[4/28, 9:59 AM] khaleesat Haiydar π✍️: *If you
should come across this post plss say a prayer for my late father, Allah ya
sabunta masa rahama, ya gafarta masa da duk musulman da suka riga mu gidan
gaskiya, Allah ya kyautata makwancinsu gaba daya, ya sa mutuwa hutu ce a
garesu, Allah ya yafe masu kurakurrensu, Allah ya bamu guzurin tar da su* π₯Ί
**All thanks to Allah S.W.T for the chance and privilege to
commence this new book, yanda muka fara lafiya Allah ya sa mu idar lafiya*
_Hmm ga fa Halysaah, Allah ka bani ikon delivering babu cece ku ce_
*This first page goes to all the members of Mayraah
Conversation, i love and appreciate you all*π₯°
✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
1....
Tsaye take ta jingina da trunk din bishiya a wani babban
garden dake dauke da shukoki iri iri da suka kawata wajen, tsuntsaye sai
shawagi suke a garden din happily making a chirping sound as the sun set
slowly, the view was so beautiful and breathe taking, duk da yanda ta kafe view
din da ido gaba daya hankalinta baya gun, she was just staring at the setting
sun absentmindedly, tayi nisa cikin tunanin da take, daga gefenta wata
ma'aikaciyar asibiti ce in her mid 40, likitar ta dafa ta tana kallonta cikin
kwantar da murya tace "Magariba ya gabato mu je kiyi alwala ko"
Kallon likitar kawai take babu ko kiftawa kamar bata fahimci abinda take cewa
ba, sai ga hawaye ya fara taruwa idonta tana sauke numfashi a hankali, likitar
ta kama hannunta ta jawota jikinta calmly tace "C'mon sweet heart, are you
breaking ur promise already?" ta kwantar da kanta jikin likitan hawaye
wasu na bin wasu a fuskarta, likitan ta lumshe ido tana patting dinta duk
jikinta a sanyaye, a tare suka juya jin footstep a garden din, ya tsaya daga
inda yake bai karaso ba yana kallonsu, likitan ta fara gaishesa cikin
girmamawa, zame jikinta tayi daga na likitan ta juya masa baya alamar ko
ganinsa bata son yi hawaye na zuba idonta, ji take kamar numfashinta zai dauke
kamar ko da yaushe, ta fashe da matsanancin kuka ta dafe trunk din bishiyar
dake gefenta, ko amsa gaisuwan likitar bai yi ba ya juya ya fice daga garden
din, da sauri likitan ta kamota ganin faduwa zata yi, ta fara kokarin zaunar da
ita akan lallausan carpet dake shimfide wajen trying to calm her down tace
"Haba kanwata, me yasa baza ki cika min alkawarin da kika daukar min
ba?" Muryarta na rawa tace "Kiyi hakuri bazan iya ba wallahi"
Rungumeta likitan tayi tana bubbuga bayanta a hankali wani mugun tausayinta na
shigarta, tayi attending to different cases in her career as a medical Doctor
amma babu wanda ya taΙa daga mata hankali ya tsaya mata a rai irin na baiwar
Allahn nan, she wish she can take away her pains, she wish she can make her
happy once more, she wish she can make her forget the past and face the
present, a hankali likitar tace "Halysaah...." khaleesat ta daga
rinannun idonta tana kallon likitan, likitan tace "Kiyi hakuri Halysaah,
kiyi hakuri" Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, likitan ta daga ta
tana rike da hannunta suka bar garden din zuwa babban compound din gidan.
Few years back!
"Talk to Abdul about it, nasan bazai taΙa yarda da haka
ba, and he will definitely find a way out for u immediately..." Khaleesat
ta daga manyan idanuwanta tana kallon kawarta Safiyyah, kamar bazata ce komai
ba sai kuma ta sauke idonta a hankali tace "That will be another huge
burden Safiyyah, u know how expensive apartment can be in this state, gida da
akwai tsada sosai, kuma na fa ce maki ni bazan sake tambayarsa komai ba, ko
kuma ince yayi min wani abu...." Safiyyah tace "Cabdi, to in ba ki
tambayesa ba kina da wanda zaki tambaya? Balle ma kinsan halinsa lokaci daya
tsaf zai juya situation din nan against you, i think gwara kawai ki sanar masa
yafi maki kwanciyar hankali" Khaleesat tayi shiru tana nazarin abinda
Safiyyah ta ce, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tana girgiza kai tace
"It's fine Safiyyah, ba sai na gaya masa ba i will cope in sha Allah,
after all we have just a year and a half to go" Safiyyah na kallonta ta
kamo hannunta tace "Ko zaki dawo wajena sai in gaya masu kawata zata zo ta
Ιan zauna da mu zuwa wani Ιan lokaci?" Khaleesat ta girgiza kai tace
"Let not inconvenience them Safiyyah, kar ki damu kawai, i will sort my
self out...." Safiyyah tace "No, i will talk to Ya Musty about ur
current situation khaly, nasan bazai ce a'a ba, matarsa ce dai gagarumar er
iska, and do i even care? Ba ki ma san me take min ba yanxu a gidan, duk dare
bata girki da ni sai dai in nemi abinda zan ci tunda kinsan Ya Musty night
shift yake, ni kuma dama kin san i prefer junk food, kawai sai in hada cornflakes
in sha abu na" Khaleesat tayi murmushi tace "Shine kike son in bi ki
zuwa gidan a haka ko? You are very funny" Safiyya ta juya ido tace
"So what? Naga ai ba kanta zaki zauna ba in kin dawo gidan, Yaya Mustyn
nan fa is my cousin brother ko kin manta ne? Saboda haka ko taki ko ta so dole
in zauna a gidan har in gama karatuna, very wicked and self centered woman,
wallahi kar ki wani damu in dai nayi ma Ya Musty magana kawai ki dauko kayanki
ki dawo gidan ko zuwa gobe ne...." Khaleesat tace "Aa gaskiya don't
even start that Safiyyah, i will cope with my present situation with time,
nasan zan saba gradually, beside it's something that is normal kawai dai ni ce
nake damun kai na saboda addinina da culture dina da dai wasu abubuwan da baza
a rasa ba, any way... it's fine Safiyyah" Tana fadin haka ta kalli wayarta
dake hannunta jin shigowar notification, tace "I think my Lyft is here
Sophie, sai gobe in Allah ya kai mu" Safiyya ta sauke ajiyar zuciya tace
"Ohk then, take care of ur self, i will stroll home too" a haka suka
rabu, Khaleesat ta nufi Lyft din da tayi ordering zai maida ta gida. Khaleesat
na kitchen wajen karfe goma na dare ta gama girka Noodles da zata ci for dinner
kenan taji alamar an bude kofar parlor, a hankali ta karasa juye Indomie dinta
a plate ta dau fork ta saka sannan ta wanke pot din ta ajiye, ta bude fridge ta
dau bottle water ta fita daga kitchen din, hanyar dakinta ta nufa direct, dai
dai corridor aka bude kofar wani room that is just few steps away from her own
room, ko kallon direction din bata yarda tayi ba tana kokarin bude kofar
dakinta taji ance "Hi, good evening, we didn't get to meet when i was here
in the morning I guess you've already left for school then, you can call me
Jay, and i am ur new House mate, I moved in this morning...." Sai a sannan
Khaleesat ta juya ta kallesa amma bata ce komai ba, ya gyada mata kai yace
"Jay" babu yabo babu fallasa tace "I see" Ganin zata shige
daki yace "A minute pls" Ta juya ta sake kallonsa da wani expression,
a takaice yace "Ke bahaushiya ce?" Ta Ιan hade rai tace "I don't
know what u are talking about" Yace "Oh ohk, i am asking for a
permission..." Ita dai kallonsa kawai take, Ya gyara tsayuwarsa yace
"As u can see it's late already now, can i use some of ur portable water
and Beverages before i get mine tomorrow if you don't mind?" Khaleesat ta
dauke kanta a takaice tace "Ohk" Yace "Alright" Daga haka
ta shige dakinta ta kulle kofar ta saka key, ko da ta gama cin Indomie din bata
ji zata iya bude kofa ta fita kai plate din kitchen ba, daga karshe kawai ta
bar shi a wajen bayan ta shiga bandaki ta wanke bakinta ta dauro alwala ta fito
ta zauna edge din gadon dakin ta dau wayarta, Miss calls din Abdul ta gani har
biyu wanda yayi mata tun karfe shidda, ta sauke ajiyar zuciya tana duba agogon
wayarta dake nuna mata karfe goma da kusan rabi, meanwhile karfe kusan biyar
kenan na asuba agogon Nigeria, bude WhatsApp dinta tayi ta dubasa taga yana
online, hakan yasa ta masa WhatsApp call, yana dagawa tayi kasa da murya ta
gaishesa a hankali, Bai amsa ba yace "Yanzu kika ga kirana?" Ta sauke
boyayyen ajiyar zuciya tace "Kayi hakuri, yanzu naga kiran wallahi"
Yace "You mean tun daxu wayarki baya gun ki kenan?" Tace "Not
really, tun dai da na dawo schl nake karatu, in few months time zamu fara
exams" Yace "I see, shi ne yasa kika ga ban yi deserving lokacin ki
ba don zaku fara exams, ta yaya ma wayarki zai yi ring ki ce baki sani ba in ba
rainin hankali ba?" Rasa abinda zata ce masa tayi, don wayar a silent yake
kuma ya hanata barin waya a silent on several occasions, to avoid further
issues sai bata ce masa wayar a silent yake ba, a hankali tace "Kayi
hakuri, wallahi ba haka bane, i am sorry..." Yace "Sorry for ur self,
malama so nake ki gaya min kina ina har wayarki rang twice baki ji ba? ur
lectures today terminated by 4pm Baltimore time, so ina kika je daga nan?"
Ta rufe ido ta bude don ta fara gajiya da tuhumar tasa, After few seconds ta
marairaice tace "Ina parlor ne ina karatu, wayar kuma na daki" Yace
"Kin fara zaman parlor kenan, when did that start? House mate din taki ta
dena shigowa da saurayinta ne gidan?" sai da gaban Khaleesat ya fadi, A
hankali tace "Bata nan, taje LA jiya"
Yace "Sau uku kenan ina kiranki a satin nan baki dagawa sai sanda
kika ga dama ki biyoni, that nonsense shouldn't repeat it self again, a kanki
aka fara karatu ko ni zaki gaya ma karatun Exams?" Shiru Khaleesat tayi
lkci daya hawaye ya cika idonta, a Ιan fusace yace "Baki ji na ne?"
Cikin sanyin murya tace "Naji, kayi hakuri hakan bazai sake faruwa ba in
sha Allah" Yace "Good, you can go to bed" Tana goge hawayen da
yaki tsaya mata tace "Nagode, sai da safe" Shi ya katse call din ta
ajiye wayarta gefen gadon ta dora kanta a pillow hawaye na zuba idonta, after a
while ta mike ta tafi bandaki ta wanke fuskarta ta dawo ta kashe wutan dakin
tayi addu'an bacci ta kwanta....
Washegari Friday da wuri Khaleesat suka gama lectures dinsu, suna zaune
a exact spot din jiya ita da Safiyyah dake waya, sosai Khaleesat tayi nisa
tunanin da take har bata san sanda Safiyyah ta gama waya ba, dafa kafadarta da
Safiyyah tayi ne ya dawo da ita duniyar tunanin da ta shiga, Safiyyah tace
"What is wrong Khaleesat, ina ta magana baki ma san ina yi ba, tunanin me
kike haka?" Khaleesat ta Ιan kirkiri murmushi tace "Kawai ina kewar
Ummanmu ne da siblings dina" Safiyyah ta girgiza kai tace "Ban yarda
ba, there is definitely something that is bothering you" Khaleesat ta
kauda zancen tace "Ke da George ne ke waya ko?" Safiyyah tayi kasa da
murya tace "Pls gobe weekend ki shirya mu tafi Virginia Leesat, George is
throwing a party for his birthday tomorrow, kuma za mu je Beach, don Allah kar
ki ce a'a, we need to take a break and rest our brain, ba ko da yaushe karatu
ba kamar mu muka kawo boko duniya...." Khaleesat dake ta kallonta tace
"Ke yanzu sai ki kama hanyar Virginia Safiyyah??" Safiyyah ta hade
girar sama da ta kasa tace "To menene, it's just a 4 hours ride from
Maryland, kamar fa ace daga kaduna zuwa kano shi ma in mota bai yi gudu ba, pls
for once ki zama social mana Khaleesat, ke baki gajiya da zama guri daya ne a
kasar nan? Baki gajiya da karatu? ranan Monday fa za mu dawo in sha Allah, kuma
babu wanda zai san mun je wani Virginia, dama Ya Mustapha na riga na gama plan
din abinda zan ce masa, ke da ba ma ki da wanda zai sa maki ido kike mis using
opportunities haka, da mun koma Nigeria fa shikenan, tafiyar nan maza ne hade
da mata" Khaleesat ta girgiza kai tace "Lallai... Ni dai ina baki
shawara kar ki je Safiyyah" Safiyyah tace "Bana ma son shawaran,
abinda mu goma za mu je" Khaleesat tace "Toh Allah ya tsare hanya ya
dawo da ku lafiya" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Baza ki je ba
kenan dai?" Ba tare da Khaleesat ta kalleta ba tace "Kema kin san
bazan je ba ai" Safiyyah tace "Ke kika sani, mu dai za mu je
wallahi" Safiyyah na kai wa nan ta mike tace "Sai ran Monday"
Khaleesat na kallonta a hankali tace "Wai tafiya za ki yi? Da sauran time
fa Safiyyah" Safiyyah tace "Aa toh me za mu zauna yi a schl bamu da
aji? Yau kuma kece ke cewa da sauran time duk son ki da komawa gida da wuri?
Ikon Allah" Khaleesat ta kasa cewa komai, ita har ranta take jin ta tsani
gidan nata yanzu, she no longer see the home as her comfort zone, and she don't
think she can cope staying together with an Hausa Guy under same roof, da ma
bature ne ko kadan bazata damu ba kamar yanda ta damu yanxu, har ta taho school
bata hadu da sabon Housemate din nata ba da safe, Safiyyah ta Ιan buda ido ta
koma ta zauna tace "Ohh now i remember, wai saboda new House mate dinki?
To wai ke meye damuwarki ne da shi? Yayi harkan gabansa kiyi naki ne fa a
gidan, ko magana in baki son ya maki you just call the cops a maki iyaka
da shi, just dial 911 and that's all,
balle nasan kilan da kyar aka kukuta masa ya taho makaranta kasar nan to kuwa
ina zai tsaya bata lkcnsa akan abinda ba shi ya kawo sa ba, don dai in wani
Shege ne shi bazai zauna a shared apartment ba a USA, kuma 'ya yan masu kudin
nan sun fi iskanci su kuwa talakawa abinda ya kawo su kawai suke yi, kiyi ta
kanki kawai shi ma yayi ta kansa, kar kiyi mamaki ta scholarship ya zo kasar
ma" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take, Safiyyah ta kyabe baki tace
"Tashi mu je gidan, ni banda Ya Musty bazai yarda ba da ba sai in tattaro
in dawo gidan naki ba mu zauna kawai" Khaleesat ta marairaice tace
"Plss ki sake masa magana ko zai bar ki mana, ai sanda ya hanaki kinga
bamu dade da fara makarantar ba" Safiyyah tace "Kar ma ki bata
bakinki mutumin nan bazai yarda ba, tashi mu je in raka ki, in House mate din
ma yaga kina wani yin abu a tsorace renaki zai yi wallahi, yi zaki yi kamar kema
er gari ce kawai sai ki ga ya fara shakkar ki a gidan" Khaleesat ta mike
tace "Kar fa muje kiyi ta Hausa, just pretend we are not Hausa"
Safiyyah tayi dariya tace "Kece dai is not Hausa, ni kam Bahaushiya ce
cikakkiya kuwa" A haka dai suka bar makarantar suka nufi gidan da
Khaleesat take.... Khaleesat ta bude handbag dinta ta ciro makulli ta bude
kofar shiga gidan suka shiga parlor Safiyyah na biye da ita a baya, Safiyyah na
gyada kai jin wani kamshi da parlon yake tace "Da alama bai dade da fita
ba ma" Khaleesat dai bin parlon take da kallo ganin duk reading materials
dinsa ne saman kujera ya tula a kai, Safiyyah tace "Kinga don Allah ki
saki ranki ki ci gaba da harkokin ki Khaleesat, a Maryland fa kike a Amurka ba
Kano Nigeria ba, ki dinga abu irin na wayayyu mana pls" Wani kallo
Khaleesat tayi mata ta ajiye handbag dinta tace "Ance maki in bature ne ko
wani yare ni zan damu, kawai my issue here is about him being a Hausa Guy, har
fa tambayata yayi jiya ko ni bahaushiya ce" Safiyyah tace "Ohh kun ma
yi magana kenan...." Khaleesat tace "Ni ban kulasa ba kuma ban nuna
masa ni Bahaushiya bace, i will just pretend i am from Morocco" Safiyyah
ta dinga dariya har da saukowa daga kan kujera tace "Gashi kuwa an ma fi
saninsu da fararen mata kyawawa na ajin karshe, tsaf zai yarda daga can kike,
kinga da larabci ya zauna daram a bakinki sai kiyi ta zabga larabci nasan ba
lallai yana ji ba, daga haka zai kama kansa yayi zaton ke balarabiyar gaske
ce... sai ma Abdul yaji kuna gida daya da Bahaushe kilan Baltimore yayi maku
kadan wallahi, shi sa nace ki gaya masa kika ki" Khaleesat ta ajiye
jakarta bata sake kallon Safiyyah dake ta dariya ba tayi wucewarta kitchen tana
tunanin me zata dafa masu dama ko breakfast bata yi ba ta fita daga gidan,
tsaye tayi kitchen din tana kallon cartons din bottle water kusan bakwai wanda
duk yafi tsada a state din, sai kuma ta juya ta kalli beverages masu yawa da ya
ajiye kan cabinet, ta karasa cikin kitchen din ta bude babban fridge zata dau
kwai da za ta dafa masu Noodles, kallon fridge din ta dinga yi ganinsa fully
stocked with everything, tun daga tsadaddun drinks kala kala, fresh milk,
varieties of fruits, with many eggs, muryar Safiyyah taji a bayanta tace
"Kai kai kai, shi ya zuba abubuwan nan a fridge Leesah?" Khaleesat ta
juya ta kalleta looking speechless, can dai ta dau eggs din da zata dauka ta
kulle fridge din ta tafi inda foodstuffs dinta suke shi ma taga kayan abinci ya
siyo, Safiyyah ta rike haΙa tace "Duk a kudin scholarship din yake facakan
nan? Ko dai bashi da hankali ne bai san bin komai ake a sannu a kasar nan
ba" Khaleesat dai ta dau Noodles dinta ta bar wajen tana kallon Safiyyah
tace "Ga Indomie ki dafa mana, ina son inyi magana da Ummanmu kafin Aunty
Sha'awa ta fita kasuwa" Safiyyah tace "Ohk to" Khaleesat ta bar
kitchen din ta dau jakarta ta wuce dakinta, WhatsApp dinta ta bude ta shiga
contact din makociyarsu Sha'awa tayi mata voice note kamar yanda ta saba a duk
sanda take son magana da Ummanta. Sai kusan karfe hudu na yamma Khaleesat ta
raka Safiyyah zuwa gun Lyft din da tayi ordering don tun daxu Cousin brother
dinta ke kiranta ganin bata dawo gida ba, Safiyyah ta shige motar ta kulle tana
daga ma Khaleesat hannu, sai da Lyft din ya bar wajen sannan Khaleesat ta juya
tana tafiya a hankali ta nufi apartment dinta, dai dai apartment din taga mota
yayi parking a space din da aka tanadar don parking for that apartment, bata
karasa ba ta jingina jikin fence din dake inda take tsaye tana kallon motar ta
little space din dake between the wooden fence din, taga ya fito daga motar ta
bi sa da ido har ya shiga apartment din yana danna wayarsa, ta fi minti biyar
tsaye a inda take, daga karshe tana tafiya a hankali ta karasa apartment din ta
murda kofar parlon taji ya kulle, hade rai tayi tana kallon kofar, daga karshe
da ta gaji da tsayuwa kawai tayi knocking, sau uku tana knocking sannan ya bude
kofar, yana ganinta yace "Hi" ita dai ko kallonsa bata yi ba fuskarta
babu yabo babu fallasa ta bi gefensa ta shiga parlon, direct gun wayarta dake
kan kujera ta nufa ta dauka tare da reading materials dinta dake saman kujeran,
har zata dakinta sai kuma ta dawo ta tafi kitchen ta dau goran ruwa daya sannan
ta nufi dakin, sai da ta bude kofar tayi masa kallon gefen ido taga he is just
busy sorting out some textbooks that were inside a carton he came with, har ta
shiga dakin nata bai juya ba balle ya kalli direction dinta....
07087865788✍π»
[4/29, 5:07 PM] khaleesat Haiydar π✍️:
https://chat.whatsapp.com/KVY8hjs3iNq5ntSN4Z5g6V
✨✨ HALYSAAH ✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
2.....
Washegari har karfe sha daya Khaleesat na dakinta bata fito
ba duk da yunwan da take ji, tayi tagumi don gaba daya ta ma rasa what is her
problem particularly, ta dau wayarta jin shigowar WhatsApp message, tun daxu
suke chatting ta VN da Ummanta ta wayar makociyarsu Sha'awa, da taji shiru ta
ma zata an maida ma Aunty Sha'awa wayar nata ne, ta bude VN din tana sauraren
voice din mahaifiyarta, Addu'a Ummanta ke mata tana mata fatan nasara a karatun
ta, sannan kamar ko da yaushe ta sake jaddada mata ta kula da mutuncinta ta
kula da kanta, daga karshe ta Ζare da cewa za a kai ma sha'awa wayarta don zata
fita kasuwa, Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta ajiye wayar a hankali sannan
ta mike ta dau hijab din sallanta ta saka ta nufi kofa ta bude a hankali ta
fita daga dakin don ta gaji da horan kanta da yunwa ita da ke breakfast da
wuri, kitchen ta tafi almost bumping into her new House mate shi kuma yana
kokarin fitowa daga cikin kitchen din, komawa baya yayi at the same time yace
"Good morning" Bata yarda su hada ido ba ta matsa gefe allowing him
to pass, ya fito daga kitchen din yayi wucewarsa without looking at her, sai a
sannan ta shiga ciki, tsaye tayi tana kallon littered cups da plates din da
yayi amfani da su ya bari a sink din wanke wanke without washing them, ga bowl
din fruit salad da shi ma ya ajiye bai sha ba, bin kofar kitchen din tayi da
kallon mamaki, to wa ya bari yayi masa wanke wanke? Ta fi minti daya tsaye a
inda take da tunani iri iri a ranta, wata zuciyar ta ce mata kawai tayi abinda
ya kawota ta fita daga kitchen din ta bar unclean utensils din a yanda ya bar
su, amma dai kawai ta jawo liquid wash da sponge fuskarta a daure ta fara wanke
kayan wanke wanken kawai, bayan ta gama ta goggoge kitchen din ta hada shayi ta
debi cookies a plate sannan ta fita daga kitchen din ta wuce dakinta. Wajen
karfe uku Khaleesat ta fito daga dakinta, tun da ta gama breakfast take karatu
sai sallah kawai ta tashi tayi da azahar, jin ko ina shiru and to be sure baya
gidan ta nufi kofar parlon zata bude taji an kulle da makulli, dakinta ta koma
ta dauko makullinta ta bude kofar tana duba garage taga babu motarsa a ciki,
komawa cikin gidan tayi ta kulle kofar sannan ta tafi kitchen, tun shekaranjiya
take son cin shinkafa da miya amma kasancewar she is not comfortable tun da ya
dawo gidan yasa ta hakura da girkawa, yanzu da taga baya nan kawai tayi
deciding tayi shinkafa da miyar, bayan ta daura shinkafar, ta fara hada miyar
dama tana da sauran chicken thighs a fridge, fitowa parlor tayi da sweeper zata
yi shara, ta ajiye sweeper din hannunta to tidy the couch first, dukawa tayi
tana kallon takardun Housemate din nata da ta gani, sai kuma ta kyabe baki ta
bar su nan yanda ya bari a kan kujeran, share rug din parlon ta fara yi bayan
ta dauke makullin da ta gani a kasa, ta dinga juya makullin ganin kamar na
Bedroom ne, kafin minti arba'in ta gama girkin da take ta tsaftace ko ina na
gidan, ta debi abincinta ta tafi daki da shi, sai da ta fara yin sallahn Asr
sannan ta dau wayarta tana dubawa, sosai gabanta ya fadi ganin miss call din
Abdul, nan da nan taji abincin ya fita ranta gaba daya, ta zauna gefen gado a
hankali tana kallon wayar, ta fi minti goma zaune a haka, she was soo worried,
to yanzu me zata ce masa ma in ta kirasa, daga karshe ta daure tayi dialing
number nasa, har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, duk da
yunwan da take ji haka nan taji abincin ya fita ranta, ta tsani duk wani abu da
zai sa Abdul ya daga mata hankali, haka tayi forcing din kanta ta ci abincin
sannan ta kwanta side din gado, bata san sanda bacci ya dauketa ba a haka....
knocking kofar dakinta da ake yi ne ya farkar da ita daga baccin da take, ta
mike zaune da kyar tana murza idonta tana kallon kofar at the same time tana
mamakin me zai sa ya dinga bubbuga mata kofa haka, to ko dai bashi da kai ne??
ta jawo wayarta tana duba agogo taga karfe shidda da mintuna, bata yi tunanin
ta dade tana bacci haka ba, sake knocking da aka yi yasa ta mike tsaye ta saka
hijab fuska daure tace "What is that??" Ta ji yace "Ohk i think
i misplaced my keys, just want to know if you saw it while tidying up the
parlor?" Sai a sannan ta tuna makullin da ta gani a parlor daxu da take
shara, tana tafiya a hankali ta karasa kofar dakinta ta murda key din jiki
sannan ta bude door din, tuni har ya bar corridor din ya koma parlor ya tsaya
yana jiranta, da alama dawowarsa gidan kenan a lkcn, ta karaso cikin parlon ba
tare da ta kallesa ba, shi dai duba message din da ya shigo wayarsa yake with
all his attention, ta tafi inda ta ajiye makullin sannan ta dawo ta ajiye masa
kan takardunsa dake kan kujera tace "Here" Yace "Ohk"
dakinta ta koma ta shiga tana mamakin wai Ohk, ba ma thank you ba kamar irin ya
ajiyeta din nan, kwafa tayi ta saka ma kofarta key, bayan Khaleesat ta idar da
isha ta sake kiran Abdul bai daga ba, sau hudu kenan tana kiransa tun karfe
bakwai bai yi responding ba, yanzu dai tafi tunanin yana bacci don dare ne
sosai a can kasar, even at that tasan she is in soup, mikewa tayi ta dau plate
din da ta ci abinci daxu ta nufi kofa ta fita daga dakin, a parlor ta ga sabon
Housemate dinta yana tattara takardunsa at the same time yana answering phone
call taji yana cewa "I am on my way now" Daga haka ya katse wayar ya
mayar aljihunsa ya dau takardunsa da makullin mota ya mike tsaye, ido hudu suka
yi for the first time tunda ya dawo gidan, ita dai ta dauke kai kamar bata ma
gansa ba ta karaso cikin parlon zata tafi kitchen taji yace "I ate a
little out of the food you cook, and...." Yayi pointing takeaway din da ke
kan kujera yace "I am taking some to my frnd too" duk wannan abun bai
kalli inda take tsaye ba yake magana, sai ita ce ma da ta dinga kallonsa da
mamaki babu ko kiftawa, ya dau takeaway din ya nufi kofa cikin hanzari, yace
"Good night" Ta bi sa da kallo har ya fita ya kulle gidan da makulli
ta waje, mamaki yasa ta kasa karasawa kitchen din, after some seconds ta tafi
kitchen din, da plate din da ya ci abincin, da cup din da ya sha coffee, da
bowl din da ya sha fruits salad duk suna ajiye a sink babu wanki, ta jingina da
kofar kitchen din ta rungume hannu tana kallon sink din kamar zata fashe don
bakin ciki, can ta karasa ciki tana duba shinkafar da ya bar mata, taga da kyar
in zai yi spoon uku, gashi duk yayi littering din wajen da shinkafar wajen diba
kuma ya bar shi haka, haka nan ta juye er shinkafar da ya rage a karamin bowl,
ta wanke duk utensils din, ta gyara ko ina ta goge sannan ta hada shayi ta koma
daki da bowl din sauran abincin, zaunawa tayi gefen gado ta dau wayarta tayi
dialing number Safiyyah, sai da ya kusa katsewa Safiyyah tayi picking daga daya
bangaren tace "Allah da gaske baki da kirki Khaleesah, to ko baki kira ba
dai na isa Virginia cikin koshin lafiya" Khaleesat ta Ιan yi murmushi tace
"Dama nasan kin isa lafiya ai, hope you are doing good?" Safiyyah ta
tabe baki tace "Oho dai, wannan ba matsalar ki bane" Khaleesat tace
"Amma don Allah ina kika ce ma Ya Musty za ki?" Safiyyah tace "Ahaf
tsaya wasa, sai kace baki san ni ba, munafukar matarsa da yake ba son zamana a
gidan take ba ita ce ma ta kara convincing dinsa, duk zatonsu ina gidanki muna
group reading with some of our Coursemate" Khaleesat tayi murmushi tace
"To ai shikenan, yanxu yaushe zaki dawo?" Safiyyah tace "Gobe ne
birthday din ai, in sha Allah i will be back on Monday" Khaleesat tace
"Toh Allah ya kai mu, kinsan mene?" Safiyyah tace "Aa"
Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Wallahi in gaya maki Abdallah ne ya
kirani nayi missing call dinsa as i am speaking to you now tun daxu nake kiransa yaki picking, nasan fushi yayi sosai,
ni kuma...." Safiyyah ta dakatar da ita tace "Ke kuma me? Shikenan
rayuwa babu uxuri dama?" Khaleesat tayi kasa da murya tace "He warned
me times without number kar in sake missing call dinsa Safiyyah, kuma wallahi
ina kitchen sanda ya kira wayar kuma na daki ba da gangan nayi missing kiransa
ba" Sounding so pissed off Safiyyah tace "Wai don Allah me yasa kika
dauki tsoron duniya kika dora ma mutumin nan ne Khaleesat? For how long will
things continue this way? Yaushe za ki fara nuna masa ke fa mace ce? yanzu haka
za ku yi auren ya maida ki slave a gidansa tunda kin nuna masa kina mugun
tsoronsa tun a waje? wannan wani irin gantalallen relationship ne? Gaskiya ina
jinjina maki Khaleesat, don wallahi in nice bazan iya ba Allah ma ya gani sai
dai duk abinda zai faru ya faru" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "I
have no choice nor option Safiyyah...." Tana fadin haka hawaye ya fara
gangarowa idonta, a Ιan fusace Safiyyah tace "To wai ke kadai ce mace a
gidanku ne da ya gani? Naga ga Labibah da Lamisah, ina ce sati biyu kika ba
Labibah a shekaru, ita kuma Lamisah wata daya, ga kuma yayyinki Samira da
salamatu, to wai halan su ba mata bane sai ke??" Khaleesat dai bata ce
komai ba tana goge hawayen dake zuba idonta, Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya
tace "Ai shikenan, but u really need to speak up for ur self Khaleesat, ni
dai nasan their worst mistake is sending you to school abroad, aje dai zuwa, ke
kuma in har baki waye kin kwatar ma kanki 'yanci daga karshe ba to sorry to say
this, wallahi u will live a miserable life in the nearest future Khaleesat,
this is just the fact i am saying, na gaji da lamarin so called Abdul din
ki" Cike da karfin hali Khaleesat tace "Ki daina cewa haka pls
Safiyyah, ke me tayani addu'a ce kan Allah ya kawo min komai da sauki amma ba
ki dinga fadin wa ennan maganganun ba...." Safiyyah ta taΙe baki bata dai
ce komai ba, a hankali Khaleesat tace "Pls ko zuwa gobe da safe ki masa
magana ta Whatsapp ki tayani basa hakuri cause nasan bazai daga kirana ba no
matter what..." Safiyyah tace "To naji, Allah ya kai mu goben"
Khaleesat tace "Ameen" Sallama suka yi, Khaleesat ta ajiye wayarta.
Karfe goma saura na safe Khaleesat ta fito daga dakinta rike da wayarta don kar
ma Abdul ya kira by mistake tayi missing call dinsa, tun jiya take makale da
wayar duk don kar ya kira bata sani ba, kuma sau uku tana kiransa bayan da tayi
sallan asuba bai daga ba still, yanzun ma da ta tashi sae da ta kirasa sau daya
nan ma no answer, zaune taga new Housemate dinta a Ιan reading nook da aka
tanadar a living Room din studying with a huge textbook dake gabansa, she had
no idea ma ya shigo gidan, don bayan da tayi sallan asuba ta fito ta hada shayi
ta sha da cookies a nan parlon sannan tayi karatu har zuwa bakwai na safe, daga
nan ta shiga daki ta kwanta sai kuma yanzu da ta tashi feeling hungry, sau daya
ya kalleta yana ci gaba da duba Textbook din gabansa yace "Good
morning" Ta karaso cikin living room din a takaice tace "Ok"
Ajiye wayarta tayi kan 1 sitter ta nufi kitchen, Ya daga kai yana kallon
direction din da ta bi da harshen turanci yace "In baki yi breakfast ba,
ga wani nan ki dauka....." Tsayawa tayi sai kuma ta juya ta kalli Centre
table da yake nuna mata, ledan abinci ne
kan table din duk da bata san wani kalan abinci bane a ledan, ta kallesa taga
ya ci gaba da karatun da yake, girgiza kai tayi with no interest tace "No,
tnx" Daga haka tayi wucewarta kitchen, ta fi minti uku tsaye kitchen din
tana tunanin me zata yi, seeing her House mate sitted in the living room yasa
ta zama uncomfortable to cook anything, hakan yasa kawai ta dauko kwalin
cereals da bowl zata hada cornflakes, wayarta ta ji yana ring a parlor don tun
jiya ta cire wayar a silent, bata san sanda ta saki both d bowl and the Cereal
din hannunta ba ta fito daga kitchen din within few seconds, House mate dinta
ya bi ta da kallo har ta nufi gun wayarta ta dauka da sauri, sai da gabanta ya
fadi ganin Abdul ne ke kiranta, babu bata lokaci ta daga call din, zuciyarta na
bugawa tayi masa sallama, jin shiru tace "Hello" kallon wayar tayi ta
sake maidawa a kunnenta har sannan bata daina cewa Hello ba, House mate dinta
dai ya ajiye Textbook dinsa gefe ganin yanda ta rude ya maida duk concentration
dinsa akan ta, Khaleesat ta sake kallon Screen din wayar jin shiru Abdul ya ki
ce mata komai kuma tana jin maganar mutane a background, marairaicewa tayi ta
duka nan kasan living room din ta saka wayar a handsfree tace "I know u
can hear me pls, don Allah kayi hakuri, i am making u this promise hakan bazai
sake faruwa ba wallahi, don girman Allah kayi hakuri" Sai a sannan yayi
magana da husky voice yace "Hold on to ur promise malama, sau biyar kenan
kina missing call dina within a short period, are you out of ur senses or is
anything wrong with ur brain?" Da sauri ta girgiza kai kamar zata yi kuka
tace "Wallahi ina kitchen ina girki san da ka kira jiya, kuma...."
Cutting dinta yayi yace "ke, bana bukatar jin komai daga gare ki, none of
ur lies and excuses will convince me, naga kamar u are beginning to take me for
granted this days.... Kinsan Allah kika sake missing call dina zaki sha mamakina
wallahi cause it will take me nothing to be in America...." Hawaye ya cika
idonta cikin sanyin murya tace "Amma me yasa baka min uxuri?" Yace
"Baza ayi uxurin ba, ni za ki gaya ma uxuri? A kanki aka fara
karatu?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Wato ke kin fi karfin ki
bude baki ki bada hakuri ko" Kasa cewa komai Khaleesat tayi don tun da ta
daga kiransa ta fara basa hakuri bata kuma san wani hakurin yake nufi ba, A
takaice yace "Anyway, i called to warn you to stop disturbing me with
unnecessary calls, na biyu kuma ki ja ma kawarki kunne she should never come
into my DM and tell me nonsense again don zan dau mummunan mataki a kanta, ke
kuma duk sanda yayi suiting dina i will call you, don't try calling my line
again" Yana kai wa nan ya katse wayar, Khaleesat ta dinga kallon screen
din wayar hawayen dake makale idonta ya gangaro, House mate dinta ya Ιan yi
murmushi wanda iyakarsa lips after paying attention to their conversation,
mikewa Khaleesat tayi tana share hawayen dake sauka idonta, sai a sannan ta
lura da shi a parlon, dauke kai tayi da sauri bayan sun hada ido, gaba daya ta
ma mance yana parlon, taji yace "Is that ur Father?" Wani kallo ta
jefa masa tayi wucewarta dakinta wasu sabbin hawayen na zuba idonta, ruf da
ciki tayi kan gadonta tana kuka har da shessheka, ta kusa minti arba'in kwance
a yanda take, zuwa sannan ta dena kukan da take kawai ta lumshe ido, knocking
din kofar dakinta da taji anyi at the same time aka bude ne yasa ta mike zaune
da sauri don bata san bata kulle kofar ba, hada ido suka yi da new Housemate
dinta, yayi dropping ledan hannunsa ya jingina jikin kofar dakin ya rungume
hannu yana kallonta da kyau, calmly yace "Like seriously, Namiji kika
kwanta kike yi ma kuka?" Ta wani hade rai ta kauda kanta zuwa wani
direction din daban, how did he even know she understands Hausa?? yana juya
counter din hannunsa as if counting his words yace "It's... funny" Ta
juya ta kallesa har sannan fuskarta a daure tace "Excuse you, why will u
barge into someone else's bedroom just like that?" Ya daga kafadarsa yace
"Zan yi shisshigi in baki shawara ni dai, run for ur dear life cause u are
dating a monster as a boyfriend" Yana kai wa nan ya juya ya fita daga
dakin closing the door behind him, Khaleesat ta dafe kanta da yayi mata nauyi,
daga karshe ta mike ta kulle dakinta da makulli sannan ta shiga bandaki, karfe
sha biyu da yan mintuna ta gama shiryawa don wanka tayi, kallon ledan da ya
ajiye mata tayi ta dauke kai sannan ta nufi kofa ta bude ta fita, satan kallon
kofar bedroom dinsa tayi ta karasa living room, tana tafiya a hankali ta tafi
kofar parlon ta murda taji a kulle an sa makulli, leka windon parlorn tayi taga
babu motarsa a garage alamar ya fita, tana tafiya a hankali ta shiga kitchen,
ta jingina da kofa tana kallon Cereal da bowl din da ta dauko daxu an ajiyesu
kan cabinet din kitchen din, juyawa tayi ta fita daga kitchen din ta koma
dakinta, ledan da ya ajiye mata ta dauka ta zauna kan kujeran dake dakin tana
duba abinda ke cikin ledan, Breakfast Sandwiches ne sai fresh fruit smoothie a
ledan.....
07087865788✍π»
[4/30, 5:36 PM] khaleesat Haiydar π✍️:
https://chat.whatsapp.com/KBwGIidDZY683SzzudJ0zc
✨✨ HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
3.....
Bayan magrib Khaleesat ta fito living room saboda yunwan da
take ji, har sannan bata ji alamar House mate din nata ya dawo gidan ba, gaba
daya haka ta wuni ranan babu walwala, all of a sudden yau ta ji a zuciyarta ta
fara gajiya da attitude din Abdul da abubuwan da yake mata, da ta tuna
Housemate dinta overheard all her conversation with Abdul da kuma maganar da ya
gaya mata sai taji wani bakin ciki da takaici ya tokareta at the same time tana
wishing that never happened, zaunawa tayi kan kujera ta jinginar da kanta jikin
kujeran ta afka duniyar tunanin rayuwarta, after a while ta sauke ajiyar zuciya
ta mike tana tafiya a hankali ta shiga kitchen tana tunanin abinda zata dafa ta
ci, absently ta fara wanke few utensils din da yayi amfani da shi ya bari a sink
sannan ta kunna gas, stir fry pasta ta girka, bayan ta gama ta debi kadan da
zata ci ta fita daga kitchen din, dai dai corridor din dakunan ta kusa cin karo
da House mate din nata, a firgice tace "Innalillahi...." Sai kuma
tayi shiru ta hade rai, ya koma gefe yana kallonta, har ranta taji tsoro don
bata san yana gidan ba amma tayi pretending ta hanyar daure fuska, ya daga
kafada ya bar wajen ta bi sa da kallon gefen ido.... reading nook dake cikin
living room din ta ga ya nufa yana kwashe takardunsa dake kan table, ta dauke
kanta ta shiga cikin dakinta ta kulle da makulli, karfe takwas da few minutes
ta gama duk abinda zata yi ta dauro alwala sannan kwanta don gobe Monday tana
da aji da safe, tana lumshe ido bacci ya dauketa. Cikin bacci Khaleesat taji ana
knocking kofar dakinta, ta mike zaune da kyar tana murza ido ta jawo wayarta
tana kallon agogo taga karfe goma saura minti biyar, kallon kofar tayi da
mamakin dalilin da yasa yake mata knocking by this time, can dai ta daure fuska
tace "Waye wannan?" Taji yace "I could use ur help if u don't
mind" Bluntly tace "I beg ur Pardon?" A takaice yace "Nayi
misplacing makullina again" Da farko rasa ma me zata ce masa tayi don
mamaki, she was mute for almost a minutes, taji yace "Hello" Sosai ta
hade rai tace "I don't understand kayi misplacing makullin ka?" Yace
"Look, ni fita zan yi yanzu idan na fita sai ki kulle gidan" Bata san
sanda tace "Idan fita zaka yi ka fita mana, me yasa zaka tambayeni
makulli? ko makullinmu a hade yake?" Shiru yayi at first, sai kuma yace
"Ta yaya zan fita nace maki ban ga makullin kofa ba" Tace "But
our keys are separate isn't it?" Yace "Sai yanzu da kika fada na sani
ai, fito ki bude min kofa zan fita" Wani bakin ciki taji ya tokareta, yace
"I am waiting at the parlor" Bata tanka sa ba, can tayi tsaki ta
sauka daga kan gadonta ta dau hijab ta sa, ta bude handbag dinta ta dau
makullinta ta nufi kofar dakin, fuskarta a daure ta bude ta fito ta karasa
living room ta gansa tsaye bakin kofar parlon yana jiranta, ko kallonsa bata yi
ba kamar yanda shi ma din wayarsa yake dannawa bai kalli inda take ba, ta
karasa ta bude kofar parlon da makullin hannunta tace "You weren't given a
needle as key da zai dinga Ιata kullum, and i shouldn't be responsible always
for someone else carelessness" Shi dai bai ce mata komai ba ya fita
without looking at her yace "Na zata ai needle aka bani Housemate" Da
ido ta bi sa har ya isa inda motarsa take, wato godiyar da zai mata kenan? Ta
gyada kai ta kulle kofar parlon a ranta kuma tayi vow bazata sake masa amfani
da makullinta ba sai dai kar ya fita, banda ma rainin hankali me yasa baya
misplacing makullin motarsa sai na gida, next time sai dai ya fasa zuwa inda za
shi don bazata sake sharing key dinta da shi ba, fuska daure ta koma cikin
parlor, sai kuma ta tsaya tana kallon plate din da ya ci abinci ya bari a
parlon da container din soft drink ga goran ruwa, tsabar mamaki bata san sanda
ta nemi waje ta zauna ba, is this guy okay? After fetching her food without
asking for permission he still have the mind to leave the plate for her at the
parlor, anyway... she believe he didn't leave it for her, he left it for
himself instead, don ko sati daya zai yi bai dawo gidan ba zai dawo ya tarar da
plate din at that same spot don bazata daukesa ba, tashi tayi ta tafi daki fuskarta
a daure. Da safe Khaleesat ta gama shirin fita makaranta, har a lkcn bata dauke
plate din da ya bari a parlon ba, amma fa zuciyarta kawai ta kai nesa don ta
tsani ganin abu ba inda ya kamata ba, zata kai cup din da ta sha shayi kitchen
taji ta taka makulli a kan ash carpet din parlon, dukawa tayi ta dau makullin
tana kallo taga nasa ne, he is just careless, tabe baki tayi ta mike ta ajiye
makullin nan kan kujera, ta kalli plate din jiya da ya bari, tsaki tayi ta
dauke tare da gwangwanin soft drink din da na ruwa, ta hada da cup din hannunta
ta tafi kitchen, bayan Ιan lokaci ta dawo parlor ta dauki handbag dinta tana
duba wayarta, ganin Lyft din da tayi order ya kusa isowa ta nufi kofa ta fita.
Wajen karfe sha biyu Khaleesat na zaune tare da Safiyyah warce shigowarta
makarantar kenan, Khaleesat na kallonta tace "Kun sha birthday"
Safiyyah tace "Oho dai tunda ke baki je ba, yau me ku ka yi a aji?"
Khaleesat tace "Nothing much" Safiyyah ta bude handbag dinta ta ciro
cake tana mika ma Khaleesat tace "Gashi ba don halin ki ba" Khaleesat
tayi murmushi ta amsa tace "Nagode" Safiyyah tace "Kun yi waya
da Abdallan ne?" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "Sophie me
kika ce masa ta chat?" Safiyyah ta dau wayarta tayi unlocking cikin few
seconds ta shiga DM din Abdul sannan ta mika ma Khaleesat wayar, Khaleesat ta
amsa tana duba chat din, it was nothing worth taking personal Safiyyah ta gaya
masa a chat din, Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba tana kallon wayar
hannunta, Safiyyah tace "Me yace maki halan?" Khaleesat ta mika mata
wayarta tace "Nothing, kawai yace min kin masa magana" Safiyyah ta
tabe baki tace "Kin dai ga yanda yake amsa min chat din ma kamar wani Ιan
sarki, wallahi Abdallah bai yi deserving dinki ba, u are too good to be Abdul's
or to end up with him, Allah ya maki sauyi cikin ruwan sanyi ya kawo maki
mafita" a hankali Khaleesat tace "Ki tashi mu je aji" Safiyyah
tace "Oh baza ki ce Ameen ba??" Murmushi Khaleesat tayi tace
"Wani mafita kenan Safiyyah? Cewa zaki yi Allah ya canza min halayyarsa
kawai...." Safiyyah ta tabe baki ta mike tace "Mu je" Khaleesat
ta mike suka bar wajen a tare... Khaleesat na sauka Uber din da ya dawo da ita
gida ta nufi apartment dinta, dai dai sanda Co-tenant dinta ya fito daga cikin
motarsa dake inda aka tanadar domin parking, sau daya ta kallesa ta dauke kai
tana ci gaba da tafiyarta toward their apartment, ya bi bayanta yace "I've
waited all day long, i forgot some paperwork a cikin gidan gashi zanyi
Submitting tun daxu" Ba tare da ta juyo ba tana ci gaba da tafiya tace
"Serves you right" Kallonta yake yana biye da ita, ta ciro makulli a
jakarta ta bude kofar ta zare makullinta sannan tayi shigewarta ciki ta nufi
dakinta da makullin... Bayan Khaleesat ta idar da sallah ta sauya kaya ta fito
parlor don daura girki, bata gansa a parlon ba, kuma bata ji alamar ya shiga
dakinsa ba, ta nufi tagar living room din tana leka parking space, ganin babu
motarsa ta karasa gun kofa ta murda taji a kulle, kallon inda ta ajiye
makullinsa daxu da safe tayi taga ya gani har ya dauke, wucewarta tayi zuwa
kitchen. Wajen karfe tara na dare Khaleesat ta gama karatun da take ta jawo
wayarta ta bude WhatsApp dinta don ganin ko Neighbor dinsu Aunty Sha'awa tayi
replying sakon da ta tura mata amma sai taga bata yi reply ba har sannan kuma
ta bude message din, ajiye wayar tayi ta mike ta dauke darduman da take zaune
kai, ta dau hijab ta saka sannan ta fito parlor zata debi abinci, Zaune taga
House mate dinta a parlon yana operating laptop dinsa, without looking at him
ta tafi kitchen, after some minutes ta fito, ya daga kai yana dubanta yace
"Can i have some of ur food if you don't mind?" Mamaki ma ya bata,
har da baza ta tanka sa ba sai kuma ta tsaya tace "Duk na baya da kake
diba gaya min kake halan?" Ya Ιan buda ido yana gyada kai yace "Haka
ne kuma fa, i just decided to ask politely today" Bata sake bi ta kansa ba
tayi tafiyar ta daki, in har sai tace ya diba to ashe bazai ci ba. Washegari da
safe Khaleesat na kitchen tana ma kanta snacks da zata kai school don har yamma
suke da Lecture gashi suna da er jarabawan da za su yi ranan da safen,
Housemate dinta ne ya shigo parlon, tun jiya da daddare da ya fita sai a sannan
ya dawo gidan, har zai tafi dakinsa sai kuma ya tsaya yana kallon Handbag dinta
da makulli dake ajiye gefen jakar, karasawa yayi ya dau makullin sannan ya juya
ya fice daga parlon gaba daya closing the door gently ya kulle da key,
Khaleesat tafi minti sha biyar tana duba makullinta bayan ta fito daga kitchen,
tun daga dakinta har parlor zuwa kitchen babu inda bata duba ba amma bata ga
alamar makullin ba, she can't even tell ko ta fito da shi parlor, she was so
confuse gashi tayi latti, daki ta koma sai da ta birkice ko ina amma babu
alamar makullin, how comes will her keys disappear just like that, tunda ta
fara karatu a kasar bata taΙa misplacing makulli ba banda wani lkci da Safiyyah
ta yar mata guda daya, ko gyara dakin da ta birkita bata yi ba ta dawo parlor
looking so frustrated, tsaye tayi trying to calm her brain ko Allah zai sa ta
tuna inda ta ajiye keys din, ta Ιaga kai da sauri tana kallon kofar parlon jin
ana budewa, House mate dinta ne ya shigo living room din da wasu takardu a
hannunsa, sai da ya kulle kofar ya zare makullinsa sannan ya karasa cikin
living room din ya ajiye takardunsa kan kujera without looking at her yace
"Good morning Housemate...." Bai tsaya yaji amsarta ba yayi wucewarsa
daki yana cire jacket din jikinsa, Khaleesat ta bi sa da kallo har ya shige
daki ya kulle, zaunawa tayi gefen kujera ta dafe kanta da taji har ya fara
ciwo, yanzu ina ta jefar da mukullin nan for God sake gashi lokaci na ta
wucewa, after few minutes sai gashi ya sake dawowa parlon, har sannan bai yarda
ya kalli direction dinta ba, taga yayi wucewarsa kitchen ya fito rike da ruwan
gora ya sake komawa dakinsa ya kulle, wayarta dake jaka ne ya fara ring ta bude
jakar ta ciro wayar taga Safiyyah ce, dagawa tayi ta kai kunne Safiyyah tace
"Ya baki shigo schl ba har yanzu, duk latti na yau na riga ki shigowa
makaranta, ko kin manta muna da test ne" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya
tace "Ina sane Safiyyah" Safiyyah tace "Na fa ce akwai tutorial
da zaki min kafin mu shiga test din" a hankali Khaleesat tace "Zan
taho yanzu" Safiyyah tace "Don Allah ki taho, wallahi ba abinda na
sani a course din kema kin sani" Khaleesat ta ajiye wayar bayan Safiyyah
ta katse, agogon wayarta ta kafa ma ido, bayan wasu yan mintuna ta mike after
gathering courage to do what her mind is telling her, walking slowly ta nufi
dakinsa, tsaye tayi tana facing kofar, a hankali ta kai hannu kofar tayi
knocking tana turo baki, Yana jin knocking din ya kalli kofarsa, gyada kai yayi
letting out a grin, sai da ta sake knocking din sannan yace "Waye
wannan?" Exactly yanda take yawan fada, Shiru tayi bata ce komai ba ta
kara turo baki, ya mike ya tafi gun kofar ya bude yana kallonta daga sama har
kasa da alamar mamaki, tuni ta kauda kai, still keeping a surprise face yace
"Madam hope nothing??" Trying to sound a little polite tace "I
need you to open the door for me" ya gyara tsayuwa yace "I don't
understand, dama a hade makullinmu suke? Where is ur key?" A takaice tace
"It's fine, no long talk" Juyawa tayi zata bar wajen, yace "Ko
baki ga naki bane?" Ta wani kallesa tace "Banda haka ai da ban zo nan
nace ka bude min kofa ba" Yace "Ohh i see, does this mean u are
careless too?" Barin wajen tayi ta koma parlor ta zauna, ya gyada kai with
smile of satisfaction sannan ya koma daki ya dauko makullinsa ya fito, sai da
ya shigo parlon yace "Ta yaya ma zaki yi misplacing a whole bunch of key
sai kace allura, this is kind of weird" Daukar handbag dinta tayi ta nufi
kofar yana budewa ta fice daga parlon tayi wucewarta without turning her back,
ya gyada kai yace "Zaki dawo ai, zan ga ta inda zaki shigo gidan"
Kulle kofar parlon yayi still smiling, ko ba komai ya rama abinda ta masa jiya.
Safiyyah na kallon Khaleesat tace "To ko ya shige cikin Couch ne
makullin?" Khaleesat tace "Ta yaya zai shiga kujera?" Safiyyah
tace "Kuma har kitchen din kin duba?" Khaleesat tace "Babu inda
ban duba ba fa" Safiyyah tace "Toh kawai kiyi ma agent din gidan magana
su baki wani makullin mana" Khaleesat tace "Gani nake kamar dogon
process ne hakan, kuma ai biyu ne makullin kika yar min da daya shine na dauko
spare key din nake using, to shima gashi ban gansa ba yanzu" Safiyyah tace
"Kar ki wani damu kanki, makullin na nan zaki gansa, kawai kin mance inda
kika jefar ne, amma definitely it's either in ur room ko kuma parlor, yanzu
jira zaki yi sai sanda housemate dinki ya dawo ki koma gidan kenan?"
Khaleesat tace "Wani housemate? Shi da ba kwana ma yake a gidan ba, kuma
ba shi da exact time da yake zuwa" Safiyyah tace "Kai haba, to a ina
yake kwana?" Khaleesat ta zaro ido tace "Kin ji ki da wani tambaya,
ta yaya ni kuma zan sani? what is my business with him da zan san inda yake
kwana" Safiyyah tace "To kawai mu je gidanmu ki kwana" Khaleesat
tace "Kina ganin babu matsala hakan?" Safiyyah tace "Wani irin
matsala? To gidanta ne ko na ubanta da za a samu matsala? ta shi mu tafi
jare" Safiyyah na gaba Khaleesat na biye da ita a baya suka shigo parlor
da sallama, Surayya matar cousin brother din Safiyyah dake zaune parlorn ta
daga kai tana kallonsu, Safiyyah tace "Sannu da gida Mom Aslam"
Surayya ta ci gaba da danna wayar hannunta tace "Yauwa" Khaleesat ta
zauna kan kujera ta gaisheta, Surayya ta amsa without looking at her tana danna
wayarta, Safiyyah tace "Ai kin ganeta Mom Aslam, kawata ce kuma Coursemate
dita Khaleesat" Surayya tace "Ohk" Safiyyah tace "She will
be passing the night here, makullinta ne ya Ιata" Surayya ta daga wayarta
da ya fara ring ta kai kunne hade da amsa sallama ta mike ta bar masu parlon,
Safiyyah ta kalli Khaleesat tace "Tashi mu je ciki" Mikewa Khaleesat
tayi ta bi bayan Safiyyah zuwa dakinta, Safiyyah na idar da sallah ta canza
kayan jikinta tana kallon Khaleesat dake zaune saman darduma tace "Bari in
samar mana abinda za mu ci a kitchen" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata,
Safiyyah ta fita daga dakin... Khaleesat was so uncomfortable a gidan cause
it's a home that she is not welcome, ko daga irin tarban da aka mata tasan she
isn't welcome, karatun da take ta yi na boko ne ke while din mata lokaci,
Safiyyah kuwa tun da suka ci abinci take ta bacci har yanzu da magrib yayi,
Khaleesat tayi alwala sannan ta fito ta tasheta, bayan sun idar da sallah
Safiyyah tace "Bari in je in ga me waccan matar ta girka" Ita dai
Khaleesat bata ce komai ba tana ci gaba da azkar dinta, Safiyyah ta fita daga
parlon, Surayya na parlor tana ba yaronta Cereal da ta hada masa, Safiyyah ta
karasa parlon tace "Aslam yanzu ya tashi ne, ban gansa tun daxu ba"
Surayya tace "Ehh" Safiyyah ta Ιan masa wasa sannan ta wuce kitchen,
abinci ne iya cikinta taga Surayya ta ajiye mata a kitchen din, Safiyyah ta fi
minti biyu tsaye kitchen din tana kallon abincin, can tayi kwafa ta dau plate
ta juye ma Khaleesat kawai ita idan ya so ko cornflakes ne sai ta sha anjima,
ta fito kitchen din kenan sai ga Cousin brother dinta ya shigo parlor, gaishesa
tayi ta amshi ledan hannunsa yace "Leave it, kije ki ci abincin ki"
Tace "Ai ba nawa bane ba ma, kawata zan kai ma, ni sai dai in sha cornflakes
tunda abincin iya wannan ya rage" Surayya dai kallonta kawai take, Musty
yace "Wace kawarki?" Safiyyah tace "Khaleesat, she lost her
house key shine ta zo zata yi spending night din a nan" Musty yace
"Oh Allah sarki, ba ayi abincin da yawa bane?" Safiyyah ta karkace
masa plate din sosai tana nuna masa tace "Iyakarsa kenan aka bari a
kitchen, tun da rana muka dawo kuma" Musty yace "Ohk, me ku ke son ci
let me get it yanzu a restaurant" Safiyyah ta Ιan yi murmushi ta ajiye
plate din saman center table kusa da Surayya tace "Bari in tambayi
Khaleesar abinda zata ci" Surayya ta bi ta da wani kallo har ta shige
daki, Safiyyah na shiga dakin tace "Khaleesat ki fito ku gaisa da yaya
Musty nace masa kina nan" Khaleesat ta daga kai ta kalleta tace "Is
it necessary Safiyyah?" Safiyyah tace "Ban gane is it necessary ba,
yayana ne fa, kuma nace masa kina nan, ai ya kamata ki gaishesa dai ko"
Khaleesat tayi shiru, can ta mike suka fito daga dakin tare, tana tsaye daga
jikin kujera ta gaida Musty ba tare da ta kallesa sun hada ido ba, ya amsa da
fara'a yana kallonta, Surayya dai fuskarta babu yabo babu fallasa take tura ma
yaronta Cereal a hanci maimakon baki ba tare da ta sani ba, Khaleesat ce kadai
ta lura da hakan, Safiyyah na murmushi ta kalli Khaleesat tace "Wai yaya
yace me za mu ci zai fita yanzu ya siyo mana" Khaleesat taki cewa komai,
Safiyyah tayi fari da ido ta fara lissafo masa abubuwan da zai siyo masu,
Surayya ta ajiye bowl din Cereal din hannunta kan Centre table ta ciro Aslam
daga kekensa tace "Mu je in maka wanka Aslam" Daga haka ta bar parlon
tayi wucewarta daki, Khaleesat dai ta sunkuyar da kanta, Muryar Musty da taji
yana mata magana yasa ta daga kai ta kallesa, yace "Su kenan iya abinda
Safiyyah ta lissafo za a siyo maku Khaleesah?" Kai kawai Khaleesat ta
gyada masa, bayan nan ta juya ta koma dakin Safiyyah jiki a sanyaye.
07087865788✍π»
[5/1, 5:20 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨ HALYSAAH ✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
4.....
Khaleesat ta zauna gefen gadon dakin Safiyyah duk jikinta a
sanyaye, jawo wayarta tayi tana duba agogo taga karfe bakwai har da rabi, sam
bata ji zata iya kwana gidan nan ba, tasan probably yanzu House mate dinta na
gida, to ya ta iya? Hakan dai zata koma gidan tayi masa knocking, the thought
of this made her weak, shigowar Safiyyah dakin yasa ta daga kai, Safiyyah ta
rike haΙa tace "Kinsan kuwa shegiyar matar nan bata ajiye mana abinci ba,
ai ko sai ga yaya Musty kamar an jefosa kuma night shift fa yake yi wallahi,
kinga ko ba komai sai ta hadiyi zuciya ta mutu don bakin ciki yau, abincin da
na lissafo masa ko rabinsa baza mu iya ci ba kuma kwalelenta sai dai in har shi
yayi dubaran siyo mata nata daban, ban taΙa ganin me tsinannen hali kamar matar
nan ba tirr, ni ai na zata in mutum zai taho wata kasar barin baΖin halinsa
yake a gida, to ita dai da nata ta taho wallahi" Khaleesat tayi murmushin
karfin hali tace "Lallai kam, kinga ni kuma tafiya zan yi fa, da ma bai
siyo abincin ba, yanzu Housemate dina ya kirani yace he is back home"
Safiyyah ta bude baki da mamaki tana kallonta, can tace "Ban gane ba,
yaushe kika samu number Housemate dinki har ya kira ki? Wallahi ban yarda ba
kawai so kike ki tafi, bari ki ji in dai don Surayya ce nima fa zaman hakuri
nake da ita a gidan nan Khaleesat, mugun halinta bai da part 2, gwara kawai
kiyi zamanki in ma shekara zaki yi a nan babu yanda ta iya tunda ba gidan
ubanta bane kuma warmly Ya Musty zai yi welcoming din ki" Khaleesat tace
"Sophie ni fa tunda Housemate dina ya dawo bazan kwana a gidan nan ba,
dama bani da kayan da zan canza sannan na ma manta na bar kaya a washing
machine kin ga bani kadai bace a gidan, may be zai yi laundry shi ma"
Safiyyah ta hade rai tace "A takaice me kike nufi kenan? Kina ji ina
lissafa ma Ya Mustapha abinda zai siyo mana don walakanci ki ce ke zaki tafi?
shima ai bazai ji dadi ba idan ya dawo da abincin yaga kin tafi kuma saboda ke
ya fita ya siyo don in dan ta nice sai dai yunwan ya kasheni in bai ga dama
ba" Khaleesat ta Ιan yi murmushi tace "Zan jira ya dawo, sai in tafi
da abincin gida kawai" Safiyyah da har ranta ya Ιaci tayi mata banza ta
tafi ta dau wayarta tana dannawa, Khaleesat dai bata sake cewa komai ba, komin
fushin Safiyyah ita kam baza ta kwana gidan nan ba, after a while Ya Mustapha
ya dawo gidan da abincin da ya siyo masu, Safiyyah ta mike ta nufi kofa bayan
ya kirata a waya, Khaleesat ta bi ta da kallo har ta fita sannan tayi murmushi,
Safiyyah ta karasa dinning table ta dau abincin da Cousin din nata ya ajiye
masu ta koma daki, iya wanda zata ci ta cire ta bar ma Khaleesat duk abincin,
Khaleesat tace "Ya zanyi da abincin nan me yawa Sophie?" Ba tare da
Safiyyah ta kalleta ba tace "Wannan kuma ke kika sani" Khaleesat bata
son jan maganar yayi tsayi kawai ta mike ta dau veil dinta da handbag sannan ta
dau ledan abincin tace "Sai mun hadu gobe, thank you so much dear"
Safiyyah tace "Kinyi order din ride ne?" Khaleesat tace
"Sure" Mikewa Safiyyah tayi suka fito dakin a tare, dai dai fitowar
Mustapha parlor shi ma, yana kallonsu da mamaki yace "Ya aka yi
kuma?" Safiyyah ta langwabar da kai tace "Her Housemate is back,
shine kawai zata tafi gida wai" Yace "Isn't it late?" Safiyyah
ta kyabe baki tace "Nima dai haka nace mata" Ya kalli Khaleesat da ta
sunkuyar da kanta, yace "Kiyi hakuri ki bari gobe mana Khaleesah, yanzu ai
dare yayi...." Khaleesat ta Ιan yi murmushi ta dago kai cikin sanyin murya
tace "Akwai abinda nake son zan yi ne idan na koma gida" Mustapha ya
daga kafada yace "While, if you insist...." Ta gyada masa kai tace
"Nagode" Safiyyah ta wani harare ta, Mustapha yace "Zan koma
aiki ne dama, mu je sai inyi dropping din ki ko" Khaleesat bata yi
expecting offer din nasa ba, ta Ιan kallesa tace "Na riga nayi order din
Lyft ai...." Safiyyah ta mata wani kallo tace "Haka kuma you can
cancel it ai ko...." Kasa cewa komai Khaleesat tayi, lkci daya ta zama
uncomfortable, Mustapha dai kallonta kawai yake, after few seconds a hankali
tace "Ohk" in response to Safiyyah, Kofa Mustapha ya nufa, Safiyyah
tayi kasa da murya tana kallonta tace "Ke in zaki saki jiki ki saki jiki,
a ko da yaushe sai kin nuna ke er.... Ya ma sunan wannan unguwan naku a
kano?" Khaleesat ta dinga kallonta, can ta juya ta nufi kofa tana tafiya
slowly, Safiyyah ta fara dariya kasa kasa tace "Good night
girlfriend" Ko tankata Khaleesat bata yi ba. Yana zaune cikin motarsa yana
jiranta har ta karaso, ta bude gaban motar ta shiga, sai kallon entrance din
gidan take tana fatan kar matarsa ta fito ta gansu, ya tada motar suka bar
garage din, sai a sannan ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tayi fastening seat
belt dinta a ranta ta dau alwashin wannan shine zuwanta na karshe gidansu
Safiyyah, bayan sun hau saman hanya taji yace "Where do u stay?"
Idonta na kan titi ta gaya masa, yace "Co-living kike yi kenan?" Tace
"Um" Yace "Menene yasa baki dawo ku zauna gidana tare da
Safiyyah ba instead of living alone with a stranger?" Ko rufe baki bai yi
ba tace "Ai yawanci ni kadai ce a gidan, my Housemate is not always
around" Yace "Ok then" After almost a minute yace "Kema er
kano ce?" Tace "Um" Yace "Wani anguwa?" Tayi shiru,
sai kuma ta Ιan kallesa ta gefen ido taga kallonta yake at the same time yana
tuki, ta sauke idonta kasa ta gaya masa, she is so uncomfortable with him, Yana
gyada kai yace "Ohk, i am also from kano, Sharada to be precise" Ita
dai tayi shiru bata ce komai ba, cikin minti 13 ya kawota gida, ya juya yana
kallonta bayan yayi parking, daukar ledan abincin tayi tace "Nagode sosai,
Allah ya saka da alkhairi" Wayarsa taga ya mika mata, ta daga kai ta
kallesa, yace "Ki sa min digit dinki sai mu dinga gaisawa, in kina bukatar
wani abu kuma feel free to ask me anytime" Khaleesat ta sauke idonta, ita
da ta sani babu abinda zai kai ta gidansa yau, da kawai dawowarta tayi ta zauna
bakin apartment dinta ta jira har sanda Housemate dinta ya ga daman dawowa ya
bude mata kofa, muryarsa ya dawo da ita duniyar tunanin da ta tafi ta daga kai
da sauri ta kallesa, bata ma san me yace ba taga dae yana kallonta, da kyar
tayi stretching hannu ta amshi wayar ta sa masa digit din nata, yayi dialing,
ita dai kanta na kasa, wayarta dake cikin jaka ya fara vibrate, yace "Kiyi
saving nawa digit din" Tace "Um" Yace "Good night, take
care Khaleesah" Tayi karfin halin cewa "Nagode" Daga haka ta
bude motar ta sauka, kallon window din kitchen na apartment dinta tayi ganin
wuta a kunne, sannan taga mota a Garage, she felt relieved sanin cewar her
Housemate is around, ta zaga zuwa gaban apartment din tana jin sanyi na
shigarta sosai don sanyi ya fara shigowa kasar, knocking din kofar parlor tayi
gently, sai da ta kwankwasa sau uku sannan taji muryarsa yace "Who is
there?" Ta kauda kai a takaice tace "Somebody" Yace
"Somebody? I am not expecting somebody this late" Ta wani hade rai
tace "Ni ka bude min kofa in shiga gida" Yace "Ke wa zan bude ma
kofa?" Kin cewa komai tayi cause she is already provoke, yace "Ohk
then, i am going back to my room after all i am not a door keeper" Tana
jin haka a fusace tace "Don Allah ka bude min" Yace "Ke
wa?" Tace "Ban gane ni wa ba?" Yace "Ohh, tsawa ma kike
min?" Ta kara marairaicewa tace "Don Allah ka bude mana" Yace
"To ai ni ban san wacece ba, baki da suna ne?" Shiru tayi tana kallon
kofar kamar zata fashe da kuka, Yace "Ke zan fa yi tafiyata daki in baza
ki fadi sunanki in san wa zan bude ma kofata ba cikin daren nan" Ta sauke
idonta kasa, after a few seconds ta dake tace "Khaleesat" Yace
"Halysaah..." Wani harara ta zabga ma kofar, Kamar yana counting
harufan sunan yace "Ha.. lee...saah" A fusace kamar zata yi kuka tace
"Sanyi fa nake ji ka ki bude min kofa, ko don ba kai bane tsaye cikin
sanyin?" Bude kofar yayi yace "Baki san da sanyin ba kika je kika yi
dare a titi?" Ko kallonsa bata yi ba ta kusa bangajesa ta shige parlon
fuskarta a murtuke, yace "Wajen saurayinki kika tafi kenan kika yi dare, naga
ma shi ya ajiye ki a mota, Allah sa ba me sa ki kukan nan bane dai" Direct
dakinta ta nufa without even looking at him abinda ya fada na sinking zuwa
cikin kanta, ya bi ta da kallo yace "Ok.... ga Door keeper dinki ya bude
maki kofa ko? Tomorrow is another day, better look for ur lost key in ba so
kike ki kwana a waje ba next time" Tuni ta bude kofar dakinta tayi
shigewarta ta sa makulli tare da jan dogon tsaki. Da safe tunda Khaleesat ta
tashi take zaune tana tunanin how today will be like, taje schl din ne ko ta
hakura kawai tunda bata da makulli yanzu, zaro ido tayi bayan ta tuna lecture
din da za su yi ranan, she just can't miss that class don course din is a bit
complicated, mikewa tayi ta shiga bandaki, wajen karfe tara ta fito parlor
hoping house mate dinta bai fita ba, don jiya wajen karfe sha biyu da rabi na
dare ta fito don saka abincin da bata iya ta ci ba a fridge ta gansa kwance a
parlor yana bacci, har ta gama abinda zata yi a kitchen ta fito bai farka ba,
tun zuwansa gidan ranan ne rana na biyu da taga ya kwana a gidan, babu kowa
parlorn ta karasa kusa da tagan parlon tana leka Garage ko zata ga motarsa taga
motar na nan alamar he is around, ajiyar zuciya ta sauke don da ya fita shkkn
babu tafiyarta makaranta kenan, kitchen ta tafi ta hado shayi ta debi cookies ta
dawo parlon, har ta gama breakfast bai fito parlor ba, sai kallon agogo take
don goma ta kusa gashi bata son tayi latti, kuma ita dai bazata taΙa masa
maganar ya bude mata kofa zata fita ba, goma saura minti goma ya fito parlorn,
ita dai bata dago kanta ba tana ci gaba da danna wayarta, taji yace "Good
Morning, Halysaah" Without looking at him tana ci gaba da danna wayarta
kamar tana ma kanta magana tace "Ok" Ta gefen ido ta bi sa da kallo
ganin ya nufi kofa ta mike ta bi bayansa, yana lura da ta biyosa sai ya fasa
bude kofar, ya juya yana kallonta keeping a serious face yace "Me ya
faru?" Ta kauda kai taki cewa komai, mayar da makullin yayi aljihunsa zai
bar wajen ta wani kallesa tace "Ni dai ka bude min kofa zan tafi
makaranta" Yana gyada kai yace "Ohhh, ohk kin boye makullinki ne don
in zama door keeper dinki dama?" Taki kallonsa don bata ma san me zata ce
masa ba, ganin da gaske barin wajen zai yi ta marairaice tace "Makaranta
zan tafi fa" Ya juyo yace "Be a good girl and beg politely
first....." Shiru tayi tana bin sa da kallo har ya koma cikin parlor ya
zauna kan kujera, Ta dake da kyar tace "Please ka bude min. i am going to
school" Yace "Ban ji ba" Takaici yasa ta dauke kai taji ranta ya
kara Ιaci, ganin lokacinta kawai take Ιatawa ta sake juyowa trying to be calm
tace "Plss ka bude min kofa i am going to school" Ζan murmushi yayi
ya mike ya dawo bakin kofar ya ciro makullin a aljihunsa yace "Never knew
u can be this Obedient" Ita dai bata kallesa ba, ya bude kofar yace
"In kika sake yin dare baza ki shigo gidan nan ba sai dai ki kwana bakin
Ζofa ko kuma a Garage..." Bata tankasa ba ta fice daga parlon with
annoyance almost brushing his shoulders, ya bude baki yana bin ta da kallon
mamaki yace "Ohh, is this ur thank you??" Tuni har ta kusa titi abun
ta, ta ja tsaki feeling so fed up with him. Bayan Khaleesat sun fito daga aji
Safiyyah tace "Kinsan me Khalee?" Khaleesat ta juya ta kalleta,
Safiyyah tayi dariya har da kyakyatawa tace "Wai Ya Musty ke tambayata ko
kina da saurayi" Sai da gaban Khaleesat ya fadi, Safiyya bata fasa dariyar
da take ba tace "Wallahi kuwa, he chatted me up yesternight wajen karfe
sha biyu, bari ma in nuna maki ki ga, ni ko nace masa baki da kowa
wallahi" Sai a sannan Khaleesat ta kalleta tace "Ban gane bani da kowa
ba Sophie?" Safiyyah tace "To kina da shi ne? To in kallon saurayinki
kike ma Abdul to ni wallahi kallon Ιan daba nake masa, ni dai nace ma Ya Musty
bakya kula kowa saboda karatu don haka baki da saurayi, kema kin dai san da Ya
Musty na da mugun hali da tuni na fesa maki ni da bakina baya shiru, ai ko don
wannan er banzar matar tasa zan so ya kara aure, kuma ace kawata ya aura huhuhu
za a ga rashin nasiha da jahilci wajena" Khaleesat ta mike tana gyara Veil
din jikinta tace "Zan tafi gida sai gobe" Safiyyah ta tsuke fuska
tace "Ban gane zaki tafi gida ba daga na kawo maki maganar arziki"
Khaleesat tace "Wallahi da na sani babu abinda zai sa in bi ki gida jiya
Safiyyah, haba fisabilillah, put ur self in the wife's shoe in kece aka ma haka
zaki ji dadi?" Safiyyah tace "Godforbid, her shoes will never size me
sef kafin in sa kafata ciki Khaleesat, ai ni bani da mugun hali kamar ta, kina
ga fa ko tsayawa ta amsa gaisuwarki bata yi ba ta wani Ζara waya a kunne ta
wuce daki ita er iska, sannan bari kiji jiya iya cikina ta ajiye abinci a
kitchen bayan nace mata nan zaki kwana kuma ta sani, ni dai wallahi in kika ce
baki son yayana nice kawai baki so, Ya Musty bai da wani aibu wallahi, ga
arziki ga Ilimi ga kyau, baza ma ki ce ya taΙa auren wata er iska ba wai ita
Surayya, Ιan saurayi da shi" Khaleesat tace "In matarsa kike son tura
ma haushi ai kema zaki iya aurensa tunda he is ur cousin brother kuma da aure
tsakanin ku" Daga haka Khaleesat ta bar wajen tayi wucewarta, Safiyyah
tace "Oho dai wallahi ce masa zan yi kin amince sai dai ki mutu, haka
kawai kin makala ma kanki Ιan daba kina kiransa da wanda zaki aura, ki auresa
ki ci uwar me da shi, wannan har duka sai ya dinga nakada maki babu me kwatarki
in ku ka yi aure" Khaleesat na isa gida taga babu motar Housemate dinta a
parking space, jingina tayi jikin entrance din apartment din nasu, gashi ta
gaji sosai ga yunwar da take ji, babu wanda ta saba da shi a Neighborhood din
balle ta shiga gidansa, balle su turawa basu yarda da hakan ba ma, ta kusa
twenty minute a tsaye sai ga motarsa ta hango, sunkuyar da kanta tayi har yayi
parking ya karaso kofar entrance din, gefe ta koma without looking at him, tun
kan ya karaso kofar apartment din ya sa hannu a aljihunsa yaji babu makullin,
ya Ιan bude ido still yana laluba duk aljihunsa, sai a sannan ta daga kai tana
kallonsa, juyawa yayi ya koma motarsa ta bi sa da ido, ya gama dube dubensa a
motar bai ga makullin ba, ai tana ganin yanda yake dube dube tasan kilan ya yar
da makullin, shikenan ta shiga uku, she is soo tired, har wani jiri take ji a
tsayen da take, dawowa yayi yana kallonta yace "Look Halysaah, i think i
left the key at where i am coming from" Ita dai bata ce komai ba kuma bata
bari ta hada ido da shi ba, yace "Ko zaki shiga apartment din Neighbor
dinmu kafin in dawo" Sunkuyar da kanta tayi still keeping mute, yace
"Or ain't you familiar with them?" A takaice tace "Eh" Yace
"Ok i will be back as soon as possible" Juyawa yayi ya koma gun
motarsa ta bi sa da wani kallo.... Khaleesat na ta tsaye har bayan wani minti
sha biyar sai gashi ya dawo, yana kallonta yace "Allah ya taimake ki na
gani" Wani kallo tayi masa wato ita Allah ya taimaka ma, yana bude kofar
tayi shigewarta ciki ta nufi dakinta ba tare da ta juya ba, sai da ta kwanta na
kusan minti sha biyar sannan ta mike a hankali ta shiga bandakinta, bayan
Khaleesat tayi wanka tayi sallah tana zaune kan darduma taji yayi knocking
kofar dakinta, kallon kofar take bata ce komai ba kuma bata amsa ba balle ta
tashi, taji yace "Halysaah" Bluntly tace "Me ya faru?" Jin
ya murda kofar dakin ta zaro ido ta mike tsaye da sauri tace "What?"
Tuni ta isa gun kofar ta bude tana masa kallon tuhuma, ledan hannunsa ya ajiye
mata yace "I got you food, naga kin yi laushi" Ta kalli ledan, ya
juya ya bar wajen ta bi sa da kallo har ya koma parlor, sauke idonta tayi,
bayan few seconds ta duka ta dau ledan ta juya ta koma dakin. Khaleesat ta bude
abincin da ya kawo mata ta fara ci kenan wayarta ya fara vibrate, mikewa tayi
ta bude handbag dinta ta ciro wayar, sosai gabanta ya fadi ganin Abdul ke kiran
ta, zaunawa tayi gefen gado tana kallon screen din wayar har sannan gabanta na
bugawa, kafin kiran ya katse tayi karfin halin dagawa ta sa handsfree sannan
tayi sallama cikin sanyin murya, maimakon ya amsa sai ji tayi yace "Wato
all this While ni kike jira in kiraki ko Khaleesat?" Ta sauke idonta a
hankali tace "To ai cewa kayi duk sanda kake son magana da ni zaka kirani
amma kar in sake in kira ka" Yace "Don nace kar ki kirani sai ki ki
kiran nawa? Me yasa baki reason ne?" A sanyaye tace "Kayi
hakuri" Yace "In ban hakura ba ya zan yi da ke? Ai saboda baki damu
da ni bane yasa kika zama comfortable without calling me all this while, ko da
bazan daga ba ai kamata yayi ki kira" Cikin sanyin murya tace "Kayi
hakuri" Yace "Yaushe za ku fara jarabawa?" Tace "Probably
nan da 6 to 7 weeks" Yace "I can't wait har zuwa nan da sati bakwai
ban gan ki ba Khaleesat, idan na samu lokaci zan shigo anytime from now in sha
Allah" Shiru Khaleesat tayi as if trying to process what he just said,
yace "Hello" Da sauri ta kifta ido tace "Na'am ina ji" Yace
"Me yasa kika yi shiru? Ko baki son in zo ne?" Tayi yake tace
"Aa ban yi shiru ba network ne, ban ji me kace ba" Yace "Ohk,
nace you should expect me any moment from now" A hankali tace "Toh
Allah ya kai mu" Yace "Ameen, me kike yi yanzu?" Tace
"Abinci nake ci" Yace "Ohk switch to video call" A hankali
tace "Toh" Mayafinta ta jawo sannan tayi yanda yace mata.
07087865788 for more info✍π»
[5/2, 5:50 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨ HALYSAAH ✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
5......
Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat ta fito parlor daga
dakinta, window ta nufa tana leka garage ta ga motar Housemate dinta alamar
yana gidan, juyawa tayi ta tafi kitchen zata yi disposing takeaway din da yayi
mata daxu, ta window din kitchen din ta hangosa zaune a Lawn din dake bayan
kitchen din waya Ζare a kunnensa alamar he is making a phone call, komawa baya
tayi don kar ya hangota ta window din kitchen din, ta ajiye ledan hannunta a
hankali ta juya ta fita daga kitchen din ta dawo parlor, tsaye tayi tana kallon
handle na kofar living room din, sai kuma ta tafi gun da ya ajiye takardun
karatunsa ta hau bincika Books din da sauri, har ta gama dube dubenta bata ga
abinda take nema ba, ta koma kitchen din tana kara lekansa, seeing he is still
on call ta dawo da sauri ta tafi corridor din dakunansu, tsaye tayi gabanta na
faduwa as if contemplating on whether to do what is on her mind or just forget
it, ganin she is just wasting time ta runtse idonta ta bude, sai kuma ta kai
hannu handle din kofar dakinsa a hankali ta bude ta shiga ciki zuciyarta na
bugawa, bin dakin that was neat and tidy ta fara yi da kallo kafin ta karasa
can ciki da sauri, har sannan tana kallon ko ina na dakin, ta ma rasa daga inda
zata fara duba abinda ta shigo nema, zagaye dakin ta fara yi tana dube dube
with confusion, daya wayarsa dake gefen gado yayi haske alamar shigowar sako,
kallon screen din wayar take yi ganin wani matashi kamarsa a shekaru ne a
fuskar wayar, ta juya ta kalli Trouser dinsa, gabanta na faduwa ta dauka ta kai
hannu aljihun wandon, Dollar ta ciro masu yawa tayi saurin ajiyesu gefen gado,
sannan ta duba daya aljihun, zaro ido tayi jin makulli da Counter a ciki, ta
ciro da sauri tana kallon makullin taga makullin kofar parlor ne, bata san
sanda tayi murmushi ba ta ajiye wandon a inda ta dauka sannan ta juya da sauri,
Ζamewa tayi a spot din da take ganinsa tsaye bakin kofar dakin ya rungume hannu
yana kallonta daga sama har kasa, kawai ta juya masa baya zuciyarta na bugawa
taji kamar Ζasa ya bude ta shige ta huta, after some seconds taji yace
"Sannu da aiki" Ita dai ta kasa juyowa, she felt so ashame at that
moment, she wish this never happened, sai juya makullin hannunta take with
shame, Calmly yace "Give me the key" Ta wani turo baki taki juyowa tace
"To ba amfani zan yi da shi ba" Yace "Dama in bana nan bincike
kike shigowa ki min a daki?" Bata san sanda ta juyo tana kallonsa babu ko
kiftawa ba jin abinda yace, sai kuma ta ajiye makullin a gefen gado ta nufi
kofa ta bi gefensa ta fice daga dakin ta shiga nata ta tura kofar, nan da nan
taji hawaye ya cika idonta ta zauna gefen gado, sai kuma ta Ιora kanta saman
pillow hawaye na sauka idonta har da shessheka. Karfe bakwai da few minutes
Khaleesat na zaune kan darduma, tun da ta idar da sallah take zaune wajen, da
ta tuna abinda Housemate din nata yace mata sai taji hawaye ya cika idonta,
gaba daya taji ta tsani zaman gidan, kuma bata jin zata iya ci gaba da zama as
far as he is here, ta yanke shawaran kawai zata gaya ma Abdul ya canza mata
gida kamar yanda Safiyyah ta bata shawara tun farko taki dauka, wayarta dake
gefen gado ta dauka jin ana kira, tana dubawa taga Mustapha ne ke kiranta,
ajiye wayar tayi gefenta taki dauka har ya katse, ya sake kira nan ma taki
dagawa, bayan Ιan lokaci aka sake kiranta kallon wayar tayi a bit fed up
thinking it's still Mustapha sai taga Abdul ne ke kiranta this time around, ta
jawo wayar a hankali tayi picking ta kai kunne, sallama tayi masa sannan ta
gaishesa, yace "Ya naji muryarki haka?" Tayi shiru tana tunanin ta
inda zata fara sanar masa the situation at hand, muryarsa ya dawo da ita
tunanin da take, a Ιan tsawace yace "Ke, baki ji na ne zaki min
shiru?" Kasa gaya masa tayi don bata ma san yanda zai fara daukar lamarin
ba barin yanda taki gaya masa tun farko, Ta Ιan yi yake tace "Ina jin ka,
kawai muna da wani jarabawa ne gobe, kuma ina jin ciwon kai, and I haven't
covered up, shi yasa nake damuwa" Yace "Na ce ki dena stressing kanki
da karatu, u are not dull to be studying as if ur life depends on it, read a
little and get enough rest, nasan za ki yi passing ko ma me za kuyi gobe"
Tana murmushin karfin hali a hankali tace "To" Yace "Kin ci
abinci ne?" Ta girgiza kai tace "Ban ci ba" yace "Ohk get
something to eat, idan kin gama sai ki kirani ina jiran ki" Tace
"Toh" Katse wayar yayi, ta bude WhatsApp dinta tana duba ko Neighbor
dinsu ta mata reply taga ta hau WhatsApp din amma still bata yi reply ba, yau
kwana uku kenan basu yi magana da Ummanta ba, Dialing din Number Sha'awa tayi
ta direct call, har ya katse ba a daga ba, sai da ta sake kira aka daga,
sallama Khaleesat tayi mata sannan ta gaisheta, Sha'awa ta amsa tace
"Lafiya lau Khaleesah, ya karatu?" Khaleesat tace "Alhamdulillah
ya gida ya su Kamilu?" Sha'awa tace "Duu lafiyansu lau wallahi"
Khaleesat tace "Su Ummanmu suna lafiya..." Sha'awa tace "Kwana
biyu kinyi magana ta wassap kinji shiru ko, to Ummanku dai bata da lafiya amma
da sauki yanzu" Nan da nan Khaleesat taji hankalinta ya tashi don dama tun
da taji shiru for days tasan ba lafiya ba, don ko bata yi ma Ummanta magana ba
ita zata mata ta wayar Sha'awa taji ko tana lafiya, Hankalinta a tashe tace
"Aunty Sha'awa tun yaushe?" Sha'awa tace "Ina jin yau kwana uku,
ai an ma ce kar a gaya maki, shi yasa ko mayar maki da sakon da kika yi ta
wassap din ma ban yi ba, yanzun ma kar ki wani ce zaki kira kowa kiyi ta mata
addu'a kawai Allah ya bata lafiya" Khaleesat taji hawaye na sakko mata ta
kasa cewa komai, Sha'awa tace "Wai daga ta tashi zata fito daki tayi
alwalan magariba shi ne fa ta yanke jiki ta fadi a bakin kofar dakin, duk kwanan
nan ina rabata da saka ma kanta damuwa tunda tasan matsalarta na hawan jini, to
kinga ai irin haka ake gudu gashi kuma ya faru, Farida ma ta taho daga legas
tun jiya ta iso, kar ki wani tada hankalinki don jikin da sauki" Cike da
karfin hali Khaleesat tace "Suna asibiti ne yanzu?" Sha'awa tace
"Wani asibiti? To har sai da Farida ta zo sannan ta kai ta asibiti jiya in
gaya maki, amma duk kwanakin nan tana gida gashi ko taΙata kika yi a daya barin
jikinta bata ji wai, ko magana ma in tayi sai kin sa kunne sosai zaki ji, ke
abun fa ba kyau, har yanzu hankalinmu a tashe yake, an dai ce kar a gaya maki
kar hankalinki ya tashi...." Khaleesat in hankalinta yayi dubu ya tashi a
lkcn, ta kalli Screen din wayarta jin kiran ya katse alamar katin ta ya kare, ajiye
wayar tayi ta fara rera kuka kamar an sanar mata da mutuwa... Har karfe goma na
dare Khaleesat ta kasa tashi daga kan darduman da take, sosai ta shiga damuwa
ba kadan ba, a inda take zaune Abdul ya kirata sau biyu amma ta kasa picking
call din nasa, karfe goma da rabi taji anyi knocking kofar dakinta, ta juya ta
kalli kofar tana share hawayen dake idonta amma bata tashi ba sai ma hade rai
da tayi, after a while ya sake knocking still dai bata tanka ba, sai kuma taji
yace "Assalamu alaikum" kawai ji tayi ya bude kofar dakin ta juya da
sauri daga inda take zaune suka hada ido, daga nan bakin kofar ya tsaya yana
kallonta, ita dai taki yarda ta sake hada ido da shi, ya karasa ciki ya tsaya
still leaving enough distance between them, calmly yace "Maganar da na
maki yasa kike kuka? But i was only pulling ur legs Halysaah, i am sorry about
that, was just joking" Wasu hawaye suka cika idonta sai kuma ta fara kuka,
bude ido yayi alamar mamaki sosai yana kallonta, can dai ya kwantar da murya
yace "Look, do not take my words serious Halysaah ni wasa nake maki
wallahi" Ta rufe fuskarta da Hijab din jikinta tana kuka a hankali, dukawa
yayi da mamaki sosai yana kallonta ya ma kasa cewa komai, after few seconds da
taji shiru ta Ιan bude fuskarta don tunaninta ya fita daga dakin, suna hada ido
ta daure fuska tace "Ni saboda kai nace nake kuka?" Yace "Toh
why are you crying?" Shiru tayi bata ce komai ba wasu sabbin hawayen na
cika idonta, Yace "Tell me Halysaah, what is making you cry?" Kamar
bazata ce komai ba sai kuma tace "My mother is sick" Yace
"Hasbunallah, what's wrong with her?" bata sake ce masa komai ba tana
goge idonta, After few seconds ya sauke ajiyar zuciya yace "Amma ai ba
kuka zaki zauna kina yi ba, addu'a zaki mata Allah ya bata lafiya" Nan ma
dai bata ce komai ba, ya mike yace "Allah ya bata lafiya" Sai a
sannan tace "Ameen" Yace "Are you going back home to check on
her?" Ta daga kai ta kallesa amma bata ce masa komai ba, yayi shiru shima,
can yace "Are you from kano?" Ta gyada masa kai, Yace "Allah
Ubangiji ya bata lafiya, and try getting something to eat for Dinner" Ta
sunkuyar da kanta kawai, ya juya ya fita daga dakin ya kullo mata kofar gently.
Wajen karfe sha biyu na dare Khaleesat na kwance taji ya sake knocking kofar
dakinta, juyawa tayi ta kalli kofar, bayan wasu yan sakwanni ta mike zaune tana
kallon kofar, sai da ya sake knocking sannan ta sauka daga saman gadon ta dau
hijab dinta ta saka ta nufi kofar ta bude, yace "Are you still
crying?" Ta hade rai ta girgiza kai without looking at him, yace "Ok
naga baki fito kinyi dinner ba and it's past 12, ki nemi abinda za ki ci kar ki
kwanta haka" Ita dai bata ce komai ba, yace "Hello" Daga kai
tayi ta kallesa tace "Naji" Yace "Good" Kullo kofar dakin
nata tayi ta nufi kitchen tana tafiya a hankali, sai da yaga ta shiga kitchen
din sannan ya shiga dakinta yana bin ko ina da kallo, after a while Khaleesat
ta fito daga kitchen din with a cup of tea and some cookies, tsaye ta gansa
corridor, bayan ta karaso yace "Kin ga nima Ummi na bata da lafiya amma
ban zauna ina kuka ba kamar yanda kika yi" Khaleesat bata kallesa ba ta
shige dakinta ta kulle kofa, tana gama shan shayin ta koma saman gado ta
kwanta, tasan yau da kyar ta iya bacci, she wish she can just see herself in
Nigeria, but how?? Wasu hawaye ne suka zubo idonta ta lumshe ido, after a while
ta jawo wayarta a hankali tayi dialing number Abdul bayan ta tuna ya kirata har
sau biyu daxu bata iya tayi picking ba, har kiran ya katse bai daga ba, ta sake
kiransa nan ma bai daga ba, tasan as usual yayi fushi kenan, ko uxuri bazai
mata ba, ajiye wayar tayi ta juya zuwa daya side din gadon. Washegari da safe
Khaleesat na zaune daki tana ta kokarin kiran Aunty Farida amma baya shiga, har
Sha'awa sai da ta kira ita ma wayarta baya shiga, ta rasa wa kuma zata kira, ta
kalli agogon wayarta dake nuna karfe goma sha daya ta ajiye wayar tayi tagumi,
tun daga daren jiya har yau bata da sukuni, ko schl din ma yau tasan bazata iya
zuwa ba, juyawa tayi jin knocking a kofar dakinta, tana dai zaune har sai da ya
kwankwasa kofar sau uku sannan ta sauka daga saman gado, walking slowly ta tafi
ta bude kofar, Yace "Good morning Halysaah, how was ur night?"
Without looking at him tace "Fine" Yace "Ya jikin Mama? Kun yi
communicating da su?" Kai kawai ta gyada masa bata ce komai ba kuma bata kallesa
ba, Paper da pen din hannunsa ya mika mata yace "Can i get ur Email
Address?" Ta daga kai ta kallesa da mamaki tace "I don't
understand" Yace "I mean ur Email Address" wayarsa ne ya fara
ring ya mika mata takardan da pen ya daga kiran sannan ya juya ya bar wajen,
ita dai ta bi sa da kallon mamaki, can ta juya ta koma daki ta ajiye takardan
da pen da ya bata, after some minutes sai gashi ya dawo yayi knocking yace
"Can i get the paper" Tasowa tayi ta bude kofar bayan ta dau pen da
takardan tace "Why are you asking for my Email Address?" Yace
"Ki dae rubuta ki bani" Shiru tayi, sai kuma ta jinginar da paper din
jikin kofa ta rubuta sannan ta mika masa ya amsa ya juya ya bar wajen, yana
fita da few minutes taji message ya shigo wayarta, ta dau wayar ganin E-mail ne
ya shigo ta bude, kallon Image din da ta gani as Email din ta dinga yi babu ko
kiftawa, she look shocked and confused at the same time, ta daga kai tana
kallon kofar dakinta babu ko kiftawa, dai dai sanda taji sallamarsa, kasa tashi
tayi daga inda take zaune, har sai da yayi knocking sau biyu tayi karfin halin
mikewa ta isa kofar ta bude tana kallonsa, Yace "I don't know if you find
this okay and a good idea" Ita dai bata fasa kallonsa ba looking
speechless, Yace "Hope they won't be Mad at this back home Halysaah?"
Jin bata basa amsa ba ya gyada kai yace "I guess it's a bad idea, I should
have ask for ur opinion first before doing this" Nan da nan hawaye ya cika
idonta ta sunkuyar da kanta, yace "Ok it's fine, i will get the ticket
cancelled" Daga kai tayi da kyar tana kallonsa hawaye na zuba idonta tace
"Thank you so much, i appreciate" Yace "Sure??" Ta gyada
masa kai, yace "Ohk, u can order a Lyft that will be taking u to the
airport later, ur flight is at 3pm today" Sauke idonta tayi cause she is
totally speechless, ya mika mata travelling documents dinta, amsa tayi cike da
mamakin how he got them, ya juya ya bar wajen, komawa cikin daki tayi ta kulle
kofar tana kallon inda take ajiye travelling doc din nata a dakin, did he come
to her room to check ne, to ai throughout babu inda taje, ta karasa gefen gado
har sannan jikinta a mugun sanyaye ta zauna, kallon screen din wayarta ta sake
yi tana kallon ticket din don ganin abun take kamar a mafarki, tana kara duba
taga tun daren jiya ya siya ticket din and kamar yanda yace the flight is by
3pm today, ta ma rasa ko farin ciki zata yi ko kuma wani reaction zata yi, amma
da ta tuna she is going back home to see her Mom which was her wish since
yesterday sai taji wani farin cikin da tunda take bata taΙa jin irinsa ba a
rayuwarta, 80% a cikin dari na damuwarta ya ragu cikin lokaci kankani, kallon
agogo tayi taga sha daya ya wuce sosai, the weakness she is been feeling since
this morning immediately vanished, mikewa tayi tana share hawayenta ta dau
medium box din kayanta.... Karfe biyu Khaleesat ta gama duk abinda take, har
sallan zuhur tayi, Lyft din da tayi ordering kawai take jira, tana zaune gefen
gado xuciyarta fal da tunani kala kala, babban burinta a yanzu bai wuce ta
ganta kusa da mahaifiyarta ba, in yaso koma me zai faru daga baya sai ya faru,
kallon wayarta tayi taga Safiyyah ce ke kiranta, tun daxu da safe ta kirata
amma sbda damuwar da take ciki ko picking bata iya tayi ba, Khaleesat ta daga
kiran ta kai kunne, Safiyyah tace "Khalee me yasa baki shigo schl ba yau?
Are you okay?" Khaleesat ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace
"Ummanmu ce bata da lafiya Sophie" Safiyyah tace "Subhanallah,
amma ya jikin yanzu?" Khaleesat tace "Da sauki" Safiyyah tace
"To Allah ya bata lafiya, plss nasan ki kar ki sa ma kanki damuwa kawata
addu'a kawai zaki dinga mata, nasan kilan kina nan kina ta kuka ko?"
Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah tace "In sha Allah in
mun gama lectures zan taho" Khaleesat tace "I am sorry ban kira ki na
gaya maki ba i will be leaving for Nigeria by 3pm" Da mamaki Safiyyah tace
"Zaki tafi Nigeria? Abdul ne ya siya maki flight ticket?" Khaleesat
ta sauke idonta tace "Uhm" Safiyyah tace "Is it that critical
Khaleesat?" Khaleesat tace "To da sauki dai, amma kinsan bazan samu
rest of mind ba in ban je ba" Safiyyah tace "To kina airport yanzu
ne?" Khaleesat tace "Aa ina jiran Lyft ne yanzu zan tafi"
Safiyyah tace "Toh shikenan mu hadu a can kawai sai mu yi sallama, bari in
nemi Uber nima" Khaleesat tace "To nagode Sophie" Da haka suka
gama wayar, Khaleesat ta mike bayan Lyft dinta ya iso, tana rike da trolley
dinta da handbag ta fito daga dakin ta kulle kofa, sanye take da Maroon Abaya
sai veil dinta, tana tafiya a hankali ta karaso cikin parlorn, ya ajiye wayar
da yake yace "Kin shirya?" Without looking at him tace "Eh"
yace "Kin yi ordering ride ai?" Tace "Eh" yace
"Ohk" Mikewa yayi ya ciro 1000 Dollars ya mika mata yace "Sort
ur self out with this" Girgiza masa kai tayi tace "Aa Nagode"
Yace "C'mon, u didn't beg me Halysaah" Ζin kallonsa tayi kuma taki
amsan kudin, ya dau handbag dinta da ta ajiye saman trolley din gabanta ya bude
zip din jakar ya sa mata kudin tare da wani farin takarda, ta Ιaga kai tana
kallonsa, ya koma ya zauna yace "Allah ya tsare, my regards to ur Mom and
everyone back home, Allah ya bata lafiya" Da kyar tace "Ameen
nagode" Yace "Zaki ga digit na rubuta maki a takarda, idan kun sauka
Airport sai ki kira number kice masa kun sauka" Ta kasa cewa komai, after
few seconds ta dau handbag dinta cikin sanyin murya tace "Nagode "
Yace "U are welcome, wishing u a Safe trip" Tana jan trolley dinta a
hankali ta nufi kofa, tana bude kofar ta fita ta daga kai tana kallonsa taga
Idonsa na kan wayarsa da yake dannawa, kulle kofar parlon tayi, taga Lyft din
dake jiranta ta nufi wajensa. A Airport Khaleesat suka hadu da Safiyyah,
Safiyyah na rike da hannunta tace "Tun yaushe ne Umman bata da
lafiya?" Khaleesat tace "Jiya Aunty sha'awa ke gaya min"
Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "To Allah Ubangiji ya bata
lafiya" Khaleesat tace "Ameen" Safiyyah tace "Lallai Abdul
ya fara hankali da yayi tunanin biya maki jirgi kije ki duba Umma, nayi mamaki
sosai wallahi" Khaleesat ta Ιan yi murmushi da iyakarsa lips, Safiyyah
tace "Yanzu kwana nawa za ki yi?" Khaleesat tayi shiru at first, sai
kuma tace "Sai dai naje tukunna in sha Allah" Safiyyah tace "Toh
Allah ya kai ku lafiya, don Allah ki gaida min Umma da jiki" Safiyyah na
fadin haka ta jawo handbag din Khaleesat ta saka mata dala dari tace "Plss
manage this kawata" Khaleesat ta Ιan bude baki tace "Haba meye haka
Sophie" Sophie bata tsaya ta saurareta ba ta daga mata hannu tana murmushi
ta bar ta tsaye wajen, Khaleesat dai ta bi ta da kallo. Khaleesat was more than
shock bayan ta amshi boarding pass dinta ganin ticket din Business Class ya
siya mata, Business class fa? Kikkifta ido tayi ta sake kallon ticket din sosai
to confirm, taga Business class din dai ne still, sosai jikinta yayi sanyi,
tana jan kafa da kyar ta shiga jirgin, this is the first time she will be
traveling Business class, wata Flight Attendant that gave her all the maximum
attention ta yi leading dinta har zuwa Seat dinta a cikin jirgin da fara'a tana
welcoming dinta, bayan wani Ιan lokaci jirgin ya tashi, Khaleesat ta ajiye
Amenity kit da aka bata ko duba abinda ke ciki bata yi ba tana bin ko ina na
Business class din da ido, the Flight from Baltimore Washington International
to Amsterdam Schiphol Airport in North Holland for Layover was smooth and
comfortable, duk zuwanta Amurka bata taΙa tafiya feeling so comfortable like
this ba, bayan few hours aka sauya masu jirgi zuwa Nigeria a nan North Holland,
Khaleesat tayi shiru da mamaki jin announcement na cewar Lagos Nigeria jirgin
ya nufa, ticket dinta ta sake dubawa taga ashe haka ne a jiki, bayan tafiyar
kusan awa bakwai jirgin nasu ya sauka a MMI Airport Lagos.
[5/3, 6:15 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
6.....
Bayan Khaleesat ta dau trolley dinta a cikin airport after
going through custom ta tsaya cikin airport din tana tunanin yanda zata yi
cause karfe shidda saura ne na asuba, should she check for available flight to
Kano? To nawa ne ma a account dinta before she think of doing so, ko dai kawai
ta tafi Motor park ta hau mota zuwa kano, dollars din da Housemate dinta ya
bata ne ya fado mata a rai don gaba daya ta ma mance, ta bude handbag dinta ta
ciro kudin tana kallo, takardan da ya saka mata hade da kudin a jaka ya fadi
kasa, ta duka ta dau takardan tana kallon numbers din jiki sai kuma ta mayar
cikin jaka tare da Dollars din, masallacin dake cikin Murtala Muhammad
International airport ta tafi don yin sallan asuba, tana ta zaune cikin
masallacin bayan ta idar da sallah tana azkar dinta, can ta ciro wayarta a
handbag ta duba agogo taga karfe bakwai da minti goma, dollars din jakar ta
sake cirowa ta kirga taga dala dubu ce, kallon kudin ta dinga yi jiki a sanyaye
don bata yi tunanin har haka ya bata ba, ta dau white paper din dake dauke da
digit tana tunanin to ko digit dinsa ne wannan din, kati ta siya ta Ussd sannan
tayi dialing number a wayarta, sai da ya kusa katsewa aka daga, daga daya side
din aka yi sallama ta amsa, amma sai taji kamar ba muryarsa bane, ta dai ce
"Ina kwana?" Yace "Hajiya ko kece kika taho daga America?"
Tace "Eh" Yace "To barka da isowa Hajiya, ina ta sauraren kiran
naki dama tun daxu, kina cikin airport din ne yanzu?" Tace "Eh"
Yace "Ohk to gani nan tahowa ba da dadewa ba in sha Allah" Bayan ya
katse wayar ta kalli screen dinta, to waye kuma wannan, maida kudin tayi jaka
ta ciro nose mask dinta ta saka sannan ta mike ta fito daga Masallacin da
trolley dinta with handbag, bayan wasu mintoci sai gashi ya sake kiranta, ta
fito outside of the airport, yana hangota ya nufota ya gaisheta da ladabi har
da bowing kansa yace "Ya hanya Hajiya?" Ta sauke idonta tace
"Lafiya Alhamdulillah" With respect yace "Ga mota can Hajiya,
zaki je hotel ki huta zuwa karfe daya na rana don Flight dinki zuwa kano na
karfe Biyu ne in sha Allah..." Khaleesat was speechless ta dinga kallonsa
babu ko kiftawa cike da mamaki, can kuma ta kalli lafiyayyen motar da ya nuna
nata, tuni ya karasa ya amshi trolley dinta ya tafi ya bude booth ya saka,
sannan ya bude mata bayan mota yace "Bismillah Hajiya" Sauke idonta
tayi kasa taji kafafuwanta sun mata nauyi amma a haka tana tafiya a hankali ta
tafi ta shiga back seat sannan ya kulle motar, ya zaga ya shiga driver seat,
Hotel me tsada sosai that isn't far away from the airport ya kai ta, sai da ya
tabbatar tayi check in har zuwa dakinta sannan ya bar hotel din, tana shiga
babu jimawa wata ma'aikaciyar hotel din ta kawo mata lafiyayyen Breakfast, ita
dai Khaleesat ba um bare um um, gaba daya kanta ya gama kullewa, tashi tayi ta
bude trolley dinta ta dau Shower gel zata yi wanka. Khaleesat na bacci wajen
karfe daya da minti ashirin vibration din wayarta ya tasheta, ta jawo wayar a
hankali tana duba me kiranta taga mutumin da ya kawota Hotel ne, ta mike zaune
sannan tayi picking call din ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren yayi
mata sallama sannan yace "Hajiya fatan kin shirya in taho in dauke ki,
flight din naki nan da minti talatin ne in sha Allah" a hankali Khaleesat
tace "Toh" Yace "Gani nan tahowa yanzu da izinin Allah"
Yana katse wayar Khaleesat ta sauka daga saman gado taje tayi alwala a bandaki,
tana idar da sallan Azahar sai ga kiransa, ta dau trolley dinta da handbag ta
bar dakin hotel din ta sauko downstairs, yana hangota a Reception din hotel din
ya tafi da sauri ya amshi trolley din hannunta, ya karbi makullin dakin ya kai
ma Receptionist, sannan suka fita haraban hotel din ya bude mata back seat
bayan ya saka trolley dinta a booth, cikin mintuna kadan suka isa MMI Airport,
sai da ya tabbatar ta amshi boarding pass dinta sannan yayi mata sallama da
murmushi fuskarsa yace "Toh Allah Ubangiji ya tsare Hajiya, idan kun sauka
kanon za a karasa dake gida in sha Allah... We will keep in touch" a
hankali Khaleesat tace "Toh Nagode, Allah ya saka da alkhairi" Yace
"Ameen Hajjaju, nagode kwarai, Allah Ubangiji ya kai ku lafiya" A
haka suka rabu ta nufi Departure lounge walking slowly, bayan kusan minti
ashirin jirginsu ya tashi zuwa garin kano. Suna sauka kano Khaleesat ta fito
daga cikin airport gabanta na faduwa, sai gyara nose mask din fuskarta take
tana waige waige, yanzu ina ma ta nufa tukun, tasan ko da wasa bazata nufi gida
ba dai, wayarta ya fara ring ta duba da sauri gabanta na ci gaba da faduwa,
wata lamba ce ke kiranta tayi picking tayi shiru, taji an mata sallama ta amsa,
mutumin ya gaisheta yace "Hajiya Hamisu ne ya aiko min lambarki, naga
jirgin ku ya sauka yanzu, yace za a karasa dake gida, kina ta ina yanzu?"
Tace "Na fito outside of the airport" Tahowa taga mutumin yayi zuwa
inda take tsaye bayan ya hangota, nan ya kai ta har motar dake jiranta, motar
shigen wanda ta shiga a Abuja ne, mutumin ya bude mata back seat ta shiga tace
"Nagode" Yayi bowing kansa yayi mata sallama yace "Allah ya kai
ku lafiya" Tace "Ameen Nagode" Drivern dake mazaunin driver ya
gaisheta yana tambayarta ya hanya sannan ya tada motar suka fita daga airport
din yace "Ina muka nufa Hajjaju?" Khaleesat ta Ιan yi shiru kamar me
nazari, sai kuma tace "Hotoro zaka kai ni" Yace "To Allah ya kai
mu lafiya" Suna isa dai dai kofar gidan da ta nuna masa ya tsaya, ya bude
motar ya sauka don fiddo mata Trolley dinta a booth, bude motar tayi ita ma ta
sauka tana gyara facemask dinta, ta amshi akwatinta a hannunsa sannan tayi masa
godiya ta shiga cikin gidan da sauri, Baaba Gaje dake zaune tana tankade garin
tuwo ta daga kai tana kallonta, Khaleesat ta Ιan sauke Facemask dinta tana
murmushi tace "Baaba sannu da aiki" Baaba Gaje ta ajiye rariyar
hannunta tace "Khaleesatu? Daga ina kuma haka?" Khaleesat ta duka nan
gabanta har sannan tana Ιan murmushi tace "Makaranta" Baaba Gaje tace
"Ikon Allah, to ai ko minti ashirin banyi da dawowa daga gidanku ba kuma
ba ace min kina hanya ba" A hankali Khaleesat tace "Baaba ya jikin
Ummanmu fa?" Baaba Gaje tace "Kaddai ba a san kin biyo hanya ba kika
taho Khaleesatu?" Khaleesat ta gyada mata kai kawai, Baaba Gaje tace
"Ikon Allah, to ai jikin nata da sauki er nan, shi Awdul din ne ya biya
maki kudin jirgi kika dawo?" Khaleesat ta girgiza kai gabanta na faduwa
tace "Bai san na dawo ba Baaba" Baaba Gaje tace "Ikon Allah, to
bari in kira Parida, ko kuma ke ki kirata da kanki, Gwara da kika yi dubaran
zuwa nan kada Salubabben uban nan naki ya sa ki a bakin duniya mu shiga uku, Ga
tabarma taho ki zauna ki huta, irin wannan tafiya me nisa haka, naji ance
Amurkan har yapi legas nisa ko? Kira Paridan mu ji yanda za ayi" Khaleesat
ta zauna gefenta ta bude handbag ta ciro wayarta, duk da yanda gabanta ke
faduwa haka tayi dialing din lambar kanwar Ummanta Aunty Farida, Baaba Gaje
tace "Auu to ai Parida ba waya a hannunta wai an sace a mota"
Khaleesat ta daga kai tana kallonta, Baaba Gaje tace "Abinda zai faru
kawai ga garin tuwon nan ki karasa tankade min ga can murhu na dora ruwan tuwo
in yayi ki min talgi ki tuka tuwon in ya silala ki kwashe, ga kuma kayan miya can
bai dai da yawa ki jajjaga ki kada min miyar kuka, ni kuma sai in koma can
Mariri yanzu in sanar ma Ummanku kin zo" Khaleesat tace "Toh
Baaba" Mikewa Baaba Gaje tayi ta figi yakunennen gyalenta a igiyar shanyan
dake Ιan karamin tsakar gidan ta yafa tace "Bara inje, dama ina da canjina
dari da hansin sai in roke masu Ιan sahu su kai ni ko Farawa ne sai in karasa
Maririn da kafa ta" Khaleesat ta bude handbag dinta amma sai taga Dollars
kawai, ta daga kai ta kalli Baaba Gaje tace "Wallahi bani da kudin Nigeria
a nan Baaba, amma bari in ciro a POS yanzu sai in baki kudin adaidaita
sahun" Baaba Gaje tace "Aa yi zamanki kiyi aikin da na sa ki, minti
nawa ne nan da Mariri, kawai dai ga wanke wanke can bakin kwararo ki wanke min
har su, ki share tsakar gidan nan, in yaran nan suka dawo islamiyya ki dauraye
masu Uniform dinsu, dakin ma na nan sunyi kaca kaca da shi babu kyan gani"
Daga haka ta fice daga cikin gidan bayan ta saka slippers dinta, Khaleesat ta
cire mayafin abayan jikinta ta dora kan akwatinta sannan ta ci gaba da tankaden
da Baaba Gaje ta bar mata, Baaba Gaje makociyarsu ce a can unguwansu Mariri
kafin 'ya yanta su siya mata wani Ιan kararramin gida a nan Hotoro Tsamiyar
boka ta dawo tana zaune da jikokinta biyar tana dubasu, zaman mutunci da amana
Baaba Gaje suka yi da Mahaifiyar Khaleesat da ta dauki Gajen tamkar uwa. Wajen
karfe shidda saura Khaleesat ta gama duk aikin da Gaje ta loda mata sannan ta
dora ruwan da zata yi wanka a sauran rushi, zaunawa tayi kan tabarma ta jingina
da bango don ta gaji likis, Housemate dinta ne ya fado mata, ta dai yi shiru
staring into space, after a while ta sauke idonta a hankali ta mike ta shiga da
kwanukan da ta wanke cikin dakin Gaje, dai dai nan Gaje ta shigo cikin gidan da
Aunty Farida, Khaleesat ta tafi da gudu ta rungume Aunty Farida cike da murnan
ganinta, Aunty Farida na kallonta tace "Ke kuma da wa kika yi shawara kika
biyo hanya Khaleesah? Abdul din ne yace ki taho?" Gaje ta daga hannu sama
da sauri tace "Aaaa tace bai ma sani ba" Aunty Farida na kallon Khaleesat
da mamaki tace "Ban gane bai sani ba??" Khaleesat ta marairaice ta
kauda zancen ta hanyar cewa "Aunty ya jikin Ummanmu?" Aunty Farida ta
kamo hannunta suka zauna saman tabarma tace "Ai jikin Umma da sauki sosai
Khaleesat, gashi har an sallamemu a asibiti, wa yace maki bata da lafiya ne ma
tukun?" Khaleesat da har hawaye ya ciko idonta tace "Aunty
Sha'awa" Gaje tace "Lahh ha ila, wato Sha'awa bazata dena munafurci
ba ko? Wato bazata canxa hali ba ko? Da kaina fa sai da na jaddada mata kar ta
gaya maki ko kin mata sako ta wassol don kar hankalinki ya tashi, ashe sai da
munafukar ta zaga ta fada maki" Aunty Farida tace "Toh Allah ya
kyauta, kwata kwata Sha'awa bazata canza ba" Khaleesat da hawaye ke cika
idonta tace "To Aunty ta yaya zan ga Ummanmu yanzu?" Aunty Farida
tace "Kar ki damu kiyi zaman ki nan wajen Baaba Gaje, gobe da safe in za
mu tafi asibiti sai mu fara biyowa ta nan da Umman tunda asibitin Malam Aminu
kano ne" A hankali Khaleesat tace "Toh Allah ya kai mu Aunty" Sai
bayan Magrib Aunty Farida ta bar gidan bayan ta ci tuwon da Khaleesat tayi ma
Gaje, sosai Khaleesat taji ta samu rest of mind bayan taji jikin Ummanta da
sauki, bayan Isha Gaje ta gyara mata Ιan lungun da zata kwanta a dakin ta daura
mata net din sauro tace "Allah dai ya rabaki da cinnaku" ita dai
Khaleesat tayi murmushi kawai bata ce komai ba, ita matsalarta ma zafi, ko ya
zata yi da zafi yau gashi karamin dakin wani Ιan mitsitsin window ne kawai ke
garesa, su bakwai kuma zasu kwana a ciki, Khaleesat ta gama shirin kwanciya don
tayi wanka sannan ta shiga net din ta kwanta, ta amshi maficin da gaje ke mika
mata ta cikin net din, tun dawowarta sai a sannan tayi subscription ta shiga
WhatsApp dinta, Message din Safiyyah dake tambayarta ko ta isa lafiya kadai
tayi ma reply, bata yi mamakin rashin ganin message din Abdul ba don she isn't
even expecting his message, ajiye wayar tayi ta gyara kwanciyarta ta lumshe
ido, Housemate dinta ne ya fado mata, she have no access to him balle ko godiya
ma tayi masa, bata yi tunanin da ta fito zata tafi airport bazai tambayeta
phone number dinta ba, ko Airport din ma bata yi tunanin bazai yi offering yace
zai kai ta ba, juye juye kawai take yi a net din idonta a rufe, after a while
of thinking bacci ya dauketa. Washegari Khaleesat ta gama yi ma Baaba Gaje duk
aikace aikacen gidan, ta hura gawayi ta daura ruwa tayi ma kananun jikokinta
wanka sannan ta dama kunu, Baaba Gaje ta fita siyo masu kosai a titi, har karfe
goma Khaleesat bata ga Aunty Farida sun zo gidan da Ummanta ba, gaba daya ta
damu taga Ummanta, Baaba Gaje tace "To ke sai ruwan ya salance zaki je
kiyi wankan? Ba fa wani gawayin" Khaleesat tace "Zan yi" Daga
haka ta mike ta tafi yin wankan, tana fitowa daga wanka taga takalmin da Aunty
Farida ta zo da shi jiya a bakin kofa da wani takalmin daban wanda ko ba a fada
ba tasan na Ummanta ne, da sauri ta shiga dakin Baaba Gaje taga Ummanta da
Aunty Farida a zaune, tsallake Aunty Farida tayi ta tafi gun Ummanta da gudu
cike da farin cikin ganinta ta durkusa gabanta ta rungumeta, Aunty Farida tace
"Ko dai baki da hankali ne?" Baaba Gaje tace "Toh da sauki dai
kam" Ita dai Umman sai kallon Khaleesat take, gaba daya Khaleesat ta ma
mance wai Umma bata da lafiya tsabar farin cikin ganinta, a hankali Umma tace
"Meyasa zaki biyo hanya Khaleesah? Abdul din ne yace ki dawo?"
Khaleesat ta kamo hannunta cike da damuwa tace "Umma ya jikin?" Umma
tace "Naji sauki Alhamdulillah" Khaleesat tace "Aunty Sha'awa
tace min ko magana fa baki yi" Baaba Gaje ta rike haΙa tace "Oh ni
'ya su, kun ji er iska ko? Wallahi Sha'awa da kyar taga annabi, babu yanda bamu
yi da ita ko da wasa kar ta gaya maki ba ashe sai da ta zaga ta fada, har ce
mata nayi tace maki tayi tafiya ko da zaki buga nata wassol" Khaleesat ta
daga kai ta kalli Baaba Gaje tace "Ni ce na kirata don ina ta magana bata
min reply ba" Aunty Farida tace "Ai tsabar munafurci yasa ta gaya
maki ba wani abu ba" Khaleesat ta Ιan yi murmushi ta gaida Aunty Farida,
Aunty Farida ta amsa tace "Amma shi Abdul yasan Umma bata da lafiya shine
ko kira ya dubata bai yi ba?" Khaleesat ta sauke idonta kasa tace "Ni
fa bai san na dawo ba Aunty" Aunty Farida tace "Wai ban gane bai san
kin dawo ba, wa ya biya maki kudin jirgin?" Khaleesat ta daga manyan
idanuwanta tana kallonsu, Sai kuma a hankali tace "Wani ne ya biya min ba
Abdul ba" Umma ta kalleta da sauri tace "Wani?" Da mamaki Aunty
Farida tace "Wani a ina?" Khaleesat na kokarin mikewa tace
"Neighbor dina ne" Umma ta bude baki tana kallonta, sai kuma tace
"Ko baki da hankali ne, waye ya biya maki kudin jirgi Khaleesah?"
Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Gaje tace "Bude baki zaki yi ki
mana bayani dalla dalla, waye shi zai biya maki zunzurutun kudi na jirgin da
naji ance ya fi miliyan daya? A ina kika san sa?" Still dai Khaleesat taki
cewa komai, Aunty Farida tace "Ke bana son rainin wayo uban wa zaki ma
shiru ana maki magana? Ko baki ji tambayar da ake maki bane?" Umma dai
kallon Khaleesat kawai take da mamaki, Khaleesat ta koma baya ta Ιan sunkuyar
da kanta a hankali tace "Ni fa nace makocina ne ya biya min, kuma ai gani
yayi ina ta kuka Ummana bata da lafiya shine ya biya min jirgi in dawo in
dubota" Cikin sanyin murya ta kare maganar, Baaba Gaje tace "Atoh
dama ai ko ina ana samun na Allah, Allah ya masa albarka, Bature ne ko?" A
takaice Khaleesat tace "Um" don bata son ma a ci gaba da zancen,
Baaba Gaje tace "Ko da naji, ai sai baturen dama, wani baΖin fata ne zai
biya maki jirgi don yana makocinki, ai ko mutuwa uwar taki tayi iyaka ya maki
gaisuwa ya kama gabansa, to Allah ya saka masa da alkhairi, abinda ma baturen
kudin jirgin ba wani kudi bane a wajensa, ji zai yi kamar naira dubu goma ya
kashe fa" Khaleesat na kallon Aunty Farida tace "Aunty yanzu za aje
asibitin ne?" Aunty Farida tace "Aa mu har mun dawo daga asibiti sai
kuma na gobe in Allah ya kai mu" a hankali Umma tace "Toh da ya biya
maki kudin jirgin zuwa wa zai maki na komawa yanzu? Kinsan dai ko hauka kike
baza ki bari Abdul yaji wannan batun ba ki ja mana masifa ko?" Sai da
gaban Khaleesat ya fadi, a hankali ta sunkuyar da kanta, ita gaba daya ta ma
mance ashe biyan jirgi za ayi a koma, nan da nan jikinta yayi mugun sanyi,
yanzu ina zata samu kudin ticket din komawa, she became so weak at once, Aunty
Farida tace "Toh shi Abdul din baki ce masa Umma bata da lafiya
bane?" Khaleesat da har sannan jikinta yake a sanyaye ta girgiza kai tace
"Baya nan ne" Daga haka ta mike ta tafi zata shirya don zanin da tayi
wanka ne daure jikinta har a lkcn, Khaleesat na cikin saka kayanta da ta fiddo
a akwati 1000 dollar din da Housemate dinta ya bata suka fado mata a rai, ta
zaro ido lkci daya taji hankalinta ya kwanta har sai da ta sauke ajiyar zuciya,
tasan probably in ta canza har da 100 dollar din da Safiyyah ta bata kudaden za
su iya maidata Amurka, she felt so relieved, nan da nan walwalarta ya dawo,
tana jin Baaba Gaje na tambayar Aunty Farida ko kishiyoyin Ummanta sun shiga
dubata yau, Aunty Farida tace "Jiya ma basu shigo dubata ba sai yau Baaba
Gaje" Baaba Gaje tace "Shegu matsiyata, so fa suka yi ace ta mutu, to
shi Malam Alin ya ku ka Ζarke da shi? Ya bada kudin?" Aunty Farida tace
"Aa ni fa ban bi ta kansa ba Baaba Gaje, dama me ya tsinana kafin in zo
kanon? daxu ma aka turo min sauran kudin adashina da nake jira, duk na siya
sauran magungunan" Baaba Gaje tace "Atoh dai bai taΙuka komai ba a
takaice, shi ma da zaki basa yanxu tsaf zai amshe" Har aka yi azahar su
Umma da Aunty Farida na gidan, Umma har tayi bacci ta tashi saboda maganin da
take sha, har a sannan da kyar take taka kafarta daya, hannunta dai ya sake ya
dawo normal tun a jiya, Khaleesat ta shigo dakin da shinkafa da waken da ta
dafa, Baaba Gaje kuma ta shiga makota dubiya, Aunty Farida dai sai bin
Khaleesat take da kallo, sosai taga ta kara kyau tayi fresh, duk da dai tana
nan a yanda take babu kiba, komawa tsakar gida Khaleesat tayi ta dauko man
gyadan da ta soya ta dawo dakin, ta fara zuba ma Umma da Aunty Farida abincin,
Umma dake zaune kan darduma tana kallonta tace "Kun fara jarabawan
ne?" Aunty Farida tace "Haba dai sun fara jarabawa zata taho? Ai
bazai yiwu ba, ko ana haka ne?" Khaleesat dake sauraronsu ta girgiza kai
tana Ιan murmushi tace "Da sauran lokaci bamu fara ba tukun" Aunty
Farida tace "To yanzu dai tun kan wani munafukin yasan kina garin nan mu
shiga uku yaushe za ki koma Khaleesah?" Khaleesat ta daga kai a hankali
tace "Cikin satin nan in sha Allah" Aunty Farida tace "Toh inji
dai Abdul din ya rage abubuwan nan nasa da yake maki?" Khaleesat ta ajiye
masu abincin a gabansu kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "Babu abinda
ya fasa, ni na gaji da halinsa ma yanzu" Umma ta daga kai tana kallonta,
Aunty Farida ma kallonta take don bata taΙa cewa ta gaji da halin Abdul ba,
Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya ta fara cin abincin gabanta tace "Na
dai gaya maki babu me canza maki shi sai ke da kanki, ke macece ya kamata ace
zuwa yanzu kinsan wanene Abdul kinsan kuma yanda zaki zauna da shi" Mikewa
Khaleesat tayi without saying anything don ita yanzu taji ko zancen nasa ma
bata so har cikin ranta, tun shekaranjiya da yayi fushi har yau bai kirata ba
ita kuma as far as tayi masa miss calls har biyu to bata ji zata iya sake kiransa
ba unlike before da ta dinga kiransa kenan ko da bazai daga ba, ko kuma tayi ta
masa magana ta WhatsApp, to yanzu kam bata ji zata iya ba.....
07087865788✍π»
*Still on free pages*
[5/4, 8:14 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
7.....
Kwanan Khaleesat hudu yau a garin kano, kuma har a sannan
babu wanda yasan da zuwanta a cikin yan gidansu, ko nan da can bata fita a
gidan Baaba Gaje don ma kar tsautsayi ya sa ta hadu da daya daga cikin yan
gidan nasu, a kwanaki hudun nan sau biyu Ummanta da Aunty Farida suka zo gidan
Baaba Gaje dominta, zuwa sannan Umma ta warware gaba daya tafiyarta ya dawo
normal, tun kwanaki biyu da suka wuce ta gama amsan treatment dinta a hospital
sai magunguna da take sha kawai, har zuwa ranan kuma Abdul bai kira Khaleesat
ba, ita kuwa kawai taji ko a jikinta da ya kira da kar ya kira, there wasn't an
atom of disturbance a tattare da ita, ko ta WhatsApp bata yi gigin yi masa
magana ba Unlike before da bazata iya hakuri ba sai ta masa, tana bakin murhu
tana dafa shinkafa da wake ga turmi gabanta tana Ιaka yajin da za ayi amfani da
shi wajen cin shinkafa da waken, Su Ummanta da Baaba Gaje kuma na can uwar Ιaka,
tunanin yanda zata fara shirye shiryen komawa USA take don suna da wani
presentation nan da kwana uku, daxu da safe ta duba available flight da
farashinsu online and she is hoping in ta canza dollars din da Housemate dinta
ya bata zai isheta ta koma, Khaleesat ta bar daΖan yajin da take yi bayan taji
Aunty Farida na kwalo mata kira, mikewa tayi ta wuce dakin tana amsawa, tun da
ta zo gidan Baaba Gaje ta sakar mata aikin komai, hatta jikokinta ita ke masu
wanka kan su tafi makaranta, ita taga kamar har ta Ιan yi duhu tsabar girki
cikin rana da take yi tun zuwanta, Aunty Farida tace "Ana kiran
wayarki" nan da nan mood din Khaleesat ya canza ta karasa gun wayar
without much interest, duk tunaninta Abdul ne cause she isn't expecting any
call from anybody, Number mutumin da ya tarbeta a Airport din Lagos ta gani a
gaban Screen din wayarta, ta dinga kallon number bata ko kiftawa, duk da bata
yi saving ba amma ta gane nasa ne, daukar wayar tayi ta fita daga dakin ta koma
bakin murhun sannan tayi picking ta kai kunne, sallama yayi ya gaisheta da
ladabi, tace "Ina yini?" Yace "Alhamdulillahi Hajiya, ya jama'ar
gidan?" Tace "Alhamdulillah" Yace "To maa sha Allah, dama
na bugo ne inji ko zaki kara kwanaki nawa nan gaba kan ki koma America?"
Khaleesat tayi shiru trying to understand why he is asking her that, yace
"Hello?" Tace "Ina jin ka, ban gane tambayar bane" Calmly
yace "Aa so nake in san ranan da zaki koma ne Hajiya, in ya kama ayi
rescheduling din ticket dinki sai ayi hakan in sha Allah" Khaleesat was
speechless, a ranta tace Ticket kuma? Kasa cewa komai tayi with surprise, taji
ta ma kasa ci gaba da tsayuwa, jin ya sake cewa "Hello" ta kifta ido
da kyar ta duka kusa da turmin da take daka yaji tace "Ina ji" Yace
"Ina ga a bari duk sanda kika shirya zaki nemeni ta waya ko Hajiya?"
Sauke idonta tayi kasa, lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, cikin sanyayyen
murya tace "Ranan Lahadi nake son zan koma idan Allah ya yarda" Yace
"To Maa sha Allah, dama booking din ranan aka maki da zaki taho, flight
din karfe daya ne, za ku tashi ta Airport din Abuja in sha Allah" Ita dai
Khaleesat ta kasa cewa komai, yace "Sai kin ji ni in sha Allah
Hajiya" A hankali Khaleesat tace "Nagode" Khaleesat na zaune
dakin Baaba Gaje tana jujjuya shinkafa da waken dake gabanta da cokali, gaba
daya ta kasa cin abincin, ita kanta ta rasa dalili, ko tsabar yanda jikinta
yayi sanyi ne tun bayan da suka yi waya da mutumin daxu da ya sanar mata da
ticket dinta na komawa America sannan tana gama aikin da take ta bude WhatsApp
taga ya aiko mata da Flight Ticket dinta which was also business Class kamar
dai yanda ta zo, this made her so weak, gaba daya ta ma rasa gane feeling din
dake ranta a lokacin, bata taba tunanin Housemate din nata zai mata ticket din
komawa ba, Duk Ummanta na lura da sauyawanta lkci guda, Aunty Farida ta gama
shafa powder din da take zata leka gidan wata kawarta Maman Fu'ad a nan
hotoron, ta dau jakarta da mayafi tana kallon yayarta tace "To sai na dawo
Umma" Umma tace "Amma kar ki dade don Allah Farida" Aunty Farida
tace "Haba ai yamma tayi bazan zauna ba Umma" Daga haka ta fita daga
dakin tayi ma Baaba Gaje dake waje tare da bakuwarta sallama sannan ta fita
daga gidan, Umma ta daga kai tana kallon Khaleesat tace "Menene kika saka
abinci a gaba kika kasa ci Khaleesat?" Khaleesat ta daga kai da sauri tana
kallon kyakkyawan fuskar Ummanta, babu wanda zai ce Umma ce ta haifeta sai dai
ma yayi tunanin yayarta ce don kama suke ba na wasa ba kamar an tsaga Ζara,
Khaleesat tayi murmushin yake ta kai shinkafa da waken baki tace "Babu
komai fa Umma" Umma tace "Yaushe za ki koma? Kuma yaya za ayi da
batun kudin jirgi? Har yanzu Abdul din bai san kina nan ba?" Khaleesat ta
girgiza kai tace "Umma ai nace baya nan kuma ba a samunsa ta waya, ranan
lahadi zan koma in sha Allah" Umma tace "Ranan Lahadi? To ina za ki
samu kudin komawa?" Khaleesat ta gyara zamanta tace "Makocin nawa ai
tare ya biya min na zuwa da dawowa" Kallonta Umma ta dinga yi da alamar
tuhuma ga mamaki kwance fuskarta, Khaleesat taki yarda ta bari su hada ido sai
tura abincin gabanta take, Umma tace "Khaleesah" Da kyar Khaleesat ta
daga kai gabanta na faduwa, Umma tace "Meye tsakaninki da wannan mutumi da
ya biya maki kudin jirgin zuwa har da na komawa?" Khaleesat ta hadiye
sauran shinkafar da ya makale a throat dinta da kyar tace "Wallahi Umma
babu komai, makocina ne kawai shi, kuma don yaga yanda na daga hankali baki da
lafiya shi ne yasa yayi hakan, ni kaina sai bayan da ya biya min na sani, amma
ki yarda dani Umma babu komai tsakanina da shi" Kamar zata yi kuka ta kare
maganar, Ummanta ta sauke ajiyar zuciya tayi shiru, bayan some seconds tace
"Toh shikenan, amma dai kinsan in Abdul ya samu labarin nan da matsala
ko?" Khaleesat ta sunkuyar da kanta bata sake cewa komai ba, jin Umma tayi
shiru alamar ta fada duniyar tunani Khaleesat ta daga kai a hankali tace
"To ai Umma babu wanda yasan na zo kano har yanzu, don haka bazai sani ba"
Umma ta sauke wani ajiyar zuciyar tace "To gudun kada hakan ya sake faruwa
kar ki sake yarda ko wata mu'amula ta hadaki da shi makocin naki Khaleesat, ki
rufa mana asiri" Khaleesat bata ce komai ba sai kuma ta jawo handbag dinta
ta ciro dala dubu dayan da Housemate dinta ya bata ta nuna ma Umma cikin sanyin
murya tace "Wannan ma shi ya bani da zan taho" Umma ta dinga kallon
kudin duk da bata san ko nawa bane ta dai ce "Ki kula don Allah Khaleesat
kar ki ja mana magana kin dai san wanene Abdul kin san kuma waye Babanki"
Khaleesat dai tayi shiru, tasan Umma bata san har nawa bane Dollars din in an
canza zuwa Naira, ita dai tayi shiru bata gaya mata ba kar ta kara daga mata
hankali. Washegari da wuri Khaleesat ta shirya ta saka Nikab dinta ta fita don
zata je canza dollar din nata ta dan yi siyayya, bayan ta canza dalolin taga
har ya wuce yanda take tunani a Naira, nan ta fara zuwa inda zata siyi waya, ta
siya ma Ummanta da Aunty Farida sabbin wayar Android iri daya na dubu dari da
hamsin each, Ganin Baaba Gaje ma bata da waya kuma ba iya amfani da Android
zata yi ba ta siya mata karamar waya na dubu ashirin, daga nan ta karasa kasuwa
tayi siyayyar yan abubuwan da zata koma USA da shi, ta siya ma siblings dinta
twins mata sabbin school bag da schl shoe da socks, ta siya masu atamfofi kala
uku each da mayafai da takalma masu kyau da inner wears, jikokin Baaba Gaje ma
ta siya masu takalma da inner wears gaba dayansu, pharmacy ta shiga da takardan
da aka rubuta magungunan Ummanta ta siya mata na wata biyu duk da tsadar magungunan,
kusan Azahar ta koma gidan Baaba Gaje ta tarar su Ummanta basu zo ba. Washegari
asabar Khaleesat na shanya kayan jikokin Baaba Gaje da ta wanke, Baaba Gaje
kuma na shirin fita kasuwa Ummanta suka shigo gidan tare da Aunty Farida da
Siblings dinta yan biyu Islam da Noor that are just 11 years old, da gudu suka
tafi suka rungumeta suna mata oyoyo, sosai kannin nata ke kama da ita,
Khaleesat was so happy seeing her twins Siblings wanda su uku kawai Ummansu ta
haifa, Baaba Gaje tace "Basu tafi islamiyya bane?" Umma tayi kasa da
murya tana kallon Gaje tace "Sun ma kwana biyu rabonsu da zuwa, ba a biya
kudin wata ba" Baaba Gaje tace "Ikon Allah to Alin ca yayi bazai biya
ba kenan?" Umma tace "Cewa yayi in dora masu talla kamar yanda yan
uwansu ke yi tunda su ba 'ya yan Gwal bane, dama ba fa shi ke biya masu ba
wannan karan ne bani da kudi duk jarin ya lalace shine nace su tambayesa"
Baaba Gaje tace "To Allah ya kyauta, amma Ali dai haΖΖin 'ya ya da kyar ya
bari ya jiyo kamshin aljanna balle yaje kusa da ita" Ita dai Khaleesat a
sanyaye ta kama hannun kannin nata zuwa dakin Baaba Gaje, tana jin Baaba
Gaje na cewa "Amma de suna zuwa
bokon?" Umma ta sauke ajiyar zuciya tace "Ina fa, islamiyya ma da ya
zama dole ba aje ba sae wani boko" Aunty Farida ta girgiza kai cike da
takaici tace "Allah de ya kyauta, shi fa bakin cikin bata dora ma yaran
talla kamar yanda sauran matansa ke dora ma nasu 'ya yan talla ba yake"
Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi don duk sanda ta tambayi Ummanta ko kannen
nata na zuwa boko da Islamiyya ta wayar Sha'awa sai tace mata eh suna zuwa,
ashe basa zuwa, Umma dai bata ce komai ba suka shiga dakin gaba daya, Baaba
Gaje tace "Kun ga bari inje kasuwa in dawo" Su Umma suka mata Allah
ya kiyaye ta figi gyalenta ta fita daga gidan, Khaleesat ta fiddo duk siyayyan
da tayi jiya, daga Ummanta har Aunty Farida kallonta suka tsaya yi, Aunty
Farida ta rike haΙa tace "Haka kudin suke da yawa da kika canza? Kuma wa
ya aike ki kashe kudi haka mu da muke da sabga a gabanmu Khaleesat? Maimakon ki
bada a ajiye maki ko kujeru da setin gado ne da kudaden? Kin de san ko
tsintsiya mahaifinki ba lallai ya siya maki da sunan a kai ki dakinki da shi ba
ko?" Khaleesat tayi murmushin karfin hali bata ce komai ba, Umma dai ta ma
rasa abun cewa, Aunty Farida tace "Ni da kin yi shawara da ni duk baza ki
yi wannan siyayyan ba, iyaka ki siyi abinda zaki koma can Amurka da shi, in
suka tado da maganar aure me garemu da za a kai ki da shi Khaleesah?"
Khaleesat na murmushi tace "Allah zai rufa asiri zuwa sannan Aunty"
Aunty Farida tace "Yanzu duk kudin sun kare kenan?" Khaleesat ta
girgiza kai tace "Aa, saura dubu dari biyar" Daga Aunty Farida har
Umma bude ido suka yi sosai suna kallonta with shock, Aunty Farida ta gyara
zama tana zaro ido tace "Har nawa ya baki haka? Ko dai baki da hankali
ne" Khaleesat ta kauda zancen ta hanyar cewa "Har fa da kudadena duk
na canxa" handbag dinta ta jawo ta bude ta ciro sauran kudaden da suka
rage don har wanda Safiyyah ta bata ta canza, ta kirga dubu dari a ciki ta
ware, sannan ta kirga dubu dari da hamsin shi ma ta ware, kallonta kawai Umma
da Aunty Farida suke, ta ba Aunty Farida dubu dari tace "Aunty kiyi kudin
mota da wannan idan zaki koma Lagos sannan ki kara jari" Ta ajiye ma Umma
150k tace "Umma ki rike wannan a biya kudin makarantar su islam da Noor a
kuma canza masu Uniform" Umma tace "Ko dai baki da hankali ne
Khaleesah? baki ji shawaran da Farida ta kawo bane halan?" Aunty Farida ta
mayar mata da 100k din tace "Aa gaskiya ban ga alamar da kan nan ba Umma,
ina ga hakoranmu za mu je mu jera mata a gida idan bikin ya tashi...."
Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba tace "Akwai fa kudade a account
dina wanda Abdul ke bani kuma suna da yawa za su isa ayi duk abinda za ayi
sannan Aunty" It took Khaleesat almost an eternity to convince her Mother
and aunt akan su rike kudin da ta basu, nan kuma bata da wani kudin a zo a gani
a account dinta sai miliyan 10 na Abdul da ya ajiye a account din wanda nashi
ne ba nata ba, iya kudin foodstuff kawai yake tura mata duk karshen wata sai
kuma kudin Uber na zuwa makaranta, sai house rent dinta da yake biya at due
time, iya abinda kawai yake mata kenan amma naira biyar dinsa baya bata a
matsayin kyauta, instead sai dai ya siya mata kaya masu tsada, monthly kuma
yake mata subscription a waya, apart from this bai bata kudi da sunan kudin
kashewa, a haka dai ta samu tayi convincing Umma da Aunty Farida suka amshi
kudin da ta basu, Aunty Farida na kallon Umma tace "To kinga sai kiyi
kaffa kaffa da wayar nan kar su sace maki tunda sun saba maki haka, kin dai ga
ba dan karamin kudi aka siyo wayar da shi ba" Umma na kallon Khaleesat
tace "To shi Malam din me kika siya masa?" Aunty Farida ta wani kalli
yayarta, Khaleesat ma dai kallon Ummanta tayi bata ce komai ba, Aunty Farida ta
kyabe baki ta kauda kai, Umma ta kalli Aunty Farida tace "Wai saboda
hakki, naga ta siya min waya shima da sai ta nemi abinda ta siya masa
kwatankwacin wayar, kuma bashi da wayar shi ma wallahi" Aunty Farida na
kallon yayarta da kyau tace "Umma in kinsan zuwa za kiyi ki kyautar da
wayar nan da ta siya maki to gwara dai ki bar mata kayanta, ina ce kwanaki can
matansa ya siya ma Atamfa yar gadagalle lkcn bikin Salisu ke ya siya
maki?" Umma tace "Aa ba ruwanta da wannan Farida, ai ubanta ne, kuma
don ta siyi abu ta basa ai ba faduwa tayi ba" Aunty Farida bata sake tanka
Umma ba ta fara harhada ma Khaleesat kayayyakin abinci da ta siyo waje daya,
Sai kusan la'asar su Umma suka bar gidan kuma har sannan Baaba Gaje bata dawo
ba, a boye Khaleesat ta ba Siblings dinta 50k wanda ta saka a karamin jakar
Islam tace masu in sun je gida su ba Umma kuma ta ja masu kunni sosai kan
daukan sabon wayar da ta siya ma Umma kar su lalata mata. Washegari da safe
Khaleesat ta fito wanka wayarta ya fara ring tana dauka taga mutumin nan ne
dai, bayan ta daga suka gaisa sannan yace "Hajiya nan da karfe tara da
rabi wani driver zai kiraki sai kiyi masa kwatancen inda zai zo ya daukeki ya
kai ki airport, don flight dinki zuwa Abuja na karfe sha daya ne, in kun iso
Abuja kuma jirgin da zaki bi zuwa Amurka jirgin karfe biyu saura ne"
Khaleesat tace "To ba damuwa Nagode" Aunty Farida kadai ce ta zo
gidan Baaba Gaje yi ma Khaleesat sallama, Khaleesat bata ji dadin da Umma bata
biyo ta ba, duk jikinta yayi sanyi sosai, a haka drivern da zai kai ta airport
ya iso, Baaba Gaje ta dinga sa mata albarkan wayar da ta siya mata da abubuwan
da ta siyo ma jikokinta, bayan an kai akwatin kayanta cikin mota su Aunty
Farida da Baaba Gaje suka rakata har bakin motar, bayan Khaleesat ta shiga
motar ta daga masu hannu a sanyaye tana murmushin karfin hali, har cikin ranta
bata ji dadin da bata yi sallama da Ummanta ba, a haka suka kama hanyar airport
da drivern da ya zo daukarta, suna sauka Abuja karfe daya da minti 40 jirgin su
ya tashi. The flight to the United state was so comfortable for Khaleesat in
her business class seat, don throughout bacci tayi, karfe hudu saura na asuba
jirginsu ya sauka Maryland, It was soo cold in Maryland gashi bata da sweater a
kayanta, bayan ta fito da luggages dinta tana duba Uber da zai kai ta gida tana
rike da wayar kamar ance ta daga kai taga motar da yayi parking, kallo daya
tayi masa sai kuma ta sauke kai kasa, ya karaso har inda take yace "Jirgin
ya dade da sauka ne?" Sai a sannan ta kara kallon Sleepy face dinsa, sai
kuma ta girgiza kai tace "Aa" Yace "Ohk let me drop you
home" Daga haka ya koma gun motarsa ta bi bayansa with both of her
luggages, ya bude booth ya amshi daya trolley dinta ya sa a booth, ita ma ta sa
dayan, ya zaga ya shiga driver seat, tana jan kafa ta karasa front seat ta bude
motar sannan ta shiga tana kallonsa da gefen ido, jinginar da kansa taga yayi
da kujeran motar idonsa a lumshe, ta kulle motar gently, after few seconds ta
sake kallonsa ga mamakinta sai taga kamar fa bacci yake, kallonsa ta dinga yi,
and they seated for almost 3 minutes a haka ita dai bata tashesa ba kuma bata
ce komai ba, Vibration din wayarta ne ya sa ya bude ido, ya wara ido ya fara
kokarin tada motar, bude jakarta tayi to stop the alarm din da ya sa wayarta ke
vibrate, bayan ya ja motar sun bar wajen, still not sounding normal yace
"Ya jikin Mama?" Ta sauke idonta tace "Alhamdulillah, You
shouldn't have bothered coming tunda akwai Lyft ko Uber" Without looking
at her yace "The house key is with me, shi yasa na taho, cause i estimated
when u are arriving" Bata sake ce masa komai ba shi ma haka, a haka har
suka iso gida yayi parking, ya sake jinginar da kansa da kujeran motar, ita dai
ta bude motar gently ta fita, jin fitarta ya sa ya bude ido, shi ma ya sauka
daga motar, Entrance din shiga gidan ya nufa ta bi bayansa, Pajamas ne jikinsa
sai Jacket da ya saka saboda sanyi, yana isa kofar ya kai hannu aljihu alamar
zai ciro makulli, still taga yayi a bakin kofar, ita dai kallonsa kawai take,
after some seconds ya juya yana kallonta, zuwa sannan his eyes are very clear gaba
daya baccin ya gudu jin babu makulli jikinsa, ko bai gaya mata ba ta fahimci
baya tare da makullin gidan, ya Ιan sosa kai yace "I think.... I think, i
left the key at where i am coming from, i am sorry about that Halysaah"
Sauke idonta tayi without saying anything, ya juya ya nufi motarsa ta bi sa da
kallo, sai da ya isa gun motar ya juyo, da sauri ta dauke kanta daga kallonsa,
yace "Mu je in dauko makullin, ba wani nisa zuwa can, kinga it's cold out
here baza ki iya tsayawa cikin sanyi ki jirani in dawo ba" Bata yi musu ba
ta koma gun motar don yanzun ma sanyin take ji sosai, sai da ya shiga sannan
ita ma ta shiga, his car was so warm, ya tada motar suka bar garage din, inda
yace mata babu wani nisa taga sunyi tafiyar kusan 15 mins basu kai ba, nan taji
gabanta ya fara faduwa, lkci lkci take Ιan satan kallonsa ta gefen ido, wani
unguwa suka shigo wanda ko wani gida da gate dinsa unlike some houses in US,
daga karshe taga yayi parking ba tare da ya kashe motar ba yace "Let me
get the keys" Bude motar yayi ya sauka ta bi sa da kallo taga gate din
kusa da su ya bude ya shiga, tsaf take iya kallon hadadden gidan dake ta cikin
gate din don ba irin gate dinmu na gida bane, ita dai sai bin unguwan take da
kallo wanda ko ba a fada maka ba kasan na masu hannu da shuni ne a Amurka din,
ba a wani dau lokaci ba sai gashi ya fito da wani Huge Dog dake biye da shi
yana shisshige masa, wani faduwa gabanta yayi don a duniya tana mugun tsoron
kare, ya duka yana patting Dog din yana masa magana at the same time, wani matashi
ne dogo just like him ya fito daga cikin gate din gidan sanye da Pajamas shi
ma, Khaleesat ta dinga kallonsa as if ta taΙa saninsa amma kuma bata san sa
from anywhere ba, tana kallonsa tana gyara mayafin kanta kar ma ya kalli
direction dinta su hada ido da shi, gabanta kuwa sai faduwa yake kamar mara
gaskiya, matashin ya jingina da gate crossing his both legs yana kallon Housemate
dinta taji yace "Daga ina kake?" Ζin basa amsa Housemate din nata
yayi instead ya mike yana tura masa Ζaton karen don karen tsaf zai ce zai bi
sa, Calmly matashin yace "Ina za ka?" Housemate dinta ya kallesa yace
"You have any issue with that?" Matashin ya Ιan kalli motarsa calmly
yace "Is that a lady in ur Car?" Housemate dinta yayi kamar bai ji sa
ba still pushing the Dog to him, Matashin ya sake kallon motar, Khaleesat tayi
saurin kauda kanta, tabe baki yayi yace "Enjoy" Daga haka ya ja karen
suka koma cikin gidan, Khaleesat da duk taji conversation din nasu taji ranta
ya baci, House mate dinta ya dawo cikin motarsa ya kulle without looking at her
yace "Sorry for keeping u waiting Halysaah" Yana fara driving ta hade
rai tace "Mene yasa bazaka gaya masa i am just ur housemate ba da kuma
dalilin da yasa ka kawo ni nan din?" Housemate dinta yace "Never mind,
ba wai yana da hankali bane"
07087865788✍π»
[5/5, 6:00 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
8.......
Har suka isa gida babu wanda ya sake cewa komai a cikinsu,
yana parking a garage ya bude motar ya sauka, ita ma ta sauka tana satan
kallonsa, kofar entrance din parlor taga ya nufa without looking at her, hakan
yasa tana tafiya a hankali ta bi bayansa, ya bude kofar parlon ya juya ya
kalleta, ita ta fara shiga parlorn sannan shi ma ya shiga ya kulle kofar,
dakinta ta tafi bayan ta bude kofa ta juya ta kallesa, kwanciya taga yayi a kan
3 seater ya lumshe ido, ta shiga dakinta kawai ta kulle. Washegari da safe
karfe takwas da 'yan mintuna Khaleesat ta fito daga dakinta, zaune ta gansa da
text books a gabansa alamar he is studying, yana daga kai tayi saurin dauke
idonta daga kallonsa, har ta karaso cikin parlon ta tsaya jikin kujera tana
wasa da edge din mayafin jikinta, a hankali tace "Ina kwana" Ya ajiye
pen din hannunsa yace "Good morning Halysaah" Still bata dago kanta
ba kuma bata fasa wasa da gefen gyalenta ba, yace "How was ur trip?"
Ta Ιan kyafta ido tace "Alhamdulillah" Yace "Sorry jiya ban
tambayeki jikin Mama ba, i was sleepy hope she is better now?" Sai a
sannan ta daga kai ta kallesa, tace "She is fine Alhamdulillah" Yace
"Hope ur mind is now at rest?" Sunkuyar da kanta tayi bata ce komai
ba, sai kuma ta Ιan gyada masa kai, wayarsa ne ya fara ring ya dauka sannan
yayi picking ya kai kunne, ta Ιaga kanta tana kallonsa, taga shiru yayi alamar
yana sauraron abinda ake gaya masa a wayar, after few seconds yace "It
should be upstairs then" Daga haka ya katse wayar ya ajiye ya daga kai, da
sauri Khaleesat ta dauke kanta daga kallonsa, Yace "Hope nothing
Halysaah?" A hankali tace "Kawai, i want to appreciate you, thank you
so much, Allah ya saka da alkhairi...." Cikin calm voice yace "No,
You need not to Halysaah, iya abinda zan yi ma kanwata na maki ai" Cikin
sanyin murya tace "To Nagode Allah ya saka da alkhairi" Ya Ιan yi
murmushi yace "To Ameen, so u can be this calm?" Ta wani kallesa,
yace "Makarantar zaki tafi baza ki bari ki huta from ur long journey
ba?" Ta sauke idonta tace "I am having presentation today" Yace
"Ohk then, Allah ya bada sa'a" A hankali tace "Ameen" Ya
nuna mata Trolley dinta da ya shigo mata da shi parlon yace "Ga boxes
dinki can" Ta kallesu tace "Thank you" Yace "You are
welcome" Daga haka ya ci gaba da abinda yake, Sai da ta kai su dakinta
sannan ta dawo ta nufi kitchen, Tea kawai Khaleesat ta sha da Cookies sannan ta
dauko jakarta zata wuce makarantar, makullin gidan ya mika mata yace "The
house key...." Ta tsaya tana kallonsa, sai kuma tace "Ain't u using
it?" Ya daga kafada yace "Will sort my self out" Shiru tayi at
first, can kuma ta nufesa ta amshi makullin tace "Thank you" Yace
"You are welcome" Daga haka ta fita daga gidan ta kullo masa kofar.
Khaleesat na tafe tare da Safiyyah dake mata mitar Ya Mustapha yace bata daga
kiransa, ita dai Khaleesat tafiyarta kawai take bata ce komai ba, Safiyyah ta
tsaya tace "Ohh ga gantalalliya na maki magana ko?" Khaleesat ta
tsaya tana kallonta tace "To me zan ce Sophie? Ke kanki kinsan ina da
wanda zan aura to menene amfanin in daga wayar Yaya Mustapha? Beside wallahi ko
da bani da wanda zan aura ni bazan kulasa ba, ai ana barin halaq ko don
kunya" Da wani expression Safiyyah tace "Ban gane ba, as per cewar
Surayya cousin sis dinki ce ko kuma kawarki ce? Where did u know her from? Meye
hadinki da ita da har za a bar halal don kunya? Can you hear ur self pls? If
you are not interested in my cousin brother ba sai kin ta corner corner ba kina
kawo zancen da hankali ma bazai dauka ba, meye hadinki da wata Surayya da zaki
bar halal don kunya?" Khaleesat tace "Ni dai don girman Allah ki ma
bar wannan zancen, Ya Mustapha kuma kiyi ma Allah ki gaya masa i am engage, ni
bazan daga kiransa ba" Safiyyah tace "Wallahi bazan fada ba ai kina
da baki ki gaya masa da kanki, ke da wa aka yi engaging da zance masa u are
engage? Ai as far as i am concern ni ban san wannan batun ba, kawai nasan kina
da wanda baki da wani option sai na aurensa, but as time goes on ke kanki zaki
san kina da option, za kuma ki ji baza ki iya auren ba sai dai duk abinda zai
faru ya faru" Khaleesat ta taΙe baki tace "Kin ga ni yunwa nake ji
zan tafi gida, sai gobe in mun hadu" Safiyyah bata tanka ta ba ta ci gaba
da tafiya ta bar ta tsaye a wajen, Khaleesat ta bi ta da kallo, to wai ma ta
yaya zata daga kiran Ya Mustapha, ita a rayuwarta abinda tasan in an mata
bazata ji dadi ba ko by mistake ne bata yi ma wani, ita Safiyyah in ita ce a
shoe din Surayya ya zata ji, wannan ai son zuciya ne ma kawai, bin bayanta
Khaleesat tayi tace "Ni dai tunda ba mu da aji mu je gida pls ki mana
girki i am very hungry and at the same time tired from yesterday's
journey" A haka ta samu ta lallaba Safiyyah dake jin haushinta suka kama
hanyar gidanta, suna sauka daga Uber ta nufi apartment dinta tana kallon Garage
taga babu motar Housemate dinta, does this mean a bude ya bar kofar tunda
makullin na hannunta, tana murda kofar taji sa a kulle, to ina ya samu key? ko
dai magana yayi aka basa wani makullin, bude jakarta tayi ta ciro key ta bude
kofar suka shiga cikin living room din tare da Safiyyah dake biye da ita,
Safiyyah ta dinga bin parlon da kallo ta lumshe ido tace "Kai amma wannan
turaren Housemate din naki ba dai dadin kamshi ba, the perf is so cool"
Khaleesat dai bata ce mata komai ba, ta ajiye jakarta da mayafi ta zauna saman
kujera tana ciro wayarta a jaka, Safiyyah ta zauna ita ma kan kujera tace
"To kun hadu da Abdul din a Nigeria?" Khaleesat tayi shiru cause
kawai taji ita ko maganar Abdul ma bata son ana mata yanzu, ganin yanda
Safiyyah ta tsareta da ido, a takaice tace "Eh... me zaki dafa mana pls,
wllhi yunwa nake ji" Safiyyah ta mike tace "Toh bari in je in ga what
is available in the kitchen" Daga haka ta mike ta nufi kitchen, tana shiga
bayan few minutes sai ga ta ta fito, tana kallon Khaleesat da mamaki tace
"Kee wai Housemate din naki ne ke maku restocking abubuwa a kitchen haka?
Look how ur kitchen is stocked up with costly food items, where is he getting
the money to buy all this from?" Khaleesat tace "Baza dai kiyi girkin
ba kenan in zo inyi?" Safiyyah tayi dariya tace "No wallahi mamaki
nake naga abubuwa masu tsada yake siya, don ni dai nasan kudin da Abdul ke turo
maki bazai taΙa siya maki wnn uban abubuwa dake kitchen din nan ba, anya bazan
dawo gidan nan ba kuwa Khaleesat? Kinga wasu tsadaddun cookies da drinks da na
gani, even the table water in this kitchen ba na yara bane wallahi, the fridge
is full to the brim" Khaleesat taki tanka ta tana danna waya, hakan yasa
Safiyyah ta juya ta koma kitchen tana kara jaddada anya bazata dawo gidan ba
kuwa, Lafiyayyen girki Safiyyah ke yi a kitchen din komai baja baja malam,
Sallah kawai Khaleesat tayi a daki ta dawo ta kwanta kan 3 seater tana danna
wayarta waiting for the food to be ready, kiran Abdul ne ya shigo wayar
hannunta, sosai gabanta ya fadi lkci daya mood dinta ya canza ta hade rai, ta
dinga kallon screen din wayar fuskarta babu fara'a tana jiran sai ya kusa
katsewa kafin tayi picking call din, dai dai nan taji alamar ana bude kofar
parlon, ta mike zaune tana gyara scarf dinta sai ga Housemate dinta ya shigo
parlon, sallama yayi ganinta zaune living room din, ta ajiye wayar hannunta ta
fasa picking call din Abdul din ta amsa sallamar House mate din nata, yana cire
takalman kafarsa yace "Good evening" Ta sauke idonta tace "Ina
yini" Yace "Alhamdulillah, bakuwa kika yi?" Double foot wear da
ya gani bakin kofar yasa yayi tambayar, tace "Um she is my course
mate" Yace "Good" Daki ya nufa, sai a sannan ta kalli wayarta
taga kiran Abdul har ya katse tuntuni, she wasn't bothered at all kuma bata yi
attempting bin kiran nasa ba ta ajiye wayar kawai, mikewa tayi ta wuce kitchen,
tare suka fito kitchen da Safiyyah bayan Safiyyar tayi dishing masu abincin a
plate daya, Safiyyah na bin parlon da kallo tace "Ko dai Housemate din
naki ya dawo ne kamshin turaren nake kara ji a parlon" Khaleesat ta dau
spoon ta fara cin abincin tace "Ko dai kin san sa ne Safiyyah?"
Dariya Safiyyah tayi tace "Ina kuwa na san sa, kawai so nake in gansa ne
wallahi, irin wannan kayan alatu a kitchen haka, where is he even getting the
money shi da ya zo ta scholarship" Khaleesat dai cin abincin gabanta kawai
take taki ce mata komai, Safiyyah ta dau spoon ta fara cin abincin ita ma, basu
jima da fara cin abincin ba sai ga shi ya fito daga dakinsa, bai kalli
direction din da suke ba ya nufi kofa rike da laptop dinsa, Safiyyah ta bi sa
da kallo kamar idonta zai fita ya bi sa, ita dai Khaleesat kallo daya tayi masa
ta ci gaba da cin abincinta har ya fita daga parlon ya kulle masu kofa,
Safiyyah ta ajiye spoon din hannunta tace "To fa, shi kuma haka yake? Ji
wani Ιaga shoulders da yake ko kallon inda muke bai yi ba, haka yake maki a
gidan dama?" Khaleesat tace "You can be funny Safiyyah" Safiyyah
ta hade rai tace "No like seriously haka yake feeling kansa? Ko don
abincin da yake ajiye maki na yan gayu a kitchen ne ya ja haka? Ta yaya zai
wani wuce mu babu ko Hi, ni fa bana son harkan walakanci" Khaleesat tace
"Look Safiyyah ni ba shi ya ajiye min duk abinda kika gani a kitchen ba,
shi baya ma zaman gidan nan, jifa jifa kawai nake ganinsa, beside ai mun gaisa da
ya shigo kina kitchen, to kuma kallon me zai yi mana don zai fita?"
Safiyyah zata yi magana wayarta ya fara ring, mikewa tayi ta dauko wayar, ta Ιan
buda ido tana kallon Khaleesat tace "Ke Abdul ne ke kirs" Sosai gaban
Khaleesat ya fadi ta ajiye cokalin hannunta ta dinga kallon wayar Safiyyah,
Safiyyah ta rike haΙa tace "Ikon Allah, ko ya kiraki baki daga bane? Let
me pick dai inji me zai ce" Da sauri Khaleesat ta kamo hannunta zuciyarta
na bugawa tace "Safiyyah kar ki ce masa naje Nigeria plss cause bai sani
ba wallahi" Safiyyah ta saki baki tana kallonta hangangan, da mugun mamaki
tace "Ban gane bai sani ba? To wa yayi sponsoring tafiyar taki? Ina kika
samu kudin tafiya" Sosai hankalin Khaleesat ya tashi a lkcn, tana girgiza
ma Safiyyah kai tace "Just don't tell him pls, nace maki bai sani ba"
Safiyyah da mamaki ya kasa barin ta tace "Ai kiran nasa ma ya katse"
Khaleesat taji gaba daya abincin ya fita ranta, sai ga kiransa ya sake shigowa
wayar Safiyyah, Safiyyah ta gwalo ido tace "Abdul ne da kirana har sau
biyu? Anya lafiya" Khaleesat tayi gathering courage tace "Just pick,
in ya tambayeki ni kawai kice masa bani da lafiya yanzu ma kika baro
gidana" Safiyyah tace "Ohk" Picking call din tayi ta saka
handsfree, ita ta masa sallama ya amsa yace "Ya kike?" Safiyyah tace
"I am good" yace "Are you together with Khaleesat?" Babu
bata lkci Safiyyah ta sanar masa exactly abinda Khaleesat tace ta gaya masa, ya
dan yi shiru at first, sai kuma yace "Tun yaushe ne bata da lafiya?"
Safiyyah ta kalli Khaleesat, da sauri Khaleesat tayi mata alamar sati daya da
fingers dinta, Safiyyah tace "Yau ina jin sati daya kenan" Daga daya
bangaren yace "Sati daya? Me yasa ba a gaya min ba, and what's wrong with
her?" Safiyyah tace "Oh ni na zata ai ta gaya maka" Abdul yace
"Wani irin rashin lafiya take haka dake hindering dinta from picking
calls?" Safiyyah ta wani yamutse fuska jin useless question din da yake yi
taki basa amsa tana kyabe baki, ita dai Khaleesat gabanta sai faduwa yake, Yace
"Where is she now?" Sounding uninterested with the conversation
Safiyyah tace "Tana gidanta mana" Da sauri Khaleesat tayi typing a
wayarta sannan ta nuna ma Safiyyah, bayan Safiyyah ta ga abinda Khaleesat ta
rubuta tace "Jikin nata dai da sauki sosai fa" A takaice yace
"Thanks" Daga haka ya katse wayar, Safiyyah ta ajiye wayarta tace
"Tirrrr, ki ji wani magana gatsau gatsau kamar dan daba, ko tashi
hankalinsa fa bai yi ba, ni wallahi da ina da yanda zanyi ku rabu rabuwa na har
abada da Abdul din nan wallahi yi zan yi, ko kadan bashi da features din miji
na gari, babu caring babu tausayi babu affection, so pompous and full of
himself always, nonsense and ingredient, wallahi in wani mutumin kirki ne da
yanzu hankalinsa ya tashi duk ya birkice min a waya amma kiji yanda yake magana
a tsattsaye kamar ubana daga karshe wai Thanks, kamar wanda nayi ma albishir me
dadi wai Thanks, ke ki ji fa wai thanks" a hankali Khaleesat tace
"Baza ki gane ba Safiyyah, nima naji i am fed up with him, na gaji da
halinsa yanzu" Safiyyah ta rike haba da sauri tace "Ke Khaleesat, anya
kece ke fadin haka kuwa?" Khaleesat ta wani taΙe baki ta jawo abinci ta
fara ci tace "Kawai naji na gaji all of a sudden wllhi" Safiyyah ta
sako baki tana mata kallon mamaki, can tace "Ni ba wannan ba ma, Khaleesat
wa yayi sponsoring flight dinki zuwa Nigeria?" Khaleesat ta daga kai tana
kallonta amma tayi shiru, Safiyyah tace "Kin yi shiru, waye ya biya maki
kudin jirgi?" Khaleesat ta sauke idonta kamar bazata ce komai ba sai kuma
tace "Housemate dina ne ya siya min Ticket" Safiyyah ta gwalo ido da
wani expression na mamaki sosai tace "Ban fahimta ba Khaleesat, Housemate
dinki as how?" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Eh shi ne ya
biya min ticket din jirgin...." Khaleesat bata boye ma Safiyyah duk yanda
aka yi Housemate din nata yayi sponsoring tafiyarta ba, Safiyyah was totally
speechless and Surprise, after few seconds tace "Did you know what flight
ticket is saying from USA to Nigeria Khaleesat?" Khaleesat tace "I
went to Nigeria in business class and came back in Business class Sophie"
Buda baki Safiyyah tayi ba tare da ta san tayi hakan ba tana kallon Khaleesat
kamar idanuwanta za su fito, a hankali tace "Business class fa kika ce
Khaleesat?" Khaleesat ta gyada mata kai, Safiyyah ta fara bin gidan da
suke ciki da kallo that is for the average here in America, da wani Expression
tace "Business class? To me yake yi a wannan gidan if he is doing this
well that he can afford to pay for business class to and fro? Dama ni tun daga
irin abubuwan da na gani a kitchen nasan wannan mutumi might be trying to disguise
himself for a reason best known to him, idan ba haka ba why share an Apartment
bayan zai iya affording shi kadai ya zauna a gidan, beside zai iya samun wanda
ma yafi wannan in a more better area" Ita dai Khaleesat kallon Safiyyah
kawai take ganin yanda tayi concluding lokaci daya, Safiyyah ta wani juya ido
tace "Or did he have any mission here da bamu sani ba?" Khaleesat ta
girgiza kai tace "Daga sanda nayi misplacing makullina ne ya fara kwana
gidan nan tunda yasan bani da makulli, amma tun da yayi move in zuwa gidan nan
i can count sau nawa ya kwana if i remembered well, baya kwana nan wallahi, ba
har na gaya maki ba...." Safiyyah tayi dariya tace "But i am trying
to understand me yasa yake zaune a gidan nan, ko dai ya sanki from somewhere ne
shine ya dawo nan saboda ke?" Khaleesat tace "Ji fa wani magana, bai
san ni a ko ina ba wallahi, ni bamu taΙa haduwa da shi ba, ranan da suka fara
zuwa gidan i overheard him asking if his housemate is a Male or female, lkcn
ina dakina, kilan he is in a haste to settle down ne shi yasa kawai he opt for
this, amma bai san ni ba wallahi" Safiyyah dai tayi wani murmushi tace
"Ae shikenan we shall see" Sai kusan karfe bakwai Safiyyah ta bar
gidan shi ma saboda azababben kiran da Ya Mustapha ke mata ne, tana mita haka
ta bar gidan, bayan Khaleesat ta rakata ta dawo tayi sallahn magarib a nan
parlon tana zaune saman darduma bayan ta gama azkar ta dau wayarta don dubawa
ko Ummanta tayi mata reply, tun Safiyyah na nan suke Voice chat da Ummanta da
kannenta, ganin Umma bata yi reply ba ta gane wayar ya mutu don dama Umma tace
mata babu caji wayar ta kusa mutuwa, mamakin Abdul kawai Khaleesat ke yi a
ranta, duk da ce masa da Safiyyah tayi bata da lafiya amma har yanzu bai kira
wayarta ba, ko ta Whatsapp bai mata magana ba, tana cikin wannan tunanin taji
an bude kofar parlon, juyawa tayi Housemate dinta ya shigo, sallama yayi
ganinta a parlon, ta dauke idonta ta amsa, ya karaso cikin parlon without
looking at her ya tafi inda Books dinsa suke yace "Kawar taki ta tafi
kenan...." Khaleesat tace "Ina yini" Yace "Good evening
Halysaah" Bayan ya gama daukan text books da zai dauka ya dawo cikin
parlon yace "Alright Good night" Ta bi sa da kallo, sai da ya nufi
kofa ya sake juyowa yace "Sai da safe" Ta sauke idonta tace
"Allah ya kai mu lafiya" Daga haka ya bude kofar ya fita tana jin ya
kulle kofar da makulli daga waje. Washegari Khaleesat bata da karatun da za su
yi a makaranta, don haka har karfe goma bata fito parlor ba tana kwance, ita
har sannan fa ta kasa daina mamakin Abdul don har sannan bai kirata ba, tashi
tayi daga karshe ta shiga bandaki tayi wanka ta shirya, wajen karfe goma da
minti arba'in ta fito daga dakinta, kwance taga Housemate dinta saman 3 seater
yana bacci, kulle kofar da tayi ne yasa ya bude ido a hankali, walking slowly
ta karaso cikin parlon, juyawa yayi bayan ya sake rufe idonsa as if murmuring
yace "Good Morning Halysaah" Tace "Ina kwana" Bai bude ido
ba bai kuma amsa ba alamar ya ci gaba da baccinsa, ita dai ta wuce kitchen.
After an hour Khaleesat ta fito daga kitchen bayan ta gama girkin da take,
zaune ta gansa a parlon ya dafe kansa, tsayawa tayi tana kallonsa, ya daga kai
suna hada ido ta Ιan koma baya tace "Is everything okay?"
07087865788✍π»
[5/6, 4:37 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
9.....
Still bai dago kansa ba yace "Tashi na kika yi" Ta
Ιan bude ido tana kallonsa tace "How?" Ya koma ya kwanta ya rufe ido
yace "With the noise ur utensils were making in the kitchen" At first
kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "To ai ba nan ya kamata ka kwanta
kana bacci ba" Ya bude ido yace "Ok u intentionally woke me up
kenan?" tace "Ni ban ma san kana parlon ba ai..." Murmushi kawai
yayi bai ce mata komai ba, tana Ιan kallonsa a hankali tace "I made some
breakfast, you can have some" Yace "Ok thanks, baki je schl yau
ba?" Tace "Ba mu da lectures" Yace "Ohk, wani school
kike?" Shiru tayi tana kallonsa, ya mike zaune yace "University of
Maryland Baltimore? Loyola University Maryland? Morgan state University?
Stevenson University? Johns Hopkins University?" Tace "Duk kuma a nan
garin su ke?" Yace "Ohh, kina gari baki san makarantun dake garin
ba?" Ta girgiza masa kai kawai still looking at him, shi dai bai kalleta
ba yace "To ke wanne kike zuwa a cikinsu?" Ta sauke idonta tace
"Na karshen da ka kira" Ya Ιan yi murmushi yace "John Hopkins
kenan? Buh ni ban taΙa ganin ko me kama dake a schl din ba ai" Yayi dariya
yace "Just joking kafin ki fara min kuka" Ta wani kallesa, duk wannan
abun bai kalli direction dinta ba yana magana ne yana kallon agogon wrist
dinsa, yace wani course kike yi?" Tace "Pharmacology" Sai a
sannan ya kalleta yace "Really?" Ta gyada masa kai, yace "That's
a very good course, year what kike yanzu?" Calmly tace "Year 3"
Ya gyada kai yace "Good, Allah ya bada sa'a" Ta sauke idonta tace
"Ameen" Yace "Ban yi tunanin makarantar kike ba da na dinga
dropping dinki in zan je ai, ko da yake ba lallai sanda zan je kina da Class
ba...." Sunan wani lecturer dinsu ya kira mata, kawai ta Ιan yi murmushi
tana kallonsa cause he is one of her favourite lecturer, yace "He took us
during our Undergraduate Degree, and Master's degree also, that was 3 years
back, and he is still among my Supervisors currently...." Khaleesat dai
sai kallonsa take, ta kasa hakuri har sai da tace "And you are still a
student till date?" Ζan murmushi yayi yace "I am a Medical Dr,
pursuing my PhD on Cardiology" Khaleesat couldn't stop staring at him,
Yace "I have been studying since i was a baby" Tace "Amma
lecturer kake son zama?" Er dariya yayi yace "Not at all
Halysaah...." Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba tana kallonsa, ya
dau wayarsa da ake kira ya mayar ya ajiye yace "Kin ci abincin ne a
kitchen naga ban ganki da plate ba as usual?" Ta wani kallesa bata ce
komai ba ta juya tayi wucewarta daki, shayi ta sha da cookies a kitchen sanda
take girki, bayan ta gama girkin kuma taji bata ma jin yunwan shi sa bata zuba
abincin ba, Khaleesat ta koma dakinta da kusan 45 minutes tana duba wani course
dinsu ta laptop taji kamar ana knocking din kofar parlor, ta mike ta fito
parlorn, tsaye taga Housemate dinta bakin kofar living room din har ya bude
kofar, Safiyyah ce ta shigo parlon tana kallonsa tace "Hello" Ya
dauke idonsa yace "Hi" Komawa daki Khaleesat tayi, Safiyyah tace
"Pls is Khaleesat around?" Yace "Sure...." Dakin Khaleesat
ta nufa, shi kuma ya tafi ya ci gaba da karatun da yake a parlor, Khaleesat ta
mike tana kallon Safiyyah bayan ta shigo dakinta tace "Why are you looking
this way Sophie?" Safiyyah tace "Wallahi kwanan nan zaki ji nayi ma
matar can duka a kasar nan" Khaleesat tayi murmushi tace "Me kuma
tayi maki again?" Gefen gado Safiyyah ta zauna kana ganinta kasan ranta a
bace yake tace "Tun fa da kika je gidan mugun halinta ya ninku akan wanda
take min a baya Khaleesat, she is trying all possible best to make the house miserable
for me, dama yanzu ta dena ajiye min abinci kwata kwata, cornflakes da Golden
morn sai ta boye a dakinta da sunan taje hada ma yaronta ne duk don kar in
sha...." Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "To Allah ya kyauta,
ko zaki dawo nan?" Safiyyah tace "In dawo nan for what reason? ashe
ma riba ta ci kenan idan na bar mata gidan, ai we die together with her in that
house, babu inda zan dawo wallahi, kawai rabon ta ci duka ne ba wani abu
ba" Lkci daya expression din Safiyyah ya canza daga bacin rai ta kamo
hannun Khaleesat tana washe baki tace "Kee naga Housemate dinki ido da ido
yau, dama haka yake gayen? Wallahi he is so well flavoured komai yaji, ina masa
magana ma ko kallona bai yi ba amma ya amsa min cikin girmamawa, wallahi ya
burgeni" Tana blushing ta karasa maganar nata, Khaleesat dai ta saki baki
ta kasa cewa komai, can ta kalli kofar dakinta da sauri don ta tabbatar a kulle
yake kar ace yana jiyo Safiyyah, sai kuma tayi kasa da murya fuska daure tace
"Meye haka Safiyyah what if yana jin ki?" Safiyyah tace "Wallahi
raina a bace yake amma yana bude kofar kawai na mance da abinda er iskar matar
can ta min, a very calm gentleman, yace min Hi nace Hello... kuma kuna Hausa da
shi ko turanci ku ke? Ni sai nake ga kamar ba bahaushe bane ba fa"
Khaleesat ta hade rai sosai tace "Don Allah ki rufa mana asiri Sophie,
What's all this?" Safiyyah tayi dariya tace "Ni dai kinyi girki? Don
wallahi yunwa nake ji" Khaleesat ta mike ta nufi kofa ta fita daga dakin,
a corridor ta gansa zai shiga dakinsa, bai kalli ma wanda ya bude kofa ba yayi
shigewarsa daki, Khaleesat ta tafi kitchen ta dibar ma Safiyyah abincin da ta
girka, jin alamar har ya fito daga dakin nasa ta dawo parlor ta tsaya sai gashi
ya shigo parlon, makullin motarsa taga ya dauka da wani littafi, ya daga kai
suka hada ido ta fara kame kame tace "Ain't you eating the food?"
Yace "Oh, ok na manta" Kitchen din taga ya nufa ta bi sa da kallo,
sai da ya shiga sannan ta bi bayansa zata gaya masa kar ya bar mata plate bai
wanke ba, tsaye ta gansa kusa da abincin ya dau spoon ya bude tukunyar sannan
ya debi shinkafar kadan ya kai baki, kallonsa kawai take da mamaki, ya juya ya
kalleta yace "Bad habit right?" Sake dibar abincin yayi ya kai baki,
daga haka ya rufe tukunyar yace "Kinga ni ba yunwa nake ji ba, I am
full" Ta dinga kallonsa, bata san sanda tace "Ko in zuba maka ka tafi
da shi?" Ya bude fridge ya ciro bottle water yace "Aa in na dawo
anjima zan ci" Daga haka ya fita daga kitchen din ya nufi kofar living room
ya bude, sai a sannan ya juya, ta dauke idonta, yace "See yah" Fita
yayi ya kulle kofar daga waje. Sai wajen karfe shidda na yamma Khaleesat ta
raka Safiyyah zata hau Uber da tayi ordering, Safiyyah na kallonta tace
"Ya Mustapha dai ya hakura dake, jiya nake gaya masa gaskiya kina da wanda
zaki aura a gida, don nima na gaji da damuna da yake yi shi sa kawai na gaya
masa, ai ko ina gaya masa yace to shikenan dama tun farko ai da kin gaya masa
he will understand" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "To ai
kinga gwara haka" a haka suka rabu Khaleesat ta koma cikin gida, har goma
na dare bata ji shigowar housemate din nata ba hakan yasa ta gane bazai dawo
gidan ba ranan. Washegari da safe ta shirya ta tafi makaranta, bata dawo gidan
ba sai kusan karfe hudu na yamma, tana shiga living room ta gane ya dawo gidan
da bata nan, bedroom dinta ta wuce bayan tayi wanka tayi sallah ta canza kaya
ta fito kitchen zata yi Ιan wake don shi ne a ranta, bayan ta gama hada duk
ingredients din taji an bude kofar parlor, ta dai ci gaba da abinda take,
kitchen din ya shigo ya ajiye ledan hannunsa yace "Good evening
Halysaah" Tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, Are you
baking?" Ta kalli flour din da take kokarin kwabawa tace "No"
Yace "What are u using flour for?" Bata yarda su hada ido ba tace
"Dan wake" Da mamaki yace "Meye shi?" Ta wani kallesa ganin
da gaske jiran amsarta yake tace "Dan waken ne baka sani ba?" Yace
"Ban san shi ba" Tace "Toh zaka gansa" Turning stick ta
dauko ta fara kwabin danwaken shi dai yana tsaye yana kallo, yace "Hey,
why did it change to that color? Ko dai ba flour bane?" Ta Ιan kallesa
amma taki basa amsa, yana ta kallo with astonishment har ta gama kwabin, sannan
ta wanke hannu ta fara saka dan waken a ruwan dake tafasa kan gas, shi dai
kallonta kawai yake, can yace "To haka ake cin sa?" Tace "Aa da
bread ake ci" Sounding amused ya kalli sauran bread din dake a kitchen din
yace "Really?" Bata san sanda tayi murmushi ba batare da ta sake ce
masa komai ba don taga da gaske ya yarda da Bread za a ci Ιan waken, he
couldn't stop looking at her and the food har ta gama, ya ga ta soya man gyada,
sannan tayi dishing din abincin a plate, ta saka eggs din da ta bare a gefe, ta
dauko roban yaji, yace "Dama wai wannan abincin ne? To ai na san sa when i
was a kid, idan munje wajen Grandma dinmu tana mana" Without looking at
him tace "Da ka girma ne ka dawo America ka mance sa kenan" Dariya
yayi ya karasa cikin kitchen din yace "Ohk, Can i taste some inji yanda
yake?" Komawa gefe tayi bayan ta saka cokali a danwaken, ya dau cokalin
ita dai kallonsa kawai take har ya Ιan juya Ιan waken ya debi seed biyu ya kai
baki, she couldn't stop looking at him yana tauna abincin gently as if trying
to figure out the taste, can ya karyar da kai yace "It's nice, i like it,
i still remember the taste, it's nice" Murmushi kawai tayi, ya sake diban
abincin ya kai baki, tace "To kaje da shi, i will make another one"
Yace "Aa bazan iya cinyewa ba ai" Yana fadin haka ya dauko wani plate
din ya debi Ιan kadan a ciki yace "Thank you" Ta karasa ta amsa
cokalin a hannunsa ta kara masa Ιan waken ta saka masa kwai daya, ya kalleta ya
Ιan bude ido yace "Thanks Halysaah, but seriously I can't finish all
this" Tace "Eat and remain" Ruwa ya dauka a fridge ya fita daga
kitchen din. Khaleesat na idar da sallan Isha'i ta fito parlor zata dafo black
tea don tana son tayi karatu har zuwa karfe dayan dare, tunda ta shiga daki
daxu da yamma bata sake fitowa ba sai lkcn, bacci ta tarda Housemate dinta yake
yi a 3 seater, da mamaki take kallonsa ganin wai bacci yake bayan Isha'i, ita
bata ma san yana gidan ba sai yanzu da ta fito, kallon wayarsa dake gefensa
tayi ganin yana haske, ta leka screen din taga an rubuta A-jay, kiran na
katsewa taga 5 miss calls aka yi masa, kamar ta tashesa sai kuma dai bata yi
hakan ba, ta dau wayar kawai tana dubawa taga babu password balle pin a jiki,
cire wayar tayi a silent mode sannan ta mayar inda ta dauka tayi wucewarta
kitchen, ta gama dafa shayi ta fito parlon kenan taji wayar ya fara ringing
loudly, da kyar ya bude idanuwan sa, ita dai ta koma kusa da kofar kitchen din
ta makale a jiki, ya Ιan kalli wayarsa ya jawo yana duba screen din, Ιaga kiran
yayi ya kai kunne yayi shiru har sannan yana lullumshe ido, can ya ja tsaki ya
ajiye wayar sannan ya mike zaune, har sannan bai ganta ba ita ma bata bar jikin
kofar da ta makale ba, mikewa tsaye yayi daga karshe yana lumshe ido, gani tayi
kamar baccin yake yi a tsayen, ta wara ido tana kallonsa with shock , sai da
yaga ya kusa faduwa sannan ya bude idonsa sosai, ta kai hannu bakinta saboda
dariyar da taji ya taho mata, tafiya yayi ya isa jikin pillar dake parlon ya
jingina ya rufe ido, kasa daina kallonsa tayi da mamaki, he stood there for
almost 3 minutes yana bacci, ringing din wayarsa ne yasa ya bude ido da sauri
as if frightened, kitchen ta shige don bata son yin dariyar da ya taho mata a
wajen, sai a sannan ya ganta bayan ta shige kitchen da sauri, ya fara bin
parlon da kallo as if trying to understand what was happening, lkci daya idonsa
yayi clearing gaba daya ya fara sosa kai, at first bai yi niyyar bin ta kitchen
din ba, can kuma dai ya nufi kitchen din, ta ajiye kofin shayin hannunta ta
dafe cabinet tana dariya ciki ciki, tana ganinsa ta hade rai tana juya shayinta
da cokali as if nothing happened, fridge ya bude ya dau ruwan gora yana
kallonta yace "You are still awake?" Ta Ιan kallesa tace "To
karfe nawa ne yanzu da zan yi bacci, as if i am you" Bai ce komai ba ya
fita daga kitchen din, murmushi tayi ta bi sa da kallo, daukan shayin tayi ta
bi bayansa, taga ya dau makullin motarsa da waya without looking at her yace
"Good night Halysaah" Bata san sanda tace "To kar fa kaje kana
driving bacci ya dauke ka a kan steering" Bai kalleta ba sai murmushi da
yayi kawai ya nufi kofa, ta bi sa da kallo har ya fita sannan ya kulle kofar ta
waje, karasawa kusa da window tayi ta Ιan bude curtain kadan tana kallonsa har
ya shiga motarsa a garage yayi reverse, sai da ta daina hangen motarsa sannan
ta sake curtain din a hankali, tafi minti uku a tsaye wajen ta jingina da
window, daga karshe tana tafiya a hankali ta wuce dakinta bayan ta kashe wutan
parlon..... Washegari Khaleesat na sauka daga Lyft bayan ta dawo school taga
motar Housemate dinta heading toward the garage, kafin ta karasa apartment din
nasu har ya shiga ciki, murda kofar tayi taji a bude ya bar mata alamar ya
ganta shi ma, tana shiga parlon yana fitowa daga kitchen rike da Lemon
gwangwani me sanyi, ya karaso cikin parlon yace "Are you just coming back
from school?" Gaishesa tayi, yace "Good evening Halysaah"
Bedroom dinta ta wuce ta bar sa a parlon, it's almost 6pm na yamma kuma
Safiyyah ce ta bata masu lkci tana mata bayanin wani course dinsu da tace bata
ganewa, wanka Khaleesat tayi ta sauya kayan jikinta zuwa kananun kaya sannan ta
saka hijab ta fito parlor, yana parlon har sannan yana operating laptop dinsa,
ganin zata shiga kitchen yace "Ki bari ki hutu, zan fita sai na siyo
abinci" Khaleesat ta kallesa tace "I am cooking noodles" Yace
"Ohk then" Tana fadin haka ta wuce kitchen, Ya mike ya wuce dakinsa
da laptop dinsa, cikin mintunan da basu da yawa Khaleesat ta gama dafa noodles
din da take, ba da yawa ta dafa ba don bata san ko zai ci ba, zata yi dishing
din abincin a plate taji ana knocking kofar parlor, ta ajiye plate din hannunta
sannan ta fito daga kitchen din, Housemate dinta ta gani har ya fito shi ma to
check on who is at the door, amma ganinta kawai ya juya ya koma dakinsa,
karasawa tayi ta bude kofar, lkci daya taji komai ya tsaya mata cak ta dinga
kallonsa babu ko kiftawa kamar ranan ta fara ganinsa, Yana kallonta daga sama
har kasa yace "Meye kike kallo na haka Malama?" Tayi wani yake
zuciyarta na bugawa tana in-ina da kyar tace "Ya Abdul, I.. I.. was
surprised, san..nnu da zuwa" Da sauri ta juya ta koma parlon, ya bi
bayanta yana duba wayarsa dake vibrate a hannunsa alamar ana kiransa, ita dai
ta koma bayan kujera ta tsaya kamar munafuka tana kallonsa zuciyarta na bugawa
sosai, kana ganinsa kasan ba a lkcn ya shigo America ba, probably tun daxu ya
shigo ya sauka hotel, ya Ιaga kiran da ake masa ya kai kunne, tana ganin haka
ta juya ta nufi corridor din dakunan apartment din tana waige waige, ganin
attention dinsa na kan wayar da yake ta bude kofar dakin Housemate dinta ta
shiga da sauri ta kulle kofar, Housemate dinta ya juya yana kallonta da mamaki,
gaba daya a rude take ta nufesa tana yarfe hannu ta duka kusa da shi, ya mike
still looking at her with surprise yace "Are you alright Halysaah?"
07087865788✍π»
[5/7, 6:25 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨ HALYSAAH ✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
10.....
