinsa take ji daga shi har matar
tasa da alkaba'in yarinyar da suka haifa amma da ta tuna da BabaΖarami sai ta
ce da Abban kawai a sayar da gidansu na gado kawai idan ya so ya Ζara akan
jarin nasa, gidan bai wani yi kuΙi ba saboda ginin duk ya zube saboda rashin
mutane a ciki, nan Dada ta damΖawa Abba kudin tana masa addu'ar buΙi.
A hankali aka fara kasuwa kuma alhamdulillah, babu abun da
za ce don babu laifi komai na tafiya daidai wanda a bangaren Dada har yau ba ta
Ζara Ιaukar Imaan a hannunta ba hasali ma uwar Imaan Ιin ma dai ba tsira ta yi
ba.
BABI NA 14
TUNA BAYA
SOME
YEARS BACK
1970
Layin
Nadada, Azare, Bauchi state of Nigeria.
Gida ne ginin Ζasa mai Ιauke da Ιakuna kusan huΙu a Ζofar
gidan wanda suka kasance na almajirai, idan ka bi ta Ζofar gidan kai tsaye wani
dogon lungu ne wanda zai sada ka da Ζofa da ke ta kudu, wannan Ζofa ita ce za
ta sada ka da ainihin cikin gidan. Ζakuna kusan biyar ne a jere, sai kuma bayi
jikinsu, ta Ιaya Ιangaren kuma madafa ne da aka kewaye da langalanga. A
tsakiyar wantamemen filin da ke tsakar gidan kuma, Ζatuwar bishiyar ceΙiya ne
da kuma maina wanda suka samar da yalwatacciyar inuwa mai sanyi a gidan.
Gidan Nadada ko a ce Malam Nadada sanannen gida ne a cikin
garin Azare da ke Jahar Bauchin Najeriya kasancewarsa gidan babban malami wanda
ke da tarin almajiran da ke karatu a Ζarkashinsa. Malam Ashiru Salmanu, shi ne
ainihin sunan Malam Nadada, sunan Nadada kuma da ake masa inkiya da shi sunan
matarsa ce DADA da aka Ιamfara masa shi.
kasancewar shi Malam Nadada ba shi da wata sana'a bayan
koyarwa, hakan yasa wasu lokutan hatta abinci yakan so ya gagari gidansa,
wannan dalili ne yasa ya fantsama kan aikin noma, da taimakon almajiransa kuwa
suke aikin, cikin sahalewar Ubangiji noma ta karΙe shi, daga nan kuma komai ya
fara tafiya masa yadda ya kamata.
Malam Nadada na da Mata uku, Dije, wacce suke cewa Dada ita
ce uwargida, Maryo ita ce turaki, sai kuma Hali amarya. Auren Dada da Malam
Nadada auren haΙi ne kasancewar Dada Ιiyar malaminsa, kuma yabawa da halinsa da
mahaifin nata yayi ne ma ya sa ya bashi auren nata. Sosai suke zaman lafiya duk
da cewa kuwa Dada irin matan nan ne masifaffu da ba a iyar musu kuma ba sa iya
gani su yi shiru, faΙa kuwa babu irin wanda ba ta yi wa mijin nata babu ruwanta
da idon mutane masu shigowa, shi kuwa Malam sai ya sunkuyar da kai kamar shi ne
matar ita kuma mijin. Malam Nadada ya kasance irin mazan nan ne masu sanyin
hali, ko kaΙan ba ya son rigima ko tashin hankali, da wannan Ιabi'a tasa matan
nasa ke ganin sun uzzurawa rayuwarsa. Suna amfani da wannan sanyin halin nasa
ne su tayar da rigima wanda shi kuma sam ba ya iya kashe ta.
Aurensu da Dada da kusan shekaru goma ba su taΙa haihuwa ba,
wannan dalilin yasa Malam Ζara aure, sai dai auren matar tasa ta biyu, Inna
Maryo, babu abun da ya Ζara sai tayar da gobarar masifa da bala'i a gidan
kasancewar yana auranta da watanni ta samu ciki, kar ku so ku ga rikicin da aka
tafka da Dada lokacin da Inna Maryo ta haifu, da Ζyar da kuma siΙin goahi aka
samu wutar masifar nan ta lufa, ranar suna kuma yaro yaci sunan kakansa na
wurin uwa Abdullahi, ba a wani daΙe da
haihuwar ba, Malam Nadada ya Ζara aure,
Hali mace ce ba kamar sauran ba, mace ce mai sanyin hali da rashin son fitina,
hakan yasa da wuya duk wata rigima da za ta Ιullo a gidan kaji ta a ciki
musamman da ko takalarta kayi ba kula ka za ta yi ba.
Shekarar Hali Ιaya a gidan ta samu juna biyu, itama ta haifi
Ιanta kyakkyawa da shi, yaci suna Muhammad. Muhammad yaro ne kyakkyawan da ya Ιauko
siffofi da kamar mahaifiyarsa Inna Hali wacce ta kasance bafulatana Usul, sam
yaron ba shi da hayaniya hatta irin kukan da jarirai ke yi shi kam da wuya ka
ji nasa, a haka ya fara girma har ya kai shekarun tafiya, farin jininsa da kuma
rashin rigimarsa yasa harta almajiran Babansa ke Ιaukarsa su fita da shi a haka
har ya fara sabawa da yaran da ke unguwarsu, lokuta da dama idan rikici ya Ιarke
babu abun da Muhammad ke yi sai kuka duk da cewa ba da shi ake yi ba, wasu
lokutan har shiΙewa yake musamman idan rikicin ya haΙa da kokawa, cizo da kuma
yaguni, wannan dalilin yasa Inna Hali hana shi fita.
Ζaki guda aka warewa Muhammadu da Abdullahi, lokutan da yawa
Abdullahi wanda halinsa ya banbanta da na Muhammad ya kan gallaza masa, Ζ΄ar
katifar da aka saya musu ta kwanciya sai ya hana Muhammad kwanciya akanta ya
dudduka shi, sai dai shi Muhammad ko sau Ιaya bai taΙa kawo Ζarar Abdullahi ba.
Ana haka Inna Hali ta Ζara samun juna biyu, wannan karon
yarinya mace ta haifa wacce ke da matuΖar kyan fuska tun tana Ζarama, kamanni
kuwa da mahaifiyarta har ta dama irin ta Muhammad. Bayan suna yarinyar ta ci
suna Fatima. Yadda Malam Nadada ke ji da Fatima yasa sauran matansa jin kishin
hakan musamman Dada da ita ko Ζwaya ba ta da shi, rikicin yau daban na gobe
daban in har sai sayi wani abu yace na Fatima ne.
Watarana, ranar da ta bar wa ahalin Malam Nadada tarihi.
Ranar wata juma'a da daddare, gobara ta tashi a Ιakin Inna Hali, a ranar kuma
Malam a Ιakinta yake, a takaice dai wannan gobara da Ζyar aka kashe ta sai dai
ba a samu ko da burbushin mutanen da ke kwance a Ιakin ba daga kan Malam
Nadada, Inna Hali da kuma yarinyarta
Fatima.
Wannan babban rashi da aka yi ya taΙa kowa musamman Muhammad
da a lokacin yake jin ina ma tare da shi iyayen nashi suka tafi sai dai abun
mamaki Dada ta tsaya ta ba shi kulawa sosai ganin ya mance da al'amarin da ya
faru, tabbas aiki Ja Dada ta yi don kuwa ta yi iyakar iyawarta wajen ganin
Muhammad bai yi maraici ba don sosai take aiki tuΖuru wajen ganin ya samu
ingantacciyar rayuwa, duk da cewar a ba
a karatun boko a gidan sai da Dada ta tsaya ta saka Muhammadu a makarantar
gwamnati ta je ka ka dawo wato Yagana Lawan primary school azare yadda aka saka
shi a aji biyu lokaci guda saboda girmansa, sai dai hakan ko kaΙan bai dami
Muhammadu ba wanda shi a lokacin burinsa kawai yaga ya yi karatu kamar yadda
Dada ke ce masa in ya yi karatun za su yi kuΙi su kuma manta da wahalar da suke
sha, cikin ikon Allah kuwa sosai yake ja, ganin haka yasa malam makaranta
tsallakar da shi zuwa ajin gabansa, a taΖaice dai lokacin da suka gama primary
shi ne Ιalibi mafi hazaΖa. Wannan dalili yasa malakansu takawa har gida suka nemi
izinin Dada kan Muhammadu ya yi jarrabawar shiga makarantar kwana amma Dada fir
tace A'a, hakan yasa ta ci gaba da biya masa kudin karatu a makarantar
sakandare ta je ka ka dawo (government day school Azare).
Shekararsu uku kuma suka kamalla da wani sakamakon mai kyau,
daga nan suka shiga aji Ιaya na babbar sakandare, bayan wasu shekarun suka zana
jarrabawar fita, abun mamaki a kaf jahar Bauchi babu Ιalibin da ya kai
Muhammadu fita da sakamako mai kyau, wannan dalilin yasa wani malaminsu samar
masa da aiki da hukumar Ζ΄ansada, sosai shi da Dada suka yi farin ciki mara
misaltuwa.
Ganin yadda kuΙi suka Ιan fara shigowa Muhammadu yasa Dada
tsayawa kan haΙa aurensa da wata Ζ΄ar moΖatansu Balkisu sai dai shi sam ya Ζi
amincewa kasancewar bai yarda da tarbiyyar yarinyar ba sam, ran Dada sosai ya Ιaci
game da hakan har ta yi fushi da shi. Ganin haka ya sa ya sauΖo ya aminta da zaΙin
Dada a lokacin da ya tuna irin wahalar da tayi da shi a rayuwa ganin ya zama
wani, butulce mata da zai yi akan ΖanΖanin abu sai duniya ma ta zage shi. Haka
babu jimawa ya fara zuwa hira wurin Balkisu bayan nema masa izini da tilon Ιan'uwan
mahaifinsa Mal. Abdurrazak yayi. Ko kaΙan Ιabi'un Balkisu ba su da kyau don sai
a lokacin ya tabbatar, amma idan ya yi ΖoΖarin nunawa Dada illar hakan sai ta
fashe masa da kuka tace wai ya nuna mata ba ita ta haife shi ba, haka dolensa
ya ba ta hakuri daga nan ya ja bakinsa ya kulle.
Sati biyu da bikinsa da Balkisu zancen ciki ya bayyana a
jikinta, a wannan karon ita kanta Dada ta nuna Ζinta ga haΙin duk da cewa
mahaifiyar Balkisun aminyarta ne tun aurenta a gidan Malam Nadada, abun mamaki
da aka titsiye Balkisu akan wa ya mata sai ta ce Muhammadu, an sha gwagwarmaya
sosai kafin gaskiya ta bayyana, tun daga nan Dada da Baba Kaule suka daina
mu'amala.
Duk da cewar dai an sha gwagwarmaya kafin gaskiyar ta
bayyana ko ma dai yaya ne, shi kam Muhammadu ya ji daΙi, da wannan dalili
Muhammadu ya Ζara nusar da Dada kan rayuwa, ai kuwa ta Ιauka amma ta Ζara roΖon
alfarmarsa kan ya ba ta dama ta zaΙar masa mata a karo na biyu, ko kaΙan bai ji
komai ba ya ma ba ta damar yayin da a nashi Ιangaren yake neman matar shi ma da
kansa, a niyyar sa idan Dada ta riga shi, to fa ko ba daΙe shima zai auri zaΙinsa,
idan kuma a tare suka samo to sai yayi sangaya tun da dai babu laifi samunsa
zai iya rikesu.
Ana wannan gaΙar ne wata rana suna tafe a motar Ζ΄ansanda
sakamakon kira na gaggawa da aka musu gidan wani hamshaΖi suka kaΙi wa Ζ΄ar
budurwa da kallo Ιaya za ka mata ka san cewa Buzuwa ce, ba ta wani ji ciwo ba
amma ta kiΙime irin da yawan nan, da kyar dai suka samu yarinyar ta dawo daidai
har ta samu bakin surutu da tsiwa, lokaci guda kuma yarinyar ta tafi da
zuciyarsa, komai nata ya burge shi, daga nan suka miΖa yarinyar gidansu wanda
yake sananne ma a garin, har ciki suka shiga, maigadin gidan ya yi musu godiya
a matsayinsa na mahaifin yarinyar har ma ya ba su damar gaisawa da mahaifiyarta
wacce itama dai buzuwar ce kamar uban. Sosai ta yi wa su Muhammadu godiya, daga
nan suka wuce, tun daga wannan rana Muhammadu kan zo su sha hirarsu da Baba
Souley buzu, haka Amma matarsa, ita ma dai Yarinyar mai suna Rahanatou har sabo
ya shiga tsakaninsu.
