ZANEN DUTSE CHAPTER 5 BY AISHA-SHAFIEE
ZANEN DUTSE CHAPTER 5 BY AISHA-SHAFIEE
Www.bankinhausanovels.com.ng
ASALIN LABARIN.+
Kowanne labarin duniya yana da tushe. Kowanne yana da mafari. Me kenan? Wani abu da ya faru har ya zama sanadin wanzuwar jirkitattun al’amura.
Zahra Tabi’u. (Farin Wata)2
YOLA, Jimeta.
Shekarar 1987.
Motar Ζirar Peugeot ce 305, mai kalar ruwan Ζasa sabuwa dal sai Ζyalli take cikin hasken safiyar da rana bata gama buΙewa sosai ba, fitilar danjojinta a kunne suke yayin da Ζarar horn ke fita daga cikinta alamun matukin na jiran a bude masa tangamemen gate din ginin dake gabansa wanda a samansa aka zana harafan sunan ‘Sectariate’ (Sakateriyar Ζaramar hukumar ta Jimeta)
Minti daya, biyu, sai gate din ya bude cikin sauri motar ta kutsa ta karasa ciki.
“Allah ya huci ranka yallabai, Allah ya Ζara girma, ayi mana afuwa wallahi muna can ciki ne ana tattauna wani al’amarin da ya faru.”
Dattijon da ya bude kofar ta fada cikin durkusawa yayin da hannunsa ke dunkule a iska yana kallon matuΖin cikin motar wanda yaja ya tsaya bayan shigarsa ciki.
Alhaji Ahmad Uba Kamsusi wanda ke riΖe da muΖamin ‘H.O.D Community Development’ anan cikin sakateriyar ya juyo ya kalli maigadin da mamakin daya maye gurbin Ιacin ransa kafin yace.
“Wane al’amari ne ya faru?”
Lawan maigadi ya sake sunkuyawa.
“Wallahi yallabai yaro su Haruna suka tsinta a can ta baya wajen da ake kiwon shanun nan Ιazu da asuba, to shine ake ta jajanta zancen.”
“Yaro? Wane irin yaro Lawan?”
“Alhaji wallahi yaro dai, dan mutum, zai kai kusan shekaru huΙu a Ζiyasi, kuma anyi maganar duniyar nan yaΖi cewa komai balle a san dagaina yake, tunda tun da duhu a gari shi Harunan ya ganshi tsakanin shanu biyu yana bacci.”
Maganar ta Ιan tsaya a ran Alhaji Ahmad kafin ya girgiza kansa yace.
“Allah ya sawwake.”
Sannan yaja motarsa zuwa ciki, Ζaton waje ne mai dauke da Ζ΄an gine-gine tsilli-tsilli na mabanbantan ma’aikatu kamar dai kowacce sakateriya take, ga bishiyu fal na darbejiya da wasu dangin na Ζ΄aΖ΄an itatuwa, daga gaba ne ma kaΙai wajen yake da katanga da kuma gate, amma zuwa can Ζarshe baya ya haΙe ne da dajin da zai fidda kai har wani bangare na cikin garin yola.
Alhaji Ahmad ya Ζarasa gaban ginin ofishinsa ya ajiye motarsa sannan ya fito, sai dai saΙanin yadda a kullum yadda zai zo ya tarda da ofishin nasa a bude masinjansa ya share ya jera abubuwa, sai arba yayi da katon kwaΙon da bai taba ganinsa ba, ya sani cewa akwai muΖullin kwaΙon a cikin na wajensa, amma maimakon ya buΙe sai ya zagaya ta baya don neman wanda zai tambaya yaji lafiyar masinjan nasa, tunda a jiya sun rabu lafiya Ζalau kuma bai taba ganin ya makara irin haka ba.
Ai kuwa yana zagayawa ta baya, sai ga Musa, wani matashi dake aikin kula da shuke-shuken wajen yana jan ruwa, bayan Musan ya gaishe shi be sai ya tuntuΙe shi da tambayar inda Iliya masinjan nasa yake.
“Ai yallabai can na baro shi Ιazu wajen yaron nan da aka tsinta, da yake yana wajen sanda su Haruna suka kawo shi, kuma naji dai suna maganar tafiya wajen mai unguwa, to bayan na taho dai ban sani ba ko sun tafin.
Alhaji Ahmad ya tsaya da mamakin wane irin yaro ne haka da za’a tsinta kuma gabadaya hankalin ma’aikatan yayi kansa? Kamar ya juya ya koma ofishinsa sai kuma ya sake kallon Musa yace.
“Kaini in da suke naga yaron.”
Musa ya ajiye gugan hannunsa sannan yayi gaba tinkis-tinkis suka dinga bi ta kan barandun gine-ginen wajen har zuwa wajen harabar ginin masallaci, inda bishiyu suka yi wajen Ζawanya, iskar safiya na ratsa ganyayyakinsu tana fitar da wani Ζamshi mai daΙi.
STORY CONTINUES BELOW
Daga bayan masallacin ya tadda dandazon mutane wanda mafiyawancinsu masu aikin wajen ne sai kuma tsilli-tsillin ma’aikata irinsa wanda suma da alama zuwansu kenan suka tsinci zancen.
“A’a yallaΙai, da kanka? Ashe ka samu labari kenan? Wallahi yanzu isowata kenan nima Lawan maigadi ke sanar dani nace bari nazo na gani.”
Cewar Alhaji Isah, wani ma’aikaci shima a cikin sakateriyar, mai yawan son burga da nuna iko yana magana muΖullin motarsa Ζirar marsandi a hannu sai kaΙa shi yake yi. Alhaji Ahmad ya gyaΙa kansa sannan yace.
“Allah ya sawwaka, ni ai har na karasa ofis sai na ganshi a Ζulle Iliya bai buΙe ba, na tambaya kuma akace yana nan shine nace to bari inzo in gani me akeyi ne haka.”
“Wallahi fa ranka ya daΙe…” Alhaji Isan ya faΙa, yana kiransa da inkiyar da kowa a ma’aikatar ke laΖaba masa ta ‘yallaΙai’ ko kuma ‘ranka ya daΙen’ sanin cewa shine Ιa na farko a wajen mai martaba sarkin Kiyari.
“Yaro ne Ζarami na ganshi, kuma ba hausa ba fulatanci, anyi masa yare kala-kala ma ya kasa mayarwa, kuma an rasa wanda ya sanshi, to shine wai suka yi masa wanka zasu kaishi wajen mai unguwa ayi cigaba da cigiya.”
Alhaji Isah ya rufe bakinsa daidai lokacin da wasu ma’aikatan da suka iso a lokacin ke Ζarasowa wajensu don suma su ji ba’asin me ke faruwa. Alhaji Ahmad yasa aka kira nemo masa Iliya a cikin mutanen wanda ya Ζaraso da sauri yana mai neman afuwa.
“Je kace su Ζaraso mana yaron mana nan su ganshi.” Alhaji Isah ya faΙa cikin nuna son iko irin nasa tun kafin Iliyan ya gama durkusawa.
Iliya ya juya da sauri ya nufi can gefen masallaci, Ζ΄an mintuna kaΙan sai gashi tare da wasu mutane biyu sun nufo inda suke, kums tun kafin su Ζaraso idanun Alhaji Ahmad suka gano masa yaron dake riΖe a hannunsa, Ζarami ne kamar yadda suka siffanta don ba zai fi shekaru hudun ba, sai dai bai san me yasa ba idonsa ya kasa Ιaukewa daga kansa ba har sanda suka karaso gabansu, yaji muryoyinsu na gaishe shi amma har a lokacin yaron yake kallo.
Daga ganinsa zaka kiyasta cewa yana da jikin da yafi nasa girma, amma wataΖila saboda wahala ko yunwa, ya rame Ζwarai har wuyansa na nunawa, idanunsa madaidata ne, masu aheΖi kamar ya tara kwalla a ciki yayin da suke jujjuyawa kan dukkan mutanen dake tsaye a wajen.
“Wallahi yallaΙai a tsakanin shanu biyu muka dauko shi, da fari da kyar ma muka yarda mutum ne sai da duhun asuba ya yaye tukunna sannan muka ganshi sarai! Yanzu ma Lado ne ya kawo kayan Ιansa aka canja masa da yake na jikin nasa sunyi datti kwarai.”
Cewar Ιaya daga cikin mutanen kenan, yayin da yake bayanin suna duban yaron.
“Yanzu gidan Mai unguwan zaku kaishi kenan?” Alhaji Isah ya tambaya.
“Eh yallabai, don anyi masa tambayar duniyar nan baya iya mayarwa, to can zamu kaishi in Allah yasa anyi sa’a, sai a samu iyayensa.”
Mafi yawan mutanen dake wajen suka hada baki da fadin ‘Allah ya kyauta’ kafin kowa ya juya ya nemi hanyar ofishinsa.
Sai dai har sanda Alhaji Ahmad ya isa cikin nasa ofishin, fuskar yaron nan bata bar wulgawa a ransa ba, mamaki yake mai haΙe da tunanin yadda iyayen Ιan Ζaramin yaro kamar haka zasu yi sake dashi har ya baro gida a cikin duhun asuba haka, a halin da ake ciki shekararsa uku kenan da aure babu haihuwa, kuma a yadda suke Ζulafucinta shi da matarsa, baya hango cewar ko sun haifi guda goma zasu iya wannan gangancin.
Haka yayi ayyukansa a daddafe a wannan ranar ya koma gida, fuskar Ιan talikin yaron nan bata bar ransa ba, kuma duk tarin ayyukan da yaci karo dasu a kwanakin da suka biyo baya basu kore waΙannan kyawawan idanun yaron ba.
Ζ³an kwanaki kaΙan bayan hakan sai ga Iliya masinjansa ya shigo da tsakar rana.
“Iliya ya akayi? An karbo min sako na daga layin Jodan?”
STORY CONTINUES BELOW
Iliya ya kai har kasa a gefen teburinsa kafin ya amsa.
“Eh ranka ya dade shirin tafiyar naje dama, to sai Haruna kuma yazo da wani zance.” Ya faΙi haka yana Ιan sosa bayan kunnensa.
Ba tare da ya Ιago ba ya tambaya.
“Zancen mene ne?”
Iliya ya sake Ζasa da muryarsa.
“Wallahi Alhaji akan yaron da aka tsinta ne kwanakin baya, to bayan an kai shi can gidan mai unguwar anyi neman duniya ba’a sami ko da wanda ya sanshi ba, shi kuma yaron yaΖi yayi magana har yanzu, to shine mai unguwar yasa aka dawo dashi yace wai wallahi ya daina riΖe yara irinsa saboda wai ana samun matsala daga baya, kuma a yanzu haka ma gaskiya da yara da yawa a wajensa, ba zai iya Ιaukanr nauyinsa ba.
To shine yanzu Harunan yake neman kudin mota wai zamu je mu kai shi gidan marayu na can kan hayi, sai nace bari in tambaye ka yallaΙai ko zamu samu Ζ΄an canji aje a kai yaron…”
Tunda ya fara magana Alhaji Ahmad ya ajiye biron da yake rubutu ya Ιago ya kalle shi.
“Yanzu ina yaron?”
“Suna can bakin gate ranka ya daΙe don basu ma shigo dashi ba.”
“Je ka ce su kawo shi.” Kai tsaye ya faΙa ba tare da wani tunani ba. Kuma shima Iliyan bai yi wani tunani ba ya mike da saurinsa ya juya.
Alhaji Ahmad yabi kofar da kallo abubuwa da yawa na wassafawa a tunaninsa, tausayin yaron dake kwance a Ζasan ransa ya sake tasowa, wannan wace irin masifa ce? Ace har kwana nawa iyayen yaron nan basu neme shi ba, ashe shi yasa ya kasa mantawa dashi?
Mintuna kaΙan sai ga Iliya sun shigo dashi da Haruna da kuma yaron, kallo daya Alhaji Ahmad yayi masa ya tabbatar da cewa inda aka kaishi Ιin babu wani canji daga wahalar da ya fito, wataΖila ma sai Ζarin rashin kwanciyar hankali da fargaba don waΙannan idanun nasa da ya kasa mantawa dasu sun Ζara Ιashewa cikin maiΖonsu
Wani Ιari na zuciyarsa ya matse tare da tunkudowar wani abu da bai gama tantance shi ba a lokacin, abinda ya sani kawai shine, gidan marayu ba maslaha bace game da yaron, rayuwarsa zata cigaba da tafiya ne babu wani bigire mai inganci. Sai yaji cewa kamar Allah ya nuna masa wata alama ne da zai iya kare hakan daga faruwa ta hanyarsa, don da ace ba wajen sa suka zo neman kuΙin motar nan ba da wataΖila a yanzu haka ma suna titi.
“Yaka zo.”
Kai tsaye muryarsa ta kira yaron dake rakuΙe a hannun Iliya yana kallon sa cikin rauni.
A lokacin guda tsananin mamaki da da kaduwa ta sanya su Haruna da.l Iliya buΙe bakinsu, don tun daga lokacin da suka tsinto shi, yaron baya taΙa gane dukkan maganar da ake masa, amma sai gashi a yanzu ya saki hannun Harunan ya nufi wajen Alhaji Ahmad, wani abu daya dasa mafarin rubutacciyar Ζaddarar dake ajiye a gurin Allah, domin a take a wajen zuciyar Alhaji Ahmad bata nemi shawarar kowa ba ta yanke hukuncin karΙar yaron, su kansu su Iliya sunyi mamakin jin hakan don har aka gama fafutukar cike-cike a ofishin gidan marayun inda suka hadu suka tafi gabaΙaya basu bar tunanin cewa Alhaji Ahmad zai iya fasawa ya canja ra’ayi ba.
Sai da ya buΙe gidan gaba na motarsa ya bude ya sanya yaron a ciki ya ja motar zuwa hanyar gidansa, sannan zuciyarsu ta tabbatar da zahiri.
Su suka tsaya suka bada shaida mai kyau akansa bayan an debi duk wasu bayanai da manya da Ζanana nasa, sannan dasu aka tabbatar cewa zai riΖe yaron tsakaninsa da Allah kamar yadda yayi alΖawari kuma wataΖila hakan ne ya faranta ransa har yayi musu kyauta mai tsoka bayan fitowar tasu.
***
Hafsat Muhammad Gani.
Matashiyar budurwa ce dake tsananin ji da kanta a bangaren kyau da kuma dukiya ta mahaifinta wanda ya kasance hamshaΖin Ιan kasuwa. Tayi tashe mai tsawo a zuciyoyin Ζ΄an siyasa da kuma Alhazawan da suke ganin sun isa su mallake ta, sai dai Allah baiyi ita Ιin rabon kowa bace sai Alhaji Ahmad Uba Kamsusi, Ιa na farko a wajen Sarkin garinsu da kowa ke mutuΖar darajawa.
STORY CONTINUES BELOW
Sun haΙu ne a watarana da ta raka mahaifiyarta fada don halattar tafsirin Ζarshe na azumin watan ramadana, anyi sallar magriba har ma an raba Ιimbin kayan cima kala-kala a matsayin kayan shan ruwa, ana dab da fara tafsirin ne ta biyo hanyar soro na uku don komawa sashen da suka sauka na matar Galadima ta dauko jakarta.
Ta shiga soron a daidai sanda ma’aikatar wutar nepa suka zabi lokacin don su dauke wuta, sai kawai ji tayi taci karo da mutum yana tahowa, tayi baya zata fadi amma sai taji hannu ya tare ta.
“Idan waje babu haske, ki dinga tsayawa har sai hasken ya dawo ko kuma ki juya.”
Mai maganar ya faΙa cikin wani irin sauti mai kwarjini. Sai tayi saurin yin baya ta fita daga hannun nasa sannan tace.
“Kaima ya kamata kayi amfani da hakan don ka daina buge Ζ΄aΖ΄an mutane a cikin duhu.”
“Wanda ya san hanyarsa bashi da matsala musamman a gidansu, Ζ΄aΖ΄an mutanen da basu san koina ba su ya kamata su dinga kiyayewa.”
Ya faΙi hakan a daidai lokacin da hasken wutar ya dawo, don daman Ιaukewar tata bata wuce wasu Ζ΄an sakanni, Hafsatu ta Ιago ido ta kalli wanda ke tsaye a gabanta, wata fuska da ko yaro mai rarrafe a Kiyari ya santa, fuskar da ko a jiya da safe data je kaiwa mahaifinta shayi, akwai ta a jikin jaridar da yake karantawa.
Shi kadai kwallin kwal! Amma ya cika rabin soron a idanunta, sanye yake da rantsatstsun kayan da samari mara sa aikin yi zasu iya musu har da zage-zage akan tantamar farashinsu, sai tayi saurin sadda kanta kasa sannan tace.
“Ayi hakuri ranka ya daΙe.”
Mafarin kenan! Domin ba’ayi sati ba sai da yasa aka nemo ta har cikin gidan mahaifinta da wani bayani mai girma, wani bayani daya haddasa farin ciki a zuciyar iyayenta dama duk wanda ya raΙe su, wani bayani da yasa ta tattara duk wasu samarinta sababbi da tsoffi ta zuba a kwandon shara, don Ahmad shi kaΙai yana da duk wani qualities da guda ashirin Ιinsu suka tara, to me take nema dama? KuΙi, Ιaukaka, mulki, wayewa dama duk wasu Ζananan abubuwa da mace zata iya hasashensu a mijin da take fata.
Tana tuna wannan lokacin kamar jiya, bidiri da bikin da aka sha sai da labari ya mamaye garuruwa cewa ita din tayi aure na girma! Wani aure da har a yanzu da ake lissafin shekaru bata ga makamancinsa a kurkusa ba.
Ta gama yanka tufa ta Ζarshe ta rufe farantin, a yanzu Ζarfe shida ne na yamma, aikin Ahmad na Ζananan hukumomi ne, don haka a kodayaushe cikin canje-canjen wajen zama suke, Ιadinta shine tun bayan da suka baro gidansu inda aka yi mata jere, kayan sawarta kawai take dauka a duk sanda aka canja masa wurin aikin, suna tadda komai a gidan da zasu tare. Don haka tun bayan dawowarsu Jimetan Ζarfe huΙu da Ζ΄an mintuna kullum yake dawowa gida, amma a yau sai gashi har Ζarfe shida bashi ba alamarsa, ta tabbata dai duk abinda ya tsare shi to lallai a yanzu yana kan hanyarsa.
Bata kai Ζarshen tunaninta ba kuwa taji Ζarar motarsa na durfafowa, kasancewar wajen quaters ne shi yasa shiru ke fallasa komai. Sai ta ajiye farantin kan Ιan Ζaramin teburin tsakiya na falon inda ta jera masa kulolin abincinsa kafin tayi hanyar fita. A yau tayi ado ne da wani rantsatstsen leshinta da tun daren amarcinsu rabon data sanya shi, don haka take son ya fara yin tozali da hakan tun kafin ya shigo don ta sanya farin ciki a zuciyarsa.