Khaleesat ta gyada masa kai tana rufe bakinta da hannunta
murya can kasa tace "Plss i have a visitor, i want u to plss pretend you
are not staying here, just pretend u came to drop some books for ur Female
friend living here plssss" Kamar zata yi kuka ta kare maganar tana
kallonsa, yayi shiru shima yana kallonta at first, sai kuma yace "As in
how Halysaah?" Ta marairaice masa tace "Kawai dai kayi kamar ba a
gidan nan kake ba don girman Allah ka rufa min asiri, u know my former housemate
mace ce, act as though u are her friend, kayi kamar wajenta ka zo pls, don
Allah ka taimake ni" Bata jira cewarsa ba ta mike ta juya da sauri ta fice
daga dakin kafin Abdul ya biyo ta, ya bi ta da kallon mamaki baya ko kiftawa,
can kawai yayi murmushi ya zauna ya ci gaba da abinda yake yi a Laptop dinsa,
parlor Khaleesat ta dawo suka kusa cin karo da Abdul da ya nufo corridor yace
"Me kika je yi a ciki? You didn't even get me something to drink" Ta Ιan
yi murmushi a hankali tace "Why didn't you let me know u are coming? Me
yasa baka gaya min zaka zo ba?" Yace "Sai na gaya maki in zan zo? Ko
ke zaki biya min ticket din jirgin?" Ta girgiza kai cikin sanyin murya
tace "Aa ba haka nake nufi ba, ya hanya?" Yana kallonta daga sama har
kasa yace "What is wrong with you, why were you sick?" Ta sauke
manyan idanuwanta kasa a hankali tace "I don't know too, but i am much
better now, naji sauki Alhamdulillah" Yace "Rashin lafiyar ne yasa
kika dena daga kirana all this while?" Ta marairaice masa tace "Don
baka san yanda nake ji bane a sannan, let me get you water to drink" Daga
haka ta wucesa da sauri, ya bi ta da kallo har ta shiga kitchen, Khaleesat ta
jingina jikin cabinet din kitchen din ta dafe kirjinta that was heaving so
fast, after few seconds ta sauke numfashi sannan ta dau tray ta bude fridge ta
dauko ruwa da lemo da glass cup sannan ta fito daga kitchen, zaune ta gansa a
parlon yana danna wayarsa, ta karasa ta duka gabansa ta ajiye masa ba tare da
ta bari sun hada ido ba, shi dai tunda ta fito kitchen din yake bin ta da ido,
ta zauna kan carpet ta tankwashe kafarta ba tare da ta bari sun hada ido ba
tace "Ya su Mumy da Daddy?" Jin yayi shiru ta daga idanuwanta ta
kallesa taga kallonta kawai yake, a hankali ta sauke idonta kasa, yace
"Duk kwana biyun nan kin canza Baby, you don't look critically ill da har
zaki kasa daga kirana, menene yasa kika dena kirana kuma idan na kira ki ki
dagawa? Common WhatsApp kin dena min magana yanzu" Ta kasa kallonsa, tana
wasa da gefen hijab dinta a hankali tace "To kwanan nan sai kayi ta min
fada ta waya baka considering dina, ga kuma course dinmu da wahala ka
sani" Ita kanta ta rasa dalilin da yasa hawaye ya cika idonta, He let out
a sigh har a sannan yana kallonta, sai kuma ya dagota sitting her down by his
side, gabanta ne ya fara faduwa, in da akwai abinda ta tsana kuma take fargaba
a rayuwarta bai wuce Abdul ya zo America wajenta ba, duk da yawanci zuwan da
yake it's either tare da Mom dinsa or his Dad, amma duk da haka a dar dar take
da shi saboda wasu abubuwan da ya tsira wanda a baya baya mata haka, duk
zuwansa kasar sai ta kirko wani abu da zai maidata unhealthy wani lkcn har sai
an kai ta hospital, ita da tasan zai kamo hanya ya taho da bata fara ce ma
Safiyyah tace masa bata da lafiya ba, yana caressing fingers dinta yayi kasa da
murya yace "But you know i love you Khaleesah, ke ce kike jawowa nake maki
fada a ko da yaushe" Ita dai bata ce komai ba hawayen dake makale idonta
ya gangaro bisa kuncinta, ya kai hannu yana goge hawayen a hankali yace
"Ohk, but you know i love you so much right?" ta gyada masa kai
kawai, a hankali yace "Housemate dinki fa? Is she around?" Sosai taji
gabanta ya fadi, taki barin su hada ido tace "No ban sani ba, i saw she
had a visitor daxu ya zo nemanta, probably her friend...." Yana kallonta
yace "Friend? Namiji kenan?" Khaleesat ta gyada masa kai, lkci daya
ya hade girar sama da ta kasa yace "Yaushe ta fara kawo namiji gidan? When
did that start?" Khaleesat tayi karfin halin cewa "Dama tana kawowa
time to time ai but not frequently, sai in kilan sun kawo mata reading materials
ko bata da lafiya sun zo dubata" Yace "Kuma mazan na kwana a
nan?" Khaleesat ta hadiye wani abu da kyar tace "Ni ban sani ba
gaskiya, tunda ina dakina always a kulle ai" Kallonsa tayi to cut short
the conversation tace "Na dafa noodles yanzu bari in kawo maka kar ya
huce" Tana fadin haka ta mike da sauri zuciyarta na bugawa, dai dai nan
Housemate dinta ya fito daga dakinsa, Khaleesat taji zuciyarta ya kusa shigewa
cikinta tsabar kidimewa, tayi saurin dauke kai tayi hanyar kitchen, Abdul ya
juya jin an bude kofar daki, hada ido suka yi da Housemate din nata da ya shigo
parlon yana tafiya slowly waya kare a kunnensa duk da ba magana yake a wayar ba
hannunsa daya rike da wani Textbook, idonsa kuma na kan Abdul, hannu ya daga
masa calmly yace "Hello" Abdul ya bi sa da kallo babu ko kiftawa
without replying to his Hello, shi dai Housemate din nata yana tafiya calmly ya
nufi kofa ya fita daga parlon, tuni Khaleesat har ta shige kitchen hankalinta a
tashe ta dafe kirjinta tace "Na shiga uku....." A haka dai ta fara
zubo noodles din a plate, cike da karfin hali ta dawo parlon, Abdul dake ta
kallonta yace "Who is he Baby?" Khaleesat ta Ιan yi fari da ido tace
"Ni ban ma taΙa ganinsa ba sai yanxu, Nancy ya kawo ma littafi ina
ga" Abdul ya mike yace "Ta yaya zaki dinga rayuwa under same roof da
wani gardi Baby? Yaushe Nancy din ta fara shigo da samari gidan nan? All this
while dama yana cikin gidan nan?" A hankali Khaleesat tace "Na fa ce
maka ban taΙa ganinsa ba, i have never seen him before sai yanzu" Ajiye
abincin hannunta tayi cike da karfin hali tace "In dafo maka black
tea?" Komawa yayi ya zauna yaki cewa komai, kana ganinsa kasan he is
boiling inside, ita dai ta juya tana tafiya kamar munafuka ta koma kitchen,
mikewa yayi ya bi bayanta har zuwa kitchen din yace "Ta yaya wani banza
can zai dinga shigowa yana kalle min ke anyhow Khaleesah?" A hankali
Khaleesat tace "Ya Abdul kar ka manta communal living muke a gidan nan,
this is America.... this isn't my apartment alone, bazan iya cewa ga wa enda za
su shigo gidan ba tunda ba gidana ni kadai bace" Tsawa ya mata yace
"And so what??? An gaya maki bazan iya kama maki hayar gidan ke kadai
bane? Banda kince kina tsoron zama ke daya a gida do you think u will be
sharing an Apartment with anyone in America? Do u think I can't afford a full
apartment for you??" Har jikin Khaleesat ya fara rawa ganin how fiercely
he was speaking to her yana huci, ga idanuwansa sun fara sauya launi, sosai
take jin tsoron Abdul ita kam, hawaye ya fara gangarowa idonta muryarta na rawa
tace "Ka fara kuma ko?" Kamo hannunta yayi fuskarsa a murtuke suka
fito daga kitchen din, ta fashe masa da kuka a hankali har suka dawo cikin
parlon, cike da fada yace "Ya bazan fara ba naga wani katon banza under
same roof with you? Me yasa tun tuni baki gaya min Housemate dinki na shigowa
da gardawa cikin gidan nan ba in samar maki other alternative? Me yasa baki da
hankali baki da tunani ne ke a rayuwarki?" Zaunawa tayi ta fashe da kuka
sosai ta hade kanta da kujera, ya zauna yana huci, ita dai kuka kawai take tana
shessheka, after few minutes ya koma kusa da ita ya dagota drawing her closer
to him kamshin turarensa ya cika mata hanci, nan da nan ta hadiye kukan da take
tana zare ido, Gently yake caressing dinta murya can kasa yace "I am sorry
Baby, amma da kin gaya min da na samar maki wani apartment din ai...." Ta
fara kokarin komawa baya tana son kwace kanta daga hannunsa, kin saketa yayi a
fusace yace "Why do u always act like a Bush gal Khaleesah? Har yanzu
rayuwar Ghetto bazai fita a kanki ba? What is the meaning of this
nonsense?" Ta ki barin su hada ido, da kyar tace "To ai... This is a
promise you made, amma kuma sai ka dinga..." Cikin tsawa yace "So f
what if i break the promise? Ko ance maki tsoronki nake ne? Ko kuma wani ne zai
aure min ke dama?" Ta marairaice masa kamar zata yi kuka tace "Ni dae
bari in kawo maka black tea" zata mike ya fixgota har sae da fado kansa,
ya fige hijab din jikinta yace "Naga alamar kin ma maida ni wani gara don
kinga ina biye ki" Ta takure waje daya wasu hawayen na taruwa idonta taki
yarda su hada ido tana kokarin kwatar kanta daga grip dinsa, skirt karami ne
sosai jikinta sai half vest shi sa ma take ta yawo da hijab tun daxu da ta dawo
schl, ya sake fixgota sosai jikinsa, kuka ta fara yi muryarta na rawa tace
"Don Allah ka bari plss, this wasn't our deal, you are not keeping to ur
promise" Kallonta ya dinga yi saboda yanda tayi provoking dinsa, duk da
shi bai yi niyyar mata komai ba da ya wuce ya lallasheta amma tsabar yanda ta
hasala shi sai ya fara kokarin kissing dinta, Ζin yarda tayi tana kiciniyar
kwace kanta tana kuka, House mate dinta ne ya shigo parlon a lkcn, ya kalli
yanayin da suke da kuma yanda take struggling din kwatar kanta daga jikinsa,
direct ya nufi cikin parlorn har inda suke without a second thought ya cakumo
Abdul yana kallonsa da kyau "Hey, this is America guy, what sort of
molestation is this??" Mikewa Abdul yayi yana kallonsa da wani irin
Expression na mamaki, bai yi wata wata ba kawai ya sauke masa fist dinsa a
kirji har sau biyu, ya wani cakumosa yace "Are you insane? How dare
you??" Khaleesat ta zaro ido ta mike cikin tashin hankali ta riko Abdul
tana zaro ido with shock, lkci daya ta kalli Housemate dinta da ya tsaya yana
kallon Abdul baya ko kiftawa kuma bai yi attempting rama abinda yayi masa ba,
da kyar tace "He is my boyfriend, I don't think u have any problem with
this, who are you? And where do you know us from? You have no right to
intrude!" Housemate dinta dake kallonta ya sauke idonsa kamar bazai ce
komai ba, sai kuma calmly yace "My bad! And i am sorry, i thought u were
in danger, i am only here to drop some books, sorry about that plss"
Khaleesat ta wani kallesa tace "Do i know u from anywhere that warrant u
intruding?" Ya girgiza kai yace "Not at all... I am sorry"
Kallon Abdul yayi, bowing his head gently at the same time yace "I am
sorry, dude" Daga haka ya ajiye book din hannunsa ya juya ya nufi kofar
parlon ya fita waje, that was when Khaleesat realized she was half dressed all
this while, dukawa tayi ta fara kuka a hankali ta hade kanta da kujera tana jin
kanta na wani irin sara mata, wani kallo Abdul yayi mata yana huci, kawai ya
dau wayarsa ya nufi kofa ya fice daga parlon kamar zae tashi sama, ta bi sa da
kallo hawaye na sauka idonta, mikewa tayi da sauri ta nufi window tana duba
waje taga babu motar Housemate dinta har ya tafi, sae Abdul da ta hango yana
tafiya down the street, dawowa parlon tayi tana goge hawayen dake sauka idonta
ta dau Hijab dinta ta wuce daki da sauri, har wajen karfe tara na dare
Khaleesat ta kasa tashi daga saman darduman da take zaune ga wani ciwo da kanta
yake mata, jawo wayarta tayi a hankali, tun daxu take son kiran Abdul amma ta
kasa kiransa saboda tsoro, daga karshe tayi gathering courage tayi dialing
numbersa har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai Ιaga ba, tasan ba
lallai ya Ιaga ba dama, ajiye wayar tayi ta kwanta gefen gado wasu sabbin
hawayen na zuba idonta. Da safe duk da yanda Khaleesat ke jin ta wani iri kamar
zata yi rashin lafiya haka nan tayi shirin makaranta ta saka Facemask dinta sannan
ta bar gidan, ta kusa awa daya a makarantar kafin Safiyyah ta shigo, Khaleesat
ta zauna gefenta tana kallonta tace "Why are you sitted here Khalee? Is
the lecturer not around?" Khaleesat ta sauke idonta bata ce mata komai ba,
Safiyyah ta sauke Facemask dinta ganin swollen eyes dinta cike da damuwa tace
"Subhanallahi, what is wrong Khaleesat? Kukan me kika yi? Ko jikin Mama
ne?" Khaleesat ta girgiza mata kai hawaye na taruwa idonta, hankalin
Safiyyah ya tashi tace "Innalillahi, don Allah me ya faru? Is everything
ok?" Khaleesat ta girgiza mata kai tana goge idonta a hankali tace
"Abdul ne ya zo" Safiyyah ta gwalo ido tace "Abdul kuma??
Yaushe? Kuma me ya maki kike kuka?" Khaleesat tace "He came yesterday
evening" Safiyyah tace "Ji jaraba, to me ya zo yi? Kuma me ya faru da
ya zo din?" Safiyyah na jefa mata wannan tambayar taji hankalinta ya tashi
lkci daya, let it not be what just crossed her mind now, tunda tasan ko wanene
Abdul, ta kamo hannun Khaleesat da sauri cikin tashin hankali tace "Ko ya
maki wani abu ne? A gidanki ya kwana???" Khaleesat ta girgiza mata kai a
hankali tace "A'a" Safiyyah bata san sanda ta sauke wani ajiyar
zuciya ba, can tace "Toh meye kuma na kuka don ya zo, ko rashin mutuncin
da ya saba ya shuka maki?" Khaleesat na shessheka a hankali tace "He
met my Housemate" Safiyyah ta bude baki tace "Kai don Allah, cikin
gidan ya gansa? To ke ma dai wallahi baza ki iya karyan kare kanki ba kice masa
kawai baΖon Housemate dinki ne shi tunda bai san Nancy ta tashi a gidan ba, to
sai kika ce masa me?" Khaleesat na gyada mata kai tana goge hawayen da
yaki tsaya mata tace "Haka nace masa, amma ai kin sansa kinsan halinsa, he
even fought with my Housemate" Safiyyah ta zaro ido tace "Fight? To
akan wani dalili?" Khaleesat tace "Kema kinsan yanda yake yi ai
Sophie, kawai wai zai yi kissing dina ni kuma naki yarda sai ga Housemate dina
ya shigo shine yayi approaching dinsa seeing what he was doing to me, hakan da
yayi ne yasa Abdul yayi fada da shi, he hit him so hard" Safiyyah tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, to Housemate din ya rama ne?"
Khaleesat ta girgiza kai a hankali tace "Bai rama ba, kawai hakuri ya
basa" Safiyyah tace "Wallahi in ance min Abdul na shan giya ni bazan
musa ba, cause his actions portray that, kawai daga ganin mutum ka fara fada da
shi kamar wani Ιan daba, kuma in banda rainin wayo zai zo me yasa bazai ce maki
zai zo ba kawai sai dai ki gansa kamar an jefosa a gidan?" Khaleesat tace
"Wai fa ce masa da kika yi bani da lafiya shine yasa ya taso ya taho, da
na sani da ban ce kice masa haka ba" Safiyyah ta bude baki tana kallon
Khaleesat don ita ma sai a sannan taga da basu ce masa haka ba tunda ba
isasshen hankali ke garesa ba, Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya tace
"To yanzu Housemate din naki fa? Hope he didn't hurt him?" Khaleesat
ta fara goge wasu sabbin hawayen idonta tace "Kinsan menene ya
dameni?" Safiyyah ta girgiza kai, a hankali Khaleesat tace
"Maganganun da na gaya ma Housemate din nawa, meanwhile he was just trying
to be protective ganin kamar Abdul molesting dina zai yi, ni kuma abinda yasa
nayi masa haka don kar Abdul din ya zargi mun san juna da Housemate din nawa,
cause i told him frnd din Nancy ne kuma ni ban taba ganinsa ba" Safiyyah
da ta kasa rufe baki tace "Wasu irin maganganu ki ka gaya ma Housemate din
naki?" A hankali Khaleesat ta gaya mata duk bakaken maganganun da ta gaya
ma Housemate din nata, Safiyyah ta dinga mata wani kallo cike da takaici, can
tace "To shi katon banzan da kika fadi bakaken maganganun a kansa hope
yayi considering dinki at the end of everything?" Khaleesat ta girgiza kai
tace "He walk out on me, na kirasa sau biyu jiya yaki dagawa, kuma har
yanzu bai kirani ba" Safiyyah ta ja tsaki tace "In ma ya Ιaga shi
babban Ιan iska ne, kada Allah yasa ya daga, kuma shi Housemate din naki kun
sake haduwa bayan abinda ya faru jiya?" A hankali Khaleesat tace "Shi
ma tunda ya bar gidan jiya har yanzu bai dawo ba" Safiyyah tace "To
wallahi ki kirasa don mutumin nan yafi karfin walakanci a wajen ki"
Khaleesat ta fara wani hawayen tace "I don't have his Number"
Safiyyah tace "Ban gane baki da lambarsa ba?" Khaleesat tace
"Wallahi, even when i was going to Nigeria kawai hadani yayi da wani mutum
ya bani number mutumin amma bai bani lambarsa ba" Safiyyah tayi shiru, can
ta sauke ajiyar zuciya tace "Ki tashi kawai ki koma gida kilan Allah zai
sa ya dawo sai ki basa hakuri, Abdul kuma kar ki kuskura ki sake kiransa in ba
haka ba in tsine maki wallahi" Duk da bakin cikin da Khaleesat ke ciki sai
da ta Ιan yi murmushi, a haka ta koma gida ta bar Safiyyah a school din bayan
Safiyyah tace ta kirata duk abinda ake ciki, in ma Abdul din ne ya sake dawowa
gidan ta kirata zata taho..... Throughout ranan Khaleesat bata ga Housemate
dinta ya dawo gidan ba har karfe takwas na dare, ta rasa me yasa ta kasa samun
nutsuwa hankalinta yaki kwanciya, ko tunanin Abdul bata saka a ranta ba tun
bayan barin ta school daxu da safe da Safiyyah tayi encouraging dinta kar ta
sake kiransa, but she was so restless ganin Housemate dinta bai zo gidan ba,
she wish she had his number ta kirasa, wajen karfe goma saura wayarta ya fara
vibrate ta jawo a hankali tana duba screen din taga Safiyyah ce, Safiyyah ta
kirata yayi sau 6 daga barinta school da safe har zuwa yanzu, Safiyyah tace
"Is he back Khaleesat?" Khaleesat ta girgiza mata kai a hankali tace
"A'a bai zo ba" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Kilan sai
gobe zai zo gidan, ki kwantar da hankalin ki pls" Khaleesat dai tayi shiru
bata ce komai ba, Safiyyah tace "Plss kar ki wani damu kanki da yawa
kawata, hope kin ci abinci?" Khaleesat tace "Na ci" Safiyyah
tace "To kiyi kwanciyarki, good night" A haka suka rabu, Khaleesat ta
ajiye wayarta ta lumshe ido duk da tasan ba baccin zata yi ba.......
*Continue making your payment before the end of free pages
fanss, in ba haka ba aji shiruuu...*π
07087865788✍π»
[5/8, 6:48 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨ ✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
11.....
Tun da gari ya waye Khaleesat ta kira Safiyyah tace mata
bazata shigo school ba don tana son tayi bacci, Safiyyah tasan sarai bata yi
baccin kirki ba kenan daren jiya, har mamakin yanda Khaleesat ta iya saka abu a
rai ya dameta take, Safiyyah tace "Shikenan kawata, after our classes zan
zo ko da yamma ne in sha Allah" a hankali Khaleesat tace "To Allah ya
kai mu, Nagode" Daga haka suka yi sallama ta ajiye wayar ta koma ta
kwanta. Wajen karfe hudu na yamma Khaleesat ta tashi daga baccin da take,
bandaki ta shiga ta wanke baki sannan tayi wanka ta dauro alwala ta fito, tun
wayewar gari babu abinda ta ci har zuwa sannan, rabonta da abincin kirki zae yi
kwana uku yau tun dai faruwar incident din few days ago, bayan ta idar da
sallah ta shirya cikin kaya marasu nauyi ta fito parlor ta tafi kitchen ta hada
shayi kawai sannan ta koma dakinta, laptop dinta ta jawo ta kunna zata saka
movie ko zata Ιan samu nutsuwar abubuwan dake damun ta a rai ta hanyar kallon
film, daga karshe ma ta fasa kallon ta dauko takardunta ta fara karatu, nan ma
taji bata fahimtar komai a karatun, rufe takardan tayi ta kwantar da kanta
gefen gado ta lumshe ido with different thoughts running her mind, it's not as
if she is disturb don Abdul bai daga kiranta ba ko bai kirata ba, kawai dai bata
ma san abinda ke damunta bane in particular, bayan lokaci me tsawo ta sauke
ajiyar zuciya ta bude idonta ta jawo wayarta ta bude WhatsApp, status taga
Abdul yayi updating few hours ago, ta bude hoton da yasa taga har ya ma koma
Nigeria cause a field din kwallo yayi hoton da abokansa dukkansu sanye da
jersey, ko kadan bata yi mamakin komawarsa Nigeria ba don zai ma iya abinda
yafi hakan, da taji shiru har kwana uku dama ta zargi ya koma, dai dai nan taji
an bude dakin that is opposite her's, sosai gabanta ya fadi don tun ranan sae
yau Housemate din nata ya zo gidan, ta kalli agogon wayarta taga karfe biyar
har ya gota, ta ajiye wayar ta dago kanta, tana ta zaune har bayan 15 mins da
shigarsa daki sai kuma ta mike tsaye tana jin jikinta ba karfi ta dau gyalenta
tana tafiya a hankali ta nufi kofarta ta bude ta fito corridor, sai kallon
kofar dakin nasa take gabanta na faduwa, ta rasa courage din karasawa bakin
kofar, she stood der for some minutes daga karshe ta lumshe ido ta bude tana
tafiya slowly ta isa bakin kofar nasa ta tsaya, ta kai hannu tayi knocking a
hankali kamar tana tsoron kofar, komawa gefe tayi kamar mara gaskiya waiting
for his response, jin shiru bai amsa ba ta sake knocking din a hankali, ta jira
for like a minute again taga dai ba a amsa ba, babu abinda yayi crossing mind
dinta sai ko yana bacci ne, but bacci da yamma haka? handle din kofar ta kai
hannu gently without thinking twice ta bude kofar tana kallon cikin dakin with
throbbing heart, a edge din gadon dakin ta gansa a duke yana operating laptop
dinsa da alamar abinda bai gama ba ranan da ya bar gidan yake karasawa, ya daga
kai ya kalleta sai kuma ya ci gaba da abinda yake yi, she felt really really
bad, ashe yana ma jin tana knocking din, da tasan yana ji ya kyaleta da bazata
fara bude kofar dakin nasa ba, ya mike tsaye yace "Good evening
Halysaah" Taki amsawa kuma taki yarda ta kallesa, da kyar tace "Dama
kana ji kaki amsawa?" Har muryarta ya fara rawa, ya Ιan bude ido yace
"To na sani ko saurayinki ne Halysaah?" Nan da nan hawaye ya cika
idonta ta juya ta bar bakin kofar ta kullo masa dakin ta koma nata, dukawa yayi
ya ci gaba da abinda yake yi a laptop, tana komawa daki ta fara kukan da bata
san dalilinsa ba, she felt really hurt kuma tayi da ta sanin zuwa dakin nasa,
tana nan a yanda take har shidda saura sannan taji yayi knocking kofar dakinta
gently, daga kai tayi tana kallon kofar sai kuma ta hade rai, lkci daya ya bude
kofar tare da sallama, sai dai daga nan bakin kofar ya tsaya yana kallonta yace
"I was trying to finish a power point Housemate, how are you doing?"
Ta sauke idonta a takaice tace "It's fine" Yace "Baki je
makaranta ba yau?" Ta gyada masa kai looking toward a different direction,
yace "Why?" A takaice tace "Ba komai" Yace "Ok, hope
everything is okay?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa sai kuma ta dauke
kai don kar ma ta fara kukan dake taruwa idonta, bayan like 10 seconds yace
"Saurayin da ke maki fada a waya ne guy din nan ko?" Ta kasa cewa
komai at first, sai kuma muryarta na rawa tace "Kayi hakuri da abinda ya
faru" Ya Ιan buda ido yace "No it's fine Halysaah, ai ba ma abinda ya
faru, but where did you know him from?" Tayi shiru ta kasa cewa komai tana
share hawayen idonta, yace "I am intruding ko?" Ta girgiza masa kai
kawai, yace "Ohk can we talk if you are comfortable Halysaah" She
kept mute Kamar me nazari, can kuma a hankali tace "Ohk" yace
"Then meet me at the parlor" Daga haka ya juya ya fita, ko da
Khaleesat ta fito parlon bata tarda sa ba a ciki, ta zauna kan kujeran parlon
tunani iri iri na yawo a kanta har ta rame a kwana ukun nan, bayan some minutes
sae gashi ya fito daga kitchen with a cup of coffee, ya karaso cikin parlon ya
zauna yana kallonta yace "You look pale Housemate, are you okay? Ko ya
maki wani abun ne?" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta girgiza
masa kai a hankali tace "He left immediately u left too" Yace
"Oh really? That's weird" Ita dai tayi shiru, ya Ιan yi murmushi ya
ajiye coffee din hannunsa yace "Amma baki ci abinci ba" Nan ma tayi
shiru tana kallonsa, yace "Naga kamar its been a while da kika yi girki a
kitchen, so me kike ci a gidan?" Ta sauke idonta, he could see tana cikin damuwa
sosai, yace "Tun ranan da ya tafi bai dawo ba kenan?" Tace
"Um" Ya kalli agogon wrist dinsa yace "Do u mind me taking u out
for dinner?" Kallonsa Khaleesat take babu ko kiftawa kuma bata ce komai
ba, ya mike yace "Get ready, let me get my car key" Yana fadin haka
ya mike ya tafi dakinsa ta bi sa da ido, Khaleesat ta fi minti uku zaune parlon
tana contemplating on weather to go out with him or not, what if Abdul bai bar
kasan ba kawai old picture yayi uploading a status dinsa? The thought of this
sent her quivers all over, Tana cikin wannan tunanin sai gashi ya fito daga
dakinsa, yana shigowa parlor ta mike ba tare da ta bari sun hada ido ba ta wuce
dakinta, canza kaya tayi ta dau veil dinta ta yafa sannan ta zauna gefen gado
tana tunane tunane iri iri, bayan 15 mins da shigowarta dakin taji yayi
knocking yace "Baki shirya ba Halysaah?" A hankali ta mike ta dau
wayarta ta nufi kofa ta bude ta fita, ta samesa har ya koma parlor yana
jiranta, tana isowa parlon yana kallonta yace "Where u contemplating
inside the room?" Bata san sanda ta dan yi murmushi ba bata dai ce masa
komai ba, yace "To mu je, this is after 6 already" Shi ya fara nufar
kofar fita living room din sannan ta bi bayansa, yana tsaye bakin kofar bayan
ya fita ya jira har ta fito daga parlon sannan ya kulle kofar yana kallonta
yace "Why this much Deodorant Housemate?" Ta wani kallesa tace
"Ni nace maka na sa?" Bai bata amsa ba ya nufi garage tana biye da
shi a hankali, ita dai bata sa turare yanzu ba sai tun wanda ta saka da tayi
wanka daxu, sai in ko kamshin kayanta yaji amma ba dai ita ba, bude mata motar
yayi tun bata karaso ba sannan ya zaga ya shiga motar yana jiranta, bayan ta
shiga suka bar Garage din, wani babban restaurant sananne ya kai ta a
Baltimore, bayan yayi parking ta dinga kallon restaurant din da ta ga an rubuta
The Capital Grille, sai da ya fara sauka daga motar sannan ita ma ta sauka,
tana biye da shi suka shiga ciki, shi yayi offering dinta seat bayan ta zauna
shi ma ya zauna ya dau food Menu dake saman table yana nuna mata na kusa da ita
yace "Ki duba abinda za ki ci" Ita dai bata dau Menu din ba, yace
"I am talking Halysaah" Without looking at him tace "Ko ma meye
zan ci" Yace "Ohk" Tana danna wayarta yayi masu ordering
abincin, mamaki Khaleesat ta dinga yi ganin amount of different type of foods
that he ordered kamar za ayi karamin feast a wajen, abinci kuma masu tsadan
gaske, da yawa cikin abincin da aka kawo masu sai a ranan ta fara ganinsu, duk
da dai abincin turawa ne, drink ma ya kusa kala hudu ya siya masu, ta daga kai
ta kallesa a karo na farko tace "Su waye za su cinye duk wannan?"
Orange Crush ya dauka yana sha bai ce mata komai ba, after a while ganin bata
fara cin abincin ba shi kuma sai cin abinda zai ci yake ya daga kai ya kalleta
yace "Ko babu abinda kike so a nan ne?" A hankali ta dau Tacos daya,
shi ko ya ci gaba da cin abincinsa, Ζasa Ζasa Khaleesat take kallonsa, ta lura
yanda baya wasa da bacci haka baya wasa da abinci, because he didn't even mind
she was in front of him abincinsa kawai yake ci sosai, ganin ko kallonta baya
yi ta abincin gabansa kawai yake yasa ta Ιan saki jiki kadan ta fara cin
abincin duk da ba sosai ba, ta ci iya abinda zata iya ci ta dau drink tana sha
a hankali, sai a sannan ya daga kai ya kalleta after almost finishing his food
yace "Ko dai a maki packaging abincin ki ci a gida, naga kamar kina kunyan
ki ci abinci cikin mutane, or should i give u privacy?" Tana kallonsa a hankali
tace "Privacy in an open restaurant? Ni nace ina kunyan in ci
abincin?" Ya Ιan bude ido yace "Naga u ate just the Tacos bayan ga
abinci da yawa a gabanki" Ta sauke idonta tace "Nafi son sa ne"
Yana goge lips dinsa da tissue alamar ya koshi yace "Ohk, so now can i
talk to you?" Shiru tayi na few seconds, sai kuma ta kallesa a hankali
tace "Ohk" Ya karasa shanye drink dinsa yace "A nan America kika
hadu da saurayin naki ko a Nigeria?" Khaleesat was silent, sai kuma ta
sauke idonta tace "Nigeria" Yace "Ohk, but me kike tunanin yake
janyo maku matsala tsakaninku?" Ta girgiza kai tace "Nima ban sani
ba" Yace "Saboda ke ya taho nan daga Nigeria or he have a business
here?" Ta gyada masa kai tace "Saboda ni ya zo" ya gyara zama
yace "Kinga yana sonki kenan, sosai ma kuwa yake sonki, he left everything
he was doing and came over just to see you, in na fahimta bai son kiyi sharing
apartment da namiji a kasar nan ko?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba
tana wasa da gefen mayafinta, yace "Sure... yana da gaskiyarsa, don ko ni
bazan bar budurwata tayi communal living ba" Khaleesat ta daga kai ta
kallesa, Yace "Yanzu dai kiyi kokari ki basa hakuri ku dai daita kanku, ni
kuma i will think of another alternative for peace to reign between u and ur
boyfriend, sannan shawaran da zan baki shine try all possible best ki dinga
nuna masa abinda baza ki yi tolerating ba tun kafin kuyi aure, ya kamata ace
akwai mutual understanding tsakanin ku, he look cool though kawai yana da hot
temper ne and i notice insecurity na daya daga cikin matsalarku da shi, but you
can definitely change him gradually Halysaah, so last maganar da zan maki ina
ga ba abinda ya shafeni bane, kawai dai zan tunatar da ke Do's and don't din
addininki ta bangaren relationship tsakanin mace da namiji" Khaleesat dai
sauraronsa kawai take without looking at him, kuma taki ce masa komai tana
kokarin fahimtar abinda zancensa na karshe ke nufi, shirun da taji yayi yasa ta
daga manyan idanuwanta ta kallesa, at the same time ta kalli wa enda yake kallo
a cikin restaurant din, 3 Guys ne suka shigo restaurant din gaba dayansu yan
Africa, amma daya ne Ιan Nigeria a cikin su, guys din da ba yan Nigeria ba suka
daga ma Housemate din nata hannu alamar girmamawa, and he waved back at them
with smile on his face, Khaleesat ta dinga kallon daya mutumin da ya nufo su
don ta ma ganesa, su sauran biyun kuma suka tafi yin abinda ya kawo su
restaurant din, Mutumin na isowa kusa da table dinsu yana kallon Housemate
dinta yace "Done with the power point?" Tuni kamshin turarensa ya cika
wajen, Housemate dinta ya daga kai ya kallesa yace "Yau kuma har da kai za
a ci abinci a nan kenan...." Yace "Not at all, i am getting some
Steak for legend, meanwhile ashe kana nan" Housemate dinta yace "Yea,
i came with my friend for Dinner" Khaleesat dai danna wayarta kawai take
don mutumin yi yayi kamar bai san da Allah yayi ruwanta a wajen ba, ita ma ko
kallon direction dinsa bata yi ba, Housemate dinta ya nuna masa bill dinsu yace
"Get the bill cleared" juyawa mutumin yayi ya bar wajen yana tafiya irin
ta Ζasaita, Khaleesat ta bi sa da kallon gefen ido, he was wearing a Jogger and
a white Polo, ta dai ci gaba da danna wayarta, muryar Housemate dinta taji yace
"That's my gee Halysaah, we share the same name with him...."
Khaleesat ta daga kai without interest tace "Ohk" Yace "Sorry
about his attitude, he isn't friendly, but i promise you he is good"
Khaleesat tace "Likewise myself" Murmushi housemate dinta yayi sannan
yayi excusing kansa ya mike ya nufi gun wanda ya kira da gee dinsa, daga inda
take zaune taji mutumin na cewa "Kai kuma ina ka samo waccan yarinyar dake
zaune kamar gunki bata iya gaisuwa ba, duk wani harkar raini ka iya ja ma
mutane, that was how the other day da ka kawota karfe ukun dare a mota ta dinga
kallon mutane kamar statue da aka dasa a gaban motar" Definitely yayi
maganar ne ta yanda zata ji, Housemate dinta dake kallonsa yace "Ban gane
bata iya gaisuwa ba, ba kai ka sameta a wajen ba, kayi mata magana ne kaga bata
amsa maka ba?" Maimakon ya ba Housemate dinta amsar abinda yace sai taji
yace "Na kai Legend gun Veterinary daxu" Taji Housemate dinta yace
"Hope he is better now?" Mutumin yace "Let me get the bill
cleared mu tafi gidan Mike yanxu...." Housemate dinta yace "No kayi
tafiyarka zan yi dropping frnd dina first" Taji mutumin yace "Like
seriously kai ko wani irresponsible being sae kace friend dinka, why are you
stooping your self soo low Jay" Taji Housemate dinta yace "C'mon
Ajay, come off it, this is so harsh..." Mutumin da ya kira da Ajay ya tafi
ya bar sa gun a tsaye, Dawowa Housemate din nata yayi inda take, tuni ta mike
tana gyara gyalenta without looking at him tace "Thanks for the dinner,
kawata na kirana zan tafi gida" Housemate dinta yace "Ke kika kawo
kanki da za ki koma ke kadai?" Taki kallonsa tace "Ae naga ur
responsible frnds are here, so let me get going" Yace "Halysaah"
ta daga kai ta kallesa, yace "Jira ni inyi clearing bill dinmu in yi
dropping dinki gida" Yana fadin haka daya daga masu aiki a restaurant din
ya nufosa da ladabi ya sanar masa anyi clearing bill din su, ya bi A-jay da ya
fita daga Restaurant din da kallo, wa enda suka shigo tare na biye da shi a
baya. Khaleesat bata yarda ta hada ido da Housemate dinta ba har suka fito daga
Restaurant din zuwa inda yayi parking motarsa, sai da ya shiga motar sannan ita
ma ta shiga ta zauna tana danna wayarta, bai tada motar ba ya kalleta, speaking
calmly yace "Hope you are not offended Halysaah?" Without looking at
him tace "Offended at what?" Yace "I don't really know" Ta
kada baki tace "Ai ni ban yi kama da someone that isn't responsible ba
balle in zama Offended at what a random stranger spew out, out of his
ignorance, shi dai da bashi da manner shi ne babban irresponsible being, ai da
ya fada a gabana yaji abinda zan gaya masa" Housemate dinta ya bude baki
yana kallonta da mamaki looking completely speechless, bai yi tunanin taji
abinda Ajay din ya fada ba, bai kuma yi tunanin tana ma da baki haka ba, after
few seconds yayi kasa da murya yace "Pls kiyi hakuri Halysaah, bana son
wannan yasa ranki ya bace, i purposely brought you out to cheer you up and make
you lively don naga kamar kina cikin damuwa, amma ba don a kara bata maki rai
ba, plss ignore Ajay's attitude, wani lkcn yana da problem i think today is one
of those days" Khaleesat bata sake cewa komai ba but she is trying hard
not to cry, ya ci sa'a ba yana tsaye gabanta ya fadi haka ba da tsaff zata
mayar masa da baΖar magana dai dai da abinda ya gaya mata a wajen, Housemate
dinta ya tada mota suka bar Restaurant din, hakuri ya dinga bata kamar shi ne
yayi mata laifi har suka isa gida, direct dakinta kawai ta wuce, after like 40
mins ta fito wanka tana duba sleeping dress din da zata sa taji yayi knocking
kofar dakinta, hijab din da tayi sallah ta dauka da sauri ta saka, bai bude
kofar dakin ba har sai da taje ta bude tana kallonsa, yace "Sae da safe
Halysaah, pls ki kwantar da hankalinki and get some rest, gobe kuma ki je
school" ta sauke idonta bata ce komai ba, taji yace "Take care"
Sai da ya juya ya bar wajen sannan ta daga kai ta bi sa da kallo cikin sanyin
murya tace "Thank you so much, for..." Sai kuma tayi shiru, ya juya
yace "For?" Ta langwabar da kai tace "The Dinner" Ya Ιan
buda ido yace "My pleasure Halysaah" A hankali tace "But.... i
don't... know, ur name" Yace "Oh really, amma ranan da na fara zuwa
gidan nan ai nayi introducing kaina sai dai in kin manta, I am Ahmad Jawwad
Yusuf, my frnds call me Jayy" Kallonsa Khaleesat ta dinga yi without
blinking, yace "Are you okay with that?" Ta sauke idonta tace
"Alright, i really appreciate you" Ya sakar mata murmushi yace
"See yah tomorrow" daga haka ya bar wajen ta bi sa da ido har ya fita
daga gidan gaba daya sannan ta juya a hankali ta koma dakinta ta kulle kofar.
*Make ur payment before the end of free pages, kar a ji
shiru*
07087865788✍π»
[5/9, 4:49 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
12.....
Washegari da safe Khaleesat ta gama duk abinda zata yi a
gida ta shirya ta tafi makaranta, tana zaune favourite spot dinsu ita da
Safiyyah bayan sun fito daga aji, Safiyyah na facing dinta tace
"Tsakaninki da Allah ina kika je jiya da yamma da naje gidan baki nan? Ni
dai nasan babu inda kike zuwa a garin nan, ba kuma frnds gare ki ba, So where
did u go?" Khaleesat da idonta ke kan jotting da tayi a aji tace "To
ke meye na zuwa da yamma likis, i was expecting you around 5pm not 7pm" Safiyyah
ta amshi takardan hannunta tace "Ina maki tambaya kina min tambaya, ko
akwai abinda kika fara boye min ne Khaleesat?" Tagumi tayi tana kallon
Khaleesat din da tuhuma, sai a sannan Khaleesat ta daga kai ta kalleta, dariya
ta bata amma bata yi ba, kamar dai bazata ce mata komai ba sai kuma ta bude
baki tace "Mun fita zuwa restaurant ne da Housemate dina" Safiyyah ta
buda baki tana kallonta with surprise, can tace "Waw, really? Housemate
dinki fa kika ce?" Sai kuma tayi dariya tana gyara zama idanuwanta kamar
za su fito tace "Anya Khalee babu magana a kasa kuwa? Restaurant fa kika
ce? How did he convince you har kika bi sa zuwa restaurant?" Khaleesat ta
tabe baki tace "Toh meye kuma a kasa? Daga dai ya kai ni restaurant mu ci
abinci? Kinsan yaushe rabon da inci abincin kirki a gidan?" Khaleesat ta
sauke idonta a hankali tace "He notice i haven't been eating shi ne yasa
har ya kai ni restaurant" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai
kece da dora ma kanki abinda Allah bai dora maki ba kawata, akan Abdul din da
naga yayi updating status da jersey jiya alamar har ya koma Nigeria ya ci gaba
da harkokin gabansa ke kina nan kina neman kashe kanki, wallahi in zaki ajiye
lamarin gayen nan a gefe da zai fi maki alkhairi a rayuwarki, very very
heartless guy with no conscience, dubi tsabar zuciyarsa ta dutse ne ya gwammace
ya kara siyan ticket yayi juyawarsa ya koma Nigeria, Allah ma yasa yayi maki ya
jiki zuwan da yayi" Khaleesat dai tayi shiru tana kallon Safiyyah,
Safiyyah ta daga kafada tace "Ga dai Housemate din nan naki duka duka yaushe
har ma ku ka san juna? Amma ya gane kina cikin damuwa har da kai ki restaurant
for dinner, to this is how a caring and understanding Boyfriend and a Gentleman
should be" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya a hankali tace "Ni babban
damuwata kar ya sake dawowa kasar ban sani ba Sophie, ce masa nayi Housemate
dina frnd din Nancy ne fa, kinsan bai san Nancy bata gidan ba ai har yanzu, to
kar ya sake dawowa unexpectedly ya gansa" Safiyyah tace "Abinda zai
faru kawai kiransa zaki yi ta yi har sanda ya ga daman daga kiranki, ki basa
hakuri ki samu ku shirya, in har ku ka shirya duk wani movement dinsa zaki
dinga sani, yanzun ma ai don baku communicating ne all this while shi yasa
kawai ya taho kamar an jefosa, banda haka ai duk sanda zai zo yana gaya maki"
Khaleesat tace "Haka ne, amma kin san irin zuciyarsa wallahi zan iya
kiransa sau goma ma bazai daga ba, ko na masa magana ta WhatsApp bazai yi reply
ba" a sanyaye ta kare maganar, Safiyya tace "Bari in kirasa ta wayana
yana picking zan ce ya kirani, daga nan in ya kira sai in baki wayar ku yi
settling dispute din karyan ku" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba,
amma tasan hakan kadai shi ne way out, Safiyyah ta ciro wayarta ta fara kiran
Abdul, har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa sai gashi ya daga, sallama
tayi masa ta gaishesa tace "Pls in ba damuwa ka kirani" Katse kiran
yayi sai gashi ya kira tayi picking sannan ta mika ma Khaleesat wayar,
Khaleesat ta amshi wayar gabanta na faduwa ta kai kunne, Safiyyah ta tashi ta
bar ta a wajen ta koma wani waje ta zauna, a hankali Khaleesat tace "Don
Allah kayi hakuri ka saurareni..." Shiru yayi da yaji muryarta, nan da nan
hawaye ya cika idonta muryarta na rawa tace "Pls kayi hakuri da abinda ya
faru, i promise you hakan bazai sake faruwa ba" Yace "Dama akwai
abinda ya faru ne?" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "I am asking
you, akwai abinda ya faru ne dama?" Ta sunkuyar da kanta tace "Don
Allah kayi hakuri, i am truly sorry plss" Yace "Look i am super busy now,
idan kin shirya gaya min abinda ya faru kike ban hakuri sai ki kirani ta layin
ki anjima" Cikin sanyin murya tace "Toh Nagode" Katse wayar
yayi, ta juya tana kallon Safiyyah, Safiyyah ta kyabe baki ta dawo kusa da ita
ta zauna tace "Ya ku ka yi da shi?" Khaleesat ta ja tsaki tana tattara
reading material dinta tace "An gaya masa banda ina tsoron kar ya dawo
without notice ni zan sake magana da shi ta waya ne" Safiyyah ta bude baki
tana kallon Khaleesat tana tunanin yaushe bakinta ya fara budewa haka akan
Abdul ne wai, Dariya Safiyya tayi tace "Shi Abdul din naki Khalee?"
Khaleesat ta ki bata amsa, har ranta ita fa yanzu tana jin bazata iya ci gaba
da tolerating abubuwan Abdul ba, ita kanta bata san daga inda wannan liver din
yake zuwa mata ba, sai dai duk abinda zai faru ya faru but she is not
tolerating anymore. Wajen karfe biyu ta koma gida, bayan tayi wanka tayi sallah
ta sauya kayanta ta kwanta, sai bayan da tayi la'asar ta shiga kitchen ta
jingina da cabinet tana tunanin abinda zata girka, tuwo taji take son ci, kawai
daga karshe tayi deciding tayi tuwon since tana da duk ingredients din girka
tuwon, kan kace me ta gama girka tuwo da miyar kuka with enough obstacles a
ciki, ta gama goge gogen kitchen din sannan ta fito parlor wajen karfe biyar,
dai dai shigowar Housemate dinta gidan, ita dai tana tsaye kusa da kitchen, ya
juya ya kalleta bayan ya kulle kofar parlon yace "Good evening
Halysaah" Tace "Good evening" Yace "What are you cooking
with such a nice Aroma" Tace "Tuwo ne" Ya karaso cikin parlon
yace "Really, it's been long na ci tuwo fa" Tana kallonsa tace
"In kawo maka?" Ya dan buda ido yace "Ok thank you" Juyawa
tayi ta koma kitchen din, ya zauna saman kujera hoping ba da yawa zata saka
masa ba, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta dawo parlon da plate dauke da tuwo
with a diff bowl of soup, tun da ta duka ta ajiye abincin yake kallon bowl din
miyan babu ko kiftawa, can dai ya daga kai ya kalleta yace "Wani miya ne
wannan Halysaah?" Ta koma gefe tace "Miyar kuka ce" Lkci daya
yayi yaΖe yana shafa kansa yace "Wow, but bana cin irin miyan, i thought
vegetable soup ne, baki yi stew ba?" Ta wani kallesa, a takaice tace
"Babu, kuma kayi tasting miyan ne kafin kace baka cin irin sa?" Ya
jingina da kujera ya sauke ajiyar zuciya yace "Na ma ci abinci few minutes
ago fa" Dukawa tayi ta dau bowl din ta mika masa miyan tace "Taste it
first before concluding" Ya dan kalleta yana murmushin dole yace "Ok,
where is the spoon?" Tace "Shi ba a cin sa da cokali ai, da hannu
zaka sha" Yayi shiru sai kuma yace "Then bari in wanke hannu"
Yana fadin haka ya mike, ta koma gefe don basa hanya sannan ta bi sa da kallo
har ya tafi bandakin dake parlorn ya wanke hannu sai gashi ya dawo, bayan ya
zauna ta mika masa miyan tana kallonsa, shi dai bai yarda ya hada ido da ita
ba, tun da ya kai finger ya lasa miyan ya kai baki ya kasa dago kai, ita dai
kallonsa kawai take bata ko kiftawa, can dai yana murmushi da kyar ya dago yace
"It's sooo nice amma na ci abinci wallahi Halysaah" Duk da dariyar da
ya bata ta dake tace "To ai tunda ka sa na zuba sai ka ci ko kadan ne
cause i am not throwing it away" Bata jira cewarsa ba ta juye masa miyan a
kan tuwon dake plate ta dau plate din ta mika masa tana kallonsa, he was
totally speechless and confuse at the same time, tana kallonsa da kyau tace
"Karba" Ya kai hannu a hankali ya amsa plate din tuwon, in ya debi
tuwon sai ya dangwala miyar kamar yana tsoronsa sannan ya kai baki, sosai ya
bata dariya amma fa bata yi ba, instead sai murmushi take, sau uku yana diban
tuwon yana ci kuma har sannan yaki yarda su hada ido da ita, kana ganinsa kasan
da kyar yake cin abincin, his facial expression says it all, wayarsa ne ya fara
vibrate, ya ajiye tuwon da sauri ya fiddo wayar yana kallon screen, sai kuma ya
kalleta yace "This is an urgent call Halysaah bari in shiga daki in
daga" Kasa basa amsa tayi don kar ma tayi dariyar da take dannewa, ya mike
ya nufi dakinsa da sauri don ko jiran jin abinda zata ce bai yi ba, tana ji ya
sa ma kofar dakin makulli bayan ya shiga, sai a sannan ta zauna gefen kujera ta
rike kanta tana dariya, after some minutes ta mike ta dau plate din tuwon still
smiling ta wuce dakinta. Khaleesat na Voice call ta WhatsApp da Ummanta wajen
karfe tara da rabi na dare taji Housemate dinta na knocking kofar dakinta,
bayan tace ma Ummanta tana zuwa ta ajiye wayar sannan ta sauka daga kan gado ta
saka hijab ta tafi ta bude kofar, yana jingine jikin bangon opposite din
dakinta idonsa a kulle, yana jin bude kofa ya bude idon da sauri, kana ganinsa
kasan daga bacci ya tashi, tun da ya shige daki daxu yace ana kiran wayarsa
bata sake ganinsa ba sai yanzu, yace "Zan tafi sai da safe Halysaah, but
pls ki dan kulle kofar i can't find my key" Ita dai bata ce komai ba tana
kallonsa, he look so sleepy, ya ciro wayarsa dake ta vibrate a aljihu, tsaki
yayi after picking yace "Kai dalla ina hanya" Daga haka ya mayar da
wayar aljihu ya sake yi mata sai da safe ya juya ya fara tafiya, ta bi sa da
kallo har ya isa parlor, jingina taga yayi ta bayan kujera ya rungume hannunsa
ya rufe ido, Khaleesat ta sauke idonta sannan ta fito daga dakinta tana tafiya
a hankali ta tafi parlon, bude ido yayi da sauri jin tafiya, sai kawai ya nufi
kofar fita daga parlon, tace "Since u can't control ur self a ko ina ka
samu bacci kake, be it standing, sitting, driving and even walking, then why
not sleep over?" Ya dan kalleta jin abinda tace, nan da nan kuwa yaji
baccin ya bar idonsa gaba daya, yana mata kallon mamaki at the same time yana
sosa kai yace "Yaushe kika ga nake yin duk wannan da kika lissafa
Housemate?" Ita dai ta rungume hannu tana kallonsa bata ce komai ba, ya
dauke kai yace "I was only meditating ba wai bacci nake ba, in dai kika ga
na rufe ido to i am meditating" Yana fadin haka ya nufi kofa ya bude yace
"Good night, kar ki manta ki kulle kofar" Daga haka ya fita ya tura
mata door din, Ιan murmushi tayi tana tafiya a hankali ta isa kusa da window ta
dan bude curtain din tana lekansa, parking space taga ya nufa ya bude motarsa
ya shiga, she is just hoping yana shiga bazai fara wani baccin ba a cikin
motar, after few seconds taga ya fara reverse, ta sauke ajiyar zuciya tana kallonsa
har ya bar Garage din ya dau hanya, sake curtain din tayi slowly, ta dan tsaya
for few minutes sai kuma ta tafi daki ta dauko key dinta ta kulle kofar ta wuce
dakinta, sake kiran Ummanta tayi ta WhatsApp, bayan Umma ta daga Khaleesat tace
"Ko kin fara bacci ne Umma?" Umma tace "Aa idona biyu ina jiran
ki, Abdul ya maki wata magana ne?" Khaleesat tayi shiru jin abinda Umma
tace, ta girgiza kai tace "A'a bai ce min komai ba, me ya faru Umma?"
Umma tace "Daxu Hasiya Matar Malam Saleh ta zo gidan nan" Sosai
Khaleesat taji gabanta ya fadi, Malam Saleh aminin mahaifinta ne, yawanci
abubuwa da yawa a bakin matarsa Ummanta ke ji tunda ba gaya mata baban nasu ke
yi ba, abu da yawa ma sai dai taji a duniya ba dai a bakinsa ba, Khaleesat tayi
karfin halin cewa "Me tace Umma?" Umma tace "Wai ko an tsaida
maganarku da Abdul, haka dai tace min" Khaleesat was short of words,
lokaci daya jikinta yayi sanyi, sosai maganar ta zo mata a bazata, she could
feel her self tearing up, hankalinta yayi mugun tashi cikin lkci kadan, Umma
tace "To ina jira dai in ga ko Malam din zai yi min magana, in ba ayi
hankali ba kuma in ji a bakin matansa tun da su zai gaya masu ai, kuma kin ce
Abdul din bai ce maki komai ba har yanzu ko?" Khaleesat ta goge hawayen da
ya gangaro idonta, tana gyada kai da kyar kamar Umma na ganinta amma ta kasa
cewa komai, Umma tace "Khaleesah?" Da kyar Khaleesat ta bude baki ta
amsa don bata son Ummanta tasan kuka take, Umma tace "Naji kinyi shiru
ne" Khaleesat ta dake tace "Ba komai Umma, ina duba wani karatu ne a
takarda" Umma tace "To shikenan, kiyi karatun ki ma yi magana
washegari ko?" A haka suka rabu, Khaleesat ta ajiye wayar hannunta ta
kwantar da kanta saman pillow hawaye na sauka idonta, bata san menene ya sa all
of a sudden taji she can't marry Abdul ba unlike before da har cikin ranta
tasan bata da option dole ne aurenta da shi, tana kuma masa fatan ya canza
wataran, yanzu kam bata jin haka a ranta, instead ji take bazata iya aurensa ba
ma, Khaleesat bata yi wani baccin kirki ba daren ranan nan fargabanta daya kar
ma yace a daura auren nan take, tasan in har suka ce ma iyayenta haka babu
abinda zai hana a daura auren nan sai wani ikon Allah. Da safe Khaleesat ta
tashi da ciwon kai sosai, kana ganinta kasan tana cikin damuwa ba kadan ba,
haka dai ta shirya ta fita zuwa makaranta, warce take son tayi ma magana ta dan
ji saukin abinda ke damunta sai bata shigo school ranan ba, wayarta ta ciro
kawai tayi dialing number Abdul cause she can't hold it anymore, kiran na shiga
ya katse ya kirata, ta daga ta kai kunne a hankali ta gaishesa, amsawa yayi
yace "Ya aka yi?" At first tayi shiru, sai kuma tace "Ba komai i
only called to greet you" Yace "Which side of the bed did you wake up
from today da kika kirani ki gaisheni?" Tayi masa shiru, yace "ke dai
fadi abinda kike so Malama, foodstuffs din ki ne ya kare ko me?" Ta hade
rai tace "Yaushe ka siya da har zai kare?" Yace "Bazai kare ba
dama mana tunda baki wani cin abinci sai cookies da kayan kwadayi" Ta wani
turo baki bata ce masa komai ba, after few seconds tace "Kawai naji a
jikina ne kamar da wani abu dake shirin faruwa shi sa na kira ka" Yace
"Wani abu kamar me fa?" She was mute bata basa amsar tambayarsa ba,
yace "Anyway, ko ma me kika ji a jikin ki haka ne, zan shiga meeting yanzu
sai anjima" Katse wayar yayi a nan take, ta dinga kallon screen din
wayarta wani tsanarsa na yawo a zuciyarta, a baya duk abubuwan da yake mata
bata taba jin tsanarsa ba sai dai haushinsa yanzu kuwa kawai ji tayi ta
tsanesa, ta ja tsaki ta mayar da wayarta jaka tana jin wasu hawaye na cika
idonta, rashin zuwan Safiyyah makaranta ya sa bata tsaya su gama karatun ranan
ba ta kama hanyar gida kawai cike da damuwa, tana jiran Lyft din da tayi
ordering sai ga kiran Safiyyah ya shigo wayarta, tun daxu ta kirata bata daga
ba sai yanzu ta biyo ta, Khaleesat ta daga ta kai kunne tana jin muryar
Safiyyah tace "Baki da lafiya ne?" Da kyar Safiyyah tace "Tun
jiya da daddare, na ma zata rasuwa zan yi kawata" Khaleesat ta Ιan bude
ido tace "Me ya sameki?" Safiyyah tace "To ina ma na sani
Khaleesat, Allah sa ba poison dina matar nan tayi ba don tun jiya sai yanzu
nasan mutanen dake kaina" Khaleesat tace "Subhanallah, kina gida ne
yanzu?" Safiyyah tace "Har da karin ruwa kuwa" Khaleesat tace
"To bari in taho gidan yanzu" Khaleesat na maida wayarta jaka ta nufi
gidansu Safiyyah, bayan tayi knocking kofar Surayya ta bude mata, Khaleesat ta
sauke ido ta gaisheta, in ba kasa kunne sosai ba ma baza kasan Surayya ta amsa
ba, Khaleesat taji muryar Mustapha na tambayar matar tasa wanene, ji tayi kamar
ta juya ta fasa shiga cikin gidan, amma kasancewar a bude Surayya ta bar kofar
yasa ta karasa ciki walking slowly, without looking at Mustapha dake parlor ta
gaishesa, ya amsa yace "Ya karatun Khaleesat?" Khaleesat tace
"Alhamdulillah, ya jikin Safiyyah?" Yace "Alhamdulillah, she is
inside her room" Khaleesat ta juya ta nufi dakin Safiyyah, da gasken ruwa
ta tarar ake kara mata don ta zata kawai tace mata haka ne don ta zo, Khaleesat
ta zauna gefenta da damuwa tace "Sannu Sophie, ya jikin?" Safiyyah
tace "Ba sauki Khaleesat, wallahi kilan abu matar nan ta saka min a
abinci" Khaleesat tace "Don Allah ki dena cewa hka, kin ga yayanki ai
bazai ji dadi ba in kina wnn magana" Safiyyah tace "Wallahi ita ce
don lafiya na dawo gida jiya, ni na zata ma na rasu, sai da na farfado naga ba
haka ba" Khaleesat tace "Allah dai ya baki lafiya, kin ci
abinci?" Safiyyah tace "Ni bazan ci abincinta ba gaskiya tun daxu sai
fruit kawai nake ta sha da lemon kwali" Khaleesat tace "Ko in je gida
in maki girki? Me kike son ci?" Safiyyah tace "Ko tuwo da miyar kuka
ne ki min in kina da ingredient, kawai shi naji nake so wallahi" Khaleesat
tace "To ba damuwa, bari inyi sallah sai in tafi in maki girkin" A
haka Khaleesat tayi sallahn azahar ta bar gidan bayan tayi ma Surayya da
mijinta sallama, Mustapha ne ma ya tambayeta har zata tafi, Shine tace masa
zata dawo anjima, Khaleesat na isa gida taga motar Housemate dinta a Garage,
tana bude kofar ta shiga parlor ta gansa kwance kan 3 seater yana bacci, har ta
kulle kofar bata ga ya bude ido ba, ta nufi dakinta ta shiga ciki ta canza kaya
sannan ta fito ta shiga kitchen, tuwon ta dora har zata fara hada ingredient na
miyar kukan sai kuma ta fasa taji gwara tayi vegetable soup kawai, ita kanta
bata san menene yasa take son yin vegetable soup din ba duk da bata wani son
cin miyar ganye she prefer slimy soup, sai da ta gama tuwon sannan tayi
ordering lyft da zai kai ta nearest African store da zata iya siyan ingredients
din miyan Vegetable.
*Make ur payment before the end of free pages*
_Halysaah is just 500 naira_
07087865788 ✍π»
[5/10, 10:07 AM] khaleesat Haiydar π✍️: Read My Book
"HALYSAAH" on
ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6
✨✨ HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
13....
Har Khaleesat ta fita daga gidan zuwa Supermarket Housemate
dinta bai tashi ba, bayan ta dawo sai bata gansa a parlor ba alamar ya shiga
dakinsa, kafin karfe hudu da rabi na yamma Khaleesat ta gama miyan da take,
tayi dishing ma Safiyyah abincin a warmer din da zata kai mata, kan kace me
aroma din girkin ya cika gidan, ko tuwon bata ci ba ta tafi dakinta tayi wanka
tayi alwala tayi sallan la'asar sannan ta shirya, fitowa parlor tayi ta nufi
kitchen, tsaye ta ga Housemate dinta ya jingina da cabinet din kitchen din
idonsa a lumshe, ya dora lipton a gas, tace "Bacci kake a kitchen
din?" Bude ido yayi ya juya ya kalleta yace "Not at all" Tace
"To me kake yi?" Ya dan shafa kansa yace "I am having a terrible
headache" Tayi kasa da murya tana kallonsa tace "Ka sha magani?"
Ya kashe gas din yace "Zan sha" Tace "To in sa maka
abinci?" Yace "What did you cook?" Tace "Tuwo...." Bai
jira ta karasa ba da sauri yace "A'a, Alhamdulillah, am full"
Murmushi tayi tace "To ai ba miyar kuka bane, vegetable soup ne" Tana
fadin haka ta bude masa tukunyar miyar tana kallonsa, bayan ya ga miyar a
hankali yace "Ohk, but let me dish the food my self" Ita dai bata ce
masa komai ba ya dau plate ta nuna masa inda tuwon yake, kallon dan tuwon da ya
zuba ta dinga yi, sai kuma tace "Wannan dan kadan din?" Without
looking at her yace "Zai isheni" bata sake cewa komai ba ya zuba
miyar a gefe with just one protein ya saka spoon a gefe, sannan ya dau mug ya
debi lipton da ya dafa ya dau plate din tuwon yace "Thank you" Bin sa
tayi da kallo har ya fita daga kitchen din. Ko da ta fito parlor da abincin
Safiyyah ta samesa zaune kan kujera bai fara cin abincin ba, ya daga kai ya
kalleta, ta dau handbag dinta dake saman kujera, yace "Are you going out
with food?" Tace "Yea, kawata zan kai ma abinci she is sick"
Yace "Ohk Allah ya bata lafiya" Tace "Ameen" Daga haka ta
fita daga gidan. Har kusan Magrib Khaleesat na tare da Safiyya, sosai jikin
Safiyyah yayi sauki sai labari take ma Khaleesat da tayi shiru hankalinta baya
kan hirar, da ta tuna maganar da Ummanta tayi mata jiya da kuma abinda Abdul
yace mata da ta kirasa daxu sai taji duk duniyar tayi mata zafi babu abinda ke
mata dadi a rai, Safiyyah da ta kula da yanayin Khaleesat tace "Wai me ke
damun ki ne kawata?" Khaleesat ta kalleta, sai kuma ta dan yi murmushi
tace "Bakomai Sophie, kawai na gaji ne sosai har na fara jin bacci"
Ba don khaleesat bata son gaya mata damuwarta bane yasa tace mata haka sai don
bata son fadin damuwar tata a wnn lkcn, but tasan dole zata gaya ma Safiyyah
abinda ke faruwa, Safiyyah tace "To ki kwana a nan mana tunda bamu da
lectures gobe, it's already pass 7 yanzu" Khaleesat ta dan bude ido tace
"In kwana a ina? A'a ni dai kin ga tafiyata" duk yanda Safiyyah ta so
convincing Khaleesat ta kwana gidan, khaleesat ta ki sauraronta tayi sllhn
magariba ta kama hanyar gida, dama tun da ta kawo tuwon da tayi ma Safiyyah
daxu Mustapha ya shigo har dakin ya diba ta zama uncomfortable zama a gidan,
matarsa kuwa ta kasa ta tsare a parlon gidan, ko da ta fito parlorn ita kadai
ta samu zaune fuska a murtuke, Khaleesat tayi mata sallama ita dai har ta fita
daga gidan bata ji ta amsa mata ba. Khaleesat na isa gida ta kulle kofar parlon
ta karasa ciki tana kallon plate din dake saman kujera da yayi covering with
another plate, mug din shayin ma na ajiye bai sha ba, ta tafi ta bude plate din
tuwon taga bai ci ba, abinda ya fada mata a kitchen ne daxu ya fado mata that
he is having headache, ta juya tana kallon kofar dakinsa, tana tafiya a hankali
ta nufi dakin tayi knocking gently, sai da ta sake knocking jin bai amsa ba ta Ιan
bude kofar slightly, bacci ta gansa yake yi saman gado, ta sauke idonta kasa,
lkci daya ya bude ido yana kallonta, ta Ιan koma baya kamar mara gaskiya tana
kame kame tace "Are you okay?" Kansa kawai ya nuna mata ta karasa
cikin dakin ta duka ta side dinsa da damuwa tace "Baka sha maganin
bane?" Bai yi responding ba hakan yasa ta kai hannu kusa da forehead dinsa
sai dai bata taΙa sa ba, amma she could feel he is running temperature, a
hankali tace "Should i order an Uber ride sae kaje asibiti?" Ya
girgiza mata kai idonsa a lumshe, rasa abinda zata yi tayi, lkci daya taji
hankalinta ya tashi, mikewa tayi ta fita zuwa dakinta ta dau karamin towel tayi
soaking dinsa da ruwa bayan tayi squeezing ta dawo dakin, ta nufi inda yake
kwance ta duka kusa da shi ta dora karamin towel din da ta linke saman forehead
dinsa, ya bude idonsa, cikin sanyin murya tana kallonsa tace "In yi
ordering ride din?" Ya dafe towel din da ta dora masa a forehead yace
"Don't worry Halysaah" ita dai kallonsa kawai take, can ta tuna tana
da pain reliever a daki, mikewa tayi dai dai nan taji kamar ana kwankwasa kofa
a parlor, ta juya ta nufi kofar ta fita zuwa parlorn, tsaye tayi bakin kofar
parlon tana tambayar waye at the same time tana bude kofar, ta Ιan koma baya
tana kallonsa with surprise, shi ma daga sama har kasa yake kallonta hannunsa
rike da wayarsa, su biyu ne tsaye bakin kofar, lkci daya ta hade rai tace
"How may i help you?" Kai tsaye shi wanda yake mata kallon sama da
kasa ya shigo parlon har sai da ta matsa gefe da sauri kar ya bangajeta, shi
dayan mutumin dake tsaye bakin kofar calmly yace "Hello, plss is Jay in
here? Ahmad Jay...." Mutumin da ya shiga parlon ya juya yana masa wani
kallo yace "Kaii wajenta ka zo halan?" Shi wanda ke waje ya Ιan yi
murmushi ya shiga parlon ya sauke kai kasa, amma sai ya tsaya daga bakin kofar
bai karasa can cikin parlon ba, shi ko wanda ya fara shigowa har ya nufi hanyar
dakunan dake apartment din, da sauri Khaleesat ta nufesa a fusace tace
"How will you just barge into someone's apartment without excuse or an
explanation?" Juyawa yayi ya kalleta from head to toes, ita kanta bata san
me yasa ta tsaya Ιan nesa da shi ba taki ci gaba da bin sa ba amma bata fasa
masa kallon da take masa ba fuska a daure, ya gyada kai ya ci gaba da tafiyarsa
kamar yasan dakin, kawai taga ya bude ya shiga ciki, ta juya ta kalli mutumin
dake tsaye har sannan a parlor tace "Ku haka ake yi daga inda ku ka
fito?" Cikin nutsuwa mutumin yace "We are sorry Madam, location shi
Jay din ya tura masa wai bashi da lafiya and here is the location sannan mun ga
motarsa a garage din apartment din nan, hope we are in the right place?"
Khaleesat tace "Sai bayan kun shigo za ka tambayeni ko kuna right place
din?? Where Is it done this way?" Mutumin ya hade hannunsa biyu alamar
bada hakuri yace "Kiyi hakuri dai" Yana fadin haka ya bi bayansa ya
shiga har cikin dakin shi ma, bin su tayi amma ta tsaya a corridor, ji tayi
wanda ya fara shiga dakin da farko na cewa "Jay me kake yi a gidan nan da
wannan karamar yarinyar da bata da manners? Is this the reason why ka dena zama
24/7 a gida yanzu? When did u start this useless life? First of all who is the
little brat i want to know?" Da wani expression yake kallon Jay dake fama
da kansa a kwance yaki basa amsa, shi dai mutumin da ya shigo a karshe na tsaye
daga daya gefen Jay yana masa sannu, sai kuma ya kalli Ajay calmy yace
"Kaga dai bashi da lafiya yanzu Ajay, all this question isn't necessary
now" Da kyar Jay yace "Ka kyale Ιan iska mana, laifina ne da na tura
masa location" Ajay dai sai bin dakin da kallon mamaki yake yi ganin
property din Jay duk a dakin, can ya kallesa yace "To ma menene yasa za ka kirani? in baka da lafiya
ita yarinyar ta kai ka hospital mana, ba tare ku ke zama a gidan ba"
Mikewa zaune Jay yayi yace "Kai wai did you know how i am feeling? Ka wani
zo nan ka isheni da unnecessary surutu, pls get out Ajay, gerrout pls"
Khaleesat dake sauraron conversation dinsu ta wani taΙe baki ta juya ta koma
parlor ta zauna wani mugun haushin mutumin da taji ana kira da Ajay take ji a
ranta, taga Abdul ma balle shi, Salem ya mika ma Jay hannu zae taimaka masa ya
tashi, Jay yace "Pls kace mata ta kawo min bottle water, or you check the
kitchen ka dauko min" Salem ya juya ya fita, Ajay dake taΙe baki ya juya
ya fice daga dakin shi ma, direct ya nufi kofar fita daga apartment din yayi
ficewarsa ya koma can waje ya tsaya jikin motarsa, Salem dai ya bi sa da kallo
ya sauke ajiyar zuciya ganin fita yayi, sannan ya kalli Khaleesat ya gaya mata
ta dauko ma Jay ruwa, ta mike ta tafi kitchen ta dauko ruwan ta basa, ba a dau
lokaci ba sai ga shi sun fito tare da Jay, mikewa tsaye tayi tana kallonsa, Jay
ya zame hannunsa a na Salem ya zauna saman kujera ya jinginar da kansa da
kujeran ya lumshe ido, a hankali Khaleesat tace "Amma hospital zaku je
ko?" Da kyar yace "No, gida za mu je ya min treatment" Khaleesat
tace "To Allah ya sauwake, Allah ya baka lafiya" Ya gyada mata kai
sannan ya mika ma Salem hannu ya mike tsaye, Khaleesat na son tambayarsa abu
amma ta kasa, ganin za su fita daga parlon ta dake tace "Can i get ur
digit so i can be checking up on you?" Salem dai ya juya ya kalleta da Ιan
mamaki jin tambayar da tayi, does this mean basu san juna ba kenan tunda har
bata da lambarsa, Housemate din nata ya juya ya kalleta yace "Ai zaki gane
gidan da muka je ranan da na mance makulli da daddare bayan kin dawo Nigeria,
that's our home, zaki iya zuwa at anytime...." Khaleesat dai ta dinga
kallonsa, sai kuma yace "Salem give her my digit, ko kuma ka bata nata kar
ta kira bata sameni ba" Salem yace "Ohk bari in bata nawa"
Khaleesat ta dauko wayarta sannan ta amshi number Salem, bayan ya gama bata
suka fita daga parlon tare da housemate din nata, tana tafiya a sanyaye ta
karasa gun window ta bude labule tana kallonsu, sae da suka fito Ajay ya shiga
motarsa, bayan sun shiga yayi zoom off. Khaleesat ta sauke idonta sannan ta
juya a hankali ta koma cikin parlon. Bayan kwana uku Khaleesat sun fito daga
aji tare da Safiyyah dake waya, ita dai Khaleesat na tafiya ne amma gaba daya
hankalinta na wani gun daban, Safiyyah tace "Wai ya jikin Housemate din
naki yanzu? Ko ya dawo ne baki gaya min ba?" Khaleesat ta kalleta tace
"Har yanzu ai bamu yi magana da shi ba" Safiyyah tace "To wanda
ya baki number sa fa ko har yanzu bai daga kiran naki ba?" Khaleesat tace
"Aa ya daga jiya, amma sai yace min he is much better, da na tambayesa ko
yana kusa sae yace min a'a yana bacci, kawai ni dai i hope da gasken jikin nasa
da sauki..." Safiyyah tace "Shegen mutumi in ba kinibibi ba me yasa
zai wani Ζi baki lambar Housemate din naki sai na shi, me za kiyi da lambarsa
when u have no business with him, in ni ce ke cewa zanyi a'a ba nasa zai ban ba
gaskiya, amma fa har yanzu abun na ban mamaki ace duk mutuncin Housemate din
nan naki bai taΙa requesting phone number din ki ba ko sau daya, ji ma sanda
kika je Nigeria, to ko me yasa oho" Ita dai Khaleesat kallonta kawai take
bata ce komai ba, Safiyyah tace "To wai ma ba kince har cewa yayi ki je
gidan nasu ba, tun jiya nake ce maki mu shirya mu je kin ki, in baki je kin
dubasa ba ta yaya zai san kema kin damu da halin da yake ciki, ai ance gaida me
gaisheka, beside da bakinsa ya maki kwatancen gidan nasu ai, to me yasa baza ki
je ba, da Nigeria muke sai mu ce ai bai kamata ba saboda yan sa ido da yan
fassara lamari but this is USA Khaleesat, kuma abu ai kamawa yake for 3 days
baki san halin da mutumin nan yake ciki ba gashi ke kanki kina testifying
kyawawan halayyarsa, wallahi ki shirya in rakaki mu je ki dubasa da jiki, kuma
kafin nan mu fara biyawa ta shopping mall kiyi masa shopping da zaki kai masa,
shi ma sae yaji dadi wallahi" Khaleesat tace "Kawai sai in kama
tafiya har gidan nasu duba shi? Ai bai ma dace ba sai kace wasu marasa kamun
kai Safiyyah, be it in USA still bai dace ba, mu mata ne fa" Safiyyah ta
mata wani kallo, can tace "Ai da naki matsalar ya taso haka ya cire
kudadensa sama da miliyan goma sha biyar ko fin haka if i am not mistaken yayi
solving maki matsalar ki, shi kuma bai da lafiya rai kwakwai mutu kwakwai kince
zuwa dubasa rashin kamun kai ne, to rashin dacewa ya wuce zaman da ku ke yi
gida daya? Shi wannan me za ki ce masa? Wani lokacin baki ma nazarin maganar
dake fitowa bakin ki Khaleesat, in zuwa dubasa bai dace ba to zamanku gida daya
ma ai bai dace ba be it in USA" Khaleesat dai sai kallonta take ta kasa
cewa komai, can dai tace "Ban gane ba, Miliyan goma sha biyar for
what??" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Ohh for what ko? da yake
business class ticket din da ya siya maki an gaya maki na wasan yara ne ai, to
bari ki ji Business class ticket kusan 5000 dollars ne base on Airline, ki
lissafa 5000 ko 4000 dollars kudin Nigeria kiga nawa zai baki" Khaleesat
was speechless after realizing Safiyyah is saying the truth, banda dala dubu
dayan da ya bata da zata tafi, sannan ga kuma domestic flight ticket from lagos
to kano, and from kano to Abuja, bata mance irin hotel din da ta zauna na few
hours a garin Lagos ba, sauke idonta kasa tayi bata sake cewa komai ba,
Safiyyah ta ja tsaki tace "Wallahi ki ajiye wnn kauyancin naki ki zama
wayayyiya ki dinga yin abun da ya dace, komai a rayuwar nan kamawa yake
Khaleesat, to wai ku ka zauna apartment daya ba ace rashin kamun kai ba sai don
zaki je dubasa bai da lafiya? ni abinda ke daure min kai kenan" Khaleesat
dai taki cewa komai with many thoughts running her mind, a haka dai suka rabu
kowa ya tafi gida... The next day sai da Safiyyah tasan duk yanda tayi
convincing din Khaleesat da dadin baki da masifa da bacin rai, daga karshe
Khaleesat ta yarda su je can inda Housemate dinta yace gidansu ne su dubosa
amma fa don babu yanda ta iya da Safiyyah ne don har cikin ranta tsoron zuwa
anguwan take don unguwa ce na masu kudi a kasar, to in ma sun je su ce me ya
kai su? What if iyayensa ko wasu yan uwansa mata na gidan sai su yi yaya kenan?
Kasa hakura tayi har sai da tayi ma Safiyyah wannan tambayar, Safiyyah tace
"Dai dai kenan in ma iyayensa na gidan, ai ba Nigeria bane nan USA ne,
kuma tsaf za su amshe mu hannu bibbiyu su yi farin ciki da zuwan mu don duba Ιan
su muka je yi bai da lafiya" Khaleesat ta sauke wani boyayyen ajiyar
zuciya, Safiyya tace "Amma ni har raina ina son sanin dalilinsa na dawowa
apartment dinki ya zauna bayan ga nasu gidan can, nace da wani abu a kasa kince
min ba haka ba, wallahi kilan ya san ki from somewhere Khaleesat"
Khaleesat tace "Sai kuma kiyi ai, nace maki bamu taΙa sanin juna da shi
ba" Safiyyah tace "Ma ji ma gani dai" Sai da Safiyyah ta fara
jan Khaleesat zuwa inda za su siya kayan ciye ciye sannan suka yi ordering Uber
da zai kai su unguwan, tun da suka shigo Safiyyah ke kallon manyan Gidaje with
fascination, Khaleesat kuwa gabanta sai faduwa yake sai addu'a take a ranta,
ita banda Safiyyah tayi insisting da babu abinda zai kawota wai duba Housemate
dinta, dai dai kusa da gidan Uber din ya tsaya duk suka sauka, Safiyyah dake
zaro ido tana kare ma Glass house din kallo tace "Ke kin tabbata nan ne
kar mu shiga gidan mutane a kira mana 911 mu shiga uku Khaleesat"
Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba amma bata tanka ma Safiyyah ba,
Khaleesat ta ciro wayarta tayi dialing number Salem ita kanta zuciyarta bugawa
yake gaba daya she is afraid, sai da kiran ya kusa yankewa ya daga, sai gashi a
mota zai fito daga cikin gidan, sauka yayi daga motar ganinsu, yana kallon
Khaleesat da mamaki yace "Ohh you are here, sannu da zuwa...." Gaishesa
tayi ta sauke idonta kasa kamar munafuka, ya amsa da fara'a, Safiyyah ma ta
gaishesa sannan tace "Dama ta zo duba jikin Housemate dinta ne shi ne na
rakota" Yana gyada kai yace "Ohh that's so thoughtful of her, mu je
ciki to...." Suna biye da shi suka shiga cikin katon gidan, Safiyyah dai
sai gwale ido take tana bin gidan da kallo ta gefen ido, ita dai Khaleesat
gabanta sai faduwa yake sosai ko daga kai ta kasa, after walking briefly sai
gasu sun iso entrance din shiga parlon gidan, kofar shiga parlon ma kadai sai
ka kalla ka sake kalla, Safiyyah ta saci kallon motoci uku dake compound din
kuma masu tsada, suna shiga parlon gidan Khaleesat ta hada ido da Ajay dake
zaune kan kujera ga different fruits daga gefensa yana kallon abu a wayarsa at
the same time yana cin apple dake hannunsa, 3 quarter ne baΖi a jikinsa with
gray polo, tuni ta dauke idonta tsabar yanda ta rikice bata ma san sanda ta
bude baki ta gaishesa ba tana makale bakin kofa, hade rai yayi ya dauke kai ya
ci gaba da kallon abinda yake a wayarsa.
07087865788 ✍π»
[5/11, 5:06 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
14....
Safiyyah ma dake kallonsa kamar munafuka tana in-ina tace
"Good... good evening sir" Without looking at Safiyyah ya amsa yana
cin apple dinsa, Salem na kallonsa speaking calmly yace "Ajay sun zo duba
jikin Jay ne" Ajay ya ajiye apple din hannunsa, sai kuma ya kai wayarsa
kunne alamar bashi da lkcn basa amsa, ganin haka Salem ya juya ya kalli su
Khaleesat yace "Bari in masa magana a sama, za ku iya zama ku jira ni,
have a sit pls" Daga haka ya nufi stairs, ko haurawa saman bai yi ba
Khaleesat ta zaro ido tace "Innalillahi" da sauri ta koma bayan
Safiyyah ganin wani jibgegen kare ya nufo su yana haushi, Safiyyah ta dinga
buga ma karen jakar hannunta tana koransa ita ma a tsorace, Salem ya dawo
parlon da sauri ganin haushin da karen ke yi zai yi attacking dinsu, Ajay ya
mike ya nufi karen yana kiransa yace "C'mon Legend" Karen ya juyo da
gudu ya dawo gun Ajay da yayi patting din kansa, Salem ya dawo kusa da su yana
murmushi yace "Mu je saman kawai tunda tsoron kare ku ke, ai ba abinda zai
maku kawai yaga baΖin fuskoki ne shi yasa" Khaleesat da jikinta ke rawa ta
bi bayan Salem da sauri Safiyyah na biye da ita, a haka Salem yayi leading
dinsu har sama zuwa Bedroom din Jay, knocking yayi yana tsaye bakin kofar,
Khaleesat sai waige waige take tana ganin kamar karen zai sake biyo su saman,
sai da Jay ya amsa ma Salem knocking din da yayi sannan ya kallesu yace
"Bari in sanar masa yana da baΖi" Daga haka ya bude kofar dakin ya
shiga ciki ya kullo, Safiyyah ta rike haΙa ta kalli Khaleesat murya can kasa
tace "Ke wani tantirin Ιan iska ne wannan muka gaida a kasa ya mana
walakanci haka?" Khaleesat bata tanka ta ba, har sannan kuma bata daina
waige waigen da take ba don gani take fa karen nan zai iya biyo su har sama,
sai ga Salem ya fito daga dakin yana kallonsu yace "Za ku iya shiga, ni
zan Ιan fita sai na dawo" a hankali Khaleesat tace "Ohk mun
gode" Bude kofar dakin tayi still gabanta na faduwa ta shiga cikin massive
room din da sallama Safiyyah dake gwale ido na biye da ita a baya, wani Ιaddadan
kamshi hade da sanyin Ac ne yayi welcoming dinsu a cikin babban dakin,
Housemate din nata na zaune saman makeken gadonsa alamar Salem just woke him
up, his room was just something else wajen tsaruwa da haduwa, Khaleesat taki
yarda ta hada ido da shi zuciyarta na bugawa ta zauna nan Ζasan lallausan
carpet din dakin, a hankali yace "C'mon Halysaah, ga gefen gado ku zauna,
ko ku zauna kan kujera" Khaleesat bata dago kanta ba tace "I am
comfortable here" Ya lura kamar she is frightened, ya kalli Safiyyah dake kallonsa
bayan ita ma ta zauna, dan murmushi yayi mata yace "Hello...." Kana
jin muryarsa kasan he is still recovering, Safiyyah ta gaishesa da fara'a tana
tambayarsa jikinsa, yace "Alhamdulillah, ya karatu?" Tace
"Alhamdulillah" Ya kalli Khaleesat yace "Ya kwana biyu
Housemate? Hope you are doing good?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa
tace "Ya jiki?" Yana murmushi yace "Da sauki,
Alhamdulillah" A hankali tace "To Allah Ubangiji ya sauwake ya kara
lafiya" Yace "Ameen ya Allah" Safiyyah ta ajiye ledan hannunta
kusa da gadon dakin tace "She got you this" Khaleesat ta kalleta,
godiya yayi masu gaba daya, sai kuma ya fara kokarin sauka daga saman gadon
yace "Bari in kawo maku ruwa" Edge din gadon ya zauna kamar bazai iya
tashi ba, Khaleesat tace "Aa mun gode, we are okay" Ya kalleta a
hankali yace "To ai ba ke kadai nayi offering ba Housemate" After
some seconds ya tashi ya bude portable Fridge din dake dakin ya dauko masu ruwa
da tsadaddun lemuka duk ya ajiye masu sannan ya fita daga dakin walking slowly,
exactly irin kayan jikin Ajay ne a jikinsa shi ma, Safiyyah ta rike haba tana
kallon Khaleesat bayan ya fita, sai kuma tayi kasa da murya tace
"Khaleesat kin dai ga arziki ko? Gidansu kenan fa a Amurka ina ga Nigeria
kuma?" Khaleesat ta hade rai tace "Pls stop this Safiyyah"
Safiyyah ta rufe baki da sauri, sai kuma tayi kasa sosai da murya tace
"Kuma haka fa, kar ace da Cctv a dakin mu ji kunya" Khaleesat ta wani
kalleta tace "Ki ji kunya dai, tun da mun gaishesa ki tashi mu tafi
kawai" a hankali Safiyyah tace "Gaskiya Housemate din nan naki is
more than nice and calm, ni har naji yana burgeni wallahi, look how he welcomed
us warmly duk da bashi da lafiya" Khaleesat ta daga ido ta kalleta sai dai
bata ce komai ba, ita dai Safiyyah sai bin katon dakin take da kallo with
fascination, tayi kasa da murya tace "In na samu irin wannan dakin ai
mance me ya kawo ni kasar ma zan yi gaba daya, anya ma kuwa student ne
Housemate din nan naki" Khaleesat ta hade rai tace "Tashi mu tafi
tunda mun dubasa Safiyyah" Safiyyah tace "Amma ai kya jira ya shigo
mu yi masa sallama ko, dadina dake a ko ina sai kin nuna halin ki, kamar ana
koranmu daga shigowa gida kice mu tashi mu tafi" Budewar kofar dakin ya sa
duk suka yi shiru, Housemate dinta ya shigo da sallama ya zauna kan kujeran
dakin ya jinginar da kansa da kujeran, sai ga wani chef din gidan ya shigo da
wasu tsadaddun cookies ya ajiye masu kusa da su, sannan ya juya ya fita, Jay na
kallon Khaleesat yace "Naga kina son cookies sosai Housemate, here are
some for you and ur frnd" Bata yarda ta kallesa ba tana wasa da gyalenta
tace "I am okay, tafiya ma za mu yi" a hankali yace "So soon?
Amma sai kun ci cookies tukun" Khaleesat ta Ιan kallesa suka hada ido a
karo na farko tun shigowarsu dakin, sosai taji gabanta ya fadi tayi saurin
sauke idonta, ya kalli Safiyyah yace "In bazata ci ba ke ki ci abunki...
Amma ban san sunanki ba kawar Housemate" Safiyya tayi murmushi tana bude
cookies din ta dau guda daya tace "Sunana Safiyyah Adam" Yace
"Maa sha Allah, it's nice meeting you Safiyyah, i am Jawwad Ahmad, or you
call me Jay" Safiyyah tace "Nice meeting you too Jay" ita dai
Khaleesat wasa da gefen veil dinta kawai take kanta a kasa, Safiyyah ta bude
handbag dinta saboda kiran wayarta da ake yi, tana dubawa taga Cousin brother
dinta ne, ta mike tace "Let me pick a call pls" Jay yace
"Alright Safiyyah" Kofa ta nufa ta bude ta fita sannan ta kullo masu
kofar, ledan da suka shigo dakin dashi ya Ιan bude yace "You got me all
this Halysaah" Khaleesat ta Ιan kallesa tace "Um" Yace "Ohk
thank you so much i really appreciate" Tana kallonsa a hankali tace
"Ya jikin?" Yace "I am getting better gradually, daxu sai naji
ina sha'awar wannan tuwon da kika yi some days back" Tana kallonsa tace
"Na vegetable soup?" Yace "No, wannan da na kasa ci, the dark
soup, I can't remember the name" Bata san sanda tayi murmushi ba tace
"Ok miyan kuka?" Yace "Shi... kawai naji shi nake son ci
sincerely" a hankali tace "Ohk zaka je can gida anytime soon
ne?" A hankali yace "Idan na samu lafiya in sha Allah" Ita dai
Khaleesat kallonsa kawai take, shi kam idonsa na gun different direction, Ajay
ne ya bude kofar dakin, kai tsaye ya shigo ya nufi Jay yana mika masa wayar
hannunsa yana kallonsa, ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta bata kalli inda
yake ba, Jay ya amshi wayar yana duba screen din, sauke Ζafafuwansa yayi daga
kan kujeran da yake zaune ganin wanda ke kan layi, ya kai wayar kunne da ladabi
yayi sallama hade da gaisuwa, sai kuma yace "Alhamdulillah Abba da sauki,
wayar a silent yake ne shi yasa" Sai kuma ya daga kai ya kalli Ajay jin
abinda Abban ke ce masa, a hankali yace "A'a ba haka bane Abba, i do
eat... but not much, ba gaskiya ya fada ba" Daga haka yayi shiru bai sake
cewa komai ba, after a minute yace "To in sha Allah Abba, Allah ya kara
girma" Sai da ya jira Abba ya katse wayar sannan yayi wurgi da wayar saman
gadonsa yana kallon Ajay, wani kallo Ajay yayi masa ta gefen ido ya juya ya
tafi ya dau wayarsa a kan gadon sannan ya fice daga dakin, Khaleesat ta gama
tura ma Safiyyah text din da take na cewa tayi masu ordering Lyft su tafi gida,
sai kuma ta daga kai ta kalli Jay, ganin mood dinsa ya canza, a hankali tace
"Baka cin abincin ne ko?" Yace "Ki kyalesa mana, i took cereal
daxu da safe kuma a gabansa, shi in bai bata min rai ba baya jin dadi a
rayuwarsa" Khaleesat tayi shiru kamar bazata ce komai ba, can dai tace
"To ai Cereal ba abinci bane, ka dai dinga ci ko kadan ne" Ζan
murmushi kawai yayi bai ce komai ba, tace "Shikenan, za mu koma, Allah
Ubangiji ya baka lafiya" Yace "Baza ki bari Salem ya dawo yayi
dropping din ku ba?" Tace "Aa, Safiyyah nasan brother dinta ne ke
kiranta a waya, kaga tun daxu muka gama lectures bata koma gida ba" Yace
"Ohk ni bari in ajiye ku" Khaleesat ta zaro ido tace "Aa kai da
baka da lafiya, za mu yi ordering Uber do not worry about us pls"
Khaleesat ta mike, yana ganin haka shi ma ya tashi, amma sai da ya dafa kujera
for sometime saboda juya masa da kansa ya fara yi, A hankali Khaleesat tace
"Pls kar kayi stressing kanka, just lie down and rest" Ya dago kansa
yace "No, let me see you downstairs" Juyawa tayi ta nufi kofa, ya bi
bayanta, ga mamakinta sai ta ga Safiyyah tsabar samun waje tana zaune parlon
dake upstairs tana kallo tana cin cookies ga lemo a gabanta, to a ina ta samo
lemun da cookies, Safiyyah ta washe baki ganin Khaleesat sannan ta mike tace
"Shikenan mu tafi?" Jay da ta hango ne yasa tayi tsit, Khaleesat ta
nufeta suka fara sauka downstairs a tare amma gabanta faduwa yake kar su kara
ganin karen daxu, hakan yasa ta bari Safiyyah ta shiga gaba, Jay na biye da su
a baya har suka sauko downstairs, ai ko karen na ganinsu ya nufo su da gudu
yana haushi, Khaleesat ta juya a tsorace zata koma sama ta ci karo da Housemate
dinta dake bayanta, ya rikota da sauri yace "C'mon, are you afraid of dog
Halysaah?" Bayansa ta koma zuciyarta na bugawa, Safiyyah kuwa sai kora
karen take da jakar hannunta fuska daure, shi dai Ajay na zaune parlor tun da
ya kallesu sau daya ya dauke kai ya ci gaba da kallon Football da yake, sai da
Jay ya kori karen sannan ya juya da gudu ya koma gun Ajay ya zauna saman
kujeran kusa da shi, Jay ya juya ya kalli Khaleesat da ta marairaice ita ma
tana kallonsa, ya Ιan yi murmushi yace "Ba abinda zai maku ai, bai san ku
bane shi yasa...." ita dai bata ce komai ba, Jay ya jufi Ajay yace
"Ajay ina makullin motana?" Ajay yace "Me zaka yi da makullin
mota?" Khaleesat dai tuni ta nufi kofar fita parlon da sauri don ko kallon
Ajay bata son yi, Safiyyah kam tana kallon Ajay tace "To sai anjima,
Nagode sosai" Yace "Allah ya tsare" sallama tayi ma Jay shima
sannan ta bi bayan Khaleesat, Jay yasan bazai basa makullin ba, hakan yasa ya
duba aljihun Ajayn ya zaro few dollars sannan ya juya ya bi bayan Safiyyah, duk
yanda yayi da Safiyyah ta amshi kudin taki amsa, Khaleesat tuni ta kusa fita
daga gidan gaba daya, a haka Safiyyah ta bi bayanta. Safiyyah na kallon
Khaleesat bayan sun shiga Lyft har sun fara tafiya ta rike haΙa tace "Ke
ashe wannan gayen da muka yi misunderstanding da farko da muka shigo gidan yana
da kirki sosai, in gaya maki da na zauna parlon nan na sama ni kadai ya zo
wucewa ya ganni sai ya tsaya yayi powering min TV, har da kunna min wutan
parlon, ya kuma nuna min fridge in dau lemo in sha, wallahi i never expect such
kind gesture from him duba da yanda ya amsa mana gaisuwanmu da muka shigo
parlon da farko, ashe mun yi misperceiving dinsa ne" Khaleesat tayi kamar
ma bata ji abinda Safiyyah ke cewa ba.
07087865788 ✍π»
[5/12, 6:46 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Read My Book
"HALYSAAH" on
ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6
✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
15.....
Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune parlor tana
duba wani reading material dinta wayarta ya fara vibrate, daukan wayar tayi
taga number Salem, ita dai kallon screen din kawai take at first, after some
seconds ta daga ta sa Hands-free tayi shiru tana saurare, daga daya bangaren
aka mata sallama, muryar Housemate dinta ta ji, ta amsa sallamar tare da
gaishesa, yace "Ya kika je gida Halysaah?" Tace "Lafiya
lau" Yace "How about Safiyyah?" Tace "Tana can gidansu"
Yace "Good, thank you so much for the visit" a hankali tace
"Allah ya kara lafiya" Yace "Ameen Housemate" Daga haka
yayi mata sallama ya katse wayar, bata kai ga ajiye wayar ba wani kiran ya sake
shigowa ta ga Abdul ne, sai a sannan ta tuna damuwar da take ciki for days now,
nan da nan mood dinta ya canza, tayi picking call din ta saka hands free sannan
ta ajiye a gefenta tana ci gaba da duba reading material dinta a hankali ta
gaishesa, yace "Didn't you see the money i sent to you?" Ta girgiza
kai tace "Ban kula ba" yace "To ki duba" Katse wayar yayi
ta jinginar da kanta jikin kujera with many thought running her mind....
Washegari da yamma bayan Khaleesat ta idar da sallah tana zaune tayi dialing
number Salem, yana fara ring ya daga, bayan sun gaisa tace "Dama abinci ne
zan ma Housemate dina yace min yana so, ban san ko zaka iya zuwa karfe biyar
sai ka tafi masa da shi ba, that's if you are available and u don't mind doing
so pls" Yace "Oops naje Pennsylvania daxu da safe, but za ki iya zuwa
gidan ki kai masa ai, he is at home" A hankali Khaleesat tace
"Ohk" Yace "Yeah, ki kai masa kawai can gidan" Tace
"To nagode" a haka suka yi sallama ta ajiye wayar, Allah ya so bata
dora girkin ba don ta san babu abinda zai sake maida ta gidan nan dai, tayi
zuwan farko tayi na karshe. Khaleesat na zaune tare da Safiyyah bayan sun gama
lectures din su na ranan, Safiyyah tace "Are you checking on ur Housemate
even if ta waya ne kuwa Khaleesat?" Khaleesat ta kalleta tace "I
don't have his number ai" Safiyyah ta dinga kallonta da mamaki, can ta
girgiza kai tace "Ni ban san me yasa kike haka ba, why won't u ask that
guy Salem ya baki? It's almost 10 days now da muka je gidan dubasa tunda kika
ga har yanzu bai zo apartment dinku ba kinsan kilan ko bai ji sauki bane"
Khaleesat tace "There was a time da muka yi waya da Salem din yace zai
turo min lambarsa kuma bai turo ba shi sa har yau ban sake masa magana ba naga
kamar baya son tura lambar ne, sannan kawai i assume kilan wannan arrogant guy
din ne na gidan yayi stopping dinsa from coming to the house, i suspect they are
kind of related or something like that" Safiyyah ta tabe baki tace
"To ko in raka ki mu sake zuwa dubasa ne?" ko rufe baki bata yi ba
Khaleesat tace "I am going no where, sai dai in ke zaki je sai in masa
tuwo ki kai masa, dama ranan da muka je yace min yana son tuwo da miyar kuka,
but for me babu abinda zai sake maidani gidan nan wallahi" Safiyyah ta
dinga kallonta, can tace "Gaskiya zuciyarki kamar dutse yake Khaleesat,
wato har ce maki yayi yana son cin tuwo amma kika kasa yi ki kai masa saboda
wani banzan dalilinki, gaskiya you are not nice at all sorry to say"
Khaleesat ta mike tace "Ki kirani ko ma me zaki kirani amma wallahi bazan
koma wannan gidan ba as far as that bossy Man is in the house, kawai sai in
kama hanya in sake komawa don yaji dadin kara raina min hankali ya walakanta
ni, in dai ke zaki je zan yi girkin in baki, after all kince the arrogant guy
is nice to you ai" Safiyyah bata tanka ta ba ta fara danna wayarta kawai,
a haka suka rabu ko sallaman kirki basu yi da juna ba, har Khaleesat ta isa
gida a lyft bata san sun iso ba, a duk kwanakin nan Allah ya sani Housemate
dinta na ranta don babu ranan da zai zo ya wuce bata tunasa a zuciyarta, ba
willingly taki zuwa gidan ta dubasa ba kawai wannan mutumin ne bata son ta sake
haduwa da, sannan she is afraid of the huge dog in the house, kar ma taje
mutumin ya sakar mata karen ta shiga uku, amma a ko da yaushe Housemate dinta
yana ranta tana kuma son sanin how he is feeling, a hankali ta bude motar ta
sauka duk jikinta a sanyaye ta nufi apartment dinta ta bude kofar ta shiga,
turus tayi a living room din ganinsa kwance kan 3 seater yana bacci, juyawa
taga yayi with his eyes still close yace "Good evening Halysaah"
Sauke idonta tayi daga kallonsa, walking slowly ta karasa cikin living room din
ta nufi can kusa da single sitter ta tsaya still looking at him, a hankali ya
bude ido ya fara bin parlon da kallo alamar he is looking for her, suna hada
ido calmly tace "Good evening" Mikewa zaune yayi trying to recover
fully from his sleep yana shafa fuskarsa yace "How are you?" Tace
"Alhamdulillah, ya jikin?" Yace "Naji sauki ai" Shiru tayi
kamar me tunanin abinda zata ce, can kuma dai tana rike da edge din gyalenta
cikin nutsuwa tace "Naga baka zo bane, i thought jikin ne har
yanzu...." Ya girgiza kai without looking at her yace "Abbana ne yasa
na je Nigeria, we spent 6 days in Nigeria, jiya muka dawo" Yana fadin haka
ya daga kai yaga kallonsa take, da sauri ta kauda kanta tana nodding tace
"Ohk" Daga haka ta juya ta nufi dakinta kamar munafuka, ya koma yayi
kwanciyarsa. After almost an hour Khaleesat ta fito parlor, ta samesa zaune ya
gama baccin yana danna laptop dinsa, kanta a kasa ta karasa cikin living room
din ta dan kallesa suka hada ido tana kame kame tace "Dama tambayarka zan
yi in maka tuwon ne yanzu zaka ci?" Yace "Tuwo kuma? Aa kinga you
just came back from school, ki bari next time in sha Allah" Tace
"Ohk" Daga haka ta tafi kitchen to make a light dinner, bayan ta gama
girkin ta fito parlor, har sannan yana nan zaune, ta Ιan kallesa tace "You
care for some?" Ya kalli hanyar kitchen din sai kuma yace "Let me
dish it my self" Daga haka ya ajiye laptop dinsa ya mike ya tafi kitchen
din, ita dai tana tsaye ta bi sa da kallo, bayan few minutes ya fito da bowl
din pasta din ya zuba very little quantity, with another plate of the pasta,
ita dai kallonsa take, ya mika mata na plate din ta sauke idonta ta amsa, ya
zauna ya ajiye bowl din nasa, a hankali tace "Wannan ne zai isheka?"
Yace "Eh" juyawa tayi zata bar wajen, yace "Bedroom za ki je ki
ci abincin kenan" Ta gyada masa kai tayi tafiyarta daki. Wajen karfe tara
na dare Khaleesat ta saka hijab dinta jin yana knocking kofarta sannan ta tafi
ta bude kofar, yace "Sai da safe Halysaah, i am going home" at first
shiru tayi, can kuma a hankali tace "Why are u having two home?" Ya Ιan
buda ido yayi murmushi yace "One is a home, the other... a comfort
zone" Ta langwabar da kai tace "U said two same thing ai, A Home is
also known as a comfort zone" Dariya yayi yace "Not in my case
Halysaah, they are two different thing to me" Shiru tayi kafin tace
"So now, which is home and which is comfort zone?" Yayi murmushi yace
"Kema dai kamar er jarida, how is ur frnd?" Tace "She is
fine" Yace "And ur Bossy boyfriend, hope ya daina saka ki kuka dai
yanzu?" Ta wani kallesa zata kulle kofarta da sauri yace "Wait, it's
just a harmless question Halysaah" Tace "To da nace maka kuka yake sa
ni?" Yace "Ohk, Allah sa kar in zo ina baki hakuri kwanan nan bayan ya
saka ki kukan, and before i forget me yasa baki cin cookies dake kitchen?"
Tace "Nawa ne da zan ci?" Yayi shiru kamar bazai ce komai ba, can
kuma yace "To ki dinga ci daga yau duk abinda kika ga na siya ki dauka
idan kina bukata, I didn't buy them all because of my self alone, ko da namiji
ne a gidan nan ko wata mace daban in zan siya abu in ajiye zan siya ne in
surplus not for only me, kin gane ko? Har bottle water ina siya mana ne mu biyu
ba ni kadai ba, after all there is love in sharing" Ita dai idonta na kasa
bata ce masa komai ba, Yace "Good night" juyawa yayi ta bi sa da
kallo har zuwa parlor, sai kuma ta kulle kofar dakinta a hankali. Washegari
Asabar Khaleesat ta gama laundry da take a kitchen, tayi tidying din duk gidan
sannan taje tayi wanka ta fito parlor tana tunanin abinda zata girka kafin ta
fara karatu cause it's almost 12pm, tun karfe goma Housemate dinta ya shigo
gidan ya wuce Bedroom dinsa, ta ma san bacci, ita kam mamakin yanda baya gajiya
da bacci take, knocking kofar parlon aka yi, she is expecting Safiyyah dama
amma bata yi tunanin da wuri zata zo ba, ta karasa gun kofar ta bude a bit
relieve ta samu me taya ta girki, da mamaki ta bi sa da kallo bayan ta koma
gefe don da ta ci gaba da tsayuwa wajen taga alamar bangajeta zai yi ya shiga
parlon, direct taga ya nufi dakin Jay ya bude ya shiga, kasa rufe baki tayi
tsabar mamaki, tana jin sa yana ma Jay bala'i a dakin, ita dai bata ji muryar
Jay din ba, Jay ne ya fara fitowa daga dakin, kamar yanda ta zarga kuwa baccin
yake, laptop din da ya bari kan kujera da ya shigo daxu ne ya dauka, Ajay na
fitowa ya mika masa laptop din, a mugun fusace Ajay yace "What the hell
should i do what with it again bayan lokaci ya kure? Kasan implications din da
abin nan da kayi zai ja min kuwa?" A karo na farko Jay yace "Kai
dalla wayar a silent yake, kuma ni ban san akwai recent aikinka a ciki ba, da
bazan taho da shi ba ai" Ajay dai kallonsa kawai yake kamar ya shaΖo sa,
Jay ya zauna kan kujera ya jinginar da kansa tare da lumshe ido, banda hararan
Ajay babu abinda Khaleesat da ke tsaye parlon take yi, lkci daya Jay ya mike
yace "Hey let me see you off, wanka zan yi" a takaice Khaleesat tace
"And pls Housemate warn him not to ever barge into someone else's
apartment like this again, this isn't a shopping Mall da zai shigo kai
tsaye" A tare suka juya suna kallonta gaba dayansu, Ajay yayi facing dinta
calmly yace "Ke, da ni kike wannan maganar ko wa?" Ta wani kauda kai
fuskarta a daure tace "In baka son ayi da kai kar ka sake shiga gidan
mutane babu Excuse, after all ba tare muke renting apartment din ba da zaka
shigo min gida without notice, idan wajen abokinka ka zo maturely sai ka jirasa
a waje, you don't have to push ur way into people's apartment like it's a
shopping complex" Ajay that was speechless ya kalli Jay, Jay ya shafa
kansa yace "Why didn't u knock and wait for me outside, after all she is
saying the truth" Khaleesat tace "Ni in ya sake shigo min gida haka
wallahi 911 zan kira masa..." Ajay ya ciro wayarsa a aljihu yana mika mata
yace "Call them immediately" Ta jefa masa wani kallo tayi hanyar
dakinta, Yana kallonta da kyau yace "I will definitely deal with you"
Ita dai tuni ta shige dakinta ta kulle kofar da makulli, Jay na kallonsa yace
"Me yasa zaka shigo mata gida kamar tsohon barawo?" Ajay yace
"Za kayi bayanin me kake yi da mace under the same roof in America, macen
ma da ka kusa haifa, i promise to report you back home, ita kuma i will teach
her the lesson of her life" Yana kai wa nan ya fixge laptop dinsa a hannun
Jay, Jay dake murmushi yace "Babu abinda ka isa kayi mata don ta gaya maka
gaskiya Malam, kai waye da baza a gaya ma gaskiya ba" Tuni Ajay ya fice
daga parlon, Jay ya zauna kan kujera ya dafe kansa yana dariya, the incident
was just funny to him, kallon kofar dakinta yayi yana mamakin dama wai haka
yarinyar nan take amma take ma saurayinta kuka? Mikewa yayi ya nufi dakin nata
yayi knocking kofar yace "Halysaah" sai da ya kirata sau uku sannan
ta bude kofar a hankali tana leka parlon kana ganinta kasan a tsorace take,
dariya yayi yace "Kinsan waye shi da kika masa rashin kunya Halysaah?"
Ta wani turo baki tace "To ni ina ruwana da koma wanene shi, saboda me zai
shigo min gida kamar wani barawo, where is it done that way? Ni dai wallahi kar
ya sake zuwa min gidan nan in ba haka ba in kira 911" Jay dai sai
sauraronta yake, can yayi murmushi yace "So dama kina da baki haka amma
kike ma saurayin ki kuka?" Khaleesat ta wani kallesa ta hade rai tace
"Ni bana son haka" still smiling yace "Ok, sorry" keeping a
straight face tace "Ya tafi?" Jay ya juya zai bar wajen yace "Ya
tafi mana" Da sauri tace "Plss ni dai kayi masa magana kar ya sake
zuwa, if there is anything ai sai ya kira kaje can gidanku ka samesa kawai ba
sai ya zo nan ba" Jay dai murmushi kawai yake yace "Ohk" parlor
taga ya tafi, ta koma dakinta ta zauna bakin gado, har sannan gabanta faduwa yake,
ita kanta bata san inda ta samu courage din gaggaya masa abubuwan da ta gaya
masa ba, ko don dama tana jin haushinsa ne yasa ta samu irin wnn courage din
oho, bata fito daga dakinta ba sai da tayi sallan zuhur, a hankali take tafiya
ta shigo cikin parlorn, gani take kamar zai sake dawowa gidan at anytime, ai ko
wallahi yan sanda zata kira masa, Zaune taga Jay a parlon yana danna wayarsa,
tana tsaye bayan kujera tace "Did u warn him not to come back plss?"
Jay yace "To ke meye damuwarki ba kin masa warning kar ya sake dawowa ba,
ai bazai dawo ba" Kamar zata yi kuka tace "Wallahi zai iya dawowa,
kuma in ya dawo baka nan ya zan yi?" Dariyar da yake dannewa ne ya taho
masa yace "Ina kuwa zan san yanda za ki yi, ke wa ya aike ki yi masa
rashin kunya? Da sai ki yi shiru da bakinki har in fitar da shi daga gidan,
Laptop dinsa na dauko daga can gida yana bacci ban san akwai aikinsa da zai yi
put foward ta email ba, yana ta kiran wayana kuma ina bacci na sa wayar silent,
that was what brought him here" Zaunawa tayi kan kujera tace "That
doesn't still warrant him ya shigo gidan mutane kai tsaye, ko magana bai min ba
ina bude kofa ya kusa bangajeni fa ya shigo parlon, am i a joke to him?"
Dariya Jay yayi yana gyada kai yace "This energy u used in attacking him
Allah ya baki irin energy din kiyi using ma Boyfriend din ki" Wani kallo
Khaleesat tayi masa, shi dai murmushi kawai yake still not looking at her yace
"Naga kamar kin damu da abinda kika masa, ko in kirasa ki basa hakuri ta
waya komai ya wuce?" mikewa tayi a takaice tace "Allah ya
kiyaye" Daga haka tayi wucewarta kitchen, shi dai murmushi kawai yake
looking at a different direction, yasan yau da kyar Ajay yayi bacci akan abinda
tayi masa. Bayan Khaleesat ta gama girkin da take ta fito parlor tana kallon
Jay ganin fita zai yi don har ya shirya yana saka agogon wrist dinsa without
looking at her yace "I think sai gobe zan dawo in sha Allah" Ta
marairaice amma bata ce masa komai ba, har cikin ranta ta fara jin tsoron
kasancewarta ita kadai a gidan, ya Ιan kalleta yace "Any problem?" Ta
hade rai tace "Toh ka bani makullinka idan ka zo goben sai kayi knocking
in bude maka kofar" Da mamaki yace "Why?" Tace "So that
baza kaje ka ajiye key din recklessly ba wannan mutumin ya gani ya dauka"
Yayi dariya yace "To ya dauka yayi me da shi?" Ta nufesa tace
"Bani" ba musu ya bata makullin ta amsa sannan a hankali tace
"To abincin fa?" Yace "Abinci? Wani iri?" Bata tanka sa ba
ta juya ta koma kitchen din, after some minutes sai ga ta ta dawo da plate din
rice and stew, ya Ιan bude ido yace "Wa zai cinye duk wannan?" Tace
"Kai mana" Ya zauna sannan ta mika masa abincin, yana girgiza kai
yace "It's very plenty" tace "Should i get you water?" Yace
"I will appreciate that" kitchen din ta koma ta dauko masa ruwan gora
da drink din gwangwani, yace "Thank you Halysaah" dakinta ta wuce,
after a while taji yayi knocking kofar dakinta, bayan ta bude yace "Zo ki
bude min kofar zan tafi" Makulli ta dauko ta tafi ta bude masa kofar yace
"Thank you, see yah tomorrow" ita dai bata ce komai ba ya fita daga
parlon ya nufi garage, a hankali ta kulle kofar da makulli sannan ta tafi
window ta Ιan bude labulen tana kallonsa har ya bar garage din after some
minutes, Sake curtain din tayi, walking slowly ta tafi kitchen, bude abincin da
ya rufe tayi taga kadan ya ci a ciki, Allah yasa yayi spoon hudu, naman ma
kawai daya ya ci, kulle abincin tayi ta dawo parlor ta zauna, dai dai nan taji
anyi knocking kofar parlon mikewa tayi da sauri tana kallon kofar a tsorace, da
kyar tace "Waye??" Muryar Safiyyah taji, lkci daya ta sauke ajiyar
zuciya sannan ta tafi ta bude kofar, Safiyyah tace "Har kin gama laundry
din?" Khaleesat tace "Na gama" Safiyyah tace "Housemate din
naki ya fita kenan?' Khaleesat tace "Eh" Safiyyah tace "Jiya da
daddare da kika gaya min ya zo gidan ta chat wallahi nayi farin ciki, don
mutumin na da kirki sosai" Khaleesat bata tanka ta ba, ta koma cikin
parlon ta zauna tace "Ban gan ki da laptop dinki ba" Safiyyah tace
"Abeg i will use urs, bani da strength din dauko laptop, kin yi girki kuwa?
Don yunwa nake ji, wancen er iskar matar faten wake tayi saboda tasan ba na ci,
hegiya dama bayerabiya ce ta wajen uwarta ai" Dariya kawai Khaleesat tayi
ta mike ta tafi kitchen, abincin ta zubo ma Safiyyah, ita kuma ta dau wanda
Housemate dinta ya rage, ta dauko masu ruwan gora da lemon kwali daya....
07087865788✍π»
[5/13, 6:21 PM] khaleesat Haiydar π✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
16.....
Ko da wasa Khaleesat bata ba Safiyyah labarin abinda ya faru
tsakaninta da Ajay ba, amma fa bata da rest of mind gani take kamar zai iya
dawowa gidan at anytime, upon all her restlessness bata ji tayi da ta sanin
abinda tayi masa ba, dama haushi yake bata, Safiyyah na kallonta tace "Ke
kwana biyu shiru banji kince ga abinda Abdul yayi maki ba ko dai ya fara
canzawa ne? This is so unusual, ko baki gaya min ba in dai ya maki wani abu you
are always moody in school, ta haka nake ganewa" Khaleesat na powering laptop
dinta ta tabe baki tace "Ni ina naga wannan time din yanzu ga exams a
gabana" Safiyyah tace "Atoh dai, wallahi naji dadin da kika fara
daukar shawarata kina fita sabgarsa, sauranki abu daya yanzu" Khaleesat ta
daga kai ta kalleta, Safiyyah ta gyara zama tace "Saura ki fara mayar masa
da magana, in ya gaya maki daya ki gaya masa biyar" Ita dai Khaleesat bata
sake ce mata komai ba tana neman softcopy na course din da za su yi studying
tare da Safiyyah. Bayan tafiyar Safiyyah... Khaleesat ta wanke utensils da suka
yi amfani da sannan ta wuce dakinta, wayarta ta dauka ta shiga WhatsApp don
ganin ko Ummanta tayi mata reply din message da ta ajiye mata daxu, wajen karfe
goma da rabi tana shirin kwanciya wayarta ya fara ring, dauka tayi taga Abdul
ne ke kiranta, ta dinga kallon wayar, tun sanda Ummanta tace mata tana ganin
kamar lkci aka tsayar take wani jin tsanarsa a zuciyarta, gashi yaki gaya mata
ko da gasken an tsaida lkcn ko ba a tsayar ba don Ummanta ba wai ta tabbatar
bane ita ma a gari ta ji, dama tana Nigeria din ne ta san gun warce zata je
taji ko hakan ne ko ba haka ba, Ιaga kiran tayi kafin ya katse ta kai kunne,
muryarta kamar me bacci ta gaishesa, ya amsa, a hankali tace "Ya
aiki?" Yace "Lafiya lau" Shiru tayi bata sake cewa komai ba,
yayi Ζasa da murya yace "I don't know, kawai ina missing din ki ne yau, i
want to be with you Baby" Ta kauda kai kamar irin yana kusa da ita din nan
tace "Um" Yace "Yaushe za ku fara jarabawan?" Tace
"Nan da wata daya" A hankali yace "Ohk, sai da safe, naga kamar
kin fara bacci" Tace "Um, ina son tashi inyi karatu ne anjima shi sa
na kwanta da wuri" Yace "To ci gaba da baccinki, sai mun yi
magana" Daga haka ya katse wayar, ta jefar gefenta ta ci gaba da chatting
da take da Ummanta. Washegari lahadi Khaleesat na zaune dakinta tana morning
Supplications dinta taji ana kwankwasa kofar parlor, wayarta ta jawo tana duba
agogo taga bakwai ya wuce, ta daure ta mike tana tafiya a hankali ta fito
parlor, bayan ta karasa bakin kofar with calmness tace "Waye?" Taji
muryar Housemate dinta yace "Good morning" bude kofar tayi ta koma
gefe ya shigo, sau daya ya kalleta yace "How was ur night" Ta kulle
kofar tace "Alhmdlh" Materials din hannunsa ya ajiye saman 1 seater
sannan ya kwanta kan doguwar kujera, ita dai bin sa tayi da kallo taga har ya
kulle idonsa yana gyara kwanciyarsa alamar bacci zae yi, tana tafiya a hankali
ta koma dakinta, ta karasa azkar dinta sannan ta kwanta. Har wajen karfe daya
na rana Khaleesat bata fito dakinta ba, ta Ιan juya daga kwancen da take tana
kallon kofar dakinta jin ana knocking, kiranta taji Housemate dinta ke yi,
mikewa zaune tayi still tana kallon kofar amma bata sauka daga kan gadon ba,
Calmly tace "I can hear you" Yace "Are you alright? Naga kamar
baki yi breakfast ba ko?" Shiru tayi bata ce komai ba, bude kofar taga
yayi, ta gyara blanket din jikinta tana kallonsa, ya tsaya daga bakin kofar
dakin yace "Hope nothing?" Ta langwabar da kai tace
"Nothing" Yace "To me yasa baki fito kinyi breakfast ba or are
you fasting? Beside today is sunday" Ta kauda idonta tace "Kawai
dai..." Sai kuma tayi shiru, ya karasa cikin dakin yace "Kawai dai
me?" Kamar baza tace komai ba sai kuma dai tace "Ina jin ciwo a
kafana ne" Yace "Ciwo a kafa kuma? Yana maki haka ne?" A hankali
tace "Once a while" Shiru yayi jin abinda tace, can yace "Then
what is the cause?" Ta Ιan kallesa, sai kuma ta bude hannu alamar bata
sani ba, yace "Kun taΙa zuwa hospital a kan hakan?" Ta dai yi shiru
without looking at him, sai kuma tace "It's fine, i will get better before
evening in sha Allah" Ya juya as if trying to diagnose without examination
the cause of her leg pain at her age, sau daya ya kalli gaban dressing mirror
dinta sai kuma ya juyo yana kallonta yace "Ok i get, Allah ya
sauwake..." Ta Ιan kallesa, yace "Try getting a hot shower, you will
feel better" Juyawa yayi ya fita daga dakin, a hankali Khaleesat ta koma
ta jingina da pillow, ko tashi tsaye bata jin zata iya a yanzu dai, kilan zuwa
can anjima ta Ιan ji relieve before she can stand up and do anything, kiran
Abdul ne ya shigo wayarta ta kife wayar taki dagawa don ko magana bata so,
after some minutes ta kalli kofarta jin knocking at the same time ya bude kofar
dakin ya shigo ciki rike da cup din hot chocolate, sauke idonta tayi daga
kallonsa ya karasa har side din da take ya duka yana mika mata Mug din hot
chocolate din yace "Try drinking this, will get u pain reliever now"
Ta amshi Mug din without looking at him a hankali tace "Thank you"
Yace "You are welcome" Daga haka ya fita daga dakin ta bi sa da kallo
babu ko kiftawa, yana fita kiran Abdul ya sake shigowa wayarta still taki
dagawa daga karshe ma tayi silencing wayar, khaleesat na gama shan hot
chocolate din ta ajiye cup din a bedside drawer sannan ta koma ta kwanta tayi
lamo kan pillow, kamar zata kira Safiyyah daxu wajen karfe sha biyu sai kuma ta
fasa hoping the ache will subside, har ta fara bacci Housemate dinta yayi
knocking wajen karfe biyu almost 20 mins bayan fitarsa daxu, sai da ta amsa
sannan ya bude kofar, ita dai bata juyo ba, ya zaga ta inda take calmly yace
"Are you sleeping Halysaah?" Ta bude ido tana girgiza kai, ya ajiye
ledan abincin hannunsa da pain reliever da ya siyo mata yace "Baki yi hot
shower da nace kiyi ba?" Tace "Zan yi" Yace "Ohk ga maganin
sai ki ci abinci ki sha" Ta mike zaune without looking at him, a hankali
tace "Thank you" Yace "Zan fita but i will come back around 6pm
in sha Allah" Tana kallonsa tace "Toh makullin gidan fa?" Ζan
murmushi yayi yace "Ai a jikin kofar kika bar sa daxu da kika bude min da
safe" Tace "Amma baza ka tafi da shi ba ai" Yace "To taso
ki kulle kofar" Ta wani kallesa, er dariya yayi yace "Shi fa Ajay
nasan yanxu kuma ya mance abinda ya faru tsakanin ku, may be sai ranan da ya
kara ganinki zai tuna, but for now i am assuring you ya mance wallahi he is
even busy with his upcoming defense, beside you misperceived him, Ajay is more
than nice and calm, ba shi da matsala, kawai dai shaidan ne ya saka rashin
jituwa tsakaninku tun a ranan da ku ka hadu" Khaleesat dai ta kyabe baki
don ko duk jikinta kunnuwa ne bazata taΙa yarda da abinda yake fadi ba, Jay
yace "Baki yarda ba ko?" Ta buda ido sosai tace "To dama saboda
me zan yarda?" Dariya kawai yayi yace "Take care of ur self Halysaah,
in kin ci abincin ki sha magani, let me get you bottled water" Daga haka
ya nufi kofa ita dai ta bi sa da kallo har ya fita, sai gashi ya dawo mata da
ruwan gora mara sanyi ya ajiye a inda ya ajiye mata ledan abinci da magani wato
bedside drawer, yace "See yah later" a hankali tace "Thank you,
and pls do not mishandle the key" Murmushi kawai yayi ya gyada mata kai ya
fita daga dakin ya kullo mata kofar, ta sauke idonta kasa, after some minutes
ta dau ledan abincin da ya ajiye mata a hankali tana budewa don ganin abinda ya
siyo mata. Karfe shidda saura Khaleesat na zaune kasan dakinta ta kwantar da
kanta jikin gado tana voice note da Ummanta, zuwa sannan she is feeling very
much better don har ta gyara dakinta ta wanke bandaki tayi wanka, parlor ne dai
taji bazata iya gyarawa ba, wajen karfe hudu suka yi chatting da Safiyyah tace
mata zata zo karfe bakwai, Khaleesat ta dan yi jim bayan taji kamar an bude
kofar gidan, gabanta ne ya fadi bayan Ajay ya fado mata, ta ajiye wayar
hannunta a hankali tana kallon kofar dakinta, after few minutes taji an yi
knocking kofar dakin, she felt a bit relieved, with calmness tace "I can
hear you" Taji muryar Housemate dinta yace "Can i open the
door?" Tace "Okay" bude kofar dakin yayi yana daga bakin kofar a
tsaye yace "Good evening Housemate, how are you feeling?" Tace "Da
sauki" Yace "Are you sure?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa,
ta dan kwantar da kanta gefen gado tace "It's better than before"
Yace "To Allah ya sauwake, where you able to go to the kitchen?" Ta
gyada masa kai, yace "Ohk" Har zai kulle mata kofar sai kuma ya tsaya
yace "Ko mu dan yi strolling as exercise, around the neighborhood, it will
help you feel much better too" Khaleesat ta daga ido ta kallesa, yace
"I will be waiting for you at the parlor, make sure to put on ur jacket
cause it's freaking cold outside" Yana fadin haka ya fita daga dakin, Khaleesat
dai na ta zaune kamar me nazari, it took her almost 5 mins of deciding kafin ta
mike a hankali, veil dinta kawai ta dauka ta yafa ta dau wayarta tana tafiya a
hankali ta fito daga cikin dakin, tsaye ta gansa ya jingina jikin pillar dake
kusa da study area yana danna wayarsa daya hannunsa rike da jacket dinsa, yana
ganinta yace "Are you ready? Where is ur jacket?" Karasawa yayi inda
take tsaye yace "It's cold outside" Yana fadin haka ya ajiye mata
Jacket dinsa kan kujeran dake kusa da ita yace "Use this, bari in dauko
wani" Dakinsa ya koma ita dai ta bi sa da kallo, ba a dau lokaci ba sai
gashi ya dawo parlon with another Jacket, ya saka a kan rigar jikinsa yace
"Mu je" Ta sauke idonta ta dau Jacket din nasa, Kofar parlon ya nufa
ta bi bayansa har suka fita daga parlon, ya kulle kofar ya kalleta yace
"Na lura kina son so much perfume ke dai" Ta girgiza kai tace
"A'a ni ban sa ba yanzu" Yace "Ohk" A tare suke tafiya with
nobody saying anything, tun ba su kai ko ina ba taji tana jin sanyi sosai,
hakan yasa ta Ιan saci kallonsa sannan ta saka jacket din hannunta yace
"Ai na zata baza ki sa ba kina forming big gal" Kawai dai tayi
murmushi bata ce komai ba, tana jin kamshin turarensa da ya cikata na jikin
Jacket din, dai dai yake tafiya da ita to keep same pace with her, slowly suke
tafiyar with absolute silence har suka yi nisa away from home, Jay yayi
breaking silence din yace "Soon za a fara snow" Tace "In sha
Allah kafin nan mun gama Exams dinmu" Zai yi magana wayarsa ya fara vibrate
ya ciro a aljihunsa yana duba me kiransa, ta gefen ido ta kalli wayar tasa taga
Ajay, yayi silencing wayar ya mayar aljihunsa, ta tabe baki tace "Shi dole
sai ya dinga damunka da kira ne as if you are with his kidney?" Jay yayi
dariya yace "Kidney ai me sauki ne, cewa za ki yi kamar life dinsa na
wajena dai, a rana sai ya kirani sau ashirin in banyi hankali ba"
Khaleesat ta kyabe baki sai ga shi ya sake kiran wayar, Jay ya kara ciro wayar
yayi picking ya sa Hands-free yana tafiya yace "What again?" Daga
daya bangaren Ajay yace"I need ur laptop, zan duba references dinka, na
mance zan shiga schl gobe, i am outside with my frnd now" Jay yace
"Da laptop din na fita ai, kuma i am not coming back home anytime
soon" Ajay yace "Gidan wannan mara kunyan ka koma kenan? Wai are you
even okay Bruh? Me kake yi da wannan yarinyar da ya sa kake zama gidanta? Ko
iskanci ka fara ne? In ma iskancin zaka yi why with that little local brat
pls?" Jay that was trying not to laugh yace "Kai kar ka bata min rai
fa" Ajay yace "On a serious note idan baka daina zuwa gidan nan ba i
promise you am gonna report you back home kasan karamin aikina ne hakan
ko?" Jay yace "In ka fasa, kai duk takurani da kake da yan iskan
abokanka a can gida ban kai report ba sai ni da na bar maka gidan for peace to reign
shi ne zaka kai karata? To references din ma baza a nuna ba, go and sort ur
self out" Yana kai wa nan ya katse wayar ya mayar cikin aljihu, ita dai
Khaleesat bata kallesa ba kuma bata ce komai ba amma har cikin ranta take jin
Ajay bai mata ba, she doesn't like him
or anything concerning him, ta tsani mutum that is too pompous and proud of
himself, Jay yace "Baya karatu fa, in ma wani aiki ne sai dai kai kayi ya
gani sannan yayi nasa, har ma nasan yafi naka at the end" Khaleesat tace
"To me yasa har yanzu ba a koresa ba daga makarantar?" Dariya sosai
Jay yayi yana kallonta yace "Baya karatu doesn't mean he is dull Halysaah,
kinsan Genius? That is who Ajay is, he is naturally gifted, he graduated as one
of the best medical student during our degree program in this state and
masters, kuma kar kice wani karatu yake, mu ne dai sai mun yi karatun za mu
wuce" Yana murmushi ya kare maganar, Khaleesat ta wani kyabe baki kamar
bazata ce komai ba, sai kuma tace "To ai gwara kai karatun kayi ka wuce,
shi kuma banza kawai yake ci" Jay na dariya yace "Ai shi sa na bar
masa gidan cause idan na ci gaba da biyesa da abokansa wucewa zai yi ya bar ni,
su kansa abokan nasa ina tausaya masu biyesa da suke" Khaleesat tace
"Shi ne yasa kake Co-living?" Yace "Yeah, shekaranmu na karshe
kenan idan Allah ya yarda so i need much privacy to study very hard to earn my
PhD, in kana tare da Ajay ba wani abun arziki da zaka yi in dai bangaren karatu
ne, sannan baya barina inyi bacci sosai, nuisance ne shi fa, Ya
Subhanallah" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, sai kuma ta sauke idonta,
yace "Year nawa kike yanzu?" A hankali tace "Year 3" yace
"Kince Pharmacy ko?" Ta gyada masa kai, yace "Kin kusa gamawa
kema ai in sha Allah" ita dai tayi shiru bata ce komai ba suna ci gaba da
tafiya slowly, ita ce tayi breaking silence din after almost 10 mins da ya biyo
baya tace "You know him back home?" Jay ya kalleta yace "Wai
Ajay? Yeah he is my favorite, yanzu ma dai kin ga budurwa nake nema masa bashi
da mashinshiniya ko daya wallahi" Khaleesat tace "Ashe bazai taba
samu ba, ai he is way too rude and full of himself, wacece zata yarda ta auresa
in dai ba auren dole aka mata da shi ba, ko makala mata shi aka yi?" Jay
dai dariya kawai yake yana kallonta yace "Ya kai Saurayin ki?" Nan da
nan mood dinta ya canza, taki ce masa komai tana ci gaba da tafiyarta, yana
kallonta yace "Naga kin yi shiru ko compare and contrasting kike yi a
zuciyarki? Tell me pls ya kai saurayinki?" Without looking at him tace
"Kamar lokacin sallah yayi, and it's getting dark already" Yace
"Ke ina ruwanki da sallah tunda ba yi kike ba?" Khaleesat was
dumbfounded jin abinda yace, ta kasa kallonsa kuma taki basa amsa still walking
slowly, Roadside chair ta hango ta tafi ta zauna, ya karasa wajen yace "Ko
har kin gaji ne?" Tace "To da bazan gaji ba, muna ta tafiya for
almost an hour now" Yace "Akwai wani Eatry a area din nan, mu je sai
mu yi dinner before going back home, the eatry isn't far away from here"
Khaleesat tayi shiru, ta san Eatry din da yake magana don sun taΙa zuwa da
Abdul kuma abincin wajen shegen tsada ne da shi, yace "Let go" Yana
fadin haka ya juya ya fara tafiya, hakan ya sa ta mike ta bi bayansa, ya jira
har ta iso inda yake sannan suka ci gaba da tafiya a tare har suka isa Eatry
din, suna shiga ta kalli Jay that was grinning kamar yaga wanda ya sani a cikin
Eatry din, lkci daya ta hango Ajay that was sitted da wata baturiya a cikin
eatry din yana mata magana, ga abinci kala kala a gabanta, shi kuma ruwan gora
ne kawai a gabansa, Khaleesat ta dauke idonta speaking calmly tace "I
think zan tafi gida kawai, dama ba wani yunwa nake ji ba, i will order a Lyft
in koma gida" Jay ya riko gyalenta don har ta juya zata fita yace
"C'mon Halysaah, so kike ya kara raina ki, kina fita zai yi zaton tsoronsa
ne yasa kika kasa shigowa kika fita and he will be very happy, kawai kiyi fuska
ki tafi ki zauna" Khaleesat ta tsaya bayan ta Ιan yi nazarin abinda Jay
yace, kuma fa haka ne zai yi zaton tsoronsa take, hakan yasa ta karasa Jay na
biye da ita a baya ya jawo mata kujeran dake facing inda su Ajay ke zaune ta
zauna, Jay ma ya zauna sannan ya kalli direction din Ajay dake kallonsu babu
yabo babu fallasa, Jay ya daga masa hannu with smile all over his face alamar
Hi, Ajay ya dauke kai kamar bai taΙa saninsa ba a rayuwa, Jay ya daga kafadarsa
yana murmushi sannan ya dau menu dake saman table ya mika ma Khaleesat yace
"Duba abinda zaki ci" Ta amshi Menu din tana kallo, cikin few minutes
Jay ya saka masu order aka kawo masu abincin, duk da Khaleesat tana facing din
Ajay ko da wasa bata yarda ta kallesa ba, tayi kamar bata san da shi a Eatry
din ba, Jay kuwa cin abincinsa kawai yake with full concentration not minding
her in his front, lkci lkci Khaleesat ke kallonsa, ta lura he doesn't joke with
food and sleep for anything, dariya ma ita yake bata, ita kam a hankali take
cin abincin gabanta, ya daga kai ganin bata wani ci Crab patatoe Chips din
gabanta ba yace "Should i fetch some of urs?" Ta wani kallesa tace
"Do you have an extra stomach?"
Bai san sanda yayi dariya ba yace "I don't understand an extra
stomach?" Tana kallonsa calmly tace "Naga duk kai ka kusa cinye
abincin kan table din nan" Jay ya bude ido sosai yace "Har da sharri?
Me da me na ci a table din?" Ta tallabi chin dinta tana murmushi tana
kallonsa wanda har sai da dimples dinta ya lotsa, Mistakenly ta daga ido suka
hada ido da Ajay dake kallonsu babu yabo babu fallasa, nan da nan murmushin
dake fuskarta ya bace ta sha kunu, Jay bai ma san tana yi ba don tuni ya ci
gaba da cin abincinsa har ma ya diba na gabanta, Khaleesat ta kalli wayarta
dake vibrate kan table, sosai gabanta ya fadi ganin Abdul ne ke kiranta, Jay ya
daga kai ya kalleta yace "Ba kiran ki ake ba?" A hankali tace
"Na sani" Yace "Why are you not picking?" Tayi shiru, sai a
sannan ta tuna fa ashe ya kirata severally bata daga kiransa ba, Jay yace
"Ko de saurayinki ne?" Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, yace
"Ki daga mana kar kiyi laifi" Sauke idonta tayi ta daga kiran a
hankali ta kai kunne tare da sallama cikin sanyin murya.....
07087865788✍π»
[5/14, 5:45 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Read My Book
"HALYSAAH" on
ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6
✨✨ HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
17....
Daga daya bangaren Abdul yace "What is wrong with you
these days Khaleesat? Me yake damun ki?" Tunanin abinda zata ce masa ta
fara yi, tayi shiru gabanta na faduwa, ita ta ma rasa me yasa take Ζin daga
kiransa kwanan nan, kawai a zuciyarta take jin bata son waya da shi, Jay ya
daga kai ya kalleta jin tayi shiru ga waya Ζare a kunnenta, amsar wayar yayi ta
zaro ido tana kallonsa da mamaki with fear, ya sa wayar handsfree ya rage
volume sannan ya ajiye saman table ya ci gaba da cin abincinsa, a fusace Abdul
yace "Wai baki ji na ne, or is something wrong with you?" A hankali
Khaleesat tace "Ina jin ka mana, na mance wayar ne a gidansu Safiyyah, i
just got it now" Sounding so provoked yace "Ni zaki raina ma hankali?
Ke ce zaki bar wayarki tun jiya gidansu Safiyyah?" Khaleesat ta wani kyabe
baki ta kauda kai tace "Haka dai kawai bazan ki daga kiranka ba, me yasa
baza ka min uxuri ba?" Abdul yace "Wait Khaleesat, where are you
getting ur liver from these days? Who is ur vendor? Yaushe kika fara samun
courage din mayar min da magana?" Khaleesat tace "Toh ni yanzu me
nayi? Nace maka wayar baya wajena and u are trying to create an issue out of
nothing, Nan da few weeks fa za mu fara jarabawa, you are only adding more
pressure to the one i am already in, ka dinga considering dina mana pls"
Jay ya Ιan daga kai ya kalleta, sai kuma yayi murmushi ya dau ruwan gora ya
bude yana sha, Abdul yace "A kanki aka fara jarabawa? What is the big deal
ah jarabawan da zaki yi? Ko dai Safiyyah ce ke dora ki akan abinda bazai fisshe
ki ba? Safiyyah ce take zuga ki har kika fara samun courage din mayar min da
magana ko? Switch to video call now" Khaleesat taji gabanta ya fadi sosai,
Jay dai murmushi kawai yake, a hankali Khaleesat tace "Ohk i will, amma
kayi hakuri let me dress up first..." A mugun fusace yace "Ki bar
shi" Yana fadin haka ya katse wayar, Khaleesat dai tayi shiru tana kallon
wayar nata, Jay yace "Ki gama cin abinda zaki ci mu tafi Halysaah, it's
pass magrib now zan je inyi sallah" Khaleesat ta daga idanuwanta tana
kallonsa, yace "Ko ayi maki takeaway din abincin?" Ta sauke idonta
bayan sun hada ido da Ajay da ya mike daga inda yake zaune, Jay ya juya ya Ιan
kalli Ajay yace "Hey man, ka hada har nawa bills din" Ajay yaki
kallon direction dinsa kai kace bai san sa ba ma, Jay ya kira daya daga
ma'aikatan wajen ta karaso, ya sa tayi masu packaging abincin da Khaleesat bata
ci ba, ita dai Khaleesat har sannan taki cewa komai kana ganinta kasan she is a
bit disturb, Jay ya bi Ajay da kallo har ya fita daga Eatry din da baturiyar da
suke tare, shi bai ma taΙa ganinta ba sai ranan duk kwashe kwashen Ajay ne,
bayan ma'aikaciyar wajen ta gama packaging abincin, yana kallonta ya tambayeta
bill dinsa, nan ta sanar masa Ajay ya hada har nasu ya biya, Khaleesat ta daga
kai ta kalli waitress din jin abinda tace, Jay yace "Ok then" Mikewa
yayi ya dau ledan abincin Halysaah yana kallonta, ta tashi ta dau wayarta, yana
gaba tana biye da shi suka fita daga wajen cin abincin, Lyft din da Jay yayi
masu order har ya iso, ya bude mata back seat yana jiran ta shiga, Khaleesat
felt somehow hakan da yayi, don duk fitar da suke yi da Abdul bai taΙa mata
haka ba, yawanci ma shi yake fara shiga sannan ta shiga, bayan ta shiga motar
Housemate dinta ma ya shiga, sai da suka kusa gida wayarta ya fara vibrate, ta
kasa duba me kiranta sanin kila bazai wuce Abdul ba, Jay dake danna wayarsa ya
kalleta yace "Kiran ki ake ai" Bata ce masa komai ba ta kalli screen
din wayar sai taga Safiyyah ce ke kiranta, ta daga da sauri ta kai kunne tace
"Hello Sophie" Safiyyah tace "Am at the door, nayi knocking
shiru" Khaleesat ta Ιan saci kallon Jay, sai kuma a hankali tace "Ohk
na Ιan fita ne amma ina hanya yanzu" Da mamaki Safiyyah tace "Kin
fita? Ban gane kin fita ba, Ina kika je?" Khaleesat tayi shiru, Safiyyah
tace "Ko da Housemate din ki?" Khaleesat tace "Um" Safiyyah
tace "Hmmm i see, to in dai baku kusa dawowa ba bari inyi tafiyata
kawai" Da sauri Khaleesat tace "Aa ki jirani am on my way" Tana
fadin haka ta katse wayar, ajiyar zuciya ta sauke don tayi tunanin Abdul ne ya
kira Safiyyah shine ta kirata, after some minutes suka isa gida, ta bude side
dinta ta sauka daga Uber din, Jay ma ya sauka, Apartment dinsu ta nufa, ta Ιan
rage pace dinta ganin kamar motar Mustapha a vicinity din, shi dai Housemate
dinta na biye da ita a baya, sai ga Safiyyah ta fito daga motar Mustapha, da
murmushi fuskarta ta nufesu ta gaida Jay, ya tsaya ya amsa mata sannan ya wuce
cikin gida, Safiyyah ta kalli Khaleesat tace "Toh ki gaida ya Mustapha,
dama girki na tsaya maki na zata har yanzu bakya iya tashi" Khaleesat ta
kirkiro murmushi tace "Ohk bari in gaishesa" Zagawa tayi zuwa side
din Mustapha taga yanda ya bi Jay da kallo har Jay ya shiga cikin gida,
gaishesa tayi kanta a kasa, ya kalleta yace "Who is he Khaleesat?" A
hankali Khaleesat tace "Housemate dina ne" Mustapha ya kalli Safiyyah
yace "There was a time da kika ce min mace ce Housemate dinta?"
Safiyyah tace "Eh wallahi the lady packed out shine shi ya shigo, ai bai
wani dade sosai da dawowa apartment din ba" Mustapha ya kalli Khaleesat
yace "Me yasa zaki dinga zama gida daya da namiji da sunan Co-living
Khaleesat, why not come stay together with ur frnd Safiyyah in my house?"
Safiyyah ta wani kallesa, sai kuma ta kyabe baki, sai kace ya gama kwatar mata
'yan ci gun shegiyar matarsa balle ya kwatar ma ita da kawarta, ita dai
Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba tana wasa da veil dinta, Mustapha yace
"Wani yare ne Housemate din naki?" Caraf Safiyyah tayi tace "He
is from Tanzania, yaren can kasar yake yi, beside shi baya ma wani zama a gidan
once a while yake zuwa yayi karatu kawai" Mustapha ya wani kalleta yace
"Ke na tambaya?" Gefe ta koma bata sake cewa komai ba, Mustapha yace
"Daga ina ku ke da daddaren nan Khaleesat?" Khaleesat tace "I
was sick tun da safe shine muka je ya siya min abinci yanzu" Mustapha dai
sai kallonta yake, after some seconds yace "I will talk to my wife, sai ki
dawo nan gidana kiyi zamanki tare da Safiyyah har ku gama Exams, i think the
exam is by the corner...." Khaleesat tayi murmushi kawai bata basa amsa
ba, Safiyyah tace "Mu je in kai maki abincin da na kawo maki ciki"
Bude bayan motar tayi ta ciro abincin, Khaleesat tayi ma Mustapha sai da safe
sannan suka wuce apartment dinta tare da Safiyyah, nan parlor Safiyyah ta ajiye
abincin tayi kasa da murya tana washe baki tace "Ban gane wannan fitar da
ku ke yi da Housemate dinki ba Khaleesat? Ina ku ka je?" Khaleesat tace
"Abinci fa muka je ya siya min, kuma ba wai lapiyata lau muka je ya siya
min abincin ba" Khaleesat ta ajiye ledan abincin hannunta ta zauna gefen
kujera tare da sauke boyayyen ajiyar zuciya, Safiyyah dake washe baki tana ma
Khaleesat wani kallo tace "To ya aka yi yasan baki da lafiya, kuma how did
he know what was wrong with you?" Khaleesat tace "Kinga Sophie wnn ba
shine damuwata ba yanzu, muna gidan cin abinci Abdul ya kirani" Safiyyah
ta wani yatsine fuska tace "So? Da ya kiraki sai aka yi yaya?" Cike
da damuwa Khaleesat ta bata labarin yanda aka yi da kuma call dinsa da ta ki
picking tun jiya, Safiyyah tace "Haba, to ko ke fa da kika fara kokarin
kwatar ma kanki 'yan ci, ni sai nake ga kamar Housemate din nan naki ne ke baki
Liver kike wasu abubuwa yanzu, banda haka yaushe har kika yi bakin gaya ma
Abdul magana haka" Tana dariya ta kare maganar, Khaleesat ta dinga
hararanta ganin ta ma maida abun joke, Safiyyah tace "In ni ce ke ma bazan
kirasa ba wallahi, gwara kawai komai ya ruguje kowa ya huta" Khaleesat
tace "Kin manta abinda yayi kwanaki kawai muka gansa kamar an jefosa
Sophie? Kinsan yanzun ma ba karamin aikinsa bane sai ya iya kamo hanya ya
zo" Khaleesat ta dafe kanta tsabar she is confuse, Safiyyah tayi shiru,
can kuma ta kyabe baki tace "Kuma haka ne ba kai ne da shi ba sai ya iya
kamo hanya tunda ba su dau kudi bakin komai ba, kawai anjima ki kirasa sai ki
kisa abinda zaki ce masa da zai gamsar da shi, kuma kina iya cewa baki da
lafiya gantalallen ya kamo hanya, ni dama ya tafka wani tsiya America su kwace
visan sa kowa ya huta" Duk da damuwar da Khaleesat ke ciki sai da tayi
dariya, Safiyyah tace "Allah kuwa, ban ki ba ya zo ya maki hauka da kaina
zan kira masa 911 wallahi" Khaleesat dai tayi murmushin karfin hali kawai,
wayar Safiyyah ne ya fara ring ta duba taga Mustapha ke kiranta, turo baki tayi
tace wannan mutumi yana takura rayuwata a kasar nan, wai daga cewa zan kawo
maki abinci ya zata yawo zani shine fa ya biyoni, kema baki ji ba wai ki dawo
gidansa da zama, salon wataran matar ta saka mana guba a abinci mu ci mu mutu
gaba daya, yanzu haka fa ko ga maciji bama yi da ita, Ιan fitar nan da yayi da
ni muna nan dake sai ya zamar masa matsala, tana can ta cika tayi fam tana
jiransa, ko a jikina kuwa, sai na ma lallabasa ya kai ni ya siya min ice-cream
ta yanda zata ga na dawo rike da leda" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya
bata ce komai ba, Safiyyah ta mike tace "Bari in je, sai mun hadu Monday
in sha Allah" Khaleesat ta rakata bakin kofa a hankali tace "Thank
you Safiyyah" Safiyyah tace "No thanks kawata, ki ce ma Housemate
dinki na tafi" Khaleesat ta gyada mata kai, a haka Safiyyah ta fita daga
gidan, Khaleesat ta kullo kofar a hankali, abincin da Safiyyah ta kawo mata ta
dauka ta kai fridge da wanda Housemate dinta ya sa ayi mata takeaway. Khaleesat
ta fito wanka kenan taji Housemate dinta na knocking kofarta, ta dau Hijab
dinta ta saka sannan ta nufi kofar ta bude tana kallonsa, yana rike da laptop
dinsa yace "Good night Halysaah, i am sleepy" Khaleesat tace "To
sai da safe, thank you for the dinner" Yace "No thanks.... kin kira
BF din naki?" Khaleesat taki basa amsa, yace "Amma bari in tambayeki,
a ina kika hadu da gayen nan ne? Don't know ko na taΙa tambayarki
kwanaki...." Khaleesat ta jingina da kofa without looking at him tace
"Back home" Yana gyada kai yace "I see, ni at first na zata you
are not Nigerian, was thinking you are from Niger or Chad, probably Shuwa
Arab" Khaleesat ta dinga kallonsa, bata san sanda tace "Why?"
Yace "Na ganki kamar Buzuwa" Khaleesat ta sauke idonta bata basa amsa
ba, yace "Ok, i will be on my way, good night" Daga haka ya juya ya
bar wajen, a hankali ta sauke idonta sannan ta kulle dakinta ta jingina jikin
kofar, she stood there for almost 5 mins kafin ta karasa cikin dakin ta cire
hijab din jikinta ta ciro sleeping dress dinta ta saka, sanitary pad dinta dake
gaban dressing mirror ta dinga kallo, sai kuma ta dauke daga wajen, sai da ta
kwanta sannan tayi dialing number Abdul gabanta na faduwa, har ya katse bai
daga ba dama tasan ba lallai ya daga ba, ta sake kiransa nan ma bai daga ba, ta
bude WhatsApp tayi masa magana ta nan, reply yayi mata yace "I don't have
ur time so do not border me" tabe baki tayi ta ajiye wayar ta kashe wutan
dakin sannan tayi kwanciyar ta lumshe ido, nan da nan bacci ya dauketa.
Washegari bayan Khaleesat ta gama azkar din da take yi, ta jawo wayarta a
hankali, tunda ta tashi jikinta yake a sanyaye don mafarki tayi Abdul ya zo
kamar yanda ya zo wancan lkcn still kuma ya sake haduwa da Housemate dinta a
gidan, ba karamin daga mata hankali mafarkin nan yayi ba, WhatsApp dinta ta
bude bayan tayi deciding zata masa message din ban hakuri duk da bata saka ran
reply dinsa ba, cause it won't be funny if her dream comes true, tana shiga
WhatsApp din ta ga ya turo mata hotuna kusan biyar tun 3 hours ago, bude
message din tayi zuciyarta na bugawa don bata san hotunan menene ba, nan taga
har da message yayi mata kafin yayi sending hotunan, ta fara downloading
hotunan at the same tana duba message din da ya rubuto mata kamar haka "So
now, kina kokarin nuna min cewa i made the mistake of letting you go to America
to study right? Kin mance wacece ke ko? kin mance daga inda kika fito, then
that is so foolish and stupid of you Khaleesat, amma ina me tabbatar maki idan
har kika ci gaba da daukata for granted kamar yanda kike yi kwanan nan sai na
sa kinyi da kin sani wallahi" Lkci daya Hawaye ya cika idon Khaleesat, ta
sauke idanuwanta kan hotunan da ya turo mata, daya hoto ne da shi yayi mata a
bakin kofar dakin Ummanta, yana zaune kan tabarma ta duka gabansa zata ajiye
masa ruwa a Cup shine ya dauketa hoton, shekaru hudu da suka wuce kenan, she
look so so young and meek a hoton, hoto na biyu kuma tana wajen debo ruwa a nan
unguwansu ya zo ranan ya ganta a wajen, ita bata ma san yayi mata hoton ba ga
zaninta duk a jike, hoto na uku kuma tana baΖin murhu a tsakar gidansu tana
juye alalan siyarwan Ummanta a Cooler shi kuma ya zo gidan ranan, duk bata san
ya mata hotunan nan ba sai yau da ya turo mata ta gani, hoto na hudu kuma ranan
da ya kai ta zata zana Jamb ne, jamb din da bata ma yi amfani da shi ba daga
karshe, sai kuma hoton karshe na ranan da zai kawota USA for the first time,
looking at all the pictures da kuma looking at her now zaka ga banbanci me
tazara sosai, infact the difference is very obvious don a yanzu she looks more
beautiful, matured, nourished and well taken care of, yanzu skin dinta har wani
glowing yake, in ma ba ka santa ba bazaka taba cewa ita ce a hotunan ba, bata
san sanda ta fashe da kuka ba ta hade kanta da pillow tana kuka sosai, but like
seriously Abdul bai yi deserving haka daga gareta ba, but did she also deserve
irin abubuwan da yake mata? Kuma tun asali haka yake mata, Kuka sosai tayi babu
me rarrashinta, bata ma san me take ji a zuciyarta ba a lkcn, she cried
profusely for almost 30 mins, daga karshe tayi karfin halin mikewa zaune ta dau
wayarta, she don't even know where to start from, Voice note ta fara masa
muryarta na rawa trying to tell him she is sorry, amma bata kai ko ina a basa
hakurin ba ta fashe da kuka sosai, cikin kuka ta ci gaba da basa hakurin, sai
da tayi masa Voice note uku sannan ta ajiye wayar still crying....
07087865788✍π»
[5/15, 3:23 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Read My Book
"HALYSAAH" on
ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6
✨✨ HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
18.....
Wajen karfe goma na safe Khaleesat na kwance dakinta idonta
rufe duk da ba bacci take ba, ji tayi ana kwankwasa kofa, kamar bazata iya
tashi ba daga karshe dai ta mike ta sauka daga kan gadon ta dau hijab dinta ta
saka, tana tafiya a hankali ta fito parlor, ta tagar parlon ta duba ta ga
Housemate dinta ne, ta karasa ta bude kofar, Yace "Sorry na tashe ki kina
bacci, i forgot the key at home" Ita dai bata yarda sun hada ido ba a
hankali tace "Ina kwana?" Yace "Lafiya lau, how are you feeling
now?" Ta juya going back to the parlor tace "Alhamdulillah" Ya
bi ta da kallo sannan ya shiga parlorn, dakinta ya ga zata koma yace
"Halysaah" Ta tsaya, after few seconds ta juyo but couldn't let her
eyes contact his, shi dai kallonta kawai yake, ya karasa inda take tsaye yace
"What happened?" Girgiza masa kai kawai tayi, lkci daya hawaye ya
fara sauka idonta, ya dauke kai na 'yan dakiku kafin ya sake juyowa ya nuna
mata kujera yace "Sit" Komawa tayi ta zauna, ya zauna shima yana
kallonta yace "Tell me what's wrong" Ta sunkuyar da kanta, yace
"Are you sick?" Ta girgiza masa kai, yace "Wannan saurayin naki
ko?" Ta kasa basa amsa wasu hawayen na sauka idonta, sai kuma ta fashe
masa da kuka, mikewa yayi yace "Waye ya hadaki da wannan mutumi ne? Why did
u allow him know ur weak point? Why are you always crying because of him? Is he
happy making u sad now and then?" Khaleesat dai kuka take a hankali, yayi
shiru for almost 2 mins yana jin ransa na baci, can ya kalleta yace "Kee
in zaki yi facing study dinki is better you do so, give that ur so called
boyfriend space, ur exam is around the corner" Sai a sannan Khaleesat ta
daga idanuwanta da suka yi ja ta kallesa, sae kuma ya kwantar da murya yace
"Kiyi hakuri Housemate, zan dinga sa ki a addu'ata Allah ya maki mafita, i
can't just intrude cause ban san sanda ku ka san juna da shi ba, ban kuma san
me ya hada ku ba, i will only include you to my prayers i promise
Halysaah" Khaleesat ta gyada masa kai da kyar, sannan ta mike cikin sanyin
murya tace "Nagode" Daga haka ta juya ta nufi dakinta, Jay ya koma ya
zauna yana mamakin irin son da take ma gayen da har ta kasa rabuwa da shi duk
da musguna mata da yake yi a soyayya, bata da aiki sae yi masa kuka, da
kanwarsa ce daga ita har saurayin zai hada ya ci ubansu, kuma ya rabata da shi
na har abada, tausayinta yaji har cikin ransa don bai san wani irin so bane
wannan take masa da har take iya tolerating abubuwan da yake mata, and ya lura
the guy is taking advantage of this to hurt her always, mikewa yayi ya tafi
kitchen kamar yanda ya zarga yaga alamar bata yi breakfast ba har sannan don
kitchen din ma bata shigo ba, fridge ya bude ganin abincin da Safiyyah ta kawo
mata jiya yayi mata microwaving dinsa ya hada mata shayi sannan ya kai mata
daki, sai da yayi knocking ta amsa sannan ya shiga dakin, tun da ya shigo
Khaleesat ke kallonsa har ya ajiye mata abincin, ta sauke idonta a hankali tace
"Nagode" kai kawai ya gyada mata, sai kuma ta bi sa da kallo har ya
fita daga dakin, karfe sha biyu saura Khaleesat ta jawo wayarta jin yana vibrate,
tana duba screen din taga Abdul ke kiranta, ta sauke idonta kasa tayi picking
call din ta kai kunne amma bata ce komai ba, yace "Khaleesah...." ta
kasa amsawa hawaye ya fara sauka idonta, yace "Can you hear me?" Da
kyar tace "Um" Yace "How was you night" tana share hawayen
dake sauka idonta tace "Alhamdulillah" Tun daga wannan rana Khaleesat
ta fara avoiding duk wani abu da zai hadasu fada da Abdul, she want just
nothing but peace with him for her sanity, bin sa kawai take a yanda yake so
for peace to keep reigning, in ma bala'i yake mata a waya zata yi shiru ta gama
saurarensa sannan daga karshe ta basa hakuri kamar yanda take yi masa da, ranan
da bai kirata ba kuwa ita zata kirasa, hakan kuma da tayi ya sa ta samu
kwanciyar hankali har take concentrating a karatun ta, amma fa in ta tuna irin
kulawar da Housemate dinta ke bata always wanting to make sure she is fine sai
taji she isn't lucky having Abdul, ana haka har exams dinsu ya rage some days,
ranan Wednesday tana kitchen da safe taji ana kwankwasa kofa, ta fito daga
kitchen din don dama she is expecting Safiyyah, ta bude mata kofa, Safiyyah ta
shigo tace "Ai na zata zan zo in tarar baki tashi ba?" Khaleesat tayi
kasa da murya tace "Aa i am in the kitchen" Safiyyah tace "Ohk,
why are you lowering ur voice?" Still
Whispering Khaleesat tace "My Housemate is sleeping" Safiyyah
ta sake baki tana kallonta, sai kuma ta rike haΙa tace "Ikon Allah gadinsa
kike kenan?" Khaleesat ta hade rai tace "Ban gane gadinsa ba, daxu fa
ya zo, and dama bacci yake zuwa yayi da safe don yace min baya bacci da
daddare" Safiyyah couldn't stop smiling tana kallon Khaleesat, Khaleesat
ta wani harareta ta juya ta koma kitchen, Safiyyah ta karasa ta zauna kan
kujera har sannan bata daina murmushi ba, sai ga Khaleesat ta fito daga kitchen,
still tana magana kasa kasa tace "Ko dai kawai mu je waje ki min gyaran
gashin, kinga Hand dryer yana Ζara in ana using dinsa, it's noisy"
Safiyyah ta buda baki tace "Ikon Allah, to akwai socket ne a wajen?"
Khaleesat tace "Zan sa Extension a kitchen sai mu fito da shi ta window ai
zai yi, kuma akwai tap a garden din sai mu wanke gashin ma a nan" Safiyyah
dai murmushi kawai take bata ce mata komai ba, yanda Khaleesat tace haka din
tayi duk don kar karan Hand dryer ya tada Housemate dinta or any of their noise
kamar yanda tace, abinda bata sani ba ashe ba bacci yake ba aiki yake yi a
Laptop dinsa a daki, bayan sun isa karamin Garden din dake bayan kitchen
Khaleesat ta ajiye duk shampoo da Conditioner din hannunta sannan ta bude
gashinta, Safiyyah na kallon gashin tace "Tab, Allah sa Shampoo din da
Conditioner su isa dai" Khaleesat ta wani hade rai tace "Ban gane ba,
saboda bargo za ki wanke?" Safiyyah tayi dariya tace "To meye
banbancin wannan da bargon Khaleesat? Babancinsa kawai wannan akan ki yake, ni
naga ma kamar karuwa gashin yake Tabarakallah Maa sha Allah" Khaleesat
tace "Ba abinda ya karu yana nan yanda yake" A haka Safiyyah ta fara
wanke mata gashin, suka dau time sosai bayan ta gama wankewa ta fara busar mata
shi da Dryer, Jay ya shigo kitchen zai yi making Coffee drink ya dinga kallonsu
ta window din kitchen, he was confuse seeing her hair, is all that Hair or
what? long, full and black, kawai yaji bai yarda gashinta bane, ya juya ya fara
yin abinda ya kawo sa kitchen din, Khaleesat ta kasa kunne sosai jin kamar
sound a kitchen, ai ko ta jawo mayafinta da sauri ta rufe kanta bayan ta
hangosa a kitchen din ya juya masu baya, Safiyyah dai sai kallonta take,
Khaleesat ta mike ta isa kusa da window din kitchen din tana kallonsa tace
"You woke up early today" Ya juya ya kalleta yace "This is to
12" Khaleesat ta zaro ido don bata san lkci ya wuce haka ba, ashe sun bata
lkci sosai wajen wanke gashinta, yace "Me kike yi a nan?" Tace
"I am together with my frnd Safiyyah" Ya ci gaba da abinda yake yi
yace "Ohk my regards" Juyawa tayi ta koma gun Safiyyah, bayan Drying
har Stretching gashin sai da Safiyyah tayi mata, Safiyyah tace "You know
what Khaleesat, anjima ki zo can gida sai in maki Kalaba din, i think i can
feel my period, i need to go home" Khaleesat ta juya ta kalleta tace
"Da gaske?" Safiyyah tace "Wallahi, gwara in tafi gida kar ya
zo" Khaleesat tace "Ohk, amma ki bari in dafa mana indomie ki ci
tukun ki tafi" Safiyyah tace "Ke bazan ci ba, bari in tafi kawai i am
uncomfortable" A hankali Khaleesat tace "To shikenan" Safiyyah
tace "Sannan pls Khaleesat nace ma Ya Musty ran sunday zaki zo gidan tunda
kinga Monday za mu fara exams, ko 2 days ne sai kiyi kafin matarsa ta fito da
baΖin halinta gaba daya, kin dai ga bazai ce bamu ji maganarsa ba yace ki dawo
gidansa baki dawo ba, even if it's just 2 days come and spend in his house
pls" Khaleesat tace "Wallahi ba wai bana son zuwa bane ko kuma ban ji
maganarsa ba Safiyyah, bana son issue ne da matarsa, i don't want any
problem" Safiyyah tace "I know, shi yasa nace ko kwana biyu ne kawai
ki zo kiyi ai bazai ce baki zo ba, ranan Sunday sai ki debi kayanki kala uku ki
taho kawai, probably ma daga karshe nima nan gidan zan dawo mu yi karatu tare,
ni nasan ba lallai ma kiyi kwana biyun ba matarsa bata kirkiro wata matsala ba,
so just chill ba zama zaki yi a gidan ba Likewise myself" Khaleesat tayi
shiru kamar me nazari, sau biyu Mustaphan ke mata magana da kansa ta WhatsApp
akan dawowar da yace tayi gidansa, iyaka sai tace masa in sha Allah tana nan
zuwa before exam, Safiyyah ma tayi mata magana yafi a kirga, ko don Safiyyah
zata daure kawai taje tayi kwana biyun a gidan, let it not be as if bata jin
magana, a haka ta raka Safiyyah bayan tayi order din Uber da zai maida ta gida,
Khaleesat na dawowa parlor taga Housemate dinta ya shirya zai fita, yana
kallonta yace "Wai duk gashinki ne wannan ko dai Ζarin gashi kike yi
Halysaah?" Ta daga idanuwanta ta kallesa bayan tayi realizing ashe ya
ganta kenan daxu, sauke idonta tayi tace "Ζarin gashi kuma?" Yace
"Naki ne? Ai na gansa kamar ba naki bane, sorry" Ζan murmushi kawai
tayi without giving him an answer, can yace "Wait, amma ba ki jin zafi na
damun ki? I mean baya takura ki gashin? isn't it too much?" Tace
"How?" Sounding so serious yace "Ki rage mana, just cut half of
it off kema ki huta, sai kiyi azumi uku, wannan ai burden ne Halysaah, it's too
much, ji fa sai da kawarki ta zo taya ki wankewa don kema baza ki iya wankesa
da kanki ba, all this while ni na zata irin wannan acuci mazan da ku ke yi ne
kike daurawa a kanki, i never knew gashin ki ne" Khaleesat tayi murmushi
ba tare da tasan tayi hakan ba, can ta kallesa calmly tace "But i am not
complaining, kuma ai ba nauyi gashin yake min a kai ba" Ya wara ido yace
"Ohh! my bad, haka ne kuma fa, hope you are reading so well for ur exam,
kinga in few days time zaku fara, i think monday ko?" Ta gyada masa kai,
yace "Wishing you the very best of luck Halysaah" a hankali tace
"Thank you" Yace "See ya later" Ta gyada masa kai, daga
haka ya juya ya nufi kofa ya fita daga parlon.... Da yamma Khaleesat ta gama
shiryawa bayan Safiyyah ta isheta da kira wai taje ta mata kitson, Khaleesat ta
dau handbag dinta da mukullin gida bayan Uber din da tayi order ya iso sannan
ta fita daga gidan ta kulle, tana hanya kiran Safiyyah ya shigo wayarta, ta
daga tace "Ina hanya fa" Safiyyah tace "Allah in baki zo ba sai
dai gashinki yayi ta zama haka bani da lokacin maki wani kalaba kuma idan aka
fara jarabawa" Khaleesat dai tayi murmushi, tasan kawai Safiyyah so take
ta je gidan, karfe hudu da yan mintuna ta isa gidan ta sauka Uber sannan tana
tafiya a hankali ta nufi apartment din, tsayawa tayi bakin kofa ta danna bell,
lkci daya aka bude kofar, sai da gaban Khaleesat ya fadi ganin Surayya ce ta
bude mata kofa, ta sauke idonta tace "Ina yini?" A takaice Surayya
tace "Wa kike nema?" Khaleesat ta daga kai ta kalleta tace
"Wajen Safiyyah na zo" Bluntly Surayya tace "To bata nan, sai ki
juya ki koma inda kika fito" Khaleesat was just looking at her babu ko
kiftawa, sai ga Safiyyah ta fito daga daki fuuu, tana huci tace "Wajenta
kika zo da zaki tsaya sauraronta baki bangajeta ba kinyi shigowarki?"
Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah, wato ta bangaje matar gida ta
shigo tsabar neman jifa'i, Surayya ta juya a fusace tana kallon Safiyyah tace
"Tunda gidan na ubanta ne ko naki uban sai ta shigo mu ga" Safiyyah
tayi cilli da wayar hannunta ta fige dankwalin kanta tace "Wallahi kar ki
ga na raga maki daxu saboda yaya, to yanzu baya nan cin kaza kazanki zanyi
la'ada waje" Khaleesat was shock, ta kasa rufe baki tana kallonsu, Surayya
ta nufi Safiyyah tana kunduma mata zagi kamar dai yanda tayi mata few hours ago
a gaban cousin brother dinta, instead sai cousin din ya dinga ba Safiyyah
hakuri without taking any action, dama Safiyyah a wuya take, sbda bakin ciki ne
ma yasa ta dinga kiran Khaleesat ta zo gidan, Khaleesat ta zaro ido ganin yanda
Safiyyah ta finciko Surayya cikin zafin nama, ba ayi wata wata ba suka fara
tikar dambe a wajen, Khaleesat ta karasa ciki da sauri tace "Innalillahi
wa inna ilaihi raji'un, meye haka kuke yi Safiyyah? Don Allah ku bari"
Yaron Surayya dake kan kujera sai tsala ihu yake, Khaleesat tayi kokarin rabasu
taga an cillar da ita gefe har sai da ta kusa faduwa, bata sake gigin zuwa kusa
da su ba, ta bude wayarta da sauri ta fara neman number Mustapha, tana kokarin
kiransa taga Surayya na harin fixgo wani flower vase zata buga ma Safiyyah a
kai, hakan yasa Khaleesat ta tafi da sauri ta dauke Vase din daga inda yake,
Safiyyah tayi using opportunity din ta fixge vase din a hannun Khaleesat ta
maka ma Surayya a goshi, sai ga jini kuma hakan bai sa sun fasa damben da suke
ba, ko da Khaleesat ta kira Mustapha ashe yana hanyar dawowa, cikin few minutes
sai gashi ya shigo gidan, sai shi ne ya rabasu bayan sun yi ma juna laga laga,
Surayya bata daddara ba tayi kukan kura tayo kan Khaleesat zata cafkota tana
cewa "Kika bata Vase ta buga min, wallahi kema sai na ci kaza kazan
ki" A nan ne Mustapha ya sauke mata mari ya fincikota yace "Ko kin
fara hauka ne Surayya? Me kike son mayar da ni a kasar nan ne?" Ita dai
Khaleesat ta tsorata sosai, Safiyyah na huci tace "Shegiya bayerabiyar
banza kawai jaka jahila..." Bata rufe baki ba ita ma Mustapha ya kai hannu
zai gaura mata mari ta kauce da sauri tana harare harare tana huci, Surayya
dake kuka wiwi ta figi Ιan ta zuwa sama tana cewa "Wallahi sai dai ka zaba
ko ni ko Safiyyah a gidan nan yau, in ko ba haka ba ni zan bar maku gidan kayi
zaman auren da ita" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya ko ba komai dai ta
fasa mata kai hankalinta ya kwanta ta kuma ji dadi, Mustapha ya zauna saman
kujera ya dafe kai, juyawa Khaleesat tayi sum sum ta fita daga parlon wishing
dama bata zo gidan ba kilan da haka bai faru ba, da tasan bala'in da za ayi
kenan babu abinda zai fara fitowa da ita daga gida, Safiyyah ta figi dankwalinta
zata bi ta, Mustapha ya mata tsawa yace "Kar ki kuskura ki fita daga gidan
nan" Safiyyah ta fashe da kuka tana bubbuga kafa tace "Ni wallahi
yaya na gaji, na gaji kuma haka, na gajiiii, dubi cin mutuncin da matarka ta
min daxu kace in kyaleta, yanzu kuma daga kawata ta zo wajena in mata kitso
shikenan sai ta fara kunduma mana zagi ta kamani da dambe??" Yace
"Wuce dakin ki nace" Ita dai Khaleesat tuni ta kara gaba ta bar
gidan. That same day wajen karfe biyar da rabi sai ga Safiyyah ta zo gidan
Khaleesat, Khaleesat ta zauna gefenta bayan sun shigo parlor tana kallonta tace
"Ban ji dadin abinda ya faru ba yau Sophie, da na sani da ban je gidan ba
ma wallahi" Safiyyah tace "Ai abun duniya ne ya dameni kamar in
hadiye zuciya shi sa nayi ta kiranki ki zo daxu, wai fa bayan na gama yi maki
gyaran gashi na koma gida matar nan kamar jirana take ta kama zagina ta uwa ta
uba a gaban mijinta wai don me zan zubar mata da sauran miyarta dake kitchen,
kuma fa kar kice da miya a tukunyar Khaleesat, wallahi ba komai ciki sai wani
guntun miya da yayi tsami sai bugawa yake, ni kuma na wanke na dafa indomie na
ci kafin in taho nan daxu in maki gyaran gashi, Ya Mustapha ya hanani cewa
komai ya bani hakuri na wuce daki, a banza tunda dai shi ma har uwayensa ta
zaga, shine bata daddara ba da kika zo zata sake hadamu ta zage ga yan iska sai
muyi shiru muna kallonta, ni wallahi so nayi ace ma na cire mata hakora biyu ta
dawo wawulo, amma dai a juri zuwa rafi wallahi sai na mata illar gaske kafin in
gama karatu a kasar nan, dama tun 3 weeks ago da muka zo muka kawo maki abinci
da ni da Y Mustapha ta kara kullatata ta kara tsanata tunda har yau tayi
tunanin da akwai wani abu tsakaninki da Mustapha, ko ga maciji fa bama yi da
ita a gidan" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta kamo hannunta tace
"Ki dai dinga hakuri plss Sophie wataran sai labari, da ni ce ke ma
wallahi bazan dinga biyeta ba a gidan nan" Safiyyah tace "To ai ba
kowa ke da matattciyar zuciyar da kare ya lashe irin taki ba, amma wallahi tayi
kadan in ki biye mata, tana ce min kule zan ce mata casss don ubanta, an gaya
mata ita ta isa ta shiga tsakanina da Mustapha? Cousin dina ne fa, Uwarsa ce ta
sha nono ta bar ma uwata, Babansa kuwa Cousin din babana ne halaq malaq, ina ga
bai taΙa zaunar da ita ya mata bayanin nan dalla dalla bane, kuma ya ci sa'ar
bana kai karar abinda matsiyaciyar matarsa ke yi min gida, don wallahi da tuni
an dau mataki, amma dai bari mu yi hutu in koma Nigeria" Khaleesat ta
sauke ajiyar zuciya tace "Zancen gaskiya ke ma fa kina da naki Safiyyah,
babu ta yanda za ayi kina zaune da mata ko Ιan wanke wanken nan da shara baza
ki ke taya ta ba a gidan, Abinda fa idan an mana mun san baza mu ji dadi ba to
kar mu yi ma wani, she is also human, kuma at times bacin rai ne ke triggering
wani mugun halin mutum, kece kika yi triggering din halinta a gidan, babu ta
yanda zaki ji dadi wataran kanwar mijinki ta zo gidanki ta zauna bata taya ki
aikin komai sai dai in kinyi girki ta deba ta ci ta ajiye maki plate, ki duba
wannan lamarin fa, mu mata muna da son kanmu wani lkcn..." Safiyyah ta
dakatar da ita tace "Ohh wato goyon bayanta ma kike kenan Khaleesah? you
are trying to say duk abinda take min yayi dai dai ko?? To nagode, dama ke baki
taΙa goyon bayan mutum a duk halin da yake ciki, in dai mutum zai kawo maki
damuwarsa to ya kara dulmiya kansa cikin damuwa ne, ni kuma ban taΙa kin
supporting dinki ba no matter the situation, ko Abdul da nake zagi kullum kamar
Ιa na nake goyon bayanki an gaya maki kema baki da naki baΖin halin ne wani
lkci? Dama mistake nayi ma na zo gidan nan asirina a rufe da gidan Sandra na
wuce da ba a kara bata min rai ba" Tana fadin haka ta mike ta figi jakarta
ta nufi kofa kamar zata tashi sama, Khaleesat ta mike tace "Safiyyah"
Banza da ita Safiyyah tayi har ta fice daga parlon ta kullo mata kofa,
Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta koma ta zauna, a hankali tace "Ae
shikenan"
07087865788✍π»
[5/15, 7:17 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Read My Book
"HALYSAAH" on
ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6
✨✨ HALYSAAH✨✨
By _Khaleesat Haiydar_✍π»
19....
Ranan friday wajen karfe sha daya na safe Khaleesat ta gama
Laundry da take a kitchen ta fito, a reading nook din parlon ta tarar da
Housemate dinta yana duba textbooks dinsa, cikin few seconds ya dau wanda zai
dauka ya dawo cikin parlon yana kallonta yace "Har kin gama kenan"
Kai kawai ta gyada masa ta fara tidying din parlon, rana na farko kenan da ta
fara ganinsa yayi shiga irin ta Hausa cikin fararen kaya, Taji yace "Hope
you are studying well Halysaah" kai kawai ta gyada masa, yace
"Alright, till later" Ta Ιan kallesa tace "Are you
Nigerian?" Ya buda ido yace "Why do u ask?" Tace "Kawai
nayi zatan ko daga Chad kake, or Niger" Dariya yayi yace "Hope it's
fine now tunda kin rama?" Hanyar dakinta ta nufa ba tare da ta basa amsa
ba, ya dau makullin motarsa ya nufi kofar parlon, sai bayan da ya fita sannan
ta dawo cikin parlon ta tafi gun window ta Ιan bude drapery din jiki tana leka
garage, ganin har ya tafi ta ci gaba da aikin da take yi a parlor. Wajen karfe
biyar na yamma Khaleesat na kitchen tana girki at the same time suna waya da
Abdul, tun 40 mins ago ya kirata suke magana har sannan, duk kwanan nan dai
lafiya suke waya da shi, ya kuma Ιan rage mata wasu abubuwan da yake mata, he
is being a little caring these days, a rana sai su yi waya sau biyu wani lkcn
har sau uku har hakan na bata mamaki kamar dai ba shi ba, yanzun ma shi ne yayi
encouraging dinta ta tashi ta fara girkin da take yi don bata yi niyyar girki
ba, for weeks now kullum Housemate dinta ke masu takeaway na dinner wani lkcn
har lunch, this made her soo lazy to go to the kitchen, breakfast dama tea and
cookies take ci yawanci ko kuma ta ci da bread idan Housemate dinta ya siyo,
wani lkcn ta ci french fries da kwai ko ketchup, kwankwasa kofar parlor taji
ana yi, ta Ιan zaro ido sanin bazai wuce Housemate dinta ba, kilan ya mance
makullinsa ko kuma yayi misplacing dinsa as usual, ta kalli wayarta dake ajiye
a kan kitchen cabinet har sannan Abdul was on the line kuma a handsfree ta sa
wayar, tana Ιan kame kame tace masa "Can u excuse me pls, i will call u
back in the next 2 minutes pls" Abdul yace "Why? Me zaki yi? Is the
call hindering you from doing anything?" Da sauri tace "Noo" don
bata son tayi laifi, sai kuma a hankali tace "Just want to round up the
cooking ne, na kusa gamawa ai" Yace "But my call isn't preventing you
from doing so, wayan ba a ajiye yake ba? Continue with ur work kawai"
Knocking ta sake ji, ta ma san Housemate dinta ne cause haka yake knocking
dinsa, ta kalli wayarta tace "Ohk then" Abdul ya ci gaba da maganar
da yake mata, a hankali ta dau wayar ta fita daga kitchen din almost tiptoeing
kamar tana tsoron yaji sound din tafiyarta, ta nufi kofar parlon ta bude at the
same time tana kokarin yi ma Housemate dinta alamar da yayi shiru ta hanyar
dora finger dinta daya a lips dinta, lkci daya taji komai nata ya tsaya cak, a
hankali ta zame finger dinta daga lebbenta tana kallonsa bata ko kiftawa
zuciyarta na bugawa, ta cire wayar dake kunnenta looking speechless and
Surprise at the same time, Calmly yace "Ko in koma ne?" Ta zaro ido
cikin in ina tace "No, no, not at all, i... i was just being surprise,
sannu da zuwa" Da sauri ta koma gefe zuciyarta na bugawa da karfi, Ya
katse wayar dake kare kunnensa sannan ya shiga parlon, ta bi sa da kallo still
shocked, gani take kamar she is daydreaming, ta kikkifta idanuwanta ta bude to
be sure but still she is still seeing him, har sai da ya karasa cikin parlon ya
zauna sannan ta bi bayansa, a hankali ta duka kusa da shi tana yaΖen karfin
hali tace "Wai dama all this while kana garin nan ne? I am so
confuse" Yace "Gashi kin gan ni, in baki yarda ba sai ki taΙa ki ji
don ki tabbatar" Still feigning smile tace "I am seriously surprise,
this is the least thing i expected today wallahi..." Sai kuma ta tashi da
sauri tace "Let me get u water" Kitchen ta tafi zuciyarta na bugawa,
sai da ta jingina jikin cabinet ta dafe kirjinta a hankali tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku" Tasan at anytime
Housemate dinta zai iya shigowa gidan don yamma yayi sosai, cikin hanzari ta
bude fridge ta dauko masa ruwan gora da drink with glass cup sannan ta fita da
sauri, tana kirkiran murmushi ta durkusa gabansa ta ajiye masa tace "Tun
yaushe kake garin nan amma?" Ya dau ruwan goran yana kallo yace "You
are buying expensive water now? Sannu er gayu" Tayi dariyar karfin hali
tace "Not at all, miyar ma ya kusa yi sai in zuba maka abincin, ko dama
shi sa kace sai nayi girki?" Kawai murmushi yayi bai bata amsa ba, ta mike
ta koma kitchen, gaba daya she is confuse on what to do, ta fara dube duben
wayarta ta tuna ta ajiyesa kan kujera a parlor, fitowa ta sake yi ta tarar
Abdul yayi picking din kiran da ake masa ta waya, cikin dubara ta dau wayarta
ta nufi dakinta da sauri tana kallonsa ta gefen ido taga attention dinsa na kan
wayar da ya fara, bandakinta ta shige ta kulle tace "Na shiga uku" Da
ta tuna bata ma da lambar Housemate din nata ta sake jin mugun tashin hankali,
yanzu ya zata yi? Da sauri ta fara dialing number Salem, ai ko yana fara ring
ya daga, murya can kasa ta gaishesa without waiting for his full reply tace
"Plsss how can i get in contact with my Housemate? ina son zan masa magana
ne urgently" Salem yace "Ohk, muna ma tare, gashi nan" Bata san
sanda ta sauke wani irin ajiyar zuciyar relieve ba, taji muryar Housemate dinta
yace "Hello Halysaah, is everything alright?" Ta girgiza masa kai da
sauri kamar yana ganinta tace "Plss i am sorry amma kar kace zaka dawo
yau, my fiance is around, he just came without notice" Yace "Tohhhh,
haka kuma aka yi ashe?" Ta wani turo baki kamar yana ganinta, yayi murmushi
yace "Alright Halysaah, keep ur cool, duk sanda ya tafi sai ki sanar
min" A hankali tace "Thank you" Yace "Not a problem"
Shi ya fara katse wayar, ta kalli screen din sannan ta sauke ajiyar zuciya ta
fito da sauri bayan ta bar wayar a dakinta, har sannan ta tarar Abdul bai gama
wayar da yake ba, da alama business call ne, Khaleesat na tafiya a hankali ta
tafi kitchen don saka masa abincin da ta girka, har sannan she is shock, babban
damuwarta yanzu kasantuwarsu su biyu kadai a gidan, a da bata jin tsoron
kasancewa da shi guri daya and that was almost 4 years back, but not anymore,
he is complete changed all of a sudden in just a year, da tunanin nan ta fito
daga kitchen, ta karasa har gabansa ta ajiye masa abincin, yana kallonta yace
"How about ur Housemate, bata nan ne?" Ta Ιan yi murmushin karfin
hali tace "Yeah bata nan" Ta mike ta koma edge din kujera ta zauna
kamar bakuwa a gidan, a hankali tace "Ya su Momy da Aunty Hafsah?"
Yace "Lafiya lau" Bata sake cewa komai ba, Ya kalli abincin da ta ajiye
masa yace "I am full, ki rufe sai dai anjima" A hankali tace "Ok
tafiya zaka yi da shi?" Yana dubanta yace "In tafi da shi ina?"
Ta kirkiri murmushi tace "A'a ai tambaya kawai nayi" Yace "Na
riga nayi lodging out of the hotel, i was in Maryland since morning"
Khaleesat was speechless, bata gane yayi lodging out of the hotel ba, to ina
zai kwana ko kuma wani hotel din zai kama? kai bata ma yarda ba don in yayi
lodge out to ina trolley din kayansa yake, Tana murmushi da kyar tace "To
ina akwatin ka?" Yace "Tana cikin mota" Ta hadiye abu da kyar
tace "Motar wa?" A takaice yace "Ban sani ba" sunkuyar da
kai tayi bata sake cewa komai ba, yace "Ko kina da plans ne yau? Naga
kinyi mamakin zuwana da gaske" Ta zaro ido tace "Not at all wallahi,
ai kai ma kasan daga schl babu inda nake zuwa, kawai dai nayi mamakin muna ta
waya tun daxu ashe kana garin nan" Ya mike yace "To ki dena mamaki
tunda ba ke kika siya min ticket din ba" Ta sunkuyar da kanta tayi shiru,
dakinta ya nufa yace "Let me take a shower" Khaleesat ta gyada masa
kai kawai ta bi sa da kallo, a very tall and masculine guy he is, just like her
Housemate, and they are all handsome in their own different ways kamar su suka
yi kan su, sai dai ita tafi ganin kyan Housemate dinta ko me yasa, a zahiri duk
macen da ta samu Abdul in dai mayyar kudi ce kuma tana son namiji me tsantsan
kyau ga kuma qualities na cikakken namiji pertaining to body structure not
behavior... to duk walakancin da Abdul zai dinga mata zata jure tayi ta
shanyewa don mijin nuna ma sa'a ne shi din, that is if behavior isn't included,
amma Khaleesat dai dai da rana daya qualities din nan biyu na Abdul bai taΙa
dada ta da kasa ba, a haka stepsisters dinta ko ga maciji basa yi da ita all
because of Abdul, kiri kiri suke nuna mata jealousy dinsu daga su har iyayensu
a fili, ba su kadai ba hatta wasu daga sa'aninta a anguwa sun dena kulata
saboda shi, basu san baΖin cikin da take kunsa day by day ba, she wish zai koma
ma daya daga stepsisters din nata da ita kam ta huta, kwantar da kanta tayi
jikin kujera tana jin hankalinta na kara tashi, yana nufin kenan bazai tafi
anytime soon ba? kilan ma yace nan zai kwana fa? Sosai hankalinta yayi mugun
tashi da tunanin hakan, after a while ta mike a sanyaye ta dau abincin da ta
zubo masa ta tafi da shi kitchen ta rufe, ana haka har lkcn sallan magarib yayi
bai fito daga dakinta ba, Khaleesat dake ta zaune a parlor kamar bakuwa a gidan
ta kalli kofar dakin nata a sanyaye, sai kuma ta tashi walking slowly ta nufi
dakin, a hankali tayi sallama sai da ya amsa sannan ta bude, ta samesa zaune
saman darduma alamar sallah ya idar yana danna wayarsa, gaba daya dakin ya cika
da kamshin turarensa, murmushin karfin hali ta kirkiro ta dau hijab dinta tace
"Sallah zan yi" Sai kuma ta juya zata fita yace "Ina zaki yi
sallan?" Ta sake juyowa cikin sanyin murya tace "Parlor" Mikewa
yayi ya bar kan darduman yace "Pray here, dama kin saba sallah a parlon
ne?" Ya koma gefen gado ya zauna still pressing his phone, da kyar ta
karasa kan darduman ta fara sallan, bayan ta idar ta dinga addu'ar Allah ya taΙa
zuciyarsa ya tashi ya tafi ya bar mata gidan ita dai, muryarsa taji yace
"Make me a cup of hot chocolate" Ta gyada masa kai tace
"To" Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita zuwa kitchen, abinda yace tayi
ta masa sannan ta koma dakin rike da mug din, bedside drawer ta ajiye masa tace
"In kawo maka abincin?" Yace "Aa bazan ci abinci ba, me yasa
kike yawo da Hijab kamar matar liman" Tana murmushin karfin hali da kyar
tace "Aa ina jiran lkcn isha ne" Yace "Cire Hijab din nan"
Ba musu ta cire a hankali ta linke ta ajiye, yace "Ke kin ci abincin
ne?" Duk da bata ci ba ta gyada masa kai don gaba daya ta nemi appetite
dinta ta rasa, gun reading material dinta ta tafi ta zauna ta kunna laptop
dinta tayi kamar karatu take, ya gama danne dannensa a waya ya dau chocolate
dinsa ya fara sha, gaba daya Khaleesat bata fahimtar me take dubawa a laptop
din gabanta, sun kusa awa daya a yanda suke, ita dai har sannan tana gaban
laptop taki tashi, ta gefen ido ta kallesa ganin ya mike daga inda yake zaune,
taga sallan isha zai yi, sai da ya idar sannan ita ma ta tashi ta tafi tayi
sallan, nan ma babu kalan addu'ar dabata yi ba kan Allah ya taΙa zuciyarsa ya
koma hotel dinsa, after a while ta mike ta dauke darduman ta linke ta ajiye, ya
mike ya kamo hannunta yana kallonta yace "Why are you uncomfortable kamar
kina tare da stranger a gidan nan ne Khaleesat?" Tayi dariyar yake tace "Stranger
kuma Ya Abdul? Ai kai ba stranger bane, kai yayana ne, kuma da ai ka sha kwana
gidan nan farkon da na zo kasar, kana kwanciya a parlor ni kuma in kwanta a
daki" Yace "Kinsan da haka kike dari dari?" Ta sunkuyar da kanta
ganin kallon da yake mata, zuciyarta ya dinga bugawa, har ji take kafafuwanta
suna neman kasa daukarta, ya matso da ita dab da shi har tana iya jiyo breathing
dinsa, calmly yace "Kinsan menene yasa nake kwanciya a parlor a
sannan?" Ta girgiza masa kai without looking at him don she is soo
uncomfortable with him drawing her closer to himself, yayi kasa da murya yace
"Saboda u were still a baby sannan" Ta daga idanuwanta da kyar ta
kallesa amma ta kasa cewa komai, yace "Yanzu kuwa ke ba baby bace, how old
are you?" Ta kasa basa amsa, ya Ιan mata tsawa yace "Tambayarki
nake?" Ta hadiye wani abu da kyar tace "I am 20" yace "To a
sannan ina keeping distance between us because i was still grooming you"
Ta kauda kai seeing how closer he was coming to her, juyo da kanta yayi yace
"Meye haka?" Muryarta na rawa tace "This is against the teaching
of islam Ya Abdul, ni ba muharramarka bace" Yace "Oh really? Dama
wani ne zai aure ki ba ni ba ashe?" Ta kasa ce masa komai lkci daya hawaye
ya cika idonta, duk tsiyar da yake mata da yaga hawaye idonta yake calming
down, ya jawota jikinsa yayi kasa da murya yace "Kin zata ke irin matan da
zan yi using inyi dumping ne Khaleesat? You are diff from them, ke matar da zan
aura ce" Ta kasa basa amsa hawaye na zuba idonta, ita kanta tasan Abdul so
na aure yake mata, a shekarun da suka yi tare iyaka yakama mata hannu babu dadi
babu kari, amma daga 2 years back labarin ya sauya har bata son ya zo inda take
don sai ya mata wasu abubuwa dake damunta, in ya tafi ta sha kukanta kuma ta
kan yi kwana da kwanaki bata dawo dai dai ba, amma bai taΙa attempting saninta
ba, muryarsa ne ya dawo da ita daga tunanin da ta tafi, as if whispering yace
"I have tried Khaleesat, i abstained from doing anything that will
distabilize you all this years because i want you to have the best education ta
yanda zan iya nuna ki a ko ina as my wife, amma kullum ina jin urge dinki a
raina I've tried so many times to ignore the urge, but menene ya rage yanzu?