Watarana Dada da Muhammadu na zaune suna hira ya kawo mata
batun cewa ya yi budurwa, sosai Dada ta rikice har da kukanta wai ta nuna masa
ba ita ta haife shi ba, da wannan kukan nata take iya karyar da zuciyarsa don
kuwa kalamanta rauninsa ne. Bayan ta nustu ya mata bayanin yarinyar har yake
tabbatar mata da cewa za ta so ta, amma fir Dada ta ce a'a, ganin yadda ta hau
yasa yace to su yi wani alΖawari, ta nemo masa mata ya amince amma dole zai haΙa
ta ne da Rahanatou, ganin dai a yau ta kasa yin nasara kan Ιan nata yasa ta
shige Ιaki ta rufe.
Bayan kwana biyu da faruwar hakan bai Ζara Ιago zancen ba
kwatsam sai Dada ta tunkare da batun cewa ta amince ya auri Rahanatou amma duk
lokacin da itama ta kawo Tata zaΙin dole ya bi, sosai yayi farin ciki maras
misaltawa, a daren ranar da ya je hira gidansu Rahanatou ya sanar da ita cewa
yana sonta kuma aurenta zai yi, kasancewarta mace mai tsananin kunya yasa ta
shige dakin Amma da gudu har suka ci karo da Amma wacce ke fitowa da nufin
kawowa Mahammadu shayinsu wanda yake matuΖar so tun ranar da ya fara sha.
"Ke lafiyarki?'
Rahanatou ta kasa magana sai zazzare idanuwa take kamar Ιarauniya
tana wani Ζunshe baki.
Amma tace "Sai kuma ki yi ta yi ai Raha, kina tafe
kamar ba kya gani."
Daga haka ta fito, ganin yadda Muhammad ke dariya yasa Amma
faΙin "Lafiya kuwa Muhammad?"
Yace "Amma lafiya Ζalau, kawai dai Ιiyar taki ce ta ba
Ni dariya"
Amma tace "Tooo, me kuma ya faru, hala ta Ζara yi maka
Ζauyancin ko?"
Dariyar tasa ya tsagaita tare da faΙin "A'a ko kaΙan,
na dai ce Baba zai ba Ni aurenta wai shi ne take kunya"
"Ikon Allah" Amma ta faΙa tana miΖa masa shayin da
ta zuba masa a kofi "To in ban da abunta jn ta samu ya kai a ta huta,
Baban nata ma cewa yake ko yau ta samu miji aurar da ita zai yi"
Muhammadu yace "Aaaa, ma sha Allah to ai kawai da zai
yarda da sai a yi Ζ΄ar gida, sai dai matsalar an ce ku buzaye ba kwa aurarwa
bare"
Ya karasa cikin sanyin Muryar da ke nuna karaya.
Amma tace "A'a Muhammadu, duk da ba a cika hakan ba
amma na san Ba ba zai hana ka auren Raha ba, kai Ιin mutumin kirki ne, in ka ga
ya hana to" sai kuma ta yi shiru "Amma dai, kai Ιin wai kana son Raha
ne?"
A kunyace yace "E Amma, da za ku ba Ni ita in sha Allah
zan riΖe ta amana" ya Ζarasa a kunyace "To ma sha Allah, Allah ya zaΙa
muku abun da ya fi Alkhairi, ka ΖoΖarta ka tuntuΙe ta da maganar, idan har tana
so Ba shi ma zai amince musamman da ya san kai waye"
"To Amma na gode"
Ζaki Amma fa shiga can ta fito hannunta riΖe da wani Ζaramin
flask na ruwan zafi, mikawa Muhammad tayi tare da faΙin "ungo"
"A'a, har da wahala haka Amma?"
"Babu komai" itama ta ba shi amsa tana murmushi
Yace "To Allah ya saka da Alkhairi ya bar zumunci"
"Amin Muhammad"
Tsabar yadda yake jin dadi kasa zaman gidan yayi hakan yasa
yayi wa Amma Sallama don ji yake tamkar ma an ba shi Raha, yana fita bai tsaya
ko ina ba sai gidansu wanda a yanzu iya shi da Dada ne suka rage a gidan don
tuni Abdullahi ya Ιauke Inna Maryo suka koma Lagos da zama don shi ma ba laifi
yanzu kam samu yake sosai saboda yana kai kaya daga arewa zuwa Lagos Ιin da
babbar motarsa.
Washegari kuwa Muhammad ya ci karo da Rahanatou taba dawowa
daga islamiyya da yamma, tsayawa tayi ta gaishe shi a kunyace don har yanzu ta
kasa mantawa da abun da ya faΙa mata, yana amsawa ta raba gefensa za ta wuce
cikin zafin nama yace, "Haba Rahanatou, na dai san ke ba yarinya ba ce da
za k ce har yanzu ba ki fahimce Ni ba"
"Na fahimce ka kuma kamar yaya, ka ga Ni kam matsa na
wuce gida kada Amma ta ce na tsaya yawo"
Ζ³ar dariya yayi yace "Shi ke nan, tun da ba za ki tsaya
ma faΙa Miki abun da ke raina ba a nan sai ki je, da daddare lokacin Ba da Amma
na nan sai na faΙa a gabansu."
Saurin saka tafin hannayenta biyu ta yi ta rufe bakinta tana
Zara idanuwanta da ke Ζara gizgarsa gare ta.
"Wuce mana" Muhammad ya faΙa yana nuna mata hanya
Kasa magana ta yi sai jijjiga kanta da take yi tukun can ta
samu bakin yin maganar "To ba ina jinka ba" ta faΙa tana wani
harararsa.
Yace "Ok, to na dai san ke ba yarinya ba de zuwa yanzu
kuma na san kin fahimci manufa ta gare ki, jiya mun yi magana da amma na ce ta
taimaka a aura min ke saboda ina son ki"
Idanuwanta waje tace "So kuma?"
Yace "E, ko ba kya so na?"
Sauron rufe fuskarta ta yi da hijabinta sannan ta raba shi
ta wuce shi kuma ya bi ta da ido yana sakin wani murmushi har ta Ιace wa
kallonsa tukun ya haye Mashin Ιinsa roba-roba ya wuce.
Ko da Amma ta yi wa Ba magana akan batun da Muhammad ya zo
da shi na son Ζ΄arsa abun mamaki bai Ιata lokaci ba ya amince yana nuna farin
cikinsa, daren ranar da Muhammad ya zo musu musu kuwa Ba yayi masa godiya don
gani yake kamar rufa musu asiri yayi tun da dai ba su da kowa a garin daga su
sai su kansu. Haka Muhammad yayi ta jin kunyar Ba da Amma ita kuwa Raha a can Ιaka
murna take don babu laifi duk yadda namiji ya kai to fa shi ma ya kai abu mafi
farin ciki gare ta ma ya yi karatun boko wanda idan yana magana sa'i Sa'i yakan
jefo kalmar turanci a ciki, hakan ne yake burge ta da shi.
Bayan Muhammad ya koma gida ya sanar da Dada cewa shi fa ya
samu matar aure, don yanzu haka ma har iyayen yarinyar sun san da batun soyayar
tasa. Hankalin Dada sosai ya tashi don ita fa har ga Allah ko baya ta amince
masa da batun zai auri zaΙinsa ne saboda ganin abun da ya faru a baya
tsakaninsa da Balkisu, amma yanzu ba za ta yi sake wata macen da ba ta sani ba
tazo ta more shi bayan kuma ita ta sha wahalarsa. Ganin ta yi shiru yasa yace
"Dada ko ba kya farin ciki ne?"
Saurin kau da kai gefe tayi sai kuma ta dawo da kallonta
gare shi tana murmushi tace "Wane Dada ta Ζi farin ciki da farin cikin Ιanta?
Shima dariyar yayi, Ιan gyara zamanta tayi tace "To
yanzu faΙa min wace ce wannan mai Sa'ar da take shirin mallakar Muhammadu a
matsayin miji"
A kunyace yace "Sunanta Rahanatou"
"A garin nan take?"
Yace 'E, amma ainihinsu Ζ΄an Nijar ne"
Idanuwa Dada ta Ζwalalo tace "Kai Muhammadu" tana
riΖe baki
"Amma ka san an ce yan Nijar din nan mugun asiri ne da
su? Allah dai ya sa ba Buzuwa ba ce"
Idamuwansa ya ΖanΖance yace "Dada me yasa kika
tambaya?"
Muryarta ta saisaita sannan tace "Ka san buzayen nan
mallake miji gare su, sai su raba Ιa da iyayensa, idan yana da mata kuma
wallahi sai su raba su"
Shiru yayi na wani lokaci kana yace "Kar ki damu Dada,
babu abun da zai faru da bawa sai abun da Ubangiji ya tsara masa, yarinyar
Buzuwa ce kyakkyawa da ita Dada, kuma ba su da wani mugun hali don kuwa na
tambayi mai gidan da suke gidansa ma ya ce ba su da wani aibu"
"To faΙa maka gaskiya ake ce maka za a yi?" Ta faΙa
a Ιan zabure "Fisabilillah na faΙa maka buzayen nan ba ababen aure ba ne
Muhammadu, ba ka ma san me ya dawo da su nan Ιin ba amma kake kokarin haΙa jini
da su, Ni tsorona ma kada su raba Ni da kai"
Ganin yadda hankalin Dadar ya tashi yasa ya sauΖe muryarsa
Ζasa sannan ya kamo hannunta ya saka cikin nasa, cikin sassanyar murya yace
"Haba Dada, su ma mutane ne, kuma na faΙa Miki na yi bincike akansu kafin
na isa musu da zancen, kuma kin san me?"
Kamar wata Wawuya ta jijjiga kanta "Yarinyar tana da
biyayya, na san za ta so ki itama, za ta kula da ke Dada, yanzu hutu kike
buΖata kin ga, ya kamata a ce kin bari an gwada ta, idan har kika same ta marar
ladabi ko kuma ta zo miki da rashin girmamawa da wulaΖanci to zan rabu da ita,
don a duniyar nan ke ce Uwata kuma ubana"
Tsim Dada ta yi ba wai don ta amince ba tace "Shi ke
nan Allah ya sa Alkhairi Muhammadu. Allah yasa kada ta raba Ni da kai"
Shima cikin sanyin murya yace "Amin Dadana, Allah ya
Ζara miki lafiya da tsawon rai ya ba Ni ikon kyautata Miki da duk abun da na
samu."
Dada tace "Amin Yarona" daga haka ya miΖe ya fice
zuwa nasa Ιakin yana mamakin hali irin na Dada.
BABI NA 16
Abun yau daban na gobe daban, komai yanzu abun magana ne a
wurin Dada, a Ιangaren Imaan kuwa yarinyar sam ba ta da hayaniya, kukanta kuwa
ba kasafai ake ji ba saboda haΖurinta sai dai in yunwa ta addabe ta shi ka daga
zarar ta sha shi ke nan, soyayya kuwa kar ku so ku ga Yadda iyayen ke nuna mata
musamman Abba da ba ya iya Ιoye hakan a gaban kowa don wasu lokutan Dada ji
take kamar ta kai masa duka don yadda yake ririra alkaba'i (Sunan da Dada ta
laΖabawa Imaan kenan), Babakarami ma dai ji yake da sister Ιinsa don kuwa in
dai ba ya school to yakan zauna ya sa ta gaba yana mata wasa, wasu lokutan har Ιaukarta
yake don lokacin ya kai shekaru bakwai da haihuwa, Duk iyakar ΖoΖarin Dada na
ganin ta hurewa BabaΖarami kunne kan ya daina kula yarinyar amma abun ya ci
tura, don bahaushe ya ce, jini ba wasa ba. Hakan ce kuwa ta kasance don kamar
zuga shi Dada ta yi, sai ma ya fara Ιauke Ζafarsa a Ζofarta wanda da can ne
sansaninsa.
Imaan na da watanni takwas kacal Mami ta kura da shigar ciki
a tattare da ita, hamdala kawai ta yi wa Ubangiji sannan ta fara rainon cikin
sai dai tun ba a je komai ba ta fara jigata ita da Imaan wacce ke hannu, kar ku
so ku ga Yadda laulayi ya haΙu wa Mami da shayarwa, tuni ta fara ramewa haka ma
Imaan Ιin. Wannan dalilin yasa suka ga likita, Likitan ya kuma yi insisting ta
yaye Imaan daga Mama kawai sai a haΙa ta da supplementary feeding in ba haka ba
wahalar za ta Ζara Ζaruwa mata.
Da wannan shawara suka dawo bayan an yi musu recommending
supplements Ιin da za su yi wa imaan amfani da su, haka dai ciki ya ci gaba da
girma Imaan kam a nata Ιangaren ba wani kumari sosai sai jinyace-jinyace ma da
take yi, Dada kuwa duk tana lura da su amma ko kaΙan ba ta da matsala don wasu
lokutan har addu'a take Imaan Ιin ma ta mutu, bayan watanni kuma Mami ta sunΙulo
yarinyarta mace fara kyakkyawa dai wacce kamanninsu da Imaan babu wani banbanci
a lokacin tana jaririya, sai dai kuma, ita wannan akwai wani baΖin tabi a
mazaunanta wannan ne kaΙai banbancin da za a iya cewa akwai tsakaninsu.