Tana son Ahmad kuma a zamansu bata da wata matsala, kuΙi ne gasu nan falala da zarar ta tambaya sannan ga tsananin kulawa da take samu daga gare shi, idan akace sunje Kiyari kuwa cikin masarauta, to ko mahaifiyarsa bata fita iko ba. Matsalar Ιaya ce, Haihuwa! Ta sami magaji don ta jefi tsuntsu biyu da dutse Ιaya, ta faranta ran Ahmad na samun Ζ΄aΖ΄a, ta kuma samarwa kanta magajin dukiyarsa, kuma hakan mai yiwuwa ne kwanan nan don mahaifiyarta ta haΙa ta da wani sabon malami a yanzu kuma bata da shakka a kansa.
STORY CONTINUES BELOW
Ta fito ta barandar gidan lokacin da motarsa ke tsayawa, fuskarta dauke da murmushi tana kallonsa ta cikin motar, kuma ko kaΙan idanunta basu hango Ιan kan yaron dake zaune a kujerar gefe ba. Ya kashe motar ya fito sannan ya zagayo, sai dai maimakon ya iso ya rungumeta kamar yadda tayi hasashe sai taga yaja hannun Ζofar gefe ya buΙe, kuma har ya gama kwance seatbelt Ιin jikin kujerar bata yi tunanin Ιan mutum zai fiddo ba, a hasashenta ya wuce ledar lesuka da atamfofi sababbin yayi daya gani ya siyo mata?
Ζan yaro ne Ιan Ζarami, sai dai duk Ζankantarsa akwai wani abu mai girma kamar kwarjini tare dashi, zuciyarta ta buga sanda kyawawan idanunsa masu sheΖi suka kalle ta, wani kallo kamar na Ιan da yaga uwarsa bayan tsawon kwanaki.
“Ranka ya dade, kai da waye haka?”
Babu dalili, muryarta ta fito kusan a shaΖe.
“Ibrahim, sunansa Ibrahim.”
Cewar Alhaji Ahmad, don sunan da ya laΖaba masa kenan a tun lokacin da akayi cike-ciken takardu a gidan marayun.
“Daga ina yake? Na dauka sanda zamu taso kace baka san kowa a Jimeta ba.”
Maimakon ya bata amsa, sai ya iso har gabanta ya kamo hannunta daya kawai suka nufi cikin gidan, na dama riΖe da yaron, na hagu kuma rike da ita. Wani tubali da ya zamo mafari kenan wajen haddasa wutar tsanar yaron da bata ko gama sanin kammaninsa ba a zuciyarta.
“Ban gane ka yanke shawarar riΖe shi ba Ahmad, wane yare ne wannan?”
Fuskarta a haΙe murtuk ta tambaya a lokacin da ta kasa ko zama tana jiran fitowar mijin nata daga wanka, bayan ya fito Ιin ne kuma ta kasa ta tsare cewar sai yayi mata bayanin Ιan da suka bari a falo yana cin abincin da ko ita bata kai bakinta ba.
Ya juyo ya kalle ta jin sautin ta ya canja akan yadda ya sanshi, yayin da yake goge ruwan fuskarsa.
“Hausar ce yau ke haΙe miki Hafsat? To in baki gane ba sai ince yaren Jimeta ne wannan. Tun daga farko ai kin fahimce ni, to me yasa ba zaki gane karshen ba?”
“Ta yaya kuwa zan gane manufarka Ahmad, cewa fa kayi a riΖe shi kafin mu sami namu, kana nufin har na gaza kenan? Shekara uku kawai amma ka kasa hakuri sai ka kawo Ιan da bamu tabbatar da halaccinsa ba kace in riΖe? Ni na hana kaina haihuwar da na kasa samar maka Ζ΄aΖ΄a ko kuwa…”
“Kinga ya isa…!” Kakkaurar muryarsa ta katse ta cikin iko irin nasa na Ζ΄aΖ΄an sarauta.
“Nace miki ina zarginki da rashin haihuwa ne? Ko kuwa nace miki Ζulafucin Ζ΄aΖ΄a ne yasa na Ιauko wannan yaron? Ina imaninki ya tafi ne Hafsat? Ke baki tsinci tausayi a labarin dana baki ba? Ta yaya zan bari rayuwar yaro kamar wannan ta salwanta alhali ina da hanyar da zan iya karewa?”
Yana rufe baki ta cafe.
“Tausayi? Ina tausayi yake da mazauni anan? Su Ζ΄aΖ΄an da ka baro a gidan marayun baka jin tausayinsu kenan? Ko kuwa ka manta tulin yara marayun dake taruwa duk juma’a a Fada ne wajen sadaka? Naga kafin tahowarmu ma sai da muka je sansanin da yaΖi yaci garin FarΙe, ka manta waΙannan kananan yaran da aka rabawa sutura da kayan abinci ne? Yaran da harda na goye babu uwa balle uba? Me yasa duk su baka dauko Ιaya ko ka tattaro min su kace in riΖe kafin in sami nawa ba? Sai wannan da ban san asalinsa ba?
Haba Ahmad! Mace kamar ni? Zan riΖe yaron da aka tsinto a kwararo? In ya girma ince me? Nawa ne ko na wata da baza ta wuce karuwa ba?”
Maganganunta sunyi zafi kwarai! Amma duk da haka sai ya tattaro dauriya da matsayinsa na miji yayi mata uziri, mace ce ita, mai zuciya a Ζirji, ta taΙa yi masa hakan ne tsawon zamansu? Idan bata nuna kishinta ba ai ko shi ya dasa ayar tambaya akanta, saboda haka ya kamo hannunta duka biyu sannan yayi Ζasa da tasa muryar.
STORY CONTINUES BELOW
“Dan Allah ki fahimci ni Hafsatu, na sani cewa dama zaki ji zafin wannan al’amarin, tabbas na hasaso cewa zaki ji haushinsa har ma ki faΙa mun waΙannan maganganun, sai dai a duk bayan haka kuma na hango cewar zaki fahimce ni, zaki dubi yaron nan da idon rahama, zaki kwatanta irin abinda nake ji a zuciyata game dashi ko don ki cika alkawarin da muka Ιaukarwa juna cewa komai tsanani da halin rayuwa ba zamu bari wani abu ya shiga tsakaninmu ba.
Ki Ιauki kanki a matsayin mahaifiyar yaron nan mana, wata mata da giftwar Ζaddara ta raba ta da abinda ta kawo duniya, yaya zaki ji idan har…”
Hafsatu ta kara tunzura, ranta ya kai Ζololuwa wajen Ιaci, idanunta suka rufe ruf! da baΖin hayaΖi, bata iya ji da ganin komai sai abinda zuciyarta ta wassafa mata a lokacin, abinda zuciyarta ke biya mata har take koΖarin fara haddacewa saboda haka har Alhaji Ahmad ya kai Ζarshen zancen sa bata fahimci komai ba, sai da taji muryarsa ta daina amsa amo a cikin kanta sannan ta dube shi da idanunta jawur!
“Ka san Allah Ahmad? Ka san ubangijin da ya halicce mu ya halicce duniyar nan? To na rantse da buwayarsa idan na riΖe yaron nan ban haifu a cikin uwata ba! Tun wuri gwara ka san inda zaka kaishi don ba zai raΙe ni ba wallahi balle har abinda zanzo in haifa a gaba.”
Kalaman sunyi mutuΖar shayar da Alhaji Ahmad mamaki, don bai taΙa ganin wannan Ιangaren na matarsa ba, zamansu mai daΙi ne cike da biyayyar da ko me yace tayi, a tunaninsa in ma tayi Ζorafi to zata yin, amma har wannan Ιan Ζaramin abin da a wajensa bai kai ya kawo ba zai sanya ta gaya masa waΙannan maganganun? A tunaninsa komai ra’ayinta zata so duk wani abu daya buΙe baki yace yau yana sonsa ganin irin tsananin biyayyar da take masa.
Saboda haka sai ya saki hannayenta sannan ya miΖe tsaye, ya Ιauki rigarsa dake gefe sannan ya tabbatar mata da cewar ya san Allahn.
“…kuma na san Ζarfin buwayarsa Hafsat, don haka ba zan sa ki shega ta kanki ba, yaro ne baza ki riΖe ba to na fahimta, amma ni a yanzu mutuwa ce kaΙai zata iya yanke min wannan alΖawarin dana Ιauka, don haka kisha zamanki ke da abinda zaki zo ki haifa Ιin. Ni zan riΖe yaron kamar yadda nayi alΖawari don haka kar ki sake ki Ζalubalanci duk wani abu da zanyi akansa daga wannan daren har Ζarshen rayuwarki, in kika yi hakan_- ina tabbatar miki baza ki sake samun matsala daga ni ba insha Allahu.”
Kalaman daya faΙa kenan yana mai ΖoΖarin saka rigarsa a gaban mudubi, wasu kalamai da Hafsatu taji su kamar Ιoruwar Ζarfen da yayi ja a wuta cikin zuciyarta, don sun bar wani tabo da ta yarda cewa har ta koma ga mahallicinta ba zai goge ba.
Kuma wannan daren shi ya zama na farko da suka fara raba makwanci ita da Ahmad, ta kwana ne ita kaΙai a Ιakinta yayin da ya kwanta a nasa Ιakin tare da yaron!
Kuma washegari da sassafe yayi wani abu da duk Ζarfin zuciyarta sai da ta tsorata, sai da tuna cewa da gaske namiji ta aura, namijin da ko a cikin maza ya amsa sunansa, wanda duk Ζarfin ikon mace a zuciyarsa bata isa taja da al’amarinsa ba.
Wata Dattijuwar mata ya shigo da ita gidan mai sunan Atine, kuma ba tare da yayi mata bayanin komai ba yasa aka buΙe musu Ιaki a can boys-quaters Ιin dake bayansu, a ranan aka cika Ιakin nan da duk wani kayan buΖata na amfanin uwa da yaro Ζarami, sannan ya dauki yaron da bai ko barshi a gidan ba tun safe ya danΖawa Atinen da cewar ta zauna ta kular masa dashi, tana kallon komai ta taga kuma har ya shigo gidan daga baya ‘ta tafasa, sauke’ akan al’amarin baice da ita ba.
Don haka a wannan ranar ne shaiΙan ya taka mummunar rawa wajen halittar wata irin Ζiyayya da za’a shafe tsawon zamani guda kafin a samu mai makamanciyarta a Ζirjinsa, kuma mafarin kenan!
Mafarin Komai!
*
Ibrahim Ahmad Madaki.
STORY CONTINUES BELOW
Tsawon watanni hudu da fara wata sabuwar rayuwa, waΙannan kalaman guda biyu sune kaΙai a cikin kwakwalwar Ιan talikin yaron nan, bayan haka babu abinda yake ganewa daga cikin yaren mutanen da suka Ιauke shi sai dai kawai yayi amfani da alamar inkiya kawai ya kintaci maganar da ake masa. Bashi da wani wayo kuma bai san tarin abubuwa ba, bai san ya akayi ya tsinci kansa a wajen nan da aka tsinto shi ba, abinda yake tunawa kawai shine fuskar wani mutumi a lokacin da yake gaya masa wani abu da ba zai iya tunawa ba, a lokacin da Ζafafunsa suka kumbura sannan a lokacin da yake wani irin tari wanda yake fitowa tare da fallatsowar jini…!
Ya san cewa ya san fuskoki da yawa ta mutane a can inda ya taho, amma bai zai iya zayyano sunayensa ba ko matsayinsu a rayuwarsa.
Matar da ake kira Baba Atine ita ke kula da komai nasa, tana kula dashi kamar kaka da jikanta, kuma a hankali yake fahimtar duk harafan da take masa magana dasu sai dai har zuwa wani lokaci bai damu da yayi magana ba don bai san me zaice ba, har asibiti aka kaishi wai don ayi bincike ko da akwai wata matsala a makogwaronsa, amma da aka gano ba komai sai Alhajin ya rabu dashi da fatan cewar zaiyi maganar wata rana.
Tun bai san ma’anar kalmar Kirki ba, ya fahimci cewa Alhaji Alhmad mallakinta ne don yayi wayo ne kamar yadda kowanne Ιa yake tasowa yaga mahaifinsa, ya kula da dukkan wata Ιawainiyarsa ta duniya, ya bashi dukkan wata kulawa da Uba ke bawa Ιansa, ya kyautata rayuwarsa, ya daraja shi ta kowanne fannin daya bashi cikakken suna na ‘Mutum’ sannan bai juya masa baya ba ko a lokacin da ya samu nasa Ζ΄aΖ΄an.
Ya tashi yana ganin girmansa fiye da kowanne mutum a duniya, ya tashi yana kare daraja da martabarsa da dukkan wata iyawarsa, baya yi masa musu, bai taΙa bijirewa umarninsa ba balle har ya saΙa masa. A kullum yana kallonsa ne kamar mudubi, yana fatan watarana ya tashi ya zama tamkar shi, yana kwaikwayon duk abinda yaga yana yi, hatta tafiya wannan, Ibrahim sai wadda yaga Alhaji Ahmad nayi sannan zaiyi tasa, bai taΙa kallonsa da matsayin komai ba sai na Uba kuma mahaifi.
Amma komai yasha banban a Ιangaren matarsa, wata halitta da tun daga zamanin da baya iya fahimtar komai sai motsin fatar bakinta ya san cewa shine abinda tafi tsana a rayuwarta, yasha azaba da tsinuwarta tun baya fahimtar hakan har yazo ya gane, don kasancewarsa a wajen Baba Atine baiyi mata katanga da komai ba, tana samin damarta da zarar Alhaji Ahmad ya fita zuwa aiki, shi kuma yana samun Ζ΄ancinsa ne da zarar lokacin dawowarsa yayi.
Wani abu da sai da aka shafe shekara da shekaru anayi kafin Alhaji Ahmad din ya farga, don a gabansa babu ruwanta da sha’anin yaron balle har yayi tunanin wani abu, tana nuna masa cewar ta dauki maganganunsa na cewar ba zata sami matsala dashi ba in har zata tsame kanta a sha’anin yaron, don haka koda Allah yayi wa Baba Atine rasuwa, sai bai sake neman wata mai kula dashi ba ganin shi kansa Ibrahim Ιin ya fara tasawa kuma a lokacin sun haifi Ιansu na farko ‘Saifudden’, sai yayi zaton ko Hafsatu bata janye Ζudirinta akan Ibrahim ba, ba zata cutar dashi ba tunda a yanzu ta san ciwo darajar haihuwa.
Kuma haka rayuwar ta tafi tsawon shekaru har zuwa haihuwar Ιansu na uku Umarul Faruk, Ibrahim bai tab’a bashi shakkun da zai canja tunaninsa akanta ba.Yana jure dukkan dubunnan wahala da tsinuwarta ba don komai ba sai don darajar miji irin wanda ta samu, miji wanda yake wa kallon Uban da bashi da tamkarsa a duniya. Don haka ne ma duk irin abinda take masa bai hana shi son Ζ΄aΖ΄an ta ba, bai hana shi jansu a jiki yana nuna musu soyayya irin wacce kowanne d’anuwa ke yiwa Ζ΄anuwansa, irin son da ubangiji ke halittawa a tsakanin jini da jini, kafin hakan ya shuΙe daga lokacin da ya fahimci cewa su babu hakan a tasu zuciyar.
Musamman bayan da saki ya shiga tsakanin Alhaji Ahmad da mahaifiyar tasu akansa, wata rana da ya dawo ya tadda shi yana dirzar manya-mayan carpets Ιin gidan a maimakon kasancewarsa a makaranta. A wannan ranar duk wani bayani da kwana-kwanar Hafsatu bai shiga kunnensa ba, ransa ya kai Ζololuwa wajen Ιaci har ya furta cewar ya sake tan! Wani saki da ko bayan yayi shi baiyi dana sanin ba, don sai da aka kai ruwa rana da ban bakin manya da komai sannan ya yarda ta dawo, tare da nata ban hakurin itama na cewar tayi nadama kuma zata riΖe shi tamkar ‘Ιanta’, asalin sunan kenan! Asalin dalilin da yasa har zuwa yau, mai martaba baya kiransa da kowanne suna a wajenta sai ‘Ζanki’.
Sai dai daga lokacin da ya kammala secondary ya fito da wani irin sakamako mai kyau sannan komai ya dawo sabo, a lokacin da Alhaji Ahmad Ιin ya ware wasu makudan kuΙi ya tura shi Ζasar waje don yin karatun degree a fannin kasuwanci kamar yadda yake buri.
Alheri ba zai tab’a isar maka ba, kasa a ranka wannan itace nasara ta k’arshe da zaka samu a rayuwarka, wannan rantsuwa ta ce…
Kalamanta a wannan lokacin suna Ιaya daga cikin abubuwan da ba zai taΙa mantawa, wanda kafin dawowarsa ne kuma rayuwa ta sauya a bangare da yawa, don Alhaji Ahmad ya ajiye aikinsa ya karbi sarautar mahaifinsa wanda ya rasu, wani tsohon da bai taba Ζin Ibrahim Ιin ba amma dai ya hana shi amfani da jigon sunan zuri’ar masarautar wato ‘Kamsusi’ don haka ne ma sunansa yake a Ibrahim Ahmad kaΙai, sai bayan rasuwar tsohon nan Madaki ne sannan ya samu laΖabi na uku a sunansa, wani laΖabi daya manne a bakin mutane ya mantar dasu sunansa na Ibrahim Ιin.
Bayan kammala karatun jami’ar tasa har zuwa bigiren Masters ne kuma wani babban al’amarin ya sake faruwa, Mai martaba ya Ιauki dukiyar da yayi shekara da shekaru yana tarawa ya danΖa ta a hannunsa baki Ιaya, da cewar shi ya juya dukiyar, Saifudeen kuma da yake Ιansa na jini ya gaji sarautar gidansu. Wani hukunci da ya sake taso da tsohon tsumin tsanarsa a zuciyar Fulani, don me yasa baza’a hadawa Ζ΄aΖ΄anta duka biyun ba? Me yasa za’a raba abinda yake halalinsu da wani bare?
Idan har kana ganin wannan wata dama ce ta sake bud’e maka to kayi kuskure, Allah ya sani na tsaneka Madaki, ka riga ka san hakan kuma a yanzu ina ganin lokaci ya wuce da kalamaina ma zasu dinga b’oye manufata, kasa a ranka cewa ko zanyi yawo tsirara sai na kwatowa ‘ya’yana hakk’i da matsayinsu daka danne, ratsuwa ta ce Ibrahim!
Rantsuwarta. Rantsuwar da ta sake tada ta tsaye wajen koΖarin ganin bayansa ta hanyoyi mababanta har kuwa zuwa matakin da ake ciki a yanzu.