You have just a year and few months to round up, aurenmu kuma ko yau aka ce a
daura babu abinda zai hana daurasa, i came all the way from Nigeria because all
this days my feeling for you is distabilizing me and making me go nut Khaleesat,
so now trust me, relax and keep calm pls baby gal" Khaleesat ta dade bata
shiga tashin hankalin da ta shiga a sannan ba, don sarai ta fahimci inda
maganarsa ya dosa, kuma lkci daya yake magana yana cire mata hijab din jikinta,
common ya taΙa ta idan taki ta karfi yake yi mata balle wnn, gashi gaba daya
yanayinsa ya canza alamar ya fara fita hankalinsa ma, ta kamo hannunsa jikinta
na rawa tace "But kwanakin da suka rage ai basu da yawa ko Ya Abdul, why
not be patient pls..." Ya kalleta da idanuwansa da suka kada strictly yace
"I can't wait any longer" Muryarsa kadai sai da ya tsoratata hakan
yasa tayi gum da bakinta, tana jin zuciyarta kamar zai fito daga kirjinta
tsabar tashin hankali, kafin ya rabata da kayanta tayi kasa da murya still
holding his right hand tace "Ohk pls ka bari inyi wanka tukun, kai ma ai
ka yi" Ya dinga kallonta da idonsa da suka yi ja, ta sunkuyar da kanta
trying to control herself kar ta fashe da kuka tace "I won't take
long" Saketa yayi ya koma gefen gado ya zauna, tana tafiya da kyar ta nufi
bandaki tana kallon wayarta dake gaban dressing mirror, ta Ιan kallesa, taga
bin ta yayi da kallo, ta dake da kyar tace "Zan dau shower gel dina"
Gaban mirror dinta ta nufa, dai dai sanda ya fara cire rigar jikinsa da sauri
ta dau wayarta da wani Container din lotion da tayi pretending shower gel ne
sannan ta shige bandaki ta kulle kofa, tap ta bude jikinta na rawa hawaye na
sauka idonta ta fara dialing number Salem, yana fara ring ya daga, da kyar tace
"Plss i want to speak to my Housemate plss" Salem yace "Oops
wllhi bama tare yanxu" Ko rufe baki bai yi ba tace "Don girman Allah
ka turo min lambarsa yanzu" Yace "Ohk let me send you" Yana
katse wayar ta dinga kallon screen dinta tana jiran shigowar lambar Housemate
dinta, her body was just shaking, ga wani bugawa da zuciyarta yake, cikin few
seconds sai gashi ya turo mata lambar, da sauri tayi dialing ya fara ringing
amma har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, sau uku tana
kiransa bai daga ba, ta saki kuka ta durkusa kasan bandakin tace "Na shiga
uku" Sake dialing number Salem tayi, yana picking tace "Pls bai daga
ba ko zaka..." Salem bai jira jin sauran bayaninta ba yace "Bari in
tura maki number Ajay, nasan dama ba lallai Jay ya daga ba don ba ko wani kira
yake dauka ba, sai kice ma Ajay ya basa suna tare yanzu" Tana gyada kai da
sauri tace "Ohk to Nagode" yana katse wayar sai gashi ya turo mata
number Ajay, tayi dialing number da sauri hannunta na rawa, ai kuwa yana fara
ringing da few seconds aka daga, da kyar tace "Plsss ina son zan yi magana
da Housemate dina ne" Shiru taji yayi as if processing the voice, sai kuma
a takaice yace "Waye wannan?" Ta fara shesshekar kuka muryarta na
rawa tace "Don Allah kayi hakuri ka rufa min asiri ka basa ina son zan
masa magana" Yace "Me ya faru?" Cikin kuka tace "I need his
help plss" katse wayar taji yayi, hankalinta in yayi dubu ya tashi a
moment din nan, ta shiga uku ta lalace, yanzu ya zata yi, ko dai ta kira
Safiyyah, number Safiyyah ta duba da sauri tayi dialing amma har ya katse bata
daga ba, ji tayi kamar za a bude kofar bandakin tayi saurin tsoma wayar
hannunta cikin ruwan da ta fara tarawa a bath tub a gigice, ashe kunnenta ne ma yaji kamar an
taΙa kofa amma ba kowa gun kofar, ta ciro wayarta taga screen din yayi baΖi, ta
dinga yarfe ruwan da ya shiga tana kokarin kunnawa amma yaki kunnuwa, hade
kanta tayi da bath tub hawaye masu zafi na sauka idonta....
*End of free pages, za mu ci gaba da update a payment group*
*For continuation of the
book Halysaah, pay 500 into 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah*
_And ur evidence of payment via 07087865788_✍π»
*My special thanks to those that have already patronized
since the beginning of this book, Thank you so much and i appreciate you*π₯Ί
[5/18, 3:12 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat ta
kusa minti sha biyar a bandakin cikin tashin hankali da confusion, banda kuka
babu abinda take yi, she can't even think straight tsabar yanda ta shiga tashin
hankali, to ko dai kawai ta fita ta gudu ta bar gidan ne, ko kuma taje ta basa
hakuri ya rufa mata asiri, ta ma san bazai taΙa sauraronta ba, da kyar ta mike
daga durkushen da take hawaye sosai na zuba idonta har sannan jikinta rawa
yake, gani take kamar the world have come to an end for her, hannunta na rawa
ta wanke fuskarta tayi karfin halin bude kofar bandakin a hankali tana leka
Bedroom dinta, zaune ta gansa edge din gado yana danna wayarsa, suna hada ido
ta bude kofar ta fito, ya dinga kallonta daga sama har kasa, hakan yasa ta
sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa, Mikewa tsaye yayi yana mata wani kallo
yace "So you just wasted my time all this while ba wankan kike ba
dama?" tears was just rolling down her cheek tana girgiza masa kai
muryarta na rawa tace "Don girman Allah kayi hakuri, kar kace zaka...."
Dakatar da ita yayi ta hanyar daga mata hannu, tuni ta ja bakinta tayi shiru
tana kallonsa a tsorace ganin yanda lkci daya yanayinsa ya canza, tana ganin ya
nufota ta juya zata koma bandakin da gudu yayi saurin fixgota, ta rushe da kuka
sosai tana cewa "Don girman Allah kar ka min haka ka rufa min asiri Ya
Abdul" Yana mata wani kallo yace "You think i will just waste my time
and money coming here at the end in kyaleki da childishness dinki in koma
Nigeria? You must be joking, In kika ga na kyaleki yau sai in faduwa nayi na
mutu" Zuwa sannan Khaleesat bata ma san kalmomin dake fitowa bakinta ba ta
dinga basa hakuri a rikice, ta dai san ko da wasa bazata ce zata yi kokuwa da
shi ba, ta ina ma zata fara, da hannu daya in ya riketa ko kwakkwaran motsi
bazata iya ba balle ta kwace kanta, Knocking kofar da ta jiyo a kunnenta ne
yasa ta zaro ido bakinta na rawa tace "Wallahi Housemate dita ce ta dawo
kuma bata da makulli nata ya Ιata..." Yace "And so what? Ita zata
hanani abinda nayi niyya ne?" Hawaye na sauka idonta tace "Don Allah
ka bar ni in bude mata kilan mantuwa tayi, she is not spending the night
here" Saketa yayi fuskarsa babu yabo babu fallasa yace "Remain here,
i will open the door for her" Gyada masa kai kawai take zuciyarta na
bugawa da karfi, ya dau rigarsa ya saka sannan ya nufi kofa ya fita, a hankali
Khaleesat ta sulale kasa tana jin kamar numfashinta zai dauke tsabar tashin
hankali, gashi sai knocking kofar parlon ake babu kakkautawa, da sauri ta mike
jikinta na rawa ta bi bayansa tana shesshekar kuka at the same time tana
tunanin to wa ke kwankwasa kofar Allah Ubangiji ya sa Housemate dinta ne, nan
corridor ta makale don tuni har Abdul ya isa kofar parlon zai bude, ya murda
makullin ya bude kofar, Khaleesat couldn't believe who she saw standing at the
doorstep, ai bata san sanda ta karaso parlon da sauri ba hawaye na sauka
idonta, Abdul dake kallonsa daga sama har kasa Calmy yace "How may we help
you? Who are you looking for?" Maimakon wanda ke bakin kofar ya basa amsa
kawai ya bi gefensa ya shigo parlon yana kallonta yace "Why did you call
my line?" Da mamaki Abdul ya juya ya kalli Khaleesat da ta sunkuyar da
kanta hawaye na sauka idonta ta lumshe ido, bata san sanda wani relieve ya zo
mata ba lokaci daya, ta sake jin muryarsa yace "Me yasa kika kirani?"
Ta daga kai ta kalli Abdul ganin irin kallon da yake mata at the same time ya
nufo inda take cikin zafin nama, ganin haka ta fara komawa baya cikin rawar
murya tana kallon AJ tace "I need you to help me pls" Ko rufe baki
bata yi ba taji Abdul ya sauke mata wani wawan mari a kuncinta, AJ could not
believe what he just saw cause bude baki yayi at first, ganin ya kara sauke
mata wani marin cikin few seconds AJ ya isa gaban Abdul sending him double fist
a fuska, he took Abdul unaware don bai gama recover daga fist din ba ya kara
masa wasu ukun a jere, kan kace me ya fara punching dinsa kamar an aikosa,
Rikicewa Khaleesat tayi da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,
na shiga uku plss stop it" Tana matsowa kusa da su zata rike AJ da ya wani
hankadata sai da ta fada kan kujera, Dai dai sanda aka bude kofar parlon Jay ya
shigo, buda baki yayi ya jefar da wayar hannunsa saman kujera ganin Abdul a
hannun AJ kamar ya samu punching bag, AJ gave Abdul no single space to
retaliate, dukansa kawai yake kamar suna gidan dambe, Jay ya nufesu da sauri
yana kiran AJ, da kyar ya samu nasaran rabasu yana ma AJ tsawa yace "Are
you out of your mind Junaid? Are you mad, Meye haka?" Jay bai rufe baki ba
Abdul ya koma kansa da fist din da bai samu yi ma AJ ba, ai ko ya kara ja ma
kansa wani dukan wajen AJ, Jay that was shock at the attack Abdul just attacked
him ya bude baki yana kallonsu, kar AJ yaje ya ma Abdul illa su shiga uku ya sa
Jay ya kara rike AJ, Abdul that was beaten blue black ya nufi kitchen kamar
mahaukaci vowing to unalive AJ, Khaleesat tsabar shock ko motsin kirki bata yi
a inda AJ ya wurgar da ita, Jay na ganin Abdul ya shiga kitchen yasan makami
kawai yaje daukowa, ya kalli Khaleesat da sauri yace "Tashi ki tafi
daki" Ai kamar jira take ko rufe baki Jay bai yi ba ta mike a guje tayi
Corridor ta tsaya tana zare ido, Jay ya fara jan AJ su tafi daki amma AJ yaki
yana cewa "Don babansa me yake takama da shi a Nigeria? Who the F is he?
Kakkaryasa zanyi in karya banza wallahi, in ya cika shege mu hadu a
Nigeria" Jay yaki biye AJ haka dai ya ja sa har corridor zai shigar da shi
daki, sai ga Abdul da wuka ya nufo su kamar Ζan daba, ai ko karasa shigewa
dakin basu yi ba Khaleesat ta riga su, tuni Jay ya sa ma dakin Key ya zare
makullin ya saka a aljihu don tsaf yasan AJ sai yace zai bude kofar ga makami
hannun Abdul, Abdul ya dinga bubbuga kofar saying all sort of abusive words at
the same time yana alkawarin sai ya ma AJ illa, AJ ya tafi jikin window ya
tsaya yayi crossing kafa yana kallon kofar dakin, Jay dai ya zauna gefen gado
looking speechless and confuse, sai kuma ya dafe kirjinsa da ya fara masa ciwo
saboda fist din Abdul, ita dai Khaleesat na rakube jikin gado hawaye na sauka
idonta tana kuka a hankali, banda bugawa da karfi babu abinda zuciyarta ke yi,
taji muryar Abdul na cewa "Ke kuma sai na maki abinda har ki koma ga
mahaliccinki baza ki mance ba, i will make sure you become useless and
miserable, i promise you this, kasar nan kuma kamar kin bar sa don karatun ki
ya zo karshe" Khaleesat ta kara sautin kukanta, Ajay ya daka mata tsawa
yace "I will fling you out of this room in baki rufe ma mutane baki a nan
ba" Jay ya wani kallesa, ita dai Khaleesat ko kallonsa bata yi ba kukanta
kawai take, after a while ko ina yayi tsit a gidan ko tafiya Abdul din yayi
oho, da kyar Khaleesat ta mike bayan kusan minti goma zata dau hijab dinta, Jay
ya bi ta da kallo, bayan ta saka Hijab din ta juya suka hada ido, sauke idonta
da ya kumbura don kuka tayi, sai kuma ta tafi ta dau karamin towel da ta gani
gefen gado seeing traces of blood in Jay's lips, bandaki ta tafi ta jika towel
din da ruwan dumi sannan ta dawo dakin without looking at him ta duka gabansa
ta dafa gadon ta fara goge masa lip dinsa a hankali, AJ ya wani kallesu sai
kuma ya tabe baki ya kauda kai yana kallon outside of the window, Jay dake
kallonta yace "Thank you Halysaah" Ita dai bata ce komai ba kuma bata
yarda ta hada ido da shi ba ta mike ta tafi bandaki da towel din, AJ ya juyo
yace "Kai Malam bani makulli in bude kofar nan in fita" Mikewa Jay
yayi ya nufi kofar ya fara budewa a hankali, AJ ya bi bayansa incase of
necessity, yana bude kofar AJ ya rigasa fita at the same time being very
conscious of everywhere in the house, both angle and corner, a haka ya fito
parlon Jay ma that was at alert na biye da shi a baya amma fa sai da ya kulle
kofar dakin da makulli sbda Khaleesat, and they realized Abdul ya fice daga
gidan, AJ ya juya ya kalli Jay yace "Dau wayarka mu tafi gida" Jay
yace "You think i can just go and leave her in here?" AJ ya masa wani
kallo yace "How sure are you u are safe being in this apartment tonight?
Mahaukaci ne fa gayen kuma zai iya dawowa at anytime, it's already dark
now" Jay yace "Nasani, but bazan iya barin ta ita kadai gidan nan ba"
AJ yace "Are you her family member or something?" Jay yace "Kai
da ka taho nan family member dinka ce?" AJ yace "Look Jay, Billah
bazan bari ka zauna a gidan nan ba, koma wani taimako zaka mata kayi mata ni
babu ruwana amma baza ka zauna a gidan nan ba, i can't risk leaving you here
even for 1 second" Jay that was quiet for a while yace "Toh ka tafi,
zan biyoka a baya" AJ yace "Kafata kafar ka Malam, kaji nayi rantsuwa
bazan bar ka gidan nan ba, dubi kullin da ya dinga maka babu abinda ka tabuka
sai sake baki kayi kana kallonsa" A hankali Jay yace "So kake mu hade
masa at the end mu zo mu yi abinda za ayi da an sani, ai gwara da na kyalesa
kawai kai ba gashi ka basa kashi yanda ya kamata ba, beside in muka ce zamu
dokesa tare hakan zai sa mu gigita yarinyar ne" AJ yace "Aa haukatar
da ita za mu yi ba gigita ta ba, pls do what ever you want to do ka fito mu
tafi gida, ni yunwa ma nake ji" Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace
"Wait for me outside then" Yana fadin haka ya juya ya koma dakinsa da
Khaleesat take, AJ kuma ya fice daga parlon ya tsaya nan bakin kofa yana
jiransa, bayan Jay ya bude dakin da makulli sai da yayi knocking sannan ya
shiga ciki, tsaye ya ganta jikin bangon dakin hawaye na sauka idonta tana
shessheka, ya tafi can jikin window ya tsaya yana kallonta, ita dai ta sunkuyar
da kanta tana kuka a hankali, Calmly yace "Halysaah" Ta kasa daga kai
ta kallesa, yace "Tell me how did you get to know this guy? A ina ku ka
hadu? For how long ku ke tare da shi, kuma who is he? Iyayenki sun san da
alakar ku?" Sai a sannan ta daga kai wasu hawayen na sauka idonta tana
kallonsa, ya sauke ajiyar zuciya yana shafa kansa yace "Where are ur
reading material? Suna dakin ki ne?" Kai ta gyada masa kawai, yace
"Mu je ki dauka" A tare suka tafi dakinta, bayan yaga inda reading
materials din nata suke ya karasa ya dauka har da laptop dinta, ya kalleta yace
"Ina wayarki fa?" A hankali tace "Ya fada ruwa" Shiru yayi
sai kuma yace "To mu je" Ta Ιan yi jim tana kallonsa, yace "Mu
je mana" ba musu ta nufi kofa ya bi bayanta bayan sun fita ya kullo kofar,
ita dai duk a tsorace take sai zare ido take tana ganin kamar Abdul zai sake
dawowa gidan at anytime, ganin a tsorace take Jay ya shiga gaba yace
"Follow me" Bin bayansa ta dinga yi hawaye na sauka idonta har suka
fita daga parlon, har sannan Ajay na tsaye waje, ya juya ya kallesu, Jay ya
nufi motarsa ganin Khaleesat ta tsaya yace "Mu je mana Halysaah" tana
tafiya a hankali ta ci gaba da bin sa, back seat ya bude ya ajiye laptop dinta
da sauran reading material dinta ya kulle sannan ya bude mata front seat, ta
sauke idonta ta shiga motar ya kulle, yana kallon direction din AJ yaga har ya
nufi gun motarsa ya shiga, zagawa yayi ya shiga driver seat ya tada motar, tuni
AJ yayi zoom off, Jay ya bi bayansa. A hankali Khaleesat ta sauko daga motar
tana kallon Jay da shi ma ya sauka ya bude back seat ya dauko laptop dinta da
takardu ya kulle motar yace "Mu je" Sauke idonta tayi ta fara bin sa
a baya walking slowly har suka shiga parlon gidan, ya nuna mata kujera yana
kallonta, ta sunkuyar da kai sannan ta zauna, ya ajiye laptop da takardunta
dake hannunsa sannan ya wuce sama, ta bi sa da kallo hawaye na taruwa idonta,
sai kuma ta fara kuka a hankali tana jin kanta na sara mata, Jay ya tafi dakin
AJ yana bude kofar dakin yaji yana wanka a bandaki, hakan yasa ya tsaya bakin
kofar dakin don baya son issue, yana ta tsaye da tunani iri iri a ransa har AJ
ya fito bandakin, AJ na ganinsa ya dakata da goge gashin kansa da karamin towel
yace "Me kake nema a nan kuma?" Jay yace "Ban sani ba" Sai
kuma ya karasa cikin dakin that was extra clean, kan kujera ya zauna without
looking at AJ yace "We need to talk AJ" Ajay yace "Shi ne sai ka
shigo min daki?" Jay yace "Zauna mu yi magana" Ζan tsaki AJ ya
ja yana ci gaba da goge gashinsa yace "Ina jin ka ba sai na zauna ba"
Jay yace "I think my Housemate will stay here for a day or 2, before she
sort her self out" AJ yace "As per you are her family member or who?
Bata da iyaye ne? Ko nan din hotel ne?" Jay yace "Ban sani ba" AJ
yace "No i am just asking a harmless question, like naga dai ba daga sama
ta fado ba, kuma ba kai ka kawota America ba balle kace zaka samar mata
solution, who are you to her? Yayanta ko Ubanta? Wanda muka mata ma Allah ya
bamu lada, come off it Jawwad" Jay yace "Ai ba permission din ka na
shigo nema ba Junaid, kawai sanar maka nake yarinyar nan zata yi kwana daya
zuwa biyu a gidan nan kafin komai yayi settle" AJ yace "Toh ni na
haifeka da zaka shigo ka gaya min zaka kawo yarinya tayi kwana biyu gidan nan?
Ai sai dai ka kira su Abba ka gaya masu, beside the house is very big with
multiple rooms to accommodate her, so ni ina ruwana, i just pray u don't have
to explain ur self one day" Jay ya mike ya fice daga dakin banging the
door behind him, AJ ya tabe baki yana feshe jikinsa da turaren jiki. Bangaren
masu aikin gidan Jay ya nufa bayan ya sauko downstairs, ya basu umarnin da zai
basu sannan ya dawo babban parlon gidan, Khaleesat dai na zaune ta jinginar da
kanta jikin kujera tayi nisa tunanin da ta fada, ganin komai take kamar a
mafarki, sai in taji tana da ta sanin abinda ya faru amma da ta tuna raping
dinta Abdul yayi niyyar yi da Ajay bai zo ba sai taji ta nemi da ta sanin ta
rasa, amma fa bata da nutsuwa bata da kwanciyar hankali, she was just restless
and sick, bata san kuma me zai faru next ba a rayuwarta, muryar Jay ne ya dawo
da ita daga tunanin da take ta gyara zama tana kallonsa a sanyaye, ya zauna
kujeran dake kallon wanda take zaune yace "Bana son ki sa ma kanki damuwa
Halysaah, ki kwantar da hankalinki pls kin ga kina da jarabawa a gabanki"
Khaleesat ta sunkuyar da kanta hawaye ya fara sauka idonta, Yace "Kin yi
sallah?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk za a kawo maki abinci sai ki ci
kafin mu yi magana" Ta girgiza masa kai tace "Bana jin yunwa"
Yace "No, sai kin ci abinci ko ba yawa" Dai dai nan kukun gidan wanda
bature ne ya taho da abinci zai kai dinning Area, Jay ya masa umarnin ya kawo
parlon sanin abincin AJ na kan dinning din, dawowa kukun yayi Jay ya nuna masa
inda zai ajiye abincin, nan ya jerasu a kasan lallausan Centre carpet, ya koma
ya dauko sauran, bayan ya ajiye komai ya tafi Jay ya mike yana kallonta yace
"Ki sauko ki ci abinci, let me pray" Ta gyada masa kai kawai, ya wuce
sama sannan ta sauko kasa a hankali tana duba abincin da aka kawo mata taga duk
abincin jajaye ne gashi abincinsu da yawa ita ba iya ci tayi ba duk shekarun da
tayi a kasar su. Almost 30 mins after Khaleesat dake ta zaune tana tunane
tunane ko abincin ta kasa ci ta daga kai taga Ajay ne ya shigo parlon, sunkuyar
da kanta tayi, bai kalli inda take ba yayi wucewarsa dinning Area ya fara cin abincinsa,
after a while Khaleesat ta daga kai a hankali jin footstep, taga Housemate
dinta ne ke saukowa downstairs, ya karaso har inda take ya zauna kan kujera
yace "Kin ci abincin?" Ta gyada masa kai, cook din gidan ya kira ya
dauke sauran abincin ya tafi da su, Jay yace "To ki koma kan kujera"
Ita dai Khaleesat kanta na kasa bata ce komai ba, har sai da Jay ya sake mata
magana sannan ta mike ta koma kan kujeran ta zauna, AJ ya dawo cikin parlon ya
tafi reading nook dake parlon, Jay ya bi sa da wani kallo har ya gama kakkabe
kakkabensa ya zauna, ko uban me zai yi a can don yasan dai baya ma zuwa nan
balle yayi karatun a nan, muryar Jay ya dawo da hankalin Khaleesat jikinta,
taji yace "So Halysaah i want to even know what happen first of all at ur
apartment today, don ni ban san me ya faru ba, Salem called me yace kin kirani
ban daga ba and you sound disturb, and he gave you AJ's number, i rang you back
quickly sai kiran bai shiga ba, shine nayi deciding in je can gidan kawai,
menene ya faru?" Khaleesat ta sunkuyar da kai don bata ma san me zata ce
masa ba, ta yaya ma zata fara cewa raping dinta Abdul ya so yi, muryar AJ suka
ji a parlon yace "Allah ma yasa ba rashin kunyan da ta saba yi ma mutane
taje tayi masa ba, kawai ta sa na doki bawan Allah a banza" Khaleesat dai
bata dago kanta ba, shi dai Jay yayi murmushin da bai yi niyya ba yana kallon
direction din da AJ yake, A hankali Jay yace "You are not saying anything
Khaleesat" Hawaye ne ya cika idonta, ganin haka Jay yace "Or you
don't want to talk about it?" Ta girgiza masa kai hawaye na sauka idonta
da kyar tace "Ba haka bane, he tried molesting me" AJ that heard what
she said duk da ba kallon direction dinta yake ba yace "He tried molesting
you, amma da hannunki ai kika bude masa kofar ba ta window ya shigo ba"
Jay ya wani kallesa yace "Stop this please AJ, why are you so wicked and
heartless" AJ yayi wata dariyar bosawa, Jay ya dinga hararansa, ita dai
Khaleesat hawaye ne kawai ke zuba idonta, tsabar ciwon da kanta ke mata har
wani dishi dishi take gani, Cikin kwantar da murya Jay dake kallonta yace
"Tell me who he is, and where did you know him from" Ta gyada masa
kai tana share hawayen da yaki tsaya mata a hankali tace "Shekara hudu
kenan na san shi....."
*Don't even know where to start from, the patronage was
massiveπ₯Ί, thank you soo much for encouraging me fans, Allah ya biya
maku bukatunku na alkhairi, Allah ya raya zuri'a, i soo much appreciate ur
patronage, marasu auren cikin ku Allah ya baku mazaje na gari, masu aure kuma
Allah ya ci gaba da baku zaman lafiya a gidajenku, Allah ya karo maku budi
ninkin ba ninki, ya raba ku da iyayenku lafiya* π₯Ί
_Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah,
it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar
hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta i owe you 500_
[5/19, 5:53 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat ta
sunkuyar da kanta har sannan bata daina goge hawayen da ya ki tsaya mata ba,
she look pained and traumatized, Shi dai Jay kallonta kawai yake waiting for
her to continue with what she is saying, jin tayi shiru yace
"Halysaah" Ta daga idanuwanta ta kallesa, Calmly yace "I am
listening" muryarta na rawa tace "Kawai dai shi ne ke sponsoring
dina" Ba Jay da ya kafeta da ido ba yana mata kallon mamaki, har AJ sai da
ya juya ya kalleta daga inda yake zaune jin abinda tace, Jay was just
speechlessly staring at her, can dai ya gyara zama yace "You mean shi yake
sponsoring dinki a kasar nan? Are you related in anyway with him?" Ta
girgiza masa kai kawai, da mamaki kawai yake kallonta, after few seconds yace
"And ur parent allowed him to sponsor you har zuwa nan America?" Ta
gyada masa kai without looking at him, mikewa AJ yayi, yayi wucewarsa sama, Jay
ya bi sa da kallo don shi ma ya rasa abun cewa don mamaki, Jay ya maida dubansa
kan Khaleesat a hankali yace "Ya kai kudin aurenki ne an sa maku
rana?" Ta daga idanuwanta ta kallesa cikin sanyin murya tace "Nima
ban sani ba, amma kamar ya kai" Jay yayi shiru for almost 3 minutes with
different thoughts running his mind, everything just took him unaware, bai taΙa
tunanin saurayin nata ne sponsor dinta all this while ba, can ya daga kai ya
kalleta yaga ta jinginar da kanta jikin kujera looking so tired and pale, yana
son sanin me ya hadata da Abdul, meye ma dalilin haduwarsu, sannan a ina ma
suka hadu da shi din, what is this great thing that motivated her parent har
suka amince ma stranger da basu hada komai da shi ba ya turo er su har wata
kasa karatu, he just don't want to believe it's because of money they did
this.... amma ganin yanayinta yasa yayi keeping all the questions to himself
for now don baya son ya kara stressing dinta, she is already stressed, mikewa
yayi calmly yace "I will be back now" Ita dai ta bi sa da kallo har
ya haura sama, wasu hawaye taji na taruwa idonta, kawai so take tayi kuka me sauti
ko zata ji saukin abinda take ji a ranta, ta hade kanta da kujera tana
shessheka a hankali, Jay na haurawa sama ya tafi dakin da ya sa daya daga
worker din gidan ya kara gyarawa, the room was big sai dai bai kai nasa da na
AJ ba, kuma babu abinda babu a dakin sai Duvet na saman bed spread, ya bude
press din dakin yaga babu a nan ma, juyawa yayi ya fita ya dau hanyar dakin AJ,
yana isa ya danna code din bude kofar dakin ya murda yaga bai buduwa, yasan
canzawa yayi kenan saboda ya shigo masa dakin daxu, knocking din kofar yayi,
after a while AJ ya bude kofar yana kallonsa alamar what happen, Jay ya turasa
gefe ya shiga cikin dakin, AJ ya bi sa da kallo yace "Ka dai san bana son
haka Jawwad, what are you looking for?" Jay ya kunna wutan dakin that is
more brighter yace "Duvet zaka bani, i don't understand dalilin da yasa
zaka kwashe kaf duvet din sauran rooms din all to ur self, this is greed"
AJ dai kallonsa kawai yake cause he is already angry shigo masa da Jay yayi
daki, ganin Jay ya nufi inda duvet dinsa suke yace "Jay me zaka yi da
duvet bayan kana da naka a daki?" A takaice Jay yace "I am giving my
visitor" AJ ya bude baki yana kallonsa yace "What??? I don't
understand, Duvet dina zaka dauka ka kai ma visitor dinka? are you even okay?
Can you hear ur self pls?" Jay bai tanka sa ba ya dau na saman gadonsa
kawai ya nufi kofa, AJ ya tare kofar on a serious note yace "In ka fita da
duvet din nan ka canza min suna yau" Jay ya wani turasa daga bakin kofar
har sai da ya kusa faduwa sannan ya fice daga dakin, sai bayan da ya fita ya
juya ya kalli AJ da ya bude baki yana kallonsa with shock, Jay yace
"Emmanuel" daga haka yayi wucewarsa ya bar AJ da bin sa da kallo, Jay
na komawa ya ajiye duvet din kan gadon dakin da aka gyara ma Khaleesat sannan
ya sauka downstairs, tana nan zaune yanda ya bar ta idonta a lumshe amma ba
bacci take ba, yace "Halysaah" Bude ido tayi da sauri bayan ta dawo
duniyar tunanin da ta tafi, yace "Tashi mu je sama, u need rest" Ita
dai tayi shiru bata ce komai ba, ya dau laptop dinta da takardunta yace "Mu
je" Sai bayan da ya fara tafiya sannan ta mike a hankali ta bi bayansa,
har wani jiri take ji amma a haka ta daure ta bi sa har zuwa sama, ya bude
kofar dakin ya shiga tana biye da shi, bayan ya ajiye laptop din hannunsa ya
kunna mata na'uran da zai dumama dakin, ya nuna mata hanyar bandaki ita dai kai
kawai ta gyada masa, ya ciro wayarsa a aljihu yayi dialing number sannan ya
mika mata yace "In case u need anything sai ki kira number da nayi dialing
it's my other line" Nan ma dai kai kawai ta iya gyada masa, yace
"Good night Halysaah, pls kiyi bacci sosai, do not bother ur self kin
ji?" a hankali tace "Toh" kofa ya nufa ta bi sa da kallo sai da
ya bude kofar a hankali tace "Nagode" Ya juya ya sakar mata murmushi
yace "I gat ur back" Daga haka ya fita ya kullo mata kofar dakin,
Khaleesat ta ajiye wayar tasa da ya bata sannan ta zauna gefen gadon dakin a
hankali staring at the window absently. Har karfe dayan dare Khaleesat bata ji
ko digon bacci ya zo mata ba, tana dai kwance tayi lamo cikin duvet, her heart
is soo heavy, har wani zafi take jin yake mata, ga wani zazzabin da taji ya
lullubeta, tun da Jay ya bar ta take kuka, gani take kamar duniyar ya tsaya
mata ne cak, ta ma rasa wani kalan tunani zata yi, abubuwan da suka faru daxu
suka dinga dawo mata abun sai yake mata kamar mafarki, she wish mafarkin ne ma
kawai, yanzu babban tashin hankalinta bata san me zai faru a Nigeria ba, bata
san next step din Abdul ba, bata san me zai ma iyayenta ba, duk wannan tunanin
ya hadu yayi distabilizing dinta, zazzabin da take ji ya karu sosai, tana son
tashi taje tayi alwala tayi sallah ko zata samu sukuni amma ta kasa, duk
jikinta ciwo yake mata ga ciwon kai kamar kanta zai fashe, da taji azaban yayi
mata yawa kamar zata kira Housemate dinta ta tambayesa maganin ciwon kai amma
ta fasa don bata san ko bacci yake ba, haka tayi ta juye juye jikinta yayi zafi
sosai, yanda taga rana haka taga daren nan that was soo long to her, bacci ko
na barawo bai dauketa ba, jin vibration din da wayarsa yayi yasa tayi karfin
halin jawowa tana kallon screen taga alarm ne na karfe biyar, ta kashe alarm
din tana son tashi don tayi sallah amma ta kasa, daga karshe dai haka tayi
karfin hali ta daure ta tafi bandaki ta dauro alwalan, tana idar da sallan taji
zazzabin da yafi na baya ya lullubeta gaba daya, kwanciya tayi saman gado ta
rufe har kanta da duvet din. Wajen karfe takwas na safe Jay yayi knocking kofar
dakinta, tana ji amma ta kasa amsawa, sau uku yana knocking jin bata amsa ba
sai ya kira wayarsa dake wajenta nan ma tana kallon kiran amma ta kasa daga
hannu ma ta dau wayar, sai da ya katse sannan ya bude kofar dakin da sallama ya
shiga, yana kallonta da mamaki ya nufeta yace "Are you Okay
Halysaah?" Kai kawai ta girgiza masa, ya duka kusa da ita yace "Baki
da lafiya ne? Why didn't you call my line?" Hawaye ya gani idonta, yace
"Haba Halysaah, ba nace kar ki sa ma kanki damuwa ba? Did you want to hurt
ur self?" Ita dai bata ce komai ba, ya juya ya fita daga dakin, after some
minutes ya dawo da Hot chocolate ya ajiye mata yace "Ki daure ki sha pls,
let me get you medicine" Yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin, ko da
ya dawo ya ga bata tashi ba still, duk yanda yayi da ita ta tashi ta sha shayin
ya bata magani taki tashi, gaba daya ya ma rasa yanda zai yi da ita, can ya
kara dukawa kusa da ita yace "Did you have ur frnd safiyyah's number
offhand?" Da kyar ta girgiza masa kai, yace "U have her IG handle? Is
she active on IG?" Bata ce masa komai ba don ta ma kasa maganan, he look
confuse at this point, can dai yace "To zaki iya daurewa ki tashi mu tafi
asibiti?" Ta girgiza masa kai, mikewa yayi kawai ya fita daga dakin,
downstairs ya sauka don AJ na dinning yana breakfast ga Legend dinsa zaune Ιan
nesa da shi a dinning area din, Jay ya nufesa looking confuse yace "AJ,
the girl is seriously sick fa" AJ dake sipping tea dinsa yace "Which
girl?" Jay ya masa wani kallo yace "Please be serious AJ, wallahi
bata da lafiya sosai" AJ yace "To yanzu daukar ta zaka yi ka kai ta
Hospital kenan..." Jay yace "How?? ko tashi fa bata iya yi, plss ko
zaka mata allura ta Ιan samu relieve tukun?" A hankali AJ ya ajiye Mug din
hannunsa yana kallon Jay baya ko kiftawa, can ya matsar da shayin gabansa yace
"Amma dai don Allah me yasa ka raina ni haka ne Jay? Me nayi maka? Kai me
hannunka yake da bazaka mata allura ba sai ni?" On a serious note Ajay ke
masa tambayoyin nan looking at him and waiting for his answer, Jay yace
"Da gaske fa you are Heartless Junaid, ince maka yarinya ko tashi bata iya
yi? Why are you like this pls?" AJ yace "But like seriously kai uban me
hannunka yake da bazaka mata allura ba sai ni? Baka fi ni zama likita ba? Wato
ni ne Ιan iska ko?" Juyawa Jay yayi ya bar wajen ya koma sama, yana bude
kofar dakin ya ganta duke kusa da kofar bandaki, ya karasa kusa da ita da sauri
ganin yanda ta galabaita yace "Did you throw up?" Kai kawai ta gyada
masa tana maida numfashi, gun da ya ajiye hot chocolate din ya tafi ya dauko
mata yace "Pls ki sha ko kadan ne sai in baki magani" Ta girgiza masa
kai, yace "C'mon Halysaah, kadan fa za ki sha" Yana rike da cup din
don kar ya sakar mata ta zubar, a haka ta kurbi shayin kadan, sai da yasa ta
kara sha sannan ya ajiye shayin ya dauko magani, tana ganin maganin ta fara
girgiza masa kai da sauri don har taji wani aman zai taho mata, bude kofar
dakin aka yi Jay ya juya, AJ ya gani tsaye bakin kofar yana kallonsu, Jay bai
sake kallon inda yake ba ya maida dubansa kan Khaleesat yace "Pls ki daure
ki sha Halysaah, ko baki son ki samu relieve?" Kara girgiza masa kai tayi
hawaye ya fara sauka idonta, lallabata Jay ya fara yi akan ta sha maganin, AJ
ya wani hade rai yace "Kee baza ki amshi maganin da ake baki ba? Wa zaki
ba wahala?" Jay yace "Ba ruwanka pls AJ, get out" Ita dai
Khaleesat ko kallonsa bata yi ba tana fama da kanta, Jay bai sake takurata kan
ta sha maganin ba ya mike yace "Toh ki daure ki hau kan gado ki kwanta, i
am coming now" Ta gyada masa kai, ya juya ya nufi kofa, ko kallon Ajay bai
yi ba ya fita daga dakin, AJ ya tabe baki ya juya ya koma downstairs. Haka nan
Jay ya hado alluran da za mata don saukar mata da zazzabin, sai da ta ga ya
dawo dakin sannan ta daure ta koma saman gadon tana ganin jiri ta kwanta, ya
tsaya gefen gadon yana rike da alluran yana kallonta, ta marairaice ta girgiza
masa kai kawai alamar bata so, ya kwantar da murya yace "To ya kike son in
maki Halysaah? Kin ki shan magani" wayarsa dake aljihunsa ya ciro jin yana
ringing ganin Salem ke kiransa ya ajiye alluran hannunsa yace "I am coming
Halysaah" Fita yayi daga dakin, ya sauka downstairs ya tarar da Salem
zaune parlor, bayan sun gaisa Salem yace "Slide dina nake son zaka duba
min Jay" Shi dai AJ na zaune yana kallon kwallo ga Legend a gefensa, Jay
yace "Ohk, but tunda ka zo pls zaka yi injecting Housemate dita she is
sick" Salem yace "Ayya, shi sa ta kira jiya, Allah ya bata lafiya,
tana can gidan nata ne?" Jay yace "No, she is upstairs, mu je in nuna
maka dakin da take" A tare suka wuce sama, AJ dai kallonsa kawai yake a TV
kamar bai san suna parlon ba, Jay bai shiga dakin ba bayan ya nuna ma Salem ya
dawo downstairs ya zauna, Khaleesat bata yi ma Salem wani musu ba don ba ma ta
da wannan strength din duk da yanda bata son allura haka nan ta bari ya mata,
tsabar zazzabin dake jikinta ko zafin shigar alluran bata wani ji ba, Salem
yayi mata Allah ya sauwake sannan ya fita daga dakin ya koma downstairs, Jay
yace "Thank you, bari in duba maka" Sai bayan kusan minti talatin Jay
ya tafi dakin Khaleesat ya sameta tayi bacci, ya sauke ajiyar zuciya ya karasa
kusa da gadon ya kai hannu kusa da goshinta sai dai bai taΙa ta ba, nan yaji
temperature dinta ya fara sauka, juyawa yayi ya dau sauran shayin da ta bari ya
fita daga dakin..... Wajen karfe sha daya da rabi Khaleesat na kwance hannunta
rike da wayar Housemate dinta, tun 20 min ago ta tashi daga baccin da ya
dauketa daxu, she felt a bit relieved now da alluran da Salem yayi mata, sai
dai har sannan kanta bai daina mata ciwo ba kamar ta cire ta huta, tayi kokarin
ta tashi ma ta tafi bandaki amma ta kasa, she is so weak kamar warce ta dade
tana ciwo, hakan yasa kawai ta jawo wayar Jay, da har zata shiga gallery dinsa
to while away time amma sai taga it's not proper ta shiga hotunansa, hakan yasa
ta shiga wani game da ta gani kawai tana yi daga kwancen da take, bude kofar
dakin aka yi ta daga idonta, Jay ne ya shigo dakin AJ dake bayansa yaki karasowa
ciki ya tsaya daga bakin kofar, Jay ya nufota yace "Ashe kin tashi, how
are you feeling now Halysaah?" Ta gyada masa kai a hankali tace "Good
morning" Yace "Morning Housemate, are you feeling much better
now?" Kai kawai ta gyada masa, yace "Ohk bari a kawo maki breakfast,
idan kinyi sai ki daure ki sha magani kin ji" Ita dai bata ce masa komai
ba ya juya ya nufi kofa ya fita ya mika ma AJ wayarsa sannan ya sauka
downstairs zai kawo mata breakfast, shi dai AJ daga sama har kasa yake
kallonta, ta Ιan saci kallonsa to see if he is still standing by the door ko ya
tafi, hada ido suka yi ta dauke idonta tana ci gaba da game dinta da take,
after a while ta kara satan kallon bakin kofar taga ya bar wajen, sai ga Jay ya
shigo ya ajiye mata tray din breakfast ta dinga kallon plate din baked beans
irin na turawa a gefe da soyayyen kwai a gefe, with veggies, sai sausages, ga
cup din hot chocolate with few slices of bread a gefe su ma, ita dai tasan ba
iya cin wannan abincin zata yi ba, yana kallonta yace "Can you give me ur
frnd Safiyyah's Home address?" Ta sauke idonta ta gaya masa address din,
yace "Ohk, na ma san area din, i have a frnd there" Ita dai tayi
shiru, ya dauko mata maganin da taki sha daxu ya ajiye kusa da ita yace
"Pls ki daure kiyi breakfast din, sai ki sha drug din kafin in dawo"
A hankali tace "Toh nagode" ya mata murmushi ya juya ya fita daga
dakin ta bi sa da kallo. Jay ya tarar da AJ zaune a waje gurin shan iska dake
compound din yanna danna wayarsa, hakan yasa ya nufesa ya zauna kujeran dake
facing dinsa yace "AJ, i think i am confuse at this point, what do u
suggest about this young girl's issue?" AJ ya daga ido ya kalli Jay yace
"My suggestion is that... ka barta ta tafi duk inda ma zata ka cire
hannunka da bakinka cikin wannan case din babu abinda ya shafe ka, a cikin
kunnenka kaji tace shi gayen ne ke sponsoring dinta, babu kuma ta yanda zai yi
sponsoring dinta without the consent of her parent, kaga they are comfortable
with that, so who are you to intrude Jawwad? Baka san komai akan ta ko kan
saurayin ba don me zaka zakalkale haka? Tare fa ka gansu, da can baya zuwa
America din ya sameta ne a gidan? sai yanzu tasan yana molesting dinta? Girl's
can be very cunning fiye da tunaninka, don't start what u can't finish
Jawwad" Jay dake ta kallonsa yace "So now what are you
insinuating?" AJ yace "Since you are daft kar Allah ya sa ka gane
abinda nake insinuating" Jay dai
kallonsa kawai yake, after a while a hankali yace "But duba da abinda ya
faru tsakaninka da guy din kasan zai iya hurting dinta idan nace ta koma gidan
nan AJ, she is no longer safe in that apartment, ka dai ga ba ma cikakken
hankali ke gare gayen ba, ka duba fa wuka yaje ya dauko a kitchen" AJ ya
gyara zama yace "Sai kayi mata hanyar komawa gun iyayenta as the good
Samaritan that you are from Samaria, kaga in ta koma sai ta gaya ma iyayen nata
abinda ke faruwa da abinda selfishness dinsu ya ja mata a kasar mutane, sai su
yi sorting kansu a can kawai" Jay yace "Kar kace haka, we know
nothing about why they allowed him to sponsor their daughter, we shouldn't
judge them har sai mun san dalilinsu AJ" AJ yace "Dalilin banza, babu
responsible parent din da za su damka ma kato irin wannan mutumin er su ya kai
ta wata kasa da sunan karatu, it doesn't even make sense, sai kace ba musulmai
ba, ko da cousin brother dinta ne ma abun bai yi tsari ba balle babu ko wani
relationship na jini tsakaninsu, who does that" Jay ya sauke ajiyar zuciya
yace "Duk da haka dai ni bazan yi judging dinsu ba tare da nasan komai ba,
let give them benefit of doubt" AJ yace "Sai kayi ta basu ai, ni kam
bazan bayar ba" Jay yace "But komawarta Nigeria yanzu bazai yiwu ba
AJ, ba shine solution ba, Monday za su fara exams, John Hopkins university take
ita ma fa" AJ yayi dariya har da kyakyatawa yace "Tabb, lallai gayen
ya kashe kudi ba na wasa ba" Jay dai kallonsa kawai yake, AJ yace
"Toh za a fara exams me kake nufi kenan? Naji ka ce apartment din nata is
not safe for her anymore..." Jay yace "She will remain here har su
gama exam kafin ta koma Nigeria wajen iyayenta" AJ ya wani kallesa da
sauri yace "What do you mean? Kana nufin mu zauna gida daya da
balagaggiyar yarinya da ba muharramar mu ba kamar wasu jahilai marasu tsoron
Allah? Kai da wa za ku yi wannan nonsense din??" Jay yace "Duk yan
iskan turawan da kake kawowa gidan nan ka basu daki su zauna dama muharramanka
ne ban sani ba?" AJ yace "Turawa kace ai, kuma babu komai tsakanina
da su kai ma ka sani, i am only helping most of them tunda ba a garin nan suke
ba" Jay ya mike yace "Ita ma haka za mu yi helping dinta tunda ba a
garin take ba, take it or leave it" yana kai wa nan yayi wucewarsa inda
yayi parking motarsa, Ajay ya bi sa da wani kallo, can yace "Sai dai ku je
can ku biya wani apartment din ku zauna tare, babu wanda zai takurani a gidan
nan wallahi, dama ai kun saba zama gida daya tare, it's not a new thing, dole
ne sae ta zauna gidan nan cikinmu mu ba maguzawa ba" Shi dai Jay ya shiga
motarsa ya fita daga compound din ya kama hanyar gidansu Safiyyah....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
[5/20, 5:24 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Jay na isa
unguwan da gidansu Safiyyah yake sai ya mance apartment din da Khaleesat ta
gaya masa, hakan yasa ya kira wayarsa dake wajenta, Khaleesat na zaune saman
gado har sannan tana playing game da wayar, sosai gabanta ya fadi ta dinga
kallon screen din wayar ganin image din hotonsa da number da yayi appearing,
sai taga kamar shi din ne a gabanta take gani, sai da kiran ya katse ta zaro
ido bayan tayi realizing bata yi picking ba har ya katse, bayan few seconds ya sake
kira, dagawa tayi ta sa handsfree tayi shiru, yace "Halysaah" Tace
"Na'am" Yace "I think i forgot the apartment u told me"
Gaya masa ta sake yi yace "Thank you" Daga haka ya katse wayar ya ci
gaba da driving dinsa, dai dai gaban apartment din yayi parking don motar
Mustapha baya nan, yana tsaye bakin kofa yayi knocking gently, after a minute
aka bude kofar parlon, komawa baya Safiyyah tayi tana kallonsa da mamaki daga
sama har kasa, ya Ιan mata murmushi yace "Hi Safiyyah" Ta bude ido
sosai tana leka motarsa da taga yayi parking thinking may be he is together
with Khaleesat, ganin motar ba kowa ciki tace "Hi, good afternoon"
Yace "How are you doing Safiyyah?" Lokaci daya tace "Ko dai
Khaleesat bata da lafiya ne?" Da damuwa sosai tayi tambayar, Yace
"Yeah bata da lafiya" Tace "Wallahi yanzu na gama shiryawa nake
son in ci abinci inje gidan naga miss call dinta jiya ina ta kira har yau wayar
baya shiga, and i am disturb" Yace "Shi yasa na zo in dauke ki idan
ba damuwa so you can be together with her she is sick, probably idan kin mata
magana zata ci abinci ta sha magani" Da sauri Safiyyah tace "Sure,
bari in dauko gyalena" Juyawa tayi da sauri ta koma cikin gidan, shi kuma
ya koma parking space, Surayya dake zaune a parlon ta kasa kunne duk tana jin
conversation dinsu kafin Safiyyah ta shigo, Safiyyah ko kallon direction dinta
bata yi ba ta tafi dakinta da sauri ta dauko jakarta da gyale sai wayarta
sannan ta fice daga gidan, ganin Jay cikin motarsa yana jiranta ta bude gaban
motar ta shiga tana cewa "Tun jiya ne bata da lafiyan? Kuma me yasa ta
kashe wayarta?" Jay yace "Tace wayar ya fada ruwa ne" Safiyyah
tace "Ohk" Sai da suka dau hanya sannan Jay yace "Amma tana can
gidanmu fa, can za mu je yanzu" Safiyyah ta juya da sauri tana kallonsa da
mamaki tace "Gidanku? Why? What happened?" Calmly yace "Before
then za mu fara zuwa apartment dinmu sai ki dau mata kayanta da zata yi amfani
da shi, we left yesterday with nothing" Safiyyah bata sake cewa komai ba
tunani iri iri na yawo a ranta, to me ya faru? ta yaya Khaleesat da ta sani me
shegen taurin kai ta yarda har ta bi sa can gidan nasu? Ko dai rashin lafiyar
nata is critical ne haka? Da tunane tunanen nan suka isa apartment din, suka
shiga ciki tare da Jay ta nufi dakin Khaleesat shi kuma ya zauna a parlor, bayan
few minutes ta fito tace "Kala daya zan dau mata kayan ai ko?" Jay ya
mike yace "No, 3 to 4 will be okay" Duk da confusion din da Safiyyah
ta shiga bata dai ce masa komai ba ta juya ta koma cikin dakin, ta dau akwati
ta saka ma Khaleesat kayanta da duk abinda zata bukata a ciki, tana fitowa daga
dakin Jay ya mike yace "Kin dau mata duk abinda zata bukata?"
Safiyyah ta gyada masa kai, suka fita daga parlon, duk ta kagu taje wajen
Khaleesat ita dae, silently suka yi tafiyar har suka iso gidan, bayan Jay yayi
parking ya sauka Safiyyah ma ta sauka, ya fiddo akwatin sannan suka nufi
entrance din apartment din Safiyyah na biye da shi, bai ga motar AJ a gidan ba
alamar ya fita, suna haurawa sama Jay ya tafi dakin da Khaleesat take yayi
knocking, ya mika ma Safiyyah akwatin yace "Zaki iya shiga, zan je inyi
sallah" Safiyyah ta amshi box din tace "Ohk" Bude kofar dakin
tayi Khaleesat ta dinga kallonta har ta shigo, Safiyyah ta ajiye box din
hannunta ta nufeta da sauri tace "Me ya sameki Khaleesat?" A hankali
Khaleesat ta sauke idonta ta kasa cewa komai don bata ma san ta inda zata fara
ba, sai ga hawaye. Safiyyah na tsaye dakin kusa da window bayan Khaleesat ta
bata labarin duk abinda ya faru, tsabar yanda labarin ya kidima Safiyyah kasa
ci gaba da zama tayi gefen gadon, Safiyyah tayi shiru for almost 2 minute tana
tsaye jikin window tana girgiza kafa, ita dai Khaleesat goge hawayen dake sauka
idonta kawai take, can Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya me cike da takaici
tace "A baya da nake gaya maki Abdul Ιan daba ne ba kin maida maganata
abun wasa ba? Tunda uwata ta haifeni ban taΙa ganin Ιan iska kamar Abdul ba,
yanzu da baki samu lambar kowa ba haka zai lalata maki rayuwa babu digon tsoron
Allah a ransa? Ya kashe uban kudin zuwa USA kawai don ya zo yayi lalata? Innalillahi
wa inna ilaihi raji'un, amma naji haushi da Ιan uwan Housemate dinki bai sumar
da shi ba an maida sa Airport a haka, tirr da Abdul, tirr da halinsa, i am so
happy that things turn out this way, in sha Allahu karshensa ne ya zo a
rayuwarki" Khaleesat ta fashe da kuka tace "Sophie ban san next
action dinsa ba idan ya koma Nigeria, i am so restless" Safiyyah tace
"Next action dinsa? Sai ya koma ya gaya masu uban da ya kawosa USA da
Intention dinsa, ke in zaki dena wannan crocodile tears din naki ki dena don ba
tausayinki zan ji ba, tunda dai bai samu nasaran lalata maki rayuwa ba ni duk
abinda zai faru ma ya dade bai faru ba, kukan uban me kuma kike ma mutane? Ko
nasaran da bai samu a kanki bane ya dame ki? Kuma wallahi ya ci sa'ar baki
sameni a waya ba don kafin in karaso gidan sai 911 sun riga ni, tuni zan kirasu
ince gashi can za ayi fyade, banda iskanci duk karuwansa basu ishesa ba sai ya
zo ya kara dake? Gaskiya ki rike Housemate dinki da Ιan uwan nan nasa da kyau
don mutane ne su wallahi, da ba don su ba da yanzu wani zancen ake ba wannan
ba, don da na kai maki ruwan zafi yafi a kirga zuwa bandaki yanzu"
Khaleesat dai bata sake ce mata komai ba tana share hawayen da yaki tsaya mata,
Safiyyah ta rike haΙa har sannan tana mamakin Abdul, can tace "Kamar irin
ya zo wajen matar nan tasa, ni wallahi da yaji suka barbada masa mu ga ta
iskanci, shege kawai prostitute" Duk tashin hankalin da Khaleesat ke ciki
sai da tayi dariya don ita bata taΙa jin inda aka ce ma namiji prostitute ba
sai yau a bakin Sophie, Safiyyah tace "Ga dai katon daki an baki, kiyi
karatun exams dinki cikin kwanciyar hankali, nima in abun duniya ya isheni in
taho nan in sameki kafin dare yayi in koma den dina, don ko da wasa bazan ce ki
dawo gidanmu ba ni kaina ban tsira gun tsinanniyar matar Yaya Musty ba kuma
yaki kwatar min en ci, da zai bar ni ba nima sai in dawo nan kusa dake ba tunda
ba rasa abincin da za su bamu mu ci za su yi ba, wannan dakin ai ya ishemu
rayuwar America, bari kiji Khaleesat dama Allah ya riga ya rubuta Abdul ne
silan zuwan ki Amurka ki hadu da mutanen arzikin ki, babu me canza haka ko yaki
ko ya so dole sai ya kawoki ya hadaki da mutanen arzikin ki tunda Allah ya
rubuta haka, iya role dinsa kenan a rayuwarki, kuma Allah ne zai basa ladan
hakan bamu ba, ba shikenan ba?" Khaleesat dake ta kallonta ta girgiza mata
kai tace "Ni bazan zauna gidan nan ba Sophie" Safiyyah na mata wani
kallo tace "Ohk, Apartment din naki zaki koma ki kai ma Abdul din kanki
kenan?" Khaleesat ta sauke idonta kasa muryarta na rawa tace "Bazan
iya jarabawan ba Sophie, gwara kawai in koma gida, i want to go home, i want to
go to my mother" Safiyyah zata yi magana aka yi knocking kofar dakin,
Safiyyah ta amsa aka bude kofar Jay ya shigo, kallon Khaleesat yake yace
"Kin sha maganin Housemate?" Ta gyada masa kai without looking at
him, Safiyyah ta kallesa cike da damuwa tace "Ashe kuma iftila'in da ya
faru kenan jiya Yaya Housemate? To Allah Ubangiji ya tsare na gaba, ku kuma
Allah ya saka maku da alkhairi ya baku ladan hidimar da ku ke yi da kawata don
bata da kowa a garin nan sai Allah sai ni da ku, kuma she is not longer safe in
this state don Abdul can be cunning, azzalumi ne mugu, nasan har yanzu yana
labe garin nan bai tafi ba, kuma ba imani ne da shi ba ina jin tsoron next move
dinsa, Allah kadai yasan sau nawa ya koma apartment din nan yaga babu kowa
ciki" Jay dai ya Ιan yi murmushi yace "She will remain here har ta
gama exams dinta in sha Allah" Khaleesat ta kallesa ta girgiza kai cikin
sanyin murya tace "Bazan iya exam din ba, Nigeria nake son tafiya"
Safiyyah ta mata wani kallo kamar zata ce in tana da kudin jirgi ta tafi sai
dai kuma kawai tayi shiru tana hararanta, Jay ya kwantar da murya yace
"Saboda me baza ki iya exam ba Khaleesat, stop saying that pls, in sha
Allah zaki yi jarabawan ki lafiya, in kun gama sai ki koma Nigeria"
Safiyyah tace "Atoh shi dai na gani, kan wani tantirin Ιan iska take son
lalata future dinta, duka duka fa shekarar karshe za mu shiga yanzu a
makarantar" Khaleesat ta sauke idonta hawaye na sauka idonta don tasan
baza su gane abinda take nufi ba, Jay ya sauke ajiyar zuciya yace "Try
calming her down Safiyyah, and naga tun jiya bata wani ci abinci ba ban san ko
tafi son abincin Nigeria ne ba, nasa cook din gidan yayi ordering ingredient
din har an kawo, i don't know ko zaki girka mata a kitchen tunda kina nan"
Safiyyah tace "To ba damuwa, let me cook for her" Yace
"Alright" a tare suka bar dakin Khaleesat ta bi su da kallo hawaye na
bin fuskarta. Tunda suka shigo kitchen din Safiyyah ke bin ko ina da kallo don
the kitchen is so big and well equipped, irin modernize kitchen din nan, bayan
Jay ya fita cook din gidan ya nuna mata ingredients din shinkafa da miya sannan
shi ma ya fita, tuni ta hau girkin a kitchen din. Wajen karfe biyar Safiyyah na
daki tare da Khaleesat hira kawai take mata kamar ba abinda ya faru, ita dai
Khaleesat tayi shiru tana kallonta amma gaba daya hankalinta baya kan hiran,
wayar Safiyyah ya fara ring ta jawo jakarta ta ciro wayar ganin Mustapha ke
kiranta ta wani turo baki sannan tayi pick ta sa handsfree tace "Ina wuni
yaya" Ko amsa gaisuwar bai yi ba yace "Waye ya zo ya daukeki a mota
Safiyyah?" Safiyyah ta bude baki tace "Ohh haka matar taka tace maka?
to ta manta a jirgi aka zo aka daukeni ba a mota ba, kuma munafurcinta zai kare
mata wallahi" Tsawa ya daka mata yace "Ina maki magana kina min
maganar banza? Are you okay?" Ta wani murguda baki tace "Toh ba ina
hanya bane wai, haka kawai dai babu dalili bazan kama hanya in fito cikin
sanyin nan ba yaya, ko ka manta jibi za mu fara exams ne?" Kashe wayarsa
yayi, Safiyyah tace "Allah dai ya tsine ma Surayya albarka, kuma wallahi
kafin mu gama exam mu bar kasar nan sai na mata abinda bazata taΙa mantawa ba a
rayuwarta, ko da wasa kuma bazan ma gaya masa abinda ya faru dake ba kar yayi
burgan cewa ki dawo gidansa ya kara ma matarsa extra nama" Ita dai
Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah ta mike ta dau jakarta da gyale
tace "Sai na zo gobe in sha Allahu, saura kar ki karasa cinye abincin ki
zauna kina asaran hawayenki akan Ιan daba, ga lambata na sa maki a waya in da
wani abu ko kuma kina bukatar komai kawai ki kirani" Daga haka ta fice
daga dakin, Khaleesat ta sauke idonta kasa, Downstairs Safiyyah ta hadu da AJ
wanda shigowarsa gidan kenan tana Ιan murmushi ta gaishesa ya tsaya ya amsa
yana danna wayarsa yace "How are you doing" Tace "Alhmdlh ya
karatu" Yace "Fine, ya naki" Tace "Muna ta fafatawa dai, to
fa mun gode da hidima yaya, Allah ya saka da alkhairi da abinda ku ka ma
kawata, Allah ya biya ku" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta jin wai tana
masa godiya, ita dai ta ci gaba da godiyar ta ba kakkautawa, Yace
"Ameen" Tace "Yaya Housemate din ya fita ne, ni zan koma gida ne
yanxu" Sai ga Jay ya shigo parlon from outside, ganinta yace "Ohk
zaki koma Safiyyah?" Tace "Eh wallahi yamma tayi amma in sha Allahu
zan shigo gobe da safe" Yace "To Allah ya kai mu, mu je inyi dropping
dinki" Tuni AJ yayi wucewarsa sama, Safiyyah ta bi bayan Jay suka fita
daga parlon tana mamakin inda karen gidan yake bata gansa ba tun daxu, sai
bayan da suka dau hanya tace "Yaya Housemate...." Dariya ta ba Jay
bai jira me zata ce ba yace "I am Jawwad Safiyyah" Tace "To ni
dai don Allah kayi dubara ka amshe wayar da ka ba Khaleesat kar taje ta kira
yan gidansu su gigita ta, kaga bamu san ko Abdul din na kasar nan ba ko ya koma
Nigeria, in ta kira suka gaya mata wani maganar da kyar ta iya abun arziki a
jarabawan nan" Jay yayi shiru cause he reason with what Safiyyah is
saying, can yace "Haka ne kuma, i will tell her not to speak to anyone for
now, amma bazan iya amsan wayar ba naga kamar it's whiling away her time"
Safiyyah tace "To in da kati a wayar don Allah ka kone sa, in da WhatsApp
kayi uninstalling dinsa kaga ta haka babu wanda zata ma magana, the exams is
just for a few weeks, kamar gobe ne za mu gama" Yace "Sure i will do
so Safiyyah" A haka suka isa gidansu ta sauka daga motar ta masa godiya
yace "Ki gaida mutanen gidan" Tace "To za su ji" Yayi
reverse ya dau hanyar gida hoping Khaleesat bata riga ta ma kowa magana back in
Nigeria ba. Washegari da safe Jay yayi booking appointment na ganin likita
saboda daren ranan ma Khaleesat dai bata yi bacci ba, yasan dai ba lallai su
samu ganin likitan a ranan ba, so he was just helping her to manage her self
with the drugs available, da Safiyyah kuma ta zo sai taji ta nemi zazzabin ta
rasa dama kadaici ne da damuwa suka mata yawa. Ranan monday da safe Jay yayi
dropping din Khaleesat school for her first exam, and he stayed behind har zuwa
sanda za su gama don su koma gida tare, kawai shi dai baya son barin ta ita
kadai, Jay is trying his very best na ganin Khaleesat ta sake ranta domin tayi
karatun jarabawanta da kyau kar ta samu matsala, ga kuma Safiyyah dake
encouraging dinta a gefe ita ma, kuma hakan yayi tasiri sosai don ta Ιan sake
ranta tana karatun, AJ dai tun ranan da ya shigo ya ganta zaune a daki har
bayan da suka yi Exams uku bata sake saka shi a ido ba, bata san ko yana gidan
ba ma ko baya gidan, ita dai 24/7 tana daki, hatta abinci cook din gidan ne ke
kai mata sama yayi knocking ta fito ta amsa, in ta gama still shi yake zuwa ya
amshi tray din, bayan sati biyu da fara exam dinsu ranan suna da interval
Safiyyah ta zo gidan da yamma, abinci ta kawo ma Khaleesat, Khaleesat taji dadi
sosai ganin tuwo ne don dama tun jiya take sha'awan tuwon, Safiyyah tace
"Kinga ba dadewa zan yi ba yanzu zan tafi kafin mutumin can ya fara kirana
kamar Surayya ce ta bar gida" A hankali Khaleesat tace "Baza ki bari
anjima kadan ba pls" Safiyyah tace "Wallahi yanzu Ya Mustapha zai
fara kirana, bai ma san na fito ba, kuma nayi order din Lyft ma da zai maidani
gashi nan ya kusa karasowa nan, tashi ki rakani kofar gida" Khaleesat ta
girgiza kai tace "Kawai ki tafi za mu hadu schl tomorrow in sha
Allah" Safiyyah tace "Wai ke baki gajiya da zama ke kadai a daki, don
Allah ni dai tashi ki rakani kema ki Ιan yi strolling kafafuwanki" a
hankali Khaleesat tace "Baza ki gane ba Sophie, wallahi i am not
comfortable staying in this house, na kagu mu gama jarabawan nan in koma
Nigeria" Safiyyah tace "Ae ranan Housemate dinki ya gaya min wai kince
masa zaki koma apartment dinki nace lallai baki da hankali, Allah ma yasa Abdul
bai sake gidan ba" Tana dariya ta kare maganar, sai kuma ta kwantar da
murya tace "Kiyi hakuri kawata, nan da sati kadan zaki ga mun gama exams
din in sha Allah, ki kwantar da hankalinki pls, yanzu dai tashi ki rakani"
a hankali Khaleesat ta sauko daga kan gadon ta dau gyalenta suka fita dakin
tare da Safiyyah, suna saukowa downstairs suka tarar da AJ a parlor da Jay,
Khaleesat dai ta sunkuyar da kanta don sai yau taga AJ for almost 2 weeks, ita
ta zata ma baya gidan ne, Jay na kallon Safiyyah yace "Are you going soon
Safiyyah?" Safiyyah tace "Eh wallahi Yaya Jawwad Lyft dina yana hanya
ya kusa" Yace "Alright, ki gaida mutanen gidan" Tace "In
sha Allah za su ji" Sallama tayi ma AJ ya amsa mata, sannan ta kama hannun
Khaleesat suka fita daga parlon, suna tsaye waje suna jiran karasowar Lyft wata
mota ta shiga gidan bayan matukin motar ya fito daga cikin motar ya bude gate,
Safiyyah tayi kasa da murya bayan sun shiga ciki tace "Ke kinga wani Ride
me suna ride Khaleesat? Su dai da masu kudi kawai suke harkar su a kasar nan,
in kin bibiya abokansu ne 'ya yan masu kudi irinsu" Khaleesat dai bata ce
komai ba, bayan kusan minti uku sai ga Lyft din Safiyyah ya iso, Safiyyah ta
bude bayan motar ta shiga, Khaleesat ta daga mata hannu, Safiyyah na mata
murmushi tace "Sai mun hadu a schl
kawata, kiyi karatu da kyau fa" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata
sannan ta koma cikin gidan, duk a dar dar take tafiya a babban compound din
gidan, har yau ita dai ta kasa sakin jiki a gidan nan gani take kamar a kaya ma
take she is so very uncomfortable, a haka ta isa parlon gidan ganin baki biyu
dake parlon tare da su Jay wanda da alama abokansu ne Khaleesat ta sauke kai ta
gaishesu, suka amsa da fara'a, ita dai ta nufi stairs, daya daga frnds din nasu
taji yace "Bakuwa ku ka yi a gidan" AJ dake shan fruit salad yace
"Eh, yarinyar wani abokinmu ne a Nigeria ta zo jarabawa" Jay ya saki
baki yana kallon AJ da ke ta shan fruit salad dinsa ko ajikinsa, Ita kanta Khaleesat
sai da ta Ιan juya ta kallesa sannan ta wuce sama, abokin na gyara zama yace
"Waow, amma da gani da wuri abokin nan naku yayi aure, ya huta abunsa
gashi mu duk mun kasa har yanzu" AJ dai ya ci gaba da shan fruit salad
dinsa yace "Ai kam ya huta, mu ma da munyi auren da wuri duk da mun haifi
kamarta ai"
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
[5/21, 6:02 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat na
zaune da daddare tana duba course din da za su yi washegari a laptop dinta,
sosai take kewan Ummanta tasan kilan tana ta mata magana ta WhatsApp taji
shiru, she just pray everything is alright back home in Nigeria, duk in wannan
tunanin ya fado mata sai taji ta kasa karatu, haka nan dai ta tsura ma laptop
dinta ido, knocking din kofar dakin aka yi ta mike a hankali ta karasa gun
kofar ta bude don tasan Jay ne, sau da yawa sai dai yayi mata knocking bai fiye
shigowa dakin ba, daga nan bakin kofa yake tsayawa yayi mata duk maganar da zai
mata, yana kallonta bayan ta bude kofar yace "Are you sure u are studying
for ur next course Halysaah?" Ta gyada masa kai tana kallonsa, ya Ιan
jingina da bangon wajen yace "Erm, sorry about what you overheard AJ
saying few hours ago Halysaah, kinga dalilin da yasa nake barin masa gidan shi
kadai ya karata kenan, he is a serious nuisance... Kiyi hakuri da abinda yace
kin ji Housemate?" Khaleesat ta Ιan yi murmushi tana wasa da gefen
gyalenta kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "Ai ni ban ma san tsoho
bane sai yau" Jay couldn't help it but laugh out loud, Khaleesat ta daga
idanuwanta tace "Allah kuwa ban san shi tsoho bane, don wanda ya isa
haifata ai tsoho ne" akan kunne AJ da ya fito daga parlon dake sama, tsaye
yayi yana kallonta, tana hada ido da shi ta kulle kofar dakin gbamm, AJ ya
kalli Jay dake ta dariya, can ya juya fuuu ya bar wajen, Jay dai ya bi sa da
kallo still laughing, har ransa yaji dadin abinda Khaleesat tace akan kunne
Ajayn. Jay na dakinsa wajen karfe goma da rabi yana duba laptop dinsa AJ ya
shigo dakin, sau daya ya kallesa ya ci gaba da abinda yake, AJ yace "That
brat will not continue staying in this house anymore, ka samar mata wani
alternative kawai in ba haka ba in kira gida in fada masu ka kawo mana yarinya
tana rayuwa cikin gidan nan" Jay ya daga kai ya kallesa yace "Ni ai
na zata har ka kira ka gaya masu, kuma tunda ba gidanka bane baka isa kace
bazata zauna ta gama exams dinta ba" AJ yace "Ohk zaka sha
mamaki" Daga haka ya fice daga dakin, Jay ya ja tsaki ya ci gaba da abinda
yake. Washegari tare Jay ya dauko Khaleesat da Safiyyah ya kawo su nan gida
bayan sun gama exams din ranan, bai shiga compound din ba ya tsaya a waje yace
"I will be going out now, sai na dawo later" Khaleesat ta sauka daga
motar tana kallonsa, a duk sanda baya gidan sai taji gidan duk babu dadi, duk
da ko yana nan yawanci yana dakinsa sai in da wani abu ne yake zuwa kofar
dakinta ya mata magana, but she prefer him to be at home always ko da baza su
ga juna ba, duk sanda ya fita sai ta shiga kadaici wani lkcn har da damuwa,
kuma in dai zai fita din sai ya gaya mata zai fita, yau kam she felt relieved
tunda tare suka dawo gidan da Safiyyah, yana kallonta yace "Zan kiyi girkin
yau tunda ga kawarki sai ta taya ki?" Khaleesat ta sauke idonta tace
"Ohk" Yace "Alright take care" ta gyada masa kai ya ja
motarsa ya wuce, ita da Safiyyah suka shiga gidan, Safiyyah tace "Kai na
dade banga mutumin me kirki irin bawan Allahn nan ba, he is just extra nice, ni
dai Allah ya sa it's what i am thinking" Khaleesat ta kalleta, Safiyyah ta
washe maki tana wani murmushi, Khaleesat taki tanka ta, Safiyyah tace
"Kinga kamar jiya muka fara exams gashi saura mana course biyu mu gama,
baki ga farin cikin da nake ba za mu koma gida" Suna shiga parlon gidan
suka ga AJ a zaune da kare a gefensa, sosai gaban Khaleesat ya fadi don tun da
ta zo gidan ita dai bata ga karen da idonta ba sai da taji haushinsa wani lkcn,
karen ya mike tsaye yana kallonsu AJ ya masa umarnin ya koma ya zauna, tuni
Khaleesat tayi wucewarta sama, Safiyyah ta tsaya ta gaida AJ da fara'arta, ya
amsa yace "How was ur exam?" Tace "Alhamdulillah, sauran mu
kwara biyu, kawai intervals din ne ke da tsayi" AJ yace "Allah ya
bada sa'a" Tace "Ameen" Daga haka ta wuce sama, dakin da
Khaleesat take ta shiga, ta rike haΙa tana kallonta tace "Ni fa karfin
halinki mamaki yake ban Khaleesat, ya kina gidan mutane zaki zo ki wani wucesa
babu gaisuwa? Me yasa kike yin haka ne?" Khaleesat ta cire mayafinta without
looking at her tace "Don baki ji abinda yayi min bane jiya, frnds dinsa
suka zo gidan yace masu ai ni yarinyar abokinsa ce na zo exam" Safiyyah ta
kyalkyale da dariya har da kyakyatawa tace "To meye a ciki, in bai fadi
haka ba so kike su yi zaton zaman kanki kike cikin maza? Ai nan kare maki
mutunci yayi, kinga dai ai abokan za su yi tunanin baban naki ne da kansa ya
kawo ki gidan abokansa ki zauna kiyi exams" Khaleesat ta wani kalleta tayi
shigewarta bandaki, Safiyyah ta zauna gefen gado tana kyakyala dariya tace
"To duka duka shekararki nawa da bazai ce ke 'yar su bace, ni dai ban ga
laifinsa ba" Bayan duk sun yi sallah Safiyyah tace "Kin ga ki tashi
mu je in taya ki girkin kafin mutumin can ya fara doka min kira yanzu kamar
makaho" a hankali Khaleesat tace "Ni kamar ma kar inyi girkin, i
don't want to go downstairs" Safiyyah tace "Amma ai ko don saboda
Housemate dinki sai kiyi, tunda kika ga haka kilan shi ma yana son cin tuwon da
vegetable soup ne" Khaleesat ta marairaice tace "To ai ni i am not
comfortable ne, ban ma taba shiga kitchen din ba fa" Safiyya ta mike tace
"Mu je, ai ni na taΙa shiga har nayi girki" A haka ta ja Khaleesat
suka sauka downstairs, da ba don Safiyyah tace kilan Housemate dinta na son cin
abincin ba da babu abinda zai sa ma ta yarda tayi girkin, har sannan AJ na
parlon amma babu karen a kusa da shi, shi dai wayarsa kawai yake dannawa bai
kalli direction dinsu ba, a haka Safiyyah ta ja ta har zuwa kitchen din gidan,
after a while suka gama girkin, Safiyyah tayi take away din wanda zata tafi da
shi gida tana kallon Khaleesat tace "Ke ba yanzu zaki ci abincin bane naga
baki zuba ba?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Sai anjima"
Safiyyah ta tabe baki tace "To mu je, Allah dai ya sa Yaya Musty bai
kirani ba" Suna fitowa main parlor suka tarar babu kowa a parlon, suka
haura sama, kafin su karasa hanyar dakin da Khaleesat take aka bude kofar wani
Bedroom din wata mace da bazata wuce 23 years ba ta fito, English dressing ne
jikinta amma kana ganinta kaga Hausa Fulani, she is so beautiful, yarinyar ta
bi su da kallo da mamaki, Safiyyah na murmushi tace "Hi dear"
Yarinyar ta mayar mata murmushin tace "Hlo" Ita dai Khaleesat ta
dauke kai tana biye da Safiyyah suka tafi dakin da take, Safiyyah ta kulle
kofar ta dora hannu a ka tace "Na shiga uku, ke yanzu Khaleesat me yasa
baza ki daina abu kamar warce bata waye ba? Mun ga yarinya ta fito daga daki
kika san ko gidansu ne maimakon kice mata Hi kamar yanda kika ga nayi amma kika
wani yi shiru kamar kurma kina bin ta da ido?" Innocently Khaleesat tace
"To ai naga bamu santa bane" A fusace Safiyyah tace "Gaskiya na
gaji da halin ki, ke ko ina sai kin sa an mana kallon en kauye? Ki ga yarinya
er gayu wayayyiya abinda kema wayancewa zaki yi yanda nayi ki ce mata Hi, to
meye amfanin ilimin in baka iya zaman duniya da kowa ba? Ko Ιan uwan nan nasa
da kike complain a kai kece baki iya siyasar zama da shi ba, ba gashi ni yana
kulani ba har da tambayata ya exams, gaskiya ki canza hali Khaleesat, ya ci ace
kin yi koyi da ni akan abubuwa da yawa" Khaleesat dai bata tanka ta ba,
Safiyyah tace "Duk sai kika sa kunya ya kama ni tsamo tsamo, yanzu zata su
kuma wa ennan en kauyen daga ina" Safiyyah ta dau jakarta tana ciro
wayarta taga miss calls din Mustapha tace "Ahaf ai na sani" Tsaki ta
ja ta fara kokarin order din ride din da zai maida ta gida. AJ ya bude kofar
dakinsa jin ana knocking, tana kallonsa daga inda take tsaye ba tare da taje
kusa kusa da kofar ba tana Ιan kame kame tace "Ya Ajay, naga wasu mata ne
a gidan, kun yi baki ne?" AJ ya gyara tsayuwarsa yace "Ohk, su
nawa?" Ta Ιan bude manyan idanuwanta tace "Su biyu" Ya gyada kai
yace "Good, you saw the fair Slim one that is like yellow pawpaw?"
Yarinyar tace "Sure" Yace "To sabuwar budurwar saurayinki ce,
all of a sudden ya tattaro ta ya dawo da ita gidan nan suke zama tare, when i
said i am reporting him back home he threatened me" The lady look totally
speechless and confuse, a hankali tace "Budurwarsa kuma Ya Ajay?" Ya
wani hade rai yace "Ina wasa da ke ne balle in maki karya?" Shiru
tayi bata ce komai ba ta sauke idonta kasa, yace "She's been in this house
for 3 weeks now, ya kai ta school ya dawo da ita" Yarinyar ta sake daga
ido ta kallesa, AJ ya daga kafada ya kulle kofarsa, juyawa tayi tana tafiya a
hankali ta bar wajen. Har waje Khaleesat ta raka Safiyyah bayan ta takurata ta
rakata, sai ma da suka jira Lyft din ya karaso sannan Safiyyah ta shiga ta mata
sallama, Khaleesat ta daga mata hannu sannan ta juya ta koma cikin gidan, zaune
ta ga yarinyar daxu a parlor, suna hada ido Khaleesat ta sauke kanta sai ta
kasa wuce sai da tace mata "Hi, i am Khaleesat" Ido kawai yarinyar ta
zuba mata tana kallonta babu yabo babu fallasa kuma babu alamar zata amsa mata,
hakan yasa Khaleesat ta fara tafiya ta wuce sama, lkci daya jikinta yayi sanyi
ta shiga dakin da take ciki ta kulle. AJ ya fito dakinsa zai sauka downstairs
kenan sai ga Jay ya hauro sama fixgosa yayi a fusace yace "Are you out of
ur senses Junaid, what did u just do?" AJ yace "Ban gane what did i
just do ba, Hadeeyah came, she requested to know the lady she saw in this
house, kai kuma baka isa inyi karya saboda kare ka ba tunda ba tsoronka nake ji
ba, when i told u to look for another alternative for the brat ai mayar dani
mahaukaci kayi" Bude kofar wani daki aka yi sai ga Hadeeyar ta fito da Handbag
dinta, Jay ya sake AJ, ya bi ta da kallo yace "Hadeeyah" ko juyawa
bata yi ba ta ci gaba da sauka downstairs, ita dai tasan AJ ba wasa yake yi da
ita ba balle yayi mata karya, yaushe ma ya sake maka fuska balle ya maka karya,
Jay yace "Look Hadeeyah, ko da wasa kika ce zaki ma people back home
wannan magana i won't take it likely with you, and that will be the end between
me and you, cause u never gave me a listening ear" Sai a sannan ta juyo
tace "And so effing what? Wannan ne dalilin da yasa all this days baka da
lokacina dama ko Ya Jawwad? I am not surprise" Tana kai wa nan ta sauka ta
nufi hanyar fita gidan, Jay ya kalli AJ da ya daga kafada shima yana kallonsa.
Jay wasn't even that bordered kamar babu abinda ya faru, amma gaba daya ya fita
harkan AJ a gidan, ko kallon inda yake baya yi, ya canza code din kofar dakinsa
ta yanda ma bazai shigo masa daki ba, yasan ba lallai ma Hadeeyah ta gaya ma
yan gida komai ba, she won't even dare try that, amma still yaki ko da kiranta
a waya, dama ita ce me kiran nasa, daga Oxford University take kuma bata ma ce
masa zata shigo Maryland ba she just came without notice, ita ko Khaleesat bata
ma san abinda ke faruwa a gidan ba amma abinda Hadeeyah ta mata ya tsaya mata a
rai. Ranan friday Khaleesat suka yi second to the last exam dinsu, na karshen
kuma za su yi ranan talata, gaba daya ta kagu su gama ta bar kasar zuwa sannan
hankalinta yayi gida, she just want to go home, duk da tasan Housemate dinta
zai ce zai siya mata flight ticket amma gani take she is just a burden to him,
for weeks now hidima kawai yake da ita, ya kai ta schl, at times ya jira ta
gama jarabawa ya maidota gida, wani lkcn dab da sanda yasan zata fito exam zai
koma schl din don daukota, he really tried for her during this period and he is
always making sure that she is fine, bata ma san ta inda zata fara appreciating
din shi da Safiyyah ba, they where by her side all through, ba don su ba da
bazata iya jarabawan ba ma, yau kam tunda ta tashi take jin ta wani iri tana
dai kwance da tunani iri iri a ranta, ji take kamar ta jawo monday. AJ na zaune
reading nook din dake parlor yana kokarin hada references dinsa a laptop dinsa,
ga textbooks kaca kaca a gabansa, gaba daya Jay ya bi ya goge duk wanda ya tura
masa ta WhatsApp, infact duk wani abu da Jay yasan AJ zai karu da shi na
bangaren PhD da suke sai da yabi ya goge tas, shi da AJ bai nuna masa ma yasan
abinda yayi ba, shi yasa ya dukufa tun asuba yake reading nook, Ιaga kai yayi
bayan yayi perceiving din wani turare da ya gauraye ko ina na parlon, he was a
bit shock ganin wanda ya shigo parlon tare da wasu mutane biyu suna biye da
shi, ya sauke idonsa, he was surprise and shock, sai kuma ya mike ya dawo cikin
parlon, ya Ιan dukar da kansa yace "Sannu da zuwa Abba" Wanda ya kira
da Abba yace "Ya karatun? Ina Ahmad?" AJ yace "He is upstairs,
Abba surprise visit ka mana" Zaunawa Abban yayi saman kujera yana amsa
gaisuwan da ma'aikatan gidan ke masa cike da ladabi sannan ya kalli AJ yace
"I just branched to check on u both, daga England mu ke munje wani
taro" AJ dai ya sunkuyar da kansa, sai kuma ga wata mata da bazata wuce 50
ba cikin shiga ta alfarma ta shigo parlon da wata yarinya that is 16 years old,
AJ dai ya shafa kansa don shi abun ma dariya ya fara basa, ya dai gaisheta ta
amsa, yarinyar ta tafi ta rungumesa tace "Ya AJ naga ka zama kato, are you
going to the Gym?" Matar da suka shigo tare ta nemi waje ta zauna tace
"Allah sa karatun yake" Wani kallo ya mata ta gefen ido ya wuce sama
su kuma masu aikin gidan suka tafi dauko bottle water da lemo, direct dakin Jay
ya nufa a dai lkcn da Jay ya bude kofar dakinsa ya fito, AJ yayi wata dariyar
bosawa yace "Wallahi ga Abba da Aunty a parlor" Jay ya dinga kallonsa
babu ko kiftawa, can yace "Abba da Aunty kuma?" AJ couldn't stop
laughing, Jay ya Ιan leka downstairs yaga da gaske ne, buda baki yayi yana
kallon AJ da ya kasa daina dariya, Jay ya sauke ajiyar zuciya ya jawosa yace
"Look, let's talk pls Ajay...." Ajay yace "Talk about what? Ba
dai baka jin maganata ba, zaka san yanda zaka yi da yarinyar nan yau, kaga ban
ma kai report ba sun zo da kansu za su gane ma idonsu rayuwar da ka jefa kanka
a Maryland" Jay dai kallonsa kawai yake, AJ ya daga kafada irin ko a
jikinsa din nan ya sauka downstairs yana murmushi, Jay ya fi minti biyu tsaye
thinking of what yo do, daga karshe dai ya nufi bangaren AJ, yana tura kofar
dakinsa yaji dakin a bude, juyawa yayi ya tafi dakin da Khaleesat take yayi
knocking, duk da ba bacci take ba amma idonta a kulle, ta bude idonta ta mike
zaune sai gashi ya shigo dakin, Calmly yace "Bacci kike ne Halysaah?"
Ta girgiza masa kai tace "A'a" yana kallonta yace "Ya na ganki
haka ko baki da lafiya ne?" Nan ma ta girgiza masa kai tayi shiru, ya
kwantar da murya yace "Gaya min gaskiya, ko dai tunani kike Housemate?"
Calmly yake mata maganar kamar ba komai, ta Ιan yi murmushi cikin sanyin murya
tace "A'a" Yace "Good, i think we have visitors a gidan nan yau,
i will change you to another room wanda babu wanda yake shiga zuwa har sanda za
su tafi, nasan baza su wuce kwana biyu ba bakin za su tafi in sha Allah"
Ita dai tayi shiru tana kallonsa, ya sakar mata murmushi, ta sunkuyar da kanta,
yace "Alright, ta so mu je ko?" Sauka tayi daga kan gadon ta dau
gyalenta, yace "I will bring you all u need to the room afterward"
daga haka ya nufi kofa tana biye da shi, direct ya nufi bangaren AJ da ita, ya
bude kofar dakin yana kallonta yace "Here" ta sauke idonta tana
kallon cikin dakin dake wani kamshi na musamman sannan ta shiga, ko da wasa
bata san dakin AJ bane, Jay yace "I will be back soon Halysaah" Ta
gyada masa kai, ya jawo kofar sai dai bai kulle ba tunda bai san code dinsa ba
yanzu, sai bayan da ya bar wajen yaji dariya ya taho masa, to yanzu ta ina ma
zai fara lallaba AJ, kawai yasan ya ma gama kashe AJ, to in ba haka ba bai san
way out ba don bangaren AJ ne kadai Halysaah zata tsaya da babu wanda zai san
tana gidan tunda babu me zuwa ko kusa da bangaren nasa sanin halinsa, amma kaf
din gidan yasan Aunty sai ta bude ta shiga banda part din AJ, downstairs ya
sauka da sauri don zuwa gaida su Abba, Khaleesat dai ta kasa daina bin dakin da
kallo, komai na cikin dakin fari ne kal har wani kyalli yake tsabar neatness,
ita abun yana mata kamar dakin wani important person ne a gidan Jay ya kawota,
ta karasa ta zauna gefen gadon a hankali, she just don't know why she is not
comfortable with the room. Jay dai na zaune parlor ne amma gaba daya hankalinsa
na kan AJ dake ta shan fruit din da aka kawo ma Abba hankali kwance kamar shi
aka kawo ma, Aunty kuwa tana dakin Abba dake nan downstairs tana gyara masa, AJ
ya mike zai tafi sama, Jay na ganin haka ya mike ya bi bayansa da sauri, bayan
sun haura sama Jay yace "Hey let's talk AJ" AJ ya wani kallesa, sai
kuma yayi wani dariyar shakiyanci yace "Talk about what? Pls sort ur self
out, ka daina ma involving dina a crime din nan da ka aikata, kar a zata tare
muka aikata" Jay dai ya fara kokarin danne dariyar da ya taho masa don bai
ma san ta inda zai fara masa bayani ba.
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
[5/22, 6:50 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Parlon dake
sama Jay ya ja AJ zuwa can yace "Ohk now, let me explain Bruh" AJ na
girgiza kai yace "I am not interested pls Jay, ni fa bana son ma kana min
magana a gidan nan kar ayi zaton tare mu ka kawota" Jay yace
"Naji.... bayan yanzu bazan sake maka magana ba, kawai dai na duba naga
duk gidan nan dakin ka ne kadai yake da wahalan shiga..." Nan da nan AJ ya
hade girar sama da ta kasa yana kallonsa yace "I don't understand, me yasa
kake using dakina kake misali? What are you insinuating? What is ur
point??" Jay ya shafa sumar kansa a hankali yace "My point is, na kai
Housemate dita dakin ka for the meantime before i find a way out, nasan can ne
kadai su Aunty baza su ganta ba, tunda dakin ka out of bound ne" Haka AJ
yayi dropping jaw yana kallon Jay baya ko kiftawa with shock written all over
his face, Jay ya sosa kansa zai yi magana suka ji muryar Hajiya Rukayya warce
suke kira da Aunty, ta karaso parlon tace "Jay ka je Abbanku na magana a
parlor" Jay yace "To gani nan zuwa Aunty" Ta Ιan kalli AJ sannan
ta juya ta bar parlon, Jay ya sauke ajiyar zuciya yana kallon AJ that was still
looking at him ko kwakkwaran motsi baya yi, da alama ya ma kasa cewa komai, Jay
yayi patting Ιin shoulder dinsa yace "I know u gat my back Bruh, you won't
love seeing Abba Mad at me" Yana fadin haka ya juya ya bi bayan Aunty yana
sauke wani ajiyar zuciya, after almost 15 mins Jay ya dawo sama, zaune ya tarda
AJ a parlon dake sama ya tallabi chin dinsa da duk hannunsa biyu yana girgiza
kafa, he looks restless, Jay dai ya danne dariyar da ya taho masa da kamar zai
juya ya koma downstairs, AJ na ganinsa ya mike ya nufesa a fusace ya fixgosa
yace "What offense have i done to you Jawwad? Why my room? Why will u take
her to my privacy, my own comfort zone, what sort of nonsense is this plss?
Dakina fa? Meye hadina da ita zaka kai ta har Bedroom dina?" AJ was so mad
at him, nan da nan idonsa suka sauya launi, Jay yace "To Abba dai na kiran
ka, je ka dawo sai ka ci gaba" AJ dai sai kallonsa yake yana huci, can ya
turasa ya bar parlon kamar zai tashi sama, Jay ya wara ido yana shafa kansa
yana Ιan murmushi, karkari dai iya abinda zai yi kenan bazai wuce haka ba, kuma
ba wani kiransa da Abba yake yi kawai wahala ne bai so yasa yace masa ana
kiransa downstairs, dakin Khaleesat ya koma ya dauko mata box dinta da abubuwan
da yasan zata yi needing ya kai dakin AJ, Khaleesat ta mike da sauri ganinsa, a
hankali tace "But Housemate i am not comfortable in this room" ya Ιan
bude ido yace "Why? Meye da dakin Halysaah?" Tayi shiru bata ce komai
ba, Calmly yace "C'mon Halysaah wannan ma ai yafi wancan da kike
ciki" Yana murmushi ya kare maganar, ita dai tayi shiru bata ce komai ba,
ya ajiye mata kayanta da wayarsa yace "If you need anything just call my
line" Ta gyada masa kai, ya nuna mata hanyar bandakin dake babban dakin
yace "In zaki yi sallah ga bandaki can" Nan ma dai ta gyada masa kai
kawai, ya juya ya fita daga dakin ta koma ta zauna, gajiya tayi da zama tana
son kwanciya amma ta kasa kwantawa saman gadon, ita kanta ta rasa dalili, can
dai ta zamo kasa a hankali ta kwanta saman lallausan carpet dake dakin ai ko
nan da nan bacci ya dauketa, throughout ranan haka Khaleesat ta yini a dakin
ita kadai, tun da Housemate dinta ya kawo mata lunch har lokacin magrib yayi
bai dawo dakin ba, sai Cook din gidan ne ya kawo mata dinner, tana zaune saman
darduma bayan ta idar da sallahn isha taji an bude kofar dakin ta daga kai,
sosai gabanta ya fadi ganin AJ, ta sauke idonta daga kallonsa, shi kam ko
kallon inda take bai yi ba fuskarsa a murtuke ya tafi ya dau second phone dinsa
da laptop, ya bude press dinsa ya dau pajamas dinsa sannan ya fice daga dakin,
sai a sannan ta daga kai ta bi sa da kallo tana mamakin abinda ya shigo yi, don
bata san me ma ya dauka a dakin ba, har sannan bata kawo cewar dakinsa bane,
har ta fara bacci Jay ya shigo dakin da sallama, ta mike zaune daga kwancen da
take a kasa, da mamaki yake kallonta yace "Me yasa kika kwanta a kasa
Halysaah?" Ta girgiza masa kai kawai, yace "C'mon don't do that pls,
ga gado zaki wani kwanta a kasa" Ta kalli gadon tace "Zan
kwanta" Yace "Good, hope u need nothing?" Tace "Bana
bukatar komai" Yace "Alright then, good night" A hankali tace
"Thank you" ya mata murmushi yace "In kashe maki wutan dakin ko
a maida maki dim light?" Tace "Dim light" Ya mayar mata wutan
mara haske sosai sannan ya juya ya fita daga dakin, bayan fitarsa ta koma tayi
kwanciyarta a kasa, ita gani take kamar master bedroom din gidan ne, may be
that's why she is not comfortable, wajen karfe dayan dare dakin yayi sanyi
sosai amma taki daukan duvet din saman gadon ta rufa, kawai ta lullube da Hijab
dinta, she was so cold gashi Safiyyah bata hado mata kayanta da Sweater ba,
tana ta kwance ta kasa bacci saboda sanyin da ya dameta sai juye juye take taji
an bude kofar dakin, a hankali ta sauke Hijab dinta kasa kadan tana son ganin
wanda ya shigo don har kanta ta rufe, taga AJ ne ya shigo, kallo daya yayi mata
ya tafi daukar abinda zai dauka, zaro ido tayi bayan ta zargi anya ba dakinsa
bane nan kuwa, sai bayan da ya fita taji ya kullo kofar ta mike zaune tana sake
bin dakin da kallo with shock, dumin da taji dakin ya fara dauka gradually ne
yasa ta gane ya kunna mata heatern dakin, ta koma a hankali ta kwanta sai da
dakin yayi dumi sannan bacci ya dauketa..... Washegari da safe Jay na zaune
main parlor tare da Abba da Aunty, cikin nutsuwa Abba ke masa magana amma shi
gaba daya hankalinsa na sama kan Halysaah don tun da gari ya waye bai je
wajenta ba, kawai dai Cook din gidan ne ya kai mata breakfast, AJ ya shigo parlon
daga reading nook da yake zaune ya nufi dinning area zai yi breakfast, Abba ya
bi sa da kallo, after a while yace "Baka yi breakfast din bane" Jay
ya Ιan kalli AJ, Aunty kanta kallonsa take ita ma, without turning back AJ yace
"Ban yi ba" Aunty tace "To ai naga cook din gidan ya kai maka
Breakfast din sama daxu" Ko tankata AJ bai yi ba ya tafi dinning ya zauna,
Abba na kallon Jay calmly yace "Is he Okay?" Jay ya Ιan shafa kai
yayi kasa da murya yace "I think supervisor dinsa ne bai yi approving
Article din da yayi publishing ba tukunna" Aunty tace "To banda abun
sa ai ba wani abu bane he should add in more effort to his work kawai" Shi
dai Jay bai ce komai ba, haka shi kansa Abba, after a while Jay ya mike ya tafi
sama, direct part din AJ ya nufa bayan yayi sallama ya tura kofar dakin ya
shiga. Wajen la'asar AJ na zaune parlorn dake sama, gaba daya he look moody,
dama jiya da daddare a nan parlorn ya kwana tsabar takaici, har zuwa yanzu yaki
ce ma Jay komai a gidan, Jay kuwa ko a jikinsa don ko kallonsa ma baya yi, su
biyu ne kadai a gidan don Abba ya fita tare da Aunty da autarta zuwa gidan wani
prominent friend dinsa a garin, da yake gobe da safe za su bar kasar zuwa
Nigeria, AJ ya gyara zama yana bin Jay da kallo trying to be sure of what he is
holding in his hand, he was very shock ya dai bi sa da kallo har yaga ya nufi
bangarensa, ya tallabi chin dinsa yana girgiza kafa, sai bayan da Jay ya fito
for the first time since yesterday AJ yace "Wallahi i will never forgive
you for these Jawwad, i promise you am not forgiving you" Jay dai ya dake
bai yi dariyar da ya basa ba, kuma yaki tankasa yayi wucewarsa ya bar sa zaune
a gun, da daddare Khaleesat na duba laptop dinta Jay ya shigo dakin da sallama
ta daga kai tana kallonsa ya zauna kan kujeran dakin yace "Hope you are
better now?" Ta gyada masa kai, yace "Toh Allah ya sauwake, amma ki
tabbatar kin sha maganin so that u get enough night rest" Tace "Zan
sha" Yace "Alright Good night Housemate, bacci nake ji" Ta Ιan
yi murmushi tana kallon agogo dake nuna karfe goma tace "Ai baka ma yi da
wuri ba" Yayi murmushi kawai yace "Saura kar ki kwanta saman gadon
yau" A hankali tace "Zan kwanta" Yace "Good" Daga haka
ya fita daga dakin, shi kansa yasan tunda ta dawo gidan yake tauye ma kansa
bacci, kuma ba wai baccin baya damunsa bane kawai daurewa yake yi, har ciwon
kai yake yawan yi yanzu saboda baya bacci sosai, Khaleesat ta kashe laptop
dinta ta ajiye sannan ta mike a hankali ta dauko maganin da ya kawo mata daxu
ta sha sannan ta kwanta saman gadon, amma fa a dar dar take saman gadon, Jay na
isa parlorn dake sama ganin AJ kwance kan kujera yana danna wayarsa yace
"Do you care sharing my room with me today?" AJ yaki tankasa yana
danna wayarsa, Jay ya daga kafada yayi wucewarsa dakinsa, after like an hour AJ
ya mike zaune jin muryar Abbansa, Abba dake kallonsa yace "Is everything
Alright Ahmad? Why are you lying down on the Couch?" AJ ya fara sosa kai
yace "Eh yanzu zan tafi daki Dad, ban san sanda bacci ya daukeni ba"
Yana fadin haka ya mike tsaye ya dau wayarsa ya nufi dakinsa, Khaleesat ta juya
jin an bude kofa don ba bacci take ba, yana shigowa dakin kuma ya kulle kofar
ya tsaya nan bakin kofar, rufe har kanta tayi da duvet, ya tafi gaban madubi ya
tsaya yana tunanin Jay bai taΙa cutarsa ba irin na wannan lokacin, sosai abun
nan ya tsaya masa a rai, ita dai Khaleesat tana ta sauraren taji ya bude kofar
ya fita daga dakin amma taji shiru, hakan yasa ta sauke duvet din kanta a
hankali suna hada ido ya watsa mata kallo yace "Meye kike kallona?"
Ta wani kallesa, sai kuma ta juya masa baya bata ce komai ba, after almost 5
minutes ya bude kofar dakin ya fice, tsabar yanda bai yarda da neatness din duk
dakunan dake gidan ba ya sa ya gwammace ya kwanta a parlor instead of going
into any of the room. Da Asuba Jay ya fito dakinsa kenan zai sauka downstairs
su yi sallah da Abba, tunda Abba ya zo tare suke sallah amma banda AJ da baya
saukowa ayi sallan da shi sai dai yayi shi kadai a sama, Jay ya hadu da Abba
yana haurowa sama, Abba yace "This shows baku sallah tare a gidan nan Jawwad,
ma'aikatan gidan nan guda biyu duk Musulmai ne, ga ka ga Junaid, amma ace baza
ku hadu ku yi sallah ba?" Da sauri Jay yace "Muna yi Abba..."
Abba bai ce masa komai ba ya nufi bangaren AJ, Jay ya buda ido sosai, sai kuma
ya bi sa da sauri yace "Zan kira maka shi Abba..." Abba yace
"Jiya da nace ka kirasa ya sauko?" Jay ya kasa cewa komai, duk
tunanin Jay za su ga AJ a Parlor a kwance amma sai yaga baya parlon, nan
hankalin Jay ya tashi ya tsaya a inda yake tsaye ya kasa ci gaba da bin bayan
Abba, he wish Junaid bai cire code din nambobin kofar dakinsa ba, Abba na tura
kofan sai ga AJ da ya shiga bandakin dake parlorn da suka baro yayi alwala ya
taho zai dau pray mat, shi ma zaro ido yayi yana kallon Abba kamar yanda Jay ma
ya tsaya kallonsa, AJ ya juya suka kalli juna da Jay, tunda Abba ya kunna wutan
dakin ya tsaya for like a minute bakin kofar dakin yana kallon Khaleesat dake
bacci, sai kuma ya juyo ya fito closing the door gently, Daga AJ har Jay suka
sunkuyar da kai a tare kamar munafukai, Abba dai sai kallon AJ yake, after 30
seconds of silence, speaking Calmly Abba dake kallon Jay yace "Abinda ke
faruwa gidan nan kenan Jawwad, and you told me nothing about it?" Jay ya
kasa cewa komai kuma ya kasa barin su hada ido da Abba, cikin nutsuwa babu fada
Abba yace "Magana nake maka Jawwad" Da kyar Jay ya girgiza kai yace
"I know nothing about it Abba" AJ ya bude baki yana kallon Jay da
yaki kallonsa, Abba ya gyada kai yace "Ohk then, ku mu je mu yi sallah
lokaci na wucewa" Daga haka ya juya ya bar su tsaye a wajen, Jay ya bi
bayan Abba da sauri, AJ ya bi sa da kallo baya ko kiftawa, tuni har Abba ya
sauka downstairs hakan yasa Jay ya tsaya Parlor sai ya tuna tuggun da AJ ya
hada masa gun Hadeeyah just 3 days back, bai san sanda dariya ya taho masa ba,
sai ga AJ da jikinsa yayi sanyi ya shigo parlon yana kallonsa, hakan yasa Jay
ya danne dariyarsa ya hade rai ya sauka downstairs da sauri, AJ ya bi sa da
kallo, sai kuma a hankali ya zauna saman kujera ya kai hannunsa baki, ganin
abinda Jay yayi masa yake kamar a mafarki, bai taΙa shiga shock irin na wannan
lokacin ba. Da safe kamar babu abinda Abba ya gani a gidan don bai sake masu
maganar baz kuma da alama ko Aunty bai gaya ma ba, Jay ma yasan bazai taΙa gaya
mata ba, karfe sha daya jirginsu zai tashi zuwa Nigeria don haka har sun gama
shirin tafiya Airport, Abba ya kalli Jay yace "Junaid bai sauko yayi
Breakfast ba ko an kai masa sama ne?" Jay yace "I don't really
know" Abba ya dau wayarsa ya kira AJ, ba a dau lkci ba sai ga AJ ya sauko
parlor shi dai ya kasa hada ido da Abbansa, Abba na kallonsa yace "Kayi
breakfast ne, naga baka sauko ba" Without looking at his Dad yace "Na
yi" Abba yace "Ohk, za mu tafi airport ne yanzu, get ready" a
hankali AJ yace "Ohk" Daga haka ya juya ya koma sama, sai da AJ ya
fara zaunawa a parlon sama for almost 5 mins, gaba daya jikinsa a sanyaye yake,
gashi ya tsani shirun Abbansa don ba alkhairi bane shirun, gwara ace ma fada
yayi ta masa ba kakkautawa da wannan basarwan da yayi kamar bai ga komai ba,
his next move might not be funny, Jay ya cucesa, bai taΙa zaton haka daga Jay
ba, to ko yace ma Abba bai santa ba ta yaya zai yarda da shi tunda a dakinsa ya
ganta ba dakin Jay ba, ganin bata lkci kawai yake ya mike yana tafiya a hankali
ya tafi dakinsa don dauko kayan da zai sa, yana shiga dakin Khaleesat na fitowa
daga bandaki da hijab dinta har kasa ta fito wanka, ya wani kalleta daga sama
har kasa fuskarsa a daure, ita dai tunda suka hada ido ta dauke kanta bata sake
yarda ta kallesa ba tana dai tsaye hanyar shiga bandakin, ya dau kayan da zai
dauka ya karasa gaban madubi ya dau tsadadden turarensa ya fice daga dakin, ta
wani kyabe baki ta karasa shigowa cikin dakin. Har Abba suka isa Airport bai ce
ma AJ komai ba akan daxu da asuba, kuma da alamar babu abinda zai ce masa, he
was just speaking about something different in the car, a haka suka rabu normal
normal a airport kamar babu komai, AJ yaki jiran Jay ya ja mota ya bar airport
din ya kama hanyar gida, dole sai Uber Jay ya samu da zai maida shi gida, ko da
ya isa gida ya ga AJ zaune a compound da non alcoholic wine a gabansa trying to
use it to calm himself down at the same time trying to figure out wani hukuncin
Abbansa zai ce zai dauka a kansa.....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
[5/26, 9:45 AM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat
felt so much relieve after leaving AJ's room, tana biye da Jay ta koma dakin da
take, ba tare da Jay ya kalleta ba bayan ya ajiye laptop dinta dake hannunsa
yace "Kin ji sanda aka bude kofa da asuba ne?" Khaleesat na kallonsa
ta girgiza kai tace "I am not sure, may be ina bacci sannan, banyi bacci
da wuri ba" Yace "Ohk" Tace "Why are you asking?" Ya
juyo yana kallonta, ya Ιan mata murmushi yace "Nothing" Tace
"But ai frnd din ka yana shigowa ya dau stuffs dinsa wani lkcn" Jay
yace "Ohk" Har ya juya sai kuma ya sake dawowa yace "Kince baki
yi bacci da wuri, ciwon kan ke damunki har yanzu?" Ta girgiza kai tace
"A'a, kawai baccin ne dai bai zo ba" Yace "Ohk" Khaleesat
ta bi sa da ido har ya fita daga dakin sannan ta zauna gefen gado a hankali,
har cikin ranta take jin kamar ta jawo ranan talata, she is so tired tana
bukatar kawai ta ganta kusa da Ummanta, she need her Mom's hug, Jay na fita ya
kira ma'aikatan gidan su gyara ma AJ dakinsa, Jay made sure the workers left
nothing untouched a dakin duk da babu abinda dakin yayi, amma irin gyaran da
aka ma dakin da bandakin ba na wasa bane, sai da ko ina ya dawo yana sparkling
tsabar gyara sannan Jay ya koma downstairs, amma still a ranan ma AJ bai kwana
dakin ba, yayi kwanciyarsa a parlor kan kujera. Washegari which was monday AJ
na zaune usual spot dinsa a compound da Coke din gwangwani a gabansa, har a
sannan yaki ce ma Jay komai a gidan, not even Jay hatta ma'aikatan gidan duk ba
wanda yake yi ma magana he is just keeping straight face, Jay ya fito daga
cikin gida ya karasa har inda yake zaune, ko kallon direction dinsa AJ bai yi
ba yana juya counter din hannunsa, Jay na kallonsa yace "Abba wants to
speak to you" Yana fadin haka yace "Abba gashi nan" Ya ajiye
wayar gaban AJ, Calmly Abba yace "How are you doing Junaid" AJ ya
sauke idonsa ya gaida Abba, Abba ya amsa yace "You didn't call to know if
we arrived safely" AJ yace "Ayi hakuri" Abba yace "It's
fine, yaushe za ku dawo hutu" AJ yace "Ran Thursday zan dawo in sha
Allah" Abba yace "What about Jawwad" A takaice AJ yace "I
don't know" Abba yace "Hand the phone over to him" Jay ya dau
wayarsa sitting in one of the chairs beside AJ yace "Na'am ina ji
Abba" Abba yace "Kai yaushe zaka dawo" Jay ya Ιan yi shiru, sai
kuma yace "Probably next week in sha Allah" Abba yace "Ohk Allah
ya kai mu, earlier today you said you have something to tell me unfortunately
ina tare da baΖi a lkcn, so what is it Jawwad" Jay ya Ιan shafa kansa
thinking of where to start, can dai yace "Abba dama it's about the girl u
saw yesterday" Abba yayi shiru at first, sai kuma "Ohk, what about
her?" Jay yace "Abba ni ne na kawota gidan ba AJ ba, she is a student
of John Hopkins also, she is having issue with House rent and she's writing
exam, so shine kawai na kawota gidan nan zuwa sanda zata gama
jarabawan...." Abba ya dakatar da shi yace "Did you and Junaid birth
me or i birth you both?" Jay ya girgiza kai da sauri yace "Billah
Abba i am not cooking up stories, believe me, all what i am saying is the truth
ai kasan bana maka karya Abba, kawai dai ni na kai ta dakin AJ ne without even
his knowledge cause Aunty will definitely see her in the house, part din AJ ne
kawai nasan bazata shiga ba, kuma because of this... AJ parlor ya dawo yake
kwana, wallahi babu komai tsakaninmu da ita kawai taimako ne, you can even
speak to her to confirm ranka ya dade" Abba yace "If she is having
rent issue don menene baza ku bata kudin hayan ta biya ba ko kuma ni ku min
magana, na menene sai kun kawota nan gida cikin ku ta zauna? Is that ur home
training? Dama addininku ya yarje maku da haka?" Jay ya sauke ajiyar
zuciya a hankali yace "Kayi hakuri ka gafarce mu Abba, she will be
rounding up her exam on Tuesday, and she will leave in sha Allah" Abba
yace "Kaga da ba don nasan baza ka min karya ba Ahmad i won't listen to
you, da Junaid ne ya tsaya mun wannan bayani bazan yarda da shi ba, and my plan
was to start making arrangement na samar masa mace da zan aura masa a kai masa
ita can Ζasar, tunda ka min wannan bayanin naji na kuma yarda amma daga kai har
shi sati biyar na baku kacal ku gabatar min da macen da za ku aura, ita kuma i
will send you some money to sort out her House rent" AJ ya daga kai yana
kallon Jay bayan yaji abinda Abbansa yace, sai kuma ya mike kamar zai tashi
sama ya bar wajen, shi dai Jay was speechless this was the least thing he was
expecting to hear from Abba, jin Abba ya katse wayar ya zuba ma screen din ido,
ya basu 5 weeks?? jay ya fi minti goma zaune a wajen kafin daga karshe ya sauke
ajiyar zuciya ya mike ya dau wayarsa ya shiga cikin gida. The next day
Khaleesat suka gama jarabawansu na karshe and she was so happy amma kuma da ta
tuna wasu abubuwa kawai sai mood dinta ya canza, suna zaune tare da Safiyyah a
cikin makarantar ganin yanayinta da yanda ta sauya lokaci daya tayi shiru,
Safiyyah ta kalleta tace "Why are you like this Khaleesat?" Khaleesat
ta daga kai ta kalleta, a hankali tace "I don't have the means of going
back to Nigeria Sophie, the burden i am placing on my Housemate is too much ba
shi ya kawo ni kasar nan karatu ba, he knows nothing about me, don me zan yi ta
dora masa nauyina har haka?" Safiyyah tace "To ya za kiyi Khaleesat,
tunda ba ke kika rokesa ya maki ba ai kawai addu'a zaki masa Allah ya saka masa
da alkhairi, he is ur God sent Angel, ba gashi with or without Abdul kin gama
jarabawanki lafiya ba" Khaleesat ta sauke idonta jin hawaye ya ciko mata,
Safiyyah ta hade rai tace "To meye na kuka kuma?" Muryarta na rawa
tace "Ni dai bana son yace zai sake kashe min kudi masu yawa in koma Nigeria,
i am feeling guilty" Safiyyah ta wani kalleta, can tace "Kya rube a
kasar nan kuwa, ke kina da hanyar komawa ne? Ko kuma aikatau zaki nema a kasar
ki tara kudin komawa Nigeria? In ba dai kudaden Abdul dake account dinki zaki
yi using ki biya kudin jirgi ba" Safiyyah na kai wa nan ta kyalkyale da
dariya tace "Ko ya kwashe en kudaden nasa ne?" Ita dai Khaleesat tayi
shiru taki ce mata komai, Safiyyah tayi dariyarta me isarta sannan tace
"Allah ba batun wasa ba, ya kwashe kudaden nasa ne?" Khaleesat ta
girgiza kai a hankali tace "Suna nan" Safiyyah tace "Miliyan
nawa ne ma?" Khaleesat ta sauke idonta tace "Almost 9.5 Million"
Safiyyah tace "To kawai ki siya Ticket abunki tunda dai yasan ba uban wani
gareki a kasar ba da zai baki kudin komawa Nigeria ba, bayan shi kawo ki, in
nice ke ma har shopping sai nayi na komawa Nigeria a cikin kudin wallahi, ai
bazai san kin taΙa ba tunda ba shi ke ganin alert ba" Safiyyah na dariya
ta kare maganar, ita dai Khaleesat bata tanka ta ba, Safiyya tace "Naji
kinyi shiru ko baza ki taΙa ba? Wallahi yanzun nan in raka ki shopping mu
fatattake kudin" Khaleesat tace "Ai ba nawa bane da zan fatattake
su" Safiyyah ta kwashe da dariya tace "To ai sai kiyi ta zama a
kasar, dama gulma ce yasa kika kawo maganar ba wani abu ba don nasan Jay kike
saka ran ya biya maki ticket" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take ta
kasa ce mata komai, amma ita kadai tasan abinda take ji a zuciyarta, Safiyyah
tace "In kuma in ma Ya Musty magana to, don dai Economy class ticket da
zai siya mana bazai ce ya gagaresa ba" Da sauri Khaleesat tace "A'a,
zan yi amfani da kudin account dina" Safiyyah tace "Atoh dai"
Khaleesat ta gaya mata haka ne kawai don bata son taje ta ma Ya Musty
magana.... Jay ne ya zo daukansu a schl din as usual, sai da ya fara dropping
din Safiyyah sannan ya kama hanyar gida da Khaleesat, daxun nan yaga Abba ya
sako masa dala dubu goma wai na House rent dinta, da ya gaya ma AJ sai cewa
yayi ya masa transfer din Dala dubu biyar shi ma ya rike dubu biyar din tunda
ba su suka kawota kasar ba, shi da Jay bai tankasa ba, Jay dake driving ya Ιan
kalli Khaleesat jin shirun yayi yawa, yaga alamar tayi nisa tunanin da take,
sai a sannan ya kula da idonta da yayi ja, a hankali yace "Halysaah"
Juyawa tayi ta kallesa trying to look alright ta Ιan yi murmushi tace
"Na'am" Yace "Are you okay?" Tayi yake tace "Na gaji
ne kawai" Jay yayi shiru, bai sake ce mata komai ba amma yasan ba gaskiya
ta fada masa ba, a Ιan few months din da yayi da ita har ya gama studying dinta
gaba daya, he knows when she is happy, sad, bored, disturbed, and even tired,
wannan karan yaga damuwa ne karara a fuskarta, ya dai ci gaba da driving dinsa
har suka isa gida, bayan yayi parking ya juya yana kallonta, a hankali yace
"Me ke damunki Halysaah?" Duk kokarinta na ganin ta nuna masa ba
komai hakan yaci tura, don kawai ita ma gani tayi kuka ya taho mata, Jay ya
jinginar da kansa da kujeran motar bai ce mata komai ba, kwana biyu ya huta da
kukanta don a sanda ya dawo da ita gidan rana daddaya ne bata kuka don ma Safiyyah
na taka mata burki kuma ya ga tana Ιan jin maganar Safiyyar wani lokaci, sai da
tayi kukanta me isanta sannan yace "Sauka mu shiga ciki to" Ba musu
ta bude motar ta sauka tana goge idonta, shi ma ya sauka, yana gaba tana biye
da shi suka shiga cikin gidan. Khaleesat na kwance da yamma ta shiga Hisnul
Muslim dake wayar Jay sai ga kira ya shigo wayar, a hankali ta mike zaune tayi
picking call din ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren taji yace
"Kin tashi?" Tace "Uhm" Yace "Kin yi sallah?"
Tace "Nayi" yace "Ohk will you mind going out to the park with
me?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma a hankali tace "Ohk, thank
you" Yace "You are welcome, i will be waiting for you at the parlor
downstairs" Tace "Ohk" After almost 15 mins Khaleesat ta sauko
downstairs cikin shiri, sosai kayan jikinta yayi mata kyau sai dai ta rame
sosai, shi kadai ne zaune parlon yana jiranta, tun da suka hada ido ta sunkuyar
da kanta, ya mike ya jira har ta iso parlon yana kallonta, a tare suka fita
zuwa parking space din gidan ya bude mata motar, ta Ιan kallesa tayi murmushi
tace "Thank you" Ya bude ido yace "No thanks" bayan ta
shiga ya kulle motar sannan ya zaga ya shiga driver seat, one of the best park
na state din ya kai ta and she love everything about the park, the view was so
fascinating and breathe taking, she felt so refresh and relieve taji kamar bata
da wani damuwa a lkcn, Jay ya siya masu Wraps da fresh lemonade, wannan karan
bata ji kunyar cin abinci gabansa ba, lkci lkci yake daga kai ya kalleta, ita
dai ta dinga kallon feral horses dake park din from a far distance, can ta
kallesa tace "Su ba a hawansu ne?" Yayi murmushi ya girgiza mata kai
yace "Ba a hawa" Tace "And nobody is controlling them?"
Yace "Sort of, they are just on their own with no supervision, ko kina son
in kai ki inda zaki hau doki ne?" Er dariya tayi ta girgiza masa kai
kawai, ya Ιan kalleta, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki a lokacin, ta
kalli wraps dinsa da bai karasa ci ba tace "You are not eating?" Yace
"Za ki ci ne?" Tayi murmushi tace "A'a, na koshi, kawai naga
baka ci da yawa bane" Yace "Na ci abinci daxu ne, i am full" Ta
kalli lemonade din gabansa tace "To in dauka?" Yace "A karo maki
wani kenan?" Ta girgiza kai da sauri tace "Aa fa, i just don't want
it to waste ne" Ya dauki sauran lemonade din nasa ya ajiye mata a gabanta
yana kallonta, ta dau straw din ta fara shan lemonade din a hankali, dauke ido
yayi daga kallonta, wayarsa ya fara ring yana dubawa yaga AJ ne ke kiransa,
yayi picking ya kai kunne, ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, after few
seconds Jay yace "Ni sai next week probably, ban gama abinda nake ba, do
not book with me" Ajiye wayar yayi bayan AJ ya katse, ya kalli Khaleesat
yace "Zaki jira har next week mu tafi Nigeria, or you will leave before
then?" Khaleesat tayi shiru at first, a hankali ta sauke idonta tace
"Yanda kace" Yana murmushi yace "Ko zaki bi AJ, he is leaving
soon, yanzu ma ticket zai yi booking" Ta daga manyan idanuwanta ta
kallesa, sai kuma tace "He that dislikes me shi ne zan bi sa?" Jay
yayi dariya yace "How will you say he dislikes you Halysaah? He dislikes
you shi ne yaje har apartment dinki yayi rescuing dinki? Ke ce dai baki ganesa
ba har yanzu, AJ is nice just that yana da son girma ne kuma baya son raini,
which i understand him because that's our heritage, kinga ke ko gaishesa baki
yi" Tana wasa da straw din lemonade din gabanta tace "To ai nasan ko
na gaishesa bazai amsa ba, saboda na taΙa gaishesa bai amsa min ba" Jay
dai yayi murmushi yace "In kin ci gaba da gaishesa ae zae amsa" Tace
"Ur frnd doesn't like me at all, he prefer my frnd" Jay yace
"Who told you he is my frnd? AJ is my cousin bro Halysaah" Khaleesat
ta daga kai ta kallesa tace "Da gaske?" Yayi murmushi yace "Ba
ma kama ne?" Khaleesat ta buda hannu tace "Ni ban wani san yanda
fuskarsa yake ba ai, ban taΙa kallonsa sosai ba" Jay yayi dariya, a
hankali yace "To cousin brother dina ne, His dad is my father's junior
bro" Khaleesat tace "To amma dai ka girmesa ko?" Jay na murmushi
yace "Not at all, just 3 months ne tsakaninmu, we will clock 34 next year"
Khaleesat tace "Shi ne yace ya haifeni?" Jay bai san sanda yayi
dariya ba sosai, sai kuma yace "Zolayarki fa yake, but how old are
you?" Ta sauke idonta kasa kamar bazata ce komai ba, sai kuma a hankali
tace "I am 20" Jay ya wara ido yace "Waw, you are still a Baby
Halysaah" ta wani kallesa, yana murmushi yace "To ai in AJ mace ne
kuma an masa auren wuri ya isa ya haifeki" Yana dariya ya kare maganar,
Khaleesat dai taki cewa komai still playing with the straw in front of her, a
hankali Jay yace "Are you angry?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma
tayi murmushi ta girgiza masa kai still looking at him, Jay ya kwantar da murya
yace "U misunderstood AJ, yana da kirki sosai, kuma yana da tausayi, just
that he is a no nonsense kuma baya son raini, sannan truly yana da girman kai
na sani, but that doesn't make him bad, kuma da kinsan wanene shi zaki san yana
ma da saukin kai" Khaleesat ta karasa shan lemonade din gabanta taki ce ma
Jay komai, Jay ya kalli agogon wrist dinsa yace "Let go for horseback
riding before it gets late" Khaleesat ta zaro ido tace "A'a ni dai
bazan hau doki ba" Yana murmushi yace "To mu je dai" Shi ya fara
tashi sannan ita ma ta mike suna tafiya a tare, satan kallonsa tayi suka hada
ido ya ciro wayarsa yace "Let's take some pictures with this beautiful
view" A hankali tace "Ok" Tana tsaye kusa da shi yayi masu hoton
da wayarsa, yana kallon hoton da yayi masu ya taΙa hancinsa yace "Ya naga
hancinki yafi nawa tsayi, ya naga kamar kin fi ni kyau" duk lokaci daya ya
jero tambayar yana sake kallon hoton da kyau, ita dai Khaleesat tayi murmushi
tace "Uhm is that an irony?" Jay yayi dariya yace "I am serious
Halysaah" Wata er Africa ce ta zo wucewa ya mika mata wayarsa politely
yace ta masu hoto pls, yarinyar ta amshi wayar zata masu hoton, yanda Khaleesat
taji ta uncomfortable kusa da shi, shi ma dai kamar hakan ne cause he left a
little gap between them, yarinyar ta masu hotuna masu kyau kuwa, ita kanta
yarinyar sai kallon hoton take kafin ta mika ma jay wayarsa tana kallon Khaleesat
admiringly tana murmushi tace "You are so Beautiful" Khaleesat ta
sauke idonta tace "Thank you" Yarinyar ta daga masu hannu ta bar
wajen, bayan Jay yayi mata godiya, kallo daya yayi ma hotunan ya mayar da wayar
cikin aljihunsa yace "Let go for horseback riding Housemate" Wani
park din ya kai su daban da ake hawa doki, duk yanda yayi da Khaleesat ta hau
doki bayan ya biya masu kudi taki wai ita bata iya ba tsoro take ji, daga
karshe ta marairaice tace "Ni dai kawai ka bani wayarka in dinga maka
video sai kai ka je ka hau" Yayi murmushi kawai ya mika mata wayarsa yace
"To ai shikenan" Khaleesat was so impressed with his horse riding
skills kamar irin dama ya saba din nan, sai murmushi take masa, mutanen wajen
ma suna ta kallonsa, Khaleesat's eyes were glued to him all through, tana yi
tana masa video, sai after 7 suka bar wajen, tana kallonsa kafin su shiga mota
tace "Where did you learn to ride horse confidently?" Yayi dariya
yace "Back home" Tana murmushi tace "To ka taΙa zuwa nan
ne?" Jay yace "Tab ai nan wajen zuwan AJ ne, kawai dai of recent ne
muka dena zuwa" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, sai da ya fara
biyawa African Restaurant ya siya mata abinci, ganin leda daya ya mika mata
yace "This is for you" Tace "Kai fa?" Yace "No, i am taking
tea and bread this night" A hankali tace "Ohk, thank you" Bayan
sun isa gida yayi parking, ta juya tana kallonsa a hankali tace "Thank you
so much, Allah ya saka maka da alkhairi, i appreciate you" Without looking
at her yace "Amma nace ki dena min godiya ko Housemate?" Tayi shiru,
ya bude motar ya sauka sannan ita ma ta sauka, yana gaba tana biye da shi har
suka shiga gidan, AJay na zaune parlor yana shan fruit salad yana kallon
kwallo, ya juya ya kalleta don shi bai ma san bata gidan ba, suna hada ido
abinda Jay yace mata daxu ya fado mata, ta sunkuyar da kai, kamar munafuka tace
masa "Good evening" AJ ya gyara zama yana kallonta yace "Kin
saba gaisheni ne zaki ce min Good evening??" Khaleesat ta Ιan kalli Jay da
ya karasa cikin parlon, Jay yace "Good night Halysaah, if you need anything
you call my line" A hankali tace "Thank you" Daga haka ta wuce
sama, Jay na kallon AJ yace "Ba don na mata magana ba kana tunanin zata
gaisheka ne dama? Ni ne nan na saka ta, sai me kuma in baka amsa ba?" AJ
yace "Zamana take a gidan da zata gaisheni" Jay dai yaki tanka masa.
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
[5/26, 9:45 AM] khaleesat Haiydar π✍️: Washegari
Wednesday da yamma Jay na zaune parlon dake sama tare da AJ da ya maida parlon
wajen kwanansa, don tun da Khaleesat ta kwana dakinsa tsakaninsa da dakin kawai
ya shiga ya dau kaya, ko bandakin dake dakin baya shiga, Jay dake kallonsa yace
"Yanzu dai zan iya dawowa dakinka kenan tunda ka tashi a dakin?" AJ
yayi banza da shi yana ci gaba da hada few kayansa da yake yi a tsadadden box
dinsa da zai yi tafiya gobe, Jay yace "To wai kayi booking flight din ne
da naga kana hada akwati?" AJ yace "Bana son Airline din da na gani
jiya, anjima zan siya Ticket din Turkish Airlines" Jay yace "How many
hours connection time for the layover?" AJ yace "Baya wuce 2 to 3
hours, ko ma bazai kai haka ba" Jay yace "Will you mind travelling
same plane with my Housemate? I just remembered I will be meeting my Mami at
the UK, tare za mu koma Nigeria da ita daga can" AJ yace "Of course I
will mind Jawwad, because my OCD will never allow me board the same plane with
her, ga Airline kala-kala ka nemi wani ka siya mata ticket mana, what is my
business with her da zaka hadani da ita sai kace ni na kawota America, there is
this Airline na mance sunansa Economy class ticket dinsu naga is just 600
dollars, you can get her the ticket as the Good Samaritan that you are"
Mikewa Jay yayi bai ce masa komai ba ya bar parlon. Wajen karfe biyar da rabi
Jay ya kwankwasa ma Khaleesat kofa, bayan ta bude yace "Ba abinda zaki
dauka a can apartment din da zaki koma da shi Nigeria Housemate?"
Khaleesat tace "Ohk, zan dau wasu kayan" Yace "To ki shirya sai
in kai ki can ki dauka" Khaleesat na kallonsa a hankali tace "Pls kar
kace zaka siya min ticket ina da kudi a account dina, i will get the
ticket" Yayi murmushi yana kallonta yace "To Hajiya me kudi, kudin
zai isa ki mana booking har ni da AJ?" Tana murmushi ta fara wasa da gefen
gyalenta tace "Sae dai kai kadai, ni ai ban san wani AJ ba" Akan
kunnen AJ da ya taho daga parlor zai sauka downstairs, ya tsaya yana kallonta
babu fara'a, Jay ya juya ya kallesa yana murmushi yace "Je ki shirya ina
jiranki downstairs Halysaah" Juyawa tayi ta tura kofar dakin a hankali, ko
da Khaleesat ta sauko downstairs ta tarar da Jay yana jiranta, and it's almost
6pm, ya mike suka fita daga parlon, bayan sun bar compound din a motarsa ya Ιan
kalleta yace "Kinga kin kara tsokanar AJ ko?" Ta marairaice tace
"To ni ai ban san yana wajen ba, why is he always eavesdropping?" Jay
yayi dariya yace "Ni dai ba ruwana" Ita dai tayi shiru bata ce komai
ba, she can't even wait ta dena ganin AJ she is already exhausted with him and
his problem, she can't wait to stop seeing him, suna isa apartment dinta abinda
ya faru ya dawo mata fresh, kawai sai take ganin kamar trauma din ya dawo mata
sabo a kwakwalwarta, lkci daya duk jikinta ya mutu, haka dai jikinta ba kwari
ta tafi dakinta ta fara hada kayan da zata hada shi kuma Jay ta bar sa parlor
yana jiranta, sau uku Safiyya na zuwa gidan debo mata kayanta kwanaki kuma duk
Housemate dinta ne ke kawota, after a while Khaleesat ta gama daukan abubuwan da
zata dauka a akwatinta, sauran kayan dakin duk ta haΙa su waje daya, ko zata
dawo kasar ko bazata dawo ba ita dai bata sani ba, ta kuma bar ma Allah komai,
ta gama tidying ko ina a dakin sannan ta fito wajen karfe shidda tana jan
akwatinta a hankali zuwa parlor, kwance taga Housemate dinta kan doguwar kujera
ya fara bacci, ta tsaya tana kallonsa, sai kuma ta tafi kusa da kujeran still
looking at him ta Ιan tapping din jikin kujeran gently, a hankali ya bude ido
sai kuma ya mike zaune yace "Kin gama ne?" Tace "Are you
sleeping?" Yace "A'a, kawai na kwanta ne ina wani tunani, it's even
time for magrib bari inyi sallah, kema kije kiyi" Bandakin dake parlor ya
shiga ita kuma ta koma dakinta, sai bayan wani minti sha biyar din suka bar gidan,
tunda suka fito gidan Khaleesat tayi shiru, shi ma kuma bai ce komai ba, amma
ya lura mood dinta ya canza, kawai ya sa a rai bazai tafi da ita gida a haka
ba, after a while ya Ιan kalleta yace "Would you mind watching a movie in
Cinema tonight?" Khaleesat ta juya ta kallesa, sai kuma ta sauke idonta
bata ce komai ba, yace "Ko baki kallo?" Tace "Ina yi, amma ba
sosai ba" Yace "To yau za ki yi"
Waje ya samu yayi parking, ya dau wayarsa ya shiga website din Cinema
din dake Maryland to check their schedules for that day, yayi selecting movie
din da za su kalla, da lokacin da za su kalla sannan ya siya masu ticket aka
turo masa ta online, ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, yana daga kai tayi
saurin dauke idonta daga kallonsa, ya ci gaba da driving dinsa, without looking
at her yace "I hope you will enjoy the movie" Ita dai bata ce komai
ba har suka isa Cinema din, ya siya masu popcorn and lemonade, sannan suka nufi
cikin Auditorium din da za a haska film din da ya siya masu ticket, in some
minutes kuma za a fara haska film din, wannan ne zuwan Khaleesat Cinema na
farko a rayuwarta duk da a baya babu irin takuratan da Safiyyah bata yi akan su
je tare da frnds din Safiyyar amma ita dai bata yarda taje, suna shiga Jay ya
fara cin popcorn dinsa kamar abinda ya kawosa kenan, ita dai Khaleesat dama
bata wani damu da popcorn ba hakan yasa take Ιan ci jifa jifa tana kallon film
da ake, she is beginning to like the film hakan ya sa ta tattara gaba daya
hankalinta kan film din, after almost 35 mins da fara film din ta juya ta kalli
Jay taga bacci yake, ta dade abu bai bata dariya haka ba, she couldn't believe
he is seriously sleeping abun sa, ta rufe fuskarta da hannunta tana dariya a
hankali, she don't know why she feel relieve a duk sanda take tare da shi,
there is never a boring moment with him, gently ta kai hannu kusa da shi ta
dauki popcorn dinsa daya, he was still sleeping ta dinga kallonsa maimakon film
din da ya kawota ta kalla, idan yana bacci komawa yake so gentle and calm, a
nan ne kuma ainahin handsomeness dinsa ke fitowa, if there is the sleeping
princess then he will be the sleeping prince, har awa daya da fara film din Jay
baccinsa yake kuma ta kyalesa bata tashesa ba, she watched the movie har sai da
ya kusa karewa and she really enjoyed every bit of it, ta juya ta kallesa sai
kuma ta dau popcorn daya ta matsa dai dai kusa da shi a hankali ta saka masa a
baki, da sauri ta gyara zamanta ta maida hankalinta kan movie, ya bude ido,
taji yace "What a nice movie" Sai a sannan dariya ya taho mata ta
juya ta kallesa tace "Ain't you ashame of saying this?" Yana gyara
zama yace "You don't like the movie? But it's nice, i like it" Tana
murmushi tace "To in ka gama baccin ka tashi mu tafi, ni na gama
kallona" Ya Ιan shafa kai trying not to smile yace "Wa yace maki
bacci nake, i was only meditating duk nasan abinda ake yi ai, ba gashi an kusa
gamawa ba" Ita dai murmushi kawai take tace "Naji, tashi mu tafi, a
hanya sai ka bani labarin film din don akwai inda ban gane ba" Yayi shiru
yaki cewa komai, tana danne dariyarta ta tashi ta dau sauran popcorn dinta da
nasa, tashi yayi ya bi bayanta suka fita daga Auditorium din, lokaci lokaci
take juyawa ta kallesa don ta tabbatar he is not walking and sleeping at the
same time, da sauri ya jawota ta fado jikinsa bayan tayi missing step saboda
waige waigen sa da take sai kuma yayi saurin saketa, within few seconds aka yi
hakan, ta rufe bakinta da hannu don ba karamin tsorata tayi ba, yace
"Yanzu da kin fadi kika fara min kuka kilan har mu kai gida" Ta
marairaice tana kallonsa, Softly yace "Alright Sorry Halysaah" Ta
juya ta fara tafiya a hankali, a haka suka fita daga cinema din bata sake
waigen bayanta ba, yana biye da ita yana kallonta har suka isa gun da yayi
parking. Wajen karfe goma suka isa gida bayan yayi parking ta juya ta kallesa a
hankali tace "Thank you so much" Ya mata murmushi yace "You are
welcome House mate" A haka suka sauka daga motar tana biye da shi suka
shiga gidan, kafin ta shiga daki yace "Get me ur travelling
documents" Ta kallesa zata yi magana ya daura fingers dinsa biyu a lips
dinsa, ta sauke idonta sannan ta juya a hankali ta shiga cikin dakin, after
some minutes ta fito ta mika masa, ya amsa yace "Good job, zan tura maki
ticket din ta Email dina, sai da safe" A hankali tace "Allah ya tashe
mu lafiya" Juyawa tayi ta koma cikin dakin ta kulle kofar, Jay ya tafi
parlon sama yaga AJ kwance kan Couch yayi bacci, shi dariya ma yake basa, kawai
mutum ya dora ma kansa wahala, juyawa yayi ya wuce dakinsa, wajen karfe sha
biyun dare Khaleesat na ta juye juye ta kasa bacci ita kanta ta rasa dalili,
message taji ya shigowa wayar Jay dake wajenta ta mike zaune ta jawo wayar tana
duba message din taga Email ne ya shigo, tana bude Email din taga ticket din ya
turo mata na Turkish Airline, kuma Business class seat, bata san me yasa taji
hawaye ya cika idonta ba, ta ajiye wayar a hankali ta koma ta kwanta.
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
[5/26, 9:47 AM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat na
zaune gefen gado tana kallon Jay dake kulle mata akwatunan ta, yana dagowa ta
juya a hankali tana kallon window dake dakin, ya dau boxes din biyu yace
"Let me get them in the car" Daga haka ya fita daga dakin, ta
jinginar da kanta jikin gadon dakin har ya dawo, yana kallonta yace "Hope
you didn't forget anything Halysaah" Ta gyada masa kai, yace "Ok, you
know what? in dai muka fita kika hadu da AJ thank him and tell him you are
leaving" With a smile on his face ya kare maganar yana kallonta, ta sauke
idonta tana wasa da fingers dinta a hankali tace "Ohk" Yace
"Good gal, mu tafi" Mikewa tayi ta bi bayansa tana rike da karamin
handbag dinta walking slowly, suna fitowa walk way din babban corridor din sama
sai ga AJ ya taho daga parlorn dake nan sama, Jay ya kalli kayan jikinsa ganin
iri daya suka sa kuma tun safe ba wai sun hadu bane kawai coincidence, tunda AJ
ya kallesu sau daya ya ci gaba da tafiyarsa, Khaleesat ta Ιan kalli Jay, ya
gyada mata kai sannan ya nufi stairs, ita dai tana tsaye ta jira har AJ ya iso
kusa da inda take sannan ta sauke idonta a hankali tace "Good morning, i
want to thank and appreciate you for everything, i will be leaving today in sha
Allah" Without looking at her yace "Jay dai zaki ma godiya ni me na
maki" Ta bi sa da kallo har ya fara sauka downstairs, sai bayan da ya
sauka sannan ta tabe baki ta bi bayansa tana tafiya a hankali, parlor ta tarar
da Jay zaune yana jiranta, Jay ya bi AJ da kallo yace "Flight din naka na
gobe ne amma?" AJ yace "I am leaving for the airport now" Jay
yace "Ohk, zaka jira inyi dropping Housemate dina sai in dawo in kai ka
airport din?" AJ yace "No, don't bother" Daga haka ya fita daga
parlon tare da daya daga workers din gidan wanda da alama shi zai yi dropping
dinsa airport din, Jay ya daga kai ya kalli Khaleesat, ya lura tunda gari ya
waye jikinta yake a sanyaye, yana kallonta yace "Are you Okay
Halysaah?" Ζan murmushi tayi tace "Sure" yace "Kin gaya ma
kawarki yau zaki tafi?" Khaleesat ta gyada masa kai tace "Na gaya
mata" Yace "Ok, ita yaushe zata tafi?" Khaleesat tace
"Yayanta yace ta bari ranan lahadi" Jay yace "Kin tabbatar baki
mance komai ba kuwa a sama?" Ta gyada masa kai, yace "Je dai ki sake
dubawa Housemate" Bata masa musu ba ta juya zata koma sama yace "Toh
ki ajiye jakar taki mana" Ta dawo ta ajiye jakarta a kan kujera sannan ta
wuce sama, Mikewa Jay yayi ya tafi gun jakar ya dauka ya bude sannan ya ciro
Dala dubu daya a aljihunsa ya sa mata a jakar ya kulle ya mayar ya ajiye mata
ya koma ya zauna, ba a dau lokaci ba Khaleesat ta dawo downstairs tace
"Ban manta komai ba" Yace "Good" Mikewa yayi bayan yaji
fitar motar AJ don dama jira yake yaji sun fita daga gidan, yana kallonta yace
"Mu je, ur Flight is in an hour time in sha Allah" Khaleesat ta gyada
masa kai ta dau handbag dinta, tana biye da shi suka fita daga parlon gidan,
har gari ya fara duhu, suna shiga motarsa ta mika masa wayarsa dake hannunta
kar ta manta, a hankali tace "Thank you so much" Ya amshi wayar
sannan ya dauko pin a motar ya cire sim card din cikin wayar snn ya mayar mata
yace "Your ticket is on the phone, in kin koma Nigeria sai kiyi SIM card
replacement, in kuma baki son wayar sai in sa a kai maki sabo a Nigeria"
Tayi murmushin karfin hali tace "Saboda me zance bana so, nagode sosai,
Allah ya saka da alkhairi" Yace "To ai nasan ku mata da son sabon
abu" Ta girgiza masa kai kawai tana murmushi bata ce komai ba, a haka suka
bar gidan suka dau hanyar airport da tunani iri iri a ran Khaleesat, ko baccin
kirki bata yi ba daren jiya ga wani daren, ko me zata je ta tarar a Nigeria sai
Allah, it's now that reality is dawning on her, bayan sun isa airport Jay ya
juya ya kalleta yace "You can sort ur self out ba sai na shiga ciki ba ai
ko?" Ta gyada masa kai, da kyar tayi karfin halin cewa "Thank you so
much Housemate, Allah ya saka da alkhairi da abubuwan da ka min" Kasa ci
gaba tayi saboda hawayen da ya fara sauka a idonta she just can't thank him
enough, gani take words aren't enough to thank him, shi dai Jay kallonta kawai
yake with surprise, can yace "C'mon Halysaah, to menene abun kuka?"
Ta kasa basa amsa ta rufe fuskarta da gyalenta tana kuka a hankali, Jay ya
kwantar da murya yace "Pls ki dena wannan kukan, in nasan abinda zaki yi
kenan i will have just order either Lfyt or an Uber that will be taking you to
the airport" Dena kukan tayi tana goge hawayen da yaki tsaya mata tana
kallonsa, ya bude motar ya sauka ta bi sa da ido taga Luggages dinta dake booth
zai dauko, a hankali ta bude side dinta ta sauka daga motar tana bin sa da
kallo, daya daga porters dake wajen ya ba luggages din nata ya shigar mata da
shi ciki ya hada masa da tip dinsa, ita dai Khaleesat kallonsa take, ya juya ya
dawo kusa da ita yace "Alright safe trip Halysaah, idan kinyi replacing
Sim card dinki sai ki min magana ta WhatsApp, my regards to everyone back
home" Ta sauke idonta a hankali tace "I will miss you" sai bayan
da ta fada haka ita kanta tayi realizing abinda ta fada, sai kuma ta kasa dago
kanta, ya Ιan yi murmushi yace "I will miss you too Housemate, in sha
Allah next week i will be in Nigeria too" Bata iya ta kallesa ba ta gyada
masa kai kawai ta juya a hankali ta bi bayan porter din da ya shigar mata da
luggages dinta zuwa check in counter for her Boarding pass, kasancewar Business
class ticket gareta all the processes were smooth and straight for her, daga
karshe ta nufi waiting lounge don in 15 mins time za su fara boarding jirgi,
tunda ta shiga lounge din take kallon wanda ta gani zaune da mamaki, ta kalli
boarding pass dinta sannan ta kalli na hannunsa taga iri daya, wayarsa kawai
yake dannawa, ganin bai ganta ba ta juya a hankali ta koma wani wajen daban ta
zauna ta inda ma bazai ganta ba, bata sake waigen inda yake ba, iya drink kawai
ta amsa a lounge din unlike wasu da ke ta cin abinci duk a cikin kudinsu, gaba
daya ta nemi appetite dinta ta rasa saboda damuwa, da ta tuna inda zata sae
taji har wani juya mata kanta yake kamar bata da lafiya, ta saΖa wancen a ranta
ta kwance har daga karshe aka fara boarding din jirgi, sai da Khaleesat ta jira
AJ ya fara tafiya sannan ta mike ta bi bayansa walking slowly, Har seat dinta
wata Flight Attendance da ke welcoming dinta da fara'a ta kai ta, hada ido
Khaleesat tayi da AJ that was sitting few seats away from hers, ta sunkuyar da
kanta ta zauna Seat dinta tana mayar da Amenity kit din da aka ajiye mata a
gefe, AJ ya kasa daina kallonta fuskarsa babu yabo babu fallasa, he can't even
explain what he is feeling at that moment don bai taΙa ganin wanda ya gama rena
masa wayo a duniyar nan kamar Jay ba, jiya wajen karfe sha biyun dare ya farka
ya gansa yana duba masa waya ashe ticket din da ya siya yake dubawa, he felt
like just leaving the plane at that moment, after a while kawai ya dauke kai
yana kara gyara barrier din da zai sa ko hangota bazai dinga yi ba, Ita ma
Khaleesat ko by mistake bata sake kallon direction din sa ba, a haka jirgin ya
tashi, Khaleesat bata taΙa jin motion sickness ba tun da ta fara tafiya a jirgi
amma yau ko don saboda pressure din da ta saka ma ranta ne kawai sai ji tayi as
if she wants to throw up tun da jirgin ya daga, ta cire seat belt dinta da
sauri ta mike ta nufi Lavatory din jirgin almost running, shi dai ya bi ta da
kallo, Flight Attendance din da ta kawo mata Hot towel kafin tashin jirgin ne
ta bi bayanta tana tambayar if she's okay, Khaleesat ta gyada mata kai kawai
bayan ta fito daga Lavatory din, AJ ya bi ta da kallo har ta koma seat dinta ta
zauna sannan ya tabe baki, Flight Attendance din ta duka kusa da ita tana
tambayarta ko tana bukatar wani abu ne, Khaleesat ta girgiza kai tana murmushin
karfin hali tace "Thank you, i am okay" Matar ta sake tafiya sai ga
ta ta dawo da ruwa da orange drink, sai kuma wani drink daban duk a glass daban
daban akan tray daya, ta duka tana mika ma Khaleesat ta dauki wanda take so, glass
din ruwa kawai Khaleesat ta dauka ta mata godiya sannan ta sanar mata bazata ci
abinci ba all throughout the flight don ma kar matar ta sake dawo mata, gani
take tana cin abu zata yi aman da bata yi ba daxu, gyara kujeranta tayi ta
kwanta ta lulluba da blanket din da jirgin yayi providing for business class
passengers, nan da nan bacci ya dauketa, da za su sauka Turkey wajen karfe
hudun asuba sai da wata Flight Attendance daban ta zo ta tasheta ta sanar mata
jirgi zai sauka, Khaleesat ta mike zaune da kyar don ciwo kanta ke mata, tayi
fastening seat belt dinta, bayan sun sauka Istanbul ta bi AJ da kallo har sai
da ta daina hangosa sannan ta mike ta dau handbag dinta da waya ta bi bayansa
tana tafiya da kyar leaving her Amenity kit behind, jiran awa biyu za su yi a Business
Class waiting lounge na airport din kafin a canza masu jirgin da zai kai su
Nigeria, ta riga AJ shigowa lounge din kilan masallaci ya tafi, ita ma tana
ganin lokacin sallahn asuba yayi ta tafi tayi sannan ta dawo ta zauna a
business lounge din, after like 15 mins sai gashi ya shigo, not far away from
her ya zauna da ruwan gora a hannunsa, Ita dai ta jinginar da kanta jikin
kujeran da take zaune ta daura handbag dinta a kafarta, she is having a
terrible headache a lokacin, after almost 30 mins of sitting wani Ιan Nigeria
ya dawo kusa da ita ya zauna, wanda shi ma daga nan Turkey zai je Nigeria a
Business class, kuma jirginsu daya kamar yanda ta ga ticket irin wanda ta amsa
bayan sun sauka Istanbul din a hannunsa shima, yana kallonta yayi mata sallama
cikin nutsuwa, ta Ιan kallesa sannan ta amsa, yace "Guess you are coming
from America right?" Tace "Uhm" Yana kallon Flight ticket dinta
yace "Oops you are having the same name as my Mum, can i call you Jiddah
instead of the real name?" Khaleesat dake sauraronsa without looking at
him tace "Ohk" Yana murmushi yace "Alright, are you traveling
alone Jiddah?" Ta girgiza kai tace "No" Ya buda ido yace
"Ohk with who?" Ta kalli direction din AJ, shi ma mutumin ya kallesa suka
hada ido don kallonsu kawai Ajayn yake yana jin conversation dinsu, mutumin na
murmushi ya tashi yaje ya gaisa da AJ sannan ya koma ya zauna, shikenan
Khaleesat ta samu lafiya, don bai sake ce mata komai ba kawai danna wayarsa
yake tayi tunda shi dai bai san ko waye Ajayn a gunta ba, daga karshe ma ya
tashi ya bar wajen, at last aka fara boarding din jirgin da zai kai su Lagos
Nigeria daga Istanbul, Usman ya juya ya kalli Khaleesat da ta mike tana rike da
handbag dinta, har AJ ya wucesu sai kuma ya tsaya amma bai juyo ba, ita dai
tana tafiya a hankali har ta isa inda yake tsaye sannan ya ci gaba da tafiya
tana biye da shi, har jirgi ya tashi Usman dake zaune not far from Khaleesat
but close to AJ bai ce mata komai ba, this time around ma dai bacci kawai tayi
har zuwa Nigeria. Karfe hudu saura suka sauka Nigeria washegari Friday, ita dai
Khaleesat tun da ta ganta Lagos bayan ta gama da Custom da Immigration ta fara
tunanin kuma yanda zata yi, to ko dai kawai ta tafi gidan Aunty Farida tunda a
nan Lagos take, to ko tace zata je bata da sim din da zata kirata don ba gane
anguwan zata yi ba kuma bata da lambarta a kai balle ko waya ne ta ara ta
kirata a airport din, sai kuma tayi tunanin kiran Ummanta tunda tana da
numberta a kai sai tace ta turo mata number Aunty Farida, gun wata mata warce
taga kamar Bahaushiya ce ta nufa, ta gaisheta sannan tace "Don Allah Aunty
wayarki zaki ara min in Ιan yi kira nawa ba caji" Matar ta fara kallonta
daga sama har kasa, sai kuma ta bude handbag dinta ta ciro wayarta ta mika
mata, Khaleesat ta amsa tace "Nagode" Dialing number Umma tayi ta
kira taji a kashe, sosai jikinta yayi sanyi, ta kira har sau uku duk ana ce
mata a kashe, a hankali ta zame wayar a kunnenta ta mika ma matar tace
"Nagode, wayar ma a kashe yake" sai da matar tayi dialing wayar ta
tabbatar eh a kashe din yake, kana ganin matar kasan she is not comfortable
giving off her phone, Khaleesat na jan trolley dinta a hankali ta fito daga
cikin airport din tana tunanin yanda zata yi, ko dai kawai ta tafi tashan da
zata samu mota zuwa kano, since she have some money in her bank account, wani
mutumi ne taga ya nufota, ya gaisheta da ladabi yana mata barka da zuwa, sannan
ya nuna mata mota yace "Ke mu ke jira ki fito dama" She was looking
at him with confusion, can ta kalli motar, shi ko har ya amshi Akwatunanta yayi
booth din mota da su, sannan ya dawo ya bude mata back seat, zata yi magana sai
ta hango AJ zaune front seat din motar, ta Ιan yi jim, sai kuma ta fasa cewa
komai, ta tafi ta shiga motar, hotel drivern ya kai su kasancewar next
available flight to lagos na karfe bakwai na magrib ne, dakin da aka biya mata
na downstairs, shi kuma AJ sama taga ya tafi, All this while kuma bai ce mata
komai ba, ita dai tana son ce masa ta gode amma bai bar space din hakan ba, ko
tsayawa bai yi ba balle tayi godiyan, sai da driver din ya amshi passport din
ta da zai mata booking din jirgi tare da AJ zuwa kano sannan ya bar hotel din,
bayan Khaleesat ta shiga dakin babu dadewa aka kawo mata lafiyayyen lunch, duk
da tana jin yunwa bata iya ta ci da yawa ba she is just restless, taje bandaki
ta wanke baki tayi wanka ta dauro alwala ta fito, bayan ta saka wasu kayan tayi
sallah sannan ta dau handbag ta bude zata ciro lip gloss dinta, a nan taga
kudin da Jay ya saka mata, ta dinga kallon kudin ko kiftawa bata yi a sanyaye.
Karfe shidda da yan mintuna drivern ya sake zuwa ya daukesu ya maida su
airport, daga nan kuma suka hau jirgi zuwa garin kano, inda suka sauka airport
din Aminu kano karfe tara saura na dare, this time around ma sai da drivern da
ya zo daukan AJ ya sauka yayi mata magana tare da kai akwatunanta booth, ita
dai tana ta tsaye don taxi kawai ta so dauka da zai kai ta gida, ganin drivern
ya bude mata back seat ta karasa jiki a sanyaye ta shiga motar, sai da suka
fita daga Airport din drivern ya kalleta ta madubi yace "Ranki shi dade
wani anguwan za a ajiye ki?" Khaleesat ta Ιan kalli AJ dake zaune gaban
motar yana danna wayarsa, sai kuma ta kalli drivern tace "Inda zan je da
nisa, kar in bata maku lokaci gashi dare yayi, duk inda ka samu kawai ka ajiye
ni zan samu abun hawa" Sai a sannan AJ yace "Ce maki yayi sauri
yake?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma tace "Ni Mariri zan je"
Driver yace "Toh Allah ya kai mu lafiya Hajiya" Bayan tafiyar kusan
minti arba'in suka iso Maririn, A hankali Khaleesat dake kallon drivern tace "Zan
iya sauka a nan sai in karasa cikin layin saboda kar ku shiga baku samu wajen
juyawa ba...." Drivern yace "Layin baya bulla ne? In dai yana bulla
babu damuwa za mu samu hanya in sha Allah" Tace "Toh shikenan,
nagode" Nan ta nuna masa inda zai bi ya shiga unguwan, shi dai AJ kallon
ikon Allah kawai yake without uttering a word, haka jama'an anguwan suka dinga
bin motar da ya dalle ko ina da haske da kallo, ba ko wani mai mota bane zai
yarda ya shiga hanyar nan da motarsa cause driving is uncomfortable there in
baka yi hankali ba sai ka goge motarka, gashi gidan nasu can ciki ciki ne, at
last dai tace "Kawai in ka samu waje a nan zan sauka, ga gidan can"
Drivern yace "Toh shikenan Hajiya" Haka ya samu yayi parking motar,
sannan ya sauka zai dauko mata akwatunanta a bayan booth, ta bude motar ta
sauka tana kallon kofar gidansu hankalinta ya Ιan kwanta ganin bata ga Babanta
a kofar gidan ba, kan kace me yara yaran anguwan da suka ga ita ce a motar suka
taho da gudu ana mata oyoyo, haka dai ta samu ta hadasu da akwatunanta sannan
ta zaga zuwa side din da Ajay yake, tana wasa da gefen gyalenta ta kasa
kallonsa tace "Thank you so much Allah ya saka da alkhairi" yace
"Wanda ya hada ki jirgi daya da ni zaki ma godiya, Jay kenan" Sai a
sannan ta Ιan kallesa, bata dai ce komai ba ta juya tana tafiya a hankali ta
bar wajen, godiya tayi ma drivern ta masa kwatancen unguwan da zai shiga wanda
a nan zai samu hanyar billa zuwa titi, yayi mata godiya shima ya shiga mota
sannan ta nufi cikin gidansu gabanta na faduwa, a hankali tayi raising sack din
cement that was use as barrier between the door and inside of the house zata
shiga cikin gidan ta ci karo da kanninta da suka fito yi mata oyoyo da gudu
bayan yara sun shiga da akwatunan ta, a haka suka shiga cikin gidan tare tana
Rungume da su, zazzaune taga kishiyoyin ummanta biyu da 'ya yansu rakacaa a
tsakar gidan har a lkcn ba a sauke tuwon dare ba gashi ana neman karfe goma,
kananun yaransu ne kawai suka taso yi mata oyoyo da gudu, muryar wata
makociyarsu dake zaune cikin gidan taji tana cewa "Ikon Allah sannu da
zuwa Amarya ashe dai kina hanya dama" Khaleesat dai kallonta kawai take
jin abinda tace, taji kishiyoyin ummanta na cewa "Ai ko dai, kinga mu da
muke gidan ma ko gaya mana ba ayi ba balle mu shiga mu fita tahowar nata ya
fasu, kinsan haka aka maida mu a gidan, to ga dai ta mun ganta kamar an jefota,
mun kuma yi murna" Khaleesat ta gaishesu without waiting for response ta
shige dakin Ummanta, zaune ta ganta a bakin kofa Umma dake kallonta cike da
damuwa tace "Khaleesat me ya samu wayarki kusan wata daya? Dama kina hanya
shine Abdul din bai gaya mana ba?" Khaleesat ta rungumeta a hankali tace
"Umma lalacewa wayar yayi" Umma ta dago kanta tana kallonta tace
"To shi ya dauko ki a tashar jirgin?" Khaleesat ta sauke idonta tace
"A'a" Muryar kawar Ummanta da taji a dakin yasa ta daga kai don bata
ma san tana ciki ba, Khaleesat ta gaisheta da murmushi, Mama Salame ta amsa da
fara'a tace "Ashe dai kina hanya amarya" Khaleesat tace "Amarya
kuma Mama?" Mama Salame tace "Au shi Awdul din bai gaya maki ba dama,
ai yau ana saukowa sallan juma'a aka daura auran ku"
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
[5/26, 9:48 AM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat ta
kwala wani karan da ya gigita Ummanta da Mama Salame, Umma ta mike da sauri
tana kallonta a kidime, haka ma Mama Salame da tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, menene haka Khaleesah?" kishiyoyin Umma duk suka yo dakin
a guje su ma don Khaleesat bata fasa ihun da take kwalawa ba cikin tashin
hankali take cewa "Wallahi bana son shi bazan iya zaman aure da shi ba, na
shiga uku na lalace, don Allah Umma ku min rai ku rufa min asiri, wallahi bana
son sa" Umma dai sake baki tayi tana kallon Khaleesat tashin hankali
karara a fuskarta gashi ta kasa cewa komai, daya daga kishiyoyin Umma da ake
kira Mama Shatu tana gyara zaninta da ya kusa kwancewa saboda gudun da suka yi
tace "Ji wani gulma da kinibibi? Shi Abdul din ne da ya daukeki ya kai ki
kasan turai karatu yayi ta kashe kudadensa ne baki so yau? A ajiye batun ubanki
a gefe, ke abinda ya kashe maki yau ko kaf kasar da uwarki ta baro za a siyar za a iya biyansa
aka ce maki?" Ita ma daya Co-wive din da suke kira Mama Zubaida tace
"A'a rainin wayo mana Shatu, gwara ai a rena mana hankali, don uwarta
kasuwa ne nan da zata cika mana gida da Ζuwa, wannan ai iskanci ne da
walakanci" Khaleesat bata fasa kuka da ihun da take a dakin Ummanta ba
tana surutai ita kanta bata san takamaiman abinda take cewa ba tsabar tashin
hankali, Kanninta Noor da Islam kuwa har sun fara kuka su ma a dakin, kan kace
me har makota sun fara tururuwan shigowa gidan, aka tsaya cirko cirko bakin
kofar dakin Ummanta ana salallami, Mahaifinta ne Malam Ali ya shigo gidan yana
zazzare ido, shi ma ya karaso da sauri yana tambayar abinda ke faruwa a gidan,
Mama Shatu ta tabe baki tace "Wai er da ta fi kowa ce ta sauka yau daga
Amurka shine uwar ke sanar mata ai an daura aurensu da shi wanda ya kai ta waje
karatu har ta dena ganin kowa da gashi, shine fa ta cika anguwa da ihu da koke
koke wai ita bata son auren bazata zauna da shi ba, ga jama'a na ta shigowa an
zata gobara muke, wannan ai tsabar sangarci da iya shege ne" Juyawa Malam
Ali yayi ya nufi gun da ake ajiye itacen girki da sauri ya suri daya ya dawo ya
nufo dakin Umma yana cewa "Ina take..." Matan makota dake tsakar
gidan suka hau basa hakuri suna don Allah ya kyaleta, yaki sauraron kowa yana
zazzare ido, Khaleesat na hangosa ta tafi bayan Ummanta da gudu tana kuka ta
rungumeta, kanninta ma suka yi bayan Umma gaba daya suna kuka, Mama Salame ta
tsaya tayi bake bake gabansa tace "Haba haba, haba Malam Ali, meye haka
kake kokarin yi?" Yace "Salame ki bar ni dai inci malfar ubanta a
wajen, mu zata tona ma asiri? Ni zata ja ma sabon bala'i da fitinan da ya
girmeni?" Mama Salame tace "A'a wallahi baza ka doketa da wannan
rafkeken icen ba ita ba jaka ba, mu je waje Malam Ali" Ita dai Umma kanta
na kasa bata ce komai ba, haka Mama Salame ta samu ta tasa keyarsa ya fita daga
dakin tana biye da shi, Mama Zubaida ta rike haΙa tace "Ikon Allah, mu
muke ganin kinibibi iri iri a gidan nan, to in aka bibiya wani ta kyallara ido
ta gani a Amurkan shine zata tona ma uban asirinsa da ke rufe, da can menene
yasa ta hakura zata aurensa? Sai ranan da aka daura aure ta nemi tara mana
mutan anguwa tace bata san zance ba? Yau ni nake ganin iskanci, to ta tsotsi
nonon buzuwa ba dole ta iya makirci da kissa ba" Ita dai Khaleesat kuka
kawai take a jikin Ummanta siblings dinta na kusa da ita suna taya ta, Mama
Salame ta sake labulen dakin Umma duk don matan dake tsaye bakin kofar su kama
gabansu, Umma ta juya tana kallon Khaleesat gaba daya ta kasa cewa komai,
zamewa kasa Khaleesat tayi ta hade kanta da gwiwa tana kuka kamar ranta zai
fita tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na
lalace" a sanyaye Umma ta tafi gefen katifar dakin ta zauna ta kasa cewa
komai. Karfe biyun dare Umma na zaune kan darduma da carbi a hannunta,
Khaleesat ta tsallake kanninta ta fito daga cikin net din da take kwance bayan
ta tuna ko isha'i bata yi ba, tunda Mama Salame ta daura mata net tace ta shiga
ta kwanta wajen karfe sha daya take kwance duk da ba bacci take ba, don ko
bacci barawo bata gani ba, amma tayi shiru cikin net din tunani iri iri na yawo
a kanta, gaba daya ta ji kamar hawayenta ma ya kafe, har a lkcn babu maganar da
ya hadata da Ummanta, tana jin jiri da zazzabi ta nufi kofa zata fita ta dauro
alwala, Umma dai ta bi ta da kallo, bayan ta dauro alwalan ta dawo ta saka
hijab dinta ta tada sallah, bayan ta idar tayi nafila raka'a biyu, tana zaune
kan darduman ta jingina da bango tayi nisa tunanin da take, gani take kamar a
mafarki ake sanar mata an daura mata aure da Abdul amma ta ki farkawa daga
mummunan baccin nan har yanzu, muryar Ummanta yaji ta kirata a hankali,
Khaleesat ta juya ta kalleta amma ta kasa amsawa, Umma ta mike ta koma kusa da
ita ta zauna tana kallonta, cikin sanyin murya tace "Me ya faru kuma
tsakaninki da Abdul din Khaleesat? Wani abun ya kara maki? Me yasa kika ce baki
son auren?" Khaleesat ta fashe da kuka a hankali tace "Umma wallahi
bana son sa, bazan iya zama da shi ba, in aka ce za a kai ni gidansa zan iya
mutuwa wallahi, don Allah Umma ku taimakeni ku yi min rai" Umma ta kasa ce
mata komai hawaye ya cika idonta ta fara gogewa da hijab dinta, Khaleesat ta
daura kanta kan kafadar Ummanta tana kuka me tsuma zuciya tace "Don Allah
ku taimakeni Umma, bazan iya ba wallahi" Umma ta rungumeta tana patting
bayanta ita ma hawayen na sauka idonta amma bata iya ta ce mata komai ba, they
sat there for almost 40 mins, jin tana sauke numfashi a hankali Umma ta gane
bacci tayi, a haka Umma ta zauna wajen Khaleesat na jikinta don bata son
tashinta har kusan lokacin sallahn asuba. Da safe wajen karfe tara Umma ta
shigo dakinta rike da cup din kunu da kosai a roba, ta karasa kusa da Khaleesat
dake kwance gefen katifarta ta ajiye mata sannan ta zauna cikin kwantar da
murya tace "Ta so ki ci ko kadan ne Khaleesat" Khaleesat dai kallon
cup din kunun kawai take, lkci daya hawaye ya cika idonta, Umma dai ta sunkuyar
da kai, Islam ce ta shigo dakin rike da paracetamol da Umma ta aiketa ta siyo
ma yayar tata, ta zauna kusa da Umma tace "Umma ga maganin na siyo ma
Aunty" Umma ta amsa ta ajiye a gefenta tace "Tashi ki je ki karasa
min aikin da na sa ki" Islam dake kallon Khaleesat ta mike a hankali ta
fita daga dakin, Umma ta maida dubanta kan Khaleesat tace "So kike ki sa
ma kanki wani ciwon ne Khaleesat nima ki sa min damuwa? Ki tashi ko kunun ne ki
sha" Khaleesat ta girgiza mata kai cikin rawan murya tace "Ni bazan
iya sha ba Umma" a sanyaye Umma tace "Toh ya kike son in maki
Khaleesat?" Umma ta kasa ci gaba hawaye ya fara sauka idonta ta dafe
kanta, kuka kawai Khaleesat take tana kallon Ummanta, Umma ta dake tana share idonta
tace "Ko wajen Nenne zaki sai ki gaya mata ki ji abinda zata ce, ni kin
san babu abinda zan iya yi akan lamarin nan Khaleesat" Ita dai Khaleesat
bata ce komai ba, Umma ta mike a sanyaye ta fita daga dakin don juye mata ruwan
wankan da ta dora mata a kan wuta yana ta tafasa, a haka ta ta dawo ta samu ta
lallabata ta Ιan sha kunun sannan ta tafi waje yin wanka, kafin ta fito har
Umma ta fiddo mata kayan da zata sa tayi tagumi tana jiranta, karfin hali kawai
Khaleesat take amma ji take kamar zata iya collapse at anytime, bayan ta shirya
Umma tace "Amma bana son yan gidan nan su san inda zaki, kar su gaya ma
Malam" Khaleesat ta jinginar da kanta da bango, a hankali tace "Umma
bazan iya zuwa ni kadai ba don Allah ki rakani" Umma tayi shiru, can tace
"To zan fita in shiga gidansu Er Lami in jira ki a can, bana son su ga mun
fita tare, bayan na fita da minti goma kema sai ki fito" Kai kawai
Khaleesat ta gyada mata, Umma ta mike ta dau hijab dinta ta saka sannan ta dora
nikab ta fita daga dakin, Su Mama Shatu da Mama Zubaida suna ta girka abincin
siyarwansu da yaransu za su fita talla da shi, tace masu zata shiga makota
sannan ta fita, duk suka bi ta da kallo sun tabe baki, Mama Shatu tace "Ma
ji ma gani dai, a sanda ake mana fafa an tura 'ya kasar waje ga namu yaran a
zube ai babu bakin cikin da ba a kuntsa mana ba" Mama Zubaida tace
"Sun gana tattatse Ιan mutane rana daya su fito su ce basu san zance ba,
ke ina kika taΙa ganin anyi haka? Ai na so Malam ya rarrade shegiya jiya da
daddare, to dai ba kanta kadai zata ja ma babban magana ba, har shi Malam
din" Duk Khaleesat na jin su, ita dai tana zaune ta jinginar da kanta da
bango tana sauke numfashi a hankali, bayan minti goma da fitar Ummanta ta tashi
da kyar ta fiddo gogaggen Hijab dinta ta saka sannan ta dora Nikab ta fita daga
dakin, tunda ta fito suke kallonta, a haka ta nufi hanyar fita daga tsakar
gidan tana ji kamar iska zai kadata ta fadi. Gidan da Ummanta tace zata jirata
ta nufa, ta samu Ummanta a tsakar gida tana jiranta yan gidan ma duk basa nan,
Umma ta taso suka fita daga gidan, tafiyar kusan minti sha biyar ne zuwa gidan
Nenne daga gidansu, Nenne ta ajiye tsintsiyar hannunta tace "Dawowa yayi
da ita daga inda take karatun don an daura aure?" Umma ta zauna kan
tabarman tsakar gidan ta cire Nikab din fuskarta ta gaida Nenne, Khaleesat ta
zauna gefen Ummanta, Nenne ta amsa tace "Ai dama nace ko da ta dawo sai ta
huta an kintsa ta kafin ayi maganar wata tarewa tunda yace baya bukatar taron
komai, amma baza mu dau yarinya haka kawai ace an je kai ta ba" Umma dai
tayi shiru bata ce komai ba, a hankali Khaleesat ta cire Nikab din fuskarta ta
ajiye, Nenne ta Ιan duka tana kallonta tace "Lapiya naga idanuwanta sun
kumbura haka, me ke faruwa?" Umma ta sauke ajiyar zuciya ta kasa cewa
komai, A fusace Nenne tace "Magana nake ku ka min shiru fa? Meye haka aka
shigo min da ita da kumburarrun ido" Cikin rawan murya Khaleesat tace
"Nenne ni bana son sa, bana son auren..." Nenne ta saki baki tace
"Baki son auren kuma?" Khaleesat ta gyada mata kai hawaye wasu na bin
wasu a kuncinta, Nenne ta nemi waje ta zauna tace "Atoh dai, ni dama
shegen bai taΙa kwanta min ba, amma abun dubawa a nan shine na isa da Alin?
Ashe ma ba er banza bace ni a gunsa kenan" Nenne ta mike ta shiga dakinta
ba a dau lokaci ba ta fito ta dire wani babban ledan hannunta sannan ta bude
tace "Kun dai ga duk wata shegiyar kyautarsa da yake kawo min ban taΙa
amfani da ko daya ba duk na tara masa kayansa waje daya, ga atamfofinsa nan da
turarurruka da tarkace, ba ruwana ban yi amfani da su ba, ke ma Zahra'u inda
abunsa da kika san ya taΙa baki ki tattaro su waje daya, shi Ali ina ma yayi
amfani da nasa shi ya sani, sai ya shiga kasuwa da wuri wuri" Ita dai Umma
tayi shiru bata ce komai ba, Khaleesat kuwa kuka take a hankali, Cikin sanyin
murya Umma tace "Kin mance abinda ke kasa ne Nenne, ai yanzu ba maganar
wai abinda ya bamu bane damuwar" Nenne tace "Yo ina ruwana da abinda
ke Ζasa, ko ina ruwan yarinya da abinda ke kasa? Sai a ma jikata auren dole
kike nufi kenan? Ni fa tun asali katon mutumin nan bai min ba sam, ayi mutum ba
fara'a ya shigo maka sandan sandan ya fita gansan gansan? A duba fa wannan
lamari, da kyar kaga murmushinsa kamar rikakken Ιan ta'adda da aka kusa yi ma
preedom, yo wannan uban kudi na ubansa wa ma yasan ko ta'addancin suke da
garkuwa da jama'a, hatta ruwan gidana gansamemen mutumin nan bai taΙa sha ba,
yanda na ajiye masa haka yake barin min tsiyata bai san yarana mata ruwan gora
suke siya min ba ya zata durawa nake, haka zai zauna maka kamar sarki yayi ta
danna waya ga gidan er banza ya shigo, to ban isa da Ali ba kannensa mata ma
basu isa da shi ba, shi kawai ta kansa yake a rayuwar nan baya duba makomar er
da ya haifa a cikinsa, ko dan yaga yaran rakacaa an haifa masa ne ba kwantrol
oho, gashi ba jin maganar yayyin uban nasa zai yi ba balle ince ku je ku
samesu, in kuma muka ce mu tafi mu kai rahotu gidan yan sanda daga karshe mu za
a kulle, to ni Ramatu ya zan yi? Amma dai ba komai zan aika a kira min Alin
anjima, hatta batun daurin auren sai jiya da za a daura muke samun labari"
A hankali Umma tace "Shi ma Malam din shekaranjiya da yamma suka kirasa
suka sanar masa ga abinda suke so za ayi" Nenne tace "Tirrr, duk sun
rainamu sun mayar da mu yan iska kawai, na tabbata shi kansa Alin bai taΙa
rokon Awdul din naira biyar ba balle uban Awdul" Umma ta girgiza kai tace
"Bai taΙa ba kam, jarabawa ce kawai Allah ya dora mana babu yanda mu ka
iya" Nenne tace "A'a har da dai iskanci, ku baku da baki? ke da er
taki baza ku iya kwatar en cin ku ba, ita kadai ce mace a gidan? Tun asali dama
kin maida kanki gantalalliya a gidan" Umma dai tayi shiru, Nenne tace
"Ko kuma kawai ku tafi gida zan daidaici lkcn da zai koma gida da magariba
in taho gidan" Umma tace "Toh shikenan Nenne" a haka Khaleesat
da Ummanta suka bar gidan bayan Nenne ta dama mata fura da nono ta tilastata ta
sha. Khaleesat na kwance dakin Ummanta wajen karfe shidda na yamma, har zuwa
sannan ta kasa cin komai tun bayan furan da ta sha gidan Nenne, tun da suka
dawo gida take karatun qur'ani don ta rasa me ke mata dadi a duniyar kawai bata
son tayi ta daga ma Ummanta hankali yasa ta hakura da kuka sai na zuci kawai da
take yi, gaba daya taji duniyar yayi mata zafi, da ta tuna wai fa ita matar
aure ce yanzu kuma matar Abdul, sai taji dama kawai Allah ya dau ranta ta huta,
bayan taji she is exhausted da karatun qur'anin da take tayi shine ta kwanta
gefen katifar Ummanta, tayi nisa tunanin da take jin hawaye na taruwa idonta ta
mike zaune tana kallon Ummanta dake gyara kayan su Islam a dakin tace
"Umma ina wayarki?" Umma ta kalleta tace "Ko sati ba ayi ba na
nemeta na rasa an dauke a gidan nan" Khaleesat tayi shiru tana kallon
Ummanta, sai kuma ta jawo handbag dinta a hankali ta bude ta ciro wayar da Jay
ya bata duk da babu SIM card a ciki, she just want to do something that will
keep distracting her from her worries, har zata shiga game sai kuma ta fasa ta
shiga gallery din wayar, ta Ιan yi jim na few seconds kafin ta bude hotunan, a
hankali take flipping tana kallon each and every image of him and AJ, sai a
sannan ta lura da kaman da suke yi even though it's not obvious, wani hotansu
tare ta tsura ma ido ganinsu cikin shiga ta alfarma irin ta sarauta, ita dai
tana ta kallon hoton babu ko kiftawa, sai kuma tayi flipping zuwa next image,
haka ta dinga ganin ire iren hotunan, wani taga Jay shi kadai wani taga Ajay
shi kadai, ko kuma ta gansu tare, with horses and so many things related to
gidan sarauta, kashe wayar tayi a hankali ta mayar cikin jakarta ta ajiye jin
muryan Babanta ya shigo gidan, ya Ιaga labulen dakin Ummanta yana kallonta yace
"Ki fita ga Abdul can ya zo yanxu" Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta
dinga kallon Babanta bata ko kiftawa, Umma ta juya ta kallesa tace "Ta
fita kuma Malam? Dama ana haka? Ai ina ga ba sai ya zo ba sai ya jira har zuwa
sanda zata tare ko" Malam Ali da ya bude baki yana kallonta yace
"Wato dai duk wani salon dauko min magana kun iya shi Zahra'u, in ya zo ta
fita sai aka yi yaya? Addini ne ya haramta hakan ko kuwa shirmen ku? Kuma da
kike batun tariya ko gobe yace yana bukatar ta tare mu muna da ja ne
dama?" Umma tace "Ai ko muna da ja Malam, tunda baza mu dau yarinya
haka kawai mu kai ta dakin miji ba, duka duka ma yaushe ta dawo kasar"
Khaleesat ta fashe da matsanancin kuka tana jin kamar zuciyarta zai fashe ta
huta, Babanta da ya bude baki yana kallonta yace "Ni kike neman tona ma
asiri ko ko ya kike so inyi? Sabon magana za ku ja min ke da uwarki kenan? In
ma ba yanzu za a tare ba tunda ya zo ai sai ki fita ku gaisa tunda ba haramun
bane, in kun gaisa sai ki dawo cikin gida" Khaleesat taki cewa komai sai
kuka take, Ya daka mata tsawa yace "Kar ki ga ina lallabaki don uwarki,
zaki tashi ki fita ko sai na rarrade ki da icce" Khaleesat na kuka ta
sauka daga kan gadon, Umma da hawaye ya cika idonta ta kauda kanta, Khaleesat
ta dau Hijab dinta ta saka ta fita daga dakin tana kuka sosai, Kishiyoyin
ummanta dake zaune tsakar gida duk suna sauraron abinda ke faruwa sai tabe baki
suke, ganin Malam Ali ya bi bayan Khaleesat, Mama Shatu tace "To rakata
wajen nasa zaka yi ne Malam?" Sai kuma ya juyo da sauri yace "Au
to" Ya nufi Ιan karamin dakinsa dake tsakar gidan, Mama Zubaida ta tabe
baki tace "Ma ji ma gani dai" Khaleesat na fita kofar gida hawaye na
sauka idonta taga motarsa wanda ke dauke da tinted glass yayi parking dai dai
inda su AJ suka tsaya jiya, ko saukowa bai yi daga cikin motar ba, hawaye na
bin fuskarta ta tafi ta tsaya kusa da motar taki budewa kuma tasan yana
kallonta, after almost 5 mins taga ya sauke glass din motar yace "Ni zan
sauko in same ki?" Ita dai taki kallonsa, kuma taki cewa komai, after few
seconds ta bude gaban motar a hankali ta shiga amma ta ki kulle motar, yace
"Sauron unguwan ku zaki cika min a motata, are you in ur right
senses?" A hankali ta ja motar har sannan taki yarda ta kallesa ta kulle,
gabanta sai faduwa yake don jin muryarsa take kamar ana tsira mata allura a
kunne, Lokaci daya ta juya da sauri tana zaro ido ganin ya zuge glass din ya
tada motar ya kara volume din sautin da yake ji sannan ya ja motar, a rikice ta
fara kokarin budewa motar taji a kulle gam, ta kwala wani azababben kara tace
"Na shiga uku na lalace, don girman Allah kayi hakuri ka rufa min asiri
ina zaka kai ni? Ka bude min in sauka...." Ko kallonta bai yi ba fuskarsa
babu yabo babu fallasa yake driving dinsa idonsa na kan hanyar dake gabansa, ta
rikosa da hannu biyu cikin gigicewa tana masa magiyan ya bude mata motar, bai
yi wata wata ba ya sauke mata wani lafiyayyen back hand slap a fuska, sai da
taji dumm na few seconds, lkci daya jin ta da ganinta ya dauke na Ιan lokaci,
duk da haka bata sake sa daga rikon da tayi masa ba tana kururuwan ya bude mata
motar, ya fincikota ya jefar kan kujeran motar cikin kaushin murya yace
"Kika sake taΙa ni sai na wanka maki wani marin" Lokaci daya duk
jikin Khaleesat ya mutu saboda shock, ta dinga sauke numfashi da kyar idonta na
ganin dishi dishi daga marin da yayi mata tana kallonsa, shi dai driving dinsa
kawai yake fuskarsa babu yabo babu fallasa......
[5/26, 9:48 AM] khaleesat Haiydar π✍️: Sai da
Khaleesat taga sun bar unguwansu gaba daya sannan reality yayi hitting dinta ta
kara fahimtar me Abdul ke da niyyar yi, she felt so helpless at this point, ta
jinginar da kanta jikin kujeran motar hawaye masu zafi na sauka idonta ta kasa
cewa komai, shi dai driving dinsa kawai yake bai ko kalleta ba, ganin tafiya
kawai yake ta juya tana son ko hakuri ne ta bude baki ta basa amma tsoron kar
ya sake marinta yasa ta kasa don babu alamar rahama a fuskarsa, ta rufe fuskarta
da hijab din jikinta hawaye wasu na bin wani a idonta, tsabar tashin hankali da
firgicin da ta shiga a wannan moment din kilan da za a duba jininta za a ga ya
hau, bayan tafiyar kusan minti talatin taji ya tsaya cak, da sauri ta sauke
Hijab dinta zuciyarta na bugawa tana kalle kallen inda suke, taga dai dai wani
eatry ya tsaya, ita dai kallonsa take har sannan hawaye bai daina sauka idonta
ba, ya sauka daga motar without looking at her ya kulle, ta bi sa da kallo har
taga ya shiga gidan cin abincin, ta fashe da matsanancin kuka tana waige waigen
wajen cikin tashin hankali, babban wajen cin abinci ne sosai, ga mutane suna ta
kai kawo a gurin, glass din motar ta fara bubbugawa da hannunta amma taga
nobody is noticing her, ta fara kalle kallen cikin motar taga bunch of keys da
ya ajiye ta dauka da sauri ta fara bubbuga glass din motar da shi da karfi,
hakan ya ja attention din wani mutumi da ya fito daga cikin eatry din zai shiga
motarsa dake kusa da inda Abdul yayi parking, ita dai bata fasa bubbuga glass
din ba tana kuka sosai tana cewa don girman Allah ya taimaketa, da alama baya
ganin cikin motar saboda tinted glass din, ya zaga ta gaban motar yana duba
ciki, ta dinga kuka tana cewa don Allah ya taimaketa, ba ta damu ko yana jin
abinda take cewa ba ko baya ji ita dai kawai ya taimaketa, mutumin ya tafi ya
taho da wani security dake wajen, dai dai nan wani soja da ya fito eatry din
zai shiga motarsa shi ma ya karasa gun motar kan kace me attention din jama'an
dake gurin gaba daya ya dawo kan motar Abdul, Khaleesat bata fasa kukan da take
ba duk da ta samu relieve ganin mutanen da suka zagaye motar wasu na kokarin
mata magana suna haska cikin motar da fitila, mutane duk suka tsaya aka yi
cirko cirko a kusa da motar, ita dai kuka me sauti kawai take kamar ranta zai
fita, babu wanda bazai ce sato ta aka yi a lkcn ba, bayan wasu mintuna Abdul ya
fito daga Eatry din rike da abinda ya siyo, yana zuwa inda yayi parking yaga
jama'a jikin motar ya tsaya yana kallon ikon Allah, Security din dake tsaye
wajen don yaga sanda Abdul yayi parking ya shiga eatry din, ya kalli sojan dake
tsaye yace "Ga me motar nan ya fito" Da wani expression Abdul yace
"What happened?" Sojan yace "Bude motar ta sauko Malam"
Abdul yace "Ban gane in bude mota ta sauko ba, matata ce a ciki"
Sojan yace "Ai bamu mu sa ka ba, mota kawai zaka bude ta sauko, ba wani
abun tashin hankali bane ai" Nan jama'an wajen suka dinga cewa ya bude
motar suna hayaniya, Abdul ya bude motarsa da Key din hannunsa daga inda yake
tsaye, Khaleesat na jin alamar yayi unlocking din motar ta bude ta sauko da
sauri tana kuka, Sojan ne ya fara mata magana yana nuna mata Abdul yace
"Waye wannan?" Ta fashe da matsanancin kuka muryarta na rawa tace
"Ni ban san shi ba" Kallonta Abdul ya dinga yi da mamaki babu ko
kiftawa, hayaniya sosai mutanen wajen suka hau yi sojan na kokarin calming
dinsu, Sai kuma ya sake kallon Khaleesat yace "Baki san shi ba? To garin
yaya kika shiga motarsa?" Tana shessheka tace "Kawai dauko ni yayi a
unguwanmu wallahi, ni ban san shi ba" Tuni matasa yan zaman kashe wandon
dake wajen suka fusata suka zagaye Abdul suna dure duren ashar suna kokarin
fara mazgarsa, gaban Eatry din ya cika da jama'a an zo kallo wasu har sun fara
video, with the intervention of the soldier and the security men da wasu responsible
mutanen dake wajen aka saka Abdul cikin motar Sojan don tsaf sun kula matasan
za su yi aika aika ne a wajen, wannan opportunity din Khaleesat tayi using
cikin dubara ta sulale cikin jama'ar wajen without letting anyone to notice her
don gaba daya hankalin mutane ya koma kan Abdul a wajen, a haka ta samu ta
tsallaka titi ko waigawa bata yi ta afka wani layi, nan ma tayi ta tafiya da
sauri da sauri gabanta na faduwa, duk inda taga alamar hanya ce haka ta dinga
bi ba tare da tasan inda zata ba, tafiyar kusan minti arba'in tayi a kafa
hawaye na zuba idonta, ko sanin unguwan da take bata yi ba, daga karshe tsabar
yanda ciwon kai ya matsa mata ga jiri dake ta kwasarta ya sa ta samu gaban wani
gida ta zauna ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kuka, tana ta zaune for
almost 10 mins wani mutumi dake Ιan nesa da ita yana zaune kofar gidansu ya
mike ya nufota, don tun da ta shigo layin ta zauna ya ganta, sallama yayi mata
ta dago kanta a tsorace, yace "Baiwar Allah lafiya dai ko?" Ta
girgiza masa kai da kyar tana goge idonta tace "Bana jin dadi ne, kuma
gida zan je" Yace "Ikon Allah, to ina ne gidan naku?" Without
second thought tace "Hotoro" Yace "Hotoro? To bari in samo maki
adaidaita sahu sai ya kai ki" Ta gyada masa kai cikin rawan murya tace "Nagode"
Ya juya ya bar wajen, bayan wani minti goman sai gashi ya dawo cikin adaidaita
sahu bayan yaje har bakin titi ya samo mata adaidaita sahun, ya sauko daga ciki
yana kallonta yace "Toh ga adaidaita sahun na samo maki Hajiya" Tace
"Nagode" Ta mike da kyar ta dafa adaidata sahun sannan ta shiga ciki,
mutumin ya ciro wayarsa ya mika mata yana kallonta yace "Ki saka min
lambarki sai inji ko kin isa gida lafiya" Ta girgiza masa kai a hankali
tace "Matar aure ce" Mutumin yace "Ohh, na gane to, Allah ya
tsare Hajiya, Allah ya baki lafiya, na biya sa kudinsa ba sai kin basa ba"
Ta gyada masa kai tace "Nagode, Allah ya saka da alkhairi" yace
"Ameen ya Allah" a haka mai adaidaita sahun ya bar layin. Har suka
isa hotoro Khaleesat bata san sun iso ba, sai da me adaidaita sahu ya ankarar
da ita, dai dai kofar gidan Gaje ta sa ya tsaya, ta sauka tayi masa godiya ta
shige cikin gidan, nan gaban Gaje dake zaune tsakar gida ta zuba tana kuka
kamar zata shide, Gaje tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una,
Khaleesah? Me ya faru? daga ina kike haka?" Da kyar Gaje ta lallashi
Khaleesat tayi shiru bayan lokaci me tsayi, sannan ta fara gaya mata abinda ya
faru, Gaje ta saki salati a rikice tace "Mun shiga uku mun lalace, yanzu
gidan yan sanda suka tafi da Awdul din kenan?" Cikin kuka Khaleesat tace
"Ban sani ba nima" Gaje tace "To kuwa zaman gidan nan bai kama
ki ba Khaleesah, yasan bayan gidanku baki da inda zaki taho a kano da ya wuce
gidana ko gidan Nenne, wannan fa ba karamin kess bane, Awdul na zuwa nan ya
ganki sai ya zata da hadin bakina kika yi abinda kika yi, ya sa yan sanda su
kulleni in shiga uku" Cikin kuka Khaleesat tace "Toh ya zanyi yanzu
Baaba Gaje?" Gaje ta mike ta figi gyalenta a igiya tace "Ta shi mu
je" Jikin Khaleesat na rawa ta mike ta bi Gaje suka fita daga gidan, da
kafa suka tafi gidan kawar Aunty Farida da ake ce ma Maman Fu'ad, bayan sun
shiga gidan Gaje tayi mata bayanin duk abinda ke faruwa, Maman Fu'ad tunda ta
rike haΙa har gaje ta gama bada labari bata iya tace komai ba, Gaje tace
"Don haka ki rufa mana asiri Sadiyah ta kwana gidanki zuwa gobe a ga
abinda hali zai yi" Maman Fu'ad ta sauke ajiyar zuciya ta kalli Khaleesat,
gwalo ido tayi ganin jinin da ya kwanta idonta tace "Me ya samu
idonki?" A hankali Khaleesat tace "Marina yayi" Maman Fu'ad ta
saki salati tace "Mari?? Har sai da jini ya kwanta maki a ido? ga lebenki
ma a fashe? A'a gaskiya tsinanne ne wannan mutumi" Gaje ta rike haΙa tana
kallon idon Khaleesat sai kuma ta fashe da kuka tace "Yanzu wannan har
mijin aure ne in ba don Ali ya cuceki ba, dubi fa tafin hannunsa a
fuskarta?" Maman Fu'ad tace "Da kyar ma in baya shaye shaye wannan,
gaskiya duk yanda za ayi a raba auren nan domin ceto yarinyar nan daga halaka,
yanxun nan zan kira farida kuwa" Gaje ta rufe bakinta da sauri tace
"Ki kirata kice mata me? Rufa mana asiri ba wanda yasan tana nan, ina me
tabbatar maki kilan yanzu an tafi da Awdul din police station, kinga ai dole ya
kai yan sandan gidansu Khaleesat don wanke kansa su tabbatar matarsa ce, in
kuma yayi haka ai za a bazama nemanta ne a gari" Maman Fu'ad tace "Ba
komai Gaje, ki tafi kawai ki kyaleta a nan kar su je can gidan naki baki
nan" Gaje ta mike da sauri tace "Don Allah ki bata ruwan zafi in kina
da shi tayi wanka" Maman Fu'ad tace "Kar ki ji komai Gaje" A haka
Gaje ta bar gidan, yanda Khaleesat taga daren jiya wannan daren ma haka ta
gansa, ga ciwon kai, ga ciwon ido, ga zazzabi duk ta rasa inda zata sa kanta
taji dadi, she don't even know who to speak to at this point. Washegari karfe
tara Gaje ta shigo gidan, tun daga bakin kofa ta fara ba Maman Fu'ad labarin
abinda ke faruwa tace "Sadiyah wajen karfe goma suka zo nemanta a gidana
wallahi jiya har da shi Awdul din, ni dai jikina sai rawa yake don tare yake da
yan sanda, yanxu haka daga can Mariri nake, uwarta na can hankalinta a tashe ko
bacci bata yi ba sai koke koke, uban kuma yace da hadin bakin uwar Khaleesat ta
gudu, babu kalan tijaran da Awdul bai yi ba jiya, keee abun dai babu kyau, ni
dai hankalina ya tashi sosai, ina tsoron kar a gano ni na ajiyeta Awdul ya
hadani da hukuma, shine na zo kawai ta shirya tayi hakuri ta koma gida duk
abinda Allah yayi dai dai ne" Khaleesat dake jin duk abinda Gaje ke cewa
ta fashe da matsanancin kuka tace "Don girman Allah kar ki ce masu ina nan
Baaba Gaje, wallahi har duka zai iya min" Maman Fu'ad dai na tsaye da
atamfar mutane da zata yanka ta hau kan keke ta kasa cewa komai sai zazzare ido
take, ita ma tsoro take kar daga karshe ace ai a gidanta aka boye Khaleesat, ta
ina zata fara ma Baban Fu'ad bayani in aka zo tafiya da ita gashi bai gari,
Gaje tace "Toh ya kike so inyi Khaleesah, Awdul fa ya maida maganar nan
babban magana wallahi, wai kin tozartasa a cikin mutane jiya kin sa an tafi
caji opis da shi, ba ki da kowa da zai tsaya maki a lamarin nan sai Allah,
Malam Ali na can kamar zai haukace shi ma ya saka uwarki a gaba sai ta fito
dake" Khaleesat ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kukan, Gaje ta make
hannun Fu'ad dake ta jan yakunannen gyalenta sannan ta ja kujeran tsugunno ta
zauna ta rafka uban tagumi tace "Ni dai ban san kuma yanda zan maki ba
Khaleesah, ina talaka da ni Awdul yasa a daureni wa zai cece ni, sai ma Kinga
kallon da yake min jiya kamar bai yarda da ni ba" Khaleesat ta dago da
kyar tana kallon Baaba Gaje hawaye na sauka idonta, Baaba Gaje dai zai zazzare
ido take tace "Ni ban ma yarda bai sa CID unguwar nan su kula da shige da
fice na ba, yanxu hka sai da na zaga kamar zan je Yan kaba sannan na taho gidan
nan" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "Don Allah Baaba Gaje ki min
alfarman dauko min jakana a can gidanmu" Baaba Gaje ta gwalo ido tace
"Wani jakar?" Khaleesat tace "Karamin jakata, akwai wayata a
ciki zanyi amfani da shi" Baaba Gaje tace "Um um Khaleesat, ta yaya
zan dauko jaka ana gani na da rana tsaka?" Khaleesat ta girgiza mata kai
tace "Karamin jaka ne bai da girma, ko a gyalenki zaki iya boyewa don
girman Allah ki rufa min asiri ki taimakeni Baba Gaje ki dauko min, har da kudi
cikin jakan, zaki ga jakar kusa da akwatina a gefen katifar Umman mu"
Maman Fu'ad dai sai baza ido take taji Khaleesat zata bar gidanta amma shiru bata
ji ba, can dai tace "To ke ina kika nufa daga gidan nan yanzu?"