Dada ta yi matukar farin ciki da ta ji mace aka haifa, take
ta manta da wata Ζiyayya ta shiga aka fara hidima da Mami, ta kuma Ιaukewa
Mamin wasu hidindimu da yawa amma ban da na Imaan, don kayanta wasu al'alarta
duk Dada ba ta da damuwa da su sai dai Mamin ta yi abun ta ko kuma Abba ya
taimaka mata da wasu abubuwan idan yana gidan.
Ranar suna yarinya ta ci sunan Dada kamar yadda Abba ya yi
alΖawari, ai kuwa dai Khadijatul_ihsan kowa ya shaida takwarar Dada ce don kuwa
yadda Dada ta shigo ake hidima da ita uwa uba kudaden da ita kanta ta kashe a
hidimar.
Haka dai rayuwar ta ci gaba da tafiya, a yanzu dai Mami ta Ιan
murmure saboda Ιawainiyar Imaan ne kawai kanta, Ihsan tana wurin Dada kullum,
in an dawo da ita kuma to kukan yunwa tayi duk da cewa ma ita Ιin kam akwai ta
da Shegen kuka. Kusan lokaci guda Imaan da Ihsan suka fara takawa don imaan Ιin
kam babu laifi ta yi nauyin Ζafa, a yanzu ne kuma kamanninsu ke Ζara fitowa
fili sai dai kuma banbance su ba wani abu ba ne mai wahala coz in ka ga marar
suturun, Imaan ce yayin da Ihsan kuma ta kasance fitinanniya ga kuma ta'adin
masifa, taurin kai kuwa kamar arnan farko don da za ka kwana kana mata magana
in ba ta so ba ko kallonka ba zata yi ba bare ka sa ran za ta daina abun da
kake maganar akai. Idan kuma za a hukunta ta Sau Dada ta yi tsalle ta hana,
yadda take shirin tafiyar da rayuwar ihsan Ιin gaba daya ba ya yi wa Mami da
kuma Abba daΙi amma gudun masifar Dada yasa suke shiru.
A duk lokutan d suke wasa kuma idan faΙa ya rincibe haka
Ihsan ke dukan Imaan kamar ita ce Yayar, idan Babakarami ya ramawa Imaan haka
Dada za ta yi ta surfa masa masifa tana yada maganganun da ta saba yi akan
Imaan wacce duk Ζarancin shekaru irin nata ba ta kusantar Dadan don in ta je
dukanta take ta koro ta bayan ta zazzage mata masifar da ba ta san me take nufi
ba ma, daga Ζarshe ma sai ta daina zuwa sashen Dadan, ko wasa za su yi da Ihsan
sai dai su yi a part Ιin Mami.
A ranar da Imaan ta cika shekaru huΙu cur Imaan kuma shekaru
biyu da watanni uku Mami ta shirya tare da yaran nata suka nufi Ζasar Nijar don
kuwa tun haihuwar Babakarami da ta je ba ta Ζara zuwa ba. Sai kuwa da aka yi
daga da Dada ta bari aka tafi da Ihsan bayan lallashin Da Abba ya dinga yi,
haka Abba ya haΙa wa Su Mami tsarabq suka tafi.
Sati huΙu suka yi a can tuΖin suka dawo. Bayan sun dawo ne
Abba ya yi recommending Mami kan a saka Imaan a makaranta yanzu kam, Mami ta yi
na'am da hakan, a cikin satin kuwa aka gama mata cuku-cukun makaranta, uniform Ιinta
da littafa duka an ba ta amma sai sati mai zuwa za ta fara zuwa, mai Mashin Ιin
Babakarami ne kuma zai ke kai su.
Ranar da sati ya zagayo Mami ta shirya Imaan don fara zuwa
makaranta, da mai Mashin ya yi sallama Imaan da BabaΖarami suka tafi Makaranta.
Dawowarsu ya yi daidai da dawowar Dada Da Ihsan daga wani wurin, da Ido Dada ta
bi Imaan don tabbatar da cewa ita din ce, ai kuwa da ta tabbatar an sha masifa
kam, hakan ne ma ya sa Abba na dawowa Dada ta ritsa shi har sai da ya yi
alΖawarin itama Ihsan Ιin za a saka ta a washegari.
Hakan ce kuwa ta kasance, aka yi wa Ihsan ma registration,
aji Ιaya da Imaan, Imaan wacce take matuΖar son Ζ΄ar'uwarta ta yi farin ciki da
hakan, bayan sun fito tara kuwa ta tafi wurin Ihsan Ιin amma Ihsan ta Ζi kula
ta saboda karatun da Dada ta Ιaura mata na kada ta kuskura a san cewa gidansu Ιaya
a makarantar nan, haka dai rayuwar ta ci gaba da tafiya tun Dada na hana Ihsan
kula Imaan Ιin a iya makaranta har ta kai ta hana ta mu'amala da ita a gidan ma
kullum cikin sabuwar huΙuba take wa Ihsan Ιin, har ta kai Wani irin Ζulli ya Ιarsu
a zuciyar Ihsan Ιin game da Ζ΄ar'uwarta, Abba da Mami sun yi iyakar iyawarsu
wajen ganin sun nusar da Ihsan Ιin amma da zarar Dada ta mata sabon Ιori to fa
shi ke nan an rufe wannan magana, zagi kuwa da hantara babu irin wanda Imaan ba
ta gani a wurin Dada, Ζiyayya da aibatawa kuwa tun ba ta san me ne ne su ba har
ta fahimce su, sauΖinta itama Abba da Mami na son ta, da ba don haka ba da ba
za ta iya rayuwar duniyar ba, sai dai kuma sanyi hali da rashin son fitina nata
da ya haΙu da nasihar su Mami yasa zuciyarta kasantuwa cikin salama a kowanne
lokaci.
Wata ranar Juma'a ne al'amarin Ζiyayyar Dada da kuma Ihsan
wacce ita ma ta sha karatu ta Ζoshi ya Ζara ta'azzara, rana mai Ιinbun tarihi
da ta bar wa wannan ahali tabo a zukatansu, a ranar juma'ar su Imaan da Ihsan,
tare da BabaΖarami suka tashi a makaranta, suna zaman jiran mai Mashin Ιinsu
shiru bai zo ba, shi kuma Babakarami ko kaΙan ba ya taΙa missing sallar juma'a
don kullum tare da Abba suke tafiya masallaci, ganin mutane akan hanya na ta
wucewa za su tafi masallaci yasa yaji yana buΖatar tafiya amma mai gadin school
Ιin su ya hana su tafiya, ganin dai lokaci na ta tafiya yasa BabaΖarami kama
hannun Imaan ta dama Ihsan kuma ta hagu sannan suka faki idon Mai gadi suka
fice daga school Ιin, kasancewar school Ιin nasu kan titi take bai hana su
neman layuka su bi ba saboda a tunanin Babakarami za su haΙu da mai Mashin Ιin
a hanya don bai taΙa irin wannan makarar ba.
Sun yi nisa sosai amma shiru kake ji, hakan ya matuΖar yi wa
Babakarami babu daΙi don ya saddaΖar ma ya rasa sallar juma'ar yau, wannan
dalili yasa ya nemi bakin wata bishiya ya zaunar da Ζannen nasa sannan shima ya
zauna don in sun ga wulgawar mai Mashin Ιin nasu sai su tsayar da shi.
Shiru shiru har masallacin juma'ar da ke hanyar makarantar
rasu suka idar da juma'a can kuma mutane suka fara fitowa, tuni hanya ta yi
cunkoso, Ihsan ce ta faki idon Babakarami kawai ta nufi bakin titin da gudu,
Imaan ce ta nuna masa ita ai kuwa daga wurin da yake ya fara Ζwala mata kira
amma ta Ζi juyowa bare kuma ta tsaya. Hakan yasa shi ma ya miΖe ya bi ta da
gudu don ganin ta hau titi kuma akwai ababen hawa, Imaan ma biyo shi tayi don
kada ta je su Ιata su duka biyun su bar ta.
A lokacin da BabaΖarami ya cimmawa Ihsan ya cafko ta ne suka
juyo, unexpected wani Mashin da ya yi aron hannu ya fito taho da matsiyacin
gudu ga shi space Ιin da ke tsakaninsa da Imaan da ke jiran su tsallako ya rage
kaΙan, ifanuwa Babakarami ya zaro tare da sakin hannun Ihsan ya tafi da mugun
gudu don ceto Imaan Ιin unexpected kuma wani Mashin Ιin ya taho, subhanallah,
kafin Babakarami ya kai ga Ζarasawa Mashin Ιin ya buge shi, wani ikon Allah
Mashin Ιin bai tsaya ba kawai ya bi ta kan Babakarami wanda ya cilla wata irin
Ζara yana faΙin "Imaaan"
Wani tartsatsin jini ne ya watsu akan titin sai kuma a
lokacin ne Allah ya ba wannan mai Mashin Ιin damar tsayawa, take mutane suka
fara taruwa sai dai ana ganin yadda kan Babakaramin yayi daga-daga kowa sai ya
dafe kai ya juya, don kuwa dai babu wani taimako da za a ba shi ya rayu tun da
kai ya riga ya tarwatse, Allah sarki mai Mashin Ιin nan kar ku so ku ga Yadda
ya rikice shima ga kuma yadda mutane ke ta masa masifa ya ma rasa abun yi, a
gefe guda kuwa Imaaan ce wacce babur Ιin da ke shirin bige ta ha tsaya ganin
yarinya, tun da ta hango Ιan'uwan nata da ya Ζwala mata kira Mashin ya taka shi
ta wani irin cilla ihu itama ta faΙi a wurin.
Lallai Allah shi ya san gawar fari, shi Babakarami na shirin
taimakawa Ζ΄ar'uwarsa kada a kade ta ashe shi ne za a kade, ga shi har ta yi
silar rayuwarsa, wani mai mota ne yayi Ζarfin halin kiran Ζ΄ansanda, can suma
bayan sun Ιata nasu lokacin tukun suka iso, babu bata lokaci aka saka gawar
BabaΖarami da kuma sumammen jikin Imaan a mota tare da mai Mashin da kuma
Mashin Ιinsa, ana shirin tafiya ihsan da Idanuwanta suka firfito ta kasa magana
sai a lokacin ta samu dama tace "Yaaaayaaaa!"
Hakan ne ya ankarar da Ζ΄ansandan suka tafi da ita asibitin,
tashin farko ma ba a karbi gawar BabaΖarami ba, kawai dai an rufe gurbin kan da
bandage wanda ya jiΖe da jini, ita kuma Imaaan an samu damar ceto numfashinta.
Ihsan wacce ita ma ta kasa daidaita kanta bare ta yi bayani
ko za a nemo iyayensu kai tsaye yasa Aka nemi school Ιin su, babu jimawa kuma
aka samu malami Ιaya ya zo don sun riga sun tashi, da Ihsan ya gane su, ashe ma
Abokin Abba ne da suka yi karatu a Government Comprehensive Day sec school,
take ya kira Abba sai dai bai ce masa ga abun da ya faru ba saboda umarnin Ζ΄an
sandan, kawai ya ce masa ya zo asibiti ne babu lafiya.
Allah sarki Abba da bai san me yake faruwa ba, yana zuwa aka
gabatar masa da Imaaan wacce ta farka daga sumar da ta yi sai kuka take tana
Ζiran "Yaaaaya", daga nan kuma aka gabatar masa da gawar Ιansa gudan
jininsa mai sunan mahaifinsa, tsabar yadda Abba ya kaΙu kasa furta komai ma
yayi, kasancewar Imaan Ιin a lokacin ba ta bukatar wani treatment yasa likita
ya ba da shawarar a tafi da ita in ta ga na gida la'alla ta rage firgicin da
take ciki.
A can gida kuma Mami da Dada sai kiran Abba suke don sanar
da shi abun da ake ciki na rashin dawowar yaran da mai Mashin Ιin su ya sanar
da su, sai dai duk koran da suke yi wa Abba kam ba ta shiga ba su san shi ya
riga ya riski ainihin tashin hankalin ba.
Daga Asibitin kai tsaye su Abba ofishin Ζ΄ansanda suka wuce
aka yi cuku-cuku daga nan aka ba su gawar BabaΖarami. Allah sarki Imaaan da
Ihsan, tabbas suna cikin firgici da kuma matsanancin tashin hankali don
fuskarsu kadai kan bayyanar da hakan. Mami da Dada waΙanda ke harabar part Ιin
Mamin ne suka tare su suna faΙin "Lafiya sai yanzu kuka dawo? Ina kika
je??" Ba su ga komai ba sai da aka shigo da gawar BabaΖarami kowacce ta ja
da baya tana dafe Ζirji, Allah sarki Mami suma ta yi take, Dada ma bayan
fahimtar komai sukewar tayi, maΖota da suka zama kamar dangi su ne suka zauna
tare da su Mamin suna lallashinsu, cikin ΖanΖanin lokaci aka sanar a masallatai
game da rasuwar Ζaramin yaron, washe gari kuma aka yi jana'izarsa aka kai shi
gidansa na gaskiya.