Madaki mutum ne mai saukin kai, mai daraja mutane, mai son jama’a, mai kyauta, mai alkunya da kara, mai sanin halacci da kuma ya kamata. Zuciyarsa mai tsafta ce, bashi da mugunta balle cuta, yana da alΖawari da kuma tsayawa akan gaskiya, ya rasa wata rahama da mafi yawan mutane a duniya ke da ita ta sanin iyaye da kulawarsu, musamman ma Uwa! Wadda ke zama ginshiΖin farin ciki na kowanne Ιan adam, amma bai taba bari hakan ya shafi Ιabi’unsa ba.
Wannan shi ya kawo mu har ga matakin da ake ciki a yanzu!1
***~~~~
Komai ya faru ne a lokacin da ya saki hannun bindigar, a lokacin da harsashin ciki ya fito cikin tsananin gudu zuwa inda aka aike shi…. A lokacin da wannan matashin ya shigo cikin hoton da yake hangowa ta cikin ramin bindigar alamun yazo ne ya buΙe Ζofar motar da yarinyar ta kasa buΙewa…!+
*
“Kin kasa buΙewa ne?” Madaki ya tambaya a lokacin da ya bude Ζofar tasa motar ya zira Ζafa Ιaya ciki.
Jidda ta sake jan Ζofar ba tare da ta amsa ba da hannunta Ιaya, Ιayan kuma riΖe da robar yughurt dinta, sai kawai ya mayar da tasa ya rufe shima sannan ya zagayo wajenta, ya tsaya a daidai bayanta sannan muryarsa ta fito a hankali daidai saitin kunnenta.
“Matsa, let me.”
Al’amarin ya faru ne cikin abinda bai fi wucewar sakan Ιaya ba, daidai lokacin da Jidda ta zare hannunta daga handle Ιin Ζofar tana shirin matsawa, daidai sanda take ΖoΖarin motsa Ζafafunta su bar wajen… sai kawai ji tayi Madakin dake tsaye a bayanta ya taho da wani irin Ζarfi ya bugu da jikinta, ta haΙe gabaΙaya da murfin Ζofar yayin da kanta ya bugu matsanancin sauri da gilashin Ζofar cikin wani irin Ζarfin da yasa har sai da motar ta girgiza, kuma hatta robar Yogurt Ιin hannunta data fadi sai da murfinta ya fice saboda yadda ta daki Ζasa da Ζarfi, ragowar na ciki ya fallatse a iska da kuma rabi na jikinsu.
A mutuΖar tsorace ta juyo da fuskarta ta kalle shi hannayenta dafe da motar yayin da shima yake ΖoΖarin tsayawa akan kafafunsa, taga sanda ya dafe saman kafaΙarsa ta hagu da sanda yake ΖoΖarin juyawa bayansu yana kallon can saman asibitin… Sai dai tazarar dake tsakanin yunΖurinta na buΙe baki tayi magana da sanda ya sake dawowa da baya ya bugu da jikin motar bai fi Ζiftawar ido da budewarsa ba.2
Kuma kafin ta gai ga furta wata maganar idonta ya hango mata tashin hankalin da ya juya ΖwaΖwalwarta ya kasa fahimtar da ita gaskiya da zahirin abinda ta gani Ιin… Jini! Wani irin jini mai kauri na tsatstsafowa daga tsakanin yatsunsa inda ya dafe kafaΙar tasa ta baya…3
Innalillahi wa’inna ilahir raji’un…. Me ya faru?
“Wani ne ya jefe ka? Da dutse ko da me?… A baya ne? Ta yaya? Banji Ζara ba…”
Muryarta ta fito yayin da take kokarin mantawa da nata buguwar tana ΖoΖarin kai hannunta wajen, sai dai da saurinsa Madaki yasa Ιaya hannunsa da bai danne wajen ba ya hana ta.
“Kar ki taΙa, ina tunanin harbi ne.” Muryarsa ta fito da wani irin amo mai tsitstsinkewa da bata taΙa ji ba.
“Harbi? Harbi ta ina? Wane irin harbi? Da danΖo?”1
Tsakani da Allah tayi tambayar muryarta a rikice don nauyin ΖwaΖwalwarta ko kaΙan bai kai yayi tunanin wani harbin bindiga ba, to ina ma ta santa banda a suna? Ko a can gida ba kallon fim Ιin turawa take ba balle har tunanin bindigar ya zauna a ΖwaΖwalwarta…
**
“You missed the target?”
(Baka same ta ba?)
Cewar gabjejen Ζaton mutumin nan cikin tsananin mamaki da fushi daga can saman ginin asibitin, yayin da idanunsa ke kare da binoculars (madubin hange) yana kallo can Ζasa.
“I’ve already set the fire when he just came into the view… Tell me how was I supposed to control that?”
(Na riga na gama sakin harsashin kawai sai ganinsa nayi ya shigo wajen, ka gaya min ta yadda zan tsaida komai?
Muryar mai bindigar ta fito cikin nata karaji itama yana kallon Ιayan. Na tsayen ya dafe kansa cike da takaici yana hasaso muryar ogansu a lokacin da yake jaddada masa cewar kar su sake wani abu ya sami matashin, yarinyar kaΙai itace target Ιinsu, ya sake kara binoculars Ιinsa yana hango su daga can Ζasan.
STORY CONTINUES BELOW
Yarinyar ta rikice sai ΖoΖarin tara hannunta take a kafadar matashin inda jini ke zuba, yana ganin yadda yake ΖoΖarin hanata amma tana fizge hannunta tana taya shi dafe wajen har daga baya…
“You know what? Shoot again, shoot the girl…”
(Ka san me? Sake wani harbin, Harbi yarinyar itama..)
Ya faΙa ba tare da ya sauke binoculars Ιin daga idanunsa ba.
“What? Is that on the list? ‘Cus you pay for only one bullet?”
(Hakan na cikin tsarin? Don kuΙin harsashi Ιaya kawai aka biya ni?)
Na tsayen ya Ιauke madubin hangen daga fuskarsa, sannan ya juyo ya kalle shi sosai sannan yayi maganar dalla-dalla.
“I. say. shoot. the. girl!”
(Nace ka harbe ta!)
Mai bindigar ya gyada kansa kawai sannan ya koma ya Ιora idonsa cikin kwarmin bindigar.
Yarinyar ta kasa tsayawa waje daya, juye-juye kawai take alamun tana neman taimako tunda sun baro harabar asibitin wajen mutane, parking space ne kawai inda sai mutum zai dauki motarsa zai Ζaraso… Duk da haka yayi ΖoΖarin gama saita Ιan hasken bindigar tasa ta bayanta kafin mummunar rashin sa’ar ta faru, kamar matashin nan yaga hakan, sai kawai gani yayi yaja hannunta sunyi Ζasa, kuma wata Ιindimemiyar Rav4 ta kange shi daga ganinsu…!
*
“Kar ki tashi, kar ki sake tashi suna nan basu tafi ba…”
Muryar Madaki ta fito a tsakiyar numfashi lokacin da ya damΖe hannayen Jidda dake ΖoΖarin sake tashi.
“Su waye? Wani zanje in nemo, ba zan iya Ιaukan ka ba, ka manta a asibiti muke? Jini ne fa yake zuba daga jikinka… Innalillahi wa’inna ilahir raji’un..”
“Nace ki… ki… Ιauke ni ne?” Ya tambaya yana furzar da numfashi daga bakinsa.
“Nace kar ki tashi!” Ya sake faΙa cikin tsawar da muryarsa zata iya dauka ganin da gaske ΖoΖarin fizge hannun nata take zata tashi. A lokacin jikinsa gabaΙaya ya fara rawa don jinin da yake zubarwa ya fara yawa, ta baya ne amma har ta gaba tsatstsafowa yake don kusan rabin gaban rigar tasa ya jiΖe da jinin yayin da yake sake tunkuΙowa ta tsakanin yatsunsa dake dafe da wajen.
Jidda ta rikice iya rikicewar da bata taba yi ba a rayuwarta, jikinta yafi nasa rawa sannan in banda karar bugun zuciyarta ba abinda take ji yana dokawa a Ζirjinta, so take kawai ta ga wani yazo, an kawo agaji, mutane sun taru an Ιauke shi zuwa cikin asibitin, amma yace kar ta ta tashi… Kar ta tashi… Ga jininsa ya na ΖoΖarin Ζarewa a gabanta… Shi yake jingine da motar amma duk da haka kansa ya lanΖwashe ta gefe alamun babu wani Ζarfi a jikinsa sai wanda yasa ya damΖe hannayenta…
Bata san lokacin da wani irin Ζarfin yazo mata ba, ta fizge hannayen nata a lokaci guda sannan ta shiga ΖoΖarin zaro bakin Ιankwalin data daure kanta dashi wanda shima mayafin wata rigar ne, ta Ιaura daya, ta yafa Ιaya…
“Me zaki yi?”
Muryarsa ta sake tambaya babu amo alamun rauninsa na kara tasiri, kuka take sosai tun daga Ζasan zuciyarta tana kallonsa, idanunsa sun fara ja kamar suma jinin na ΖoΖarin cika su ne.
“Babu inda zaki je…” Ya sake faΙa da muryar dake nuna cewa ko da zata tashin ma, a yanzu ba zai iya riΖe ta ba.
“Babu inda zani…” Ta faΙa itama tana kukan.
” … Zan Ιaure maka wajen ne kar jininka ya Ζare…”
Ta fada tana ΖoΖarin janye hannunsa daga yadda ya fafe shi kuma da yake Ζarfinsa ya riga ya tafi dama, tana taΙa hannun ya faΙi ya koma gefe yayin da hakan yasa karuwar tunkudowar jinin ta karu, fitowa yake kamar ana turo shi har da wani guda-guda alamun ko meye ya fasa wajen ba Ζarami bane…
STORY CONTINUES BELOW
“Ibrahim..! Ka kalle ni… Ka kalle ni Ibrahim..”
A lokaci guda muryarta ta fito kusan da Ζarfi ganin idanunsa sun fara lumshewa… Sai ta saki Ζullin da take yi ta hau tattaba fuskarsa da hannayenta dake Ιace duk da jinin suna karkarwa, so take ta buΙe idanun nasa…
“Ibrahim, Madaki… Ka kalle ni kar ka rufe idonka, yanzu wani zai zo… Yanzu zanje in kira wani…”
“Kar ki tashi…”
Kwata-kwata sautin muryarsa bai fito ba, motsin fatar bakinsa kawai ta kalla ta gane me yace, sai ta hau gyaΙa kanta kamar Ζaramar yarinya…
“Ba zan tashi ba, babu inda zanje… Ka bude idonka ka kalle ni, yanzu wani zai zo yanzun nan… Zamu koma ciki asibitin… Dan Allah ka buΙe idonka kar ka rufe su, kar ka mutu, kana jina… Ibrahim….”
A tsugunne a gefensa take amma kusan gabaΙaya tana kansa ne yayin da fuskarta tayi dab da tasa, ta rike ta cikin hannayenta sai faman jujjuyata take tana ΖoΖarin bude idanunsa da yatsunta… Idonta ya sake kaiwa kan kafadar tasa inda bata gama Ζullewa ba jini ke cigaba da fita yana jiΖa su gabaΙaya… Sai ta saki fuskarsa da sauri ta koma Ιaurewar da hannayenta dake karkarwa suma babu wani Ζarfi a jikinsu…
Ta sake juyowa kan fuskarsa, kansa lilo kawai yake yayin da idanun nasa ke cigaba da rufewa..
“… Ibrahim, Ibrahim ka kalle ni, ina kusa da kai, Ba abinda zai same ka… Ka buΙe idonka, ga mutane nan suna tahowa, ka ji su? Kaji motsin su? Gasu nan… Yanzu zamu shiga ciki, zaka ji sauΖi kaji? Kana ji na? Ka buΙe idonka, ciwon zai daina.. ka buΙe idanunka don Allah…”
A yanzu kusan marin fuskarsa kawai take yi kotawanne bagare tana ΖoΖarin bude idanunsa da suka rufe ruf! Yayin da kukanta ya karu.
“… Ba zan tashi ba, su zasu zo… Gasu nan suna tahowa, ka buΙe idonka zasu fi gane ka Ibrahim, dan Allah, ka kalle ni, ba zan bari wani abu ya same ka ba, Ina kusa da kai, kana gani na? Ibrahim… Ibrahim… Ibrahim… Ibrahim…”
A daidai wannan lokacin wasu magidanta biyu suka karyo kan kwanar parking space Ιin inda su Jiddan suke, jin muryar mace na ta ambaton suna cikin tashin hankali yasa dukkaninsu suka taho wajen.
“Innalillahi wa’inna ilahir raji’un… Me ya faru?”
“Me ya same shi?”
Muryoyinsu suka sa Jidda ta Ιago da kanta ta kalle su, domin har suka karaso girgiza fuskar Madaki kawai take tana kiran sunansa. A lokaci guda hawaye ta ya sake tunΖuΙowa cikin wani irin kuka…
“Harbinsa akayi, yace harbinsa akayi dan Allah ku taimaka mana.”
“Harbi??”
“Innalillahi wa’inna ilahir raji’un.”
Ζaya daga cikinsu yayi salatin kafin dukanninsu su zube a gabansa yayin da ita ta miΖe, sai dai ganin baya ko motsi yasa basu Ιata wani lokaci ba suka shiga kiciniyar Ιaukarsa, wanda ya Ιan fi Ζwari a cikinsu shi kusan ya cicciΙe shi yayin da Ιayan ya riΖe Ζafafunsa suka juya zuwa hanyar asibitin nan cikin sauri.
Kamar wata sabuwar mahaukaciya haka Jidda ke jin kanta, gaban rigarta gabaΙaya ya Ιaci da jini yayin da kanta ba Ιankwali sai mayafin kawai dake zamewa, da sauri ta tsugunna ta Ιebi takalmansa da suka zube da kuma muΖullin motarsa da ya faΙi a Ζasa sannan ta ruga da gudu itama tabi bayansu, bata ko lura da cewar ta bar nata takalmin a wajen ba balle matar Ιaya mutumin dake tsaye tana kallon komai cikin tashin hankali.
Tun a hanya mutane ke ta binsu da kallo ana matsawa ganin yadda har a lokacin jini ke zuba daga jikinsa yana bin Ζasa, a cikin asibitin kuwa tun kafin su karaso wasu Nurses biyu dake magana a gefe suka hango su, ai kuwa da sauri suka taho kansu suna nuna musu hanyar A&E, yayin da taga Ιaya daga cikin mutanen nan yanuna musu ID Card Ιinsa, Jidda na binsu a baya har a lokacin tana kuka, nata Ζafafun da babu ko takalmi na taka duk inda jininsa ya Ιiga akan farin tiles din dake wajen, da ita aka shiga har cikin A&E Ιin aka kwantar dashi a wani gado, sannan daya Nurse Ιin ta juya da sauri don zuwa kiran likita, yayin da sauran Nurses Ιin dake cikin Ιakin suka juyo gabaΙaya suka yo kansa.
STORY CONTINUES BELOW
Kuma kafin Jidda ta gama fatan cewa su maza don taga fuskarsa, Nurse din nan ta dawo tare da wani likita don haka aka tattaro ta ita da mutanen da suka kawo shi akace su fito waje. Suna fitowa wanda ya nuna ID Card Ιin nan nasa ya zaro wayarsa ya shiga kira yana wani bayani da ba jinsa Jidda ke yi ba.
“Kiyi hakuri kinji baiwar Allah, zai sami sauΖi insha Allahu.”
Cewar Ιaya mutumin da kusan shi ya dauko shi.
“Ai kowanne irin ciwo ne bai taΙa zuciyarsa ba, a kafaΙa ya tsaya insha Allahu komai zai zo da sauΖi.” Ycigaba da faΙa sai kuma ya kara da…
“Ki kira gida, Ζ΄anuwanki ko nasa ki faΙa musu halin da ake ciki.”
Ζayan ya Ζaraso a daidai wannan lokacin.
“Kar ki damu kinji Madam, komai zai zo da sauΖi, harbin a kafaΙarsa kawai ya tsaya don haka zasu yi handling situation Ιin, suma waΙanda suka yi abin ina fatan za’a kama su don na kira patrol na Ζ΄an sanda, indai suna wajen nan baza su fita ba.”
Daga yanayin yadda hausar sa ke fita zaka san cewa ba bahaushe bane balle musulmi, sai dai da alama yana da dan muΖami mai girma a harkar tsaron duk da ba kayan aiki ne a jikinsa ba.
Jidda kuka kawai take tana Ιaga kanta alamun ta fahimci zancen da bata fahimta ba Ιin, kuma ganin yadda ta rikice sai basu tafi ba suka tsaya suna Ζara bata hakuri da tabbatar mata cewar zai warke, Ιayan ma yayi-yayi ta faΙo namba a kira wani da zai zo ganin babu wayar a hannunta amma banda kuka ba abinda take yi, a lokacin matar Ιaya mutumin da yake Ζabila ta Ζaraso itama, babba ce sosai kamar mijin nata, saboda haka ta zaunar da ita a wasu kujeru dake gefe tana bata baki cikin tata hausar da bata fita itama.
Sai kusan bayan isha sannan Nurse Ιaya ta fito riΖe da tarkacen wasu kaya a cikin wani silver faranti irin na aiki, a lokacin Ιan sandan nan ya fita waje don bada bayani ga mutanensa, sai matarsa kawai da Ιaya mutumin a wajen, Jidda na ganin Nurse Ιin ta miΖe tsaye da sauri koina a jikinta na faman rawa kuma har a lokacin hannunta riΖe fa takalminsa da kuma muΖullin motarsa. Nurse Ιin ta Ζaraso ta miΖawa mutumin kayan hannunta sannan tace.
“Ga kayan dake jikinsa, an shiga dashi operation ne za’a cire bullet Ιin, zaku biya kuΙi a can wajen lab na farko, aikin yana bukatar sauri ne shi yasa har aka fara ba’a tuntuΙe ku ba.”
“Babu komai, babu komai Allah yasa a dace.”
Cewar mutumin yana mai haΙe kayan cikin hannunsa.
Ya juyo wajen Jidda sannan ya miΖo mata su duka, wayoyi ne guda biyu sai wallet dake dauke da kudi fal, da kuma wasu Ζ΄an I.D cards da basu shiga cikin wallet din ba.
“Ki buΙe wayar tasa a kira wani yazo don su san halin da ake ciki.”
Har a lokacin hawaye bai bar sukalowa akan fuskarta ba ta gyaΙa kanta kawai alamun ta gane, duka wayoyin suma sun Ιaci da jini, Ιaya ma ta mutu alamun jinin ya shiga jikinta sosai Iphone Ιin ce kawai a kunne, yatsunta na rawa tasa hannun ta bude ta, cikin wata sa’a sai babu password a jiki, hannayenta suka cigaba da karkarwa akan wayar ba tare da ta san nambar wa zata nema ba. Babu wanda ta taΙa sani nasa sai Mai martaba, to nambarsa za’a kira yanzu a gaya masa cewa an harbe shi? Sai tayi saurin gigiza kanta, ganin hakan ba mai yiwuwa bane ta hau laluben wata hanyar.