Khaleesat na share hawayenta a hankali tace "Idan ta dauko min jakar zan
san inda zan je in sha Allah" Maman Fu'ad ta sauke boyayyen ajiyar zuciya,
faridan ma bazata kira ba kar daga karshe a gane ita ta ajiye Khaleesat a
gidanta ta shiga uku, Da kyar Baba Gaje ta yarda zuwa Mariri dauko jakan don
duk a tsorace take, shi ma sai da Maman Fu'ad ta saka baki tunda taji ance in
dai aka dauko jaka to za a bar gidanta, shi sa tayi ta lallaba Gaje taje Mariri
dauko jakar, bayan kusan awa daya sai ga Gaje da jakar ta kudundunosa a
gyalenta, Khaleesat ta amsa jakar ta bude ta ciro wayar Jay dake ciki, ta ga
dollars din da ya bata suna ciki har sannan, Call log ta shiga sai kuma ta
kalli Maman Fu'ad tace "Don Allah ki ara min wayarki bani da Sim card a
nawa" Maman Fu'ad tace "Ai ko babu kati, tunda ga wayar Gaje bari in
bada dari biyu a siyo sai ki saka a nata wayar ki kira" Nan duk dubara
Maman Fu'ad tayi kar a ga Khaleesat tayi kira da wayarta idan bincike yayi
bincike, Gaje ta mika ma Khaleesat wayarta ta fita ta amso mata katin dari
biyun da Maman Fu'ad ta dauko ta bada, Khaleesat na saka katin ta fara dialing
number Jay, ta kira yafi sau biyar sai dai kiran ya dawo mata alamar bai je ba,
bata hakura ba still tayi ta kira baya shiga bata san ko katin ne yayi kadan ba
kuma Number sa na Nigeria yake using a can din ma, wasu sabbin hawayen suka
fara sauka idonta ta sake shiga call log din wayar tana scrolling slowly,
number AJ ta gani shi ma Nigeria Line dinsa, ta Ιan yi jim tana kallon number,
sai kuma tayi dialing tana share hawayen dake zuba idonta, ringing ya fara yi
har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa, sai da ya kusa katsewa sannan yayi
picking, muryarta na rawa tace "Good Afternoon" Shiru yayi, kafin
yace "Wacece?" Ta sauke idonta tace "Ni ce" Yace "Ke
wa?" Da kyar tace "Plss i want to speak to you" Kawai ta fashe
da kuka uncontrollably, shiru yayi for almost 15 seconds, can yace "What
happened?" Tana kuka tace "I need to speak to you pls" Ya kara
yin wani shirun, can yace "Where are you?" Tace "Hotoro" He
still kept quiet for some seconds kafin yace "Address" Katse wayar
Khaleesat tayi ta tambayi Maman Fu'ad address din unguwan, Maman Fu'ad ta gaya
mata sannan ta tura masa ta message, Gaje dake zaune kan kujera tace
"Wanene wannan din da kika kira?" Ita dai Khaleesat tayi shiru wasu
hawayen na taruwa idonta, Baba Gaje tace "Gashi idon naki sai kara ja yake
yi, wallahi makantar da ke kawai yayi niyyar yi matsiyacin nan" Bayan
kusan 35 mins wayar Gaje ya fara ring, Gaje ta mika ma Khaleesat da sauri tace
"Ko wanda kika kira ne?" Khaleesat ta amsa tana kallon wayar taga AJ
ne ke kira, dagawa tayi yace "I am outside" Khaleesat ta ajiye wayar
sannan ta kalli Maman Fu'ad tace "Aunty don Allah kina da Nikab?"
Maman Fu'ad tace "Yaushe rabona da Nikab, bani da shi yanzu kam"
Khaleesat ta mike tana rike da handbag dinta da wayar Jay ta fita daga gidan,
not far away from the house yayi parking, yana jingine jikin motar ya rungume
hannunsa looking at a different direction, tana tafiya a hankali ta nufesa tana
kallonsa, tana isowa kusa da shi ya juya jin Footstep, ya gyara tsayuwarsa ya
dinga kallon idonta babu ko kiftawa, she tried her best na ganin bata fashe da
kukan da ya taho mata ba amma ta kasa daurewa ta hade kanta da jikin motar ta
fara kuka har da shessheka.
[5/26, 9:21 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Ajay bai ce
mata komai ba sai da tayi kukan me isarta don kanta tayi shiru, tana share
idonta ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake har sannan, Calmly yace
"He did all this to you?" Kai ta gyada masa wasu hawayen na taruwa
idonta, yayi shiru for a while kamar me nazari, sai kuma yace "Ζan kano
ne?" Nan ma ta gyada masa kai, yace "A ina yake a kano?"
Muryarta na rawa tace "I don't really know" Zai yi magana Baba Gaje
ta leko kofar gidan kamar munafuka tana zazzare ido, Ajay ya Ιan sauke kansa ya
gaisheta bayan sun hada ido da ita, fitowa tayi da sauri tana kalle kallen
Unguwan tace "Lafiya lau Ιan nan, wallahi yarinyar nan tana cikin mummunan
masifa, bata da kowa sai Allah, ta dawo daga turai ta tarar an daura mata aure
da lafcecen yaron nan Ιan iska, dama kuma duk mun san Ιan iska ne muke kauda
kai tunda bamu da yanda za mu yi, ashe bai ma yi shawara da ita ba kansa tsaye
ya taho ya samu iyayen da ya raina suka daura aure shekaranjiya, to tunda tace
bata son auren in dai ba tsinannen mutumi ba ai sai ya kyaleta ga mata kaca
kaca a duniya, wani mugun kuduri ne a ransa haka da yasa aka daura auren a
gaggauce ko shiri babu? dubi fa abinda ya mata a fuska daga ya dannata a mota
taki bin sa, yanxu haka duk ya baza CID a unguwan nan ana nemanta, sai kaga
tijaran da yaje ya ma iyayen nata jiya da daddare, shi sa ka gan mu duk a
tsorace" Tun da ta fara magana Ajay ke kallonta ko kiftawa baya yi, mamaki
ne sosai kwance a fuskarsa, can ya kalli Khaleesat dake kuka kamar Baaba Gaje
na dada tunzurata, ya sake kallon Gaje yace "Aure kuma Mama?" Gaje
tace "Wallahi da gantalallun igiyoyinsa har uku a kanta yanxu haka, tun
jiya ta gudo nan bayan ta samu ta tsere da kyar daga hannunsa" Gaje ta
fashe da kuka tana matsar kwalla da gyalenta tace "Wallahi bata da kowa
sai Allah, iyayen basu da bakin magana, basu da ta cewa, ni kuma ba kowa bace
makociyarsu ce mun yi zaman Mariri tare kuma ni talaka ce, ni ko taimaka mata
ne kayi ka kai ta wajen masu kare hakkin Ιan Adam ta kai masu kukanta su kwato
mata hakkinta da ake neman tauyewa" Har sannan Ajay ya kasa cewa komai,
can ya bude gaban motarsa yana kallon Khaleesat, Baaba Gaje ta fara tura ta
ciki tace "Maza shiga ku je ya kai ki ofishinsu, in ma rike ki za su yi su
rikeki ki zauna har sai sun bi maki hakkin ki, amma kar ki ce nasan komai, kar
ma ki saka ni a maganar" Khaleesat dai kuka kawai take ta shiga motar,
Baba Gaje ta amshi wayarta dake hannunta ta kulle motar gbamm tace "Maza
ku je" Ajay dai ya zaga ya bude driver seat ya shiga, Da sauri Baaba Gaje
ta koma gate din Maman Fu'ad kamar ba daga kusa da motar ta taho ba, ta makale
tana kallonsu har suka fita daga layin, driving kawai AJ yake idonsa a kan
titi, gaba daya he look speechlesss, tunda ya kalleta sau daya bai sake
kallonta ba, ita dai Khaleesat ta rufe fuskarta da Hijab dinta saboda hasken
rana dake damun idonta kuma tana tsoron kar ace su hadu da Abdul dan motar babu
Tint, har sannan bata daina kukan tashin hankalin da take ba, after driving for
20 mins AJ ya kalli wayarsa dake vibrate, Number Jay ne ke kiransa, hakan ya sa
ya rage tafiyar da yake ya gangara gefen titi yayi parking sannan ya dau wayar
yayi picking ya kai kunne a hankali yace "Jay" Khaleesat ta zame
hijab dinta daga fuska jin sunan da ya kira ta juya ta kallesa, Calmly taji
yace "I am cool" tambayarsa Jay yayi ko ya bar Kano, AJ yace "Am
still around, when are you leaving Maryland?" After few seconds AJ yace
"Alright, we will talk later" Daga haka ya katse wayar ya ajiye ya
jinginar da kansa jikin kujerar motar ya kafe titi da ido for almost 2 mins,
can ya sake daukar wayarsa don duba available flight to Abuja ranan, yaga
jirgin karfe uku kuma saura just few seats, National ID card dinta da passport
dake motarsa tun ranan da suka dawo US da drivern su na Lagos ya amsa a wajenta
don mata booking ticket to kano, ticket ya siya mata immediately na zuwa Abuja
sannan ya ajiye wayar, Aunty na nan gidansu na kano sun zo biki shi sa ma bazai
fara kai ta can gidan ba, juyawa Khaleesat tayi da kyar ta kallesa tana dafe kanta
pleadingly tace "Kanwar Ummata tana Lagos, don girman Allah ka taimakeni i
want to go to her plss" Shi dai kallonta kawai yake, Calmly yace
"Where in Lagos?" Tace "Zan kira in tambayeta, amma bani da
numberta ne" Ya ga alamar gaba daya she is confuse and in fear, yace
"Ta yaya zaki kirata baki da numberta?" Wayarsa ta dauka da sauri ta
shiga call logs dinsa tana duba number Baaba Gaje, dialing tayi yana fara ring
Baaba Gaje ta daga, da sauri Khaleesat tace "Baaba Gaje don Allah number
Aunty Farida za a duba a wayarki sai a turo ta wannan layin" Baba Gaje
tace "Har kun je wajen kare hakkin Ιan Adam din?" Khaleesat tace
"Ki dai turo min don Allah yanxu Baaba" Baaba Gaje tace "Toh
bari in je makota kin san ban san kan wayar ba ai" Khaleesat ta gyada kai
da sauri tace "To ina jira" Katse wayar tayi ta jinginar da kanta
jikin kujera tana sauke numfashi, wani dishi dishi take gani tsabar kuka, Shi
dai Ajay idonsa na kan titi alamar dai kansa ya gama kullewa, ya kalli agogon
wrist dinsa yaga karfe biyu ya gota, driving motar ya ci gaba da yi da tunani
iri iri a ransa ya nufi wani eatry ya sauka ya shiga ciki, Khaleesat ta dinga
bin haraban wajen da kallo sai kuma ta rufe fuskarta da Hijab dinta da sauri
zuciyarta na bugawa, incident din jiya ne kawai ke dawo mata a kai as if she is
hallucinating, sai taga kamar yanzu incident din ke faruwa yanda Abdul yayi
parking ya fita daga mota ya shiga eatry, kan kace me ko ina na jikinta ya fara
rawa taji kamar numfashinta zai dauke, ba a dau lokaci ba Ajay ya fito daga
gidan cin abincin da leda a hannunsa, yana shiga motar ya ajiye ledan da sauri
yana kallonta yace "Me ya faru??" Ta dago kanta hawaye caba caba a
fuskarta, sai kuma ta kamo hannunsa gam tace "I just want to leave here
plss, don Allah mu bar nan" Gaba daya ta dawo kamar warce ta zauce, ya
fara bin area din da kallo tunaninsa ko Abdul din ta gani, can ya sake kallonta
bayan ya zauna cikin motar, cikin nutsuwa yace "Look, stay calm.... You
are safe" Ya gyara mata kujeran motar a hankali ta yanda zata Ιan kwanta
yana kallonta, sai da ya jira for almost 10 mins yaga ta Ιan nutsu tana sauke
numfashi a hankali, lkci lkci yake kallon agogonsa saboda flight din da yayi
booking, after a while ya Ιan duba fuskarta yaga kamar ta fara bacci, tada
motar yayi ya bar wajen, still sai da ya kara tsayawa a pharmacy ya siya mata
magunguna, ko kashe motar bai yi ba don kar ta ma san yayi parking, har yaje ya
dawo kuma bacci take, ya ja motar ya dau hanyar airport hoping jirgin bazai
tashi kafin su isa ba, suna isa airport din bayan yayi parking yaga saura minti
sha biyar kawai jirgin ya tashi kamar yanda suka sa a ticket, tapping din
kujeran motar yayi gently don har lkcn bacci Khaleesat take, a tsorace ta farka
kamar yanda tayi daxu a eatry tana ganinsa kuma tayi shiru tana sauke ajiyar
zuciya, ya bude ledan abincin da ya siya ya ciro mata takeaway din ya bata yace
"Take a little before ur flight..." Ba musu ta amshi abincin tana
kallonsa a hankali tace "Lagos din zan je?" Yace "In kin je zaki
gani" Sai da ya hade mata rai sannan ta ci abincin cokali uku da kyar tana
hadiyewa kamar magani, ya bude drugs dinta ya bata ta amsa ta sha da ruwan
goran hannunta, without looking at her ya mika mata wayarsa yace "Saka min
number mutumin nan" Zaro ido tayi tana kallonsa, yace "Ko bakya ji na
ne?" Kamar zata yi kuka tace "Kiransa zaka yi?" Yace "Amsa
ki sa min number sa nace" Hannunta na rawa ta amshi wayar ta saka masa
lambar Abdul don tana da shi a kanta, ya amshi wayar yana kallon number sannan
ya ajiye wayar yace "Dama an mashi alkawarin aurenki ne?" Ta sunkuyar
da kanta cikin sanyin murya tace "Um, tun shekara hudu da suka wuce"
Shiru Ajay yayi yana kallonta, but because of how cautious he is with time kar
tayi missing flight dinta kawai ya ciro Eye drop din da ya siya mata ya mika
mata ta diga a idonta, tsoro ya sa ta kasa digawa don bata san wani kalan azaba
zata ji ba, daga karshe ya fixge eye drop din babu yabo babu fallasa ya diga
mata a cikin idon, tuni ya sauka daga motar yana jiran in ta gama kururuwan da
take ta sauko, daga karshe ta sauko daga cikin motar tana rufe idon da Hijab
dinta, dayan wayarsa ya mika mata wanda ticket dinta ke ciki, daga ita sai
handbag din ta da wayarsa ta nufi cikin airport din tana waige waige kamar iska
zai kadeta ta fadi, kana ganinta kasan ba dai dai ta ke ba, she is traumatized
and stressed, tsoron Abdul kuma ya gama shigarta sosai, shi dai yana tsaye
jikin motarsa yana kallonta har ya ga shigarta cikin airport din, komawa cikin
motarsa yayi yana duba full name din Abdul ta true caller, wani number yayi dialing
yana fara ring aka daga yace "Zan turo maka wata number yanxu, ina son
kasa a bincika min location dinsa a cikin garin kano, i will be waiting for
feedback" Bayan ya katse wayar ya ajiye ya jinginar da kansa da kujeran
motar, yana nan zaune har bayan 20 mins just to be sure bata yi missing flight
dinta ba kafin ya bar airport din, Khaleesat ta dinga bin cikin jirgin da kallo
kamar idanuwanta za su fito jin anyi announcing za su tashi zuwa garin Abuja,
Abuja kuma? Ita wa ta sani a Abuja? Hawaye ne ya cika idonta ta dinga waige
waigen cikin jirgin, me yasa ya mata booking ticket din Abuja.
[5/28, 8:42 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat na
zaune hall din da jama'a ke jiran Luggages dinsu a Arrival, duk da bata da
kayan da zata jira amma rashin sanin inda ta nufa yasa ta zauna wajen tana bin
kowa da kallo, tun 15 mins ago jirginsu ya sauka Abuja, daurewa kawai take don
wani bacci take ji tare da gajiya, vibration taji a jakarta dake cinyarta
alamar ana kiran waya, a hankali ta bude jakar ta ciro wayar da AJ ya bata tana
kallon screen din, har ya katse bata daga ba don number kawai ta gani ba ayi
saving ba bata san ko ta daga ba ko kar ta daga, kiran wayar da ake ta yi
continuously ne yasa tayi picking tayi shiru tana sauraron me magana taji
namiji ne, ta amsa sallaman da yayi mata, sannan yayi introducing kansa ya
sanar mata shi ne ya zo daukanta Airport, a hankali Khaleesat tace
"Ohk" Mikewa tayi ta fita daga Arrival din tana kalle kallen inda
yace mata yake a Airport din, sai ga shi ya nufota bayan ya gane ita ya zo
dauka, gaisheta yayi da ladabi yace "Babu kaya ko Hajiya?" Khaleesat
ta gyada masa kai kawai, yace "Bismillah, Motar na can nayi parking"
Tana biye da shi suka isa inda motar yake, ya bude mata back seat ta shiga ya
kulle sannan ya zaga ya shiga driver seat, Ita dai Khaleesat ji tayi kawai yana
sanar mata sun iso, bata san for how long suka yi tafiyar ba don bacci ne ya
dauketa throughout the journey, gyara zama tayi tana kalle kallen compound din
gidan da suke ciki, ta kalli Drivern da ya bude mata back seat, ta sauko a
hankali tace "Nagode" Gida ne babba irin na zamani, tana biye da shi
ya kai ta har zuwa Entrance din shiga babban parlon gidan ya danna bell, ba a
dau lokaci ba aka bude kofar wata budurwa ce warce bazata wuce ta ba ta gani
tsaye, da ladabi Drivern yace "Bakuwar da na dauko Airport ce Hajiya"
Yarinyar ta Ιan yi murmushi ta koma gefe tana kallon Khaleesat tace "Sannu
da zuwa sister, come in" Khaleesat ta shiga parlon yarinyar ta kullo kofar
tana nuna mata kujera ta zauna, bayan Khaleesat ta zauna yarinyar na kallonta
tace "I am Inteesar" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kalleta tace
"Sunana Khaleesat" Yarinyar tace "Welcome Khaleesat, bari in ma
Ammin mu magana" Daga haka ta juya ta bar parlon, after a while sai ga ta
sun shigo parlon da wata dattijuwa that is in her middle 50, zamowa kasa
Khaleesat tayi a hankali tana gaisheta, da fara'a matar da ake kira da Ammi ta
dagota tace "A'a, koma kiyi zamanki kan kujera diyata" Khaleesat ta
koma ta zauna kan kujeran, Matar ta zauna kusa da ita tace "Sannu da zuwa,
ya hanya?" Khaleesat tace "Alhmdlh, ina yini" Ammi tace
"Lafiya lau, ya kika baro mutan gidan?" Khaleesat tace "Suna
lafiya lau" Ammi tace "Ai na zata tare da Yariman ku ke, ashe ke
kadai ce" Ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta tayi shiru tana wasa da
gefen hijab dinta, Ammi ta kalli Inteesar tace "Inteesar ki kai ta daki ta
huta" Inteesar tace "Ohk" Tare suka tafi dakin Khaleesat na biye
da ita, Ammi ta bi su da kallo. Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune
daki tare da Inteesar da ta mayar da ita Television, ita dai a hankali take cin
fruit salad din gabanta, tun zuwanta gidan in dai ta kalli Inteesar by mistake
zata ga kallonta kawai take, da sun hada ido kuma sai Inteesar ta mata
murmushi, Khaleesat wasn't bothered da kallon don farkon haduwarsu da Sophie
haka ita ma take mata, tayi ta kallonta a makaranta ko gajiya bata yi kuma da
sun hada ido sai ta mata murmushi, bayan sun zama best of friends ne Sophie ke
gaya mata she is soo beautiful shi yasa bata gajiya da kallonta, sai bayan sun
zama kawaye Sophie ta dena mata maganar kyanta, kuma dama da wuya taje waje
bata ga mutane na kallonta ba, ba maza ba hatta yan uwanta mata haka suke
kallonta, muryar Inteesar taji a hankali tace "You are Beautiful
Khaleesat" Khaleesat ta Ιan kalleta sai kuma ta mayar mata da murmushin da
take mata kawai, Inteesar tace "Sosai fa" Cikin sanyin murya
Khaleesat tace "And you too Inteesar" Inteesar tayi dariya tace
"A'a gaskiya ba kamarki ba, ni dai ina son mu zama frnds in baza ki damu
ba, Ya Prince yace gobe zaki tafi Lagos da safe, don Allah ki bani numberki mu
dinga zumunci ta waya, probably baza ki sake dawowa gidanmu ba" Sosai
Khaleesat taji wani relieve ya zo mata bayan taji Inteesar tace zata tafi Lagos
da safe, dama gaba daya hankalinta yayi gun kanwar Ummanta, Allah ya gani
daurewa kawai take amma ita kadai tasan me take ji both mentally and
physically, tana cikin tashin hankali sosai but she is trying her best to act
normal, Khaleesat tace "Ohk amma nayi misplacing wayana ban yi welcome
back, idan nayi zan amshi lambarki gun sa" Inteesar tace "Ohk to ba
damuwa, amma zaki dade a lagos ne in kin je?" Khaleesat tace "Zan Ιan
yi kwana biyu a can in sha Allah" Inteesar tace "Akwai sisterna dake
aure can, idan baza su dawo gida for New year ba in sha Allah zan je Lagos din
so that i will meet with you there" Murmushi Khaleesat tayi tace "Toh
shikenan Allah ya kai mu lafiya" Inteesar ta tashi ta bude press ta dauko
mata kayan baccinta don dakinta ta kawo Khaleesat, bayan ta ajiye kayan gefen
gado tace "You can change to this idan kinyi wanka, i will be back
later" Khaleesat tace "Alright, thank you so much" Bayan few
minutes da fitan Inteesar Khaleesat ta tashi a hankali ta tafi bandaki, da ta
tuna auren Abdul dake kanta tashin hankalinta ninkuwa yake, sai da ta ci
kukanta me isarta sannan tayi wanka ta fito daga bandakin, ta gama saka kayan
da Inteesar ta bata kenan tana kokarin daure gashinta sai ga ta ta shigo dakin,
Inteesar ta wara ido tace "Waow is all that ur hair Khaleesat?"
Khaleesat dai ta mata murmushin karfin hali tana ci gaba da daure gashinta,
Inteesar that was looking at the hair with fascination tace "Bari in baki
Hair net" Hair net dinta ta dauko ta ba Khaleesat, Khaleesat ta amsa tace
"Nagode sosai" Washegari karfe
tara da rabi na safe Khaleesat ta gama shiryawa tana jiran Drivern gidan, kayan
Inteesar ne jikinta da yake yanayin jikinsu daya babu me cewa ba kayanta bane,
tana zaune gefen gadon Inteesar duk da Hijab ne har kasa jikinta amma sanyi
take ji sosai, ga AC dake dakin a kashe amma she is shivering, tun da ta tashi
da asuba tasan she is not feeling okay, breakfast din ma da kyar ta sha shayi
kawai, ko irish din bata ci ba balle bread, she is trying all possible best to
look alright don kar ayi cancelling tafiyarta zuwa lagos yau, Mai aikin gidan
ce ta Kwankwasa kofa ta sanar mata driver yana jiran ta, Khaleesat ta tashi da
kyar ta dau handbag dinta ta fita daga dakin zuwa parlor, nan ta tarar da Ammi
zaune, Khaleesat ta karasa ta duka kusa da ita tana mata godiya don sosai suka
sake mata kamar da can sun taba saninta, daga karshe dai Inteesar ta bi su har
Airport don rakiya, haka kawai jininta ya hadu da Khaleesat, ita kanta
Khaleesat don bata cikin nutsuwarta ne amma she so much appreciate Inteesar's
care toward her, a haka dai suka rabu kamar sun jima da sanin juna, Khaleesat
ta shiga cikin airport din ta amshi boarding pass dinta don Ajay ya tura mata
ticket ta Email din wayar da ya bata hade da hoton National ID dinta da yayi
snapping tun karfe bakwai na safe, bayan ta amshi boarding pass dinta ta nufi
Departure Lounge. Karfe sha biyu saura suka sauka garin Lagos, Khaleesat ta
sauka a jirgi da taimakon wata mata don zazzabi ne sosai ya rufeta but she is
still pretending to be fine, a haka suka fito Airport din daga Arrival matar na
tambayarta za a zo daukanta ne ko Taxi xata hau, Kafin Khaleesat tace komai ta
hango wani kamar AJ tsaye jikin wata mota yana danna wayarsa, sai da ta kifta
ido ta bude to be sure he is the one she is seeing, ta kalli matar kusa da ita
da kyar ta sanar mata yayanta ya zo daukanta, a haka suka rabu da matar,
Khaleesat ta nufi inda ta hango Ajay, sae da ta iso kusa da motar ya daga kai
ya kalleta, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Ina yini" Calmly yace
"Ina wayar da na baki?" Jakar hannunta ta nuna masa tace "Yana
ciki, na sa silent ne" Driver seat ya bude ya shiga sannan ya bude mata
daya side din motar, zagawa tayi ta shiga ta jinginar da kanta ta lumshe ido,
ya tada motar suka bar Airport din, Google map yayi ta using after almost 45
mins ride Khaleesat ta fara gane inda za su, amma kuma sae ko ina yayi mata
sabo a area din ko don she is not stabilize ne bata dai sani ba, ta juya ta
kallesa shi dai driving dinsa kawai yake with the assistant of his google map,
at last suka shigo wani unguwa yayi parking ya dau wayarsa yayi dialing number,
muryar Aunty Farida taji bayan anyi picking, Khaleesat taji kamar an yaye mata
Ζaso tamanin cikin damuwarta jin muryar kanwar Ummanta, bayan few minutes sae
ga ta ta fito daga cikin wani gate, tun da AJ ya hangota daga nesa ya fahimci
da ita yake waya don kana ganinta ka ga Khaleesat, yayi driving din motar har zuwa dai dai kofar
gidan da ta fito, yana parking Khaleesat ta bude motar da sauri ta sauka da
sauran last strength dinta ta nufi Aunty Farida ta fada jikita, Aunty Farida ta
rikota da sauri kafin ta kai kasa, wata makociyarta ce ta taimaka mata suka
rike Khaleesat suka shiga da ita cikin gidan, shi dai AJ na tsaye kusa da
motarsa yana kallonsu har suka shiga ciki, sai kuma ya jingina da motarsa yana
kallon yara dake wasa few houses away, wayarsa ya ciro jin yana ringing ganin
me kiransa ya daga yace "Ya ake ciki?" Daga daya bangaren mutumin
yace "Ranka shi dade sai daxu ya kunna wayar tasa, an kuma duba location
din nasa yana cikin garin Abuja yanxu haka" AJ yayi shiru kafin yace
"Ohk, i will get back to you nagode" Daga haka ya katse wayar ya
mayar aljihunsa, sai ga Aunty Farida ta fito daga cikin gidan, yayi Ζasa da
kansa ya gaisheta, ta amsa cikin sanyin murya tace "Sannu da kokari fa,
Allah ya saka da alkhairi, mu shiga ciki sai mu yi magana ko" Bai ce mata
komai ba ya bi bayanta zuwa cikin compound din, Compound ne me dauke da
apartment uku self contain each, AJ ya tsaya daga balcony din apartment din bai
shiga ba har sai da Aunty Farida ta kara lekowo ta masa magana sannan ya cire
takalmansa ya shiga parlon ya zauna saman kujera yana kallon Khaleesat da ta
juya baya kan 3 seater din da take kwance, Aunty Farida ta tafi kitchen dauko
masa ruwa, ya ciro wayarsa yana dannawa absentmindedly, Sai ga Aunty Farida ta
fito kitchen ta ajiye masa ruwan a kusa da shi sannan ta zauna, da damuwa tace "Sannu
da kokari Junaid, Allah ya saka da alkhairi, mun gode sosai" AJ ya daga
kansa ya kalleta yace "Amma dai kince bai san inda kike a lagos ba ko
Aunty?" Aunty Farida tace "Gaskiya bai san nan gidan ba, tsohon gidan
da na baro ne dai ya sani, shi ma wani lokaci ne da ta zo Lagos dubani bani da
lafiya, ta zo da kwana uku sai ga shi shima ya zo, to yau wata hudu kenan da
barina wancan Unguwan na dawo nan" Ajay dai yayi shiru idonsa a kasa,
Aunty Farida tace "Kuma ba unguwa daya bane, shi wancan Unguwan da na baro
a Ojota ne, daga can zuwa nan ma tafiya ce me zaman kansa, ba kuma wanda yasan
nan na dawo" Ajay yace "Toh shikenan, jikinta da zafi ne?" Aunty
Farida tace "Ehh na ji da zafi sosai gaskiya, makociyata da ta rike min
ita muka shigo yanzu nurse ce, tace zata rubuta min magunguna in siyo
mata" Ajay yace "Ohk, bari zan fita yanzu sai in siyo magunguna da
allurai da drip ayi mata karin ruwa" Aunty Farida tace "To Allah ya
saka da alkhairi, amma baka sha ko ruwa ba Junaid" Ajay ya Ιan yi murmushi
yace "Bari in je in dawo dai" A haka ya fita daga parlon ya tafi
pharmacy ya harhado mata magunguna da drip da allurai. Wata mace ce warce
bazata wuce shekaru hamsin da bakwai ba zaune wani kantamemen parlor cikin isa,
mai aikinta na duke gabanta tana yanke mata kumbar kafafuwanta, cikin fada take
cewa "Banda ma naci irin naka dama ina kai ina er matsiyata? Er talakawa?
Wanda cin yau da kyar na gobe da kyar, ai kai ba class dinta bane ta ko ina,
you just stoop ur self so low Abdul, babu wanda ya isa da kai babu wanda zai
baka shawara ka dauka, na rasa irin wannan taurin kai naka, tun asali i am
against you marrying that poor wretched girl, kuma har gobe ba wai nayi na'am
bane kawai bani da yanda zanyi da kai ne Babana, baka jin maganata ko na ubanka
balle na yayarka, yanxu ina amfanin kaskantar da kai da matsiyaciyar tayi cikin
talakawa yan uwanta a gaban gidan cin abinci, abu har police station, da
mutuncinka da iliminka a maka haka? In zaka dau shawarata yanzu gwara kawai ka
saketa case ya dawo sabo fil, uban me zaka ci da ita kuma bayan wannan abun da
ta maka a idon duniya? Idan yarinya kake so ni duk inda zan shiga zan je in
samar maka yarinya karama da ta fi ta komai kuma er gidan arziki ba tsiya ba,
kai ko Nijar din ne ma ni sai in shirya inje da kaina in samo maka wata buzuwar
er gidan arziki ba talakawa ba, kai ga ma er wata kawata shuwa Arab yanda kaga
ita wannan da makale ma ita ma haka take tass da ita, ga gashi, sannan su ba
talakawa bane" Wata matashiya ce er shekara 39 dake zaune parlon ita ma ta
juya da sauri ta kalli warce ke magana tace "Momy ban gane abinda kike
nufi ba? Wai nufinki ya saketa kenan?" A fusace Momyn tace "Toh uban
me zai ci da ita idan bai saketa ba Meema? Er talakawa ce fa, a kanta aka fara
kyau a duniya ne da bazai rabu da ita ba?" Warce ta kira da Meema ta
girgiza kai tace "A'a wallahi Momy, ai idan ya rabu da ita yanzu ma ita da
iyayenta ne suka ci riba, duk uban hidimar da yayi mata sai kice ya saketa daga
karshe ko tausayinsa ba ki ji ba Momy? Ae wallahi bata isa ya saketa ba, ko don
mu kuntata mata yanda ta kuntata ma Abdul baza mu yi fatan ya saketa ba, dole
sai ta shigo gidan nan, balle shi ba mahaukaci bane da zae saketan, yarinyar da
ya tura har America karatu duk don dai ta zama presentable cikin mutane kar a
mana dariya daga karshe ta saka masa da wannan walakanci da tijara haka?"
Abdul dake zaune parlon shi ma duk yana sauraronsu ya mike yace "In har
aka ga na saketa to bana numfashi ne a duniya, kuma duk inda ma take zata dawo
hannuna nan ba da jimawa ba kuwa, a nan ne zata gwammaci bata taΙa sanina a
rayuwarta ba, i will make life a living hell for her" Momy ta tabe baki
tace "Shi dama talaka ai bai gaji abun arziki ba, shi yasa babu ruwana da
su ko da wasa, hanyar jirgi daban ta mota daban, kai ne da jajibe jajibenka
kasa ubanka ya tafka asaran kusan miliyan dari akan matsiyaciyar yarinyar
nan" Tuni Abdul ya fice daga parlon, Meema na kallon uwarsu tace "Ai
ki ma dena maganar asaran miliyan dari Momy, don yanxu babu wannan zancen
asaran nake ji" Momy dai ta tabe baki tana kallon me aikinta tace "Ke
kar fa ki yanka ni inyi mugun bata maki rai yanzu, ya zaki dinga gaftare min
naman yatsu" Hakuri mai aikin ta hau bata. Wajen karfe biyar na yamma
Khaleesat ta Ιan kishingida a 3 seater, hannunta rike da bowl din pepper soup
din da Aunty Farida tayi mata, gaba daya ta kasa shan pepper soup din Offals
din, don jinsa take kamar magani a bakinta gashi har sannan jikinta babu kwari
ga ciwon kai, ta kalli drip din dake hannunta taga ko quarter bai yi ba amma
har ta gaji ta rasa inda zata sa kanta taji dadi, tun da AJ ya kawo magungunan
da drip ya ajiye ya bar gidan har sannan bai dawo ba, ga abincinsa Aunty Farida
ta zuba a cooler ta ajiye a tray tun daxu tana jiransa, tambayoyi ne da yawa ke
yawo a zuciyar Aunty Farida tana son tambayar Khaleesat ko shine ya taΙa biya
mata jirgi kwanaki da Umma bata da lafiya amma ganin yanayin da Khaleesat ke
ciki ta bar duk tambayoyin nan a zuciyarta, Aunty Farida ta kalli Khaleesat
tace "Ki daure ko kadan ne ki sha, ko in dama maki custard?"
Khaleesat ta girgiza mata kai, dai dai nan aka kwankwasa kofar parlon, Aunty
Farida ta mike ta yafa gyalenta sannan ta tafi ta bude kofar ta koma gefe, da
sallama Ajay ya shigo parlon yana kallon Aunty Farida yace "Tare da
brother dina muke" Aunty Farida tace "To ku shigo mana" a
hankali Khaleesat ta gyara zamanta tana kallon Jay babu ko kiftawa, ganinsa ta
dinga yi kamar a mafarki, Jay ya sauke kansa ya gaida Aunty Farida ta amsa da
fara'a, sannan ya juya yana kallon Khaleesat shi ma babu ko kiftawa, lkci daya
hawaye ya cika idonta tana kallonsa, walking slowly ya karasa har cikin parlon
ya duka gabanta yana kallonta, a hankali yace "Are you feeling better now
Housemate?" Da sauri ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta, and truly
she felt better immediately, shi dai AJ na tsaye yana kallonsu, haka Aunty
farida da ta koma one sitter a sanyaye ta zauna, Jay yayi kasa da murya still
looking at her yace "Kiyi hakuri, everything will be okay soon in sha
Allah, i promise you" Ta gyada masa kai da sauri with so much hope from his
assurance, yana kallon bowl din hannunta Softly yace "Take ur soup"
Ba musu ta dau spoon din ta fara shan pepper soup din a hankali, Aunty Farida
ta kalli Ajay tace "Baka zauna ba Junaid" Ajay ya sauke kansa ya
karasa 2 seater ya zauna, Aunty Farida ta share hawayen da ya cika idonta, da
kyar tace "Mu ma duk ba da son ran mu bane abubuwan nan ke faruwa haka ba,
ba mu da yanda za mu yi ne kawai, amma babu nagartattun iyayen da za su dau er
su su ba Abdul aure"
[5/29, 8:10 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Sai da Jay
yaga Khaleesat ta ci pepper soup din me Ιan yawa sannan ya mike ya koma kusa da
Ajay ya zauna, After a while Ajay yayi breaking din silence din da ya ziyarci
parlon yace "Iya daukar nauyin karatun ta kawai yayi Aunty?" Aunty
Farida zata yi magana wayarta ya fara ring, dauka tayi ganin Umma ce ke kiranta
ta wayar makociyarsu Sha'awa, ta mike ta tafi dakinta don daga wayar, Ajay dai
kallon Khaleesat yake kamar yanda Jay ke kallonta don har ta shanye pepper soup
din, ta ajiye bowl din kasa tana kokarin disconnecting drip din hannunta ta
yanda zata bar cannula din kawai, Jay ya mike yana kallonta yace "What
happened? Do u want to ease ur self" Da kyar tana girgiza masa kai tace
"I think i want throw up" Ya karasa cikin hanzari yayi disconnecting
din mata, ta tashi ta wuce bandakin Aunty Farida da sauri tana toshe bakinta,
sai ga Aunty Farida ta fito daga daki, ta kalli inda Khaleesat ke zaune ganin
bata nan ta kalli kofar bandaki, zaunawa kan kujera tayi a sanyaye tana
kallonsu tayi kasa da murya tace "Yanzu yayata ta kirani wai an zo an tafi
da mahaifin Khaleesat" Da mamaki Jay da Ajay ke kallonta, Ajay yace
"Kamar yaya kenan?" A sanyaye Aunty Farida tace "Baban Abdul din
ne yasa aka je aka tafi da shi" Daga Ajay har Jay kallonta suke with
confusion da kuma mamaki, fitowar Khaleesat daga bandaki ya sa Aunty Farida
tayi shiru bata sake cewa komai ba, bayan Khaleesat ta kwanta kan 3 sitter din
Aunty Farida ta juya tana kallonta tace "Ko zaki shiga daki a maida maki drip
din?" Khaleesat ta gyada mata kai don ita ma ta gaji da kwanciyar kujeran,
Aunty Farida ta mike tace "Bari in ma makociyata magana sai ta sa maki a
daki" Daga haka ta fita daga parlon, after some minutes sai ga ta ta dawo
da Neighbor dinta Bayerabiya, Khaleesat ta tashi ta koma dakin Aunty Farida,
Bayerabiyar ta bi ta ciki ta sa mata drip din, ita dai Aunty Farida na zaune
parlor tayi nisa tunanin da take har makociyarta ta fito ta tafi, Aunty Farida
ta kalli su Ajay a hankali tace "To abinda yayata ta kirani ta gaya min
kenan" Ajay yace "So suke a biya su kudin makarantar da ya dinga biya
mata?" Aunty Farida ta girgiza kai tace "Ai ba iya kudin makaranta
bane Junaid" Ajay yayi shiru yana kallonta, Jay yace "Bayan makaranta
akwai wani abu na kudi da ya hadasu ne?" Aunty Farida tace "Kwarai
kuwa.... Shekarun baya Malam Ali wanda shi ne mahaifin Khaleesat dreban babban
mota ne, babu garin da baya zuwa da kaya a babban mota a fadin Nigeria, kuma
motar tasa ce iyaka idan kana da lodi ya kai maka kayan ka har inda kake so
sannan ka biyasa, har Nijar ya sha shiga da kaya daga nan Nigeria ta haka ma ya
hadu da yayata Aunty Zahra'u warce ita ce mahaifiyar Khaleesat, don mu yan
Nijar ne mahaifinmu har yanzu yana nan da ransa mahaifiyarmu ce dai Allah yayi
ma rasuwa shekarun baya, to bayan ya auri yayata ya kawota Kano Nigeria ya
ajiyeta cikin matansa biyu, bayan en watanni da auren shine na dawo wajen
yayata tunda bata da kowa a Nigeria bata san kowa ba, nan rikona ya dawo
hannunta a lkcn ina da shekara goma, tsangwama da kyara babu irin wanda ban sha
ba a wajen kishiyoyin yayata, gashi bata iya ce masu komai tunda ita ma ba
barin ta suka yi ba, mace ce me hakuri da kauda kai, in zanyi magana ma sai ta
hanani, a haka ta samu makaranta ta saka ni tunda a can kasarmu ina karatu aka
daukoni aka kawo mata, sai da tayi shekara biyar a gidan sannan Allah ya bata
Khaleesat, Mahaifin Khaleesat na da rufin asirinsa sosai don haka bamu rasa
komai a gidan ba sai zaman lafiya da kwanciyar hankali daga kishiyoyinta wani
lokacin har da uwar mijin, jifa jifa mu kan kai ziyara Nijar gun iyayenmu da
yan uwa da abokan arziki, bayan shekaru 12 da auro yayata a lkcn Khaleesat na
da shekara bakwai sai abokan Mijin yayata da yan uwa suka dinga zugasa akan ya
shiga siyasa ya nemi wani babban mukami zai samu tunda yana da jama'a sosai,
kuma ba laifi yayi karatunsa, matansa ma suka dinga zugasa akan ya fito takara,
yayata tayi kokarin ganin ta hanasa tunda bai rasa komai ba a sana'arsa ta
dreban mota amma ya ki, haka nan ya daga babban motarsa ya siyar har da sabon
gidan da ya fara ginawa a nan Ζan Ladi na sidi, ya daga duk en kadarorinsa ya
siyar ya shiga siyasa gadan gadan, duk matansa sai da ya biya masu Hajji suka
tafi da mahaifiyarsa, ya kuma canza ma ko wacce kayan daki, ya ba kowa kudi a
hannu, kusan mutane goma sha biyu ya biya ma Hajji a lkcn, banda matasan anguwa
da ya dinga biya ma kudin makaranta, yayi ta facaka da kudi a karshe dai ya zo
ya fadi zabe, duk wa enda suka dinga zugasa suka juya masa baya, Allah ya rufa
masa asiri bai amshi bashin banki da wani abokinsa ke ta zugasa ya amsa ba
kasancewar da zaben ya gabato bashi da kudi kuma a hannu, bayan faduwarsa zabe
aka shiga yanayi na babu a gidan, cin yau da kyar na gobe da kyar ga yayata na
da cikin yan biyu, dama gidan da yake haya me tsada tuni ya saki bayan kudin
hayan sun kare muka dawo mariri gidan gadonsa da ya bari a walakance don saura
kadan ya kyautar lokacin da yake campaign sai gashi gidan ya mana amfani ya
rufa mana asiri, makaranta me tsada da yaran gidan ke zuwa duk ya ciresu suka
dawo gida suka zauna babu karatu, iyayen basu yi dubaran mayar da su na
gwamnati ba, duk muka shiga mawuyacin hali a gidan, sai sanda ya samu mota yake
lodin kaya ya kai a biyasa, sanda babu mota kuma sai dai kowa ta ciyar da kanta
a gidan, yana kuma fin wata da watanni bai samu ko da karamar mota ba, duk ka
zo kofar gida zaka gansa a zaune babu abun yi shi ma duk ya fita hayyacinsa,
tuni yayata ta siyar da kayan dakinta ta fara sana'a ina taimaka mata, ta kuma
saka Khaleesat a makarantar da zata iya biya don Khaleesat ta taso da kwazo da
hazaka ga ta yarinya ce me shiga rai ko don kalan fatarta, don a unguwan ma
gidan buzaye ake kiran gidanmu, hatta Mahaifinta kiri kiri yake nuna yafi sonta
a cikin sauran yaransa wanda hakan ya ja mata tsana da kyara a gun matansa da
yan uwanta, ko sanda yake da mota a hannu tsaraba na musamman yake ma Khaleesat
ko da bazai yi ma uwarta ba, ana haka yayata ashe duk cinikin da nake sai ta
kwasa ta ba mijinta a boye ban sani ba, ga dai matansa duk da hali na babu da
aka shiga a gidan basu bar yayata ba, kullum cikin hada mata tuggu da makirci
ake wajen miji da uwarsa, cikin wannan yanayi yayata ta haifi yan biyunta wanda
haihuwan da tayi na karshe kenan a gidan, a lkcn matsaloli har sun fi na da,
jarin yayata ya karye kuma babu wani abu da zata siyar ta tada jarin, ga jegon
yan biyu tana yi ga yunwa wani lkcn sai makota ke zubo abinci a kawo mata,
iyayenmu a can Nijar ba masu karfi ba balle su taimaka mana, a haka na bi wata
kawata zuwa nan garin Lagos tana siyar da abinci, kafin nan fa nayi aure har na
fito, duka auren bai cika shekara daya ba, na auri wani abokin mahaifin
Khaleesat, karayar arziki na samun Malam Ali na dinga fuskantar matsaloli gun
mutumin da matansa uku wanda daga karshe ya sakeni dama ba saboda Allah yayi
auren ba saboda kalan fata ta yayi, ina nan Lagos nake tallafa ma yayata da 'ya
yanta uku, don bana son karatun Khaleesat ya tsaya duk da ta samu Foundation
sosai sbda makarantar da ubanta ya sa ta ma a sanda yake da rufin asirinsa yafi
na sauran yan uwanta tsada, na zo Lagos da yan shekaru yayata ta kirani wataran
wai gashi an ba Baban Khaleesat babban mota har zai kai kaya kudu, matsaloli
sun fara warwarewa tunda har an biyasa kudin kai kayan kuma kudade masu tsoka
gashi har ya siya kayan abinci masu yawa ya ajiye a gida, tace in Maza in dawo
gida kawai dama ita hankalinta ba a kwance yake da zamana a lagos ina sana'a
ba, a haka ta takurani har sai da na dawo Kano, a sannan Khaleesat na da
shekaru sha shidda tana kuma gab da gama secondary don da wuri aka sakata a
makaranta, na dawo da wasu kwanaki ranan muna zaune tsakar gida da yamma sai ga
mahaifin Khaleesat an shigo mana da shi ranga ranga ko motsin kirki bai yi,
wanda duk gaba daya mun zata yana hanyar kudu har ya kusa Lagos, ga dai shi babu
ko kwarzanen ciwo a jikinsa kuma wa enda suka
kawosa suka ce ai daga asibiti ma aka taho da shi a can
wajajen garin yarbawa, sannan kwanansa uku a asibiti aka sallamosa wasu mutane
da suka shaidasa tunda dreba ne suka biya kudi aka sako sa a mota aka dawo da
shi Kano, sosai hankalinmu yayi mugun tashi a wannan lokacin, sae da Malam Ali
yayi kwana biyu a gida ana ta addu'a da neman taimako kafin ya farfado gaba
daya har yana iya magana, nan fa yake sanar mana barayi ne suka kwace Trailer
da kayan mutane a ciki bayan sun shaka masa wani farin abu, tashin hankalin da
duk muka shiga bazai misaltu ba a lokacin, daga Trailern har kayan cikin
trailern ya doshi miliyan dari da tamanin" Shiru Aunty Farida tayi tana
goge hawayen dake zuba idonta, Jay that was shock ya kalli Ajay dake kallon
Aunty Farida babu ko kiftawa jin zunzurutun amount din da ta kira, Aunty Farida
na share idonta ta ci gaba tace "A ranan yan sanda sun kusa goma suka zo a
motoci, a haka aka sa ma mahaifin Khaleesat ankwa ana jan sa kamar barawo aka
fita da shi yaransa da matansa na kururuwa suna ihu, Khaleesat kadai ce bata
motsa daga inda take zaune da littafi a hannunta ba sai hawaye kawai, duk aka
cika kofar gidanmu babu masaka tsinke kai kace barawon gaske aka zo dauka, mun
shiga tashin hankalin da baya faduwa a wannan rana, kuma duk mutanen da yayi ta
biya ma Hajji a sanda yake da hali, da kuma mutanen da ya taimaka ma aka rasa
wanda zai bi yaga inda ma aka kai sa, ashe daga kano Abuja aka nufa da shi,
bayan dogon binkice aka gano trailern an yasar a wani gari an kuma juye duk
kayan cikin trailern, dama me trailer daban, me kaya daban, adadin kayan cikin
trailern kuma zai yi na miliyan dari, to ba kowa bane me kayan cikin trailern
nan illa mahaifin Abdul, sam ba a yarda babu sa hannun Mahaifin Khaleesat a
juye kayan cikin trailern ba, dama kuma yan unguwa na jin haushin ya samu lodi
me yawa haka ya tafi kai kayan shi kadai ko yaron mota bai dauka ba, kuma ko
wani dreba an san sa da yaron mota daya ko biyu, nan aka yi ta zuga baban Abdul
akan kar ya yarda wai dama planning Baban Khaleesat yayi don ya taΙa yi ma wani
mutum haka da dadewa yace barayi sun kwace kaya a hanya sai yafewa mutumin
yayi, kuma wai don yaga Alhaji Musa wato mahaifin Abdul me kudi ne sosai shi
yasa zai cucesa yace an sace kaya tunda yanxu ta kare masa bai da komai, kuma
wallahi sharri ne ba haka Baban Khaleesat yake ba, bai cin kayan wani baya taΙa
abu in ba nasa bane, beside bai taΙa sanin Baban Abdul ke da kayan ba sai da
iftila'in ya faru sannan yaga me kayan, shi dai kawai ance masa ga Lodi zai kai
lagos ya kuma amince tunda sana'ar sa kenan kuma kullum fatan samun Lodi yake,
ko da babu zugin yan anguwa baban Abdul bai yi kama da mutumin da zai iya yafe
kudinsa ba don kana ganinsa kasan bashi da mutunci bashi da kirki, sai da
Mahaifin Khaleesat yayi wata uku bamu sa shi a idonmu ba kafin aka dawo da shi
kano duk ya rame yayi baki ya dawo kamar ba shi ba, da kyar aka bari muka gansa
a fursin da aka ajiyesa na nan kano, ranan duk bamu yi bacci ba bayan mun dawo
gida, yayata ta shiga tashin hankali mara misaltuwa don tun dauke mahaifin
Khaleesat dama ta fara alalan siyarwa don mu rufa ma kanmu asiri saboda Ιan
jarin da nake da shi nima duk ya karye bani da komai, kafin ma a dawo da
mahaifin Khaleesat kano sau uku muna zuwa gidan Alhaji Musa a Nassarawa GRA
domin mu basa hakuri ko zai dubi halin da muke ciki ya taimaka a sake mana
Baban Khaleesat amma duk aka mana koran kare, na farko masu gadi ne suka kore
mu, na biyu Matarsa ranan ta rako baΖinta ta gan mu tayi mana cin mutunci ni da
yayata da Baaba Gaje ta sa aka kore mu, na uku kuma Ιan cikinsa Abdul wanda
dama shi kadai ne namiji a 'ya yansa, ana haka aka shiga kotu ko lauya baban
Khaleesat bashi da tunda bamu da halin daukan Lauya, rana na farko da aka kawo
Malam Ali kotu daga prison ni da Khaleesat da kishiyar yayata Mama Shatu ce
muka je kotun don sauraron karan, to a ranan Abdul yaje kotun shi ma a matsayin
daya daga lauyoyin mahaifinsa ashe shi ma Lauya ne, sarai na ganesa da na gansa
a kotun don ranan karshe da muka je gidansu har ce ma masu gadi yayi in muka
sake dawowa su rike mu yan sanda ne za su zo su tafi da mu, zaman kotu da akayi
a wannan rana babu wani positive outcome da ke nuni da cewar da nasara a case
din, kwata kwata babu alamun nasara tunda Malam Ali ba kowa bane, kuma ba shi
da kowa bai da komi, bashi da wanda zai tsaya masa, haka aka dage shari'ar zuwa
wani watan shi kuma za a maidasa prison cikin motar da ta kawosa ko belinsa
anki badawa, Khaleesat ta dinga kuka sosai a haraban kotun tana kallon yanda
aka shigar da babanta motar prison, nima ina rungume da ita ina hawaye, wanda
wannan ne ya ja hankalin Abdul da fitowarsa daga kotun kenan zuwa kanta, ba shi
ba hatta sauran jama'an wajen kallonta suke, Alhaji Musa babban mutum ne kuma
me kudi wannan yasa har da yan jaridu a haraban kotun, wani Ιan jarida ya nufo
mu yana tambayar me za mu iya cewa game da zaman da aka yi yau a kotu, budan
bakin Khaleesat cikin kuka sai cewa tayi Allah ya saka ma babanta sharrin da
aka masa, ina tunanin a nan ne Abdul ya fahimci er gidan wanda suke Ζara ce
Khaleesat, duka duka shekarunta sha shidda a sannan amma duk wanda ya kalleta
sai ya sake kallonta, ranan ma tsautsayi yasa ta fito babu Nikab duk da ba a
shiga da Nikab amma duk inda zata bata fita babu Nikab, in ma bata sa ba uwarta
zata tilastata ta saka, hatta nima bana fita babu shi haka Mahaifiyarta saboda
bakin jama'a, kun ji inda Abdul ya fara ganin Khaleesat, a sannan kuma kawai
motarsa ya shiga, sai wani Lauya me zaman kansa ya nufo mu, ya ja mu gefe yana
kokarin calming din Khaleesat, nan ya tambayeni me ya faru, me ya kawo mu kotu,
nayi briefing din masa komai nima ina kuka, ya tambayeni zuwa yaushe aka daga
karan, na sanar masa, yace to in basa lambata in sha Allah anjima zai kirani
yaga abinda za ayi akan case din kuma mu kwantar da hankalinmu, ko wayar bani
da shi a sannan, instead sai na basa Address din unguwanmu Mariri, ita dai
kishiyar yayata na zaune karkashin bishiya tayi tagumi, a haka muka bar kotu
ranan rai babu dadi muka koma gida, bayan kwana biyu ranan da yamma wajen karfe
shidda muna zaune tsakar gida ko wacce na fafutukar abinda zata dora ta ciyar
da kanta da yaranta, don yanzu kowa takai takai a gidan, kishiyoyin yayata har
sun sake 'ya yan su maza kanana suna fita almajiranci suna ciyar da kansu,
matan kuma a dora masu talla su tafi can bakin kasuwa, yayata dama ina taimaka
mata muna sana'a a gida, kudin waec din Khaleesat ne dai muka kasa hadawa gashi
saura kwanaki kadan a fara, kamar daga sama sai ga Mahaifin Khaleesat ya shigo
gidan kamar an jefosa, Khaleesat ce ta fara ganinsa ta tafi da gudu ta
rungumesa, duk muka mike tsaye a tsorace muna kallon ikon Allah baki bude,
yayata tayi karfin halin tunkararsa tana tambayarsa daga ina yake haka, kar dai
gudowa yayi daga gidan yari, Baban Khaleesat yace kawai shi dai ce masa aka yi
an bada belinsa daxu da rana, sai gashi kuma aka daukosa aka kawo har gida aka
ajiyesa, tsabar mamaki duk muka kasa cewa komai a tsakar gidan, yayata ta kama
hannunsa hawaye cike idonta ta kai sa dakinsa don shi ma duk a firgice yake
kana ganinsa kasan ba karamin wahala ya sha ba, sai a sannan yaran gidan suka
fara ihu suna murnan dawowan mahaifinsu suna ta tsalle tsalle, sauran matan duk
suka bi bayan yayata zuwa dakin Baban Khaleesat"
[5/30, 7:48 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat na
zaune hall din da jama'a ke jiran Luggages dinsu a Arrival, duk da bata da
kayan da zata jira amma rashin sanin inda ta nufa yasa ta zauna wajen tana bin
kowa da kallo, tun 15 mins ago jirginsu ya sauka Abuja, daurewa kawai take don
wani bacci take ji tare da gajiya, vibration taji a jakarta dake cinyarta
alamar ana kiran waya, a hankali ta bude jakar ta ciro wayar da AJ ya bata tana
kallon screen din, har ya katse bata daga ba don number kawai ta gani ba ayi
saving ba bata san ko ta daga ba ko kar ta daga, kiran wayar da ake ta yi
continuously ne yasa tayi picking tayi shiru tana sauraron me magana taji
namiji ne, ta amsa sallaman da yayi mata, sannan yayi introducing kansa ya
sanar mata shi ne ya zo daukanta Airport, a hankali Khaleesat tace
"Ohk" Mikewa tayi ta fita daga Arrival din tana kalle kallen inda
yace mata yake a Airport din, sai ga shi ya nufota bayan ya gane ita ya zo
dauka, gaisheta yayi da ladabi yace "Babu kaya ko Hajiya?" Khaleesat
ta gyada masa kai kawai, yace "Bismillah, Motar na can nayi parking"
Tana biye da shi suka isa inda motar yake, ya bude mata back seat ta shiga ya
kulle sannan ya zaga ya shiga driver seat, Ita dai Khaleesat ji tayi kawai yana
sanar mata sun iso, bata san for how long suka yi tafiyar ba don bacci ne ya
dauketa throughout the journey, gyara zama tayi tana kalle kallen compound din
gidan da suke ciki, ta kalli Drivern da ya bude mata back seat, ta sauko a
hankali tace "Nagode" Gida ne babba irin na zamani, tana biye da shi
ya kai ta har zuwa Entrance din shiga babban parlon gidan ya danna bell, ba a
dau lokaci ba aka bude kofar wata budurwa ce warce bazata wuce ta ba ta gani
tsaye, da ladabi Drivern yace "Bakuwar da na dauko Airport ce Hajiya"
Yarinyar ta Ιan yi murmushi ta koma gefe tana kallon Khaleesat tace "Sannu
da zuwa sister, come in" Khaleesat ta shiga parlon yarinyar ta kullo kofar
tana nuna mata kujera ta zauna, bayan Khaleesat ta zauna yarinyar na kallonta
tace "I am Inteesar" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kalleta tace
"Sunana Khaleesat" Yarinyar tace "Welcome Khaleesat, bari in ma
Ammin mu magana" Daga haka ta juya ta bar parlon, after a while sai ga ta
sun shigo parlon da wata dattijuwa that is in her middle 50, zamowa kasa
Khaleesat tayi a hankali tana gaisheta, da fara'a matar da ake kira da Ammi ta
dagota tace "A'a, koma kiyi zamanki kan kujera diyata" Khaleesat ta
koma ta zauna kan kujeran, Matar ta zauna kusa da ita tace "Sannu da zuwa,
ya hanya?" Khaleesat tace "Alhmdlh, ina yini" Ammi tace
"Lafiya lau, ya kika baro mutan gidan?" Khaleesat tace "Suna
lafiya lau" Ammi tace "Ai na zata tare da Yariman ku ke, ashe ke
kadai ce" Ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta tayi shiru tana wasa da
gefen hijab dinta, Ammi ta kalli Inteesar tace "Inteesar ki kai ta daki ta
huta" Inteesar tace "Ohk" Tare suka tafi dakin Khaleesat na biye
da ita, Ammi ta bi su da kallo. Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune
daki tare da Inteesar da ta mayar da ita Television, ita dai a hankali take cin
fruit salad din gabanta, tun zuwanta gidan in dai ta kalli Inteesar by mistake
zata ga kallonta kawai take, da sun hada ido kuma sai Inteesar ta mata
murmushi, Khaleesat wasn't bothered da kallon don farkon haduwarsu da Sophie
haka ita ma take mata, tayi ta kallonta a makaranta ko gajiya bata yi kuma da
sun hada ido sai ta mata murmushi, bayan sun zama best of friends ne Sophie ke
gaya mata she is soo beautiful shi yasa bata gajiya da kallonta, sai bayan sun
zama kawaye Sophie ta dena mata maganar kyanta, kuma dama da wuya taje waje
bata ga mutane na kallonta ba, ba maza ba hatta yan uwanta mata haka suke
kallonta, muryar Inteesar taji a hankali tace "You are Beautiful
Khaleesat" Khaleesat ta Ιan kalleta sai kuma ta mayar mata da murmushin da
take mata kawai, Inteesar tace "Sosai fa" Cikin sanyin murya
Khaleesat tace "And you too Inteesar" Inteesar tayi dariya tace
"A'a gaskiya ba kamarki ba, ni dai ina son mu zama frnds in baza ki damu
ba, Ya Prince yace gobe zaki tafi Lagos da safe, don Allah ki bani numberki mu
dinga zumunci ta waya, probably baza ki sake dawowa gidanmu ba" Sosai
Khaleesat taji wani relieve ya zo mata bayan taji Inteesar tace zata tafi Lagos
da safe, dama gaba daya hankalinta yayi gun kanwar Ummanta, Allah ya gani
daurewa kawai take amma ita kadai tasan me take ji both mentally and
physically, tana cikin tashin hankali sosai but she is trying her best to act
normal, Khaleesat tace "Ohk amma nayi misplacing wayana ban yi welcome
back, idan nayi zan amshi lambarki gun sa" Inteesar tace "Ohk to ba
damuwa, amma zaki dade a lagos ne in kin je?" Khaleesat tace "Zan Ιan
yi kwana biyu a can in sha Allah" Inteesar tace "Akwai sisterna dake
aure can, idan baza su dawo gida for New year ba in sha Allah zan je Lagos din
so that i will meet with you there" Murmushi Khaleesat tayi tace "Toh
shikenan Allah ya kai mu lafiya" Inteesar ta tashi ta bude press ta dauko
mata kayan baccinta don dakinta ta kawo Khaleesat, bayan ta ajiye kayan gefen
gado tace "You can change to this idan kinyi wanka, i will be back
later" Khaleesat tace "Alright, thank you so much" Bayan few
minutes da fitan Inteesar Khaleesat ta tashi a hankali ta tafi bandaki, da ta
tuna auren Abdul dake kanta tashin hankalinta ninkuwa yake, sai da ta ci
kukanta me isarta sannan tayi wanka ta fito daga bandakin, ta gama saka kayan
da Inteesar ta bata kenan tana kokarin daure gashinta sai ga ta ta shigo dakin,
Inteesar ta wara ido tace "Waow is all that ur hair Khaleesat?"
Khaleesat dai ta mata murmushin karfin hali tana ci gaba da daure gashinta,
Inteesar that was looking at the hair with fascination tace "Bari in baki
Hair net" Hair net dinta ta dauko ta ba Khaleesat, Khaleesat ta amsa tace
"Nagode sosai" Washegari karfe
tara da rabi na safe Khaleesat ta gama shiryawa tana jiran Drivern gidan, kayan
Inteesar ne jikinta da yake yanayin jikinsu daya babu me cewa ba kayanta bane,
tana zaune gefen gadon Inteesar duk da Hijab ne har kasa jikinta amma sanyi
take ji sosai, ga AC dake dakin a kashe amma she is shivering, tun da ta tashi
da asuba tasan she is not feeling okay, breakfast din ma da kyar ta sha shayi
kawai, ko irish din bata ci ba balle bread, she is trying all possible best to
look alright don kar ayi cancelling tafiyarta zuwa lagos yau, Mai aikin gidan
ce ta Kwankwasa kofa ta sanar mata driver yana jiran ta, Khaleesat ta tashi da
kyar ta dau handbag dinta ta fita daga dakin zuwa parlor, nan ta tarar da Ammi
zaune, Khaleesat ta karasa ta duka kusa da ita tana mata godiya don sosai suka
sake mata kamar da can sun taba saninta, daga karshe dai Inteesar ta bi su har
Airport don rakiya, haka kawai jininta ya hadu da Khaleesat, ita kanta
Khaleesat don bata cikin nutsuwarta ne amma she so much appreciate Inteesar's
care toward her, a haka dai suka rabu kamar sun jima da sanin juna, Khaleesat
ta shiga cikin airport din ta amshi boarding pass dinta don Ajay ya tura mata
ticket ta Email din wayar da ya bata hade da hoton National ID dinta da yayi
snapping tun karfe bakwai na safe, bayan ta amshi boarding pass dinta ta nufi
Departure Lounge. Karfe sha biyu saura suka sauka garin Lagos, Khaleesat ta
sauka a jirgi da taimakon wata mata don zazzabi ne sosai ya rufeta but she is
still pretending to be fine, a haka suka fito Airport din daga Arrival matar na
tambayarta za a zo daukanta ne ko Taxi xata hau, Kafin Khaleesat tace komai ta
hango wani kamar AJ tsaye jikin wata mota yana danna wayarsa, sai da ta kifta
ido ta bude to be sure he is the one she is seeing, ta kalli matar kusa da ita
da kyar ta sanar mata yayanta ya zo daukanta, a haka suka rabu da matar,
Khaleesat ta nufi inda ta hango Ajay, sae da ta iso kusa da motar ya daga kai
ya kalleta, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Ina yini" Calmly yace
"Ina wayar da na baki?" Jakar hannunta ta nuna masa tace "Yana
ciki, na sa silent ne" Driver seat ya bude ya shiga sannan ya bude mata
daya side din motar, zagawa tayi ta shiga ta jinginar da kanta ta lumshe ido,
ya tada motar suka bar Airport din, Google map yayi ta using after almost 45
mins ride Khaleesat ta fara gane inda za su, amma kuma sae ko ina yayi mata
sabo a area din ko don she is not stabilize ne bata dai sani ba, ta juya ta
kallesa shi dai driving dinsa kawai yake with the assistant of his google map,
at last suka shigo wani unguwa yayi parking ya dau wayarsa yayi dialing number,
muryar Aunty Farida taji bayan anyi picking, Khaleesat taji kamar an yaye mata
Ζaso tamanin cikin damuwarta jin muryar kanwar Ummanta, bayan few minutes sae
ga ta ta fito daga cikin wani gate, tun da AJ ya hangota daga nesa ya fahimci
da ita yake waya don kana ganinta ka ga Khaleesat, yayi driving din motar har zuwa dai dai kofar
gidan da ta fito, yana parking Khaleesat ta bude motar da sauri ta sauka da
sauran last strength dinta ta nufi Aunty Farida ta fada jikita, Aunty Farida ta
rikota da sauri kafin ta kai kasa, wata makociyarta ce ta taimaka mata suka
rike Khaleesat suka shiga da ita cikin gidan, shi dai AJ na tsaye kusa da
motarsa yana kallonsu har suka shiga ciki, sai kuma ya jingina da motarsa yana
kallon yara dake wasa few houses away, wayarsa ya ciro jin yana ringing ganin
me kiransa ya daga yace "Ya ake ciki?" Daga daya bangaren mutumin
yace "Ranka shi dade sai daxu ya kunna wayar tasa, an kuma duba location
din nasa yana cikin garin Abuja yanxu haka" AJ yayi shiru kafin yace
"Ohk, i will get back to you nagode" Daga haka ya katse wayar ya
mayar aljihunsa, sai ga Aunty Farida ta fito daga cikin gidan, yayi Ζasa da
kansa ya gaisheta, ta amsa cikin sanyin murya tace "Sannu da kokari fa,
Allah ya saka da alkhairi, mu shiga ciki sai mu yi magana ko" Bai ce mata
komai ba ya bi bayanta zuwa cikin compound din, Compound ne me dauke da
apartment uku self contain each, AJ ya tsaya daga balcony din apartment din bai
shiga ba har sai da Aunty Farida ta kara lekowo ta masa magana sannan ya cire
takalmansa ya shiga parlon ya zauna saman kujera yana kallon Khaleesat da ta
juya baya kan 3 seater din da take kwance, Aunty Farida ta tafi kitchen dauko
masa ruwa, ya ciro wayarsa yana dannawa absentmindedly, Sai ga Aunty Farida ta
fito kitchen ta ajiye masa ruwan a kusa da shi sannan ta zauna, da damuwa tace "Sannu
da kokari Junaid, Allah ya saka da alkhairi, mun gode sosai" AJ ya daga
kansa ya kalleta yace "Amma dai kince bai san inda kike a lagos ba ko
Aunty?" Aunty Farida tace "Gaskiya bai san nan gidan ba, tsohon gidan
da na baro ne dai ya sani, shi ma wani lokaci ne da ta zo Lagos dubani bani da
lafiya, ta zo da kwana uku sai ga shi shima ya zo, to yau wata hudu kenan da
barina wancan Unguwan na dawo nan" Ajay dai yayi shiru idonsa a kasa,
Aunty Farida tace "Kuma ba unguwa daya bane, shi wancan Unguwan da na baro
a Ojota ne, daga can zuwa nan ma tafiya ce me zaman kansa, ba kuma wanda yasan
nan na dawo" Ajay yace "Toh shikenan, jikinta da zafi ne?" Aunty
Farida tace "Ehh na ji da zafi sosai gaskiya, makociyata da ta rike min
ita muka shigo yanzu nurse ce, tace zata rubuta min magunguna in siyo
mata" Ajay yace "Ohk, bari zan fita yanzu sai in siyo magunguna da
allurai da drip ayi mata karin ruwa" Aunty Farida tace "To Allah ya
saka da alkhairi, amma baka sha ko ruwa ba Junaid" Ajay ya Ιan yi murmushi
yace "Bari in je in dawo dai" A haka ya fita daga parlon ya tafi
pharmacy ya harhado mata magunguna da drip da allurai. Wata mace ce warce
bazata wuce shekaru hamsin da bakwai ba zaune wani kantamemen parlor cikin isa,
mai aikinta na duke gabanta tana yanke mata kumbar kafafuwanta, cikin fada take
cewa "Banda ma naci irin naka dama ina kai ina er matsiyata? Er talakawa?
Wanda cin yau da kyar na gobe da kyar, ai kai ba class dinta bane ta ko ina,
you just stoop ur self so low Abdul, babu wanda ya isa da kai babu wanda zai
baka shawara ka dauka, na rasa irin wannan taurin kai naka, tun asali i am
against you marrying that poor wretched girl, kuma har gobe ba wai nayi na'am
bane kawai bani da yanda zanyi da kai ne Babana, baka jin maganata ko na ubanka
balle na yayarka, yanxu ina amfanin kaskantar da kai da matsiyaciyar tayi cikin
talakawa yan uwanta a gaban gidan cin abinci, abu har police station, da
mutuncinka da iliminka a maka haka? In zaka dau shawarata yanzu gwara kawai ka
saketa case ya dawo sabo fil, uban me zaka ci da ita kuma bayan wannan abun da
ta maka a idon duniya? Idan yarinya kake so ni duk inda zan shiga zan je in
samar maka yarinya karama da ta fi ta komai kuma er gidan arziki ba tsiya ba,
kai ko Nijar din ne ma ni sai in shirya inje da kaina in samo maka wata buzuwar
er gidan arziki ba talakawa ba, kai ga ma er wata kawata shuwa Arab yanda kaga
ita wannan da makale ma ita ma haka take tass da ita, ga gashi, sannan su ba
talakawa bane" Wata matashiya ce er shekara 39 dake zaune parlon ita ma ta
juya da sauri ta kalli warce ke magana tace "Momy ban gane abinda kike
nufi ba? Wai nufinki ya saketa kenan?" A fusace Momyn tace "Toh uban
me zai ci da ita idan bai saketa ba Meema? Er talakawa ce fa, a kanta aka fara
kyau a duniya ne da bazai rabu da ita ba?" Warce ta kira da Meema ta
girgiza kai tace "A'a wallahi Momy, ai idan ya rabu da ita yanzu ma ita da
iyayenta ne suka ci riba, duk uban hidimar da yayi mata sai kice ya saketa daga
karshe ko tausayinsa ba ki ji ba Momy? Ae wallahi bata isa ya saketa ba, ko don
mu kuntata mata yanda ta kuntata ma Abdul baza mu yi fatan ya saketa ba, dole
sai ta shigo gidan nan, balle shi ba mahaukaci bane da zae saketan, yarinyar da
ya tura har America karatu duk don dai ta zama presentable cikin mutane kar a
mana dariya daga karshe ta saka masa da wannan walakanci da tijara haka?"
Abdul dake zaune parlon shi ma duk yana sauraronsu ya mike yace "In har
aka ga na saketa to bana numfashi ne a duniya, kuma duk inda ma take zata dawo
hannuna nan ba da jimawa ba kuwa, a nan ne zata gwammaci bata taΙa sanina a
rayuwarta ba, i will make life a living hell for her" Momy ta tabe baki
tace "Shi dama talaka ai bai gaji abun arziki ba, shi yasa babu ruwana da
su ko da wasa, hanyar jirgi daban ta mota daban, kai ne da jajibe jajibenka
kasa ubanka ya tafka asaran kusan miliyan dari akan matsiyaciyar yarinyar
nan" Tuni Abdul ya fice daga parlon, Meema na kallon uwarsu tace "Ai
ki ma dena maganar asaran miliyan dari Momy, don yanxu babu wannan zancen
asaran nake ji" Momy dai ta tabe baki tana kallon me aikinta tace "Ke
kar fa ki yanka ni inyi mugun bata maki rai yanzu, ya zaki dinga gaftare min
naman yatsu" Hakuri mai aikin ta hau bata. Wajen karfe biyar na yamma
Khaleesat ta Ιan kishingida a 3 seater, hannunta rike da bowl din pepper soup
din da Aunty Farida tayi mata, gaba daya ta kasa shan pepper soup din Offals
din, don jinsa take kamar magani a bakinta gashi har sannan jikinta babu kwari
ga ciwon kai, ta kalli drip din dake hannunta taga ko quarter bai yi ba amma
har ta gaji ta rasa inda zata sa kanta taji dadi, tun da AJ ya kawo magungunan
da drip ya ajiye ya bar gidan har sannan bai dawo ba, ga abincinsa Aunty Farida
ta zuba a cooler ta ajiye a tray tun daxu tana jiransa, tambayoyi ne da yawa ke
yawo a zuciyar Aunty Farida tana son tambayar Khaleesat ko shine ya taΙa biya
mata jirgi kwanaki da Umma bata da lafiya amma ganin yanayin da Khaleesat ke
ciki ta bar duk tambayoyin nan a zuciyarta, Aunty Farida ta kalli Khaleesat
tace "Ki daure ko kadan ne ki sha, ko in dama maki custard?"
Khaleesat ta girgiza mata kai, dai dai nan aka kwankwasa kofar parlon, Aunty
Farida ta mike ta yafa gyalenta sannan ta tafi ta bude kofar ta koma gefe, da
sallama Ajay ya shigo parlon yana kallon Aunty Farida yace "Tare da
brother dina muke" Aunty Farida tace "To ku shigo mana" a
hankali Khaleesat ta gyara zamanta tana kallon Jay babu ko kiftawa, ganinsa ta
dinga yi kamar a mafarki, Jay ya sauke kansa ya gaida Aunty Farida ta amsa da
fara'a, sannan ya juya yana kallon Khaleesat shi ma babu ko kiftawa, lkci daya
hawaye ya cika idonta tana kallonsa, walking slowly ya karasa har cikin parlon
ya duka gabanta yana kallonta, a hankali yace "Are you feeling better now
Housemate?" Da sauri ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta, and truly
she felt better immediately, shi dai AJ na tsaye yana kallonsu, haka Aunty
farida da ta koma one sitter a sanyaye ta zauna, Jay yayi kasa da murya still
looking at her yace "Kiyi hakuri, everything will be okay soon in sha
Allah, i promise you" Ta gyada masa kai da sauri with so much hope from his
assurance, yana kallon bowl din hannunta Softly yace "Take ur soup"
Ba musu ta dau spoon din ta fara shan pepper soup din a hankali, Aunty Farida
ta kalli Ajay tace "Baka zauna ba Junaid" Ajay ya sauke kansa ya
karasa 2 seater ya zauna, Aunty Farida ta share hawayen da ya cika idonta, da
kyar tace "Mu ma duk ba da son ran mu bane abubuwan nan ke faruwa haka ba,
ba mu da yanda za mu yi ne kawai, amma babu nagartattun iyayen da za su dau er
su su ba Abdul aure"
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buΙe
a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!π
‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za
ku haskaka a wannan Sallah!
MG’s Beauty Lounge ya buΙe da kwalliya, tsafta da Ζamshi
irin na sarauniyar zamani!
Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu:
Gyaran gashi da kitson zamani
Kwalliyar Sallah mai Ιaukar ido
Wanke Ζafafu da pedicure mai sanyaya rai
Kayan gyaran fata na gaske
Lalle mai kyau da salo na zamani
Tura-turai, humra, incense da Ζamshi masu daΙi
Shirin amare da na musamman
Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace
sarauniya.
Zo ki ji daΙin wanke Ζafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan
kyau da Ζamshi – komai a wuri guda mai kyau.
Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan
gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna.
Tambaya/Booking:
WhatsApp: 08062991549
Kira: 09016108092 / 08064532391
Ki zo ki gani da idonki – ki ji daΙin sauyin MG’s Beauty
Lounge.
Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge
[5/30, 8:55 PM] khaleesat Haiydar π✍️: *Gaisuwa da
fatan alkhairi zuwa ga me kasuwar garin Dutse Hajiya Aunty Zahrah da Hajjaju
Sadiya Chamo Ex in-law, Hajiya Nafeesah Mom twins da Ummu Zainab Maman Ramla,
Aunty Maryam Dan Ladi nasidi kema na gaisheki da katon murya, Hajiya Jumare da
Hajiya Asmy me kayan amare, Oum Nabeelah, Mardiyyah, Uwar Janan, Halysah Garbaπ
i hail you all with respect yan Palace*
Manyan Membobin _❤π©ΉKhaleesat's Citadel_❤π©Ή
*Su Meenah parrotπ, Oum Noor, Nafeesah Jawwad,
Rukayya, Fidomashi, Siyam, M manal, Mrs Barrister, Shanono Esq, Ummilos,
Na'imatu, Zulaiha, Ummu Abdrhm,
Khaleesat Haiydar is saying a big thank you to you all for ur support
always, Allah ya bar min ku*π₯°
Aunty Farida ta numfasa a hankali tace "Da yake Abdul
shi kadai ne namiji gun mahaifinsa, mahaifin ya dauki son duniya ya dora masa
kuma bai jin maganar kowa sai nasa, duk abinda Abdul yake so shi mahaifinsa ke
so, bayan yaga Khaleesat a kotu babu tantama zuwa yayi ya samu uban ya nuna
yana sonta zai kuma aureta, wannan dalili yasa babu bata lokaci suka janye kara
a kotu suka bar maganar miliyan dari da sharadin Malam Ali zai ba Abdul auren
er sa Khaleesat, mu dai har yau bamu san ko da wata yarjejeniya da aka yi a
kotun ba ko babu, mun dai san an janye kara kawai kuma duk muka yi farin ciki
sosai da hakan, burin mu kawai Malam Ali ya dawo gare mu ko da bazai tsinana mu
da komai ba amma mu dinga ganinsa a tare da mu a matsayin kantangar gida, balle
duk mun san yayi ma iyalansa hidima dai dai gwargwado ya kuma kyautata masu
yanda ya kamata, jarabawa ce kawai ta fada masa, bana mantawa Khaleesat ta
shiga damuwa sosai a lkcn tana ta koke koke wai ita bata son Abdul tun ma bata
san kalansa ba bata gansa ba tace bata sonsa bazata iya aurensa ba, mu kam
idonmu duk ya rufe da son ganin an wanke Malam Ali daga laifin da ake zarginsa
da shi, ni da uwarta muka yi ta bata baki muna kwantar mata da hankali muka ce
ko tafi son a maida mahaifinta prison ne, ko don mahaifinta bazata hakura ba ta
amince da bukatar Abdul na son aurenta don case din ya mutu gaba daya, gashi
tun bayan dawowar Malam Ali yayi ta rashin lafiya ko kudin kai sa asibiti babu,
duba da hakan ne ma yasa muka yi ta karfafa ma Khaleesat gwiwa muna bata baki,
a haka dai muka samu muka lallabata ta fara hakura, nan kishiyoyin Ummanta suka
fito da baΖin cikinsu da hassada a fili tunda su ma ai suna da 'ya ya mata
sa'annin Khaleesat da ma wa enda suka girmeta amma shine Abdul zai ce sai
Khaleesat, nan fa duk suka hau gaba sosai da yayata saboda Ιan mai kudi ya ga
Khaleesat yace yana so, ranan farko da Abdul ya fara zuwa unguwan cewa yayi shi
bazai shigo da motarsa layin ba ta fito bakin titi ta samesa, gashi daga gidan
zuwa bakin titi akwai tafiya sosai, haka nan uwar ta lallabata ta shirya ta
saka nikab dinta kannenta biyu suka rakata har bakin titin ta samesa, a ranan
kuma ya bata babban waya ya kuma hadata da dubu hamsin, ba ma ita ta amsa ba
don nuna masa tayi bata so shine ya ba kannenta yayi tafiyarsa, da kudin aka
samu aka biya mata waec dinta tunda ba mu da yanda za mu yi, a kaf tarihi ban
taΙa jin wanda yake neman yarinya da isa da gadara da walakanci kamar Abdul ba,
for almost 2 months in Abdul zai zo unguwan mu sai dai dole ta fito titi ta
samesa shi bazai shiga layin da motarsa ba, watarana ne ya kira bata da lafiya
shine da ya tashi zuwa dubata da yamma ya shigo layin a karo na farko tunda ya
fara zuwa gurin ta, daga nan kuma ya dena cewa ta fito bakin titi in ya zo sai
dai ya karasa ciki da motarsa, ya kai ya kawo har cikin gida yana shigowa, tun
a wannan lokacin Abdul baya raga ma Khaleesat, fadan yau daban na gobe daban,
bashi da fahimta bashi da uxuri, ga nuna isa da gadara abinda yace yake so dole
shi zata yi, haka nan yarinyar nan ke hakuri da halinsa duk don saboda
mahaifinta, rana daddaya ne baya sa ta kuka, sai dai ni da uwarta mu yi ta bata
hakuri muna ganin duk me sauki ne tunda har yana sonta kuma yaji zai aureta ya
zauna da ita wataran zata canza sa da kanta, ni dai a sanda na fara sarewa da
lamarin Abdul jikina yayi sanyi shine watarana da ya daga hannu ya mareta har
sai da shatin yatsunsa ya kwanta fuskarta, mu dai har yau bata gaya mana me
tayi masa da yayi mata haka ba don a cikin motarsa hakan ya faru, nan jikin
uwarta ma ya fara sanyi kan lamarin har ta samu Mai gidanta ta gaya masa amma
Malam Ali yayi ta kakkarewa har da cewa duk wanda ma ya kara tada maganar Allah
ya isa, ana haka har ya biya mata jamb ya kai ta da kansa ta zana don fara
jami'a tunda waec dinta ya fito kuma sakamakonta yayi kyau sosai, kawai rana
daya kwatsam ubansa ya kira mahaifinta wai ga abinda Abdul yace yake so, wato
zai tura Khaleesat Amurka tayi karatu a can, duk kawaicin da yayata take wannan
karan sai da ta nuna bata amince da hakan ba, don ana ta bin su a yanda suke so
ba hakan ke nufin bamu da ta cewa akan lamarin Khaleesat ba, ba Yayata ba har
kakar Khaleesat Nenne ta nuna rashin amincewarta a wannan bukatar tasu, babu ta
yanda za a dau yarinya karama haka da ko mallakan hankalinta bata gama yi ba
ace za a tura ta har Amurka da sunan karatu, in haka ne kawai a daura auren
mana sai ya kai ta duk inda ma zai kai ta tayi karatu, in ko ba haka ba babu
inda er ta zata je da sunan karatu sai dai duk abinda zai faru ya faru, a nan
dai laifin Mahaifin Khaleesat ne da ya dau tsoron duniya ya dora ma Abdul da
mahaifinsa ba kuma tsoron komai ba sai tsoron kar su sake maidasa inda ya baro
wato prison, dama tunda ya baro can ya dawo gashi nan gashin nan dai kamar ya Ιan
samu matsala a kwakwalwarsa, yau lafiya gobe akasin haka, ya dawo kamar ba
Malam Ali ba, a lokacin duk ya gigice yayi ta bala'i wai ina ne ba a tura yaro
karatu a zamanin yanxu, yarinya me shekara sha bakwai ce za ace ma yarinya,
inda yake shiga ba nan yake fita ba, hakan ya zame masu bacin rai sosai da
mahaifiyar Khaleesat har sai da ta bar gidan ta koma gidan Mahaifiyarsa warce
ita ma yaki sauraronta, haka nan Malam Ali ya dau Khaleesat ya damka ma Abdul
ba tare da amincewar uwarta ba ya kai ta karatu Amurka, Shiru Aunty Farida tayi
tana kallon su Ajay dake kallonta duk suna sauraronta, a hankali tace "Tun
daga sannan shi yake sponsoring komai nata a Amurka, cin ta da shan ta, da
suturanta komai dai shi ne, sai san da ya ga dama ne yake bari ta zo hutu
Nigeria, mu tsakaninmu da ita dama sai sanda muka ganta ko kuma muyi magana ta
WhatsApp, gashi yaki a daura auren nasu wai sai ta gama karatun wanda wnn ne ke
kara daga mana hankali, a haka ake ta rayuwar bamu da kwanciyar hankali, a ko
da yaushe fatanmu shine ayi ayi auren don duk wasu iyaye nagari baza a same su
da kwanciyar hankali ba ace yau er su budurwa bata gabansu, kusan kullum sai
uwarta ta zubda hawaye kan wannan lamari sanadiyar hakan har sai da hawan jini
ya kamata, ace bata da iko da er ta sai dai abinda Abdul da ubansa suka tsara
gashi mai gidanta ya dau tsoron duniya ya dora masu sai jan sa suke kamar
rakumi da akala.... ko wata biyu ba ayi ba ranan yayata ta kirani take sanar
min sun kawo kudin auren Khaleesat, duk muka yi farin ciki sosai da hakan, muka
yi fatan Allah ya sa hakan alkhairi ne a rayuwar Khaleesat tunda mu ma mun fi
son ayi auren kowa ma ya huta, kawai ranan juma'an nan da ta wuce sai ga kiran
yayata wai an daura auren Khaleesat da Abdul, nace mata ban gane ba, Khaleesat
din ta dawo ne? Sannan dama ana daura aure haka ba shiri? Nan take gaya min ai
mahaifin Abdul din ne ya kira Baban Khaleesat da yamma likis yace ga bukatarsu
gobe juma'a, babu bata lokaci kuma aka daura auren kamar yanda suka bukata
washegarin, nace mata to shikenan Allah sa hakan shine mafi alkhairi, zuwa
satin da za a shiga zan shigo kanon tunda tace Khaleesat din ma na Amurka bata
dawo ba, ban kuma san komai dake faruwa ba sai ranan Lahadi da kirani, mun yi
waya da kai babu dadewa sai ga yayata ma ta kirani tana kuka" Ajay ya
sauke idonsa kasa, Calmly yace "Amma dai baki ce mata tana nan ba har
yanxu ko?" Aunty Farida ta girgiza kai tace "Ai tunda muka yi waya
kace kar in nuna ma kowa nasan inda take wallahi ban nuna ma yayata nasan komai
ba, ita kanta har yanxu bata san inda Khaleesat take ba, Nasan Baaba Gaje
bazata gaya mata ba ita ma" Ajay ya sauke ajiyar zuciya yace
"Shikenan, yanxun ma kar ki nuna tana wajenki, in sha Allah za mu ga yanda
za ayi, in ma kudin baban nasa da abinda ya kashe mata na makaranta za a mayar
masu wannan ba matsala bane in sha Allah" Aunty Farida ta gwalo ido jin
abinda yace, ko dai bai ji amount din da ta kira bane da kyau, a hankali tace
"Kudaden ne da yawa ai Junaid, miliyan dari fa banda abinda zai ce ya
kashe mata na makaranta da bamu sani ba" Ajay yace "Bazai dai ce ya
kashe mata sama da miliyan dari a makarantar ba, mu ma duk makarantar muke ai,
in ma yace haka miliyan dari biyu ba abu bane da muke fatan zai gagara a mayar
masu, so kawai kar ki ce ma kowa tana wajenki, we will see how things will go
in sha Allah" Ita dai Aunty Farida tsabar yanda jikinta yayi sanyi ta kasa
cewa komai, dama tun da ya sakko daga mota jiya taga kalansa take ta kallonsa
tana mamakin inda Khaleesat ta samo shi, hatta wanda ya kira Ιan uwansa bata ga
yayi kalar tsiya ba shima, Shi dai Jay yayi shiru bai ce komai ba idonsa akan
buhun shinkafa biyu da babban jarkan man gyada da carton din taliya dake parlon
Aunty Farida, kana gani kasan food vendor ce, Ajay ya mike yana kallon Jay alamar
ya tashi su tafi, Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yana kallon Aunty Farida
a hankali yace "Bacci take ne?" Ajay ya wani kallesa sai kuma yayi
ficewarsa daga parlon, Aunty Farida ta mike tace "Bari in duba ta"
Dakinta ta nufa Jay ya bi ta da kallo, after few seconds sai ga ta ta fito tana
kallonsa tace "Ehh bacci take" Yace "Ohk, amma Drip din na
raguwa kuwa?" Aunty Farida tace "Eh yana sauka" Mikewa yayi yace
"Toh shikenan, sai anjima Aunty, kilan zuwa gobe da safe in sha Allah za
mu shigo" Aunty Farida ta Ιan yi murmushi tace "Toh Allah ya kai mu
Jawwad, mun gode sosai" Murmushin ya mayar mata ya nufi kofa, har ya fita
ya sake juyowa yace "Amma Aunty ki Ιan dinga duba drip din idan ya kare
sai kiyi ma makociyar taki magana ta cire" Aunty Farida tace "Ina sha
Allah, mun gode Jawwad" Daga haka ya fita daga parlon ya nufi kofar gida,
cikin mota ya tadda Junaid har ya tada mota, ya karasa ya bude front seat ya
shiga ya zauna ya jinginar da kansa da kujeran motar ya lumshe ido ya bude,
saukansa kenan daga America ko hutawa bai yi ba balle ya ci abinci, yayi wanka
kawai suka taho gidan Aunty Farida da Ajay, har suka isa gidan Cousin sister
din parent dinsu dake Banana Island babu wanda yace komai a cikin motar, it's
almost 7pm tsabar traffic din Lagos da ya rike su a hanya, bayan Ajay yayi
parking Jay ya sauka daga motar ya nufi entrance din shiga gidan Ajay na biye
da shi, a parlor suka tarar da Hajiya Fatima warce suke kira da Ummi, ta amsa
gaisuwar da suka mata ta bi su da kallo, Ajay dai ya nufi sama, Tana kallon Jay
tace "Baka ci abincin da aka ajiye maka ba Jawwad, ina ma ku ka je haka
sai yanxu ku ke dawowa?" Jay ya shafa kansa a hankali yace "Wajen
wani abokinmu" Daga haka shi ma ya wuce sama, ta bi sa da kallo. Wajen
karfe tara na dare Ajay ya gama saka pajamas dinsa, Jay ya ajiye mug din tea
dake hannunsa yana kallonsa Calmly yace "So now what is ur suggestion
Ajay, gaba daya kai na ya kulle akan issue din nan, that guy have evil in mind
shi yasa ya saka aka daura auren tun bata dawo ba, he have a different plan,
abinda kayi masa a USA na ransa har yanzu.... He married her immediately just
to deal with her, I don't think he still loves her, he married her to take
revenge" Ajay yace "Dama ai ba saboda Allah ya sa aka daura auren ba,
akwai abinda yake nufi da hakan, ashe ma karamin Ιan iska ne shi ban sani ba
tun da bai yarda da kansa ba, da ya yarda da kansa bazai dinga kashe waya
ba" Jay yace "Kamar ya?" Ajay yace "Na karbi numbersa na sa
a duba min location dinsa, his location was showing Abuja on Sunday, tun sunday
din har zuwa yau bai sake kunna wayarsa ba, kuma baya location din da aka gansa
bayan na sa an je can" Jay ya bude baki yana kallonsa, can yace "Ban
gane ka sa an je can ba, what are you trying to do? Plss ni bana son wannan
dabancin naka Ajay, ni na zata fa ka shiryu, is that why u were busy shouting
ku hadu a Nigeria on that very day? No pls ka girmi haka yanxu Prince, why
spare ur precious time for a tout like him, don ni wallahi kallon tout nake ma
gayen, sannan kar ka manta barrister ne shi kamar yanda kanwar mamarta ta gaya
mana, definitely yasan plan dinka a kansa da yasa ka dage ku hadu a Naija, kaga
bazai bar wayarsa a kunne ba kuwa" Ajay yace "Ai sai dai bai kunna
wayarsa ba amma wallahi duk sai ya janye batancin da yayi min a parlon nan
ranan, ya zata ana zagina a tafi scot free? I will so deal with him" Jay
ya tabe baki yace "Yanxu dai that aside, meye abun yi" a takaice Ajay
yace "Abun yi kawai a makasa a kotu ya fadi duk abinda ya kashe a biyasa
ya saketa taje tayi rayuwarta, cause in har ta zauna zaman aure da mutumin nan
zai iya kasheta har lahira, don prisoner zai mayar da ita kawai" Jay yayi
shiru at first, can yace "But Ajay bamu san ko anyi a rubuce kan cewar an
basa aurenta a madadin kudin da mahaifinta zai biya mahaifin Abdul din ba,
sannan gayen nan Barrister ne, kana ganin zai bari ayi wannan yarjejeniyar babu
sa hannu or anything of such ta bangaren shari'a?" Ajay yace "Su na
ma iyayenta kallon talakawa marasu galihu da basu da wani say shine za su tsaya
wani yarjejeniya? Ai masu arziki ke yarjejeniya, bayan sun san har a tashi
duniya iyayen nata ba samun hanyar biyan miliyoyin kudin nan za su yi ba? Ai
hankalinsu da tunani ma bazai je kan wata yarjejeniya ba cause they just assume
sun samu yarinyar sun gama kuma ba wani abu da zai gifta ya hana hakan, so now
we are taking this case to court, da bakinta zata ce ma alkali bata auren a
kotu, iyaka ace ta biyasa abinda ya kashe mata na karatu sannan tayi masa wani
auren ba shikenan ba" Jay yayi murmushi yace "Case din babanta da shi
mahaifin Abdul din fa?" Ajay yace "We will reach der also" Jay
yace "I just hope the agreement isn't in written form, but before mu je
kotu nawa ne a account din ka Ajay?" Dariyar da Ajay bai yi niyya ba yayi
yana shafa kansa, can ya kallesa yace "Why are you asking me that silly
question Jay?" Jay yayi murmushi yace "Let me know first cause the
money in my bank account isn't more than that amount" Ajay yace
"200M?" Jay yace "Ban sani ba" Dariya sosai Ajay yayi yace
"Na raina capacity dinka Bruh, meye kuma 200M a account dinka? Na zata
account dinka ya doshi 1 Billion yanxu, Ohhh i remember baka wasa da investing
fa, sannan kai Momy's boy ne har account din Momy ajiye kudi kake, Allah sa
200M din ma baya account dinta" Jay yaki tanka sa, Ajay yace "Kasan
me, yanxu 600M or more ya kamata ace mun ajiye aside for this case cause I
don't trust that stupid guy zai iya tripling kudin a kotu, i will get some more
money from dad, Billah i am doing all this for the sake of humanity not because
of that little brat, in don ta ita ne bazan yi ba, infact in don ta ita ne ba
ruwana a case din ma" Jay dai danna wayarsa kawai yake bai ce komai ba don
hankalinsa gaba daya yayi kan drip din da aka sa ma Khaleesat, yasan zuwa yanxu
dai ya ci ya kare. Abdul na zaune gidan wani cin abinci tare da abokansa biyu
da ke sauraronsa, Abdul yayi sipping energy drink din gabansa ya ajiye ya ci
gaba da magana yace "I am still trying to gather more informations about
the guy, kuma duk inda take yanxu da taimakon guy din taje can don bata da kowa
a cikin garin kano or anywhere da zata je sai wajen sa, all of a sudden fa
kawai naga yarinya ta canza attitude tana min wani sabon kalan raini, at first
na zata naughty frnd din nan nata Safiyyah ce ke zugata duk da ita ma sai nayi
maganinta don nasan da hadin bakinta a abubuwan nan da ke faruwa, i will fish
her out too, ashe wai er ficiciyar yarinyar nan maza take kulawa a kasar suke
bata liver take min raini, Billah sai na kauda gayen nan a doron kasa this is a
promise i am making, sai dai uwarsa ta haifi wani, zai san gonata ya shiga
sannan zai san bai daki banza ba, ba a dukana a ci gaba da rayuwa lafiya, he
said we should meet in Nigeria ko? nasan yanxu shi ma yana bibiyan inda zai
sameni, i don't want to be taken unaware shi yasa nake kashe wayata don nasan
definitely zata basa lambata, idan na gama shirya masa tuggu zan bude wayar
yayi tracking dina ya zo ya sameni inda nake, wallahil Azeem sai na kawar da
shi kuma babu abinda zai faru, ita kuma duk inda take zata shigo hannuna nan ba
da jimawa ba kuwa, sai dai in ban cika Abdallah Musa ba" Abokinsa Aminu yace
"Toh kai baka ga fuskar guy din bane?" Abdul yayi wani murmushi yace
"Ai ni yanxu ban damu da naga fuskarsa ko ban gani ba, burina in ga na
aika sa barzahu, kun yankar mana ticket din da nace?" Aminu yace "But
ta yaya zaka samu informations din wanda baka taba sani ba, baka da lambarsa
ba, baka san komai kansa ba, baka san wanene shi ba, baka ma san inda yake a
Nigeria ba ko kuma wanda ya san sa, How will that be possible Abdul?"
Abdul yayi wani irin murmushi yana bubbuga kafarsa da kasa a hankali, sai kuma
ya karyar da kai yace "Na zata you will be among people that will never
underate my capacity and intelligence Aminu, ai ina da lambar wayarta ko? Kuma
ni nayi mata registering sim card din, toh abokina dake aiki a kamfanin network
din sim da take amfani na ba phone number dinta ya duba min duk calls dinta ya
kuma turo min numbers din da take waya da su frequently a America, he just sent
them to me few minutes ago" Yana kai wa nan ya mike yana wani murmushi
yace "Let go" Dariya kawai abokan nasa ke yi, suka tashi duk suka
fita daga eatry din.
[6/2, 1:05 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Wajen karfe
goma na dare Khaleesat na zaune dakin Aunty Farida da fruits a gabanta ta kasa
sha, ita dai Aunty Farida na zaune opposite dinta ta zuba mata ido don har ta
gaji da ce mata ta sha fruit din, ga abinci ma taki ci, tun tuni makociyar
Aunty Farida ta shigo ta cire mata drip din bayan ya kare, ta daga kai ta kalli
Aunty Farida a hankali tace "Aunty su Housemate dina sun tafi ne?"
Aunty Farida tace "Waye kuma Housemate din ki?" Khaleesat ta sauke
idonta tayi shiru, Aunty Farida tace "Junaid din ne Housemate din
ki?" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "Wanda suka zo tare"
Aunty Farida tace "Ohk, tun daxu ai suka tafi kina bacci, ta yaya ya zama
Housemate din ki?" Khaleesat na juya fruits din gabanta a hankali da fork
tace "Gida daya muke da shi a America" Aunty Farida ta Ιan buda ido
da confusion tace "Gida daya kuma? Kamar yaya? Amma ba kin ce makociyarki
mace bace?" Khaleesat tace "Eh daga baya ta tashi daga apartment din,
shi ne shi ya dawo gidan" Aunty Farida tace "Ikon Allah, shi kuma
Junaid din a ina kika san shi?" Khaleesat tace "Cousin brothers ne
ai, dalilin Housemate dina na san shi" Aunty Farida ta kafe ta da ido,
Khaleesat ta sauke kanta bata boye ma Aunty Farida duk abun da ya faru tun daga
dawowar Housemate apartment dinta, yanda ya biya mata kudin jirgi to and fro ta
dawo Nigeria ta duba Umma, irin zaman da suka yi da shi da kirkin da yayi ta
mata, har zuwa lkcn da Abdul ya zo kasar a karo na biyu da kuma abinda ya faru
tsakaninsa da Ajay, da yanda suka maidata gidansu har ta gama Exams, babu
abinda ta boye ma Aunty Farida hawaye na zuba idonta, Aunty Farida ta kasa cewa
komai sai kallonta kawai take jiki a sanyaye, after almost a minute Aunty
Farida ta sauke ajiyar zuciya tayi tagumi don she is just speechless bata san
ma me zata ce ba, amma ta fahimci wani abu a labarin da Khaleesat ta bata.....
Washegari wajen karfe goma na safe Jay ya bude kofar dakin Ajay ya samesa tsaye
yana buttoning din shirt dinsa ya gama shiryawa, Jay ya jingina da jikin kofar dakin
ya rungume hannu yana kallonsa calmly yace "You know what Ajay?" Ajay
ya dau face cap dinsa ya saka, yana kokarin daura agogonsa a hannu yace
"All ears" Jay yace "I think we shouldn't say anything to Abba
akan kudin da muka yi magana jiya" Sai a sannan Ajay ya juya ya kallesa
yace "Why?" Jay yace "Kasan zai yi querying dinmu about what we
are using that huge amount of money for, i think gwara in amshi kudi wajen
Mamina kawai, cause you know i can't lie to Abba idan yayi insisting akan
abinda za mu yi da kudi haka, zan iya gaya masa me za muyi da kudin if he
insist" Ajay ya masa wani kallo daga sama har kasa yace "Sannu saint,
ita Mamin ce bazata yi querying dinka akan me zaka yi da huge sum of money din
ba?" Jay yace "Yeah, but i know how to convince her" Ajay yayi
wani murmushi yace "Mamin ce zaka yi convincing, i see" Bai jira
amsar da Jay zai basa ba ya dau makullin mota da wayar sa ya bi gefensa ya fice
daga dakin ya sauka downstairs, Jay ya bi sa da kallo, after a while ya jawo
kofar dakin ya kulle sannan ya bi bayansa, Ummi dake zaune parlor ta bi su da
kallo ganin alamar fita za su yi tace "Ina kuma za ku da safen nan?"
Without looking at her a takaice Ajay yace "Bar beach" Ummi tace
"Dama ana zuwa Bar beach da safe?" Ajay yace "Eh" daga haka
ya fice daga parlon, Ummi ta kalli Jay tace "Wai Beach za ku?" Jay ya
Ιan sosa kansa yace "A'a sai da yamma, yanxu dai kawai yawo za mu yi a
gari" Ummi ta tabe baki tace "Ai shikenan, traffic ma kadai ya
isheku, Mami ma suna hanya yau in sha Allah, sun ma kusa sauka" Jay ya
sauke kansa yace "Eh haka tace min" Ummi tace "To sai kun
dawo" Jay yace "Allah ya sa" Daga haka ya fita daga parlon, ya
tarar da Ajay a mota yana jiransa, yana shiga motar Ajay yace "Ko ina
ruwanta da inda za mu, ni bana son sa ido a rayuwata, shi yasa bana sauka
gidanta a garin nan, i hate what i don't like" Jay yace "Ikon Allah,
what's wrong with her asking us where we are going?" Ajay yace
"That's very wrong, we are not kids da zata dinga tambayar mu inda za mu
idan za mu fita, ko Abba baya controlling din mu yanda matar nan take yi, i
don't think i am going back to that house zan je in kama hotel kawai" Jay
ya girgiza kai yace "Kai fa matsala ne da kai kamar gidan haya, ni ban ga
wani abu ba don ta tambayemu inda za mu da safe, it's normal ai" Ajay ya
kallesa yace "To ni ba kai bane da ake controlling yanda aka ga dama a
family, kai da kaga za ka iya sai ayi ta controlling dinka Jawwad" Jay bai
sake ce masa komai ba, Ajay ya ja motar suka fice daga gidan. Da sallama
Safiyyah ta daga buhun dake makale kofar shiga compound din gidansu Khaleesat,
Mama Shatu da Mama Zubaida ne tsakar gida ko wacce na zaune bakin murhunta ana
girka abincin talla hayakin icce duk ya cika ko ina na gidan, Mama Zubaida sai
mita take an siyo masu jikakken icce, gaishesu Safiyyah tayi suka amsa ana mata
wani kallo kasa kasa, Safiyyah ta tsaya suka gaisa da Labiba dake wanke robobin
da za a zuba abincin siyarwa, sannan ta nufi dakinsu Khaleesat ta daga labulen
ta shiga da sallama, zaune ta tarar da Umma ta jingina da bango hannunta rike
da carbi ga kawarta Mama salame da wata Zaliha makociyarsu sai Sha'awa ita ma
makociyarsu zaune dakin ko wanne yayi jigum, zaunawa Safiyyah tayi tana kallon
Umma ko gaisheta bata yi ba ganin yanayinta tace "Umma baki da lafiya ne?"
Umma tayi karfin halin cewa "Sannu da zuwa Safiyyah" Safiyyah ta
gaisheta sannan ta gaida sauran mutanen dake dakin, ta sake maida dubanta kan
Umma kan tace komai Mama Salame da ta san kawar Khaleesat ce ita tayi kasa da
murya tace "Tsakaninki da Allah Sapiya baki san inda kawarki Khaleesah
take ba?" Safiyyah ta zaro ido tace "Kamar yaya Mama?" Sha'awa
ta gyara zama tace "Ae tun ranan asabar rabon da a saka Khaleesat a ido,
daga ta dawo kasar waje ta tarar an daura mata aure da audallah washegari
Asabar aka nemeta aka rasa, babu inda ba a shiga neman Khaleesah ba amma babu
ita babu labarinta, jiya jiya yan sanda suka zo suka tafi da Malam Ali"
Safiyyah da ta shiga wani shock jin wai an daura ma Khaleesat aure da Abdul ta
ajiye jakarta a gefe ta dafe kirji tace "Wani Abdul din aka daura mata
aure da?" Sha'awa na gyara barkakken zaninta tace "Audullah
saurayinta dai da kika sani, ranan juma'an nan da ta wuce aka daura masu aure,
tana dirowa kasar aka sanar mata shine ta gudu har yau babu ita babu labarinta,
gashi an tafi da Malam Ali an kullesa" Safiyyah tace "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un" Mikewa tayi tsaye ba tare da tasan tayi hakan ba
tsabar shock din da ta shiga maganganun Sha'awa na yawo a kanta, hawaye ne ya
cika idonta tana girgiza kai ta kasa cewa komai, ina jin bayan Khaleesat da
tayi bakin cikin auren da aka daura mata da Abdul idan aka cire su Jay babu
wanda yayi bakin ciki kuma irin Safiyyah, don ji tayi kamar an aza mata katon
dutse a kirji tsabar bakin cikin wannan labarin, kawai ta fashe da kuka cike da
tausayin kawarta, Abdul fa?? Housemate din Khaleesat ne ya fado mata a rai, nan
Safiyyah ta dinga rera masu kuka kamar ita ce Khaleesat din, muryar Nenne suka
ji a tsakar gida tana kunduma ma su Mama Shatu da Mama Zubaida zagi tana cewa
"Wato har sararin kunna rubabbun murhun ku kuka samu a gidan nan baku dubi
bala'in da ake ciki ba, ai in dai Ιa ne kowa ma ya haifa wallahi, yanda ku ke
nuna halin ko in kula da abinda ya samu Ιa na ku ma dai kun haifi 'ya yan nan
naga, shegu masu fararen kafafuwa tunda Ιa na ya auro ku yake shiga bala'i
sinka sinka a duniya amma saboda baku da imani da tausayi ko wacce ta zauna
bakin shegen murhun ta" Mama Zubaida ta kauda kai tana tabe baki tayi kasa
da murya tace "Sai kuma yunwa ta kashe mu saboda yan sanda sun zo sun
dauki Malam" Ita dai Mama Shatu sai juya miyarta take kar ya kone taki ko
kallon inda Nenne take, Nenne na huci ta nufi dakin Umma ta dage labulen tana
kallon cikin dakin tace "Saka dogon hijabi da rike carbi ba shine
mafitarki ba Zahra'u, duk inda kika tura yarinyar nan waya kawai zaki buga masu
ki ce ta dawo tun lamari bai lalace mana gaba daya ba, in ko ba haka ba wallahi
sai a wanke daya daga kanninta a ba ma Awdul din tunda abinda yayi ta shi yayi
su, in jar fata da gashi irin ta buzaye ne su ma duk suna da shi, babu abinda
zata gwada masu sai shekaru tunda ta basu shekaru bakwai, don bazan zuba ido a
karo na biyu Ιa na ya koma fursin ya tagayyara ba, Allah kadai yasan nawa na
kashe wajen shige shige har Allah ya bamu mafita a wancan lokacin da aka
kullesa, tun asali bata san bata son Awdul din ba sai bayan da ya kashe mata
uban dukiya da bazai lissafu ba? Wace masifa ku ke son ja ma Ιa na ke da er ki
a garin kano? Shi kadai fa ya rage min namiji sai mata, wallahi ki fito da ita
Zahra'u in ya so su riketa a sake min Ιa na, nasan har da hadin bakin makirar
tsohuwar can Gaje, yanxu kuma zan kama hanya in tafi Hotoron duk inda ku ka
boye Khaleesah sai kun fito da ita baza ku kara ja min salalan tsiya ba,
sha'awa taso ki rakani gidan tsohuwar banzan can Gaje" Da sauri Sha'awa ta
mike ta figi baΖin gyalenta ta fita daga dakin ta bi bayan Nenne dake huci suka
fita daga compound din gidan, Mama Zubaida da Mama Shatu suka saki guda a tare
bayan Nenne ta fita, Mama Shatu ta kyalkyale da dariya tace "Ana yi muna hura
murhu, ma ga dai karshen wannan dirama me dadin kallo a gidan nan, su buzuwa
sai a koma dajin da aka shiga aka nemo maganin farin jini ayi ma Malam bayanin
lamari ya kwabe, ba dai 'ya yanmu bane munana masu baΖin jini, maji ma gani
dai" Umma dake jin duk abinda suke cewa ta jinginar da kanta da bango
hawaye na sauka idonta Mama Salame na bata hakuri, Safiyyah dai jingina tayi
daga bango a inda take tsaye hawaye na zuba idonta ita ma, ganin abun take
kamar a mafarki wai an daura auren Khaleesat da Abdul, to amma ina Khaleesat
zata tafi tun ranan Saturday ita da tasan Khaleesat ko kawaye bata da su a
kano, Housemate ne ya fado mata, ta dau jakarta da sauri tana share hawayenta
ta fita daga dakin Umma, Umma ta bi ta da kallo hawaye masu zafi na bin idonta
daga ranan asabar zuwa yau har ta rame, ko abinci bata iya ci ta kira Aunty
Farida yafi a kirga akan ta zo gareta ko zata ji saukin radadin da take ji a
zuciyarta, Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi Safiyyah da wani kallo suna tabe
baki har ta fita daga compound din, Mama Zubaida ta matsa kusa da Mama Shatu da
yake murhunsu kusa da kusa yake, tayi kasa da murya tace "Kin ga ki hakura
da dafa waken nan da kika ce don gaskiya zai bata mana lokaci ga waje da nisa,
gwara mu je a kara kada hankalinta taji ta tsanesa da auren kuma taki dawowa,
in ya kama a kadata ta shiga duniya duk sai mu ce ayi, kudi ne dai zai yi kuka
ba wani abu ba, kinga daga karshe in ma Labiba ko Lamisah duk wanda yace a basa
duk daya ne a wajen mu babu banbanci, babu abinda zata gwada masu sai farin
fata da uban gashi kamar na doki, in idanuwa ne su ma suna da shi, sannan suna
da hancinsu dai dai gwargwado, tun asali kece kika yi ta makon fiddo kudi da ba
a kai ga haka ba ma wallahi" Mama Zubaida ma tayi kasa da murya tace
"Wallahi ban taba zaton aikin mutumin na ci haka ba Shatu, kinsan Malaman
Jabu sun yi yawa yanzu sai dai ka kai masu kudinka su yi cefanen gidansu, shi
sa kika ga ina ta ja da baya naki sakin kudi dama jarina ba jarin arziki ba,
kinsan tun bayan rasuwar Malamin nan da yayi mana aiki kan Parida naki sakewa
da Malamai don asaran kudi kawai mutum yake shi din dai ne malami gangariya
amma mutuwa ta dauke mana shi kwatsam, gashi har yau duk uban kyan parida babu
mashinshini tana can tana tuwo tuwo a Legas tana aiko ma yayar kudi kuma in sha
Allahu a haka zata kare ga dai kyan da diri da komai amma babu mashinshini, to
in anyi duniya don manzon Allah haka Khaleesar ma zata kare, amma yanxu tunda
muka samu sabon Malamin nan naga aiki da cikawa kema kin san fiddo kudi bazai
kara min wahala ba, ba gashi har na sa an amso min adashina ba daxu, in sha
Allah sai mun karkato da hankalin Abdul kan 'ya yan mu, ko Labisah ko Labibah,
ba dai kyau suke takama da shi ba wai su buzaye, to wallahi sai dai su ga ana
aure....." Shiru Mama Zubaida tayi ganin Salame ta fito daga dakin Umma ta
ci gaba da juya miyarta with serious face, Safiyyah na fita kofar gida ta ciro
wayarta a jaka don tana da number Housemate, tayi dialing numbersa gabanta na
faduwa tana hoping yasan whereabout din Khaleesat, jin Khaleesat take a ranta
kamar er uwarta ta jini, she can't imagine halin da take ciki yanxu, yana fara
ring Jay dake mota tare da Ajay ya daga wayar ganin Safiyyah ke kiransa yayi
picking ya kai kunne calmly yace "How are you Safiyyah?" Da kyar Safiyyah
tace "I am fine, ina kwana?" Yace "Lafiya lau, kin dawo Nigeria
kenan?" Ta gyada kai da kyar tace "Pls tambaya nake son in maka Ya
Jawwad" Jay yace "Ina jin ki Safiyyah" Safiyyah tace "Don
Allah kasan whereabout din Khaleesat, wai tun Saturday ta bar gida har yanxu ba
a san inda take ba, yanxun nan na zo gidansu nake samun labarin" Hawaye na
zuba idonta ta kare maganar, a hankali Jay yace "Halysaah?" Lkci daya
Ajay ya juya ya kallesa, sai kuma ya fixge wayar ya katse ya ajiye, Jay dai
kallonsa kawai yake, can yace "Kawarta ce fa" Ajay yace "And so?
Assignment din announcing whereabout dinta aka baka ne? Me yasa baka da sirri
ne kai?" Jay yace "But it's nothing, kawarta ce kuma tana sonta
sosai, nasan bazata gaya ma kowa komai ba" Ajay ya dau wayar jin ya fara ringing,
yayi rejecting call din Safiyyah sannan ya saka wayar a silent ya zura a
aljihunsa yace "Dama ka saba tona ma mutane asiri kayi ruining plan dinsu
ai" Jay yace "Bani wayata malam" Calmly Ajay yace "Bazan
bayar ba" Dai dai sanda Ajay yayi parking a kofar gidan Aunty Farida ya
kashe motar ya sauka ya bar Jay a ciki. Nenne na isa kofar gidan Gaje tare da
Sha'awa er rakiyarta suka ga yan sanda biyu kofar gidan Gaje da motarsu, ga yan
unguwa sun tsaya cirko cirko ana salallami, Nenne ta ja burki inda take tsaye
tana gwaggwale ido sai ga wata er sanda ta kado keyar Gaje sun fito daga cikin
gidan, Gaje na rusa kuka cikin rudewa take cewa "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, wallahi ban san inda take ba tsakanina da Allahn da ya halicce
ni, in nasan inda take Allah ya tsine min albarka, Al-qur'anin Allah babu
abinda na hada da ita ba dangin iya ba na Baba haduwar gidan duniya ne kawai,
don manzon rahama ku min rai ban hada komai da ita ba" Er sandar tace
"Amma ai an ganta ta shigo gidan ki ranan asabar da daddare, iya gaskiyar
ki kadai ne zai cece ki a wannan case din aki kai ki furson, in kuma kika ce
zaki ci gaba da karya zaki ga illar karya kuwa" Cikin tashin hankali zufa
na keto ma Gaje ta ko ina tace "Wallahi zan fada gaskiya ku tsaya ku saurareni,
tsakanina da Allah ta zo gidana da daddare wajen karfe goma tace in rufa mata
asiri amma bata gaya min abinda ke faruwa ba, ni kuma da na tashi sai na kai ta
gidan wata er dakina Sadiyah Chamo, Sadiyah ce ta bata mafaka a gidanta ta
kwana, kashegari kuwa ta kira wani gingimemen mutumi a wayarta ya zo da katuwar
motarsa ya dauketa suka tafi inda ban sani ba, idan na maku karya a wannan
zance kada Allah yayi min rahama" Er sandar tace "Ina gidan Sadiyar
yake?" Jiki na rawa Baba Gaje ta nuna hanyar gidan Maman Fu'ad, er sandar
tace "Shiga mota mu je ki nuna mana gidan" Gaje ta rushe da kuka tana
cewa "Na shiga uku na lalace ni Al-haqqatu na ja ma kaina masifa a garin
kano" Bayan mota aka bude ma Gaje tana kuka ta shiga er sandar ta dago
mata yakunannen gyalenta dake jan kasa ta dora kan cinyarta sannan ta shiga
bayan motar ita ma, tuni Nenne ta juya sum sum tun ba a lura da ita ba ta shige
wani layi, sai juyawa sha'awa tayi taga gefenta wayam babu Nenne.....
Next update at night in sha Allah.
[6/2, 8:30 PM] khaleesat Haiydar π✍️: A hankali
Khaleesat ta Ιan bude curtain din dakin Aunty Farida tana leko cikin parlon ta
hada ido da su gaba daya, sauke idonta tayi ta shigo parlon walking slowly ta
tafi ta zauna kan kujera kanta a kasa, tun da taji sallama ta tashi ta tafi
dakin Aunty Farida don saka Hijab dinta, gaishesu tayi still not looking at
them, Jay ne kawai ya amsa yana kalllonta calmly yace "How are you feeling
now Housemate?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa a hankali tace "I
am much better now" Kallon Ajay tayi suna hada ido ta sunkuyar da kanta
tace "Ina yini?" Yana danna wayarsa yace "Fine" Aunty
Farida ta shigo parlon daga kitchen ta ajiye masu tray din Can drink da ruwa da
taje dauko masu, sannan ta zauna kan kujera tana kara gaishesu, Jay yace
"Ya me jiki" Aunty Farida tace "Da sauki, abinci ne dai bata ci
har yanxu" Jay ya daga kai ya kalli Khaleesat, sauke idonta tayi ta dau
plate din abincin da Aunty Farida ta zuba mata not long ago, ta bude murfin ta
ajiye sannan ta dau spoon ta fara cin abincin a hankali, Aunty Farida na
kallonsu tace "Bari in kawo maku abinci" Ajay ya kalli Jay, Jay yace
"A'a mun yi breakfast Aunty, mun gode" Aunty Farida tace "To ai
rana tayi yanzu" Bata jira taji me zai ce ba ta tafi kitchen zata zubo
masu abincin, ita dai Khaleesat a hankali take cin abincin hannunta, mikewa
Ajay yayi, Jay ya sa hannu a aljihunsa ya ciro wayarsa, Ajay yace "Zan yi
waya a waje" Daga haka ya fita daga parlon kafin Aunty Farida ta fito daga
kitchen, Jay yayi murmushi bai dai ce komai ba, bude wayarsa yayi yaga miss
calls din Safiyyah har shidda, yayi dialing number dinta ya saka handsfree,
yana fara ring Safiyyah ta daga kamar jira take, yayi kasa da murya yace
"Can you hear me Safiyyah?" Tace "Ina jin ka, plss ba a san inda
Khaleesat take bane tun ranan asabar, kuma ni nasan bata da inda zata je a
garin kano" Yace "Where are you at now?" Da sauri tace
"Nima a kano nake ai, jiya da yamma na dawo daga Maryland shi ne na zo
gidansu yau nake samun labari she is away from home tun ranan Saturday after
receiving the news of her marriage with Abdul, wai Abdul fa aka daura mata aure
da" Safiyya na kai wa nan ta fashe da kuka, Jay yace "I mean are you
at home or where?" Cikin kuka tace "A'a yanxu na baro gidansu, ina
bakin titi ma haka, i am just confuse, Khaleesat bata da kawaye bata zuwa ko
ina, i don't know where she will be now, i am disturb don Allah in kasan inda
take kar ka boye min plss Ya Jawwad trust me" Calmly yace "Look, this
should be confidential Safiyyah, i trust you are saying nothing to anybody
about this...." Da sauri Safiyyah tace "Na rantse babu wanda zan ce
ma komai Ya Jawwad, trust me, i am also not in support of the fruitless
marriage" Jay yace "Ohk, here is ur frnd speak to her....."
Mikewa yayi ya mika ma Khaleesat wayar, ta amshi wayar tana kallon screen din
dama tun jiya take wishing ace Sophie na kusa da ita ko ba komai zata dinga
Consoling dinta tana karfafa mata gwiwa da bata assurance, lkci daya hawaye ya
cika idonta cikin rawan murya tace "Sophie" Safiyyah ta sauke ajiyar
zuciya tace "Khaleesat, i am so happy you are safe and sound, dama fatana
kenan, plss kina ina haka yanxu in taho don Allah" Khaleesat ta girgiza
mata kai cikin sanyin murya tace "Bana kano Sophie" Da mamaki Safiyya
tace "To kina ina?" Khaleesat ta daga kai ta kalli Housemate dinta
dake kallonta, sauke idonta tayi da kyar tace "Ina Lagos" Safiyyah
tace "Lagos wajen wa? Ko wajen Aunty Farida?" Khaleesat tace
"Um" Safiyyah tace "Amma Umma bata san kina nan ba" a
hankali Khaleesat tace "Bata sani ba" Safiyya ta sauke wani ajiyar
zuciyar tace "Pls kar ki tada hankalinki kinji kawata, i know ur Housemate
won't allow u do that, kuma in sha Allah babu zaman aure tsakaninki da Abdul
don bai yi deserving din ki ba, i can't imagine what he will turn you into, in
Allah ya yarda bazai ci nasara akan ki ba, Allah zai raba auren cikin gaggawa,
shi kadai yasan mugun Intention din dake ransa akan ki shi yasa yayi haka, amma
Allah ya fi sa" Khaleesat dai gyada mata kai kawai take hawaye na sauka
idonta ta kasa cewa komai, Housemate dinta ya mike ya nufeta ya amshi wayar a
hannunta ya koma ya zauna yace "Safiyyah" A sanyaye Safiyyah tace
"Na'am Ya Jawwad, Please kawata bata da wanda zai tsaya mata akan issue
din nan, ba da intention me kyau ya saka aka daura auren ba wallahi, mugu ne
azzalumi, har abusing dinta yana yi" Jay dake sauraronta yace "In sha
Allah we will try our very best ki taya mu da addu'a" Safiyyah tace
"In sha Allah, but how can i be reaching her?" Yace "Don't you
have her aunt's number" Safiyyah tace "Sure ina da shi, i will be
calling her ta wayar Aunty Farida" Jay yace "Keep this confidential
pls Safiyyah" Safiyyah tace "Trust me Ya Jawwad, i now have rest of
mind knowing my frnd is safe" Da haka suka yi sallama ya ajiye wayar,
Khaleesat ta ajiye plate din abincin hannunta don ta kasa ci, iya spoon uku
kawai ta iya yi, tuni Aunty Farida har ta ajiye ma Jay abincin da ta zubo ta
nemi waje ta zauna, sai da ta jira suka gama waya da Safiyyah sannan ta kallesa
tace "Ina Junaid din ga abincin na zuba maku" Jay yace "Aunty
bamu dade da cin abinci ba da gaske" Aunty Farida tace "Ai ko in baku
ci ba bazan ji dadi ba, haka jiya ku ka bar min abincin ku ka ki ci, yanxu fa
karfe biyu da rabi ake nema kuma breakfast kace kawai ku ka yi" Jay dai
murmushi kawai yake, can yace "Toh zan ci Aunty" Tace "To ko kai
fa, ina Junaid din kayi masa magana ya shigo ku ci" Jay na shafa kansa
yace "Ai shi ya ci snacks a mota bazai ci abincin ba na sani, bai fiye cin
abinci da rana ba" Aunty Farida tace "Ikon Allah to saboda me?"
Jay yace "Haka yake, iya breakfast da Dinner kawai yake yi" Aunty
Farida tace "Iko sai Allah" Jay na kallon abincin da Khaleesat ta
rage ya mike ya dauko yace "Zan ci wannan kar mu bata abincin Aunty"
Aunty Farida tace "Don Allah ka ajiye ka debi abinci ga plate nan
Jawwad" Yace "Aunty wannan fa ya isheni ba iya cinyewa zan yi ba
ma" Spoon din ya dauka ya fara cin abincin, Khaleesat dai kallonsa kawai
take, Aunty Farida tace "Ai shikenan" Karfe uku da yan mintuna Ajay
da Jay suka bar gidan, Jay ne ke driving din idonsa akan titi yace "To ya
ku ka yi da Lauyan?" Ajay yace "He said we should meet in kano"
Jay ya Ιan kallesa yace "Zuwa gobe kenan?" Ajay yace "Sure,
tomorrow in the morning za mu tafi kano" Jay bai sake cewa komai ba har
suka isa gida, yau dai traffic din da Ιan sauki, bayan Jay yayi parking ya juya
yana kallon Ajay yace "Please since gobe za mu tafi kano ka bar maganar
hotel da kace zaka koma" Ajay yace "Ai matar ne ta fiye takura da sa
ido" Jay yayi dariya bai dai ce masa komai ba suka sauka zuwa cikin gidan,
Ummi na zaune parlon Hadeeyah na kwance kusa da ita da daura kanta a saman
cinyar Ummin, ba tare da Ajay ya kalleta ba ya gaisheta a takaice zai wuce sama
Hadeeyah ta gaishesa ya amsa yana haura stairs, Jay ya zauna parlon ya gaida
Ummi ta amsa tace "Sai yanxu? Ko dai ba Bar beach din ku ka je ba?"
Jay ya Ιan buda ido yace "Mun fasa" Yana magana ne yana kallon
Hadeeyah da ta hade rai tana danna wayarta kamar bata gansa ba, Ummi ta kalleta
tace "Ke baki ga yayanki bane" Hadeeyah na ci gaba da danna wayarta
tace "Oh, ok, Good evening" Jay yace "Ya hanya?" Tace
"Lafiya lau" Ummi na kallonsa tace "Mami tana sama" Jay ya
mike yace "Ohk" Sama ya wuce, Hadeeyah ta bi sa da kallon gefen ido
har ya fara hawa stairs, bayan ya tafi Ummi na kallon Hadeeyah tace "Fadan
ku ka sake yi kenan?" Hadeeyah ta Ιan yatsine fuska taki cewa komai tana
danna wayarta, Ummi ta kyabe baki tace "Kun fi kusa dai" Jay na bude
kofar dakin da yasan Maminsa na ciki ya sameta zaune tana waya, ya karasa ya
zauna kusa da ita yana kallonta yayi mata side hug ya jinginar da kansa a
shoulder dinta a hankali yace "Mami" Mami tayi ma warce suke wayar
sallama ta ajiye wayar hannunta tana kallonsa tace "Ina ka je tun safe
Son? I was thinking zaka zo airport kayi picking din mu" Jay ya Ιan
kalleta yace "Karfe nawa ku ka iso Mami?" Tace "Karfe sha daya
da rabi na safe" Jay yace "Mun fita ne da Ajay, Ummi bata gaya maki
ba" Mami tace "Kaga da ubansa ne zai sauka Lagos duk abinda yake yi
barin sa zai yi ya tafi ya taro sa, amma kai uwarka ta sauka Lagos ya ja ka kun
tafi gantali" Jay bai ce mata komai ba, Mami na kallonsa tace "Duk
karatun ne yasa ka fada haka? Are you okay?" Jay yace "Stress din
tafiyar da nayi zuwa Nigeria ne" Mami tace "Nasan shi zai zugaka ku
dawo Nigeria kar ka biyo min ta UK" Jay ya Ιan hade rai yace "Ya fa
riga ni dawowa Nigeria Mami, ni ba jiya na dawo ba, shi kuma ai tun last week
yake Nigeria" Mami ta tabe baki bata ce komai ba, Jay ya mike ya nufi kofa
yace "Zan je inyi wanka" Mami tace "Dama gobe ka shirya mu tafi
Bauchi ban san gantalin da yake jan ka ku ke yi a Lagos ba, kai da ko ance ka
sauka Lagos baka taba yarda sai gashi saboda Junaid na lagos kai ma ka zauna a
lagos, to gobe za mu tafi Bauchi kuma Hadeeyah ma a can zata yi hutu" Jay
ya juya ya kalleta yace "Mami ni ban gama abinda nake yi ba, kawai ku yi
tafiyar ku" Bai jira me zata ce ba ya fice daga dakin. Wajen karfe biyar
da rabi Jay da Ajay suka sauko downstairs, dakin dake kasa suka nufa don Mami
na ciki tare da wata bakuwarta warce suka hadu da dadewa a Saudia suna zumunci
sun zama kaman en uwa, jin Mami ta shigo Lagos sai matar ta taho gidan gaida
Mami tunda ita ma a Lagos din take, Ajay ya zauna kan 1 sitter dake dakin ya
gaida Mami sannan ya gaida frnd dinta, Jay ma ya zauna ya gaida kawar Maminsa,
matar me suna Hajiya Batula ta amsa da fara'a tana kallonsu sai kuma ta kalli
Mami tace "Wanne ne son din naki a ciki Hajiya?" Mami tayi pointing
Jay tace "That is my son" Matar na kallon Jay tace "Maa sha
Allah, ai kuwa ga kama na gani" Shi dai Ajay danna wayarsa kawai yake bai
dago kansa ba, Jay ya mike yace "Mami za mu je Gym ne" Mami ta
kallesa tace "Da yamman nan ga uban traffic din Lagos ne zaka je
Gym?" Jay yace "Ai ba nisa Gym din" Hajiya Batula tace "Nan
Area din ma ai da Gym ba sai sun je da nisa ba" Jay ya kalli Ajay yace
"Mu je" Mikewa Ajay yayi ya nufi kofa Jay ya bi bayansa suka fice
daga dakin, Hajiya Batula tace "Amma Ιan uwansa ne wannan din ai ko, naga
suna yanayi sosai" Mami tace "Eh Cousin dinsa ne" Hajiya Batula
tayi kasa da murya tace "Ko dai shi ne Ιan sarkin dai?" Mami ta tabe
baki tace "Shi ne" Hajiya Batula tace "Ya sunansa?" Mami
tace "Sunansu daya Ahmad amma Junaid ake kiransa" Hajiya Batula tace
"Ikon Allah, shi kam Jawwad babu ruwansa..." Cike da takaici Mami
tace "Ni babban bakin cikina yanda har yanxu Jawwad bai san ciwon kansa
ba, hakan na ci min tuwo a kwarya wallahi, controlling dinsa kawai yake yana
bin sa, ko a America din ma Junaid din ne ke juyasa" Hajiya Batula tace
"A'a gaskiya bai san ciwon kansa ba naga alama, shi ko kishi baya yi, kuma
gaskiya Mai martaba ya nuna son kansa a fili karara nada Ιan sa da yayi Yarima
me jiran gado a maimakon Jawwad, ina ce Jawwad din ya girmi Ιan sa?" Mami
tace "Ya basa watanni har uku" Hajiya Batula ta rike haΙa tace
"Amma in tambayeki mana Fulani, bayan rasuwan mahaifin Jawwad wato me
martaba Sarki Ahmadu Yusuf shi brother din nasa wanda shi ne sarkin yanxu bai
nemi rikon Jawwad a gabansa ba?" Mami tayi shiru, can tace "Cikin
Jawwad na da wata bakwai mahaifinsa me martaba ya rasu aka nada kaninsa wato
mahaifin Junaid, dama su uku ne gun babansu Sarki Yusuf Ibrahim, daga Mahaifin
Jawwad wanda shi ne babba sai Mahaifin Junaid sannan Maimuna warce nake gidanta
yanxu suna kiranta da Ummi...." Hajiya Batula tace "Ikon Allah, to
amma...." Shigowar Ummi dakin ne yasa Hajiya Batula tayi saurin canza
topic din tace "Yanxu goben za ki koma Bauchi kenan Hajiya?" Mami
tace "In sha Allah" Ummi ta ajiye plate din hannunta tace
"Sannun ku, gashi nan kaza na tsaya gasa maku" Hajiya Batula na
murmushi tace "Allah sarki, sannu da aiki" Ummi tace "Bari in
kawo maku drinks din, a can parlor mai aikin ta ajiye" Daga haka ta fita
daga dakin, Mami tace "Da ma kin ci gaba da maganar ki, ita ma ai bata so
Junaid din da aka nada Yarima me jiran gado ba" Hajiya Batula tace
"To ke sai kika zuba ido aka yi hakan Fulani? In uban Jawwad din bai mutu
ba a ina kanin nasa zai samu har yayi sarauta? Kuma shine bazai yi kara ya nada
Ιan yayansa da ya mutu ya bar masa sarautan Yarima me jiran gado ba sai ya nada
Ιan cikin sa?" Mami tayi wani murmushi tace "Ni fa ko a jikina hakan
da aka yi, Jawwad is doing fine beside shi mulki ma baya gabansa, as far as my
son is okay, i think da a nada sa Yarima da kar a nadasa duk daya..."
Hajiya Batula tace "To halan Junaid din kadai sarkin ya haifa?" Mami
tace "Wani Junaid? Amaryarsa da suke kira da Aunty na da Ιa me shekara 29,
ita in son samu ne ma a nada Ιan ta Yariman ai" Hajiya Batula ta rike haΙa
tana kallon Mami. Ajay yayi parking kenan bayan sun dawo gida wajen karfe
bakwai na dare ya kalli Jay zai yi magana wayarsa ya fara ring, ya dauka yana
duba me kiransa ganin number wani abokinsu ne da kamar bazai yi picking ba
kawai sai kuma ya daga ya kai kunne, after few seconds of listening to what the
frnd was saying ya zaro ido yace "What???" Kallonsa Jay yayi da sauri
don intonation din da yayi using ya nuna ba lafiya ba, Da kyar Ajay ya cire
wayar a kunnensa yana kallon Jay dake kallonsa shi ma babu ko kiftawa, Nan da
nan Jay yaji hankalinsa ya tashi don babu inda mind dinsa yaje immediately sai
gun Khaleesat, Ya fixge wayar hannun Ajay yace "What's happening
plss?" Ajay ya kasa cewa komai tsabar yanda ya girgiza, Jay ya shiga call
logs din wayar da sauri yaga Adams abokinsu ne ya kira nan yaji hankalinsa ya Ιan
kwanta don yasan ba abu bane da ya shafi Khaleesat, dialing number yayi amma
har ya gama ring ba a daga ba, a hankali Ajay yace "Salim aka harba"
Jay bai san sanda ya ajiye wayar hannunsa ba yace "What? Harbi kuma? Is he
dead?" Ajay ya dau wayarsa shi ma ya kara dialing number Adams amma har ya
katse bai daga ba, available flight to kano ya fara dubawa immediately.....
[6/3, 9:01 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Washegari sai
da rana Ajay da Jay suka samu ganin Salem a hospital din da aka yi admitting
dinsa, iya kafadarsa ne kadai aka nannada ma bandage alamar a nan aka harbesa
amma duk kamanninsa ya canza alamar ya ci duka ba na wasa ba, Jay ya zauna
kujeran dake kusa da gadon yana kallon Salem that was in pain yace
"Hasbunallah, How did this happen Salem?" Shi dai Ajay na tsaye ya
rungume hannu shi ma yana kallon Salem ganin yanda aka canza masa kama, ya ma
kasa cewa komai, Salem dake kishingide jikin pillow da kyar don ko iya motsa
kafadarsa daya baya yi ga duk jikinsa yayi tsami yayi karfin halin cewa
"Ban san su ba suka yi attacking dina" Jay yace "Har gida suka
same ka?" Salem ya girgiza kai yace "I stayed out late yesterday in
wudil naje gurin wani abokina, he insisted i stay till the next day amma saboda
ina da abun da zanyi washegari da safe a kano sai naki kwana a garin muka yi
sallama da shi, bayan na kusa unguwan da nake da zama sai na lura da wata mota
na biye dani a baya amma ban yi tunanin komai ba na zata ya shigo layin ne bai
san hanya ba shine yake bi na ko nima fita zanyi daga unguwan mun fita tare,
bayan na shigo layin mu babu kowa saboda dare yayi tun kan ma in sauko daga
motata in shiga gida in bude gate sai nake ma motar alama da hannu ya tafi gaba
zai samu hanya, sai kawai matukin motar ya fito ya nufo ni, duk da haka ban
wani damu ba na zata direction zai tambayeni, na tsaya har ya iso dai dai
gabana ban ankara ba kawai sai jin saukan naushi nayi ta ko ina a fuskata ina
kokarin defending kai na sai sauran mutane ukun dake cikin motar suka fito su
ma suka hau dukana ta ko ina at the same time they were asking me about a girl
i know nothing about, wai inyi providing dinta ko su kashe ni" Da wani
expression Jay ke kallonsa, sai kuma ya mike da sauri ya dafa gadon da Salem
yake kai yace "A girl?" Salem ya gyada kai da kyar yace "Wai
Khaleesat, ni ban ma taba jin sunan ba wallahi, suka yi ta dukana wai sai na
fadi inda take ko su harbeni" A tare Ajay da Jay suka kalli juna, Salem
yace "Kashe ni suka yi niyyar yi banda Allah ya rufa min asiri kururuwan
da nake yi wani soja dake kusa da gidanmu ya fito da bindiga, da wani makocina
da ya fito da adda, kafin makota na su fito ne suka min harbi har biyu daya ya sameni
a kafada daya kuma bai sameni ba ya sami gate, sojan da makoci na suna fitowa
suka shige motarsu suka tsere, ni wallahi ban taba jin sunan yarinyar da suka
ambata ba ma" Aunties din Salem biyu ne suka shigo ward din da sallama,
Ajay ya gaida su sannan ya fita daga ward din ya tafi haraban asibitin ya
zauna, after almost 10 mins Jay ma ya fito, inda Ajay ke zaune ya nufa ya zauna
bai dai ce masa komai ba, Ajay yayi breaking silence din yace "He is
tracking me, ni yake nema ba Salem ba, but tana da number Salem a wayarta
ne?" Jay ya sauke wani ajiyar zuciya yace "Yawanci shi take kira ya
bani waya if there is anything she wants to tell me, ko number ka ma ai Salem
ne ya tura mata, instead cewa zaka yi he is tracking the both of us tunda nima
ta kira layina ai ranan, but how did he get Salem's line?" Ajay yayi
murmushi yace "Definitely layinta ya sa a duba masa numbers din wa enda
take waya da, and he is using that to track us" Jay ya mike yace "We
need to take down our sim card AJ, decidedly zai samu information mun shigo
kano since we are in his list, sannan i think before anything ya kamata mu fara
fighting for her innocent father's release tunda ita Halysaah yanxu bai san
inda take ba and she is safe where she is, but the Man needs help" Ajay
yace "No, i don't think she is safe with her aunt, although aunt din tace
bai san inda ta koma ba amma as far as yana da number wayarta zai iya sakawa
ayi tracing din inda take ita ma" Jay ya juya yana kallonsa yayi shiru, he
just realize of course hakan zai iya faruwa cause ya daina underrating Abdul
yanxu, Jay ya sauke wani ajiyar zuciya yace "That guy is something else
Ajay, duk wata salon mugunta ya sani adding it to his career skills, ina jin
kawai a duba mana if there is flight zuwa Niger republic a biya masu kawai su
tafi can da aunt dinta har zuwa sanda za mu gama da Case din dad dinta, in the
other hand shi kuma mun yi sue dinsa requesting for divorce for her" Ajay
yayi shiru, can yace "But what if she is needed in court?" Jay yace
"For now her lawyer will represent her, in ma an bukace ta a court we will
sort that out" Jay yace "I think that's cool, amma ya kamata mu je
gidan su gun mahaifiyarta" Ajay dai kallonsa kawai yake, can yace "Is
that necessary?" Jay yace "Of course, kasan aunt dinta tace mana the
mother is not medically fit, kada wannan damuwar yayi weighing dinta down"
Ajay yace "Sai mu je a matsayin su wa?" jay ya mike yace "Human
right" Abdul na tsaye rike da takardan da mahaifiyar sa ta mika masa daga
shigowar sa parlor idonsa na kan takardar yana karanta content din jiki, Meema
yayarsa ma na zaune parlon tana kallonsa fuskarta dauke da bacin rai karara,
wani murmushi Abdul yayi ya cukuikuye takardar ya jefar kan kujera, Mahaifiyar
sa dake ta kallonsa ta tabe baki tace "To yanxu menene amfanin wannan tozarcin
da kaskantar da kai da ake yi? Sam kace kai baza ka ji maganata ka dau shawara
ta ba Abdallah?" Meema ta katse ta tana kallonta a fusace tace "Haba
Momy ta yaya kike son ya ji maganarki bayan uban kudin da ya kashe ma
tsinanniyar shegiyar yarinyar? Ai jin maganar ki ba nasa bane wallahi, kuma don
an kawo masa sammaci ba shi ke nufin ya hakura zai saketa ba, kotu ce kawai za
a shiga ayi ta gwabzawa, kuma in sha Allahu duk inda kafafuwana za su shiga sai
na shigar da su don Abdallah yayi nasara a wannan case din, bazan taΙa bari a
tozarta min kanina ba ga mari ga tsinka jaka bazai taΙa yiwuwa ba wallahi,
alamar koma waye ya zugata ta yarda aka yi karansa zai iya biyan ko nawa aka ce
ya biya a kotu, kai jama'a amma yarinyar nan anyi babbar er iska butulu, dama
ni tun asali ban goyi bayan da yace zai kai yarinyar nan Amurka ba ina jiye
masa tsoron kar idonta ya bude, to gashi nan bayan karatun har da karuwanci ta
dinga yi da manyan kasar nan tunda gashi har ta samu wanda zai tsaya mata da
lauya ya biya makudan kudin da aka kashe mata kilan yace har da miliyan 100 da
ubanta ya salwantar, abun arziki dai bai amshe mu ba a family din nan, ban ga
laifin ki da baki son talakawa ba Momy, shi yasa nima bana son su na tsane
su" Momy dai girgiza kafa kawai take tsabar takaici da bakin ciki ta kasa
cewa komai, Meema ta kalli Abdul daka safa da marwa a parlon yana Ιan murmushi
tace "Ka kwantar da hankalin ka Abdul, as far as ina numfashi kuma uwar mu
na numfashi ko don ka rama duk abinda yarinyar nan tayi maka za mu shiga mu
fita har sai kotu ta baka ita, in sun san wata ai basu san wata ba, koma waye
ke taka mata baya daga karshe kashe kudadensa kawai zai yi a banza don sai ta
shigo gidan nan mun ci ubanta da izinin Allah, banda kaddara me ma zaka yi da
er gagurumin barawo kuma makaryaci, daga basa dukiya ya kai Lagos yace an kwace
mota" Sama Abdul ya wuce kamar zai tashi sama, Momy ta bi sa da kallo
cikin bacin rai tace "Kai Allah Ubangiji ya tsine ma mutanen nan albarka,
yanda suka sa Ιa na a damuwa Allah ya saka duk zuri'arsu a damuwa, ita kuma
yarinya Allah ya kasheta ma duk mu huta, tun da lamarin nan ya faru ko abincin
kirki Abdallah yaki ya zauna ya ci a gidan nan, in ya fita tun safe sai dare
muke ganinsa gaba daya ba shi da sukuni akan er talakawa, wannan wani irin
iftila'i ne ya same mu" Meema tace "Tashi tsaye kawai za mu yi ayi
abinda ya kamata Momy, gidan nan ai kamar ta shigo sa ne in sha Allahu, da
bakinta zata ce ita ta hakura a kai ta gidan mijinta kawai, kuma ta shigo nan
ta same mu muna jiranta" Daga haka Meema ta mike ta bi bayan Abdallah. Jay
na zaune tare da Ajay a office din lauyansu suna sauraron sa, lauyan yace
"He is trying to re-litigate a case already resolved in court, don an riga
an rufe case din a kotu tunda yace ya yafe, har lauyoyinsa sun yi filing notice
of discontinuance kuma kotu tayi approving sannan ta kulle case din ta yi
releasing debtor dinsu from any further liability, but like seriously ban san
wani irin lauya bane Ιan sa, don har da written confirmation of debt
forgiveness da suka yi a kotu duk yana nan, why let them arrest the man again?
Ko dai Ιan nasa bai gaya masa consequences din hakan da yayi bane cause this is
pure abuse of process and malicious prosecution" Jay yace "To yanxu
meye abun yi Barrister?" Lawyern ya ajiye pen din hannunsa yace "Za
mu yi Filing motion to dismiss the already forgiven case, and we will plead
abuse of process, sannan muyi Raising estopped from pursuing the debt again in
near future, just that za mu yi presenting
documentation of the original debt forgiveness and court records to the
court, wannan ma ai sun yi breaching court order ne kuma hakan laifi ne me
zaman kansa" Ajay yace "That is because suna ganin ba shi da wanda
zai tsaya masa ko shekara nawa zai yi a kulle, his family have no voice to do
so, that was why the breached the court order for their selfish interest"
Lauyan yace "Babu matsala in sha Allah za mu shigar da kara kotu, and the
man will be bailed out while the case is going on, they will even have to pay
him damages...." Bayan la'asar Ajay yayi parking a kofar gidansu
Khaleesat, dai dai inda yayi parking ranan da suka yi dropping dinta da
daddare, a bayansu kuma wata mota ce ita ma tayi parking, Guard uku ne suka
fito daga cikin motar dukkansu suka yi tsaye jikin motar da suka sauka, shi dai
Jay kallon unguwan kawai yake, Ajay ya bude mota ya sauka, ya jingina da motar
ya rungume hannunsa, Jay ma ya sauko sannan ya zagayo inda Ajay yake tsaye yace
"Where is the house?" Ba tare da Ajay ya kallesa ba yace "Gashi
nan kana kallo" Jay ya kalli gidan dake opposite dinsu, wani almajiri ne
ya zo wucewa Ajay ya kirasa, yaron ya taho da sauri Ajay yace "Shiga cikin
gidan can kace ana sallama da Maman...." Sai kuma ya kalli Jay alamar ya
fadi sunan, Jay na kallon almajirin yace "Kace ana sallama da Maman
Halysaah" Almajirin yace "Toh" Da sauri ya nufi gidan, Ajay yace
"Meye kuma Halysaah? How is that even a name? In zaka kira sunanta na
asali kawai ka kira" Jay na kallonsa yace "Meye sunan nata na asali?"
Ajay bai kallesa ba har sannan yace "Ka fi ni sani ai, tunda ka fi kusa da
ita" Jay ya Ιan yi murmushi bai sake ce masa komai ba, Nenne ce ta leko
kofar gidan tana zazzare ido kuma bata yarda ta fito waje ba, tana yin ido hudu
da su Jay sannan ga wasu samudawa da ta gani har uku tsaye jikin wata motar ta
juya ta koma cikin gidan da sauri har tana tuntube, sai ga Mama Zubaida tana
gyara gyalenta da ta yafa akan daurin kirjin da tayi, Mama Shatu na bayanta
tana kokarin saka hijabinta ta bai bai, tsaye duk suka yi daga cikin gidan suna
leko su Ajay da samudawan dake jikin mota a tsaye, Mama Shatu tayi karfin halin
cewa "Ina wuninku?" Jay ne ya karasa har inda suke tsaye, shi dai
Ajay na rungume da hannunsa yana kallon ikon Allah, Jay ya gaishesu duk suka
amsa kamar munafukai suna gwale ido, Jay yayi kasa da kai yace "Mahaifiyar
Halysaah mu ke son gani" Da sauri Mama Zubaida tace "A'a to ku shigo
mana, Bismillan ku ai tana ciki, fakewa kawai suka yi da cewar bazata iya
fitowa ba bata da lafiya, lafiyarta lauz ku shiga har dakin ku sameta" Duk
tunaninsu an zo tafiya da Umma ne kamar yanda aka zo aka tafi da Malam Ali, Jay
ya juya ya kalli Ajay dake jin duk conversation din su daga inda yake tsaye, ko
ba a gaya masa ba yasan stepmom din Khaleesat ne matan, ya kulle motarsa yana
kallon wa enda ke tsaye jikin mota yayi masu alamar da cewar za su fito in 5
mins sannan ya karasa har inda Jay ke tsaye yana jiransa su shiga gidan, su
Mama Zubaida kuwa har sun koma tsakar gidan sun tsaya cirko cirko suna jiran su
ga yanda za a shigo a fitar da Umma, da hannu suka nuna ma Jay da Ajay hanyar
dakin Umma, Jay ne yayi sallama bakin kofar dakin, shi dai Ajay na tsaye a gefe
yana kallon white t-shirt dinsa to be sure ruwan taΙon da yayi gaja gaja a
compound din bai fallatsar masa a jiki ba, Mama Shatu da Mama Zubaida a tsakar
compound din suke zubar da duk wani ruwan da suka yi aiki haka ma yaransu, sun
maida compound din kamar na mahaukata, gashi simintin da aka masa duk ya dagargaje
ya kusa komawa kasa, shi yasa in suka zubar da ruwa sai ya cabe, kudaje sai
safa da marwa suke ta ko ina, ga kwanuka gaja gaja, igiyoyin gidan kuwa duk an
rataye kaya, Ajay na ganin Jay ya shiga dakin Umma shi ma ya shiga ciki da
sallama, dukawa Jay yayi daga bakin kofar ya gaida Umma da Maman Salame dake
dakin, Ajay ma yayi hakan ya gaishe su, ganin haka Maman Salame ta tashi da
sauri ta shimfida masu darduma a kan ledan dakin tana masu sannu da zuwa, duk
tunaninta ita ma zuwa aka yi za a tafi da Umma amma sai bata ga alamar hakan a
tattare da su ba duba da yanda suka yi gaisuwa cikin girmamawa, Jay ne kawai ya
zauna kan darduman Ajay kuwa ya kasa zama ga wani zafi da yake ji a duk
jikinsa, ya ciro handkerchief dinsa yana goge zufan goshinsa, Mama Salame ta
dau mafici ta mika masa, ya Ιan yi murmushi ya amsa yace "Nagode"
Mama Salame ta dage labulen dakin tana cewa "Yau mun fi sati biyu basu
kawo wutan ba, ance tiranspoma tayi bindiga" Nenne dake makale kofar
bandaki rike da buta ta dinga leka dakin Umma bayan Maman Salame ta daga
labulen, haka su Mama Zubaida da suka ji shiru ba a taso keyar Umma an fito da
ita ba, Jay na kallon Umma dake zaune don ko ba a gaya masa ba yasan ita ce
mahaifiyar Khaleesat duba da kalan fatarta sannan babu ta inda Khaleesat ta bar
ta, ba karamin kama Khaleesat ke yi da mahaifiyarta ba a nan ta samo asalin
kyanta, Yayi kasa da murya yace "Ya jikin Umma?" Cikin sanyin murya
Umma tace "Alhamdulillah da sauki" Ajay ma yayi mata ya jiki ta amsa
tana kallonsu gaba daya don jira kawai take taji me ke tafe da su, in ma cewa
za su yi tafiya suka zo yi da ita dama a shirye take tunda hijab dinta na
jikinta, shiru ne ya biyo baya a dakin, don Jay bai san ta inda zai fara
introducing kansa ba ma, haka ma Ajay da yayi shiru zafi na neman hallaka sa,
after few seconds Ajay yayi karfin halin breaking silence din a hankali yace
"Makaranta daya mu ke tare da Jidderh a can America, so kawarta ta sanar
mana abinda ke faruwa shi ne muka nemi ta bamu address mu zo nan duba ki"
Sosai hankalin Mama Salame ya kwanta jin abinda Ajay yace, Mama Salame tace
"Allah yayi maku albarka, kuma mun ji dadi mun kuma gode da zuwan da ku ka
yi" Jay ya kwantar da murya yace "Kiyi hakuri Umma kuma ki kwantar da
hankalinki, muna tabbatar maki in sha Allah komai zai wuce nan ba da dadewa ba,
don za ayi duk abinda ya kamata, mahaifinta ma in sha Allahu za mu yi abinda ya
dace a sakesa a yan kwanakin nan, ita kanta Halysaah zata dawo gida in sha
Allah" Maman Salame ta daga hannu sama cike da farin ciki tace
"Alhamdulillah ya Allah, gaskiya mun ji dadin jin hakan daga gare ku, don
bamu da wanda zai tsaya mana sai Allah, Alhamdulillah" Ita dai Umma kanta
na kasa hawaye na zuba idonta, Ajay yace "Zuwa gobe da safe in sha Allah
za mu shigo" Mama Salame tace "To Allah Ubangiji ya kai mu goben
lafiya, mun gode, mun gode" Mikewa Ajay yayi ya kara yi ma Umma sallama
sannan ya fita daga dakin kar yayi suffocate, heat wan finish prince, don in
akwai abinda baya shiri da shine zafi, baya son zafi ko yaya yake, Nenne na
ganin Ajay ya fito daga dakin Umma ta sake komawa cikin bandaki da sauri, su
Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi sa da kallo har ya fita daga compound din,
to su waye wannan kuma su da suka baza ido da kunne su ga an fito da Umma tana
kuka, bayan fitar Ajay da few minutes sai ga almajirai suna shigowa gidan da
buhun shinkafa biyu, carton din taliya biyu, carton din indomie biyu, manyan
gallon na manja da mangyada, da carton din maggi duk kuma aka dinga dire su a
kofar dakin Umma, daga Nenne har su Mama Zubaida haka suka saki baki suna
kallon ikon Allah, Maman Salame ta taso zuwa bakin kofa tana kallon kayan
abincin da mamaki tace "Ikon Allah, har da uban hidima haka??" Jay ya
ajiye ma Umma 100k yace "Gashi Umma ayi cefane da wannan, in sha Allah
gobe za mu shigo da izinin Allah" Bai jira cewar Umma that was speechless
and shock ba ga hawayen dake sauka idonta kawai ya fita daga dakin.....
[6/6, 5:08 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Jay na fitowa
dakin Umma, Nenne dake tsaye tsakar gida bayan ta fahimci ba yan sanda bane ta
rushe da matsanancin kuka ta nemi er kujera ta zauna tana kallonsa tace
"Da wannan uban kudaden da ku ka kashe na siyo kayayyakin abincin nan ai
da belin Ιa na ku ka yi, wallahi maraya ne ba shi da kowa, in ba wani ikon
Allah ba sai dai ya rube a can, wancan karan ni kadai nasan wahalan da na sha
na ganin an sako sa, babu inda kafata bata shiga ba wallahi, na dinga bi gida
gida ina neman taimakon kudi" Jay ya kwantar da murya yace "In sha
Allah za mu yi bakin kokarin mu na ganin an sako sa kaka, ki kwantar da
hankalin ki" Nenne na matsar kwalla da gefen haΙar zaninta tace "Ζan
nan ina hankalina zai kwanta Ιa na na can furson? In dai daga gidan radio da
talabijin ku ke ni dai na amince ku zo ku dau muryata da fuskata in nemi
taimakon al'ummar musulmai ku watsa ni duniya ta gan ni ina jawabi, kilan
gwamna ma in ya gani yaji tausayina ya saka baki a sakar min Ιa na" Jay
yace "Ba sai anyi haka ba Kaka, ina tabbatar maki nan ba da dadewa ba zai
dawo gida in sha Allah" Nenne tace "To daga ina ku ke? Ko dai
kungiyar kare haΖΖin en Adam ne" Jay ya Ιan yi shiru, Mama Zubaida da Mama
Shatu dai sun yi cirko cirko a tsakar gida suna gwale ido suna kallon Jay, Jay
yace "Makarantar mu daya da Halysaah a can Amurka, shi ne muka samu
labarin abinda ya faru mu ka zo" Nenne ta mike da sauri tace "To ai
yau kusan sati daya kenan ana neman ta ko sama ko kasa, wallahi bamu san inda
take ba, ita uwar ta na daki tana jimamin ta, ni kuma ina nan ina jimamin Ιa
na, haka muka raba abun, amma tun da yarinyar nan ta samu labarin daurin
aurenta da annoban nan Awdul ta shiga duniya, wallahi bakina da nata tace min
bata son sa bazata iya auren sa ba, tun da uwata ta haifeni ban taΙa ganin inda
ake auren dole ba" Nenne na kai wa nan ta fasa sabon kuka, Jay dai ya ma
rasa abinda zai ce mata, beside baya ma son yayi magana gaban su Mama Zubaida
da suka wangale kunnuwa suna saurare, kawai ya saka hannu a aljihunsa ya ciro
dubu ashirin din da yayi saura, yaje har gaban Nenne ya mika mata da ladabi
yace "Ga wannan Kaka, in sha Allah za mu shigo gobe" Nenne ta daga
hannu da sauri tace "A'a, gwara ku hada kawai ku kai furson a sako min Ιa
na, don yafi min ko wani kudi a duniya" Jay yayi murmushi yace "Ki
amsa kaka, na maki alkawarin za a sako sa nan ba da dadewa ba in sha
Allah" Nenne ta amshi kudin da hannu bibbiyu tana sa masa albarka cikin
rawan murya tace "In ma Allah ya sa kun zo gobe ba ku sameni a nan ba ku
sa a raka ku gidana babu nisa daga nan" Yana murmushi yace "In sha
Allah Kaka" Daga haka yayi mata sallama sannan ya fita daga gidan su Mama
Zubaida suka bi sa da kallo babu fara'a ko wacce da abinda ke yawo a ranta,
Nenne ta kulle kudin a habar zaninta ta soke tace "Dama gobe da asuban
fari zan je gun Malam Na ta'ala, Allah ya sa in samu kwale kwalen da zai
tsallakar da ni da sassafe" Dakin Umma ta nufa tace "To ke Salame
kike ko wa? Ki fito mana ki shigar mata da dukiyar nan dake bakin kofa kar a
faki ido a sungume mata wani abun, kayan abinci ai dukiya ce me zaman kanta a
yanxu, Allah kadai yasan dubu dari nawa suka kashe wajen siyo kayan abincin
nan...." Maman Salame ta fito daga dakin Umma ta fara shigar da kayan
abincin ciki, Mama Shatu ta shige dakinta fuska a murtuke, Mama Zubaida ma ta
tabe baki ta shige nata dakin ta sako tsumman labulenta dake rataye da kyauren
dakin. Jay na fita waje ya tarar da Ajay cikin mota yana zaune a kujera me
zaman banza ya kwantar da seat din kujeran idonsa a lumshe, Jay ya bude driver
seat ya shiga yana kallon Ajay jin yanda ya kure AC din motar gaba daya, Ajay
ya gyara zamansa yana kallonsa, Jay dai yayi murmushi ya fara driving motar
Ajay ya nuna masa hanyar da suka bi suka fita ranan da yayi dropping Khaleesat,
motar dake bayan su ma ya bi su, Ajay sai sake kare ma unguwan kallo yake with
distress har suka isa main road, bayan sun hau saman titi ya kalli Jay yace
"In za a samu gida ko na 30M zuwa 50M ne a siya pls su bar wannan vicinity
din" Jay yace "I think that will be okay idan anyi releasing mai
gidan but not now" Ajay yace "Duk daya ne Bruh, plss kayi ma Salisu
magana a fara duba gidan daga yau zuwa gobe, that house isn't healthy for a
living thing, ta yaya me rai zai dinga rayuwa a gida irin wannan? This is so pathetic,
or am i exaggerating pls?" Jay yace "But haka kawai baza mu yanke
decision without the release of the head of the House ba, so kake mu kara
triggering saurayin nata bayan har yanxu ba mu yi achieving ko abu daya ba, we
are following everything step by step Ajay, we will reach der in sha
Allah" Ajay bai sake cewa komai ba, amma da gaske hankalin sa ya tashi
kwarai ganin condition din cikin gidan most especially the compound, in ba dole
ba shi kam babu abinda zai sake kai sa gidan nan, it's not about the house
structure or where it's located but the hygiene of the house, sai kace cikin
prison, ji yake kamar har ya kamu da cholera don har wani zazzabi zazzabi ya
fara ji, ya kai hannu ya rage Ac din motar, shi dai Jay driving dinsa kawai
yake. Washegari da yamma haka nan suka sake komawa gidan bayan Lauyan su yayi
requesting su tambayi matan Malam Ali ko da akwai wani written debt forgiveness
document kuma original one din da kotu ta bashi bayan masu karansa sun janye
karar, cause in dai babu takardun to sai dai ayi case din biyan bashin da yake
bin Alhaji Musa amma ba dai su yi karan sa ba, Bayan Ajay yayi parking ya juya
yana kallon Jay yace "Zan jira ka" Er dariya Jay yayi yace "Toh
ai da baka biyo ni ba kayi zaman ka a gida kawai" Bai jira cewar Ajay ba
ya sauka daga cikin motar ya nufi cikin gidan, yau ma dai kamar jiya ba su
kadai suka zo unguwan ba don securities da suka biyo su har sun fi na jiya
tunda basu san ko Abdul na da Spy a unguwan ba, infact bazai ma rasa ba,
definitely za a basa labarin wasu sun zo gidan su Khaleesat jiya, so they are
not loosing guard by any means, and they are never going to let him take them
unaware, A takaice Jay ya gaida Kishiyoyin Umma dake zaune tsakar gidan sun yi
rashe rashe da su, yau ko murhu basu kunna ba don dawowar su kenan daga wajen
Malamai, tun asuban fari suka bar gida sai yanxu suke dawowa, duk suka bi Jay
da kallo, Jay dai yana tafe yana kallon Islam da Noor dake ma Umma wanke wanke
a tsakar gidan don ko ba a gaya masa ba yasan siblings din Khaleesat ne duba da
pheomelanin din su, a tare suka gaishesa ya sakar masu murmushi yace "How
are you?" Murmushin kawai suka yi basu ce masa komai ba Islam na wanke
wanke Noor na mata dauraya, Jay ya isa har kofar dakin Umma yayi sallama, Umma
da ta gama gyara dakinta kenan ta saka turaren wuta na tsinke ta amsa sallaman
sa, a kullum in zaka shigo dakin Umma a haka zaka tarar da shi fes fes, duk da
ba komai bane a dakinta don ta siyar da komai nata amma kullum a gyara zaka
same dakin da turaren tsinke, Jay ya shiga dakin Umma na kallonsa tace
"Sannu da zuwa" Tabarma ta dauko ta shimfida masa don bata yi tunanin
zai dawo yau kamar yanda yace mata jiya ba, Jay ya zauna yana murmushi ya
gaisheta, Umma ta zauna kan dardumanta ta amsa gaisuwar sa, har a sannan zaka
ga damuwar dake tare da ita alamar karfin hali kawai take, sai kuma ta mike
tace "Bari in kawo maka ruwa" Ruwa ta debo masa a cup din stainless
ta karaso ta ajiye masa a gabansa sannan ta koma ta zauna, yace "Nagode
Umma" Ζan murmushi kawai tayi, Mama Zubaida da Mama Shatu suka yi tsit a
tsakar gida ko wacce ta kasa kunne ko zata ji abinda ake cewa a dakin Umma,
Ajay ne ya shigo gidan duk suka zuba masa na mujiya, sau daya ya kallesu ya
dauke kai ya nufi dakin Umma, yau dai tsakar gidan a bushe yake bai yi gaja
gaja da ruwa ba da yake basu yi girkin siyarwa ba, Islam na tsaye bakin kofar
dakin Umma bayan ta shiga da kayan wanke wanken da suka yi da twin sis dinta,
Ita kuma Noor na share inda suka yi wanke wanke, Idan Ajay ya kalli Noor sai ya
kalli Islam, ya amsa gaisuwar da Noor ke masa tana rike da tsintsiya, yana isa
bakin kofar dakin Umma ya ja dogon hancin Islam don ita ce ke mugun kama da
Khaleesat har bakinsu iri daya ne, murmushi tayi tana kallonsa yace "How
are you?" Ta sauke idonta bata ce komai ba yanda dai Khaleesat ke yi, da
sallama ya shiga dakin Umma, Jay ya daga kai yana kallonsu don bai yi tunanin
zai shigo ba, Umma ta amsa sallamansa, ya zauna daga gefen Jay sannan ya
gaisheta, Umma ta amsa da murmushin karfin hali tana masa sannu da zuwa, after
some seconds Jay ya fara magana a hankali yace "Umma akwai wasu takardu na
yarjejeniyar kotu na yafiyan bashin da aka yi ma Mai gidan nan, Allah yasa kun
san in da takardun suke ana bukatarsu ne" Umma tayi shiru, can tace
"To, amma wallahi ban sani ba sai dai ko a duba dakinsa ko suna nan"
Jay yace "Eh a duba Umma, Allah ya sa a gani" Umma tace
"Ameen" Mikewa Umma tayi ta fita daga dakin, Mama Zubaida da Mama
Shatu suka bi ta da kallo har ta shiga dakin Malam Ali, after almost 8 mins sai
ga Umma ta fito da wasu takardu wanda bata san ko na menene ba dai zata kai
masu su duba ko akwai wanda ake nema a ciki, a haka ta wuce Kishiyoyinta da
idanuwansa duk ke kanta, ta koma dakinta ta mika ma Jay takardun sannan ta koma
kan dardumanta ta zauna, Jay ya dinga duba takardun daya bayan daya, yaga har
da takardun makarantar Malam Ali, ashe har Degree garesa a Agriculture, kafin
nan kuma sai da yayi diploma, yana ta dai duba tulin takardun har daga karshe
yaga wasu takardun da yake saka rai na yarjejeniyar yafiyar da aka yi ma Malam Ali
a kotu na biyan bashin Mahaifin Abdul ne, ya mika ma Ajay shi ma ya amsa yana
duba takardun, Jay ya kalli Umma yace "Ina jin wannan ne takardun da muke
nema" Umma tace "To Alhamdulillah" Jay yace "To za mu koma,
duk yanda ake ciki za mu dawo in sha Allah" A hankali Umma tace "To
Allah ya saka da alkhairi, amma sai dai akwai wata uwar dakina da bata ji ba
bata gani ba yan sanda suka tafi da ita shekaranjiya har yanxu ba a ma san wani
caji ofis din aka kai ta ba" Ajay dake kallonta yace "Ko Baabar nan
ta Hotoro?" Cike da karfin hali Umma tace "Ita, wallahi bata ji ba
bata gani ba aka je aka tafi da ita" Ajay yayi shiru yana kara mamakin
stupidity din Abdul, he don't think that guy is okay in anyway, after some
seconds ya kalli Umma a hankali yace "Za mu bincika inda aka kai ta mu yi
bailing dinta in sha Allah" Umma ta share hawayen da ya kawo idonta ta
kasa cewa komai, Jay yace "Ki kwantar da hankalin ki Umma, in sha Allah
komai zai wuce da izinin Allah" Cikin rawan murya Umma tace "Allah ya
sa" Jay ya kalli Ajay, tsabar tausayin Umma kawai yaga gwara su gaya mata
gaskiyar inda Khaleesat take ko zata Ιan samu sukuni a ranta, Jay ya sauke
idonsa a hankali yace "Sannan Umma akwai maganar da zan gaya maki yanxu,
amma don Allah kar ki gaya ma kowa har zuwa sanda za mu gama abinda muke"
Ajay ya juya ya wani kallesa don har ya gano maganar da Jay zai gaya ma Umma,
Umma na share idonta tace "To in sha Allah" a hankali Jay yace
"Halysaah na Lagos, amma don Allah ba ma son kowa yasan hakan Umma, ko
makusantan ki kar ki gaya ma tukun....." Umma da zuciyarta ke bugawa tace
"Lagos kuma? Wajen wa a Lagos?" Jay yace "Tana wajen sister din
ki ne, amma mun ce mata kar ta nuna maki tana wajenta har sai sanda komai ya
dai daita, shi yasa ma har yanxu bata gaya maki ba" Umma tayi shiru, amma
fa ji tayi wani nutsuwa ya zo mata, lkci daya kuma taji hankalinta ya kwanta
kamar an yaye mata kashi saba'in na damuwar da take ciki, Umma tace "In
sha Allahu babu wanda zai ji hakan daga gare ni, yanda ku ka tsaya mana ku ma
Allah Ubangiji ya tsaya maku haka, Allah ya saka maku da alkhairi..." Umma
ta kasa ci gaba hawaye masu zafi na sauka idonta, A haka Ajay da Jay suka fita
daga dakin Umma za su koma Office din lauya din su da takardun hoping shi ne
kotu zata bukata, yau ma dai Ajay ji yayi kamar zafi zai kashesa a dakin Umma
amma haka ya dinga daurewa har suka fita daga dakin sannan ya ciro handkerchief
dinsa yana goge zufan da yayi, ya kalli Islam dake zaune bakin kofar dakin Umma
da takardan makaranta a hannunta alamar karatu take, Noor kuma na hura gawayi a
can gefe, ya saka hannu a aljihu ya ciro kudaden da bai san ko nawa bane ya
mika ma Islam yana kallonta yace "Ku raba ke da er uwarki" Islam taki
amsan kudin, ya hade rai yace "C'mon collect it" Jay dake kallonta
shi ma ya sakar mata murmushi yace "Karba mana cutie" Islam ta kalli
Noor amma still taki amsan kudin, Ajay ya zare mata ido yace "Kee, amsa
nace" A hankali ta kai hannu ta amshi kudin, Ajay da Jay suka fita daga
compound din, Kishiyoyin Umma suka dinga kallon uban kudin da aka ba Islam
kamar idanuwansu za su fito ko kiftawan kirki basa yi, Islam ta tashi ta shiga
dakin Umma da kudin a hannunta, Mama Zubaida ta mike ta ma Mama Shatu alamar su
shiga daki, duk suka shiga dakin Mama Shatu sannan suka sake labule, Mama
Zubaida ta rike haba tace "Anya kuwa Shatu baza mu san yanda za mu yi
Abdul ya samu labarin abinda ke faruwa a gidan nan ba? Ni wallahi ban yarda wa
ennan samarin basu san inda Khaleesat take ba, kina fa ganinsu kin ga 'ya yan
masu kudi, dubi suturan da suka sa wa, ji motocinsu, sannan kalli fatarsu kalan
ta yan hutu, in fa muka yi sake Shatu bakin ciki ne zai kashe mu a gidan nan
muna ji muna gani" Mama Shatu tace "Ke ma dai wallahi kin fiye
gaggawa, sai kace kin manta me Malamin yace mana, duka duka ba yau muka kai masa
kudin ba, to mu zuba ido ya fara aiki mana tukun" Mama Zubaida tace
"Duk da haka dai gwara mu ma mu dinga yin namu ta bayan fage Shatu, kada
mu sakankance mu bar malami da aiki shi kadai, ya kamata tun wuri mu san yanda
za mu yi mu ankarar da Abdul abinda ke faruwa a gidan nan, don gaskiya na sha
jinin jikina da wa ennan zaratan samarin, ke ki ga tulin kudin da suka ba
Islam, sannan kalli uban kayan abincin da suka jibge jiya daga karshe don
walakanci aka biyo mu da kwano uku uku da taliya bibbiyu da man gyada da manja,
sai maggi leda bibbiyu ga mayunwata, ke kiji wai yau Zahra'u ce da tsam mana
kayan abincin da aka jibge mata, bayan haka Allah kadai yasan nawa suka bata a
daki tunda ba gaya mana zata yi ba, ga Nenne ma a gaban mu aka bata rafar kudi
yan dubu dubu, anya bamu shiga uku ba Shatu? Ni fa jikina yayi sanyi hankalina
ya tashi, meye hadin su da Khaleesat din da har suke wannan hidima haka a
kanta, mu ga 'ya yanmu a zube har yau babu mataya sai talla suke, ni fa wallahi
ko tsirara zan yi yawo gwara inyi da dai Zahra'u da zuri'arta su ji dadi a
duniya" Mama Shatu tace "Yanxu dai Gwaska za mu samu ya raka mu gidan
su Abdul din tunda yace yasan gidan uban sa, nasan Abdul din zai taka ma yan
iskan burki har ma ya bamu makudan kudi fallasa asirin abinda ke faruwa da mu
ka yi" Mama Zubaida tace "Atoh dai tun wuri my gaya masa abinda ke
faruwa, zuba ido ba namu bane wallahi, amma sai dai jibi kenan za mu je gidansu
Abdul din don Gwaska ya tafi dambatta daxu uwarsa ke gaya min yaje kai kaya
can" Mama Shatu tace "Ai jibin kamar gobe ne, kin ga gobe dama mu
gama girkin mu da wuri mu tafi inda wannan matar ta mana kwatance daxu a gidan
Malam" The next day wajen karfe biyar da rabi na yamma Sha'awa tayi
sallama bakin kofar dakin Umma dake yi ma yan biyun ta gyaran gashi, babu kowa
gidan don duk yan matan gidan basu dawo talla ba, kananun yaran kuma sun tafi
gantali, tun Sha'awa bata shigo dakin Umma ba take cewa "Umma yanxu
Ladingo ke sanar min an sako Gaje, wai daxu taje unguwan taga ana ta shiga
gidan yi mata jaje" Umma ta sake gashin Noor ta mike da sauri tace
"Da gaske Sha'awa?" Sha'awa tace "Wallahi kuwa Ladingo bazata
min karya ba Umma, tace Gaje dai ta dawo gida ga yan unguwa na ta tururuwan
shiga yi mata jaje tun daxu" Umma ta jawo Hijab dinta tace "To bari
in je gidan Allah ya sa da gaske ne dai" Sha'awa tace "Da ina da
kudin mota ai da mun je tare Umma, kusan kwanan ta biyar fa a kulle, don ma
akwai kanwarta da zata kula da jikokinta tunda uwarsu na can Libiya ta tafi
aikatau, ubansu kuma yayi watsi da su, banda haka da yaya makomar jikokin nan
nata fisabilillahi?" Umma bata tanka ta ba ta gama saka hijab dinta ta
daura nikab ta dau purse zata fita, Noor da Islam suka marairaice wai za su bi
ta, ganin in ta tafi su kadai zata bari a gida yasa tace su saka hijab gaba
daya, haka nan duk suka saka Hijab suka fita daga dakin Umma na biye da su,
kusan kullum sai Umma taje gidan Gaje sau biyu ta duba ko ta dawo amma sai taga
akasin haka sai dai ta samu kanwarta Iya a gidan, jiki a sanyaye take juyawa ta
koma gida don Iya na ganinta take fara masifar ita ta saka er uwarta a uku,
Umma zata fita gidan tare da yan biyunta sai ga su Mama Shatu da Mama Zubaida
sun shigo wujiga wujiga da su, kana ganin fuskokinsu kasan a gajiye suke likis,
ga wuyan hijabinsu duk yayi jagab da zufa, kafafuwarsu kuwa kamar wa enda suka
dawo daga gona, Umma dai tayi masu sannu da zuwa kawai ta fita daga gidan su
Islam na biye da ita, ai ko tana isa gidan Gaje taga da gaske an sako Gaje,
Gaje na ganin Umma tayi kamar bata taΙa saninta ba a duniya, yanda take amsa
gaisuwa da jajen masu shigo mata haka ta amsa ma Umma kamar ranan ta fara
ganinta, ita dai Umma na zaune tayi shiru ta ma rasa me zata ce, su Islam na
zaune gefenta, Gaje bata sake kallon direction dinta da yaranta ba, duk wanda
ya shigo haka take sanar masa yanda Maman Fu'ad ta ci amanarta tace ma yan
sanda ita bata taΙa ganinta ba ma balle wata Khaleesat, In tayi bayanin sai ta
rushe da kuka tace "Ban taΙa tunanin Sadiyah zata min butulci haka ba duk
alakar da ke tsakanin mu wai bata taΙa gani ba, kaji tsoron Allah kaji tsoron
mutumin yau kawai, duk kyautata ma yarinyar nan da nake amma ta barni ni kadai
raina a cikin matsalar da na tsoma kaina" Ita dai Umma tayi tagumi tana
sauraron duk abinda Gaje ke cewa.
[6/9, 7:26 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Sai bayan da
aka yi sallan Magrib Umma ta bar gidan Baaba Gaje da yan biyun ta, kuma har ta
bar gidan Gaje bata nuna ta taΙa saninta ba don casually ma take amsa mata
kamar yanda take ma kowa da ya shigo mata jaje, Umma dai a sanyaye ta baro
gidan, tana isa gida taga mutane tsattsaye a kofar gida kowa da abinda ke
fitowa bakinsa, sosai taji gabanta ya fadi gashi ta kasa fahimtar akan me ake
ta surutu haka, can dai ta dubi wata makociyarsu dake tsaye wajen tace
"Munnira me ke faruwa?" Munnira tace "Wallahi Umman su Khaleesah
nima fitowa ta kenan da naji hayaniyar tayi yawa, amma wai kamar wasu mutane ne
da ba a san ko su waye ba suka shiga gidan naku suka yi aika aika, ance a
katuwar mota suka zo...." Umma ta kasa cewa komai tana kallonta, da kyar
take jan kafa tana rike da su Islam ta shiga gidan har sannan gabanta bai daina
faduwa ba, Su Mama Shatu da Mama Zubaida ta gani tsaye da 'ya yan su duk sun yi
cirko cirko a tsakar gidan da makota ana ta maida magana, tsakar gidan dai cike
yake da jama'a kowa na fadin albarkacin bakinsa, Umma ta dake tace "Wai me
ke faruwa ne a gidan?" Mama Zubaida ta wani kalleta a walakance tace
"Ina kuwa za mu san me ke faruwa tunda mu dai muna zazzaune sai ga wasu
kattin gardawa sun kusa goma babu annuri a tare da su sun shigo mana gida da
makamai suna tambayar dakin Malam, basu tsaya iya dakin Malam ba hatta sauran
dakunan gidan nan sai da suka shiga..." Sai a sannan Umma ta lura da bakin
kofar shiga dakin Malam Ali, gaba daya yayi kaca kaca da takardun da ta mayar
daxu bayan su Jay sun dau wanda za su dauka, har kayan cikin dakin sai da aka
watso su waje har da er katifarsa da akwatin kayan sakawan sa da butar
alwalansa, Umma ta juya tana bin tsakar gidan da kallo taga har dakinta an fito
da kaya an yi watsi da su waje, da kyar Umma ta karasa kofar dakin Malam Ali ta
leka ciki taga basu bar komai ba, dama ba wasu abun kirki ke cikin dakin ba,
can ta juya tana kallon Kishiyoyinta amma ta ma rasa me zata ce, Mama Shatu ta
kyabe baki tace "Ni takaicina dakunan mu da suka shiga wai ina takardun da
Malam ya ba mu ajiya, ni ko nace mu muka san wasu takardu mu da bamu yi karatu
ba ta yaya Malam zai bamu takardu mu ajiye ai sai dai ko ya ba er sa da aka kai
turai karatu daga karshe tayi ma wanda ya kai ta karatun butulci wai bata son
sa kuma, amma ina mu ina ajiyar takardu mu da muke jahilai" Umma bata
tanka ta ba ta duka tana tattara takardun dake watse bakin kofar su Islam suka
je suna tayata, a haka duk ta maida kayan Malam Ali cikin dakinsa, su Mama
Zubaida sai hararanta suke, can Mama Shatu ta kyabe baki tace "Mu dai mun
san ko ma wani takarda suke nema bazai wuce yana da alaka da er ki ba kilan
kotu za a shiga, tun da kika haifi yarinyar nan muke shiga jarabawa munana a
gidan nan, ko kuma muce tunda aka auro ki, mu da bamu san wani talauci ba balle
wahalar rayuwa, daga auro ki karayar arzikin da ba a taΙa yin irinsa a tarihi
ba ya samu Malam, sannan gashi sanadin er da kika haifo ga abinda ya samu Malam
a karo na biyu, daga ke har 'ya yanki babu wani abun alkhairi a tare da ku sai
masifa, ina ma Malam zai yada kwallon mangwaro ya huta mu ma mu huta ki tattara
ki koma can kasar ku ki auri buzu Ιan uwanki" Sha'awa dake tsakar gidan
wanda tana daga cikin mutanen farko da suka shigo bayan Mama Zubaida da Mama
Shatu sun kurma ihu, amma fa sai da gardawan suka fita sannan suka samu bakin
ihun neman agaji su da yaransu, Sha'awa tace "Haba Mama Shatu, wannan wani
irin magana ce kike yi haka don kin ga Ummansu Khaleesah bata tanka ku a gidan
nan, wannan ai cin fuska ne, kar fa wataran ku kureta ayi dauki ba dadi a gidan
nan, don mai hakuri bai iya fushi ba wallahi" Wani zagi Mama Shatu ta
kundumo mata a fusace, Sha'awa ta rama tace "Wallahi ba dai ubana ba, sai
ko in naki uban me gyaran keke dake kabari" Ganin fada na kokarin kaurewa
a tsakar gidan Umma da wasu mata suka fitar da sha'awa dake kunduma ma Mama
Shatu zagi ta uwa ta uba, ga su Labeebah na kokarin dambe da Sha'awa dake zagar
masu uwa su ma duk aka rirrike su, a haka dai aka fitar da Sha'awa dake gyara
daurin zaninta da ya kusa faduwa gashi babu komai kasan zanin, tana huci take
cewa "Shegu en kutumar uba masu bin bokaye, ko jiya sai da aka bani
labarin kun je wajen wani boka na kuma san warce ta raka ku, kun ga kuwa Umman
Khaleesah ta fi ku ko a wajen Allah tunda bata san hanyar zuwa gun Malamai
ba" A haka dai aka fitar da Sha'awa daga gidan, Umma dai jiki a sanyaye ta
tafi kofar dakinta ta tarar su Islam suna ta maida kayan cikin dakin da aka
watso waje bayan sun kunna er fitilar dake ba dakin hasken, Noor na kallon Umma
tace "Umma kinga babu kayan abincin a inda suke" Umma ta kalli inda
Maman Salame ta ajiye mata kayayyakin abincin da su Jay suka kawo taga wayam,
tsayawa tayi tana kallon wajen babu ko kiftawa tsabar mamaki yasa ta kasa cewa
komai, muryar Nenne taji a tsakar gidan cikin fushi tana cewa "Innalillahi
wa inna ilaihi raji'un, meye haka aka cika gidan nan kamar ana taron farin
ciki? Ku yan unguwan nan tsabar munafurci da gulma bakwa tashi shigowa sai
iftila'i ya faru sannan ku bi ku cika ma mutane gida ko wacce da warin jikinta,
farin cikin iftila'in ku ke ko menene haka? Doo Allah duk ku fita ku ba mutane
waje mu ji da daya, ai ba kanmu farau ba, en iska kawai magulmata" Rai
bace ta nufi dakin Umma hannunta rike da jarkar manja daya hannun kuma rike da
tocilan ta, ta tsaya daga bakin kofa tace "Zahra'u me suka dauka a dakin
Alin da suka zo?" Umma da ta zauna gefen katifar ta tace "Shigowa ta
kenan nima Nenne, na je gidan Baaba Gaje an sakota daxu da yamma" Nenne ta
kalli kayan da su Islam ke shigarwa daki tace "Har dakin naki suka shiga
ne? To ni Usama ce min yayi iya dakin Ali suka shiga suka watso kayan ciki, ke
kuma wa ya watso naki tsummokaran waje?" Mama Shatu tace "To shi da
ya sulale ya gudu ya bar gidan ta yaya zai ce iya dakin Malam suka shiga? Ai
babu dakin da basu shiga ba a gidan nan yau, mu ma duk mayar da namu kayan mu
ka yi, hatta babban jarkan mangyada da na siya jiya sun dauke, iya shi suka
dauka a dakina, Ita kuwa Zubaida kwashin adashin da aka kawo mata suka
dauke" Nenne ta fara matsar kwalla cikin rawan murya tace "Lallai na
ga abinda ya isheni bai ishi Ubangijina ba, to yan fashi Awdul din ya aiko mana
wannan karan? Don dai duk mun san yafi karfin wani kudin adashin da bai taka
kara ya karya ba balle wata jarkan mangyada, Allah mun gode maka da wannan
rantsattsiyar jarabawan da mu ke ciki mun gode maka Allah, Alhamdulillahi ya
Allah, Ina ga in ba tattarawa muka yi muka hakura da zaman birni mu koma kauye
gaba daya ba muna cikin mummunan hatsari a Mariri gashi ba mu da gata, kar
wataran cikin dare mun saki baki muna bacci su babbake mu, su babbake banza
tunda babu me tsaya mana" Ita dai Umma tayi shiru bata ce komai ba, Nenne
na kallonta tace "Su kuma samarin da suka sha uban fararen kaya suka zo
mana nan suna kwambo dama yaudarar mu suka zo yi bamu sani ba, sun zo nan sun
gama cika mana baki sai gashi tunda suka karkade wandonsu suka fita bamu sake
ganin keyar su ba, to ina amfanin karya? har da ce min za a saki Ali kwanan nan
ashe duk yan iskan gari ne makaryata bamu sani ba" Umma dai kallon Nenne
kawai take, Nenne ta mika ma Islam jarkan manjan hannunta tace "Ba ruwana,
wahalan da nake ta sha kan Ali ko shi ya halittoni duniya ai sai haka, kai
kenan kullum ayi ta garkame ka kamar kasungumin barawo, sai kace wanda yayi ma
Allah wani saΙon da bamu sani ba, saura kadan kwale kwalen da na hau jiya zan
je nema masa taimako ya kife da mu banda Allah ya tsare, to ina dalili bayan ba
shi kadai na haifa ba, in ya kasheni sauran su yi yaya? ke ungo amsa ki mika ma
uwarki ta tsiyaya min manja, nawa ya kare" Islam tace "To ai an
kwashe kayan abincin gaba daya Nenne" Nenne ta gwalo ido tana kallon
direction din da aka ajiye kayan abincin taga wayam, bude baki tayi tana kallon
Umma tace "Zahra'u ina kayan abincin? Ko kasuwa ki ka kai kika siyar?