Allah sarki, tabbas wannan ahali sun shiga tashin hankali
Ζwarai da gaske, sai dai babu yadda za su yi haka Allah ya Ζadarta, kwana uku
da rasuwar su Amma da wasu dangin Ba suka zo suka yi wa su Mamin ta'aziyya tare
da Ζara nusar da su cewa ba wai don Allah bai son BabaΖarami ba ne ya Ιauke shi
ba, a'a sai don lokacinsa ya yi, wannan Ζ΄ar nasiha da Amma ta yi wa Mami yasa
ta Ιan saki jiki, shi dai Abba babu laifi don ba za ka ga damuwar akan
fuskarsa, Dada ce dai har yanzu jiya iyau don sai tana zaune ta yi shiru za ka
ji ta rafka salati sai kuma kuka. Imaan kuwa ta Ζara zama so silent, ita kanta
Ihsan a wannan lokacin ta zama so calm kamar ba ita ba.
Tabbas da ba a manta raΙaΙi da Ζuncin da mutum ke tsintar
kansa idan ya rasa nasa da babu wani bawa da zai shiga wuta domin nutsuwa da
kuma tsoron Allah sukan dira a zukatan waΙanda mutuwar ta shafa, sai dai,
mantawar kuma dole ne, ga shi yanzu dai su Imaan sun koma school, Dada ma ta
fara warewa, Mami ta saki jikinta ta rungumi Ζaddara. Ranar da su Imaan suka
koma makaranta ne Ζ΄an'aji suka yi ta musu ta'aziyya bayan zuwa gidansu da aka
yi, bayan an fito break, Imaan na zaune a wurin zamanta wata Ζawarta mai suna
Zainab Abba Muhammad ta zo take sanar da ita abun da Ihsan ta faΙa musu a waje
wai ita ce ta saka Yayansu ya rasu, da ba don ita ba da bai mutu ba.
Jikinta ne yayi sanyi ba tare da ta ce komai ba ta fita
wajen, tana fita ta tarar da Ζ΄an ajinsu sun yi forming group group sai nuna ta
ake da yatsa, a haka aka samu wata maras kunyar ta zo ta tunkari Imaan da batun
wai ita ta kashe yayansu sai masifa take mata, take kuka ya suΙuce mata, haka
ta yi ta yi har Malaminsu ya shigo, da Zainab ta faΙa masa dalilin nan ya zane
Ζ΄an ajin sannan ya ja kunnensu da in ya Ζara jin zancen nan duk sai ya sa an
kulle su a police station, nan suka tsorata suka masa alkawarin ba za su Ζara
ba.
Ko da su Imaan suka koma gida ihsan ta sanar da Dada wai
malam ya duka su akan Imaan, nan Dadar ta yi ta surfa ma Imaan bala'i tun kafin
ta sa a kirawo mata ita.
"To me yasa aka duka ku?"
Nan Ihsan ta yanko zance tiryan -tiryan ta fara karantawa
Dada shi. Salati kawai Dada ta rafka tana tafa hannaye kafin ka ce me ta fashe
da kuka tana faΙin "Ni dama na sani! Na riga na san wannan yarinya annoba
ce ga wannan gida amma an kasa fahimta ta, tun ranar da zancen mutuwar
BabaΖarami ya zo min na san cewa ba mutuwar Allah ta'ala ya yi ba ashe baΖar
ashana ce sila, na shiga uku Ni Dije!"
Face hanci Dada ta tsaya tayi sannab tace "Yi maza ji
kira min ita yau Ιin nan ita ma ta bi yadda ta kai min jika" ta nunawa
Ihsan Ζofa da hannu.
Da yake duk abun da ke faruwa Mani ba tsaye taba sauraron
abun da yake faruwa, guntun hawayen da suka maΖale mata ne suka zubo ta goge
su, jin umarnin Dada yasa Mami juyawa ta koma parlournta, ko da Ihsan ta zo
Mami nasiha ta mata tace ta je ta ce wa Dada Imaan ba ta da lafiya, don ko kaΙan
Mamin ba ta son abun da zai Ιagawa Imaan Ιin da a yanzu itama ta fara jin kamar
she's guilty.
Tun daga wannan Rana da Dada ta tsananta Ζiyayyarta ga
Imaan, fiye da zaton mutum don ko da wasa ba ta taΙa zama inuwa Ιaya da Imaan Ιin
ba tare da ta balbale ta da bala'i ba, Ζarara take nuna wariya tsakanin
Ζ΄an'uwan guda biyu, a ko da yaushe kuma cikin goyon bayan Ihsan take wa lau kan
daidai ko akasin haka, idan ta yi ba daidai ba za a hukunta ta sai ta kasa ta
tsare tace A'a wasu lokutan kuwa har waje Dada kan fita ta tsula ruwan bala'i
ga duk wanda ya taΙa mata shalelenta, Abba yakan yi ΖoΖarin nunawa Dada illar
hakan sai ta saka masa kuka tace yana nuna mata ba ta isa ba ne ko ba ita ta
haife shi ba, wannan dalili yasa yake yin shiru don ba ya so ko kaΙan Dada ta
ji wani abu maras daΙi dalilinsa musamman da ta inganta rayuwarsa.
A hankali Imaan da Ihsan suka fara tashi har suka kammala
makarantar primary school, jituwa tsakaninsu kuwa babu ko kaΙan sai ma tsananin
Ζiyayya da ta gama cika zuciyar Ihsan wacce Dada ta Ιaura ta kan karatun cewa
ita da Imaan ba Ιaya ba ne. Ana wannan hali ne kuma wata Ζaddarar ta Ζara
shigowa rayuwar wannan ahali da ta Ζara rarraba kan Ζ΄an'uwa biyun da aka samu
tazarar alaΖar jini tsakaninsu.
BABI NA 17
Gobara ce ta kama a shagon Abba da wani dare gaba Ιaya komai
da ke shagon babu abun da aka samu, wannan tabbas jarrabawa ne, both Abba da
kuma Mami sun yi tawakkali bisa faruwar hakan kuma sun yi imani cewa jarabta ne
daga Ubangijinsu yayin da suke roΖonsa da ya ba su nasarar lashe ta, Hajiya
Dada a nata Ιangaren sam ta Ζi karbar Ζaddara sai ma tsinewa Imaan da take tana
ikirarin ita ce silar wannan gobara, shi dai Abba ba ta kalaman Dada yake ba
don ba su da wani ma'ana, tunaninsa a yanzu bai wuce yadda zai tsara sabuwar
rayuwa ma kansa da kuma iyalansa ba, domin a yanzu in ka cire gidan da suke
ciki to fa babu wani abu da ya rage wa Abban don kuwa satin da ya gabata ya
sayar da filayensa uku, gida Ιaya ya Ζara fadada shagonsa zuwa wani makeken
sannan ya Ζara zuba kaya, ashe dai ba rabi ba ne.
Ganin ya rasa madafa yasa ya tunkari Mami don su yi shawara
kasancewar yana da yaΖini kan shawarwarin Mami da suke kasance masa Alkhairi
idan har ya yi amfani da su. Mami ba ta Ζi ba amma dai ta ce ya sanar da Dada
ya kuma nemi amincewarta. Da ya tunkari Dada da zancen ba ta Ζi amincewa ba,
hasali ma ta yi na'am da shawarar, alhamdulillah cikin ikon Allah kuwa shawara
Dada ta kawo kyakkyawar maslaha don kuwa dai komai ya fara tafiya daidai har an
yi wa su Imaan registration na secondary school a Hamida Academy da ke garin
Azare.
Rayuwar ta ci gaba da tafiya wa waΙannan ahali yadda ya
kamata, su Imaan da kuma Ihsan an fara zama Ζ΄anmata, tsayinsu Ιaya, Ζibar ma
dai haka ga kuma muguwar kama da ta Ζara bayyana don kuwa da yawa ba sa iya
banbance Imaan da Ihsan by just mate looking sai dai ko da wani move nasu,
banbance banbancen Ιabi'u kuwa sun Ζara bayyana don duk wata Ιabi'a da za ka
samu a wurin Ihsan, to Imaan will be contrary different from her, Ihsan being
an extrovert, Imaan is an introvert, fitinanniyar Ihsan, calm Imaan, da dai
sauransu.
An gama farfaΙowa daga karayar arziΖi da ta same su, Dada
kullum cikin Ζawata Ihsan take, duk wani kayan ado da Ζ΄an'mata ke amfani da su
ta tabbatar Ihsan Ιin ta mallaka , kullum kuma cikin nuna mata irin tazarar da
ke tsakaninta da Imaan take yi, tun a yanzu Dada ke nuna mata cewa ita Ιin ba
kalar talakawa ba ce, matar babban mutum ce, ita Ιin daban take cikin mata,
blabla this and that, a haka suka
kamalla makarantar Ζaramar Sakandire, ma sha Allah, the result Uhm, so
colourful, kowaccensu tana murna da kasancewar hakan, a cikin wannan tsukun
lokacin kuma wata Ζaddarar ta Ζara rafkowa Abba, ya tura maΖudan kuΙaΙe za a
kawo masa kaya daga waje ashe Ζ΄an damfara ne, Allah sarki Abba, wannan karon ya
taΙu sosai fiye da wancan karon sai dai babu yadda zai yi, ya Ιauki hakan karo
na biyu a matsayin kwajin Ζaddara fatansa Allah ya ba shi ikon ci.
Bayan kuΙaΙen hannunsa da suka rage sun Ζare ne ya fara
tunanin abun yi, Dada dai ta ce ba za a sayar da gidan da suke ciki ba sai da
Ζyar ta yadda aka sayar suka nemi wani Ιan madaidaicin gida a Odoji, daga nan
komai ya sauya, rayuwar Imaan ta Ζara
shiga cikin Ζaulani domin a yanzu in Dada za ta zage ta ba da iya baΖin hali,
mutuwar BabaΖarami ko gobarar shagon Abba ba ne kaΙai, wannan Ιamfarar Abban ma
Dada ta Ιamfarawa Imaan shi, tsangwama da kyara kuwa ba a magana don har Ζ΄an
sabuwar unguwar tasu sun fahimci hakan.
Ζiri da muzu haka Dada ta kasar tsare aka mayar da Ihsan
Makaranta ta ci gaba da karatu ita kuma Imaan Dada tace ta yi haΖuri tun da
babu kuΙi sosai a lokacin, ba don ta so ba sai don sanin babu mai ja da wannan
hukunci yasa ta zuba ido tana gani, a hankali kuma Abba ya samu rumfa a kasuwa
ya fara kasa kayan miya kuma babu laifi yana samu don sun fi Ζarfin abun da za
su ci, haka har Ihsan ta shafe kusan watanni biyu d fara zuwa shiru, Mami ce
abun ya dame ta tayi magana shi ne Dada ta ce ta amince a kai Imaan Ιin
makarantar gwamnati ta Ζarasa ita Ιin.
Bayan kayan miya Ιanye ya ja baya ne kasuwar Abba ta ja
baya, lokacin kuma su Ihsan sun gama first term a Ummul Qura Science Academy,
Allah sarki Abba babu abun da ya sa a ransa a lokacin sama da samun kudin da
zai biya wa Ihsan Ιin kudin term da za su biya ya kuma saka Imaan a makarantar
gwamnatin kamar yadda Dada ta ce.
Rashin samun mafita har lokacin komawar Ihsan yasa Abba
shiga tashin hankali, Ζwarzaba iri iri babu wacce Dada ba ta masa ba akan ya
nemo ya biya mata kafin a koro ta, ana cikin wannan damagar wata mata kusan Ζawar Mami ce sosai da suka yi zama a
tsohuwar unguwarsu t kawo musu ziyara.
Sun sha hirarsu da Mami sun Ζoshi, tana shirin tafiya Dada
ta dawo daga maΖota nan ta tare ta suka dawo gida, bayan sun dawo suka gaisa da
Hajiya Saudat wacce tun tana amarya ta je Makka, bayan sun gaisa ne Dada ke
tambayar ta kwana biyu, Hajiya tace "Wallahi yarinya take nema wacce za ta
taimaka mata da ayyukan gida kasancewar ita har yau Ubangiji bai ba ta haihuwa
ba, "Imaan" ita ce wacce ta faΙowa Dada babu wani tunani tace
"to ai ga yarinyar nan Imaan, ba ta aikin
komai sai jawo wa mutane bala'i, da za ki tafi da ita za ta Miki aiki
don kamar jaka haka take ba ta gajiya da aiki."