A lokaci guda kuwa sai ta tuno da wani abu da bata taΙa tunanin ta riΖe ba, ta tuno da wata magana da ya fada a ranar da yake waya a mota bayan ya dauko ta daga Kiyari…
Kar ka damu Mubarak, babu abinda zai gagare ni insha Allah.
Idan har zai iya kiran wani Mubarak ya gaya masa halin da yake ciki a wannan lokacin to tabbas yanzu ma kuwa ba zai damu ba don an gaya masa abinda ya faru yanzu, saboda haka ba shiri yatsanta ya danna Ιangaren call log, ilai kuwa sai ga nambar Mubarak Ιin a sama Ιaro-baro alamun shine mutum na karshe da yayi waya dashi a wannan wayar, don haka kai tsaye ta danna nambar kiran ya shiga, sai kuma ta miΖawa mutumin alamar cewa shi yayi masa magana don har ga Allah ita bata san me zata ce ba.
STORY CONTINUES BELOW
Yazo an harbi abokinsa ko kuma yazo mijinta zai mutu?
***
“Daddy idan na girma zan iya girki kamar mommy?”
Hanan ta tambaya a lokacin da suka baje akan carpet suna cin abincin dare. Mubarak ya kai lomar abincin bakinsa kafin ya amsa mata.
“Idan kika girma Hanan, sai kin fi Mommy ma iya girki…”
Ya faΙa daidai lokacin da Khadijan ta Ζaraso da wani bowl na sauce a hannunta, ta zubawa Aliyu dake gefe yana kallon cartoon din ‘How To Train Your Dragon 3’ a Tv, sannan ta matso kan Hanan lokacin da take kallon Daddyn nata da tsantsar farin ciki tana tambayar…
“Da gaske kake daddy? Da gaske da gaske?”
Mubarak ya sake gyaΙa kansa yana tauna.
“Ba girkin mommy kaΙai ba, idan kika girma sai kinfi kowa iya komai Babyna, sai kin zama kamar princess dinki ta ‘Silver Castle’ da mutane ke sonta.”
Bakin Hanan ya washe lokacin da Khadija ke zuba wa Mubarak tasa sauce Ιin akan abincinsa, dariya kawai take tana kallonsu cike da farin ciki irin wanda zuciyar kowacce mace ke yi in taga iyalinta a farin ciki, har zata wuce ta koma kitchen sai Mubarak yayi saurin kamo hannunta Ιaya.
“Ina Salwa?”
“Tana Ιaki tunda kuka dawo.”
“Lafiya?”
“Tace dai kanta ciwo yake shi yasa na kyaleta.”
Sai ya gyaΙa kansa a hankali sannan ya saki hannun nata, sai dai kafin tunaninsa ya janye zuwa wani abin, wayarsa dake gefe tayi Ζara, yana dubawa yaga sunan ‘Mdee’ Ιaro-Ιaro akai sai kawai yayi murmushi sannan ya haΙiye sauran abinda ke bakinsa.
“Ka san me Man? Muyi ciniki kawai in buΙe maka class na yadda abubuwa zasu dinga tafiya..”
Ya faΙa tun kafin ma yaji muryar na cikin wayar.
“Uhm, yi hakuri ba shine akan layin ba…”
Muryar mutumin data fito ta sanya Mubarak sakin kwanon abincinsa a take ya miΖe tsaye, don ya sani cewa ba Ζaramin abu ne a duniyar nan zai raba Madaki da wannan layin nasa ba.
Khadija dake shirin komawa kitchen din taja ta tsaya idanunta na kallonsa da ruΙanin neman Ζarin bayani, don ta sani cewa ba Ζaramin abu ne zai sa ya zubar mata da abinci ba. Aliyu ma ya rage volume Ιin kallonsa ya juyo.
“Innalillahi wa’inna ilahir raji’un…. Innalillahi wa’inna ilahir raji’un.”
Abinda Mubarak ke fada kenan kawai a lokacin da ya shiga laluben muΖullin motarsa a kujerar dake bayansa.
“Wane asibitin ne?” Muryarsa ta tambaya cikin tsananin ruΙani.
“Daddy me ya faru? Waye ba lafiya?” Khadija ta tambaya a lokaci guda.
Ya juyo ya kalle su, su duka ukun sun zuba masa ido sunyi tsuru-tsuru, idan yace ba zai gaya musu ba ma zai Ζara sanya taraddadi ne a zuciyarsa, don haka a sai kawai ya girgiza kansa sannan a hankali yace.
“Madaki ne bashi da lafiya, amma da sauΖi, zanje in duba shi yanzu zan dawo.”
“Innalillahi wa’inna ilahir raji’un… To Daddy muje tare mana muma mu duba shin.”
Ya sake girgiza kansa.
“Ku zauna, zan fara zuwa, yanzu zan dawo.”
Yana faΙin haka yayi waje da sauri ya faΙa motarsa. Ya kunna ta a lokacin da maigadin gidansa ya fito da sauri cike da mamaki kafin ya shiga ΖoΖarin buΙe masa gate Ιin, da wani irin sauri Mubarak ya fitar da motar ya hau kan titi yayin da yake ΖoΖarin tattaro dukkan nutsuwa a ransa, bakinsa kuma nata maimaita kalmar Innalillahi wainna ilaihir raji’un har a lokacin…
STORY CONTINUES BELOW
Waye zai harbi Madaki a wannan daren? Laifin me yayi? Ta yaya ma aka san inda yake? WaΙannan tambayoyin su ke yawo akansa lokacin da yake ΖoΖarin lalubar titunan da ba zai haΙu da traffic ba… A lokaci guda kuma sai wani tunanin ya Ιarsu a ransa, kar dai ta sanadiyyar yarinyar nan haka ta faru? Don itace a tare dashi kuma babu wanda ya san taΖaimaimai location Ιinsa sai ita, kar dai zargin da Madaki yake akanta tun farko gaskiya ne…? In ba haka ba me yasa duk tsawon rayuwarsa ba a taba samun abu makamancin haka ya same shi ba sai yanzu data shigo ciki??
Hasashen hakan ya cigaba da yawo a kansa yana haskawa ta cikin idanunsa da wani irin tsantsar Ιacin rai mai cike da ruΙani, a lokacin ne kuma ya karyo kwanar asibitin ta cikin wani layi, fitilolin ginin asibitin dake ci tamkar rana suka haska tar! a idanunsa.
***
KIYARI.
A cikin falon Fulani, a tsakiyar kasaitattun kujerunta, Jakadiyar soro ce tsugunne tana lissafo wani bayani dake rubuce a takarda, yayin da Fulanin ke kame kan daya daga cikin kujerun mai zaman mutum uku, kwata-kwata idonta baya kan Jakadiyar balle har ta fahimci dukkan abinda take cewa.
“… Su waΙanda zasu yi abincin an basu odar yin komai na faranti Ιari, sannan katan Ιin lemo da ruwa suma guda Ιari akace za’a kawo…”
A lokacin kalmar Ιari ta shiga kunnen Fulani da idonta ke manne da rantsatstsun labulayen falon, sai ta juyo ta kalle ta.
“Ζari?” Ta tambaya.
“Tun farko ban shaida muku cewa ba taro zanyi ba, to don me za’ayi odar komai Ιari? Wa zan bawa?”
Jakadiyar tayi diri-diri da idanunta sannan ta shiga ΖoΖarin canja rubutun tana faΙin
“Afuwa ranki ya dade, na sha’afa ne, Afuwa dai garkuwar al’umma.”
“Nawa zaki mayar da kike koΖarin canjawa? Kinji nace wani abu ne?”
Muryar Fulanin ta sake fitowa cikin faΙa tana kallon hannun jakadiyar dake ΖoΖarin rubutu, jin haka yasa tayi saurin tsayawa sannan ta Ζara sunkuyar da kanta tana jiran umarni.
Ran Fulani ya kai Ζololuwa wajen Ιaci, zuciyarta ta sake matsewa, har yaushe rabonta da fuskantar irin wannan shirmen, da ace komai bai faru tsakaninta da Jakadiya Babba ba wa zata Ιora kan wannan harkar in ba ita ba? Shirye-shiryen bikin nadin Saifudeen a matsayin Ciroma suke, amma ita gani take kamar shirin wani al’amarin daban ake, don zuciyarta kwata-kwata ta kasa kwanciya da komai, ta kasa samun nutsuwa a ranta shi yasa ma ta yanke shawarar cewa ba wani taro zata yi ba.
Sannan kuma daΙin tashin hankalinta shine rashin dawowar Jakadiyar Babbar har yanzu da gari ya rufe, ta san cewa dare zai iya yi musu a hanya in sun fito gari su sami wajen su kwana zuwa gobe amma zuciyarta ta kasa nutsuwa da hakan ma, gani take aΖalla in hakan ne kamata yayi Ιaya daga cikinsu ita da Sanin ya kira ya gaya mata abinda ake ciki amma babu wani bayani har yanzu, ta kira wayoyinsu yafi sau shurin masaki kowanne baya shiga, to ta yaya kuwa hankalinta zai kwanta?
Ta cigaba da kallon Jakadiyar dake tsugunne tana jiran umarni kafin ta ja tsaki a hankali sannan tace.
“Ki maida adadin hamsin, kuma kar a kara min komai daga hakan.”
“An gama ranki ya daΙe, an gama.” Cewar Jakadiyan soron tana mai rufe littafinta sanin cewa an sallame ta.
Bayan fitar ta ne Fulani ta miΖe tayi hanyar Turakarta da niyyar kiran Hajiya Bilki, don bata san me ya dace tayi ba bayan hakan, dole ta ajiye duk wani girman kai a yanzu ta lallaΙa ta sami gsashshen bayani game da asirin nan, tana tsoron Ζurewar lokaci kuma tana tsoron bacin rana.
A Falo na uku ta tadda Safina sun fito ita da Ζawarta Juwaira zasu fita, Juwairan ta durkusa har kasa ta gaishe ta yayin da Safinan ke amsa waya, dukkaninsu sunci uwar kwalliya sai tashin Ζamshi suke.
“Ina zuwa haka?” Muryarta ta tambaya a shake tana Ζara kallonsu.
Safina ta kashe wayar da take yi.
“Mama bikin Sarah da na gaya miki last week, yau ne dinner.”
Fulani ta jinjina kanta.
“Waye ya muku wannan uwar kwalliyar kuma?”
“Mai kwalliya ce, Ιazun nan ta fita, nasa an maida ita.”
A daidai lokacin wayar Juwairan tayi kara itama, don haka tayi gaba tana faΙin.
“Mama mun tafi sai anjima.”
“Ke Safina koma ciki, ba inda zaki.” Cewar Fulanin.
Safina ta haΙe ranta a lokaci guda cikin alamun rashin fahimta.
“Kamar yaya? Mama ban gane ba, bikin ne ba zani ba?”
“Eh..” Fulani ta tabbatar mata.
“… Saboda banga lokacin da aka tafi wata dinner a yanzu har aka dawo ba.”
“Mama ni fa ban gane ba? Kin taΙa hana ni zuwa biki ne? Ta yaya za’ace duk shirin da nayi ba zani ba?”
“Ni ba uwarki bace, har akwai abinda zance miki ne ki kalubalance ni?”
Har Safina ta buΙe baki zata yi magana wayarta ta sake Ζara alamun kira, ganin haka yasa Fulani ya shige hanyar Ιakinta ta barta nan a tsaye wayar na motsi a hannunta yayin da fuskarta ke a haΙe, don a sanin da ta yiwa mahaifiyar tata, duk sanda take cikin hali irin wannan to kar ka sake ka kalubalance ta zai fi komai sauΖi, amma me yasa ran nata bai tashi Ιaci ba sai a yau data shirya fita ta musamman zuwa wani party da Ahmad ya gaiyace su? Me yasa sai a yau data gama tanadin komai sannan zata zo ta rushe mata? Sai da kiran yaje can Ζarshe yana dab da tsinkewa sannan ta tsaida zuciyarta waje Ιaya.
“Hayatim muna hanya.”
Abinda ta faΙa a ciki kenan kawai sannan ta kashe, ta riga ta tsaida zuciyarta kuma baza ta fasa Ζudirinta ba, don wani abu can ya Ιata mata rai ita baza ta Ιauki alhakin hakan ba, ba zata fasa niyyarta ba, ta juya tayi hanyar fita.
Fulani ta isa cikin turakarta daidai lokacin da kiran da take dannawa a wayarta ya shiga.
“Salamu Alaikum..” muryar Hajiya Bilkin ta ratso cikin speaker wayar tar da ita.
Tun bayan ranar da suka yi waya ta Ζarshe har ta kashe mata wayar, babu wanda ya sake neman Ιanuwansa.
“Ki gaya min an sami aikin nan Hafsatu, kice kin gano inda yake komai ya dawo hannunki.”
Hajiya Bilkin dake nuna cewar ta manta da saΙaninsu ta bata Ζarfin gwiwar iya yin magana.
“Wallahi komai yana nan a yadda kika sanshi Bilki, daga ni har Jakadiyar munyi iya ΖoΖarin mu wajen neman jakar nan ba tare da an fahimci komai ba amma mun rasa ta, a yanzu dai halin da ake ciki na tura Jakadiyar wajen wani tsohon malami na don ya duba mana mu sami sauΖin gano ta.”
Hajiya Bilki tayi shiru kamar mai nazari kafin ta gyaΙa kanta.
“To kinyi kyan kai, amma fatana shine Allah yasa dai a ganta kafin komai ya lalace, don wallahi ina tsoron sharrin malamin nan, don hatsabibin gaske ne baya taba aikin da bai ci ba, kuma kin san dai yanayin yadda harkar nan take, in har sunyi aikin nan da cewar dole sai yaci wani ba zai tafi a banza ba to kuwa in har aka sami matsala kanki komai zai dawo tunda da sunanki aka tsuma aikin.”
Gaban Fulani ya fadi, zuciyarta ta dungura ta sake dungurawa sannan ta tafi gaΙar wani rami mai zurfi. Da kyar ta iya tattaro karfinta ta hadiye yawu a cikin busashshen maΖogwaronta sannan tace.
“Abinda na kira ki tabbatar min kenan dama, amma kar ki damu Bilki, zan yi iya ΖoΖarina gani komai bai lalace ba, babu abinda zai faru ina tabbatar miki, Hafsat bata karaya.”
“Ina miki fatan hakan, don ni kaina har cikin zuciyata ba zan so wani abu ya same ki ba.”
Da haka suka yi sallama, sai dai abinda daga Fulani har Hajiya Bilkin basu sani ba shine komai zai fara ne daga lokacin da agogon Ιakinta ya kaΙa Ζarar cikar Ζarfe tara na dare.
A yanzu haka, tara saura minti bakwai!Tara saura minti biyu!+
Fulani ta jefar da wayar hannunta kan gadon da take zaune cikin takaici, Ζ΄an mintuna tsakaninta da gama waya da Hajiya Bilki amma ta kira wayar Jakadiya kusan sau goma kenan har yanzu labarin dai bai sauya ba, kiran baya shiga, kamar yadda kai baya shiga ramin tulu.
Da haΖoranta na sama ta tamke lebbenta na kasa tana cigaba da gyaΙa kai cikin Ζwafa, biyawa kawai take a ranta cewa ko bayan wannan hargitsin ya Ζare Jakadiya Babba sai ta biya bashin wannan zulumi da Ιacin ran da ta saka ta, ita ce fa! Hafsatu. Wannan Hafsatun dake take jama’a da ikonta tamkar yadda takalmi ke murΖushe kwayar gyaΙa a dandaryar Ζasa.1
kamar ta kwanta ta Ιan runtsa tunda yau ba itace da turakar Mai martaba ba, sai kuma ta yanke shawarar fara yin wanka tukunna, wataΖila hucin da take ji a ranta ma ya tafi da saukar ruwan sanyin da take marari, saboda haka ta miΖe ta isa ga Ζofar makeken bandakinta na alfarma dake manne da da Ιakin.
A cikin banΙakin taji bata son sakin shower akanta balle shiga kwarmin wankan na bathtub, saboda haka ta jawo wani Ζaton bokiti dake gefe ta shiga tara ruwan zafi dana sanyi daga famfo yayin da ta koma ta buΙe wata drawer a gefe ta Ιauko wani Ζaton towel tana shirin naΙe jikinta dashi.
A daidai wannan lokacin ne daga can cikin Ιakinta, agogo ya karaΙe da sautin kiΙan algaita, kiΙan dake shaida cikar Ζarfe tara daidai na dare! Kuma a daidai lokacin ne ba tare Fulani ta sani ba wasu abubuwa suka juya a cikin ΖwaΖwalwarta, suka canja mazauninsu daga daidai zuwa akasinsa. Ta dai ji kanta ya sara kaΙan sai dai kafin ta fahimci komai ta tsinkayi Ζarar bugun kofar Ιakin daga can waje, wani bugu da yazama sila kuma masomin faruwar wata Ζaddara da ΖoΖari da taimakawarta ya samar da ita, don tabbas ne wasu ΖaΙororin, bawa nr ke zana su da hannunsa cikin allon rayuwarsa!1
Bugun Ζofar da Ιan Ζarfi yake don har sai da bugun zuciyarta ya daya a lokaci guda tare da mamakin wanda zai Ζaraso mata har ciki haka kuma ya tsaya buga Ζofar tunda ta san da Safina ce ba lallai ne ta buga Ιin ba, sai kawai ta fasa cire kayan sannan ta juya ta kashe ruwan da tara ta fita.
Kanta babu ko Ιankwali sai manya-manyan kalbar da ta kitse gashinta dashi saboda rashin lokaci ta Ζarasa ta bude Ζofar, kuma a take zuciyarta ta sake Ιaukewa da wani guntun taraddadi.
Wata fuska mai cike da haiba da kamala ta baΖunci idanunta, ta ninka taraddadin ta ya tashi daga wani abu guntu sannan haka kurum kuma jikinta yayi sanyi. Mai martaba a turakarta? Da wannan daren? Me ya kawo shi?? Yaushe rabon da ya tako Ζafarsa zuwa cikin sashenta?… Tun a ranar da yazo ya sanar da ita zancen maneman auren Aisha, zuciyata ta bata amsa kai tsaye shima kuma yazo ne ba da daddare ba, ta juya ta kalli agogon dake bayanta… karfe tara daidai, ai bai daΙe da shigowa cikin gida ba ma, to me zai sa ya nemeta a wannan dare kuma a lokacin da ba gurbinta ba? tabbas dai ta san ba Ζaramin abu ne zai kawo shin ba, sai dai ta kasa aunowa? Zancen bikin naΙin ne ko wani abu daban?
“Ranka ya daΙe…” A lokaci guda bakin ta ya ambata cikin Ζ΄ar Ζaramar gigicewa.
“Tare da naki sarautar mata…” Muryarsa ta fito a hankali yana ΖoΖarin yin murmushi.