Fatarar taki ta kai haka Zahra'u?" Umma tace "Saboda me zan kai kayan
abinci kasuwa in siyar Nenne, daga zuwa gidan Baaba Gaje in dawo nima na tarar
an kwashe kayan abincin" Nenne ta ajiye jarkan hannunta a kidime ta saki
salati tana tafe hannu tace "Baki kulle dakin bane Zahra'u?" Umma
tace "In zan fita ai ina sa ma dakina kwado, to fasa kwadon aka yi, ga
makullin ma a jakata" Nenne ta juya ta fita daga dakin dai dai shigowar
Usama wani almajirin Malam Ali dake tare da shi tun yana da arzikinsa, kuma har
yanxu dai yana tare da shi, Nenne na haska sa da tocila tace "Yauwa Usama
kace iya wani daki mutanen suka shiga a gidan nan?" Usama yace "Iya
dakin Alhaji kawai suka shiga" Nenne bata sake cewa komai ba ta nufi dakin
Mama Zubaida don yafi kusa da ita, tana dage labulen dakin ta fara haske hasken
tocila, sai kuma ta duka karkashin gadon karfen dake dakin ta hango carton din
indomie biyu an tura su can ciki, ta kwalo ma Usama kira ya karaso da sauri
tana haska masa karkashin gadon tace "shiga ka jawo min kwalayen taliyar
yaran can" Ai ko ya shiga ya kwaso su ya fito da su, Nenne ta shiga cikin
dakin tana duba bayan kyaure nan ma taga Babban jarkan man gyada ta sa Usama ya
fiddo waje, ta gama duba dubenta a dakin bata ga wani kayan abincin ba sannan
ta nufi dakin Mama Shatu, a bayan kyaure taga buhun shinkafa daya da quarter an
lullube da zani, ta kwalo ma Usama kira shi ma ta saka ya kinkimo su ya fitar
waje, a dakin Mama Shatu still taga kwalayen taliya da na maggi da jarkan manja
duk ta sa Usama ya fiddo su waje, Nenne na kallonsa tace "Kwashe su ka
mayar dakin Zahra'u Usama" Yace "To Nenne" Sai a sannan Nenne ta
juya tana kallon su Mama Shatu da suka yi wuki wuki da ido ko wacce na kokarin
diban ruwan alwala a buta, Nenne tace "An dai yi asara duniya da lahira,
barayin banza barayin wofi, tirrr da halin ku, wato ga sabon jarin kayan abinci
kun samu ko, tunda Zahra'un ta maida kanta er wahala warce bata san ciwon kanta
ba, da ban ce a tsam min manja ba shiru zata yi maganar ta bi rariya ta bar ku
da haram, ko zama da ku kadai ya isa ya dinga jefa Ali a masifa iri iri, ai ba
kyau zama da jahilai shine kawai bai gane ba" Daga haka ta juya ta koma
dakin Umma. Khaleesat na bakin pampon dake compound din Aunty Farida tana wanke
wanke, ita kadai ce a gidan gaba daya don duk sauran tenant dake gidan sun fita
aiki, Aunty Farida kuma ta tafi kasuwa, juyawa Khaleesat tayi jin an bude gate,
ta mike tsaye tana kallonsa, murmushi ya sakar mata ya rufe gate din ya karaso
cikin compound din shi ma yana kallonta, ta sauke idonta a hankali tace
"Sannu da zuwa" Yace "Good morning Halysaah" Ζan murmushi
tayi ta sunkuyar da kai ta gaishesa sannan ta juya ta tafi ta bude masa kofar
shiga parlon Aunty Farida tana kallonsa, yace "Aunty fa? ina ta kiran wayarta
no response" Khaleesat tace "Eh ta bar wayar a gida ne ta tafi
kasuwa" Ya kalli plastic chair dake veranda din Aunty Farida yace
"Let me seat here ba sai na shiga ba, i just came to check on you"
Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "I really appreciate
Housemate" Yace "To ki zauna mana" Ta kalli second chair din
dake wajen sannan ta zauna, sake gaishesa tayi da ladabi tana kallonsa, yace
"Lafiya lau Halysaah, how is ur body?" Tana wasa da gefen karamin
veil din jikinta tace "Naji sauki" Yace "To amma naga kin rame,
baki cin abinci ne?" Tayi shiru, yace "Baki ci ko?" Ta Ιan yi
murmushi tace "Ina Ιan ci kadan" shiru ne ya biyo baya for almost 30
seconds, ta Ιan daga kai ta kallesa taga kansa a kasa, ajiyar zuciya ya sauke
calmly yace "Everything will be alright soon in sha Allah Housemate"
Nan da nan hawaye ya cika idonta, da kyar tace "But i don't know my mom's
condition, i am really worried" Jay yace "Don't worry, Umma tasan
kina nan, mun je can gidanku da Ajay, i assure you everything is fine back home
do not worry ur self pls, yanxu dai we are working on clearing ur dad first
before anything, soon in sha Allah he will be free from the debt" Hawaye
na sauka idonta tace "To amma ni bazan iya zama da Abdul ba tsoron sa nake
wallahi, kawai torturing dina zai yi yayi revenging abinda nayi masa, i am
afraid" Jay yace "Do not be Housemate, we won't allow that happen in
sha Allah, we will go to any extent na ganin hakan bai faru ba" Khaleesat
dai tayi shiru tana share hawayen idonta, after some seconds yace "Baki
tambayi Ajay ba?" Ta daga kai tace "Na zata tare ku ke yana
waje" Jay yace "Not at all yana kano, bai ma san nayi tafiya ba, i
took an early morning flight, zuwa 12 noon kuma zan koma kano in sha Allah, i
just came to check on you" Khaleesat na kallonsa cikin sanyin murya tace
"Nagode sosai, kuma naji dadi" Ya kalli agogon wrist dinsa dake nuna
karfe sha daya saura yace "I will be leaving for the airport now kar inyi
missing flight dina, kafin Ajay yayi noticing i am not home ya fara damuna da
kira" Khaleesat tace "Ko ruwa baka sha ba, ko in kawo maka shayi?
Kilan ma baka yi breakfast ba ko?" Da damuwa tayi tambayar tana kallonsa,
Yace "No i am okay Housemate" Wayarsa ne ya fara ring ya ciro yana
kallon screen din yayi murmushi sannan ya nuna mata screen din taga Ajayn ne ke
kiransa, mayar da wayar yayi aljihunsa sannan ya fiddo 100k ya mika mata yace
"In case you need anything Halysaah" ta girgiza masa kai tace
"A'a Nagode, bana bukatar komai wallahi" Mikewa yayi ya ajiye mata
kudin a kafarta ya fita daga balcony din yace "Take care of ur self
Housemate, idan na sake samun lkci ko zuwa nan da few days ne zan dawo in sha
Allah, my regards to Aunty Farida" Khaleesat ta mike tana kallonsa ta kasa
ce masa komai wasu sabbin hawayen suka cika idonta, ya daga mata hannu kawai ya
nufi gate don bai ma son ganin hawayen nata, tana kallonsa har ya fita sannan
ya rufo gate din, parlon Aunty Farida ta shiga ta zauna kan kujera ta rufe
fuskarta tana rera kuka tana shessheka..... Bayan few weeks na zirga zirga a
cikin garin kano, da kuma zuwa court lauyan su Jay yayi Succeeding na amsan
Bail din Malam Ali, afterward suna sa ran kotu tayi dismissing claim din Alhaji
Musa saboda previous debt forgiveness dake kasa, a kuma yi masa imposing
monetary sactions for abuse of process, all this weeks Jay da Ajay where so
cautious of der movement in kano and they were at alert In case of necessity ko
kadan basu ba Abdul chance din yi masu ba zata ba cause sun san bazai rasa
informant a unguwan ba, ranan da suka yi dropping din Malam Ali a gida bayan
kotu ta bada bail dinsa farin ciki gun iyalinsa da wasu yan unguwan ba a cewa
komai barin ma Umma, sai shigowa gidan ake ana taya sa farin ciki, shi ko Malam
Ali har kasa ya duka cikin ladabi yana gode ma Jay da Ajay, shi dai Ajay ya
juya ya koma jikin motarsa ya tsaya ya rungume hannu, ga motar escort dinsu a
bayan motar tasa, Jay har ya gaji da ce ma Malam Ali ya dena masu godiya,
Calmly yace "Don Allah Baba ka dena mana godiya, mu saboda Allah muka
yi..." Malam Ali na gyada kai yace "To... to...to wannan gaskiya ne,
Allah Ubangiji ya maku albarka, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara
daukaka, Nagode Nagode" Duk a birkice yake godiyan, Mama Shatu ta dauko
tabarma ta shimfida tace "Taho ka zauna ka huta ko zaka dawo seti Malam,
naga duk a firgice kake" Nenne ce ta shigo unguwan bayan wani almajiri
yaje har gidanta ya sanar mata Malam Ali ya dawo, mayafin nata ma a baibai ta
yafa ga dankwali da ta kima a kan mayafin tana hade hanya ta taho gidan Ιan
nata, bata kula da Ajay a kofar gidan ba ta shige ciki da sauri, Ajay ya ciro
wayarsa dake vibrate a aljihunsa yana duba me kiran sa, gyara tsayuwarsa yayi
yana kallon screen din wayar babu ko kiftawa ganin Aunty Farida ke kiransa,
haka kawai yaji zuciyarsa ta harba don Aunty Farida bata kiransa all this
while, in ma da wani abu shi ne ke kiranta, ya kalli Jay da ya fito daga cikin
gidansu Khaleesat, har sannan ya kasa daga kiran Aunty Farida.
[6/10, 6:29 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Jay ya karasa
har inda Ajay ke tsaye yace "I think we can take our leave now, nan da
friday sai a basa makullin sabon gidan, we just hope he will accept it"
Shi dai Ajay bai ce masa komai ba don bai ma san me yake cewa ba, ganin
yanayinsa Jay yace "Are you alright Bruh?" Jin Ajay bai basa amsa ba
ya kalli wayar hannunsa that was still vibrating yace "Who is calling
you?" Ajay ya sake kallon screen din sannan yayi picking dab da kira na
biyu zai katse, kunne ya kai wayar yayi shiru yana sauraron yaji abinda Aunty
Farida zata ce, muryar Khaleesat yaji a hankali tace "Good evening, Plss
can i speak to my Housemate?" At first shiru Ajay yayi, can babu yabo babu
fallasa yace "About?" Khaleesat ta girgiza kai murya can kasa tace
"Ba komai, kawai dai ina son zan masa magana ne" Jay dai kallon Ajay
kawai yake don bai san da wanda yake wayan ba, a takaice Ajay yace "Don't
you have his digit?" Bai jira cewarta ba ya katse wayar ya mayar aljihu,
Jay yace "Who is that?" Banza Ajay yayi masa ya bude driver seat ya
shiga ya tada motar fuskarsa a daure, Jay ya daga shoulder sannan ya zaga ya
shiga gaban motar shi ma bai sake kulasa ba, Ajay ya ja motar suka bar anguwan
motar bayansu na biye da su. Bayan
sallahn magariba Malam Ali na zaune tsakar gida tare da Nenne da duk matansa
sai yaran gidan gaba daya, Nenne ce kadai zaune kan kujera er tsugunno, sauran
duk kan tabarma suke a zaune kowa na jiran jin dalilin zaunar da su da Nenne
tayi, Umma dai na kusa da bakin kofar dakinta da su Islam da Noor a jikinta,
Nenne tayi gyaran murya tace "Da farko dai nayi farin ciki ainun da
dawowan Ιa na daga furson a karo na biyu, ina rokon Allah ya sa iya bakin
wahalarsa kenan sannan muna fatan yayi zuwan karshe kenan, wa ennan samari da
suka zo suka tsaya mana kuma har suka kubuto da Ali Allah Ubangiji ya masu
albarka don da farko na zata makaryata ne kawai en neman suna, duk da dama inda
naje ance min za a roki Allah ya kubutar da Ιa na, nafi tunanin ma rokon Allahn
da aka yi ne kawai hakan ta faru ba wai don samarin nan ba, mun dai gode koma
ya ya ne, sannan shawaran da zan bada shi ne muyi bulaguro mu koma kauye gaba
dayanmu na en shekaru kafin komai ya lafa, mu ma hankalinmu zai fi kwanciya da
hakan don Alhaji Musa da tsinannen Ιan sa ba barin mu za su yi mu zauna lafiya
ba, duk da kotu ta wanke Ali amma Allah kadai yasan wani sharrin za su billo da
shi don mutane ne wa enda babu Allah a ransu, wallahi sai su iya sa wa duk a
kona mu cikin dare muna bacci, kunga ance zaman lafiya yafi zama Ιan sarki shi
sa cikin rufin asiri mu tattara komatsanmu ko zuwa gobe da magariba ne Ali ya
mana shatan katuwar tirela mu koma kauyen mu" Mama Zubaida da Mama Shatu
da suka saki baki suna kallon Nenne kusan a tare suka ce "Kauye kuma
Nenne?" Nenne na kallonsu da kyau tace "Kwarai kuwa kauye, don dama
can ne asalinmu, na gaji da tsallaka kogi cikin kwale kwale zuwa neman ma Ali
taimako wataran inje in kife, gwara tun da sauran mutuncinmu mu bar garin
nan" Mama Zubaida na girgiza kai tace "Inaaa, ai bazata saΙu ba gaskiya,
sai dai ni a bar ni a nan in ci gaba da kasuwancina ina rufa ma kaina da 'ya ya
na asiri, akan matsalar da buzuwar matarsa da er ta suka jawo baza a cucemu a
mayar da mu riga ba, bazai ma taΙa yiwuwa bane gaskiya" Mama Shatu ta
cafke tace "Sai dai ya tattara matarsa da 'ya yanta su kuma kauye Nenne,
amma mu kam muna nan tunda ba mu ko 'ya yanmu muka jawo magana ba, dama mu ke
ciyar da kan mu balle mu ji tsoron zamu rasa abinci" A fusace Nenne tace
"A yaushe ku ka fara ciyar da kan naku munafukan Allah? ba sai bayan da ku
ka tsiyace sa da fararen kafafuwan ku ba tukun? Ai ko Alhamdulillah kowa zai ma
Ali shaidan kula da iyalinsa banda jarabawan shegun mata da Allah ya hadasa da,
ku ne nan ku ka ja masa karayar arziki, dama ance min dukkanin ku babu alkhairi
a tare da shi gwara ma Zahra'u, wallahi ce min aka yi in dai zai rabu da ke da
Zubaida to arzikinsa zai dawo kaca kaca har fin na Ιa, Zahra'u ce kadai matarsa
ta arziki aka ce min, da zai ji ta nawa ma duk ya sallameku in ga inda za ku
koma idan ba kauyen ba, ke Zubaida kin manta kauyen da uwarki da ubanki suke
sai sati sati ake kawo ruwan pampo? Kin manta ko wutar lantarki ba a ja maku
har yau a kauyen ba? Kauyen da muka je na dawo ina ta amai da gudawa watana
daya a asibiti amma har kina da bakin kushe namu kauyen da babu abinda babu? To
wani Ιan iskan ne ma yace Rano kauye ce tukunna? Sannan ke shatu baza ma a kira
garin iyayenki da kauye ba sai dai ace daji, haka nan muka dawo kano maguzawan
mayu suka kamani da kyar aka samo kaina ba don Allah yayi da sauran shan ruwana
a duniya ba da tuni na rasu wallahi" Shi dai Malam Ali yayi tagumi yayi
shiru bai ce komai ba don tun kan Nenne ta kawo wnn shawara dama yake jin gwara
ya koma garinsu don bai san da me Alhaji Musa da Ιan sa za su billo ba kuma,
shi dai bai yarda kotu zata wankesa akan kudaden nan masu yawa ba gani kawai
yake dadin baki su Ajay suke masa, Nenne tace "Yau ga samun waje kai, ita
Zahra'u me yasa bata kushe shawarata ba sai ku masu fararen kafa, ko da yake
ita ta guduwan er ta da ta shiga duniya ma take, mu bar ta taji da wannan
ma" Mama Shatu tace "Wace er ta? Ai wallahi ko rantsuwa nayi bazan yi
kaffara ba Zahra'u tasan inda er ta take, mu dai ne kawai aka rena ma wayo aka
raina mana hankali" Mama Zubaida tace "To ai ba ma sai kin rantse ba
Shatu, kwarai kuwa Zahra'u tasan inda Khaleesat take" Nenne dai sai kallon
Umma da ko kallon kishiyoyin nata bata yi ba take, a hankali Nenne tace
"Lallai biri yayi kama da mutum, na kuma yarda da maganarku don Zahra'u da
na sani da har yanzu tana nan kan darduma sanye da dogon hijabi tana rike da
carbi tana kuka ba dare ba rana duk ta fita hayyacin ta, kawarta Uwar Salame da
makociyarku sha'awa me daddawa su yi ta shigowa suna dannarta su zazzauna kusa
da ita kamar me takaba, amma ina lura da ita yau kusan sati uku kenan tana ta
harkar gabanta kamar babu abinda ya faru, nima dai ko rantsuwa nayi bazan yi
kaffara ba tasan inda Khaleesah take" Malam Ali ya gyara zama yana kallon
Umma cikin lallami yace "Kiyi ma girman Allah Zahra'u ke da er ki ku rufa
min asiri yanda Allah ya rufa maku, duk inda er nan ta tafi kiyi masu waya ta
dawo ta amshi auren mijinta hannu bibbiyu, dama Allah ya riga ya kaddara Abdul
ne mijinta mu din banza ne za mu canza
hakan? don girman Allah ta rufa min asiri, ina cikin tashin hankali har yanxu
wallahi don ban san kuma da me Alhaji Musa da Ιan sa za su dawo min ba, rufin
asirina shi ne na damka masu Khaleesah kawai, in har suka kasheni wallahi banza
kawai za su kashe tunda ba galihu ne da ni ba, tunda aka maida ni furson din
nan nake rashin lafiya me tsanani, yanzu haka maganar da nake yi kirjina kamar
an aza min katuwar dutse, ku yi min rai ke da er ki" Kamar zai yi kuka ya
kare maganar, Nenne na matsar kwallan da babu tace "In wani abu ya same ka
dama da Zahra'u da er ta zan yi kuka wallahi, don su ke kokarin salwantar min
da kai ta karfi da yaji" Umma da hawaye ya cika idonta tace "To wai
ta yaya zan san inda Khaleesah take ni ba waya ba balle ku yi tunanin tana
kirana? Ko kun ga ina zuwa wani waje daga cikin dakina ne?" Mama Zubaida
tace "Na rantse da wanda raina ke hannunsa Zahra'u kinsan inda makirar er
ki take, don haka sai dai ki rena ma wani hankali amma ba mu ba, duk abinda ya
samu mijinmu dama har karshen duniya mun yi ta ja ma ke da 'ya yanki Allah ya
isa kenan, banda samun waje ita Khaleesah har tana da ta cewa da har zata bude
baki tace bazata zauna da Abdul ba? Da me tafi Abdul din banda rufa mata asiri
da yayi zai aureta? Mutumin da ya maida ta fess ya maida ta mutum ya kashe mata
dukiya babu adadi don butulci da samun waje tace ita bata son sa kuma a ina aka
taΙa tafka wannan iskancin? Wallahi ba a samu wanda zai ci ubanta bane shi yasa
ta samu waje da yawa" Umma tace "Tun da har kuke tunanin nasan inda
take kuma baza ku rasa sanin inda take ba ai, kilan ma za ku fi ni sani, don
haka sai ku je ku fito da ita ku kai ta gidan Abdul din" Umma na kai wa
nan ta mike ta shige dakinta, Mama Shatu tayi kasa da murya tace
"Al-qur'an tasan inda take, da bata san inda take ba wallahi da har yau
bata dena koke koke ba kilan har sai tayi rashin lafiya, kuma ni na ma fi
zargin tana wajen kanwarta ne a garin Legas wallahi, in da ba haka ba ai da
tuni mun ga Farida a gidan nan kamar an jefota amma gashi kusan sati uku har
yau shiru Farida bata zo ba" Mama Zubaida tace "Ahaf ai mu ba yara
bane" shi dai Malam Ali sai zazzare ido yake, Nenne tayi kasa da murya
tace "Gaskiya na yarda da maganarku, don nima ina ta mamakin me yasa har
yau farida bata zo ba, ita da ko tari yayarta tayi zata hawo mota ta kamo
hanyar kano, amma ace an rasa Khaleesah yau sati uku shiru bata kamo hanya ba,
ai da alamar tambaya" Malam Ali ya share zufar goshinsa duk da sanyin da
ake shi ma yayi kasa da murya yace "To yanxu meye shawara? Ko ni zan
shirya in tafi Lagos din ne?" Sosai hankalin Umma dake tsaye bakin kofarta
daga cikin daki ya tashi don duk tana jin abinda suke cewa, Mama Zubaida tayi
kasa da murya tace "Ai ban ma yarda da shiga dakin da tayi ba kilan er
uwar zata kira, ko da yake bata da waya, kawai ina ga a gaya ma...." Mama
Shatu ta Ιan tsunguli Mama Zubaida alamar tayi shiru, lkci daya Mama Zubaida
tayi tsit, Nenne ta mike tana kallon Malam Ali tace "Mu je daga gefe mu yi
shawara Ali" Mikewa Malam Ali yayi ya nufi can hanyar fita daga compound
din Nenne na biye da shi, Mama Shatu ta mike tayi ma Mama Zubaida alamar su
shiga ciki, suna shiga daki Mama Shatu tace "Ke ya muna neman maganar
auren nan ya rushe gaba daya ko zai hakura yace a basa Labeebah ko Lamisah amma
kike basu shawaran su je Lagos?" Mama Zubaida tace "Wallahi gaba daya
na sha'afa kinsan kwakwalwar tawa, kuma kece kika kawo maganar Khaleesah, tun
asali ma bai kamata mu ce komai ba gashi yanxu mun karkato da hankalinsu zuwa
Lagos, sai fa Malam ya iya shiryawa ya kama hanyar Lagos wallahi" Mama
Shatu tayi shiru, can tace "Ai ko in yaje lagos din nan shikenan tsarinmu
ya lalace don taso keyarta zai yi su dawo kano ya mika ma Abdul ita, kinga
shikenan mun tashi a tutar babu mun kai ba malamai kudadenmu a banza, tunda duk
mun san Abdul din na sonta kuma hannu bibbiyu zai amsheta su fara rayuwar aure"
Mama Zubaida tace "Toh kuwa ina ga da kaina zan kira Farida ince mata in
har tasan Khaleesah na wajenta to tayi maza maza su bar gidan don Malam zai
kama hanyar lagos tare da Abdul" Mama Shatu tace "A'a bari in shiga
dakin Zahra'u in gaya mata hakan, tunda ga Nenne da Malam can sun kebe bamu san
maganar da suke ba" Bata jira cewar Mama Zubaida ba ta fita zuwa dakin
Umma, Zaune ta tarar da Umma bakin katifarta abun duniya ya isheta gashi babu
waya hannunta, kuma in tace ta fita daga gidan ta amshi waya a makota tasan
dole za a zargeta, kuma daxu da safe suka yi waya da farida ta wayar Mama
Salame take sanar mata jibi za su Nijar da Khaleesat, Mama Shatu na kallon Umma tayi kasa da murya
tace "Zahra'u, ga can Nenne da Malam suna shirya yanda za a tafi legas
wajen Farida gobe da asubar fari, in dai kinsan Khaleesah na wajenta wallahi
kiyi maza ki buga mata waya su bar gidan su tafi wani wajen, a ajiye batun
kishi a gefe abinda baza ka so ma danka ba kar ka so ma Ιan wani, don duk mun
san Abdul ba mutumin kwarai bane, kuma a zamanin nan an dena auren dole, mu ma
ba a mana dole ba don haka baza mu yi ma 'ya yan mu ba" Mama Shatu na kai
wa nan ta juya ta fice daga dakin, Umma ta mike gabanta na faduwa ta Ιan leka
tsakar gidan taga Nenne da Malam Ali tsaye a can lokon tsakar gidan suna magana
kasa kasa.... Jay ya fito daga kitchen hannunsa rike da mug din shayi yana
juyawa a hankali, Step Mom din Ajay ce zaune parlon cikin shiga ta alfarma, a
ranan ta sauka gidan tare da jakadiyarta sun dawo daga kaduna, Jakadiyarta na
dinning area tana yanka mata fruit, Jay ya tsaya dai dai inda yake don bata san
ya fito daga kitchen din ba, da wani kallon tsana kawai yaga take bin Ajay dake
haurawa sama hannunsa rike da laptop dinsa, after few seconds Jay ya ci gaba da
juya shayin hannunsa yana kallonta, tana jin sound din cokali ta juya da sauri
tana Ιan murmushi ta hau canza channel din TV, shi dai Jay ya karasa cikin
parlon bai sake kallonta ba, Jakadiyarta ta taho ta ajiye mata fruit din da ta
gama yankawa cikin ladabi take sanar mata ga kayan marmarin, Cike da isa Aunty
ta dau Apple ta fara ci, ta Ιan kalli Jay ganin sama zai wuce shi ma tace
"Gobe Abbanku zai shigo wani taro" Jay yace "Mun yi waya da
shi" Daga haka shi ma ya wuce sama, ta wani taΙe baki ta bi sa da kallo,
Jakadiyar da ta zube gefenta cikin girmamawa tayi kasa da murya tace
"Ranki shi dade, Allah ya ja zamaninki, daxu na jiyo mana wani labari
Allah ya sa zaki yi maraba da wannan labarin" A takaice Aunty tace
"Labari akan me?" Jakadiyar ta gyara zama tace "Akan Yarima"
Aunty ta ajiye Apple din hannunta ta ba jakadiyar gaba daya attention dinta
tace "Me kika jiyo?"
[6/11, 8:28 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Har mahaifin
Abdul ya gama bambamin da yake yi a parlon Momy kamar zai ari baki bata ce masa
komai ba illa rungume hannu da ta yi tana zaune kan kujera tana girgiza kafa
fuskarta babu fara'a, Meemah dake zaune parlon ita ma dai bata ce komai ba
fuska a murtuke, Alhaji Musa yayi bala'in sa me isarsa sannan ya juya zai bar
parlon a fusace, sai kuma ya sake dawowa yana huci yace "Ina wawan
Abdallan yake? Ina yake yaga abinda rashin tunaninsa da rashin daukan shawarar
sa ya ja min" Momy ta tabe baki ita ma cike da takaici tace "Ai
Alhaji yau kwana uku curr rabonsa ma da gidan gaba daya, kuma ba a samun sa a
waya, ya kashe wayar" Rai bace Alhaji Musa yace "Duk shi ya ja min
wannan bala'i ina zamana, wa yace masa dama ana harkar arziki da talaka? Sam ai
ba a shige ma talaka duk yanda yake kuwa, tun asali zuri'ar da yake son in hada
da wancan barawon mutumi ba wai nayi na'am da hakan bane, kawai bani da yanda
zan yi da Abdallah ne" Momy ta gyara zama zuciyarta na tafarfasa tace
"Atoh dai, har na gaji da nanata wannan sentence din da kayi Alhaji, ai ba
a abun arziki da talaka don tun asali dama a tsiyace ya zo duniya kuma a
tsiyace zai koma, kana zaman zaman ka gashi Abdullah ya ja maka asaran makudan
kudi har da su taran kotu, wai kai da aka zalunta kai ne kuma da biyan tara
saboda rashin adalci, ai Abdul bai kyauta mana bai duba mana ba, ace shi bazai
dau maganata a matsayina na uwarsa ba? Babu yanda banyi discouraging dinsa kan
tsinanniyar yarinyar nan ba na nuna masa ba ajinsa bace yaki saurarata wallahi,
kyanta ne kawai ya rudesa wato kyan Ιan maciji, har tayin er aminiyata nayi
masa amma firr yaron nan yaki, to ga dai abinda ya ja mana" Meemah tace
"Ni duk ba wannan ba Momy, kawai so nake in san wasu 'ya yan shegun ne
suka tsaya mata haka har suka maida case din kotu? Sannan ga auren ma suna
kokarin kotu ta rabasa ta karfi da yaji, kun ga kenan mun tashi a tutar babu,
kuma babu tantama duk yanda aka yi ma su suka boye yarinyar, su waye en iskan
nan ne?" Alhaji Musa na safa da marwa a parlon yace "Don kotu ta kori
karar nan ba shi ke nufin na bar wannan mutumi da ya salwantar min da dukiya
ba, mu zuba mu gani da shi, sai na lahira ya fi sa jin dadi wallahi" Daga
haka ya bar parlon kamar zai tashi sama, Momy ta sauke wani ajiyar zuciyar
takaici tana girgiza kai tace "Abdallah bai duba mana ba wallahi, ya
kaskantar da mu a idon duniya kawai, wai yau talaka ne ya ci nasara a kan mu a
kotu, this is a big slap to us, kuma ko uban menene dalilinsa na dinga kashe
waya ba a samun sa oho? Ni taran da aka ci Alhaji ne ma yafi Ζona min rai
wallahi, ga mari ga tsinka jaka, ki sake kiran wayarsa kiji ko zai shiga"
Meemah tace "Baza fa a samesa a waya ba Momy, mu da ganin Abdallah sai ya
cika burin dake ransa kema ai kin san halinsa, gwara ma ki saka ma ranki salama
mu bi sa da addu'a kawai" Momy ta kalleta tace "Wato kin san inda
yake kenan?" Meemah tace "Ke dai kawai ki bi sa da addu'a Allah ya
basa nasaran abinda ya saka a gaba Momy, amma shegiyar yarinyar nan ai kamar ta
shigo gidan nan ne babu me hana hakan, don baza mu yi biyu babu ba" Momy
ta tabe baki tace "Har ga Allah ni so nayi kawai ya hakura da er
matsiyatan nan Meemah, kada tsautsayi ma yasa a hada iri da ita mu shiga uku,
hada iri da talaka ai ci baya ne Meemah, don ni har cikin raina naki jinin
talaka wallahi balle in hada zuri'a da su" Meemah tace "To ai dama
bama fatan a hada iri da ita Momy, personally bazan ma bar hakan ya faru ba
trust me, kawai ta shigo gidan ta gane Allah daya ne, ke kuma ki fara masa
fafutukar wani auren da wuri wuri" Momy dai tayi shiru, can ta tabe baki
tace "Allah ya sa ya saurareni to" Meemah tace "Haba dai zai
saurareki, da kaina zan masa magana, a samar masa yarinya dai dai class
dinsa" Momy tace "To ai shikenan, yanxu tracing din matsiyaciyar
yarinyar ya sa a masa kenan?" Meemah tace "Ko ma dai menene mu dai mu
zuba ido mu bi sa da addu'a kawai Momy" Mikewa Momy tayi tace "Bari
in je in lallaba babanku, na dade ban ga ransa ya baci irin haka ba, haba ai
abun da bacin rai, wai ace talaka yayi nasara akan ka a kotu bayan kai ne me
gaskiya ai abun da ciwo" Daga haka ta wuce sama, Meemah ta dau wayarta
tayi dailing number da take samun Abdul da shi ta tashi ta shiga dakin dake
parlon. Da asuba ko sallah ba ayi Malam Ali ya fito da er jakar da yake tafiya
da shi bayan ya mulke jikinsa da basilin saboda sanyin da ake, bin dakunan
matan nasa yayi duk ya kwankwasa masu kofa, Mama Zubaida da Mama Shatu suka
fito suna kallonsa da mamaki suka ce "Lafiya Malam?" Mama Zubaida
tace "Ko tafiya kauyen ne ya taso?" Shi dai bai tanka su ba ya dinga
goge takalminsa da yayi Ζura, Umma ce karshen fitowa ita ma ta tsaya tana
kallonsa ta kasa cewa komai don tasan manufarsa, ko baccin kirki bata yi ba
daren jiya tsabar yanda hankalinta ya tashi, Nenne ce ta shigo gidan yafe da
zaninta tana ganin Malam Ali tace "Yauwa ko sallah kar ka jira kayi idan
kaje tashar kayi a can Ali, ga er soyayyiyar nama da gurasa na kullo maka ka ci
a hanya" Mama Shatu tace "Tafiya zai yi ne Nenne?" Nenne tace
"Babu ruwan ku, ku dai ku yi masa fatan Allah ya kiyaye hanya" Malam
Ali ya amshi kullin nama da gurasan da Nenne ke mika masa, yana kallon matan
nasa yace "Toh sai Allah yayi min dawowa" Mama Shatu tace "To ai
shikenan, Allah Ubangiji ya tsare Malam" Mama Zubaida ma tace "Allah
ya tsare duk da muna da hakkin ka sanar mana inda zaka je da asuban fari
Malam" Nenne tace "Bazai sanar ba Zubaida, uban me sanin inda za shi
zai kara maki?" Mama Zubaida ta juya ta koma daki, Mama Shatu ma ta tabe
baki ta koma dakinta, Nenne ta kalli Umma tace "Wato ke ce isasshiyar da
bazata yi masa Allah ya kiyaye ba ko Zahra'u" Shi dai Malam Ali tuni har
ya fice daga gidan, Nenne na nuna Umma tace "Mugun abun ku zai kare maku
da ke da er ki wallahi, babu wanda ya isa ya salwantar min da Ιa na lokacinsa
bai yi ba" Daga haka ta bi bayan Malam Ali da sauri zata rakasa bakin titi
ya samu adaidaita sahun da zai kai sa tasha. That same day bayan an idar da
sallahn asuba Jay ya shigo parlorn Mai martaba da sleepy face ta dalilin kiran
da yayi masa, ganin irin zaman da Abba yayi kamar yana fadarsa ya gane serious
issue Abban zai yi discussing da su kenan, ya kalli Ajay dake parlon zaune shi
ma alamar kiran sa Abban yayi, Aunty ma na zaune parlon, Jay ya sauke kansa ya
karasa kusa da Ajay ya zauna kasan lallausan carpet din parlon, dabi'ar Abba ne
sai ya iya minti biyar zuwa goma kamar me nazari kafin ya fara magana in ya
tara ku, Jay ya sunkuyar da kansa ya lumshe ido, Ajay ya Ιan kallesa sanin sai
ya iya bacci a haka, ai ko yaga baccin yake, Ajay ya Ιan tunkudesa da elbow
dinsa, Jay ya bude ido da sauri yana gyara zama, shi dai Abba kallonsu kawai
yake, At last Abba yayi gyaran murya cikin nutsuwa yace "First of.... Ina
son sanin zaman me ku ke har yanxu a garin nan baku karasa gida ba?" Duk
suka yi shiru babu wanda yace komai kansu a kasa, Calmy Abba yace "Ohk
take ur time, amma kuyi kokari ku je gida kafin hutun ku ya kare, Secondly....
maganar da nayi da ku a Maryland naji babu wanda yace min komai a kai har
yanxu, ga lokacin da na baku ya cika, nayi maku uxurin mantuwa shi yasa nake
tunatar da ku yanxu..." Nan ma duk suka yi shiru babu wanda yace komai,
shi ma Abban yayi shiru yana kallonsu yana jiran amsa a duk sanda suka shirya,
sun san shirun da Mai martaba yayi amsarsu yake kira ko da zai dau 10min ko fin
haka ma kafin su basa amsan he won't mind zai jira su patiently, sanin halin
Abban nasa yasa Ajay ya daga kai, Softly yace "Ayi hakuri ranka shi dade
ba mantawa muka yi ba, in sha Allah we are working on that very soon" Mai
martaba yace "Is that so?" Ajay ya sauke kansa don kalman Abba na
nufin bai gamsu da abinda yace ba kenan, Shi dai Jay yaki dago kai, a hankali
Ajay yace "A gafarce mu a Ιan kara mana lokaci Abba..." Aunty da har
ta fahimci maganar da ake ta Ιan yi gyaran murya ta nemi permission din magana
gun Mai martaba, ya gyada mata kai alamar ta fadi abinda zata fada, cikin
nutsuwa tace "In na fahimci maganar da ake ranka shi dade, magana ce akan
su fito da matan aure duba da yanda shekarunsu ke gaba ba baya ba, wannan
magana kuma ba sabuwar magana bace don an fi shekara 3 ana yin ta amma babu
wani progress, a takaice basa daukar maganar da muhimmanci, to amma dai ina ga
ka Ιan sha'afa ne ur Highness, don shi Jawwad ai akwai maganar sa da Hadeeyah a
kasa duk da ba wai maganar tayi karfi bane kuma wannan hadi, hadi ne me kyau da
zai kara karfafa zumunci don mahaifiyar Hadeeyah jininka ce kuma ita ta kawo
wannan shawara duk da Fulani wato mahaifiyar Jawwad uwar dakinta ce tun asali,
shi kuma Junaid a yanda na lura da shi zai fi maraba da zabin ka garesa duba da
nature dinsa da rashin choice dinsa, don haka shi Jawwad a tsaida maganar sa da
Hadeeyah kawai ina ga hakan zai fi, shi kuma Yarima i think we should get him a
princess from neighbouring states, ko ni zan iya jagorantar hakan don arranged
marriage zai fi suiting dinsa duba da nature dinsa, kuma ina son a bar komai a
hannuna ranka shi dade..." Ajay ya daga kai ya kalleta zai yi magana mai
martaba ya dakatar da shi, Ajay ya sauke kansa, Speaking Calmly Mai martaba
dake kallon Ajay da Jay yace "Za ku iya tafiya, Allah yayi maku
albarka" Sai a sannan Jawwad ya dago kai ya kalli Aunty dake Ιan murmushi
ganin Mai martaba yayi na'am da shawaranta, tuni Ajay har yayi disappearing
daga parlorn fuska a murtuke, Jay ya mike shi ma ya bi bayan Ajay yana tafiya a
hankali, bai taΙa sanin baya son Hadeeyah da aure ba sai yau da Aunty ke bada
shawaran a tsaida ranan aurensu da ita, yasan kuma duk abinda Aunty tace kamar
Abba ya aikata hakan ya gama ne, kawai yaji hankalinsa yayi mugun tashi yaji
wani zufa na keto masa, dakinsa ya shige ya kulle da makulli ya jingina da
kofar ya lumshe ido zuciyarsa na bugawa, Ajay na shiga dakinsa shi ma ya kulle
da makulli ya zauna gefen gado ya dafe kansa da hannu biyu, this is not the
first time da Aunty ke kasalanda akan duk abinda ya shafesa gashi Abbansa baya
basa listening ears ko me Aunty tace masa kawai haka za ayi abun nan komin
munin abun, at this point he felt he is of no importance to his father, he felt
dejected, and it's been like this for so many years, he have no one to stand
for him, a hankali ya juya yana kallon wayarsa dake vibrate, Number Aunty
Farida ya gani a gaban screen din wayar, ya kalli agogo yaga karfe shidda da
minti biyar na safe, request din Khaleesat na jiya da ta kirasa ya tuna, hakan
yasa har kiran ya katse bai daga ba knowing she might be the one calling, kiran
ya sake shigowa ya kalli screen din nan ma bai daga ba har ya katse, sau hudu
kiran na shigowa continuously, hakan yasa ya maida attention dinsa kan wayar ya
Ιan yi jim with different thought running his mind, ganin kiran ya katse an
sake kira making it the 5th time of calling yasa ya dau wayar ya daga ya kai
kunne yayi shiru waiting to hear who is on the line, a hankali ya mike jin
abinda Aunty Farida ke ce masa ta wayar, bai san sanda ya zame wayar daga
kunnensa ba rate din heartbeat dinsa na karuwa, da sauri ya nufi kofarsa ya
bude ya fice daga dakin ya murda kofar dakin Jay yaji a kulle, knocking ya
dinga yi non stop kafin Jay ya bude kofar da mamaki yana kallonsa yace
"What is it?" Ajay ya shiga dakin yana shafa gashin kansa da wani
expression yace "He tracked her to Lagos" Still Jay yayi a inda yake
tsaye ko kwakkwaran motsi baya yi yana kallon Ajay, Ajay ya ja numfashi sannan
ya zauna kan kujeran dakin ya lumshe idanuwansa ya jinginar da kansa jikin
kujeran trying to calm himself, Jay was speechless and shock at the same time,
da kyar ya ja kafa ya zauna gefen gadonsa ya dafe kansa da yaji yayi masa
nauyi, kamar an tsikare Ajay ya mike yace "Book us ticket to Lagos"
Daga haka ya fice daga dakin.
[6/12, 8:02 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Aunty Farida
ta share hawayen da yaki tsaya mata tana kallonsu Ajay da kyar tace
"Wallahi ban san ko har su nawa bane a motar, ban ma san ya motar take ba
tunda ina cikin gida sanda abun ya faru, yaran makota dake diban ruwa a bakin
rijiyar tare da ita ne suke cewa kawai suna diban ruwa sai ga motar ta shigo
street din, wasu mutane suka sauka a motar suka ja ta zuwa cikin motar suka
tafi da ita, a sannan an idar da sallahn subahi kenan kun ga gari bai waye ba
ai" Ajay was speechless, bai taΙa zama confuse haka a rayuwar sa ba don ya
ma rasa abun cewa, likewise Jay dake jingine jikin mota tun da suka iso unguwan
dama shi bai ce komai ba, Ajay ya daga kai after some seconds ya kalli Aunty
Farida a hankali yace "Amma yana da number ki ne Aunty?" Aunty Farida
tace "Ba shi da wannan number tawa gaskiya sai tsohon layi na, kwanaki
Maman Khaleesat tayi rashin lafiya sai na tafi kano dubata to a hanya na yar da
wayata, da na zo kano sai na siya sabon layi kafin inyi welcome back din tsohon
layin, to har yanxu ban yi welcome back din ba" Ajay yayi shiru yana
nazari, Aunty Farida na hawaye tace "Tsautsayi yasa ta fita deban ruwan
yau, amma tunda ta xo wallahi ni ke diban ruwana bana barin ta dibar min tunda
har yanxu gata nan ne dai bata dawo dai dai ba, wani lkcn ma da daddare idan na
dawo kasuwa nake yi tunda ana wahalar ruwa a season din nan don yawanci
rijiyoyi kafewa suke yi sai ana bari ruwan na taruwa sannan a diba, gashi ba a
samun wuta balle a samu ruwan pampo, a jiyan nayi girki me yawa ne na wani biki
duk sai na gaji ban deba ruwan da daddare ba, da na tashi kuma sai nake jin
zazzabi, kun ji dalilin fitarta ta debo mana ruwa kenan" Ajay ya jingina
da motarsa ya lumshe ido ya bude, gaba daya Ζansa ya gama kullewa, bai yi zaton
Abdul ya wuce yanda yayi zatonsa ba, the guy is really something else ko wani
salon tactics na mugunta ya san sa gashi har yau yaki kunna wayarsa balle a san
inda yake, ko by mistake baya kunna layin, shi dai Jay dama bai taΙa
underrating Abdul ba dai dai da rana daya duba da irin actions din da ya dinga
portraying, kawai dai tracing din Halysaah har zuwa Lagos is the least thing da
yayi zaton Abdul zai yi, tunda bashi da access da Aunt dinta, but like
seriously how did he even find his way, bayan bashi da active line din Aunty
Farida sannan bai san unguwan da take ba, ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya
yana tunanin ta inda za su fara billo ma wannan lamari, tunda dai babu ta yanda
za su ce yayi kidnapping Halysaah da ke a matsayin matarsa ta sunna. Khaleesat
na zaune at the far end of the large room ta hade kanta da gwiwa, zuwa sannan
ta hakura da kukan da take don ba ma ta da strength din kukan amma tana jin
zuciyarta na mata zafi ga wani azababben ciwon kan da take ji da kishin ruwa da
ya dameta, tafi awa sha biyu zaune a dakin ba ci ba sha, don tunda aka shigo da
ita har zuwa sannan babu wanda ya sake zuwa dakin, infact bata ji motsin kowa a
gidan ba alamar ita kadai ce a ciki, bandakin dake cikin dakin take shiga tayi
alwala ta fito tayi sallah duk da ba sanin lokaci tayi ba kawai tana amfani da
instinct dinta ne, at this point in time tasan bata da wani sauran gata sai
wajen Allah, domin kuwa tasan Abdallah ne kawai zai sa a zo ayi mata irin
wannan daukan, wasu hawaye masu zafi suka zubo idonta tana tausayin rayuwarta,
all she could remember vividly was that tana bakin rijiyan dake kusa da gidansu
Aunty Farida tana diban ruwa wasu mutane biyu suka zo a mota, lokaci daya kuma
suka yi leading dinta zuwa motar tasu, at first turje masu tayi ta fara kokarin
raising alarm tana ihu, yaran dake bakin rijiyan duk suka gudu suka shige
gidajensu, tana kururuwa daya mutumin ya rufe fuskarta da wani Handkerchief da
sauri, taji ta shaΖi wani abu kamar dust, lkci daya kuma ya cire handkerchief
din a fuskarta, daga nan kuma ko kokarin ihun bata sake yi ba cause she became
weak, ita dai tasan all through the ride she was conscious but not fully, gashi
ta kasa tabuka komai don duk jikinta ya mutu, kanta yayi mata nauyi idonta suka
dinga juya mata.... Da sauri Khaleesat ta dago kanta ta mike tsaye jin ana
ΖoΖarin bude kofar dakin ta waje da makulli, gabanta ya dinga bugawa da karfi
idonta na kan kofar har ya bude ya shigo, she wasn't expecting anyone but him
dama, ta sauke kanta bayan sun hada ido, wasu sabbin hawayen suka fara zuba
idonta, muryarsa taji ya daki kunnenta cike da isa da gadara yace "Har
yanxu Body guards din naki basu biyo bayanki bane? Ai yaci ace sun iso zuwa
yanxu don naga It's almost 12 hours now, how comes basu zo cecen ki ba duk
capacity din su" Sai a sannan Khaleesat ta daga kai ta kallesa cikin rawar
murya tace "Ka ji tsoron Allah...." Kasa ci gaba tayi ta fashe da
matsanancin kukan takaici, shi dai yana tsaye yana kallonta da wani murmushin
mugunta kwance fuskarsa, ta dago kai da sauri jin yana takowa har zuwa inda
take tsaye, mannewa tayi da bango tana jin kamar bangon ya tsage kawai ta shige
gabanta na bugawa da karfi, sai da ya zo dab da ita cikin kwantar da murya yace
"Me kika ce?" Ta girgiza masa kai da kyar gabanta na ci gaba da
faduwa muryarta na rawa tace "Kaji tsoron Allah Ya Abdul, kaji
tsoron...." Bata rufe baki ba taji saukan lafiyayyen mari a fuskarta wanda
sai da taga taurari, ta dafe kuncinta tana kallonsa babu ko kiftawa, cikin
husky voice dinsa yace "You still have the guts to repeat what u just said
saboda baki da kunya ko? Ni zaki gaya ma in ji tsoron Allah? To tsoronki zan ji
ko tsoron uban ki dake Mariri idan ban ji tsoron Allah ba?" Da kyar
Khaleesat ta dake tace "Ka zageni amma kar ka sake zagar min uba"
Still bata rufe baki ba ya sake sauke mata wani wawan marin a other side of her
face, this time around sai da dakin ya juya mata don ba marin wasa yayi mata
ba, ya fixgota yana mata wani irin kallon da ya gigitata don tuni idonsa yayi
jajur yana huci yace "Ina magana kina mayar min how dare you poor wretched
girl?" Ta fashe da matsanancin kuka tana jin dama Allah ya dau ranta kawai
ta huta a wannan lokacin, zata durkusa kasa ya hadeta da bango yace "Yau
ina body Guards din naki dake goya maki baya kina min iskanci? Tell me where they
are today? Da aurena a kanki kike hulda da wasu banzayen gardawa saboda ke
jahila ce warce bata san me take ba" Tana kuka sosai bata san sanda tace
"To wai ana aure dole ne dama Abdul? Nace bana son auren, bana son ka,
gwara kawai ka kasheni duk mu huta" Da karfi ya bugata da bango har sai da
taji numfashinta ya dauke na few seconds, yana mata wani mugun kallo yana huci
yace "Dama ke baki san aurena wajibi ne a gare ki ba ko kina so ko ba kya
so? Dama shi ubanki bai gaya maki hakan ba ko mantawa kika yi saboda kin fara
bin maza? Wallahil Azeem kin ji rantsuwar musulmi ko? Duk ranan da kika sake
yunkurin guduwa ko kuma yin wani silly act to rayukan twin siblings din ki za
su zama fansar aurena idan kika kuskura kika min jakanci, ko kina so ko baki so
lallai dole ki zauna da ni ko kuma in salwantar da ran kanninki i am promising
you this Billahil Azeem, kuma babu abinda zai faru don tamkar na kashe banza ne
daga ke har iyayenki babu abinda za ku yi, su kansu Body guards din naki ba
kyalesu nayi ba don sai na dau revenge din intruding da suka yi a sabgata, i
will teach them a lesson kina ji kuma kina gani" Khaleesat ta kasa cewa
komai don sama sama kawai take jin numfashinta kalmansa na cewa zai salwantar
mata da siblings dinta ya sa jikinta ya fara rawa, ya juya cike da isa ya tafi
ya bude closet din dakin wanda duk kananun shegun kaya ne yace "All this
are your wears, in kin yi sallah kin shirya ki zo ki sameni a dakina which is 3
rooms away from this, ina jiranki at exactly 7pm and this is just 6:30pm"
Yana kai wa nan ya fice daga dakin yana rike da key din dakin, a hankali
Khaleesat ta sulale kasa tana sauke numfashi tana jin wani abu ya tsaya mata
cak a zuciya, gashi ba ta ma da strength din da zata yi kuka sosai ko zata ji
relieve don tun jiya rabonta da abinci, she was just weak and helpless, ga
idonta da taji ya fara ciwo saboda marin da yayi mata don dama ba warkewa idon
yayi gaba daya ba lkci lkci tana jin yana damunta, tsoro da fargaban kada ya
sake dawowa dakin yayi mata fiye da abinda yayi mata yasa Khaleesat tayi karfin
halin mikewa da Ιan sauran strength din ta da ya rage tana tafiya da kyar ta
shiga bandakin dake cikin dakin ta tara ruwan pampo tana sha ko zata ji saukin
abinda take ji a zuciyarta, bayan ta sha ruwan ta dinga kallon fuskarta da yayi
ja ta madubi, a hankali ta zame kasan bandakin ta jingina da tile din bangon
hawaye masu zafi na zarya a fuskarta, tafi minti goma a haka lokaci daya ta
yunkura ta mike bayan ta tuna time din da ya bata kar ya sake dawowa, she wish
akwai makulli a jikin kofar bandakin don da kulle bathroom din kawai zata yi in
ma mutuwa ne tayi a haka don yafi mata kasancewa da Abdul, cikin rashin kuzari
ta cire hijab dinta da kayan baccin dake jikinta ta fara wanka da shower gel
din dake bandakin, komai na bukatar mace akwai a banΙakin everything is just
set, after a while ta gama wankan ta wanke bakinta ta fito sanye da dogon hijab
dinta with different thoughts running her mind, tunda ya bar kofar dakin a bude
ko dai ta samu ta lallaba ta fita and find a way for her self, duk da tasan
Abdul will never be that stupid da zai bar kofa a bude har ta samu ta fita,
infact in ma ta fita daga building din gidan tasan definitely akwai mai gadi a
bakin gate kuma babu ta yanda zai bar ta ta fita, kilan ma Abdul din ya sanar
masa in zata fita kar ya bude mata gate, but still ita dai burinta ta samu ko
daki me makulli ne ta shige ciki ta kulle kofar sannan ta bar key din a jiki
yanda ko spare key idan aka saka za a bude kofar bazai budu ba sbda key din da
ta bari a jiki, da wannan tunanin ta nufi kofa gabanta na faduwa ta bude kofar
dakin a hankali zata fita suka kusa cin karo da shi, rikicewa tayi ta juya da
sauri zata bar bakin kofar ya fixgota, bakinta na rawa tace "I am very
thirsty" fuskarsa babu wani rahama yace "Follow me" Bata iya ta
masa musu ba tunda taga kiris yake jira ya mareta a ko da yaushe, at every
slight opportunity marin ta kawai yake, tana biye da shi zuciyarta na bugawa
suka shigo Main parlor din gidan, karshen haduwa gidan ya hadu amma ita ko lura
da hakan bata yi ba don ta kanta kawai take, tana biye da shi ya kai ta har
kitchen din gidan, ya juya ya kalleta a takaice yace "Gashi nan ki dafa
abinda zaki ci don bani da time din fita in siya maki komai tunda kina da
hannun girki, after that ki dafa min lipton ki kai min dakin da nace" Ita
dai Khaleesat na rakube jikin kofar kitchen din gaba daya hankalinta baya
jikinta, taga yayi ficewarsa ya bar mata kitchen din, ta bi sa da kallo har ta
dena ganinsa, ta zame kasa ta hade kanta da gwiwa cikin rawan murya tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace" ta kusa
minti biyar a haka kafin ta yunkura ta mike tana goge hawayen da yaki tsaya
mata, tana tafiya a hankali ta nufi kofar parlon ta murda taji a kulle kuma
babu makullin a jiki she wasn't surprise don tasan dole zai kulle gidan, haka
duk sai da ta bi dakunan dake gidan ta murda su taji a kulle kuma babu
makullansu a jiki, a sanyaye hawaye na bin fuskarta ta koma kitchen din, duk da
rabonta da abinci tun jiya amma ko yunwan bata ji tsabar tashin hankali, kawai
jikinta ne yayi weak taji strength dinta duk ya kare, wnn yasa ta Ιan hada
shayi kadan a cup zata sha, shi ma dai ta kasa sha don bata da appetite, haka
nan ta zubar ta dau black tea din da yace ta dafa masa ta fito daga kitchen
din, dai dai san da ya shigo parlon, sunkuyar da kai tayi rate din heartbeat
dinta na karuwa cause he is just wearing short and singlet, cike da karfin hali
tace "Ga tea din" Babu yabo babu fallasa taji yace "A nan nace
ki bani tea?" Ita dai bata ce komai ba amma kana ganinta kasan a mugun
tsorace take, tana hade hanya ta nufi inda yace ta kai masa shayin yana biye da
ita a baya, da ace tashin hankali da fargaba na kashe mutum ya ci ace ya kashe
Khaleesat a wnn moment din, a bakin kofar dakin ta tsaya cikin rawan murya tace
"Ga tea din" Wani tsawan da ya kidimata yayi mata don bata ma san
sanda ta shige dakin ba ta je ta ajiye masa Mug din tea din a kasa tana waige
waige, ya shigo dakin ya tura kofar fuska a daure yace "Cire Hijab din
nan, kuma yau ya zama first and the very last day da zaki min yawo da Hijab a
gida" Ta durkusa kasa ta fashe masa da kukan tashin hankali tana kallonsa,
ya mata tsawa yace "Are you daft?" Cikin kuka tace "Wallahi
sallah nake son inyi ne kayi hakuri" Darduma ya nuna mata a takaice yace
"Je kiyi" Jiki na rawa ta mike ta tafi kan darduman ta fara sallah
jikinta na rawa, tayi raka'a ya fi sha biyar ita kanta bata sani ba, kawai daga
bayanta taji ya fixge hijab din, tun bai karasa cirewa ba ta fara kokuwa da shi
ta rike hijab din gam tana kiran Ummanta cikin rikicewa, amma da yayi mata wani
riko da hannu daya sai da ta gane Allah daya ne, don ko kwakkwaran motsi kasawa
tayi, tana ji tana gani ya fixge hijab din ya jefar da ita kan gado rokonsa ta
dinga yi da duk kalman da ya fito bakinta tana cewa "Ina rokon ka da
girman Allah kayi hakuri Yaya Abdul, don Allah ka min rai kayi hakuri, in kana
yi ma darajan iyayenka kayi hakuri, wallahi ban gama sallan da nake
ba...." Ya gama kare mata kallo at the same time yana surveying every bit
of her beautiful and breathe taking body, komai yayi masa yanda ya kamata, ashe
asalin kyanta na boye all this while bai sani ba, yayi tarayya da mata iri iri
amma bai taΙa ganin mace that is so beautiful while naked kamar ta ba, iya
haskenta kadai ya isa ya rikita mutum, tuni idanuwansa suka sauya launi ya cire
singlet dinsa yana kallonta kasa kasa yace "In ma kika yi taurin kai kece
a wahale don that isn't stopping me in anyway Baby gal, just relax and i won't
be rough" Kara gigicewa Khaleesat tayi tana rokonsa at the same time tana
kokarin sauka daga kan gadon ya fixgota ya mayar da ita saman gadon yana
kallonta cikin husky voice dinsa yace "Do not allow me give you a dirty
slap...." Bata ma san me yake cewa ba still zata sake sauka taji ya
danneta kan gadon, roughly ya fara exploring dinta kamar ya samu er hannu....
[6/13, 9:19 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Ko minti uku
Abdul bai yi da fara taΙa ta ba Khaleesat taga ya koma gefe lkci daya, da sauri
ta mike tana komawa baya har sannan bata dena kukan da take tana basa hakuri ba
cikin rikicewa, after some seconds ya juya ya kalleta da rinannun idonsa, suna
hada ido ta kara rikicewa muryarta na rawa cikin kuka take cewa "Don
girman Allah kayi hakuri, i am begging you please kayi hakuri" Ya jefa
mata wani kallo ya mike kamar zai tashi sama ya nufi kofa ya fice daga dakin,
ganin hakan tayi kamar a mafarki ta kasa ko kwakkwaran motsi, kamar ance ta
sauke kanta taga jinin da ya Ιata farin zanin gadon da take kai, ta dinga
komawa baya a hankali tana kallon jinin babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa at
the same time, and she realize daga jikinta yake fita, lokaci daya ta tuna
rabonta da period tun a Maryland almost a month and some days, from nowhere
taji relieve ya zo mata, ta jingina da jikin gadon hawaye masu zafi na sauka
idonta, tafi minti biyar a hakan ganin zata ci gaba da soiling zanin gadon ta
sauka ta dau hijab dinta ta rungume, har sannan jikinta bai daina rawa ba, tana
ta tsaye a dakin tana tunanin yanda zata yi, ta kalli kafarta jin period din
yana gangaro mata, ajiye hijab dinta tayi ta shiga bandakin da ke cikin dakin,
after few minutes ta fito ta dau hijab dinta ta saka, tana kallon zanin gadon
da ya baci ta fara ΖoΖarin cirewa a hankali har ta cire gaba daya, bude kofar
dakin taji anyi ta mike tsaye da sauri zuciyarta na bugawa tana kallonsa, ya
wani harareta yace "What are you using that for?" Bakinta na rawa
tace "A'a wankesa zan yi ne" Yace "Ajiye bana so, zo ki fitar
min a daki" Ta sunkuyar da kanta babu musu ta ajiye zanin gadon a gefen
gado ta nufi kofa a tsorace kamar munafuka, amma ta kasa bin gefensa ta fita
daga dakin saboda fargaba, gashi he is blocking the way, ta fi 30 seconds tsaye
zuciyarta na bugawa ta kasa fita, shi dai kallonta kawai yake babu yabo babu
fallasa, da kyar tace "Zan wuce" Ganin kallon da yake mata bata sake
cewa komai ba haka nan ta raΙa ta gefensa ta fita daga dakin, kallon inda ta
tsaya yake don nan din ma dai sai da tayi staining dinsa da jini, ita dai tuni
har ta shige dakin da aka fara ajiyeta ta tafi bandaki da sauri tana jin
maranta na kullewa, ita da ko ciwon mara bata yi sai dai wani lkcn tayi ciwon
baya ko kafafuwanta su rike shi ma kawai na 'yan awanni ne, ta samu dai ta
wanke jikinta ta fito tana dukawa sbda ciwon da take ji a mara, a haka ta bude
closet din da ya nuna mata tana duba ko zata ga pad, amma taga babu alamarsa, ta
fara tunanin yanda zata yi gashi tana jin alamar saukan period din nata a
jikinta, ita ko da kyalle ne idan ta samu zata iya manage da shi, amma duk dube
dubenta bata ga alamar akwai kyalle ko dankwali a closet din ba, duk kananun
kaya ne, she was so confuse and in pain at the same time, ta rasa yanda zata
yi, sai da tayi sahu ya fi a kirga zuwa bandaki ta wanke jikinta ta sake
fitowa, kuma a haka ba heavy flow take ba a ranan farko, ko zama ta kasa yi
ciwon mara ya addabeta, hawaye ya fara sauka idonta ta karasa kusa da gadon
dakin ta durkusa ta daura kanta saman gadon ta lumshe ido trying to endure the
pain she is feeling, tafi 20 mins a haka taji budewar kofar dakin, da sauri ta
dago kanta daga gefen gadon har sannan tana duke, ta kallesa gabanta na faduwa,
ya shigo dakin ya ajiye ledan hannunsa yana mata kallon sama har kasa a takaice
yace "Me ye ma'anar hakan?" Muryarta na rawa tace "I am having
cramps" Yace "Yaushe kika fara cramps? Is this also among ur
lies?" Ta sunkuyar da kanta wasu sabbin hawayen na sauka idonta, yace
"Bazan sake fita gidan nan da daddaren nan ba saboda ke, after all mate
din ki ne ke enduring labor pain" Ita dai bata ce masa komai ba har ya
fita daga dakin, sai a sannan ta dago kanta with tears rolling down her face,
ta kalli ledan da ya ajiye, rarrafawa tayi zuwa gun ledan ta bude taga Sanitary
pad ne, daya ledan kuma abinci ne da ya siyo mata a eatry da bottle water, ta
daure ta mike tsaye da kyar bayan ta cire pad daya ta bude closet ta dau sabon
underwear dake ciki ta tafi bandaki, bayan ta gyara jikinta ta wanke hijab
dinta da yayi staining a bandakin sannan ta fito, rigan bacci wanda ya Ιan fi
sauran mutunci ta dauka ta saka, ya saukar mata har kusa da gwiwa, kasa cin
abincin da ya siyo mata tayi, haka nan ta bude ruwan goran ta sha sannan ta dau
pillow ta ajiye a kasan dakin ta dau duvet din saman gado ta kwanta tana jin
ciwon cikinta na tsananta, ita rabonta da ciwon mara tun ranan farko da ta fara
period, haka nan hawaye yayi ta zuba idonta, har ta samu bacci ya dauketa taji
budewar kofa, taki bude idonta tayi lamo a inda take bugun zuciyarta na
tsananta, ya zagayo har inda take ya duka gabanta, hannu ya kai forehead dinta
hakan yasa ta bude ido da sauri, magani ya mika mata da ruwa a hannunsa ta
sauke idonta sannan ta daure ta mike zaune ta amshi maganin da ruwan hannunsa
ta sha, ajiye sauran ruwan tayi a gefenta har sannan ta kasa kallon idonsa,
taji yace "Meye da gadon da baki hau ba?" Kai kawai ta girgiza masa
yace "Get on the bed now" Tashi tayi ta koma gefen gadon ta zauna,
kana ganinta kasan a tsorace take, ya dau pillow da duvet din ya ajiye mata
saman gadon, kwanciya tayi ta lulluba da duvet din ta kulle idonta, tana ji ya
fita ya kullo mata dakin, ta bude idonta da sauri taga ya kashe mata wutan
dakin, hawaye taji na gangarowa ta gefen idonta, gradually taji ciwon maran ya
fara subsiding after almost an hour of taking the drug he gave her, daga nan
kuma bata san sanda bacci me nauyi ya dauketa ba, wajen karfe ukun asuba yunwa
ta farkar da ita, ta mike zaune tana bin dakin da kallo har wani rawa jikinta
yake saboda yunwa don rabonta da abinci tun shekaranjiya ga kuma maganin da ta
sha babu komai a cikinta, zamowa tayi daga kan gadon tana laluba ledan abincin
da ya kawo mata taga ya dauke, rasa yanda zata yi tayi, tana ta zaune a haka
kawai taji ya bude kofar dakin hannunsa rike da wayarsa da ya kunna fitila,
shigowansa na uku kenan zuwa dakin amma duk bata sani ba tana bacci, haskata
yayi da wayarsa ya karaso cikin dakin ya kunna switch din fitila, ita dai ta
sunkuyar da kanta kamar munafuka tana jin zuciyarta na throbbing, yace "Me
kike yi a nan?" Sai a sannan ta daga kai da kyar ta marairaice amma bata
ce komai ba, ya daure fuska yace "Nace me kike yi a nan?" Da kyar
tace "I am hungry" Yace "Me yasa baki ci abincin da na kawo maki
jiya ba?" A hankali tace "Na kasa ci" Juyawa yayi ya fita daga
dakin, ta lallaba ta koma saman gadon ta kwanta tayi lamo, after almost 10 mins
sai gashi ya dawo dakin da abincin bayan yayi microwaving din mata, nan kan
bedside drawer ya ajiye mata abincin da ruwan gora, bata jira yace mata komai
ba ta mike zaune tana sunkuyar da kai kamar mara gaskiya ta kai hannu ta dau
abincin, shi dai yana tsaye yana kallonta, a hankali ta fara cin abincin har
sai da ta ci rabi sannan ta kallesa cike da karfin hali tace "Na
koshi" Yace "Cinye sa" Bata masa musu ba ta ci gaba da cin
abinci har sai da ta cinye, amma fa da kyar ta dinga turawa, ta ajiye plate din
a saman beside drawer, juyawa yayi ya fice bayan ya kashe wutan dakin,
Khaleesat ta koma ta kwanta tayi lamo kan pillow, ta ma rasa wani tunani zata
yi at this point, ta goge hawayen da taji yana gangaro mata, ba ita ta koma
bacci ba sai da aka yi sallan asuba. Wajen karfe bakwai na safe ta fito daga
wanka daure da towel tana tafiya a hankali ta bude closet din dakin tana
tunanin abinda zata saka, kana kallon fuskarta kasan tana cikin damuwa me
tsanani, fargabanta yanxu idan ta gama period ya kenan? Ta ina zata fara nema
ma kanta solution yanxu, what next? ta fashe da kuka a hankali tana jin
kirjinta na mata zafi, ta jingina da closet din tayi kukanta me isanta tana
tausayin rayuwarta, daga karshe ta goge hawayenta a sanyaye ta dau wata riga
wanda har kasa ne amma it's transparent, ajiyewa tayi gefen gado ta cire hair
net din dake kanta tun shekaranjiya, tana tafiya a hankali ta karasa gaban
madubin dakin, turarurruka iri iri ne da mayuka, da man kai, ta dau turaren
jiki kadan ta shafa sannan ta shafa ma kanta man gashi don tana barin sa ya
kara kwana daya a haka bata shafa mai ba duk tangling zai yi barin dama
cukuikuyesa kawai tayi cikin Hair net din Aunty Farida, ita ma Aunty Farida
haka gashinta yake, infact dukkansu har Umma da su Islam duk texture din
gashinsu daya, tana cikin shafa ma gashinta oil aka bude kofar dakin, still
tayi a inda take gabanta ya fara faduwa, taki yarda ta kalli direction dinsa,
da kyar ta ajiye oil din hannunta ta dau Hair net zata mayar da gashinta ciki,
taga ya amshe net din a hannunta ya juyo da ita yana kallonta, ta sunkuyar da
kanta kirjinta na heaving shi dai kallonta kawai yake, short ne kadai jikinsa
shi ma da alamar he just took his bath, ya jawota jikinsa ya daura goshinsa
saman gashinta at the same time yana shafa dogon baΖin gashinta a hankalin,
Khaleesat ta runtse ido zuciyarta na bugawa, murya can kasa taji yace "Why
did u change ur mind abou me? It's all my fault right?" Jin bata ce komai
ba ya dago kanta yana kallonta, kawai jin bakinsa tayi a nata bayan ya lumshe
idanuwansa, tsoron turje masa take yi don bata san me zai biyo baya ba idan
tayi hakan, jikinta ya dinga rawa kamar me zazzabi hawaye na sauka idonta tana
girgiza masa kai amma ta kasa cewa komai kar ya mareta kamar yanda ya saba, a
haka ya ja ta zuwa saman gadon dakin yana sarrafata, he made sure he romanced
her deeply to the extent that sai da ya birkice mata kamar ba shi ba, daga
karshe kuma ya kyaleta kar ya kasa controlling kansa gashi tana period, amma fa
sosai ya iya kai zuciyarsa nesa kafin ya kyaleta ya koma can edge din gadon
yayi rub da ciki tare da lumshe idonsa, everything about Khaleesat is just perfect
for a Man, laushin jikinta kadai ya isa ya kara gigita mutum, Khaleesat ta koma
daya side din gadon a hankali take kukan takaici faduwar gabanta ya tsananta,
juyawa yayi ya kalleta after some minutes yaga yanda dogon gashinta ya rufe duk
fuskarta tana kuka, sai kuma ta zamo a hankali daga saman gadon ta kife kanta
da jikin gadon tana shessheka, ji tayi ya dafata ta juyo a firgice tana komawa
baya don bata san sanda ya zagayo ba, ya sa hannu biyu ya maida duk gashinta
zuwa gefen fuskarta yana kallonta, tuni ta daina kukan da take saboda tsoro, ta
sunkuyar da kanta kirjinta na heaving, jawota yayi jikinsa ya rungumeta ya
lumshe ido, ita dai tayi tsit tsabar firgici, a haka ta dinga jin bugun
zuciyarsa tana jikinsa, they were like that for 3 mins daga karshe taga ya mike
a hankali ya fita daga dakin ta bi sa da kallo tana share sabbin hawayen dake
sauko mata a fuska, throughout ranan haka Khaleesat tayi ta zama a daki sai dai
ya kawo mata abinci, da ta tuno abubuwan da Abdul yayi mata daxu sai ta firgita,
sai ya zama kamar tana hallucinating ne, hakan ya dinga sa mata ciwon kai taji
kamar zazzabi zai rufeta, saura kadan panic attack ya kamata a dakin banda
Allah ya takaita mata, gaba daya yanxu tunanin menene makomar rayuwarta take,
shikenan haka zata hakura tayi zaman aure da Abdul ta ci gaba da shanye duk
bakin cikin da zai kunsa mata a zaman aurensu bata da me tsaya mata tunda shi
din mijinta ne? Did she even have a way out with the way things turn out to be
all of a sudden? Is this going to be the beginning of a new era a rayuwarta?
Shikenan irin rabuwar da zata yi da su Housemate dinta kenan? Kilan ma ba
lallai ta sake ganinsu ba a rayuwarta? Shikenan haka Abdul zai ci gaba da
caging dinta a gidansa ga threatening din kashe mata siblings da yayi idan taki
zama da shi? Duk wa ennan tunanin suka sa ta dinga kuka tana tausayin sabuwar
rayuwar da take kokarin fadawa, don tasan Abdul na gane ta gama period bazai
daga mata kafa ba and that is the end of her, kuma shikenan dole ta zauna tayi
zaman aure da shi ko da yankan naman jikinta zai dinga yi kuwa don azabtarwa,
tunda Ummanta ta haifeta tana jin bata taΙa shiga irin wannan tashin hankalin
da take ciki ba a wannan lokacin, tana jin alamar zai shigo dakin take goge
fuskarta ta langwabe a zuwan ciwon ciki take.... Cikin wannan yanayin Khaleesat
tayi kwana uku a gidan tare da Abdul, a wannan kwanaki ukun kuwa duk da halin
da take ciki a haka yake sakawa taje tayi masu girki a kitchen wai shi baya son
abincin restaurant, Khaleesat bata taΙa fatan kar period dinta ya dauke ba
kamar irin wannan lokacin, she wish she will keep on flowing continuously like
the woman with the issue of blood amma tasan dole ya dauke nan da kwana biyu
don bata wuce 5 days in tana period, sosai hankalinta ke kara tashi idan ta
tuna hakan, yau tunda gari ya waye tayi wanka ta saka pad take kwance kan gado
saboda azababben ciwon kan da take, all these pass days bata wani samun baccin
kirki da daddare tsabar damuwar da ta saka ma kanta da tunane tunane, daga
karshe dai haka ta daure ta fita zuwa kitchen da kyar don dora breakfast kafin
ya fito daga dakinsa kamar yanda yayi mata umarni 2 days back, tana fita parlor
ta leka compound din gidan taga babu motarsa alamar ya fita, ta murda kofar
parlon taji a kulle kamar yanda tayi tunani, Zaunawa tayi kan kujera ta dafe
kanta hawaye masu zafi na zuba idonta, after a while ta mike tana shesshekan
kuka ta wuce kitchen din, tana cikin hada breakfast taji alamar shigowar
motarsa gidan, after a while aka bude kofar parlon, Ζasa kunne tayi jin kamar muryar
mace take ji a parlor, can kuma taji tsit, ita dai ta ci gaba da abinda take yi
jiki babu kuzari har ta gama ta tsaftace kitchen din sannan ta juya zata fito
ta kusa cin karo da wata mace in her late 30's zata shigo kitchen din, daga
sama har kasa matar dake tsaye kofar kitchen din take mata wani irin kallo da
za a iya kira da kallon kaskanci, ita dai Khaleesat tunda ta kalleta sau daya
ta sunkuyar da kanta ita kanta bata san sanda ta gaisheta ba don duk ta rude
gashi kuma taga suna kama da Abdul duk da bai taΙa nuna mata wani nasa ko da a
hoto ba, a walakance matar tace "Da ban kwana ba zaki gan ni munafukar
Allah, Er gidan matsiyata ma ci amana.... A gidan ubanki kika san ni da zaki
gaisheni?" Sai a sannan Khaleesat ta sake daga kai tana kallonta da mamaki
cause kalmomin matar kawai a bazata suka zo mata, bata san sanda tace "Ki
zageni amma banda iyayena...." Bude baki Meema tayi da mamaki tana
kallonta ganin guts dinta, kafin tace komai Khaleesat ta bi gefenta zata fice
daga kitchen din wanda saura kiris ta bangajeta wajen fitan, cikin zafin nama
da bacin rai Meema ta fincikota ta dawo da ita gabanta sannan ta sauke mata
wani wawan mari ta shakota tana kokarin kai ta kasa ta nakadi banza, Khaleesat
ta kwala wani kara, dai dai isowan Abdul wajen, lkci daya yanayinsa ya canza
don a kan idonsa yayar tasa ta sauke ma Khaleesat mari sannan ta shakota tana
kokarin dukanta, cikin daga murya yace "Zo ki fita ki bar min gidana
Amina, how dare you? Me tayi maki zaki mareta haka? Baki da hankali ne? Get out
of my house pls, fita ki bani waje" Sake baki Meema tayi tana kallonsa
babu ko kiftawa, cikin zafin nama ya tafi ya bude kofar parlon kirjinsa na sama
da kasa yace "Ki fita nace Amina kar in rama mata" Cikin karfin hali
Meema ta dafe kirjinta da hannu daya tace "Abdallah ni kake cewa in fita a
gidanka?" Ya jefar da wayar hannunsa yana huci ya nufeta kamar zai kai
mata duka cikin daga murya yace "Na ce ki fita din ko gidanki ne? Get out
of this house before i loose my control Amina, gerrout" Ita dai Khaleesat
makalewa tayi jikin kofa jikinta na rawa, sum sum sum Meemah ta karasa ta dau
handbag da karamin travelling bag dinta don dama daga airport yaje ya daukota
saukanta garin kenan, ta nufi kofar fita parlon sannan ta juya tana kallonsa da
mamaki tace "Abdallah ni kake daga ma murya kake cewa in fita in bar
gidanka akan wancan matsiyaciyar? Har kake ikirarin zaka kai min hannu? Ni din
Abdallah?" Da karfi yace "Duk nayi, fitaa ki bar min gidana
malama" Fita tayi daga parlon ya bi bayanta kamar zai tashi sama ya tafi
ya bude mata gate din gidan, ta fita yayi banging gate dinsa ya kulle, har ya
dawo parlon Khaleesat na makale jikin kofa ita tsabar yanda ta tsorata ma ko
digon hawayen marin da Meemah tayi mata babu a idonta, ya karasa kitchen din
yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi, sai a sannan taji hawaye ya fara zuba
idonta.
[6/14, 9:16 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Juyawa Abdul
yayi ya fice daga kitchen din ba tare da yace mata komai ba ya dau wayarsa ya
nufi dakinsa, Khaleesat ta bi sa da kallo tana goge hawayen dake zuba idonta
har ta dena hango sa, jingina tayi da kofar kitchen din ta kai hannunta
fuskarta dai dai inda Meemah ta mareta don sai a sannan ta fara jin zafin
marin, fashewa tayi da kuka tayi me isarta kafin ta fito daga kitchen din tana
tafiya a hankali ta tafi ta zauna kan 1 seater dake parlorn tana share hawayen da
yaki tsaya mata, abubuwan da Abdul yayi ma Meemah ne suka dinga dawo mata a kai
don hakan yayi mugun shock dinta, but she just don't want to believe senior
sister dinsa yayi harrassing haka har da koranta, to ko dai ita ce Aunty Aminan
da suke ce ma Meemah don taga sosai suke kama da ita, tana ta zaune parlon
bayan wani lokaci sai gashi ya fito daga dakinsa, sunkuyar da kanta tayi tana
wasa da fingers dinta, ya karaso cikin parlon yace "Kin yi breakfast din
ne?" Da Authoritative voice yayi tambayar yana kallonta, hakan yasa ta Ιan
rikice kamar mara gaskiya ta girgiza masa kai with fear all over her face, sai
kuma ta mike da sauri ta nufi kitchen ya bi ta da kallo har ta shiga ciki,
shayi rabin cup ta hada sannan debi Irish kadan a plate don tension yasa ta
rasa appetite dinta gaba daya , sai kuma ta tuna shi ma bata basa breakfast din
ba, tunanin ko ta kai masa parlor ta fara yi don a kwanaki ukun nan Bedroom
dinsa take kai masa breakfast din kamar yanda ya umarce ta, kamar munafuka ta
makale jikin kofar kitchen din tana kallonsa tana son tambayarsa ko ta kawo
masa breakfast din nasa parlorn amma ta kasa don bata san me zai ce ba kar yayi
mata masifa, wayarsa kawai yake dannawa bai ma san tana wajen ba, juyawa tayi a
hankali ta koma kitchen din a sanyaye ta hada masa breakfast din ta fito da shi
parlor, jikin kujera ta tsaya a hankali
tace "Ga breakfast din nan" Daga kai yayi ya kalleta, gabanta ya
dinga faduwa ta sauke idonta daga kallonsa, jin bai ce komai ba yasa ta karasa
har gabansa ta duka ta ajiye masa breakfast din, yace "Ke ina naki?"
Taki barin su hada ido tace "Yana kitchen" Yace "Dauko"
Mikewa tayi ta tafi ta dauko nata ta dawo tana kallonsa, yace "Ajiye ki ci
a nan" Bata masa musu ba kanta a kasa ta zauna gefensa da ya nuna mata ta
fara tuttura irish din kamar dole tana satan kallonsa ta gefen idonta, a
hankali taga ya jawota jikinsa taji gabanta yayi mugun faduwa, calmly yace
"I am a monster to you right?" Da sauri ta girgiza masa kai zuciyarta
na bugawa, yace "Gashi nan, kin maida ni dodonki" Ita kanta bata san
sanda hawaye ya cika idonta ba, yayi kasa da murya yana zame hulan kanta yace
"Now tell me what u want from me, tell me what's on ur mind.... amma
before then ki sani bazan taΙa rabuwa da ke ba saboda ina son ki Khaleesat,
rabuwa dake will be the last thing i will do on earth no matter what, You know
i love you genuinely from onset, i loved you wholeheartedly and i gave u the
best of everything I could, i loved you even before you become the woman you
are today, i love you since when u were just a 15 year old teenager tun baki
girma ba, yea i know about my flaws but loving you is all that matters, not in
the sense that abubuwan da nake yi are right, i am obsessed with you Baby, may
be you can change me in ur own way...." Khaleesat ta rufe idonta tana jin
kamar ta fashe da kuka, jin kalamansa take kamar ana soka mata mashi a kirji,
Ya dora forehead dinsa a nata murya can kasa yace "Why not give me a
chance and forgive my flaws Khaleesat?" Bude idonta tayi hawaye suka hau
zarya a idonta, har cikin ranta taji bata son jin maganganun da yake mata, a
hankali yace "Forgive me, i know i wronged you in all ways, but don't
forget ina sonki, ina kuma sonki ne saboda Allah, they are many beautiful
ladies out der buh i chose you Khaleesat" Lokaci daya gaba daya tunaninta
ya tafi kan Housemate dinta, kasa daurewa tayi ta fashe da matsanancin kuka, ya
daura kanta a saman shoulder dinsa patting her softly, ta dinga kuka kamar an
aikota, shi dai bai ce mata komai ba, sai da tayi kukan me isarta sannan ta
hakura don kanta tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya, ya daga kanta yana
kallonta taki yarda su hada ido, breakfast dinta ya ajiye mata a kusa da ita,
ba musu ta fara ci a hankali da tunani iri iri a ranta, muryarsa taji ya daki
dodon kunnenta "Yaushe zaki gama period?" Gabanta yayi mugun faduwa,
ta ajiye cup din shayin dake hannunta ba tare da ta kallesa ba, a hankali tace
"Ai ban dade da farawa ba" Yace "Yau kwana hudu da farawan
ki" Da kyar ta dake tace "A'a, uku ne.... first day din ai bana yi
sosai..." Yace "Saura kwana nawa ki gama kenan?" Sosai gabanta
ke bugawa, ta sunkuyar da kanta cike da karfin hali tace "Kilan nan da
kwana uku ko hudu" Jin bai ce komai ba ta daga kai a Ιan tsorace ta
kallesa, taga kallonta yake without blinking, sauke idonta tayi tana wasa da
karamin cokalin dake cikin mug din shayinta, ya dauke shayin ya mayar gefe,
taga ya kai hannu shoulder dinta zai sauke siririn hannun rigar dake jikinta,
sosai hankalinta ya tashi amma bata ce masa komai ba gabanta na ci gaba da
faduwa, ya sauke rigan gaba daya yana kallon bare chest dinta, hawaye ne ya
cika idonta taki yarda su hada ido, can dai tayi karfin hali muryarta na rawa
tace "Toh baka sha shayin ka ba zai huce" Yayi kasa da murya yace
"Wa ennan zan sha... " Momy ce
tsaye parlor tana kallon Meemah dake rusa kukan bakin ciki uwa er yarinya, ga
trolley dinta a gefenta, bacin rai ne karara kwance fuskar Momy da idanuwanta
suka Ζankance tana huci, mai aikin gidan ce ta shigo parlon rike da bowl din
pepper soup din da tayi ma Momy, cikin ladabi ta risina tace "Hajiya ga
farfesun nan ya kammala" a fusace Momy ta figi throw pillow ta jefa mata
tace "Don ubanki wuce ki ban waje ke da farfesun, baki ga magana nake bane
zaki shigo min parlor kai tsaye, yau ga jahilar mata kai" a tsorace mai
aikin ta juya da sauri ta bar parlon ta koma kitchen ta kullo kofar, Momy tace
"Na kusa daina daukan tsinannun masu aikin nan don sun isheni haka kuma,
na kori wancan shegiyar da ta shigo min parlor da yan uwan Alhaji da suka zo
daga kauye babu izinina yanxu kuma an kawo min wannan jakar da ko kwana biyu
bata yi ba ta fara nuna halayyan dabbobi" Ita dai Meemah kuka kawai take
tana fyace hancinta da handkerchief, tsabar kuka idonta har sun suntume, Momy
ta kara kankance idanuwanta tana kallon Meemah tace "Shi Abdallahn ne yayi
maki haka Meemah?" Meemah ta hadiye wani abu da ya tokare mata wuya don
bakin ciki tace "Momy da kin ga tijaran da Abdallah yayi min akan yarinyar
nan ko, hmmm, ki bari kawai Momy, Momy kare bazai ci abinda Abdul yayi min ba,
bayan zagi da cin mutunci wai ni ya kora a gidansa, kora irin ta
walakanci" Momy ta zauna kan kujera with disbelief, duk da AC dake aiki a
parlorn sai zufa take yi dama ga ta narkekiya, tana gyara zama tace "Ko
dai ya sha wani abu ne Meemah??" Cikin rawan murya Meemah tace "Babu
abinda ya sha wallahi Momy don lafiyan Allah ya dauko ni a airport muna ta
hira, tare fa da ni duk aka yi tracking yarinyar nan tunda akwai wani tsohon
saurayina wanda aikinsa kenan, amma wai yau akanta Abdallah zai min irin wannan
tijara haka tun ba aje ko ina ba, duka duka fa kwananta yau hudu da shiga
hannunsa, amma ya rufe ido ya zazzageni ya ci min mutunci ya koreni" Momy
tayi wani murmushin takaici tana girgiza kafa tace "Kin ga abinda nake ta
gudu kika kasa ganewa kenan ai ko? Dama ance duk abinda babba ya hango yaro ko
uban me zai hau bazai taΙa hangowa ba wallahi, ba ya kwana da ita ba dole ki ga
abinda yafi haka ai, babu yanda banyi in lalata batun auren nan ya hakura ba
amma sam Meemah kika ki bani hadin kai ki ka koma bayan Abdallah, har da bin
wasu malamanki da basu taka kara sun karya ba duk don yarinyar ta shigo
hannunsa, to ai ta shigo kuma kin ga abinda ya biyo baya daga shigowarta, to
wallahi zai kai ya kawo wataran Abdallah yace bai san mu ba akan yarinyar nan,
ni na haifesa ba wani ya haifar min shi ba sarai nasan abinda zai iya
aikatawa" Meemah ta dinga kallon Momy babu ko kiftawa don ita sai yanxu ta
kara fahimtar dalilin Abdul nayi mata irin wannan mugun tijara kan yarinyar da
yake ta ikirarin zai koya ma lesson idan ta shigo hannunsa, sarai kuwa ya kwana
da ita dole ya birkice haka ya haukace kanta, dama buzaye da aka sani da
mugayen asiri, Meemah tayi wani murmushin takaici tace "To kuwa yanda nayi
ruwa nayi tsaki har sai da yarinyar nan ta shiga hannunsa to haka zan yi har
sai ya rabu da ita a kwanan kuwa ba da jimawa ba" Momy ta kwado ma sabuwar
me aikinta kira, matar ta taho a guje har sai da tsantsin tiles ya kwasheta
sbda ruwan dake kafarta sai ga ta a kasa timmm, A fusace Momy tace
"Wallahi tallahi kika kuskura kika illata min tiles sai na cire cikin
kudin albashinki, yau naga er iskar mata kawai, kullum na kiraki sai kin
azabtar min da tiles saboda kauyanci? Wannan wace irin mata Adama ta kawo min
haka da sunan me aiki?" Har kasa mai aikin ta zube tana ba Momy hakuri, cikin
tsawa Momy tace "Miko min wayata dallah ki fita ki bamu waje, er kauyen
banza" Mai aikin ta kalli wayar dake kan center table dab da inda Momy ke
zaune, ta karasa da sauri ta dau wayar ta mika ma Momy, Momy ta warce, mai
aikin ta bar parlon, Momy ta mika ma Meemah wayar tace "Dubo min lambar
Godiya, glasses dina yana daki" Meemah ta amshi wayar ta dubo number
aminiyar Momy sannan tayi dialing ta mika mata, a kashe suka ji wayar, Momy
tace "Tayi tafiya me muhimmanci kenan, bari zuwa anjima in sake
kiranta" Meemah da kanta ya gama kullewa tace "Tabddi jam, lallai
nayi babban kuskuren da ban taΙa yin irinsa ba Momy, sai ma fa kinga kayan dake
jikinta da naje gidan, tana kitchen tana soye soye" Momy dai tayi shiru
tana girgiza kafa don bakin ciki da takaici, can tace "Dauko min gyale da
jaka a daki, ina zaman zamana kin janyo min kashe kudin da banyi budgeting ba
Meemah, duk ke kika ja min wannan masifa da kika ki jin maganata wallahi, in
hada iri da matsiyata akan wani dalili? A farko dai na hakura na zuba masa ido
da yaki jin maganata, amma yanxu kuwa wallahi sae ya rabu da yarinyar nan, babu
dalilin da zai sa in hada zuri'a da ita, ga kuma rashin adalcin da aka yi ma
Alhaji ga asara ga biyan tara" Tashi Meemah tayi ta tafi dauko ma Momy
gyalenta da handbag, all this while dama ita ke ta shiga malamai don Khaleesat
ta shiga hannun Abdul Momy ko bin ta kanta bata yi tunda dama ba son auren take
ba, Momy na ficewa daga gidan da driver dinta Meemah ta tafi dakinta da wayarta
tayi dialing number Malamin da tasa yayi mata aiki. Runtse ido Khaleesat tayi
bayan taji duk maganganun da Abdul yayi, yana rungume da ita saman gadonsa
kamar zai maidata jikinsa, it's past 8pm na dare, jin taki cewa komai s hankali
yace "Khaleesat" Bude idonta tayi wasu hawaye masu zafi suka silalo
fuskarta tace "Um" Yace "Say something" Still tayi shiru
hawaye na zuba idonta don bata ma san me zata ce masa ba at this point, ya dago
kanta yana kallonta yayi kasa da murya yace "Say something pls" Da
kyar muryarta na rawa tace "Ban san me zan ce ba" Yace "Say
anything" Shesshekan kuka ta fara yi masa tana jin zafi a zuciyarta, me
kuma yake son ta ce masa, tunda yace bazai taΙa rabuwa da ita ba ko me zai
faru, meaning dole ko tana so ko bata so haka zata ci gaba da rayuwa da shi a
matsayin mijinta, so me yake son ta ce, ta dai dake da kyar har sannan muryarta
na rawa tace "Kawai alfarma daya zan nema wajenka" Murya can kasa
yace "Say it Khaleesat" Tayi karfin halin cewa "I don't want you
to hurt anyone because of me...." Kasa ci gaba tayi tana kuka a hankali,
ya dinga kallonta don sarai yasan su wa take nufi, Calmly yace "Ohk u mean
ur Body Guards that sue me?" Ita dai kuka kawai take, Ya Ιan yi wani
murmushi yace "I don't think i will leave dem cause they started
everything first, they intruded in what wasn't der business, basu baki labarin
harbin da aka yi ma wani dake da alaka da su ba, I mean Salem..."
Khaleesat ta daga kai da sauri ta kallesa hawaye na sauka idonta gabanta na
faduwa, lkci daya ta tuna sanda Aunty Farida ke sanar mata Ajay yace mata an
harbi wani abokinsu a kano, yana wani murmushi yace "To su ma ana nan ana
targeting din su, amma in kince in kyalesu i will do that under 2
condition..." Khaleesat dai kallonsa kawai take ta kasa cewa komai duk
jikinta yayi sanyi, yace "The first condition is that.... zaki yi magana
ta waya da su ki gaya masu ke za ki zauna da mijin ki they should back off,
sannan ki gaya masu su janye karan da suka kai kotu..." Bata san sanda ta
fashe da matsanancin kuka ba, ya dinga kallonta sai kuma yayi murmushi yace
"Baza ki yi ba kenan?" Muryarta na rawa tace "Ban ce bazan yi
ba" Wayarsa ya dauko ya mika mata yana kallonta, da kyar tace "Bani
da number ai" Yace "Amma aunt dinki na da shi ai... Call her and ask
her to send you the number" Ta girgiza masa kai tana jin kamar numfashinta
zai dauke sbda rikicewan da tayi bayan ya fadi conditions dinsa, cikin kuka
tace "Bani da numberta offhand" Yace "Ni ina da shi, i will call
her now sai ki gaya mata ta turo maki number daya daga cikinsu, and mind you kada
ki kuskura ki ce mata komai, number kawai zaki yi requesting ta turo maki"
Ta fashe masa da kuka sosai tace "Why are you doing this plss Ya
Abdul" Yace "Ohk, i will revenge and nothing is gonna stop me, i
promise you this, shi abokinsu da aka harba ai yayi surviving, i hope they
survive too....." Tana kuka sosai tace "No plsss..." Wayar ya
dauka yayi dialing number din Aunty Farida yana fara ringing ya mika mata yana
kallonta.
[6/17, 7:43 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Har Aunty
Farida ta Ιaga kiran Khaleesat bata amshi wayar da Abdul ke mika mata ba hawaye
na zuba idonta, lkci daya ya hade rai yana mata wani irin kallo, babu shiri ta
amshi wayar hannunta na rawa, a sanyaye tace "Aunty" Cikin rikicewa
Aunty Farida tace "Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta tayi shiru,
hankali tashe Aunty Farida tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,
Khaleesat kina ji na? Don Allah kiyi magana, Hello Khaleesat" Khaleesat ta
kasa ce mata komai hawaye masu zafi na sauka idonta, kiris ya rage ta fashe
mata da matsanancin kuka a wannan lokacin, Abdul ya fixge wayar yayi a hannunta
ya katse yana mata wani mugun kallon da ya tsorata ta sosai yace "Are you
daring me?" ta fashe masa da kukan da take dannewa tana girgiza masa kai,
a fusace yace "Ohk then, since abinda kika zabar masu kenan to ina me
tabbatar maki zan aikata hakan nan ba da jimawa ba kuwa, sannan bayan nayi zan
sanar maki, don bani da imanin kyale duk wani mahalukin da yace zai shiga
hurumina, i don't mind sending that person to his early grave, and mind you....
i will so deal with them yanda in their next life baza su kara shisshigi akan
abinda bai shafesu ba, if you think i am bragging watch and see, bani da
conscience...." Khaleesat ta
girgiza masa kai cikin karfin hali tace "Duk ba sai ka masu komai ba, zan
yi abinda kace" Wayar ta amsa a hannunsa ta cire a Flight mode din da ya
saka sannan ta sake dialing number Aunty Farida, yana fara ringing Aunty Farida
ta daga da sauri tace "Khaleesat, kina ji na Khaleesat?? Hello"
Khaleesat ta dake ta hadiye sauran kukanta cike da karfin hali tace "Na'am
Aunty" Cikin tashin hankali Aunty Farida tace "Kina ina
Khaleesat?" A hankali Khaleesat ta daga kai ta kalli Abdul taga ya wani
murtuke fuska yana kallonta kamar bai taΙa fara'a ba a rayuwarsa, ta sunkuyar
da kanta wasu sabbin hawayen na zubo mata cikin sanyin murya tace "Aunty
Number Ahmad za ki turo min yanxu plss" Aunty Farida da duk ta rude tace
"Ahmad kuma Khaleesat? Wanene Ahmad? Kina ina ne yanxu?" Shi dai
Abdul wani devilish look kawai yake mata, tayi kasa da murya tace "Aunty
Number Junaid zaki turo min" Da sauri Aunty Farida tace "To bari in
turo maki yanxun nan" Katse kiran Aunty Farida tayi cikin rawan jiki ta
tura ma Khaleesat number Ajay, number na shigowa Abdul ya amshe wayar a
hannunta yana kallon number for almost 5 seconds, can yayi wani murmushi ya
mayar mata da wayar, cike da isa yace "Kirasa ki gaya masa abinda nayi
instructing din ki" It took Khaleesat almost 30 seconds kafin ta iya
dialing number Ajay, shi ma saboda irin kallon da Abdul ke mata ne, exactly
irin kallon da yake mata in zai gaura mata mari, cikin muryarsa dake tsoratata
taji yace "Kika kuskura kika yi magana da wata muryar da ba normal voice
dinki ba zaki sha mamaki wallahi, and immediately he picks just go straight to
ur point, do not give him a breathing space to say anything to you, go straight
and tell him kin hakura zaki zauna da mijinki, kin ji me nace maki?" Ita
dai bata ce masa komai ba hawayen takaici na zuba idonta, sai da kiran ya kusa
katsewa Ajay ya daga, ta Ιan kalli Abdul da bai fasa mata wani irin kallo ba,
da kyar ta daure tace "Hello, good evening....." Mikewa Ajay yayi jin
muryarta, bata jira ya gama processing ba ta ci gaba a hankali tace "Dama
ina son in ce maka ni na hakura zan zauna da mijina, and i appreciate all what
you've done for me kai da Yaya Jawwad, thank you so much" Ajay ya juya ya
kalli Jay da shigowar sa dakin kenan, as if counting his words yace "Come
again!" Yana fadin haka ya saka wayar a handsfree sannan ya nufi Jawwad
yana kallonsa, Khaleesat ta kalli Abdul, sai kuma ta sunkuyar da kanta tace
"Cewa nayi ni na hakura yanxu, zan zauna da mijina, and thank you for all
what you've done for me...." Wasu sabbin hawaye suka hau zarya a fuskarta
tana ji kamar ta fashe da kukan dake cin ta, Abdul ya fixge wayar a hannunta ya
katse sannan ya kashe wayar gaba daya, Ajay ya kalli Jay that looks speechless
and shock at the same time, lkci daya ya jefar da wayarsa saman gado, cikin nutsuwa
yace "Nayi da na sanin bata lokacina akan yarinyar nan, i regret wasting
my very precious time...." Jay ya ma rasa me zai ce, walking slowly ya
karasa gaban window din dakin yana kallon Ajay that was boiling from inside, a
hankali yace "Look Ajay, i think those words are not coming from her
heart, sakata yayi ta fadi hakan pls mu yi mata uzuri, she is forced to say all
what she said, ba mu san situation din da take ciki ba let consider that
plss" Ajay ya masa wani kallo yace "Billah na cire hannuna a
lamarinta kaji na rantse Jay, i have nothing to do with her case again, after
all i was just doing it just for the sake of humanity not because of her, ko
kasheta yake ya kamata ta gaya mana haka? Mu zata dauka for granted? Beside she
spoke confidently meaning she is okay with what he asked her to say, i am
leaving this state first thing tomorrow morning, so unfortunate i waste my time
on the brat, don taga mun yi stooping kan mu so low shi yasa ta dauke mu for
granted" Yana kai wa nan ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, Jay ya
lumshe ido ya bude don bai san me zai sake ce masa ba da zai sa ya sauraresa,
kuma tunda har ya rantse magana ta kare, ya zare hannunsa kenan babu abinda zai
sa ya sake involving kansa, zaunawa yayi gefen gado ya dafe kansa da yaji ya
masa nauyi, at the same time letting out a sigh, kalmomin Khaleesat ne suka
dinga dawo masa kai, he felt really disappointed in her too, but can kasan
zuciyarsa tausayinta ne ya mamayesa ya kuma yi mata uxuri, ya rasa menene yasa
shi shiga yanayin da ya shiga a wnn lkcin, da kyar dai daga karshe ya mike ya
fita daga dakin yana tafiya a hankali. Daren ranan nan Khaleesat bata yi baccin
awa biyu ba cikakke, da bacci barawo ya saceta zata farka a firgice, bata taΙa
jin abu ya tsaya mata a rai irin abinda Abdul ya sa tayi ma su Housemate dinta
ya tsaya mata ba, gashi ko digon hawaye yaki fita idonta, her heart is just
heavy, but did she have a choice? In bata yi hakan ba yayi ma su Housemate
dinta wani mugun abu ai bazata taΙa yafe ma kanta ba, tunda har yake ikirarin ba
shi da imani babu abinda bazai iya aikatawa ba, tasan kuma sarai zai iya
aikatawa din, tunanin sabuwar rayuwar da take kokarin fadawa take, is she going
to survive this at all? Is this not going to be her end? A ranta taji kilan
lokacin mutuwarta ne ke tinkarota, sai a sannan taji hawaye masu zafi for the
first time a idonta, ta kai hannu a hankali tana sharewa ta juya tana kallon
Abdul dake baccinsa hankali kwance, dai dai nan alarm din wayarsa ya kada, ta
juya da sauri tayi backing dinsa tana goge hawayen da ya fara zubo mata sosai,
after some seconds taji alamar ya tashi yana karanto addu'an tashi bacci, ita
dai hawaye kawai take, sai da taji yayi sallah ya fita daga dakin sannan ta
mike zaune tana kuka a hankali. Nenne ta bude hannu tana kallon su Aunty Farida
cikin nutsuwa tace "To kun ga ai baza mu shiga hurumin Allah ba, ko akwai
me tsaurin idon da zai shiga a cikin ku? Allah Ubangiji ne kadai yasan daliliin
da ya maidata hannun mijinta cikin ruwan sanyi babu tashin hankali, to don me
za mu shiga hurumin da ba namu ba? A'a gaskiya banda ni tunda ni dai nasan
wanene Allah, kuma shi kadai yasan hikimarsa ta yin hakan, da yasan Khaleesah
zata cutu hannun Awdul da bazai fara basa sa'ar sungumeta ba don bamu fi sa
sani ba, ko ba komai Ιa na zai samu kwanciyar hankali ya ci gaba da sabgogin
rayuwarsa kamar ko wani Ιan adam, mu mun yarda da kaddara mummuna ko kyakkyawa
tunda mu musulmai ne, kuma duk abinda Allah yayi mu din banza za mu ce don me,
domin haka nake cewa Allah ya bata zaman lafiya da mijinta, Ιan halayyarsa da
yake yi mara kyau Allah ya gyara sa ya dena, ai babu wanda bai da taΙon wani
mugun abu a rayuwar nan, in sun dawo kano mu kuma sai mu je ganin daki mu sa
albarka, duk sanda ya bar ta ta zo ta gaida mu a Mariri sai ta zo bakinta
alekum, shi kuma Ali Allah ya sa karshen wahalarsa kenan a duniya" Wani
irin kallo Aunty Farida ke ma Nenne zuciyarta na tafarfasa, Umma dai kanta na
sunkuye bata ce komai ba amma ita kadai tasan abinda take ji a zuciyarta, Mama
Zubaida tace "Amma dai Nenne ai ya kamata a bibiyi halin da take ciki, an
taΙa tarewa haka kawai a zo a sungumi yarinya a mota da asuba ba a san ko shi
din ne ba ko ba shi ba amma duk a rasa me bibiyar hakan, wannan ai abun dubawa
ne, tun da mu dai har yanzu bai ce mana shi ya dauketa ba" Nenne tace
"To er bakin ciki, shi din ne ya sungumeta ba kowa ba aniyarki ta bi ki,
kuma ai halaliyarsa ya sunguma ba wata ba, duk wanda ya sake cewa zai bada
shawara a wannan lamari idan ban sa Ali ya sallamesa ba shegiya uwata da ubana
suka haifeni, kwata kwata bakwa neman ma Ιa na sauki a rayuwar nan, burin ku
kawai tashin hankali ya kashe Ali ku huta ni kuma in shiga uku, ita uwar da ta
tsugunna ta haifi yarinyar bata da bakin magana sai ke me baki kamar ta dorinar
ruwa?" Mikewa Mama Zubaida tayi ta shige dakinta, Mama Shatu ta kyabe baki
tace "To Allah ya kyauta, in ya dawo mana da gawar ta ai sai mu zauna mu
yi zaman makoki ba shikenan ba" Nenne tace "Sai dai ki ga gawar er ki
Labeebah amma ba Khaleesah ba, kuma bakin cikin da ku ka kasa boyewa ne zai kashe
ku ke da Zubaida" Mikewa Umma tayi hawaye cike idonta ta shiga dakinta,
Nenne ta kyabe baki ta mike tana kallon Aunty Farida tace "In Ali ya dawo
ki ce masa nace ya zo ya amshi tuwo da miyar taushe zan ajiye masa, wallahi
wata guda zan yi ina masa girki ya marmaro" Daga haka ta fice daga gidan,
Aunty Farida tayi tagumi hawaye cike idonta.
Meemah ta shigo parlon Momy ta zauna tana Ιan murmushi, ta
jira har Momy ta gama wayar da take yi da aminiyarta godiya sannan tace
"Momy na samesa a waya" Da sauri Momy tace "Ya daga kuma?"
Meemah tace "Eh ya daga bayan yaga text din da na tura masa kenan"
Momy na gyara zama tace "Toh Alhamdulillahi nagode ma Allah, sai yace maki
me?" Meemah tace "Kema kinsan dole zai taho ai, amma tsorona daya
kada ya kira Daddy kuma ya daga waya yace masa ba haka ba" Momy tayi wani
murmushi tace "Bazai daga ba, tunda na riga na gaya masa abinda ke faruwa
ai" Meemah ta sauke ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah, in ya samu
flight yau za mu iya ganinsu a gidan nan" Momy tace "Me zai hana ya
samu jirgi, ai da sauran lokaci dole zai samu" Mai aikin Momy ce tayi
sallama tana makale jikin kofar parlon duk da a bude yake amma bata shiga ba,
hannunta rike da tray me dauke da plate din gasasshen kaza da lemon kwali biyu,
Meemah ce ta amsa sallaman tana mata wani kallo tace "Tun da kika ga kofa
a bude ba sai ki shigo ba, kin wani raΙe jikin kofa kamar munafuka, don Allah
ki dena wannan kauyancin yana damun mu a gidan nan" Momy ta hade rai tana
kallonta har ta karaso ta ajiye plate din, cikin ladabi tace "Ga kazar ta
kammala Hajiya" Momy tace "Kalan Hijabin nan naki na daga min hankali
a gidan nan, kar ki sake saka min shi, in yar wa zaki yi to ki yar bana son shi
kwata kwata yayi kalar talauci" Mai aikin ta dukar da kai tace "Toh
Hajiya in sha Allah bazan sake sa shi ba, kiyi hakuri" Fita tayi daga parlon
da sauri, Momy ta dau plate din tulin kazar da aka ajiye mata ta fara ci tana
cewa "Ai dama tunda aka ce min zai taho da ita hankali na ya kwanta, don
dama taho da ita shi ne me wuyan...." Meemah tayi murmushi ita ma ta dau
yankan kaza daya tana ci tace "I trust you Momy" Khaleesat ta saka
Hijab dinta har kasa tana harhada wasu daga kananun kayan dake cikin closet din
dakin kamar yanda Abdul ya umarceta tayi, absentmindedly take aikin don tayi
nisa a tunanin da take, bude kofar dakin yayi ya shigo, ita dai bata juya ba
tana ci gaba da abinda ya sakata, ya karasa har bayanta ya tsaya, taki juyowa
gabanta na faduwa, juyo da ita yayi yana kallonta ta sunkuyar da kanta, yace
"Me ya sa baki son ki saki ranki har yanxu? Always looking worried" A
hankali ta daga kanta ta kallesa amma bata ce komai ba, yace "Kin gama
hada kayan ne?" Girgiza masa kai tayi, yace "To gama" ta juya ta
ci gaba da abinda take, shi dai yana tsaye yana kallonta, pad ta dauko a karshe
zata saka cikin karamin trolley din yace "What are you using that for? Ba
yau zaki gama ba?" Taki kallonsa zuciyarta na bugawa tace "Amma ban
gama ba ai" Bata jira me zai ce ba ta saka a akwatin sannan ta kulle ta
mike tsaye, kamo hannunta biyu yayi yana kallon cikin idonta, speaking slowly
yace "Promise me you won't act silly har mu isa kano Khaleesat" Ta
rasa dalilin da hawaye ya cika idonta, shi dai kallonta kawai yake, after some
seconds yace "If you try anything silly, zaki yi matukar mamakin abinda
zan yi, i promise you" Da kyar tace "Toh, amma plss ina son inyi waya
da Safiyyah, i am missing her" Yace "Baza ki yi waya da Safiyyah ba,
amma idan muka isa kano zan fara kai ki gidanku ki gaishesu sannan mu tafi
gidanmu" Ita dai bata ce komai ba hawaye na zuba idonta, a haka suka bar
gidan zuwa airport tunda yana da hoton National ID dinta a wayarsa. Da yamma
suka sauka garin kano, driver din gidansu har ya iso airport din yana jiransa,
Drivern ya bude ma Khaleesat back seat bayan ya gaisheta, kanta a kasa ta shiga
motar, kana ganinta kasan tana cikin damuwa sosai gashi ta kara zagbewa gaba
daya, Abdul ya shiga ta daya side din, sannan drivern ya shiga motar ya tada
suka bar airport din, sai bayan da suka fita daga cikin airport Abdul ya gaya
ma drivern inda zai fara kai su, sun yi nisa sosai da tafiyar Abdul ya juya ya
kalli Khaleesat da tayi nisa cikin tunanin da take, hannunta ya saka cikin nasa
wanda hakan ya dawo da ita reality, ta Ιan kallesa, yayi kasa da murya yace
"Are you hungry?" Girgiza masa kai tayi, ya jawota zuwa jikinsa yana
kallonta, ita dai bata ce masa komai ba zuciyarta na bugawa, a haka suka isa
Mariri wajen karfe biyar da rabi na yamma, Drivern na parking daga opposite din
gidansu Khaleesat Abdul ya bude motar ya sauka, jiki a sanyaye Khaleesat ta
sauka daga motar, ta ma rasa ko farin ciki zata yi ko akasin haka ganinta a kofar
gidansu, Abdul ya bi ta da kallo har ta shiga cikin gidan sai a sannan hawaye
suka cicciko mata ido, Noor ce ta fara hangota tana hura gawayi ta taso da gudu
ta rungumeta, sai a sannan sauran en gidan duk suka juya suna kallon Khaleesat,
Umma dake zaune bakin kofar dakinta ita ma ta dinga kallonta, Mama Zubaida da
Mama Shatu suka taΙe baki suna kallon juna, Aunty Farida dake gyara dakin Umma
ta fito da sauri jin sunan wanda Noor ta kira, Khaleesat ta tafi ta rungumeta
ta fashe da matsanancin kuka, Farin ciki wajen Aunty Farida ba a cewa komai don
duk tunanin su Ajay ne suka dawo da ita gida, sallaman Abdul yasa duk suka juya
suna kallon hanyar shigowa gidan da mamaki, nan da nan fara'ar Aunty Farida ya
bace, su Mama Shatu ne kawai suka amsa masa sallaman, ya karaso cikin compound
din, Aunty Farida ta saki Khaleesat ta tafi ta zauna kusa da Umma fuskarta babu
yabo babu fallasa, Mama Zubaida ta mike da sauri ta shimfida masa tabarma ita
da Mama Shatu na masa sannu da zuwa, ya zauna kan tabarman yana kallon Umma ya
gaisheta, Umma ta amsa tace "Sannu da zuwa" Aunty Farida ta mike ta
shige dakin Umma, Abdul ya gaida su Mama Zubaida dake ta washe baki, duk suka
amsa da fara'a, Ita dai Khaleesat na durkushe kusa da Ummanta kanta a kasa,
Abdul ya kalli Umma yace "Baba baya nan ne" Umma tayi karfin halin
cewa "Eh bai dawo ba" Ko rufe baki bata yi ba sai ga Malam Ali ya
shigo gidan da rabin buhun dankalin Hausa a hannunsa, ajiyewa yayi ganin Abdul
da Khaleesat, yace "A'aa, ikon Allah, baki mu ka yi yau a gidan"
Abdul ya tashi ya tafi har inda Malam Ali ke tsaye ya gaishesa, Malam Ali ya
amsa yana kame kame, ya tafi da sauri ya dauko tabarma ya kara shimfida ma
Abdul yace "Yi zaman ka a nan, bari in zubo mana ruwa a buta lokacin
Magariba yayi" Da sauri ya tafi ya dauko butoci biyu ya tafi zai debo
ruwan, Umma ta mike ta shige dakinta, Khaleesat ta bi bayanta, Nenne ce ta
shigo gidan da sallama tace "Allah me hikima, sannunku da zuwa Awdul"
Abdul ya gaisheta, ta jawo kujera ta zauna tana facing dinsa tace "Lafiya
lau wallahi, ya iyayen naka, ina kokarin daura sanwa kenan sai ga wani almajiri
da gudu ya zo ya sanar min ai kun zo, kasan Ιan albarka ne almajirin nan duk
wani abu da ke faruwa a gidan Ali kamar kiftawan ido yake rugowa ya sanar min,
ni kuma in ina da er dabino kwara uku in basa la'ada, nayi farin cikin ganin ka
wallahi, ina matar taka, in ji tare ku ke?" Yace "Tare mu ke"
Sai ga Malam Ali da ruwa a butoci yace "Ai ina jin tana dakin uwarta"
Nenne tace "Kai kuma lafiya? ina zaka da butocin ruwa ko karfe shidda bai
yi ba?" Malam Ali yace "Au? To to bari a ajiye, na zata magariba ta
yi" Da sauri ya koma ya ajiye butocin ya dawo, Nenne tayi kasa da murya
tana kallon Abdul tace "To Awdallah, ka dubi girman Allah ka rike amanar
da muka baka, yanxu kai ne uwarta kai ne ubanta, duk ta kuskure maka ka kawota
wajena ni zan san yanda zan yi da ita, kuma albarkacin auren da ya shiga
tsakaninka da jikata ka kara ba Mahaifinka hakuri ya yafe ma Malam Ali komai ya
wuce a wajensa don girman Allah, don yanxu kam duk mun zama daya tunda ga aure
har ya shiga tsakani, Allah Ubangijin ya baku zaman lafiya ya kauda duk wata
fitina ya kawo zuri'a dayyaba" Abdul yace "In sha Allah Kaka"
Nenne na murmushi tace "To madallah, gashi ko tuwon dare ban yi ba balle
in zubo maka" Yace "Ba komai, can gidanmu za mu wuce yanxu yamma
tayi" Nenne tace "Gaskiya kam, bari in fito maka da ita ku tafi, go
slown hanyar nan bata da kyau" Tashi Nenne tayi ta nufi dakin Umma, kuka
kawai Khaleesat take Umma tayi tagumi tana kallonta ta ma rasa abun cewa amma
daurewa kawai take ita ma hawayen bai zubo mata ba, don bakin ciki Aunty Farida
na jingine jikin bangon dakin ita ma ta kasa cewa komai, a haka Nenne ta shigo
dakin ta same su, taΙe baki tayi tace "Ta so ki fita mijinki na waje na
jiranki" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana kuka kamar ranta zai
fita, Nenne tayi kasa da murya tace "Wato a yanda kanwar uwarki ke zube ba
mashinshini shekara da shekaru haka kema kike son ki zauna mana tunda kyau
kawai gare ku amma babu farin jini, banda samun waje ki samu miji zankadede
kamar Awdul amma son zuci irin taki da na uwarki da kanwarta bazai sa ku yi
farin ciki da hakan ba, in a baya Awdul Ιan iska ne dama Allah ya taΙa halittar
da bai shiryar ba in yayi niyya? Daga yanda Awdul ke magana a kintse na gane ya
shiryu wallahi, to ko kawota da yayi ta gaishemu kadai ya isa mu shaida
shiriyarsa, wallahi ku dinga jin tsoron Allahn da ya halicce ku, duk wanda
burinsa ya raba aure to tsinuwar Allah ne zai tabbata a garesa, kuma in sha
Allahu Khaleesat tayi aure kenan mutuwa kadai ne zai rabata da mijinta tunda
duk mun san yana sonta, tashi ki fita gun mijinki ku tafi munafuka kawai, duk
da can baki san baki son shi ba sai da ya aika ki kasar turawa idonki ya bude a
can" Cikin kuka Khaleesat tace "Ni wallahi bana son sa, bana son sa,
bazan iya zama da shi ba" Nenne tace "Aikin banza, to uban me ya rage
kuma bayan ya kwana da ke? Ai duk rashin son da kike masa dole ki zauna da shi
tunda ya kwana dake yau kusan satin ki daya a gidansa ba kuma ajiye ki zai yi
yana kallo kamar hoto ba tunda shi ba Ιan iska bane, kuma gidan Ali ba Obalande
bane da za a tara masa fararen zawara har biyu a gida, Farida ma kadai ta
ishemu, tashi ki fita ki bani waje ko in tafi in kira maki Ali yanxun nan ya
fitar min da ke, tun da uwata ta haifeni ban taΙa ganin er da bata son
kwanciyar hankalin ubanta ba sai ke" Umma ta share hawayen dake zuba
idonta tana kallon Khaleesat tace "Ta shi ki je Khaleesah, Allah ya maki
albarka, Allah kuma ya baku zaman lafiya" Mikewa Khaleesat tayi tana kuka sosai
ta fita daga dakin Ummanta, Nenne tace "Atoh dai, iya addu'ar da za mu yi
mata kenan a matsayin mu na rikakkun musulmai, tun da muka ga haka to Allah ne
kadai ya san hikimarsa nayin hakan, kuma dama an gaya min aurenta da Awdul aure
ne me kyan gaske in har zata kwantar da hankalinta, gashi mun shaida yana son
ta, kuma ta dalilinta arzikin ubanta duk zai dawo har ma ya fi na da, wallahi
haka aka ce min, kawai dai babba ba a son yayi ta surutu ne shi sa nake jan
bakina nayi shiru" Har suka bar gidan da Abdul hawaye ne kawai ke zuba
idon Khaleesat, dubu talatin ya ba kishiyoyin ummanta ko wacce 15k, ya ba Islam
50k, Nenne ya bata 20k, Malam Ali kuwa bai amsa kudinsa ba sai ajiye masa Abdul
yayi kan tabarman dake bakin kofar dakinsa, babban tashin hankalin Khaleesat
yanxu period dinta da ya dauke, don kafin su taho kano a dari dari tayi sallahn
Azahar kar ya shigo ya ganta, tasan yau
dai Ζaryar ta ya kare kawai, a haka suka iso gidansu Abdul bayan sallan magrib,
Driver na shiga babban compound din da mota Khaleesat taji gabanta ya tsananta
faduwa, bayan yayi parking a space din parking Abdul ya sauko daga motar yana
kallonta, da kyar ta iya saukowa daga motar zuciyarta na bugawa sosai wanda ita
kanta bata san dalilin hakan ba all of a sudden, ya fara tafiya tana bin sa har
suka isa entrance din shiga parlorn gidan....
[6/18, 7:34 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat na
tafiya a hankali ta shiga parlon tana karanto addu'o'i a ranta don irin faduwar
da gabanta yake yi isn't normal, ga tsikar jikinta sai tashi yake, she was so
uncomfortable and restless at the same time, Abdul ya kulle kofar parlon ya
kalli mahaifiyarsa dake zaune cikin parlor ita da kanwarta Aunty karima da
Meemah, ko wannensu da bowl cike da farfesun kayan ciki a hannu, Khaleesat ta
sunkuyar da kanta ganin gaba dayansu zubo mata ido suka yi suna kallonta
fuskarsu babu yabo babu fallasa, amma kana kallon kwayar idanuwansa babu abinda
zaka gani sai tsantsan kiyayyarta, da kyar ta karasa tsakar parlon kamar zata
harde ta fadi, ta duka kasa cikin sanyin murya ta gaishesu gaba daya, instead
Momy sai ta dauke kai tana kallon Abdul tace "Flight din sai na dare ka
samu kenan Babana, bayan tun sassafe Meemah tayi maka text" Aunty Karima
ta hau kwalo ma mai aiki kira ta zo ta karo mata farfesu, Abdul bai ce ma Momy
komai ba ganin babu wanda ya amsa gaisuwar Khaleesat cikinsu ya kalleta yace
"Ta shi mu je" Khaleesat ta Ιaga kai ta kallesa amma bata tashi ba ga
zuciyarta sai bugawa yake, Momy tace "Ta tashi ku je ina? Wacece ita din
tukunna?" A takaice yace "Matata ce" Aunty Karima ta gyara zama
da mamaki tace "Ikon Allah, ita ce er gidan barawon da yayi ma Alhaji sata
har na miliyan dari kenan?" Meemah tace "Kwarai kuwa gashi kin gane
ma idonki, ita ce dai er matsiyatan da Abdul ya makale ma saboda rashin sanin
darajan mahaifinsa bai dubi rashin kirkin da aka yi ma Daddy a kotu akan
hakkinsa ba ya koma ma yarinyar, dama yawon ta zube uwarta ta shigo yi Nigeria
shi ne ta hadu da ubanta bayan sun yi watsewarsu ya aureta...." Katse ta
Abdul yayi a fusace yace "Idan kika ci gaba da voicing gibberish zaki sha
mamakin abinda zan maki a nan Amina, bridle ur tongue" Aunty Karima ta
bude baki da mamaki tace "Amina kai tsaye? Ko ka fara shaye shaye ne
Abdul? Akan shegiyar yarinyar nan kake nema kayi ma yayarka rashin kunya?"
Abdul ya kalleta yace "Kar ki sake sako min baki tunda ba dake nake ba,
stay out of anything that concerns me, Momy ce dolen ki ba ni ba" Momy
tayi wani murmushi tace "Rabu da su Babana, take her inside ta huta,
sannunku da zuwa" Tana fadin haka ta tashi ta taho kusa da Khaleesat ta
dafa ta tace "Welcome my daughter, ku je sama kin ji" Da kyar
Khaleesat ta mike tsaye duk jikinta a sanyaye ta bi bayan Abdul, Momy ta koma
ta zauna ta bi ta da kallon gefen ido, har ta ga sun haura sama sannan ta kalli
su Meemah tayi kasa da murya tace "Sam baku da hankali baku da tunani,
haka muka yi da ku daxu?" Meemah da ke huci tace "Ni matsala ta
kinsan ban iya pretending bane Momy, wallahi ban iya ba ko nace zan yi" A
fusace Momy tace "To in kin san ruguza min plan za ki yi ki ja min asara
to tun wuri ki tattara ki tafi gidan Suwaiba bana son hauka, duk ba ke kika ja
mana wannan bala'i ba? da sa hannun ki fa abubuwan nan suka faru, ai wallahi
sati daya yayi ma yarinyar nan yawa a gidan nan in dai ni na haifi Abdallah,
don haka duk wanda bazai iya abinda nace yayi ba to ya bar gidan nan kawai kar
ya ja min asara" Aunty Karima tace "Toh Momy kar kuma fa yace zai
koma can gidansa da ita, kin san babu me sa shi babu me hanasa idan yayi niyyar
yin abu" Momy tace "Ku dai ku zuba min ido kawai ku ga ikon Allah,
ance maku ni mahaukaciya ce warce bata san abinda take yi ba irin ku? Ai ni ba
yarinya bace nasan me nake yi" Mikewa Momy tayi tana tafiya gansan gansan
ta nufi staircase, Meemah ta kyabe baki tace "Wallahi ji naki zuciyata
bazata iya wani pretending ba akan shegiyar yarinyar nan me kamar sadaka yalla,
ban taΙa jin tsanar mutum a duniya irin yanda na tsaneta ba, Abdul bai taΙa min
kalan tijaran da yayi min akan ta ba, kuma fa a gabanta yayi min haka tana ji
tana kallo" Aunty Karima ta sauke ajiyar zuciya tace "Nima ba gashi
yayi min ba Meemah, fatan mu kawai komai ya zo karshe cikin gaggawa, mu yi
yanda Momy tace kawai" Khaleesat ta dinga bin dakin da Abdul ya kawota da
kallo wanda babu tantama dakinsa ne, a hankali ta zauna saman kujeran dakin
tana kallonsa yana cire agogon wrist dinsa alamar zai shiga bandaki yayi
alwala, abinda aka yi mata a parlor ne kawai ke yawo a kanta, tayi nisa tunanin
da take yi sai gashi ya fito daga bandakin yana kallonta yace "Shiga kiyi
alwala" Sosai gabanta ya fadi ta daga kai tana kallonsa, ta dake tace
"Ai ban gama ba" Wani tsawan da ya gigitata ya daka mata, yana mata
wani mugun kallo yace "Kar ki raina min hankali, is it going to take u
forever to finish ur period? Karya kike yi kin gama" Tsabar yanda ta
tsorata jikinta har bari yake ta ma rasa me zata ce masa, yace "Idan na
dawo masallaci i will check for my self" Daga haka ya fice daga dakin
kamar zai tashi sama, hawaye ya fara zarya a idonta, wannan moment din take ta
tsoro gashi ya zo kuma babu yanda ta iya, shesshekan kuka ta fara yi cikin
tashin hankali, bayan ya fita da kamar minti biyu taji an bude kofar dakin, ta
juya da sauri gabanta na faduwa, Momy ce ta shigo dakin ta sakar mata murmushi
ta nufota tace "Ya sunanki daughter? Mu sai yace mana Khaleesat, ni dai
nace Khaleesat ai ba sunan yanka bane" Khaleesat ta sauke idonta zuciyarta
na bugawa a hankali tace "Sunana Hauwa" Momy tace "Maa sha
Allah, ashe uwata ce, welcome to the family my dear, taso mu je kiyi
sallah" Khaleesat felt a bit relieve da gesture din Momy toward her, ta
mike tsaye Momy ta kama hannunta suka fita daga dakin, can bangarenta ta tafi
da ita har cikin Bedroom dinta sannan ta nuna mata bandakin dake dakinta tace
"Ki shiga ciki kiyi alwala, amma kafin nan let's do a mother and daughter
talk first my dear" Khaleesat ta daga kai tana kallon Momy, Momy ta nuna
mata kan kujera tana mata murmushi tace "Get sitted Mamana" Khaleesat
ta zauna kan 2 seater dake dakin Momy ta zauna gefenta tana facing dinta tace
"Kar ki boye min komai mamata, ki daukeni tamkar mahaifiyarki, ki gaya min
gaskiya wani abu ya shiga tsakaninku da Abdul ne tun bayan da ya dauke
ki?" Sosai Khaleesat taji tambayar yayi mata nauyi a kai, hakan yasa ta
kasa kallon Momy ta sunkuyar da kanta kawai, Momy ta kwantar da murya tace
"Akwai dalilin da ya sa nake tambayarki haka ne Mamana, kar ki ji kunya ki
boye min komai, open up to me" Girgiza mata kai kawai Khaleesat tayi ba
tare da ta bari sun hada ido ba, Momy ta kamo hannunta tace "Kar fa ki ji
kunyata ki boye min komai mamana, gaskiya zaki gaya min" a hankali
Khaleesat tace "Gaskiya na gaya maki Momy" Momy ta dinga kallonta
kamar dai bata yarda ba, can tace "To saboda me? Anya kuwa gaskiya kike
gaya min Mamana?" Khaleesat bata dago kanta ba tace "Period nake yi
ne" Momy tace "Toh kin gama yanxu?" A hankali Khaleesat tace
"Daxu na gama" Momy ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "To
naji dadin jin hakan mamana, don nasan irin daukan da Abdul ya tafi ya maki
bayan dawowar ki daga makaranta, hakan bai ba iyayenki daman yi maki duk
abubuwan da ya kamata su maki ba a matsayinki na budurwa kafin ki tare gidan
mijinki, basu samu daman yi maki shirin xuwa gidan miji ba, amma tunda ya kawo
ki nan in sha Allah zan maki duk abinda ya kamata diyata...." Ita dai
Khaleesat tayi shiru har sannan bata dago kanta ba, Momy ta mike tace "Ta
shi mu je bandaki ki ga...." Khaleesat ta mike tsaye ta bi bayan Momy har
zuwa bandakinta, Momy ta nuna mata wani babban flask tace "Kin ga wannan
flask din? To zaki dinga tsiyayan ruwan ciki ki sirka da ruwan zafi a pampo ki
dinga tsarki da shi" Momy ta dauko wasu Ιakakken sabulai dake nannade a
leda ta mika mata tace "Sabulan nan su ma tsarki zaki dinga yi da ko
wannensu, in kin yi sai ki ajiyesa inda kika ga na dauko yanzu don naki
ne" Momy ta nuna mata wani roba dake rufe a bandakin shi ma tace "Wannan
ma diba zaki yi kiyi tsarki da shi, kin ji?" A hankali Khaleesat tace
"Toh Momy" Momy ta dauko wani kwalba dake boye a cikin bandakin,
Khaleesat dai bin ta kawai take da kallo ta bude flask din ta tuttule abinda ke
cikin kwalban, sannan ta mike tace "Yauwa mamana, duk ki tabbatar kinyi
amfani da su yanda nace, sai kiyi alwala ki fito" A hankali Khaleesat tace
"Toh Momy" Daga haka Momy ta fito daga bandakinta ta shimfida ma
Khaleesat darduma, sannan ta zaune kan kujera ta jirata har ta fito daga
bandakin, Momy ta mike ta nuna mata darduman tace "In kin idar da sallan
kar ki fito, kiyi zamanki zan kawo maki abinci" Khaleesat tace "To
Momy" Daga haka Momy ta fita daga dakin ta kulle da key ta tafi da
makullin tana Ιan murmushi, a corridor ta hadu da Abdul ya taho daga dakinsa
bayan ya shiga bai ga Khaleesat a ciki ba, Momy tace "Har ka dawo
masallacin Babana?" Yace "Na dawo, tana ina ne Momy?" Momy ta ja
kunnensa tace "Yanxu abinda kayi ma yayarka ya kamata Babana? Kasan ta fa
wani lokacin ba hankali ya ishi yayar taka ba, da sai kayi hakuri ka kyaleta da
halinta kawai" Ya hade rai yace "Dukanta fa take kokarin yi Momy? A
ina ta san ta ko kuma me tayi mata da zata zageta kuma ta nemi ta
doketa??" Momy ta kama hannunsa suka shiga dakin baΖin dake kusa da su
tana kallonsa tace "Ai na mata fada sosai Babana, yanxu ma haushin abinda
kayi mata ne yasa tayi abinda tayi a parlor amma kayi hakuri kaji Babana"
Yace "Naji, ina Khaleesat din take?" Momy tace "Bazan fa baka
matar ka ba sai zuwa jibi in ma zaka cire ido a kanta ka cire, tun da baka bari
iyayenta sun gyarata yanda ya kamata ba to ni zan gyarata" With confusion
Abdul yace "Gyarata kamar yaya Momy?" Momy tace "Ka taΙa ganin
inda aka dau mace budurwa aka kai ta gidan miji haka nan? To fin karfin
iyayenta da kayi kuma suna shakkar ka shi yasa suka baka ita haka babu yanda
suka iya maka, amma a al'adar mu ta Hausa babu inda ake yin haka, ni kuma kaga
bazan baka ita ba sai nayi mata duk abinda ya kamata na gyarata, in kuma rashin
kunya zaka yi min to yi Babana, Khaleesah dai bazan baka ita ba sai zuwa nan da
jibi in sha Allah, zan mata duk abinda ya kamata a matsayin ta na 'ya ta"
Abdul ya kasa cewa komai yana kallon Momynsa, Momy tace "Mu je ka ci
abinci" Bata jira cewarsa ba ta fita daga dakin, bin bayanta yayi ya fita
amma duk tsaurin idonsa sai yaji nauyin ce ma uwar tasa komai, haka nan Momy ta
dauko masa abincinsa da ta hada masa da kanta ta jera masa su a dinning sannan
ta koma kitchen zata hada abincin Khaleesat, Abdul ya zauna kujeran dining amma
ya kasa cin abincin, shi fa bai yi niyyar ma kwana gidan da Khaleesat ba don
irin burin da ya ci a kanta yau ai sai Allah, nan da nan yaji ransa ya baci, ya
mike ya shiga kitchen ya samu Momy ta sa mai aikinta ta jera ma Khaleesat
abinci a tray, don irin abin da ta hada mata har ya fi na Abdul, Momy na kallon
mai aikin tace "Tafi ki kai mata bangarena ki jirani ina zuwa" Mai
aikin ta fita daga kitchen din da tray din, Abdul na kallon Momy a fusace yace
"Toh wai menene yasa Meemah zata ce min Daddy ba shi da lafiya critically
bayan ma ashe baya kasar?" Momy tace "To ai ganin likita yaje a
Amurka, ko bai gaya maka bane? Karfe hudu na yamma jirginsu ya tashi, shi yasa
kaji nake cewa baka taho da wuri ba don duk zatona zaka tarar da shi"
Abdul yayi shiru yana kallon Momy, Momy tace "Ni dai bari in je wajen
diyata, kar ka wani huce kan Meemah don ba ita ta hanaka matarka ba" Daga
haka Momy ta bar sa tsaye a kitchen din, tsaye ta tarar da Mai aikinta a
bangarenta tana jiranta don kofar a kulle yake, Momy ta bude mata suka shiga
ciki, Mai aikin ta ajiye abincin gaban Khaleesat, Momy na kallon mai aikin
wanda ranan ne ranan farkon da ta shigo mata daki tace "Toh fita ki ban
waje...." Mai aikin ta fita da sauri ta kullo kofar, Momy tayi murmushi
tana kallon Khaleesat tace "Ga abinci nan Mamata" Momy ta tafi ta
dauko handbag dinta ciro wani kulli ta dawo kusa da Khaleesat ta bude kullin ta
barbada mata abinda ke ciki a farfesun kayan cikin dake cike a bowl tace
"Maza ki shanye har romon kin ji" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata,
Momy ta tafi ta zauna kan kujera tana murmushi ta dau remote ta kunna TV din
dakin, a hankali Khaleesat ke shan farfesun tunani iri iri na yawo a kanta, to
yanxu kenan hakuri kawai zata yi da auren Abdul, since gaba daya family dinta
sun nuna sun yi accepting auren, sannan ga Mum dinsa ma ta ga tana sonta, kilan
zaman aure da Abdul a kaddarar rayuwarta yake, she should just accept it with
good faith, most important of all gashi mahaifiyarsa na sonta, his sister won't
be an issue tunda mamansa na sonta, kawai ta saka ma ranta salama ta amshi
auren tunda haka Allah ya kaddara mata, Housemate dinta ne ya fado mata, lkci
daya taji hawaye ya cika idonta, da sauri ta sunkuyar da kai kar Momy ta gani
cikin dubura ta dinga goge hawayen tana jin wasu masu zafi na sakkowa, sai da
Momy ta tabbatar ta ci abincin sosai, sannan ta umarceta da taje tayi wanka ta
tabbatar ta sake tsarki da duk abubuwan da ta nuna mata a bandaki, kafin
Khaleesat ta fito Momy ta dauko mata kayan bacci da inner wears, Khaleesat ta
shirya tayi sallan isha'i, Momy bata tashi barin dakin ba sai kusan karfe tara
da rabi, bayan ta sa Khaleesat ta kwanta kan gadonta sannan ta kashe mata wutan
dakin ta bata remote din Ac a kusa da ita, tayi mata sai da safe ta fita daga
dakin, har ta kulle kofar ta sake budewa ta shiga tana kallon Khaleesat tace
"Ko tashi kika yi zaki kama ruwa cikin dare kiyi tsarki da abubuwan nan fa
Mamana kar ki manta" Khaleesat tace "Toh Momy" Momy ta kara mata
sai da safe sannan ta fita ta kulle kofar da makulli ta sauka downstairs, Abdul
kadai ne zaune parlor yana kallon kwallo amma kana ganinsa kasan ransa a bace
yake, Momy tana kallonsa tace "Sai da safe Babana" Ciki ciki ya amsa
mata, ta juya ta koma sama zuwa dakin da su Meemah suke, duk suka dinga kallon
Momy bayan ta shigo, Aunty Karima tace "Ya dai Momy duk ta yi?" Momy
tayi wani murmushi tace "Tun yaushe kuma" Meemah tace
"Alhamdulillahi, shi Abdul din fa?" Momy tace "Shi ai dama a
miyar shinkafa aka ce na zuba masa maganin, sai ruwan lipton, na kori mai aikin
taje bakin pampo tayi wanke wanke shine na samu duk na zuba masa nasa"
Meemah tayi murmushin mugunta tana gyara zama sanin Momy bata bin malaman
banza, kai in malami yace zai amshi kasa da 1M a wajenta ma bata yarda da
ingancin aikinsa ba, inda ake aikin da gaske take zuwa, ko da kuwa miliyan
biyar zata kashe bata kyashi don tasan aiki na gaske ake mata.
[6/19, 8:55 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Washegari da
safe bayan Khaleesat ta shirya cikin tsadadden Abayan da Momy ta bata, Momy ta
gama hada mata shayin da take yi cikin cup tace "To zo kiyi breakfast din
kar ya huce Mamana" Khaleesat bata ce komai ba ta karasa ta zauna kan
darduman da aka jera mata breakfast din, Momy tayi murmushi tace "Idan
farfesun bai isheki ba sai ki bude warmer ki Ζara, dankalin ma akwai saura a
warmer in bai ishe ki ba" Ita dai Khaleesat kai kawai ta gyada mata, tana
juya shayin gabanta a hankali da spoon din ciki, Momy ta koma kan kujera ta
zauna tana kallonta tace "Duk da ma ina lura jiya baki wani ci abincin da
aka kawo maki da yawa ba, ko maganin cin abinci zan sa a samo maki mamana"
Khaleesat tayi murmushin karfin hali bata dai ce komai ba ta dau shayin tana
kallon ciki, sai tayi tunanin lipton din ne kilan ya fashe a cikin ruwan
shayin, sipping din shayin tayi kadan ta ajiye sannan ta fara cin irish din,
Momy dai kallonta kawai take kasa kasa, Bude kofar dakin aka yi Momy ta juya,
ganin Abdul tace "Sai yanxu ka tashi Babana" Bai ce mata komai ba ya
karasa ya zauna saman kujera, Khaleesat ta Ιan kallesa taga kallonta yake,
sauke idonta tayi a hankali tace "Ina kwana" Ya kauda kai yace
"Lafiya" Momy tace "Ka tashi kaje kayi breakfast din ka"
Yace "Momy za mu je shopping ne, bata zo da kaya ko daya ba" Momy na
kallonsa tace "To wanda ka gani a jikinta yanxu kai ka siyo mata?"
Shiru Abdul yayi yana kallon Momy, Momy tace "To har na tura ma Meemah
kudi su je su yi mata siyayya ita da Karima tunda kai baka da Ζara" Mikewa
Abdul yayi ya nufi kofa ya fice daga dakin, Momy ta bi sa da kallon gefen ido,
sai da Momy taga Khaleesat ta gama cin abinda zata ci na breakfast din sannan
ta mike ta fita ta kira mai aikinta ta fitar da sauran abubuwan da Khaleesat ta
rage, bayan mai aikin ta fita Momy ta bude bayan labulenta ta dauko wani
karamin jarka ta kawo ma Khaleesat tace "Wannan tsumi ne Mamana, daga
yanxu har zuwa dare nake son ki shanyesa gaba daya" Ita dai Khaleesat
kallon jarkan take, Momy tace "Kin ji ai ko?" Khaleesat ta gyada mata
kai tace "Toh Momy" Momy ta dauka ta mayar bayan labule sannan tace
"In zaki yi kallo sai ki kunna TV abun ki, bari in je zanyi bakuwa ban san
ko ta iso ba" Khaleesat tace "Toh" Momy ta fita daga dakin ta
kulle da makulli tana rike da makullin ta sauka downstairs don aminiyarta
godiya ta kirata ta sanar mata tana hanya, tana shigowa parlor taga Abdul zaune
dinning area da breakfast din da Khaleesat ta rage a gabansa, da karfi Momy ta
kwala masa kira, ya juya yana kallonta, ta karasa wajen da mugun sauri tace
"Banda abun ka ba ga naka a kitchen ba Abdul me zaka yi da wanda aka rage?
Ko har kaci wannan din ne?" Abdul dake kallonta yace "Ban ci ba, amma
menene idan na ci?" Momy ta kwalo ma mai aikinta kira, Mai aikin ta taho
da sauri Momy ta kunduma mata wani ashar tace "Nan nace ki ajiye sauran
abincin er iska kawai er neman jidali? Me yasa ke dakikiya ce? Wallahi zan kore
ki fa a gidana na gaji da maganar da kike sa ni kamar kanwar uwarki, yau ga
shegiyar mata kawai" Abdul ya kalli Momy yace "Ni fa nace ta kawo min
nan, beside what is wrong with the food da bazan ci ba?" Momy ta mata
tsawa tace "Dauka ki wuce ki ban waje guntuwar banza kawai" Mai aikin
na ba Momy hakuri ta dauke jiki na rawa ta tafi kitchen da breakfast din, Momy
ta kalli Abdul dake kallonta, yace "I want to understand meye da abincin
da bazan ci ba Momy?" A takaice Momy tace "Kayan gyaran mata mana? Ko
kai na mace ne?" Bata jira cewarsa ba ta bar wajen ta shige kitchen ya bi
ta da kallo, Tuttular da shayin tayi a sink sannan ta juye sauran irish din da
kwai da farfesun duk ta cakudesu waje daya tace "Gasu nan ki kai ma
karnuka, in kuma kwadayin ki ya ja ki kika ci ke kika jiyo" Mai aikin ta
risina ta amsa tace "Toh Hajiya" Sai da Momy ta jirata har ta dawo
bayan ta kai ma karnukan can cage dinsu sannan Momy ta dau breakfast din Abdul
ta kai masa kan dining din tace "Ga naka nan" Daga haka ta juya ta bar wajen, dai dai
shigowar Godiya gidan, da fara'a Momy ke mata sannu da zuwa Abdul ya dauke kai
kamar bai ganta ba don ya tsani matar with passion, tun asali dama baya gaida
ta, Haka Momy ta ja ta zuwa sama tana cewa "Mu je ki ga surkar tawa ku
gaisa" Da ido Abdul ya bi su har suka haura sama, Momy na isa kofar
dakinta ta bude da makulli suka shiga, Khaleesat dake gyara gadon Momy ta mike
tsaye tana kallonsu, Momy na murmushi ta kalli godiya tace "Kin
ganta" Da fara'a sosai Godiya tace "Maa sha Allah, ai ko ga ta kamar
balarabiya Maa sha Allah, sannu amarya, ya sunanki?" Momy na murmushi tace
"Sunan Baabata gareta, Hauwa sunanta" Khaleesat ta zame kasa ta sauke
idonta ta gaida Godiya, Godiya ta karasa kusa da ita ta dafata tare da Ιagota
ta zaunar da ita gefen gadon Momy tace "Lafiya lau diyata, ya
bakunta?" Khaleesat bata ce komai ba kuma bata dago kanta ba, Momy na
kallon Khaleesat tace "Kin sha tsumin da nace ki sha kuwa?" Khaleesat
ta gyada mata kai tace "Na sha" Momy tace "To maa sha Allah,
Allah ya maki albarka Mamana, zuwa anjima sai ki kara sha kin ji"
Khaleesat tace "To" Bayan few minutes Momy da Godiya suka fita dakin,
Momy ta sake kulle kofar da makulli sannan ta cire makullin suka tafi wani daki
dake sama, bayan sun shiga Momy ta kulle kofar tana kallon Godiya tayi murmushi
tace "Duk tayi amfani da abubuwan babu gardama godiya, iya na jarkan nan
ne kawai ya rage yanzu" Godiya ta zauna gefen gado tace "To madallah,
shi ma Abdul din duk kinyi yanda aka ce kiyi da na sa?" Momy tace
"Kwarai kuwa" Godiya tayi wani murmushi ta bude handbag dinta ta ciro
wani babban laya bakikirin da shi ga er karamar kwado a jiki ta mika ma Momy
tace "To aikin karshe kenan wannan Hajiya, Malam ya ce ki samu inda kika
san baza a taΙa tono sa ba ki binne a cikin gidan nan" Momy ta zauna
gefenta tana murmushi ta amshi layan tace "To laya nawa na binne gidan nan
ba a tono ba godiya, ai wannan karamin aiki ne a wajena don ba sabon abu
bane" Godiya tace "Yauwa, bayan kin binne Malam yace ki basa yarinyar
kawai, wallahi yace min in har ta wuce sati biyu Abdul bai rabu da ita ba to
bazata wuce sati biyar ba a gidansa" Fara'ar fuskar Momy ya bace tace
"Har sati biyar Godiya? Ni da yace min sati daya kacal a waya" Godiya
tace "Halan bai gaya maki irin abubuwan dake Ζan dan ki bane? Da yaya ma
aka samo kansa har asirin nan yayi tasiri? Ai abubuwan Ζan Abdul sun fi karfin
wani asirin wallahi kiji in gaya maki" Momy ta sauke ajiyar zuciya tace
"An taΙa gaya min haka da dadewa wallahi, don ni akwai malamin da yace min
ma yanda asiri ke cin ubansa shi sai an wahala asiri zai ci sa" Godiya
tace "To wallahi Malam sai da ya tura masa aljanu don ma ki ji Hajiya,
aikin nan sai da Malam ya hada da wasu malaman don aiki ne me wahalan gaske
yace min wallahi" Momy tace "To ni fargabana kada fa in mika masa
yarinya ace asirin nan bai ci ba abinda muke gudu ya afku mu shiga uku Godiya"
Godiya tace "Sai kace yau Malam ya fara maki aiki? Ai da aikin bai yi ba
kinsan bazai boye mana ba, sai dai ya kara mana lokaci yayi wani sabon aikin
fa, dama yace in na yarinyar ya ci shine zai sa na Abdul din ma yayi tasiri
sosai" Momy tace "Haka ya ce kam" Godiya tace "Don haka
zuwa gobe ki basa ita kawai su tafi an gama aiki sai jiran result, kuma ina me
tabbatar maki zaki sha mamaki" Momy na murmushi tace "Toh shikenan
godiya, nagode sosai, zan tura masa cikon dubu dari biyar dinsa anjima" Da
yammacin ranan bayan Momy taga Abdul ya fita gidan tayi maza ta aiki mai
aikinta kasuwa saboda tayi amfani da daman ta haΖa rami a garden din gidan ta
binne layan da Godiya ta kawo mata, bayan mai aikin ta tafi Momy ta zaga zuwa
garden din gidan ta samu spot me kyau ta fara haΖa rami da wuka, bayan ta haka
yayi zurfi yanda take so sannan ta jefa layan ta mayar da Ζasan wajen ta dau
wani dutse ta dora dai dai wajen don kada a ga alamar an tono kasa, tap ta bude
don wanke hannunta da wuΖan da tayi using, Khaleesat ta karasa bakin window din
dakin Momy jin Ζaran bude ruwan pampo, in ta gaji da zaman dakin dama jikin
window take zuwa ta tsaya tana kallon waje, ta tsaya jikin window din tana ta
kallon Momy dake ta wanke hannunta bayan ta wanke wuΖan, bayan ta gama ta kara
komawa kusa da dutsen tana seta sa da kyau ta yanda ko da wasa baza a ga
tonannen Ζasa ba, sai kuma ta mike ta fara tsinko doddoya dake Garden din,
sannan tayi using wuΖan hannunta ta yanki pumpkin leaves isasshe bayan ta gama
ta bar garden din tana rike da ganyayyakin hannunta, babu abinda Khaleesat ta
kawo a kai don tunaninta ganye Momy taje diba a garden din, Momy na kai
ganyayyakin kitchen sai ga su Meemah sun dawo daga shopping din da ta aikesu su
yi ma Khaleesat, dariya Momy ta dinga yi a parlor ganin wasu shegun abayoyi
masu saukin kudi da suka kwaso ma Khaleesat irin wanda ake dinkawa a kano, ga
wasu shegun dogayen riguna su ma masu arha, hatta inner wears da suka siyo duk
very low quality ones ne, babu wani abu na arziki da suka siyo ma Khaleesat,
Momy na ci gaba da dariya tace "Duk maida su cikin ledojin kawai na yafe
ganin wannan tarkace haka karima, amma baku da kirki yaran nan" Aunty
Karima na dariya ta maida kayan cikin leda ta kulle tace "Su ne dai dai er
talakawa ai Momy, da so kika yi ki ga abayan dubu hamsin zuwa sama? Ai ita
Meemah ma en gwanjo ta so mu je muyi selecting mata kawai" Dariya kawai
Momy take, ita kuwa Meemah danna wayarta kawai take don duk wani abu da ya
shafi Khaleesat ko kadan baya bata dariya, she just can't wait taga irin rabuwan
da Abdul zai yi da Khaleesat don shine babban abinda ke gabanta yanxu. Wajen
karfe takwas da rabi Momy na zaune parlor da Abdul tana ta yi masa hira, shi
dai wayarsa kawai yake dannawa baya responding kamar ma bai san me take cewa
ba, Momy ta kwalo ma mai aikinta kira, Mai aikin ta taho da gudu tace
"Na'am Hajiya?" Momy tace "Zaki ga Kankana da na yanka a kitchen
ki dauko ki kai ma Mamata a sama"
Mai aikin tace "To Hajiya" Juyawa tayi ta koma kitchen sai ga
ta ta dawo rike da bowl din kankanan tana kallon Momy cikin ladabi tace
"Amma Hajiya dakin a kulle yake" Momy tace "A'a a bude yake tun
daxu, ki je ki kai mata" Bayan mai aikin ta tafi ta kai water melon din ta
dawo ta tafi kitchen ta ci gaba da aikin da take, Momy ta dau wayarta tace
"Bari in inyi waya da Alhaji, daxu na ga kiransa ina kitchen wallahi"
Shi dai Abdul bai ce mata komai ba har ta shiga dakin dake downstairs ya bi ta
da kallo... Bayan minti biyu ya mike ya nufi stairs direct ya tafi bangaren
Momy, yana bude kofar dakin Khaleesat dake zaune saman darduma bayan ta idar da
sallah ta gama duk addu'o'in da zata yi ta juya ta kalli kofar, sosai gabanta
ya fadi bayan sun hada ido da Abdul, ya karasa cikin dakin babu yabo babu
fallasa yace "Ta shi mu je shopping...." Khaleesat da gabanta ke
faduwa ta nuna masa ledan da Momy ta kawo mata daxu duk da bata duba kayan ciki
ba cikin sanyin murya tace "Ai Momy ta sa an min shopping din, ka gan su
can ma" Ya hade rai yace "Kee... Get up nace, i am not asking for ur
opinion" Ta sauke idonta ta mike tsaye da kyar ta dauke darduman tana
linkewa, sosai taji hankalinta ya tashi, a ranta ta dinga addu'an Allah ya kawo
Momy dakin immediately, fixge darduman hannunta yayi ganin it's taking her a
whole eternity to fold, ya ajiyesa saman kujera sannan ya kama hannunta suka nufi
kofa fuskarsa a daure suka fita daga dakin, Khaleesat dai bin sa kawai take a
tsorace, downstairs suka sauka har sannan yana rike da hannunta, babu kowa a
parlorn sai mai aiki dake goge goge a dining area, ya dau makullin motarsa da
ya bari kan center table, Khaleesat ta marairaice masa cikin rawan murya tace
"Ya Abdul Momy fa bata sani ba, kar ta shiga dakinta taga bana nan, kaga
babu dadi haka" Wani kallon da yayi mata yasa tayi shiru zuciyarta na
bugawa, bata sake gigin ce masa komai ba har suka fita parlorn gidan zuwa
parking space, Khaleesat taji hawaye ya cika idonta bayan ya sa ta shiga
motarsa ya shiga driver seat, mai gadi ya bude masa gate ya fice gidan da
motar. Momy ta fito parlor tana kallon Mai aikinta tace "Naji kamar fitar
mota, waye ya fita?" mai aikin tace "Alhaji karami ne ya fita"
Momy tace "Shi da wa?" Mai aikin tace "Shi da matarsa"
Shiru Momy tayi don bata yi tunanin zai ce zai tafi da Khaleesat yau ba, don so
tayi taga yanda za su kwashe, shi yasa ma ta basa hint din dakinta a bude yake,
ta zata can din kawai zai bi ta ko kuma ya kai ta dakinsa, Momy ta sauke ajiyar
zuciya, ganin mai aikinta sai kallonta take ta hade rai tace "Lafiya kike
kallona haka munafuka?" Da sauri mai aikin ta juya ta bar wajen, Momy ta
juya ta koma daki amma fa zuciyarta ya kasa nutsuwa sam sam, gani take kamar
Abdul zai yi tarayya da Khaleesat, duk da malaminta bai taΙa mata aiki bata ga
result me kyau ba amma a wnn case din sai take Ιari Ιari kada abinda suke gudu
yaje ya afku dama ga Godiya tace aikin me wahala ne, ai kuwa da ta shiga uku ta
lalace, number Godiya tayi dialing ta zauna gefen gado tana jiran tayi picking.
Hawaye kawai Khaleesat take tana dafa shayin da Abdul ya sa ta dafo masa a
kitchen, ita ta ma riga tayi give up yau don bata da wani dubaran da ya rage
mata in ba so take ta fusata Abdul ya doketa ba, she will just accept her kadr
with good faith, gwara tayi accepting dinsa kawai a mijinta tunda haka Allah ya
kaddara mata, goge hawayenta tayi tana tafiya a hankali ta tafi kai masa lipton
din dakinsa, tana bude kofar ya ajiye wayar hannunsa yana kallonta, kanta a
kasa ta karasa har inda yake ta duka ta ajiye masa black tea din, ta mike zata
bar wajen ya jawota ya zaunar da ita gefensa yana kallonta, ita dai bata bari
sun hada ido ba zuciyarta na wani irin bugawa, ya dago kanta suka hada ido,
sauke rigar baccin jikinta yayi slowly yana kallonta babu ko kiftawa, ta
sunkuyar da kanta bugun zuciyarta ya tsananta sosai, tana ji tana gani ya cire
duk abinda ke jikinta yana kare ma each and every part of her body kallo, bata
sake yarda sun hada ido ba, a hankali ya kwantar da ita, ta runtse idonta da
sauri jikinta na rawa ganin inda yake kokarin kai bakinsa, after some seconds
Khaleesat ta bude idonta a hankali tana kallonsa jin bai yi abinda yayi niyya
ba, taga wani wajen daban yake kallo babu ko kiftawa, after some seconds ta ga
ya mike ya nufi kofa ya bude, fuska daure yake kallonta babu yabo babu fallasa
yace "I need my privacy....." Khaleesat ta mike zaune da kyar tana
kallonsa, lokaci daya jikinta yayi sanyi, ta jawo Hijab dinta da ya cire tun
zuwansu gidan ta saka sannan ta dau kayan baccinta ta nufi kofa, bata bari ta
hada ido da shi ba ta fita daga dakin taji ya kulle kofar da makulli, juyawa
Khaleesat tayi tana kallon kofar.....
[6/20, 7:35 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Da Asuba
Khaleesat na zaune kan gado ta dafe kanta da yayi mata nauyi sosai, tun karfe
uku da rabi bacci ya kaurace mata, bayan tayi sallahn nafila ta kai ma Allah
kukanta shine take ta zaune saman gado tana tunanin rayuwarta, in 3 weeks time
za su yi resuming school wanda shekarar su na karshe kenan za su shiga a
makarantar but unfortunately tasan baza a koma da ita ba, ko kadan bata saka
ran zata koma John Hopkins ba dama, but it's really hurtful don duk shekarun da
tayi a makaranta zai tashi a banza kenan, ta goge hawayen da ya gangaro mata
jin ana kiran sallan asuba ta sauka daga saman gadon, sai da ta dafa bango sbda
juya mata da kanta ke yi, tun da ta tashi daxu take jin jikinta kamar ba ita
ba, she can't even understand how she is feeling, sai da ta koma ta zauna na
yan mintuna sannan ta tashi tana tafiya slowly ta wuce bandaki, wanke bakinta
tayi sannan ta dauro alwala ta fito daga bandakin, bayan ta idar da raka'atanil
fajr tayi sallan asuba, har karfe bakwai na safe Khaleesat na zaune kan darduma
duk da ta idar da azkar din ta, in tayi wannan tunanin tayi wancan a haka dai
har ta mike daga karshe tana tafiya a hankali ta nufi kofa ta bude ta fita daga
dakin, bata karasa parlon ba ta tsaya tana kallon Abdul dake kwance saman 3
seater idonsa a lumshe yana sauraron karatun qur'ani ta wayarsa dake gefensa,
duk tunaninta bacci yake ganin yanda ya lumshe ido, har zata juya ta koma
dakinta taga ya bude ido yana kallonta, ta sauke idonta ta karasa cikin parlon
tana tafiya a hankali ta duka kusa da shi cikin sanyin murya tace "Ina
kwana" Yace "Lafiya" Bata sake cewa komai ba kanta a kasa, after
some seconds ta mike zata bar wajen, calmly yace "I need breakfast, ban ci
abinci da daddare ba" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tace
"Toh...." Juyawa tayi ta nufi kitchen don ganin me zata girka, doya
da kwai tayi deciding tayi don shi tagani available a kitchen din, wajen karfe
takwas ta gama komai ta kai har gabansa a parlon ta durkusa ta ajiye, ganin
bread a kan dining table ta mike ta tafi ta dauko sannan ta dawo ta ajiye masa
tana kallonsa a hankali tace "Gashi na gama, in hada maka shayin?"
Without looking at her yana danna wayarsa daga kwancen da yake yace
"Ohk" Hada shayin tayi bayan ta gama ta koma gefe tana kallonsa a
hankali tace "Na gama" Ajiye wayarsa yayi ya sauko daga saman
kujeran, shayin ya dauka yana sha, ba tare da ya kalleta ba yace "Ke ina
naki shayin?" Shiru tayi bata ce komai ba, jin tayi shiru ya daga kai ya
kalleta, sunkuyar da kanta tayi, sai kuma ta mike ta nufi kitchen, ba a dau
lokaci ba sai ga ta ta dawo da cup da tea spoon, ta duka kasa ta fara hada
shayin nata, ya kalli madaran da ta zuba a shayinta ya dau wani spoon ya kara
mata madaran, ita dai bata bari sun hada ido ba, a plate daya ya dibar masu doyan
ya fara ci, ita dai juya shayinta kawai take a hankali, after some minutes
ganin bata fara cin doyan ba ya daga kai ya kalleta yace "Ko a baki za a
baki?" Ta Ιan yi murmushin karfin hali ta dau fork ta fara cin doyan a
hankali, da ta kallesa sai su hada ido, kana ganinta kasan she is not
comfortable a wajen don ya riga ya sa mata tsoronsa a zuciya, daga karshe ta
ajiye fork din hannunta a kan tray, ya daga kai ya kalleta, a hankali tace
"Na koshi" Bai ce mata komai ba, ta koma gefe tana shan shayinta
slowly, after a while Abdul ya mike ya koma saman kujera, ta tashi ta dau
sauran abincin ta kai kitchen, sai da ta wanke utensils da suka yi using sannan
ta fito daga kitchen din, magana take son yi masa amma tana tsoro, ya kalleta
tayi saurin sunkuyar da kai kamar munafuka tana wasa da yatsunta, yace "Me
ya faru?" Ta karasa ta duka daga gefensa a hankali tace "Dama pls ina
son zan yi magana da Safiyyah, ka taimaka ka kira min ita ta wayarka" A
takaice yace "Bazan kirata ba, kanwar baabarki ce Safiyyar?" Sosai
jikin Khaleesat yayi sanyi, ta sunkuyar da kanta tayi shiru bata ce komai ba,
yace "Tafi ki bani waje" A hankali ta mike a sanyaye ta wuce dakinta,
goge hawayen da ya taru idonta tayi ta zauna gefen gado, after a while ta share
hawayen da ya ki tsaya mata ta mike ta cire hijab din jikinta ta linke ta ajiye
sannan ta shiga bandaki, brush tayi sannan tayi wanka, ganin abubuwan wanke
gashi a bathroom din ta wanke gashinta ta tsane da karamin towel sannan ta dau
wani towel din ta daura ta fito, tana
tsaye gaban madubi tana shafa man gashi taji an bude kofar dakin, da sauri ta
juya gabanta ya fadi sosai ganinsa, kana ganinsa kasan daga wanka ya fito shi
ma, cikin dubara ta gyara daurin towel dinta tana jin zuciyarta na bugawa ta ci
gaba da oiling gashinta, ya karaso har inda take tsaye ya tsaya a bayanta yana
kallonta ta madubi, ita dai ta kasa dago idonta tana jin saukan numfashinsa a
bayanta, ta ajiye oil din hannunta a hankali don duk ta daburce, shi dai yana
tsaye dab da ita yana kallonta ta madubi, ya kai hannu zai yi loosening din
towel din kirjinta, juyowa take son yi da sauri kamar zata yi kuka cause bazata
iya ganin kanta ta madubi a yanda yake ganinta ba, yaki barin ta juyo hakan
yasa ta runtse idonta zuciyarta na bugawa, bai fasa kallonta ta madubin ba har
ya cire towel din jikinta ya jefar saman gado, he kept his eyes glued to her
cause he just can't stop admiring her bare body any time he set his eyes on
her, gaba daya taki yarda ta bude idonta, bata ankara ba kawai sai jin su tayi
a saman gado, bata san sanda ta bude ido ba ta fashe da kuka tana turasa a
tsorace ganin yau kai tsaye kawai far mata yake kokarin yi babu bata lokaci,
ita kanta bata san inda ta samu courage din turasa ba duk da tsoronsa da take,
da mamaki yake kallonta yana sauke numfashi, ganin kiciniyar sauka take yi daga
saman gadon tana kuka, cikin kakkausan murya yace "I will give u a dirty
slap" Danneta yayi yanda ko motsin kirki bazata iya ba balle tace zata
sauka daga saman gadon, ta dinga masa kururuwa tana kokarin kwatar kanta don
bata taΙa tsorata ta gigice da lamarin nan ba irin yau, duk yanda Abdul ya so
cimma burinsa a wnn moment din hakan ya faskara, kawai ya tuna ita ba irin
matan da ya saba mu'amala dasu bane, he couldn't have his way no matter how
hard he tried, he was so confuse as at how intact she is even though he knows
she is a virgin, hakan yasa ya fara romancing dinta roughly to make his way
more slickier, cause he was determined in fulfilling his mission today, wani
wawan marin da yayi resetting dinta back to default ya sauketa mata don duk da
yanda ya danneta she is still struggling so hard to free her self under him,
Khaleesat taji kamar numfashinta na yi mata gardama, at this moment tasan babu
me kwatar ta hannunsa sai Allah, she was so weak and in severe pain hakan bai
hanata struggling ba cikin kuka take cewa "Don girman Allah ka rufa min
asiri Abdul, wallahi mutuwa zan yi bazan iya ba, it's soo painful...." Ya
kara sauke mata wani marin cause he is seriously trying to find his way by all
means, Gaba daya Abdul komawa yayi kamar bai taΙa tarayya da mace ba a wnn
lkcn, ya koma kamar Amateur da ta mance inda zai bi, duk wani dubaransa was
fortile, he was really frustrated and vexed, Ganin how helpless she was ga
numfashinta na neman daukewa ya rungumeta gam jikinsa yana kallon fuskarta da
tafin hannunsa ya kwanta ta dalilin marin da yayi mata, lumshe ido yayi yana
sauke numfashi kamar wanda yayi tsere, saukan hawayenta ya dinga ji a kirjinsa
ya lumshe idonsa zuciyarsa na bugawa, after almost a minute yayi kasa da murya
da kyar, yana shafa dogon gashinta yace "I am sorry Khaleesat, i am
sorry" Ita dai hawaye kawai take tana sauke ajiyar zuciya, tana jin wani
azaba in between her, they were like this for almost 5 mins, Abdul ya saketa ya
koma can karshen gadon ya dafe kansa dake sara masa, ga wani azababben ciwon
mara da yake ji, da kyar ya mike ya dafa bango na Ιan lokaci kafin ya nufi kofa
ya fice daga dakin, Khaleesat ta takure cikin duvet tana sauke ajiyar zuciya
hawaye wasu na bin wani a idonta, bata san lkcn da baccin wahala ya dauketa ba
a haka. Karfe sha biyu saura taji hannu a forehead dinta, bude idonta da suka
kumbura tayi a hankali don sosai kanta yayi mata nauyi, suna hada ido ta sauke
idonta, Calmly yace "Ta shi ki shirya mu tafi shopping" Da kyar ta
mike zaune tana kara rufe jikinta da duvet, sai kuma ta fara jawo towel din da
ya cire mata daxu, shi dai bai ce mata komai ba yana kallonta, har cikin ransa
he felt bad ganin yatsunsa kwance a fuskarta, cikin dubara ta daura towel din
sannan ta mike tsaye lkci daya ta duka kasa da sauri tana runtse ido, yana
kallonta yace "What?" Lokaci daya hawaye ya idonta, cikin rawan murya
tace "Bazan iya ba, zafi nake ji sosai" Ya hade rai yace "Zafin
me?" Ta kasa kallonsa hawaye na sauka idonta, yace "Me na maki da za
ki ji zafi?" Ita dai bata dago kanta ba gabanta na faduwa, mikewa yayi ya
fice daga dakin ta bi sa da kallo, after a while Khaleesat taji fitar motar sa
a gidan, ba karamin daurewa Khaleesat tayi ba ta tafi bandaki, sai da tayi sit
bath sosai sannan taji ta samu sukuni, tayi wanka ta dauro alwala ta fito.
Karfe biyu saura tana tafiya a hankali tana dingishi ta fito parlor, ledan
kayan da Momy ta bata ta gani a parlon, ta karasa ta bude ledan sai a sannan
taga irin kayan da su Meemah suka siyo mata, a hankali ta daure ledan ta dau
kayan walking slowly ta koma dakinta da su ta ajiye ta dawo parlon ta tafi
kitchen don daura girki... Momy dake zaune parlor tana kallon Meemah da wani
expression tace "Bacci fa kika ce Meemah??" Meemah ta ajiye gyalen
jikinta tace "Wallahi kuwa Momy" Momy tace "To baccin me take
wajen karfe sha dayan safe??" Meemah tace "In kin tambayeni in
tambayi wa?" Momy ta gyara zama tace "Toh baki tafi dakin kin dubo
ba?" Meemah tace "In lafiyarta qlau ai kinsan taso ta zai yi ta fito
ta gaisheni barin ma da nace masa kin bani sako in bata, sai ce min yayi magani
ta sha tana bacci" a hankali Momy tace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un" Meemah tayi wani murmushi tace "Kinsan Allah Momy, kawai
jikina ni tun asali ya bani ba lallai irin wannan asirin yayi tasiri lokaci
daya ba, bance bazai yi tasiri ba amma sai ya gama moreta tukun, kin ga in rabo
ya shiga kafin nan kuma ai mun shiga uku mun lalace, hada iri da talaka ya
tabbata" a fusace Momy tace "Ke dai a rayuwarki baki taΙa furta
alkhairi sai sharri Amina? Asirin kusan miliyan biyun kike ce min ba lallai
yayi tasiri ba? Ko kina hauka ne?" Meemah tace "A'a ni bance bazai yi
tasiri ba Momy, cewa nayi..." Momy ta dakatar da ita rai bace tace
"Bana son ki sake saka min mugun bakin ki a lamarina, ki tashi ki ban waje
kar in yi mummunan bata maki rai wallahii" Mikewa Meemah tayi ta kyabe
baki tace "Shi Abdul din da duk mun san yanda idonsa ke kan mata ne kike
tunanin zai bar yarinyar nan su kwana gida daya babu abinda ya shiga
tsakaninsu?" Wani zagi Momy ta kunduma mata tace "Baza ki tafi ki ban
waje ba, me mugun alkaba'i kawai, duk ba ke kika ja mana wannan bala'i
ba?" Meemah na tabe baki tayi tafiyarta sama, Mikewa Momy tayi ta fara
zaga parlor tana jin zufa na keto mata duk da Ac dake kunne, sai kuma ta dau
wayarta ta wuce sama da sauri. Wajen karfe hudu da rabi Abdul ya dawo gida,
Khaleesat ta idar da sallah tana zaune kan darduma ya shigo dakin ya ajiye
shopping bags din hannunsa, ta mike a hankali tana kallonsa tace "Sannu da
zuwa" Yace "Ki duba ko akwai abinda ba a siya ba" Tana kallon
bags din ta karasa inda ya ajiyesu tana duba tsadaddun Abayan da ya siya mata
kala kala, da takalma da handbags, irin dai quality din da yake siya mata a
baya, duk wani abu da zata bukata sai da ya siyo mata, har da tsadaddun
turaruka iri iri da man gashi, da na shafawa, kallon lube din da ta ciro a
siyayyan ta dinga yi don at first tayi zaton na shafawa a fuska ne, sosai
gabanta ya faΙi ta Ιan kallesa taga kallonta yake, da sauri ta dauke kai zata
ci gaba da ciro sauran abubuwan da ya siyo ya mika mata hannu alamar ta basa
lubricant din, ta mika masa ba tare da ta bari sun hada ido ba, juyawa yayi ya
dau ledan kayan da Meemah ta kawo daxu ya fitar da shi daga dakin, a hankali
Khaleesat ta zauna gefen gado nan da nan hawaye ya cika idonta, bata san sanda
ta fashe da matsanancin kuka ba tana tuna azaban da ta sha daxu.
Wajen karfe takwas da rabi na dare Khaleesat ta gama dafa ma
Abdul tea din da ya sa ta ta dafa masa, gaba daya tun daga sanda ya dawo har
zuwa yanxu bata da sukuni a gidan, tana sanye da hijab ta karasa har inda yake
zaune a dakinsa yana karatun Alqur'ani, ta durkusa ta ajiye masa shayin, zata
mike ya jawota jikinsa bayan ya rufe qur'anin, yayi kissing goshinta yana
kokarin cire mata hijab din har dai ya cire, lkci daya jikinta ya fara rawa
tana son kwace kanta, Ζin saketa yayi ya riketa gam, tun tana ganin abun kamar
wasa tunda a zaune yake, har sai da ta gansu saman gado ya rabata da komai na
jikinta sannan idonta yayi clear, ihun da ta dinga masa tana kuka tana kokuwa
da shi bai sa ya fasa abinda yake yi ba, upon yayi using lube da ya siyo amma
kamar daxu yanxun ma dai bai iya yayi mata komai ba, after a while ya sake ta,
fuskarsa a daure yace "Fita" Ta sauka kan gadon da sauri ta dau hijab
dinta ta saka ta fice daga dakin jikinta na rawa, zaunawa yayi gefen gado ya
rike kansa da yayi masa nauyi yana sara masa. Throughout washegari Abdul bai bi
ta kanta ba a gidan, ta dai gaishesa da safe ya amsa babu yabo babu fallasa,
amma hatta breakfast da tayi bai ci ba balle lunch, sosai taji guilty
conscience na damunta don tana tsoron kamun Allah, tunda tayi karatun addini
tasan kuma meye aure, amma yanxu ita kanta tasan ba intentionally bane taki
basa hadin kai, kasa daurewa tayi wajen karfe uku na rana jiki a sanyaye ta
samesa a parlor ta durkusa daga gefensa a hankali tace "Don Allah Ya Abdul
kayi hakuri idan nayi maka laifi" Shiru tayi don ita kanta tasan she
sounds stupid, Babu yabo babu fallasa yace "Laifin me?" Ta sauke
idonta ta kasa cewa komai, Yace "Ohk kinsan ma abinca kike yi kenan"
Ta girgiza masa kai da sauri, kallonta kawai yake don duk yau ji yayi kamar an
dauke masa sha'awarta, unlike before da ko me zata yi feeling din nan nata dai
na nan a ransa, kawai ji yayi baya ma son ganinta kawai, Calmly yace
"Tashi ki bani waje" A hankali ta mike ta bar parlon. Da daddare
bayan magrib yana kwance parlor ya kunna karatun Alkur'ani ta wayarsa yana
saurare, tun da Khaleesat ta fito zata je daukan abinci a kitchen ya bi ta da
kallo, har ta fito daga kitchen din ta wuce dakinta da abincin, ya mike zaune,
after a while sai ga ta ta sake fitowa ta kai plate din kitchen, hijab ne har
kasa a jikinta, still da ta fito haka ya bi ta da kallo, ita dai ta gefen ido
kawai take kallonsa har ta koma dakinta, Bayan isha'i ya bude kofar dakinta,
sosai ta tsorata ganinsa, suna hada ido ta sunkuyar da kanta don dama zaune
take kan darduma ta idar da sallah, Yace "Make me a cup of tea" A
hankali tace "Toh" Jiki a sanyaye ta tashi taje ta dafo masa tea din
ta kai masa dakinsa, haka kawai gabanta ya dinga faduwa ganin kallon da yake
mata, ta dai ajiye cup din tea din sannan ta fita ta koma dakinta ta kashe wuta
ta kwanta ta shige cikin duvet, banda faduwa babu abinda gabanta yake yi, har
ta fara bacci ta ji ana cire duvet din jikinta ta mike zaune a tsorace tana
kallonsa kamar zata yi kuka don ya kunna dim light a dakin, yace "Nan wai
wayo kika yi kika zo kika kwanta da wuri?" Sunkuyar da kanta tayi
zuciyarta na bugawa bata ce masa komai ba, ya xauna gefenta ya jawota jikinsa a
hankali, yayi kasa da murya yace "Kar ki manta you are my wife legally
Khaleesat, why are you making everything seems hard for us both?" Kuka ta
fara yi a hankali, yana magana kamar me rada yace "You just have to stay
calm and relax plss, i promise i won't hurt you Khaleesat, the lube will help,
jiya kin ki sakin jiki shi yasa bai yi ba" Khaleesat dai kukan tashin hankali
kawai take bata ce masa komai ba tana kallon lube din da ya ajiye saman gado,
kwantar da ita yayi taking off her nighty ya fara bi da ita gently kamar yanda
yace, duk yanda Khaleesat ta saka ma ranta yau dai zata daure kawai tayi hakuri
yayi abinda zai yi amma yana fara taΙata ta fara masa kuka da karfi tana
turjewa, tsabar feelings dinta da yake ji yau duk bai ma san tana yi ba, banda
lallabata da bata hakuri babu abinda yake yi yana bi da ita a hankali, don
burinsa kawai yayi accomplishing mission dinsa yau ya maida ta mace, amma me?
even with the help of so much lube hakan yayi seeming impossible, magiya ya
dinga yi mata kamar zai mata kuka yake rokonta she should let him pls don gani
yake kawai don taki sakin jiki ne, sosai yake rokonta as if his life depend on
what he is trying to do, ita banda kukan azaba babu abinda take tana kokarin
kwace kanta tana turasa da duk sauran karfinta, mari ya sauke mata a fusace ya
shakota yana huci yace "Is all this among ur plan??" Kasa magana tayi
saboda shaΖeta da yayi da karfi, ya wani turata har sai da ta fadi kasan dakin,
yana huci ya sauka daga saman gadon ya nufeta yace "Ni xaki raina ma
hankali? Ni zaki dinga dauka for granted?" Cikin kuka tana komawa baya ta
dinga cewa "Don girman Allah kayi hakuri, wallahi bani bace Ya Abdul, nima
ban san me yasa haka ba" Ya dagota da karfi yana kallonta da idanuwansa da
suka yi jajir yana wani irin numfashi yace "Saboda kin saka a ranki baki
son aurena baki son zama da ni shi yasa baza ki bani hakkina ba?" Jikinta
na rawa ta dinga girgiza masa kai tace "Wallahi a'a, don girman Allah kayi
hakuri...." Wurgata yayi da karfi har sai da ta buga da bango, ya juya ya
fice daga dakin kamar zai tashi sama, Ζasa motsi Khaleesat tayi tana ganin duk
dakin na juya mata, yana fita dakin da minti goma taji fitar motarsa a gidan,
kuka Khaleesat ta dinga yi sosai ko ina na jikinta na mata ciwo a dakin, ta fi
awa daya kwance inda ya wurgata, ji take kamar bazata iya tashi ba ga azaban da
take ji a Ζasanta, da kyar ta rarrafa zuwa bandaki daga karshe, bayan ta gyara
jikinta ta fito ta kwanta nan kasan dakin tana kuka a hankali ga wani azababben
ciwo da kanta yake mata, tashi zaune tayi ta jingina da gado tana tunanin what
exactly will be the problem, don ita ta riga tayi give up din Abdul a matsayin
mijinta, ko dai tana da wani ciwo ne da bata sani ba a wajen, if not ko yanda
yayi using lube din nan should have been enough, to ko ce masa zata yi su je
asibiti don ya dena zargin hanasa take yi, bazata so Allah ya kamata da laifin
hana mijinta kanta ba, hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta, she wish zai
bata listening ears ya saurareta yasan she is not doing this purposely, sai
wajen karfe daya da rabi na dare taji shigowar motar Abdul, gabanta ya dinga
faduwa tana kwance kasan dakin har taji alamar ya shiga dakinsa, mikewa tayi da
kyar ta saka hijab dinta tana dingishi ta fita daga dakinta, tsaye tayi tana
kallon kofar dakinsa gabanta na faduwa don bata san me zai ce zai mata ba idan
ta shiga dakin, daga karshe tayi shahada ta bude a hankali ta shiga gabanta na
faduwa, wanka taji alamar yake yi a bandaki, ta dinga kallon wrist watch dinsa
da wayoyinsa da sauran ledan Prophylactic dake ajiye gefen gadon, sosai jikinta
yayi sanyi ta dinga kallon prophylactic din, taji hawaye masu zafi na sauka
idonta, bayan few seconds ta juya a hankali ta fita daga dakin, wasu sabbin
hawaye na sauka idonta ta koma dakinta ta kwanta saman gado tana shesshekan
kuka.
[6/23, 2:54 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Wajen karfe
bakwai Khaleesat ta fito daga dakinta tana tafiya a hankali, duk da zazzabin da
ta tashi da shi yau haka nan ta daure ta fito,
tana hangosa kwance kan kujera yana danna wayarsa sai da gabanta ya fadi
sosai, ta sauke kanta ta karasa har inda yake kwance ta durkusa cikin sanyin
murya ta gaishesa, wayarsa kawai yake dannawa yaki kallon direction dinta balle
ya amsa gaisuwarta fuskarsa a daure, bayan kusan minti daya ta mike jiki a
sanyaye ta juya ta wuce kitchen, hawaye taji ya cika idonta ta kai hannu tana
gogewa sannan ta fara preparing breakfast, bayan kusan minti arba'in ta fito
daga kitchen din zata tambayesa ko ta kawo masa breakfast din yanxu duk da
yanda gabanta ke faduwa, amma sai bata gansa a parlon ba, hakan yasa ta juya ta
koma kitchen din ta dauko breakfast din ta kai dinning table ta ajiye, zata
tafi dakinta kenan sai gashi ya fito daga nasa dakin har ya shirya alamar wanka
yayi, tana kallonsa a hankali tace "Na gama preparing breakfast din"
Banza yayi mata ya wuce ta, ta bi sa da kallo har ya shiga parlor, a sanyaye ta
bude kofar dakinta ta shiga hawaye na taruwa idonta, ta zauna gefen gado tana
goge hawayen a hankali, lamo tayi kan pillow tana shesshekan kuka, tunani iri
iri ne ke mata yawo a rai, me ke faruwa da ita ne? Ko tana da wani ciwo ne da
bata sani ba, who is she going to talk to about this? Hawaye taji na zubo mata
sosai, how is she going to explain to Abdul that this isn't her fault? Ta yaya
zata fahimtar da shi ya gane? Tafi awa daya kwance tana saΖe saΖe a ranta, a
hankali ta mike zaune jin alamar fitar motarsa daga gidan, da kyar ta mike daga
karshe ta tafi parlor tana tafiya a hankali, dinning area ta nufa ta duba taga
bai taΙa komai ba a breakfast din da ta ajiye masa, ta juya a sanyaye ta koma
parlor ta zauna ta jinginar da kanta da kujera hawaye na sauka idonta, after a
while ta tashi da kyar ta fara gyara gidan sannan ta hada shayi ta dawo parlorn
ta zauna amma ta kasa sha saboda damuwa, daga karshe kawai ta koma dakinta.
Wajen karfe uku taji ya dawo gidan, ita dai tana ta zaune dakinta bata fita ba,
bayan kusan minti biyar ya bude kofar dakin nata, kallo daya yayi mata yace
"You have Visitors" Daga haka ya juya ya bar wajen, tayi jim tana
tunanin su waye visitors din, mikewa tayi ta dau veil din Abayan dake jikinta
ta rufe kanta sannan ta fito parlor tana tafiya a hankali, buda ido tayi ganin
Aunty Farida da Nenne da step mothers dinta zaune a parlor, da gudu ta tafi ta
fada kan Aunty Farida ta rungumeta cike da farin cikin ganinta, Nenne ta hade
rai tana kara hakikancewa kan kujera tana kallon TV da aka kunna a parlon,
Aunty Farida ta dago kan Khaleesat tana kallonta ganin yanda ta rame, a hankali
tace "Ya kike Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta cikin sanyin
murya tace "Lafiya lau Aunty, Ummana fa? Me yasa baku zo da su Islam
ba?" Aunty Farida tayi kasa da murya tace "Ke baki gaida su Nenne
ba" Sai a sannan Khaleesat ta tuna da sauran mutanen parlon, zamowa Ζasa
tayi a hankali tana kallon Nenne tace "Ina yini Nenne?" Nenne tace "Akan
me zaki ce min ina wuni ni da nake er banza mara mutunci a idonki? Ita Faridar
da kika makalewa kina shigewa jikinta da an biye ta tata da bata kashe auren
nan har lahira ba? Da an biye ta Farida da Zahra'u idan kin ganki a wannan gida
haka Allah ya tsine min albarka, to sai me don kin gan ni kin kauda kai kinyi
kamar baki ganni ba da sauran matan ubanki? Ai babu komai" Khaleesat ta
hade rai ta gaida su Mama Shatu dake zaune fuska duk babu walwala suka amsa
mata babu yabo babu fallasa suna kare mata kallo, Nenne ta gyara zama cikin
bacin rai tace "Banda matan ubanki da suka takura aje a san inda kike a ga
halin da kike ciki sannan ni da na amshi sabon lambar Awdul wajen Farida nayi
ta doka masa kira har yaje ya dauko mu ya kawo mu kin zata akwai wanda zaki
gani a gidan nan ne? Ita farida Allah Allah take ta koma Legas ta ci gaba da
tuwo tuwonta a can, uwarki kuma ba sanin ciwonki tayi ba balle ta samar mana
hanyar zuwa ganin halin da kike ciki, amma me? haka nan albarkacin Ali nace
dole dole sai naje naga halin da kike ciki, haka nan na uzura ma Awdul da kira
yaje ya dauko mu, kuma Alhamdulillahi ga ki nan har wani haske kika kara alamar
kina cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya da mijin ki, to meye zaki yi kamar
baki taΙa sanin mu ba daga abun arziki dai" Mama Zubaida tace "To ai
sai a zaga damu cikin gidan mu sa albarka tunda Allah bai yi mu za mu kawo
amarya ba" Nenne tace "A'a, ba bin kwakkwafi da tsegumi ya kawo mu ba
kaman en iska, tunda dai yarinya na cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya
dama mu hakan ne kadai fatan mu, don haka babu me shiga mata ko ina a gidanta,
in ma ce maku aka yi ku yi hakan don wata mugun manufa taku to baza ayi ba, don
ni ban yarda da yanda ku ka dage sai an zo gidan Khaleesah ba tunda ni ba
yarinya bace, dama kuma Ali yace ko minti sha biyar kar mu yi, da mun samu
ganinta mu kamo hanya mu dawo tunda mu ba iyayen banza bane" Mikewa
Khaleesat tayi ta tafi kitchen ta bude fridge ta dauko ruwa da drinks ta daura
kan tray ta kai masu parlorn ta ajiye, ita dai Aunty Farida sai bin ta da kallo
take don kana kallon fuskarta tasan akwai damuwa, gashi tana son kebewa suyi
magana da ita amma tana gudun fitinar Nenne, Nenne na kallon Farida tace
"Karfe nawa yanxu?" Farida tace "Uku da minti goma" Nenne
na gyara mayafinta tana kallon Khaleesat tace "Toh kitchen za ki kai ni mu
gana ko kuwa? in mun gama magana sai kije ki ce masa za mu koma ba zama muka zo
yi masa ba" Aunty Farida ta dake ta mike tace "Kafin nan bari in Ιan
yi magana da ita Nenne" Nenne ta kalleta da sauri tace "Ai ba kashe
aure ya kawo mu ba Farida, in baza kiyi mata magana a gabanmu gaba daya ba to
ki rike maganar ki kawai don ba alkhairi bane, haka kawai baza ki ja yarinya ki
keΙe da ita ki kitsa mata tsiya da salon kashe aurenta ba" Aunty Farida ta
dinga kallon Nenne, Nenne ta mike tana rike da babban jakarta tana kallon
Khaleesat tace "Kai ni kitchen din" Khaleesat taji kamar tayi kuka
bayan Nenne ta hana Aunty Farida tayi mata magana, rai babu dadi ta nufi
kitchen Nenne na biye da ita a baya bayan ta jaddada ma farida a kunne kar ta
bari su Mama Zubaida su shiga ko ina na gidan, su Mama Shatu da Mama Zubaida
sai tabe baki suke, Nenne ta tura kofar kitchen din bayan sun shiga, tana kare
ma kitchen din kallo tace "Maa sha Allahu kai kaji waje sai kace daki uku
a hade, kuma iya girki kawai ake yi a nan?" Ita dai Khaleesat bata ce
komai ba, Nenne ta zauna kasan tiles din kitchen din ta zuge jakarta tana
kallon Khaleesat tace "To kin tsaya min kerere a kai" Dukawa
Khaleesat tayi a gabanta tana kallonta, Nenne ta fito da wasu kulle kulle har
Ζashi biyar, ta dinga kwancesu daya bayan daya cikin nutsuwa, murya can kasa
tace "Kin ga wannan?" Khaleesat dai kallon kullin da Nenne ke nuna
mata kawai take, Nenne na magana a hankali kamar tana tsoron wani ya ji tace "Cikin
ruwan wanka zaki dinga diba kadan kadan kina zubawa kiyi wanka, duk wani mugun
abu da mutum zai maki ko kuma yayi maki to da izinin Allah zai koma kansa da
zuri'arsa, sharrin zai lalace na har abada, Wnn kuma a kunu zaki dinga zubawa
ki sha kayanki ke kadai, wannan girki zaki dinga yi maku da shi gaba daya ku
ci, ba wani mugun abu bane kawai saboda zaman lafiyanku da kwanciyar hankalin
ku babu kuma Ιan iskan da zai iya shiga tsakaninki da mijin ki, sai ki ga kanku
ya hadu kuna ma juna nutsattsen soyayya bakwa son laifin juna, wnn na hayaki ne
shima duk wani mugun abu idan an maki zai karye ya koma kan me shi da izinin
Allah, da kyar aka tsam min wallahi, kin dai gansa Ιan mitsitsi ko Ali ban
dibar ma ba tunda naga bashi da yawa na kawo maki ba don halin ki ba, wannan na
karshen shi kuma na sha ne da wanka, in kinyi wankan sai ki kada shi ko cikin
ruwan shayi ne ki dinga shan abun ki" Ita dai Khaleesat tayi shiru tana ta
kallon abubuwan da Nenne ke mata bayaninsu sinka sinka cikin nutsuwa, Nenne ta
gyara zama fuskarta a daure tace "Wallahi in kika sa nayi asaran lokacina
da en kudadena kika ki amfani da wannan abubuwan da na shiga kauyuka takanas na
samo maki to in na maki Allah ya isa sai ya bi ki tunda ni ba baiwar buzuwar
uwarki bace, duk ita ya kamata ta maki wannan abun amma gantalalliyar bazata yi
ba, dama kuma sari nasan ke da ita bakwa amfani da duk wani abun taimako da
nake baku, wani lkcn matsalarku ce ma ke shafan Ιa na yayi ta wahala a duniya,
to wannan in ma kinki yi wallahi kanki kika cuta don dangin Awdul ba mutanen
arziki bane duk mun sani, kuma ba lallai su barki ki zauna lafiya a gidan mijin
ki ba barin yanda suka dau Ζaran tsana suka dora ma ubanki saboda shi talaka
ne, to ni dai gashi nan albarkacin ubanki na maki wannan wahala, haka nan na
shiga wani kauye duk mayu na fito da kyar, to ya rage naki kiyi ko kar ki yi,
in ma baki yi ba Allah ya isa" Khaleesat dake kallonta tace "Toh in
ya gan su sai in gaya masa na menene su?" Nenne ta saki baki tana
kallonta, a fusace tace "Ke dai sokuwa ce mahaukaciya, to uban wa yace
maki a gabansa za ki yi? Yau naga bala'i, wannan wace irin shashashar yarinya
ce? dama ba sai ya fita ba zaki yi maza kiyi duk abinda zaki yi kafin ya dawo?