Tsim haniya tayi kafin tace "Wace Imaan Ιin Dada?"
Washe baki Dada tayi tace "wacce kuwa ban da ta gidan
nan? Ai kawai sai ta Miki aikin ke kuma sai kike biya a wata"
"Lallai Dada" Hajiya ta faΙa a ranta "Anya
kuwa Imaan jininta ce?" Zuviyarta ta yi saurin ba ta amsa da "Ζwarai
kuwa, ga kamanninta da Ζ΄ar'uwarta."
"Then why take nuna wasu irin ΖasΖantattun halaye kan
poor creature?"
Jin tw yi shiru yasa Dada faΙin "Kin yi shiru"
Hajiya tace "To babu komai amma dai a tuntubi iyayen
nata idan sun amince"
Dada ta yi sauri tace "To wata shawara kuma? In ban da
abun ki ai Ni ce mai yanke shawarar gidan kuma babu wanda ya isa ya Ζetare
umarnina" saisaita murya Dada tayi tace "Ai kawai yanzu ki faΙi nawa
za ki ke biya a watan"
Hajiya tace "Ya danganta da yadda naga aikin nata Dada,
zan tafi yanzu, idan kun gama shawarar zan bar lambar wayata a hannun Maman
Imaan idan kun amince Ιin sai ta zo"
Haka Hajiya ta tafi tana jin wani irin don kuwa abun ya Ιaure
mata kai, yarinyar kamar Imaan so cool, a ce wai za a tura ta aikatau? Haka ta
yi ta nanata batun cikin ranta.
Bayan tafiyar Hajiya, Dada ta sanar da Mami da Abba ta kuma
ja kunnensu akan kada wani ya kuskura yace zai ja da maganarta. Haka kuwa kowa
ya gimtse baki, Mamk da kanta ta Ζira Hajiya ta sanar da ita cewa sun amince
Imaan Ιin za ta zo sati mai zuwa, bayan ta gama faΙa ta koma Ιaki ta yi ta
share Ζwalla abun tausayi, da Ζyar ta iya faΙawa Imaan Ιin wacce ko kaΙan ba ta
nuna wani abu kan fuskarta ba game da decision Ιin Dada, haka Abba da Mami suka
mata nasiha kan ta ci gaba ada haΖuri ta Ιauki komai a matsayin Ζaddara, in sha
Allah wata rana za ta ji daΙi.
Dada kam nata nasihar faΙa ne cike da gargaΙi da jan kunne
tare da nanata mata cewa "Duk kuΙin aikin da za a sallame ke da shi ne za
a ci gaba da kulawa da karatun Shalele, ke dai kam ke da karatun boko kadaran
kadahan don ba a san wani irin bala'in za ki haifar wa al'umma ba a zo ana nuna
mu da yatsa cewa daga nan kike ba."
Allah sarki Imaan, she can't help it sai da ta sha kuka, don
a yanzu dai da hankali ya zo mata ta san wace ce Dada gare ta, ta kuma san cewa
ita Ιin ba mai sonta ba ne, amma takan yi ma ta uzurin rashin sanin takamaimai
dalilin Dada na yi mata irin wannan baΖar Ζiyayya ba, ita dai ta Ζudiri aniyar
kyautata mata da duk wata dama da ta samu a rayuwa, haka Ζ΄ar'uwarta ma da ke
nuna mata tsagwaron tsana da Ζyama har take ganin abun kunya ne a ce ita Ιin
jininta ce.
Ranar wata asabat aka kai Imaan gidan Hajiya bisa rakiyar
Dada wacce tun a hanya take surfa mata gargaΙi tana shata mata wasu layuka
kamar a ita ne za ta yi wa aikin, abun takaici haka ta yi t ΖoΖarin baΖanta ta
a gaban Hajiyar, ba don Hajiya ta san wace ce Imaan ba to tabbas za ta Ζi Ιaukarta
aiki ne ma. Bayan tafiyar Dada Hajiya ta nunawa Imaan nasauΖinta ta kuma ce
mata ta saki ranta ta ji kamar gaban Mami take, ko da wasa kada ta yi shiru
idan ta ji kewar Mamin ko yaushe tana daidai da Kaita su haΙu, hakan ya yi wa
Imaan daΙi, daga nan Kuwa ta fara taimakawa Hajiya da aiki, sosai Hajiya ke jin
daΙin aikin nata uwa uba kuma yadda take girmama manya, wannan dalilin yasa
Hajiyar Ζaguwa da son jin dalilin Dada na ΖoΖarin baΖanta ta a idon mutane.
Kwanci tashi asarar mai rai Imaan ta yi aikin wata guda, Hajiya ta haΙa ta da
sha tara ta arziΖi sannan ta ba ta albashinta cas a hannunta tace ta je gida ta
yi kwana uku sai ta dawo.
Kar ku so ku ga irin farin cikin da Imaan ta tsinci kanta
saboda za ta je ta ga Mami, Abba kai har ma da waΙanda ke nuna mata ita Ιin ba
tasu ba ce. Bayan ta je Gida Mami sai nan da nan take da ita, Dada na jin labarin isowar Imaan Ιin ta yi
saurin dawowa daga maΖota ta zo tana tambayar kudin aiki, cike da takaicin hali
irin na Dada Mami ta miΖa mata su kamar yadda Imaan Ιin ta zo da su, idon Dada
na kai wa ga kayan da Imaan ta zo da su haka ta kwashe tace ai nata ne tun da
ita ce silar tafiyar Imaan Ιin aikin, don haka kuwa komai ta zo da shi dole a
ba ta. Bayan ta karΙa kuwa babu kunya ta baza bujenta ta wuce da kayan Ιakinta.
Bayan kwana uku da Imaan ta yi ta shirya komawa, Ζ΄an
kayayyakin da ta zo da su wanda Hajiya ce ta Ιinka mata ihsan ta gani tace tana
so, Dada da kanta ta zo ta karΙawa Ihsan Ιin duka kala ukun sannan ta ba ta
wasu mataccun kayan Ihsan wai ta saka ta cire na jikinta, ba yadada ta iya ta
cire ta miΖawa Dadan ta karba ita kuma ta wuce.
Da yawa za su yi mamakin hali irin na rashin girma na Dada,
haka take, haka Ιabi'unta suke, yadda take nunawa Imaan miyagun Ιabi'u ka yi
tunanin Imaan Ιin Ζ΄ar tsintuwa ce ko kuma Ζ΄ar abokan gaba ba wai jikarta ba, Ιiyar
yaron da ta nunawa so ta kuma inganta rayuwarsa.
Bayan komawar Imaan gidan Hajiya haka ta ci gaba da aiki,
wata rana suna zaune a parlour, Hajiya, Alhaji Usman mijinta da kuma Imaan suna
kallo, da yake tashar da suke kallo an sako wani quiz competition da pz cusson
suke yi duk shekara, idan aka yi failing question imasn sai ta yi caraf ta fadi
amsa wacce idan alΖalan quiz Ιin suka faΙa sai a ji ta daidai. Wannan dalilin
yasa Alhaji Usman ganin kyautatuwar inganta rayuwar yarinyar don a nasa tunanin
rashi ne ya sa yarinyar ba ta samu karatu ba. Da wannan shawara da suka yanke
shi da mai Ιakinsa suka tuntuΙi mahaifin Imaan Ιin kai tsaye, ai kuwa Abba har
da kukan farin ciki, nan ya amince ya kuma roΖi Alfarmar kada ko mahaifiyarta a
sanar. Daga nan Alhaji Usman ya yi wa Ihsan registration a makarantar private
wacce Ihsan ma ke zuwa, hatta uniform da sauran stationaries duka kafin ta fara
zuwa aka ba ta, godiya kuwa kwando kwando haka imaan ta yi ta zubawa su Hajiya,
su ma sun yi farin cikin da sanya ta farin cikin.
A ranar da Imaan ta fara zuwa mutane sai tambayarta suke ita
sistern Khadija Muhammad Nadada ne? In ta tuna wace ce Ihsan da irin Ζyamarta
gare ta sai ta shafawa kanta lafiya tace A'a, ba ta san ta ba ma, mamaki sosai
yakan bayyana a fuskar mutane ciki kuwa har da malamansu sai dai idan suka ji
cewa ba ma unguwa Ιaya suke ba sai su ce ikon Allah ne wata Ζila, sai dai fa
sun kasa yarda da cewa babu wata alaΖa tsakanin Imaan Ιin da ihsan kasancewar
kamanninsu da har su wasu lokutan sukan
kasa banbance Ιaya daga Ιaya.
Hajiya ihsan wacce a yanzu za mu ce rayuwarta ta gama ginuwa
kan kishi da Ζ΄ar'uwarta kuma gudan jininta Imaan, a ranar da ta fara ganinta a
school haka ta dawo gida tana tayar da rigimar sai an sauya mata school ko kuma
dai a cire Imaan daga school Ιin su, Dada da ta ji bayanin Imaan har gidan
Hajiya taje ta yi wa Kmasn gargaΙin kada ta kuskura ta nuna ta san Ihsan bare
bakinta ya suΙuta tace Ihsan Ζ΄ar gidansu ce, ba tare da sanin Dada ba ashe
Hajiya na jin ta, sai dai har ta gama ba ta ce uffan ba bare ta nuna ta ji har
ta yi tambaya, sai da Dada ta tafi Hajiya ta saka Imaan Ιin da tambayar dalili,
sai dai rashin sanin takamaimai dalilin Dada na nuna mata wannan Ζiyayya yasa
ta ce ita ma ba ta sani ba, abun da Hajiya ta so ta sami tun farkon zamansu da
amintakarsu da Mami amma Mamin ba ta faΙa mata. Wannan yasa ta kira Mami ranar
ta ce in har ba ta faΙa mata dalili ba to fa ta san matsayinta, nan Mami ta feΙewa
HaJiya biri har wutaiya tana share Ζwalla, ita kanta Hajiya wannan abu ya taΙa
ta, amma babu yadda za ta yi, nan dai ta ci alΖawarin riΖe Imaan Ιin kamar
Ζ΄arta, ta kuma yi alkawarin riΖe Sirrin da Mani ta ba ta.
Tun daga nan rayuwar Imaan ta sauya a cikin gidan Hajiya,
yadda Hajiya ke janta a jiki yasa ta sake sosai da ita, cikin ΖanΖanin lokaci
sabo ya shiga tsakaninsu kai ka ce Hajiya ita ce mahaifiyar Imaan Ιin. A haka
aka zo Ζarshen zango na biyu, wato second term, aka yi jarrabawa abun mamaki
Imaan ita ce ta lashe kambun na Ιaya a ajin, ba abun mamaki ba ne duba da yadda
Ιalibar take maida hankali ta kuma ke da nutsuwa da tarbiyya, don ko faΙa ake
wa students Ιin ajin in sun yi ba daidai ba akan ce da su su yi koyi da Imaan
wanda hakan ba Ζaramin baΖamtawa Ihsan yake ba.
Bayan an faΙi sakamako kar ku so ku ga Yadda Ihsan ke nuna
tsantsar baΖin ciki da hassadarta a fili har sai da wasu daga cikin Ζ΄an'ajin
suka fara nuna mata rashin kyautawar hakan, da fushinta dai ta koma gida, da
Ζyar Dada ta lallashe ta kan ta yi haΖuri babu yadda za su yi, don in ta ce a
wannan karon a cire Imaan a makarantar ma ba ta da iko tun da ba wanda take
gadara da shi Ιin ba ne ya saka ta ba.
A Ιangaren Imaan sosai Hajiya da Alhaji suka yi farin ciki
da sakamakonta har dai suka mata kyauta, bayan an koma makaranta haka zango na
uku ma ya kasance, Imaan ta lashe kambun na Ιaya a karo na biyu, sosai wannan
karon ka ihsan ta nuna hassadarta sai dai Hausawa sun ce, hassada ga mai rabo
taki ne. Ai kuwa hakan ne, don ba ta ga komai ba, ranar bikin yaye Ιalibai,
wato speech and prize giving day imaan ta karΙi kyauttuttuka da yawa tun daga
na first position overall na set Ιinsu, 1st position a Bclass (wato ajin mata),
best in subjects da yawa, overall best student of the year! Award guda aka ba
ta bayan kyaututtukan kuΙaΙe da ta samu, daga nan aka watse, tun da Ihsan ta
koma ko abinci ba ta ci ba sai da Dada ta mata alΖawarin karΙo duka
kyauttuttukan Imaan da kuΙaΙen da ta samu wanda tuni Alhaji Usman ya turawa
Abba ta akawun Ιinsa. Haka Dai Dada ta tattara kyaututtukan ta wuce da su ita
dai Hajiya ba ta ce mata komai ba ta bi ta da kallon mamaki.