“… Yau ikon naki ne ai tunda kece riΖe da kofa.” Ya sake faΙa da wata Ζ΄ar guntuwar raha a cikin sautin nasa.”
Sai a sannan ta lura tana tsaye ne riΖe da hannun Ζofar har yanzu, bata bashi damar shigowa ba, saboda haka tayi saurin yin baya kafin tace.
STORY CONTINUES BELOW
“Mamaki ne ya riΖe ni ai kuma na kasa tsinto komai a cikinsa.”
Ya shigo tare da mai da kofar sannan ya girgiza kansa.
“Ya kamata kuwa ace kin tsinto wani abun a cikinsa Hafsatu, bai kamata ki manta baya ba.”
Sai ta tuno wani zamani a lokaci guda, wani zamani daya shuΙe, wani zamani da mutanen yanzu zasu hasaso shi cikin kalar baΖi da fari, a lokacin da suke gaΙar cin amarcinsu, a sanda yake matsayin Ahmad Ιinta ba wani mai sarauta ba, a lokacin da zata Ιaura zani da Ζ΄ar blouse shi kuma yasa wando da shirt babu mai hana su, babu mai tare su… A wannan lokacin ya kan zo ya ΖwanΖwasa Ζofarta yazo ban haΖuri a fakaice duk sanda suka sami Ιan saΙani. Sai ta girgiza kanta.
“Tuna baya ai shine roΖo ranka ya daΙe, ta yaya zan manta kuwa? Kawai dai naga zamani ya shuΙe ne, abubuwa sun canja, a cikinsu kuma har da cewar yau bani ce da lokacinka ba.”
Duk yadda Mai martaba yaso ga daurewa, sai da yaji wani Ιari na zuciyarsa na ΖoΖarin karyewa da maganarta don yafi kowanne mahaluki saninta a duniya. Ya san Hafsatunsa tun asali, ya san irin Ζaunar da take masa, kuma har a yanzu da yake kallon Ζwayar idanunta gani yake kamar komai Ιin bai canja ba, gani yake kamar yau ne ya haΙu da ita a soro cikin daren azumin nan har ya kasa sukuni sai da ya sami bayanin inda take, yana ganin kamar yau ne aka kawo masa ita dauke da tarin Ζaunarsa fal a idanunta da kuma burin ganin cewa shi Ιin nata ne shi kaΙai…
Amma kamar yadda ta faΙa ne abubuwa sun canja Ιin. Zamanika sun shude kuma a yanzu ya riga ya horar da zuciyarta da tarin abubuwan da bata yi tunanin akwai mai saka ta ba sai don shi Ιin shine! Yasa ta yarda ta ture dukkan wasu burika da mafarkanta ta canja tsarinta saboda shi Ιin dai! Ya riga ya san da hakan tun daga daren da ta nuna masa bata son rikon Madaki har zuwa kan gangarowar fara aure-aurensa. Wata mace ce ita kamar kowa mai zuciyar dake son cigaban mijinta dana Ζ΄aΖ΄anta… Matsalar Ιaya ce, rashin iya daurewa zuciyar tata har shaidan yaci galaba akanta ta wurare da dama.
Sai kawai ya Ζaraso daidai gabanta sannan ya riΖo hannyenta da yake ganin kamar sun fara rawa.
“Zuwa nayi in baki wani labari Hafsatu, wani labari da baya canjawa a rayuwar kowanne Ιan adam. Don haka ki kwantar da zuciyarki dan Allah ki fahimce ni.”
Kalaman tsofaffi ne waΙanda Fulani bata saba jinsu a wannan zamanin ba, saboda haka yadda take kallonsa, gani take kamar za’a saka wani abu ne mai zagwanye shekaru a maido mata da matsayinsa na Ahmadunta ba wani mai muΖami ga kowa ba.
“Zuciyata ta kasa tsayawa, ka gaya min me ya faru kawai.”
Ta tambaya bakinta na shirin fara rawa, duk kuwa da yadda take ΖoΖarin danne taraddadin nata.
Mai martaba yaja hannunta zuwa bakin makeken gadonta suka zauna sannan shima ya tattaro dauriyar da ya hado kafin ya iya shigowa wajen nata, dauriyar gayawa UWA mutuwar ΖANTA!
“Hafsat, zaki iya tuna shekararmu nawa da aure kafin mu fara samun haihuwa ko?”
“Ta yaya zan manta? Shekarar mu uku har da watanni biyar kafin na sami cikin Saifudeen.”
Kai tsaye muryarta ta furta, tana fatan a tsallake komai a kai gaΙar da zata kai su ga bayanin da take son ji.”
“Zaki iya tuna abinda nake gaya miki a duk lokacin da kika damu kanki da tunani a wancan lokacin?”
Ta sake Ιaga kanta.
“Ζ³aΖ΄a da dukiya wata rahama da kyauta ce ta ubangiji duk sanda yaso sai ya baka ko ya karΙe.”
Mai martaba ya haΙiye yawu a maΖogwaronsa kafin yace.
“Na san kin yarda da hakan ko Hafsat? Tunda gashi ubangijin ya bamu Ζ΄aΖ΄an a lokacin da yaso kuma har mu raine su tsawon lokacin nan mun ma aurar da wasu. Haka ne?”
STORY CONTINUES BELOW
Wannan karon Fulani bata amsa ba, kallonsa kawai take yi, tana son tabbatar da abinda zuciyarta ke wassafawa.
“Ina so ki Ζarfafa zuciyarki Hafsatu, kiyi tawwakali kamar yadda kika yi tsawon shekarun da kika zauna a gidana ke kaΙai kina fatan haihuwa, ki sani cewa…”
“Ahmad!”
Sunansa da ta kira kai tsaye yasa dukkan wata magana dake bakinsa ta guntule, don ko a baya sai ranta ya baci sannan take tufe ido ta kira sunan nasa, daga lokacin da Ζ΄aΖ΄ansu suka fara wayo ma sai ta yakice sunan a bakinta gabaΙaya ta dinga binsa da ‘ranka ya dade ko Daddy’ saboda haka zai iya cewa shekaru da yawa sun wuce rabon da ta kira shi hakan sai dai ko cikin wasa.
“Waye ya rasu? Ka gaya min wa na rasa? Saifudeen? Nadiya? Aisha? Umar? Ko kuwa Safinan data fita yanzu?”
Cikin wani irin amo mai karyewa ta lissafo sunayen duka Ζ΄aΖ΄an nata, yayin da duk yadda yake hango dauriya a idanunta sai da wata guntuwar Ζwalla ta baiyana. Kallonsa take kamar tana son ya zaΙa a ciki ya faΙa mata kamar kuma tana son ya girgiza kansa yace ba haka zancen yake ba.
“Umarul-Faruk.”2
Ya furta sunan kai tsaye cikin wata dakakkiyar murya da a yanzu ke shaida cewa shi Ιin Sarki ne.
Fulani bata ko Ζifta ba, sai kawai ta cigaba da kallonsa kamar bata ji me yace ba tana jiran ya maimaita ne.
“Ba’a sanarwa da kowa ba, da yamman nan aka kira Saifudeen daga can Embassy aka faΙa masa rasuwar, sun ce cancer ce ta kama shi kuma shi kansa bai sani ba, yana ta karatunsa ne kawai yana shan Ζ΄an Ζananan magunguna, sai da ciwon ya Ιanyi karfi sannan abokansa suka kaishi asibiti. Kuma abin yazo da ajali ne kawai Hafsatu, ki yarda da hakan ki sawa zuciyarki hakan don na san ki san cewa akwai waΙanda ciwonsu yafi nasa Ζarfi ma amma sun tashi. Ki yarda cewa Faruk ya tafi ne dama ba don ya dawo ba, a can ajalinsa yake ko da wannan cutar ko babu.”
Kalaman tafiya suke a hankali, Fulani na jin shatin da suke bari akan fatarta har zuwa cikin kanta inda suke yiwa kansu masauki a bayan kan, don ta kasa gane ta yadda zata karΙe su ma balle har suyi ma’ana a cikin ΖwaΖwalwarta, Umar din nata ne ya mutu? Ζan da ta shekara huΙu bata ganshi ba sai dai taji muryarsa a waya? Ζan da taci burin ya kammala karatunsa ya dawo ya karΙi dukiyar mahaifinsa ya cigaba da juyawa? Me shi kansa Ahmad Ιin ke gaya mata ne a duk lokacin da tayi masa maganar kasuwanci wa Saifudeen?
…ki d’ora wannan burin naki akan Umarul-Faruk, fa’idar samun ‘ya’ya da yawa kenan…
To sai da ta gama yarda da hakan ta tsara komai cewar kafin Umar Ιin ya kai ga kammala karatunsa ta cimma manufarta ta kassara Madaki, ta karΙo dukkan dukiyar dake hannunsa ta kawo masa don shi ya juya, sannan kuma zai Ιauko Ζafa yazo yace mata wai ya mutu? Tsaya! Wace irin mutuwa ma wai?
“Nifa ban gane ba, ka gaya min komai yadda zan fahimta, wane Umar Ιin ne ya mutu? Sannan don me?”1
“A’uzubillah! Kar kiyi saΙo Hafsat, an taΙa tambayar ubangiji don me zai Ιauke bawansa? Naki ne? Halittarki ce? Ba kulawarsa ya bamu na Ιan wani wucin gadi ba? A yanzu don yaga damar karΙe abinsa sai muce bamu yarda ba? Ko kuwa…”
“Kaga tsaya, ya isa! Nace ya ishe ni Ahmad!”
Ta faΙa tana mai zare hannuwanta daga cikin nasa, a wannan lokacin me kuma waΙannan abubuwan da suka canja mazauninsu a cikin kanta suka shiga aiki.1
“Wallahi karya kuke! Daga kai har wanda ya kira wayar ya gaya muku wai Umar Ιin ya mutu! Ai ba’a halicci duniyata don inzo a tutar babu in koma ba wallahi, shikenan ribar me naci kenan? Na aure ka na haifi Ζ΄aΖ΄a? Ban tara abinda har tsawon shekaru sunana da na zuri’ata ba zai bar zukatan al’umma ba? In haka ne meye fa’idar halittar tawa tun farko?2
STORY CONTINUES BELOW
In don Cancer ce ke damun Farouk ai ba matsala, kasa Saifudeen da wasu su hau jirgi su Ιauko min abina zuwa gobe, ba dai ni na kawo shi duniyar ba to ina nai tabbatar maka cewa na san yadda zanyi in tashe shi da Ζafafunsa! Kai kanka shaida ne ai, tsawo zamana da kai akwai wani abu da na taΙa sawa a gaba kaga ban ci nasara ba? Ko zancen Madaki da duniya ke ganin na gaza Ιan taΖin kaΙan ne a yanzu, dawowar Jakadiya Babba kawai nake jira balle kuma akan abinda ni na haifa da kaina? Don haka kar ma a fara wata sanarwa, ka aika a Ιauko min Ιana Ahmad ni na san yadda zanyi dashi!”
Tun da ta fara maganar, wani abu ya sarΖafe Mai martaba a zaune, wani abu da bai san menene ba balle har ya fassara shi da suna… ΖwaΖwalwarsa na Ιaukan duk kalamanta tana sake biya su ne a Ιangaren ΖwaΖwalwarsa mai tacewa da fahimtar kowanne bayanai.
Abinda ya sani kawai shine ya fahimci abubuwa guda biyu kwarara… Dukkan maganganun da take faΙa maganganu ne dake fitowa tun daga Ζasan zuciyarta cike da wani yaΖini da babu shaci faΙi a cikinsa, sannan kuma Ζarara komai yake cewa ba’a haiyacinta take faΙarsu ba, watakila ma ba’a hankalinta ba!
Kallonta kawai yake kamar yadda tayi shiru itama tana kallonsa, dukkan jikinta na rawa, gaΙobinta na girgizawa da wata irin karkarwa yayin da zuciyarta ke dokawa a Ζirjinta har yana jin Ζarar bugunta daga inda yake zaune, tana bugawa tamkar zata daka tsalle ne ta faso ta Ζirjin nata.
A daidai wannan lokacin ne kuma motar Hamza tare da motar Ζ΄an sanda guda Ιaya dake binsa a baya ta shigo cikin ginin masarautar, hannunsa na hagu riΖe da sitiyarin motar yayin da hannunsa na dama ke riΖe da I.D Card na shaidar aikin direban matar sarki, wanda ke Ιauke da sunan Sani direba da kuma wasu Ζ΄an bayanansa!
***
LAGOS.
VoilΓ‘ Private Hosital, No 1388 Gyari Park.
Ζarfe bakwai ne na safiya don haka komai daidai yake da irin yanayin da yake buΖata a Ιakin, iskar mai daΙi da gamsarwa yayin da hasken Ιakin yake madaidaici mai rangwamen tasiri. Ibrahim Ahmad Madaki ya buΙe idanunsa a hankali bayan yunΖirin da yayi kusan sau uku.
Kuma a lokaci guda nauyin dake gefen Ζirjinsa ya tuna masa da halin da yake ciki, abinda ya faru jiya, komai yana kansa. Yadda zafin harbin nan ya ratsa kowacce jijiya ta jikinsa, yadda ya dinga jin zafin na tafiya zuwa sauran Ιangare na jikinsa, da yadda kowacce gaba ta jikin nasa tayi nauyi zafin na harbawa zuwa duk inda ya san saΖonsa zai isa.
Ya tuna sanda ya sake hango Ζyallin wannan Ζ΄ar jar fitilar a jikin baΖin mayafin Jidda, alamun waΙanda suka yi harbin basu gama ida manufarsu ba, sai ya maida idanun nasa ya sake rufewa sannan ya buΙe su, duk yadda ya kai ga tuna zafin da yake ji a wancan lokacin, muryarta da yake tunawa taso ta daine hakan, yana iya tuno yadda sautin nata ke karyewa cikin wani irin kuka kamar wancan lokacin da take roΖonsa cewa kar ya mutu, kamar shine abu mafi muhimmanci a rayuwarta, kamar zata shiga wani hali ne in har babu shi Ιin…
A lokacin ne kuma tunaninsa ankarar dashi wani abu na biyu a jikinsa bayan nauyin da yake ji a Ζirjinsa, wani abu tamkar Ιumi a tsakanin Ιaya hannunsa wanda babu ciwon, sai ya murza yatsunsa, yaji sun hadu da wasu daban Ζ΄an Ζanana masu madaidaicin laushi, saboda haka ya yunΖura ya kai idonsa wajen, a take kuwa idanun nasa suka yi kyakkyawan gani.
Jiddan ce zaune kan wata kujera dake jikin gadon da yake kwance, ta kwantar da kanta a gefen gadon itama inda jikinsa bai cinye ba. Sai dai ba wannan ne abinda yafi Ιaukar hankalinsa ba illa hannunta dake cikin nasa, yatsunta da suka ratsa a tsakanin nasa Ιauke da Ιigo-Ιigo na wani abu tamkar jinin da bai gama fita ba, yadda yatsunta suka shiga nasa sak irin yadda ya riΖo ta ne ranar da ya rabo ta da Ζ΄an uwanta a Kiyari, ranar da ubangiji ya Ζaddaro ta cikin rayuwarsa.
STORY CONTINUES BELOW
Baya iya ganin duka fuskarta don ta cusa ta cikin bargon da aka rufe jikinsa dashi, sai saman kanta kawai inda mayafinta ya zame babu Ιankwali, gaban gashinta da yake rabi kitso rabi a tsefe ya fito da yawa, yaji kamar ya miΖa Ιaya hannunsa ya rufe mata shi amma ya kasa, wani irin tausayinta ya ratsa zuciyarsa, kayan jiya ne a jikinta wanda har yanzu suna bace da jini alamun bata koma gida ba. Ya sani cewa a yanzu zan iya dafa Alqur’ani cewar zuciyar yarinyar nan mai kyau ce, tana tausayi ga kowanne Ιaya adam a duniya tunda har zata shiga irin wannan tashin hankali ga shi Ιin da bai taΙa tsinana mata komai, shi Ιin da Ζarara ya nuna mata cewar zarginta yake akan wani abu da a yanzu yake fahimtar bata san dashi ba.
Don tun sanda ya fara bincikensa a kanta bai taba samun wani abu da ya aibata masa halinta ba, komai yana siffanta ta ne da dukkan halin da ya same ta dasu, bata taΙa bashi wata kofa da zai Ιorar da zarginsa guda Ιaya akanta ba, ana cikin hakan ne kuma yazo ya rungume, yasa zuciyarsa ta kara damalmalewa da al’amarinta, ya fara jin wani abu game da ita da bai taΙa danganta kowacce mace dashi ba, kuma wannan abin shine tunanin cewa zai iya samun wani farin cikin rayuwa ta hanyarta bayan aiki da ibadar da yake ganin su kaΙai ne hanyar annashuwarsa.
A hankali idonsa yakai kan drawer dake gefen gadon inda wasu Ζ΄an tarkace suke, takalminsa ne da muΖullin motarsa sai wayoyinsa da wallet, bayan haka babu ko robar ruwa akai, alamun tun a jiyan nan bata sa komai a cikinta ba kenan tana gadinsa dashi da kayansa.
Kulawa irin wannan, wani rami ne mai zurfi da bai taba samun wani yayi koΖarin cike shi ba a rayuwarsa, bai san ma yaya take ba balle har ya taΙa hasashenta, watakila ita a wajenta abinda take yi ba komai bane illa taimakawa, amma a wajensa wani abu ne da a baya yasha hasashen cewa zai iya bada dukkann abinda ya mallaka don ace yau bayan mutane biyu a rayuwarsa wato Mahaifinsa da Mubarak, an wayi gari akwai wata zuciya da zata rikice wajen alhinin lafiyarsa irin yadda tayi, ace tsakani da Allah ba don wani abu nasa ba wata zuciya tayi taraddadin rasa shi, yaji cewa atleast he matters to one more person out there…!
Sai kawai ya sake haΙe yatsunsa da nata a hankali yayin da tunaninsa ke tariyo maganganun Mubarak.
…ina gaya maka ka saki ranka game da yarinyar nan ka juye sharrinta zuwa alkhairi, ka fahimtar da ita cewa ba Ζaramar sa’a tayi ba data same ka.’
Sai ya maida idanunsa a hankali ya rufe saboda allurar baccin bata kai ga gama sakinsa ba, zuciyarsa ta ayyana cewa wataΖila lokaci yayi da zai maida sharrin Fulani ya koma alkhairi gare shi!
**
11:30 Am.
“Anyi sa’a sosai, da yake a gefen kafada ne, bullet din bai lalata masa wasu organs da tissues masu yawa ba, sannan duk zuciyarsa ta buga bata yi bugun da zai haifar masa da wani ciwon ba, muna da visiting doctors na ciwon zuciya sosai, zaku iya magana da can asibitin nasa, a kawo file dinsa nan sai su duba da da zarar sun zo… Akalla dai bana jin zai wuce kwana bakwai zuwa takwas kafin mu sallame shi.”