Ni da ban yi boko ba ma nafi ki hankali da wayo? wannan wace irin jaraba ce
Zahra'u ta haifar ma Ali? To ki kwasa ki nuna masa tunda baki da seti"
Khaleesat ta wani hade rai ta kauda kai, Nenne tayi kasa da murya tace "Ae
sai ya fita duk zaki yi komai cikin sirri, yanxu boyewa zaki yi inda ko da wasa
bazae gani ba" Khaleesat tace "Toh ae zae ji warin hayakin kuma,
sannan ni bama ni da abun yin turaren wutan ai" Nenne tace "To dama
ai shegen a gantale ya dauko ki bai bari duk mun shirya maki turaren wuta ba da
sauran abubuwan da ake kai mata da su gidan miji, yanxu dai nasan shi zai maida
mu gida ina da manyan robobin turaren wuta har biyu da na ajiye maki zan basa
turaren da kasko ince ya tsaya gun masu siyar da gawayi a bakin hanya ya siya
maki ko leda uku ne ya taho maki da shi, sai ki dinga hurawa a kaskon tunda ga
AC a parlon nan da nan zai kama maki in kika hura" Khaleesat bata san
sanda tayi dariya ba, Nenne tace "To shikenan ki maida ni mahaukaciya ina
kokarin taimakon rayuwarki" Khaleesat tace "Na ji" Nenne tace
"Yauwa to, yanxu gasu nan maza ki je ki boye inda bazai gan su ba kwata
kwata" Khaleesat ta amsa ta nemi waje a nan kitchen din ta boye, Nenne
tace "Yauwa to haka ake yi, yanxu maza tafi ki ce masa zamu tafi kar ya ga
mun zaune masa a gida, dama ni wnn abubuwan yasa nayi ta doka masa kira yau
kwana uku kenan, har Allah yayi ya zo ya dauke mu" Mikewa Khaleesat tayi
ta fita daga kitchen din Nenne na biye da ita murya can kasa tace "Ko
ruwan gidansa mu dai bamu sha ba balle yace" Khaleesat na tafiya a hankali
ta nufi dakin Abdul, knocking tayi tana jiran ya amsa, after almost a minute ya
bude kofar, ta sunkuyar da kanta tace "Za su tafi" juyawa yayi ya
koma dakinsa, hakan yasa ta dawo parlor, Nenne na kallonta tace "Kin gaya
masa?" Kai ta gyada mata ta tafi kusa da Aunty Farida ta zauna a kasa, Su
Mama Shatu kana ganin fuskokinsu kaga bakin ciki da hasadda karara a kwance,
bayan kusan minti biyar Abdul ya fito daga dakinsa yana murmushi yace "Har
za ku koma Kaka?" Nenne tace "Wallahi kuwa Awdul, ai dama ba zama za
mu yi ba, ni dai nayi farin cikin ganin jikata cikin kwanciyar hankali dama duk
haka muke so" Shi dai bai ce komai ba, Nenne ta mike tace "Don haka
yanxu sai ka maida mu gida kawai" Abdul yace "Toh naga ko abinci bata
baku ba ai" Nenne tace "A'a mu muka hanata don duk a koshe mu ke,
ruwan ma in ka lura ai bamu sha ba" Shi dai murmushi kawai yayi, a haka
Nenne ta kada keyarsu Mama Zubaida da Mama Shatu suka fita daga parlon, Ita dai
Khaleesat na biye da su duk jikinta a sanyaye, Aunty Farida ce last din fita a
parlorn, tana kallon Khaleesat tayi kasa da murya tace "Za ki ga sako na
ajiye maki bayan throw pillow din kujeran da na zauna, kar ki damu kafin in
koma lagos zan samu lokaci in zo ni kadai kin ji?" Kai kawai Khaleesat ta
gyada mata, Bayan Abdul ya bude motarsa ya kalli Khaleesat da duk jikinta yayi
sanyi ganin su Aunty Farida za su tafi, yace "Mu je sai mu yi dropping din
su mu dawo" Nenne dake kokarin shiga bayan mota ta dakata tace "Toh
ai babu waje a motar, a ina zaka dora ta Awdul?" Aunty Farida tace
"Sai ta shiga gaban motar Nenne ni in koma baya" Nenne tace "A'a
babu ruwana wallahi, a irin narka narkan jiki na Shatu da Zubaida mu uku ma ya
muka kare a baya balle kin shigo cikinmu Farida? Ko dai a cinyar su zasu dora
ki?" Shi dai Abdul murmushi kawai yayi, Khaleesat tace "Toh ni sai in
zauna a bayan" A fusace Nenne tace "To ke dole sai kin bi mu ne kamar
en matan amare? Kawai don na zo gidanki sai in koma gida da ciwon jiki? ni
wallahi in da matsi a mota ma bana shiga, da mun sani da bamu taho da Zubaida
ba don duk ita ta cika waje..." Abdul ya kalli Khaleesat yace "Don't
worry, ki koma ciki kawai" Hawaye ne ya cika idonta tana kallonsa, Aunty
Farida ta yi ma Nenne wani kallo ta shige gaban motar, Nenne ta kyabe baki ta
shiga bayan motar tana hararansu Zubaida da su ma duk suka shiga motar kuma
babu warce tayi gigin gogan jikin Nenne a cikin motar, Nenne tace "To duk
ku sauka Khaleesah ta fara shigowa ta dawo kusa da ni tunda ba wani auki gareta
ba, ku ne abun tsoron dama" Babu musu duk suka sake sauka daga motar suka
koma gefe, Nenne na kallon Khaleesat tace "Ba sai kin yi kuka ba, shigo ki
matso kusa da ni mu ga adadin wajen da zai rage, in ya kama wata sai ta hau
adaidaita sahu" Khaleesat ta goge idonta ta karasa ta shiga cikin motar ta
matsa kusa da Nenne, space din da ya rage a motar tsaf zai dauke su Mama
Zubaida, Nenne ta tabe baki tayi kasa da murya tace "Duk fa wari suke, in
Farida ta shigo nan ai jikina za su rakube in ta shakan wari su cuce ni, in de
ba kusa dani Faridan zata dawo ba, kuma Zubaida duk ta fi warin, banda akwai
turare da AC a motarsa ai da mun ji kunya" Ita dai Khaleesat bata ce komai
ba su Mama Zubaida suka shigo motar Nenne na yatsine yatsine, a haka suka bar
gidan. Sai kusan karfe biyar suka isa Mariri, bayan Abdul yayi parking dai dai
kofar gidansu Khaleesat Nenne ta bude motar ta sauka tare da Khaleesat, su Mama
Zubaida ma duk suka sauka da Aunty Farida suna ma Abdul godiya sannan suka
shiga cikin gida, Nenne na gyara gyalenta tace "To Allah yayi maka albarka
Awdul mun gode, amma dai zan yi maza in karasa gida akwai sakon Khaleesat da
zan dauko in bata tunda Allah ya kawo ku ta tafi da kayanta kawai" Yana
zaune driver seat ba tare da ya juya ba yace "Toh Kaka" Tana kallon
Khaleesat tace "Mu je ki taho da sakon" Khaleesat bata ce komai ba ta
fara bin Nenne zuwa gidanta, bayan sun yi nisa Nenne tace "Ai kinga shegen
bai ce bari ya karasa gidan nawa da mu a motar ba, gaba daya baya ganin
mutuncin gidana dama" Ita dai Khaleesat tayi kamar bata ji me tace ba, har
suka isa gidan Nenne Khaleesat na gaisawa da mutanen anguwan, Nenne tace
"Munafukai, sun yi mamakin ganin ki haka ai, kinsan duk ca aka yi kin
shiga duniya kin gudu, sai daga baya kuma aka ji kina gidan mijin ki"
Murmushi kawai Khaleesat tayi, bayan sun shiga gidan Nenne ta dauko turaren
wutan ta saka su a katon leda da kasko biyu sannan suka fito, suna isa kofar
gidansu Khaleesat Nenne ta saka ledan a bayan motar Abdul tana cewa "Kaga
har mun dawo Awdul, dama turaren wutan ne ba wani abu ba, don haka ku yi maza
ku tafi kar Magariba ya tarar da ku a hanya" Yace "To Kaka"
Khaleesat na kallonsa tace "Zan shiga in gaida Ummata" Bata jira
cewarsa ba ta shiga cikin gidansu ya bi ta da kallo, ko minti uku bata yi da
shiga dakin Ummanta ba sai ga Nenne, tana tsaye bakin kofar dakin bayan ta dage
labule tace "Abun kuma ba hauka bane ai, taso ki fita yana jiran
ki..." Khaleesat ta daga kai tana kallon Nenne, Nenne tace "Ae sai
yayi mana kallon mutanen banza marasu hankali, taso nace ki fita kar ki ja mana
reni" Umma na kallon Khaleesat tace "Ku je Khaleesat, kin ga yamma
tayi" Fuska a daure Khaleesat ta mike ta fita daga dakin, Nenne ta rakata
har bakin motar Abdul, tana shiga gaban motar yayi ma Nenne sallama ya ja
motarsa ya bar wajen, har suka isa gida ana kiraye kirayen magrib bai ce mata
ba, ita ma bata ce masa komai ba, bayan yayi parking ya sauka motar ita ma ta
sauka, tana tafiya a hankali ta bi bayansa suka shiga gidan, Kitchen ya shiga
direct, har zata wuce dakinta ta tuna sakon da Aunty Farida tace ta bar mata
kan kujera, ta karasa inda Aunty Farida ta zauna ta dauke throw pillow din wajen
ta dinga kallon Dollars din dake ajiye da wayoyi biyu, daukan 1000 dollars din
tayi wanda Jay ne ya bata da zata dawo Nigeria, ta dau wayoyin biyu, daya na
Ajay daya na Jay, lkci daya jikinta yayi sanyi hawaye suka cika idonta, muryar
Abdul taji a kanta yace "What's that?" Da sauri ta boye hannunta a
baya tana kallonsa tsabar yanda ta gigice.
[6/24, 6:29 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Abdul ya
zagayowa ya tsaya gabanta yana kallonta ya mika mata hannu yace "Give me
what you are hiding" Sosai gabanta ya fadi tana kallonsa ta kasa cewa
komai, tsawan da ya gigitata ya daka mata yana mata wani kallo, lkci daya
hawaye ya cika idonta ta mika masa wayoyin da kudin hannunta, amsan su yayi
yana kallon su, ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa, Calmly yace "Who
gave you this?" Kasa dago kanta tayi hawaye na zuba idonta tana jiran jin
saukan mari at anytime, juyawa yayi ya bar wajen ya nufi dakinsa yana rike da
wayar da dollars din, Khaleesat ta bi sa da kallo har ya shiga dakin, taji
kafafuwanta sun kasa daukanta tsabar yanda ta tsorata, da kyar ta karasa ta
zauna gefen kujera tana jin bugun zuciyarta na karuwa, tana goge hawayen dake
sauka idonta.... Abdul na shiga dakinsa ya zauna gefen gado ya ajiye dollars
din yana jujjuya wayoyin hannunsa ganin iri daya ne with different colors, kuma
duk a mace suke babu caji, Exactly irin second phone din da yake using ne, ya
mike ya tafi yayi plugging din wayar Jay da chargern sa, sannan ya koma ya dau
kudaden ya kiraga yaga 1k dollar ne, ya ajiye su saman gadon yana kallonsu, jin
za a tada sallah a masallaci ya shiga bathroom dinsa, bayan ya fito zai tafi
masallaci ya kulle Bedroom din nasa da makulli, har sannan Khaleesat na zaune
parlor ta kasa motsi a inda take zaune, tana ganinsa ta mike tsaye a tsorace
tana kallonsa, ko kallonta bai yi ba ya nufi kofa ya fita daga parlon, a
sanyaye ta tafi dakinta hawaye na sauka idonta zata je tayi alwala ita ma.
Abdul na dawowa masallaci bayan ya bude dakinsa ya shiga ya dau wayar Jay ganin
har yayi caji ya kunna kansa, ya cire wayar jikin chargern ya dauko wayar Ajay
ya jona, sannan ya koma gefen gado yana duba wayar tunda babu lock jiki, gani
yayi ba Sim card a wayar, ya dai ci gaba da dube dubensa, babu inda bai shiga
ba a cikin wayar yana bincike but bai ga komai ba don babu any form of Media a
wayar, messages ma ko daya bai gani ba, bayan ya shiga Email yaga Business class
flight ticket da Jay ya siya mata da zata dawo Nigeria, ya dinga kallon Ticket
din for almost 30 seconds, sosai fa yayi mamaki ba kadan ba, fita yayi daga
Email din ya shiga Gallery din wayar hoping zai samu hoto a ciki, a nan ne ya
ga Hotunan Jay, wanda duk yawanci tare zaka gansu da Ajay, Zooming pic din Jay
yayi yana kallonsa with full concentration, sai kuma ya koma kan Ajay shi ma ya
dinga kallonsa baya ko kiftawa, at once ya gane da shi ne suka samu Encounter a
Amurka, but sai ya ga Ajay looks familiar, where did he know him from? mikewa
yayi da sauri ya dauko wayarsa ya shiga Instagram dinsa yayi Searching sunan da
yake tunanin ya san sa da shi a Instagram, amma sai yaga account dinsa is
locked, komawa yayi ya zauna ya kasa dena kallon hoton Ajay babu ko kiftawa,
can ya kara duba hoton Jay yayi Zooming dinsa yana kallo, kawai bai san me yasa
yaji yafi jin tsanar Jay ma akan Ajay, mikewa yayi ya dauko wayar Ajay don har
ya Ιan yi caji, babu lock a wayar hakan ya sa ya shiga, nan yaga Ticket da aka
siya mata from Kano to Lagos, iya shi kadai ya gani a wayar babu hotuna, babu
WhatsApp, babu komai, hatta sim card babu a wayar, fita yayi daga dakinsa ya
tafi dakin Khaleesat ya sameta tana sallah, tun da taga yanda ya tsaya mata a
bakin kofa taki idar da sallan da take yi da wuri kamar me Tuhajjud, muryarsa
taji cikin tsawa yace "Idan baki sallame sallan nan da kike yi
continuously ba zaki ga abinda zai faru yanxu" Sosai jikinta yayi sanyi,
haka nan ta daure ta sallame sallan tana ji kamar bango ya tsage ta fice daga
dakin tsabar tsoronsa, duk da yanda gabanta ke faduwa haka ta hade rai taki
kallon direction dinsa barin da ta ga both wayar Jay da Ajay a hannunsa, ya
karaso cikin dakin yana mata wani kallo cikin daga murya yace "Wayoyin su
wanene wannan??" Still taki kallonsa, wani tsawa yayi mata yace "Are
you stupid? Are you Mad? Ina maki magana kina kallon wani direction din
daban?" Sai a sannan ta kallesa, har sannan fuskarta a daure yak, amma
Allah ya gani daurewa kawai take, yace "I am asking you whose phones are
this?" A takaice tace "My Housemate and his Brother....." Ya
dinga kallonta babu ko kiftawa, she just realized she said her Housemate to
him, ta kallesa a sanyaye, ganin kallonta yake yi baya ko kiftawa, ta sauke
idonta a hankali tace "I mean...." Ya girgiza kai yace "No, you
mean ur Housemate, dama Housemate dinki ne ranan da na je kika min karya? Dama
gida daya ku ke tare da wannan katon banzan da na gani?" Gani tayi shiru
fa ba nata bane, don shirun nata duka kawai zai ja mata, in ma maganar tayi ba
hakan zai hana ya doketa ba in yayi niyya, ta wani hade rai duk da mugun
faduwan da gabanta ke yi, a takaice tace "Eh, he is my Housemate, Nancy
moved out of the apartment shi ne shi ya shigo, and i have no choice but to
live with him, tunda bana son in dinga bothering dinka da Expenses, kuma naga
in just few months za mu yi hutu, dama nufina idan mun yi hutu sai in ce maka
ka canza min wani apartment din since a sannan ne zaka yi renewing house rent
dina" Kallonta kawai Abdul yake yi babu ko kiftawa, ita dai ta kasa
kallonsa gabanta na faduwa tana expecting ta ji saukan mari at anytime a cheek
dinta, Calmly yace "So, shi ne kike zaune gida daya da shi ku ke rayuwa,
ku yi sharing same kitchen, same parlor and same corridor, if coincidentally
kin fito daki shi ma ya fito sai ku kusa karo da juna ko? Ki fito babu hijab ya
gan ki haka, ki fesa turare ki zo ki wucesa yana jin kamshi, in ma ya kama ki
zauna ku yi hira da shi, in kinyi girki ya diba ya ci" Sai a sannan
Khaleesat ta kallesa tace "I don't mind if you believe me or not... But
shi baya kwana gidan, karatu kawai yake zuwa yi ya tafi don suna da gidansu a
Amurka" Abdul ya dinga kallonta, sai a sannan ya tuna abubuwa masu tsadan
da ya dinga gani a kitchen sanda yaje, tun daga kan bottle water, cikin nutsuwa
yace "Shi ne dalilin da ya sa kika fara min wasu stupid attitude kenan?
Kin samu wanda yake siya maki duk abinda kike so a gidan har ma ya Ιebe maki
kewa, To bari ki ji, ko duk jikina kunnuwa ne bazan taΙa yarda babu wani
intimacy da ya hada ki da shi, ke kika san me kike basa da yasa yake siya maki
abubuwa masu tsada yake ajiye maki a kitchen, sannan har ya cire kusan 5000
dollars ya siya maki Business class ticket kawai don ki dawo Nigeria...."
Nan da nan hawaye ya cika idon Khaleesat, ta mike tsaye tana kallonsa tace
"Ko me zaka fada bazan ce maka ba haka bane, amma put this at the back of
ur mind, ba kowa ke da halin son taΙa warce ba muharramarsa ba kamar ka, kuma
shi bai dau kudin Business class ticket wata tsiya ba shi yasa ya siya min,
akwai difference sosai between you and him" Kallonta Abdul ya dinga yi da
mugun mamaki, bata ankara ba sai jin saukan tagwayen mari tayi a fuskarta, ta
fashe da kuka tace "Iya mari kawai?? ka kasheni mana ka huta kawai
Abdul...." Ya fizgota da karfi yana huci yana kallonta da idanuwansa da
suka yi jajir yace "Ni kike comparing da wani Ιan iska matsiyaci
can??" Cikin kuka tace "May be if i do that you will change ur
terrible ways, he made me realize i am dating a monster because of his kind
attitude toward me, babu komai tsakanina da shi amma shi din mutum ne me kirki
da sanin darajan Ιan Adam da sanin ya kamata, he always make sure i am fine,
baya barina da damuwa komin kankantar sa, kuma ko da kuskure bai taΙa saΙa min
ba a duk zaman mu da shi a America, kyawawan halayyarsa da irin yanda yake
interacting yasa naji i am fed up with ur attitude, all this made me realize
you are enslaving me ba sona kake ba, why not treat me the way he is treating
me idan har sona kake da gaske? Bani da daraja da mutunci a idon ka, kullum
cikin duka da cin mutunci nake a wajenka tun sanda baka aureni ba, iyayena ma
basu da mutunci a wajen ka, to menene yasa baza kayi releasing dina zuwa inda
za a ga mutuncina da na iyayena ba kuma a san darajata? Is it my father's fault
da kaddarar sa ta zo a yanda take? Ku kan ku kun san bai ci kudin mahaifinka
ba, bai salwantar masa da kayansa don son rai ba, ba ku tunanin ko ba ta
sanadin mahaifina ba sai kun yi asaran kudaden nan tunda ku ma a kaddarar ku
hakan take? Kuma meye zaka daga min
hankali a kan su bayan kace baza ka sakeni ba kuma kowa yasan igiyar auren nan
a hannun ka yake? Duk cikin rashin lissafin naka ne yasa kake kishi da su bayan
ka ri ga ka aureni??" Turata yayi har sai da ta bugu sosai da bango sannan
ya juya ya fice daga dakin kamar zai tashi sama. Wajen karfe dayan dare
Khaleesat dake kwance taji an bude kofar dakinta, da kyar ta bude idonta da
yayi mata nauyi tsabar kuka da ciwon kai, tana ta kwance a yanda take bata juya
ba duk da bata ga ya kunna wutan dakin ba, duvet din jikinta ya sauke kasa ya
jawota kusa da shi yayi kasa da murya yace "Kinsan da igiyata a kanki kike
da effrontery din kawo min maganar wani katon banza can har kike comparing
dinsa da ni? What wrong have i commit to you da kike ganin shi yana da halayya
masu kyau wanda ni bani da shi" Khaleesat taji zuciyarta na mata wani zafi
jin useless question din da yake tambayarta, tayi kamar bacci take taki
motsawa, yayi kasa da murya yace "Khaleesat..." Still tayi kamar bata
jin sa, duk da idonta a rufe yake she could feel the tears accumulating in her
eyes, kiranta ya sake yi a hankali jin bata amsa masa ba ya juyota zuwa jikinsa
yana kallonta cikin duhun, ya dora goshinsa kan nata yayi kasa da murya yace
"But you know i love you so much Khaleesat, da bana son ki bazan yi
wasting shekaru kusan biyar a kanki ba, i gave you the best of everything i can
kema kin sani" Bata san sanda ta turasa ba tsabar wani tsanarsa da take ji
a rai jin abinda yake cewa, ta mike zaune muryarta na rawa tace "Duk
saboda kana sona kake dukana kake marina kamar jaka? Shi ma duk cikin so ne?
Plss ka koma ka fahimci menene kalmar so...." Sauka ta fara kokarin yi
daga kan gadon tana shesshekan kuka, ya rikota da sauri yaki barinta ta sauka,
ta fashe da matsanancin kuka sosai tana jin zuciyarta na mata zafi saboda bakin
ciki, ya rungumeta gam a jikinsa, a hankali yace "Kiyi hakuri, amma Allah
ya sani ina son ki, in ma baki yarda ba i owe you no explanation tunda Allah
shi ya sani, kuma today should be ur first and last warning Khaleesat.... I
mean in ur life do not ever ever dare compare me with any stupid guy born of a
woman, kar ki sake kawo min zancen wani Ιan iska ko shi wanene a kunne na,
sannan bazan yi taking zaman da ku ka yi tare da shi and whosoever da kuma
alakar ku personal ba because you are my wife now, duk wannan ya zama pass and
shi ne looser, kuma har abada babu wata alaΖa da zai sake hada ki da shi don
ubansa har duniya ta nade kuwa, ba wai ban ji zafin alakar da kika yi creating
da su a America bane a raina, fadin zafin da naji ma is just an understatement
wallahi, amma considering the fact that you are my wife yasa nayi letting
bygone to be bygone, so let me keep using that to calm my self kar in masu
abinda ke raina...." Wani mugun tsanarsa ne ke karuwa a ran Khaleesat jin
kalmomin da ke fitowa bakinsa, wasu hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta
tana tausayin kanta da irin monster din da Allah ya bata as miji, kokarin kwace
kanta take yi a jikinsa zata sauka daga kan gadon yaki saketa yace "Ohk
bokare min za kiyi don ina baki hakuri? But i said i am sorry, and i promise i
won't hurt you again, na dena dukan ki...." Ζin ce masa komai tayi tana
kuka a hankali, ya kwantar da ita kirjinsa yana shafa gashinta a hankali yace
"Billah ina son ki Khaleesat, duk abinda kika ga ina maki saboda ina son
ki ne, but kin ki bani hakkina saboda ke akwai wani plan din a xuciyarki,
probably ma su suka koya maki haka" Daga kai Khaleesat tayi ta kallesa
tsabar bakin ciki bata san sanda tace "Ai ba kowa ne bashi da aikin yi
kamar ka ba" Shiru yayi yana kallonta babu ko kiftawa, ita kanta shirun
tayi gabanta na faduwa don bata san sanda kalman ya fito bakinta ba, Instead
sai ji tayi yayi kasa da murya kamar me rada yace "Where is the
Lubricant?" Sosai gabanta ya fadi jin abinda yace, yana rungume da ita
jikinsa ya bude bedside drawer kamar yasan nan din ta ajiye kuwa, ya laluba ya
dauko, shesshekan kuka ta fara yi zuciyarta na bugawa, yayi kasa da murya yace
"Kinsan tsinuwar Allah kike tara ma kanki kuwa?" Cikin kuka tace
"To ai ba ni bace" Yace "To waye?" Muryarta na rawa tace
"Wallahi ban sani ba" Cikin kwantar da murya yace "Promise me
today will be different plss Baby" Ta kasa cewa komai hawaye masu zafi na
sauka idonta ga faduwan da gabanta yake yi, gently ya fara cire kayan baccin jikinta
yana kallon kwayar idonta cikin duhun dakin, a wannan dare Abdul bai yi bacci
ba tsabar bacin rai, sai dai bai hantareta ba bai zageta ba, bai kuma doketa
ba, haka ya mike ya fice kawai ya bar mata dakinta ya koma nasa, ya shiga
bandaki ya sakar ma kansa ruwan sanyi duk da mugun sanyin da ake a garin, bayan
ya fito ya saka Pajamas dinsa ya kunna karatun qur'ani a wayarsa ya kwanta amma
ko rintsawa bai yi ba har asuba. Tunda Khaleesat ta idar da sallan asuba take
zaune kan darduma bayan ta gama azkar dinta, gaba daya jikinta a sanyaye yake,
zuwa yanxu kam sosai lamarin nan ya fara bata tsoro, ko baccin kirki bata yi ba
daren jiya tsabar yanda abun ya tsaya mata a rai, kawai tayi deciding tayi
amfani da abubuwan da Nenne ta kawo mata zuwa anjima, sai da gari ya waye sosai
sannan ta mike tana tafiya a hankali ta fita daga dakin zuwa parlor, sosai
gabanta ya fadi ganinsa zaune a parlon da cup din shayi a gabansa, ta sunkuyar
da kanta zuciyarta na bugawa ta tafi ta durkusa Ιan nesa da shi a hankali tace
"Ina kwana" Maimakon ya amsa sai ji tayi yace "Meye nake
perceiving a cikin kitchen kamar maganin gargajiya?" Khaleesat ta daga kai
ta kallesa, shi ma kallonta yake fuskarsa babu yabo babu fallasa, rasa me zata
ce masa tayi tana wasa da fingers dinta, a fusace yace "Bakya ji na ne?"
Bakinta na rawa da kyar tace "Nenne ce ta kawo min" A takaice yace
"Na menene?" Ta sauke idonta tace "Magani ne kawai, dama ta saba
bani in dinga amfani da shi a gida" Mikewa yayi yace "Mu je ki bani
su" Ta shi tayi kamar munafuka ta nufi kitchen din ya bi bayanta, ita
kanta taji kamshin itatuwan da ta shiga kitchen din, ta bude inda ta ajiyesu ta
dauko, ya mika hannu, ta karasa ta basa, yace "Ba a min amfani da irin wa
ennan abubuwan a gida" Kai kawai ta gyada masa, fuska daure yace "Kin
ji me nace maki? Kar ki sake amsa idan ta baki" A hankali tace "Na
ji" Juyawa yayi ya fice daga kitchen din ya koma parlor ya zauna, ya
ajiyesu nan kasan tiles, tana fitowa daga kitchen yace "Get ready za mu
fita, kuma kar ki bata min lokaci" Cikin sanyin murya tace "Toh"
Dakinta ta tafi, bayan kusan minti talatin sai ga ta ta fito cikin shiri, dai
dai nan shi ma ya fito daga dakinsa rike da wayarsa da car key, yana gaba tana
biye da shi suka shigo parlor, ya dau ledan magungunan da Nenne ta kawo mata ya
nufi kofar fita daga parlon ita dai tana biye da shi a baya, a booth dinsa ya
saka ledan magungunan, sannan ya zaga zuwa driver seat, ita ma ta shiga front
seat, bayan ya gama warming motar ya fita daga gidan. A sanyaye Khaleesat ta
fito daga Office din Dr Mariya with different thoughts running her mind, ta Ιan
juya ta kalli Abdul da ke bayanta shi ma ya fito office din likitan, Ζin
kallonta yayi, hakan ya sa ta ci gaba da tafiyarta slowly, sai ga Dr Mariya ita
ma ta fito daga Office din zata masu rakiya zuwa parking space, hira suke yi
kawai da Abdul suna tafiya a tare, ita dai Khaleesat na can gabansu, har dai
suka fita daga reception din hospital din suka karasa parking space, Dr Mariya
na kallonta tana murmushi tace "To amarya plss inji labari opposite of
this kin ji? There is nothing wrong with you, In kinyi amfani da duk shawararin
da na baki komai zai tafi dai dai in sha Allahu, hakuri kawai za ki yi it's
always like that dama, Allah Ubangiji ya bada zaman lafiya, in dai na samu
lokaci zan zo har gida mu gaisa" a hankali Khaleesat tace "To Nagode
Aunty, Allah ya kawo ki lafiya" Dr Mariya na murmushi tace
"Ameen" Sai kuma ta kalli Abdul tace "To Barrister ku gaida
gida, ina kuma tabbatar maka in sha Allah matsalar ta zo karshe tunda kaga mun
dade ina magana da ita, kuma hopefully ta dau duk abinda nace mata" Yace
"Thanks for your time Dr" Zagawa yayi ya shiga driver seat, Khaleesat
kuma ta shiga front seat, ya tada motar suka bar hospital din, har suka yi nisa
bai ce mata komai ba, ita ma dae shiru tayi tana ta tunane tunane, sae da taga
unguwan da suka shigo tayi realizing gidansu ya kawosu, bayan yayi parking ya
sauka motar, ita ma ta sauka, booth ya tafi ya bude ya ciro ledan da Nenne ta
kawo mata, da mamaki tana kallonsa tace "Ina zaka kai wannan?" A
takaice yace "Momy zan kai ma, naga tana dealing da irin abubuwan nan, she
can use it if she want, ke dai baza kiyi amfani da su ba a gidana"
Khaleesat ta marairaice masa tace "Noo pls, ni dai gwara kayi disposing
dinsu don Allah" Fuska daure yace "Bazan yi disposing din su ba"
Bata san dama haushinta ne fal zuciyarsa ba bayan Dr Mariya ta dubata ta
tabbatar masa lafiyarta qlau babu wani abu da yake hindering passage dinsa,
everything is normal, kawai hadin kai taki basa, Khaleesat ta sunkuyar da kai a
sanyaye bata sake cewa komai ba, ya nufi entrance din gidan nasu, tana tafiya a
hankali ta bi bayansa har suka shiga parlorn gidan, da mamaki Momy ke kallonsu
tace "A'a, daga ina ku ke da safen nan, sannun ku da zuwa" Abdul ya
zauna ya gaisheta, ta amsa tana kallon Khaleesat da ta zauna kasan carpet tana
gaisheta, Momy ta amsa da fara'a sosai fuskarta tana welcoming dinta, Momy na
kallon Abdul tace "Amma ba daga gida ku ke ba ko" Yace "Eh, daga
asibiti mu ke" Da mamaki Momy tace "Asibiti kuma, waye ba lafiya?"
A takaice yace "Bata ji dadi bane, amma da sauki" Momy na kallon
Khaleesat tana murmushin karfin hali tace "Allah sarki, sannu Mamana,
Allah ya kara lafiya" Sai kuma ta kalli Abdul tace "Ko wajen Dr
Mariya ku ka je?" Yace "Eh" Mikewa yayi ya ajiye mata ledan
magungunan kusa da ita yace "Kakarta ce ta kawo mata wnn jiya, ni kuma kin
san bana son irin abubuwan nan na gargajiya shi ne na kawo ko zaki yi amfani da
su ke" Momy tayi kuri da ido tana kallon ledan da mamaki, sai kuma ta
dauka ta bude da sauri, lkci daya ta saita kanta tana murmushin karfin hali
tace "Allah sarki, ai kam nasan halin ka baka san itatuwa, zan ko yi
amfani da su dama nawa sun kare tas" Ita dai Khaleesat kasa dago kanta
tayi, Momy was shock har cikin ranta amma tayi karfin hali take wayancewa, can
ta kalli Khaleesat tace "Amma baki fara amfani da su ba ko" Khaleesat
ta girgiza kai ba tare da ta kalli Momy ba tace "A'a jiya ta kawo min
banyi amfani da komai ba" Momy tace "To to, hakan yayi" Ta kalli
Abdul tace "In dai an samu wasu a dinga kawo min kawai" Mikewa yayi
yace "Za mu koma Momy" Momy tace "Da wuri haka? To wai ka koma
aiki ne?" Yace "Ban koma ba tukun" Momy tace "Toh shikenan,
Allah ya tsare nima in sha Allahu ina nan shigowa in kawo mata turarrukan wuta
da na jiki" Shi dai bai ce komai ba ya nufi kofa, Khaleesat ta mike tana
yi ma Momy sallama, Momy duk fa a rude take ta gyada mata kai kamar kadangariya
tace "To Mamata, sai na shigo, ku gaida gida, maza bi sa ku tafi"
Daga haka Khaleesat ta bi bayan Abdul da har ya fita daga parlon, Momy ta dau
wayarta har tana tuntube ta shiga dakin dake downstairs ta fara kiran Dr Mariya
don family Dr dinsu ce for long, Dr Mariya na dagawa suka gaisa da Momy cikin
fara'a, Momy tace "Yanxu Abdul ya zo min da matarsa yace daga asibiti
suke, naga duk ba shi da walwala nasan yana da zurfin ciki bazai gaya min ko
menene ba, shi ne na kira inji lafiya dai ko Dr? Ko juna biyu gareta? kinsan
dama yace bai son haihuwa da wuri, in dai juna biyu ne da ita gwara in yi
dubara in dawo da ita wajena don ni dai ina son ganin jikana, kar yaje ya bata
wani abu da zai lalata cikin taje ta sha" Dr Mariya tayi dariya sosai,
bata boye ma Momy komai ba tayi mata bayanin dalilin zuwansu Asibiti, Momy ta
sauke wani irin ajiyar zuciya ba tare da tasan tayi hakan ba, sai kuma ta bige da
cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kinsan yarinya ce fa, duka duka
Allah yasa tayi shekara ashirin, har da yarinta abun nata dae" Dr Mariya
tace "Wallahi nima haka nace masa don dae in kwantar masa da hankali kar
ya dinga jin haushinta, amma shekara ashirin ai ba yarinya bace Hajiya, aka ma
er shekara sha biyar aure ta zauna balle er shekara ashirin, ni dai na bata
shawarwari Allah ya sa tayi amfani da shi, kar tun yana hakuri da ita hakurinsa
ya kare a fara samun matsala gaskiya" Murmushi kawai Momy take tana Allah
Allah su gama waya da Mariya ta kira Godiya, daga karshe Momy tace "To
Allah ya sa ta dau shawaran naki Dr, kuma zan yi ma yayarsa magana ita ma taje
gidan anjima ta kara nutsar da ita in sha Allahu" A haka Momy suka yi
sallama da likitan, Momy tayi wani dariya tana girgiza kai sannan ta fara
dialing number Godiya, aikin miliyan biyu ai ba wasa bane, sun dade suna waya
da Godiya a waya, daga bisanni suka yi sallama, Momy na ta murmushi ita kadai
bayan Godiya ta sake jadadda mata Malamin yace lokacin ma da ya dibar masu za
ayi sakin baza a kai haka ba, don gab ake da yin sakin cikin kwanan nan kuwa,
Meemah da ta shigo dakin ta tarar Momy na waya ta zauna duk tana sauraron
conversation dinsu har suka yi sallama tace "To shikenan Momy yanxu haka
zai saketa ba mu ci ubanta ba na huce haushin abinda yayi min a kanta?"
Momy tace "Ke wa ke ta wani cin ubanta? Ance maki shi ne a gabana sai kace
wata yarinya? Ni dai in na samu Abdul ya rabu da ita an gama min komai, kuma
hakan kadai ne a gabana yanxu ba shashanci irin naki ba, ke kinsan menene hada
iri da talaka kuwa? Ke kiji matsiyaciyar kakarta har ta fara shige shigen
malamai tana kawo mata asiri banda Allah yasa Abdul din ya gani, to karyarsu ta
sha karya wallahi, cikin kwanan nan zai kora masu ita bayan ya saketa"
Mikewa Meemah tayi ta fita daga dakin don kwata kwata ba haka ta so ba ita, so
kawai tayi a bar ta tayi ma Khaleesat dukan mutuwa ko zata jin sanyin abinda
Abdul yayi mata a kanta.
[6/25, 8:35 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Bayan
Khaleesat sun koma gida tayi wanka sannan ta canza kaya tayi sallan azahar ta
fito ta dora lunch a kitchen, tana ta zaune parlor bayan ta gama hada komai na
girkin tayi tagumi tayi nisa tunanin da take bata san sanda ya fito daga
dakinsa ba, ya karaso parlon yana kallonta yace "Burden din mutane nawa ne
a kanki da kike tagumi haka" Juyawa tayi ta kallesa tana gyara zamanta
amma bata ce masa komai ba, tunda suka dawo gidan sai yanxu yake mata magana
bayan ya gama cika da batsewan sa kenan, Yace "I am asking you" Shiru
tayi still bata ce komai ba, ya zauna kan kujeran dake facing dinta yace
"Mutane nawa kike ciyarwa da kike tunanin yanda za ki yi?" Bata san
sanda tayi murmushi ba tana wasa da fingers dinta, kamar bazata ce komai ba,
sai dai a hankali tace "Ba ina son zan yi magana da frnd dita Sophie ba
kace bazan yi ba" Yana kallonta yace "Kiyi magana da ita ki ce mata
me?" A hankali tace "Babu komai, i am just missing her kawai"
Wayarsa dake hannunsa ya cire ma lock sannan ya mika mata yace "Speak to
her in my front" Amsan wayar tayi ta shiga contact dinsa ta duba number
Safiyyah sannan tayi dialing, yana kallonta yace "Sa a handsfree" Ba
musu Khaleesat ta saka kiran a Handsfree, yana fara ring Safiyyah ta daga, a
hankali Khaleesat tace "Sophie" Safiyyah tace "Omg Khaleesat?
Wallahi I've been expecting your call for so long kawata amma shiruu, Ya Allah,
number Abdul din ne wannan?" Khaleesat ta Ιan kalli Abdul da ya kafeta da
ido tace "Um, nasa ne" Lkci daya har Safiyyah ta gane wayar a
handsfree yake sanin wanene Abdul, a hankali tace "Ohk then, ki gaida min
shi sosai pls, but can i come over in gan ki if he will permit that pls?"
Cikin sanyin murya Khaleesat tace "I will speak to him about it"
Safiyyah tace "Alright dear, take care of ur self, i will be waiting for
ur feedback" Khaleesat tace "In sha Allah" a haka suka yi
sallama, safiyyah ta kalli wata aunt dinta dake kusa da ita cike da bakin ciki
tace "Wallahi nasan yana gefenta shi yasa ban tofa nawa ba, Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un, Her marriage and Abdul is the worst thing that have
happened to me last year, yanxu shikenan ta zama matarsa duk guje mata hakan da
na dinga yi, ba irin addu'an da ban sa ta akan Allah ya rabata da Abdul ba,
nayi ta mata sha'awan Housemate dinta amma Allah ya riga ya kaddara Abdul ne
mijinta, dubi yanda take min magana kina jin muryarta kinsan tana cikin damuwa
da matsin rayuwa, gashi karshen watan nan za mu koma school ban kuma ga alamar
zai bar ta taci gaba ba" Safiyyah ta fara matsar kwallan bakin ciki, ita
dai tana jin babu wanda ya kai ta bakin ciki da auren Khaleesat da Abdul, Abdul
ya amshi wayarsa da Khaleesat ke mika masa bayan tayi sallama da Sophie, a
hankali tace "Thank you" ajiye wayar yayi yace "Sai hankalin ki
ya kwanta yanxu tunda kin yi magana da kanwar Baabarki ko" Cikin sanyin
murya tace "Plss ina neman favour din ka barta ta zo wajena don Allah, i
am missing her so much" A takaice yace "Baza ta zo ba, in barta ta zo
ta ji dadin zuga ki kamar yanda ta saba? you think i don't know saboda tasan
wayar a Handsfree yake shi yasa tayi composing words dinta without saying
anything silly yanxu, duk ba ita bace ta fara ruining tunanin ki, very stupid
girl" Khaleesat dai kallonsa kawai take hawaye cike idon ta, kawai tayi
deciding tayi masa maganar abinda ya tsaya mata a rai all this while, hoping
Allah zai sa yayi considering din request din nata, cike da karfin hali tace
"Amma don Allah Yaya Abdul kar kace bazan koma makaranta ba, we are
resuming end of this month kuma kasan wannan shekaran kadai ya rage min plss
kar ka bari inyi asaran shekarun da nayi a baya, kayi considering expenses din
karatun plss, in kuma zai yiwu kawai a min transfer ba lallai sai can kasar
ba..." Hawaye na sauka idonta ta kare maganar tana kallonsa, ya mike yace
"You think i am stupid da zan bari ki kara komawa America ki ci gaba da
karatu? to ai kai ki can ma da nayi tun farko i deeply regret doing so, nayi da
na sanin kai ki karatu America da har ya bude maki ido, kuma tunda ba kudin ki
ko kudin wani naki aka kashe ba all this past years ina ruwanki da asaran da za
ayi? How is the lost going to affect you da kike nagging akan expenses din? Ina
ce kudina ne sai ko kudin mahaifina? So babu ruwanki, na gwammace inyi asaran
duk abinda na kashe maki da dai ki koma kasar nan, kuma kika kuskura kika sake
kawo min maganar karatu sai nayi mummunan saΙa maki wallahi, kuma bari kiji,
common University din kasar nan ma baza ki yi ba balle na wata kasar don babu
inda aka ce lallai lallai sai kinyi karatu, at first nayi tunanin kina da kamun
kai da nutsuwa ne shi yasa confidently na kai ki America, amma sai kika tafi
kina rayuwa da wani Ζaton Ιan iska a gida daya without my knowledge, ya kai ya
kawo ko kudi na tura maki sai kiyi kamar baki gani ba for days tunda kin samu Ιan
iskan dake siya maki abubuwa, not even one guy, kattin maza har biyu kika je
kina mu'amala da su a can, ko wanne kuma ke kika san abinda kike basa da yake
kashe maki kudi, so ko da kuskure kika sake kawo min maganar karatu wallahi sai
na maki abinda har ki koma ga Allah baza ki manta ba" Yana kai wa nan ya
dau wayarsa ya fice daga parlon kamar zai tashi sama, Khaleesat ta bi sa da
kallo hawaye masu zafi na sauka idonta. Har dare Khaleesat na dakinta abun
duniya ya taru ya mata yawa, wajen karfe sha biyun dare har ta fara bacci taji
an bude kofar dakinfa, a hankali ta bude idonta, wutan dakin taga ya kunna sai
kuma ya kashe, ita dai tana kwance bata juyo ba, ya karaso inda take kwance ya
cire duvet din jikinta ya cire hulan kanta yana shafa dogon gashinta ya kai
fuskarsa kusa da nata murya can kasa yace "You gave me Neither lunch Nor
dinner today, saboda kinfi karfin a gaya maki gaskiya ko?" Ita dai bata ce
komai ba duk da tana jin sa, dagota yayi zaune ya rungumeta yace "Then let
me have you since you are not giving me what u cook" Bai jira abinda zata
ce ba ya fara kissing dinta, Sosai Abdul ya bata lokaci wajen romancing dinta
irin yanda yasan zai gigita ta, in ba ita ba ma babu warce ya taΙa romancing
har haka, ko lube din bai dauko ba yau don baya ganin zasu bukace sa ma, a
wannan moment din Frustration dinsa yafi na kullum don sosai ya kai zuciyarsa
nesa bai kai mata hannu ba, yana wani irin huci ya fixgota da karfi yace
"Why are you doing this to me Khaleesat? Why are you frustrating me?"
Kasa ce masa komai tayi jikinta na rawa hawaye na zuba idonta, ta gaji da ce
masa ita bata san abinda ke faruwa ba, cikin daga murya jikinsa na rawa yace
"Ki bani amsa? Me na maki kike wahal dani kike cutata haka?"
Khaleesat dai ta kasa ce masa komai jikinta na rawa don tsoron magana ma take
ya gaggaura mata mari, yana wani irin huci ya turata yace "Ki jika abun ki
ki sha" Yana fadin haka ya sauka daga saman gadon ya saka Pajamas dinsa ya
fice daga dakin kamar zai tashi sama, Khaleesat dai ta jawo duvet ta rufe
jikinta har sannan zuciyarta na bugawa ta fashe da matsanancin kuka, bayan
kusan minti goma taji fitar motarsa a gidan gaba daya. Da yammacin ranan Momy
na parlonta da Godiya sai ga Abdul ya shigo kamar an hankado sa, Momy na
kallonsa tace "A'a Babana, sannu da zuwa" Juyawa yayi ya fice daga
parlon ganin Godiya, Momy ta Ιan zaro ido tana kallon Godiya sai kuma ta mike
da sauri ta tafi kusa da kofar ta bude tana leka corridor taga bangaren Abbansa
ya tafi, ita ta dade bata gansa cikin irin wannan yanayin ba ma, ta kulle kofar
ta dawo tana kallon godiya tace "Anya Godiya Malamin nan ba maye bane
kuwa, kin ga dama yace Abdul zai zo yau gashi kuma ya zo din kamar an
jefosa" Godiya tayi wani dariya tace "Ke ma dai wallahi sai kace yau
Danger ya taΙa maki aiki da zaki yi mamaki? Yanxu dai sai ki tashi kije ki dora
masa girkin da ya fi so da maganin" Momy tace "Ikon Allah, in dai
kana da kudin ka zaka ga aiki da cikawa kawai, yanxu ki dubi yanda ya shigo
mana a firgice kamar mara lafiya" Godiya tace "Ina kuwa lafiya dama
an hanasa angwancewa da amarya, sai kace baki san maza in suka kwallafa rai kan
wannan lamari ba" Suka kwashe da dariya gaba daya har da kyakyatawa, Momy
tace "Toh yanxu zan tura cikon aikin nan na karshe, yaushe zaki koma
wajensa mu je tare in masa godiya" Godiya tace "Nan da kwana uku in
sha Allah, kin ga bari in tashi in tafi mai gidana na hanyar dawowa yau"
Momy tace "Haka fa kika ce, toh shikenan sai mun yi waya dai kawai" A
haka Momy ta raka Godiya har gun motar ta sannan ta dawo cikin gidan ranta fari
Ζal, bangaren Alhaji ta nufa ta tarar da Abdul kwance a parlor idonsa a lumshe,
zaunawa tayi gefensa tana kallonsa cikin kwantar da murya tace "Babana
baka da lafiya ne?" A takaice yace "Hutawa nake yi Momy, i need
privacy pls" Momy tace "Toh shikenan, bari in sa a daura maka
favorite din ka, ina Mamata fa?" Shiru yayi yaki ba Momy amsa, Momy ta
mike ta nufi kofa ta fita daga dakin ta kullo kofar, sai a sannan tayi wani
murmushi ta koma bangarenta zata dau maganin da Godiya ta kawo mata wanda zata
zuba a cikin girkin abinda Abdul ya fi so, sai da ta kori mai aikinta can
compound sannan ta fara girka masa Pounded yam da Vegetable soup, cikin miyan
ta zazzage duk maganin da kyauta ta kawo har kala uku, wajen karfe bakwai ta
gama ta dau abincin ta kai masa dining table ta ajiye, dama iya cin sa kawai ta
girka wato malmala daya kuma ba babba ba, miyar ma Ιan tsut yanda zai cinye
gaba daya, sai bayan isha Abdul ya ci abincin da Momy tayi masa, ya bar ma mai
aiki ta kwashe sannan ya wuce sama zuwa dakinsa, Momy ta fito dakin Meemah
kenan ta bi sa da kallo har ya shiga dakinsa sannan ta bi bayansa, tana shiga
dakin tace "Wai lafiya Babana? Ko dai akwai wani matsalan da kake boye min
ne" a takaice yace "Ba komai, zan shiga wanka" Yana fadin haka
ya fara cire kayan jikinsa, Momy tace "To ka ci abincin?" Yace
"Na ci" Momy na murmushi tace "You like it?" Yace
"Miyan yayi dadi, but it's little" Tana murmushi tace "To maa
sha Allah, amma ai ya isheka dai" Yace "Ya isa" Tace "Toh
je kayi wankan ka nima bari inje in ci abinci" Fita tayi daga dakin ya
shiga bandaki, Momy na zaune parlonta tana cin farfesu dake cike cikin bowl din
hannunta Abdul ya shigo, kallonsa tayi ganin yanda ya shirya sai zuba azababben
kamshi yake, tace "Har zaka tafi Babana" Yace "Eh, sai da safe"
Tace "To ko in zuba maka farfesun ka kai ma Mamata" A takaice yace
"A'a ni ba gida zan kwana ba" Momy tayi murmushi tace "To Allah
ya tsare Babana" Yace "Ameen" Daga haka ya fita daga gidan. The
next 10 days a gidan Abdul was a living hell for Khaleesat, gaba daya Abdul ya
sauya mata a gidan ya dawo kamar wani monster, dukanta da yace ya dena sai dai
bai samu slightest opportunity din yin hakan ba, kawai ya maida ta punching bag
dinsa a gidan barin in ya zo gareta bai samu biyan bukata ba, kuma bai fasa
zuwa mata da bukatar tasa ba amma as usual sai dai kawai ya doketa ya fita bai
cimma burinsa ba, kwata kwata ya dena cin abincin gidan, ya dena kwana sai
sanda ya ga dama, duk wani ingredients din girki ya dena siyowa sai dai tayi ta
cin indomie, hatta bottle water ma da ya kare yaki siyowa, kuma ko Satchet
water yaki siya ya ajiye, sai dai ta sha ruwan pampo, gaba daya Khaleesat ta
fita hayyacinta a gidan ta dawo kamar ba Khaleesat ba, ga karyewa da gashinta
ya dinga yi sosai saboda tsananin damuwa, kana ganinta kasan tana cikin
jarabawan rayuwa, bata da aiki sai kuka sai kuma addu'a da sallan dare, gaba
daya ta maida duk lamarinta ga Allah, kullum haka take kwana ta tashi da
zazzabi amma ina taga fuskar ce masa bata da lafiya, sai dai tayi ta daurewa a haka,
in ma ta gaya masa don ya zagi iyayenta ba komai bane a wajensa, in zazzaΙin ya
rufeta sai dai ta kwanta har sai sanda zata ji dama dama sannan ta daure ta
tashi. Ranan Friday tana dakinta a kwance ko breakfast bata yi ba har kusan
karfe sha biyu da rabi, zuwa yanxu ta gaji da cin indomie da ma tana da
dakakken yaji sai ta dinga yin ko shinkafa da mai da yaji ne amma babu, indomie
duk ya fita a kanta bata iya ci ko ta dafa, gashi haka take dafasa babu yaji
balle albasa, bude kofar dakin nata yayi ta mike zaune da sauri tana kallonsa
gabanta na faduwa, kamar zai fasa mata dodon kunne taji yace "Ina
Cufflinks din da na bari a parlor shekaranjiya?" Sauka tayi daga kan gado,
ita dai ta gyara parlon ta goge ko ina jiya da yau amma bata ga wani Cufflinks
dinsa ba, a hankali tace "Toh bari in duba a parlon" Wani mugun kallo
yake mata hakan yasa ta raΙa tabi ta gefensa ta fita daga dakin zuciyarta na
bugawa ta tafi parlor tana dudduba Cufflinks din, da alama masallaci zai je don
yin sallan juma'a, babu ta yanda za ace iya Cufflinks din da yake tambayarta
yake da shi a gidan, amma sbda neman hanyar da zai musguna mata yake shi yasa
zai saka ta gaba ta fito da abinda bata gani ba, kuma rabonsa da gidan tun
shekaranjiyan, tana cikin dube dube a parlon shi kuma yana tsaye fuskarsa a
murtuke alamar he is loosing his patient aka bude kofar parlon, Momy ce ta
shigo da Cousin sis din Alhaji Musa, warce suke kira da Ummu, Yau kwanan Ummu
uku a Nigeria daga Dubai inda take aure da yaranta duk a can, kuma a yau zata
koma Dubai shi ne ta sa a kawota ta ga matar Abdul kafin a kai ta airport, duk
da Abdul yaje ya gaisheta san da ta zo, Khaleesat da duk a rude take ta kalli
Abdul a hankali tace "Wallahi ban gansa ba da nake gyaran parlorn jiya da
yau, kilan ka sha'afa ko a daki ka bar su ne ka manta" Bata rufe baki ba
ya sauke mata wani gigitattcen mari yana huci ya fixgota yace "Ni zaki
gaya ma a daki na bar su?" Ta dafe kuncinta hawaye cike idonta tana
girgiza masa kai, nan da nan fuskarta yayi ja, ko minding uwar sa da Cousin sis
din Babansa da suka shigo parlon bai yi ba, duk suka yi cirko cirko baki bude
suna kallon ikon Allah, cikin tsawa yace "Baza ki fito min da shi ba sai
na maki dukan tsiya a nan?" Tana shesshekan kuka tace "Nace maka ni ban
ga wani links din ka ba wallahi...." Bata rufe baki ba ya sake sauke mata
wani wawan marin, Momy da taji ranta yayi fari tass cikin kwantar da murya tace
"Subhanallahi, Babana ka bi a hankali, hakuri ake Babana" Ummu ta
jefar da handbag dinta kan kujera ta nufesa cikin bacin rai tace
"Abdallah?? kana hauka ne kake marin mace haka don uban ka?" Momy ta
wani hade rai tana kallon Ummu, Abdul yaki ko kallon Ummu dake masa magana, ya
wani haure Khaleesat a mugun fusace har sai da ta fadi kasa, Wani Mari Ummu ta
sauke masa a fuska, cikin fushi tace "Ashe kai jahili ne shashasha ban
sani ba?" Juyowa yayi yana kallon Ummu da mamaki baya ko kiftawa, Momy ta
dinga huci tana kallon Ummu ita ma, nan da nan idanuwanta suka kankance don
bacin dai, tunda ta haifi Abdul bata taΙa marinsa ba haka ma ubansa sai gashi
yau an maresa a gabanta, Abdul dake kallon Ummu kamar me counting din words
dinsa yace "Ummu akan wannan jakar yarinyar kika mareni??" Ummu tace
"Na mare ka din, zaka rama ne? Wawa kawai mahaukaci ka saka yarinya karama
haka a gaba kana duka? Tarbiyar da aka maka kenan? In na san abinda zan zo in
tarar a gidan ka kenan uban me zai kawo ni?" Abdul da idanuwansa suka
sauya launi ya kalli Khaleesat yace "Ki je... na sake ki" Yana fadin
haka ya dau makullin motarsa ya fice daga parlon kamar zai tashi sama,
Khaleesat ta bi sa da kallo babu ko kiftawa kamar bata fahimci abinda yace ba,
Momy ta sauke wani bayanannen ajiyar zuciya tace "To Alhamdulillah,
Alhamdulillah, Alhamdulillah" Sai kuma ta kalli Ummu tace "Ke kuma Muhusina
kin ci darajar Musa banda haka da babu uban da zai hanani rama ma Ιa na marin
da kika masa don tunda na haifesa ban taΙa marinsa ba haka ma ubansa, kuma
Abdul yayi min dai dai hukuncin da ya dauka, dama me ake da auren er gidan
talakawa er gidan matsiyata? Ai ba class din mu bace ita, kuma duk bama goyon
bayan wannan tsinannen auren, kawai irin wannan rana muke ta jira gashi Allah
ya kawo mu cikin ruwan sanyi, Alhamdulillah Allah na gode maka, Allah na gode
maka, yau zan yi bacci cikin farin ciki da kwanciyar hankali burina ya cika,
effort dina kuma bai tashi a banza ba" Momy na kai wa nan ta nufi kofa
tana tafiya gansan gansan farin ciki fal a ranta mara misaltuwa tana murmushi
ta bude kofar parlon, Khaleesat ta bi Momy da kallo with shock ko kwakkwaran
motsi ta kasa tsabar mamaki, maganganun Momy suka dinga yawo a kanta kamar a
mafarki, Ummu ta zauna gefen kujera ta dafe kanta tace "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un" Sai a sannan Khaleesat taji hawaye masu zafi na
silalowa fuskarta, ta mike tana tafiya a hankali ta tafi daki ta dauko hijab
dinta har kasa ta fito.....
[6/26, 9:27 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat na
fitowa parlor suka hada ido da Ummu dake kokarin kiran Alhaji Musa da wayarta
cikin bacin rai, sunkuyar da kai Khaleesat tayi tana goge hawayen dake ta zuba
idonta, Ummu tace "Zo ki zauna tukunna diyata" Khaleesat tayi shiru
bata ce mata komai ba don har cikin ranta bata ji zata iya zama a parlon ba
kamar yanda Ummu ta umarceta, amma kar tayi disrespecting matar duba da tsaya
mata da tayi sanda Abdul ke ci mata mutunci yasa kawai ta duka kasan carpet
kanta a kasa, Sau uku Ummu na kiran wayar Dad din Abdul, daga karshe ya daga
kiran, cikin fushi ta fara koro masa abubuwan da ta zo gidan Abdul ta tarar da
kuma abinda Abdul ya aikata daga karshe, Alhaji Musa dake ta sauraronta ya jira
har ta gama, sannan yayi gyaran murya yace "Ai ina ganin Muhusina wannan
ba issue bane da zaki shigar da kanki farat daya, ke da ba ma a kasar kike ba
zuwa kawai kika yi, i don't think it's proper kiyi involving kanki sama ta ka,
it's not done that way, alright? kuma tunda kika ga ya saketa definitely yana
ganin hakan shi ne dai dai so meye zaki damu kanki, ko mu iyayensa we are not
in the rightful place to question his act, okay? decision dinsa ne, so just
stay out of what u know nothing about Muhusina, ba naji kin ce flight din karfe
biyu gare ki ba? Ko kin daga tafiyar taki ne?" Kasa cewa komai Ummu tayi
tsabar mamaki, kana ganinta kasan she is speechless, ita dai Khaleesat kanta na
kasa don ba handsfree Ummu ta saka wayar ba balle ta san abinda Dad din Abdul
ke cewa, a hankali Ummu tayi ending call din ta ajiye wayar a gefen kujera don
ba ma ta da amsan da zata ba Ιan uwan nata, sosai jikinta yayi sanyi, yanxu
dama Family din Alhaji Musa basu canza ba daga yanda ta san su tun tale tale,
don ita sai tayi shekara aru aru ba a ganta a Nigeria ba in ba muhimmin abu
bane ya kawo ta, Momy ce ta bude kofar parlon fuskarta a murtuke, ashe all this
while tana kofar gida tana jiran ganin Khaleesat ta fito ta bar gidan amma
shiru shiru bata ga ta fito ba, Momy na kallon Khaleesat tace "In dai ba
gidan ubanki bane ko na uwarki nan din tunda har ya furta ya sake ki ai kya
fito ki kama gabanki, ko zaman ubanki kike yi har yanxu? Da wani abinda kika zo
gidan da shi ne kika yi waya a zo da mota a kwashe maki ko yaya?" Ummu ta
kalli Momy tana girgiza kai cike da takaici tace "Ki ji tsoron Allah
Hajiya, ki ji tsoron haduwar ki da Allah, ke ma fa kina da yaran nan
mata...." A mugun fusace Momy ta karaso cikin parlon ta dakatar da ita
tana nunata da Ιan yatsa tace "Kin ga wannan family issue ne ki cire bakin
ki a abinda bai shafeki ba Muhusina don ke bare ce a wannan Ιangaren, kuma ba
ke kika haifar min Abdul din ba da kike neman cusa kai abinda ya shafi
rayuwarsa, who are you to even interfere? Ko Musa kin zata ya isa ya hana Abdul
abinda yayi niyyar zai yi ne? To wallahi ki cire bakin ki da idonki akan abinda
ya shafi zuri'ata, 'ya ya mata kuma dama ko wani shege ya haifa ai, meye a
ciki" Momy na kai wa nan ta kalli Khaleesat cikin daga murya tace
"Baza ki tashi ki san inda dare yayi maki ba ko sai na kira su Meemah sun
fitar min da ke daga gidan nan??" Mikewa Khaleesat tayi bata bari sun hada
ido da Momy ba ta nufi kofa tana tafiya a hankali, Ummu ta kasa cewa komai tana
kallon Momy tana girgiza kai, sai da Khaleesat ta fita daga compound din gidan
gaba daya sannan ta fara share hawayen dake sauka idonta, tunanin yanda zata
koma gida bata da ko sisi ta fara yi, tafiya me nisa tayi har ta iso titin da
zata samu abun hawa, daga karshe bayan jiran kusan minti sha biyar ta samu wani
adaidaita sahun da zai kai ta Mariri a dubu biyu da dari biyar, in taje gida
sai ta basa kudinsa, har Khaleesat ta isa gida hawaye ya ki tsaya mata a ido,
ita kanta bata san yanda take ji a ranta ba game da abinda Abdul yayi mata,
farin ciki take ko akasin haka har sannan ta kasa ganewa a zuciyarta, but she
was deeply hurt and pained, daurewa kawai take kar ta fashe da kuka a adaidaita
sahun, bayan ya tsaya dai dai kofar gidansu ta sauka tace "Za a kawo maka
kudin yanxu, nagode" Daga haka ta shiga cikin gidansu, a tsakar gida ta tarar
da kishiyoyin Ummanta sun gama abincin siyarwansu na yamma yara za su fita da
shi talla, ta gaishesu ba tare da ta bari sun hada ido da su ba direct ta nufi
dakin Ummanta, duk suka bi ta da kallo, Aunty Farida da fitowar ta daga bandaki
kenan zata yi alwala don lokacin sallan La'asar yayi ta ajiye butan hannunta ta
bi Khaleesat da kallo ita ma duk da Khaleesat bata ganta ba, Khaleesat na shiga
dakin Ummanta ta fada jikinta ta fashe da kuka a hankali, Kasa cewa komai Umma
tayi tana kallonta da mamaki, sai ga Aunty Farida ta shigo dakin ita ma, sosai
gabanta ya fadi ta tsaya nan bakin kofa tana kallon Khaleesat, da kyar Umma ta
dago kanta cike da karfin hali tace "Me ya faru?" Khaleesat ta kasa
cewa komai tana kuka sosai, Umma da nan da nan ita ma hawaye ya cika idonta ta
rungumeta bata sake ce mata komai ba ta bar ta tayi kukan me isarta, cikin
sanyin jiki Aunty Farida ta karasa cikin dakin ta zauna gefen katifa tayi
shiru, Umma ta goge idonta tana patting Khaleesat a baya a hankali trying to
calm her amma bata hanata kukan da take ba, sun fi minti biyar a haka sai ga
Mama Zubaida ta dage labulen dakin tace "To Ιan sahu dai na ta jira a mika
masa kudinsa a kofar gida" Magana take amma idonta na kan Khaleesat da
Umma, tsabar gulma yaron makota me adaidaita sahun ya aiko cikin gidan amma
tayi karaf ta mike bayan yaron ya sanar masu ta nufo dakin Umma taki barin
yaron ya karasa, don tun shigowar Khaleesat suka baza kunnuwa ko za su ji wata
magana amma shiruu basu ji ko tari ba a dakin Umma, Aunty Farida ta dau handbag
dinta ta fita daga dakin ta sake labulen daga hannun Mama Zubaida dake rike da
shi, sannan ta fita zuwa gun mai adaidaita sahun, sai a sannan Umma ta iya daga
kan Khaleesat, suna hada ido Khaleesat ta sauke jajayen idanuwanta, Umma tayi
karfin halin cewa "Me ya faru Jiddah?" Khaleesat ta sauke idonta wasu
hawayen na zuba idonta tace "Yace ya sakeni" Hawayen dake makale idon
Umma ya zubo tana kallon Khaleesat babu ko kiftawa, Khaleesat ta rufe fuskarta
jikin Umma ta fara wani sabon kukan, Umma ta rungumeta sosai, cikin rawan murya
tace "Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi a gare ki, kiyi hakuri kin
ji?" Kai kawai Khaleesat ke gyada mata tana shesshekan kuka, a haka Aunty
Farida ta dawo dakin ta same su, Aunty Farida ta zauna gefen Umma tana
kallonsu, Da kyar Umma ta kalleta tace "Wai sakin ta yayi" Ζasa cewa
komai Aunty Farida tayi tsabar yanda ta girgiza, ta dinga kallon Umma babu ko
kiftawa, nan da nan ita ma hawaye ya cika idonta, after a while ta goge hawayen
dake zuba idonta ta fita ta dau buta tayi alwalanta ta dawo ta tada sallah,
Umma ta dago Khaleesat da tayi shiru a jikinta, sai taga bacci take, Khaleesat
ta bude ido a hankali, Umma tace "Kin yi sallah ne?" Girgiza mata kai
Khaleesat tayi, Umma tace "Ki je kiyi alwala kiyi sallah" Khaleesat
ta mike tana tafiya a hankali ta fita daga dakin. Khaleesat na idar da sallah
Aunty Farida na kallonta tace "A zubo maki abinci?" Khaleesat ta
girgiza mata kai cikin sanyin murya tace "Na koshi" Daga haka ta mike
ta hau saman gadon Ummanta ta kwanta, nan da nan bacci me nauyi ya dauketa,
daga Umma har Aunty Farida babu wanda ya iya cewa komai a dakin, suna ta zaune
har kusan karfe shidda, ita dai Aunty Farida tana rike da Al-qur'ani tana
karatu silently a ranta, su Islam suka dawo hadda wanda suke zuwa har ranan
friday, Umma ta sa su je su hura gawayi su dora girki, muryar Nenne suka ji a
tsakar gida tana cewa "To Zubaida sai ki dau na annabawa don kin tafka
asara lafiyayye yau, almajirai na mugun wasa suka hamΙare Suwaiba tallan da
kika dora mata ya kife a kasa, su kuma suka tsere, sanin azaban da zaki mata ta
taho ta sameni tana kuka kamar ranta zai fita, yanzu haka tana can gidana nace
tayi zamanta, ga robobin tallan da faranti nasa an kwaso maki kayanki, ko roba
daya bata siyar ba suka hambare farantin" Mama Shatu ta saki salati tana
kallon Mama Zubaida da ta nemi waje ta zauna jin abinda Nenne ke cewa, Nenne ta
kwashe da dariya har da kyakyatawa tace "Yaran layi kuwa duk suka wawushe
abincin da ya zube a kasa suka loda ma cikin su" Daga haka ta nufi dakin
Umma ta dage labulen tace "Zahra'u kina da er kuka ko kubewa ki tsam inje
in Ζada miya" Umma bata yarda sun hada ido da Nenne ba tace "To bari
in duba maki, Ina wuni" Nenne tayi mitsi mitsi da ido tace "Wacece
wancan kuma a kwance kan katifarki?" Umma dai bata ce komai ba ta tashi
zata dauko ma Nenne kubewa busasshe, Aunty Farida ta gaida Nenne ba tare da ta
kalleta ba, Nenne na kallon Khaleesat tace "Wai wa nake gani kamar
Khaleesah a kwance?" Aunty Farida ta ajiye Qur'anin hannunta still bata
kalli Nenne ba tace "Ita ce" Nenne ta shigo dakin tace "Wato ni
dai shikenan kun nuna mata banda matsayi da har zata shigo unguwan nan ta
karasa gidana ta gaisheni ko? In ma bata je ta gaisheni don Allah ba ai sai
tayi don ubanta Ali tunda ni na haifesa har ya haifeta" Daga Umma har
Aunty Farida babu wanda yace ma Nenne komai, Nenne tace "Mijin ne ya
kawota? Shi ma ai shegen ne tunda ba karasawa yake yi gidana ya gaisheni ba,
banda kaddara a ina za mu san sa har mu aura masa Khaleesat mutumin da baya
ganin mutuncin mu, kana masa magana yana amsa maka cikin gadara da yanga wai
shi Ιan Alhaji Musa, waye bai san satan da ubansa ya zabga a gwamnati ba kafin
ya koma kasuwanci, ko don muna kauda kai?" A takaice Aunty Farida tace
"To sakin ta yayi..." Nenne ta juya ta kalli Aunty Farida na en
sakwanni, can tace "Ban ji me kika ce ba Parida?" Aunty Farida da har
hawaye ya kawo idonta tace "Sakinta Abdul din yayi" Nenne ta kasa
motsi a inda take tsaye, a hankali tace "Sakin aure ko sakin me?"
Aunty Farida dai bata tanka ta ba, ita dai Khaleesat na kwance tayi backing din
Nenne bayan surutunta ya tasheta daga baccin da take, Nenne ta saki wani salati
muryarta na rawa tace "Wato dai Ιan nawa ne ba a son a ga ya zauna lafiya
a gidan duniya kamar yanda kowa yake zaune" Fita tayi ta koma tsakar gida
ta rushe da kuka sosai tace "Allah ya isa tsakanina da Zahra'u da er ta,
babban burin su a duniya su ga Ali ya tagayyara, babban burinsu su ga Ali cikin
mawuyacin hali cikin tashin hankali, banda haka ko dukanta da zaginta Awdul ke
yi a gidan bazata hakura ta zauna ba albarkacin ubanta? Shi ne har zata amshi
sakin da yayi mata hannu bibbiyu ta dawo mana gidan nan domin shari'arsu da Ali
ya dawo sabo?" Mama Zubaida da Mama Shatu tuni suka mike tsaye jin abinda
Nenne ke cewa, cikin kuka Nenne tace "Ban taΙa ganin er da burinta taga
ubanta a walakance ba, kun ga ai ta dawo taga yanda za ayi da uban nata ko
furson din za a mayar da shi ko hukuncin rataya za a yanke masa, ni dai na
shiga uku na lalace, Allah ya hada Ali da mata da 'ya yan da basa tausayinsa
kuma su za su yi ajalinsa, yanxu in Khaleesat er arziki ce da yace ya saketa ba
sai tace babu inda zata je ba tunda bautar Allah take??" Malam Ali ne ya
shigo gidan da er taliyar Hausa da ya siyo cikin Bacco bag, Nenne na ganinsa ta
rushe da sabon kuka tace "Wallahi ta kashe auren ta dawo taga yanda za su
yi da kai Ali" Malam Ali ya tsaya yana kallon Nenne, Nenne na fyace majina
tace "Ga ta can dakin uwar a kwance tana jiran taga da wace motar za a zo
a kwashe ka, dama wallahi tun da muka je gidan da parida nasan za a samu babban
matsala don babu alkhairi a ran Parida, kuma in bata yi hankali ba daga ita har
Zahra'un sai dai su koma kasar su, duk wanda baya son kwanciyar hankalin Ιa na
to kwanciyar hankalina ne baya so wallahi" Malam Ali dai ya nemi tabarma
ya zauna ya kasa cewa komai, Mama Zubaida tace "Ikon Allah, kuma abinda ya
faru kenan ni Zubaida? Aure wata daya da yan kwanaki amma har an yi saki? Yanxu
zawarawa har biyu garemu a gidan nan kenan?" A fusace Nenne tace "Ta
zauna tayi ma uban wa zawarci a gida? Ai ko taki ko ta so sai naje na ba Awdul
hakuri ya maidata dakinta don kaf zuri'armu babu wanda ya taΙa zawarci sai in
mutuwa mijin yayi, to ko bakin halinta bai isa ya sa ya korota ba bai shirya
ba, Khaleesah ce duk wani mummunan bakar maganar da ya zo bakinta take yaΙa ma
mutum, ko kuma in ka gaya mata abinda bai gamsheta ba tayi maka wani kallon
walakanci da kaskanci da tula tulan idanuwanta, wani lkcn kana mata magana tayi
maka banza wannan duk mun san halinta ne ba wai sharri ba, ga nukurci kamar er
sarkin kutare, to ai ba ko wani namiji bane zai dau wannan, don haka zan je in
basa hakuri ya dubi girman Allah ya maidata dakinta..." Mama Shatu tace
"Toh ko samun sa kika yi ai sai yayi niyya zai maidata Nenne, in zai iya
ai bazai fara sakin ta ba" Wani zagi Nenne ta kundumo mata a fusace, dai
dai nan aka rafka sallama a kofar gida, Malam Ali ya mike tsaye yana kallon
hanyar fita gidan, Nenne tayi tsit zufa na keto mata, can ta fara kuka a
hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, Zahra'u dai bata zo
mana pamily da alkhairi ba, kun ga har an zo tafiya da shi" Mama Zubaida
ce ta yafa gyale ta nufi hanyar fita daga compound din, wani mota taga anyi
parking a kofar gidan, mutumin dake tsaye kusa da motan ya nufota yana kallonta,
Mama Zubaida ta gaishesa har da risinawarta, ya amsa yace "Mai gidan na
ciki kuwa?" Mama Zubaida tace "To Allah ya sa dai lafiya Malam"
Mutumin yace "Eh to, ni Dreban Alhaji Musa ne, an bani sako ne in kawo ma
mai gidan" Mama Zubaida tace "To ni mai dakinsa ce, ni ce uwar
gidansa, ko zan iya karba in mika masa, don baya jin dadi ne" Mutumin yace
"To ba damuwa" Hannu yasa a aljihu ya ciro Envelope ya mika mata, ta
amsa yayi mata sallama ya koma zai shiga mota, Mama Zubaida ta koma gidan tana
juya takardan ita kanta sai da gabanta ya fadi don irin wannan in an kawo ai
sammaci yake nufi, Nenne na ganin Envelope din hannun Mama Zubaida ta rushe da
matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, shi kenan Ali
a haka zai kare kenan ni Zainabu? wani takardan kotun aka sake kawo masa
kenan?" Malam Ali ya amshi Envelope din hannun Mama Zubaida ya yage ya
ciro takardan ciki ya warware, "Ni Abdallah Musa, na saki er ku Hauwa saki
daya, biyu, uku" content din dake jikin takardan kenan, Shatu ta amshi
takardan hannunsa tun da tayi karatun primary, tana duba takardan ta karanto
abinda ke jiki amma fa da kyar tana in ina, Nenne ta tsaida kukan da take bayan
taji Shatu ta karanto rubutun jikin takardan tace "Ji tsinanne la'ananne
matsiyaci? saki har uku kamar warce ta kashe ubansa ko uwarsa? To Allah
Ubangiji ya tsine masa albarka, dama banda kaddara uban me Khaleesat zata ci da
Ιan barawon Gwamnati? ubansa barawon gwamnati shi kuma Ιan daba, Ai mu wannan
sakin abun farin ciki ne a gare mu gaba daya tunda ba na'am muka yi da auren
ba, kuma ko yau Khaleesat ta fita sai ta samu mijin nuna ma tsara da ya fi sa
komai wallahi, bakin cikinmu daya zawara da ya maida ta, dama kullum da fargaban
aurenta da shegen nake don har raina bana son sa babu yanda na iya ne kawai,
banda jarabawa wasu iyayen kwarai ne za su dau er su su ba tsinanne irin Awdul?
Khaleesah sai dai kawai tayi hakuri don cuta kam Ali ya cuceta, ya cuci
Rayuwarta, don duk shi ya ja mata wannan masifa, da suka ce maka er ka suke so
bayan an fito da kai furson in kai uba na gari ne sai ka cije kace sam baka
yarda ba sai dai a maida ka furson din ka mutu a can, amma saboda tsoron azaban
duniya ba na lahira ba ka zabi ka sadaukar da erka don samu encin kanka, to
gashi nan bayan ya rabata da budurcinta ya sako mana ita, dama auren sha'awa
kawai yayi da ita, Allah ya isa bamu yafe masa ba wallahi" Nenne na kai wa
nan ta fashe da kuka ta jawo kujera er tsugunno ta zauna tana rera kuka sai
kuma tace "To yanxu ko zuwa za muyi mu basu hakuri ya dubi girman Allah ya
maidata tunda malamai sun ce saki uku a madadin daya yake" Wajen karfe goma na dare Aunty Farida ta
zauna gefen Khaleesat dake zaune da cup din kunun da Umma ta dama mata tunda ta
kasa cin abinci, Aunty Farida tace "Baki shanye kunun bane?"
Khaleesat ta dau cup din ta ci gaba da shan kunun a hankali, Aunty Farida tayi
shiru bata sake cewa komai ba tana kallon buhun abubuwan da ita da Umma suka
hada zata kai ma Khaleesat gobe, don da gobe zata je wajenta, tun daga dakakken
yaji, kubewa busasshe, kuka, kanwa, su citta da kanumfari, gyadar miyar, har da
garin danwake da sauran abubuwa da yawa duk su ne a cikin buhun, ga turaren
wuta da suka siya mata masu kyau, Aunty Farida ta sauke boyayyen ajiyar zuciya
ta kalli Khaleesat da ta kasa shanye kunun hannunta, a hankali ta jawota
jikinta, soothingly tace "Kiyi hakuri Daughter, Allah yasa hakan shi ne
mafi alkhairi gare mu baki daya, kar ki saka komai a ranki kin ji?"
Khaleesat ta gyada mata kai, Aunty Farida bata sake ce mata komai ba don ita
bata ma son ta tambayi abinda ya hadasu don mayar da maganar bacin rai kawai
zai kara masu, Ita dai Umma na zaune kan darduma Islam na bacci a jikinta,
Maman Salame ce tayi sallama ta shigo dakin tana kallon Umma tace "Wani
labari ne wannan nake ji a garin nan Zahra'u?" Umma dai tayi shiru tana
kallonta, Maman Salame ta zauna kan tabarma tana kallon Aunty Farida da
Khaleesat dake gefenta tace "Farida" Aunty Farida ta Ιan yi murmushi
tace "Ina yini Maman Salame" Maman Salame tace "Wai da gaske ne?
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Aunty Farida tace "A ina kika ji
Maman Salame?" Maman Salame tace "Ga labari nan ya baza Mariri?
Dawowata daga Wudul kenan kusan mutane biyar suke gaya min haka a hanya tun ban
karasa gida ba, wallahi buhun hannuna kawai na ajiye bayan na shiga gida na yo
nan" Aunty Farida tace "To Allah ya sa mu dace" Maman Salame
tana kallon Khaleesat cike da tausayinta tace "Garin yaya haka
Khaleesah?" Khaleesat ta sauke idanuwanta bata ce komai ba, Maman Salame
tace "To Allah Ubangiji ya sa hakan shi ne mafi alkhairi gare mu baki
daya, in kuma auren bai kare ba Allah ya kaddara za ki koma sai ki ga an
koma" Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai saki uku ne Maman
Salame" Maman Salame ta kasa cewa komai tana kallon Aunty Farida, kana
ganinta kasan sosai jikinta yayi sanyi, ita dai Umma babu abinda tace a dakin,
bayan kusan minti goma Maman Salame ta mike a sanyaye tace "Toh Allah ya
sa mu dace, Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi gare mu duka, sai na shigo
da safe in sha Allah" Umma tayi mata sallama, Maman Salame ta fita daga
dakin rai babu dadi, sarai Umma tasan kishiyoyinta ne suka baza labarin a
garin, don ko Nenne bazata gaya ma kowa wannan labarin ba ita da ta tsani tonan
asiri, Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya don exactly tunanin da Umma take yi
ita ma shi ne a ranta, Khaleesat ta kalli Aunty Farida a hankali tace
"Aunty kina da number Safiyyah?" Aunty Farida tace "Ina da
shi" Khaleesat tace "Ina son zan kirata ne" Aunty Farida tace
"Babu kati a wayar, kuma yanxu dare yayi, ki bari gobe da safe sai kiyi
magana da ita" Khaleesat ta gyada mata kai sannan ta mike tayi kwanciyarta
saman gadon Umma, yaron Mama Shatu ne yayi sallama bakin kofar dakin Umma ya
daga labulan yace "Wai Babanmu yace Khaleesat ta je" Umma da Aunty
Farida dai sai kallon yaron suke, ya juya ya bar bakin kofar, Khaleesat ta mike
zaune bayan taji abinda step brother dinta yace, tun dawowarta gidan ita ko
haduwa da baban nata bata yi ba, ta sauka daga saman gadon tana gyara hulan
kanta ta fita daga dakin Umma ta bi ta da kallo taji hawaye na taruwa idonta,
Khaleesat na tafiya a hankali ta karasa har bakin kofar Babanta don yana zaune
kan tabarma shi kadai a bakin kofar nasa, dukawa tayi daga gefen tabarman ta
sunkuyar da kanta cikin sanyin murya ta gaishesa, maimakon ya amsa sai taji a
hankali yace "Kiyi hakuri Jiddah, i failed you as a father, i caused you
all this, but everything happened because I am a nobody, everything happened
because...." Shirun da taji yayi ya sa ta daga kai ta kallesa taga hawaye
a idonsa, bata san sanda ta fashe da kuka ba, yace "I am sorry for failing
you daughter, albarkacin biyayyan da kika min baza ki taΙe ba in sha Allah, my
wish for you since u were born was to give you the best of everything i could
amma Allah bai nufa hakan ba kaddara ta fada min...."
[6/27, 8:51 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Washegari da
safe har karfe goma saura Khaleesat bata tashi baccin da take ba, daga Umma har
Aunty Farida babu wanda ya tasheta don duk sun san bata yi wani baccin kirki ba
daren jiya, daga wayewar gari zuwa lokacin mutanen da suka shigo dakin Umma yi mata
Allah ya kyauta da abinda ya faru sun fi goma, don gaba daya labarin ya gama
bazuwa garin, Aunty Farida ta kalli Umma bayan wata makociyarsu da ta shigo
jajen ita ma ta fita, a fusace tace "Don Allah ki dena tanka masu Umma, ki
nuna ke baki ma san jajen uban me suka shigo yi maki ba, wallahi banda ke in
ban ci kaza kazan mace ba ta sake shigo mana dakin nan ace ba ni ba, wannan ai
iskanci ne" Umma tace "To ya kike son inyi Farida? kinga ai muna
mutunci sosai da su shine har ya sa suke shigowa, duk warce kika ga ta shigo
dakin nan to muna mutunci sosai ne da ita, kin ga ai bazan masu rashin mutunci
ko wani abu ba, wanda ya yaΙa labarin a garin ai shine vabvan munafuki ba wanda
ya shigo jajenta maka ba, kuma naga dai ba kan Khaleesat farau ba mutuwar
aure" Aunty Farida ta mike tace "Ban taΙa ganin inda ake shigo ma
mutum jajen mutuwar aure ba sai a garin nan, kuma wannan ba komai bane banda
salon gulma da munafurci" Daga haka ta fice daga dakin zata duba ruwan
zafin da ta dora kan wuta, Umma ta kalli Khaleesat da tayi backing dinsu tana
bacci, ta kai hannu ta dafata, tayi kasa da murya tace "Har yanxu baccin
dai Khaleesat?" Juyowa Khaleesat tayi tana murza ido, sai kuma ta mike
zaune, Umma na kallonta tace "Jiya da daddare baki ci abun kirki ba, ki je
ki wanke baki ki zo ki karya, ga wainar shinkafa na sa an amso maki tun daxu,
kar ya huce" Khaleesat ta jawo hijab dinta ta saka sannan ta sauka daga
kan gadon, ta tafi gun akwatinta da ta dawo da shi daga America ta duΖa ta bude
jakar ta ciro Shower gel dinta da sponge, sai toothpaste da Brush, Umma dai
kallonta kawai take har ta mike zata fita daga dakin Umma tace "Tunda
wanka za kiyi kice Farida ta juye maki ruwan zafin, tana waje" Khaleesat
tace "To Umma" Daga haka ta fita daga dakin Umma ta bi ta da ido,
Khaleesat bata ko kalli inda kishiyoyin Ummanta suke ba da dukun dukun din
zannuwan jikinsu kamar masu yin kuli kuli, ta jira Aunty Farida ta juye mata
ruwan zafi a bucket ta surka mata sannan ta kai mata har bandaki, bayan ta
shiga wankan Aunty Farida ta dora wani ruwan ta koma dakin Umma, Mama Zubaida
ta taΙe baki tana murmushi ta kalli Mama Shatu tace "To kuma yanxu ko da
uban me za ayi mana takama?" Mama Shatu ta kwashe da dariya tace "In
kin tambayeni in tambayi wa? Ba ke kike kokwanton maganar Malam ba da yace
auren karkari ayi wata daya ya sakota, to kin dai ga kwalliya ta biya kudin
sabulu, sai ki dena cewa kinyi asaran kudin ki, ji yanda hankalinki ya tashi
ranan da muka je gidan da Nenne kin ga katon gida ta shiga dakin can ta fito ta
shiga wancan ta fito kin zata watayawa take a gidan, ni dama ina kallon kwayar
idonta nasan ubanta take ci a gidan, sam ban ga alamar kwanciyar hankali ba don
duk a firgice na ganta" Mama Shatu ta sauke ajiyar zuciya ta rike haΙa
tace "Ohhh.... Ba karatu a Amurka, ba Miji, ga zawarci, wannan asara da
yawa take ni Aisha, wannan shi ne ga koshi ga kwanan yunwa, an ga samu an ga
rashi, ina Zahra'u zata saka ranta ta ji dadi" Mama Zubaida tace "Ke
baki ga haka ya korota daga ita sai kayan jikinta ba, ko er jakar hannu da ake
saka waya fa bata taho da shi ba, dama a haka ya dauketa, kuma kinga ko tsinke
ba a kai mata ba dama" Duk suke kwashe da dariya har da kyakyatawa, Mama
Shatu tace "Sai a dawo a ci gaba da alalan da aka watsar, don ita kanta
Faridan Allah ya sa Ιan zaman da ta dawo suka yi ba a cinye jarin nata ba, nan
nan a gabanmu aka yi ta hade haden garin Ιanwake da su kuka da kubewa za a kai
ma Khaleesat ashe ashe korota zai yi, ni anjima ma zan shiga a tsam min garin
danwaken don naga da yawa suka yi" Tana dariya ta kare maganar, Mama
Zubaida tace "Ae wallahi ko tsirara zan yi na gwammace inyi da dai Zahra'u
taji dadi da 'ya yanta, in ke kin manta irin cin Ζashin da Malam ya dinga mana
bayan ya aurota ni ban manta ba, duk muka zama bora a gidan nan, baya ganin
kowa sai Zahra'u tunda da asirinsu na buzaye ta shigo gidan, banda dai dama tun
asali idonmu ya bude da Malamai ai da tuni ya sake mu tun bai samu karayar
arziki ba, hatta kayan dakin da ya siya mata sai da na zaga na koma kasuwa na
tambaya aka ce min nata duk yafi namu tsada, gashi yaranta su ne 'ya yan so
barin Khaleesat din nan ai mun sha bakin ciki iri iri Shatu, Ita fa har Umra
tayi sannan ga Hajji, mu kuwa iya Hajji kawai muka je mu ka yi tsabar ya maida
mu 'yan iska" Mama Shatu ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Ki bar
tuna min wannan takaicin Zubaida, banda a tsaye muke ai da wani labarin ake
yanxu ba wannan ba, haka mu ma muka yi ta hadata da Malam da taimakon asiri,
amma shegiyar bata yi zuciya ta koma kasar su ba da ya fara cin ubanta a gidan,
in sha Allahu yanxu ta fara ganin bala'i ita da zuri'arta su da jin dadi ko
farin ciki har abada, hatta yan biyun nan ya kamata mu fara miΖa sunansu yanxu
kar lokaci ya kure, don naga wani farin jinin jama'a da suke da shi, duk inda suka
shiga sai an tankasu ayi ta nan nan da su" Shigowar Nenne gidan yasa suka
yi shiru, duk suka gaisheta ta amsa ba tare da ta kallesu ba ta nufi dakin Umma
da er ledanta a hannu, duk suka taΙe baki suna bin ta da kallo har ta shiga
dakin, Umma da Aunty Farida suka gaida Nenne bayan ta shigo dakin, Nenne ta
amsa bayan ta ajiye ledan hannunta tace "Ina Khaleesar take?" Aunty
Farida tace "Ta shiga wanka" Nenne tace "Atoh dai, dama ina zata
tsaya bakin cikin shege ya kasheta, harkar gabanta kawai zata ci gaba da yi
kamar babu abinda ya faru, da auren wannan gansamemen mutumin da rashin aurensa
ai duk daya, kuma mu muka cusa mata shi ba sonsa take ba wallahi, yanxu banda
ni da ku waye yasan tayi wani gantalallen aure ko da wani ya fito yana son ta,
banda dai gulma tayi ma jama'ar Mariri katutu, ai kawai ce ma Ali zan yi ya
siyar da gidan nan da nawa gidan mu koma ko Rijiyar Lemo ne" Dukawa tayi
ta kwance ledan da ta ajiye tace "Gashi nan, kasuwa na aiki almajirina ya
siyo min kayan ciki me kyau nayi mata farfesu ta sha ta mance abinda ya dameta,
saki ai ba kanta farau ba, mu ma duk ai an taΙa sakin mu, uban Ali saki nawa ne
bai min ba, sai da igiya daya ya rage mana sannan muka nutsu muka zauna har
mutuwa ta raba" Wata mata ce tayi sallama bakin kofar dakin Umma, Umma ta
amsa mata, matar ta shigo tana gyara yakunannen gyalenta, ganin Nenne ta duka
har kasa ta gaisheta, Nenne ta amsa tana rufe farfesun da ta kawo ma Khaleesat
kar matar ta barbade farfesun da gyalenta, Bayan matar sun gaisa da Umma tace
"Ashe abinda ya faru kenan Ummansu Khaleesah?" Nenne ta juya ta
kalleta tace "Me ya faru?" Matar ta langwabar da kai cikin rashin jin
dadi tace "Mutuwan auren Khaleesah Nenne" Nenne ta mike tsaye tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, mutuwar auren wace Khaleesar? A ina
kika ji auren Khaleesah ya mutu? Na shiga uku na lalace, wato matan Mariri baza
ku canza halin ku na tsugudidi ba ko? To daga ke har wanda ya gaya maki kun ci
kaza kazan ku yan iska kawai shegu, tashi ki fita ki ba mu waje, sai dai ki ga
mutuwar aure a dakin ki ko na uwar ki, kaji min mata dai munafuka, uban mutuwan
auren Khaleesah, fita ki bamu waje" Da sauri matar ta fita daga dakin ta
saka takalmi wari da wari ta bar bakin kofar, Nenne na huci ta kalli Umma tace
"Ke kuma Las spika ki ka dauka kike shelan an saki Khaleesah?" Aunty
Farida ta tabe baki tace "Ina fa Nenne, mu ma kawai gani muka yi ana ta
shigo mana tun da gari ya waye, wai an zo Jaje, wa enda suka fitar da labarin
ai su ne babban munafukai" Nenne na share zufan goshinta tace "Shatu
da Zubaida kenan, babu me fitar da zancen nan sai su" Tana kai wa nan ta
fice daga dakin, kafin ta fito dama su Mama Shatu duk sun shige dakunan su da
sauri bayan sun ji abinda Nenne tayi ma matar da ta fita daga gidan, nan tsakar
gida Nenne ta tsaya babu abinda ta manta bata gaya masu ba, zagi kam sun sha
har sun gode Allah, Allah ya isa shima tayi masu kwando kwando, daga karshe
tace "Kuma in har Ali ya dawo gidan nan anjima bai dau matakin fitar masa
da sirrin gida da ku ka yi ba wallahi sai dai ya zaba ko ni ko ku, da dai in
zauna da surkai magulmata munafukai gwara in sallame ma duniya Ali in shi bazai
sallama maku ba, to ai ita Khaleesar ta samu mashinshini har tayi auren ta
fito, ku kuma da naku 'ya yan ke zube kaman gwanjo babu mataya fa? Dama nace ma
Ali in har bazai bada su sadaka ba to ni a dena nuna su ace jikokina don kunya
nake ji, ko kuma in tattara in bar masa Maririn in har bazai samar ma narka
narkan 'ya yanku mafita ba, yanxu in na Jera da Labeebah ba sai ace ita ta
haifeni ba, sannan kwata kwata basa wuni a gidan nan ban san inda suke zuwa ba,
sai mutum ya shigo sau dari bai gan su sau biyu ba" Khaleesat ta fito daga
bandaki tana rike da Shower gel dinta ta nufi dakin Umma, Nenne ta bi ta a baya
tana cewa "Kin fito Khaleesah, mu je ga farfesu can na maki" Sai da
suka shiga dakin sannan Khaleesat ta gaida Nenne, Nenne ta amsa tace "Kar
fa ki ce zaki sa damuwar shegen a ranki kin ji? Allah ne ya dubemu ya rabu dake
cikin aminci bai maki wata illa ba, dama kuma ance min uwarsa har tsafi take
yi, kinga hada zuri'a da irin wannan mutane ai abun tsoro ne, kar ki saka komai
a ranki, rabuwan shi ne mafi alkhairi a gare ki dama an gaya min"
Khaleesat dai ta zauna gefen gadon Umma tana shafa cream dinta, Nenne na kallon
Umma tace "Ke kuma duk wanda ya shigo maki jaje baki koresa ba Allah ya
isa kema, ai mutum daya na shigowa kika rufe ido kika koresa komawa zai yi ya
sanar ma sauran, shikenan babu wanda zai sake shigo maki, ni kin ga tafiyata
inje in nemi abinda zan ci da rana" Daga haka ta fice daga dakin. Bayan
Azahar Khaleesat na zaune kan darduma da qur'ani a gabanta tana karantawa a
zuci, sai ga Safiyyah ta shigo dakin Umma da sallama, Khaleesat ta rufe
Al-qur'anin ta daga kai tana kallonta tana murmushi, ji tayi kamar all her
worries are gone ganin Safiyyah, Safiyyah ta ajiye handbag dinta ta zauna edge
din katifar dakin tana kallon Khaleesat a sanyaye, gaba daya ta kasa ce mata
komai, Khaleesat ta mayar da Al-qur'anin Aunty Farida gefe sannan ta mike ta
koma kusa da Safiyyah ta zauna tana kallonta har sannan murmushin fuskarta bai Ιace
ba tace "I miss you so much" Hawaye ne ya zubo ma Safiyyah a ido don
kawai ta kasa daure hakan, Khaleesat ta sauke idonta kasa, sai ga hawayen ita
ma a idonta, rabonta da zubda hawaye tun jiya a gaban Abbanta, bayan kuma ta
shigo ta kwanta bata sake yarda tayi kuka ba duk da kusan yanda taga rana haka
taga daren ga zafin da zuciyarta ya dinga mata, Safiyyah ta rungumeta tace
"It's fine Khaleesat, Allah ya saka maki abinda yayi maki" Khaleesat
ta gyada mata kai kawai, Safiyyah ta goge idonta don taga alamar kukan da take
ne yasa Khaleesat kuka, Safiyyah ta dago kanta tana kallonta tace "Su Umma
fa?" Khaleesat tace "Sun je gaisuwa ne anyi rasuwa dazu a
unguwan" Safiyyah tace "Allah sarki, Allah ya ji Ζan musulmi"
Khaleesat tace "Ameen, ya su Mama fa?" Safiyyah tace "Duk suna
lafiya lau, tace in gaisheki, bayan mun gama waya daxu tace in kira mata ke, na
sake kiran wayar Aunty Farida naji a kashe" Khaleesat tace "Ehh babu
caji ne, ta bada a kai mata wajen caji" Safiyyah tayi shiru, bata son yi
ma Khaleesat maganar da zai kara sa taji ciwo a ranta, amma duk da haka calmly
tace "Saki nawa yayi maki?" Khaleesat ta buda manyan idanuwanta tace
"Kawai ce min yayi ya sakeni" Safiyyah taji bakin cikin ba saki uku
yayi mata ba, don ita ba kukan bakin cikin sakin da yayi take ba, a'a bakin
cikin mayar mata kawa bazawara da yayi ne babban bakin ciki da takaicinta shi
ne yasa har ta zubda hawaye, a gida ma kukan da tayi kenan don taji ciwon abun
sosai, Khaleesat ta kalli inda Aunty Farida ta ajiye Envelope din da Drivern
gidan su Abdul ya kawo tace "Ga ma can takardan ya aiko" Safiyyah ta
juya ta kalli Envelope din, mikewa tayi ta dauko ta dawo ta zauna ta ciro
takardan ciki, ita dai Khaleesat kallonta kawai take don har sannan bata duba
abinda ke jikin takardan ba, daga Aunty Farida har Umma babu wanda yace mata
saki uku ne, jiya kuma da Nenne ke ta hayaniya a tsakar gida bayan an kawo
takardan Khaleesat na kwance duk bata san abinda ake ba don abubuwan da suka
dameta daban, Safiyyah ta kalli Khaleesat da sauri tace "Saki uku ne ai a
takardan" Khaleesat ta amshi takardan a hankali tana dubawa, after some
seconds ta kalli Safiyyah tace "Wannan ai ba rubutun sa bane"
Safiyyah ta hade rai tace "Do we care?? Ba dai shi aka kawo mana ba, kinga
ai da shi za mu yi aiki, don da kika ce saki daya ne sai da gabana yayi
mummunan faduwa don matsiyacin zai iya dawowa yace ya maida ke mu shiga uku,
amma tunda ga takarda an rubuta saki uku a jiki shikenan an wuce wajen,
Alhamdulillah" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take, Safiyyah ta ajiye
takardan ita ma tana kallonta, can a hankali Safiyyah tace "I don't
understand you Khaleesat, ko dai bakin ciki da sakin da Abdul yayi maki ki ke?
Kin yi give up kan cewa zaki zauna zaman har abada da shi ne? Pls let me know
first so that i will watch my words" Khaleesat tayi murmushin takaici tace
"Dukan yau daban, na gobe daban, zagi, hantara cin mutunci, living with
hunger...." Kasa ci gaba Khaleesat tayi ta fashe da matsanancin kuka tana
girgiza kai, Safiyyah ta rungumeta tace "Allah ya saka maki, Allah ya saka
maki cikin gaggawa, in sha Allahu sai yaga karshensa tun ba aje da nisa ba, in
sha Allah sai hakkin ki yayi tormenting dinsa har karshen rayuwarsa, komin
lalacewan gidanku baza a doke ki ba balle a zage ki ko a hantare ki, uwa uba a
bar ki da yunwa, In anyi duniya don manzon Allah sai Allah ya nuna ma Abdul
iyakansa, wato punching bag ya mayar dake a gidan, kalli yanda kika rame
kalanki ya disashe kamar ba ke ba, dubi yanda duk kika fita hayyacin ki, wallahi
hakkin ki bazai taΙa barin Abdul ba, ki kwantar da hankalinki ki cire ko wani
damuwa a ranki ki dau hakan a kaddarar rayuwarki" Kai kawai Khaleesat ke
gyada mata hawaye masu zafi na zuba idonta, Sosai Safiyyah ta dinga bata words
of encouragement tana kwantar mata da hankali, har Khaleesat taji sanyi sosai a
ranta, taji ta samu relieve din abubuwan da suka tunkushe mata a rai tun jiya,
a haka Umma da Aunty Farida suka dawo suka samesu, Umma ta ajiye masu Ιanwaken
da ta siyo a makota sanin Khaleesat na son Ιanwake, ba laifi Khaleesat ta ci Ιanwaken
me yawa tare da Safiyyah, dama duk yau ta kasa cin komai, ko farfesun da Nenne
ta kawo mata kaΙan ta iya ci, amma sai ga shi ta ci Ιanwaken sosai, sai kusan
karfe shidda na yamma Safiyyah ta bar gidan, with the relieve that tayi
consoling kawarta tunda gashi har tana dariya ta baro ta, sallan magrib kawai
Safiyyah tayi ta jawo wayarta tayi dialing number Housemate, wanda rabon su yi magana
tun sanda ya gaya mata abinda Khaleesat tayi masu shi da Ajay.
[6/30, 11:27 AM] khaleesat Haiydar π✍️: Jay na zaune
dakinsa wajen karfe tara na dare yana rike da mug din coffee da yake ta
stirring for almost 5 minutes now ya kasa sha, ya daga kai jin an bude kofar
dakin, Ajay ne ya shigo ya nufi inda Laptop dinsa yake, shi dai Jay kawai bin
sa yayi da ido har ya kunna laptop din ya duka yana dube dube a cikinsa, after
almost 2 minute ba tare da Ajay ya kallesa ba yace "Resend me those files
u sent yesterday via Email" Jay bai ce masa komai ba, hakan yasa Ajay ya
juya yana kallonsa, mikewa yayi ya nufesa, ya cire masa head warmer din kansa
ya saka a nasa kan yace "Hey is everything Okay? Me yasa baka fito ka ci
abinci ba?" Jay ya mike ya fixge Head warmer dinsa sannan ya koma ya zauna
yace "Kai dai ba ka ci ba, cire min Jacket dina Ajay, I can't remember
dashing you the Jacket...." Ajay na gyara Jacket din jikinsa ya koma ya ci
gaba da abinda yake yi a laptop din Jay, after a while Jay ya ajiye Mug din
hannunsa, speaking slowly yace "I spoke to Safiyyah not long
ago" Ajay ya kallesa yace
"Wacece haka?" Jay yace "My Housemate's friend" Banza Ajay
yayi masa ya ci gaba da duba abinda yake yi a laptop, calmly Jay yace "And
she...." Ajay ya dakatar da shi sounding pissed off yace "Plss Jay, i
am not interested, do not provoke me this night, banda file da nake nema a
laptop dinka baza ma ka gan ni a dakin ka da daddaren nan ba" Jay ya mike
yace "Whether you are interested or not, Safiyyah ta gaya min gayen ya
saki Halysaah" Ajay ya juya ya kalli Jay babu ko kiftawa, after some seconds
ya maida idonsa kan laptop din gabansa sai dai bai ci gaba da operating laptop
din ba, Jay ya karasa kusa da window din dakinsa ya bude drape din ya rungume
hannunsa yana kallon tiny snow din dake zuba kasa, Ajay yace "What did you
expect? Were you expecting less? He's satiated his craving, and that is all
that he is after, yayi satisfying Lust dinsa" Yana kai wa nan ya rufe
Laptop din kawai ya nufi kofa ya fice daga dakin, shi dai Jay da ido ya bi sa
kawai, can ya sauke wani ajiyar zuciya ya karasa ya rufe kofarsa da Ajay ya
bari a bude. Khaleesat na zaune gaban Coal pot wajen karfe sha biyun rana tana
ta fifita gawayin da ta hura zata dora girkin rana at the same time tana gyara
waken farantin dake cinyanta, Ummanta ce zata dora girkin don Aunty Farida ta
fita kasuwa shi ne ta amshi girkin tace zata yi, shinkafa da wake da mai da
yaji ne za su yi da rana, babu kowa a gidan sai ita da Umma don su Mama Zubaida
da Mama Shatu sun tafi gidan biki ko girkin siyarwa basu yi ba ranan, Umma ma
gidan Nenne take shirin zata je ta kai mata kubewan da ta tambayeta ranan
friday, Ιaga kai Khaleesat tayi jin sallaman Safiyyah a compound din su, ta
dinga kallonta bata ko kiftawa don bata ce mata zata dawo yau ba, Safiyyah tayi
murmushi ta karasa har inda take sannan ta dau kujeran tsugunno da ta gani a
tsakar gidan ta zauna tana kallon Khaleesat tace "Sannu da aiki"
Khaleesat ta Ιan bude ido tana murmushi tace "You didn't tell me you were
coming today Safiyyah" Safiyyah tace "Eh nima ban zata zan zo yau ba,
dama ranan Monday ko Tuesday nace maki zan dawo ai" Umma ce ta fito daga
dakinta, Safiyyah ta gaisheta da ladabi, Umma ta amsa da fara'a tace "Ya
su maman ku?" Safiyyah tace "Sun ce in gaishe ku Umma" Umma tace
"Allah sarki, to ina amsawa, bari in je gidan Nenne in dawo yanxu"
Safiyyah tace "To sai kin dawo Umma" A haka Umma ta fita daga gidan,
Khaleesat ta dora ruwan girkin ta ajiye waken da ta gyara sannan suka shiga
dakin Umma da Safiyyah, Safiyyah na kallonta tace "Don Allah ki daure ki
dinga cin abinci Khaleesat, kin ga yanda kika rame kamar ba ke ba kuwa"
Murmushi kawai Khaleesat tayi tace "To ni dama kiba gareni Sophie?"
Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Even though, yanxu raman tayi yawa
wallahi, ji fa sai idanuwa da dogon hanci kawai" Dariya kawai Khaleesat
tayi bata ce mata komai ba, Safiyyah na kallonta tace "Ba dadewa zan yi
yau ba Khaleesat, aikoni aka yi wajen ki" Da mamaki Khaleesat ta dinga
kallonta, sai kuma tace "Wajena kuma? Wa ya aiko ki" a hankali
Safiyyah tace "Ur Housemate" Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta dinga
kallon Safiyyah babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa, Safiyyah ta sauke ajiyar
zuciya ta kamo hannunta tace "Sai dai kiyi hakuri, ni dai na gaya masa
abinda ya faru, And...." Sai kuma Safiyyah tayi shiru, Ita dai Khaleesat kallonta
kawai take don ta kasa cewa komai tana jin hawaye na taruwa gradually a idonta,
a hankali Safiyyah tace "He sent me money for ur flight ticket back to
America, and you tuition fee for this semester, ya ce zai samar maki wani
apartment din for the one year that is remaining for us...." Hawayen dake
makale idon Khaleesat ya zubo, ta kasa ce ma Safiyyah komai, bata san sanda ta
fashe da kuka ba sosai, ita dai Safiyyah tayi shiru tana kallonta cause she
wasn't expecting less, sai da Khaleesat tayi kukanta me isarta sannan tana
girgiza kai muryarta na rawa tace "I don't think za a bari in koma in ci
gaba da karatu Sophie" Safiyyah tace "Ban gane ba? Saboda me baza a
bar ki ba?" Khaleesat na goge idonta da kyar tace "Saboda Abdul ma da
aka bari ya kai ni karatu babu yanda za mu yi ne hakan ta faru, we had no
choice then, dalilin haka har sai da Ummata ta samu hawan jini, kin ga yanxu
kuwa ai babu wani hujjan da zai sa a sake barin wani ya ci gaba da sponsoring
dina a wata kasar" Safiyyah tace "I don't understand Khaleesat, yanxu
me kike nufi? So kike kiyi asaran shekarun da kika yi a makarantar kenan?"
Hawaye na zuba idon Khaleesat ta girgiza mata kai tace "A'a Sophie, but
iyayena za su ji tsoron sake yarda wani ya dau dawainiyata try to understand
me" Safiyyah tace "Zan jira har Umma ta dawo daga gidan Nenne in mata
magana, ke kam bani da sauran magana dake, cause haushi zaki ci gaba da bani
idan na biyeki, banda haka ta yaya ga dama ta samu amma kina neman misusing
opportunity din, did you even know what you are saying?shekara daya kacal fa ya
rage maki Khaleesat? Dropout kike son ki zama ko me? Ai wani abun mutum ba shi
yake bargaining ma kansa hakan ba, you never bargained for all this Khaleesat,
situation ne kawai, kina tunanin har a tashi duniya akwai ranan da Yaya Jawwad
zai bude baki yace ai ya dau nauyinki a makaranta? Kina ganin Jawwad yayi kama
da mutumin da zai maki gori wataran? Ai wallahi daga shi har Cousin dinsa sun
girmi hakan, they are too classy for that, Kin zata kowa mahaukaci ne mara
aikin yi kamar Abdul? Haba wallahi har kin bata min rai, ban taΙa tunanin zaki
nemi kiyi turning down din offer dinsa ba, shi fa taimako kawai yayi saboda
yana da halin yin hakan, duba da kin kusa gamawa kuma yasan duk abinda ya
sameki, amma sbda rashin tunani irin naki kina neman gwalesa, i was thinking
zaman da kika yi da Abdul zai sa ki Ιan canza wasu tunaninki marasu ma'ana, ko
kuma in ce Childish tunani" Ita dai Khaleesat hawaye kawai take sosai ta
kasa ce ma Safiyyah komai, tasan duk bayanin da zata mata bazata taΙa fahimtar
ta ba, Safiyyah ta ciro wayarta ta fara dannawa bata sake ce ma Khaleesat komai
ba don da gaske ta Ιata mata rai, after a while Khaleesat ta mike zata je ta
wanke wake ta zuba a ruwan da to dora kan wuta, bayan ta gama wanke waken ta
zuba ta rufe tukunyar tayi tagumi tana zaune gaban Coal pot din, a haka Umma ta
shigo gidan ta sameta, Khaleesat ta sauke hannunta daga tagumin da tayi tana
kallon Umma da ta nufota, tace "Umma kin dawo" Umma tace "Na
dawo, ina Safiyyar?" Khaleesat tace "Tana ciki" Umma tace
"Shi ne kika bar ta ita kadai" Khaleesat tace "Yanxu na fito in
zuba wake ne" Aunty Farida ce ta shigo gidan da abubuwan da ta siyo a
kasuwa, Umma tayi welcoming dinta sannan ta karasa dakinta ta shiga ciki da
sallama, Safiyyah ta amsa tana mata sannu da zuwa, Umma ta cire Nikab da hijab
dinta ta linke tace "Bata baki ko ruwa ba?" Safiyyah tayi murmushi
tace "Umma ni ke nake jira ma tafiya zan yi" Umma ta zauna tana
kallonta tace "To gani Safiyyah, lafiya dai ko?" Safiyyah tace
"Lafiya lau Umma" Kafin Safiyyah ta ce komai Aunty Farida ta shigo
dakin, Safiyyah ta gaisheta tana murmushi, Aunty Farida ta ajiye kayan hannunta
tana amsa gaisuwan Safiyyah da fara'a, Umma dai kallon Safiyyah take tana jiran
jin abinda zata ce, Babu bata lokaci Safiyyah ta fara yi ma Umma bayanin duk
yanda suka yi da Housemate din Khaleesat, ita dai Aunty Farida na tsaye ita ma
tana sauraron bayanin Safiyyah, Umma ta Ιan yi murmushi bayan Safiyyah tayi
shiru tace "Allah sarki, mun gode sosai da kulawan sa, amma dai ki maida
masa kudinsa Safiyyah, don ko babanta ma bana jin zai yarda, Abdul ma da ya kai
ta karatun ba mu da yanda muka iya ne Safiyyah, Allah ya amfana abinda ta
samu" Safiyyah was speechless, Aunty Farida ta dinga kallon Umma jin
abinda tace, can tace "Allah ya amfana abinda aka samu kuma Umma? Shikenan
fa tayi asaran karatun gaba daya idan bata karasa ba, kamar ka fara gini ne fa
ya ruguje har kasa ya rage Foundation, ai kin ga kuwa baza kace Allah amfana
abinda aka samu ba" Umma ta kalli Aunty Farida tace "Farida kin fi
kowa sanin ban taΙa goyon bayan fitar Khaleesat karatu waje ba tun asali, daga
ni har mahaifinta babu yanda muka iya ne, don haka Khaleesat bazata koma Amurka
da sunan karasa karatu ba, ashe ma bamu dau darasin abinda ya faru a baya ba
kenan" Aunty Farida bata sake ce ma Umma komai ba ta hau fiddo abubuwan da
ta siyo a kasuwa, Ita ma Safiyyah tayi shiru don bata ma san me zata ce ba,
Umma na kallon Safiyyah tace "Ki masa godiya kawai ki mayar masa da
kudinsa Safiyyah, Allah ya dubi niyyarsa na alkhairi ya saka masa, ba wai ni
kadai ba, hatta Mahaifinta ma ba yarda zai yi ba Safiyyah, cutar da ita da muka
yi da farko ma da muna da wani dubaran da baza ayi haka ba, kin ga in mu iyayen
arziki ne ai baza mu yarda ayi na biyu ba" Aunty Farida ta mike tace
"To shi Umma ce maki yayi da wata manufa zai biya mata kudin karatun har
kike tunanin za ayi na biyu? Shi fa Abdul duk abinda yayi yana da manufar yin
hakan duk mun sani, ba haka kawai ya dauketa ya kai ta karatu ba...." Umma
ta dakatar da ita tace "Ban ce shi wannan bawan Allahn yana da wata manufa
ba amma dai kam Khaleesat bazata koma Amurka ba Farida" Aunty Farida bata
sake tanka Umma ba ta fitar da albasan da ta siyo zata je ta shanya a bakin
kofa, Safiyyah ta sauke boyayyen ajiyar zuciya a hankali tace "Toh
shikenan Umma, ni zan koma gida, dama abinda ya kawo ni kenan" Umma tace
"To ki gaida mutanen gidan Safiyyah mun gode kwarai, shi ma ki yi masa
godiya don Allah" Safiyyah tace "To Umma" Jiki a sanyaye ta mike
ta fita daga dakin, Aunty Farida ta dau hijab dinta da ta rataye a igiya tayi
ma Safiyyah alamar su je waje, ita dai Khaleesat na zaune inda take bata tashi
ba don duk taji conversation din Safiyyah da Ummanta, Aunty Farida na fita
kofar gida da Safiyyah tace "Safiyyah kar ki yarda ki gaya masa abinda
Umma ta ce, ki bari Babanta in ya dawo anjima zan samesa in yi masa
magana" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya tace "To
Aunty, don Allah ki yi convincing dinsa shi ma, It will be very sad idan aka ce
bata karasa karatun nan ba, shekara daya fa kawai ya rage mana" Aunty
Farida tace "In sha Allah zan yi bakin kokarina, kuma Khaleesat zata ci
gaba da karatun ta" Safiyyah tace "To Aunty, gobe da safe zan kira ki
sai inji yanda ku ka yi da Baba" Aunty Farida tace "To babu damuwa,
ki gaida gida" a haka suka rabu Aunty Farida ta juya ta koma cikin gida...
Khaleesat ta gama girkin da take bayan ta kashe gawayin tayi alwala ta shiga
dakin Ummanta, tana idar da sallah ta kwanta, gaba daya taji damuwarta ya dawo
sabo fil maganar Housemate dinta da Safiyyah ta kawo mata, Umma na kallonta
tace "Baza ki ci abincin bane yanxu?" Khaleesat ta girgiza mata kai
tace "Sai anjima" Ita dai Aunty Farida linke kayan su Islam take don
tun bayan tafiyar Safiyyah bata ce ma Umma komai kan maganar da Safiyyah ta kawo
ba sanin Umma bazata taΙa fahimta ba. Bayan Magrib Aunty Farida ta samu Malam
Ali yana zaune kofar dakinsa, bayan sun gaisa yace "Amma ba Lagos kika zo
gaya min zaki koma ba Farida?" Murmushi kawai Aunty Farida tayi don in
akwai abinda ya tsana zamanta Lagos yayi fadan har ya gaji, ta kauda tambayar
da yake mata tace "Magana na zo mu yi kan Khaleesat" Yayi shiru kamar
bazai ce komai ba, sai kuma yace "To ina sauraron ki" Cikin nutsuwa
Aunty Farida ta sanar masa batun da Safiyyah ta zo da shi daxu da rana, Malam
Ali ya girgiza kai yace "Ashe ban daddara ba kenan Farida, na yi tunanin
duk mun dau darasi kan abinda ya faru wanda duk nafi kowa laifi a
ciki...." Aunty Farida ta kwantar da murya tace "Ae wancan issue din
da wannan ba daya bane Malam, shi fa Abdul da isa da gadara ya turata karatu
Amurka kuma babu yanda muka iya haka duk muka sallama masa domin zaman
lafiyanmu da naka, Abdul da manufarsa na tura ta karatu, shi ko wannan bawan
Allahn babu wata manufa a ransa, saboda Allah zai biya mata ta karasa karatun
kar tayi asaran shekarun da tayi, iya shekara daya fa ya rage mata Malam, ka
san muhimmancin karatun nan balle ka kushe komawarta America ta karasa, in kowa
zai kalubalanci haka ai banda kai Malam, don Allah ka duba wannan lamari, kuma
shi wannan bawan Allahn da ya ce zai dau nauyin shekara dayan da ya rage mata
su ne fa suka dau maka lauya har aka wanke ka a kotu aka kashe maganar bashin
ka da Baban Abdul...." Malam Ali yayi murmushi yace "Ai nayi
appreciating hakan da suka min kuma kullum ina saka su a addu'ata, amma babu
zancen komawar Jiddah America karatu Farida, kiyi hakuri a bar batun nan gaba
dayanta, we shouldn't be a bad parent for the second time saboda son abun
duniya, tayi hakuri in Allah ya hore min sai in biya mata tayi Jamb ta nemi ko
BUK ko Northwest, duka duka shekarunta nawa suke? Ai lokaci bai kure mata na
karatu ba Farida, kuma ko aro ne zan nema in biya mata in sha Allah, don haka
bana son a sake tada zancen ci gaba da karatun ta a America" Aunty Farida
tayi shiru bata sake cewa komai ba, after a while tace "To shikenan, Allah
ya sa hakan shi ne mafi alkhairi" Yace "Ameen" Mikewa tayi ta
bar wajen rai babu dadi. Washegari wajen karfe tara Aunty Farida ta gama shirin
da take, Umma dake kallonta tace "Ina za ki ne?" Aunty Farida na dora
Nikab dinta kan Hijabin jikinta tace "Ba nace maki zan je gidan Abida ba
shekaranjiya" Umma tace "Shi ne zaki mata sammako?" Aunty Farida
tace "Jiya tace min bata da lafiya ne, kuma ina son in dawo da wuri in
wanke kai na" Umma ta tabe baki tace "To sai kin dawo" Ita dai
Khaleesat juya kokon gabanta take a hankali tana sha ga dumamen tuwo shi ma a
gabanta, da kyar take shan kokon, dumamen kuwa ta kasa ci, dama jiya da daddare
ma bata wani ci tuwon ba, Aunty Farida tayi ma Umma sallama ta fita daga dakin.
Nenne na gyara daurin dankwalinta tayi kasa da murya tace "To ke banda
abun ki ai Zahra'u Jahila ce Parida, matar da har yau bata da wayewa kanta a
murfi yake kamar matar kauye, ita ta wani san maki muhimmancin karatu kina
ganin mata haka kara zube, gashi sai yanda kazaman kishiyoyi suka yi da ita sun
mayar da ita Bora? Ai bari ki ji Parida, Zahra'u a yanxu dai ita daga tuwo sai
bautan Allah kawai ta saka a gaba, babu ruwanta da wani ci gaba na duniya ko
kyale kyalin duniya, ta riga ta amince ta kare rayuwar ta a haka in dai zata ci
tuwo tayi bautar Allah, shi yasa kullum zaki ganta rike da carbi a kuturin
dakinta da ko Ceiling din arziki babu, ni bana ma jin Zahra'u na yi ma Ali
addu'an Allah ya dawo masa da arzikinsa don in tayi hakan gani zata yi kamar ta
butulce ma Allah, duk tunaninta fa haka Allah ya so ganinsu cikin baΖin
talauci, gani zata yi in tayi ta ma Allah magiyan ya yaye masu talauci kamar
butulci tayi bata gode da ni'imarsa ba tunda tana samun tuwo ta ci, to irin
tunanin yayarki kenan Parida, in ba haka ba ta yaya zaki dinga yi ma er cikinki
bakin cikin karasa karatu ta taimake ku a rayuwa ta cire ku daga kangin
talauci? shikenan kuma don kai jahili ne sai ka rasa sanin abinda ya kamata?
Har wani kwambo fa take da jahilcin ta da rashin wayewa, ki bar ni da su kawai
zan yi maganinsu daga Alin har Zahra'un, da can uban me yasa suka bari aka kai
ta Amurkan in har da tsoron Allah a lamarinsu daga ita har Alin? Wato sai yanxu
suka zama iyayen kirki masu tsoron Allah ko? To zan yi maganinsu gaba daya, in
dai karatu ne kamar Khaleesah taje Amurka ta karasa in har ina numfashi, Allah
ya kai mu anjima da yamma, Alin ai zai dawo daga zaman kashe wandon da yake yi
a kasuwa, zan je har gidan in samesa inji ko na tauye masa karatunsa duk da
talauci na, in de ni na amince taje to ko wani Ιan iska ma kar ya amince"
Nenne na kai wa nan ta mike ta jawo kofar dakinta ta kulle da kwado, sannan ta
dau mayafinta sabo dake rataye saman igiya ta yafa, ta dau handbag dinta ta
saka makullin kofar a ciki, ta zura takalmanta ta nufi kofar fita daga gidan
tana taku dai dai don sabuwar atamfa ce a jikinta, Aunty Farida ta bi ta da
kallon mamaki tace "Wai fita zaki yi ne Nenne?" Ba tare da Nenne ta
juyo ba tace "To me zan maki, anguwa har uku zan je yau da kika gan ni,
bazan zauna a banza ki bata min lokaci ba, in ba gulma ba ganinki nake yi a
gidana, ni dai in kin gama zaman kin fito ki ja min kyauren gidana kar
almajirai su shiga su min sata" Daga haka Nenne ta fice daga gidan,
murmushi Aunty Farida tayi ta mike ta nannade mata tabarmanta ta ajiye sannan
ta daura nikab dinta, bin bayanta tayi da sauri don jadadda mata kar tace ita
ta zo ta gaya mata maganar don tasan tsaf sai yayarta ta kullace ta.
[6/30, 6:59 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Wajen karfe
shidda na yamma Khaleesat na zaune bakin kofar dakin Ummanta tana yanka mata
alaiyahu a cikin roba, stepsisters dinta Labeebah da Lamisah na can zaune su ma
daga bakin kofar dakin Mama Shatu da kawayensu sai hira suke suna shewa duk sun
cika tsakar gidan kai kace gidan biki ne, Mama Shatu da Mama Zubaida su ma suna
tsakar gidan don da su ake hiran da kawayen 'ya yan nasu, magana daya biyu sai
su kwashe da dariya, yawanci kuma duk habaici suke jefa ma Umma da Khaleesat,
ita dai Umma tana zaune gaban Coal pot tana kwashe tuwon masara da ta gama
tukawa, Aunty Farida kuma ta tafi Hotoro tun bayan la'asar da su Noor, Nenne ce
ta shigo gidan rataye da jakarta a kafada, lkci daya gidan yayi tsit, a takaice
Nenne ta amsa gaisuwan da su Mama Zubaida da Lamisah da kawayensu ke yi mata ta
nufi gun Umma tace "Zahra'u Alin ya dawo ko be dawo ba?" Umma ta
gaida Nenne sannan tace "A'a bai dawo ba tukun Nenne, sannu da zuwa"
Nenne tace "Kin gan ni nan daga Sheka nake daga can na tafi Ζan Agundi, ni
ce har Na'ibawa yau, tun safe na bar gida sai yanxu nake dawowa 'yan adaidaita
sahun kano dai sauransu yawo da bindiga kawai...." Murmushi kawai Umma
tayi tana ci gaba da kwashe tuwon da take yi, Nenne ta jawo kujera ta zauna
tace "Gidan Katime me Aya na tafi a Sheka, in gaya maki me Aya dai
kafafuwanta sun mutu murus Zahra'u, ko tashi bata iya yi, babu yanda ban yi da
matar nan ta rage cin nama ba amma taga kamar bakin ciki nake mata don mijina
baya kawo min, to yau ni da ban ci nama ba gani da kafafuwana biyu rass, ita
kuwa duk sun mutu, wai tana ganina ina taku dai dai na shigo gidan sai ta fashe
da kuka, ni dai bata ban tausayi ba wallahi, sai kinga yanda take mana fafa da
nama lokacin, kullum kya ji kamshin tafashen nama a gidanta, mu sai dai mu
watsa er daddawa a miya" Umma na girgiza kai tace "To Allah Ubangiji
ya bata lafiya" Nenne tace "Ba batun Allah ya bata lafiya ba, ai duk
kafafuwan sun rube, da kyar in baza ace za a yanke mata su ba tunda ko motsa su
bata iya yi " Su Mama Zubaida gaba daya kunnuwansa na kan labarin da Nenne
ke ba Umma, Malam Ali ne ya shigo gidan da sallama, Nenne ta juya tana
kallonsa, can ta mike ta nufesa tace "Yanxu Ali baza ka hakura da fita
kasuwar nan ba tun da ba wani abu kake yi a can ba sai zama cikin rana da iska?
Ka dubi yanda duk kayi bakikirin kamar baka taΙa haske ba a rayuwarka Ali,
tunda ba aikin fari gareka ba balle baΖi a kasuwar ka hakura da zuwa mana"
Gaisheta kawai yayi ya dau buta zai debi ruwa ya fita waje ya zauna ya jira
Magariba, Nenne ta tabe baki tace "To wajen kai da matar ka Zahra'u na
xo" Umma ta juya tana kallon Nenne jin abinda tace, Shi ma ya tsaya yace
"To lafiya dai ko?" Nenne tace "A ina lafiyar take, ba sai kun
nemi zaman lafiyar za a zauna lafiya ba, labari na samu wai masu kare hakkin
'yan Adam sun zo gidan nan sun ce za su ci gaba da daukar nauyin karatun
Khaleesat a Amurka saboda tausayin abinda tsinannen mutumin nan Awdul yayi
mata, to amma wai saboda kai da Zahra'u yan bakin ciki ne sai ku ka gwalesu ku
ka koresu, da wanne ku ke son yarinyar ta ji fisabilillahi? Da mayar da ita
bazawara da aka yi tana da karancin shekaru ko kuma da asaran karatun ta da
kuke kokarin yi mata? In ita Zahra'u jahila ce bata yi karatun boko ba kai ma
Jahili ne Ali? Ina ne ban shiga nayi aikatau ba don kayi karatu? To wallahi ko
karshen bangon duniya ne sai Khaleesat ta koma ta karasa karatun ta tunda har
aka ce za a dau nauyinta babu ko sisin ku, to ina ma ku ka ga ko sisin"
Malam Ali dake ta kallon uwar tasa yace "A ina kika ji wannan zancen
Nenne?" Nenne tace "Labarin duniya na buya ne dama? Ina zaune yan
Mariri suka zo suka tsegunta min har unguwan da naje yau...." Mama Shatu
ta kalli Mama Zubaida da ta saki baki tana sauraron Nenne, Mama Zubaida ta kasa
daurewa ta gyara zama cikin kwantar da murya tace "Amma Nenne na farkon ma
ba a wanye lafiya ba shi ne za a sake na biyu? Dama gashi duk garin nan kallon
makwaita masu son abun duniya kawai ake mana, ko ina sai zaginmu ake tun da aka
samu labarin sakin walakancin da aka yi ma Khaleesat, ana ta cewa ubanta ne ya
ja mata, A rayuwar nan yanxu fa in ba iyayenka ne za su yi maka dawainiya ba
duk wanda yace zai dau dawainiyar ka sama ta ka to da wani abu da yake hangen
zai samu a gare ka ne, Khaleesat fa 'ya mace take ba namiji ba Nenne, kuma ba
komai ke rudar maza akanta ba sai kyanta da kalan fatar ta sun ga buzuwa, shi
kenan saboda son abun duniya sai a zuba ido har sai yarinyar nan ta lalace
tukunna, Abdul ya gama nasa ya samu abinda yake so ya sako mana ita sai kuma
yanxu ace ga wani ma ya zo wai zai ci gaba da daukar nauyinta? Haba sam batun
nan babu tsari a cikinta, shikenan ita kuma haka ta zama kamar Tasi...."
Nenne ta kundumo wani zagi tace "Toh duk wanda ya fasa fadin abinda ke
ransa akan Khaleesah Allah ya tsine masa albarka, kuma in de karatu ne kamar
tayi ta gama sai dai bakin ciki ya kashe duk wani shege wallahi, ko ma ina za a
kai ta a kai ta ni na amince ta je, ai ita tasan tarbiyyar da muka yi mata in
ma ta gantalar da tarbiyar ita da Allah, kuma gobe gobe zan sa a kira min baΖar
kawar tata ta zo in gaya mata uban Khaleesah ya amince koma waye zai dau
nauyinta ya dauka, taje can ta ci gaba da karatun ta, ai gwara tayi nesa da mu
ko bakin cikin dake damunta a rai zai ragu, mu kanmu in tana ganinmu takaici da
bakin ciki take don ba mu da wani babanci da Awdul a wajenta tunda mu muka ja
mata komai, gwara ta koma ta gama karatunta ta dawo da kwalinta don bazata
tashi a tutar babu ba, shi kansa Awdul din yana samun labari an samu wanda ya
maidata Amurka ta ci gaba da karatu sai bakin ciki ya kusa kashe shegen, a nan
kuma zai san ba a banza Khaleesah take ba farin jininta ya shahara" Nenne
na huci ta juya ta kalli Umma tace "Ke kuma Zahra'u halan tallan alalen ki
ke da niyyar dora mata da kike mata bakin cikin komawa ta karasa karatun? To
kamar yanda kike takama kina da iko da ita nima haka tunda ni na haifi ubanta,
ban ga shegen da ya isa yace bazata koma ta karasa karatun ta ba" Ita dai
Umma bata ce ma Nenne komai ba, Malam Ali dai na tsaye rike da buta a hannunsa
yana kallon uwarsa, can dai yace "Amma dai Nenne sam babu tsari ace mun
sake barin yarinyar nan ta bar kasar nan da sunan wani zai dau nauyinta bayan
duk abinda ya faru, me kike son jama'an gari su ce a kaina? Sannan nace duk
sanda na samu kudi zan nema mata Jami'ar garin nan tayi, ba wasu shekaru gareta
ba balle ace lokaci zai kure mata" Nenne ta kallesa da sauri tace "A
gidan uban wa zaka samu kudin? Mutanen garin in sun fasa fadin abinda za su
fada a kanka Allah ya tsine masu albarka, kai bari kaji Ali bana bukatar
ra'ayinka ko shawararka a yanxu saboda kai ma sanda ka bi ra'ayinka ka yarje ma
Awdul ya kai ta kasar waje babu wanda ka saurara ko kaji shawaransa, don haka
ni ma yanzu wallahi bazan saurare ka ba Amurka ne sai Khaleesat ta koma ta
karasa abinda ta fara in sha Allahu, in kuma nuna ma duniya zaka yi ni er banza
ce a gareka to Bismillah" Kofar gida kawai Malam Ali ya fita da butansa a
hannu, Nenne ta kalli Khaleesat tace "Maza ki hada akwatinki ki tsaya
cikin shiri, in sun biya maki kudin jirgin ki kama gabanki kije kiyi abinda zai
taimaki rayuwarki, zama gidan nan kadai ya ishi mutum ya fada cikin mummunan
damuwa, gida kamar na 'yan sansanin gudun hijira, ga lafta laftan mata suna
yawo suna doyi a cikinsa, ai ko mutum matsiyaci ne ya kasance dai yana da
tsaftarsa dai dai gwargwado, amma gidan nan ga talauci ga kazanta, ina bawa zai
iya rayuwa a nan idan ba dole ba" Nenne na kai wa nan ta kama hanya tayi
tafiyarta, Khaleesat ta daga kai ta kalli Umma da ta bi Nenne da kallo, Mama
Shatu ta mike tana kallon Umma tace "Muddin kika ce baza ki bude baki kiyi
magana ba to kina ji kina gani za a mayar maki da er ki karuwa Zahra'u, wata
birkitacciyar tsohuwa can kamar Nenne ce zata yanke ma er da kika haifa
hukuncin abinda ya shafi rayuwarta? Ita ta tsugunna ta haifar maki er? Mu
meyasa ba a mana iko akan namu yaran ba? Saboda an san baza mu dauka ba mu ba
yan iska bane, to kuwa wallahi Nenne na dab da kai ki ta baro ki, mata me tabin
ΖwaΖwalwa zaki yarda ta yanke hukunci akan 'er ki? ai in ita Khaleesar ta bude
baki tace bazata je ba babu uban da zai tilastata ta je wallahi, waye bai san
Nenne da kwadayi da son abun duniya ba kamar tayi sata?" Muryar Nenne suka
ji ashe tana makale bata tafi ba tana jiran jin abinda za a ce, Nenne ta dinga
kwalo ma Malam Ali kira, sai gashi ya shigo da sauri yana kallonta yace
"Lafiya Nenne? Ai magana ta wuce yanda kika ce haka za ayi" Mama
Shatu tayi wuri wuri da ido daga inda take tsaye, Mama Zubaida ta mike ta
lallaba ta dau kwandon kwanon wanke wankenta ta shige daki ta sako labule,
Nenne ta rushe da matsanancin kuka tana kallon Malam Ali tace "Ali yau sai
dai ka zaba ko ni ko Shatu a gidan nan, kawai ka zaba ko ni ko ita, ni Shatu
zata kalla ta kira me tabin ΖwaΖwalwa wato mahaukaciya er macukule? Ni zata ce
ma me kwadayi da son abun duniya? Tunda nake me na taΙa zuwa gun almajirin
ubanta dake bara a bakin danja nace ya bani? Me na taΙa rokon uwarta me
shanyayyen kafa? Bata san ina labe ban tafi ba duk ina jin abinda take cewa,
cin mutunci da zagi sai wanda ta manta ne bata min ba Ali, har tana gaya ma
Zahra'u ni na haifar mata er da zan yanke mata hukunci akan ta? Me nayi ma
Shatu da har zata yi mugayen kalamai haka a kai na? Naga dai kullum ci gabanka
da na iyalan ka shi ne burina, fadi tashi babu wanda bana yi akan kai da
iyalinka, amma daga karshe sai zagi da cin mutunci ya biyo baya, tsofe tsofe da
ni Shatu tace min me son abun duniya?" Kuka sosai Nenne take tana share
idonta da gyalen jikinta, Malam Ali na kallon Mama Shatu da tayi tsuru tsuru
yace "Shatu ki tafi gida, sai na neme ki" Mama Shatu ta gwalo ido
tace "Ban gane in tafi gida ba Malam, wani gidan zan tafi?" Malam Ali
yace "Gidan iyayenki, ki je na sake ki" Mama Shatu ta zabura tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ka sake ni fa kace Malam, na shiga uku
na lalace" Labibah ta mike tana huci tace "Gaskiya Baba sai dai mu bi
Baabarmu mu ma" Nenne tace "Shegiya ku bi ta mana, yunwar cikin ku
kadai ma ya isheku ai" Malam Ali na kallon Mama Shatu dake rusa kuka yace
"Kar in dawo in sameki a gidan nan" Daga haka ya fice daga gidan,
Nenne ta bi bayansa tana goge idonta ita ma ta fita, sai a sannan Mama Zubaida
ta fito tana salati tana kallon Mama Shatu dake kuka wiwi, Umma tsabar yanda
jikinta yayi sanyi ta ma kasa cewa komai daga inda take zaune, Mama Zubaida na
kallon Umma tace "Ke kam kinyi asara wallahi Zahra'u, ko wani bala'i ta
dalilin ke da tsinannun 'ya yan ki yake faruwa a gidan nan, gashi yau saboda ke
da er ki an saki Shatu, sam babu alkhairi a tare dake da zuri'ar ki
Zahra'u" Umma ta juya tana kallon Mama Zubaida sai dai bata ce komai ba,
Khaleesat ma ta daga kai tana kallonta, Mama Shatu na kuka sosai tace
"Kuma in sha Allahu asirin da kike yi zai kare maki a gidan nan Zahra'u,
yanda kika yi sanadiyyar tsinkewar igiyar aurena daya ke da er ki wallahi sai
nayi sanadin naki igiyar kema, ko tsirara zan yi yawo kuwa, Ni saki daya aka
min ke ukun gaba daya za a maki, kuma kamar Ali ya maida ni ne don yanxu na
fara auren sa wallahi" Don mamaki Umma ta ma rasa abun ce masu ganin yanda
suka juya zancen lokaci daya, yau ga fadan karfin hali tana gani kiri kiri,
biyesu ma bata lokaci ne kawai a wajenta ga makota na jin su, tsam ta mike tayi
shigewarta daki, Khaleesat ta mike ta bi bayanta. Washegari da sassafe Umma da
Aunty Farida suka fito tsakar gida suka tarar da Mama Zubaida da Mama Shatu a
tsaye suna jiran fitowarsu za a je ba Nenne hakuri, ko wanne da Hijab dinsa har
kasa don sanyi ake sosai, duk abinda suka yi ma Umma jiya hakan bai sa tace
bazata bi su zuwa gidan Nenne ba, Su ma din sun san ta dalilin Umman sai Nenne
ta iya hakura ta sa Malam Ali ya maida Mama Shatu shi yasa Mama Zubaida da
kanta ta samu Umma ko kunya babu tayi mata magana wajen karfe biyar din asuba,
Mama Shatu dama a makota ta kwana ranan don sae da Nenne ta dawo ta korata har
da watsi da en tsummokaran ta, sae kusan hudun asuba Shatu ta dawo gidan daga
inda ta kwana, a haka duk suka kama hanya zuwa gidan Nenne da asuban. Ranan
Thursday da safe Khaleesat na zaune dakin Umma tana kallon Aunty Farida dake ta
jera mata kayanta da aka amso wajen guga a cikin akwati, ita dai Khaleesat har
sannan ta rasa gane me take ji a ranta, farin ciki take ko akasin haka duk ta
kasa ganewa, babban damuwarta yanxu bata san da idon da zata kalli Housemate
dinta ba idan ta koma America, sannan gani take kamar babban burden kawai zata
zame masa a can din tunda ita ba komai gare iyayenta da za su tallafa mata da
shi ba idan ta koma, Ιan kudin dake account dinta ba wani kudin kirki bane kuma
da shi ta siya sabon waya with new sim card, sai few abubuwan da tasan zata
bukata a can kasar, sauran kudin dake account dinta ko dubu dari da hamsin bai
karasa ba, duk wannan tunanin yasa take damuwa sosai a ranta, Aunty Farida ta
daga kai tana kallonta kafin ta rufe zip din jakar tace "Baki manta komai
ba dai ko?" Khaleesat ta gyada mata kai kawai, Aunty Farida tace "A
Airport din za ku hadu da Safiyyah goben?" A hankali Khaleesat tace
"Eh" Aunty Farida ta kulle zip din tace "Gwara ki saki ranki
kiyi abinda ke gaban ki Khaleesat, ki cire duk wani damuwar dake ranki kar ki
je ki samu matsala a karatun ki, shi kuma Jawwad Allah ya saka masa da
mafificin alkhairi...." Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, lkci
daya taji hawaye ya cika idonta, Aunty Farida ta mike ta dauko daya akwatin don
hada few foodstuffs din da suka siyo mata da Umma wanda zata iya shiga Amurka
da shi, a hankali Khaleesat tace "Toh Aunty ta yaya za a maida masa
kudinsa dake account dina?" Aunty Farida ta daga kai ta kalleta, can tace
"Kudin wa? Ko Abdul?" Khaleesat ta gyada mata kai, Aunty Farida ta
saki baki, can tace "Wai dama har yanxu kudaden nan nasa na account din
ki?" Khaleesat ta gyada mata kai, shiru Aunty Farida tayi kamar me nazari,
after a while tace "Ki ci gaba da ajiye kudin kawai Khaleesat, duk sanda
ya dawo ya bukaci kayansa sai a basa, ko Umma kar kiyi ma maganar kudin for
now, bana son a samu delay a tafiyarki don yanxu sai su iya cewa sai an maida
masa kudadensa, kuma hakan zai iya ja maki delay...." Ita dai Khaleesat
bata ce komai ba, Aunty Farida ta ci gaba da hada foodstuff din da take a akwati.
[7/1, 1:11 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Wajen karfe
uku na yamma Khaleesat na zaune bakin kofar dakin Umma Aunty Farida na combing
din mata dogon gashinta bayan ta wanke mata shi da Shampoo da Conditioner, har
wani sheki baΖin gashin nata yake yi bayan Aunty Farida ta shafa mata man
gashi, tun daga wajen wanke gashin Aunty Farida ke ta mata fadan ta bar
gashinta ya kakkarye saboda banzan da tayi da shi ta dena kula da shi, ita dai
Khaleesat bata ce mata komai ba don har sannan basu san irin zaman da tayi a gidan
Abdul ba, don ma abun ya tsaya iya kakkaryewan gashi, har bata son tuna
experience dinta a gidan Abdul hakan yana traumatizing dinta, su Mama Zubaida
da Mama Shatu dai na bakin murhu suna girka abincin siyarwansu na yamma, suna
yi suna kuskus a bakin murhun, lkci lkci sai su kalli direction din su
Khaleesat, ita dai Aunty Farida dama ko kallo basa isanta a gidan, a da dai ta
biye su har dambe sun sha yi amma yanxu bata da wannan time din, kallon stark
illiterates kawai take masu, wasu mata biyu ne suka shigo gidan babu ko
sallama, sun yi shiga ta alfarma sun sha gwala-gwalai suna taku cikin isa, at
the same time suna bin ko ina na gidan da kallo cike da kyama gashi dama su
Mama Zubaida sun yi gaje gaje da ruwa a tsakar gidan ranan, Khaleesat ta dinga kallonsu
haka Aunty Farida da ta ajiye comb din hannunta, Mama Zubaida ta mike tace
"Sannun ku da zuwa ko dai batan hanya ku ka yi ne, in gidan Hajiya Samira
matar Alhaji Bala ku ke nema can karshen layi za ku karasa sai ku yi tambaya a
nuna maku gidan, amma ba nan bane" Momy ce ta shigo gidan tana tafiya
gansan gansan da Drebanta a bayanta yana biye da ita, mayafin nata ma ko yafa
shi bata yi ba, gashi ta sha wani tsadadden baΖin glass no respect, Khaleesat
ta dinga kallonta babu ko kiftawa, lkci daya taji gabanta ya fadi sosai, ta
juya ta kalli Aunty Farida, sai ga Meemah ita ma ta shigo gidan tana yatsine
fuska, ita ko mayafin ma babu a hannunta, Aunty Farida ta dake tace "Bayin
Allah lafiya? Daga ina haka, babu ko sallama" Daya daga matan da suka
shigo da farko tana ma Aunty Farida wani matsiyacin kallo tace "Ba shi ya
kawo mu ba, a irin wannan bolan za ayi maku sallama?" Umma ta fito daga
dakinta don tana jin duk abinda ake cewa, tsaye tayi bakin kofa tana kallonsu,
Mama Shatu da Mama Zubaida dai sai zazzare ido suke kamar wa enda suka yi ma
sarki karya, Momy ta karaso har tsakiyar compound din tana tafiya cikin isa da
gadara, fuskar nan nata babu ko digon mutunci tace "Zuwa nayi in ji ko
shegiyar er ku tana da gadon Abdul ne, Ko kuma shi ma satan da ku ka yi ma
ubansa kuke da niyyar za ku yi masa, in kuwa babu gado to yanxun nan ba sai
anjima ba a maido mana kudadensa dake account din er ku..." Umma ta kalli
Khaleesat nan da nan hankalin Umma ya tashi sosai, Aunty Farida tace "Ikon
Allah, shi ne sai anyi wannan zuga haka kamar za ayi yaki?" Meemah ta
matso har gaban Aunty Farida tana mata matsiyacin kallo tace "Yakin ne ai,
ko kin ga alamar da sassauci muka zo? sanin halin familyn na ku na sata wanda
ku ka gado a gun Malam me dattin hula ya sa mu ka yo tattaki a mayar mana da
kudaden mu tun wuri, ai kowa yasan sata da cin amana shi ne tambarin gidan nan,
don haka tun wuri ba a jiyo kan mu ba a maido mana Miliyan goman Abdul, kun
zata bulus za ku ci ga banza ta fadi ko? To Sponsoring din matsiyaciyar er ku da
ya dinga yi da kudinsa ma ai ba yafewa yayi ba sai kun biyasa a lahira wallahi,
kawai babban farin cikin dake saka ni nishadi idan na tuno shi ne karewar da
zata yi as dropout din John Hopkins university, don ko kaf zuri'arku za ku
siyar baza ku samu kudin biya mata ta ci gaba da karatun a kasar Amurka ba, da
yau ta gama John Hopkins sai bakin ciki ya kasheni, amma Alhamdulillah a
dropout zata kare, Abdul kuma ya yar da kwallon mangwaro ya huta" A fusace
Momy tace "Ke Meemah tsayuwa cikin kangon bolan nan ne ke burge ki da baza
kiyi abinda ya kawo mu mu fita ba, ko so kike Cholera ya kama mu? Ina ke ina
cacar baki a irin wannan gida" Aunty Farida tayi wani murmushi tana kallon
Meemah tace "Sai dai kuwa bakin cikin nan ya kashe ki don kina ji kina
gani Khaleesat zata gama karatu a makarantar da kike fada, Allah ya ji Ζan ki
in Advance" Cikin tsawa Meemah tace "Keee, ki iya bakin ki, kar ki
gan ni tsaye a wannan bolan gidan a gabanki kiyi zata ni sa'ar yin ki ce, don
wallahi inda na bi da kafata ma baki isa ki bi ba har duniya ta nade, ni ba
sa'ar ki bace ta ko wani angle, banda Abdul yayi downgrading dinmu ya kaskantar
da darajan da Allah yayi mana ina mu ina hada hanya da matsiyata talakawa irin
ku balle har aje ga auratayya? Ke ki duba irin wajen da ku ke rayuwa wanda ko
karen gidanmu baza mu bari yayi rayuwa a cikin wannan hali ba, To wallahi ki
iya bakin ki ni ba sa'ar yin ki bace, ba karamin aikina bane in sa a shafe
babin ki a duniya" Tun kan Aunty Farida ta mayar ma da Meemah amsa Umma ta
hanata, cikin fushi Aunty Farida tace "Kamar yaya in yi shiru Umma,
gidanmu fa suka zo suka same mu kuma ki ce inyi shiru? ashe ma karyar arziki
suke in don saboda miliyan goma za su yi wannan uban zugan kamar masu bibiyan
miliyan 50 har su tsaya suna kumfar baki suna tada jijiyoyin wuya akan 10M,
uban wani ya saka ya tura mata kudin a account dinta da har za su zo nan suna
gaya ma mutane maganar banza, ko kuma rokonsa tayi ya saka mata kudin, su
arzikin ma wallahi da gani taka haye suka yi, da can su ma matsiyata ne"
Meemah ta mika ma Momy handbag dinta tana huci zata cakumo Aunty Farida, Momy
ta dakatar da ita tace "Ke me ya kai ki, ki taΙa ta ki ce kin taΙa wa?
Salon ta goga maki Ζashin tsiyarsu kike kokarin dambe da ita? Yanzu wannan har
Class din damben ki ce in ba rashin wayo irin naki ba Meemah? Ai ba a dambe da
talaka matsiyaci" Umma ta kalli Khaleesat tace "Ta yaya za ki fiddo
kudaden a account din ki Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta tace
"Sai naje banki, bani da Atm card, kuma kudin bazai fita lokaci daya
ba...." Momy na mata matsiyacin kallo tace "Sai ki tashi ki tafi
bankin ai don wallahi kudaden nan baza su kwana a account din ki ba yau, da
niyyar ki kin ci bulus tunda ubanki ne ya nema masa kudin ba" Khaleesat ta
daga kai ta kalleta, ita har sannan ta kasa daina mamakin matar nan, kai tunda
aka haifeta ma ita ba a taΙa shayar da ita ruwan mamaki yanda mahaifiyar Abdul
ta shayar da ita ba, yau sati daya da sakin da Abdul yayi mata amma kullum in
ta tashi sai ta zauna tayi mamakin uwarsa ganin abun take kamar Drama, ba ayi
ranan da zai zo ya wuce da Momy bazata fado mata ba, bata taΙa san akwai mutane
irin Momy a rayuwar nan ba, muryar Mama Zubaida taji tace "Ai ba zama zaki
yi kina zazzare ido ba kamar barauniya, tashi za ki yi ki kama hanya ki tafi
banki ki fiddo masu da kudadensu tunda ba gadon Abdul din gare ki ba kuma ba
kudin tsohon ki bane, duk wani abu na rashin gaskiya dake da uwarki da kanwarta
gaba ku ka basa ba baya ba, banda haka ta yaya za kuyi shiru da makuden
kudadensa har Miliyan goma a account dinki? So ku ka yi ku danne kudin ko yaya?
Don ma kun samu masu hakuri da kawaici da wasu ne idan ba a zo da motar yan
sanda an tafi da ku ba ku ce bani ba, wannan ai rashin gaskiya ne da rashin
tsoron Allah kiri kiri, duk kun yi mukus da bakin ku za ku cinye miliyan goma
ga banza ta samu" Aunty Farida ta juya tana kallon Mama Zubaida, sai kuma
ta nufeta tana cewa "Zubaida idan ban zubar maki da hakora a gidan nan yau
ba ki ce bani ba, don kaza kazan ki akwai tsinannen da ya sako bakin ki? Uwarki
muka yi ma rashin gaskiya ko ubanki?" Mama Zubaida tayi wani shewa tana
tafe hannu tace "To yau kika saba Farida? Ai ke fitsararriya ce dama mara
mutunci mara kunya shi yasa ga ki har yau duk kyan ki kin rasa mashinshini sai
dai kiyi tuwo tuwo a garin legas kina hadawa da karuwanci, waye bai san wannan
ba?" Aunty Farida zata cakumo Mama Zubaida Mama Shatu ta shige tsakaninsu
tace "Ke yanxu Farida Zubaida sa'arki ce zaki dinga zaginta haka ta uwa ta
uba don kawai tana kishiyar yayarki? Daga dai ta fadi gaskiya banda Ιan Adam
baya son gaskiya?" Aunty Farida tayi wani wurgi da Mama Shatu sai ga ta a
kasa timmm, tuni Mama Zubaida ta shige dakinta ta kulle kofarta da sakata tana
cewa "Haka kawai ki shafa min bakin jini irin na ku? Allah ya sauwake in
yi dambe dake Farida, ku je can ku ji da rashin sa'ar ku a rayuwa, ku kenan
daga wannan iftila'in sai wannan bala'in, ko wani fitinar duniya a kan ku ya
kare, daga wannan sai wannan, Allah kadai yasan laifin da ku ka tafka a kasar
ku, kilan ma ta zina aka sami ke da yayar taki, ga bakin jini da rashin sa'ar
ku ya shafi Malam ya talauce" Da kafa Aunty Farida ta hambare uban miyan
da Mama Zubaida ke yi na abincin siyarwanta, miyar duk suka malale kasa,
shinkafar ma dake cikin kwando ta kifar da shi a kasa tana zagin Mama Zubaida ta
uwa ta uba, Mama Shatu ganin yanda aka yi watsi da kayan sana'an Mama Zubaida
ya sa ta ja bakinta tayi shiru ta tafi gun nata miyan ta zauna tana cewa
"Hakuri kawai za kiyi Farida, hakan ba dadi kam" Momy ta rike haΙa
tace "Alhamdulillahi da na yi iya bakin kokarina na ganin ban hada iri da
gayyar tsiya ba, ku kuga wannan tsiya haka kamar 'yar tasha, ga talauci ga
tashanci, Abdul ya so ja mana abun fade a dangi Allah ya takaita min abun, kuma
ba dai kun ce kudade na banki ba, to zuwa yau da daddare in ga alert din
Miliyan goma, in kuwa ba haka ba gobe da sassafe za ku gan ni a gidan nan ba
kuma zuwan lumana zan yi ba, ai shi ramin karya kurarre ne, kuma ko kwabo daya
yayi ciwon kai a kudaden nan wallahi sai an daure er ku..." Momy na kai wa
nan ta bude handbag dinta ta ciro takarda dauke da account details dinta ta
jefa ma Khaleesat sannan ja tawagarta suka yi waje tana cewa "Haka kawai
Meemah zata ja min bala'i ta hada Ζashi da wannan iri na fitina, irin tsiya, to
kiyi dambe da ita ki ce kin yi dambe da wa? Kina ganin yarinya kamar
mahaukaciya, A'a wallahi Allah ya maki tsari" A haka duk suka fita daga
compound din, Khaleesat taji hawaye ya cika idonta, Umma komawa dakinta tayi
tayi tagumi ranta ba dadi, ita kam ta gode Allah da jarabawa iri iri, daga
wannan sai wannan, Khaleesat ta dau takardan da Momy ta jefa mata ta juya ta
shiga dakin Umma hawaye na zuba idonta, Aunty Farida kuwa bata fasa zage su
Mama Zubaida da Mama Shatu a tsakar gida ba, Mama Zubaida taki fitowa kuma taki
tanka Aunty Farida, Mama Shatu kuwa tayi tsit kamar bata san da wa Aunty Farida
take ba, daga karshe bayan Aunty Farida tayi masu wankin babban bargo ta shige
dakin Umma tana huci, Umma ta daga kai tana kallonta tace "Yanxu ban isa
ince ki bari ki bari ba Farida?" Aunty Farida ko tanka Umma bata yi ba ta
dau Hijab dinta ta saka tana kallon Khaleesat tace "Ki tashi ki shirya mu
tafi bankin" Mikewa Khaleesat tayi tana goge idonta ta dau hijab dinta ta
saka, a haka suka kama hanyar banki da Aunty Farida, amma suna isa bankin suka
tarar an tashi aiki sai ran Monday don karfe hudu har da rabi a lokacin, Aunty
Farida na kallon Khaleesat bayan sun fito bankin tace "Goben karfe nawa ne
tafiyar naku?" A hankali Khaleesat tace "Flight din karfe daya zuwa
Abuja, daga Abuja kuma jirgin yamma ne" Aunty Farida tace "Kuma bazai
yiwu a daga tafiyar ba Khaleesat? Kinga banki dole fa sai Monday idan Allah ya
kai mu" Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, ita kanta she is just
confuse bata san yanda zata yi ba. A haka suka koma gida kusan karfe biyar da
rabi, Umma na kallonsu tace "An tashi a banki ko?" Aunty Farida bata
ce komai ba ta cire hijab dinta ta nemi waje ta zauna, Khaleesat ta zauna tana
kallon Umma tace "Banki sai ranan litinin, sun tashi yau" Umma tayi
shiru bata ce komai ba, can tace "Kema kin san bai amshi kudinsa ba me
yasa zaki yi shiru har na sati daya Khaleesat? Yanxu da kinyi magana tun yaushe
za a san yanda za ayi a cire kudin a mayar masa kayansa, yanxu rashin mutuncin
da suka zo suka mana makota na ji ina amfanin sa?" Aunty Farida tace
"A'a ta min maganan kudin fa ranan Alhamis, a lkcn ma tayi zaton yau ne
tafiyar ashe gobe ne, kuma kema kinsan Khaleesat bazata taΙa ko biyar a kudin
nan ba tunda ba nata bane, kawai dai dama matsiyata ne yan iska daga Abdul din
har iyayensa" A hankali Khaleesat tace "In ma an cire kudin an basu
bazan iya tafiya babu kudi a account din ba, don baza a bari in shiga kasar ba,
they wilk see i am not financially capable idan babu kudi a account dina, shi
yasa ma ya bar kudin a account din all this years" Aunty Farida tayi shiru
don bata ma san me zata ce ba, haka ma Umma da ta rafka tagumi tun shigowarsu,
after a while a hankali Umma tace "Ni tsorona kar su dawo goben da suka ce
bamu san kuma da me za su zo mana ba" Aunty Farida ta mike tace "Sai
su zo su amshi babu tunda su yan iska ne" Daga haka ta fice daga dakin,
Khaleesat taji hawaye ya cika idonta, Umma na kallonta a hankali tace
"Kiyi hakuri Jiddah, wataran duk hakan zai zama labari, Allah ya bamu ikon
cin jarabawan mu, in ma kin koma makarantar in ma baki koma ba duk yanda Allah
yayi dai dai ne" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata ta mike ta dau
tsintsiya zata yi gyaran dakin Umma tana goge hawayen dake sauka idonta....
[7/2, 6:55 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat har
ta fara bacci wajen karfe goma da rabi Aunty Farida ta tasheta tana mika mata
sabuwar wayarta dake vibrate, mikewa tayi zaune tana gyara hulan kanta ta amshi
wayar taga Safiyyah ce ke kiranta, Ιagawa tayi ta kai kunne, daga daya bangaren
Safiyyah tace "Ko har kin fara bacci ne" Khaleesat tace "Um, da
wuri na kwanta ne" Safiyyah tace "Ayya sorry for waking you up, dama
Housemate din ki ne yace in tambayeki wani account zai maki funding, cause
nasan definitely Abdul ya amshi kudinsa dake account din ki ko?" Khaleesat
tayi shiru ta kasa ce ma Safiyyah komai, har sai da Safiyyah tace
"Hello" a hankali Khaleesat tace "Ina jin ki Sophie"
Safiyyah tace "To naji kin yi shiru" Khaleesat ta daga kai ta kalli
Aunty Farida dake kallonta, goge hawayen dake makale idonta tayi cikin sanyin
murya tace "Daxu Mom dinsa suka zo za su amshi kudin, ni kuma bazan iya
transfer ba kuma bani da Atm card, shi ne ta ajiye min account number wai in
tura masu kudin yau, and today is Friday, mun je banki sun tashi, yanxu tace
zata dawo gobe da safe idan ban tura mata kudin ba" Safiyyah dake ta
sauraron Khaleesat cikin bacin rai tace "Allah ya sauwake, ke kiji wani
tsiya don girman Allah, akan miliyan tara ne ko goma uwar ta kamo hanyar gidan
ku da kanta? Can you imagine fa? A'a gaskiya sai yanxu nake sake tabbatar da su
Abdul were once poor in this life, all of a sudden kawai Allah ya basu arziki
sama ta ka, nobody can change this my perspective wallahi, banda tsiya meye kuma
miliyan Goma a irin yanda suke show casing arzikinsu, what is 10M to them?
wannan ai abun kunya ne a garesu, Ke kuma maimakon ki kirani tun daxu ki gaya
min shi ne kika yi shiru? Yanxu ba don Housemate dinki yayi reason cewar dole
sai da sufficient fund a account dinki za ki iya tafiya ba da shiru zaki yi
kenan sai gobe da za mu tafi ki gaya min? Allah ya sauwake, ita kuma uwar Abdul
wallahi matsiyaciya ce er wahala, har ta iya kamo hanyar Mariri akan kudin da
ba ita ta bada ba, in kin bibiya ma Ιan nata bai sani ba ta kamo hanya, ki min
sending shegen account din nata da ta bar maki" Daga haka Safiyyah ta
kashe wayarta, Khaleesat ta jawo handbag dinta tana goge hawayen da ya taru
idonta, ta bude jakar ta ciro takardan account details din da Mom din Abdul ta
bar mata, tura ma Safiyyah account din tayi ta message sannan ta mayar da jakar
ta ajiye ta koma ta kwanta, ita dai Aunty Farida bata ce komai ba don duk ta
fahimci conversation din nasu. Washegari Khaleesat na idar da sallan asuba
kiran Safiyyah ya shigo wayarta, tayi picking call din ta kai kunne, a hankali
tace "Good morning Safiyyah" Safiyyah tace "How was ur
night?" Khaleesat tace "Alhamdulillah" Safiyyah tace "Na
tashi yanzu naga Housemate dinki ya tura min receipt din 10M da ya tura a
account din da kika turo min jiya, he sent the receipt via my WhatsApp, ba ki
yi activating WhatsApp dinki ba da sai in tura maki ki tura masu, sai su san su
ne matsiyata" Kasa cewa komai Khaleesat tayi hawaye ya fara sauka idonta,
Safiyyah tace "Ko kuma bari in tura ma Aunty Farida receipt din kawai
since she is on WhatsApp" Khaleesat ta gyada mata kai da kyar tace
"Nagode" Safiyyah tace "Kuka kike yi ko? Kina da aiki, ni dai
sai anjima, make sure ki fito gida da wuri kin san Flight dinmu zuwa Abuja
karfe daya ne" Daga haka Safiyyah ta katse wayar, Umma na kallon Khaleesat
tace "Wai me ya faru?" Khaleesat na share hawayen da yaki tsaya mata
tace "Ta ce ya tura masu kudin ne, zata tura ma Aunty Farida receipt"
Shiru Umma tayi ta rasa abun cewa, kana ganinta kasan jikinta yayi sanyi sosai,
Aunty Farida dake zaune kan darduma tace "Allah Ubangiji ya saka masa da
alkhairi ya kare sa sharrin masu sharri, Allah ya mayar masa da dubban abinda
ya kashe maki, yanda ya rufa maki asiri Allah ya rufa masa shi ma" a
hankali Umma tace "Ameen ya Allah"
Mikewa Khaleesat tayi don dama ta gama azkar din da take yi, ta kwanta
kan gadon Umma har sannan hawaye yaki dena sauka idonta. Da safe wajen karfe
tara Aunty Farida na bude WhatsApp dinta taga Receipt din da Safiyyah ta tura
mata, tana kallon Khaleesat tace "Yanxu ta ya za a tura masu receipt din
su gani Khaleesat?" Umma tace "Ba kina da number Abdul din ba? Ki
tura masa ta WhatsApp din kawai" Khaleesat dake cin wainar da Umma ta sa
aka siyo mata ta daga kai ta kalli Umma, sai kuma ta girgiza kai a hankali tace
"A'a Umma kar a tura masa, ba sun ce za su zo da safe ba, in sun zo sai a
nuna masu receipt din" Umma tace "Saboda me? Ba kudinsa bane kuma shi
ya aiko su karbar masa?" Aunty Farida ta kalli Umma tace "Suka aiko
kansu dai Umma, don Abdul dai a yanda yake ji da kansa bazai ce a zo a amsar
masa miliyan goma ba, dama sun san da kudin kuma kilan sun san bazai ce zai
amsa ba shi yasa suka taho su amsa" Khaleesat tace "Shi yasa nace kar
a tura masa receipt din, don nasan ba shi yace su zo ba" Umma tace
"To ko ma dai yaya ne ai kudinsa ne, ni bana son su sake dawo mana nan su
mana tijara makota na ji shi yasa nace a tura masa kawai, idan yaso sai yayi ma
uwar tasa magana tunda zai ga a account dinta aka tura kudin ai, tonan asirin
bai ishe mu bane da har za mu sake yarda su dawo gidan nan" a hankali
Khaleesat tace "Umma ni bana son abinda zai sake hadamu magana da shi
balle har yace zai dawo da wata magana kuma" Aunty Farida tace "Ya
dawo da wani magana? Saboda ba shi da hankali zai dawo da wata maganar? Ai
yanxu ba mu da abinda zai sake hadamu da shi da ya wuce kudin nan nasa, saki
uku ya aiko maki balle ace zai dawo da wata magana" Khaleesat ta sauke
idonta kamar bazata ce komai ba sai kuma cikin sanyin murya tace "Aunty ba
fa shi ya aiko da takardan sakin nan ba, ba rubutunsa bane, iya saki daya yayi
min" Daga Aunty Farida har Umma kallonta suka dinga yi, a hankali tace
"Shi yasa bana son a tura masa receipt din balle har hankalinsa ya dawo
kan mu..." Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya bayan kusan minti daya tace
"To Allah ya kyauta, yanxu su suka rubuto takardan suka aiko kenan? To su
dai suka sani Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi gare mu da ke baki daya,
idan sun kwaso kafa sun sake dawowa sai a nuna masu receipt din" Umma dai
bata ce komai ba don bata ma san me zata ce ba.
Meemah na bacci Momy ta shigo dakinta wajen karfe goma na
safe ta tasheta tana mika mata wayar hannunta, Meemah ta amshi wayar tana
kallon screen din, sai kuma ta kalli Momy tace "Kudin suka sako?"
Momy ta tabe baki tace "Gashi kuwa kina gani, nima yanxu naga alert din
ashe tun daren jiya aka sako" Meemah tace "To a gidan uban wa ta samu
ta turo bayan tace bata yin transfer kuma bata da Atm card" Momy tace
"Ke baki ga sunan wanda ya turo kudin ba? Ai ba ita bace ta turo"
Meemah ta kara kallon wayar da kyau taga sunan namiji, taΙe baki tayi tace
"To wai ke Momy da nake ce maki iskancinta ta dinga yi da maza a Amurka
kin zata wasa nake? Ai ba abun mamaki bane don kin ga ta samu wanda ya turo
miliyan goman, harkar iskancinta kawai ta dinga yi a Amurka da 'ya yan masu
kudi, kuma karya take babu miliyan goman nan a account dinta wallahi, to dai
gashi nan daya daga farkanta ya turo kudin nan take" Momy tace "Oho
dai koma wa ya turo kudin ta matse masu can, ni dai ba na amshi kudin Ιa na ba,
da ban yi haka ba har a tashi duniya in dai Abdul ne wallahi bazai yi maganar
kudin nan ba, kin ga da shikenan sun ci bulus, to ni da na haifesa ba
asararriya bace da zan yarda ya bar masu makudan kudaden nan" Meemah tace
"Wallahi Momy ni so nayi mu ce sai sun biya kudin sponsoring dinta da
Abdul yayi, ke kinsan nawa Abdul ya kashe akan yarinyar nan kuwa? Wallahi idan
na fara maki lissafi sai kin rike baki don mamaki, kudade ne ba na wasa ba da,
duk kanta dukiyarsa ya dinga tafiya kamar kin masa baki, yaushe rabon kiji
Abdul ya siya wani asset nasa ya ajiye? Tun da ya hadu da tsinanniyar yarinyar
nan ya dena yi ma kansa komai sai dai yayi mata, ranan a gabana ya siya mata
Abaya har biyu ko wanne dubu dari da hamsin, nayi masa magana ya nemi ya min
rashin kunya cikin jama'a, handbag din nan shegiya sai Abdul ya siya mata na
dubu kusan dari har fin haka, komai designer yake siya mata, suturu kam yayi
mata ba iyaka, to wai ko monthly allowance da yake tura mata a kasar Amurka in
kika ji sai hankalin ki ya tashi, uwa uba a zo kan kudin makarantar ta da House
rent" Momy tayi mitsi mitsi da ido cikin bacin rai tace "Don Allah ki
bar wannan maganar don raina baci yake Meemah, su je kawai Allah ya isa, ni da
nake uwarsa ma sai ya ga dama yake siya min abu, to yanxu ko ce masu muka yi su
biya a ina suka ga kudin biya Meemah? Ko gidan da suke ciki suka ce za su siyar
wallahi karkari yayi dubu dari biyar, kai ni dubu dari biyar din ma bazan siya
wannan kangon ba wallahi, kin ga kuwa gwara a bar zancen kawai, baki ji yanda
raina ya baci ba wallahi, kawai Allah ya isa zan ta ja masu a kan uban kudin da
Abdul ya kashe ma yarinyar kuma ba wai don bani da kudin maka su kotu
ba...." Meemah tace "Ko kuma mu je duk mu kwaso kayan da ya dinga
siya mata da jakunkuna masu tsada" Momy tace "Ki ci uwar me da su?
Kema dai wallahi, shekara 38 ban san yaushe zaki yi hankali ba Meemah, Allah ya
isan dai shi ne dai dai su, don babu abinda za mu ci da kayanta, tunda muka
samu miliyan goman ma ai mun gode Allah" Meemah ta tabe baki ta koma ta
kwanta tace "Kuma kin san wani abu Momy, da Abdul yana kasar nan har yanxu
zai fa iya waiwayanta idan asirin ya sakesa, don wallahi masifaffen so yake ma
shegiyar ke har yanxu baki gane ba, ji fa kafin su bar kasar yanda ko magana
baya yi ma mutane a gidan nan, kullum zaka gansa babu walwala" Momy ta
hade rai tace "Ni kuma ga er iska sai in sakankance har asiri ya sakesa
ko? Ai da gangan na sa uban ya tafi da shi business trip din da za shi china,
da biyu na takura uban su tafi tare don naga take takensa, ga sabon tijaran da
na lura zai fara mana, kuma ko ba komai ai kinga za su dade a can kan su dawo,
ni kuma kafin nan na sa anyi aiki sosai ya mance da wata shegiya wai ita
Khaleesat a duniyar nan, sai kuma in tanadar masa mata er gidan mutunci, yana
dawowa sai biki kawai" Meemah tace "Da dai yafi kam, yana dawowa yayi
aure, ki sama masa yarinya dai dai class dinsa ba er talakawar da ya nace ma
ba, ni wallahi ban zata talaucin iyayen yarinyar nan ya kai haka ba, har muka
dawo gida na kasa cire view din gidan a idona, wannan ko karen gidanmu aka
ajiye a gidan nan ai sai yayi rashin lafiya a bar mu da kashe makudan kudi zuwa
veterinary balle ace mutum, to yanxu da bai rabu da ita ba haka wataran abu zai
kama ki kwashi kawayenki da abokan business aje gidansu yarinyar? Misali ace
ubanta ko uwarta wani ya mutu, haka za a kwasa aje masu gaisuwa wannan
gidan?" Momy tace "Ai Abdul ya so ja min abun kunyan da bazai taΙa
goguwa ba, ya so tona min asiri a idon duniya amma Allah ya rufa min asiri ya
takaita abun, da irin rainin da Abdul zai ja min sai Allah wallahi, to ni dai
tunda na samu aka rabu lafiya ai sai su bi wani sarkin kuma" Meemah tayi
dariya tace "Kuma da bai saketa ba fa sai ya iya canza masu wani gidan don
ba hankali garesa ba, tunda don yayi ta ma shegiyar yarinyar bauta Allah ya
halitto sa" Wani shegen kallo Momy tayi mata sannan ta juya ta fita daga
dakin. Khaleesat na durkushe gaban Umma dake mata addu'an Allah ya kai ta
lafiya, ya bata sa'an karatun ta, ita dai Khaleesat kanta na kasa duk jikinta a
sanyaye, a hankali Umma tace "Ki kula da kanki don Allah, duk da na yarda
dake Jiddah amma ki kara taka tsantsan, kar ki mance tarbiyar da muka maki,
kuma ki rike addu'a da azkar, Allah ya kare min ke ya tsare ki duk inda zaki
shiga..." Nenne ce ta bude labulen dakin a fusace tace "Yau naga
jaraba wajen Zahra'u, sai me motar yayi zuciya ya ja motarsa ya wuce ne ko
yaya? Duk daren jiya da wayewar garin yau baki sakata gaba da duk wani zancen
da zaki mata ba sai yanxu da motar da zai kai ta iyapot ya iso, haba Zahra'u ya
ki ke haka ne? Ko dai maidata ciki za kiyi?" Aunty Farida ta wani kalle
Nenne tace "To kyauta zai kai ta airport din da bazai jira ba, naga dai
kudi zata basa Nenne" Nenne tace "Ai ba motar ubanta bane da zata
shanya sa a rana don zata basa kudi, kuma shi ba boyi boyinta bane da zai ta
tsayuwa yana jiranta a rana kamar Ιan iska, tunanin ku kenan 'yan Adam, don
zaka ba mutum kudi sai aka ce ka walakantasa? Ka ki darajasa?" Aunty
Farida taki tanka Nenne, Umma na kallon Khaleesat tace "Tashi ki je
Jiddah, Allah ya tsare ya kai ku lafiya" A hankali Khaleesat tace
"Ameen Umma" Daga haka ta mike ta dau handbag dinta don duk an fitar
da akwatunan ta kofar gida, Nenne na kallon Umma tace "In ji dai duk an
saka mata doya da dankalin da na kawo mata a akwatin nata?" Da sauri Aunty
Farida tace "An saka komai" Nenne tace "Wake da su albasa da
garin masara da na alkama fa?" Aunty Farida tace "Har su an sa"
Nenne tace "To mu je" Khaleesat ta bi bayan Nenne suka fita daga
dakin, Aunty Farida ta kara tura doya da dankalin da Nenne ta kawo da su garin
alkama da Masara a bayan kyaure ta boye yanda Nenne bazata gani ba ko ta dawo
dakin, daga nan ta bi bayan su, kasa daurewa Umma tayi ta mike ita ma ta fita,
su Mama Zubaida da Mama Shatu na tsaye tsakar gida duk suka bi Khaleesat da
kallo, Kana ganin fuskokinsu kasan babu farin cikin komawa Amurka da Khaleesat
zata yi, Yaron Mama Zubaida ya nufo Khaleesat da gudu yana mika mata kudin
hannunsa yace "Wai gashi inji Ummanmu da Mama Shatu ki sha ruwa a
hanya" Nenne ta karbe kudin a hannun yaron ta kirga taga dubu biyu ne,
sokesa tayi jikin haΙar zaninta tace "Ta gode" Daga haka ta kalli
Khaleesat tace "Mu je" Khaleesat tayi ma kishiyoyin ummanta sallama
sannan ta bi bayan Nenne suka fita daga gidan Aunty Farida na biye da su, a
kofar gidan Khaleesat ta kara sallama da Babanta don bai fita kasuwa ba ranan
yana jiran tafiyarta, kasa hada ido tayi da shi yana mata addu'a da fatan
alkhairi, Nenne ta bude mata bayan motar tace "Ni dai shiga don Allah, tun
jiya basu san da addu'an su ba sai yau da kike sauri salon jirgi ya tafi ya bar
ki" Khaleesat ta shiga motar Nenne ta kulle, haka kawai Khaleesat taji
hawaye ya cika idonta, ta daga masu hannu kawai sannan drivern ya ja motar suka
bar kofar gidan. Ko da Khaleesat ta isa airport ta tarar Safiyyah na ta jiranta
don tun daxu ta iso airport din, Khaleesat ta amshi boarding pass dinta suka
nufi Departure Lounge, bayan minti ashirin jirginsu ya tashi zuwa garin Abuja,
inda a nan za su hau jirgin da zai kai su kasar America.
[7/3, 9:23 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Tun da suka
sauka Amurka wajen karfe hudu na asuba gaba daya walwalar Khaleesat ya bace, ta
dawo so silent kamar mara lafiya, cikin rashin kuzari ta dinga yin komai har
suka gama da custom da Immigration, Safiyyah na kallonta tace "Wai duk
sanyin ne yasa kika dawo haka? Naga mood din ki ya canza all of a sudden, are
you okay?" Khaleesat tayi murmushin karfin hali ta girgiza mata kai kawai
tana gyara Jacket din jikinta don tun a kasar da suka yi transit duk suka saka
Jacket din su saboda sanyi, Safiyyah na kallon wayar hannunta ganin kiran
Mustapha for the 4th time tace "Shi kuma wannan daga sauka ko kashe jirgin
ba ayi ba ya fara doka min kira kamar jira yake, kilan kewan fadan da muke yi
da matarsa kullum yake yi, bai san i came fully ready for her ba, don this time
around bazan sake tolerating nonsense dinta ba wallahi" Khaleesat dai
murmushi kawai tayi bata ce mata komai ba har suka fita daga Arrivals, Safiyyah
tace "I don't want us to stress ur Housemate, naga message dinsa tun muna
Abuja yana tambayar karfe nawa za mu taso kuma a ina za mu yi transit, kilan da
na gaya masa zai iya estimating time din da za mu iso ya zo yayi picking din mu
daga airport cikin azababben sanyin nan da ake, shi yasa kawai ban masa reply
ba kar muyi inconveniencing dinsa" Khaleesat ce ta fara hango Ya Mustapha
tsaye jikin motarsa kafin Safiyyah ma ta gansa tayi kasa da murya tace
"Sai kin ga yanda ya addabi Dad din mu wai an koma makaranta naki dawowa,
sai kace zaman jin dadi nake yi a gidansa da shegiyar matar nan tasa"
Khaleesat ce ta fara gaida Mustapha bayan ya iso inda suke tsaye, ya amsa da
fara'a yace "Ya hanya Khaleesah?" Khaleesat tace
"Alhamdulillah" Safiyyah ma ta gaishesa ya amsa sannan suka nufi
motar sa gaba daya, ya amshi trolley dinsu ya saka a booth din motar yace
"Kun ji sanyin America ko, don ma yau babu snow" Khaleesat dai tayi
murmushi, Safiyyah ta bude mata back seat tana kallonta, Khaleesat ta shiga
sannan Safiyyah ta zaga ta bude gaban motar ta shiga ita ma, Mustapha ya tada
motar bayan sun bar Airport din ya kalli Safiyyah yace "Amma dai Khaleesat
won't be going to her apartment now, zai fi kyau mu je can gidana idan ta huta
sai ta koma Apartment dinta anytime she is ready" Safiyyah tace "Dama
gidan ka zaka kai mu gaba daya mana, cikin sanyin nan ta ina zata je ta fara
gyaran apartment dinta ga gajiyar hanya" Ko da wasa Safiyyah bata ba
Mustapha labarin abinda ya faru da Khaleesat ba, ita dai Khaleesat tayi shiru a
bayan motar tana tunanin another new life that she is going to begin in America
with her burden on people's shoulder, shikenan ita kuma daga wannan ya dau
responsibility dinta sai wannan ya dauka, sosai tunanin nan ke kara kashe mata
jiki, gashi rayuwar America ba dai tsada ba, kawai tasan takura Housemate dinta
zata yi da burden dinta, a haka suka isa gidan Mustapha da tunani iri iri a
ranta, bin unguwan ta dinga yi da kallo don bata san unguwan ba, sati biyu da
fara exams dinsu Last semester Safiyyah ke gaya mata Mustapha ya amshi wani
apartment da ya fi wanda suke ciki girma za su tashi a gidan da suke, ita dai
har suka bar America bata san gidan da suka koma ba, bayan Mustapha yayi
parking suka sauka a motar Safiyyah ta bar sa da shigo masu da kayansu ta kama
hannun Khaleesat zuwa cikin gidan, ita dai Khaleesat bin ta kawai take, upon
yanda ta tsani duk abinda zai hadata da gidan Mustapha saboda matarsa sai gashi
yau saboda rashin option da choice ya sa ta amince da zuwa gidansa babu ko
musu, zaune suka tarar da matarsa a parlor ta sha uban rigan sanyi ga daurin
dankwalin ture kaga tsiya da tayi da zaninta, sosai jikin Khaleesat yayi sanyi
ta rakube jikin kujera tana kallonta ta gaisheta, amma matar nan ta dinga
kallon TV tana cin popcorn kamar bata ji Khaleesat ba, Safiyyah dama ko
kallonta bata yi ba ta nufi hanyar dakinta ta murda taji a kulle kuma babu
makulli a jikin kofar, tsaye tayi fuskarta babu yabo babu fallasa tana jiran
Mustapha ya shigo gidan, bayan yan sakwanni sai gashi ya shigo parlon da
akwatuna biyu, Safiyyah tace "Yaya ina makullin dakina?" Ya karasa ya
murda kofar yaji a kulle, ya dawo parlor yana kallon Surayya yace "Surayya
ina makullin dakin can yake?" Sai a sannan Surayya ta juya ta wani kallesa
tana ci gaba da cin popcorn din hannunta tace "Makullin daki? Ban gane
Makullin daki ba, Ajiyar makulli aka bani da za a tambayeni?" Safiyyah
dake ta kallon Ya Mustapha tana huci tace "Kai dama yaya da ka wani ishi
Daddy da kira cewar mun koma makaranta in dawo a saman roofing din gidan nan
kake da niyyar ajiyeni tunda gashi an dauke makullin dakin an boye? Wannan ai
iskanci ne da walakanci, mutum yayi dogon tafiya haka ya dawo kuma yaga an
dauke masa makullin daki?" Mustapha ya karasa kusa da Surayya da sauri
yace "Ke Surayya ko dai Aslam yana wasa ya cire Makullin dakin ne a jikin
kofar?" Surayya taki ko kallonsa, Safiyyah ta wani tsuke fuska tace
"Aslam ne tsayinsa zai kai har ya cire makulli a kofar daki? Ai sai dai
Uwar Aslam, kuma Allah ya so ban bar komai da za a sace min a dakin ba sai
takardu, tunda an saba min satan dama" Mikewa Surayya tayi tana mata wani
tsinannen kallo tace "Keeee, in kina cin kasa ki kiyayi ta shuri, wallahi
ki iya bakin ki don ni ba sa'ar ki bace ki kiyaye ni, in kika yi wasa za ki sha
mamakina yanxun nan" Safiyyah tayi wani dariya tana tafe hannu tace "Osheyy
ancient of days, ashe dai ke ba sa'a ta bace, ai sai yau kike gaya min nake ji,
kuma in kin fasa bani mamaki sunanki ba Surayya ba, shege ka fasa tsakanin ni
da ke" Fada Mustapha ya fara yi yana cewa "Meye haka? Ko kuna hauka
ne? Wannan wani irin iskanci ne? A gaban nawa ku ke wannan rashin
hankalin?" Magana yake yi at the same time yana kai kawo yana dube duben
makullin dakin Safiyyah a parlon, Ita dai Khaleesat na rakube jikin kujera taji
kanta har ya fara mata wani azababben ciwo, banda rashin option me zai kawota
gidan nan ita kam, tunanin hakan yasa ta ji hawaye ya cika idonta, Safiyyah sai
girgiza kafa take tana hararan Surayyah da ta koma ta zauna tana cin Popcorn
dinta tana gyara daurin ture kaga tsiyan dake kanta tana kara cokarosa gaba,
Mustapha ya karasa inda Aslam ke kwance yana bacci a parlon ya fara tashinsa
yana tambayarsa makullin dakin Safiyyah, yaron da ko shekara biyu bai karasa
ba, a fusace Surayya tace "Wallahi kar ka tada min yarona Mustapha, shi
yasan maka wani makulli da zaka tashesa yana bacci" Mustapha ya juya ya
kalleta yace "Surayya in ke kika dauke makullin nan ki fito da shi bana
son rainin hankali" Surayya ta wani hararesa tace "Kar ka bata min
rai this early morning, in dau makulli inyi uwar me da shi? Plss do not provoke
me Mustapha" Tana kai wa nan ta mike ta figi yaronta dake bacci ta nufi
dakin ta da shi, Mustapha ya kasa cewa komai ya bi ta da kallo yana rike da
waist dinsa, can ya juya ya kalli Safiyyah dake masa wani mugun harara kamar
zata kwadesa, karasawa yayi kusa da ita yace "Look Safiyyah...."
Katse sa tayi a fusace tace "Babu abinda zaka gaya min Yaya, Don't tell me
anything, dama don matarka ta min wannan walakancin ya sa ka dage sai na dawo
an koma makaranta, wallahi ni dai Daddy zan kira a samar min wani gidan da zan
zauna in karasa final year dina kawai in peace, don bazan iya zama da wannan
devil wife dinka a gida daya ba" Kamar zata yi kuka ta kare maganar,
Mustapha bai iya yace mata komai ba, can dai ya nufi hanyar dakinsa don daki
uku ne a gidan, yana shiga dakin ya dau duk abinda zai bukata ya fito da shi
parlor ya ajiye yana kallon Safiyyah yace "Ga bedroom dina can ku
shiga" Safiyyah na jin haka ta figi hannun Khaleesat zuwa dakin nasa, da
sauri Surayya ta fito daga dakinta don bata kulle kofar dakin ba saboda ta dinga
jin abinda za ace a parlon, tana kallonsa da wani irin mamaki tace "Ban
gane ga Bedroom dinka can su shiga ba Mustapha, turakar namu za su shiga kake
nufi ko me?" Safiyyah ta kwashe da wani dariya har da kyakyatawa ta ja
Khaleesat suka shiga dakin sannan tayi banging kofar ta kulle, Surayyah zata yi
magana Mustapha ya Ιaga mata hannu fuska a murtuke alamar baya son jin komai
sannan ya fice daga parlon zai shigo da sauran akwatunan su Safiyyah, Khaleesat
da duk jikinta yayi sanyi ta dinga kallon Safiyyah tace "Haba Sophie, this
isn't proper mana, why not mu zauna a parlor har san da za a ga makullin dakin
naki, dakinsu ne wannan fa" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Ai ba
kowa ne Ιan iska mara zuciya kamar ki ba Khaleesat, kuma wallahi ina dakin nan
babu inda zan je har sai ranan da ta fito min da makullin dakina...."
Khaleesat ta kasa cewa komai don da gaske she is shock, sai ga Mustapha yayi
knocking kofar dakin sannan ya ajiye masu hand luggage dinsu yace "Me za
ku ci yanxu?" Safiyyah na zaune gefen gadonsa fuskarta babu walwala irin
ita an bata mata din nan tace "Kawai shayi da cookies kafin gari ya
waye" Yace "Ohk" Juyawa yayi ya fita daga dakin ya kullo masu
kofa, har sannan Surayyah na tsaye inda take a parlor ta kasa motsin kirki, ta
bi sa da kallo har ya shiga kitchen zai hado masu shayin, bata san sanda ta
fashe da kuka ba tana rufe bakinta ta nufi dakinta da sauri, Mustapha ya dawo
dakin nasa da Cup din shayi biyu da cookies ya ajiye masu ya fita.... Khaleesat
na idar da sallan Asuba ta kwanta kasan carpet din dakin Mustapha don dakin da
dumi saboda room heater dake kunne, amma hakan bai hanata dinga jin sanyi ba
saboda wankan da tayi, babu yanda Safiyyah bata yi da ita ta kwanta saman gado
ba amma Khaleesat taki tace kasan carpet din ya isheta, wayar Safiyyah ya fara
ring, ta mike ta dauko handbag dinta ta ciro wayar, kallon Khaleesat tayi tace
"Housemate dinki ne ke kira" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce
komai ba, Safiyyah ta zauna gefen gado sannan tayi picking call din tayi masa
sallama tare da gaishesa, daga daya bangaren yace "How are you, naga baki
yi replying message da na maki ba tun jiya" Safiyyah tace "Kawai bana
son inyi stressing dinka ne probably kace zaka zo picking din mu a
airport" Yace "Kuna ina yanxu?" Safiyyah tace "Muna gidan
yayana, ga Housemate din ka nan, let me give her the phone...." Calmly
yace "Ohk..." Safiyyah ta mike ta tafi inda Khaleesat ke kwance ta
durkusa tana mika mata wayar, Khaleesat ta kasa amsan wayar, har sai da
Safiyyah ta kai mata wayar kunne, daga daya bangaren Khaleesat taji yace
"Halysaah...." Kasa ce masa komai tayi, lokaci daya taji hawaye masu
zafi sun fara sauka idonta, a hankali yace "Can you hear me?"