A haka rayuwar ta ci gaba da tafiya, munanan Ιabi'un Ihsan
kullum Ζara ta'azzara suke, ta yanke duk wata alaΖa da Ζ΄aΖ΄an talakawa a ajin
nasu, sun haΙa clique Ιinsu na Ζ΄aΖ΄an masu da shi, suna Zuba wulaΖanci wa Ζ΄an
aji yayin da a Ιaya Ιangaren Imaan ta Ζara mayar da hankalinta ga karatunta don
gani take shi ne kaΙai a yanzu gatarta. A haka har suka kammala karatun, aka
yaye su bayan Ιinbun kyaututtukan da Imaan ta Ζara samu, har zuwa lokacin kuma
a ajinsu babu wani wanda zai ce ya tabbatar da alaΖar da ke tsakanin Imasn da
ihsan though surname Ιin su Ιaya, kamanninsu Ιaya, kasantuwar su a duniyoyi
mabanbanta da kuma Ιabi'u mabanbanta yasa kowa yake ganin babu wata alaΖar a
tsakaninsu.
Tun daga wannan lokaci ne kuma Dada ta far tunanin ta yaya
Ihsan za ta ci gaba da karatu don a yanzu kam, samun Abba ya samu tangarΙa
hatta abinci wasu lokutan ba a yi a gidan. Ko da ta yi wa Abba magana bai ce
mata uffan ba don ba shi da abun faΙin, duk da haka dai Dada sai da ta jajirce
aka samarwa Ihsan admission a FUHSA duk kuwa da tsadar da jami'ar ke da shi a
hakan mai wai ta gwamnatin Ζasa ne bayan bin sawu da ta yi ta yi a gidan
Honourable Muhammad Baba wanda ya kasance Ιan takarar Ιan majalisa.
Bayan Dada ta samu cikakken bayanin kudin registration Ιin
ne ta fito da kuΙaΙen aikin Imaan wanda take Ιoyewa saboda ba ko wanne wata ne
ake biya ba sai term, alhamdulillah cikin ikon Allah kuwa kuΙaΙen sun kai yadda
ake buΖata hakan yasa Dada damΖa su
hannun Ihsan ta yi registration, daga nan ta fito da tsurfin sai an yi mata
sabbin Ιinkuna. Ba komai take hanga ba sai kayan da Imaan ke zuwa da su, babu
shiri Dada ta sa Mani kiran Hajiya wai Imaan ta Ιan zo ta huta ko na sato ne,
ai kuwa sun ci galaba don kayan da ta zo da su wannan karon ma Dada duk ta karΙe
su ta ba wa Ihsan, yadda Imaan ta kile har ta so ta fi Ihsan kyan gani musamman
fatarta da tayi luwai yasa Ihsan jin kishin hakan har ta fara jin ina ma a ce
ita ce a stand Ιin Imaan, wata shawara ta yanke lokaci guda ta fito da darun
sai Imaan ta dawo gida. Dada kuma ta hau ta zauna a kai ba tare da tunanin
makomar karatun Ihsan da ta fara ba don babu mai Ιaukar nauyinta kuma kuΙaΙen
da yawa ba.
BABI NA 18
Allah sarki Hajiya, a lokacin da zancen barin aikin Imaan ya
zo mata ta shiga damuwa Ζwarai don ba Ζaramin sabo ne tsakaninsu ba, iron sabon
nan ne da ake kira da *HaΙin Allah*
Daga Hajiya har Imaan sun ji babu daΙi game da wannan
hukunci na Dada, sai dai babu yadda za su yi, haka aka tattara Imaan aka mayar
da ita gida, Hajiya kuka Imaan kuka duk da cewa Hajiyar ta roΖi Imaan Ιin da ta
riΖa ziyartarta lokaci bayan lokaci ta kuma sanar da ita cewa duk wani abun da
take buΖata kar ta ji komai ta faΙa mata, har lokacin matsayinta Imaan Ιin nan
ce da suka yi rayuwar aminci da ita,
goma sha tara ta arziΖi da Hajiya da mijinta suka mata
kuwa ba ta tsira da komai ba, don komai Dada ta damΖa shi ne hannun
Ihsan,
Sati guda da dawowar Imaan halayen Ihsan da Dada suka
gundure ta, kewar Hajiya duk ta bi ta cika ta, hakan yasa ta tambayi Abba don
ta kai wa Hajiyar ziyara, bayan ta je suka yini suna hira, da za ta dawo Hajiya
ta ba ta kuΙaΙe da atamfofi, ta kuma yi mata albishir da cewa za ta samar mata
aiki a SOHAAN SNACKS AND BEVERAGES tun da ta Ζware sosai a iya snacks, Imaan
har da kukanta na farin ciki ta yi ta zabgawa Hajiya godiya ta kuma ce ta yi
wata Alhaji ma godiya don aikin ta hannunsa ne ma, Ιan yayansa shi ne CEO na
Companyn.
Bayan ta koma gida da kwana biyu aka kira wayar Mami aka
sanar da ita samun aikin Imaan Ιin sannan kuma aka ce sati mai zuwa za ta fara
aikin. Murna sosai Jmaan ta yi, Abba haka ma Mani duk ba a bar su baya ba, Dada
kanta ta ji daΙi don kuwa ta samu hanyar da za ta ke tarawa shalelenta kuΙin
registration da kuma kayayyakin da Ζ΄anmata Ζ΄an jami'a kuma masu Ζwalisa ke
amfani da su. Haka Imaan ta fara aiki, cikin ikon Allah kuma ta samu Ιaukaka a
companyn don in dai ta Ιangaren snacks ne hannunta ya yi nisan faΙawa, wannan
dalili yasa da yawa daga cikin ma'aikatan wurin ke jin haushinta musamman da ta
zo a sama kuma ake wani ji da ita, ciki har da ogar sashen da take aiki, wato
Madam Talatu, sai dai fa ita ko kaΙan ba sa gabanta, hasali ma aikinta da take
tunanin za ta tallafi iyayenta da ke halin buΖata ta fi ba wa muhimmanci.
Ana cikin haka aka yi musu albashi, kaso mai tsoka Imaan ke Ιauka
bisa umarnin CEO wanda shi ma order ne daga Uncle Usman Ιinsa. Imaan na komawa
gidan haka Dada ta miΖo yaΖusasaun yatsunta ta karΙe kuΙin nan ko dubu Ιaya ba
ta iya zara ta ba wa Imaan ba bare kuma iyayenta, haka ta juya da kuΙin tanq faΙin
tanadin karatun shalelenta ne, a fuska dai ce an ga wani reaction tattare da
Imaan, ko kaΙan, hatta haΖurin da Mami ke ba ta tana jin ta ne don ba ta ga
abun ban haΖuri ba, a nata tunanin Dada ta isa da hakan ne. Tun daga wannan
lokaci kuma duk ranar da aka yi salary haka Imaan za ta damΖa kudin hannun Dada
don kashexi ta mata kan cewa in ta taΙa kuΙin za ta mata ba dadi, iyakar
amfaninta kenan tun da mahaifiyarta ta zaΙa mata rayuwar baΖin jini, bautawa
rayuwar Dada da kuma Ihsan shi ne abun da aka haifo ta tayi, ita da jin daΙi
kuma ba dai a duniyar nan ba, don sun Ζudiri aniyar toshe duk wata kafa da za
ta sada ta da farin ciki ko jin daΙi a rayuwa.
Imam dai ita ke sponsoring karatun Ζ΄ar'uwarta, yayin da ita
kuma take aiki tuΖuru ba tare da ta amfana da guminta ba, A takaice dai,
rayuwar Imaan abar tausayi ce ba wai don ta rasa iyaye ko soyayyarsu ba,
jarrabawar kaka da da Ζ΄ar"uwa shi ne nata raunin, amma ta yi alΖawarin karΙar
hakan matsayin Ζaddarar da Ubangiji ya rubuta a nata shafin rayuwar, amma tana
fatan wata rana, ko da sau Ιaya ne Dada da Ihsan Ιin su rage zafin Ζiyayyarsu
gare ta, tana fatan wata rana ta samu soyayya daga gare su ba kuma ta ganin
laifin Dada a yanzu don ta san maΖasudin Ζiyayyar Tata gare ta, amma zurfafawa
da kuma rashin mantuwa da yafiya irin na Dada yana ba ta mamaki ba kaΙan ba.
Ζarin abun da ke Ιaure mata kai shi ne, yadda Dada ko yaushe ke toshe duk wata
kafa da za ta kai ta ga ci, ita dai Ihsan ko da yaushe, babu ruwanta da kowa
sai Ihsan Ιin, ba kuma ta buΖatar duk wani abu da zai taΙa Ihsan Ιin, don ko
Abba ne ko Mami suka mata faΙa haka itama za ta musu, wanda sosai abban ke jin
rashin daΙin hakan, haka ma Mami ita ma ba ta jin daΙin hakan, don kuwa rashin
mafaΙi bala'i ne ga rayuwa, ba iya rayuwar mace ba hatta rayuwar namiji, a duk
lokacin da Abba ko Mami suka yi wa Ihsan fada sai take kumbura baki, babu damar
bugu tun da Dada ta hana, sai dai Mami kan ce mata "Ungulu ma da ta rasa
mafaΙi kashi take ci!"
Hakan kuma bai taΙa sawa ta fahimci rayuwa ba, addu'a dai
kam kullum cikin yi nata ake yi.
Rayuwar Imasn da ihsan tamkar gabas take da kuma yamma,
Imaan sanyin hali, Ihsan zafin rai, Imaan ba ta Ιauki rayuwa wani abu ba, Ihsan
son duniya da kuma rayuwar Ζarya, Imaan, ma'abociyar addini, ihsan, ma'abociyar
rayuwar nasara kama daga mu'amala zuwa tufafi, sai dai fa duk iya shegenta ya
tsaya ne ga ire-iren abubuwan nan, ba ta bin maza ba kuma ta shirka, da haka
muke mata fatan shiriya ta kuma yi koyi da Ζ΄ar'uwarta.
DAWOWA CIKIN LABARI
A can gidan Hajiya Imaan ta baro CEO Sulaiman bayan ta yi
hamdalar rashin ganinta da yayi, a nashi Ιangaren Ζwarai ya gan ta, ya kau da
kansa gefe ne kawai saboda wani dalili nasa, bayan sun gaisa da Hajiya wacce
yake kira da Aunty Saudat kasancewarta matar Ζanin mahaifinsa. Bayan sun gama
gaishe gaushen ne Yayi gyaran murya yace, "Auntyna ta kaina magana ce fa
yau ta kawo Ni"
Ζ³ar dariya Hajiya tayi tace "Tooo" tare da jan to Ιin
"Yau dai Auntynka na sauraronka, Allah ya sa dai ba wata matsalar ba ne
tsakaninka da Nauwara?"
Sosa kansa yayi yana jijjigawa "Noo Aunty, another
different issue"
Tsam Hajiya ta yi ta ba shi total attention Ιinta sannan
tace "Toh son, I'm all ears"
Gyara zamansa yayi akan kujerar sannan ya wani narke fuska
alamar roΖo kafin yace "Don Allah Auntyna ki taimaka ki fitar da Ni
duhu"
"To ina jin ka Yarona"
Gyara murya yayi yace "It's about the issue of that
girl, wacce Uncle ya samar mata aiki a SOHAAN"
Yi tayi kamar ba ta gane waye ba tace "Ai suna da yawa
waΙanda suka samu aiki ta hannunsa"
Kallon Hajiya yayi na wani lokaci kafin yace "Ina nufin
wannan snacks expert Ιinnan."
"Ka ga Sulaiman, go straight to the point"
Yace "Na san kin gane ta Auntyna, ina nufin Fatima
something Nadada Ιin nan"
Murmusawa Hajiya tayi tace "Uhm, sai ka ce min Imaan,
ai kuwa yanzu ta fice ina tunanin ma kun haΙu kafin ta fita ai?"
Jijjiga kai yayi yace "A'a, ban ganta ba" sai kuma
yayi shiru "Ba wannan ba Auntyna, don Allah who's that girl?"
Dim gaban Hajiya ya buga don ta ce ba za ta taΙa fitar da
Sirrin rayuwar Imaan ba.
A Ιan shagwaΙe wannan lokaci CEO Sulaiman yace "Haba
mana Auntyna, kin yi shiru"
Dariya Hajiya tayi ta cilla masa pillow kafin tace "Kai
dai Sulaiman Allah ya shirya ka, ga ka da yaro amma har yanzu ba ka girma
ba"
"Ta yaya ma zan girma? Ni babu ruwana da Fauzan, yanzu
gaban uwata nake"
Hararar wasa ta masa kana tace "Allah dai ya shirya
ka" ya amsa mata da "Amin" sannan yace "Auntyna kin yi
shiru"
Ba tare da ta yi tsammani ba yaji Ta ce "Aurenta za ka
yi?"
Da sauri yace "Aure kuma Auntyna?"