Duk wannan bayanin yana fitowa ne daga bakin wani farin likita dake tsaye yana rubutu a gefen gadon Madaki, yayin da Mubarak da wata Nurse ke tsaye a kowanne Ιangarensa.
A sannan ya buΙe idanunsa a karo na biyu, hasken Ιakin mai yawa a yanzu ya shiga idanunsa, da kyar ya iya saita ganinsa akan mutanen dake tsaye a gefen nasa.
Ganin ya farka yasa likitan ya saki rubutunsa ya fara wasu Ζ΄an aune-aune a jikinsa Nurse din na taimaka masa. Idanun Madaki suka tsaya akan Mubarak bayan ya tabbatar da cewar iya su kenan a Ιakin. Kallonsa yake shima da idanunsa daje shaida irin kaΙuwar daya shiga da kuma tashin hankalin al’amarin, sai dai duk da haka wani abu ya canja game dashi Ιin, a yadda ya sanshi ko da wannan tashin hankali, zaiyi ΖoΖarin yi masa wani Ιan barkwanci ko raha, amma a yanzu kallonsa kawai yake cikin tausayawa.
STORY CONTINUES BELOW
“Bugun zuciyarka na kan track daidai, ka sami abinci mai laushi da ruwa haka wanda zai Ζosar da kai kaci a yanzu, zaka Ζara jin sauki insha Allah.”
Cewar likitan yana Kallon Madaki bayan ya tamaka masa ya dan jingina da gadon, Mubarak yaso yayi wa wannan bayanin, amma wani irin kwarjini da firmness da ya tsinta a idanunsa yasa shi fahimtar cewa ko bashi da lafiya shi Ιin dai shugaban kansa ne.
Madaki ya gyaΙa kansa.
“Nagode Doctor, sai dai ina ganin za’a rage min kwananakin da naji kana faΙa, don akwai ayyuka da yawa a gabana.”
Likitan yayi wani guntun murmushi sannan ya juya ya karanto su ansa a jikin file din.
“Komai yawan aikin dake gabanka Ibrahim ai sai da lafiya zai yiwu ko? Ta yaya zaka yi signing takardu da hannunka a Ιaure. Muyi fatan sauΖi kawai.”
Da haka ya tattara Ζ΄an tarkacensa ya fita Nurse din na bin bayansa.
Ya kalli Mubarak dake tsaye kyam har yanzu yana kallonsa sannan yace.
“Kaima nagode haka zaka iya tafiya, ba sai ka nuna min cewa yau asabar na katse maka baccinka ba.”
“This is not a joke Mdee, ka gaya min waye zai harbe ka a garin nan? Laifin me kayi? Ta yaya aka san inda kake ma?”
“Ban sani ba Mubarak, harbin ya taho ne daga can sama, ta yaya zan gane su waye a can?…”
Sai kuma ya Ιan tsaya kafin ya cigaba.
“… You mean ba’ayi involving Ζ΄an sanda ba ma? Ta yaya asibitin suka yarda suka karbe ni?”
“Ζaya daga cikin mutanen da suka dauko ka security personnel ne, ya kira mutanensa sun duba koina tun a jiyan amma ba’a sami kowa ba, so now case din ya dawo kanmu, kuma I don’t care how long you sit on that bed in dai zaka tashi, the only thing I’m after is dole ne mu samo mutanen nan Mdee, wallahi zuciyata ba zata iya Ιaukan wannan al’amarin ba, na dauki abubuwa da yawa akan rayuwarka a baya, na maida komai ba komai ba, na kalli abubuwa da yawa ta fuskar alkhairi amma banda yanzu. Zuciyata ta kai Ζarshe Mdee kuma wallahi ba zan dauka ba.”
Madaki yayi shiru kawai yana nazarin maganganunsa ba tare da yace komai ba, a tsawon rayuwarsa ya san Mubarak kuma ya san dukkan abubuwan daya faΙa gaskiyane, a kullum shi mai bashi fata ne akan abubuwan da yake ganin aibunsu, shi ke Ζarfafa masa gwiwa ya tunkari dukkan abinda yake shakka komai tsaurinsa kuwa , don haka in har a yanzu yace an kaishi karshe, to tabbas an kai shi Ιin don ko masu azancin magana kan ce mai haΖuri bai iya fushi ba.
“Then who are you suspecting?” (Wa kake zargi kenan?)
Mubarak ya gyada kansa bai tabbatar da abinda yake zargi ba har yanzu don haka ba zai fallasa komai ba, don duk yadda zuciyarsa ta kai ga turniΖewa yana tsoron yin abinda zai iya dana saninsa a gaba.
“Bincike zamu fara, amma kasa a ranka cewa ba zamu kyale ko waye ba wallahi.”
Madaki ya gyaΙa kansa, kamar ya fada masa cewa bashi suka zo da niyyar harbi ba sai kuma ya tuna da Jiddan, saboda haka yayi tambayar da yake son yi tun bayan farkawarsa.
“Ina take? Ζazu na farka na ganta a nan.”
Mubarak ya fahimci wa yake nufi Saboda haka ya Ιan cije leΙΙensa.
“Nasa an maida ita gida a motarka, tana bukatar canja kayan jikinta.”
Ya fadi hakan yana tuno yadda Jiddan ta dinga kallonsa a lokacin da ya dage sai ta tafin, idanunta na shaida kamar itama bata yarda dashi bane, kamar zai sace Madakin ne bayan tafiyarta.
“Nayi waya, su Khadija zasu Ζaraso maka da abinci yanzu.”
Cewar Mubarak Ιin, sai dai yana rufe bakinsa lokacin yayi daidai da sanda kofar dakin ta bude daga bayansu, dukkaninsu suka juya a lokaci guda kuma a lokaci gudan idanunsu suka sauka akan Jidda, tayi wanka ta canja kaya cikin wata doguwar riga baΖa data Ζara fito da hasken da fatarta ta fara a Ζ΄an kwanakin, sannan hannunta riΖe yake da wani Ζaton kwali duk samansa ya yayyage, ta tallafo abinta da duka hannayenta.
STORY CONTINUES BELOW
“Cewa Baba Saminun nayi ya jira nayi wanka mu dawo tare don ban san wa zai dawo dani ba idan ya tafi.”
Muryarta ta fito bayan tayi sallama tana kallon Mubarak Ιin dake mata kallo kamar na tuhuma, a tunaninta ganin Baba Saminun daya aika ya kaita ya dade ne yasa yake binta da wannan kallon irin na dazu, a cikin kanta gani take kawai duk irinsu daya da Madaki, kowa ba mutunci ne ya ishe shi ba shi yasa har suka zama abokai, amma tunda ta iya da Madakin to shima mai sauΖi be, sai da ta karaso kamar zata wuce shi sannan tace.
“Ina kwana? Ya mai jikin?”
A lokaci guda Madaki dake can zaune yaji wani abu kamar daΙi ya ratsa zuciyarsa, ko ba komai ta girmama Mubarak Ιin dabyake abokinsa duk kuwa da cewa fuskarta babu wata fara’a.
“Lafiya Ζalau.” amsar ta fito a gutsire daga bakin Mubarak.
Abinda ya Ιan bawa Madaki mamaki kenan har ya maida idonsa kansa, a yadda ya sanshi da zumudin ganinta ya Ιauka ai gaisuwar tasu zata fi haka, ko dai wani abu ya faru ne? Shi bai ga komai ba, don haka sai kawai ya alaΖanta hakan da yanayin da Mubarak Ιin ke ciki a lokacin. Idonsa ya koma kan Jidda da ta karaso ta ajiye katon kwalinta akan Ζ΄ar drawer dake gefen gadon, Ζamshin turarensa ya ziyarci hancinsa a take, sai dai kafin ya gama nazarin kwalin sai jin hannunta Ιaya kawai yayi a Ζasan wuyansa, kamar a jiya sanda take ΖoΖarin riΖe kansa kafin ya suman da yayi ya dauke shi, mamakin hakan ya sarke shi yayin da a lokaci guda sanyin hannayen nata ya ratsa fatarsa har cikin Ιargo.
“Yaya jikin naka? Da sauΖi? Me suka ce?”
Kafin ya amsa waΙannan tambyoyin yaji Ζarar rufewar Ζofa alamun Mubarak ya fita, basu gama zancen da suke ba amm sai kawai ya juyo da idanun nasa ya kalle Jiddan, a lokacin ne ta janye hannunta da sauri sannan tace.
“Kayi haΖuri, wata Nurse ce yanzu a hanya tace in taΙa jikinka, idan da Ιumi to kar kasha abu mai zafi a yanzu.”
Jidda ta fadi hakan a lokaci da wani Ιari na gefen zuciyarta ke Ζwafa, ta san ta jawowa kanta kenan don ta sani cewa ba yarda da maganganunta yake ba kuma babu ta yadda zai fara a yanzu. Kallon fuskarsa kawai take tana tunanin waye zai kalle shi yace shi aka harba jiya? GabaΙaya jinin nan daya Ιata jikinsa da fuskarsa an goge shi tas sannan an canja kayansa da wasu na asibitin masu hannu guda, don haka hannunsa daya dake daure da bandeji ya fito waje yayin da idanunsa da kamar sun Ιashe suka kara wani kyau da haskawa. Yana da dauriya tabbas, don watakila da ita aka harbin nan ya samu, da yanzu zaman jana’iza ake.
Bata yi aune ba a cikin tunaninta sai kawai ji tayi ya miΖo hannunsa Ιaya da babu ciwon kuma babu allurar drip Ιin ya kamo nata duka biyu, ya janyo ta zuwa kan gadon sannan ya zaunar da ita a gabansa, fuskarsa dab da tata, tana jin ma kamar numfashinsa na busawa ne a saman hancinta, sai duk da mamakin dake cinta sai ta kasa dagowa ta kalle shi kamar yadda ta kasa janye hannun nata, don da zarar rike ta ba abinda take iya tunawa a cikin kanta.
“Meye a cikin kwalin?”
Ya ilahy! Yadda muryarsa ta fito a hankali da wani zaki kamar an zuba mata sukari ya sata jin wani iri, amma duk da haka maimakon ta kalle shi, sai ta maida idonta kan tsohon kwalin itama sannan tace.1
“Abinci na kawo a ciki, kuma ba zan iya Ιauko duka kayan a hannu ba shi yasa nasa su a kwalin. a cikin store na samo shi, kamar na T.v ne ko wani abun, idan zan koma zan mayar maka da abinka ai.”1
Maganar taso tasa Madaki murmushi, a tunaninta tuhumarta yake game da kwallin? kwallin da bai san dashi ba ma, bata san shi ta abinda ke cikin kwalin yake ba don ya manta rabonsa da cin wani ΖwakwaΖwaran abinci a Ζ΄an kwanakin nan. A lokacin ne kuma yaji kamar sannan ya kamata ya gode mata, ya nuna mata Ιimbin godiyarsa game da karamcinta da kuma taimakonta amma ya rasa ta ina zai fara, bai ma san me zai ce Ιin ba saboda haka ya yanke shawarar tafiya kai tsaye ga abinda yafi fahimta a lokacin.
“Me kika dafa?”
Saura kadan Jidda ta dago ta kalle shi saboda mamakin tambayar tasa, ta zata ai a yanzu ma zai ce baya cin abinci mai nauyi ne ta koma da kayanta, don sanda take girkin, har Ζ΄ar mita take a cikin kanta cewar ba Ζaramin aikinsa bane ya juyo da ita da kayanta don taga alama shi anfi yin abu arziki dashi in har baya cikin haiyacinsa, sai gashi ya bata mamaki. Amma data lura luma sai taga ba abin mamakin don yunwa ba kanwar uwar kowa bace, inda zai dore a haka ma komai zai fi sauΖi don ita ba bakuwar zafi bace har hira sai su dinga yi kafin sanda zata koma garinsu. Saboda haka ta haΙiye yawu a hankali sannan tace.
“In ka saki hannuna zan zuba maka sai ka gani.”
Ta fada tana kallon hannayen nata daya riΖe, kamar yayi murmushi kar kuma bata tabbatar da hakan taji ba, sai ya zare hannun nasa a hankali sannan yace.
“Muna kwarya.”
Karo na farko tun bayan saninta dashi Jidda tayi murmushi mai kama da dariya har haΖoranta suka baiyana, ashe in ya sauke fadin ran nan da yake yi tsaf zai koma mutum?1
A lokacin da tayi murmushin kuma ta miΖe Madaki yaji zuciyarsa ta matse da wani tunani mai nisa… Ranar da ya dara ganinta ranar da ta juyo daga gaban saurayin nan Ιauke da wannan murmushin da ba nasa ba, a yau sai gashi shima yayi nasarar samun nasa a wajenta, watakila ma har ya fi na saurayin, sai dai tsaya! Wai wanene wannan saurayin ne? Ya samu kansa da yin tambayar da bata taba Ιarsuwa a ransa ba.1
“Baddo tace alaiyahu yana da mutukar amfani a wajen wanda bashi da lafiya, wai yana sa cikin mutum ya buΙe ya dinga cin abinci sosai, shi yasa na saka a ciki.”
Muryarta ta dawo dashi daga Ιan tunaninsa a lokacin da ta buΙe flask take zuba abincin. Baddo. Kakarta kenan, har ta fara bashi labarin danginta? Sai ya juyo ya kalle ta.
Ζamshin abin da take zubawa a plate Ιin ya cika hancinsa dama iskar Ιakin, Potate Ιin dankali ne da alaiyahun da kuma nama fal! Bakinsa yayi magiya kamar bai san cewa shi za’a kawowa ba.1
“Beleive me, idan cikina ya buΙe ba zaki ya ciyar dani ba.”1
Ya faΙa yana girgiza kansa tare da kallonta, sai ta sake wani murmushin Ιan karami ba tare da ta juyo ba, dama ba wuya ne wai sata dariya?
“Tab! Ai baka sanni bane shi yasa, akwai fa sanda har tukunya guda ta tuwo muka tuΖa ni da Sadiya sanda ana wani biki a Ιangaren mu, kaga kuwa zan iya.”1
Sadiya. Ya sake rubuta suna na biyu wanda ya riga ya sanshi a zuciyarsa sanda ta Ζaraso gabansa, sai dai bata zauna akan gadon ba sai ta jawo wata kujera a gefe kamar Ιazu ta zauna sannan ta ajiye plate Ιin a akan gadon. Ya kalli plate din a hankali yana shirin ya gaya mata cewa ba zai iya ci da hannun hagu ba sai kawai gani yayi ta Ιebo a cokalin ta miΖo masa… Ya dago ya kalle ta, itama shi Ιin take kallo da alamar yaci mana.
“Babu zafi.” Muryarta ta furta a hankali tana Ιan girgiza kanta.
A cikin zuciyar Madaki, a wannan lokacin fata kawai yake a cikin zuciyarsa cewa ubangiji yasa bai cuci yarinyar nan ta kowanne bangare a dan zamansu ba, don bai san ta yaya zai wanke kansa ba. A yanzu ya fahimci cewa bayan saukin kanta, in zata yi abu kawai zata yi shi ne babu ruwanta da wani iyayi irin na mata wanda ke kaisu ya baro a mafi yawan lokuta.
Sai kawai ya lumshe idanunsa a hankali, ya ajiye komai a gefe sannan ya raba fatar leΙΙen bakinsa slightly yana shirin hango abinda bai taba hasashe a rayuwarsa ba, Jidda tayi murmushi a hankali itama sannan ta saka cokalin a bakinsa daidai lokacin da Ζofar Ιakin ta buΙe… Khadija ta shigo riΖe da Hanan yayin da Aliyu ke bin bayansu, a nasa bayan kuma, Salwa ce Ιauke da wani haΙaΙΙen basket mai Ιauke da foodflask kala-kala na abinci iri-iri!.17
A cikin wayar Madakin kuma dake gefe, text ya shigo na labarin rasuwar Umarul- Faruk!1
***Hoto Ζarya ne!
Abinda Salwa ta ambata kenan a lokacin da tayi arba da fuskar Madaki kuma numfashi ya tsaya a maΖogwaronta, don yana da wani irin kwarjini da kamala wanda ya fito karara fiye da yadda take ganinsa a idanunta. A lokacin da yayi murmushi wa Aliyu dake nufar wajensa kuwa, sai da zuciyarta ta buga cikin Ζirjinta sannan a take wani gefe na ΖwaΖwalwarta ya tuna mata da nata kammanin, kamannin fuskarta… Musamman wasu Ζananun Ζuraje da suka fito akan kuncinta duka biyu.1
Sai kawai ta juyar da kanta gefe sanda muryar Khadija kewa Aliyu daya ruga magana cewa kar taje ta hau kansa, a lokacin ne kuma idonta ya sauka a gefem, gefen gadon… Inda duk da Ιimbin abinda take ji take zuciyar ta gaya mata cewa yarinyar da take kallo itace wannan halittar dake cikin jerin abubuwan da take son kawar wa a duniya, amma yarinya kamar wannan? Ta yaya hakan zai yiwu? Ta yaya za’ace da wannan abar take gasa wajen mallakar sunan Matar Madaki? Ta yi zaton zata ga irin wayayyun matan nan ne da suka goge da duniya ta hanyar kudi da kuma dukkan wata wayewa ta zamani, amma wannan? A lokaci guda sai taji wani dunΖulen abu ya zarce cikin busashshen maΖogwaronta.1
Akan wannan yarinyar da bata da ko kyau balle daukar hankali ta rikita nutsuwarta? Akanta ta Ιata dubunnan kuΙaΙenta da har aka tafka wannan akasin? Akan wannan yarinyar da baifi cikin kwana Ιaya Namama ya tarwatsa ta da dukkan ahalinta ba? Allah ya sani ba irin nadama da takaicin da bata yi ba a lokacin da ta samu labari abinda ya faru, wanda ta danganta komai da rashin Ζwarewar mutanen kawai ba don wata Ζaddara ba.
Saboda tun a Abuja sau nawa tana ganin ana gudanar da ayyuka irin wannan kuma ba’a taba samun wani akasi ba sai akan nata? Zuciyarta taso ta kumburan tun a jiyan da Khadija ke gaya mata abinda ya faru bayan fitar Mubarak, amma da ya dawo ya shaida musu halin da ya baro shi a ciki cewar al’amarin da sauΖi sai itama ta sami nata sauΖin a zuciyarta.