Muryarta na rawa da kyar tace "Uhm" Shiru yayi, after some seconds
yace "I will come over later in sha Allah" Ta gyada masa kai kamar
yana ganinta, kashe wayarsa yayi, ta ajiye wayar wasu hawayen na sauko mata,
ita dai Safiyyah bata ce mata komai ba. Karfe takwas na safe Safiyyah ta fito
daga dakin Yaya Mustapha zata je kitchen ta duba menene available da zata girka
masu ita da Khaleesat, ga mamakinta sai taga an ajiye makullin dakinta kan
Centre table din parlon, dariya ma abun ya bata, ta karasa ta dauki makullin
sannan ta koma dakin ya Mustapha da sauri ta kulle kofar, dariya ta dinga
babbakawa Khaleesat na kallonta, tana nuna ma Khaleesat makullin hannunta tace
"Kin ga er iskar ta ajiye min makullin kan Centre table saboda taga na
tare dakin mijinta, ashe karamar er iska ce ita ban sani ba? ai wallahi boyewa
zan yi inyi kamar ban gani ba don ni kam naga dakin zama..." Safiyyah na
fadin haka ta bude zip din akwatin ta ta cusa makullin ciki, Khaleesat dake ta
kallonta ta girgiza kai tace "Don Allah tunda har ta ajiye maki makullin
kiyi hakuri mu koma dakin ki Sophie" Safiyyah tace "Wallahi bazan
koma ba for now, next time in ance ta boye min makulli bazata boye ba, ba tace
ita er iska bace ni kuma zan nuna mata er daba ce ni, ina nan dakin sai naga
abinda ya ture ma buzu nadi" Murmushi kawai Khaleesat tayi bata ce komai ba,
Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "To ni ba na manta ke buzuwa
bace" Khaleesat tace "A'a ni bafillatana ce, babana bafillatani
ne" Safiyyah tace "To Umma fa?" Murmushi kawai Khaleesat tayi
bata ce mata komai ba, Safiyyah ta nemi waje ta zauna tace "Ke kiji rashin
kunya kiri kiri ta ajiye min makulli kan Centre table da taga ba sarki sai
Allah, to da menene nufinta da ta boye makullin in koma garage da zama ko
me?" Knocking kofar dakin aka yi Safiyyah ta mike ta bude taga Mustapha
tsaye ya shirya alamar zai fita aiki yace "Zaki fito ki yi maku breakfast
ne?" Safiyyah tace "Har yanxu duk jikina ciwo yake min wallahi
Yaya" Yace "Toh bari ayi maku order" Ta gefen ido Safiyyah ke
kallon Surayya da ta fito parlon daga dakinta idonta akan Centre table wato
tana duba makullin da ta ajiye, Surayyah ta kalli Mustapha tayi mitsi mitsi da
ido tace "Mustapha bayan Aslam ya tashi bacci na tambayesa makullin shi ne
ya dauko min wani toy dinsa ashe ciki ya zura, na samu da kyar na ciro makullin
sannan na fito na ajiye mata kan Centre table 30 minutes ago, to kaga dai yanxu
babu makullin kan Centre table din sannan bata fito daga dakin ka ba, me hakan
ke nufi??" Mustapha ya kalli kan Centre table din, can ya kalli Safiyyah
da ta hade rai tana rike da waist dinta yace "Safiyyah kin dau makullin
ne?" Safiyyah ta wani kallesa tace "Ban gane na dau makullin ba
Yaya" Cikin daga murya Surayyah tace "Wallahi in baki fito min daga
dakin miji ke da shegiyar kawarki ba duk abinda na maku ku kuka ja ma kan ku a
gidan nan" Safiyyah tayi wani dariya tana tafe hannu tace "Toh ni
kuma dakin yayana ne, ita kuma Khaleesat dakin yayan kawarta ne, kin ga kuwa
baki isa ki ce mu fito ba bayan bamu da wani dakin da za mu zauna in mun
fito" Rungume hannu Mustapha yayi yana kallonsu ya kasa cewa komai,
Surayya ta yo kan Safiyyah a fusace Mustapha ya tareta yace "Kee baki da
hankali ne??" Safiyyah tayi wani shewa tace "Ka kyaleta dai ta zo ta
taΙa ni zan nuna mata da sabon dabanci na dawo daga Nigeria, wallahi sai na
tuge mata gashin kanta gaba dayansa, ta zo ta taΙa ni ta ga ikon Allah"
Khaleesat dai tayi tagumi duk jikinta a sanyaye tana jin su, Surayyah ta fashe
da kuka tace "Wallahi Mustapha zan bar maka gidan nan kai da Safiyyah ku
zauna don bazan ci gaba da zama da matsiyaciyar ba a gida daya, sai dai ka zaba
ko ni ko ita a gidan nan" Safiyyah tace "Ke din banza, minti nawa ne
ya canza ki amma ni bazai taΙa canza ni ba tunda jininsa ce ni, ke kuwa tsaf
zai iya sakin ki ya auro wata" Surayya tayi wani kukan kura zata cafko
Safiyyah, Mustapha yayi saurin riketa ya ja ta zuwa dakinta yana masifa kamar
zai ari baki, Safiyyah ta koma daki ta dinga babbaka dariya har da rike ciki,
Khaleesat dai sai kallonta take ta kasa cewa komai, after a while Mustapha ya
sake knocking dakin, Safiyyah ta fito ta wani kauda fuska tana jiran jin abinda
zai ce, nan ya fara lallabata yana cewa "Pls Safiyyah in dai kin san kin
dau makullin kiyi hakuri ki kyaleta ki koma dakin ki, don ni zaki yi ai ba don
ita ba, kin ga i am almost late for work, don Allah in kin dau makullin kiyi
hakuri ko koma dakin ki" Safiyyah taki cewa komai tana girgiza kafa daya,
haka ya dinga lallabata daga karshe ta kallesa tace "Na ji, amma wallahi
ka ja mata kunne da kyau ta fita sabgata a gidan nan idan ba haka ba za mu yi
batattciya da ita, don jahilci zan dinga nuna mata iri iri wallahi"
Mustapha yace "Na ji, i will talk to her" Juyawa Safiyya tayi ta koma
dakin, shi dai ya koma parlor ya tsaya yana jiran yaga fitowar Safiyyah.
Khaleesat felt relieve bayan sun koma dakin Safiyyah, sai sannan ne ma ta samu
bacci ya dauketa don kasa bacci tayi a dakin Mustapha. Wajen karfe uku da rabi
na yammacin ranan Safiyya ta dau wayarta dake ringing sai kuma ta kalli
Khaleesat tace "Housemate din ki ne, kilan ya zo ne, tun daxu yace in tura
masa location ta WhatsApp" Tana fadin haka tayi picking call din ta kai
kunne tare da yi masa sallama, after few seconds tace "Ohk to" Daga
haka ta katse wayar tana kallon Khaleesat tace "Yana waje" Ita dai
Khaleesat ta kasa dago kanta ga wani faduwa da gabanta yayi.
[7/4, 8:51 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Safiyyah ta
gama saka Jacket dinta da neck warmer tana kallon Khaleesat da ta kasa tashi
daga inda take zaune tace "C'mon Khaleesat, yana fa waje yana jira, and
the weather is very cold outside, don Allah ki tashi mu je" Da kyar
Khaleesat ta tashi tana jin bugun zuciyarta na tsananta ta dau Veil din Abayan
jikinta ta yafa kanta a hankali, gaba daya jikinta a sanyaye yake don bata san
ta yaya zata fara hada ido da Jay ba, Safiyyah na kallonta tace "Baza ki
saka rigar sanyin ki ba?" Khaleesat ta girgiza mata kai kawai, Safiyyah
tace "Saboda room heater ne fa yasa kike jin kamar ba sanyi sosai a garin,
amma wallahi azababben sanyi ake a waje idan kika fita" Ita dai Khaleesat
bata ce komai ba don bata ma san me Safiyyah ke cewa ba, duk tunaninta ita dai
da wani idon zata kalli Housemate dinta, Safiyyah ta tabe baki ganin Khaleesat
taki tanka mata kamar ma bata san me take cewa ba, Safiyyah ta nufi kofa
Khaleesat ta bi bayanta tana tafiya a hankali kamar mara lafiya, a haka suka
fito parlor, Safiyyah bata ko kalli Surayyah dake zaune parlor tana ba yaronta
abinci ba ta nufi kofar fita, ita dai Khaleesat na bin ta a baya walking slowly
fuskarta dauke da damuwa, Surayyah ta bi su da wani shegen kallo har suka fita
daga parlon, Khaleesat na hada ido da Housemate dinta dake jingine da motarsa
ya rungume hannunsa taji wani kuka na neman taho mata from no where, amma ta
dake ta sunkuyar da kanta tana biye da Safiyyah har suka iso dai dai inda yake
tsaye, sau daya ya kalli Khaleesat ya dauke idonsa ya mayar kan Safiyyah dake
gaishesa, ya amsa gaisuwanta da murmushi fuskar sa yace "Ya hanya?"
Safiyyah tace "Hanya Alhamdulillah" Ita dai Khaleesat gefe ta koma ta
tsaya har sannan ta kasa hada ido da shi tana wasa da veil dinta, nan kuma
daurewa kawai take kar ta fashe da kukan dake cin ta, bayan sun gama gaisawa da
Safiyyah, ya juya ya kalli Khaleesat for the second time, calmly yace
"Housemate" Kamar jira take ta fashe masa da kuka sosai, ya sauke
idonsa yayi shiru, after some seconds... walking slowly ya karasa har inda take
tsaye yayi kasa da murya yana kallonta yace "Ina Jacket din ki?" Ta
kasa cewa komai tana kuka a hankali tana girgiza masa kai, cire tsadadden rigar
sanyin jikinsa yayi yana kallonta ya zaga ta bayanta yace "Wear this, the
weather is cold" Ta gyada masa kai kawai wasu hawayen na sauka idonta ta
amshi Jacket din nasa ta saka, lokaci daya kamshin turarensa da ta dade bata ji
ba ya cikata ta ko ina ga kuma warmth din jikinsa from the Jacket, ji tayi
kamar an yaye mata duk wani damuwar dake tunkushe a ranta, Ita dai Safiyyah na
tsaye tana kallonsu, har cikin ranta take jin tausayin Khaleesat don tana jin
ta ne kamar er uwarta ta jinin, Jay ya cire neck warmer din wuyansa ya daura
mata kan Jacket din, ita dai Khaleesat ta kasa barin su hada ido, taji daddaden
kamshin turarensa na kara mata wani irin nutsuwa da relieve, Ya juya ya kalli
Safiyyah yace "Za mu je tare da ke can apartment din nata yanxu ko?"
Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ohk, let me get her luggages"
Daga haka ta juya ta koma cikin gida, ya bude ma Khaleesat gaban motarsa yana
kallonta, ita dai ta kasa hada ido da shi wasu hawayen na taruwa idonta ta
shiga motar ya kulle gently, after some minutes Safiyyah ta fito da akwatin
Khaleesat guda biyu ya bude booth ya saka a ciki, Safiyyah tace "Let me
get the rest" Daga haka ta juya ta koma cikin gidan ta dauko sauran kayan
su ma ya amsa ya saka a booth, Safiyyah ta shiga back seat sannan ya zaga ya
bude driver seat ya shiga, the ride was so silent ga snow da aka fara yi, after
almost 20 minutes suka iso sabon Apartment din da Jay yayi renting ma
Khaleesat, parking yayi a garage din apartment din yayi shiru, sai kuma ya
jinginar da kansa da driver seat ya lumshe ido bayan ya tuna makullin apartment
din na can gida ya bar sa, after some seconds ya Ιan shafa kansa yace
"Sorry... i think na mance makullin apartment din a can gidanmu"
Reverse ya fara yi bayan ya fita garage din ya dau hanyar gidansu, ita dai
Safiyyah tayi murmushi kawai bata ce komai ba, dai dai sanda wayarta ya fara
vibrate ta duba taga Mustapha ne ke kiranta, hade rai tayi, tayi silencing
kiran sannan ta kife wayar a cinyarta, wato ya dawo yaga bata gida shi ne zai
fara doka mata kira, Jay na isa gidansu yayi parking a waje ya juya ya kalli
Khaleesat da tayi nisa tunanin da take, yace "Let me get the keys
Housemate" Bata bari sun hada ido ba ta gyada masa kai kawai, ya bude
motar zai fita, ta kalli snow din dake sauka sai kuma ta kallesa, da sauri ta
fara kokarin cire Jacket dinsa dake jikinta tace "Should i give you the
Jacket? Naga akwai sanyi" Ya juya ya kalleta, sai a sannan suka hada ido
all this while, taji kamar kasa ya bude ta shige tayi saurin sauke idonta, ya Ιan
yi murmushi yace "Don't worry, i will get another one idan na shiga gida
yanxu" Daga haka ya sauka daga motar ya shiga gidansu. Bayan kusan minti
goma sai ga shi ya fito daga cikin gidan yana sanye da wata rigar sanyin,
Khaleesat dai kallonsa kawai take, ganin ya tsaya bakin gate din gidan nasu
yana kallon direction daban yasa ta kalli direction din da yake kallo, sunkuyar
da kai tayi bayan ta hango Ajay yana tahowa tare da katon karensa Legend yana
rike da Leash din karen, Safiyyah tayi kasa da murya tace "That is Ajay,
and ya kamata ki gaishesa gaskiya Khaleesat" Khaleesat ta Ιan kalli
Safiyyah, a hankali tace "Baza ki gane ba Sophie wallahi kunya nake
ji" Safiyyah tace "To ya za ki yi? Dole dai haka zaki ajiye kunyan ki
sauka ki gaishe sa, ni dai nasan baxai taΙa barin Jay yayi duk wannan hidimar
da yayi maki shi kadai ba, tunda kan su a hade yake, nasan dole Jay zai yi
shawara da shi before anything, Kuma tare za su yi komai..." Khaleesat ta
kasa cewa komai amma har cikin ranta she is so ashame of speaking to him, har
yau maganganun da Abdul yasa tayi masa ta waya na yawo a kanta, Safiyyah ta
hade rai ganin Ajay ya kusa inda Jay ke tsaye tace "Pls Buckle up kiyi
abinda ya dace Khaleesat, ni na tsani wannan halin kauyancin da kike yi
wallahi, to meye a ciki gaishesa fa kawai zaki yi, ai ko ba komai kokarin da
shi ma yayi maki ya kamata ki gaishe sa, abinda ya faru ya riga ya faru so
forget that and do the needful" Jiki a sanyaye Khaleesat ta kai hannu zata
bude motar, amma Ajay ko kallon inda suke bai yi ba ya wuce Jay dake tsaye yana
jiransa yayi shigewarsa cikin gida, Jay ya bi bayansa, a sanyaye Khaleesat ta
fasa bude motar ta juya tana kallon Safiyyah, Safiyyah ta sauke wani ajiyar
zuciya tace "He is still angry at what you did to them, nasan zai huce
definitely" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, after some
minutes sai ga Jay ya fito daga cikin gidan ya bude driver seat ya shiga yace
"Sorry for keeping u waiting, makullin apartment din na aljihun jacket
dina ne, and Ajay wore the Jacket out for a walk" Safiyyah na murmushi
tace "It's fine" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, wajen
karfe biyar da rabi suka iso sabon Apartment din, ya kashe motar yana kallon
Khaleesat a hankali yace "This is ur new apartment Housemate, i hope you
will love it" Daga haka ya bude motar ya sauka, Safiyyah ma ta sauka tana
kallon gidan tana murmushi don sama da kasa ne, Khaleesat ta goge hawayen dake
makale idonta sannan ta sauka daga motar, bude masu kofar apartment din Jay
yayi ya jira suka fara shiga sannan shi ma ya shiga, yayi switching din light
din parlon da Heater, Safiyyah na murmushi tana bin parlon da kallo ganin yafi
na tsohon Apartment din girma tace "Waow, this is soo beautiful" Jay
ya zauna kan kujera yana duba wayarsa dake vibrate alamar kira, Safiyyah ta
bude kofar da ta gani a parlor taga kitchen ne, ita dai Khaleesat na tsaye
bayan kujera tana kallon Jay ta kasa cewa komai, Safiyyah ta fito daga kitchen
din ta nufi sama zata duba dakunan gidan, after some seconds Jay ya gama
sending message din da yake a wayarsa ya juya suka hada ido da Khaleesat, sauke
idonta tayi tana wasa da gefen Veil dinta, Calmly yace "Housemate" Da
kyar tace "Um" Ya mike ya dawo gabanta ya tsaya yana kallonta, a
hankali yace "You like the new apartment?" Ta gyada masa kai tana
kokarin ganin bata fashe da kuka ba, bai sake ce mata komai ba don yana kallon
fuskarta yasan kuka zata fara masa, Safiyyah ce ta sauko downstairs tace
"Ya Jawwad wallahi gida yayi kyau Maa sha Allah, Allah Ubangiji ya saka da
alkhairi yasa kafi haka, my frnd is really grateful ba ma ta da bakin yi maka
godiya shi yasa nake magana on behalf of her, mun gode sosai, Allah Ubangiji ya
kare ka da sharrin mahassada, thank you so much Housemate we are really
grateful" Ζan murmushi yayi bai ce mata komai ba, Khaleesat ta goge
hawayen da taji ya silalo idonta, Safiyyah tace "Toh ni zan tafi yanxu,
yayana sai doka min kira yake, ya kirani yafi sau goma ban dauka ba" Jay
yace "Ohk, to bari in yi dropping din ki" Da sauri Safiyyah tace
"A'a wallahi ba sai ka ba kanka wahala ba Yaya Jawwad, har nayi order din
Lyft gashi nan zuwa" Yace "Ohk then, my regards to everyone back home
Safiyyah" Safiyyah na murmushi tace "In sha Allah" Sai kuma ta
kalli Khaleesat tace "Toh mu je ki rakani kawata" ta kama hannun
Khaleesat suka fita daga parlon, suna barin apartment din Safiyyah ta kalleta
tace "If you like kar ki dena wannan kukan ki bude baki kiyi masa godiya
sosai, shi yasa ma nace ki rakani don nasan halinki in kika fara kuka ba lallai
ki masa godiya ba, in mutum yayi kukan sau daya ba shikenan sai ya rungumi
kaddara ba yayi abinda ya kamata yayi move on, amma ke kiyi ta kuka kamar me
takaba, i understand you are lost of words amma kiyi composing kanki kiyi
appreciating dinsa plss, wallahi ban taΙa ganin mutum with kind heart like
Jawwad ba, kuma shi tsakani da Allah yake abun sa ba don komai ba" Khaleesat
ta fashe da kuka muryarta na rawa tace "I don't know where to begin
Safiyyah, ban san ta inda zan fara masa godiya ba, i am just confuse"
Safiyyah ta rungumeta tana patting bayanta a hankali tace "I understand
Khaleesat, i understand you, nasan you are confuse, but just start from
anywhere, tell him anything that means appreciation zai fahimce ki"
Khaleesat ta gyada mata kai hawaye masu zafi na sauka idonta, a haka Lyft din
Safiyyah ya karaso, Khaleesat ta kamo hannunta da kyar tace "Thank you for
everything Safiyyah, thank you for always being by my side through thick and
thin, thank you for being supportive, nagode Allah ya saka da alkhairi"
Tana magana hawaye na zuba idonta, Safiyyah ta hade rai tace "C'mon
Khaleesat, ni kar ki sake min godiya, don na dauke ki tamkar sister din da bani
da ita ne, i care so much about you" Safiyyah ta zame hannunta ta bude
bayan motar ta shiga ta kulle kofar sannan ta daga ma Khaleesat hannu, kai
kawai Khaleesat ta gyada mata tana share hawayen da yaki tsaya mata sannan ta
juya tana tafiya a hankali ta koma Apartment din, tana bude kofar parlon Jay ya
juya ya kalleta sai kuma ya ci gaba da danna wayarsa, walking slowly ta nufesa
har inda yake zaune ta durkusa kasa tana kallonsa, Kafin tace komai ya dakatar
da ita ba tare da ya kalleta ba yana magana softly yace "I don't want ur
thanks Khaleesat, bana bukata, ba don ki gode min nayi duk abinda nayi ba, nayi
ne saboda Allah, nayi ne saboda kinyi deserving in yi maki, so bana bukatar
godiyan ki pls, instead ki gode ma Allah" Khaleesat ta kasa cewa komai
kanta a kasa hawaye na zuba idonta daurewa kawai take kar ta fashe masa da
kuka, ya mike yace "Let me show you round the house before i leave"
Tana goge fuskarta ta mike ta fara bin sa tana tafiya a hankali, kitchen ya
fara kai ta, ita dai tana tsaye daga bakin kofa take bin kitchen din da kallo,
hatta foodstuff duk ya siya mata, fridge din kitchen din ma was fully stocked
up, ga cookies kala kala a kitchen din saboda yasan tana son cookies, ta kasa
daurewa bata san sanda ta kamo hannunsa ba muryarta na rawa tace "Ban san
ta inda zan fara maka godiya ba...." Ya Ιan bude ido cause he never saw
that coming, lkci daya yayi saurin janye hannunsa daga nata, yana murmushin
karfin hali yana komawa baya ba tare da ya bari sun hada ido ba yace "Nace
maki bana bukatar godiyan ki, let me show you other places" Daga haka ya
fita daga kitchen din, ta jingina da kofar kitchen din bayan ya fita tana kuka
a hankali, sai da tayi me isarta sannan ta fito daga kitchen din tana jan kafa
da kyar, tsaye ta gansa dai dai staircase yana danna wayarsa alamar ita yake
jira, yana ganin ta fito daga kitchen din ya mayar da wayar aljihunsa ba tare
da ya kalleta ba yace "The rooms are upstairs" Sai da ta karaso har
inda yake sannan ya fara haura stairs din ta bi bayansa, ya fara nuna mata
spare rooms guda biyu, sannan ya bude kofar nata dakin, calmly yace "Ur
room" Ita dai tana tsaye bakin kofa tana kallon dakin babu ko kiftawa, ba
abinda babu cikin dakin nan na comfortability, duvets ma manya hudu duk sababbi
cikin case dinsu ta gani a dakin, the room look so beautiful sai wani sparkling
yake, a hankali ta juya ta kallesa ya sauke idonsa bai dai ce mata komai ba,
sai kuma ya juya ya bar bakin kofar dakin ya sauka downstairs ta bi sa da
kallo, jingina tayi da kofar dakin for almost 5 mins tana kallon cikin dakin, a
hankali ta juya ta bar bakin kofar dakin ta fara sauka downstairs cikin rashin
kuzari, tsaye ta gansa bakin kofar fita daga parlon, yana ganin ta sauko yace
"I will take my leave now Halysaah, amma dai sai jibi zaki shiga school,
cause i see you look stressed" Ta gyada masa kai a hankali, yace
"Ohk, here are the apartment key" Ta karasa ta karbi bunch din
makullan da yake mika mata, sai kuma ta kallesa tace "Baka cire spare key ba?"
Yace "A'a ki ajiye su kawai a wajen ki" Ta gyada masa kai kawai bata
ce komai ba, ya bude kofar parlon without looking at yace "Text me ur Skin
care set via WhatsApp" Yana fadin haka ya fita daga parlon yace "Good
night Halysaah" Tana kallo ya kulle kofar parlon, after some minutes ta ji
alamar tafiyar motarsa.
[7/6, 5:55 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat ta
dade rabon da tayi bacci peacefully babu abinda ke damunta a rai kamar yanda
tayi daren jiya, bayan tayi sallan asuba ta sake komawa baccin don garin akwai
sanyi sosai, karfe takwas da yan mintuna na safe vibration din wayarta ya
tasheta daga baccin da take, ta jawo wayar a hankali tana duba me kiranta duk
da tasan bazai wuce Safiyyah ba, ai ko taga ita ce, picking din kiran tayi ta
kai kunne murya can kasa tace "Sophie" Safiyyah tace "Nasan kina
nan kina bacci ko?" Khaleesat tace "Um, Good morning" Safiyyah
tace "Morning, amma baza ki shigo school ba yau?" A hankali Khaleesat
tace "Sai gobe in sha Allah" Safiyyah tace "To Allah ya kai mu,
ni dai gani har na shigo school din, amma fa gobe akwai get together da za mu
yi na manta ban gaya maki ba, just few of us, ba mu wuce mu sha biyar ba duka,
the time is 5pm prompt" Khaleesat tace "Cikin sanyin nan za ku yi get
together Sophie?" Safiyyah tace "So? Kin ga alamar sanyi na hindering
daily activities din mutane a kasar nan ne in dai ba snow bane yayi mugun yawa?
Beside ai ba a open space za ayi get together din ba, it will take place at one
of our Course mate House" Khaleesat tace "Toh ai shikenan"
Safiyyah tace "Ban gane ai shikenan ba, banda ke za ayi get together din
kenan kike nufi?" Khaleesat tace "Kema kin san bana son gathering ko
ya yake Sophie, me yasa kika yi tunanin har da ni za ayi bayan kinsan bazan je
ba" Safiyyah tace "Plss for once ki zama Social or should i even say
Civilised Khaleesat, ko ba komai idan kika zo za kiyi nishadi ki mance duk wani
damuwar ki na Nigeria kiyi freshen up din ΖwaΖwalwar ki for this semester, amma
kawai kiyi ta zaman gida ke kadai kullum kamar me wani cuta, kin ga wannan
shekara dayan da ya rage mana so nake ki waye ki fara yin abubuwa irin na
wayayyu ta yanda babu wanda zai raina ki babu wanda zai san daga wani irin
background kika fito, yanxu fa ba da bane a gareki Khaleesat don ke kin ma
tsallake matsayin da mu bamu zo ba ma, don haka use this last opportunity in USA
ki zama wise ta yanda babu shegen da zai raina ki" Khaleesat dai idonta a
lumshe yake don har ta ci gaba da baccin ta, Safiyyah tace "Hello"
Khaleesat ta bude ido da kyar tace "We will talk later Sophie"
Safiyyah tace "Tun da ina gaya maki gaskiya ba dole kice we will talk
later ba, kuma ko kin ki ko kin so sai mun je get together din nan da ke don
yanxu ba da bane" Daga haka ta katse wayar ta, Khaleesat ta gyara
kwanciyarta ta rufa da duvet zata ci gaba da bacci, ita kanta tasan bashin
baccin da bata yi a Nigeria ne take biya....
Sai kusan karfe uku na rana Khaleesat ta tashi daga bacci, bayan tayi
wanka tayi sallan azahar ta sauka parlor don yunwa take ji sosai, kunna heater
din parlon tayi don parlon yayi sanyi kamar fridge, ta karasa ta tsaya jikin
window din parlon ta daga labule tana kallon beautiful Neighborhood din ta, ko
ina fari tas saboda snow din da aka yi sosai daren jiya da bai gama narkewa ba,
after some minutes ta sake drape din windan a hankali ta nufi kitchen, shayi ta
hada ta debi cookies ta dawo parlorn ta zauna, bayan ta gama ta kai plate din
da cup kitchen ta wanke sannan ta koma sama don harhada textbooks dinta da
reading materials, gaba daya sauran kayanta na tsohon Apartment dinta duk ta
gansu a dakin alamar Jay ne ya kwaso mata su daga old apartment din nata, ta
gama hada kan reading materials dinta, ta fara gyara kayan sawanta a press din
dakin kenan taji an danna bell din gidan, ta Ιan yi jim to be sure a apartment
din take jin karan bell din, after some seconds ta fita daga dakinta ta sauka
downstairs bayan an sake danna bell din, ta karasa har bakin kofar ta bude a
hankali tana duba waye a bakin kofar, yana kallonta calmly yace "Good
evening Halysaah" Ζan murmushi tayi ta koma gefe don basa hanyar shigowa,
yace "A'a kawai ki shirya, za mu je kiyi shopping abubuwan da kike bukata,
i will wait for you inside in the car" Shiru Khaleesat tayi tana kallonsa,
ganin zai koma motarsa tace "Amma ai ba abinda zan bukata yanxu, don naga
akwai komai a gidan" Yace "For ur personal use Halysaah, beside ai
babu cleaning agents a gidan, i forgot to get them..." Khaleesat ta sauke
idonta bata ce komai ba, yace "I am waiting at the garage" Daga haka
ya juya ya koma garage ta bi sa da kallo kafin ta rufe kofar ta juya ta nufi
sama a sanyaye, bayan minti sha biyar ta sake saukowa downstairs tana sanye da
jacket dinta, tana fita waje taji wani azababben sanyi duk da Jacket din
jikinta, ta kulle gidan tana rike da makullin ta nufi motarsa, bude front seat
din tayi ta shiga ta kulle, yace "Akwai sanyi ko?" Tana kara takurewa
waje daya tace "Sosai, ni ban ma san akwai sanyi haka ba" Yayi
murmushi ya kara dumin motarsa yace "Kina cikin gida da room heater ya za
ayi ki san akwai sanyi" Murmushi tayi tana juya makullin hannunta ta Ιan
kallesa a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya Halysaah, how
was ur night?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Hope you are
comfortable in the new house?" Ta gyada masa kai tana kallonsa, yace
"Good to hear that..." Tada motar yayi suka bar garage din, bayan sun
dan yi nisa da tafiyar a hankali tace "Yaya Junaid fa?" Sai a sannan
ya kalleta yace "Ajay yana gida, he is under the weather, baya son irin
season din nan" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "Ya kika baro su
Umma and Aunty Farida?" Tace "Mun yi chatting dasu jiya da daddare,
Umma tace tana son ta maka magana if you are around" Yace "Ohk to
idan mun koma gida sai in kira ta" Khaleesat bata sake cewa komai ba, jifa
jifa dai take kallonsa, shi kam ya maida hankalinsa kan driving din da yake,
Wani babban Shopping mall ya kai su, bayan yayi parking sun shiga ciki ya dau
shopping cart yana turawa, zata amsa cart din a hannunsa yayi murmushi yace
"No, don't worry Halysaah, i will do the wheeling and u do the
shopping" Ta sauke idonta bata ce komai ba, gun cosmetics ya fara kai su yace
"Ki dauki duk abinda kika san za ki bukata a nan Housemate..." Ta Ιaga
kai ta kallesa, ya Ιan bude ido yace "Look Halysaah, i want you to be free
and open with me, kar ki saka komai a ranki ko kiji nauyin tambayar wani abu da
kika san kina da bukata, assuming i don't have the means ai bazan ce zan yi ba
Halysaah, so feel free plss Housemate, haka jiya nace ki turo min Skin care set
din ki ba ki turo ba, ni ina maki duk abinda nasan zan ma kanwata ne ko er uwa
ta, so ki dau duk abinda kika san kina da bukata yanxu" Ita dai idonta na
kasa bata ce komai ba, ya mika mata katin kudinsa yace "Ko in baki katin
in jira ki a mota?" Ta Ιan kallesa sai kuma ta girgiza masa kai a hankali
tana murmushin karfin hali tace "A'a" yace "Then shop all you
need Housemate" Cikin sanyin murya tace "Ohk, Thank you so much"
Shi dai murmushi kawai yayi bai ce mata komai ba, few abubuwan da tasan zata yi
needing take dauka a wajen cosmetics din tana ajiyewa a cart din da yake tura
mata, amma idan ta dau abu daya sai ya kara mata biyu a kan wanda ta dauka, ita
dai sai dai ta kallesa, ta dau set din Cream din shafawanta da shower gel, nan
ma yayi doubling mata su ya zuba a cart, a hankali tace "Ina da saura
fa" Bai ce mata komai ba, ta ci gaba da tafiya, tana kallon pad amma ta
kasa dauka kawai ta wuce, shi ma kuma bai ce mata komai ba yana wheeling cart
din har dai suka gama da bangaren cosmetics, ya nufi gun cleaning agents tana
biye da shi abaya, duk shi ya dinga daukan abubuwan da yasan zata bukata a
gida, sai bayan minti talatin suka fito daga shopping mall din ya zuba duk
abubuwan da suka siya a booth din motarsa, maimakon su nufi gida sai taga ya
kai ta wani babban store din Africa yace "I didn't get much cooking
ingredients for you cause i am not good at that, so mu shiga sai ki dau duk me
zaki bukata na girki...." Ta kallesa tace "To ai ko fara amfani da
wanda ka siya ban yi ba" Yace "I know, zan Ιan yi tafiya ne
Housemate, so i want to be sure you have enough of everything" Khaleesat
tayi shiru tana kallonsa, yace "Mu je" Daga haka ya sauka daga motar,
jiki a sanyaye ita ma ta sauka ta bi sa zuwa cikin store din, Spices din girki
da su seasoning, albasa, irish, dankalin hausa, doya, eggs, all kind of
peppers, tomatoes, da dai duk wani mahadin girki suka siya a store din, sannan
ya kara mata frozen chicken da turkey, sai beef, bayan ya biya kudaden suka bar
store din, yana driving Khaleesat ta kallesa cikin sanyin murya tace
"Thank you so much, Allah ya sa kafi haka" Yayi murmushi kawai, sai
kuma ya dau wayarsa dake vibrate yana dubawa, ganin Ajay ne ke kiransa yayi
picking ya kai kunne yace "How are you feeling?" After some seconds
ya ajiye wayar, Khaleesat tace "Is he sick?" Yace "Yeah, i told
you he is under the weather" Khaleesat ta yi shiru, Jay ya kalleta yace
"Ko mu je gidan ki dubasa?" Ta Ιan buda ido, sai kuma tayi murmushi a
sanyaye tace "Bazai kulani ba ai" Jay yayi dariyar da bai yi niyya ba
yace "Saboda me bazai kula ki ba?" Ta sauke idonta tace "Jiya ma
da ka je dauko makulli ai yayi kamar bai gan mu ba a mota" Jay yace
"Jiyan nan ma da ku ka gansa ba shi da lafiya, sai da nace kar ya fita
yaki saurarana, bayan ya fita kuma aka fara snow" A hankali Khaleesat tace
"To Allah ya basa lafiya" Jay yace "Mu je can gidan za ki
gaishesa?" Tayi shiru don har zuciyarta tana fargaban kar ya shareta, Jay
yace "A bari next time ko?" Ta sauke idonta a hankali tace "To
mu je, amma idan bai kulani ba ai shikenan" Jay yayi murmushi yace
"Idan bai kulaki ba kema sai ki sharesa" Khaleesat ta Ιan kallesa
suka hada ido, murmushi tayi har sai da dimple dinta ya lotsa tana kallonsa, ya
dauke idonsa ya maida dubansa kan titi yana ci gaba da driving dinsa gently.
Kusan karfe biyar da rabi suka isa gidan, Jay yayi parking a compound ya kashe
motarsa ya Ιan kalleta yace "I can see you are tensed?" Ζan murmushi
tayi tana wasa da fingers dinta bata ce komai ba, ya bude motar yace "To
mu shiga" A hankali ta bude motar ita ma ta sauka, ta bi Jay da kallo har
ya dau hanyar entrance din babban gidan nasu, ta bi bayansa tana tafiya slowly,
bayan ya bude kofar parlon sai da ya jira har ta iso, ta sunkuyar da kanta ta
shiga parlon sannan shi ma ya shiga, sosai gabanta ya fadi bayan wasu memory
sun dawo mata, memory that is so disturbing to her, tana tafiya a hankali ta
karasa har cikin parlon ta zauna kan kujeran da ta zauna ranan da Jay ya kawota
gidan da daddare, ta daga kai ta kalli Reading Nook din da Ajay ya zauna a
ranan da daddare, sauke idonta tayi tana wasa da fingers dinta, Jay ya karaso
cikin parlon yana kallonta yace "Give me some minutes" Ta gyada masa
kai ya nufi stairs ta bi sa da kallo har ya haura sama, Jay na tafiya sama ya
karasa bangaren Ajay ya bude kofar gently yana kallon cikin dakin nasa wanda
babu haske sosai don Drape din dakin very thick one ne saboda sanyi, Jay ya
shiga ciki ya kunna dim light din dakin yana kallon Ajay, kwance yake saman
gado yayi rub da ciki yana bacci, har wani hucin zafi dakin yake tsabar yanda
ya kure room heater, Jay ya karasa kusa da gadon yana kallonsa, lallai yanxu ya
kara tabbatar da bai da lafiya, Ajay ne har za a bude masa daki a kunna wuta a
shigo bai sani ba, ai duk baccin da yake kana taΙa kofar dakinsa yake tashi tun
kafin ka shigo masa, Jay ya juya ya fita daga dakin ya jawo kofar gently amma
bai kulle ba, ya koma downstairs yana kallon Khaleesat yace "Mu je sama
Housemate, yana bangarensa" Mikewa tayi tana kallonsa ta nufesa, Jay yace
"And before i forget, kiyi masa godiya he paid for ur new apartment"
Khaleesat tayi shiru tana kallonsa amma ta kasa cewa komai, jiki a sanyaye ta
bi Jay suka haura sama zuwa bangaren Ajay, Jay ya tura kofar dakin Ajay gently
ya shiga sannan ya kalleta yayi mata alamar ta shigo, ta dake tana tafiya a
hankali ta shiga dakin, haka kawai taji gabanta na faduwa, dakin nan nasa dai
ne da tayi kwanaki biyu a ciki sanda take gidan, kallo daya tayi ma Ajay dake
kwance kan gadon sannan ta kalli Jay, Kan lallausan farin carpet din dakin ta
durkusa, Jay ya nuna mata kujera alamar ta zauna ta girgiza masa kai kawai,
kamar yanda ta san dakin har yanxu komai na cikinsa fari ne kal, ga wani irin kamshi
da dakin yake, amma fa ji tayi tana jin zafi saboda room heater din da ya kure,
Jay ya karasa har inda yake kwance ya duka yana kallon fuskarsa ya janye Head
warmer din da ya Ζima a kai, calmly yace "Hey...." A hankali Ajay ya
bude idonsa yana kallonsa, hade rai yayi cikin muryar bacci yace "Gerrout
Jay, meye na shigo min Bedroom" Jay ya mike tsaye yana kallonsa yana
murmushi yace "Kai baka shiga na mutane?" Ajay ya jawo pillow dake
gefensa da kyar ya jefa masa yace "Gerrout Jawwad, i want to be alone, i
think i am running temperature, i am feeling sleepy, can i speak to my dad? I
want to speak to Ammi too" Jay yayi murmushi don yasan duk sumbatu yake
kamar yanda ya saba in bashi da lafiya, Jay ya duka yana kallonsa yace
"Should i get u a Cup of Coffee? And some drugs?" As if murmuring
Ajay ya lumshe ido yace "Yess pls, but don't come back" Jay yace
"To ta ina za a miko maka Coffee din?" Ajay bai bude ido ba yace
"Drink it for me Jay" Jay yayi dariya yace "Ohk, amma an zo duba
ka" Ajay ya bude idonsa da kyar yace "Don Allah ka fita, leave my
room pls Jawwad" Sai kuma ya juya zai jawo wani pillown a fusace ya wurga
ma Jay kawai suka hada ido da Khaleesat dake ta kallon ikon Allah, juyawa Ajay
yayi da sauri ya kalli Jay amma tuni Jay ya nufi kofa trying not to laugh out
loud ya fita daga dakin, Khaleesat ta bi Jay da kallo taji kamar ta tashi ta bi
sa, Ajay ya kasa juyowa, yana kokarin tuna abubuwan da ya fada da Jay ya
tashesa bacci.....
[7/7, 9:34 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat dai
har sannan tana durkushe inda take a dakin ga gabanta sai faduwa yake, lkci
lkci take satan kallon Ajay, bayan kusan minti biyu ya mike zaune daga kwancen
da yake ya sauke kafafuwansa kasa yana facing bangare daban na dakin, he still
can't recall all what he said to Jay bayan ya tashesa a bacci, after some
seconds ya jawo head warmer dinsa ya saka, ya daure ya mike tsaye ya juya, hada
ido suka yi ta sauke idonta a hankali, ya hade rai yace "What happened?"
Girgiza kai tayi ba tare da ta kallesa ba tana wasa da farin carpet din da take
durkushe tace "Kawai gaisheka na zo in yi ne" A takaice yace
"Gaisheni for what? Do we have any agenda?" Sai a sannan ta daga kai
ta Ιan kallesa tace "And i want to say thank you for the apartment you got
me" Kofa ya nufa yace "Karya yake maki, meye hadina dake zan biya
maki apartment, ki dai je ki masa godiya...." Bata san sanda ta bi sa da
wani irin kallo ba har ya fice daga dakin, can ta wani murguda baki ta mike ta
nufi kofa, har zata fita sai kuma ta tsaya bayan ta hango wani abu a gaban
mirror din dakin nasa, tana tafiya slowly ta karasa har gaban madubin tana
kallon Hair ribbon dinta dake ajiye, ta dau ribbon din tana jujjuyasa tana
kallonsa, wanda da alama sanda tayi kwana biyu a dakin ne ta manta shi, kofa ta
nufa ta fita daga dakin tana rike da ribbon din nata, tana isowa dai dai stairs
ta hango Ajay downstairs yana tsaye gaban Jay sai bala'i yake masa kamar
ubansa, Jay dai na zaune yana kallonsa keenly yana cin chocolate din hannunsa,
can dai Jay yace "Where is ur rod Ahmad? Ka mance baka sakko da bulalan ba
ai" Ajay na masa wani kallo yace "Seriously kar ka sake min haka bana
so, i did all what i did because of you not her, kawai don kar burden yayi maka
yawa nayi ba don komai ba, meye na zuwa kace mata ni na biya mata apartment?
Did i send you message? Upon how i warned you not to tell her amma sai da kaje
ka fada, to yanxu riban me ka ci da kaje kace mata na biya mata gida?" Jay
yace "Ashe dai lafiyarka qlau all this while Junaid? Where did u get this
strength from all of a sudden?" Khaleesat dai ta taΙe baki ta fara saukowa
downstairs, tana saukowa Ajay ya nufi stairs din fuskarsa a daure zai koma
sama, Jay ya bi sa da kallo yana cin chocolate din hannunsa, Khaleesat ma ta bi
sa da kallo kafin ya haura sama tace "Sai anjima, and thank you for everything,
Allah ya kara budi" Ya wani juya ya kalleta yace "Kee kar ki sake min
godiya, ko kinga ina wasa da ke ne?" Kamar bazata ce komai ba sai kuma
tace "Tunda kayi abinda zan maka godiya ai dole zan maka godiya, inda baka
yi ba ai bazan maka godiyan ba, wishing you quickest recovery" Ζan
murmushi Jay yayi ya mike yace "It's getting dark, mu je inyi dropping din
ki Housemate" a hankali Khaleesat tace "Ohk" daga haka ta bi
bayan Housemate dinta ta bar Ajay tsaye bakin stairs din ya bi su da kallo har
suka fita daga parlon.... Jay ya kalli ribbon din da take juyawa a hannunta
bayan ya tada motarsa yace "Where did you get that from?" Ta kalli
ribbon din tace "A dakinsa na gani" Jay yayi shiru yana kallon ribbon
din, sai kuma yace "Kuma na ki ne?" Ta gyada masa kai tana kallonsa,
ya amshi ribbon din yana kallo babu ko kiftawa, sai kuma yace "How did it
get there?" A hankali tace "Sanda ka kai ni dakin nayi kwana
biyu" Jay bai sake cewa komai ba ya mayar mata da ribbon din without
looking at her, ya fara driving zai fita daga compound din nasu, bayan sun bar
gidan calmly yace "Where did u see the ribbon in his room? Ko shi ya
baki?" Ta girgiza kai tace "A'a, kawai hangosa nayi a gaban mirror
din dakin" Jay yayi shiru bai sake cewa komai ba yana driving dinsa with
calm, a haka har suka iso apartment din nata, bayan ya kashe motar ya sauka ita
ma ta dau makullin apartment dinta ta sauka, Jay ya zaga ya bude booth zai
fiddo shopping din da yayi mata, kawai bag din cosmetics dinta ya mika mata
yace "Go with this, i will get the rest" ta Ιan duka ta amsa sannan
ta nufi kofar apartment din ta bude ta shiga ta kunna wutan parlon, sai da Jay
ya tabbatar ya ajiye mata duk siyayyan da suka yi a inda ya kamata a kitchen
din, wanda zai zuba fridge duk ya zuba mata, sannan yayi tidying din ko ina a
kitchen din, ita dai tana tsaye jikin kofa tana ta kallonsa, yana juyowa ta
sauke idonta ta juya a hankali ta bar kofar kitchen din ta koma parlor, bayan
ya fito parlor yana kallonta yace "Ki turo min account details din ki let
me send you Money for transportation to school" Ita dai Khaleesat kallonsa
kawai tayi bata ce komai ba, yace "I am waiting, zan tafi ne" Ta
sauke idonta tace "Ai akwai kudi a account din" Yace
"Halysaah" Ta daga idanunta ta kallesa, yace "Turo min details
din ki yanxu" Shiru tayi tana kallonsa, sai kuma tace "Ai bani da
number ka" Yace "Oh, na manta, ina wayar naki?" Tace "Yana
sama" Yace "To dauko" Sama ta wuce ya bi ta da kallo, sai kuma
ya dauke idonsa ya zauna kan kujera, after some minutes sai ga ta ta dawo
parlon, ta karaso har gabansa ta mika masa wayar, ya amsa without looking at
her yayi dialling numbersa a wayar sannan ya mika mata yace "Save it"
Ta amshi wayar, ta Ιan yi jim kamar tana tunanin sunan da zata yi using tayi
saving number nasa, after some seconds kawai ta saka My Housemate, ya mike yace
"Turo min details din yanxu, zan tafi" Tura masa bank details din
nata tayi, bayan yaga shigowar message din nata yace "Alright then zaki ga
alert anjima, if there is anything just ping me via WhatsApp" a hankali
tace "Ohk" Yace "Good night?" Sai da taga ya nufi kofa ta
kasa daurewa cikin sanyin murya tace "Ka ce zaka yi tafiya?" Juyowa
yayi ya kalleta yace "Sure Halysaah..." A hankali tace "Gobe
zaka tafi?" Yace "Yeah that was my plan initially, but i think if
Ajay is still sick zan yi postponing tafiyar zuwa Wednesday or Thursday"
Khaleesat ta gyada masa kai, yace "Or is there anything Housemate?" Ta
girgiza masa kai a hankali tace "Zaka dade ne?" Yace "I am going
to UK, cousin sis dinmu ce bata da lafiya zan je in duba ta, idan naga she is
much better zan koma Nigeria da ita" Khaleesat ta sauke idonta bata ce
komai ba, after few seconds a hankali tace "Allah ya bata lafiya" Jay
yace "Ameen, but do not worry Housemate, Ajay is around if there is
anything nasan zai yi idan yaga bana nan" Khaleesat ta girgiza kai tace
"A'a babu komai, i am okay, Allah ya kai ka lafiya" Jay yace
"Ameen, amma idan ban tafi gobe ba we will meet in school in sha
Allah" Kai kawai ta gyada masa, yayi mata murmushi yace "Good
night" Tace "Thank you very much Housemate, Allah ya saka da
alkhairi" Ya dora finger daya a lips dinsa yana kallonta da kyawawan idanunsa,
sauke idonta tayi, ya juya ya fita daga parlon, ta karasa window din parlon ta
tsaya tana kallonsa ta Drape har ya bar garage din da motarsa sannan ta sake
drape din a hankali ta juya, after some minutes tana jan kafa ta karasa ta
kulle kofar parlon. Washegari Khaleesat ta fito lecture Hall saboda message din
da Jay yayi mata ya shigo school din yana jiranta, dama ba lectures suke ba
suna tutorial na wani course dinsu ne kawai ta ce ma Safiyyah tana zuwa sannan
ta fito, exact spot din da yake jiranta sanda take exam ta hango sa zaune, gaba
daya attention dinsa na kan wayarsa da yake dannawa, yanda yayi keeping serious
face ya fito da ainahin handsomeness dinsa, sam bashi da wata makusa, he is
just the real definition of handsome, everything about him is just perfect, tun
daga nesa Khaleesat take kallonsa bata yi realising ba sai ganinta tayi har ta
iso inda yake zaune, ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya mike ya mayar da
wayarsa aljihu yace "Good Afternoon Halysaah" ta sunkuyar da kai tana
Ιan murmushi don sai ta ganta er karama a kusa da shi, yace "Hope ba
lectures ku ke ba?" Ta girgiza kai tace "A'a" Yace "Ohk, my
flight is in 2 hours time in sha Allah" Ta daga kai tana kallonsa a
sanyaye, suna hada ido ta sauke idonta tace "Ya Junaid yaji sauki
kenan?" Jay yace "Yeah he is better, shi ne ma yace in tafi..."
Khaleesat bata sake cewa komai ba, yace "Kin yi lunch ne?" Duk da
bata yi ba ta gyada masa kai alamar tayi, yace "Ohk ke da Safiyyah?"
Tace "Um" Yace "To shikenan, i came to tell you i am leaving,
take care of ur self Housemate, kuma kiyi concentrating a karatun ki, if there
is anything just ping me via WhatsApp" A hankali Khaleesat tace
"Dadewa zaka yi kenan?" Yayi murmushi yace "Bazan dade ba in sha
Allah, nasan dai daga can definitely za mu je Nigeria" Khaleesat ta kasa kallonsa
don sai taji kamar hawaye na neman ciko mata a ido, ta dake tace "To
shikenan, Allah ya kai ka lafiya, ya tsare" Yana kallonta yace
"Ameen" Taki barin su hada ido tace "Muna karatu ne da su
Safiyyah zan koma" Yace "Ohk" Tace "Sai anjima" Bata
jira cewar sa ba ta juya zata bar wajen tun kan hawayen da ya cika idonta ya
zubo, Calmly yace "Halysaah" kin juyowa tayi, ya zaga har gabanta ya
tsaya yana kallonta, ta kasa kallonsa tana goge hawayen da ya fara zuba idonta,
shiru yayi yana kallonta, after some seconds ya dauke idonsa a hankali yace
"But you have Safiyyah here Housemate...." Ta gyada masa kai tana
murmushin karfin hali, yace "In sha Allah bazan dade ba i promise"
Nan ma dai kai kawai ta gyada masa, yace "Ko za ki rakani Airport din?"
Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, still tana murmushi ta girgiza masa kai,
bai yi wani insisting ba bayan ya tuna Ajay ne zai yi dropping dinsa a airport
din, dai dai nan wayarsa dake aljihunsa ya fara vibrate, ya ciro wayar yana
duba me kiransa, ganin Ajay ne yayi picking ya kai kunne, after few seconds ya
katse wayar yana kallonta yace "Mu je to ki rakani, our car is somewhere
around here" Ta gyada masa kai suka fara tafiya gun motar, tun daga nisa
ta hango Ajay dake tsaye jikin mota yana jiran Jay, wayarsa ce a hannunsa yana
dannawa with his full attention, Khaleesat ta Ιan kalli Jay, sai a sannan taga
kaman da suke yi da Ajay, Jay ya kalleta speaking slowly yace "Ko zaki
koma daga nan?" A hankali tace "Ohk, Allah ya kiyaye hanya" Yace
"Ameen" Kamar ance Ajay ya daga kai yayi ido huda da su, Jay ya dauke
idonsa yana kallon Khaleesat yace "I will drop you a WhatsApp message idan
na isa, just go" Ta gyada masa kai, ta Ιan kalli Ajay suka kara hada ido,
sai kuma ta kasa tafiya, murya can kasa tace "Ko dai kawai mu je gun motar
sai in gaishesa tunda ya gan mu?" Ba tare da Jay ya kalleta ba yace
"Ohk" a haka suka karasa gun motar, Khaleesat na kallon Ajay da ya ci
gaba da danna wayarsa tace "Ina yini?" Jay ya zaga ya bude front seat
ya shiga ya kulle motar, ita dai tana tsaye don Ajay bai amsa gaisuwan ta ba
bai kuma kalli inda take ba, after some seconds ya daga kai ya kalleta yace
"Idan kika gaishe da Jay ya wadatar, ni ki dena gaisheni" Tana
kallonsa tace "Saboda me" Ajiye wayarsa yayi yana kallonta da mamaki,
can yace "Na fara wasa da ke ne?" Still tana kallonsa tace "To
ai kar watarana kace bana gaishe ka shiyasa nake gaishe ka yanxu, once again
thank you for the new apartment" Yace "I will slap you idan baki fita
a gabana ba" Tayi masa wani kallo ta juya ta fara tafiya, ya bi ta da
kallon mamaki, ta sake juyawa suka hada ido don kallonta kawai yake, ta zumbura
baki tayi wucewarta, sai da ya dena hangota ya bude driver seat ya shiga ya
fara balbale Jay da bala'i yana cewa "Ka ga ka dena hadani da yarinyar nan
Jay, don na lura tun da taje ta san menene aure ta karo wani rashin kunya na
musamman" Dakatar da shi Jay yayi fuska daure yace "Pls bana son
hayaniya Junaid" Tada motar Ajay yayi ya fara driving, after some minutes
ya juya ya kalli Jay yace "What happened? Wa ya bata maka rai?" Jay
na danna wayarsa yace "Never Mind" Ajay bai sake ce masa komai ba ya
ci gaba da driving din da yake. Murmushi Khaleesat tayi ta bude handbag dinta
ta saka wayarta ta mike tace "Ai kuma sai kiyi, naga dai ba dole bane sai
naje wani get together ko?" Safiyyah ta rike Abayan jikinta rai bace tace
"Wallahi dole ne Khaleesat, wai don Allah me yasa kike haka ne? Me yasa
kike da taurin kai haka? Sai yaushe zaki waye ki fara abu irin na mutane
wayayyu? Wallahi na fara gajiya da halin ki, babu wanda ya isa ya baki shawara
ki dauka kike nufi ko me?" Khaleesat tayi dariya tace "Yau nake ganin
ikon Allah, duk saboda nace maki bazan bi ki ba? To naji zan je amma ni ko
minti talatin bazan yi ba a wajen" Safiyyah da fuskarta ke daure har
lokacin tace "Naji, mu tafi gidan naki mu shirya" Khaleesat tace
"Meye da kayan jikina da bazan je da shi ba?" Safiyyah tace "A'a
wallahi a gan ki tun safe da kaya anjima kuma a sake ganinki wajen get together
da shi? Ni ma ga kayana da zan canza cikin jakan laptop dina, bari in mana
order din Uber mu tafi gidan naki" Khaleesat dai ta tabe baki bata ce mata
komai ba, Safiyyah ta gama order din ride din sannan ta mike har sannan tana
rike da Khaleesat, Khaleesat tace "Ikon Allah, to ki sakeni mana ko guduwa
zan yi?" Safiyyah tace "Na san maki?" Dariya kawai Khaleesat
tayi a haka suka tafi inda za su jira Lyft dinsu, wajen karfe hudu suka isa
apartment din Khaleesat, sai da suka yi sallan azahar sannan suka shirya,
Safiyyah har da make up, Khaleesat dai ko powder bata yarda ta shafa ba,
Safiyyah ta kyaleta da baΖin halinta don lallabata take kar ta canza mind
dinta, a haka dai suka bar gidan wajen karfe biyar saura.
[7/8, 9:34 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Tun da suka
iso gidan Coursemate dinsu Clara da aka yi organizing Get together din
Khaleesat ta nemi waje a parlon ta zauna tayi isolating kanta totally daga
cikin mutane don sun tarar har an fara taron ana ta nishadi, yawanci duk turawa
ne sai few Africans da kuma student from other Continent, simple girke girken
turawa da snacks iri iri ne a parlon sai drinks with so many chocolate, sannan
ga tea with cookies, tuni Safiyyah ta shige cikin Coursemate dinsu ana ta shagali
dama duk ta saba da su unlike Khaleesat da ba kowa take hulda da shi a
department din nasu ba, lokaci lokaci Khaleesat ke kallon Safiyyah don a rayuwa
idan akwai abinda ke saka Safiyyah farin ciki da nishadi bai wuce Chilling da
partying with friends ba, har mamakinta Khaleesat take ko gajiya da harkar
party bata yi, tana son life sosai ba kadan ba, bata ki a gayyaceta wani partyn
gobe ba tsaf zata je, Khaleesat dai wayarta kawai take dannawa tana yi tana
kallon agogo don dama tace minti talatin kawai zata yi, sai ga Safiyyah ta nufo
tana washe hakora da glass din wine ta mika mata tace "Haba Khaleesat ki
tashi ki shiga cikin jama'a mana ayi shagali da ke, sai tambayata suke if you
are okay, ke in baki kunyata mutum ba baki ji dadi ba, ni dai ga glass din wine
na kawo maki" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "A'a ni bazan sha
ba, thank you" Safiyyah ta hade rai tace "Ke Non-alcoholic wine ne
fa, sai kace ban san abinda nake ba, it's non alcoholic" Khaleesat tace
"Na sani, kawai bana sha ne, kema kinsan drink ba wani damuna yayi
ba" Safiyyah ta kyabe baki ta juya ta koma cikin yan ajin su, ba iya
Coursemate dinsu kadai bane a wajen har da few masters student, wa enda suke
Pursuing masters dinsu a course din da su Khaleesat ke Degree din sa, tun da Khaleesat
suka shigo parlon dama ta lura da wani mutumi dake zaune shi ma yayi isolating
kan sa a gefe yanda ita ma tayi, shi ma kuma wayarsa kawai yake ta dannawa da
glass din wine a hannunsa, tana ganinsa ta gane bahaushe ne amma ta fuske a
inda take a zaune, lokaci lokaci yake kallon direction dinta, kawai mistakenly
ta daga kai suka hada ido da shi, ta maida kanta kasa tana danna wayarta with
full concentration, mikewa yayi ya nufota har sannan yana rike da glass din
wine, tana ganin alamar ya nufo inda take taki dago kanta har ya karaso
wajenta, jingina yayi da bango daga gefen inda take zaune yana kallonta yace
"Good evening" Ba tare da ta dago kanta ba a takaice tace
"Ohk" Ya mayar da wayarsa aljihunsa yana kallonta yace "African?"
Ta girgiza masa kai kawai, yace "But Safiyyah is your friend" Sai a
sannan ta daga kai ta kallesa a karon farko babu yabo babu fallasa tace
"So???" Ya Ιan bude ido yana murmushi yace "Safiyyah that i know
is from Africa, Nigeria precisely" A takaice tace "I don't know what
you are talking about pls, because Safiyyah is my frnd doesn't mean we have to
be from the same continent" Fuska daure ta kare maganar ta, calmly yace
"Not at all, you sound provoked, sorry if u feel offended..." Mayar
da wayarta tayi jaka with the intention of leaving the house gaba daya, sai ga
Safiyyah ta nufo su da plate din cake a hannunta zata kawo mata, tana ganinsa
tace "Ohh Aymaan, i didn't even notice you here, ashe ka zo" Ya gyada
mata kai yace "Yeah, good evening Safiyyah" Tana murmushi tace
"Evening Aymaan" Yace "Ya sunan kawar taki ne?" Safiyyah na
murmushi tace "Ohh, her name is Khaleesat" Ya gyada kai yace "Ta
ce min daga wani Continent din daban take not Africa, i saw she was sitted
alone, shi ne na zo nan so we while away time together, but she took it
personal, i think i wilk take my leave" Yana fadin haka yayi murmushi ya
fara tafiya zuwa inda yake zaune, Safiyyah ta kalli Khaleesat tayi kasa da
murya tace "Na shiga uku, yanxu kenan baza ki taΙa canzawa ba Khaleesat, ke baza ki koyi siyasa ba a
rayuwar nan? Meye ne don ya zo ya sameki? kin zata cewa zai yi yana son ki? Ai
shi kuma Aymaan ba haka yake ba, Masters dinsa ma yake shi yasa baza ki wani
san sa a department din ba, he is the son of the Deputy governor of a state in
Nigeria" Khaleesat ta wani kalleta tace "So??" Safiyyah tace
"Maida wukar, nan da kika gansa ma ba lafiya garesa ba, chronic ciwon
zuciya yake battling with, you think he have time for any relationship aside
friendship? Beside iyayensa ma sun masa aure yana da mata haka da kika gansa,
kawai don ya gan ki zaune shi ne ya zo to keep you company amma ba wani abu ba,
kuma da aka yi inviting dinsa get together din ma yace bazai zo ba, nasan Nora
ce ta takurasa ya xo, ita wai son sa take kamar zata yi yaya, ko me zai yi da
baturiya, ke kuma ki sha kurumin ki ba cewa zai yi yana son ki ba he is
Married..." Khaleesat dai bata ce komai ba, can ta kalli Aymaan din taga
ya koma inda yake zaune yana danna wayarsa kawai sai taji wani iri a can kasar
zuciyarta, sai take jin kamar bata kyauta ba yanda tayi shunning dinsa kamar
jiransa take dama, Safiyyah ta tabe baki ta mika mata plate din cake din
hannunta tace "Ni dai ga shi, kuma ki taso za mu yi hotuna, in shi ma din
baza kiyi ba sai mu ji...." Khaleesat ta amshi plate din ta ajiye duk da
ba ci zata yi ba amma kawai jaraban Safiyyah ne bata so yasa ta amsa. Haka nan
Khaleesat babu yanda ta iya ta tashi za su yi hotuna da Coursemate dinta,
yawancin su duk shakkar interacting da ita suke don ko murmushinta baka gani a
department balle dariyarta, bata kuma kula kowa sai dai gaisuwa shi ma sama
sama saboda Safiyyah, tunda Safiyyah kowa nata ne, yawanci duk hotunan da suka
yi Ayman yana ciki shi ma kuma sai da aka je aka gayyatosa ya zo ayi pictures,
daga karshe ya mika ma wani abokinsa wayarsa yace yayi masu hoto da Safiyyah,
ita dai Khaleesat na tsaye gefe kamar bata ma san abinda suke yi ba nan kuwa
slightest opportunity take nema da zata fita daga parlon ba tare da Safiyyah ta
lura ba, abokin yayi masu hoto da Safiyyah tana washe hakora as usual, sosai
kuma hoton yayi kyau, sai kuma ya mika ma Safiyyah wayar tasa yace "To yi
min da kawarki, Khaleesat ko?" Safiyyah na murmushi ta amshi wayarsa da
yake mika mata tace "Eh, her name is Khaleesat..." Komawa yayi kusa
da Khaleesat ya tsaya yana kallonta yace "Let take a snap Khaleesat"
Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, amma da ba don abinda Safiyyah ta gaya mata
a kansa ba da babu abinda zai sa ta tsaya wani yin hoto da shi, fuskarta babu
yabo babu fallasa take kallon Safiyyah da ta saita waya zata masu hoton,
Safiyyah ta wani kankance ido tana kallonta alamar ta saki ranta mana, kamar
irin uwarta din nan haka tayi mitsi mitsi da ido tana kallonta, Khaleesat bata
sanda tayi dariya ba don ba karamin dariya Safiyyah ta bata ba, Safiyyah tayi using
wannan Opportunity din tayi snapping dinsu pictures kusan biyar tare da Aymaan,
shi dai Aymaan kallon Khaleesat yake don bai zata tana dariya ba, abokansa biyu
ma suka yi joining hoton, da wasu turawa, a haka Safiyyah ta gama masu pictures
din ta mika masa wayarsa, yayi murmushi yace "Thank you Safiyyah"
Safiyyah tace "Bari in sa maka numberna ka min sending pictures din
pls" Ya bata wayar yace "Alright" Take away Safiyyah tayi ma
Khaleesat ganin bata ci komai ba a wajen, Khaleesat dake ta kula da agogo tana
ganin karfe bakwai da kusan rabi tayi ordering ride da zai maidata gida ba tare
da Safiyyah ta sani ba, ride din na isowa cikin dubara tayi sneaking ta bar
parlon without letting Safiyyah notice her. Wajen karfe goman dare sai bayan
Khaleesat ta gama duk abinda zata yi tayi shirin kwanciya sannan ta bi miss
calls din Safiyyah da tayi mata kusan hudu tun daxu, Safiyyah na dagawa tace
"Sannu kin kyauta Khaleesat, da kince min zaki tafi ai ba hanaki zan yi
ba, sai ma kilan in samar maki motar da zai maida ke gida, amma ba sai kin
sulale kin tafi ba" Khaleesat tace "Uhm ke din ce baza ki hana ni
ba?" Safiyyah tace "Ke kika jiyo kuma, da na sani ma da ban taho da
ke ba wallahi, ba wani amfanin da zuwan ki yayi, Coursemate dinmu sai cewa suke
me yasa kike haka baki da walwala ko kina battling da wani ciwo ne da yake sa
kike haka" Khaleesat tayi dariya tace "To kun gama party din ko har
yanzu kuna can kuna yi? Ko dai till dawn ne party din? Ya Mustapha bai yi ta
kiran ki ba?" Safiyyah tace "Ban sani ba" Daga haka ta katse
wayarta, Khaleesat tayi murmushi ta bude WhatsApp dinta, sosai gabanta ya fadi
ganin message din Housemate dinta ya shigo, dama saboda shi ta kunna data ta
shiga WhatsApp din nata, sai taga hoto ya turo mata kawai, ta kalli time din da
ya turo ta ga tun karfe tara ya mata sending image din kuma iya shi kawai babu
wani sako, ta shiga DM dinsa sai taga yana ma online, ta fara downloading
hoton, lokaci daya ta mike zaune daga kwancen da take tana kallon hoton da ya
turo mata babu ko kiftawa, ta cire duvet din jikinta tsabar yanda ta girgiza da
wannan hoto, hoton da Safiyyah tayi mata da Aymaan ne tana dariya, ta kasa
daina kallon hoton with confusion, to a ina yaga hoton nan? How did he get it?
Wani kyau na musamman tayi a hoton saboda dariyar da take, shi kuma Aymaan dake
gefenta ya kafeta da ido shi ma yana murmushi a hoton, ajiye wayar tayi don
gaba daya kanta ya gama kullewa, to ko dai Safiyyah ta dora a status ne tunda
yana da numberta, ko kuma yasan Aymaan ne? da sauri ta dau wayar tana kokarin
duba status din Safiyyah, ai kuwa ta ga ita ce ta dora kusan duk pictures din
da suka yi a get together din, hotunan da ta dora sun kusa 15 a status, sauka
tayi daga WhatsApp din tayi dialing number Safiyyah yana fara ring ta daga,
Khaleesat tace "Safiyyah me yasa zaki dora har da nawa hotunan a status
din ki?" Safiyyah tace "Ban gane ba? Is there anything wrong don na
dora hoton ki a status dina?" Khaleesat da taji ranta yayi mugun bace tace
"Then why will u upload har da wanda muka yi da wannan mutumin nan?"
Safiyyah tace "To fa" Sai kuma da sauri tace "Ohhh sorry wallahi
na mance the situation on ground bari in je in goge Khaleesat, wallahi na
manta" Khaleesat tace "Yanxu gashi Housemate dina ne ya min fowarding
hoton wanda muka yi da mutumin fa" Cikin sanyin murya Safiyyah tace
"Ni wallahi mancewa ma nake kina iddah ne, bari in je in goge yanxu, to
amma dai ghost viewer ne Housemate din nan naki don ni bana ganin ya bude
status dina kuma yana budewa wani lkcn... Let me go and delete them" Katse
wayar Safiyyah tayi, Khaleesat taji kamar tayi kuka saboda bakin ciki da
takaici, ita irin dariyar da tayi a hoton ne ma yafi kona mata rai, nan kuma ba
a san Safiyyah ce ta bata dariya ba, can dai ta sake shiga WhatsApp ta shiga Dm
din Housemate dinta taga yana online har sannan, ignoring hoton da ya turo mata
tayi ta tura masa Good evening, hope ka isa lafiya? Har bayan minti goma bata
ga yayi reply ba kuma yana online din, gaba daya duk jikinta yayi sanyi, after
another 5 mins tayi deciding ta kirasa ta WhatsApp call, har call din ya katse
bai daga ba, kuma tana ganinsa online, kashe datan ta tayi, ta ajiye wayar a
sanyaye ta kwanta, amma ta kasa bacci har kusan karfe sha biyun dare, daga
karshe ta mike zaune ta kara jawo wayar ta kunna data ta hau WhatsApp, har
sannan taga bai mata reply ba kuma yayi uploading status din abun kwallo 30
minutes ago, taji hawaye ya cika idonta ta kashe datan ta ajiye wayar ta koma
ta kwanta tana goge idonta. Washegari wajen karfe goma na safe Khaleesat ta
gama shiryawa zata tafi school, duk da sai karfe biyu suke da lectures ranan
amma taji gwara kawai ta tafi schl din, har sannan she is moody tun da ta bude
WhatsApp dinta bayan da tayi sallan asuba taga har sannan bai mata reply ba
bata sake hawa WhatsApp din ba, tana zaune parlor tana jiran Lyft din da tayi
ordering, ta bude handbag dinta ta ciro wayarta ta kunna data ta shiga
WhatsApp, bayan messages dinta sun gama shigowa still dai bai mata reply ba, ta
bude voice note din Aunty Farida bayan ta saurari abinda ta ce mata, ta mayar
mata da reply, WhatsApp call Aunty Farida tayi mata don tana online, ta daga
bayan ta kara gaisheta daga daya bangaren Aunty Farida tace "To Khaleesat
in Jawwad din shi baya nan ki hada mu da Junaid mana" A hankali Khaleesat
tace "To ai ba wai muna haduwa bane a schl Aunty, inda nake daban inda
suke daban" Aunty Farida tace "Ya naji muryarki haka, lafiya dai
ko?" Khaleesat ta Ιan yi yake tace "Ba komai, kawai dai akwai sanyi
ne kuma gashi zan fita school yanxu" Aunty Farida tace "Kuma rigunan
sanyi biyu kawai ki tafi da shi ko?" A hankali Khaleesat tace "Eh,
amma Ya Jawwad ya bani wani" Aunty Farida tace "Toh shikenan, ko
Junaid din ne ki hada mu da shi, kinga ba dadi har yanzu bamu ce masu komai ba
ba ayi masu godiya ba, kuma duk laifin ki ne, tun yaushe muke ta bin ki,
Babanki ma sai da yayi magana daxu" Khaleesat tace "To zan hada ku
idan mun hadu Aunty, Umma fa?" Aunty Farida tace "Umma tana
lafiya" Khaleesat tace "To shikenan, zan tafi schl yanxu sai anjima"
Aunty Farida tayi mata sallama, sannan Khaleesat tayi ending call din, status
taga Housemate dinta yayi uploading tun karfe tara na safe, ta bude status din,
kallon hoton dake status din ta dinga yi babu ko kiftawa don lkci daya ta
ganeta, ta kalli caption din da yayi mata hoton, next photo din ma na yarinyar ne
tare da shi kuma da alamar new pictures ne ba old ones ba, da har zata fita
daga WhatsApp din sai kuma tayi screenshot din hotonsa da Hadeeyah, ta shiga DM
dinsa taga yana ma online, sending masa hoton tayi sannan a kasa ta rubuta ur
sick Cousin? After few minutes taga ya mata reply yace Halysaah... Bata mayar
masa da reply ba, ta tafi zata duba last picture din status din nasa taga ya
goge duk hotunan daga status din nasa, ajiye wayar tayi for almost 5 mins, can
ta dauka zata fita daga WhatsApp din sai ga WhatsApp call dinsa ya shigo, har
ya katse bata daga ba, daga karshe ta kashe data dinta ta saka wayar cikin
handbag dinta. Har Khaleesat ta isa school bata san ta isa ba don gaba daya
hankalinta baya jikinta, ta sauka daga Lyft din tana tafiya a hankali kamar
mara lafiya, all through lectures dinsu na ranan kawai gata nan gata nan ne a
hall, ko sanin abinda ake koyarwa ma bata yi ba, ta rasa menene ya tsaya mata a
rai haka, bayan sun fito lectures din Safiyyah na kallonta tace "Wai har
yanzu fushi kike akan hoton da na dora Khaleesat? Kin san fa bazan yi hakan da
gan gan ba, don Allah kiyi hakuri, wallahi yayi escaping mind dina ne situation
din dake at hand, ko fada Housemate din naki yayi maki ne?" Khaleesat ta
girgiza kai trying to sound ok tace "A'a ni fa kaina ne ke min ciwo amma
ba wani abu ba, gida ma nake son zan tafi yanxu" Shiru Safiyyah tayi
trying to be sure of wanda take hangowa nesa da inda suke zaune, can ta kalli
Khaleesat....
[7/9, 9:08 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Sau daya
Khaleesat ta kallesa ta dauke kai bayan tayi convincing kanta ba wajensu yake
tahowa ba, Safiyyah tayi kasa da murya tace "Ni ban ma taΙa ganinsa a
school din nan ba sai yau, gwara Housemate dinki shi dama ya saba zuwa ya same
mu a nan sanda muke Exam, he is coming toward us fa" Ita dai Khaleesat
bata ce komai ba amma can kasan ranta ita ma tayi mugun mamakin ganinsa a
department dinsu, how did he even know spot din da suke zama da Safiyyah, sai
kawai tayi assuming hanya ce ta biyo da shi ta nan din, har ya iso inda suke
zaune Khaleesat bata daga kai ba but she is surprise, Safiyyah na kallonsa tana
murmushi tace "Good afternoon Ya Junaid" Ba tare da ya kalleta ba
yana kallon different direction yace "Evening, can you excuse us... I want
to have a word with ur Coursemate" Safiyyah dai bata fasa kallonsa ba tana
gyada kai tace "Sure, why not...." Sai kuma ta dau jakanta ta mike
tana kallon Khaleesat tace "Zan je wajensu Nora, if you are looking for me
ina can..." Khaleesat ta gyada mata kai kawai, daga haka Safiyyah ta bar
wajen, ita dai Khaleesat mamaki ma yasa ta kasa kallon Ajay dake tsaye kanta,
he wants to have a word with her? To me zai ce mata da zai biyota har
department din su, duk da under same faculty suke amma ko da wasa bata taΙa
haduwa da shi a school ba in ba few days ago ba da suka shigo da Jay, ta kalli
wayar da yake mika mata fuskarsa babu yabo babu fallasa, she was surprise, why
is he giving her his phone? bata amshi wayar ba ta daga kai ta kallesa a karo
na farko, ganin yanda ya daure fuska ya sa ta mika hannu ta amshi wayar tana
kallon screen din, sosai gabanta ya fadi ganin hoton da suka yi da Aymaan jiya
a get together, ta dinga kallon hoton babu ko kiftawa, gashi ba hoto daya ba ba
kuma biyu ba, can ta kalli a ina yaga hoton sai taga a Instagram ne, bata san
sanda ta gyara zama ba zuciyarta na bugawa sosai, Instagram kuma? Me ya kai
hoton Instagram? ta shiga uku, ita da ko a screen din wayarta bata taΙa saka
hotonta ba balle aje ga WhatsApp ko kuma facebook uwa uba Instagram, gaba daya
hankalinta yayi mugun tashi ta kasa cewa komai, da kyar ta daga kai ta kallesa
ta ga wani irin kallo yake mata, ta sauke idonta gabanta na ci gaba da faduwa
ta kasa cewa komai, fixge wayarsa yayi daga hannunta yace "So you came
back fully prepared to party in Baltimore Right? You came back to mingle with
jobless guys following them to party up and down, Har kin ma mance abinda ya
same ki, but wait... Baki taΙa zuwa islamiyya bane ko kuma kin je kin yi
skipping classes? Ko kuma bayan mijin da kika ce a kyaleki kina son zama da shi
ya sake ki baki zauna kin tambayi makusantan ki what next ba? Kawai saboda kina
jin kanki on a different level yanxu shi yasa kika kama hanya kika tafi cikin
kattin banza masu shaye shaye da sunan get together, har ki tsaya gefen wannan
crook guy din ayi maku hoto kina dariya" Khaleesat ta kasa daurewa ta
fashe da kukan da tun safe take son yi bata samu kwakkwaran reason din yin sa
ba, shiru yayi yana kallonta irin kallon mamakin nan, after a minute ya zauna
inda Safiyyah ta tashi amma bai ce mata komai ba, ita kuma bata fasa kukan da
take ba kamar an aiko ta, tayi me isarta don kanta ta hakura ta fara goge
idonta tana sauke ajiyar zuciya, sai a sannan ya kalleta yace "Ohk i
understand, kin dawo America ne kiyi abinda ranki yake so ba kuma kya bukatar
wani yace zai yi questioning din ki ko kuma yayi correcting din ki" Wani
sabon kukan ta fara yi kamar ana tunzurata, ya mike trying to control himself
yace "Get up" ganin taki tashi ya hade rai yace "Baza ki tashi
ba?" A hankali ta mike tana ci gaba da goge hawayen dake zuba idonta tana
shesshekan kuka, babu yabo babu fallasa yace "Mu je" Bata masa musu
ba ta fara bin sa har sannan tana goge hawayen idonta, after almost 10 minutes
walk suka iso inda yayi parking motarsa, yana bude motar ta daga kai ta kallesa
a hankali tace "Ni ban ce ma Safiyyah zan tafi ba" Ya mata wani irin
kallo yace "Baza ki ce mata ba, get in the car" Bata ce komai ba ta
zaga ta bude gaban motar ta shiga, bata taΙa shiga motarsa a America ba sai
ranan, har suka isa Apartment dinta babu abinda yace mata, bayan yayi parking
without looking at her yace "Leave my car" Sauke idonta tayi, ta bude
motar a hankali ta sauka ta kulle masa tana kallonsa tace "Don Allah tunda
ka san sa kayi masa magana ya goge hotona a Instagram" Ya jefa mata wani
kallo yace "Zan gaura maki mari, ni na hada ku nayi maku hoton da zan ce
masa ya goge?" Daga haka yayi Reverse yayi zoom off daga Neighborhood din,
wasu sabbin hawaye suka cika idonta ta juya tana tafiya a hankali ta nufi kofar
apartment dinta ta bude ta shiga, zaunawa tayi a parlor ta fara tunanin to ko
shi ma Housemate dinta ya ga hoton ne a Instagram bayan status din Safiyyah,
bata taΙa jin haushin Safiyyah irin yau ba, Allah kadai yasan mutane nawa ne
suka ga hoton nan daga jiya zuwa yau, ta goge idonta ta bude handbag dinta ta
ciro wayarta ta fara kiran Safiyyah, yana fara ring Safiyyah ta daga tace
"Ya tafi ne in fito?" Trying to be calm Khaleesat tace "Kin ga
Safiyyah kije kiyi ma wannan mutumin magana ya cire hotona a Instagram, who
does that? Ta yaya daga hoto zai je yayi posting a Instagram kamar mun san juna
from anywhere da shi? Meye hadina da shi da zai min haka? Har wani dogon magana
muka yi da shi da har zai dau hotona tare da shi yayi posting a Instagram
dinsa?" Muryarta na rawa ta kare maganar, Safiyyah tace "Innalillahi,
Instagram yayi posting hotunan? Kinsan ni ba wani damuwa da IG nayi ba, kuma fa
Aymaan ban taΙa ganin yayi posting mace a Instagram ba, sai gashi yayi posting
na ki, amma how did you know his Handle da har kika ga yayi posting din
ku?" A fusace Khaleesat tace "Ina ruwana da wani handle dinsa, kawai
daga haduwa ko maganar minti daya ban yi da mutum ba ya kama hotona yayi
posting duk duniya su gani, is he even okay? Ko ba shi da hankali ne? To
wallahi ki je kiyi masa magana ya goge min hotona" Safiyyah tace "Ni
ma dai nayi mamaki gaskiya, wallahi ban taΙa ganin yayi posting mace ba sai
gashi yayi posting din ki, kar dai shi yasa Ajay ya zo wajen ki yau? Don
definitely za su iya sanin juna kilan ma suna following juna, kinsan akwai
association na Nigeria student a makarantar mu dole ma za su sun san juna, Ιan
Deputy governor ne fa Aymaan, he is also popular on IG" Takaici ya sa
Khaleesat ta katse kiran ta jefar da wayarta kan kujera, wani mugun haushin
Aymaan da Safiyyah ta dinga ji a ranta, da tana da numbersa babu abinda zai
hanata kiransa ta gaggaya masa magana, ko an gaya masa ita irin wa ennan matan
ne da har zai yi posting din ta duniya su gani, Abdul ne ya fado mata, nan da
nan jikinta yayi mugun sanyi, don babu uban da ya kai sa zama active a
Instagram gashi da uban followers, wa ma ya sani ko yasan Aymaan din, sosai
taji hankalinta ya tashi ta jinginar da kanta da kujera wasu hawayen na zuba
idonta, bata taΙa jin Safiyyah bata kyauta mata irin yau ba, da kyar ta mike ta
dau jakarta da waya ta wuce sama. Meemah ce ta shigo dakin Momy tana mika mata
wayar hannunta hankali tashe tace "Momy kin gane wacece wannan kuwa?"
Momy ta ajiye bowl din farfesun hannunta ta amshi wayar tana kallon screen din,
can ta kalli Meemah tace "Wannan ba er matsiyatan can bace? Khaleesat take
ko wa" Meemah ta zauna gefen gado har sannan fuskarta dauke da tashin
hankali tace "Ita ce Momy, ita da Aymaan" Momy ta ajiye wayar ta dau
bowl din farfesunta ta ci gaba da ci tace "Waye kuma Aymaan?" Meemah
tace "Aymaan din kuma kika manta yau Momy, Muhammad Aymaan Ιan mataimakin
gwamna fa" Momy ta kalleta tace "Wai tsohon saurayin ki
Muhammad?" Meemah ta hade rai tace "Tsohon saurayi fa kika ce Momy, Aymaan
din ne tsohon saurayina?" Momy tace "To in ban ce maki tsohon
saurayin ki ba ya zan ce, yaron da ba Ιaga kiranki yake ba yanxu, yaushe rabon
ki da shi? kin ga kuwa ai sai in ce tsohon saurayin ki Meemah, dama ai a titin
Instagram din ku ka hadu da shi, ba sai da na dinga hada maki da rokon Allah ba
kika samu sassaucin son sa da kika dora ma kanki, dama su biyu zuciyarki ta
makale ma da shi da wani Ιan sarki yake ko wa shi ma kullum sai kin isheni da
zancensa bana ma tunanin kina da numbersa, duk samarin ki a Instagram din ku ke
haduwa kuma a can ku ke rabuwa, ni na taΙa ganin wannan wahala" cike da
damuwa Meemah tace "Wallahi mace ce ta shiga tsakaninmu da Aymaan Momy,
amma ai ya so ni kamar ran sa, ki tuna har fa kano ya sha zuwa wajena"
Momy ta tabe baki tace "Amma ai ba gidan ubanki yake zuwa ba sai dai yace
ku hadu gidan cin abinci ko wani wajen, bai taΙa biyo ki yaga gidan ku ba,
shekara kusan takwas ana abu daya in da gaske son naki yake me ya hanasa fitowa
har yau, ni dama tun da Malam Tasi'u yace min bazai fa aureki ba na hakura da
kashe kudina a iska, amma ai na kashe kudi kan wannan Aymaan din, bayan Malam
Tasi'u ma akwai wani malamin da yace min mu hakura ba auren ki zai yi ba bata
maki lokaci kawai yake, kuma uwarsa ma a tsaye take kyam" Meemah tace
"Momy duk ba wannan ba, a ina yasan yarinyar nan har suka yi hoto tare?
Kinsan shi ma a Amurka yake kuma makarantar su daya amma ya gama degree dinsa
tuntuni in dai ba masters ya koma yi ba, kuma wnn hoton daga gani a Amurka aka
yi sa" Momy tace "Atoh kika san ko tsohon hoto ne, dama ai kin ce
iskanci ta dinga yi a Amurkan don haka ba abun mamaki bane don kin ga hotonsu
tare, yanxu kuwa ai sai dai tayi karuwancinta da yan Mariri" Meemah dai ta
kasa cewa komai amma kana ganinta kasan hankalinta ya tashi sosai, Momy ta
kalleta tace "Ai kun ma fi shekara biyu baku yi waya da shi ba ko?"
Meemah ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Yanxun ma ina ganin hoton na
kirasa bai daga ba, amma ni abinda ya bani mamaki duk yanda yake da mace fa
baya posting dinta ko a WhatsApp balle har Instagram" Momy tace "Ζan
wani gari ne ma?" Meemah tace "Gusau" Momy tace "Abdul ya
san sa ne?" Meemah tace "Oho, shi wannan ana sanin cikinsa ne, ni ban
san ko sun san juna ba, kuma ai Abdul bai san ni da Aymaan ba tunda kinga ba
wai ya taΙa zuwa gidanmu bane Aymaan din, sai dai su san juna a Instagram amma
ba a sarari ba" Meemah ta kara Zooming din hoton da kyau tana kallon
tsadadden Abayan jikin Khaleesat ga wani kallo da Aymaan ya kafeta da shi, ita
kuwa tana dariya with her beautiful set of teeth, Meemah ta fice daga wajen
hoton ta sake dialing number Aymaan amma har ya katse bai daga ba, mikewa tayi
ta nufi kofa, Momy ta tabe baki tace "To ke banda abunki me zai yi da er
talakawa aka ce maki, in kin bibiya hoton ya dade, yanxu kuwa ina taga hanyar
zuwa Amurka, ai uwarsa ma ta fi mu Ζin talakawa bari ki ji in gaya maki, a
zamanin yanxu dai ko wani me kudi ya waye baya yarda ya hada zuri'a da talaka,
yanxu kwarya tabi kwarya kawai, haka abun yake" Ita dai Meemah ta fice daga
dakin tana sake dialing number Aymaan with confusion. Tana zaune usual spot din
da suke zama a school tana jiran Safiyyah da taje kai ma wani coursemate dinsu
laptop dinsa, tun daxu take zaune wajen tana danna wayar hannunta with full
concentration, lkci daya ta dakata da abinda take yi a wayarta jin wani kamshin
turaren da ta sani ya doki hancinta, waige waigen wajen ta fara yi suna hada
ido bata san sanda ta saki wayar hannunta ba zuciyarta na bugawa tana kallonsa
babu ko kiftawa, he was the least person she is expecting to see in her life,
lkci daya taji wani courage ya zo mata ta dau wayarta fuskarta a daure ta mike
da nufin barin wajen, ya fixgo gyalen jikinta yana kallonta da kyau yana
murmushi yace "You think i will let you just like that Khaleesat? Har kin
samu masu ci gaba da sponsoring din ki an dawo dake America, ga shi har ana
hoto dake ana dora ki a Instagram, u snapped a picture together with Aymaan har
yayi posting din ki duniya ta gani, ko wani Ιan iskan gaye kin sani a Amurka
and they are all ready to go through any mile for you, to ki sani na maida
aurenmu da ke, you are still my wife...." A firgice Khaleesat ta farka
daga baccin da take ta mike zaune jikinta na rawa, tun da uwarta ta haifeta
bata taΙa mummunan mafarki irin wannan ba, ta sauka daga saman gadonta har
sannan jikinta na rawa, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba tana
ganin abun kamar ba mafarki bane gaske ne, ba karamin tashin hankali ta shiga
ba ta fara karanto duk addu'an da ya zo bakinta tana kuka, duk yanda ta so ta
samu nutsuwa hakan ya gagare ta, she was really shock, da kyar ta daure ta
dauko wayarta ta kunna data hannunta na rawa, kawai taji she wants to speak
with her Housemate, tana bude data taga Aunty Farida ta ajiye mata sako, ta
shiga DM dinta taga hoton da suka yi da Aymaan ta turo mata tana tambayar
wanene shi, kuma me yasa zata yi hoto da shi.... Tashin hankalin Khaleesat ya
ninku akan wanda take ciki da, she was so confuse and shock, gashi jikinta sai
rawa yake, a ina kuma Aunty Farida taga hoton nan, ta shiga uku, shikenan kilan
Abdul ma zai gani kenan mafarkinta ya tabbata ya zamto gaskiya? Ta fashe da
matsanancin kuka tana jin zuciyarta kamar zai fito tsabar tashin hankali, ko
reply din Aunty Farida bata yi ba ta fita daga WhatsApp din ta fara dialing
number Housemate dinta da sauri, ta kirasa har sau biyu bai daga ba, rasa yanda
zata yi tayi tana kuka, can kawai ta fara dialing number Safiyyah har sannan
jikinta bai dena rawa ba, yana fara ring Safiyyah tayi picking, cikin rawan
murya Khaleesat tace "Safiyyah baki ce ma mutumin nan ya goge hotona a
Instagram ba dama??" Safiyyah tace "A'a na masa message ta WhatsApp
he is not online fa, na kuma kirasa bai yi picking ba, kuka kike yi ko me? Haba
Khaleesat sai kace warce tayi wani mugun abu? Get together fa kawai muka je aka
yi hoto ba wai club ba, kuma shigar ki ta mutunci kika yi fa, Aymaan kuma left
a reasonable distance tsakanin ku balle ace ko manne maki yayi a jiki"
Khaleesat taki bata amsa tace "Kina da number Ya Junaid pls?" Safiyyah
tace "Eh kamar ta numbersa Jawwad yayi min fowarding receipt din 10M da
aka tura ma su Maman Abdul" Da sauri Khaleesat tace "Don Allah ki
turo min yanxun nan" Safiyyah tace "Ohk bari in duba, amma ni dai
wallahi ban ga abun damuwa ba don kawai Aymaan ya daura hoton ki a Instagram,
sanannen Celebrity ne shi fa, kawai don bama Instagram ne shi yasa baza mu sani
ba, kuma kawai don dai kina Iddah ne da ace kin gama so what?? Ai kin isa ne
yasa ya dora ki" Khaleesat ta katse wayarta don bata son ta gaya ma Safiyyah
magana she is just controlling her self all this while, ba a dau lokaci ba sai
ga Safiyyah tayi mata fowarding number Ajay, Khaleesat tayi dialing number da
sauri, gaba daya zafi ta dinga ji duk da uban sanyin da ake har da snow, don
Ajay na dropping dinta daxu babu dadewa aka fara snow shi ne har ta kwanta
bacci tayi wnn mummunan mafarkin, sai da ta kira sau biyu sannan Ajay ya daga,
ta kasa daurewa ta fashe masa da kuka muryarta na rawa tace "Don girman
Allah idan kasan mutumin nan ka taimaka min kayi masa magana ya cire hotona a
Instagram page dinsa, wallahi ni ban san sa ba pls talk to him" Tana kuka
sosai ta kare maganar, Ajay dake sauraronta kamar bazai ce komai ba sai kuma
yace "Ni na ajiye ki a gefensa aka yi maku hoton da zan masa magana ya
cire?" Ta kara fashe masa da matsanancin kuka tace "Na shiga uku, don
Allah ni dai ka taimake ni wallahi ban san waye shi ba" Ajay ya ki cewa
komai daga karshe ma ya katse wayarsa, ta mike ta koma kan gado ta dinga rera
kuka, ita babban tashin hankalinta ace Abdul ya ga hoton nan, tsaf attention
dinsa zai iya dawowa kanta kuma ba da good Intention zai dawo ba, tana
rayuwarta low key gashi Safiyyah ta ja mata fitina, ji tayi kamar zazzabi na
neman rufeta tsabar tashin hankali, ta kwanta saman gado tana sauke ajiyar
zuciya hawaye wasu na bin wasu a fuskarta, ta kusa awa daya a haka daga karshe
tayi karfin halin tashi ta tafi bandaki zata yi alwala don yin sallan magrib,
ko da ta fito ta kasa yin sallan ta kwanta ta lulluba da duvet saboda rawan
sanyin da take, ba karamin kidimar da ita wnn mafarkin da tayi yayi ba, after
like 15 mins ta ji ana danna bell din gidan, ta mike zaune da sauri har lkcn
tana rawan sanyi, gaba daya a tsorace take kamar mara gaskiya, after some
minutes aka sake ringing bell din gidan, ta fara tunanin ko dai Housemate dinta
ne ya dawo, tunanin hakan yasa ta daure ta sauka daga saman gadon ta fita daga
dakin, har a sannan kuma snow bai dena zuba ba.....
[7/10, 8:55 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat na
isa kofar parlon ta bude a hankali tana kallon wanda ke tsaye bakin kofar,
sauke idonta tayi ta koma gefe ta tsaya, babu yabo babu fallasa yana kallonta
yace "Me yasa kika kira wayana kina kuka kamar ni na aike ki? Why didn't
you call Jay kiyi masa kukan sai ni?" Ta daga jajayen idanuwanta ta
kallesa, ji tayi wasu hawayen sun cika idonta ta sunkuyar da kanta, after some
seconds ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, da kyar tace "Ni dai in
ka san sa kayi masa magana he should delete my pictures off his phone plss,
Aunty Farida ma fa sai da ta turo min hoton, ni kuma wallahi ban san sa
ba" Yace "Baki san sa ba kika tsaya gefensa kina washe hakora ku ka
yi hoto?" Ta fashe masa da kuka ta juya da sauri ta bar wajen ta koma
cikin parlor ta kwanta kan kujera tana rera kuka, tsabar mamaki da haushi yasa
ya kasa cewa komai ya bi ta da kallo, ya tsani unnecessary kukan mace a
rayuwarsa, ya kuma lura bata da aiki sai kukan banza tun da ya santa a haka ya
santa da kuka, how is Jay coping interacting with her this way, shi ba shi da
irin wannan patient din, parlon ya shiga ya kulle kofar, ya saka hannunsa a
aljihun Jacket din jikinsa cause he is already cold kawai Ιan tsayuwar da yayi
a waje, ya karasa har inda ta kwanta take kukan ya hade rai yace "Don't
you dare call my line again kina kuka, ni ban aikeki ki bi silly friend dinki
zuwa party har ayi maku hoto da wani namiji ba, stop stressing me with ur troubles
pls, i am not Jay" Ta dakatar da kukan da take ta wani kallesa ta hade rai
tace "Ni ba party muka je ba, get together ne, ka dena cewa party"
Wani kallo yayi mata, ta kauda kanta tana goge idonta, ya kalli Heater din
parlon sai kuma ya tafi ya kunna, ta bi sa da kallo ganin ya nufi window din
parlon ya bude drape din yana kallon snow dake sauka waje sosai, he was just
imagining how he managed to get here in this snowstorm, mikewa tayi a hankali
tayi wucewarta sama, ya juya ya bi ta da kallo. Wajen karfe takwas da rabi
Khaleesat ta fito daga dakinta tana leka downstairs daga corridor din da take
tsaye, taga yana zaune har sannan a parlon ya jinginar da kansa jikin kujera
idonsa a lumshe, ta zata ma ya tafi, after some minutes ta sauko downstairs
tana kallonsa, har sannan bai bude idonsa ba, tana tafiya a hankali ta nufi
window tana duba waje taga it's still snowing outside, dawowa parlor tayi ta
tafi kitchen, after a while ta fito da cup din tea biyu ta tafi har inda yake
zaune ta tsaya tana kallonsa, a hankali tace "Ga shayi" Bude ido
yayi, sai kuma ya gyara zama yace "Did i send you message?" Ta wani
kallesa, sai kuma tace "To ai naga kamar sanyi kake ji tunda gashi ka kasa
tafiya" Ya kalleta yace "Zan juye maki shayin a baki in baki matsa
gabana ba, ba ke kika fito da ni cikin sanyin ba? Kin zata idan Jay yana nan
zan saurare ki ne? Ai shine wahalalle dama" Tace "Ni ban fito da kai
cikin sanyi ba, tunda ba cewa nayi ka zo ba ai, kawai kiranka nayi nace kace
mutumin nan ya cire hotona a Instagram, amma ban ce ka zo ba" Kallonta ya
dinga yi, at this point kamar he is lost of words, ta juya ta koma kitchen ta
ajiye cup daya ta fito ta wuce sama tana rike da cup din nata shayin, still ya
bi ta da kallo babu ko kiftawa, Khaleesat na gama shan tea din ta kwanta ta
rufa da duvet ta lumshe ido tana addu'an Allah ya sa kar ta kara mafarkin da
zai firgitata kamar daxu, kamar warce ta tuna abu ta bude idonta a hankali, ta
jawo wayarta tana dubawa ko Housemate dinta ya biyo kiranta bata sani ba, amma
sai taga bai biyo kiran ba, har ta ajiye wayar sai kuma ta sake dauka a hankali
ta kunna data dinta tayi login WhatsApp, tun call din da yayi mata da safe bata
daga ba bai kara mata magana ta WhatsApp din ba, and he uploaded a status not
long ago, sauke idonta tayi ta kashe datan ta ajiye wayar ta gyara kwanciyarta,
nan da nan mood dinta ya canza, duk yanda ta so tayi bacci kasawa tayi, sai
juye juye take har kusan karfe sha dayan dare, mikewa zaune tayi daga karshe ta
cire duvet din jikinta ta dau Jacket dinta ta saka sannan ta bude kofar parlon
a hankali ta fita, tsaye tayi a corridor din sama tana kallon Ajay dake kwance
kan 3 seater idonsa a lumshe don wutan parlon a kunne yake, ta fi minti biyu
tsaye tana kallonsa, sai kuma ta juya ta koma dakinta ta dau one out of the new
duvet Jay got for her, ta cire farin duvet din daga pack dinsa sannan ta fito
daga dakinta ta sauka downstairs, tana tafiya a hankali ta isa har inda yake
kwance, gida biyu ta linke soft duvet din ta rufa masa a jiki, ba wai hannunta
ya taΙa sa bane but she could feel he is running temperature, tana rufa masa
Duvet din ya cire daga jikinsa ya wurgar ba tare da ya bude ido ba yace
"Gerrout Jay...." Sai kuma ya fara kokarin juyawa a kan kujeran sai
ga shi a kasan carpet ya fadi timm, rufe bakinta tayi da sauri, ita kanta bata
san meyasa dariya ya taho mata ba don da har jikinta yayi sanyi after noticing
that he is running temperature, amma wannan reaction din nasa yayi mugun bata
dariya, cikin magagi yake cewa "Bana son haka Jawwad, why are you
stressing me, gerrout pls, i think i caught a cold, can you help increase the
room heater before getting out" Sai kuma ya bude ido a hankali yana dafe
kansa da yayi masa nauyi cause bai ji Jawwad na responding ba, ita dai kallonsa
kawai take da mamaki, he look so shock ganinta, ya fara bin parlon da kallo,
sai kuma ya kalleta ya hade rai yace "Kee, fita ki ban waje" Bata san
sanda tayi dariya ba tace "Ai to bani na fadar da kai kasa ba, ni kawai
bargo na kawo maka, and you heavily fell down on the Carpet" Ya kara daure
fuska yace "Get out of my sight, am i a joke to you?" Ta wani juya
kai, sai kuma ta nufi stairs tana waigansa har ta haura sama ta shiga dakinta,
sai a sannan ta fara dariya tana mamaki shi kuma haka yake, har bayan minti
talatin Khaleesat bata yi bacci ba tana dai zaune dakinta, after a while ta
mike a hankali ta kara fita daga dakin nata tana leka downstairs, bata gansa
kwance a parlon ba, hakan yasa ta fara saukowa downstairs, ta kalli duvet din
da ya ajiye saman kujera da makullin gidan, sai kuma ta kalli bakin kofa ta
karasa can ta murda kofar taji a kulle, window ta tafi tana leka Garage taga
babu motarsa, ta dawo parlon ta dau makullin gidan tana kallo taga ya cire guda
daya a ciki, she felt somehow ganin bashi da lafiya kuma still ya bar gidan a
haka gashi snow din raguwa kawai yayi, ta fi minti biyu a tsaye after a while
ta dau duvet din zata koma sama taji vibration din wayarsa, dube dube ta fara
yi amma bata ga wayar kan kujera ba, daga karshe sai karkashin kujeran taga
wayar, kilan sanda ya fadi daga kan kujeran shi ne wayar ya shige karkashin
kujeran, screen din wayar ta dinga kallo ganin Jay ne ke kiransa, tayi
silencing wayar ta wuce sama tana rike da wayar da duvet, sau uku Jay na kiran
wayar, ita dai ta ajiye wayar gaban madubi tayi kwanciyarta. Washegari ta idar
da sallan asuba bayan ta gama azkar dinta zata kwanta wayar Ajay ya fara
vibrate gaban madubinta, ta dinga kallon wayar sai kuma ta karasa can tana duba
screen din taga Jay ne still ke kiransa, ta juya ta koma saman gado tayi
kwanciyarta, wajen karfe tara na safe ta gama shiri zata tafi school, tana
tsaye gaban mirror din dakin tana kokarin daure gashinta sai ga Jay ya sake
kiran wayar Ajay, ta dinga kallon wayar babu ko kiftawa sai kuma ta daga wayar
ta sa handsfree bata ce komai ba, daga daya bangaren Jay yace "Why were
you not picking ur calls Bruh, hope baka fita jiya ba cause naji anyi snow
sosai, how are you doing?" Khaleesat dake sauraronsa ta sauke idonta tace
"Good morning, he forgot his phone" Shiru Jay yayi daga daya bangaren
for almost 10 seconds, can yace "Halysaah..." Tace "Good
morning" Yace "Morning, where did he forget his phone?" Tace
"In my apartment" Shiru Jay yayi bai ce komai ba, after some seconds
a hankali yace "Ohk then" Daga haka ya katse wayar, Khaleesat ta
dinga kallon screen din, sai kuma ta ajiye wayar tana kallonsa, sai bayan kusan
minti daya ta iya ci gaba da gyara gashinta. Bayan Khaleesat ta gama abinda
take ta saka wayar Ajay a jakarta zata tafi school da shi incase yaje zai amsa
a department dinta, bata nuna ma Safiyyah komai ba da suka hadu a school duk da
har sannan she is still very much angry at her, Safiyyah na kallonta tace
"Yanxu dai sai hankalin ki ya kwanta don naje na duba na ga Aymaan ya cire
hoton naku a account dinsa, ko wa yayi masa magana oho, ni kuma gashi bai min
reply din WhatsApp message dina har yanzu ba" Khaleesat tace "Toh in
ba dai he is irresponsible ba ta yaya zai dau hotona bai san ni ba yayi posting
a account dinsa? Bai ma dau matarsa da muhimmanci ba in dai haka ne, who does
that?" Safiyyah tace "Atoh, nima dai haka naji aka ce yana da mata
amma ban sani ba ban kuma tabbatar ba" Khaleesat ta kalleta baki bude,
Safiyyah tace "Wallahi kuwa, haka naji ana cewa, kuma wai yana da ciwon
zuciya, ni dai bai min kama da me ciwon zuciya ba kuma ban ma yarda da wnn
labari ba, kinsan yan mata na jin haushinsa saboda sai wanda ya ga dama yake
kulawa shi yasa aka masa wannan sharrin, amma ki kalli mutum lafiyayye kamar sa
a wani ce ciwon zuciya, gashi da son zuwa club" Khaleesat ta ma rasa
abinda zata ce ma Safiyyah, kawai ta kauda kai don lamarin Sophie ya fara bata
tsoro, the way she is saying it kamar bakinta da bakinsa suka yi magana ya gaya
mata yana da ciwon zuciya kuma yana da mata, Safiyyah tace "Ni dai tashi
mu je mu ci abinci yunwa nake ji, kilan ma haushin an sa shi ya cire hoton ne
ya sa yayi banza da ni ta WhatsApp kuma na kirasa yaki picking, dama an masa
shaidan girman kai and he is way too pompous of himself, bazai wuce Housemate
dinki ya san sa ba shine yayi masa magana ya sauke hoton, dama ni fa sam gayen
bai min ba ga wani jijji da kai da yake wai shi Ιan gidan Deputy sai kace Ιan
vice president, deputy governors da ba a ma san da zamansu ba a Nigeria, gani
yake yafi kowa a haka fa, kina kallon idonsa kinsan bazai rasa shan drugs
ba" Khaleesat tace "Amma dai yanxu idan Abdul yaga hoton nan me kike
tunani Safiyyah?" Safiyyah ta mike tace "Waye kuma Abdul? Pls mu je
mu ga abinda za mu siya mu ci yunwa nake ji wallahi" Har Khaleesat ta bar
school ranan bata ga Ajay ya zo amsar wayarsa ba, hakan kuma yasa taji a ranta
he is sick. Mamaki abun ya ba Khaleesat ganin har ta dawo school Housemate
dinta bai kirata ba ko kuma yayi mata magana ta WhatsApp, wayar Ajay ma bai
sake kira ba, sai dad dinsa da ta ga ya kira wayar har sau biyu, da daddare
taji zuciyarta ya kasa daurewa kawai tayi ma Housemate din nata magana via
WhatsApp, ta gaishesa sannan ta tambayesa ya jikin cousin dinsa, after almost
15 minutes yayi mata reply da Alhamdulillah, daga nan kuma bai sake cewa komai
ba, she was taken aback, haka nan ta ajiye wayarta kawai ta kwanta tana jin
wani iri a zuciyarta. Bayan kwana biyu Khaleesat da Safiyyah suna zaune a wajen
department dinsu, Khaleesat na yi mata explaining wani course dinsu da tace
bata gane ba, Murya can kasa taji Safiyyah na cewa "Ji gantalallen Aymaan
din can, he is coming toward us, kar ki dago kanki" Khaleesat bata dago
kai ba, ta ci gaba da bayanin da take ma Safiyyah, har ya iso inda suke zaune,
calmly yace "Good evening Safiyyah and Khaleesat" Safiyyah ta washe
baki tace "Hi Aymaan, how are you doing ya kwana biyu?" Yace
"Lafiya lau, ya karatu?" Safiyyah na washe hakora tace
"Alhamdulillah, tun ranan bamu sake haduwa ba sai yau" Yana kallon
Khaleesat yace "Good evening Khaleesat" Ba tare da Khaleesat ta
kallesa ba fuskarta babu fara'a tace "Ohk" Ya kalli Safiyyah yace
"Naga kamar kawar taki a fusace take" Safiyyah tayi dariya da
iyakarsa fuskarta tace "Ai bata ji dadin abinda kayi mata bane, duk da na
fahimtar da ita ba da wata manufa kayi hakan ba, kuma ta fahimta, ita tsoronta
ma kar matarka ta ga hoton" Yana kallon Safiyyah yace "Ke kika min
auren?" Safiyyah tayi dariya tace "To ai kaga za a sa maku ido kuma
shi yasa ta damu" Yace "Ohk in nasan haka ne ai da bazan sauke hoton
ba, don wani guy that is full of himself i think saurayinta ne ya sameni yayi
min magana about it, yasan ni, na sansa a kasar nan amma ba mu taΙa ma juna
magana ba, had i know ban cire hoton ba in ga abinda zai yi" Safiyyah ta
kwantar da murya tace "Kaga Aymaan Khaleesat fa matar aure ce babu wani
boye boye...." Aymaan yayi wani murmushi without letting Safiyyah to go
further yace "Ban yarda ba, shi wanda ya min magana in cire hoton zan nuna
masa ba aurenta yayi ba ai...." Khaleesat ta daga kai fuska daure tace
"Pls delete my pictures off your phone Mr man, don ban san ka ba, ban hada
komai da kai ba ban kuma ga dalilin da yasa zaka yi posting dina ba, no sane
person will do such, plss take my pictures off ur phone matar aure ce ni"
Tana kai wa nan ta tura ma Safiyyah Laptop dinta ta mike ta figi handbag dinta
ta bar wajen ko waigawa bata yi ba, Aymaan ya bi ta da kallo yana Ιan murmushi,
Safiyyah tayi tagumi don har ta gaji da ce ma Khaleesat ta koyi siyasa da iya
zaman duniya, da faram faram ya kamata ta samu ta rabu lafiya da Aymaan amma ga
abinda tayi, Aymaan ya gyada kai yace "We shall see then" Safiyyah ta
kallesa tace "Kasan tana da aljanu ne fa Aymaan kuma abun har ya taΙa
brain dinta, da sauki ma basu tashi a nan ba, don wallahi duka take kuma in ta
fara famfala gudu da kyar ake kamota, shi sa kullum zaka ganta babu fara'a ni
kadai nake iya zama da ita wallahi, wanda kuma yasa ka cire hoton ba saurayinta
bane believe me..." Aymaan yayi wani murmushi yace "Nima su gareni,
kin ga dai dai kenan" Daga haka ya juya ya bar wajen, Safiyyah ta kara
rafka wani tagumi. Khaleesat na isa gida wajen karfe biyar zata bude kofa taji
kofar a bude, ta kalli parking space taga babu mota a nan, tura kofar tayi a
hankali ta shiga parlon, zaune ta gansa ya kunna TV yana kallon kwallo, ko
juyowa bai yi ba har ta karasa cikin parlon tana kallonsa, ya mike without
looking at her yace "Bani wayata" Tace "Ya jikin?" Sai a
sannan ya kalleta yace "Nace maki bani da lafiya ne?" Tace "A'a
kawai na gane idan baka da lafiya surutu that is not comprehensible kake yi a
bacci....." Tana murmushi ta kare maganar tana kallonsa.
[7/11, 8:44 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat ta
bi sa da kallon gefen ido ganin ya nufi kofa, sai kuma ta juya tana kallonsa,
fita ta ga zai yi daga parlon, da sauri tace "Ka jira in dauko maka wayar
yana sama" Tuni ya fice daga parlon without looking at her, tafi minti
biyu tsaye tana kallon kofar da mamaki, does this min yaji haushin abinda ta
fada kenan? To ai ita ba da wata manufa ta fadi hakan ba, tana ta tsaye parlorn
with surprise, can dai ta taΙe baki ta karasa ta zauna kan kujera ta bude handbag
dinta ta ciro wayarta tana duba pdf da aka mata sending a school na wani course
dinsu, after a while ta mike ta tafi sama don yin sallah ta canza kayan jikinta
sannan ta dawo downstairs ta girka abinda zata ci, Khaleesat bata sauko
downstairs din ba sai kusan karfe biyar da rabi na yamma don tana sallah bacci
ya dauketa saboda sanyin garin, tana gyara hulan kanta bayan ta sauko kasa zata
shiga kitchen taji anyi knocking kofar parlor at the same time aka murda kofar,
juyawa tayi da sauri after realizing ashe a bude ta bar kofar bayan Ajay ya
fita daxu, kallonsa ta dinga yi babu ko kiftawa kuma ko kwakkwaran motsi bata
yi a inda take tsaye tsabar yanda ta tsorata, ya kullo kofar yana tsaye daga
nan bakin kofar yana kallonta yana murmushi with calm yace "Good evening
Khaleesat" Khaleesat ta sauke idonta gabanta na wani mugun faduwa, her
common sense didn't give her the go Ahead to be rude or anything of such to
him, can dai ta kallesa with calm in her voice tace "Why will you badge
into my House just like this?" Ya Ιan yi murmushi yana sauke hulan jacket
din jikinsa yace "That was because u left the door open..." Cikin
kwantar da murya tace "But that doesn't warrant you to badge in" Ya
daga hannu sama yace "My bad, sorry about that beautiful Khaleesat"
Zaunawa tayi kan kujera bata sake cewa komai ba faduwar gabanta ya tsananta,
yana bin apartment din da kallo keenly yace "Such a nice apartment,
Communal living kike, ko ke kadai ce a duk apartment din nan?" Ba tare da
ta kallesa ba calmly tace "Co-living" Ya karaso cikin parlon tayi
masa kallon gefen ido gabanta na faduwa sosai, zaunawa yayi gefenta yana
kallonta yace "Sorry i came unannounced, banyi tunanin kina da fahimta
haka ba, na zo gidanki ba tare da izinin ki ba and u are not mad at me, i even
badged in but u are still calm...." Khaleesat tayi murmushin karfin hali
tace "It's fine... How did you get to know my apartment?" Yana gyara
zama yana wani murmushi yace "Gane apartment din ki har wani wahala zai
min a Baltimore ni da na damu dake?" Khaleesat tayi shiru bata ce komai
ba, tasan babu tantama bayan ta fito school ne daxu ta hau Lyft shi ne ya
biyota without her knowledge, bin parlon ya dinga yi da kallo yace "But
seriously i really love this ur apartment, it's big and fine, ko ke da Safiyyah
ku ke sharing?" Ta girgiza masa kai, can kasan zuciyarta kuwa tunanin next
move din da zata dauka take yi, yana kallon sauran gashinta da basu gama shiga
hulan kanta ba tunda tana cikin saka hulan ya shigo parlon, ya kai hannu zai taΙa
gashin da mamaki yace "Are all this ur hair??" Da sauri ta matsa gefe
tace "Noo, i won't welcome that" Ya buda ido yace "I am sorry
Dear, you've got a beautiful soft black hair" Ita dai bata ce komai ba,
Yana kallonta speaking calmly yace "Tell me more about ur self pls
Khaleesat" Ta kirki murmushi tace "Kaga yanxu fita zanyi zan tafi
supermarket in yi shopping, and it's almost late" Yayi er dariya yana
kallonta da kyau yace "Duk salon korana ne wannan dear?" Tace
"Not at all, assuming zan kore ka ai kana shigowa zance ka fitar min a gida,
kawai zan je in yi siyayya ne yanxu don gobe ba da wuri zan dawo gida daga schl
ba" A hankali yace "Alright, dress up sai mu je shopping din"
Tayi karfin halin mikewa tsaye sai kuma ta kallesa tace "But plss respect
my privacy, ka jira ni in sauko" Yayi wani murmushi yace "Baki da
matsala my dear" Bata sake cewa komai ba ta nufi stairs har sannan gabanta
na faduwa sosai, ga wani takaici da take ji a ranta don wata er doguwar riga ne
kawai a jikinta that is not even cloth enough, a haka dai ta haura sama yana
bin ta da kallo, tana shiga dakinta ta kulle dakin da makulli hawaye ya cika
idonta ta tafi ta dau wayarta da sauri, number Housemate dinta tayi dialing
bayan few seconds ya fara ring amma har ya katse bai daga ba, zaunawa tayi
gefen gado tana goge hawayen dake sauka idonta tana tunanin yanda zata yi, bata
sake dialing number Housemate dinta ba instead tayi dialing number Ajay, a
cikin daya daga jakunkunan da take fita school taji vibration din wayar tasa,
ajiye wayarta tayi ta daura kanta kan pillow ta fashe da kukan takaici, after
some minutes ta mike tana goge hawayen da yaki tsaya mata, ta dau handbag din
da wayar Ajay ke ciki, ta ciro wayar tana dubawa taga ya ma kusa shut down,
cikin jakar da ta dawo da shi daga school ta saka wayar sannan ta dau nata
wayar tayi ordering Uber, ta saka wayarta ma cikin jakar, ta canza kayan
jikinta sannan ta saka hijab ta fito daga dakin ta kulle ta sauka downstairs,
yana tsaye parlorn hannunsa rike da can drink da ya shiga kitchen dinta ya
dauko a fridge yana sha, ya bi ta da kallo yace "The weather is cold
outside dear, ina jacket din ki?" Without looking at him tace "I will
be fine" Yace "Ohk then, mu tafi?" Tace "A'a zan Ιan yi abu
a kitchen in fito tukunna" Yace "Ohk, take ur time" Kitchen
dinta ta nufa ya bi ta da kallo har ta shiga ciki, kulle kofar tayi ta tsaya a
kitchen din tana jiran Uber dinta at the same time zuciyarta na tafarfasa tana
goge hawayen takaicin dake sauka idonta, after a while ta fito daga kitchen din
without looking at him tace "Na gama" Mikewa yayi yana gyara jacket
dinsa yace "You look cute dear, ko dai in baki jacket dina, its freaking
cold outside fa" Tace "Kar ka damu" Daga haka ta nufi kofa ta
fita, shi ma ya fito sannan ta kulle kofar da makulli, motarsa da yayi parking
ya nufa yana nuna mata yace "There is my car" Ta kallesa tace
"Ga Uber da nayi order can" Ya juya ya kalleta yace "Why? Cancel
the order, da mota na zo ae" Tace "I can't cancel it" Bata sake
sauraronsa ba ta nufi uber din without looking at him, ya bi ta da kallo with astonishment,
dariya yayi yace "Whatt? Like seriously.... this little girl played
me" jingina yayi da motarsa ya rufe baki yana murmushi yana kallonta yana
gyada kai har ta shiga uber din, wato shi zata yi ma wayo, gaskiya tana da
wayo, gyada kai yayi ya shiga motarsa ya tada sannan ya bi bayan uber din da ta
shiga.... Khaleesat na lura da yanda yake bin uber din da ta shiga a baya, sai
kusan karfe bakwai ta isa gidan, ta bude Uber din ta sauka ta nufi cikin gidan
da sauri, sai gashi shima yayi parking, ko kashe motar bai yi ba ya sauka ya bi
ta yana kiranta, amma tuni ta shiga gidan zuciyarta na bugawa, hakan yasa ya
tsaya ya bi ta da kallo har sannan yana murmushi yana gyada kai, sai da ya kare
ma babban gidan kallo sannan ya juya ya koma motarsa, Khaleesat tana hardewa ta
isa har kofar shiga gidan tana jin gabanta na faduwa sosai don gani take kamar
ya biyota har cikin gidan tunda ba juyawa tayi ba balle ta gani, bubbuga babban
kofar parlon ta dinga yi hawaye cike idonta, amma shiru ba a bude ba, sai a sannan
ta lura da madannin kararrawan gidan, ta danna da sauri hannunta na rawa, sau
uku tana danna bell din kafin aka bude kofar after almost 5 minutes, ta fashe
masa da matsanancin kuka tana kallonsa, Da mamaki yake kallonta daga sama har
kasa yace "Me ya faru?" Taki ce masa komai tana rusa masa kuka, bai
san sanda yayi mata tsawa ba sounding so apprehensive yace "Can't u speak
out? Tell me what is it? Me ya faru?" Cikin kuka tace "He followed me
to my apartment" Ya bude ido sosai yace "Who?" Tace "Wannan
mutumin nan" Da mamaki yake kallonta babu ko kiftawa yace "Ur
apartment?" Ta gyada masa kai hawaye na zuba idonta tace "Ya biyoni
har nan gidan ma a cikin motarsa" Yace "Nan gidan??" Tace
"Eh, yana waje ban san ko ya shigo ba ma...." Ya cire takalman
kafarsa ya saka wasu dake bakin kofar sannan ya fito daga parlon ta bi sa da
kallo tana goge hawayen idonta ta jingina da bango, Ajay na fita can waje ya
dinga bin Neighborhood din nasu da kallo don babu alamar ko mota daya a waje,
sannan kuma babu kowa cause the weather is sooo cold kuma gari yayi duhu, ya
juya ya koma cikin gida, har ya iso entrance din shiga parlon kallonsa take, ya
hade rai yace "Shiga ciki" A hankali ta juya ta shiga cikin parlon ta
cire takalmanta ta karasa ciki ta zauna kan kujera har sannan gabanta bai dena
faduwa ba, shi dai Ajay na tsaye bakin kofar parlon gaba daya mamakin Aymaan ya
gama cikasa, har ya fara tunanin irin matakin da zai dauka kansa, lkci lkci
Khaleesat take kallonsa, after some minutes ya karaso cikin parlon yana
kallonta fuska daure yace "Ta yaya ya san apartment din ki har ya
je?" Muryarta na rawa tace "Nima wallahi ban sani ba" Ya wani
hade rai yace "Kee, kar ki kuskura ki min kuka a nan, don't stress me with
your silly cry...." Ita dai bata ce komai ba, yace "Da ya je
apartment din naki sai aka yi yaya?" A hankali tace "Ni na manta ban
kulle kofar ba da ka tafi daxu, kawai da yayi knocking sau daya shine ya bude
kofar ya shigo da yaji sa a bude, and i told him i am going out for shopping
yace to zai kai ni, bayan mun fito sai naki shiga motarsa dama nayi ordering
Uber, shi ne ya biyo bayan motar da na shiga har muka zo gidan nan" Ajay
yace "Da ya je apartment din naki ur common sense bai gaya maki ki kira
masa cops ba immediately, ni ranan saboda rashin kunya ba cewa kika yi zaki
kira min 911 ba??" A hankali tace "To ba wayar yana sama ba, kuma ai
mantawa nayi da cops, i was confuse" Jinginar da kanta tayi jikin kujera
bata sake cewa komai ba cause she is already tired, a hankali ta jawo handbag
dinta ta bude ta ciro wayarsa ta mika masa tana kallonsa, taga direction din da
yake kallo daban yana nazari, ajiye wayar tayi a gefenta, after a while ya juya
yana kallonta a takaice yace "Go upstairs" Ta Ιan bude ido tana
kallonsa tace "Upstairs?" Ya mata wani kallo yace "Gidan za ki
koma yaje ya same ki a can?" A hankali tace "A'a i tot za mu koma
gidan tare" Yace "Sai ki zo ki daukeni mu tafi" Daga haka ya
nufi stairs, ta wani bi sa da kallo, shi dai komai masifa, sai kuma ta zumburo
baki ta kauda kai, har bayan awa daya Khaleesat bata ga ya sauko downstairs ba,
tayi ta zama a parlon har ta gaji gashi bata yi sallah ba, bata ji alamar da
workers ko daya a gidan ba cause everywhere is so silent, jinginar da kanta
tayi da kujera don ta gaji ga wani ciwo da kanta yake mata and she is very
hungry, ta lumshe ido tana zaune a haka bacci ya dauketa, cikin bacci taji
muryarsa ta bude ido da sauri ta gyara zama, yana kallonta yace "Oh baki
tafi saman ba?" Ta hade rai tace "To ni nasan inda zan je a
saman?" Yace "Baki san inda Jay ya saba ajiye ki ba?" Kin cewa
komai tayi, after some seconds ta daga kai ta kallesa taga hararanta yake, ta
mike ta dau handbag dinta ta bar masa wayarsa a kan kujeran, juyawa yayi ya
koma sama ta bi bayansa tana tafiya a hankali, tsaye ta gansa a corridor fuskarsa
babu yabo babu fallasa, sau daya ta kallesa har zata tafi dakin da ta taba zama
a gidan sai kuma ta saci kallonsa tace "Ina zan je?" Yace "Ban
sani ba" Juyawa tayi ta dau hanyar bangarensa, ya bude baki da mamaki yana
kallonta yace "Kee" kasa daurewa tayi har sai da tayi dariya don ba
karamin dariya abun ya bata ba, ta dake tace "To ba kace inda Housemate
dina ya ajiyeni ba, ae can zan je" Shi tsabar mamaki ma rasa abinda zai ce
mata yayi, can yace "To tafi ki ga ikon Allah" Ta wani kallesa ta
juya ta nufi dakin da ta zauna sanda take exam, tana shiga dakin ta kulle
kofar, the room was neat amma kana gani kasan an dade ba a zauna a ciki ba,
sosai dakin yayi sanyi kamar kankara, tayi dusting gefen gadon sannan ta zauna
tana takurewa waje daya, bayan wani Ιan lokaci ta mike da sauri bayan ta tuna
bata yi sallah ba, ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito, Heater din dakin
ta kunna amma yaki yayi function, a haka dai ta tada sallah bayan ta idar tana
zaune saman darduman taji knocking a kofar dakin, tana ta kallon kofar sai kuma
ta mike ta tafi ta bude kofar tana kallonsa, a takaice yace "The workers
in the house are yet to resume, you can go to the kitchen and sort ur self out,
this is the only help i can render" Daga haka ya juya ya bar bakin kofar
ta bi sa da kallo, sai kuma ta kulle kofar ta koma ta zauna ta takure waje daya
don sanyi take ji sosai gashi bata zo da Jacket ba, duk da yunwan da take ji ta
gwammace ta hakura don bazata iya zuwa kitchen ba, har ta kagu gari ya waye a
san yanda za ayi da Aymaan ta koma gidanta, amma duk da haka ita dai ta tsorata
da wannan apartment din ita kadai a cikinsa, mikewa tayi ta kwanta saman gadon
bayan ta kakkabe, ta lulluba da second of the bedsheet don biyu ne a kai amma
duk da haka sanyi ta dinga ji kamar bata rufa ba, a haka bacci ya dauketa,
wajen karfe goma Ajay yayi knocking kofar dakin, ta bude idonta a hankali don
restlessly take baccin saboda sanyi, still dai bata juya ba, ya shiga cikin
dakin, ya nufi gun room heater din shi ma ya kunna yaga bai yi ba, ya fi minti
daya tsaye dakin, sai kuma ya juya ya fita, dakin Jay ya nufa ya bude ya shiga
ya dauko white duvet dinsa, sannan ya fito ya koma dakin da Khaleesat take, sai
da ya fara duba tagogin dakin to be sure they are locked, sannan ya rufa mata
duvet ya juya ya fita ya kullo kofar, kamshin turaren Jay ya cikata gaba daya,
nan da nan ta nemi baccin da take yi ta rasa, and she felt so warm, a hankali
ta jawo wayarta tana kallon call logs dinta don har sannan Jay bai biyo kiran
da tayi masa ba a apartment dinta, ta kunna data dinta ta duba WhatsApp taga
nan ma bai ajiye mata message ba, and she even saw him online, sauke idonta
tayi, nan da nan taji hawaye na taruwa idonta ta fita daga WhatsApp din ta
shiga contact dinta ta goge numbersa da tayi saving daga wayarta, sannan ta
ajiye wayar ta rufe har kanta da duvet din tana kuka a hankali, wajen karfe sha
daya saura ta zamo kasa a hankali ta dalilin sharp pain da take ji a abdomen
dinta, tana durkushe for almost 10 mins daga karshe ta mike da kyar ta shiga
bandaki, sosai gabanta ya fadi ganin period dinta ne, ta kasa fitowa daga
bandakin, at last dai ta jawo kafa ta fito tana tafiya a hankali, to yanxu ya
za ta yi, ta kalli white bedsheet da duvet din Jay dake saman gadon, ba wai ta
fara flow sosai bane amma tasan dai hakan zai iya faruwa ko zuwa anjima, a
hankali ta durkusa kasan dakin, bata ma damu da sanyin da take ji ba, ta jawo
wayarta tana tunanin yanda zata yi, ko dai tayi order din Uber zuwa apartment
din nata, amma dai tsoron komawa gidan kuma take, tana jin alamar saukan period
din ta mike a hankali, duk jikinta a sanyaye ta nufi kofa ta bude ta fita, ta
dade tsaye corridor kamar mara gaskiya daga karshe dai tayi gathering courage
ta karasa har bangaren Ajay, tsaye tayi jikin kofarsa kamar tana tausayin kofar
tayi knocking gently, Ajay dake danna wayarsa ya juya yana kallon kofar, ta
sake knocking a hankali, ya mike zaune ya jingina da gadonsa ya ajiye wayarsa
ya rungume hannu yana kallon kofar, idan yace bai gaji da yarinyar nan ba yayi
ma Allah karya, daukar wayarsa yayi, yayi dialing number Jay fuska daure, after
some seconds Jay ya daga, Ajay yace "Wai yaushe ma kace zaka dawo
ne?" Jay yace "Gobe zan tafi Nigeria" Ajay yace "Na gaji da
wannan brat din da ka bar ni da ita a kasar nan, you know i have anger issues,
I can't tolerate her anymore wallahi..." Jay dake ta sauraronsa yace
"To ka iya ajiyar ribbon for more than 2 months, me ribbon din ce baza ka
iya ajiyewa under your watch ba?" Shiru Ajay yayi, Jay yace "Hang up
pls, Mami tana kirana" Ajay ya kalli screen din wayarsa don daga can
bangaren Jay ya katse wayar, ajiye wayar Ajay yayi idonsa akan screen din ko
kiftawa baya yi, after almost a minute yace "What is he talking about,
meye ma ribbon?" A hankali ya dau wayarsa ya shiga Google yayi typing
ribbon.....
[7/13, 1:42 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Ajay ya ajiye
wayar hannunsa bayan ya ga abinda google ya bayyana masa a matsayin ribbon,
kamar zai sake kiran Jay kawai ya fasa ya ja tsaki ya jingina da gadonsa
kalmomin Jay na ci gaba da yi masa yawo a kai, sai kuma ya kalli kofar dakinsa
don har sannan Khaleesat bata dena knocking continuously ba, kamar bazai tashi
ba sai kuma ya tashi daga karshe ya nufi kofar, bude kofar yayi fuska daure
yana kallonta without saying anything, ta Ιan koma baya taki barin su hada ido
a hankali tana wasa da fingers dinta tace "Don Allah dama gida nake son ka
kai ni pls...." Ya dakatar da ita yace "Sai na kai ki? Baki san
hanyar gidan ba, ko ni na kawo ki?" Ta daga kai ta kallesa ta ma rasa
abinda zata ce, ya wani murtuke fuska yace "Ni ba Jay bane da kike ma
iskanci iri iri kina controlling din sa" Juyawa tayi a hankali ta bar
bakin kofar yayi banging kofarsa ya kulle, ya koma ya dau wayarsa har yayi
dialing number Jay sai kuma ya katse kiran ya ja tsaki, Khaleesat na komawa
dakin da take ta dau handbag dinta da wayarta sannan ta fita daga dakin, tana
tafiya a hankali ta sauka downstairs ta nufi kofar fita daga babban parlon sai
taga kofar a kulle, duk kokarin da tayi na ganin ta bude kofar ta kasa budewa
gashi bata ga makulli a jiki ba, ta fi minti biyu tsaye bakin kofar tana jin
tana flow a hankali, ta juya ta kalli hanyar sama, komawa tayi tana tafiya
kamar bata so ta nufi bangarensa, jingina tayi da bango kamar bazata kwankwasa
kofar ba sai kuma dai tayi knocking din kamar tana tausayin kofar, Ajay da har
ya kashe wutan dakinsa ya kalli kofar babu ko kiftawa, sai kuma ya gyara
kwanciyarsa bai motsa daga inda yake kwance ba, Khaleesat ta fi minti biyar
bakin kofar bata kuma fasa knocking din da take ba, cire Duvet din jikinsa yayi
ya jefar gefe sannan ya sauka daga kan gadon fuska daure ya nufi kofar ya bude
yana kallonta at the same time cutting her a serious warning yace "Ki ka
sake knocking din min kofa zan maki walakanci wallahi, why are you such a
nuisance? Pls get out before i loose my temper" Khaleesat dake kallonsa ta
wani hade rai tace "To ta window kake son in fita daga gidan bayan kofar
parlon a kulle yake??" Yace "Ki bi ta roof ma ba window ba" Yana
fadin haka zai kulle kofarsa tayi saurin shiga cikin dakin kamar zata fashe da
kuka ta nufi tsakar dakin ta tsaya tace "Kasan dalilina na cewa zan tafi
gida ne? Kawai kayi ta ma mutum masifa baza ka tsaya kayi considering dinsa ba
ka basa listening ears, kawai haka nan zan taso cikin daren nan in ce zan tafi
gida? Ni ban ce sai kai ka kaini ba ka zo kawai ka bude min kofa inyi
tafiyata...." Magana take amma gaba daya hankalin Ajay na kan dakinsa da
ta shiga kai tsaye, he look shock irin he didn't see that coming, he ignored
her ailment that he understood immediately, ya Ιan yi calming din kansa yana
kallonta yace "Saboda kin ga ranan ya shigo dake nayi persuading kaina ban
yi reacting ba sai kika yi zaton public room ne wannan? An gaya maki ko shi Jay
din yana shigar min daki anyhow? Baki da hankali ne or are you out of ur mind?
Come and get out before u push me to the wall, kuma kar ki kuskura ki taka min
carpet dina da wannan kafafuwan naki, wannan filthy dakin da kika shiga kika
kwanta duk Ζura da datti common sense dinki bai gaya maki ki share dakin ki
goge ba sannan kiyi changing bedsheet, sannan zaki shigo min daΖi ki kakkabe
min duΖ kuran da kika kwasa a jikinki ki cuceni, plss come and get out before i
loose my temper...." A fusace ya kare maganar yana kara bude mata kofa da
kyau ta yanda zata zo ta fita, Khaleesat ta wani taΙe baki tace "To ai sai
kaje ka bude min kofar parlor" Tsawa yayi mata yace "Baza ki fice min
daga daki ba?" Ta fashe da kuka ta nufi kofar tace "To kasan me yasa
zan je gida ne, ko ba saboda urgent issue bane" Yace "Ke kika san
urgent issue din, get out of my room" Ganin he is damn serious don gaba
daya mood dinsa ya canza tun da ta shiga dakin yasa ta fita daga dakin tana
kallonsa tace "Don Allah ka bude min kofar parlon before it's too
late" Banging kofar dakinsa yayi ya kulle, Khaleesat ta dinga kallon kofar,
after a minute sai gashi ya fito, ya saka takalmin da yake yawo da shi a gidan,
ta bi sa da kallo sai kuma ta bi bayansa tana hararansa, downstairs ya sauka ya
tafi ya bude mata kofar parlon, tana tafiya a hankali ta karasa bakin kofar
sannan ta fita tana kallonsa, kulle kofar parlon yayi, Khaleesat taji wani
sanyi don iya Hijab ne jikinta babu rigar sanyi, walking slowly ta fita daga
compound din gidan gaba daya wani mugun sanyi ke shigarta, sai yanxu ta kara
tabbatar da Ajay mugu ne kuma ba shi da conscience, ta ciro wayarta taga ko
zata iya order din ride, tana ta tsaye a Neighborhood din bayan ta duba ride
din, after almost 5 minutes taga hasken fitilar mota daga compound din gidan,
dauke kai tayi har ya fito da motar, taga yayi parking inda take tsaye, ta wani
kallesa, fuska daure yace "Do not waste my time Malama" Ta wani tura
baki ta bude front seat, sai dai kuma tsoro take kar ta zauna ta Ιata masa
motar ta shiga uku, haka dai ta shiga sai bata sake jikinta gaba daya a zaune
ba, tana shiga ya ja motarsa, har suka isa apartment dinta bai ce mata komai
ba, bayan yayi parking murya can ciki tace "Nagode" Daga haka ta
sauka daga motar ba tare da ta kallesa ba ta nufi kofar apartment dinta ta bude
da makulli ta shiga ciki, bata kulle kofar ba ta tsaya jikin window ta Ιan bude
labule kadan tana lekawa taga ko ya tafi, haska inda ta zauna taga yana yi da
wayarsa, ta zaro ido ta juyo hijab dinta da sauri sai taga bata yi stain ba, ta
sake kallonsa taga ya gama haske haskensa ya kashe fitilar wayan, ta ma san
kilan ya gane me yasa tace zata dawo gida, turo baki tayi saboda kunyan da
taji, tana ta tsaye jikin window har bayan minti biyar bata ga yayi Reverse ba,
ita kuma so take taga tafiyarsa sannan ta kulle kofarta da makulli don saboda
zuwan da yayi daxu ya bar mata kofa a bude Aymaan ya fado mata gida kamar
barawo, bude motar taga yayi after almost 10 mins ya fito, sai da taga ya nufo
kofar apartment din sannan ta ruga sama da sauri ta shige dakinta... Ko da
Khaleesat ta shiga bandaki taga hatta kayan jikinta ma bai yi stain ba, pad din
da ta siyo tun daga Nigeria ta dauka a cikin akwatinta, bayan ta gama gyara
jikinta ta fito ta canza kaya sannan ta saka rigar sanyinta ta kwanta, wajen
karfe dayan dare Khaleesat ta farka daga baccin da ya dauketa a firgice duk da
bata dade tana baccin ba ta mike zaune zuciyarta na bugawa, mafarki tayi wai
Aymaan ya zo yana ta bubbuga mata kofa, dama kuma har tayi bacci hankalinta na
kan kofar parlor ko ya tafi ya kulle mata kofar ko a bude ya bar mata oho, a
hankali ta sauka daga kan gadon ta bude dakinta ta fita corridor tana leka
downstairs, kwance ta gansa kan kujera idonsa a lumshe ya maida wutan parlon
zuwa dim light, a hankali ta sauka downstairs din yanda bazata yi making sound
ba, after some seconds ta koma sama ta dauko masa duvet, tana dawowa parlon ya
bude ido, ta koma baya tana kame kame tace "Duvet ne, naga akwai sanyi
sosai yau...." Ya nuna kansa yace "I should use ur duvet? Me? Ke da
kika iya shiga daki duk Ζura da datti comfortably ki kwanta shi ne zaki kawo
min duvet din ki i should use saboda nayi hauka, ai duk macen da zata iya zama
comfortably cikin daki me datti da Ζura without cleaning it, kuma ta dinga yawo
a gida babu takalmi a kafarta to babu kalan kazantar da bazata aikata ba, shi
yasa taku ta zo daya da Jay, bird of the same feathers, ba gwara in kwanta
sanyi ya kasheni ba da inyi amfani da abinda ya fito daga dakin ki, kujeran nan
ma don sabbin furnitures ne yasa na kwanta" Khaleesat ta wani kallesa, sai
kuma ta juya ta koma sama da duvet din, kuma sabo ne ko amfani da shi bata taΙa
ba a ledansa ma ta ciro yanxu, can kasan ranta ta dinga ce ma kanta Allah ya
kara mata, tsaki ta ja bayan ta shiga daki ta kulle kofarta da makulli tayi
kwanciyarta. Washegari wajen karfe bakwai Khaleesat ta fito daga dakinta, bata
gansa a parlon ba, hakan yasa ta sauka downstairs ta tafi kofar ta murda taji a
kulle, ta leka garage taga babu motarsa, tabe baki tayi ta wuce kitchen don
dama da yunwa ta kwana, sai wajen karfe goma ta gama duk abinda take ta bar
gidan zuwa school, har suka gama lectures bata sake fuska ba ranan, tun
Safiyyah na jan ta da magana har ta gaji ta kyaleta, bayan sun fito department
Safiyyah na kallonta tace "Is there any problem Khaleesat? Naga gaba daya
yau mood dinki babu kyau" A takaice Khaleesat tace "Nothing"
Safiyyah tace "Ke dai ki gaya min gaskiya, kila ma haushina kike ji ban
sani ba ma" Sai a sannan Khaleesat ta kalleta tace "Saboda me bazan
ji haushin ki ba Sophie? Kawai kin ja Ιan iska mara kamun kai ya shigo rayuwata
ina zaman zamana, you caused me all this wallahi" Safiyyah tayi shiru, sai
kuma a hankali tace "Wai Aymaan? Wallahi ban san Ιan iska bane Khaleesat,
kin ji na rantse, na zata yana da kamun kai ne yanda nake ganinsa sumi sumi a
department" Khaleesat tace "To jiya wajen karfe shidda na yamma sai
gashi a apartment dina unfortunately na bar kofa a bude kawai ya fado min cikin
parlor kansa tsaye" Bude baki Safiyyah tayi tana kallon Khaleesat ko
kiftawa babu with shock, a hankali tace "Apartment din ki kuma Khaleesat?
Na shiga uku, sai aka yi yaya?" Khaleesat taki bata amsa don takaici,
Safiyyah ta hade rai tace "To kuwa sai nayi masa hauka, uwarsa yaje nema
maki a gida ko an gaya masa kowa shege ne kamar sa?" Kallonsa kawai
Khaleesat take daga nesa har ya nufo inda suke zaune, Safiyyah kuwa ko lura da
shi bata yi ba rai bace take cewa "To ke baki kira masa Cops ba? don Allah
ki gaya min sai aka yi yaya da yaje apartment din naki? Yau ga mahaukaci
kai" Juyawa Safiyyah tayi ganin shadow din mutum a gabansu, yana kallon
Khaleesat da kyau yace "Kara ta kika kai gun wancen garan don ya min me?
Me kike tunanin zai iya min? Muscles dinsa na banza har ni zai nemi ya daka?
Who did he think he is? Me yake takama da shi? Sarautar tasu da bata taka kara
ta karya ba ko me? Sannan naga kamar yana mance a America mu ke not Nigeria, ni
zai nuna ma dabanci bai san course dinsa nayi a Nigeria ba?" Safiyyah ta
mike tace "Look Aymaan, ita fa Khaleesat ba irin wa ennan shegun matan da
kake tunani bane gaskiya, ka bar ganinta sakaka a Amurka, yarinya ce ita me
mutunci da ta san ciwon kanta, kuma harkar duniya bata gabanta wallahi, wannan
get together din ma ni na ja ta don dole taje ba wai ra'ayinta bane shi yasa
throughout ta kebe gefe daya a wurin u saw that too, shi kuma wanda kake kira
da gara fiance dinta ne, ba wai shisshigi yake yi ba, sannan sarautarsu kuwa ta
taka kara ta karya don gidansu a nan Amurka ma ba ko wani shege bane a Nigeria
ke iya mallakan irin wannan babban gidan a wata kasar, kai kuma naga hayan
apartment kake a Amurkan, Sannan iyayen Khaleesat basu fara turata wata kasa
karatu ba sai da suka tabbatar da mijinta a hannu, kuma shi ma a kasar yake, ka
ga ai baza kace masa gara ba" Aymaan na mata wani kallo yace "Ke ki
iya bakin ki kar ki ja ma kanki matsala a rayuwarki, Fiance din banza, a ina
Fiance ya zama miji? ranan daurin aure ma an fasa balle common Engagement, shi
da Engagement din yake takama dama?" Safiyyah tayi wani shewa tana rike
kugu tace "Na ga kamar ba zaman lafiya kake so ba Malam, to wallahi idan baka
fita harkar kawata ba a kasar nan a gaban idon ka zan kira maka 911 in lafta
maka sharrin da babu me fitar da kai sai Allah, kamar yanda ka fada nan ba
Nigeria bane tuni za ayi mana maganinka wallahi, kuma Unguwan da take tsaf za a
bincika surveillance camera a ga sanda ka shiga apartment dinta ta yanda za a
tabbatar ba sharri aka maka ba..." Aymaan ya gyara tsayuwa yana kallonta
da kyau yace "Really?? dama ke mahaukaciya ce ban sani ba?" Safiyyah
tace "Dawanau ce ni karewa, wallahi idan baka yi hankali da mu ba a kasar
nan zaka ga jahilci tsantsa, ai ni da nake ganin ka sumi sumi a makaranta ban
san gogaggen dan iska bane kai sae yanxu, to banda Ιan iska waye zai fada
apartment din mutum kamar gidan ubansa? Ashe dama ciwon ΖwaΖwalwa gare ka ake
yada jita jitar ciwon zuciya gare ka?" Har ya daga hannu zai wanka mata
mari sai kuma ya rike fist dinsa ya cije hakora yana kallonta yana huci, Safiyyah
tayi wani dariya tace "No slap me, try it plss, mare ni mana.... wallahi
rabon ayi deporting dinka back to Nigeria a cikin jirgin ruwa ne ke tunzura ka,
try slapping me ka ga ikon Allah" Yace "Daga ke har kawar taki zan yi
maganin ku wallahi...." Daga haka ya juya kamar zai tashi sama ya bar
wajen, Safiyyah tace "Ni wallahi da aka ce min babanka Deputy ne sai da kunya
ya kamani ranan na rufe fuska, na zata Ιan vice president ne kai irin wannan
jijji da kan da kake ashe common Deputy ne ma da ba a san da ku ba a Nigeria,
kuma in ka fasa maganinmu baka cika namiji ba wallahi, dama ana ganinka an ga
kwararren Ιan shaye shaye Ιan codeine, ban san wani tsautsayin yasa har mu ke
gaisawa da kai ba banda nima dai gantalalliya ce bani da kamun kai"
[7/13, 1:42 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat
tsabar yanda ta zama shock kasa cewa komai tayi a inda take zaune kamar ruwa ya
cinye ta, ta shiga uku ita kam ga kuma wani da yafi Abdul tashanci, Safiyyah na
huci tace "Ta shi mu je, don dai ban san yanda ake yi bane a kasar nan, da
Nigeria ne ai daga nan police station na nufa in je in kai report, to su nan
ban san ko ana haka ba" Ita dai Khaleesat ta kasa tashi don duk jikinta
yayi sanyi kamar an watsa mata kankara, Ganin Khaleesat taki tashi Safiyyah tace
"Ki tashi mu tafi don Allah kar ya sake dawowa" Khaleesat ta kalleta
tace "In tafi ina? Am not going anywhere Safiyyah, haka kawai in koma
apartment dina ya bi ni can?" Safiyyah na huci tace "Kuma fa haka
ne" Khaleesat ta dafe kanta da yayi mata nauyi tace "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un" Safiyyah tace "Wannan fa kamar ya fi Abdul zama Ιan
daba, ni wallahi ban san haka yake ba da ko hanyar da ya bi a makarantar nan ma
bazan dinga bi ba, in ba dai in danna 911 yanxu su taho ba gaskiya"
Khaleesat ta wani kalleta tace "Su taho su yi maki me? Kar kiyi dialing ki
bari sai na bar nan tukunna" Safiyyah ta koma ta zauna tayi tagumi,
Khaleesat ta bude handbag dinta duk jiki a sanyaye ta ciro wayarta, ta fi
second talatin ta kasa dialing number Ajay don ta tsani masifarsa ita kam, but
did she have a choice? Haka kawai ta koma Apartment dinta Aymaan ya bi ta ko
kofar a kulle yake ya balle ya shigo mata ta shiga uku, ita sai yau ma ta kare
masa kallo kana ganinsa kaga someone on drug shi yasa idonsa suka zama kamar me
sexy eyes ashe tsabar shan kwaya ne, Safiyyah ta kalleta tace "Dole dai
wancan mara mutuncin za ki kira, don ni wallahi bana son Ajayn nan gwara
Housemate sau miliyan, ki ji fa ranan har da korata saboda kawai zai maki
magana sai kace bai san yanda muke da ke ba, ya maida ni kamar wata bare ranan,
abinda Housemate dinki bazai taΙa yi ba kenan yace in tashi wai zai maki
magana, tun daga ranan na kullacesa a raina wallahi, ashe haka yake da baΖin
hali ban sani ba, nace masa good afternoon wai ya amsa da evening tsabar rainin
hankali, pls i don't like him" Khaleesat tace "To ina da wanda zan
kira bayan shi ne?" Safiyyah tace "Yaushe Housemate din naki zai dawo
ne? Gaskiya we are missing him yayi maza ya dawo" Khaleesat tace "Oho"
Daga haka tayi dialing number Ajay, sai da ya katse ta sake kira sannan ya
daga, taji yace "What again Madam?" Hurriedly yayi tambayar as if in
a haste to cut the call, ta sauke idonta a hankali tace "Zuwa yayi ya same
mu a department ni da Safiyyah" Ajay yayi shiru, sai kuma yace "Sai
aka yi yaya?" A sanyaye Khaleesat ta gaya masa abubuwan da ya zo ya fada
da kuma yanda suka yi da Safiyyah daga karshe, Ajay dake ta sauraronta yace
"Kin ga wannan kawar taki me shegen rawan kai sai ta ja maki bala'in da
baki yi tunani ba a rayuwarki, who sent her to exchange words with him? Duk ba
ita ta kai ki inda kika hadu da gayen ba? And meye kike son in maki da kika
kirani yanxu?" Khaleesat ta katse wayarta ta ajiye, Safiyyah dake ta
kallonta tace "What is he saying?" Khaleesat dai tayi shiru bata ce
komai ba, sai ga wayarta ya fara ring ta duba taga shi ke kiranta, Safiyyah ta
taΙe baki tace "Allah sarki Housemate gaskiya yana kokari da wannan Ajay
din ashe haka yake? Wallahi yanda kika san Malamin islamiyya haka nake ganinsa
ni dai yanxu, kullum a fusace yake, ki daga kar ya katse, ni yanxu na gaya ma
Mustapha wannan magana ai zai gano na tafi Party bayan ce masa nayi baki da
lafiya zan je apartment din ki daga schl ranan" Khaleesat tayi picking
call din ta kai kunne taki cewa komai, yace "Kashe min waya kika yi?"
Tace "To me zan yi idan ban kashe ba, kawai kayi ta ma mutum masifa
kullum" Yace "Sai ki je kiyi sorting self din ki out" Daga haka
ya katse wayarsa, Safiyyah tace "Tirrr, anya wannan zai iya zama da mace
kuwa? Ina ga a world din da ya tashi iya maza ne kawai suka yi surrounding
dinsa, amma sam bashi da sympathy wa mace, kawai tashi zaki yi mu tafi gidan
Yaya Mustapha don nima ban baki goyon bayan zuwa apartment din ki ba, Aymaan
drugs din da yake sha basa gaya masa gaskiya" Ita dai Khaleesat bata ce
komai ba, gaba daya taji zaman America din ma ya fita kanta har ma da karatun,
shikenan ita daga wannan sai wannan a rayuwarta, hawaye taji ya cika idonta,
Safiyyah tace "Ke kuma matsalata dake kenan, komai sai kice kuka kamar
wata er yaye, Meye abun kuka kuma? Ni fa ina da strong mind yanda bakya
zato" Ita dai Khaleesat goge hawayen idonta kawai take don ta gaji kuma
haka, Safiyyah ta tabe baki ta koma gefe, haka suka zauna for almost 10 minutes
a wajen kowa da tunanin da yake a ransa, murya can kasa Safiyyah tace "Kin
ga kuma gashi can zuwa, wannan mutumi dai bashi da alkibla" Khaleesat ta
daga kai tana kallon inda Safiyyah ke kallo, lkci daya ta dauke kai fuskarta a
daure, A hankali Safiyyah tace "Ni dai kinga tafiyata...." Daga haka
ta dau handbag dinta kamar munafuka ta bar wajen kan Ajay ya karaso, har Ajay
ya iso wajen Khaleesat bata sake kallon direction dinsa ba, Yana kallonta yace
"Rashin kunyan ki har ya kai ki dinga katse ma mutane waya yanxu?" Ta
wani kallesa amma taki cewa komai, sai kuma ta kauda kai, yace "Ba magana
nake maki ba?" Bata fuska tayi tana shirin kukan da ya tokare mata a
makogwaro yace "Sai dai kiyi ma kanki kuka ba ni ba, and in case u don't
know.... work load dake kaina yafi karfin duk wani kananun issues din ki, Jay
ne yake iya combining both ni kam bazan iya ba, i will be taking you home ki
zauna can har sanda Jay zai dawo ku ci gaba daga inda ku ka tsaya, i don't have
much time to be fighting with a tout because of you" Ita dai bata ce komai
ba, ya hade rai yace "Baza ki tashi ba?" Mikewa tayi without looking
at him, ya juya ya bar wajen ta fara bin bayansa tana hararansa, can apartment
dinta ya fara kai ta, bayan yayi parking yace "Kar ki bata min lkci ki
shiga ki dauko duk abinda zaki bukata for now, don't waste my time" Bude
motar tayi ta sauka ta nufi apartment din, sai da ta Ιata kusan minti ashirin a
cikin gidan bata fito ba, patient dinsa ya kare ya dau waya zai kirata kenan ya
ga motar da ya tsaya dai dai apartment din, kallon motar ya dinga yi don ya
gane motar waye, wanda ke cikin motar na ganin motarsa sai yayi gaba ya wuce
apartment din yana driving slowly, Ajay ya dinga kallon motar da mamaki, wato
uban fist din da yayi masa banda frnds dinsu sun shiga tsakani bai ishesa ba
kenan, few a cikin abokan Aymaan are also his frnds shi yasa matter din ma bai
yi escalating ba har suka shiga tsakaninsu suna ba Ajay hakuri, amma fa Aymaan
ya sha kulli kafin abokan su yi intervening, haushin hakan yasa yaje ya samu su
Khaleesat a department dinsu, sai kuma yanxu gashi ya sake biyota gida, Ajay ya
gyada kai, ya ci sa'a ba a Nigeria suke ba, wayarsa ne ya fara ring ganin Jay
ke kiransa ya daga, daga daya bangaren Jay yace "Yarima me yasa baza kayi
respecting title din da kake holding ba pls, why are you like this? menene ya
kai ka fada da Aymaan? A America ku ke fa ba Nigeria ba Bruh" Ajay dake
sauraronsa yace "Ai ba mu yi fada ba, kilan dai nan gaba za mu yi, don sai
na karya masa hannu in bai yi hankali ba, dama naga ba shi da Stamina bugu daya
ya tafi kasa don haka karyasa ba wahala zai min ba..." Jay ya ja tsaki
yace "Can you hear ur self plss? I will report you to Abba in dai baza ka
dena wannan abun da kake yi ba, kai bini bini ka kai fist kamar wani Ιan dambe?
who does that pls, haba wannan zubar da class dinka kake wallahi" Ajay
yace "To wa ya jawo? Ba kai da wannan brat din bane ku ka ja har nake
fada? Da baka bar ni da ita ba hakan zai faru ne?" Jay yace "A'a dama
can hannunka kaikayi yake, stop using us to cover ur foolishness, sannan ni ban
bar ka da ita ba because i know she is old enough to care for her self with no
supervision kai ne dai ka maida care dinta hannunka voluntarily for reasons
best known to you, Kuma ni ba gashi nayi ma Aymaan din magana ba kuma ya
fahimce ni, amma kai komai sai ka sako hargagi ciki kamar jira kake ka fara
dambe" Shiru Ajay yayi, kawai sai yayi ignoring wasu daga maganganun Jay
yace "Ohk, kayi masa magana shi yasa naga motarsa yanxu a kofar apartment
dinta ko?" Jay yayi shiru, sai kuma yace "Kai me ya kai ka apartment
dinta?" Ajay ya katse wayarsa ya ajiye, sosai yaji Jay ya bata masa rai,
and he was boiling from inside, ji yayi kamar ya ja motarsa yayi tafiyarsa ya
bar ta da faith dinta a gidan tunda dama ba idea dinsa bane dawowarta America,
har ya fara reverse amma kuma sai ya kasa tafiya, ya sake kallon direction din
da Aymaan ya bi yaga babu motarsa alamar ya tafi, Jay ya dade bai Ιata masa rai
kamar haka ba, kawai ya dau wayarsa ya shiga contact dinsa ya danna masa block
sannan ya ajiye wayar, sai ga Khaleesat ta fito daga apartment dinta, ko
kallonta Ajay bai yi ba har ta gama saka duk abubuwan da ta dauko a back seat
don taga bai bude booth ba babu kuma alamar zai bude, bayan ta kulle seat din
ta bude front seat ta shiga motar ta kullo kofar a hankali, ita ma bata kallesa
ba kamar yanda shi ma bai ko kalleta ba ya fara reverse din motar. Har suka isa
gidan ba abinda yace mata ita ma haka, yayi wucewarsa ciki ya bar ta da
kayanta, haka nan ta dauka kayan bit by bit tana shiga da su gidan, har sannan
yana tsaye parlor waiting for her to finish, sai da ta gama shigo da kayan babu
yabo babu fallasa yace "Meet me in the kitchen" Daga haka ya nufi
kitchen din ta bi bayansa, Utensils da aka kebe a kitchen din ya nuna mata
wajen da suke a takaice yace "That is a no go area, duk ma me zaki taΙa a
kitchen din nan banda su" Yana kai wannan ya fice daga kitchen din ta
dinga kallon Utensils din ba ma sae an gaya mata ba ta gane iya shi ke amfani
da su, can ta tabe baki ta juya ta fita, bayan ta kai duk abubuwan ta dakin da
ta sauka jiya taji wayarta dake jaka na vibrate, ta dau jakan ta bude ta ciro
wayar, sosai gabanta ya fadi ganin number Housemate dinta, duk da tayi deleting
number amma tsaf yana kanta don special digits ne bbu wahalan haddacewa....
[7/14, 8:35 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat ta
zauna gefen gadon dakin tana kallon screen din wayarta, zata yi picking call
din ya katse, it took her almost 2 minutes before returning the call amma har
ya katse bai daga ba, ta dinga kallon wayar waiting to see if he will call back
amma har bayan minti goma bai kira ba, hakan ya sa ta ajiye wayar a hankali ta
mike ta fara gyara dakin, ta sauka downstairs tana dube duben inda zata ga abun
shara da goge goge na gidan, har ta fidda rai da samu sai gashi ta gani a under
stair storage din gidan, bayan ta gama gyaran dakin da take ciki da Babban
corridor din sama sai kuma ta sauko downstairs ta fara gyaran babban parlon
hade da goge goge, it took her almost 2 hours kafin ta gama aikin gidan gaba
daya, kitchen kuma bata ga abinda zata gyara ba cause it was very neat and tidy
alamar yana gyarawa a ko da yaushe, ta maida Household cleaners din da tayi
amfani da su a under stair storage din da suke sai gashi yana saukowa
downstairs ya canza kayan jikinsa, yi yayi kamar ma bai san me tayi ma gidan ba
ya dau makullin motarsa da ta ajiye saman Centre table ya nufi kofa ya fita
daga parlon, tabe baki tayi ta tafi sama don ta gaji sosai ba kadan ba, sai da
tayi gyaran gidan sannan ta kara tabbatar da girman gidan. Khaleesat na zaune a
daki da laptop dinta a gabanta tana studying wani course dinsu da za su yi test
dinsa ranan monday, it was a Saturday afternoon, ta juya ta kalli wayarta dake
vibrate, sau uku kenan Safiyyah na kiranta taki picking don tasan me zata ce,
can dai ta jawo wayar tayi picking ta kai kunne tayi shiru, daga daya side din
Safiyyah tace "Haba mana Khaleesat don zaki koya min abu sai kiyi ta min
walakanci gashi test za mu yi ranan Monday, is it fail that you want me to
fail?" Khaleesat ta sauke wani ajiyar zuciya tace "To ya kike son
inyi Sophie? i said u should be coming kin ki" A fusace Safiyyah tace
"A'a wallahi bazan zo wannan gidan ba kinji har na rantse, haka kawai in
zo ya koreni, shi ba wai kara garesa ba balle ince zai ji kunyan korata, gaskiya
bazan zo ba don zan iya zaginsa idan ya koreni" Khaleesat tayi dariyar da
bata yi niyya ba tace "Wai ban gane ya kore ki ba, why will he do so bayan
yasan wajena ki ka zo" Safiyyah tace "In dai baza ki zo school din ba
shikenan kawai i will look for another person to teach me, ni kinsan ba gane
lectures nake a aji ba sai in an min bayani dalla dalla gani ga mutum"
Khaleesat dai tayi shiru tana jin ta, Safiyyah tace "Sai anjima don
Allah...." Khaleesat ta Ιan yi murmushi tace "To let me see if i will
be able to come, kin ga karfe biyu da rabi yanxu fa, da tun jiya sai ki gaya
min ai, kina school ne?" Safiyyah tace "Eh mana, tun 12 na shigo schl
ai" Khaleesat tace "Ohk, i will be coming now" Katse wayar tayi,
ta sauka daga kan gadon ta canza kayan jikinta ko rigar sanyi bata sa ba don
sanyin ya ragu sosai yanxu, ta dau backpack dinta bayan ta saka laptop ciki ta
kashe wutan dakin ta fito, downstairs take leke daga passage way din da take
tsaye, ta ga Ajay zaune parlon da wasu turawa biyu alamar frnds dinsa ne ga
wine a gabansu, she can't even remember the last time da suka hadu a cikin
gidan da shi, it is more than a month now da take gidan amma zata iya kirga sau
nawa suka yi crossing part da shi a gidan, yawanci yana bangarensa take fita
school da safe, kuma daya daga ma'aikatan gidan ne ke dropping dinta sannan ta
gaya masa sanda zai je ya daukota kamar dai yanda aka basa instruction yayi, in
kuma aka dawo da ita gidan bayan ta gama lectures zata ga babu motar Ajay a
compound alamar ya fita, tunda a daki take zama bata sanin sanda yake dawowa
gidan, the next day kuma the same process will repeat it self, girki kuwa tunda
tayi sau uku da shi taga duk bai ci ba don ko kusa da abinda ta dafa baya zuwa
kawai sai ta dena sai dai tayi nata ita kadai, but tayi noticing anyi
restocking foodstuffs irin na Africa a kitchen din probably because of her, don
ita duk wani ciman turawa ba damunta yayi ba, may be yayi noticing hakan ne
yasa ya siyo mata irin wanda take so, gyaran gida kuma tunda workers din are
around iya dakin da take ciki kawai take gyarawa, tana saukowa downstairs ta
gaida friends dinsa sannan ta kallesa shi ma ta gaishesa, bai amsa gaisuwan ba
without looking at her yace "Ina za ki je?" Ta sauke idonta tace
"Zan shiga school" Still not looking at her yace "Ki yi me a
school on a Saturday?" Ta Ιan kallesa, sai kuma tace "Tutorial zan ma
Safiyyah" Sai a nan ya juya ya kalleta yace "As per the lecturer you
are in John Hopkins ko? to baza ki je ba" Tayi shiru tana kallonsa, ya
hade rai yace "Ko baki ji me nace ba?" Bata fuska tayi tana kallonsa,
ya ci gaba da maganar da yake da friends dinsa, tana jan veil din jikinta tace
"To zata iya zuwa nan?" A takaice Ajay yace "Baza ta zo, leave
this parlor Madam" Ta wani tura baki ta juya ta koma sama, tana komawa
daki ta kira Safiyyah, a hankali tace "Sophie i met the door locked kuma
no one is around...." Safiyyah ta katse ta tace "Har workers din
gidan?" Khaleesat tace "Kawai ki nemi wanda zai maki Tutorial din
Sophie, ranan Monday before the test zan sake yi maki" Safiyyah tace
"Ai shikenan, dama ban saka ran za ki zo ba, in ma Ajayn ne ya hanaki shi
ya sani don ko a jikina wallahi, dama tun ranan farko da muka je duba Housemate
dinki da na fara ganinsa sam bai kwanta min a rai ba naji tsoronsa, wai don
Allah yaushe Housemate din ki zai dawo ne abu almost 2 months yanxu, ko dai
anyi awarding dinsa doctorate Degree dinsa ne shi ne ya tafi yayi wasu abubuwan
a Nigeria? shi kuma wancan uztaz din ko anyi cancelling work dinsa ne yake
sakewa daga farko?" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, magana
Housemate din nata yake mata balle tasan sanda zai dawo? Kuma kullum da damuwan
hakan take kwana take tashi a ranta, ta rasa gane me yasa communicating din da
baya yi da ita ya tsaya mata sosai a rai har yake damunta, well... may be he
have his reasons, she is not even judging him, but deep down she knows she
misses him so much, she misses everything about him, wani lkcn in ta kasa
hakuri takan dake zuciyarta tayi masa magana ta WhatsApp, zai kuma yi mata
reply amma casually, in yayi mata haka kuma bata iya daurewa sai tayi kuka,
last maganar da tayi da shi almost a week ago ta tambayesa yaushe zai dawo,
kawai yace mata soon and that was how the conversation ended, after that basu
sake magana ba har yau, dama kuma ita ke yi masa, Safiyyah tace "Ni dai
sai anjima, ina ta maki magana zaki min shiru katina na tafiya" Daga haka
ta katse wayarta, a hankali Khaleesat ta ajiye wayar hannunta a gefen gado. Few
weeks later Khaleesat na zaune ranan friday ita kadai a haraban department dinsu,
Voice call suka gama da Aunty Farida ta WhatsApp bayan ta turo mata wasu videos
da ta kasa fahimta sai kawai ta kira Aunty Faridan don tana online, tunda suka
gama wayar Khaleesat ta kasa kwakkwaran motsi a inda take zaune, she looks so
confuse and shock at the same time, kamar ance ta daga kai ta ga Aymaan da wata
yarinya suna tafiya, yarinyar na ta masa labari da turanci, bata yi kama da er
Nigeria ba duk da kana ganinta kasan er Africa ce yarinyar, Khaleesat ta sauke
idonta tana kallon wayar hannunta har suka wuce ta, sai ga Safiyyah ta fito
daga Hall din karatu da Backpack dinta a hannu, tana isowa kusa da Khaleesat ta
zauna tace "Ke baki ga Aymaan ya wuce ba yanxu?" Khaleesat dai tayi
shiru don har sannan bata yi recovering daga shock din da take ciki ba,
Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Ni wallahi naji haushi da ya Musty
ya neme sa wai har da basa hakuri akan abinda muka masa, me muka masa in ba
cowardliness irin na Musty ba? Abinda ma shi ne ya nuna mana halin jakanta, tunda
uwata ta haifeni ban taΙa ganin matsoraci kamar Ya Musty ba, ni da nake mace ma
na fi sa dakakken zuciya, wai ka samu namiji kamar ka kana basa hakuri, wallahi
ban so ace case din nan ya mutu da wuri ba na so ayi ta gwabzawa, na tsani in
ga an shashantar da Case me zafi irin haka, bayan hakurin da Ya Musty ya basa
naga kamar yana shakkar Ajay ma, kinsan na gaya maki frnd dina Sulaiman ya gaya
min ashe narka masa duka Ajay ya so yayi aka maza aka shiga tsakaninsu, amma
duk da haka ya sha kulli wajen Ajay, to duk har da hakan ya tsoratasa ya kama
kansa da mu, amma nasan zai fake da cewa Ya Musty ne ya basa hakuri, kuma yaga
Ajay ya daukeki daga apartment din ki ya maida ki gidansu, kinga ai dole ya
tsorata da lamarin, Allah ya sa dai Housemate din ki ma bai ba Aymaan din hakuri
ba don daga yanda ya sameni yayi min magana ta WhatsApp sanda abun ya faru har
da bani lefi wai me yasa zan yi ma Aymaan rashin kunya wallahi babu tantama shi
ma Housemate din naki ya basa hakuri, ni fa na tsani in ga maza suna baya baya
da case din tashin hankali kamar wasu mata, shi yasa Ajay ya burgeni da ya nuna
masa hauka, wo koma yaya ne dai can ta matse masa shege, ai kinga bai sake bi
ta kanmu ba a school din nan, kaiii mun ga jalala ashe lafiyarsa qlau mutumin,
sannan bai taΙa aure ba sai yawon iskanci..." Shiru Safiyyah tayi ganin
hankalin Khaleesat gaba daya baya jikinta, Safiyyah tayi kasa da murya ta kamo
hannunta tace "Me ya faru kawata? Is anything the matter? Naga lafiya na
bar ki naje dauko Backpack dina, why the sudden change of mood? Ko Aymaan din
yace maki wani abu ne?" Khaleesat ta kasa ce ma Safiyyah komai, sai ga
hawaye cike idonta, Safiyyah ta dire jakar hannunta a kasa tace
"Subhanallahi, don Allah me ya faru? Me Aymaan din yace maki mu kira Ajay
yanxu" Khaleesat na goge idonta cike da karfin hali tace "I spoke
with Aunty Farida now" Safiyyah ta zaro ido tace "Me ya faru?"
Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "Kawai ce min tayi Housemate dina
yaje can gidanmu jiya" Safiyyah ta wani kalleta, can tace "Don Allah
ji yanda kika sa gabana ya fadi na zata mutuwa aka yi a gidan naku, to don ya
je gidanku sai ki fara kuka? Ko dai dama akwai abinda ke damunki kike son kiyi
kukan amma sai yanxu kika samu sarari?" Khaleesat ta girgiza mata kai,
wasu hawayen na taruwa idonta tace "Gida wai ya siya ma Abbana"
Safiyyah ta bude baki da mamaki tana kallon Khaleesat, can ta dafe kirji tace
"Gida fa Khaleesat?" Khaleesat ta kasa cewa komai wasu hawayen na
sauka idonta, ta bude wayarta ta shiga chat dinsu da Aunty Farida ta tsaya dai
dai wajen videos din ta mika ma Safiyyah wayar, Safiyyah was speechless for
almost 2 minutes bayan ta gama kallon videos din gidan, wato gida ne har gida
irin na zamani that is well furnished, a hankali Safiyyah tace "I am short
of words too Khaleesat, wallahi ban san me zan ce ba, but just know that ur
Housemate is one in a million Khaleesat...." Khaleesat ta fashe da kuka,
Safiyyah ta rungumeta soothingly tace "It's something to be happy about ba
kuka za ki yi ba, yanda ya saka iyayenki farin ciki Allah Ubangiji ya dawwamar
da shi cikin farin ciki na har abada, Allah ya saka masa da mafificin alkhairi,
ya biya masa duk bukatansa na alkhairi, yanxu kina komawa gida sai ki nutsu ki
kirasa" Cikin kuka Khaleesat tace "Ko na kirasa baya picking"
Safiyyah tayi shiru, can tace "May be he have his reasons Khaleesat, just
compose a text for him sai ki tura masa ta WhatsApp, and i will also thank him
via WhatsApp on ur behalf, duk wani abun farin cikin ki nawa ne nima...."
Ita dai Khaleesat ta kasa cewa komai but she is soo emotional, ta kasa daina
kukan da take, a haka driver ya zo daukanta, Safiyyah ta rakata har inda yake
parking ta bude mata back seat tace "Don Allah kar ki je gida kina wannan
kukan, wannan ai abun farin ciki ne ba na bakin ciki ba da zaki yi ta kuka har
haka" Khaleesat ta gyada mata kai kawai tana share hawayenta, Safiyyah ta
daga mata hannu tace "Anjima zan kira ki in sha Allah" Nan ma dai
kawai kai Khaleesat ta gyada mata a haka drivern ya ja motar suka bar wajen.
Bayan sun isa gida Khaleesat ta bude kofar parlor ta shiga da sallama can kasa,
kanta a kasa ta gaida Ajay da ta gani zaune parlor da Salem, sannan ta wuce
sama, sau daya Ajay ya bi ta da kallo sai kuma ya dauke kansa, after some
minutes yana kallon Salem yace "I am going up to get some rest, will you
still be around?" Salem yace "Ohk i will wait har ka sakko"
Mikewa Ajay yayi ya dau wayarsa sannan ya saka House Slippers dinsa ya wuce
sama, kofar dakin da take ciki ya tsaya yayi knocking, Khaleesat da ta kwanta
gefen gado ta dora kanta saman pillow feeling so emotional ta mike zaune tana
kallon kofar, yana bude kofar ta fara goge sauran hawayen idonta, ya shigo
closing the door behind him yana kallonta yace "What happened?" Sauke
idonta tayi bata ce komai ba, yace "Ba kya ji na ne?" Girgiza masa
kai tayi a hankali tace "Ba komai" Yace "Bakomai zaki shigo ma
mutane gida kina kuka?" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, yace
"Sake kula ki yayi a school din ne?" Ta daga kai ta kallesa ta
girgiza masa kai cikin sanyin murya tace "A'a, kawai kaina ne ke min ciwo"
Daga sama har kasa ya kalleta sannan yace "Kukan ya baki magani" Daga
haka ya juya ya fita daga dakin.... Wajen karfe biyar Khaleesat ta farka daga
baccin da ya dauketa tun bayan da Ajay ya bar dakin, da yake ba sallah take ba,
mikewa zaune tayi ta jawo handbag dinta a hankali ta bude ta ciro wayarta,
number Housemate dinta da bata kara saving ba har sannan tayi dialing hoping he
will pick her call today, amma har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma
bai daga ba, to yanxu me ma zata ce masa ta WhatsApp, words failing dinta kawai
za su yi in ma tace tayi masa magana ta can, bata ma san ta yaya zata fara ba, Ιaga
kai tayi ta kalli kofar dakin jin ana knocking, sai da aka sake knocking din
sannan ta sauka daga kan gadon tana tafiya a hankali ta tafi ta bude kofar,
daya daga workers din gidan ne rike da tray din abinci, mamaki tayi don tun
zuwanta gidan babu worker din da ya kawo mata abinci har daki, infact ita ce ma
ke girka abinda take ci a gidan, ta dai amshi tray din cikin sanyin murya tace
"Thank you" Sannan ta juya ta koma daki, bayan ta ajiye tray din ta
bude plate din dake rufe a kai taga Jollof rice ne yana tiriri alamar yanxu aka
gama girkin, ga wani aroma me dadi na tashi, ta bude wani plate din taga full
chicken laps biyu anyi grilling dinsu, sai kuma bowl din veggies da dressing
dinsu a gefe, with 2 bottles of water and a glass cup da can drink, still a kan
tray din taga maganin ciwon kai, a hankali ta dau spoon ta goge sa da tissue
din da aka yi wrapping dinsa sannan ta fara cin abincin, kuma sosai abincin
yayi dadi, ya kuma yi yaji kamar a Nigeria aka yi, ta dai ci abinda zata ci ta
ajiye sauran for dinner. Washegari still haka aka kawo mata breakfast har daki,
bacci ma take tunda ba school zata je ba ta sauka kan gadon ta saka hijab sannan
ta bude kofar, bayan ta amshi tray din ta kulle kofar dakin ta tafi ta ajiye
breakfast din don sai ta fara wanka.... Wajen karfe biyar din yammacin ranan
Ajay na parlor tare da Salem aka bude kofar parlon, tun da ta shigo Ajay ke
kallonta da wa enda ke biye da ita a baya, wato jakadiyarta da aminiyarta
Hajiya Usaina, sai er aminiyarta da bazata wuce 25 years ba, Salem ya mike
tsaye yana welcoming dinta da ladabi, ta amsa masa sama sama without looking at
him, sai da ta zauna parlon bayan jakadiyarta tayi saurin gyara mata throw
pillow sannan Ajay ya gaisheta, ta amsa cike da isa tace "Daga
Massachusetts Boston mu ke, mun je convocation din Afrah a Havard University,
we will be passing the night here before leaving for Nigeria tomorrow"
Ajay dai bai tanka ta ba, ya gaida aminiyarta warce convocation din er ta suka
je a Havard din, Afrah dake ta kallonsa ta gaishesa, ya amsa without looking at
her sannan ya mike ya nufi sama, shi dai Salem ya juya ya fita daga parlon,
Ajay na haurawa sama direct dakin da Khaleesat take yayi knocking sannan ya
bude kofar.
[7/15, 9:49 PM] khaleesat Haiydar π✍️: Khaleesat
dake karatu da Laptop dinta ta juya tana kallonsa, a takaice yace "Don't
look at me that way, ki dau duk wani abinda zaki bukata yanxu zaki koma dakin
Jay don muna da baki a gidan...." Ko rufe baki bai yi ba aka bude kofar
dakin, ta madubin dakin yake kallonta don tsayuwa tayi bakin kofa tana kallon
Khaleesat with mouth agape, Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "Ina
yini...." Aunty ta karaso cikin dakin da mamaki tana kallon Ajay tace
"Junaid? Wacece wannan kuma?" Ba tare da Ajay ya juya ya kalli inda
take ba a takaice yace "Kanwar Salem" da wani expression Aunty tace
"Kanwar Salem? Me take yi a gidan nan? Kuma a cikin daki zaune a saman
gado?" Sai a sannan Ajay ya juya, looking at her in the eyes yace
"The apartment she was staying was sold out yesterday, and she is
homeless, so she is here for today before moving to her new apartment
tomorrow...." Aunty tace "Da iznin wa kayi hakan? Dama gidan ka ne
nan din da zaka yanke hukunci kanka tsaye kamar me gidan? I can't remember his
Highness saying this house is urs in anyway Junaid, baka da right, sannan
iyayenta da suka turota karatu basu nema mata wani alternative ba sai kai
sarkin Hausawan Nigeria dake Baltimore? Beside ban ga ta inda take kama da
Salem ba, Salem da yake baki me ya hadasa da wannan farar yarinyar? karya kake
yi daya daga matan banzan da kake iskancin ka da su ne a kasar nan, ka zata duk
bamu san abinda kake yi ba ne?" Calmly Ajay yace "You can say
whatever, kawai dai ni dai i also can't remember Abba saying we are to share
this house with you and ur visitors, saboda ni da Jawwad Abba ya siya gida a
garin nan ba don kowa ba, don haka ban ga dalilin da za ki dinga zuwa da wasu
mutane can babu notice ba ki maida mana gida gidan saukan baki, kaf
Massachusetts babu hotels da dole sai kin taho Maryland za ki samu masauki?
Beside all this... u are not even in the rightful place to tell me what to do
and what not don da sunana da na Jawwad Abba ya siya gidan nan, don haka babu
ruwanki da duk wanda zan kawo gidan, since you can't do without intruding, ki
zo kiyi intrusion dinki in peace kiyi tafiyarki without questioning
me...." Aunty da ta bude baki tana kallonsa tace "Zagin nawa da ka
saba zaka yi Junaid? Ni kake gaya ma bakaken magana? Rashin kunyan da ka saba
yi min zaka yi a nan ma?" Ajay yace "Whatever, all i know is that u
can't just be appearing in here without notice tare da wasu mutane can kina
inconveniencing din mu kina sa mana ido" Wani murmushi kawai tayi ta kalli
Khaleesat sannan ta juya ta fita daga dakin, gaba daya jikin Khaleesat yayi
sanyi ta kasa motsi a inda take, after few seconds ta sauka daga kan gadon tana
kallon Ajay da ya kafe ma dressing mirror ido yasan fitar da tayi Abba zata je
ta kira, cikin sanyin murya Khaleesat tace "Why will u speak to her that
way Ya Junaid?" Ya dakatar da ita fuska daure yace "Ba ruwanki
Malama, kin san ta ne?" Khaleesat ta sauke idonta bata sake cewa komai ba,
ya juya ya fice daga dakin yana birkita gashin kansa, ga wani zafi da yake ji,
where is he even going to start explaining this to his dad for the second time,
gashi Jay baya gidan just him and the lady in the house, wani bayani zai yi ma
Abba da zai yarda da shi? Ιangarensa ya nufa ya zauna gefen gado ya dafe kansa
da yaji yayi masa nauyi, in mahaifiyarsa ce ai sai dai su kashe su rufe tare da
ita without her involving his dad in this issue, infact baza ma ta so wani yaji
ba, he felt soo emotional, Aunty na komawa downstairs ta zauna kan kujera ta
jawo jakarta ta ciro wayarta, Hajiya Usaina dake kallonta tace "Ya naga
ranki a bace Fulani?" Aunty tayi wani murmushin takaici tace "Bari
dai inyi waya da mai martaba tukunna Usaina" Tana fadin haka ta tafi dakin
da take sauka ta tarar da jakadiyarta a ciki tana ta faman goge goge duk da
dakin fess yake, zata fita Aunty ta mata alamar ta ci gaba da abinda take,
sannan ta zauna kan kujera tayi dialing number mai martaba tana girgiza kafa at
the same time tana fatan Allah ya sa ya samu damar daga kiran don zuwa yanxu
dai tasan yana Ιangarensa shi kadai, ai ko babu jimawa ya daga kiran, bayan sun
gaisa cikin ladabi da kwantar da murya tace "Allah ya taimake ka ya ja
zamaninka, mun iso Maryland babu dadewa yanxu" Daga daya bangaren yace
"To maa sha Allah fulani..." Ta kara yin kasa da murya tace
"Amma Allah ya ja zamaninka ban ji dadin abinda na zo na tarar a gidan nan
ba" Shiru Mai martaba yayi bayan yaji me tace, don tana fadin haka babu
abinda ya fado masa sai abinda ya gani dakin Ajay kwanaki da ya sauka
Baltimore, Jin Mai martaba yayi shiru Aunty tace "Ko kana tare da baki ne
ranka shi dade babu sararin mu yi magana?" Calmly Abba yace "Ina
sauraron ki" Aunty ta gyara zama tace "Mace na zo na tarar a dakin
Yarima cikin wani yanayi mara dadin fade, hankalina yayi matukar tashi ranka shi
dade, na dimauce ba kadan ba da abinda idona ya gane min, ban ji dadin hakan ba
ko kadan wallahi, kuma da alama ba wannan bane karo na farko, ya saba yin
hakan, Allah Ubangiji ya shirya mana su kawai" Mai martaba yayi shiru don
sosai yaji abinda ta fada ya dake sa don har sai da ya jingina kansa da kujeran
da yake zaune, tayi kasa da murya tace "Amma ba komai ranka shi dade kar
hakan ya sa kaji babu dadi a ranka ko kuma ka damu, in sha Allahu idan na dawo
sai mu san abun yi, mu san inda za mu billo ma lamarin don baza mu zuba ido a
ci gaba a haka ba, kaga wannan big slap to our faces ne idan aka samu labarin
abinda yake yi a kasar nan, hakan zai zubar mana da reputation din masarautarmu
ne kawai, shi yasa kwanaki nace maka a samu yarinya me hankali da nutsuwa er
manya a aura masa ko da kuwa ba er gidan sarauta bace, sai naga kamar hakan bai
gamshe ka ba tunda baka ba maganar tawa muhimmanci ba na lura baka son yi masa
dole ne, ni kuma abinda yasa na kawo wannan shawaran shi ne saboda shi Yarima
ba kula yan matan yake ba a gida Nigeria" Cikin nutsuwa mai martaba yace
"Bangaren nasa kika je?" Aunty ta Ιan fara kame kame tace "Ehh
can na je ranka shi dade, gani nayi tunda muka shigo gidan ga dai motarsa amma
shiru bamu gan sa ba, da yake kwanaki ai ya Ιan yi zazzabi saboda weather sai
nayi tunanin to ko baya jin dadi ne, sai na karasa bangaren nasa, shi ne fa
idona yayi mummunan gamon nan" Mai martaba yace "If possible try
conversing with the lady u saw ki ji er wace jaha ce a Nigeria, ina son sanin
background dinta, just Converse with her Fulani...." Aunty tayi shiru
bayan taji me Mai martaba yace, can tace "Ranka shi dade ai ba er Nigeria
bace matar, baturiya ce fa, kuma irin tsofaffin turawan nan, da kyar ma in bata
haifesa ba" Mai martaba ya sauke ajiyar zuciya yace "Na fahimta"
Aunty tace "Yanxu dai idan na dawo za mu tsara komai ur Highness, ka
kwantar da hankalinka, in sha Allahu anyi na karshe, we will put a stop to this
soon, kuma ko makusantan ka na fada don Allah kar ka gaya ma wannan magana, don
ba magana bace da ya kamata ace ya fita" Mai martaba was quite, don
tunanin da yake yi ma shi daban, daga karshe Aunty tayi masa sallama ya katse
wayar, tana kallon jakadiyarta dake zaune kasa tayi murmushi tace "Mace na
samu a dakin baΖi, amma ban san tun yaushe take zaune gidan ba ya dai ce min
jiya ta zo gidan, sannan babu cin mutuncin da ya mance bai min ba"
Jakadiya ta kara bajewa a kasa tace "Ja'iri, gaskiya ya kamata wannan
karan ki dau mummunan mataki akan sa ranki shi dade kar ki dau lamarin da wasa,
abubuwan da yake maki sun isa haka, duk baya ganin mutuncin ki kuma wannan abu
na saka ni damuwa uwar gijiyata, yanxu dai kamata yayi ki kira daya daga
ma'aikatan gidan ku kebe ki tambayesa ki ji tun yaushe ya ajiye yarinyar a
gidan nan..." Aunty tayi wani murmushi tace "Kin kawo shawara
kuwa...." Mikewa tayi ta fita daga dakin Jakadiya na jero mata kirari....
Bayan wani lokaci Ajay ya fito dakinsa ya tafi dakin da Khaleesat take, without
looking at her yace "Ina jiran ki downstairs" Daga haka ya fita daga
dakin, har zai sauka kasa ganin su Aunty a parlon ga uban kayan ciye ciyen da
aka baje masu a tsakar parlon, sai kawai ya tsaya a corridor, a hankali
Khaleesat ta mike tsaye ta dau Hijab dinta ta saka ta bude kofar dakin ta fito,
yana jin alamar ta fito ba tare da ya juya ba yace "Mu je, kuma ban ce ki
ce zaki gaida kowa Downstairs ba" Daga haka ya fara sauka kasa tana biye
da shi a baya jiki a sanyaya, tun da suka sauko Aunty da kawarta da Afrah ke
kallon Khaleesat, Ajay dai ko kallonsu bai yi ba ya nufi kofa Khaleesat na biye
da shi ita ma bata yarda ta kalli direction din su ba, gun motarsa taga ya nufa
ya bude ya shiga, ta karaso gun motar ganin bata shigo ba ya daure fuska yace
"Baza ki shigo ba?" A hankali ta bude seat din ta shiga, yana
kallonta yace "Haka kika fito baki dauko komai ba?" Tayi shiru, sai
kuma tace "Ai baka ce min in dau komai ba" Tsaki ya ja ya bude motar
ya fita ya koma cikin gidan, ita dai ta bi sa da kallo, dakin da take ya koma
ya dau laptop dinta da charger sai wayarta shima da Chargern sa sannan ya fita
daga dakin yayi locking kofar yanda ba wanda zai bude ya sauka downstairs, nan
ma su Aunty suka bi sa da kallo, Afrah kamar idanuwanta za su bi sa har
compound din.... Har Ajay ya isa apartment din Khaleesat bai ce mata komai ba,
ita ma dai tayi shiru da tunani iri iri a ranta, kana ganinta kasan duk a
sanyaye take, bayan sun sauka motar ya nufi entrance din shiga apartment din ya
ciro makullin a aljihunsa ya bude ya shiga parlon, ta bi bayansa. Jay na zaune
gaban mai martaba kansa a kasa yana jin duk abinda yake cewa, Cikin nutsuwa mai
martaba ya ci gaba da cewa "I am so disappointed in you Ahmad, kana kallon
abinda Ιan uwan ka ke yi amma ka kasa gaya min, i am really disappointed, even
if you can't tell me directly there are other ways to approach me and i will
understand you, to yanxu kana tunanin rufa masa asiri kake yi yana aikata sabo
kenan?" Jay ya dago kansa a hankali, after few seconds murya can kasa yace
"Abba ba abinda ku ke tunani bane, i promise you Junaid is doing nothing
that is against the teaching of Islam, ba ma shi da lokacin da yake kula mata
balle har yayi wani doguwar mu'amala da su, ka yarda da ni Abba bazan maka
karya ba" Mai martaba dake kallonsa yace "Na je Maryland na ga mace a
dakinsa, Auntynku ta je jiya and same thing happened, ta yaya zan yarda da
maganar ka Ahmad? What sort of silly coincidence is that?" Jay yace
"A gafarce ni Abba, amma nasan ba a dakinsa Aunty ta ga mace ba sai dai a
dakin baki, shi Junaid wani irin mutum ne wanda idan yaga mutum stranded be it
namiji ko mace bai ki ya ajiye ko ma waye a gidan ba har zuwa sanda mutumin zai
yi sorting kansa out, you can confirm this from the workers of the house,
wallahi halinsa kenan ba wai don ya hada komai da wa enda yake taimaka ba, Abba
kasan bazan maka karya ba wai don in rufe laifin da kake tunanin Ajay ya aikata
don in nayi hakan nima Allah bazai bar ni ba, Billah i am telling you nothing
but the truth Junaid ba shi da hadi da koma wacece Aunty ta gani a gidan
nan" Abba yayi shiru, after a while yace "Na ji, kuma na yarda, but i
am afraid hukuncin da na tsara a kansa bazai masa dadi ba, but he still have to
accept it cause hakan kadai ne zai sa in samu nutsuwa da kwanciyar
hankali" Jay sai kallon Abba yake, a hankali yace "Wani hukunci kenan
Abba?" Abba yace "Na yanke hukunci zan masa aure and he just have to
accept ko ma wacece matar, you are not excluded also, duk da kai akwai maganar
ka da Hadiyah....." Jay ya kwantar da murya yace "Don Allah kayi
hakuri Abba, we have just few months remaining da muke saka ran za mu gama
karatun nan da muke yi, bamu yi tunanin za mu kawo har warhaka bamu gama ba,
plss Abba a saurare mu har zuwa sanda za mu gama, in just 2 to 3 months"
Abba yace "Kwanaki ma haka ku ka min dadin bakin nan, kun maida ni kakan
ku" Jay yace "Kayi hakuri Abba, mun san ka bamu dama sosai and this
will be the last in sha Allah" Murmushi kawai Mai martaba yayi yana
kallonsa, kowa yasan sa a mutum mai magana daya, amma ga yara sai juyasa suke
yanda su ke so, after a while Abba yace "Yaushe zaka koma Amurkan?"