Sai lokacin Hajiya ta tuna mai tace, waskewa tayi tace
"Ai yadda takanas ka zo din nan na yi tunanin ko hakan ne?"
Ya jijjiga kansa ya e "A'a Auntyna rufa min asiri kar
ki sa Ummu Fauzan taji yau ta sake Ni"
Dariya suka yi su biyun kafin Hajiya tace "Allah ya
shirya ka" ya amsa mata da "Amin"
Sai kuma yace "Auntyna na ji kin yi shiru, please who's
that girl? Who's she?"
"Wani abu ya faru ne?" Ta mayar masa amsa da
tambaya
Yace "A'a, just na ga kamar akwai wata matsala da ke
bibiyar yarinyar ne"
"Matsala?"
Ya gyaΙa kai "Of course matsala, offer company ya ba ta
ta je tayi karatu amma ta Ζi accepting "
Numfashi Hajiya ta sauke ta ce "Allah sarki Imaan, na
san ba za ta taΙa accepting ba."
"But why?"
"Saboda..." Saurin rufe bakinta tayi tana mai
amfani da tafukan hannunta biyu.
Nutsuwa Ya Ζara yi kana ya saka idamuwansa cikin na Hajiyar
yace "Saboda me Aunty?"
Ta amsa masa da "babu komai"
"Haba Aunty, don Allah ki faΙa min, haka kawai yarinyar
ta ba Ni tausayi, it's great achievement a ce ta samu wannan damar, amma faduwa
ce a ce ta yi loosing Ιin ta, ki duba fa! Wallahi there's something fishy going
through her, yarinyar looks so clam and gentle, Anya ba daga gidansu ba ne
matsalar?"
Shiru Hajiya ta yi, CEO Sulaiman yace "Kin yi shiru!
Hakan na nufin hasashena gaskiya ne ke nan?"
"Hmm, Auntyna ke nan, shi ke nan! Zan tambayi Uncle ya
faΙa min address Ιin gidansu, I'm willing to help that girl ta yi amfani da
damarta, ina jin tausayinta Ζwarai"
Sai da ya kai aya tukun Hajiya ta samu damar sauΖe ajiyar
zuciya kana tace "Ban Ζi ta taka ba Sulaiman, amma ina ga kar ka shiga
al'amarin iyali, kawai ka bar komai a haka.."
Katse Hajiya yayi da faΙin "Haba Aunty, just support me
na yi aikin Alkhairi, rayuwar yarinyar za ta inganta nan gaba, don Allah!"
Wani numfashin Hajiya ta sauΖe kana tace "Sulaiman ba
za ka iya ba"
Yace "Amma me yasa?"
Hajiya tace "Saboda na faΙa maka abun na gida ne, idan
har ba aurenta ka yi ba Sulaiman, babu yadda za a yi ka iya taimakawa rayuwarta
"
A Ιan zabure yace "Aure kuma Auntyna?"
Hajiya t jinjina kai kana tace "Ζwarai kuwa!"
"No! Ba zan iya ba Auntyna, yanzu ma yaya nake fama da
Nusaiba bare na Ζara wata?"
In her convincing tone tace "Shi ke nan Sulaiman, to ka
kawai ka haΖura da taimaka matan da za ka yi"
Ya ji daΙin hakan amma sai ya tsinci kansa da tambayar
"Why?"
"Saboda abun da na faΙa maka tun farko"
"But I'm willing to help aunty "
"Ai kuwa babu yadda za ayi ka iya hakan Sulaiman in har
ba abun da na faΙa maka ka yi ba, wato aurenta"
"Amma me yasa kika ce haka, please aunty, ki faΙa min
wace ce yarinyar nan? Who's she? Me ne matsalarta da kika ce sai na aure ta ne
zan iya taimaka mata?"
Ajiyar zuciya Hajiya ta sauΖe kana ta fara bashi labarin
Imaan tun daga maΖwabtaka da suka yi da Mami zuwa alaΖar da ta Ζullu tsakaninsu
kamar Ζ΄an'uwa, haka ta yi briefing nasa wace ce Imaan and her obstacles"
Jikinsa ne gaba Ιaya ya yi sanyi jin wace ce Imaan Ιin,
shiru daga shi har Hajiya suka yi da ta gama ba shi labarin
"To ya kake gani Sulaiman? Har yanxu kana da Ζudurin
taimakawa Imaan ne ko kuwa?"
Jinjina kansa yayi yace "In sha Allah zan taimakawa
wannan yarinya, zan kuma inganta rayuwarta kamar yadda ke ma kike da burin
hakan, zan aure ta Ιin"
Murmushi Hajiya tayi
har sai da haΖwarenta suka fito kana tace "Ma sha Allah
alhamdulillah"
"Gaskiya yau ina cikin wani irin farin ciki da ba zan
iya misalta shi ba, Sulaiman na gode Ζwarai na gode! Ubangiji ya saka maka da
mafificin Alkhairi ya kuma ba ka ikon idar da kyakkyawar niyyarka"
Da "Amiin ya amsa jikinsa sanyaye"
Kusantowar Magrib yasa ya yi wa Hajiya sallama ya wuce bayan
ya sanar da ita zai Ζira ta a waya in ya koma sai su yi magana yadda komai zai
tafi bisa tsari daga nan ya wuce abunsa.
BAUCHI, BAUCHI STATE
Ummie ce zaune akan dardumar sallah tana lazimi, shigowar
Ummah da sallama a bakinta yasa Ummien amsa mata. Zama Ummah tayi ta dubi Ummie
kana tace "Kin idar ne?"
Ummie tace "E, wani abun ya faru ne?"
"A'a" Ummah ta ba ta amsa
"Batun dai Jalaal ne"
"Tooo, Allah ya sa lafiya"
"Lafiya Ζalau fa" sai kuma ta yi shiru.
"Dama ina ta son shigowa, kin san akwai baΖuwa a wurina
ne shi yasa"
Ummie tace "Ayya"
Fakar idon Ummie Ummah tayi ta banka mata wani irin kallo
kana tace "Yarinyar Yaya Zinatu ce, Karimah, kwananta biyu a nan, dama
dama"
Sai ta Ζara yin shiru "Ina yi wa Jalaal sha'awar
aurenta ChubaΙo"
Muskutawa Ummie tayi tare da sakin fuska tace "Ma sha
Allah, ai ya kamata ya yi auren kam, ba dai kin yaba da yarinyar ba?"
Ummah tace "Ζwarai kuwa"
"To Ubangiji ya sa albarka, bari na dubo abinci, na
zuba shinkafa kafin na shiga sallah kada ta Ζone"
"To shi ke nan, sai an jima, zan wuce Ni ma"
Ummie ce ta fara yin hanyar kitchen, sai da ta kusa shigewa
Ummah ta dube ta ta wani watsa mata kallo mai wuyar fassara kana ta ja Siririn
tsaki "Dole ne ma ya aure ta, ina nan ina jiran dawowarsa, domin cikar
burina ya wuce komai, ba dai ubansa ya goya masa baya ba? Hmm"
MiΖewa tayi ta fice tana Ζ΄an surutanta har ta koma nata
sashen.
*Bloordale village*
A can bloordale village kuwa sosai abubuwa suka cakuΙewa AK
don kuwa ya riga ya fahimci matsalarsa, wasu lokutan yakan ji ina ma Ubangiji
ya cika masa burin ko da ganin dream girl Ιin nasa ne yayin da wani lokacin
kuma yakan ji zafinta cikin ransa na kasancewarta sanadin shigarsa damuwa, and
at times ji yake kamar ya koma Nigeria just because of her, sai dai in ya tuna
babu ta yadda zai gan ta sai ya ja tsaki. Ba tare da ya san wainar da Ummah ke
toyawa kansa ba haka yake jin ko yaushe kamar ana Ζara masa tsantsar Ζaunarta
ne a kowanne wucewar sakan zuwa daΖiΖa i zuwa Sa'a...
Haka dai rayuwar ta ci gaba da tafiya a kowanne Ιangare
cikin yanayi na daΙi da kuma akasinsa, abubuwa da yawa sun faru, ciki har da
rabuwar Ihsan da kuma Barr. Junaid bisa saΙanin da suka samu shi da Ihsan bayan
Ζorafin da ya mata kan rashin Ζin amincewarta ya tura magabatansa, a maimakon
ta lallaΙa shi sai kawai ta hau shi da masifa, daidai wannan lokacin ne kuma ya
Ζara fahimtar da wa yake tare, haka Ihsan ta ci gaba da gasa masa maganganu
marasa daΙi ba tare da ta duba tazarar da ke tsakaninsu ba, ya yi matuΖar da na
sanin sanin Ihsan, har ya ji a ransa cewa soyayya da ita da yayi shi ne babban
kuskure da ya tafka a Rayuwarsa, amma ya rungumi hakan matsayin wani sashe na
Ζaddararsa, ba su rabu ba a ranar da abun ya kasance sai dai ya yi wa Ihsan Ιin
nasiha tare da nuna mata cewa ya kamata ta gyara halayenta ba don komai ba sai
don saboda gaba, idan har haka ne Ιabi'unta Ζwarai ya kamata ta sauya su, don
in ta yi wa wasu sun bar ta da duniya, wasu samarin ba Allah a zukatansu, idan
har ta aikata musu kwatankwacin abun da ta yi masa to ba za su bar ta haka ba
sai sun bi duk wata hanya da ta dace sun hukunta ta, wasu kuwa ko za su Ιata
kan hanyar Allah sai sun Ιau fansar abun da ta musu.
Amma haka Ihsan ta barbaΙe shi da mugayen kalamanta tana faΙin
"Ka yi ka gama duk maganganun da ka faΙa kaina kuma to haka za su faru da
Ζanwarka, har kana faΙin na yaudare ka? Ni nace ina son ka tun farko? Ko Ni
nace ka so Ni ka yi min hidima da kudinka? Ni bari ka ji wallahi in na raina
kasuwa, ko sautu ba na aikawa, kuma Ni ba na maimaita aji bari ka ji , kada ka
yi tunanin ko zuwa gaba Ni Khadihatul Ihsan zan dube ka, Ni da ka gan Ni ba na
bari kaina yayi rumfa, na san don na rabu da kai ba komai ba ne tun da dama can
ba sonka nake ba, ina tabbatar maka zan samu wanda ya fi ka komai a rayuwar
nan, kyau, kuΙi, nasaba da kuma wayewa, kuma wallahi babu abun da zai same Ni
sai Alkhairi, na bar ka lafiya Barr. Allah ya haΙa kowa da rabonsa."
Tana gama faΙin haka ta wuce ta bar shi a wurin yana bin ta
da kallon mamaki.
Lallai a ranar ya tabbatar da halin mata, a baya an taΙa
masa hakan amma ya yi zaton ko zai samu wacce za ta so shi don Allah, ashe dai
duka halin matan Ιaya, da wannan baΖin ciki da Ihsan ta Ζunsa masa ya ja
motarsa ya bar unguwar yana da na sani maras iyaka na sanin Ihsan. Haka dai
yayi ta fama don ganin ya cire ta a ransa yana addu'ar Allah ya saka masa abun
da ta yi masa a rayuwa don sai da suka rabu ya Ζara tabbatar da cewa ta cutar
da zuciyarsa, kai rayuwar tasa ma gaba Ιaya ta cutar da ita.
BABI NA 19
Bayan kwana biyu da maganar CEO da Hajiya ne suka yanke
shawarar gabatar da al'amarin ta sama, sun kuma Ζudiri aniyar komai ya kasance
cikin ΖanΖanin lokaci kafin su Dada su farga, Hajiya ba ta ba wa CEO damar
sanar da Imaan ba, ta dai ce ya bar hakan a hannunta, su Uncle Ιinsa kuma suka je nema masa auren
Imaan Ιin a wurin Abba wanda dama shi ma ya san da zuwan nasu don Mami ta riga
da ta sanar da shi komai. A take kuwa ya amince yana mai farin ciki maras iyaka
don ganin cewa, wani babban nauyi da ya gagara sauΖewa na gab da sauΖa, abun da
ya fi faranta masa ma shi ne, Uncle Ιin CEO ya ce ba sa so bikin ya wuce wata
guda, ke nan dai har a zo bikin Dada ba za ta sani ba bare ta ce za ta hana,
haka uwar son zuciyar ma ba za ta sani ba bare ta lalata komai.
Kasancewar yau juma'a ce da wuri suke tashi a wurin aikin
nasa yasa Imaan fara harhaΙa kayanta da wuri,
bayan sun gama komai ita da
Jamila suka fito kasancewar yau za ta je unguwar su Jamilah Ιin da yake
a can take kitso. Bayan Imaan ta yi kitso ta koma gida ne Mani ta ce ta shirya
Hajiya na nemanta.