Tana ganin watakila hakan ma ya zame mata wata hanyar da zata fara aiwatar da kudirinta akansa, watakila tunda bai raunana da yawa ba, hakan somin hanyar nasararta ne, musamman a yanzu da tayi ido biyu da yarinyar sai ta sake raina komai, take ganin cewa ba sai ta tashi hankalinta ta sake wahalar da kanta a karo na biyu ba… Babu abinda yarinyar ta sani kuma babu abinda zata iya tare mata, don in ba aikin Ζaddara ba kamar yadda Mubarak ya siffanta ta yaya ma za’a haΙata da Madakin? Ai ko makaho idan ya shafa zai san cewa banbancin a baiyane yake! Mata irinta masu wayewa da sanin rayuwa su suka dace da maza irinsa ba wannan Ζ΄ar abar da wani sai ya duba sau biyu tukunna zai ganta ba.1
Baki da wata matsala! Gefen zuciyar tata ya ayyana hakan a ranta, yana gaya mata cewa an sami wannan akasin ne don ta daina wahalar da kanta, tabi komai a sannu… Ibrahim ba zai taΙa son wannan yarinyar ba kamar yadda itama ba zata san darajar abinda ke hannunta har ta iya karkato da hankalinsa kanta ba…
Khadija na ta ΖoΖarin gaisawa da yarinyar data miΖe rike da plate Ιin abinci a hannunta yayin da har a lokacin Madaki ke murmushi wa yaran, ya miΖowa Aliyun hannu suka yi musabaha kamar wanda ke gaisawa da sa’ansa… Wani Ζullutun abu ya taru ya sake cika maΖogwaronta fam, tayi ΖoΖarin haΙiye yawu amma wannan karon ya kasa tafiya, tana jin kamar zuciyarta ce ke ΖoΖarin tahowa ta fito… Ina Naja’atu take ne? Tazo ta gaya mata tunda suke yawace-yawacensu akwai namiji irinsa da suka taΙa gani, sai dai maza wanda za’ace sun fi shi a kyawun fuska amma ba kamala da kwarjini ba, to ta yaya kuwa ba zata yi dukkan ΖoΖarin ta akan ta mallake shi ba?
Tana tsaye a kofar har a lokacin babu wanda ya lura da ita, kamar ta daurewa komai ta karasa ciki sai kuma taji cewa bata shirya ba, sun taho ne da dan guntun firgicinsu na halin da zasu zo su tarar dashi a ciki, amma tun da har ya warke haka yana iya gane mutane da wannan murmushin… To sai ta shirya tukunna, sai ta shirya a yanayin da kowannensu zai ga darajarta, kowannesu zai ga Ζimarta, Salwa ce ita! Wadda ke shirin hawa matsayin matar Madaki, don haka Madakin ba zai ganta a haka ba sai a yanayin da ko daga mafarki ya tashi zai ga banbancinta da wannan baΖar yarinyar da bata ko hango ta a cikin idanunta!
STORY CONTINUES BELOW
Saboda haka sai kawai ta sunkuya ta ajiye basket Ιin hannunta tare da katan Ιin lemon Rani dake hannunta sannan ta juya.
*
Kwarai Jidda taji dadin zuwan baΖin da daga baya ta fahimci cewa matar Mubarak ce da kuma Ζ΄aΖ΄ansa biyu, Khadija ta girme mata sosai don ko a ido zata iya cewa tafi sa’ar Jamila ma, amma yadda ta dinga janta a jiki da hira sai taji kamar ta ga wata Ζ΄aruwarta ne daga gida, kamar taga wanda ta sani bayan daΙewar wani lokaci, kuma da yake itama Khadijan tana da Ζ΄ar magana har sai suka saba kafin tafiyarsu, ta dinga mamakin yadda take da tsananin kirki sosai ba kamar mijinta ba wanda zuciyarta ta saka shi a wani layin can daban.
Sun dade har yamma bayan tayi ta kiran nambar wata a waya wai ita Salwa, tace tare suka zo amma ita dai bata ganta ba sai kayan da aka ajiye a bakin kofa tace a hannunta suke, daga baya ne ta same ta a wayar take shaida mata cewa wai bata jin daΙi ne taje taga likita anan cikin asibitin sai kuma ta koma gida. Ta lura sai a lokacin Khadijan ta dan ji dadi don tana ta faΙin dama bata san abinda zata gayawa Mubarak din ba tunda Ζanwarsa ce.
Yarinyarta mai suna Hanan itama tayi ta bibiyarta har tana faΙin cewa ta mata kitso irin nata mai iya rabi kawai, Jidda tace ai karta damu tunda sabon style ne da ita ta fito dashi to kuwa ta sami kitson yi. Kuma duk tsawon wannan lokacin in banda waya ba abinda Madaki yake yi, kala-kala wadda bata fahimtar komai a ciki saboda yadda sautin muryar tasa ke fita a hankali kamar wanda ke cikin wata damuwa, ta dai fahimci kamar ba wayar aiki bace tunda aΖalla yau asabar ma, sai dai bata san me ya faru ba.
Da kyar ma ya cinye abincin data fara bashi bayan wata Nurse ta shigo da azahar ta cire masa drip Ιin, a kayan su Khadija kuwa fruits kawai yasha, hannunsa daya riΖe dana Aliyu wanda ya manne masa alamun shima mai son manyance ne irinsa.
Abinda Jidda ta kasa ganewa shine wane irin Ζarfin hali ne da Madaki, don duk da damuwar da taga kamar yana ciki, da la’asar bayan an cire masa drip Ιin ita yasa ta miΖo masa gogaggun kayan jikinsa da aka cire yace wai masallaci zai je, sai Allah yasa lokacin yayi daidai da shigowar wani likitan yamma, shi ya dage yafi karfin hujjar da Madakin ya kafa cewar zai iya fita Ιin yace dole ba zai bar Ιakin nan ba.
Ana dab da sallar magriba su Khadija suka tafi, a lokacin Mubarak ya dawo sun fi kusan awa guda suna tattauna abubuwan da su kadai ke fahimta, don yadda suke magana Ζasa-kasa kuma Madakin na cigaba da amsa waya daya bayan Ιayan bai sa ta fahimci komai ba.
Har can waje taje ta raka su Khadijan riΖe da hannun Hanan, sai dai bata karasa wajen parking space din ba don har yanzu bata jin zuciyarta tayi kwarin da zata iya tunkarar wajen nan.
A hanyarta ta dawowa ta dinga kallon kyan tsarin asibitin da ko a ranar da suka zo bata lura dashi ga, zuciyarta ta ayyana mata cewa dole ne a cafki mugwayen kudi a wajen nan don tabbas ba zasu yi wannan haΙaΙΙen ginin a banza ba, sai ta hango asibitin garinsu na gefen masarauta, wajen da warin izal dana kwata kadai ya isa wani ya kamu da wata cutar, banda Ζ΄an banzan ciye-ciyen da mata ke yi a wajen zaman likita, suyi ta siyan abubuwa suna jefawa a baki ba tare da sanin yadda aka yi su ba.
Hanya ta kawo ta wajen wannan lab din da aka mata test Ιin nan, taji kamar ta leΖa ta gaya musu an kwantar da baban nan nata a asibitin ko zasu zo dubiya tunda ta san bayan iyalin Mabarak Ιin nan basu da kowa a garin, amma sai taga babu kowa a ciki don haka ta karkato hanya ta dawo Ιakin.1
Ζarar ruwa a famfo ya tabbatar mata cewa Madaki yana ciki yana alwalar da bata san ya yake yinta ba tunda hannu Ιaya a Ιaure yake, saboda haka sai kawai ta juya ta sake fita. A Ιan bayan ward Ιin kaΙan akwai wani waje da akayi shuke-shuke da fanfo a tsakiya wanda aka saka masa mesa don bawa fulawowin ruwa, bata ko damu Ζ΄an karafunan da aka zagayen wajen dasu ba ta tsallaka ciki ta zare mesar jikin fanfon ta kunna sannan tayi alwalarta, tana yi tana bin duk wanda suka haΙa ido dashi kallo itama tana mamakin abinda yasa suke kallon nata, ilai kuwa sai ga wani security nan yazo da bayanin cewa ba’a shiga nan ta fito.
STORY CONTINUES BELOW
Slippers Ιinta duk ruwa ta koma Ιakin a lokacin yana sallah akan wani Ιan center carpet dake gefen Ιakin, yana zaune cikin tahiyya ya juya mata bayansa Ιakin shiru baka jin komai illa Ζarar fitar A.c, sai dai yana miΖewa tsaye cikin raka’a ta uku da muryarsa ta fara rero surar fatiha a hankali cikin sautinsa sai da taji tasirin amon muryar tasa har a jikinta.
Ta matsa zuwa kan carpet Ιin da niyyar binsa jam’in, a karo na farko bin wani namiji jam’i bayan limaman islamiyarsu, har zata tayar sai kuma taga kamar bata yarda da carpet din ba tunda ta kula yawanci ma’aikatan asibitin arna ne, musamman masu shara, likitan ma Ιaya kawai ta gani kamar musulmi sai kuma waΙannan matan na lab wanda da alama su hausawa ne ma.
Saboda haka sai ta kwanto Ιankwalinta ta shimfiΙa a saman carpet din sannan ta gyara mayafin kanta kafin ta tayar.
Ko kaΙan Madaki bai san shi take bi sallah ba sai bayan da yayi sallama ya juyo sannan yaga ta miΖe tsaye, a lokaci guda sai yaji kamar wani abu ya ratsa zuciyarsa dake da tauri a lokacin, ya kasa sabawa da al’amarinta har yanzu, ya kasa sabawa cewa akwai wataa karΖashinsa dake cikin ikonsa, shekaru fiye da talatin yana rayuwa shi kaΙai, bai taΙa samun wani makusanci irin haka ba saΙanin Mubarak da suka hadu tun a makaranta, shi yasa dole a dauki lokacin kafin ya gama fahimtar hakan.
Carpet Ιin bashi da wani girma, saboda haka a yanzu da ya juyo sai yayi kusa da ita sosai, don da tayi sujjada ma kanta da kaΙan ne bai Ζaraso Ζafarsa ba. Idonsa ya sauka akan sauran jikinta, shape din jikinta… A cikin kansa tunani yake in har da gaske ya yarda zai gyara alakar tasu to ta ina ya kamata ya fara ne? Bata hakuri? Yarda da ita ko kuma shawarar da Mubarak ya taΙa bashi tun a farko? Wayarsa a Ζasan carpet Ιin tayi Ζara, ya jawo ta ya Ιauka.
“Assalamu alaikum, barka da yamma.”
Yayi gaisuwar a lokacin da ciwon kafaΙarsa ya shiga zugi, alamun lokacinsa yayi.
“Alhamdlillah, mun yini lafiya Hajja?”
Ya sake wata gaisuwar a lokacin Jidda ke yin sallama.
“Banso kika ji labari ba, ba wani ciwo ne mai yawa ba Hajja, ko ciwon wannan Ζafar taki ma yafi shi zafi.”
Akayi magana cikin wayar wanda yasa shi wani Ιan guntun murmushi, Jidda ta kalle shi sai kuma tayi niyyar tashi ganin yadda yake zaune kusa da ita sosai. Ta damΖo mayafinta a lokacin da ya riΖo nata hannun, ta juyo ta kalle shisai ya mata alama da ido cewar ta dawo ta zauna kafin ya faΙi wani abu kuma a cikin wayar da ya sanya zuciyarta bugawa.
“Gobe za’a kawo gawar tasa ne?”
Sai ta dawo ta zauna Ιin tana jin kamar hannunta na rawa a cikin nasa, ba wai don ya riΖe ta ba don a yanzu tana jin kamar ta saba ne da hakan. Tunanin waye ya rasu kawai take don daga yanayin yadda yake wayar kamar yana magana ne da wata Ζ΄aruwarsa.
“Kar ki damu Hajja, insha Allah I’ll be there, zan zo, dani za’ayi komai.”
Ya sake yin shiru sai kuma yace.
“Tare zamu zo, zaki ganta insha Allah.”
Ya gyaΙa kansa sannan ya Ζara da..
“Allah ya Ζara haΖuri.”
“Waye ya rasu?”
Yana sauke wayar Jidda ta tambaya. Ya juyo ya kalle ta sosai, ba tare da ya saki hanunta ba yace.
“Wa kika sani a cikin Ζ΄aΖ΄an Mai martaba?”
“Ban san kowa ba, Sadiya dai tana gaya min sunayensu ko kuma ta nuna min su idan ana wani taro.”
“Ta taba ce miki akwai wani Umar.” Muryarsa a hankali take fita yana kallonta.
A lokaci guda Jidda ta tuna wannan ranar da suka taΙa leΖawa b’angaren wani Ιan mai martaban da tace sunansa Umarul-Faruk, wanda tace mata yana Ζasar waje yana karatu ranar an buΙe wajen ne kawai ana share-share.
STORY CONTINUES BELOW
“Na san sunanshi… Ban taba ganin shi ba dai.”
Ya hadiye yawu a hankali har hakan ya motsa Adam’s apple dinsa sannan yace.
“Shine ya rasu, jiya, a can kasar da yake karatu.”
“Innalillahi wa’inna ilahir raji’un…. Allah ya jikansa, Allah ya gafarta masa.”
“Ameen.”
“Rashin lafiya yayi?”
“Sun ce Cancer ce ta kama shi.”
A hankali ta sake gyada kanta ta kara cewa Allah ya jikansa shima ya amsa da Amin. Sai kuma suka yi shiru ba wanda ya sake magana yana rike da ita har a lokacin, sai a sannan kuma Jidda ta fahimci dalilin da damuwarsa ta Ιazu da kuma wayar da yayi ta amsawa tun safe. Abinda har yanzu bata gane ba shine, shi qmeye matsayinsa ne a masarautar nan? Ta san kowa na masa kallon Ιan Mai martaba ne amma ita bata taba ganin wata alama a wajensa ta hakan ba, a yanzu ma me yace ne? ‘Ta san Ζ΄aΖ΄an Mai martaba?’
“Me kika dafa bayan dankali?”
Muryarsa ta sake sawa ta kalle shi, kafin ta sunkuya a hankali.
“Shi kadai na dafa, sai kayan tea a flask, amma ga abinci nan kala-kala su Aunty Khadija sun kawo.”
Yayi shiru kamar mai nazari sai kuma yace.
“Ki haΙa min tean.”
Sai ta zare hannunta sannan ta mike tsaye, a cikin kanta tana tunanin dalilin da yasa ne a yanzu yake kula ta haka, watakila don yana ganin tana tausayinsa ne.
“Idan zan tafi, in tafi da kayan abincin kenan?” Ta tambaya sanda ta sake dawowa ta miΖo masa kofin kakkauran tean data haΙa. Ya karΙi kofin.
“Ina zaki je?”
“Idan zan tafi gida.”
“Yaushe zaki tafi?”
“Idan Baba Saminun ya dawo.”
“Yace zai dawo ne?”
Sai ta Ιan tsaya tana nazari.
“Zaki iya kwana ke kadai ne a gidan?”
Tambaya ce mai ma’ana, wadda bata ma yi tunanin ta balle nazarinta, ba laifi ta san gidan na dan dan girmansa don haka dole zata ji tsoron kwana a cikinsa ita kaΙai, ranar da bashi da lafiyan nan ganinsa ne kawai bata yi ba amma ko bacci ta kasa, amma idan har bata koma ba anan zata kwana kenan?
Sai dai kafin ta sami amsarta Ζofar Ιakin ta buΙe, wasu Nurses biyu suka shigo da likita Ιaya, kowannensu da kayan aiki a hannunsa, sai tayi saurin matsawa kaΙan duk da wannan karon ba a kusa dashi take sosai ba.
“Jiki ya fara kyau kenan? Har ka sauko?” Cewar Namijin.
“Gashi kuma zamu Ιan Ζwace mata shi ba, don lokacin dressing ne yanzu.”
Cewar daya daga cikin Nurses Ιin.
Madaki yayi murmushi yana miΖawa Jidda kofin hannunsa kafin ya miΖe a hankali.
“Kar ka damu, nima ba zanyi musu ba ai ‘cus I need it.”
Suka yi murmushi bakiΙayansu.
“Sannu, ashe baban naki ne tsautsayi ya faru akansa.”
Cewar Ιaya Nurse din ta Ζarshe bayan sunyi gaba. Jidda ta Ιago ta kalle ta, a lokaci guda ta gane ta, tana Ιaya daga cikin waΙannan Nurses din nan na lab, saboda haka ta gyada kanta sannan tace.
“Eh wallahi, kuma Maman tawa bata nan ne shi yasa nake kula dashi. Mun gode.”5
Nurse Ιin ta juya kawai bayan ta fitar da wani Ιan siririn tsaki. Jidda ta bi ta da kallo sannan kuma idonta ya sauka a can kan gadon da Madaki ya koma ya kwanta, rigar asibitin mai maΙallai ce a gaba don haka namijin ya cire su gabaΙaya an buΙe Ζirjinsa suna ΖoΖarin fara aikinsu, sai tayi saurin dauke kanta saboda hakan wani abu ne da bata taΙa gani ba tsawon rayuwarta. Amma tsaya, don me ita zata juya bayan ga Nurses Ιin nan tsaye suna kalle shi? Su da basu haΙa ma komai ma dashi ba, saboda haka sai kawai tayi Ζarfin halin juyowa kofin tean nan riΖe a hannunta. Ai kuwa shima ita yake kallo, straightly ta tsakanin jikin Nurses din.1
STORY CONTINUES BELOW
Kallonta Madaki yake, cikin idanunta sosai kamar mai son binciko wani abun, kamar mai neman wani abu da yake tunanin cewa yana nan ciki, a sannan ne kuma namijin nan ya Ιage auduga da plaster dake rufe ciwon nasa baki Ιaya, sai yabi idanunta da kallo sanda ta kalli ciwon da kuma sanda ta sake dawowa ta kalli fuskarsa, sai ya girgiza mata kai a hankali alamun kar ta janye idanun nata, kamar roΖonta yake, kamar kallon nata shi zai sa ba zai ji zafin ciwon ba.2
Kuma haka kurum sai Jidda bata daina kallon nasa ba.
*
“Saura guda Ιaya…”
Muryarta ta faΙa bayan wani lokaci, bayan an gama dressing din, don har sai da idar da sallar isha’i ma sannan suka kammala, suka ajiye wasu magunguna da zummar cewa idan yaci abincin dare sai yasha su.
Wannan karon a zaune yayi sallar ishar saboda raΙaΙin da yace ciwon na masa sosai ba zai iya sunkuyawar sujjada da ruku’u ba, kuma teansa kawai ya karba ya shanye bai ce mata zai ci wani abincin ba don haka ta debo magungunan ta shiga bashi. Kuma daga yanayin yadda yake sha, sai taji dama ta bashi a lokacin da yake shan tean don watakila ruwa ya masa yawa ne.
“Ko za’a ajiye wannan sai anjima?”
Ta tambaya riΖe da maganin na Ζarshe. Sai ya girgiza kansa.
“Akwai maganin bacci a ciki, so ba lallai in kai anjiman idona biyu ba.”
Muryarsa ta fito baya kallonta, tana ganin yadda yake yamutsa fuska kaΙan alamun dannewa raΙaΙin ciwon da aka tabo kafin ya karbi Ζwayar maganin a hannunta, sai dai wannan karon maimaikon ta mika masa robar ruwan, sai kawai ta kaita daidai saitin bakinsa ta Ιago masa da ita, shima sai ya dora hannunsa na hagu akan yatsunta yana taya ta tallafewa.