Jay ya sunkuyar da kansa yace "Watan da za mu shiga in sha Allah"
Abba yace "Allah ya kai mu" Khaleesat na zaune saman darduma wajen
karfe shidda na yamma, tun da tayi sallan la'asar take zaune kan darduman take
karatu a laptop dinta don in a month and few days time za su fara Spring
semester exams din su, wayarta taji yayi vibrate alamar shigowar text, ta jawo
wayar tana duba text din taga number Ajay, "Come out" iya abinda ya
tura mata kenan, ta ajiye wayar ta mike ta dau Hijab dinta ta saka, tunda ta
dawo apartment din nata kusan kullum zai zo wani lkcn ya gama zamansa a motarsa
da yake parking a garage sai kuma yayi ordering ride ya bar motar tasa a garage
din ya tafi, wani lkci kuma ya shigo parlon nata bazai dai dade ba zai fita,
kuma ba wai magana yake yi mata ba, da ta lura bai son magana iyaka kawai ta
gaishesa ta koma ta ci gaba da abinda take, wani lkcn ma sai ta dawo school
zata ga alamar ya zo apartment din idan taji kamshinsa a parlor, duk ta lura
for security purpose yake hakan, har ma da barin motarsa da yake yi a garage
din apartment din, don ko da ya zo da safe ya dau motar ya tafi inda za shi to
zai maida nan yayi parking da yamma sannan yayi ordering ride da zai kai sa
gida, and she really appreciate all this that he is doing for her safety, don
farko da ta dawo gidan kusan kullum sai tayi kuka gashi bata iya bacci da
daddare don gani take kamar at anytime Aymaan zai iya zuwa gidan, gradually
kuma ta hakura barin da ta ga Ajay na yawan zuwa gidan, amma fa duk wannan
abubuwan ba shi ne yasa bata tunanin Housemate dinta ba, babu ranan da zai zo
ya fadi bata yi tunaninsa ba, wani lkcn har da kukanta ta rasa dalilin hakan,
zuwa yanxu kam ta ma hakura ta dena masa magana ta WhatsApp din tana ganin
kamar takurasa take maganar da take masa duba da yanda yake amsa mata kamar
baya so, tana bude kofar apartment din bayan ta sauka downstairs taga ledojin
dake ajiye bakin kofar, sai kuma ta kalli garage ta gan sa zaune cikin motarsa,
sai da ta fara shiga da ledojin parlor sannan ta fito ta nufi gun motarsa tana
kallonsa ta gaishesa, ya bude motar ya sauka ya amsa without looking at her ya
kulle motarsa, sai kuma taga ya nufi lyft din da ke jiran sa, tana tsaye tana
kallo har ya shiga sannan ta juya ta koma apartment dinta ta kulle kofar da
makulli, kayan shayi ta gani a ledojin da ya kawo mata, gwangwanin madara manya
biyu, milo biyu, kwalayen sugar, Lipton, coffee powder, da kuma chocolate, har
da bread manya uku da cookies iri iri, kilan ya shiga kitchen ne yaga babu
madara shi ne ya siyo mata, kuma lokaci ne bata samu ba tana ta son zuwa taje
tayi shopping din kayan shayin.... Bayan kwana biyu Khaleesat na isa school
Safiyyah dake zaune lecture hall ta dinga mata wani kallo tace "Wai don
Allah baza ki dena yafa manyan mayafan nan ba kina kunyata ni Khaleesat, kin fa
gama wannan kadararren iddan ba wai baki gama ba, ko sau biyu za ki yi masa
iddan ne?" Murmushi kawai Khaleesat tayi tana kallonta tace "Ni na ce
maki na gama?" Safiyyah tace "Ai shi yasa na tambaya ko sau biyu za
kiyi don ina nan ina taya ki lissafi wallahi kin gama, duk na kagu inga kin
fara cin gayu kina zuba zawarcin ki son ranki, ai yanxu kuma ba da bane kin
shiga wani level daban" Khaleesat tace "To bakya lissafi dai dai
kuwa..." Safiyyah tace "Wallahi ina yi sai dai in kece bakya
lissafin" Khaleesat bata tanka ta ba ta nemi waje ta zauna don yanxu wani
sabon gayu Safiyyah ke ji a makarantar ita ga final year student, ko ta zo da
mayafi sai ta saka a jaka tayi ta yawo da hula kawai kamar er Enugu, ko kuma
tayi azababben English dressing ta daura karamin dankwali a kai, ita dai har ta
gaji da yi mata magana ta zuba mata ido, a tare suka koma apartment din
Khaleesat ranan don danwake Safiyyah tace zata masu, sai kusan yamma likis
Safiyyah ta bar gidan shi ma Mustapha ne ya isheta da kira, Khaleesat na
kitchen ta gama wanke duk Utensils din da Safiyyah taki wanke mata tana goge
gogen kitchen din taji an bude kofar apartment din, dama tasan dole zai zo tun
da taga ya mance charger dinsa a parlor alamar da taje school ya zo apartment
din daxu, a hankali take wanke hannunta a pampon kitchen din trying to be sure
of what she is perceiving, gently tayi patting hannunta jikin towel din kitchen
din tana goge ruwan hannunta, sai kuma ta juya, sai da numfashinta ya tsaya for
some seconds tsabar yanda gabanta ya fadi, yana jingine jikin bango kusa da
kofar shiga kitchen din ya rungume hannu yana kallonta, ta sunkuyar da kanta,
sai kuma ta nufi kofar kitchen din zata fita zuwa parlor, hannunta ya kamo yana
kallonta with smile on his face, bata san sanda ta fashe da kuka ba zata kwace
hannunta ya jawota kusa da shi murya can kasa yace "Halysaah" Hawaye
kawai ke zuba idonta ta kasa kallonsa, slowly ya rungumota jikinsa murya can
kasa yace "I am sorry" Bude kofar parlon aka yi, Jay yayi saurin saketa
amma tuni Ajay ya shigo, sau daya ya kallesu sai kuma ya sauke idonsa ya tafi
ya dau charger dinsa ya juya ya fita daga parlon....
Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u
send ur evidence of payment 07087865788 ππ»,
it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar
hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500*
[23/07/2025, 1:50:42 PM]
Khaleesat Haiydar π ✍️:
https://chat.whatsapp.com/I5vo38MH2jH8pDvzVF0Q4w
Khaleesat ta bi Jay da kallo ganin ya nufi parlor, kana
ganinsa zaka gane shi ma bai so abinda yayi ba don bai yarda ya sake hada ido
da ita ba, kamar bai san sanda ma yayi hakan ba, ganin ya zauna a parlon ta
sauke idonta daga kallonsa, sai kuma ta juya ta koma kitchen, Jay yayi dialing
number AJ amma har ya katse bai yi picking ba, bai yi zaton zai shigo parlon ba
don har yana ce masa kar ya bata masa lokaci, ya mike ya tafi window din parlon
yana duba garage amma sai yaga ya tafi don babu motarsa a garage din, komawa
yayi ya zauna ya cire face cap dinsa, Khaleesat na fitowa kitchen ya maida face
cap din without raising his head, ita dai kanta a kasa ta karaso parlon tana
rike da bottle water da glass cup ta duka gabansa ta ajiye masa, still not
looking at him a hankali tace "Sannu da zuwa" Sai a sannan ya Ιan kalleta, ganin ba kallonsa take ba with calm in
his voice yace "How are you Halysaah?" Cikin sanyin murya tace
"Alhamdulillah, ya hanya?" Yace "Cool" Tana wasa da fingers
dinta tace "Yaushe ka dawo?" Har sannan bai cire idonsa a kanta ba
yace "Not less than an hour ago Housemate" A hankali tace "Ya su
Mama da mutanen gida?" Yace "They are all good Halysaah, ya karatu?
In few weeks time za ku fara Spring semester exams ko?" Ta gyada masa kai,
shi dai kallonta kawai yake, can yace "How is Safiyyah?" Ta kwantar
da kanta saman gwiwowinta har sannan tana jin kamshin turarensa na tashi a
jikinta tace "She left not long ago" Sai kuma ta daga kai ta kallesa,
sauke idonsa yayi daga kallonta, ita ma ta sunkuyar da kai tace "What
should i make for you? Daxu danwake Sophie tayi mana and it's finished, should
i make you pasta or rice?" Yace "No don't worry Housemate, Ajay made
some food for me back home" Ta Ιan bude ido
tana kallonsa tace "Can he cook?" Kawai yayi murmushi wanda iyakarsa
lips bai bata amsa ba, sai kuma ya nuna mata trolley din da ya shigo da shi
parlon yace "I got you some stuffs, hope you will love it" Shiru tayi
tana kallon akwatin, yace "Check them" Ta sauke idonta sai kuma ta
mike ta bude akwatin, tsadaddun Abaya ta fara cin karo da tana bude akwatin, ta
daga kai ta kallesa suka hada ido ya sakar mata murmushi, sauke idonta tayi ta
rufe akwatin kawai, cikin sanyin murya tace "Thank you soo much, Allah ya
saka da alkhairi, Allah ya kara budi" Yace "Ameen Halysaah"
Still bata dago kanta ba a hankali tace "And i also want to appreciate you
for what you did to my parent, Allah Ubangiji ya sa kafi haka, Allah ya biya
maka duk bukatun ka na alkhairi...." Bai tanka ta ba yana kallon agogon
wrist dinsa ganin bakwai saura yace "I will take my leave now Housemate,
it's late already" Ita dai bata ce komai don sai taji babu dadi da yace
zai tafi, ya mike yana kallonta yace "Kina da lectures gobe ne?" A
hankali tace "Sai karfe daya na rana" Yace "Ohk, i will come
before then in sha Allah, Aunty Farida ta bada sako a kawo maki, yana mota kuma
Ajay ya tafi da motar" Ita sai a sannan ma ta tuna ashe Ajay ya shigo
gidan fa, ta kallesa tace "Ohk, but how are you going back home tunda ya
tafi da motar? Kayi order din Uber ne?" Jay yace "Ohh, na ma
manta" Komawa yayi ya zauna yana danna wayarsa yace "Let me order the
ride now" Ita dai tayi shiru tana kallonsa babu ko kiftawa, har ya gama
order din ya daga kai suka hada ido, sunkuyar da kanta tayi tana jan yatsunta
tace "Toh baza kayi sallah ba kafin ride din ya karaso?" Yace
"Ohk bari in yi alwala" Mikewa yayi ya nufi bandakin dake parlon, ita
ma ta tashi ta tafi sama dauko masa darduma, bayan Jay ya idar da sallah
Khaleesat na kallonsa daga bayan kujeran da take tsaye tace "Or should i
make you tea?" Yace "My ride is waiting Outside Housemate" Ta
gyada masa kai kawai, tana biye da shi a baya har suka fita daga apartment din,
ta rakasa har gun Lyft din dake jiransa, yana kallonta kafin ya shiga motar yace
"Sai na zo gobe, take care of ur self" Ta gyada masa kai don har
cikin ranta take jin da ma kar ya tafi, sai yanxu ta kara tabbatar da irin
missing dinsa da tayi, memories dinsu tare na old apartment dinta ya dinga dawo
mata a kai, and she misses every bit of those moment, she wish it's gonna
happen again, a hankali ta juya bayan ya shiga Lyft din tana tafiya kamar mara
lafiya ta koma apartment dinta ta kulle kofar. Jay na komawa gida ya bude kofa
parlor ya tarar da Legend zaune bakin kofar alamar shi yake ta jira, tun da ya
dawo gidan daxu bayan Ajay ya daukosa a airport Legend ke ta tsalle kansa yana
haushi kamar zai rungumosa wanda hakan ke nuni da yayi missing dinsa ba kadan
ba kuma ya bi sa har daki yana wagging tail dinsa yana kada kai alamar farin
ciki ya nemi waje ya zauna a dakin, kafin su fita daxu kuwa sai da Jay ya
kullesa a Cage dinsa don bin sa ya so yi yana ta haushi, Jay ya kalli Ajay dake
zaune parlorn yana danna wayarsa ko dago kai bai yi ba, dukawa Jay yayi gaban
Legend yana patting kansa ya bude steak din da ya siyo masa a hanya ya ajiye
masa a pack din sannan karen ya kyalesa ya maida hankali kan Steak din, Jay ya
mike ya karasa cikin parlon yana kallon Ajay yace "Didn't you see my
call?" Ba tare da Ajay ya kallesa ba yace "I didn't" Jay bai
sake ce masa komai ba ya nufi kitchen, bayan wasu yan mintoci ya fito yana
kallon Ajay yace "Where is the food you said you made?" Still not
looking at him Ajay yace "Nayi zaton can zaka kwana ae, i gave all the
food to the workers" Kallonsa kawai Jay yake, can ya juya ya koma kitchen
din to make a cup of tea for him self, ko kafin ya fito kitchen din Ajay ya bar
parlon. Washegari wajen karfe sha daya Khaleesat ta sauko downstairs jin ana
danna bell, bayan ta tambayi waye ta bude kofar parlon, gaishesa tayi tana
kallonsa, ya amsa da murmushi, zata amshi ledan hannunsa yace "Don't worry
Halysaah" Juyawa tayi ta koma cikin parlon, ya bi bayanta, bayan ya ajiye
ledan yana kallonta yace "Sakon Aunty Farida da tace a kawo maki"
Khaleesat ta karasa ta dau ledan ta kallesa tace "Thank you so much"
Kitchen ta tafi da shi ta duba taga cin cin ne me yawa aka yi packaging sai
alkaki da dublan, a wani ledan kuma ta ga kayan kamshi na dafa shayi, sai
flour, kuka da kanwa, da dakakken yaji me yawa, tana gani ta gane saboda
danwake aka aiko mata, Ιan murmushi
tayi sai kuma ta dau take away a kitchen ta dibi cin cin din da su alkaki ta
saka a wani ledan ta dawo parlor da shi, dukawa tayi gefensa da ledan, yana
kallonta yace "What's that?" Tace "Cin cin ne da alkaki da Aunty
Farida ta bada a kawo, i fetch some for you" Ya Ιan
bude ido yace "No, ta bamu namu ni da Ajay, it's at home wannan naki
ne" Ta wani kallesa tace "Ban yarda ba" Yace "I am serious,
har da tea spice da grounded pepper duk ta bamu" Khaleesat tayi murmushi
tace "To na yarda" Mikewa tayi ta maida cin cin din kitchen, sannan
ta fito tace "I made you some food in kawo maka yanxu?" Yace "I
had breakfast before leaving home Halysaah" Ζata
fuska tayi tana kallonsa, yayi murmushi ya sauke idonsa yace "Ohk... amma
kadan zaki zubo min ba da yawa ba" Juyawa tayi ta koma kitchen din, ba a
dau lokaci ba ta kawo masa shinkafa da stew din kaza da tayi, yana kallon
abincin yace "Wannan ai yayi yawa" Tace "Eat and remain"
Shi dai murmushi kawai yayi, ta koma kitchen ta dauko masa ruwa da glass cup ta
ajiye masa, yace "Karfe nawa kika ce kina da lectures?" Tace
"Karfe daya" Yace "Ohk to ki shirya idan na gama sai inyi
dropping dinki nima zan shiga school din" Tace "Ohk, nagode"
Sama ta wuce ta bar sa a parlon. Ko da Khaleesat ta sauko downstairs wajen
karfe sha biyu da rabi ta gansa kwance kan 3 sitter idonsa a lumshe, murmushi
tayi cause this is one of the part she misses so much about him, ta dafa bayan
kujeran a hankali ta duka tana kallon innocent face dinsa, zagawa tayi tana
tafiya a hankali ta tafi gun Vase din artificial flower dake parlon ta zari
daya ta dawo gabansa ta duka dai dai fuskarsa ta kai flower din a hankali
moving it back and forth his face, cikin bacci ya kai hannu fuskarsa da sauri
ya kauda kai, hakan bai sa ta dena abinda take ba, yana kokarin mikewa zaune ya
kusa cin karo da ita banda tayi saurin matsawa baya, ta dinga kyalkyala dariya
tana kallonsa, murmushi yayi ya jinginar da kansa da kujeran yace "See
this girl, wa yace maki ban ga sanda kika sauko ba, i just pretended i was
sleeping" Tana dariya tace "Wallahi baka gan ni ba, you were
sleeping" Shafa kansa yayi still smiling ya mike tsaye yace "I am
waiting for you at the garage, amma ni dai nasan ba bacci nake ba i was just
meditating..." Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo tana murmushi, ta
kalli wayarsa da ya bari kan kujera without noticing, sai da ta jira har ya
fita daga parlon sannan ta duka kusa da kujeran ta dau wayar taga babu lock,
miss calls ta gani guda hudu na wani number da aka yi saving with Hadiyah tare
da text message dinta, call logs din duk yawanci miss calls dinta ne, amma kuma
yana picking wasu call din nata, Khaleesat ta dinga kallon number, can ta shiga
cikin message din da ta turo masa, "You should have at least pick, just
wanted to know if you've arrived safely" shine content din message din, A
hankali Khaleesat ke strolling text messages din taga inda Hadiyah ta turo masa
"I love you so much Baby, and i want to spend forever with you" Da
bai mayar mata reply ba sai ta sake tura masa uhmm, sai ya mata reply da
"Love yah 2" Fita daga messages din Khaleesat tayi without going any
further, tana kokarin clearing duk inda ta shiga don kar ya gani kawai taga
kamar hoton da suka yi a park da shi among many other apps da ya bude a ranan,
tayi tapping zata shiga hoton kawai ya nuna mata wajen is locked, ta fi minti
biyu durkushe a wajen rike da wayar don gaba daya jikinta yayi sanyi ko motsin
kirki ta kasa, can dai ta mike a hankali ta dau jakar laptop dinta ta nufi kofa
walking slowly, kafin ta bude kofar ya riga ta budewa har sai da ya ci karo da
ita, komawa baya yayi da sauri, ita kuma ta dafe kanta, Ya shigo parlon yana
kallonta da damuwa yace "Hope u are not hurt? I am sorry i should have
knock" Ta girgiza masa kai kawai ba tare da ta kallesa ba, yace "Are
you sure you are okay Housemate?" Zame hannunta tayi daga fuskarta tana
kallonsa, a hankali yace "Sorry Halysaah, i forgot my phone shi ne na dawo
dauka..." Mika masa wayar tayi ya amsa yana kallonta, ita dai ta sauke
idonta, bude mata kofar yayi ta fara fita sannan shima ya fita, ta mika masa
makullin apartment din ya amsa ya kulle sannan suka nufi motarsa har a lkcn bai
daina waigawa yana kallonta ba to be sure she is okay har suka iso garage, ita
dai bata sake yarda ta kallesa ba, ya bude mata gaban motar yana kallonta, Ιan murmushin karfin hali tayi still not looking at
him murya can kasa tace "Thank you" Sannan ta shiga motar, tana shiga
ya daga mata veil dinta da ya fito waje ya daura kan cinyarta yana kallonta,
sae a sannan ta daga manyan idanuwanta ta kallesa ya sakar mata murmushi, ita
ma murmushin tayi har sai da dimple dinta ya lotsa ta sunkuyar da kai tana wasa
da gefen veil dinta, ya kulle motar ya zaga ya shiga driver seat yayi igniting
motar, bayan sun yi nisa ya Ιan kalleta
murya can kasa yace "Are you sure you are okay Halysaah?" Khaleesat
ta Ιan bude ido tace
"Sure..." Don tabbatar masa da hakan tayi kokarin creating
conversation tace "Ya Junaid fa?" Jay ya maida dubansa kan titin
gabansa yace "Ba kuna magana da shi ta waya ba" A hankali Khaleesat
tace "A'a, sai if there is something important" Without looking at
her yace "Something important like?" Tace "May be idan ya kawo
min abu apartment" Yace "Abu kamar me?" Khaleesat ta juya ta
kallesa tace "Grocery shopping" Jay ya gyada mata kai yana ci gaba da
driving dinsa, har suka isa school babu wanda ya sake cewa komai a cikinsu, ita
kam Khaleesat ta tafi duniyar tunanin da take.....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
https://chat.whatsapp.com/I5vo38MH2jH8pDvzVF0Q4w
Bayan Jay yayi parking a school din ya juya yana kallonta,
zata bude motar ta sauka yayi kasa da murya yace "Halysaah" Ta juya
tana kallonsa, yace "What happened? Why the sudden change of mood?"
Khaleesat ta Ιan bude ido, sai kuma tayi
murmushin karfin hali ta girgiza kai tace "Ba komai fa" Yace
"Are you sure?" Ta sauke idonta tace "Sure" Yace
"Yaushe za ku gama lectures din?" Tace "Lecture daya kawai za mu
yi" Yace "Zuwa 3pm kun gama kenan?" Ta gyada masa kai, yace
"Ohk, i will pick you then" A hankali tace "To Nagode"
Murmushi kawai yayi mata yana kallon idonta, ta bude motar ta sauka ya bi ta da
kallo, sai kuma ya dau wayarsa, Lkci daya ya gane ta shigar masa wayar cause
yasan yana da miss calls din Hadeeyah da message a gaban screen, swiping yayi
ya bude wayar yaga alamar ta shiga har cikin message din bayan call logs dinsa,
jinginar da kansa yayi a hankali jikin kujeran motar with different thoughts
running his mind. Har Khaleesat suka gama lectures bata ga Safiyyah ta shigo
school ba ranan, tana zaune inda suka saba zama tana ta kokarin kiran Safiyyah
tun daxu amma numberta baya shiga, lkci lkci take bin inda take zaune da kallo
as if wanting to figure out something, at some point she became confuse and
afraid at the same time don wasu memories that are not welcome in her heart ne
suka hau dawo mata kai, Student sai harkan gabansu suke a vicinity din babu ma
wanda yake kallon inda take zaune, tana kokarin tashi ta bar wajen kawai sai ga
kiran Safiyyah ya shigo wayarta, Khaleesat ta koma ta zauna tayi picking call
din ta kai wayar kunne, Safiyyah tace "Kin ga ban shigo school ba shine ko
ki kirani matar nan?" Khaleesat tace "I have been trying ur line tun
daxu baya shiga, hope you are fine? Why are you not in school today?"
Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Ke da ba sai dai in kira ki ince
maki Surayya ta rasu yau ba" Khaleesat tace "Me ya faru?"
Safiyyah tace "Ni dai wallahi har na fidda rai da ita in gaya maki
kawata" Khaleesat ta hade rai tace "Don Allah ki gaya min me ya same
ta?" Safiyyah tace "To wani azababben zazzaΙi
ne ya damke ta har tana suma, sai ga Surayyan ki har da kamo hannuna yau tana
neman agaji duk ta ruda ni, yanxu haka tana can an bata gado a asibiti, ni kuma
ina gida saboda Aslam shi yasa ma ban shigo school yau ba, Aslam din da ko kusa
da ni bata bari ya zo, kinga in ni mayya ce ai yau da babu abinda zai hanani
cinye mata Ιa" Khaleesat tace
"To Allah ya sauwake, Allah ya bata lafiya, wani asibitin ne?"
Safiyyah tace "Oho ni dai ba an bar ni da baby sitting ba, Housemate dinki
fa? Wallahi naji haushi da bazan samu zuwa in masa sannu da zuwa ba, ai sai ya
zata ma walakanci ne ya dawo naki zuwa" Khaleesat tayi murmushin da bata
yi niyya ba tace "Ni dai sai anjima, har mun gama lectures din"
Safiyyah tace "Don Allah ni dai in ya je apartment din naki anjima ki
kirani ki gaya min, ko goyo Aslam ne sai inyi in taho, kin ga ba dadi ace ban
masa sannu da zuwa ba har zuwa yanxu" Khaleesat ta dake don bata son tayi
dariya tace "Till we speak Sophie, sai anjima...." Safiyyah tace
"Ke dalla ba cewa zan yi ina son sa ba, kowa yasan Housemate ai naki ne
duk wanda yace zai maku shisshigi ma ai sai dai ya mutu, kilan ma har ya
tambayi baba aurenki baba kuma ya basa bamu sani ba" Bude baki Khaleesat
tayi a bit shock, don she never saw those words coming from Safiyyah, Safiyyah
tayi dariya tace "Atoh, mu ba mu ki gobe a daura auren ba ma wallahi,
Uztax Ajay sai ya bada sadakin yayansa, shi kuma Housemate kawai ya tare a nan
apartment din naki Ajay da Salem su rakasa, in kayan mata ne sai in debo maki
na Surayyah don a kitchen ma take jerasu don in gani, Ghana must go dinsu ake
aiko mata daga gida, kin ga kawai sai in debo maki kina da gwangwanin madara da
yoghurt abun ki, yanda dai zaki dawo babu banbanci da warce bata taΙa aure ba" Khaleesat bata san sanda ta katse
wayarta ba ta kife a kafarta kamar warce taji wani mugun abu daga bakin
Safiyyah, tafi minti goma zaune a yanda take kamar an dasa ta, taji wayar
hannunta ya fara vibrate, a hankali ta juya wayar taga number Housemate, at
first ta kasa daga call din nasa, sai da taga ya kusa katsewa sannan tayi
picking ta kai kunne tayi shiru kamar munafuka, daga daya bangaren yace
"Are you done Halysaah?" Ta gyada masa kai tace "Um" Yace
"Ohk, i am waiting for you" A hankali tace "To" Sannan ta
katse wayar ta mayar cikin jakarta, ta mike ta fara tafiya zuwa inda zata
samesa. Har ta shiga motarsa bata yarda ta hada ido da shi ba, shi dai kallonta
kawai yake, Bayan ta kulle motar a hankali tace "Ina yini" Calmly
yace "Lafiya lau Halysaah, ya lectures din?" Tace "Alhamdulillah"
Yace "Frnd din ki ta tafi ne ita?" Khaleesat ta girgiza masa kai tace
"Bata zo schl yau ba, matar brother dinta bata da lafiya" Yace
"Allah ya bata lafiya" Daga haka ya fara driving zuwa gidanta, sai da
suka kusa apartment din nata ya kalleta speaking slowly yace "Do you mind
going out for dinner with me later Housemate?" Sai a sannan Khaleesat ta
dan kallesa, suna hada ido ta sauke idonta a hankali tace "Alright"
Yayi mata murmushi ya ci gaba da driving dinsa, Yana parking gaban apartment
dinta ba tare da ta kallesa ba tace "Thank you so much" Yana kallonta
yace "You are welcome Housemate..." Ta bude motar ta sauka sannan ta Ιan kallesa suka hada ido, murmushi tayi ta daga masa
hannu sannan ta juya ta nufi apartment dinta, shi dai ya bi ta da kallo har ta
shiga. Tun da Khaleesat ta ga karfe bakwai na yamma yayi ta zama tense, ta rasa
dalilin da yanxu kuma take jin nauyin Housemate din nata sosai, duk da ba yau
ta saba fita dinner da shi ba, amma yau gaba daya sai take jin wani nauyi na
musamman, har lkcn kuma bata shirya ba tana dai zaune saman darduma after
praying, karfe bakwai da minti goma kiransa ya shigo wayarta, ta jawo wayar a
hankali tayi picking ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren yace "I
am on my way now Halysaah" A hankali tace "Ohk, Allah ya kawo ka
lafiya" Sai bayan da ta ajiye wayar ta mike ta fara duba kayan da zata sa,
har ya iso apartment din nata after 15 minutes bata gama shiryawa ba, sai da ya
jirata for another 10 minutes sannan ta fito, ta gansa tsaye jikin motarsa ya
rungume hannu yana jiranta, sauke idonta tayi har ta karaso inda yake tsaye,
yayi mata murmushi yana kallonta ya bude mata front seat, ita dai taki yarda su
hada ido ta shiga motar, yana kallonta yace "Housemate" Sai a sannan
ta daga idanuwanta ta kallesa, kamar me rada yace "You look cute"
Rufe fuskarta tayi da veil dinta tana murmushi, ya kulle motar ya zaga ya shiga
driver seat. The ride was silent, tunanin da take yi daban a ranta shi ma haka,
bayan sun isa wajen cin abincin after offering her a seat ta fara zama sannan
shi ma ya zauna opposite dinta, ya dau menu din eatry din yana mika mata yana
kallonta, ta sauke idonta tace "I am okay with anything u order" Yace
"Are you sure? Ke da baki son abincin turawa ni kuma nafi son sa" Murmushi
tayi tace "Zan koya ci" A hankali yace "Really?" Ita dai
bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, yayi masu order din abincin irin wanda
yasan she can cope with, bayan an kawo abincin ta dau lemonade dinta tana
sipping a hankali, kamar ance ta daga kai taga kallonta yake, murmushi yayi ya
dau nasa lemonade din yana sha yace "Naga kin yi kyau ne sosai"
Khaleesat ta kasa kallonsa tace "Kai ma haka" Yace "Ni da baki
kalla ba ta yaya kika san haka" Tayi murmushi ta daga idanuwanta tana
kallonsa, kashe mata ido yayi slowly, ta boye fuskarta tana dariya a hankali, A
haka suka fara cin abincin, amma ta kasa sakin jiki ta ci, shi kuma sai ya
tsallake nasa abincin ya dau na gabanta, ta tallabi chin dinta tace "Ko in
hada maka dukka ne?" Yace "Ke ma zaki iya daukan wanda kika ga yayi
maki a nawa ai, it's called sharing..." Ta wani kallesa, sannan ta ci gaba
da cin abincinta a hankali, har ta mance rabon da ta jita so happy and lively
irin haka, gani tayi yayi exchanging abincinsa da nata, ta daga idanuwanta ta
kallesa bata dai ce komai ba tayi murmushi, ya buda ido yace "Naji naki
yafi dadi ne" Yana fara cin nata sai kuma taga ya mike ya dawo kusa da ita
ya zauna da abincin yana kallonta yace "I think i can see the food more
clearly from here..." Khaleesat dai kallonsa kawai take don gaba daya
kamshin turarensa ya cika ta, ya bude pizza dake kan table din, kawai gani tayi
ya dau slice daya ya kai mata baki yana kallonta babu ko kiftawa yace
"Here...." She couldn't look at him in the eyes, at the same time she
was a bit shock at his action, murya can kasa taji yace "Take
Halysaah...." A hankali ta bude bakin ya bata pizzan, duk wani abu da yaga
ta ki ci sai ya dauka ya kai mata baki, she was so shy, daga karshe ta girgiza
masa kai cikin sanyin murya tace "I am full" Yana kallonta yace
"Are you sure?" Ta gyada masa kai ta dau lemonade dinta tana sha, shi
dai kallonta kawai yake, ta mika masa sauran lemonade din don shi ya shanye
nasa, yayi murmushi ya amsa yayi sipping kadan ya ajiye sauran, after some
seconds yace "I will like to discuss something with you Housemate,
something that's bothering me, may be zaki bani shawara..." Khaleesat ta kallesa a hankali tace
"Ohk...." Amma haka kawai taji gabanta yana faduwa, Calmly ya fara
magana yace "You know i am an only child right?" Khaleesat tayi shiru
tana kallonsa don bata san da haka ba, yayi murmushi yace "Yeah, my dad
was late before i was even brought to the world" Sosai jikin Khaleesat
yayi sanyi tana kallonsa, ya ci gaba yace "Junaid's Dad was my father's
younger brother, and he inherited the throne after my father's demise who was
then a king...." Khaleesat ta sauke idanuwanta cikin sanyin murya tace
"Allah Ubangiji yayi masa rahama, ya gafarta masa" Jay yace
"Ameen, i was partially raise together with Ajay, don Mamina couldn't let
go of me gaba daya, so lokaci lokaci nake zuwa emirate din, wani lkcn inyi hutu
a can, Ajay also lost his Mom when he was just 3 years old" Khaleesat ta
dinga kallon Jay ta kasa cewa komai, Jay ya Ιan
yi murmushi yace "Yeah, it's still not easy for him till date, but
Alhamdulillah on his behalf" A hankali Khaleesat tace "Allah ya
gafarta mata, Allah ya sa ta huta" Jay yace "Ameen, so now kinsan me
yake faruwa Housemate?" Khaleesat ta girgiza masa kai, yace "I have
this cousin sister Hadiyah...." Sosai gaban Khaleesat ya fadi don tsaf ta
haddace sunan nan a zuciyarta, saura kadan tace masa ma bata son zancen amma ta
dake zuciyarta tunda shawara yace yake son ta basa, Ιan
farin cikin da take ciki na wnn moment din taji ya fara fading gradually, Jay
ya Ιan yi shiru sai kuma ya daga
kai ya kalleta directly in the eyes yace "A gida ake son hada mu aure da
ita, Mamina, Mom dinta, my late father's senior sisters, infact all the family
members, ya kai ya kawo har sun kai maganar gaban Mai martaba yanxu, kinsan
mata idan suna son abu... At first Ajay aka so hadata da and he bluntly turn
down the offer..." Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, A hankali
yana kallonta yace "I think all this explanation isn't necessary Halysaah,
kawai a takaice i want to refuse the offer too nan ba da jimawa ba for reasons
known to me alone, but i don't know where to start from Halysaah, I don't know
how everyone is going to take this, but deep down i don't think Mamina zata
tilasta ni aka abinda bana so, she is always after my happiness and comfort,
nasan bazata min dole ba...." Khaleesat was mute, don bata ma san me zata
ce ba, amma jikinta kan yayi sanyi sosai ba kadan ba, ji tayi ya kamo hannunta
murya can kasa yace "Kin yi shiru Housemate, say something pls" Kasa
kallonsa tayi, idonta a kan hannunsa dake nata tana jin heartbeat dinta na
karuwa, a hankali ta zame hannunta daga nasa tana murmushin karfin hali cikin
sanyin murya tace "Amma baka tunanin hakan da zaka yi zai ja issues a
family din naku?" Jay yace "I don't care, as far as Mami is in
support of me i really don't care ko me za ace, idan naga ran Mami ya bace da
decision dina shine kadai hankalina zai tashi, cause i love my mom so
dearly...." Khaleesat still couldn't look at him in the eyes, after some
seconds a hankali tace "Menene yayi triggering din canza decision da kake
kokarin yi all of a sudden, bayan a farko ka riga kayi masu accepting zaka
aureta?" Jay ya Ιan yi
murmushi yana kallonta, kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Look at me
in the eyes Halysaah" Khaleesat felt like she is melting cause his
intonation was something else, gaba daya ta kasa kallonsa, underneath his
breathe yace "Look at me Halysaah" Da kyar tayi karfin halin daga
manyan idanuwanta ta saka cikin nasa....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah*
Ur evidence 07087865788
https://chat.whatsapp.com/I5vo38MH2jH8pDvzVF0Q4w
Tun kan Jay yace komai Khaleesat ta kasa ci gaba da kallonsa
ta sunkuyar da kanta tana jin kamar ta nutse a wajen, bata taΙa jin tana kunyarsa ba kamar wannan lokacin, ta kasa
gane wani irin kallo ne wannan yake mata da yake sa ta kara jin kunyarsa, shi
ko bai fasa kallonta ba yana admiring kunyanta, she became so uncomfortable
lokaci daya a wajen, taji Ιan composure
din nata na neman guduwa ya bar ta, yayi kasa da murya yace
"Halysaah..." Bata yarda ta sake kallonsa ba, speaking with calmness
yace "Ban taΙa sanin akwai lokacin da zai
zo inji wata daban nake so ba Hadiyah ba, i never saw that coming, and i can't
help it...." Shiru Khaleesat tayi har sannan taki yarda su hada ido, a
hankali yace "Kin yi shiru Housemate" Tayi murmushin karfin hali, sai
kuma ta fara kame kame tace "To ai ni ban ma san me zan ce ba, the issue
is too big for me to give out any advice, it's ur family matter, or better
still kawai kayi addu'an abinda yafi zama alkhairi a gare ka, just pray about
it, pray for the best...." Yace "Is that all u have to say, ke da ake
neman shawara a wajen ki" Tayi shiru for the second time, sai kuma ta samu
kanta da cewa "To idan zaka iya masu adalci sai ka hadasu duk biyun ai ba
haramun bane" Bata san sanda furucin ya fito bakinta ba, sai kuma ta daga
kai ta kallesa taga kallonta yake babu ko kiftawa, sunkuyar da kanta tayi da
sauri, a hankali yace "Haka kike ganin yafi?" A takaice tace
"Nima ban sani ba" Yace "But you suggested it" Kin cewa
komai tayi tana wasa da edge din veil dinta, shiru Jay yayi kamar wanda ya fada
duniyar tunani, after a while Khaleesat ta daga kai ta kallesa, suna hada ido
ta dauke nata idon, slowly yace "Ohk then, i will think about that,
but..." Kafin ya karasa Khaleesat ta dau handbag dinta tace "I think
hadari ne a garin, kar ruwa ya sauko" Yace "Yea akwai hadari, i can
perceive it too" Mikewa tayi without looking at him, yace "To saurin
me kike sai kace a kafa zaki koma gidan" Ta Ιan
yi yake tace "Gobe fa akwai jarabawan da za mu yi kuma ko karatu ban yi
ba" yace "Ai ke Genuis ce...." Khaleesat dai bata ce komai ba
amma taki komawa ta zauna, a hankali yace "Kin kawo Suggestion kuma kina
fushi da Suggestion din naki Housemate" Khaleesat ta zaro ido tana
kallonsa, bata san sanda tace "Ban gane ba" Murmushi yayi ya mike
yace "To mu je kar ruwa ya sauko" Sosai ta sha jinin jikinta da
furucinsa ta kasa motsawa a inda take tsaye har ya wuce ta, after clearing the
bills ya dawo kusa da ita yana kallonta yace "Let go Housemate, ko baki
koshi bane let's place another other" Ta wani kallesa, dariya yayi yace
"To mu je in ba dai wani abincin kike son ci ba" Kamar warce aka zare
ma laka take biye da shi a baya tana tafiya a hankali har zuwa gun motarsa, ko
da suka fito an fara yayyafi amma ba da yawa ba, ya bude mata front seat bayan
ta shiga ya kulle motar ya zaga ya shiga mazaunin driver, yana fara driving
wayarsa ya fara vibrate, Khaleesat ta kalli screen din wayar, Hadiyah ta gani,
ta dauke idonta, ya kai hannu yayi silencing wayar gaba daya sannan ya kifar ta
yanda ma bazai dinga ganin hasken wayar ba, ita dai bata sake kallon inda wayar
yake ba, the ride back to her apartment was silent, ga yayyafin da ake sosai,
ko wannensu da tunanin da yake a ransa, ita kam gaba daya farin cikin da take
ciki as at 15 mins ago duk ya bace kamar bata yi sa ba, kawai taji zuciyarta ya
tunkushe babu abinda yake mata dadi a rai, sai da suka kusa gida ya Ιan kalleta a hankali yace "Amma idan kun gama
Exams za ki je Nigeria ko?" Khaleesat tayi shiru, ita har tana da choice
din cewa zata je Nigeria ko bazata je ba, abinda ba ita zata ma kanta kudin
jirgin ba, murya can kasa taji yace "Kin yi shiru Housemate..."
Murmushi tayi ta buda masa hannu alamar ita ma bata sani ba, yace "Za ki
je in sha Allah, ko 2 weeks sai kiyi kafin ayi resuming summer and final semester din ku...." A
hankali tace "To Allah ya kai mu" Yace "Ameen" Ya kalli
agogon wrist dinsa dake nuna takwas da rabi yace "Idan nayi dropping din
ki zan je wajen abokina ne da ya shigo garin nan daxu, he will be leaving early
tomorrow, ko mu je dake ku gaisa? He is looking forward to meet you"
Khaleesat ta girgiza masa kai a hankali tace "Ruwa ake yi, kuma ina son
zan yi karatu" Shiru yayi idonsa akan titi, can yace "Ohk then, may
be some other time sai ku gaisa, he is my very good frnd, a Nigerian also"
Khaleesat dai bata ce komai ba, duk ta kagu ta ganta a apartment dinta taje
tayi sallah ta kwanta ko zata samu nutsuwan da ta rasa ga zuciyarta dake a
tunkushe, dai dai garage din apartment din nata yayi parking yana kallonta yace
"But cikin ruwan nan zaki fita Halysaah, kar ruwa ya taΙa ki kiyi mura" Khaleesat ta kirkiri murmushi
tace "The rain is not heavy ai" Yace "Give me the key idan na
bude sai ki sauko..." Bude jakarta tayi ta ciro makullin ta mika masa ya
amsa yana kallonta, sai kuma ya sauke ido yace "Before then i have
something little for you" Ita dai kallonsa kawai take har ya dauko wani
karamin box a nan cikin motar ya bude yana mika mata, kallon zoben dake cikin
box din yana ta kyalli kawai take, sai kuma ta kallesa taga kallonta yake, yayi
murmushi yace "Haska da wayarki ki gani, i hope you will love it" A
hankali Khaleesat ta ciro wayarta a handbag dinta ta ajiye handbag din gefe,
sannan ta kunna fitila tana haska siririn diamond ring din dake wani kyalli,
sauke idonta tayi ta ma rasa me zata ce, ya ajiye mata a cinya sannan ya bude
motar ya fita cikin ruwan, da ido ta bi sa har ya isa kofar apartment din ya
bude, jiki a sanyaye ta dau box din zoben ta kashe fitilar wayarta sannan ta
bude motar ta sauka, zuwa sannan ruwan ya fara karfi, yana tsaye bakin kofar
yana jiranta har ta karaso ya mika mata makullin apartment din yana kallonta
yace "Good night Halysaah" Hawaye ya gani idonta, ta amshi makullin
zata yi magana ya daura fingers dinsa a lips dinsa ya girgiza mata kai sannan
ya juya ya koma gun motarsa ta bi sa da kallo tana son ce masa ko zai yi
spending night din a apartment din nata because the rain is getting heavy, amma
tuni ya bude motarsa ya shiga, a hankali ta dinga goge hawayenta, ta shiga
parlon ta kulle kofar ta wuce sama, gefen gado ta zauna ta kife kanta da pillow
wasu hawaye masu zafi na zuba idonta, bata san da ta fashe da kuka ba bayan ta
tuno maganar da yayi mata na Hadiyah, tafi minti goma a haka taji an danna bell
din gidan, mikewa zaune tayi ta kalli wayarta da ke hannunta, dawowa kuma yayi
cikin ruwan nan, sai a sannan ta tuna ta bar Handbag dinta a motarsa, ko jakar
ya kawo mata, ta kalli agogon wayarta dake hannunta, sai kuma ta mike ta bude
kofar dakinta a hankali ta sauko downstairs, sake danna bell din aka yi making it
the 3rd time, ta karasa har bakin kofar ta bude a hankali, kiris ya rage
numfashinta bai dauke ba bayan tayi ido hudu da wanda ke tsaye bakin kofar,
bata gama recovering daga matsanancin shock din da ta shiga ba kawai taga ya
shigo parlon yana kallonta, wani kara tayi duk da babu me jinta saboda ruwan da
ake, ya tura kofar speaking calmly yace "Listen to me Khaleesat" Bata
sake yarda ta hada ido da shi ba tsabar rudewa sai ta nufi kitchen maimakon ta
gudu sama, shi dai ya bi ta da kallo yana tsaye inda yake, sai da ta shiga
kitchen din taga babu makulli jikin kofar, hannunta na rawa ta shiga call log
dinta tana neman number Ajay tayi dialing, don tasan tsayawa kiran Housemate
dinta ma will be a waste of time, he might not even see the call balle yayi
picking, jikinta na rawa ta dinga addu'an Ajay ya daga kiran, rikicewa tayi
ganin sa a kitchen din ya biyo ta, ya karasa har gabanta ya amshe wayar
hannunta yana kallonta ya kashe wayar gaba daya ya ajiye saman cabinet din
kitchen din, cikin sanyin murya yace "Listen to me Khaleesat, i promise
you I am not here to hurt you" Kuka kawai Khaleesat take ta rakube jikin
bango har lkcn jikinta na Ιari tana
kallonsa, he look so lean kamar ba Abdul din da ta sani ba, sai dogon hancinsa
da haske da ya kara, daxu tana zaune department dinsu a schl taji exactly
kamshin turaren da yake using wanda hakan sai da ya sa ta tsorata ta rasa
nutsuwarta, does it mean bibiyanta yake ta yi kenan all this while? How did he
even know her apartment? Ta shiga uku ta lalace, Muryarsa taji a hankali yace
"Kiyi hakuri na shigo maki apartment without permission Khaleesat, i know
it's not right, bani da courage din tare ki a hanya don ban san yanda zaki yi
reacting ba cikin mutane, i have no choice shi yasa har kika gan ni a nan this
late, kiyi hakuri don Allah" Sai a sannan Khaleesat ta samu kwarin gwiwan
hade rai ganin how calm and soft he was speaking to her, cike da karfin hali
tace "Pls i don't want to report you to the cops, ka fita ka bar min
apartment dina tun wuri" A mugun tsorace ta dake take masa maganar,
instead sai taga ya sauke idonsa, a hankali yace "Zan fita, amma kafin nan
ina son kiyi hakuri ba don ni ba kar ki sanar ma bodyguards dinki i badged into
ur house, plss kar ki gaya masu Khaleesat.... Ni ba tashin hankali bane ya kawo
ni i promise you.... nasan you are soft Khaleesat, ke mace ce me raunin zuciya
sannan ke me yafiya ce, i am not using ur good characters to blackmail you
Khaleesat, i am just saying the fact about you, ki dubi girman Allah da
soyayyar da kike yi ma ma'aiki ki yafe min sannan ki tsaya ki saurareni ko na
minti biyar ne...." She was so shock ganin ya duka a gabanta ya sauke
idanuwansa daga kallonta cikin muryarsa da baya fitowa sosai yace "Ki duba
alkhairina gareki ki saurareni ba don halina ba Khaleesat, i am begging you to
pls give me a listening ear, na maki alkawarin ba dadewa zan yi ba zan
fita...." Khaleesat ta dauke idanuwanta daga kallonsa tana jin hawaye na
zuba idonta, alkhairansa da yace ne kawai ke ringing a kanta amma duk da haka ta
dake zuciyarta, cikin rawan murya tace "Ni dai don Allah ka rufa min asiri
ka fita in kulle apartment dina bani da lokacin sauraron ka ko na minti daya
wallahi, i am begging you plss ka fita" Kamar zai mata kuka yace
"Baza ki saurareni ba kenan Khaleesat?" Muryarta na rawa tace
"In saurareka akan me? Bani da lokacin sauraranka, ka tashi ka fita before
it's too late" Cikin sanyin murya yace "To zan fita, amma kiyi hakuri
kar ki gaya masu i am here, i came with a pure intention not otherwise, plss do
not tell them i am here" Duk don ta samu ya fitar mata a gida tace
"Na ji, ka tashi ka tafi" Mikewa yayi ya juya ya nufi kofar kitchen
din ta bi sa da kallo hawaye masu zafi na zuba idonta, sai kuma ta bi bayansa
da sauri don tabbatar da fitan zai yi ko akasin haka, yana sa takalmansa dake
bakin kofar parlon, Khaleesat ta karasa window da sauri ganin haske a labulen
parlon, tana dubawa taga motar Ajay yayi parking a garage, ta juya da sauri ta
kalli Abdul, zuciyarta na bugawa tace "My call went through, kuma gashi ya
xo..." Abdul ya bude labulen dai dai sanda Ajay ya fito daga motar,
kallonta Abdul yayi and she could see the panic in his eyes, ita kanta jikinta
rawa yake don ko kadan bata son ayi wani tashin hankali a gabanta, muryarta na
rawa tace "Ni ban san ta inda zaka fita ba, just go upstairs before he
comes in...." sama ya nufa, within a blink of an eye ta dena hangosa, ta
karasa tsakar parlor da sauri zuciyarta na bugawa ta zauna hawaye na zuba
idonta, dai dai sanda Ajay ya bude kofar parlon, tsaye yayi bakin kofar yana
kallonta, ita dai taki yarda su hada ido da shi wasu hawayen na zuba idonta, ya
karasa cikin parlon still looking at her yace "Why did you call my
line?" Kin cewa komai tayi tana goge sabbin hawayen dake sauko mata, ya
hade rai yace "Kee, baki ji na ne? Me yasa kika kirani?" Muryarta na
rawa tace "Nima ban sani ba" Tana fadin haka ta fashe da kuka sosai
tana kallonsa, ya cire takalmansa going closer to her yace "Ban gane baki
sani ba, What happened?" Tana shesshekan kuka ta bude masa hannu alamar
ita fa bata sani ba, bin parlon ya dinga yi da kallo, nan taji gabanta ya fara
faduwa sosai, cikin rawan murya tace "May be i was just
hallucinating...." Sai kuma ta rakube jikin kujera ta kwantar da kanta
tana wani sabon kukan, shi dai kallonta kawai yake, can ya zauna kan kujera
that is near to her yace "What did you see?" A hankali tace
"Abubuwa da yawa" Ya dinga kallonta kafin yace "Abubuwa kamar
me?" Ta bude masa hannu alamar bata sani ba, yace "Ina wayarki? And
why did you switch off the phone after calling me?" Ta fara kalle kallen
parlon a hankali tace "Nima ban sani ba ai" Yace "Ina kika ajiye
wayar da kika kirani?" Hanyar kitchen ta kalla tayi shiru, ya kalli
kitchen din sannan ya mike ta bi sa da kallo zuciyarta na tsananta bugawa har
ya shiga kitchen din, sai gashi ya fito yana rike da wayarta dake a kashe, tuni
ta lumshe ido da sauri don kar ma su hada ido yayi mata wani tambayar, ya
karasa har gabanta, ita dai idonta na lumshe tana sauke ajiyar zuciya a
hankali, dukawa yayi gabanta ya kai hannu forehead dinta to feel if she is
running temperature, amma yaji temperature dinta is normal, kawai with the way
she is breathing zaka gane a tsorace take, ta bude ido a hankali tana kallonsa,
sai kuma murya can kasa tace "Bacci nake ji" Yace "Why won't you
hallucinate, wani kika ba ma contract din ya dinga maki Azkar din ki?" Ta
sauke idonta bata ce komai ba, mikewa yayi ya koma kan kujera ya zauna yana Ζare ma parlon kallo, a hankali ta mike ta kwanta
saman dogon kujera ta takure waje daya tana jiran taga ya tashi ya tafi, shi
dai Ajay bai ma san wani tunani zai yi ba, ta kirasa yana jin kukanta a
background and before you know it kuma yaji an kashe wayar gaba daya, he tried
reaching her but to no avail, tunani ya fara yi ko tana da jinnu ne, ya sake
juyawa ya kalleta, ita dai idonta a lumshe yake, a haka bacci ya dauketa bata
sani ba. Khaleesat bata yi minti sha biyar tana bacci a kan kujeran ba ta farka
a gigice bayan tayi mafarkin Ajay ya ga Abdul a gidan ya kamasa yayi ta duka,
kawai daga karshe ya harbesa da bindiga, rikicewa tayi bayan ta fado daga kan
kujeran ta dinga nanata "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" jikinta
na rawa, Sai bayan da ta tabbatar mafarki ne ta daga kai har lkcn jikinta na
rawa tana kallon Ajay da ya durkusa gabanta yana tofa mata addu'o'i, jinginar
da kanta tayi jikin kujera tana jin hawaye na zuba idonta, after almost 10
minutes, speaking calmly yace "Ta shi ki tafi sama kiyi alwala ki
kwanta" Make masa kafada tayi tana shesshekan kuka tace "A'a ni tsoro
nake ji, zan kwanta a nan" Tana fadin haka ta mike ta sake kwanciya kan
kujeran, shi dai kallonta yake, tun da bacci ya dauketa yake tsaye jikin window
din parlon yana son tafiya amma bai tafi ba, kuma har lokacin ruwa ake, and
before he know it 15 minutes into her sleep ta farka cikin firgici, Khaleesat
ta dade bata ji irin wannan tsoron dake zuciyarta ba, yanxu idan ya ga Abdul a
gidan nan me zata ce? Ko dai kawai ta gaya masa gaskiya, to amma idan ta gaya
masa kuma ya kamasa da duka har ya aiwatar da abinda ta gani a mafarki ba, Da
tunane tunanen nan wani baccin ya sake awon gaba da ita bata sani ba, cikin
baccin taji an rufa mata duvet, ta bude ido da sauri sai kuma ta mike zaune
tana kallon duvet din da ya rufa mata don parlon yayi sanyi sosai, tana zaro
ido bata san sanda tace "A ina ka dauko?" Yace "Ban sani
ba" Tsoronta kar yaje ya shiga dakin da Abdul yake, ta koma ta kwanta a
hankali tayi lamo, Ajay ya tafi ya ci gaba da tsayuwarsa a jikin window din
parlon yana duba wayarsa ganin Jay ke kiransa ya maida wayar aljihu. Karfe daya
da rabi Khaleesat ta kara farkawa a bacci, ta cire duvet din jikinta tana
kallon Ajay dake zaune kan one sitter ya jingina kansa da kujeran idonsa a
lumshe, amma tana mikewa zaune ya bude ido, ta fara sosa kai taki barin su hada
ido tace "Fitsari zan je in yi" Bai ce mata komai ba, ta mike tsaye
tana tafiya a hankali ta wuce sama, waige waige ta dinga yi kamar munafuka a
corridor din dakunan sannan ta bude one of the 3 rooms dake sama, taga Abdul
baya ciki, ta dai san baya dakinta tunda har Ajay ya shiga dakin ya dauko mata
duvet, dakin dake kallon nata ta bude a hankali, ta gansa kwance kan carpet at
the far end of the room yana bacci, ta shiga uku ta lalace, how did she find
her self in to this mess, duk don saboda tausayi, a hankali ta jawo kofar ta
kulle har da makulli sannan ta cire makullin ta tafi dakinta da shi ta ajiye a
handbag dinta, bayan kusan minti 7 Khaleesat ta sauko downstairs rike da
darduma da Hijab don alwala tayi bayan ta tuna bata yi sallan isha'i ba, shi
dai Ajay bin ta da kallo yake, ta shimfida darduman ta sa Hijab din sannan ta
tada sallan, bayan ta idar tayi sallan Nafila, ta dade zaune kan darduma, lkci
lkci take satan kallon Ajay don idonsa biyu har sannan, ganin ta fara jin bacci
ta mike a hankali ta koma kan kujera ta kwanta ta rufa da duvet, a nan ne bacci
ya dauketa wanda bata sake farkawa ba sai safe, don har gari ya fara wayewa, ta
mike zaune da sauri don yaushe rabonta da makara haka, kalle kallen parlon ta
dinga yi ganin Ajay baya parlon ta mike tsaye ta nufi window tana leka garage taga
babu motarsa, ta fi minti biyu tsaye jikin window din sai kuma ta juya ta wuce
sama bayan ta dau dardumanta da hijab, tana idar da sallah ta fito da makullin
dakin da Abdul yake ta bude kofar dakin tana tsaye daga bakin kofa ta hade rai
tana kallon cikin daki, yana zaune kan carpet, alamar tun bayan da yayi sallah
yake zaune a haka, hade rai tayi tace "Ka zo ka fita don Allah"
Mikewa yayi ya nufo kofar ta matsa ta basa hanya fuskarta daure, yana kallonta
yace "Good morning Khaleesat" Ζin
amsawa tayi waiting for him to go downstairs, cikin sanyin murya yace
"Nagode da rufa min asiri da kika yi" Yana fadin haka ya nufi
downstairs, ita dai ta bi sa da kallo, sai kuma ta bi bayansa to be sure he is
leaving, ko da ta sauka downstairs taga har ya bude kofar apartment din, tana
tsaye tana kallonsa har ya fita ya kullo mata kofar, ta karasa ta saka ma kofar
makulli, ta jingina da kofar letting out a sigh of relief.....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch
box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes,
lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c.....
All at affordable prices
Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with
laces if interested....
Follow this link to join my WhatsApp community:
https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM
Wajen karfe tara Khaleesat ta sauko downstairs bayan tayi
shirin tafiya makaranta, zaunawa tayi kan kujera ta jinginar da kanta jikin
kujeran tana jin kanta na mata ciwo, banda suna da test da baza ma taje schl
din ba don har a lkcn she was still stunned at what happen yesterday, gaba daya
a dar dar take cikin gidan, ko appetite din yin breakfast bata da shi, ganin
it's almost 10am ta ciro wayarta a jaka tayi ordering Uber da zai kai ta school
din, bayan ya iso ta mike ta dau jakarta ta nufi kofa, tana isa school taga
Safiyyah bata iso ba, kiranta ta fara yi a waya amma baya shiga, dab da za su
fara test din sai ga Safiyyah, bayan sun fito Safiyyah ta sauke wani ajiyar
zuciya tace "Kawai daga na Ιan sake ma
yaro fuska uwarsa bata da lafiya shine ya kai ni ya baro Khaleesat"
Khaleesat ta kalleta amma bata ce komai ba, Safiyyah ta gyara zama tace
"Gaba daya ya lalata min jakunkuna da jambakin uwarsa, duk ya goggoga,
daga in shiga wanka in fito, ai ko ni dai na dokesa in ma uban ya kullace ni
shi ya jiyo, jakunkuna na masu shegun tsada sai kace uwarsa ce ta siya
min" Khaleesat dai ta Ιan yi
murmushi kawai without saying anything, Safiyyah na kallonta da kyau tace
"Me kuma ya faru na gan ki haka?" Khaleesat ta bude jakarta ta ciro
zoben da Housemate ya bata ta mika mata, Safiyyah ta amshi box din ta bude,
zaro ido tayi with awe tace "Oh my God, who got u this Khaleesat? diamond
ne fa, don Allah wa ya baki, kamfanin Forevermark fa...." Ganin Khaleesat
taki bata amsa Safiyyah ta hade rai tace "Don Allah ki min magana, where
did u get this from?" A hankali Khaleesat tace "My Housemate gave
me" Mikewa Safiyyah tayi baki bude tana zaro ido tace "Don't tell me
he proposed to you?" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba tace "Ko
ba propose ba, he just gave me as a gift Sophie" Safiyyah tayi wani Ζara tace "Omg, wallahi proposing yayi maki amma
saboda sense is far from you kinga ai baki gane ba, ya salam luxury brand ne fa
Forevermark, to da ya baki me kika ce masa? Kuma ta yaya ya baki, kuna zaune ne
ko kuna tsaye sanda ya baki?" Safiyyah ta koma ta zauna kusa da Khaleesat
looking so excited tace "Don Allah how did u react da ya baki?"
Khaleesat tace "Bai ma jira nayi masa godiya ba kawai ya wuce"
Safiyyah tace "A apartment din ki ya baki?" Khaleesat tace "A'a,
he took me out for dinner yesternight, bayan da muka dawo shi ne ya bani a
mota" Safiyyah ta kyalkyale da wani shegen dariya tace "Yanxu fa sai
kice har yanzu baki gane Housemate dinki is in love with you ba ko? Duk sai
kice he is just being kind ko?" Khaleesat ta wani kalleta, Safiyyah na
dariya tace "Ae ba abun mamaki bane kice baki gane yana sonki ba har
yanxu, amma wallahi Housemate dinki na bala'i son ki kawata, don wannan care
din is extra ordinary, ko kanwarsa da suka fito ciki daya bazai dinga yi mata
irin wannan hidimar da yake maki ba, kai budurwar da saurayinta zai mata haka
ma ba karamin musulmin sonta yake ba,
yan mata nawa ne yanxu ko Naira biyar baya hadasu da samarinsu kuma a
haka wai aurensu za ayi, ke dai wallahi you are very lucky om earth, Allah ya kashe
ya baki kawai, ni kuma zan baki shawara kar kiyi misusing privilege din nan,
cause it's a privilege to you wallahi, bai duba wai kin taΙa aure ba kawai shi tsakani da Allah yake son ki a
zuciyarsa, come to think of who he is, daga gidan sarauta fa ya fito, in zaki
ajiye kunya ki nuna masa kema kina sonsa to zai dai fi maki, you are not a kid
Khaleesat, kinsan sonki Jawwad yake, so me tsanani kuwa" Khaleesat ta
sauke idonta kamar bazata ce komai ba, sai kuma a hankali tace "Kinsan me
Sophie?" Safiyyah na kallonta tana washe baki tace "Ina jin ki"
After some seconds Khaleesat tace "Abdul came to my apartment yesterday
night" Mikewa Safiyyah tayi ba tare da tasan ta yi hakan ba a tsorace,
tana kallon Khaleesat with shock all over her face tace "Waye kuma Abdul?
Did you have another frnd that is Abdul by name da ban sani ba?" Khaleesat
ta daga idanuwanta ta kalleta, cikin sanyin murya tace "Abdul dai guda da
kika sani" Safiyyah tace "Na shiga uku na lalace, Abdul tsohon mijin
ki wai kike nufi?" Khaleesat ta kasa ce mata komai, Safiyyah ta koma ta
zauna tana kallonta da wani expression tace "Ta yaya yasan apartment din
ki Khaleesat? Kuma me yaje yi maki a apartment? Don Allah ki min bayani yanda
zan gane, i am lost...." Khaleesat ta sauke wani ajiyar zuciya tace
"Wallahi ban san ta yaya yasan apartment dina ba Sophie, ni kaina i am
still shock up till now, ko breakfast na kasa yi saboda tsoro, yanda kika san
an jefo sa" Safiyyah ta maida jakarta gefe tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, ji min shege Ιan iska, to
wai uban me yaje maki a apartment din, tell me what happen da yaje, ke kuma da
yaje kofa kika bude masa ya shigo?" Khaleesat tace "Bayan Housemate
dina yayi dropping dina a gida ya tafi ana ruwa, after like 10 mins sai aka
danna bell, to na mance jakana a motar Housemate i was thinking shi ne ya dawo
ya kawo min jakar, da na sauka downstairs sai na bude kofa kawai, ashe Abdul
ne" Safiyyah da tayi mitsi mitsi da ido tana sauraron Khaleesat tace
"Go on, ina jin ki, sai aka yi yaya?" Khaleesat ta sauke ajiyar
zuciya tace "I was very shock and afraid bayan na bude kofan ya shigo, shi
ne na shiga kitchen da gudu dama wayata na hannuna nayi dialing number Ya
Junaid, sai gashi ya biyoni kitchen din ya karbe wayar" Buda baki Safiyyah
tayi tana kallonta da firgici a fuskarta, cikin sanyin murya Khaleesat ta gaya
mata duk abubuwan da Abdul yace mata a kitchen din bayan da ya sameta a ciki,
da kuma yanda Ajay ya zo gidan duk bata boye mata komai ba.... Safiyyah na
girgiza kai tace "Amma kin bani mamaki Khaleesat, yanxu shi Abdul har wani
abun tausayi ne shi da zaki boyesa a apartment dinki? Abdul fa???" A
hankali Khaleesat tace "Ce min fa yayi in tuna alkhairansa gare ni Sophie,
kuma he look afraid also baya son Ajay ya gansa, shi ne yace in rufa masa
asiri" A fusace Safiyyah tace "Wani shegen alkhairin yayi maki da
zaki tuna? Harrassing dinki da ya dinga yi ko kuma gorin da yake lafta maki da
walakanta ki da yake yi? Nan nan ranan kika bani labarin zaman ukuban da kika
yi a gidansa kafin ya sake ki, da yanda ya bar ki da kwalin indomie ko albasa
babu balle tarugu, marukan da ya dinga maki da zagin cin mutunci ne alkhairin
da zaki tuna game da shi? Mutumin da ya ci mutuncinki ya sake ki bayan ya samu
abinda yake so a wajenki har shi ne abun tausayi Khaleesat? Yanxu kina nufin
kika boye Abdul har washegari a apartment din ki kika bar Ajay da gadin ku?
Ikon Allah, Gaskiya baki taΙa bani tsoro
irin yau ba Khaleesat, i fear who no fear you, me yake damun ki ne haka?"
Khaleesat da duk jikinta yayi sanyi tana kallon Safiyyah tace "Safiyyah
kar ki manta this is America, we are not in Nigeria, Ya Junaid na lura temper
dinsa a kusa yake, yana da zuciya sosai, what if yaje ya masa wani illa wajen
dukansa don nasan definitely bazai kyalesa ba idan ya gansa a gidan, kina tunanin
idan yayi masa wani abu za a kyalesa ne a kasar nan? dole doka zai yi aiki a
kansa, kuma duk saboda ni sai haka ya faru Sophie??" Safiyyah ta wani
kalleta tace "Sannu me hangen nesa, da duk baki san da hakan ba kika doka
masa kira? Why did you call him at the first place idan ba don ya zo ya fitar
maki da Abdul ba?" Hawaye ya cika idon Khaleesat tace "Ai a sannan
ban san da wani Intention ya zo min gida ba, kinga if he just came to harm me
wannan daban ne, amma he meant no harm he was even afraid, banda haka ai bazai
rokeni kar in gaya masu ya zo gidan ba" Safiyyah tayi wani murmushi tace
"Maa sha Allah, kinga shawara daya kawai Abdul ya koma Nigeria ya bada
sabon sadaki a kara daura maku aure kije can ku karata, tunda yanxu kam ya tuba
kuma har kin yarda da tubansa kina mugun tausayinsa a rai, Allah ya baku zaman
lafiya da zuri'a masu yawa" Khaleesat ta hade rai tace "Come off it
Safiyyah, ni nace maki i am ready to accept his repentance? Ko sake daura min
aure aka yi da shi ba sai dai a kai gawata gidan ba, how will I forget what i
went through so soon Safiyyah, wallahi kawai kalman alkhairi da ya furta ne da
kuma irin sigar da naga ya zo min yasa na rufa masa asiri, ni ba butulu bace
bazan ce Abdul bai min abubuwan Alkhairi ba a rayuwata, in ba don shi ba yaushe
har ma zan zo kasar nan in hadu da su Housemate dina? I lacked nothing tun da
Abdul ya kawo ni kasar nan karatu, don har nafi wasu da iyayen nasu ke daukar
nauyinsu, kinga bazan ce Abdul bai min wani abun alkhairi ba, kuma bazan taΙa iya biyansa abinda yayi min ba, ki fahimce ni plss
Sophie, ba wai nace ya kamata in sake kulasa bane, don wallahi ko ganinsa bana
son yi don hakan na fama min ciwon dake zuciyata..." Safiyyah ta tabe baki
tace "Tun da kin rufa masa asiri kin ga yau ma nasan yana can bakin
apartment din naki yana jiran ki, hauka ake zan rufa ma Abdul asiri idan ni ne
a shoe din ki? Abdul fa? Ai ko duk alkhairan duniya yayi min wallahi bazan rufa
masa asiri ba sai dai Allah ya yafe min kawai, Monster in form of human ne fa
Abdul, gaskiya kin ci amanar Junaid, kin cuce sa, kuma da ya kuskura yasan
abinda kike boyewa a gidan nasan ko ciki daya ku ka fito da shi bazai sake
barin wata alaΖa ta hada ku ba har abada,
kuma bazai taΙa yafe maki ba, in kina tsoron
kar Ajay ya masa illa me ya hanaki kiran 911?" Khaleesat dai tayi shiru
tana bin inda suke zaune da ido, Kawai ganinsa suka yi a gabansu, ta rike
numfashi tsabar yanda tayi shock tana kallonsa babu ko kiftawa, Safiyyah da ita
ma ta gwalo ido tana kallonsa da mugun mamaki ta mike tana huci tace "Kai
bawan Allah lafiya muna zaune zaka tsaya mana a kai, ko dai batan hanya kayi
ne?" Sau daya ya kalli Safiyyah sannan ya mika ma Khaleesat wayoyin dake
hannunsa guda biyu yana kallonta, daya na Jay daya na Ajay, Khaleesat ta wani hade
rai tace "Abdul kaga bana son muyi creating scene a nan, kindly stay away
from me, are you even okay? Meye zaka dinga bibiyata?" Safiyyah ta figi
jakarta tana kokarin ciro wayarta tace "Idan ban kira maka 911 ba Allah ya
tsine min albarka...." Tana ciro wayar ya fixge daga hannunta yana
kallonta da kyau yace "Wajen ki na zo da zaki kira min 911 Malama?"
Safiyyah ta kundumo wani zagi tana kallon Khaleesat tace "Kin dai ga crook
din da kika ji tausayi har kika boye a apartment din ki kar Ajay ya gansa ya
jibgesa ko, kin taΙa ganin inda shedan ya tuba
dama? Shey u can see the useless monster you are pitying har da boyesa kar a
dokesa?" Abdul na mata wani kallo yace "Hey watch your tongue, idan
ba haka ba i will teach you a bitter lesson Billah, Ajay kika kirasa ko? To ya
zo ya dokeni tunda ni statue ne, ina ga shi ko gidan dambe bai taΙa zuwa ba, ki je ki tambayi wanene ni a
Lagos..." Khaleesat ta maida box din zobenta cikin jaka sannan ta mike ta
amshe wayar Safiyyah dake hannunsa, ta dau jakar Safiyyah da nata ta fara janta
su bar wajen, banda zagi babu abinda Safiyyah ke kunduma ma Abdul idonta rufe
tana cewa "Munafuki kawai algungumi, wato saboda ka san tana da tausayi
shi ne ka dawo sumui sumui da kai kamar na Allah zaka kara yaudaranta ka
cuceta, har kana cewa ta rufa maka asiri, to kuwa sai na tona asirin nan naka
wallahi, shegen duka za ayi maka da zai sumar da kai, in ka farfado ka siya
ticket ko koma gida kayi jinya, tsabar baka samu daman ci gaba da musguna ma
kawata ba har da rama sai da kayi kamar me ciwon Aids, to wallahi in baka fita
harkar Khaleesat ba sai nayi maka abinda har ka koma ga Allah bazaka manta ba,
mugu azzalumi kawai" Gaba daya attention din mutane ya dawo kansu a wajen,
Abdul yayi wani murmushi yace "Sai kinyi regretting duk kalaman nan naki
wallahi, sai na sa an lalata maki rayuwa i promise you this...." Khaleesat
dai ta samu ta ja Safiyyah suka bar wajen gaba daya, banda rawa babu abinda
jikinta yake yi don tsoro, Safiyyah ta warce hannunta tana kallonta a fusace
tace "Kin dai ga Ιan iskan da
kike tausayi ko? ashe da sabon salo kawai ya dawo don ya samu attention din ki,
ke kuma ga sarkin masu tausayi, to kuwa rabon a karyasa yasa ya dawo Amurka don
wallahi Ajay karyasa kawai zai yi" Khaleesat ta zauna ta rufe fuskarta da
hannunta tana kuka a hankali, gaba daya ta gama tsorata, ta ma rasa wani irin
tunani zata yi, zaman apartment din nata ita kadai ya fara bata tsoro kuma, can
ta kalli Safiyyah dake ta bambami cikin rawan murya tace "Sophie ko dai in
ma Ya Musty magana da kaina ki dawo apartment dina da zama tunda exams za mu
fara? Wallahi bazan iya zama ni kadai ba kuma a gidan nan Sophie, i am
afraid..." A fusace Safiyya tace "Ai baki zama afraid ba tunda har
kika iya boye kasungumin Ιan daba a
gidanki ya kwana, Abdul har abun yarda ne bayan duk mun san Ιan iska ne shi? Wani dadin baki zai maki har ki
yarda da shi? Kin dai ga abinda yayi min ai yanxu, dama kuma me hali baya taΙa fasa halinsa" A hankali Khaleesat tace
"To ko dai in yi ma Ajay bayanin abinda ya faru jiya kar ya zo ya gano
yaji haushina? Wallahi i am so confuse Sophie" Safiyyah tace "To nima
naji haushin ki balle Ajay da yayi gadin ke da Abdul ku ka sharbi baccin ku? ai
wallahi kin cuce Ajay kuma sai Allah yayi masa sakayya" Khaleesat ta goge
hawayen gefen idonta tace "To amma sai dai inje can gidan nasu in masa
magana ko? Don kar yaje yayi misinterpreting dina ta waya idan na kirasa, i
want to explain to him ta yanda zai gane" Safiyyah tace "Dama ai
gwara ki samesa face to face kiyi masa bayani, sannan kar ki kuskura ki ce masa
a gidan Abdul ya kwana don daga nan zai fatattake ki ya kora ki, ko ya hadaki
da karensa ya kora ki, inda Ajay ke burgeni kenan wallahi, no nonsense Man kike
ji, sam baya daukan wargi, tsayayyen namiji kenan, kawai ce masa zaki yi kin
shiga kitchen zaki zuba abinci sai kika ga kamar Abdul a jikin window din
kitchen dinki yana kallonki, shi ne duk kika rude kika kirasa jiya da daddare,
daga baya kuma kika ga wajen wayam ba kowa, amma da ya zo sai baki gaya masa
hakan ba tunda baki tabbatar ba kin zata hallucination kawai ki ke yi don dama
kanki na ciwo jiyan, sai ki ce masa yau kina department muna zaune ni da ke
kawai sai ga katon a gabanmu, ashe jiya shi din dai kika gani a jikin window,
kinga ai maganata tayi making sense akan ki ce masa ai boyesa kika yi a daki jiya...."
A hankali Khaleesat tace "To bari inyi order din Uber zuwa gidan"
Safiyyah tace "Sannan idan kin je gidan ki fara masa godiyan gadin ki da
yayi jiya ya hana kansa bacci, don nasan ba hankali gare ki ba kina iya zuwa ki
fara maganar da ya kai ki kanki tsaye...." Khaleesat ta ciro wayarta za
tayi order din Uber da zai kai ta gidansu Ajay, kafin tayi order din ta kalli
Safiyyah tace "Ko zaki rakani mu je mu biyu?" Safiyyah ta rike haΙa tace "Wa?? Ni? Salon inje ya koro ni mutumin
da ba kirki ne da shi ba, a'a wallahi bazan je ba, ko kadan bai taΙa burgeni ba dama ni, tun farko tamu bai zo daya da
shi ba don na tsani mutum fitinanne, da dai Housemate ne sai in bi ki mu je,
kuma banda ma yafi Housemate zafi me zai sa ma a sako sa cikin wannan case din,
to tsorona muna iya sako Housemate yaje ya fara ba Abdul din hakuri kinga ai
lamari ya lalace kenan, babu dai yanda muka iya Ajayn zaki je ki sama duk da
mugun halinsa, ayi mutum ace bai son mutane kullum yayi ta daure fuska yana
fushi shi kadai" Khaleesat na kallon Safiyyah cikin sanyin murya tace
"Ko dai kawai in gaya ma Housemate in kyale Ya Junaid din?" Safiyyah
ta wani hade rai tace "Wani Housemate, hakuri kike son ya tafi ya ba Abdul
din kenan yanda zai ji dadin ci gaba da iskancinsa, ai karki kuskura ki gaya ma
Housemate he won't help matters at all, gwara Ajay no nonsense, tsaf zai mana
maganin Abdul, amma Housemate ai har durkusawa sai ya iya yi ya ba Abdul din
hakuri yanda suka yi ma Aymaan shi da Ya Musty, Ajay ai shi ne namiji"
Khaleesat dai bata ce mata komai ba tayi order din ride din, Safiyyah ta zaro
ido tana kallon hannun Khaleesat tace "Ina zoben naki? Mun shiga uku ko
dai Abdul din ya kwace?" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba tace
"Ga fa shi nan a jaka" Safiyya tace "Atoh, don ni yanda na gansa
wujiga wujiga anya karayar arziki bai fada masu ba kuwa, kamar wanda yake yunwa
duk ya rame sai idanuwa da hanci, da kyar idan ba talauci a tattare da
shi" Khaleesat dai bata tanka Safiyyah ba, Safiyyah tace "To ki saka
zoben mana, ko jere zaki yi da shi a gaban madubi?" Khaleesat ta bude ido
sosai tace "Ina zan je da zan saka zobe Sophie?" Safiyyah tace
"Ke dai kin ki wayewa a rayuwarki Khaleesat, ba don gayu ya siya maki ba
dama?" Warce jakar tayi ta ciro box din zoben tace "Dalla ki
saka" Khaleesat tayi murmushi ta amshi zoben ta saka tana kallonsa
admiringly, cif ya zauna mata ta kalli Safiyyah dake ta murmushi ita ma kamar
bakinta zai yage tace "It's sooo cute, gaskiya Housemate is so romantic,
har na hango kun yi aure, wallahi kashe ki zai yi kawai da soyayya, in soyayya
ne a bar ma Housemate kawai, in kuma kwato hakki ne a bar ma Ajay" Dariya
sosai ta ba Khaleesat, kawai ta mike bayan ta maida wayarta da empty box din
zoben cikin jaka, Safiyyah ta rakata har zuwa inda Lyft dinta ke jira, ta bude
motar ta shiga, hannu ta daga ma Safiyyah dake ta murmushi tana kallon zoben
yatsanta dake ta kyalli, a haka Lyft din ya bar wajen, tun da suka kama hanya
Khaleesat ke ta waige waige to be sure babu motar dake bin su a baya, don ita
kam yanxu duk a tsorace take, tunda har Abdul ya iya gano apartment dinta to
babu kuma abinda bazai iya yi ba, har dai suka isa bata ga alamar ko wani mota
dake biye da su a baya ba, ta sauka daga lyft din tana tafiya a hankali ta
shiga compound din, it's almost 4pm na yamma, motar Ajay ta fara gani a parking
space din gidan, sannan ta ga motar Jay ma alamar duk suna gidan, walking
slowly ta karasa har entrance din parlon dai dai sanda aka bude kofar parlon,
ta Ιan koma baya tana kallon
Housemate dinta dake kallonta da mamaki, cikin dubara ta boye zoben finger
dinta da veil dinta kar ya gani, tana kirkiran murmushi a hankali tace
"Good evening" Yace "Evening Housemate, come in" Ta sauke
kanta kasa ta bi bayansa har zuwa cikin parlon, ta zauna kan kujera shi ma ya
zauna yana kallonta hoping all is well don sai yaji gaba daya hankalinsa ya
tashi ganinta a gidansu, jin tayi shiru yana kallonta yace "Hope all is
well Housemate?" Tana murmushi tace "Alhamdulillah, babu komai, Ya
Junaid yana nan? I came to greet him" Jay yayi shiru yana kallonta, after
some seconds yace "Yeah, he is upstairs" Ta sunkuyar da kanta a
hankali tace "Ohk, i want to meet him" Jay ya gyada mata kai yace
"He is at the parlor upstairs, ki samesa a can" A hankali tace
"Sai na je sama?" Jay ya mike yace "He is there, ni zan fita
yanxu...." Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, ya Ιan
yi murmushi ya nufi kofar fita parlon ta bi sa da kallo har ya fita, bayan
fitarsa da kusan minti goma Khaleesat ta mike, walking slowly ta tafi sama,
tsaye tayi Ιan nesa da parlon dake sama
tana kallon Ajay dake kallon kwallo a Tv, ga grapes a gefensa yana sha, ko lura
da ita bai yi ba, he was so engrossed in the football match he was
watching.....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM
Khaleesat ta sauke idonta daga kallonsa ganin for almost 2
minute bai lura da ita ba kallon ball kawai yake da duk attention dinsa, ta Ιan yi kasa da murya tayi masa sallama, juyawa yayi
da sauri suna hada ido ya gyara zamansa don kishingide yake saman kujeran, nan
da nan yayi keeping straight face ya ci gaba da shan grape dinsa idonsa a kan
TV, tana tafiya a hankali ta karaso cikin parlon ta tsaya jikin kujera trying
to gather up courage tace "Good evening..." Ya Ιan kalleta, sai kuma yace "Yes?" Ta Ιan langwabar da kai tana kara rungume handbag dinta
tace "Ina son zan maka magana ne pls" a takaice yace "I am busy
as you can see...." Ta kalli football din da yake kallo, a hankali tace
"To shikenan, sai anjima" Tana fadin haka ta juya zata bar parlon
yace "Ke.... awa daya zaki yi using kiyi min maganar ne, say what u want
to say in few seconds i am listening" Tayi shiru tana kallonsa, after few
seconds ta zagayo ta zauna kan 1 sitter tana kallonsa, har a sannan kusan duk
hankalinsa na kan TV din kamar baya son missing kwallon da yake kallo, bayan
kusan minti biyar ya juya ya kalleta, shi har ya mance tana wajen, yace
"Kee fadi abinda ya kawo ki and stop staring at me that way" Tace
"To ai naga kallo kake" Yace "Ido ke ji ko kunne? Ina ruwanki da
kallon da nake yi?" Ζan taΙe baki tayi, ita shi yasa bata ma son abu yana
hadata da shi, komai sai yayi masifa, ta sauke idonta cikin sanyin murya tace
"Dama Abdul ne ya biyoni school yau..." Lokaci daya ya juya ya
kalleta, ta sunkuyar da kai, can yace "Waye Abdul?" Ta Ιan kallesa taga kallonta yake, tayi karfin halin
cewa "My ex" Shiru ya sake yi, after some seconds yace "In zaki
min bayani in details ki bude baki kiyi min and stop wasting my time" Ta Ιan saita kanta ta yanda zata fara koro masa duk
abinda Safiyyah tace ta gaya masa, tayi inhaling numfashi sannan ta fara masa
bayanin exactly yanda Safiyyah tace tayi, ya rage volume din TV, yana
sauraronta attentively amma ba kallonta yake ba, har ta kai aya tana kallonsa,
bai ce komai ba for almost a minute as if yana processing duk bayanin nata a
kansa, still not looking at her yace "So now what did you want me to
do?" Shiru Khaleesat tayi don bata san me zata ce ba, can taji yace
"Saki nawa yayi maki?" Ta sauke idonta a hankali tace "Kawai ce min
yayi ya sakeni, bayan da na dawo gida kuma aka aiko takarda daga gidansu da
saki uku a jiki, amma ba rubutunsa bane" Ajay ya wani kalleta yace
"Rubutun ki ne kenan?" Sunkuyar da kanta tayi, ya sauke idonsa kan
zoben hannunta dake kyalli, ta Ιan saci
kallonsa taga he is still looking at her, dauke kansa yayi bai sake cewa komai
ba na Ιan lokaci, sai kuma taji yace
"So what did you want me to do now da kika zo kika gaya min?"
Khaleesat ta daga idanuwanta ta kallesa, lkci daya jikinta yayi sanyi, yace
"Ko nan gidan kike son ince ki dawo?" Ta girgiza masa kai tace "A'a,
i will cope in sha Allah, kawai na gaya maka ne" Sai kuma ta mike a
hankali tace "Nagode, i am going back home" Ya watsa mata wani kallo
yace "Are you okay? Ina maki magana zaki mike tsaye? Ni nace ki
tashi?" Ta sunkuyar da kanta sai kuma ta koma ta zauna, nan da nan taji
hawaye ya cika idonta, da ta sani kawai da Housemate dinta ta gaya ma duk da
Safiyyah tace kar ta gaya masa, Ajay ya dau grape dinsa yana ci yace "Shi
Guardian din naki me ya hanaki gaya masa sai ni? Baki fi kusa da shi ba a kaina
zaki tsallakesa ki zo ki sameni? Am i ur Bodyguard?" Jin tayi shiru ya
juya ya kalleta, hawaye ya gani a idonta, ta kai hannunta tana goge hawayen,
bai sake cewa komai ba idonsa a kan grape din gabansa, after almost 30 seconds
ya kalleta yace "Ya ma kike da suna, Yaushe zaku fara exams?" Bata
dago kanta ba cikin sanyin murya tace "In less than a month time"
Yace "Amma kinga silly frnd din nan taki wataran sai ta jefa kanta masifar
da bazata iya fita ba, har ke sai ta jefa cikin matsala, shi tout din ta tsaya
take exchanging words da saboda rashin kamun kai...." Ita dai Khaleesat
tayi shiru bata ce komai ba, Ajay bai sake cewa komai ba a parlon yana nazarin
how to tackle the issue, shi ya dade bai ga Ιan
iska kamar Abdul ba, amma zai yi maganinsa, shafa kansa yayi still thinking of
where to start from, a yanxu dai baza su fara cewa ta zauna a gidan nasu ba don
Mai martaba went on a trip to Toronto, kwanansa hudu kenan a can kuma basu san
ko zai biyo ta Amurka ba, infact zai ma biyo don in dai ya taho overseas komin
nisan inda yaje da Amurka dole sai ya zo Maryland in har suna kasar to check on
them, so they won't take the risk of accommodating her in the house, assuming
the semester isn't late da kawai sun mata applying for On-campus residence
halls a cikin makarantar ta zauna, Ajay ya daga kai yana kallon Cousin brother
dinsa Mukhtar that was coming towards the parlor, Mukhtar yayi kasa da murya
yace "Tare mu ke da Mai martaba...." Ajay bai san sanda ya mike tsaye
ba dai dai sanda yayi ido hudu da Abbansa dake biye da Mukhtar a baya, Ζamewa yayi a inda yake tsaye with surprise, what a
bad coincidences this is, Mai martaba ya shigo parlon with a broad smile on his
face yayi kamar ma bai ga Khaleesat ba, Ajay ya sauke kansa kamar wanda ruwa ya
cinye a wajen, at first ya ma rasa abun cewa, can kuma yayi karfin halin cewa
"Barka da zuwa ranka shi dade....." Khaleesat ta daga kai tana kallon
Mai martaba sai kuma ta sunkuyar da kanta ta zamo kasan carpet ta gaishesa
cikin sanyin murya, sai a sannan mai martaba ya kalleta still smiling ya amsa
gaisuwarta, Mukhtar yayi offering masa kujera ganin bai zauna ba, Mai martaba
yace "I am fine Mukhtar..." Sai kuma ya kalli Ajay da ya kasa
kallonsa har sannan yace "Ina Jawwad?" A hankali Ajay yace "I
think he went out just now..." Mai martaba yace "Ohk" Mikewa
Khaleesat tayi da niyyar barin parlon, Mai martaba ya kalleta yace "No yi
zamanki yarinya, ya sunanki?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta koma ta
zauna a hankali tace "Sunana Jiddah" Yayi nodding kai yace "Maa
sha Allah, ke er Nijar ce?" Khaleesat ta Ιan
yi murmushi tana wasa da gyalenta tace "A'a, er Nigeria ce" Mai
martaba yace "That's good, Nigeria wani state?" Tace "Kano"
Ajay dai yaki daga kansa yana jin zufa na karyo masa a forehead, can kawai ya
juya ya bar parlon yana tafiya a hankali, Mai martaba ya zauna saman kujera
still looking at Khaleesat yace "Karatu kike a kasar nan Jiddah?"
Khaleesat tace "Eh karatu nake" Yace "That's good, wace
makarantar?" A hankali Khaleesat tace "John Hopkins
university..." Mai martaba na jinjina kai yace "Maa sha Allah, kano a
wani unguwa iyayenki suke?" Khaleesat tace "Muna mariri ne" Shi
dai Mukhtar na ta tsaye a parlon yana mamakin yanda Mai martaba ya tsaya ya
bada lokaci yana conversing da Khaleesat bringing her down to his level, Ita
kanta Khaleesat bata yi tunanin sarki bane shi duk zaton ta ko dai brother din
babansu ne shi din, Mai martaba yace "Maa sha Allah Jiddah, Allah ya bada
sa'an karatu" Tace "Ameen Abba Nagode" Mikewa tayi zata bar
parlon ya kalli Mukhtar yace "A bata dala dubu biyar Mukhtar" Mukhtar
ya Ιan risina kai da ladabi yace
"To ranka shi dade" Khaleesat na kallon Mai martaba a hankali tace
"Abba Nagode, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara girma" Daga
mata hannu kawai yayi with smile, sannan ta mike ta bi bayan Mukhtar, tun basu
fita parlon ba sai ga Jay ya shigo, kasa karasowa yayi bayan yayi ido hudu da
Khaleesat ga Mai martaba zaune a parlon, can ya kalli Mukhtar da ya daga masa
hannu alamar gaisuwa, ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, shi kam ya
sunkuyar da kai walking slowly, a hankali tace "Sai anjima" Murmushin
karfin hali kawai yayi mata without saying anything, ta bi bayan Mukhtar suka
bar parlon, Jay ya karasa har cikin parlon ya zauna kasan carpet yana gaida Mai
martaba da ladabi, Mai martaba ya amsa yace "Ina Ahmad din?" Jay ya
mike ya bar parlon zai kira Ajay, ba a dau lokaci ba suka dawo tare, shi dai
Ajay ya kasa hada ido da mahaifin nasa, ya zauna kan carpet gefen Jay, sae kuma
yayi karfin halin cewa "Ya hanya ranka shi dade?" Cikin nutsuwa Mai
martaba yace "Alhamdulillah...." Daga haka mai martaba bai sake cewa
komai ba, Jay da Ajay ma duk suka yi shiru kamar masu jiran hukunci a gabansa,
after a while Mai martaba ya kalli Ajay yace "Ita ce yarinyar da za aje
gidansu kenan..." Ajay ya Ιaga kai yana
kallon Abban nasa, can ya Ιan sosa kai
yana murmushin karfin hali yace "Abba ai budurwar Jawwad ce, wajensa ta zo
ba wajena ba" Mai martaba ya kalli Jay da bai dago kai ba, Can Abba yace
"Budurwar Jawwad kuma na gan ku zaune tare a parlor" Ajay ya gyara
zama yace "Ranka shi dade abinda na fada gaskiya ne, ba wajena ta zo ba
wajensa ta zo" Mai martaba ya kalli Jay, cikin nutsuwa yace
"Jawwad" Jay ya dago kai amma ya kasa hada ido da mai martaba, jin
mai martaba yayi shiru yasan bayani yake jiran ji daga garesa, hakan yasa ya
fara magana with calm yace "Gaskiya ya fada Abba, haka ne..." Mai
martaba yayi shiru na kusan minti daya kafin yace "Ita Hadiyar fa?"
Jay ya kasa cewa komai, Mai martaba sam bai yarda da abinda suka ce masa ba don
gani yake kamar Jay is covering for Ajay, after some minutes cikin hikima Mai
martaba yace "Ko hakan yasa kake ta jan maganar Hadiyah?" Jay ya
gyada masa kai still not looking at him, Mai martaba ya numfasa speaking with
calmness yace "So ta yaya zan yarda da ku yanxu? Don na fara kokonton ka
yanxu Jawwad, a da dai baka min karya amma yanxu ka fara" Jay yayi karfin
halin cewa "Allah ya taimake ka, believe me ba karya nayi maka ba"
Mai martaba yace "Ai shi ne nake tambayarka ta yaya zan yarda da hakan?
Yanxu nema maka auren yarinyar zan sa ayi idan na koma Nigeria so i can clear
away my doubt?" Jay ya daga idanuwansa ya kallesa, a hankali yace "Da
zan yi farin ciki da hakan ranka shi dade"
Mai martaba yace "To batun Hadiyah fa?" Jay ya rasa abinda zai
ce, after few seconds yace "I will be glad idan aka amince min na janye
daga batun auren Hadiyah" Mai martaba ya Ιan
yi murmushi yace "Ai bazan maka dole ba Jawwad, ya rage naka kayi ma
iyayenka mata bayani su bar maganar Hadiyah tunda kana da yarinyar da kake so
da aure, don waΖa a bakin me ita tafi dadi, in
kuma kaga zaka hadasu su biyun it's fine, as far as zaka yi adalci... By so
doing iyayenka mata baza su dau lamarin da zafi ba tunda duk sun saka ran auren
ka da Hadiyah" A hankali Jay yace "But i am afraid za su yi shunning
batun idan na kai masu ranka shi dade" Mai martaba yace "Not when i
am alive Jawwad, duk abinda kake so shi zan maka in sha Allah" A hankali
Jay yace "Allah ya kara girma ranka shi dade...." Mai martaba ya
kalli Ajay yace "Kai kuma ina sauraron ka har yanzu" Mikewa Mai
martaba yayi ya bar parlon, bayan tafiyarsa suna ta zaune kamar wa enda aka yi
planting a wajen sai dai ko wannensu akwai abinda yake tunani a ransa, Ajay ya Ιan kalli Jay sai kuma yayi breaking silence din yace
"Allah ya sanya alkhairi me mata biyu" Jay ya wani kallesa, Mikewa
Ajay yayi zai bar wajen Jay ya sa masa kafa sai gashi timmm ya fada kan kujera,
juyowa yayi ya hade rai yana kallon Jay da ya fara dariya, yaushe rabon su
zauna waje daya a gidan, har magana ma sama sama suke yi... Jay ya dakata da
dariyan da yake, sai kuma yayi kasa da murya yace "So what did you think
about all this?" Ajay yace "About what?" Jay ya juya ya kallesa
bai ce komai ba, Ajay yace "Getting married to ur Ward?" Jay dai
kallonsa kawai yake, Ajay ya Ιan yi
murmushi yace "All this while ka zata wataran zan so ta ne da kake
creating attitude a gidan nan? Saboda me ma zan so ta? Dama shi son haka yake
very cheap? Ai ba class dita bace yarinyar nan, i like nothing about her most
especially her silly cry, duk abinda nake mata saboda kai nake mata, if not
because you bazan taΙa saninta from anywhere ba, ba
ma abinda zai sa nayi crossing path da ita, so chill bruh.... Just that har na
fara hango maka challenges din da zaka yi facing a wannan familyn naka,
considering the fact that ta taΙa aure,
sannan she is a nobody, familynka kuwa basa son someone that is a nobody not to
talk of bazawara, kaga you have to tighten up ur belt kayi facing all the up
and downs that will approach you.... Wishing you the very best of luck"
Yana kai wa nan ya mike ya nufi dakinsa, Jay dai ya bi sa da kallo, sai kuma
Ajay ya tsaya sannan ya juya yace "In addition, tsohon mijinta na
bibiyanta yanxu haka, that was why she was here earlier on" Daga haka Ajay
yayi tafiyarsa Bedroom dinsa ya bar Jay da ya mike tsaye jin abinda Ajay yace.
Ajay na shiga dakinsa ya tafi jikin window ya tsaya yana kallon Neighborhood
dinsu, everywhere was so silent and calm as usual, sai kuma ya sauke idonsa ya
juya ya tafi ya dau wayarsa ya koma jikin windon ya tsaya, number Khaleesat
yayi dialing, yana fara ringing tayi picking, yace "Where are you?"
Khaleesat dake cikin Lyft tace "Ina cikin mota" Yace "Za ki
ina?" Kallon wayarta tayi jin shigowar kira taga Jay ne ke kiranta, ta
maida wayar kunne a hankali tace "Gidansu Safiyyah zan je" Yace
"Ohk, remain there idan kin je, do not go back to ur apartment...."
Yana kai wa nan ya katse wayarsa, Khaleesat tayi picking call din Jay don bai
katse ba har sannan yace "Kina ina Halysaah?" Tace "Ina
hanya" Yace "Kar ki koma apartment din ki, wait for me somewhere, i
will be on my way now" A hankali tace "Dama gidansu Safiyyah zan
je" Yace "Ohk to ki je, zan same ki a can" Tace "To
Nagode" Katse wayar tayi ta mayar cikin jakanta, wai yau ita ce zata kai kanta
gidansu Safiyyah yau saboda rashin choice, to ya zata yi, ko zaginta Surayyah
tayi ai sai dai kawai ta bata hakuri in dai zata barta ta zauna a gidan, a haka
ta isa gidan, bayan ta sauka Lyft ta nufi kofar apartment din ta danna
bell......
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah*
07087865788
π£️ HADJIBS DATA SERVICES
Barkan ku da zuwa HADJIBS DATA SERVICES
Wannan wuri ne da muke:
π Siyar da data (MTN, Airtel, Glo, 9mobile)
π Siyar da airtime cikin sauki (VTU)
π Biya kudin DSTV, GoTV, Startimes
π Biya wutar lantarki (NEPA/PHCN)
π Siyar da WAEC Scratch Cards
π Reseller Wallet System –
zaka iya siyarwa da riba
π Dama ga masu so su fara sana'a a wayarsu
Kawai zaku bude account dinku ku fara sana'ar ku cikin
sauki.
π±️ Shiga: https://hadjibsdata.com.ng
π² App Ιin mu yana
nan a Play Store da App Store.
Idan kana da tambaya ko bukatar taimako, tuntubi admin kai
tsaye, 07017133099.
Safiyyah na bude kofa ta washe baki tana kallon Khaleesat
tace "Wallahi na zata wasa kike da kika ce kina hanya, shigo ciki
mana" Khaleesat ta Ιan yi
murmushi ta shiga parlon, Safiyyah ta ja ta zuwa Bedroom dinta tace "Ni
kadai ce a gidan, ko ina suka tafi oho, ni sai nake ga kamar fa ciki Surayyah
tayi, in ko haka ne zan kama kaina in dena biyeta a gidan nan kar taje ta haifi
kyakkyawa kamar ni..." Khaleesat ta cire veil din jikinta tace
"Sallah zan yi" Safiyyah tace "Kin ci abinci a can kuwa?"
Khaleesat tace "Abinci kuma?" Safiyyah tace "Ko da yake waye zai
baki gida duk maza, bari inje in dafa maki noodles kafin ki idar da
sallahn" Mikewa Khaleesat tayi ta shiga bandaki, Safiyyah kuma ta fita
zuwa kitchen, bayan Khaleesat ta idar da sallah Safiyyah ta shigo dakin da
indomie da kwai da ta dafa mata ta ajiye, Khaleesat ta kalleta tace "Thank
you" Safiyyah tace "Naga duk kinyi wani sanyi, ko dai koran ki Ajayn
yayi?" Khaleesat tayi er dariya tace "Saura kadan dai ya kore
ni" Safiyyah ta kankance ido tace "Fitinanne, to sai aka yi yaya? Did
u meet Housemate in the House?" Khaleesat tace "Eh na gansa" Sai
kuma ta jawo handbag dinta ta bude ta ciro kudin da Mai martaba ya bata,
Safiyya tace "Wa ya baki wannan kuma?" Khaleesat tace "I think
their uncle, ya zo ya same mu a gidan ne, shi ne ya bani da zan tafi"
Safiyyah ta Ιan bude ido tace "Ko dai
babansu?" Khaleesat tace "Babansu kuma? babansu fa Sarki ne, a'a ba
babansu bane" Safiyyah ta amshi kudin tana kirgawa tace "Atoh, dama
sai dai ko uncle din nasu, amma ina sarki yaga lokacin tsayawa dake har ya baki
kudi, da sarki ne ai kya gansa da guards dinsa kuma yaushe ma zai tsaya maki
magana, dogarawansa ma baza su bari ba, amma fa ke Hajiya ce kinsan nawa kudin
nan in an canza a Naira?" Khaleesat tayi murmushi ta fara cin indomie din
gabanta, Safiyyah tace "Wallahi kudade ne masu yawa, har karamin gida sai
ya iya siya maki a maririn ku, yanxu ya ku ka yi da Ajay din bayan kin gaya
masa abinda ya faru?" Khaleesat tace "Ai bamu gama magana ba Uncle
din nasu ya zo, but after i left the house ya kirani yace kar in koma apartment
dina, Housemate dina ma ya kirani...." Safiyyah ta hade rai tace "Ba
nace kar ki sako Housemate a ciki ba? Shi fa Abdul namiji fitananne ne kawai
zai iya dealing da shi, shi kuma Housemate dinki ba mutum bane me son
hayaniya" Khaleesat tace "Kilan Ajay din ne ya gaya masa...."
Safiyyah ta mike jin ana danna bell tace "Kilan sun dawo daga gantalin da
suka je" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba Safiyyah ta mike ta fita daga
dakin, ba a dau lokaci ba ta dawo tace "Ban ga kowa a bakin kofar ba kuma,
ko dai kunne na ne yaji kamar an danna bell?" Khaleesat ta ajiye fork din
hannunta tace "Kuma kin bude kofar?" Safiyyah tace "Haba dai sai
kace ni ce ke, ta peephole na duba mana" A hankali Khaleesat tace
"Ban san me yasa gabana ke ta faduwa ba Sophie, Abdul can be cunning kar
ace ya fa biyo ki yaga gidan nan baki sani ba" Safiyyah tayi wani dariya
tace "Saboda yana shan codeine sai ya biyo ni gidanmu, ai yasan ni ba ke
bace hauka tuburan zan masa wallahi, to ya biyo ni akan me?" Ita dai
Khaleesat bata ce komai ba, taji abincin ma ya fita ranta, Safiyyah tace
"In zaki ci abincinki ki ci, idan su Ya Musty sun dawo zan sa ya duba
surveillance camera din bakin kofar mu ga wani shege ne ya danna bell"
After a while Khaleesat ta tura abincin gabanta don ya isheta ga baccin da take
ji, Safiyyah dai chatting kawai take da wayarta, Khaleesat ta dau kudin da
Safiyyah ta ajiye mata ta cire dala dubu biyu a ciki ta ajiye mata kusa da ita,
Safiyyah ta hade rai tace "Meye wannan?" Khaleesat bata kalleta ba
tace "Na baki" Safiyyah tace "Inyi me da shi? A'a bana so
wallahi, ki ajiye kudin ki kawai zai maki wani amfanin" Khaleesat bata
tanka ta ba ta mike tayi kwanciyarta gefen gado ta lumshe ido, cikin dubara
Safiyyah ta jawo handbag dinta ta mayar mata da kudin ciki sannan ta ajiye.
Wajen karfe shidda da rabi Safiyyah ta tashi Khaleesat dake bacci ta dalilin
wayarta dake vibrate, Safiyyah tace "Ana kiran ki a waya" Khaleesat
ta mike zaune ta jawo wayar ta duba taga Housemate ne ke kiranta, daga kiran
tayi ta kai kunne, daga daya bangaren yace "I am outside Halysaah" A
hankali Khaleesat tace "To" Veil dinta ta dauka Safiyyah ta rakata
zata bude mata kofa, Khaleesat ta riko hannunta da sauri tace "Ki fara
duba waje kafin ki bude mana" Safiyyah tace "Ke dai matsoraciya ce
wallahi, shi Abdul din ai ba Ιan iska bane
da zai zo ido na ganin ido, baki ga kamar barawo ya shige maki gida ba ranan da
daddare" Bude kofar tayi Khaleesat ta makale a bayanta gabanta na faduwa,
bayan ta hango motar Jay ta Ιan sauke
ajiyar zuciya, Safiyyah na washe hakora tace "Yau dai Allah yayi za mu
gaisa da shi" Khaleesat ma murmushin tayi suka fita zuwa gun motarsa a
tare, yana ganin Safiyyah ya sauko daga motar, ya rungume hannu yana kallonta
yace "Good evening kawar Housemate" Safiyyah ta tuntsire da dariya
tace "Welcome Yaya Housemate, sai yau Allah yayi za mu hadu tunda ka
dawo" Yace "Amma ai ina ce ma kawarki ta gaisheki" Safiyyah tace
"Wallahi bata taΙa gaya min
ba" Jay ya Ιan kalli Khaleesat dake kallonsa,
ta sauke idonta da sauri bayan sun hada ido, murmushi yayi yace "Gaskiya
ban taΙa cewa ta gaishe ki ba, it's
not her fault..." Safiyyah tayi dariya tace "Wai don ka kareta ko, ai
nafi ka sanin wacece Housemate dinka" Jay na murmushi yace "Ya mutan
gidan?" Safiyyah tace "Duk lafiya lau suke, yanxu take gaya min uncle
dinku gave her much money a taya mu yi masa godiya plss, ranan kuma ta nuna min
diamond ring da ka siya mata, Allah ya saka da alkhairi Yaya Housemate, Allah
ya bar ku tare" Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah with shock,
Jay dai yayi murmushi yace "Our father... not uncle Safiyyah" Daga
Safiyyah har Khaleesat kallon Jay suka yi, Safiyyah ta bude ido sosai tace
"Kana nufin Mai martaba da kansa? That's surprising, Allah ya kara masa
girma....." Jay na murmushi yace "Ameen" Ita dai Khaleesat tayi
shiru tana tunanin yanda yayi ta hira da ita a parlon kamar random person babu
wanda zai yi tunanin sarki ne, Safiyyah tace "To ni zan koma ciki
Housemate" Jay yace "Alright Safiyyah, thank you so much" Tana
murmushi ta juya ta koma cikin gida, shi dai Jay kallon Khaleesat yake, sai
kuma ya bude mata front seat, ba musu ta shiga motar ba tare da ta kallesa ba,
ya zaga ya shiga driver seat yana kallonta yace "Kin ci abinci ne?" Kai
ta gyada masa, jin bai sake cewa komai ba ta daga idanuwanta ta kallesa, zoben
hannunta taga yana kallo baya ko kiftawa, tayi saurin boye hannun a bayanta
kamar ta nutse don kunya, yayi murmushi yana kallonta a hankali yace "Wai
yaushe kika fara jin kunyata Housemate? I am only admiring the ring, it look
soo cute in your finger" Taki daga kai ta kallesa, ita kanta ta rasa gane
wannan sabon kunyan nasa da take yi, ya jinginar da kansa da kujeran motar yana
kallonta babu ko kiftawa, tunda taji yayi shiru tasan kallonta yake hakan yasa
ko da wasa bata yarda ta dago kanta ba balle su hada ido, murya can kasa taji
yace "Me yasa ni baki gaya min Ex dinki yaje wajenki a schl ba sai
Ajay?" Shiru tayi jin tambayar da yayi mata, can ta dan kallesa, still
speaking slowly yace "Why?" Tace "Ae ko an kira ka baka picking
call dinka..." Yayi shiru yana kallonta kafin yace "Yaushe kika kira
ban yi picking ba?" Ta langwabar da kai tace "Anytime i call, you
don't pick" Jay ya sauke idonsa kasa, after some seconds yayi kasa da
murya yace "I promise i won't do that again, i will prioritize ur call
from henceforth yanda nake prioritizing na Mami da me martaba" Khaleesat
ta daga kai suka hada ido, tayi saurin dauke idonta daga nasa, yace "Me
yace maki da ya sameki a school din?" Khaleesat tace "Safiyyah ce ta
kulasa suka yi exchanging words" calmly Jay yace "Do not worry
Halysaah, i will bring an end to ur fright about ur Ex Husband very soon in sha
Allah, i promise you this, zaki samu kwanciyar hankali fiye da yanda kike
tsammani" Khaleesat ta kallesa, cikin sanyin murya tace "But i don't
want you to confront him pls, he can be cunning" Jay ya Ιan yi murmushi yace "I am not confronting him
Halysaah, kawai dai zan yi abinda zai yi cutting duk wani Intention din da yasa
ya dawo yake bibiyan ki, i will put a total stop to that, kuma babu yanda ya
iya haka nan zai hakura ko ba don Allah ba...." Khaleesat tayi shiru tana
kallonsa, After some seconds tace "Amma yanxu i will prefer inyi ma
brother din Safiyyah magana to let me stay in their home har sanda zan gama
exams, don bazan iya zama a apartment dina ni kadai ba kuma, i am very
afraid" Jay yace "Kar kiyi inconveniencing dinsu Housemate, and I
don't want you to be a burden to them considering the high cost of livelihood
in this state.... ki zauna a apartment dinki kawai, i will be there also, i
will be there to protect you...." Khaleesat tace "Zaka dinga zuwa
kamar sanda muke former apartment dina?" Yayi murmushi yana kallon kwayar
idanuwanta yace "Sure, anything for you Halysaah" Sosai taji
hankalinta ya kwanta, cikin sanyin murya tace "To Nagode" Yace
"Lokacin sallah ya kusa, can we go home now" Tace "Let me get my
handbag" Gyada mata kai yayi, ta bude motar ta sauka, ya bi ta da kallo
har ta shiga apartment din, after some minutes sai ga ta ta fito daga gidan da
handbag dinta da waya, ta shiga motar ta rufe tana kallonsa taga kallonta
yake.... Khaleesat na zaune dakinta wajen karfe takwas da rabi na dare suna
WhatsApp call da Aunty Farida, gaba daya jikinta a sanyaye yake ga faduwar da
gabanta yake ta yi jin abinda Aunty Farida ke gaya mata, labarin biyota da
Abdul yayi har sabon Apartment dinta da kuma cikin makaranta take ba Aunty
Farida, a nan ne Aunty Farida ke sanar mata ai yaje Mariri ma yafi a kirga few
weeks ago kawai gaya mata ne bata yi ba don bata son daga mata hankali, Cikin
sanyin murya Khaleesat tace "To Aunty ya aka yi yasan ina America
ne?" Aunty Farida tace "In kin tambayeni in tambayi wa Khaleesat?
Kilan ko bincike yayi a unguwan aka gaya masa, kinsan babu abinda yan unguwan
nan baza su yi ba akan kudi, dama kuma ga tsegumi ya masu yawa, in kuma ba a
unguwan ya bincika ba kilan shi ma yaga hotonki da wannan mutumin da ya dora ki
a Instagram" Khaleesat kamar zata yi kuka tace "Toh me yake so kuma a
guna Aunty da yake bibiyana ne?" Aunty Farida tace "Mutumin da yana
zuwa cewa yayi ya maida auren ku, Allah ya so Nenne ta zo ranan sai abinda ta
manta ne bata gaya masa ba ta kusa tara masa yan unguwa, kuma tace ai kin gama
iddansa tun wani shekara in ma yau ya farka bacci tun sanda ya sake ki to yaje
ya duba calendar yaga yau shekara nawa da yayi sakin, Nenne ta sille sa tas, ni
ai shi yasa hankalina bai wani tashi ba, da dai baki idar da iddansa bane shine
babban tashin hankalinmu gaba daya, amma da baki da hakkinsa ai kinga Allah ya
kada hankalinsa sai bayan da kika gama ya waiwayo ki, yana sake zuwa inda kike
ki kira masa hukuman kasar kawai su ja maki layi da shi...." Khaleesat dai
ta kasa cewa komai, Aunty Farida tace "Dama in kika ga ya hakura da
bibiyanki ai sai in wani auren kika yi tunda babu tsoron Allah a ransa, ban taΙa ganin mara kunya ma irin sa ba, babu kunya babu
tsoron Allah fa ya zo ya marairaice ma Babanki wai ya maida ke, ya zo gidan nan
yafi sau goma wallahi, to Allah na tuba ko da ace baki gama iddansa ba da ba
sai dai mu makasa a kotu ba akan ki koma gidansa, shi Ιan
iska, danginsa matsiyata marasu mutunci" Khaleesat taji hawaye ya cika
idonta tace "Toh Aunty ni tsoro nake kar ya sake cewa zai daukeni kema
kinsan halinsa fa" Aunty Farida tace "A American zai dauke ki saboda
ba shi da seti?" Khaleesat dai tayi shiru gabanta na faduwa don har yanzu
bata mance yanda aka dauketa aka kai masa ita ba, tunanin hakan yasa hawaye ya
fara zuba idonta, Aunty Farida tace "Yanxu dai ki kwantar da hankalin ki
tunda kin ce Jarabawa za ku fara, su Junaid ma baza su bari ya cutar dake ba in
sha Allahu, kiyi ta addu'a kina neman tsari daga sharrinsa, in sha Allahu Allah
zai kare ki" Khaleesat ta gyada mata kai cikin sanyin murya tace "To
Aunty" a haka suka yi sallama da Aunty Farida tana goge hawayen da yaki
tsaya mata, kiran Safiyyah ne ya shigo wayarta tayi picking ta kai kunne,
Safiyyah tace "Khaleesat kin san wa yayi ring din bell daxu kuwa?"
Sosai gaban Khaleesat ya fadi tun kan Safiyyah ta gaya mata, Safiyyah tayi wani
dariya har da kyakyatawa tace "Wallahi shi ne in gaya maki, Abdul ne ba
wani ba, gashi nan an duba Camera na gansa, to da na bude kofar uwar me zai min
ne? Wato ban taΙa ganin Ιan iska mara aikin yi kamar sa ba, ki ji har yayi
locating inda nake saboda rashin aikin yi, to me zai min da Allah bai min
ba?" Cikin rawan murya Khaleesat tace "Kin dai ga abinda nake gudu
ko, wallahi da baki kulasa ba Safiyyah, ba kowa ake musayar yawu da ba"
Safiyyah tace "Wallahi ba abinda ya isa yayi min da izinin Allah, shi kuma
yaya Musty idan ya gama bambamin fadan da yake yana cewa ina dauko masa magana
a kasar nan sai ya daukeni mu tafi mu kai ma Cops report, sai an gano Abdul duk
inda yake ya fadi abinda ya zo yi a apartment dinmu wallahi..." Tana kai
wa nan ta katse wayarta, knocking din kofar dakin Khaleesat taji ana yi, ta
juya ta kalli kofar har sannan zuciyarta na bugawa ta mike ta dau hijab dinta
ta saka ta tafi ta bude kofar, sauke idonta tayi bayan sun hada ido, yana
kallonta da damuwa ganin hawaye idonta yace "Are you crying Halysaah? Me
ya faru?" Kamar jira take ta jingina da kofar dakin ta fashe masa da kuka
dama ta kwana biyu bata yi ba, nan da nan ta rikitasa a wajen.....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah*
*Ur evidence 07087865788*
https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM
Juyawa Jay yayi ya sauka downstairs don bai son yayi abinda
zuciyarsa ke tunzura sa yayi a wannan moment din, yasan in ya ci gaba da
tsayuwa yana sauraron kukanta a wajen the case will be totally different, sai
da Khaleesat taga ya sauka kasa sannan ta dena kukan da take har lokacin tana
jingine da kofar tana goge idonta a hankali, juyawa tayi ta koma dakinta ta dau
laptop dinta ta zauna kan gado zata yi karatun wani course dinsu amma ta kasa
karatun, sai kuma tayi tagumi tana kallon screen din laptop din babu ko
kiftawa, after a while ta maida Laptop din gefe ta sauka daga kan gadon ta nufi
kofa ta fita daga dakin, walking slowly ta fara sauka downstairs tana kallonsa,
zaune yake kan kujera idonsa a wayar hannunsa, ya juya yana kallonta jin foot
step dinta, har ta karaso karshen staircase din, ta sunkuyar da kai ganin
kallon da yake mata, mikewa yayi ya nufeta yayi kasa da murya yace
"Halysaah... " Ta daga idanuwanta ta kallesa amma bata ce komai ba,
yace "Why are you crying?" Kamar bazata ce komai ba sai kuma ta
jingina da bango ta rungume hannunta tace "Ba sai kace min inyi hakuri ba
amma ka wani tafi...." Murmushi yayi yace "To ai ban san ta yanda zan
fara cewa kiyi hakurin bane ta yanda zaki gane da gaske nake baki hakurin, shi
yasa na tafi" Ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, can ta juya zata bar
wajen, ya dakatar da ita yace "Halysaah" After some seconds ta juyo
fuska a daure, ya Ιan yi murmushi yace "Mu
je parlor in baki hakurin to" Ta wani turo baki ta kara rungume hannunta,
yana murmushi ya juya ya koma parlon, sai kuma ta bi bayansa, ya jira har ta
karaso ta zauna kan kujera, sannan ya zauna same kujeran leaving some space
between them yana facing dinta yayi kasa da murya yace "Now tell me, why
were you crying Halysaah?" Ta sauke idonta a hankali tace "I just
can't understand why Abdul is still after me..." Jay yayi shiru yana
kallonta babu ko kiftawa, can yayi kasa da muryarsa yace "But mun gama
maganan nan just few hours ago ai Housemate, i told u i will put a stop to that
soon, i promise you this, kina gama jarabawa idan mun koma Nigeria komai zai zo
karshe in sha Allah" Muryarta na rawa tace "Why not now? Ai bazai
daina bi na ba, and i want to concentrate fully on my exams...." Jay yayi
shiru yana kallonta, ya sauke idonsa with calmness in his voice yace "Are
you sure you will want that now?" Ta gyada masa kai looking so confuse
tace "Ya fa je har gidanmu a can kano so many times, sannan daxu muna
gidansu Safiyyah sai da yaje gidan fa ya danna bell and left immediately...."
jay ya daga idanuwansa yana kallonta da mamaki yace "Really?" Ta
marairaice masa tace "Aunty Farida ta gaya min yana ta zuwa gidanmu, pls
kawai we should report him to authorities don ya fita hanyata, ni wallahi
tsoronsa nake ji, he can be so cunning...." Jay was quiet for almost a
minute, sai kuma ya daga kai suka hada ido don kallonsa take, ita ta fara dauke
idonta, har zai kamo hannunta sai kuma bai yi hakan ba ya fara kokarin kara
barin enough distance tsakanin, yayi kasa da murya yace "Do you want to
get married Khaleesat?" Shiru Khaleesat tayi tana kallonsa babu ko kiftawa
don tambayar tasa ya zo mata a bazata, shi dai kallonta kawai yake yana jiran
amsarta, a hankali tace "Aure kuma?" Jay yace "Yeah" Tana
son tambayarsa aure da wa amma ta kasa, nan da nan jikinta yayi sanyi don babu
inda tunaninta ya tafi sai ko yana da wani da zai hadata aure da, speaking
slowly yace "Aure ne kawai zai sa ya hakura ya dena bibiyanki Halysaah, in
kuwa ba haka ba bazai hakura ba ko da an hadasa da hukuma he will only change
his tactics..." Hawaye taji ya fara taruwa idonta, sai tayi da ta sanin
sauko ta samesa a parlon, kilan da bai gaya mata wannan magana ba, ganin hawaye
a idonta cikin sanyi yace "Baki shirya auren ba ko Housemate?" Ζin ce masa komai Khaleesat tayi tana kokarin ganin
bata fashe da kuka ba a wajen, ta rasa me yasa ta zama heartbroken all of a
sudden da jin furucinsa, was it because that wasn't what she was expecting or
wanting, she still can't tell, Jay ya sauke idonsa daga kallonta, after some
seconds yace "To kiyi hakuri, i shouldn't have brought this suggestion up,
may be you have other plans than marriage ko" Ita dai bata ce komai ba
tana goge hawayen dake sintiri a fuskarta, ya jinginar da kansa da kujera bai
sake cewa komai ba, tayi karfin halin cewa "Ai baka ce min da wanda zan yi
auren ba" Ya girgiza mata kai still not looking at her yace "A'a,
naga ba aure bane plan dinki na gaba, i am sorry i came up with the idea, kawai
ina ganin kamar hakan kadai ne mafita... I am sorry" Tana girgiza masa kai
still trying not to cry out loud tace "Ni bani da wani plan wallahi, kawai
burina Abdul ya fita rayuwata ya kyaleni, duk wani abu da zai tabbatar da hakan
i will welcome it wholeheartedly, as far as he will stay far away from me"
Jay ya kalleta a hankali yace "To nace aure kin fara kuka ai
Housemate" Ta girgiza masa kai tace "In hakan ne best solution i will
welcome it, kawai dai ban san da wanda zaka hadani bane" Jay dai kallonta
kawai yake amma ya kasa cewa komai, ita kuwa sai goge hawayenta take without
looking at him, yayi kasa da murya yace "I don't know ko za kiyi turning
down din wanda zan hada ku Halysaah, bazan so in maki dole ba, ko kuma nauyina
yasa ki amince bayan ke ba hakan kika so ba a ranki" Khaleesat ta girgiza
masa kai cikin karfin hali tace "I won't... as far as it's ur choice i
will never turn it down, i trust ur choice, and i know it will be the best for
me, nasan baza ka min zabin da bazai yi favouring dina ba, i know this..."
Magana take amma Allah yasani karfin hali kawai take, she was very very
heartbroken deep inside her and she can't even say why, Jay dai bai fasa
kallonta ba yana tunanin what he is about to voice out and how she will react
to it, jin shirun nasa yayi yawa ta daga idanuwanta da har sun fara ja suka
hada ido, kamar me rada yace "Za ki iya aurena Halysaah?" His
question almost took away her breathe cause it hit her unexpectedly, she was
stunned into silence at the same time paralyzed with surprise, she couldn't
stop staring at him with wide eyes, shi ma kallonta yake babu ko kiftawa kamar
yanda take kallonsa, and she realize they've been staring at each other for
almost 30 seconds, da sauri ta dauke gaze dinta daga idonsa zuciyarta na
bugawa, cikin dubara ta fara kokarin mikewa zata bar masa parlon, yana gano
abinda zata yi yayi saurin rike hijab dinta yana kallonta murya can kasa yace
"Ba inda za ki je without giving me my answer Halysaah" Boye fuskarta
tayi jikin kujera da sauri taki yarda su sake hada ido tana jin kamar ta nutse
cikin kujeran, ta dade bata ji irin wannan kunyan da take ji a yanxu ba, yana
kallonta yace "Halysaah" Taki dago kanta tana kara shigewa cikin
kujeran tace "Uhm" Yayi kasa da murya yace "Look at me
plss" kamar zata yi kuka tace "Uhm ni bazan iya ba" Gaba daya ta
gama narkar da shi a wajen, ya duka gabanta yana kallonta as if he is
whispering yace "Pls say something Halysaah, i want to hear you say
something" Khaleesat dai taki yarda ta dago kai su hada ido da shi, she
can't even explain what she is feeling at the moment, slowly yace "To
tashi ki je ki kwanta, sweet dreams Dear, I love you so much...." Sake
gigitata yayi da kalamansa, ta fara kokarin mikewa daga kan kujeran tana rufe
fuskarta da Hijab din jikinta, saboda saurin da take ta bar wajen ta take dogon
hijab din jikinta kiris ya rage ta fadi har zai rikota kawai ya hana kansa yin
hakan, tayi regaining balance dinta within a twinkle of an eye har ta isa
staircase ta wuce sama da sauri ta shiga dakinta ta kulle kofa ta jingina jikin
kofar tana sauke ajiyar zuciya kamar warce tayi tseren gudu...
Daren ranan Khaleesat bata yi baccin kirki ba, she can't
even explain her emotions, da gari ya waye har karfe sha daya na safe ta kasa
sauka downstairs gashi karfe takwas suke da class ranan, har ta gaji da kiran
da Safiyyah ke ta doka mata tun daxu, da sauri ta juya jin ana knocking kofar
dakinta, ta kasa tashi ta bude kofar, ita kanta bata san kunyanta ya kai haka
ba sae yanxu, da kyar ta mike jin an sake knocking kofar, ta dau veil dinta ta
yafa kamar sabuwar amarya ta karasa bakin kofar, nan ma sai da ta tsaya for
almost 30 seconds kafin tayi karfin halin bude kofar kanta a sunkuye, yana
tsaye bakin kofar calmly yace "Good morning Housemate" Still not
looking at him cikin sanyin murya tace "Ina kwana" Yace "Lafiya
lau, baki da lectures ne?" Kanta a kasa tace "Ina da" Shi dai
kallonta kawai yake ganin wani sabon kunyansa da ta tsira kuma, ya Ιan yi murmushi ya mika mata karamin tray din
hannunsa yace "Here.... Idan kin gama sai inyi dropping dinki a school
din" Iya abinda yake mika mata kawai ta Ιan
kalla sannan ta amsa, shi dai kallonta kawai yake ta juya ta koma cikin dakin
sannan ta kulle kofar, Hot chocolate da cookies ta gani a saman tray din, ta
zauna saman carpet din dakin da breakfast din a gabanta, bayan Khaleesat ta
gama sai da ya kira wayarta sannan dai ta karasa shirinta ta dau handbag dinta
da tray din breakfast dinta ta sauka downstairs, yana zaune parlon ta samesa,
kanta a kasa ta wuce kitchen ya bi ta da kallo, bayan ta wanke utensils din ta
fito daga kitchen din ta tsaya bayan kujera tana wasa da fingers dinta a
hankali tace "Na gama" Mikewa yayi ya dau makullin motarsa yace
"Ohk mu je" Kofa ta nufa yana biye da ita a baya zata bude kofar taji
a bude yake ta fita sannan shi ma ya fita, ta tafi garage ta jirasa ya kulle apartment
din, as usual shi ya bude mata door din motar bayan ta shiga ya kulle, sannan
ya zaga ya shiga driver seat ya tada motar ya fara Reverse, sai da suka dau
hanya yace "We saw our dad off to the airport in the morning, na san kilan
bacci kike lokacin da na fita" A hankali Khaleesat tace "Ya koma
Nigeria kenan?" Jay yace "Yeah in sha Allah" Khaleesat tace
"Toh Allah ya kai su lafiya" Jay yace "Ameen" duk wannan
maganar da take taki yarda ta kallesa balle har su hada ido, ya Ιan yi murmushi kamar bazai ce komai ba sai kuma yayi
kasa da murya yace "Ko sai mun yi auren zan cire maki wannan kunyan
naki?" Wani sabon kunyan ne ya kara lullebeta a motar, ta kauda kanta
kamar zata yi kuka tace "Ni dai bana so" Yana murmushi ya gyada kai
yace "Za ki yi bayani" Gaba daya Khaleesat ta zama so uncomfortable a
motar, Allah Allah take su isa makaranta ta sauka, shi dai lokaci lokaci yake
kallonta yana kara admiring din irin kunyarta, can dai yayi murmushi yana gyada
kai, suna isa makarantar bayan yayi parking Khaleesat ta bude motar, a hankali
yace "Halysaah" Bata fita ba amma kuma bata kallesa ba tana dai jiran
jin abinda zai ce, taji yace "To kalleni mana" Ta girgiza masa kai
still looking outside, yayi kasa da murya yace "Please" Ta marairaice
tace "Bazan iya ba" Yace "Please" Shiru tayi tana jin kamar
ya hadata da wani gagarumin aiki kallonsa da yace tayi, da gasken gaske
kunyarsa take ji yanxu, a hankali tace "Don Allah nayi latti fa" Yace
"To me yasa baza ki kalleni ba" Cikin sanyin murya tace "Zan
kalle ka anjima" Yace "A'a ni yanxu nake so" Shiru tayi tana Ιan murmushi tana kallon wajen motar, shi dai
kallonta kawai yake, sai da tayi gathering buhun courage sannan ta dake ta Ιan juya a hankali ta kallesa suka hada ido, she
could see nothing but her love in his eyes, sai yanxu ta kara fahimtar irin
kallon da yake mata tun bayan dawowarsa daga Nigeria, kallon so ne tsantsarta
yake mata, ya kashe mata ido daya yana murmushi yace "I love you" Ta
rufe fuskarta da mayafinta da sauri, sai kuma ta bude motar cikin hanzari ta
sauka ta kulle without turning back ta bar wajen ya bi ta da kallo, Jay was
sitted in the car for almost 15 mins ya kasa tafiya, nan kuma duk tunanin inda
Khaleesat zata zauna har ta gama Exams dinta yake don shi dai yasan a yanxu dai
bazai iya zama under the same apartment with her ba, he just can't, a sanda
suka zauna gida daya he had no feeling toward her, ganinta yake just as his
normal Housemate and nothing more, babu komai game da ita a ransa har ma sanda
suka samu encounter din farko da Abdul a apartment din, he is just being kind
and nice to her as a Housemate sannan kuma matsayinta na er uwarsa musulma from
Nigeria, ko a sanda ya biya mata kudin jirgi taje duba Ummanta yayi hakan ne
kawai saboda shi yasan girman mahaifiya don baya wasa da tasa, but outside of
their apartment bayan abubuwa sun faru tsakaninta da Abdul ya maidata gidansu
he gradually started developing feelings for her from nowhere, shi kansa bai
san ta yaya ba amma yafi tunanin tausayinta da ya saka a rai ne ya ja hakan, he
can't even say how everything happened all of a sudden and he fell deeply for
her tun period din da suke Exams dinsu, yanxu kuma bazai ce zai kai ta gidansu
ta zauna ba don baya fatan wani family member dinsa su sake ganinta a gidan, Ya
jinginar da kansa jikin kujeran motarsa ya lumshe idanuwansa cause he is so
confuse, yasan yanxu kam ba Ιa bane and
he won't risk staying in the same apartment with just the both of them inside,
yeah she need him to protect her from her Ex amma zuciyarsa bazai jure zama
gida daya da ita ba don yasan lallai na ukun su Shaidan zai zama, and getting
another apartment for her is not even an option, bude ido yayi jin wayarsa na
vibrate yana dubawa yaga Ajay ne ke kiransa, picking call din yayi ya kai kunne
kafin Ajay yace komai yace "Are you at home?" Ajay yace "Did you
come across my debit card?" Jay yace "Tare muke amfani da card din...
Are you home now cause i need to speak to you Ajay" Ajay dake sauraronsa
yace "Bout what?" Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "I will
be home now, kar ka fita ka jira ni" Yana fadin haka ya katse wayar ya
tada motarsa ya kama hanyar gidansu......
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa bello jidda*
Ur evidence 07087865788
https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM
Ajay na cin strawberry dake gefensa idonsa a kan movie din
da ake yi a TV, Jay ya dinga kallonsa kafin ya fixge remote ya kashe Tvn, Ajay
ya juya ya kallesa yace "Wai kunne ke ji ko ido? Ina fa sauraronka
Jawwad" Jay yace "If you are not giving me ur attention i will leave
this parlor, tun daxu ina magana hankalin ka na wani waje daban, what's all
this pls" Ajay ya tabe baki, sai kuma ya juya yana kallonsa direct in the
eyes yana ci gaba da cin Strawberry dinsa yace "Oya be fast pls"
Mikewa Jay yayi zai bar parlon Ajay ya fixgosa yace "Kai matsala ta da kai
kenan banzan zuciya, ba gashi ina sauraron ka ba" Jay yace "Kar ka
rena min hankali mana Malam" Ajay dai ya ci gaba da cin fruit dinsa yace
"Ka kashe Tv din ai, i am listening" Jay ya koma ya zauna, for peace
to reign yasa Ajay ya maida hankali yana sauraron maganar da Jay ke yi masa,
can ya Ιan yi murmushi ya jawo grapes
dinsa zai fara sha yace "This is weird... All of a sudden sai ka ji bazaka
iya zama gida daya da ita ba, why is that? Meye dalilin ka? Da ba apartment
daya kake zaune da ita ba some months ago, ko ni ban san gida daya ku ke ba sai
ranan da baka da lafiya, meye kuma ya canza ra'ayin ka all of a
sudden...." Jay yace "To yanxu bazan zauna ba, period! in zaka kawo
Suggestion din yanda za ayi ka kawo ina sauraron ka...." Ajay yace
"Ai ni dalilin hakan nake son sani" Jay yace "Ni dai babu ruwan
ka da dalilina kawai solution nake nema, just tell me yanda kake ganin ya
kamata ayi.... Tunda kaga we are not going to make the mistake of accommodating
her again in this House" Ajay yayi shiru, kamar bazai ce komai ba can dai
yace "Kai din dai ya kamata ka zauna a apartment din tare da ita, that's
the only solution for now tunda jarabawa za su fara, ko da za a samar mata
sabon Apartment definitely sai ya bi ta can din ma kamar yanda ya gano wannan,
da mun san haka kawai da a cikin makaranta aka biya mata accomodation to avoid
all this, wannan wawiyar kawar tata mara hankali kuma will just worsen the
situation idan aka ce taje can gidansu ta zauna, beside no one loves being
inconvenience in this state...." Jay ya sauke ajiyar zuciya, after a while
ya fixge remote din da Ajay ya dauka yana kokarin kunna TV alamar ya gama
maganarsa, Ajay yace "Na fa baka solution din da ka zo nema, ka bar ni in
ci gaba da abinda nake yi" Jay yace "I told you staying in the
apartment with her isn't an option Ajay, kaga kenan har yanxu babu
solution" Ajay yace "Wai saboda kana gudun ka ci gaba da rungumeta ne
yasa ka kasa zama gida daya da ita? To ai wannan norms ne a wajen ku tunda iya
runguma ce kawai..." Jay ya dinga masa wani kallo, Ajay yayi murmushi yana
gyara zama yace "Ko kuma kawai ka kira gida a daura maku auren, ko ni sai
in rakaka ka tare a can apartment din kawai" Jay yace "What is this u
are saying?" Ajay yayi dariya yana shan grape dinsa bai ce masa komai ba,
Jay dai kallonsa kawai yake, can Ajay ya daga kafada yace "Or better still
idan kanwar Baabarta na da Passport kawai ka nema mata visa idan Allah yasa an
bata sai ta zo ta zauna da ita har ta gama jarabawan....." Jay yayi shiru
kamar me nazarin abinda Ajay yace, after some seconds yace "What if ba a
bata visa din da wuri ba, sannan before Everything is process kasan zai Ιan dau lkci may be kafin nan ma sun fara
jarabawan" Ajay yace "To ni iya shawaran da zan iya badawa kenan, ban
san kuma yanda zaka yi ba, stop stressing me with ur problem plss" Jay
yace "Why not stay in the apartment with her, har zuwa sanda kanwar Mom
dinta zata zo" Ajay ya daga kai ya kallesa, can yace "Wa zai zauna a
apartment din?" Calmly Jay yace "Kai....." Ajay ya ajiye fruit
din hannunsa yace "Amma ka ma raina min hankali Jay, ni ne zan zauna da
ita a apartment din ga ni Bodyguard ko? Can you even hear ur self? kawai sai in
koma apartment dinta in zauna gadin ta saboda ni bani da aikin yi, in da gaske
neman me gadinta kake ka sa Salem ya koma apartment din da zama mana tunda ya
gama masters dinsa, after all she was sharing an apartment kafin ka santa a
kasar nan, so yanxu ma zata iya sharing da Salem as her Housemate" Jay ya
dinga kallonsa babu ko kiftawa, har ransa yaji zafin abinda Ajay yace wai ya
hada Khaleesat da Salem a gida daya, duk da ba wai Salem na da wani mugun hali
bane amma yaji haushin hakan sosai, har Salem din da bai masa komai ba sai da
yaji ya fara jin haushinsa a zuciya, mikewa yayi ya fice daga parlon kamar zai
tashi sama, Ajay ya taΙe baki ya ci
gaba da shan fruit dinsa ya jawo remote ya kunna TV.
Khaleesat na zaune tare da Safiyyah bayan sun gama lectures
wajen karfe shidda saura na yamma, ita dai sai kallon Safiyyah dake bata
labarin yanda Mustapha yace zai nemi Abdul duk inda yake ya basa hakuri don shi
baya son fitina a kasar mutane, cikin bacin rai Safiyyah ke bata labarin tana
cewa "Mustapha Ιata mana sunan family kawai
zai yi a zata mu coward ne matsorata, abun duk ya dameni wallahi, har da cewa
in na sake kula Abdul zai kira babana ya gaya masa, ni kuma tsoron old Man dina
nake wallahi...." Ita dai Khaleesat kallonta kawai take ba don tana
sauraron abinda take cewa ba, infact gaba daya ma bata san me take cewa ba,
kawai memories din jiya da daddare ne ke dawo mata a kai, ko karatun ma yau
bata san abinda aka yi ba sunan ta zo school ne kawai, kana ganinta kasan she
is in a very happy mood today, Safiyyah tace "Wai yau naga sai fara'a kike
kamar warce aka biya ma kujeran mecca, meye sirrin kawata, wallahi na zata idan
na shigo school zan ga idanuwanki sun kumbura don kuka tunda aikin ki kenan, amma
naga sai farin ciki kike kina nishadin ki, yau har da kula Coursemate dinmu a
Hall kamar ba ke ba" Khaleesat tayi murmushi tana wasa da zoben hannunta
tace "To saboda me zaki ga idona ya kumbura don kuka?" Safiyyah tace
"Akan issue din Abdul mana, ai nasan halin ki sai ki iya kwana kina
kuka" Khaleesat ta taΙe baki har
sannan tana murmushi tace "That was then, I don't have time for that now
Safiyyah, ni fa na ma dena tsoron nasa yanxu, kuma ba abinda ya isa yayi
min...." Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Nagode tawan, don
Allah a wani kasuwan kika siyo liver din nan naki me shegen kyau?"
Khaleesat bata san sanda tayi dariyan ba ita ma tace "Allah da gaske i am
not afraid of him any longer Safiyyah" Safiyyah tace "Ko ke fa, yanzu
tun asali da haka kike ai babu me taka ki kawata, amma naji dadin wanda ya
siyar maki da liver din nan har kika samu kwarin gwiwa...." Shiru Safiyyah
tayi ta daga kai tana kallon Abdul that is coming toward them, tuni Khaleesat
ta hade rai bayan ta gansa ita ma, ta fara tattara reading materials dinta a
jaka, ta dau jakar tana kallon Safiyyah tace "Mu je Sophie" A tare
suka mike Safiyyah na taΙe baki,
Khaleesat na fara tafiya Abdul ya riko veil dinta yana kallonta yace "Don
Allah ki bani minti biyar mu yi magana Khaleesat" Ta juya ta kallesa
fuskarta a murtuke tace "Let go of my veil Abdul" Yayi kasa da murya
yace "Plss Khaleesat, i want to say one or two words, don Allah ki bani
lokacin ki ba don ni ba" Fixge veil dinta tayi a fusace kafin ta bar wajen
kawai taga ya shige gabanta yana mata magiya yace "Don Allah fa nace maki
Khaleesat, ko minti biyu ne ki bani" Safiyyah dai ta koma gefe tana wani
dariya kamar taga wawan zama, lallai Abdul ya zama abun dariya yanxu don
tsakaninsa da Allah ya marairaice ma Khaleesat, Khaleesat ta juya tana jin
zuciyarta na tafarfasa zata bi daya direction din taji ya riko hannunta this
time around, bata san sanda ta juyo ta sauke masa mari a fuska ba, cikin fushi
tace "Baka da hankali ne Abdul?" a hankali ya sake hannunta don bai
ma san hannunta ya rike ba, yana kallonta calmly yace "I am sorry
Khaleesat, I didn't mean to...." Tuni ta juya ta bar wajen kamar zata
tashi sama, Safiyyah da ta saki baki hangangan ta bi Khaleesat da kallo,
slapping Abdul was the least thing da tayi zaton Khaleesat zata iya yi a
rayuwa, Safiyyah ta kalli Abdul da ya zauna inda Khaleesat ta tashi ya rike
kansa, bin bayan Khaleesat tayi har sannan ta kasa rufe baki with shock, ita
kuwa Khaleesat ta sha kunu Kamar bata yi komai ba tana ta tafiyarta, bayan sun
yi nisa a hankali Safiyyah tace "Khaleesat?? Did you just slap him?"
Without looking at Safiyyah tana ci gaba da tafiyarta tace "He asked for
it, don me zai rike min hannu, ko bashi da hankali ne" Safiyyah da ta bude
baki tace "Don Allah wa ya koya maki haka? Dama kin iya haka all this
while kike maida kanki rubabbiya ake taka ki yanda aka ga dama? I still can't
believe your action Khaleesat, Omg" Khaleesat ta tsaya ta ciro wayarta
dake vibrate, number Housemate dinta ta gani dama kuma she was expecting his
call don shi yace ta jira zai zo ya dauketa, tayi picking call din ta kai
kunne, after some seconds tace "Eh mun gama tun daxu" Safiyyah dai
kallonta kawai take da mamaki har ta gama wayan, sannan Khaleesat ta kalleta
tace "He came to pick me, mu je sai yayi dropping din ki tunda hanya daya
ne" Safiyyah ta rike haΙa tace
"Ni fa na kasa yarda marin Abdul kika yi da gaske, don da bana wajen aka
yi ko jikina kunnuwa ne bazan yarda ba, ko ni duk fitina ta bazan yi gigin
marin Abdul ba wallahi" Khaleesat ta hade rai tace "Ni dai don Allah
mu tafi, kawai yayi ta bibiyata a makaranta yana daga min hankali for what
reason? babu komai fa tsakanina da shi yanxu don me bazai bari inyi rayuwata
irin na kowa ba, i am fed up with this" Hawaye ne ya ciko idonta ta fara
gogewa tana ci gaba da tafiya, Safiyyah dai tayi shiru tana bin ta, don yau kam
Khaleesat ta goge mata hadda tasss, a haka suka karasa inda Housemate yayi
parking motarsa, yana ganinsu ya sauko daga kujera me zaman banza, Safiyyah na
washe baki ta gaishesa ya amsa da murmushi fuskarsa yace "Ya lectures din?
Ko kuma ince revision, since exams is around the corner" Safiyyah tace
"Alhamdulillah Yaya Jawwad" Juyawa yayi ya kalli Khaleesat, ganin
mood dinta nan da nan fara'ar dake fuskarsa ya bace, ita kuwa Safiyyah sai
gwale ido take bayan ta hango Ajay zaune driver seat, shi kuwa dama tun da ya
hangosu da Khaleesat ya toshe kunnensa da ear pod yana kallon gabansa,
Housemate na kallon Khaleesat ya bude mata back seat, cikin sanyin murya ta
gaishesa sannan ta shiga motar, ya kalli Safiyyah yace "Tun da hanya daya
ce ki shiga mu ajiye ki ko?" Safiyyah na kirkiran murmushi ta girgiza kai
tace "A'a akwai wata Coursemate dinmu da nake jira akwai reading material
dina a wajenta" Jay yace "Alright Safiyyah sai anjima" Daga haka
ya bude front seat ya shiga, Safiyyah ta daga ma Khaleesat hannu sannan ta jefa
ma Ajay harara duk da ko kallon inda take bai yi ba, ta juya tayi wucewarta,
Allah ya rabata shiga mota daya da fitinannen nan, kila ma tana dosana kugunta
a kujeran motar zai ce ta fita, in ya mata haka kuma tsaf zata masa rashin
kunya ita kam, to ina dalili, gwara da ta kama kanta taki bin su.... Bayan sun
bar school din Jay ya kasa daurewa ya juya yana kallon Khaleesat yace
"What happened Housemate?" Khaleesat ta girgiza masa kai alamar ba
komai, yace "No there is something, why are you Moody? Tell me pls, wa ya
bata maki rai?" Kamar Khaleesat bazata ce komai ba, sai kuma ta sauke
idonta tace "He still followed me again today" Ta madubin mota Ajay
ya kalleta jin abinda tace, Housemate yace "Sai me ya faru kuma?"
Khaleesat tace "Rike min hannu yayi wai in tsaya in sauraresa ni kuma na
maresa nayi tafiyata" Ba Housemate dinta ba, Hatta Ajay sai da ya bude
baki yana kallonta ta madubi, Jay was totally speechless yana kallonta, can ya
juya ya kalli Ajay, Ajay yace "Kika maresa? Saboda baki da hankali zaki
maresa? Ana kokarin protecting dinki by all means kina kara jawo ma mutane
aiki? nasan wannan baΖar kawar
taki ce zata zuga ki ta koma gefe tana kallo, dama kuma nace idan kika ci gaba
da mu'amala da ita sai ta ja maki bala'in da yafi karfin ki don ban ga alamar
tana da seti ba yarinyar nan, kina er mitsitsiyar ki zaki daga hannu ki mari
gabjejen mutumi haka ko tsoron tsayinsa baki ji ba, da kika maresa sai ta fara
hailing din ki ko..." Kuka Khaleesat ta fara yi a motar kamar jira take,
Jay ya juya ya kalli Ajay yace "Look Ajay, no one is above mistake, we all
make mistake, don haka ba gigitata zaka yi ba, she is frustrated shi yasa tayi
hakan, so we shouldn't blame her...." Ajay ya wani kallesa sannan ya maida
dubansa kan titi bai sake tofa nasa ba a cikin motar, Jay ya kalli Khaleesat
dake kuka, cikin kwantar da murya yace "Ki kwantar da hankalin ki
Housemate, babu abinda zai maki in sha Allah, i am giving you assurance,
marinsa da kika yi kuma baki yi kuskure ba shi ya ja ma kansa" Ta gefen
ido Ajay ya kallesa bai dai ce uffan ba, Ita dai Khaleesat kuka kawai take a
hankali har suka isa apartment dinta, sauka tayi daga motar ta nufi kofar
apartment din ta bar su cikin motar. Jay ya kalli Ajay yace "You are not
suppose to scold her that way, she is already frustrated, cikin kwantar da
murya ya kamata ayi mata gyara, beside ita yarinya ce fa har yanzu" Sai a
sannan Ajay ya juya ya kallesa yace "A'a, sha'awar gado ce" Jay bai
sake ce masa komai ba a motar, bayan kusan minti daya ya kallesa yace "Ka
shiga ciki... let me get some food from the restaurant for her, kai nasan zaka
yi sorting kanka out, there is everything available at the kitchen" Ajay
yace "Wait pls, ni kaji nace maka na amince da tsarin ka ne da kake wannan
bayanin?" Jay yayi shiru yana kallonsa, can yace "Pls ka daina maido
da magana baya Ajay, i tot we are done with all this, nayi ma Aunty Farida
magana daxu tace bata da passport, but getting a passport isn't an issue, Visa
ne babban damuwan yanxu, kasan baza a samu da wuri haka ba" Ajay yace
"Yanzu me kake nufi? Shikenan ni sai inyi inconveniencing din kaina in
takura rayuwata just to please you? Bayan ka fi kowa sanin ba ko ina nake zama
comfortably inyi rayuwa ba, You know how irritating everything can be to me,
why not consider me?" Jay yace "I will make the apartment very
Comfortable for you to stay, beside i will be coming around too, wata daya ne
fa an gama exams din...." Ajay yace "To wai ba na baka shawaran kawai
kayi ma mai martaba magana a daura maku aure ba? What are you still waiting
for?" Jay yace "Me yasa kake mantawa da Mamina ne? I didn't birth my
self, har yanxu fa Mami bata san komai kan wannan maganar ba, i need to speak
to her about it face to face ta yanda zata fahimce ni... After their exams dama
tare za mu koma Nigeria, so i can speak to Mami" Ajay ya Ιan yi murmushi ya shafa gashin kansa bai dai ce
komai ba, Jay dake ta kallonsa yace "Meye ma'anar hakan?" Ajay ya
daga hannu da sauri yace "Nothing..... Just wishing you luck" Jay bai
sake cewa komai ba kuma bai fasa kallon Ajay ba, after some seconds yace
"Ban taΙa nuna ina son abu Mami taki
abun ba ko da bai mata ba, she is after nothing but my happiness, bata da kowa
sai ni, farin cikina shi ne first priority dinta, kuma kai ma kasan da wannan,
you can attest to that" a hankali Ajay ya jinginar da kansa jikin kujeran
motar keeping silent.....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah*
Ur evidence 07087865788
_We sell all kind of spices like grand masala, 7 mixed
spice, all purpose spices, Mandy spices, biryani, pepper soup spice, ginger
mix, Curry, suya spice and tsire mix all at affordable prices_
_Siyan daya ko sari, contact +234 803 298 6552 for more
info_
https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM
Wajen karfe sha daya na dare Khaleesat na zaune saman
gadonta tana karatu a laptop din gabanta, ba sosai take gane karatun ba saboda
yunwan da take ji, abincin da Housemate dinta ya siyo mata daxu Ιan kadan ta ci a ciki don bai mata dadi ba, tayi
tagumi tana kallon slide din gabanta, kofar dake kallon nata taji kamar an
bude, ta juya tana kallon nata kofar, after almost 5 mins ta sauka daga saman
gadon ta dau hijab dinta har kasa ta saka sannan ta nufi kofa zata je kitchen
ta hado shayi, dama tun daxu ta kasa fita ne don kar ta hadu da Housemate dinta
a parlor, don yanxu wani kunyansa kawai take ji, a hankali ta bude kofar ta
fito corridor tana tiptoeing, tana fara sauka downstairs ta tsaya da mamaki
tana kallon Housemate dinta dake kwance 3 sitter idonsa a lumshe, duk da ba
wuta me haske bane kunne a parlon amma tsaf take iya ganinsa, juyawa tayi ta
kalli dakin dake kusa da nata with confusion, ko dai kunnenta ne yaji kamar an
bude kofar dakin? Lokaci daya taji gabanta yayi mugun faduwa bayan Abdul ya fado
mata a rai, kaddai Housemate dinta mance kofar yayi a bude yayi bacci, tana
cikin wannan tunanin zuciyarta na bugawa aka bude kofar dakin dake kallon nata,
wani kara ta kurma a mugun tsorace tun ma bata ga wa zai fito daga dakin ba,
Jay ya mike da sauri yana kallonta, sai kuma ya nufeta da mamaki yace
"What happened Housemate?" Tana hada ido da Ajay da ya fito daga
dakin shi ma yana mata kallon mamaki ta durkusa wajen ta fara kuka tana jin har
lkcn zuciyarta bai dawo dai dai ba, tuni Jay ya karasa inda ta durkusa yana
kallonta yace "Me ya faru?" Tana kuka a hankali ta daga idanuwanta ta
kallesa tace "Tsoro ya bani ai, ni na zata fa ya tafi daxu..." Ajay
yaji kamar yayi ball da ita ta gangara downstairs tsabar yanda ta bashi haushi,
don shi kansa sai da ihunta ya juya masa kai, Jay dai kallonta kawai yake ya
kasa cewa komai ma, Ajay ya fara saukowa downstairs fuska daure yace
"Tashi ki ban waje kar inyi ball dake a nan, silly gal" Turo baki
tayi tana goge idonta ta basa hanya yayi tafiyarsa downstairs ya bar su a
wajen, ta Ιan daga kai a hankali ta kalli
Jay dake ta kallonta ya ma rasa me zai ce, boye fuskarta tayi da hijab din
jikinta tana lekosa ta Ιan space din
da ta bari a hankali tace "Kayi hakuri, ni wallahi ban san a gidan nan zai
kwana ba shi ma, na zata ya tafi tun daxu" Murmushi yayi mata, calmly yace
"It's fine Halysaah, you need something?" Ta gyada masa kai, a
hankali tace "I want to take tea" Yace "Ohk, let me get you
some, ki koma dakin ki" Tana murmushi cikin sanyin murya tace "Thank
you" Daga haka ta juya ta koma sama zuwa dakinta, shi kuma ya sauka
downstairs Ajay ya bi sa sa kallo har ya shiga kitchen, kwafa yayi ya dau
remote ya kunna TV, after some minutes Jay ya gama hada mata tea ya debar mata
cookies a plate sannan ya tafi sama, Ajay ya taΙe
baki ganin yanda ya maida kansa Boy Boy dinta kawai, alhalin ko 5% din
treatment din nan baya yi ma Hadiyah, Jay na kai mata shayin sama yayi knocking
ta fito ta amsa amma ta kasa kallonsa, cikin sanyin murya tace "Nagode
sosai" Kai kawai yayi mata nodding, slowly yace "Good night
Halysaah" Ta juya ta koma cikin dakin ta kulle kofar. Washegari wajen
karfe tara na safe Khaleesat ta sauko downstairs bayan tayi wanka ta shirya duk
da bazata je school ba ranan, kallonsa ta dinga yi yana kwance saman kujera ya
rufe fuskarsa da karamin towel ya kife wayarsa a kirji, karasawa tayi har inda
yake kamar tana son gano wani abu, lokaci daya ya cire towel din fuskarsa suka
yi ido hudu, komawa baya tayi with shock tana Ιan
zare ido tace "Ohh, I tot it's my Housemate" Ya mike zaune yana
kallonta babu yabo babu fallasa yace "Kin taΙa
ganinsa da wannan kayan? Ko kuma ina wasa dake ne?" Ta Ιan langwabar da kai tace "To ai dai bazan san
ba shi bane, since you are having the same height and complexion with him"
Yace "I could slap you idan baki fita a gabana ba Malama" Ta wani taΙe baki ta nufi kitchen, irish ta diba ta fere wanda
zata yi using, tana yanke yanken veggies da zata soya kwai da shi a ranta tana
mamakin Why Ajay is in the house instead of her Housemate, kawai daga jiya zuwa
yau ya mata masifa sau biyu, turo baki tayi ta ajiye wukan sai a sannan ta zaro
ido ta dau irish dinta ta zuba a man gyada da ta dora don har ta manta da man
gyadan, rufe baki tayi da hannunta jin fire alarm din kitchen din ya dau ruri,
gaba daya ta mance da shi, don in dai zata yi soye soye wani lokacin lullubesa
take da Shower cap dinta ta yanda bazai yi detecting komai ba balle ya fara
tona mata asiri yana ruri, ta juya ta fito daga kitchen din tana kallon Ajay
kamar munafuka tace "Don Allah ka zo ka min stopping din alarm din ya
dena" Ajay yace "A'a ki dai kona masu gida ni ina ruwana, kin zata a
Nigeria kike ba" Ta marairaice tace "Don Allah mana, kaga it's very
loud fa" Ko kallon inda take bai sake yi ba, ta juya ta koma kitchen din
tana kallon inda smoke alarm din yake, ita bata ma san ya ake kashewa yayi
shiru ba, ta rage abun girkin zata sake komawa parlor ta masa magana ta kusa
cin karo da shi zai shigo kitchen din, komawa gefe tayi tana kallonsa har yayi
silencing smoke alarm din sannan ya fita daga kitchen din, Khaleesat ta sauke
ajiyar zuciya ta ci gaba da girkin da take yi, bayan ta gama ta fito daga
kitchen din dama iya wanda zata ci da Housemate dinta kawai tayi, tana kallon
Ajay tace "Housemate dina fa?" Bayansa ya nuna mata alamar gashi ya
goya shi, juyawa tayi ta wuce sama ya bi ta da wani kallo, tana shiga dakinta
ta dau wayarta ta zauna gefen gado tayi dialing number Housemate dinta, yana
fara ringing ya daga, in his calm voice yace "Good morning Halysaah"
Ta Ιan yi murmushi kamar yana
ganinta ta fara wasa da gefen duvet dinta a hankali tace "Good
morning" Yace "How was your night?" Tace "Alhamdulillah,
naga baka nan" Yace "Yea i went to get something, i will come over
later" Tace "I made some breakfast for you" Yace
"Really" Tayi shiru bata ce komai ba don har ranta ta so ya ci
breakfast din, yace "Ohk give me 30 mins zan dawo sai in ci" Tayi
murmushi har sai da dimples dinta ya lotsa tace "Toh Allah ya kawo ka
lafiya" Katse wayar tayi sannan ta mike ta fita daga dakin ta koma downstairs,
bata ko kalli Ajay ba tayi wucewarta kitchen ta ajiye ma Housemate dinta nasa
breakfast din ta dau nata ta fito, hada ido suka yi ta sauke idonta har zata
wuce sai kuma ta Ιan kallesa tace "There is
everything available in the kitchen, idan kana son kayi making breakfast for ur
self" Ya juya ya kalleta yace "Kee, ki shiga hankalin ki, ni ba Jay
bane" ita dai tayi tafiyarta sama bata ce masa komai ba. Da yammacin ranan
Khaleesat na kitchen tana stew taji an danna bell, fitowa parlor tayi amma ta
kasa karasawa gun kofar gabanta na faduwa, kaddai Abdul ne ya biyota, tunawa da
tayi Ajay na gidan sai kuma taji hankalin ta ya kwanta, amma dai bata karasa
gun kofar ba tana tsaye inda take, sama ta kalla ganin Ajay na saukowa
downstairs, bai kalli inda take ba ya nufi kofar ya bude, Safiyyah ta koma gefe
ganinsa ta fara kame kamen yafa mayafinta tace "Yaya Ajay ina wuni" A
takaice yace "Lafiya" still kuma bai bata hanya ba, yana tsaye bakin
kofar, Ta Ιan sosa kai tace "Kwana
biyu nace ko laifi nayi maka da ban sani ba Yaya Ajay" Kamar bazai ce
komai ba, sai kuma yace "Kin taΙa Ιaga hannu ke kin mari namiji da har kika zuga
kawarki tayi hakan?" Safiyyah ta gwalo ido ta cire handbag dinta a kafada
tace "Na rantse da Allah ba da sanina tayi haka ba, ta yaya zan zugata?
yanxu ma wallahi zuwa nayi zan mata fadan abinda tayi bata kyauta ba, ita
Khaleesat bata jin magana kwata kwata ne, ko ni bazan daga hannu in mari lukeke
irin Abdul ba, i am trying my best in dinga sakata a hanya amma abun yaci tura,
ka tambayeta wallahi ni bani nace ta maresa ba" Ajay yace "Daga ke
har ita za ku san yanda za ku yi da shi duk ranan da ya cafke ku a kasar
nan..." Yana kai wa nan ya juya ya bar bakin kofar, Safiyyah ta tura masa
maki, sai kuma ta shiga parlon tana gwale ido, ganin Khaleesat a tsaye a parlon
sai kuma ta washe baki, suka zauna a nan parlon Khaleesat na tambayarta daga
inda take ganin uban gayun da ta ci, kasa kasa take bata labarin Birthday din
karen wani coursemate dinsu da taje da yanda masu karnuka ke ta zuwa da nasu ita
kuma bata da ko mage balle kare, can tace "Da na sani na su Housmate na
ara na tafi da shi wallahi" Khaleesat don takaici ma ta kasa ce mata komai
sai kallonta take, Safiyyah tace "Har hotuna fa sai da muka yi da karnuka
gwanin ban sha'awa in gaya maki" Khaleesat ta taΙe
baki ta mike ta tafi duba stew din da take yi, bayan ta fito ta ajiye ma
Safiyyah drink din da ta dauko mata ko zaunawa bata yi ba Safiyyan tace
"Me jarababben nan ke yi a gidan ki, ina Yaya Housemate din mu?"
Khaleesat bata san sanda ta fashe da dariya ba don Ajay yana bakin stairs a
tsaye, kamar Safiyyah ta sani ta juya da sauri tana ganinsa ta sinne kai kamar
munafuka, dai dai nan Housemate ya shigo parlon, Yana shigowa Ajay ya nufi kofa
ya fice alamar dai shi yake jira dama, Safiyyah ta gaida Housemate da fara'arta
tana masa sannu da zuwa, ya amsa ya karaso ya zauna parlon yana kallonta yace
"Social function kika je ne haka" Tayi dariya har da tafe hannu tace
"Eh wallahi birthday din karen wani coursemate din mu na je" Jay yayi
murmushi yace "To sannu da dawowa" Tace "Shi ne nace bari in
biyo ta nan, kwana biyu ban san me nayi ma Cousin dinka ba sai yayi ta Ιaga min hanci idan ya gan ni...." Jay ya shafa
kansa yace "Don't mind him, wani lokacin haka yake" Safiyyah ta taΙe baki tace "Gaskiya abun nasa ba kyau..."
Jay ya Ιaga ido ya Ιan kalli Khaleesat dake tsaye parlon tana kallonsa
kamar ranan ta fara ganinsa, suna hada ido ta tura masa baki ta juya tayi
wucewarta kitchen ya bi ta da kallo, duk Safiyyah na kallonsu tana Ιan murmushi, sai kuma ta rataye jakarta a kafada
still smiling tace "To ni zan koma gida Housemate, kafin yayana ya fara
kirana" Jay ya maida dubansa kanta yace "Kin jima da zuwa ne?"
Tace "Ai ko minti goma ban yi ba, Cousin dinka ne ya bata min mood dina
don ban ji dadin abinda yayi min ba, kawai albarkacin ka ya ci yasa na danne
zuciyata, har fa da ce min ni nake zuga Khaleesat a America, abun nan ya min
ciwo wallahi" Housemate na murmushi yace "Kiyi hakuri, but kinsan me
Safiyyah.... Don Allah ko da kun sake haduwa da shi a school kar ki ce zaki yi
wani sa'insa da shi" Safiyyah tace "Wai Abdul?" Yace
"Eh" Tace "Ai tun da yayana ya hanani ban sake ba wallahi, ko
zagina yayi iyaka in kira masa 911 kar yaje ya min wani mugun abu, amma na dena
kulasa" Yace "Good...." Mikewa yayi yace "Let me talk to
your frnd in the kitchen" Tana Ιan murmushi
tace "Ohk" Kitchen ya nufa bayan ya shiga ya kulle kofar ya jingina
jiki ya rungume hannu yana kallon Khaleesat dake goge goge a kitchen din bayan
ta gama stew din da take yi, ta kasa juyawa ta kallesa, a hankali yace
"Weldone Halysaah" Ta Ιan yi
murmushi kawai, yace "Let drop off your friend at home" Ta gyada masa
kai alamar to, yana kallonta yace "Sai mu je park daga can ko?" Sai a
sannan ta Ιan kallesa, sai kuma tayi
murmushi ta juya masa, shi dai kallonta kawai yake, after some seconds a
hankali yace "Get ready ina jiran ki" Daga haka ya bude kofar kitchen
din ya fita, Tsaye ya tarar da Safiyyah tana jiran su fito ta kama gabanta don
bata gane irin wannan kallon da taga suna ma juna ba, Jay yace "Ki jira ta
shirya sai mu yi dropping dinki a gida" Komawa tayi ta zauna tana murmushi
tace "Ai ko Nagode, bari in maza inyi cancelling ride dina" Yace
"Idan ta shirya ku sameni a Garage" Safiyyah tace "Toh"
Fita yayi daga parlon, Khaleesat na fitowa kitchen Safiyyah ta gaya mata abinda
Housemate dinta yace, a tare suka tafi dakin Khaleesat, Safiyyah ta zauna gefen
gado tace "I wish i have freedom like you in this country...."
Khaleesat tayi murmushi tana duba kayan da zata sa tace "Yanxun ma ai abinda
kika ga dama kike yi, gashi har da zuwa birthday din Dog" Safiyyah tace
"A'a wallahi, kinsan da yanda na fito yau kuwa, ni da ma ayi sacking
Mustapha a wajen aiki su tattara su koma Nigeria" Khaleesat bata san sanda
tayi dariya ba, tana fiddo kayan da zata canxa Safiyyah tace "Waow, dadina
dake in kika so akwai fashion, kina sa wannan kaya ai har ku dawo gida
Housemate bazai gaji da kallonki ba" Khaleesat tace "To bazan sa
ba" Zata maida kayan Safiyyah ta tare press din dakin tayi bake bake a
wajen tace "Ke dalla wasa fa nake maki" Da kyar Safiyyah ta lallabata
ta saka kayan daga karshe, bayan nan still tayi forcing dinta ta Ιan yi mata light make up a fuska, Safiyyah ta koma
gefe ta rike haΙa tana kallonta tana nazarin
ace ita Allah ya ba kyan Khaleesat irin abubuwan da zata yi a duniya ai sai
Allah, can ta sauke wani nauyayyen ajiyar zuciya tace "Kullum kika yi
sallah ki dinga gode ma Allah Khaleesat, he created you differently, wallahi
you are so beautiful...." Khaleesat ta wani kalleta, sai kuma ta tsaya
gaban madubi tana duba abinda zata goge a fuskarta, just eye pencil da powder
kadai Safiyyah ta shafa mata, sai lip gloss shi ma lightly, ta ma rasa abun
gogewa a fuskar tata, cause there is nothing special, a hankali Safiyyah dake
ta kallonta tace "Ji fa lips dinki wani ba sai ya rantse kin shafa jan
baki ba kawata, wallahi ki dinga addu'a idan zaki fita don nasan mutane ne
daddaya basa tanka ki a zuciya idan kika fita suka gan ki, duk da dai nan kasar
kowa ma da hasken sa" Safiyyah ta zaro ido tace "Lahhh, mun bar
Housemate dinki a garage tun daxu fa" Khaleesat ta marairaice mata tace
"Ni wallahi kunya nake ji Sophie, i am not comfortable with the dress and
the make up" Safiyyah tace "Naga jaraba, idan ku ka yi auren haka zaki
dinga kunyar tasa?" Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah ta ma kasa
cewa komai, Safiyyah ta fixgo hannunta bayan ta tayata daukan handbag dinta ta
ja ta suka fita daga dakin, har suka fito daga apartment din Khaleesat taki
sakin jiki, Safiyya ta karΙe makullin
apartment din a hannunta tace "Tafi ki shiga mota zan kulle gidan"
Khaleesat taki tafiya, haka kawai aje bata kulle kofar da kyau ba Abdul ya samu
hanyar shiga gidan, Safiyyah ta gama kulle kofar ta juya tana kallon Khaleesat
tace "Don Allah ki dena yin abu kamar yan unguwan ku mana, America fa ne
nan" Khaleesat ta kai hannu handle din kofar ta murda taji sa a bude, wani
kallo tayi ma Safiyyah ta kwace makullinta ta kulle kofar da kyau, Safiyyah
tace "Oho na zata ya kullu, mu je" Tunda Khaleesat ta nufi garage
Housemate ke kallonta babu ko kiftawa, Safiyyah da taya bera bari ta bude mata
front seat tana murmushi, Khaleesat ta wani kalleta sannan ta shiga motar ba
tare da ta bari sun hada ido da Jay ba, Safiyyah ta koma bayan motar ta shiga,
he wants to compliment her amma yayi shiru saboda Safiyyah, ya fara driving
yana kallonta lokaci lokaci, daga karshe ya kasa hakuri yace "You look
beautiful Halysaah" Safiyyah dake bayan motar ta fara blushing kamar ita
aka ce ma haka, tana Ιan murmushi
tace "Nima na gaya mata wallahi, amma ta zata am just pulling her legs,
nace mata kyanta na daban ne a cikin kyawawa, duk mijin da ya aureta ya more a
rayuwa, ko bacin rai yake ya kalleta zai ji ransa yayi fari Ζal, kuma ace ta samu miji me kyau kamar yanda dae
kake din nan, waiiiii Allah kadai yasan yanda kids din ku za su zama don
kyau..." Khaleesat taji da ma kawai hakura tayi da fitar nan gaba daya
tsabar kunya, shi kam Jay murmushi kawai yake idonsa akan titi yana driving,
Safiyyah ta bude jakarta ta ciro wayarta ganin Mustapha ke kiranta ta danna
wayar a silent a fusace ta mayar cikin jaka, Jay ya kalli Khaleesat yayi kasa
da murya yace "Wani park din kike son mu je?" Karaf a kunne Safiyyah,
tace "Park za ku je Yaya Housemate" Yace "Yeah Safiyyah" Safiyya
tace "To aje da ni mana don Allah sai in zama photographer" Khaleesat
ta dafe kanta, Jay na murmushi yace "To nawa za a biya ki for the
Job?" Ta kyalkyale da dariya tace "Haba, ko er lemonade ne kawai a
siya min" Yana dariya yace "To an gama, amma baza a kira ki a gida
ba?" Tace "A'a ba wanda zai neme ni wallahi" Ko da suka isa park
din Safiyyah taki yarda ta zauna kusa da su Khaleesat wai za su yi
inconveniencing dinta tana son ta nutsu tayi enjoying ambience din wajen da
kyau, Khaleesat tasan duk scope din barin ta daga ita sai Jay ne yasa Safiyyah
tace haka, shi ko Jay yaji dadin hankalin da Safiyyah tayi a nan, hotuna tace
zata fara masu kar yamma yayi sosai, dadi kamar zai kashe Safiyyah ganin
azababben kyan da hoton da ta fara masu yayi, can ta karasa inda suke tsaye tace
"Ba fa wanda zai tsaya a space din nan da ku ka bari a tsakaninku gwara ku
cike sa kawai" Khaleesat ta wani kalleta, Shi dai Jay Murmushi kawai yayi,
Safiyyah tace "Ka Ιan matsa
kusa da ita kadan Yaya Housemate so that the space won't make the picture look
somehow" Slowly ya matsa kusa da Khaleesat yana kallonta yana murmushi,
Khaleesat ta ganta er karama a kusa da shi ga daddaden kamshin turarensa da ya
cika ta, tuni Safiyyah ta koma baya da gudu ta ci gaba da daukan hoton da take
tana washe baki, farin ciki kamar ya kasheta, haka ta dinga controlling dinsu
wajen daukan hotunan, tace su koma can, tace su dawo nan, ta tabbatar tayi masu
hotuna masu bala'in kyau, har dai daga karshe Jay yace mata ya isa ita ma ta
shigo su yi hoton, zai ba wata er Africa dake wajen wayarsa ta masu hoton har
Safiyyah amma Safiyyah taki shiga tace "A'a kar in bata maku hoto ina baΖa da ni" Dariya Housemate yayi haka dai ya
lallabata ta shigo aka yi masu hoton su uku, Safiyyah na murmushi tace
"Amma fa tunda nake daukan hoto ban taΙa
daukan wanda ya dauku kamar hotunan nan da na maku ba wallahi" Jay na
murmushi yace "Dollar nawa za a baki to?" Dariya tayi ta tattara
lemonade dinta da tacos da ya siya mata tace "Wannan ma da aka siya min
Allah ya amfana" Daga haka ta kara gaba ta bar masu wajen, Jay was amaze
at how Safiyyah snapped the pictures so well, ya kasa daina kallon Khaleesat a
hoton, the pictures where so beautiful, Khaleesat tun da ta kalli hoto daya ta
kasa ci gaba da kallon sauran ta koma ta zauna kawai, after a while ta daga ido
ta Ιan kalli Jay taga kallonta
yake, da sauri ta maida kanta kasa, a hankali yace "Halysaah" Bata
dago kanta ba still tace "Uhm" Yace "Me yasa baki sakin jiki da
ni yanxu? You weren't like this before, ko don nace zan aure ki?" Sunkuyar
da kanta tayi alamar kunya, yace "To meye amfanin zuwa nan tunda baza ki
saki jikin ki ba, i want us to have a quality time together amma kiyi ta
sunkuyar da kai...." Tana murmushi a hankali tace "To ai kunya nake
ji" Yace "To kalleni zaki dena jin kunyan" Taki dagowa tayi
shiru, yace "Halysaah" Tace "Ni bazan iya ba" Bai sake ce
mata komai ba, ganin haka ta daga idanuwanta ta kallesa taga kallonta yake,
murmushi yayi mata murya can kasa yace "You are specially made
Halysaah" Rufe idonta tayi tana murmushi a hankali tace "Thank
you" Yace "Kin dai ji me kawarki ta ce ko?" Khaleesat ta daga
ido ta kallesa tace "Me ta ce?" Yayi kasa da murya yace "We will
make beautiful Babies together...." Khaleesat ji tayi wani azababben kunya
ya rufeta, yana murmushi yana kallonta yace "Ni ko guda daya kika bani me
kama dake i will appreciate..." Kamar zata yi kuka tace "Ni dai mu
tafi gida" Yace "A'a sai kin ban labari, kina ban labari ko daya ne
sai mu tafi" Shiru tayi, sai kuma tana wasa da straw din drink din gabanta
tace "Wani irin labari?" Yace "Ko ma wani iri ne, ko kuma ki
bani labarin yanda ku ka hadu da Funny frnd dinki Safiyyah" Khaleesat tayi
murmushi ta dago kai tace "Ohk...." Babu bata lokaci ta fara basa
labarin farkon haduwarta da Safiyyah a school, shi dai kallonta kawai yake ko
kiftawan kirki baya yi, everything about Khaleesat is just beautiful and
breathtaking, tsakaninta da Allah take ta basa labarin Sophie ashe ko sanin
abinda take cewa bai yi ba ya kafeta da ido with many imagination running his
mind, daga bada labarin Safiyyah kawai ta saki jiki a wajen, dama kuma haka
yake so... kamar yanda ya so hakan ne ya faru don they had a wonderful time
together, labari sai wanda ta manta ne bata basa ba a kan experience dinta a
America tun daga shekaran da ta zo har zuwa yanxu, wani yayi dariya, wani yaji
tausayinta wani ya ga wautan ta, babu abinda ya kara burgesa da ita tana basa
labarin sai turancin ta, she was so vocal, duk da timidness dinta she was very
outspoken kamar ba a unguwan nan da gidansu yake ta tashi ba, he never knows
she speak so well sai yau, yayi kasa da murya yace "You know what
Halysaah?" Ta girgiza masa kai tana kallonsa, a hankali yace "I love
you so much" Rufe fuskarta tayi da sauri tana murmushi... Sai wajen karfe
bakwai suka bar park din, sai da suka fara dropping Safiyyah a gida before
heading home, Jay na parking Khaleesat ta kalli motar Ajay dake parking Space,
can ta kalli Jay tace "Is he waiting for you?" Jay yace "I don't
think so, kinsan yana da aboki a Neighborhood din nan shi ma PhD yake, the frnd
is at the far end of this street, External defense dinsu is around the
corner...." Khaleesat tace "Ohk har da kai?" Jay yace "Yea
in sha Allah, period din exam din ku ne Defense dinmu" A hankali tace
"To Allah ya baku nasara" Yana murmushi yace "Ameen" Tace
"To a ina zaka yi parking since he is occupying the space?" Yace
"Zan je gida in dawo anjima" A hankali tace "To ni kadai a
apartment din?" Yace "Ga motar Ajay kina gani, ai yana ciki
kenan" Shiru tayi tana kallonsa, ya mata murmushi yace "Mu je in raka
ki ciki to" A tare suka sauka daga motar ya rakata har cikin apartment
din, yana kallonta calmly yace "Can i go now?" Jingina tayi da bango
a kusa da shi ta langwabar da kanta kawai ta marairaice tana kallonsa, ya sauke
idonsa daga kallonta trying to calm his self down, a hankali yace "I need
to go Halysaah, ki kulle kofar" Daga haka ya juya ya fita daga parlon
without looking at her, ta bi sa da kallo kafin ta kulle kofarta....
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and
u send ur evidence of payment
07087865788 ππ», it's better ki ji tsoron Allah ki sauke
nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika
karanta with no payment i owe you 500*
Bayan Khaleesat tayi karatun da zata yi ta kashe laptop
dinta ta ajiye sannan ta saka hijab ta fito daga dakin don tun da ta dawo bata
ci abinci ba gashi har karfe goma ya wuce, downstairs take leke ko zata ga
Housemate dinta, Ajay ta gani yana danna wayarsa, hannunsa rike da Can din soft
drink, tana ta tsaye a corridor din don da ba don yunwan da take ji ba komawa
dakinta kawai zata yi ta hakura da abincin, after a while ta fara saukowa
staircase din trying not to make any sound, tun daga nesa take kallon screen
din wayarsa ganin kamar hoton da suka yi da Jay daxu a park, tsaye tayi tana ta
kallon wayarsa da mamaki, after some seconds taga ya fita daga hoton kasa gane
inda ya samu hoton tayi, tasan dai Jay bazai tura masa pictures din ba, to
kaddai a status Housemate dinta ya dora hoton, ta shiga uku, sosai taji gabanta
ya fadi, lokaci daya Ajay ya juya bayan yayi sensing kamar mutum na tsaye
bayansa, ta Ιan koma baya kamar munafuka
tana kame kame tace "Kitchen zan je dama" Ajiye wayarsa yayi ya juya
da kyau yana kallonta da mamaki, ta langwabe kai sai kuma ta nufi kitchen din
da sauri tana Ιan waigen sa, ko da ta fito
bata gansa a parlon ba, bayan ta koma daki ta ajiye shayin hannunta ta dau
wayarta da sauri ta bude WhatsApp dinta, status din Housemate dinta ta bude
taga hoton amma ya rufe fuskarta with the caption "Halysaah" da yayi
ma hoton, to amma wanda ta gani a wayar Ajay fuskarta a bude yake, ta dinga
kallon hoton duk da fuskarta a rufe yake, bata san sanda murmushi yayi escaping
lips dinta ba don sun yi kyau sosai, har ta ajiye wayar sai kuma ta dauka tayi
masa reply din picture din tace "What if gal frnd dinka ta gani"
ajiye wayar tayi ta dau cup din shayin da ta ajiye tana juyawa a hankali, taji
wayarta yayi vibrate alamar shigowar message, daukan wayar tayi taga ya mata
reply yace "Ke ba Gal frnd dita bace? Ai ke zabina ce, ita kuma zabin
iyayena" Hmm kawai ta mayar masa sannan ta kashe data dinta ta ajiye
wayar, lokaci daya duk jikinta yayi sanyi tana maimata zabin iyayensa da yace a
ranta, duk yunwan da take ji haka nan ta neme sa ta rasa shayin ma bata wani
sha sosai ba, bayan ta gama shirin kwanciya ta dauro alwala ta fito sannan ta
kashe wutan dakin ta kwanta, wayarta taji na vibrate ta jawo wayar a hankali
tana dubawa taga Housemate dinta ne ke kiranta, sai da ya kusa katsewa tayi
picking call din ta kai kunne tayi shiru, yace "Why did you go offline
Halysaah?" Ta Ιan yi murmushin karfin hali
tace "Na je nayi alwala ne zan kwanta" Yace "Ohk, kina da class
gobe ne?" Ta Ιan yi shiru, duk da bata da
shi tace "Eh ina da...." Jay yace "Yaushe?" Tace "Da
safe" Yace "Ohk, na tsaya wani aiki ne a system dina shi yasa ban
dawo ba, may be we will meet in school tomorrow in sha Allah" Tace
"Allah ya kai mu" Yace "Ameen, Good night Halysaah, naga kamar
kin fara jin bacci ko?" Cikin sanyin murya tace "Uhm, sai da
safe" Yace "Allah ya kai mu lafiya" Daga haka ya katse wayar sa,
Khaleesat ta ajiye wayar hannunta ta juya ta lumshe ido. Da safe Khaleesat na
saukowa downstairs taga parlon soo tidy, kamshi sai tashi yake ta ko ina via
diffuser da ta gani a parlon, makalewa tayi jikin staircase tana ta kallon
parlon, ai kuma ta shiga uku da gori, after a while ta nufi kitchen, ta window
din kitchen din take kallonsa don karamin garden ne a waje, entrance din garden
din yana ta wajen Garage, tunda ta zo apartment din bai fi sau biyu ta shiga
wajen ba, press up yake yi a wajen, juyawa tayi ta kalli Yoghurt da diff kind
of berries da granola da nuts sai kiwi and apple dake ajiye kitchen din, nan ta
gane parfait zai hada, har zata hada masa wata zuciyar tace ta kama kanta tayi
abinda zata yi ta fita, noodles ta dauko zata dafa, tana cikin dafa noodles din
ta daga kai taga ya fita daga garden din, bayan ta gama girkin ta fita daga
kitchen din zuwa dakinta, after almost 20 mins ta sake saukowa downstairs ta
shiga kitchen din, har sannan fruits din suna wajen, ta Ιau
karamin bowl ta fara tsinkar different berries din wajen ta yanda bazai gane ta
taΙa masa ba, tana wankesu a sink
ta fara sha, da sauri ta juya tana kallon kofar kitchen din tayi ido hudu da
shi, ita kanta bata san dalilin da yasa ta fara dariya ba, ta ciro berry din da
ta kai baki tace "Wanke maka su zan yi fa, so that i can help you dice
them" Tana fadin haka ta ajiye bowl din hannunta ta dau wuka zata fara
fere Kiwi fruit dake wajen, taji yace "Zo ki fita ki ban waje" Ta Ιan kallesa tace "I want to help you wash
them...." Tana ganin kallon da yayi mata, ta ajiye wukan ta wanke hannunta
a sink sannan ta ajiye masa bowl din Berries din da ta diba a kofar sauran
fruits din, kofa ta nufa ta bi gefensa ta fita daga kitchen din ya bi ta da
kallo yace "Ke da baki iya gyaran gidan da kike ciki ce zaki wanke ma
mutum abinda zai ci" Khaleesat ta juya ta kallesa dama tasan sai yayi
maganar nan, tace "Tun da kai ka gyara ba shikenan ba, ai don ina zuwa
school ne...." Yace "You are dirty dai Malama, do not use school to
cover ur untidiness" Yana fadin haka ya karasa cikin kitchen din, ta tsaya
bakin kofar tana kallonsa taga ko da Liquid wash zai wanke fruits din karewar
tsafta, sai da ya fara tura bowl din Berries din da ta diba zuwa can far end of
the kitchen yanda bazai dinga ganinsa a kusa da shi ba sannan ya fara wanke
fruits din a sink, bayan gishiri har da Venegar yayi using wajen wanke fruits
din, a ranta tace to ai wannan ba sabon abu bane kowa na yi, ita tsakaninta da
Allah take jiran taga ya zuba liquid wash wajen wanke fruits din, amma taga bai
yi hakan ba, tana ta tsaye jikin kofar kitchen din har ya gama hada lafiyayyen
parfait dinsa, ta shiga kitchen din ta dau bowl din Berries dinta da ya
gantalar gefe daya ta ajiye kusa da shi ta kallesa, ko kallonta bai yi ba, can
ta ga ya jawo sauran Yoghurt da ya rage ya tsiyaya mata a bowl din ya ci gaba
da abinda yake yi, dariya ya bata amma ta dake bata yi ba, tana ta kallon rich
parfait dinsa da yaji fruits da Granola da Nuts, tana kallo ya dau zuma ya
tsiyaya a kai, dai dai nan aka bude kofar parlor, ya ajiye zuman hannunsa ya
karasa kofar kitchen din don ganin wanda ya shigo, da sauri Khaleesat ta kai
hannu ta lakaci honey din da yoghurt, akan idonsa don har ya juyo ya dawo cikin
kitchen din, komawa baya tayi da sauri, bai ko kalleta ba ya dau spoon yayi
scoping dai dai inda ta saka hannu sannan ya ajiye spoon din a sink, ita dai
bata san ya aka yi ba kawai ganin bowl din parfait din tayi ya kife a kasan
kitchen, ya koma baya yana kallon parfait babu ko kiftawa, tun tana daurewa har
ta kasa ta dafe base cabinet din kitchen din ta tuntsire da dariya kamar an
aikota, Ajay dai kallon Parfait din kawai yake a kasan kitchen din, after some
seconds ya shafa kansa trying not to laugh too, don dariyarta kadai ya isa ya
saka mutum yayi dariya bai yi niyya ba, irin dariyar muguntar nan kawai take
yi, ita kuwa ba abinda ya bata dariya ganin bai tsam mata ba gashi duk sun
tuntsire a kasan kitchen, kuma shi ya kifar da kayansa da alama, kawai ya juya
ya fice daga kitchen din ta bi sa da kallo tana kyalkyala wani sabon dariya,
sai kuma ya sake dawowa yana kallonta yayi kasa da murya yace "Kin ga idan
ina abu a kitchen kika sake shigo min i will fling you out of this window, ai
ni ban san ke mayya bace" Yana fadin haka ya sake ficewa daga kitchen din,
Khaleesat dai bata fasa dariyan da take ba, da ta kalli bowl din da ya Ιan tsiyaya mata zallan yoghurt sai ta kalli rich
parfait dinsa dake kasan kitchen a kwance, sai ta kara kwashewa da dariya, ta
dade abu bai bata dariya kamar haka ba, tayi dariyarta ma'ishi sannan ta fara
gyara kitchen din, sai kuma ta fara jin tausayinsa don duk effort dinsa bai sha
ko spoon daya ba, gwara ita ta Ιan lasa zuma
da yoghurt, the incident was so funny to her, haka duk ta kwashe fruits din da
granula dake kasa tayi disposing a shara, bayan ta gama goge kitchen din ya
dawo fess ta fito parlor taga Housemate dinta zaune a parlon yana danna
wayarsa, tana murmushi ta karasa cikin parlon ta zauna sannan ta gaishesa, ya
daga kai ya kalleta ya amsa, bata sake cewa komai ba, shi ma haka, after a
while yace "Ba kince zaki school da safe ba?" ta langwabar da kai
tace "Kawai fasawa nayi" Juyawa tayi ta kalli Ajay dake saukowa downstairs
fuskarsa babu yabo babu fallasa yana rike da makullin motarsa, ta bi sa da
kallo trying not to start another laugh har ya fice daga parlon, sai kuma ta
kalli Jay ta fara basa labarin abinda ya faru a kitchen, she couldn't hold her
self anymore ta dinga kyalkyala dariya har da saukowa daga saman kujera, shi
dai Jay kallonta kawai yake, sai kuma ta dena dariyar da take tace "Isn't
it funny?" Jay yayi murmushi wanda iyakarsa lips yace "It is, sai
yace maki me?" Tace "He was very shock too, nasan da ya san abinda
zai faru kenan da ya debar min, Allah ne ya kamasa, ga shi yayi stressing kansa
ya gyara gidan nan gaba daya yau" Tana dariya ta kare maganar, Jay yace
"Gaskiya ne, amma baza ki je school ba me yasa kika ce min za ki je?"
Shiru tayi, sai kuma tace "Kawai da gari ya waye na canza mind" Jay
yace "Ohk" Wayarsa ne ya fara vibrate ya mike yace "Zan fita sai
anjima" Khaleesat na kallonsa tace "Kayi breakfast ne?" Yace
"Nayi" Tace "Ohk, byee" Juyawa yayi ya nufi kofa ta bi sa
da kallo har ya fita.... Khaleesat na kitchen da yamma bayan ta dawo school
taji an bude kofar apartment dinta, sosai taji gabanta ya fadi don dama tunda
ta dawo taga ba kowa apartment din take a tsorace, sai da taji muryar Ajay a
parlon sannan hankalinta ya kwanta, jingina tayi jikin cabinet din kitchen din
tana kirga kwanakin da taga Jay last, after a while ta kashe wutan girkin don
ta gama, ta dan leka parlon taga Ajay da wani abokinsa ne bayerabe yana gwada
masa abu a Laptop dinsa da alama shima Phd yake yi, fitowa tayi daga kitchen
din ta gaida abokin ya amsa yana kallonta, sai kuma ya kalli Ajay yace "Is
she ur sister" a takaice Ajay yace "Yeah" Yana ci gaba da nuna
masa abinda yake nuna masa, da broken English abokin yace bazai basa ita ya
aura ba, Ajay ya daga kai ya kalli Khaleesat yace "Ke dalla malama wuce ki
ba mutane waje" Khaleesat ta kallesa da mamaki don ita dai ba tsayuwa tayi
a parlon ba, sama ma zata wuce, Femi na kallon Ajay yace "I am very
serious Prince, i will marry her as far as una go give me, she's very beautiful,
is she Halfcast?" Ajay yace "Meet Jay about that Femi" Femi ya
gyara zama yace "Jay no get joy at all, he isn't as straight as you"
Ajay yace "He will listen, since it's about you marrying his
sister..." Femi yayi dariya sosai yace "I will definitely visit
Bauchi soon be that" Ajay dai bai sake ce masa komai ba.
A kwana a tashi lokacin Exams din su Khaleesat ya matso don
satin da za su shiga za a fara jarabawan, tun ranan da ta mari Abdul har zuwa
yau bata sake ganin ko giftawarsa a school din ba, ita dai har sannan
hankalinta yaki kwanciya don gani take kawai jira yake ta koma Nigeria before
doing anything to her, sosai tayi da ta sanin marin da tayi masa, she wish bata
yi hakan ba, da kawai ignoring dinsa ta dinga yi since he is not harming her,
da ta tuna sati biyu kawai za su yi suna jarabawan sannan ta koma Nigeria sai
taji jikinta yayi sanyi sosai, During all this time haduwanta da Jay ya ragu
sosai ba kadan, ko apartment din nata sai in zai kai mata abu yake zuwa kuma ba
dadewa yake yi ba, but tayi masa uxuri tunda yace mata su ma a wannan period
din ne External defense dinsu may be he is concentrating on that and also
giving her space to concentrate on her own studies too, amma abinda ke bata
mamaki kafin taga Ajay da laptop ko wani abu da zai nuna karatu yake sau daya
to ta gansa da remote din TV da bowl din fruit yana ci yana kallon football ko
wrestling sau goma, gashi kamar baya bacci, abokansa kuwa in suka xo baya
shigowa da su apartment din.... Ranan Friday Khaleesat na school tare da
Safiyyah suna studying course din da za su yi exams dinsa ranan Monday, hadari
ne sosai a garin, Khaleesat tace "Mu je apartment dina sai mu ci gaba da
karatun a can ko?" Safiyyah tace "Tabb, ni ce zan je apartment din ki
wannan Uztaz din na nan? Ni har yanxu kin ki gaya min dalilin da yasa suka yi
switching da Housemate din ki" Khaleesat na kallonta tace "To ta yaya
nima zan sani, na tambaye Housemate dina yace kawai sbda he is busy because of
his upcoming defense ne baya samun time sosai he is always in the Library"
Safiyyah tayi dariya tace "Shi kadai zai yi defense din? Shi ma Ajay ba
defense din zai yi ba ko ba lokaci daya za su yi bane? Ni har na gano dalilin
da yasa yaki zama a apartment dinki wallahi" Khaleesat tace "Meye
dalili?" Safiyyah tayi dariya tace "Gaskiya na kara respecting
Housemate dinki, wallahi iya da addini da sanin ya kamata, kinga a baya ai babu
komai tsakaninku shi yasa ku ke zaune kowa na harkar gabansa a tsohon Apartment
din ki, iyaka kuyi mutunci, yanxu kuwa da ya fara son ki yana tsoron kada
shaidan yayi using Opportunity din zaman ku gida daya ya cuce ku, kinga hakan
bazai haifo Ιa me ido ba, gaskiya yaya
Housemate iya da addini" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba sai
ma murmushi da tayi kawai, Safiyyah tace "Abinda ya guje ma kenan kawai ba
wani abu ba, don shi zuciya ba shi da Ζashi,
shi kuma Ajay masifarsa da fitinarsa kadai ma bazai sa ya shiga harkar ki ba a
gidan, shi fitinarsa ma zai iya zuke mutum wallahi" Khaleesat na maida
wayarta cikin jaka tace "Sai ka masa abinda baya so yake masifa ai, he
just love being on his own kar a shiga harkarsa that's all, but he is kind,
caring and down to earth, sai da muka zauna yanxu na gane haka" Safiyyah
ta saki baki tana kallonta, can ta gyara zama tace "Ikon Allah, yau ke
kike yabon Ajay da kanki, to me da me yayi maki da kika ga he is caring and
kind zaman ku a apartment din naki" Khaleesat ta daga ido ta kalleta, can
tace "Kilan baza ki yarda ba idan na fara gaya maki wallahi" Safiyyah
tace "Ai ina jin ki, gaya min yanda aka yi kika gane hakan in ga ko zai yi
convincing dina..." Wayar Khaleesat ya fara vibrate a jaka, ta bude jakar
ta ciro wayar, Safiyyah ta leka screen din don ganin me kiranta, sae kuma ta riΖe haΙa tace
"Ikon Allah"
_Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa bello jidda Ur
evidence_
07087865788
*Hakika duk wacce ta Bari aka barta abaya ita taso domin mu
mata da ado da kwalliya aka sanmu.
Assalamualaikum, barkanmu dai Yan uwana ma masu albarka, ayau na zo maku
da batun sababbin kayan da na kawo Mana
masu matukar kyau da kuma inganci,oum eman collection π€π,
takawo maku jakunkuna da takalma,hadi da abayas da kuma sarkoki masu matukar
kyau da kuma sauki,07018872587
Ena amare da uwayan gida masu capacity's toh duk wacce ta yarda da
tacika mace da wacce takeso ta zamo ma abociyar kwalliya toh ta garzayo gunmu
domin hadewarki cikin ado da kwalliya kedai nemeni a wannnan number domin
kisami kayayyaki masu kyau da kuma quality akan kudi kalilan hajiyata
07018872587 ngd π€ ado da kwalliya shine takenmu*