Haka kawai ta tsinci kanta da bugawar gaba, tsintar kanta ta
yi da furta "Hasbunallahu wani'mal wakili, la ilaha illa anta subhanaka
inni kuntu minaddhalimina" a sukwane ta shirya cikin wani material Ιin ta Ιinkin
doguwar riga da ya Ιan sha ruwa ta saka hijabi ruwan shuΙin sararin samaniya,
turare kaΙan ta mulka sannan ta yi wa Mami sallama ta wuce gidan Hajiya.
Sosai Hajiya ta tarbi Imaan, duk da cewa ba sabon abu ba ne
samun tarba mai kyau a gidan amma sai take jin na yau Ιin banbaraΖwai, ajiyar
zuciya take sauΖewa kawai tana nanata addu'a cikin ranta.
A hankali Hajiya ta Ιebe ta da taΙi har ta sake. Sai bayan
la'asar tukun Hajiya ta ja ta cikin Ιaki ta zaunar da ita bakin bed sannan ta
sanya idanuwanta cikin na Imaan Ιin, a hankali ta ce
"Imaan"
Imaan ta amsa tana kawar da nata idon gefe don yadda kaifin
idanuwan Hajiyan ke affecting Ιin ta a yau.
"Ni na saka Maminki ta aiko min ke, kin yi mamaki
ko?"
Ba ta samun damar furta komai ba sai ta gyada kanta.
"To ba komai ne ya sa nace ki zo Ιin ba sai wata
muhimmiyar magana da nake so mu yi, wacce ba na so kowa ya sani"
Gaban Imaan ne ya fadi tana jin bugun zuciyarta na Ζaruwa
cikin ranta tana tambayar wacce irin magana ce wannan Hajiya za ta faΙa mata.
Hajiya tace "Imaan, ke, Ni, Maminki da kuma Abbanki, mu
kaΙai ne muka san irin rayuwar da kika yi a baya, kike yin ta a yanzu kuma muke
hasashen in ba a Ιauki wani matakin ba cikinsa za ki ci gaba da rayuwa."
Shiru ta yi ta ja numfashi sannan tace "Sannan kuma,
mun yi magana da Maminki ta ce akwai saurayin da yake son ki Ζ΄ar'uwarki ta yi
Ζarfa-Ζarfa yanzu haka suna tare ko?"
A kunyace Imaan ta gyaΙa kai
"Amma ke ce babba ai?" Hajiya ta faΙa tan jijjiga
kai "ba wannan ba dai, shekarunki sun kai a ce a yanzu kina gidan aurenki
Imaan, shekaru ashirin da Ιori?"
Wani irin yawu Imaan ta haΙiye da Ζyar sai zazzare idanuwa
take, cikin ranta tana fatan inama a ce Hajiya ta bar wannan zance don kuwa ba
shi da wani fa'ida.
Wani hawaye ne ya kwaranyo daga kan kyakkyawar fuskar Imaan,
a yanzu ne ma kuwa take jin wani yanayi maras daΙi dangane da rayuwarta, sof
course ya kamata a ce tana da abokin rayuwa a yanzu, to amma tana da kyakkyawan
yaΖini kan cewa hakan ba za ta taΙa faruwa ba matsawar Ihsan da Dada na
numfashi, idan kuwa har sun amince ta yi aure to ta tabbatar mijin ba irin
wanda ya dace da ita ba ne, amma ai aure lokaci ne, don haka nata bai zo ba da
ta yi"
"Kin yi shiru Imaan, akwai wanda kuke tare ne a
yanzu?"
Cikin jin nauyin Hajiya da ta kasance kamar uwa gare ta tace
"A'a" tana jijjiga kanta.
Numfashi Hajiya ta sauke tare da sakin wani murmushi.
"To Alhamdulillahil, dama abun da nake son ji ke
nan"
Gaban Imaan ne ya yi wani irin bugawa jin abun da Hajiya ta
ce, tsananin mamaki ne ya mamaye ta har sai da ta Ιaga ido ta kallo Hajiyar,
jinjina mata kaj Hajiya ta yi kana tace "Ζwarai kuwa Imaan, na ji daΙin
jin hakan, yanzu dai ki kwantar da hankalinki, akwai yaron yayan Alhaji sunansa
Sulaiman, ba zan ce Miki komai a kansa ba, amma dai abun da na sami shi ne yana
so ya aure ki..."
Saurin katse Hajiya ta yi da faΙin "Aure kuma
Hajiya?"
Hajiya ta jinjina kai "Ζwarai kuwa Imaan"
Cikin rawar Murya tace "A'a Hajiya don Allah ki rufa
min asiri wallahi..."
Hajiya ta katse ta da faΙin "Ai rufin asirin ke nan
Imaan, aure ne kawai zai Ζ΄antar da ke daga uΖuba da son zuciya irin ta
Dada",
Cikin kaΙewar hankali tace "Amma Hajiya"
"Shhhh" Hajiya ta Ιaura yatsarta kan lips Ιin
Imaan kana tace "Don't say anything Imaan, mun riga mun yi magana da
Abbanki, Mami duka sun amince kuma sun nuna farin cikinsu, idan har kina son
farin cikinsu ina jin za ki amince, don su ma rashin ta cewa yada suke zuba ido
suna ganin abubuwan da ke faruwa da ke, ba wai don ba son ki ba ne sai don an
fi Ζarfinsu"
"Imaan lokaci ya yi da ya kamata ki nutsu, ki yi
aurenki ke ma, ki auri mijin da zai kasance garkuwa gare ki, wanda zai tsaya
Miki kan al'amuranki"
Shiru Imaan ta yi yayin da bugun zuciyarta da kuma
numfashinta ke fita da sanri.
"Ba za a tilasta Miki ba, za a ba ki dama ku fahimci
juna da mijin amma a sirrance, don Allah Imaan, kada ki bari wannan magana ta
bayyana a cikin gidanku don hakan na nufin rushewar komai ciki kuma har da
farin cikin iyayenki da mu masu Ζaunarki, ga waya nan zan ba ki, Sulaiman ne da
kansa ga siya ya ce a ba ki, za ku yi magana, don Allah ki nutsu, mutumin kirki
ne sulaiman na kuma tabbatar Miki ko nan gaba ba zai wulakanta ki ba, zai tsaya
Miki kan al'amuranki, yana da mata Ιaya, amma hakan ba damuwa ba ne Imaan, don
matar tasa gaba Ιaya ba ta da hali, ke dai ki taimaka masa don ya samu
kwanciyar hankali domin shi ma akwai tasa matsalar."
"Kar na cika ki d maganganu, Magrib ta kusa, bari na Ιauko
Miki wayar."
MiΖewa HaJiya ta yi ta janyo wata Ζatuwar leda ta miΖa mata,
mamaki ne ya bayyana kan fuskar Imaan, ita da za a ba wa waya me ye wannan
babbar ledar? Ta tambayi kanta.
Tunaninta ya katse ne da maganar Hajiya "Ga wannan,
wayar tana ciki, abubuwan cikin kuma shi ya ce a ba ki, ki daina saka waΙannan
suturun please "
"Hajiya ki bar su wurinki kawai, ko na tafi da su ba
amfani zan yi da su ba kin sani"
"A'a, dole ko tafi da su, ki dai yi yadda za ki yi ki
adana su ko Mami kada ki nunawa don ta san da su."
Gyada kai Imaan ta yi tana faΙin "To Hajiya, na gode
Allah ya saka da alkairi "
"Amiin Yarinyata, ki tashi ki wuce, ga wannan, ki hau
abun hawa"
"A'a Hajiya" Imaan ta faΙa a kunyace "akwai
kuΙi a wurina"
"To ki ajiye wannan Ιin ko ki sadakar"
Zaro idanuwanta tayi waje kana ta amsa tana faΙin "Na
gode Allah ya saka da Alkhairi"
"Mu je in raka ki"
Tare suka fita har compound Ιin gidan tukun suka yi sallama
Hajiya ta koma ciki.
Bloordale village
A cikin kwanaki soyayya mai Ζarfi ta Ζullu tsakanin JK da
kuma Shahada wacce ta riga ta koma gidansu, sosai JK ke nuna mata kulawa haka
ita ma a nata sashen ba ta wasa da al'amarinsa, lokaci bayan lokaci idan sun yi
waya ta kan bayar da saΖon gaisuwar ga AK, haka kawai take jin tausayinsa ba
kuma wai don ta san wani abu dangane da rayuwarsa ba ne, a'a kawai dai yanayin
yadda yake ne yasa ta fahimci akwai wani abu tattare da shi. A Ιangaren AK kuma
kullum al'amarinsa Ζara ta'azzara yake don ko aiki ba kullum yake fita ba, yana
zaune shi kaΙai a kan makeken gadonsa yana aikin na tunani, zabura ya yi ya
miΖe zaune, kamar wadda ya tuna wani abun ya sauko daga kan gadon ya fara
zagaya Ιakin, tunanin mafita yake kan al'amarin yarinyar nan da ta tsaya masa a
rai da ruhinsa, tabbas ya yadda soyayya azaba ce amma kuma ya Ζudiri a yau Ιin
nan ba gobe ba ya samarwa kansa maslaha ga rayuwarsa don tsira da hankalinsa da
yake neman gushewa saboda ita.
"Shin ta ina zan fara?? Ta ina zan fara?"
Ya furta cikin yanayi na nazari kafin ya ce "Nigeria
zan koma, ba tare da sanin kowa ba, zan je Azare ko kwana nawa zan yi sai na
nemo ta, i know Jahaan will be there for me"
Samun wuri yayi ya zauna yana jinjina kansa i tare da yin
amanna da shawarar da ya yanke wa kansa.
Zuciyarsa ce ta gargaΙe shi da faΙin "Idan kuma ita ma
kamar kai ne fa? Wato zuwa tayi kamar yadda ka je?"
Kansa ya langwaΙar gefe tare da sakin wani zazzafan huci
yana dunΖule hannunsa tare da naushin isa. A hankali ya furta "Then sai in
je in Ιauki CCTV footage na wurin da muka haΙu, though it has been a long time
amma la'alla na samu idan suna ajiya"
"Idan kuma ba sa yi fa?"
Kansa ya dafe da dukkan hannayensa yace "I know her
face, her smile, and her look! Zan bi jiya ko nawa ne a zana min hotonta! Of
course, hotonta will work wurin nemanta. Amma ta ina zan fara?"
Ya Ζarashe cikin Muryar da ke nuna tsantsar karaya, da sauri
zuciyarsa ta ba shi amsa da "Ta ko ina ma! I'll publish the image a
newspaper, zan bayar da tsagwaron kuΙaΙe ko da nawa ne ga wanda ya samo min
yadda take"
Mikewa yayi zumbur tare kai wa iska naushi yana murmushi,
that'll work in Sha Allah! My dream girl, I'm here coming to your rescue, zan
ceto ki daga hannun ko ma waye kike, zan zo gare ki da zuciya ta da kuma
ruhina! Ki jiraye Ni!" Wani irin yanayi y tsinci kansa, take ga ji duk
wata damuwarsa kamar ta kau har wani irin sanyi yaji yana ratsa shi.
A Ιangaren Imaan bayan ta koma gida ba ta bi ta kan kowa ta
adana ledar da ta taho da ita tukin ta nufi Ιakin Mami, so take ta ji maganar
daga bakin Mami amma Mamin ko a fuska ba ta nuna mata da ta san wani abu da
suka tattauna akai ba sai ma tambayarta ya ta baro Hajiya, daga nan ta mike ta
je don gabatar da sallar Magrib da aka fara kiraye-kirayenta.
Bayan ta idar da Sallah ne ta janyo ledar ta fara fito da
abubuwan da ke ciki, abayoyi ne masu Ιan karen kyau guda biyar sai waya keypad
Ζirar Itel wacce ke cikin kwalinta, kayan ta fitar daga ledar ta saka su cikin
jakar kayanta sannan ta dawo ta zauna, buΙe wayar ta yi, tana kunna ta taga ta
kawo ashe dai an riga an yi charging nata. Bayan ta gama kunnuwa taga har SIM
akwai a ciki, ajiyar zuciya ta sauΖe sannan ta sanya wayar a meeting mode, wato
vibration ta yadda ba za a ji ko da ringing Ιin ta ba.
Jin sallamar Abba yasa ta fita ta masa sannu da dawowa ta
amshi ledar hannunsa da ke Ιauke da shinkafa da kuma kayan miya, ajiyewa tayi
daga nan ta hau girki, sai wuraren Isha ihsan ta dawo daga school, da kallo
kawai Imaan ta bi ta sannan ta haΙa wutar girki.
Alhamdulillah!!! Duka duka nan na kawo Ζarshen wannan
littafin, ina fatan za ku kasance masu y min uzuri ga dukkan kusakuren da ke
ciki, domin samun ci gaban wannan littafin RIKITACCIYAR ALAΖA, ya kamata
wadanda ba su yi payment ba su yi, 500 Naira ne, 7061707238, Opay, Fatima
Hassan, sai ku tura evidence of payment via: 08053328139.