A yanzu Jidda ta riga ta saba da hakan, don duk sanda ya rike tan, tana jin yatsun nasa kamar wani ciko ne da ya kamata dama ace akwai a hannun nata, kamar dama wajen bai taΙa zama complete ba sai da ya fara riΖe tan.
Bayan ya gama shan maganin, ta taimaka masa ya gyara kwanciyarsa sosai sannan ta isa wajen Ζofa ta rage hasken fitila daya a dakin, babu zancen komawarta gida ta sani don da gaske ne bai kamata ta tafi ta barshi shi kadai ba, sai a yanzu ma take ganin wautarta da ta tambayi tafiyar, ai baza ta taba samun kwanciyar hankalin bacci ita kaΙai a gidan nan ba ma.
Ta dawo ta Ιan saΙa murafan flask din abincin da su Khadija suka kawo don gudun lalacewa sannan ta Ιauko wani sabon katon bargo da wata matron ta kawo tun da yamma akan fridge sannan ta zagaya zuwa gefen gadon daidai saitin fuskarsa.
“Kana bukatar rufa?”
Muryarta ta tambaya a hankali tana kallon idanun nasa dake ΖoΖarin lumshewa, Jidda bata lissafa fa ba balle har ta hango sanda hannun nasa ya dago ya kamo nata, ta dai ji yatsunsa a cikin nata ne kawai kafin ya jata gabaΙaya ta tafi zuwa kan gadon, kanta ya sauka a gefen filonsa yayin da rabin jikinta ke cikin nasa Ιangaren da babu ciwon, gadon da take gani karami mai cin mutum daya sai gashi har da space a bayanta.
“Yes, ki rufe mu…”3
Muryarsa ta fito dab da kunnenta, dumin ta ya busa akan fatar ta, ya haddasa Ζarin rawar da zuciyarta ke yi, a hankali ta ciji saman lebbenta wajen ΖoΖarin saita kanta sannan ta ware bargon dake hannun nata ta shimfiΙa a jikinsu.
“Thank you.”
Madaki ya sake faΙa daga can kasan maΖogwaronsa, a wannan lokacin kwata-kwata bai damu da komai ba, so yake kawai ya fara aiwatar nufinsa na gyara alakar tasu don shi mutum ne mai tsari, kuma idan ya tsayar da zuciyarsa kan abu to babu wani abu dake sa shi ya canja, hakan wani sirri ne na nasarar kasuwancinsa dama dukkan rayuwarsa bakidaya, don haka bai damu da dukkan tunanin da Jidda zata yi a lokacin ba, so yake yama yi nasarar goge duk wani hasashen nata ya saka mata wani sabon tunani na yadda yake son rayuwarsu ta tafi tare daga yanzu.
STORY CONTINUES BELOW
Yana jin yadda take motsi a gefen nasa kamar mai son gyara kwanciyar tata, kamar kuma ta rasa yadda zata kwanta Ιin, a Ζasan bargon yasa hannunsa Ιaya ya riΖo nata, wani abu da yasa tayi saurin Ιago da idanunta ta kalle shi, shima ita yake kallo, don haka yaga sanda maΖogwaronta ya motsa kamar ta haΙiye wani abu kafin ta sake sadda idonta Ζasa.
Bai san me take tunanin ba amma dai ko meye Ιin, ya hango cewa bata da niyyar bijire masa a cikin idanunta, bata da niyyar challenging Ιinsa. Shiru ya wuce tsawon wani lokaci babu wanda yace wani abu amma zuciyoyin kowannensu da abinda take tunanin. Zuwa can kawai sai yaji muryarta tayi magana.
“Zan iya tambayarka wani abu?”
Sauyin ya fito a hankali kamar tana tsoron in tayi maganar da karfi zata fama masa ciwon ne, sai yayi motsi da yatsunsa a cikin nata kafin muryarsa ta fito very low shima.
“Ina jinki…”
“Umar Ζanin ka ne?”
Tambayar ta shammace shi don bai taba tunaninta a yanzu ba, amma sai hakan ya haska masa wani bangare na tunanin da zuciyarta ke yi akansa, tana son ta san wanene shi ne, tana son aΖalla ta san wani abu nasa don daga yadda tayi tambayar har cikin zuciyarta ne ya san bata sani Ιin ba, zuciyarsa ta Ζara yarda cewa ita ba yarinyar Fulani bace, bata san komai akansa ba.
Kuma idan ta tambaya din a yanzu ba laifi tayi ba, shi ya riga ya san duk wani bayani karami da babba akanta, ita kuwa da alama bata san WAYE SHI ba, kawai ta daurewa zuciyarta ne tana rayuwa da shi din da akace mijinta ne kawai. A hankali ya cigaba da wasa da hannunsa a cikin nata sannan muryarsa ta fito.
“Farouq dan Mai martaba da Fulani ne, amma bana jin zan iya kiransa da kanina.”
“Saboda me?”
“Saboda ni ba Ιan Mai martaba bane…”
Kafin tayi wani yunΖuri ya cigaba.
“Sarki ya tsince ni ne a lokacin da ban fi shekaru huΙu ba, a can state Ιin Yola wajen aikinsa, tun daga lokacin ya rike ni kamar dansa har zuwa yanzu, shi yasa mutane da yawa ke tunanin nine babban Ιansa ba Saifudeen ba.”
Yana iya hango tsananin mamaki da kuma wani abu daban a lokacin da ta dago da idonta ta kalle shi cikin hasken Ιakin mai rangwame.
“Su waye iyayenka to? Baka koma wajensu ba?”
Wani abu kamar murmushi yayi playing akan leΙΙensa.
“Ta yaya zan koma wajensu? Ban taba saninsu ba, ban taba samun wani abu da zai danganta ni dasu ba, a lokacin da Sarki ya tsince ni ko hausa bana ji kuma ban san sunan yare na ba, ban san ma wa na gani na karshe kafin Ιata na ba.”
Kallonta yake yayin da idanunta ke haskawa da dimbin abubuwan da zai so ta fassara masa su kafin ta mai da idanun nata Ζasa a hankali.
Dubunnan tunani ne ke faruwa akan Jidda wannan lokacin, ta san dama shi ba dan Fulani bane tun farko shi yasa take ΖoΖarin cutar dashi ta hanyoyi kala-kala, amma bata taba sanin cewa shi ba dan Mai martaba bane sai yanzu, ashe shi yasa Ζiyayyar tasa tayi yawa a zuciyarta? Ganin cewa Sarkin baya banbanta shi da Ζ΄aΖ΄an ta? Shi yasa har take binne asiri kala-kala a cikin kansa? Zata so kwarai ace zai san da hakan don duk rashin hankalinta ta san dai bai dace a wannan yanayin ta bude baki tace masa ta taba tone asiri akansa ba, dama yaya lafiyar kura balle..? Yaushe ya daina nuna alamun zargin ta yake akan abinda bata sanshi ba.
Tunaninta ya ganganra kan abinda ya gaya mata, bai taba sani iyayensa ba, kenan haka yayi rayuwarsa tun daga lokacin yarinta har yanzu babu wanda zai taba kalla ya kira danginsa? Haka ya taso babu mai uwa mai gaya masa daidai da akasinsa? Babu mai sanin kukansa idan abubuwa sun cakuΙe a rayuwarsa? ta tabbata akwai Ιimbin labari akan rayuwarsa ta yadda ya kawo har zuwa yanzu amma sai ta kasa kara tambayarsa komai saboda wani irin abu yake zanawa a hankali cikin hannunta, wani irin abu mai wargaza dukkan tunanin data fara…
STORY CONTINUES BELOW
“Me kike sawa hannunki?” Muryarsa a hankali ta sake fitowa cikin tambayar da bata taba tsammaninta ba, sai ta dago da idanunta ta kalle shi da Ιan sauri.
“Babu komai… Me yayi?”
“Ba kya aiki da yawa a gida?” Shima yayi mata tambayar maimakon amsa. Sai ta girgiza kanta, hancinta ya gogu da saman kafaΙarsa.
“Ina aiki sosai mana.”
“Kamar me?”
“Ζebo ruwa, shara, wanke-wanke, wanki, girki da daka, sau da yawa har geron kunu ma ina sirfawa Baddo a turmi.”
“Ke Ιin?”
Ta daga kanta alamun tabbatarwa, sannan muryarta ta fito free, alamun ta fara sakewa da yanayin nasu.
“Sosai ma, ka zata bani da Ζarfi? To har bokitin ruwa nata taba kaiwa saman bene kuma akaina.”
Madaki yayi murmushi mai dan fadi, yana mamakin irin innocense Ιinta, kafin a hankali yace.
“May be zan gwada Ζarfin naki kenan watarana.”6
Bata fahimci komai a maganar tasa ba saboda haka ta gyaΙa kanta tace.
“Allah ya kaimu, ka fada min me hannun nawa yayi?”
Ya kifta idanunsa yana kallon idanunta, wannan waΙannan idanun da suka bashi dukkan wahalar da suka ga dama a kwanakin baya wajen mannewa a tunaninsa.
“Yana da laushi sosai, so soft!”
Sai tayi wani guntun murmushi sannan tayi saurin sadda ganinta Ζasa ba tare da tace komai ba. A lokacin ne kuma Madaki yayi ΖoΖarin daurewa raΙaΙin ciwon dake harbawa a gefen kafaΙarsa, ya ture komai a cikin kansa ya sunkuyo daidai kanta ya lalubi saman kunnenta. Jidda taji saukar Ιumin numfashinsa a fuskarta yayin da tunaninta yayi cilli can wata duniya daban! RuΙani da kasala suka Ζara mamaye jikinta sannan wani abu kamar kunya ya lullubeta tun daga Ζasa har sama… Sautin bugun zuciyarta na fita da wani irin Ζarfi data tabbata ko na tsaye a gefen gadon zai ji shi balle shi kuma…
A hankali ya raΙa a cikin kunnen nata tambayar data kara girgiza duniyarta fiye da halin da take ciki.
“Kin shirya zuwa Kiyari jibi?”
***
Kiyari, Expressway.
09:05Pm.
Motar gudu take cikin wani irin saurin da kyakkyawar macen dake zaune a baya take ganin kamar ta buΙe baki tace da direban yafi haka ma, ko kuma tasa hannu ta kara tunkuΙa su don su isa ga cikin garin da wuri har zuwa cikin masarauta.
Wayar dake yashe akan cinyarta tayi kara cikin mode Ιin vibration wanda ya shiga gurzawa akan stones din hadaΙΙen lace Ιin dake jikinta, ta dago ta ta kara a kunnenta ba tare da ta damu da maida hankali kan sunan mai kiran ba don ta riga ta san waye.
“Mama mun yini lafiya?”
“Lafiya kalau.” Daga cikin wayar muryar wata dattijuwar mace ta amsa.
“Kina ina ne Nadiya?” Matar ta sake tambaya.
“Ina hanya, mun sauka daga jirgi a kano dazu, yanzu haka mun kusa Ζarasawa cikin gari.”
Kai tsaye itama Nadiyan muryarta ta fito tana kallon kyakkyawar Ζ΄arta fara tas! Dake bacci akan cinyarta, Ta riga ta san abinda zai biyo baya kenan dama, tun a safiyar yau data wayi gari da labarin rasuwar Ιanuwanta, Umar, da kuma rashin lafiyar da akace mahaifiyarta na ciki.
Kai tsaye ta shaidawa mijin nata Abdallah bayanin kiran wayar da Ζ΄aruwarta Safina tayi mata, amma budar bakinsa bayan yace Allah ya jikansa, cewa yayi ta jira zuwa jibi idan anyi luncheon din sabon branch na kamfanin sai da motocinsa anan cikin Abujan da suke sai su taho tare. Kuma hakan ba wai abin mamaki bane dama a yanayin zamansu, don tun daga zamanin amarcinta take shan takaici kala-kala na halin Abdallah, tun a wancan lokacin kuma take dana sanin auren nasa, dana sanin burin data dorawa kanta na cewar sai kyakkyawan saurayi mai aji da kudi sannan zata aura, kyakkyawan da fuskarsa zata dace da tata, wanda in sunyi kwalliya sun dauki hoto zai zaga dukkan social media musamman ace kuma da Ζ΄aΖ΄ansu a gefe..
STORY CONTINUES BELOW
Kuma sai gashi ta sami abinda take so Ιin don Abdallah dan wani shahararren minister ne da mahaifiyarsa ta kasance Shuwa-Arab, daga lokacin da yaga hotonta a social media yasa aka nemo masa contact dinta, sai ta tattara dukkan wadanda take kulawa tasa a shara, kuma da asiri da kissa da komai ita da mahaifiyarta Fulani suka samu suka ribace shi har akayi auren, wanda ko shekara guda ba’ayi ba ta fahimci cewa ta tafka babban kuskure.
Don Abdallah irin Ζ΄aΖ΄an masu kudin nan ne da aure bai taba hana su dukkan wani shashanci da watsewar da suka tashi dashi a rayuwarsu ba, ga babban kalubalen da take fuskanta na mahaifiyarsa, irin Shuwa-Arab din nan ne masu ci da asiri suma, don kamar yadda ta mallake mahaifinsa sai abinda tace to haka Ζ΄aΖ΄an ta ma da matayensu babu mai tsallaka umarninta, haka take yi tun akan matan yayyen Abdallah har zuwa ita Ιin da ta shigo, duk abinda ake ciki a gidan wani sai ta sani, hatta sirrin auratayya wannan a wajensu ba komai bane su kwashe su gaya mata, ga sauran Ζannensa mata basu da tarbiyya balle mutunci. Haka ita da kowacce a cikin matan nan ke fama dasu tunda sun rufe idonsu sunce sun ji sun gani kudi da kyau suke muradi.
A fuska dai da zahiri zaka gansu tsaf cikin kogin daula, musamman ace sun dauki hoto sun saka a yanar gizo, yanzu zaka ga tarin masu sharhi da fatan samun irin rayuwarsu, amma a cikin zuciya dubunnan talakawa da masu rufin asiri da yawa sun fi su samun nutsuwa da kuma kwaciyar hankali.
To a yanzu ma abinda ke faruwa kenan, ta tabbata Abdallan ne yaje ya gaya mata cewar ta taho ba tare da ta saurare shi ba.
“Kin san cewa Ζ΄an jaridu da masu mujallu, zasu wajen buΙe kamfanin nan kuma za’a so ganin hotonku ke da Hidaya amma shine kika tsallake kafa kika tafi bayan yace miki ki zauna zaku je tare?”
Mahaifiyar tasa ta fada cikin banbamin faΙa.
Nadiya ta hade siraran girarta waje guda.
“Mama danuwana ne fa ya mutu? Har sai in zauna jiran sai an bude wani kamfani?”
“To don ya mutu an kawo gawar tasa Ζasar ne? Ba sai ki jira sai an kawo gawar tasa ba kafin nan kuma kun gama abinda zaku yi?”
BaΖin ciki ya cike har wuyanta, ta ma rasa me zata ce akan hakan sai kawai ta canja zancen da cewar.
“Mahaifiyata ma bata da lafiya ai.”
“Ko a gadon asibiti take yi wannan zancen mijinki ne muke yi Nadiya, bai baki izini ki fita ba kin sa kafa ki fice, alhali in kin jira shi sai jibin babu abinda zai faru?”
“Akan wani kamfani Mama zan zauna uwata bata da lafiya banje na ganta ba? Idan itama ta mutu kuma fa? Shikenan sai in…”
“Eh ai kinyi kauri dole ki zaΙa kuma ki aibata masa sana’a Nadiya…” Ta katse ta.
“… kinci kin koshi kina ganin kin fara ajiye magada ko? To bari kiji in gaya miki kar nake kallon kowa wallahi, ba’a min wata muna-muna wallahi, kuma dama na dade fahimtar mugun manufarki ke da uwar taki, kyale ku kawai nake yi amma duk shirinku a banza ne, ba zan bari ina ji ina gani ki halaka min Ιa ba, don haka in kinje kar ki dawo, kije ki zauna da mahaifiyar taki zan saka ya aiko miki da takardarki kowa ya huta.”
Dib! Kiran ya katse, wata Ζatuwa Ζwalla mai dumi ta gangaro kan fuskar Nadiya, ta gangaro ta ziraro har ta sauka akan yala-yalan gashi Ζ΄arta, bata san kuma kwallar ta mecece ba don ta san in da zata kira Abdallan da ta tabbata yana kusa da ita a yanzu ta bashi hakuri, tsaf zaiyi kokarin shawo kan mahaifiyar tasa ko don Hidaya Ζ΄arsu don yana mutukar son yarinyar sosai, amma ba zata yin ba, zata barsu su aiko da tarkardar sakin, watakila lokaci yayi da ya kamata ta saukewa kanta wannan Ζaddararren auren itama ta huta kamar yadda ta faΙa.
Basu isa cikin masarauta ba sai wajen Ζarfe tara sosai, a lokacin motocin masarautar sakkwato sun cika fal a harabar ajiyar motocin gidan alamun kanwarta Aisha da tayi aure a can ta iso kenan, a lokaci taji wani abu kamar kunya da takiaici sun ratsa zuciyarta, haka ita zata shiga ziΖau! Daga ita sai Ζ΄ar ta, don ko a baya ma babu wani daga dangin Abdallah da ya taba tako Ζafarsa mahaifarta balle a yanzu.
STORY CONTINUES BELOW
Kafin ta isa bangaren Fulanin dogarawa sun rufe bayanta ana tayi mata bangajiya da kuma gaisuwar mutuwar, wani abu da ya Ιan wanke duhun zuciyarta ta dan ji ta sakayau, aka tuna mata cewa itama mutum ce mai daraja ba a wani waje da ko mota tafi ta daraja ba.
Ta isa cikin Ιangaren inda ya fara cika da mutane daban-daban wanda yawanci duk dangin mahaifiyar tata ne, a falo na uku dangin mijin Aisha ne Ζ΄an sawkwato, a can falo na Ζarshe ne kuma ta tadda makusantan Fulani sosai irin Ζannenta da yayyenta, dukkansu ta gaishe sannan suka yiwa juna gaisuwa da kuma addu’ar nemawa Fulanin sauki, wani ciwo da har yanzu ita Nadiyan bata sanshi ba. Daga nan ta miΖe tayi hanyar Ιakin Ζanwarta Safina, inda akace Aisha ma na can don tayi sallah ta huta, tunda ance ita Fulanin tasha allurorin bacci har yanzu bata farka ba.
Tana bude Ζofar Ιakin, fuskokin Ζ΄anuwanta biyu suka yi mata maraba, sai da ba’a halin farin ciki ba, dukkaninsu sunyi zuru-zuru, Safina ma idanunta a kumbure alamun tasha kuka. Sai kuma ta taso da sauri ta karΙi Hidayan da ta sake komawa bacci a kafaΙunta.
“Sannu da zuwa Adda, ya hanya?” Kusan a tare suka gaishe ta.
Da kyar ta iya amsawa saboda yadda take jin muryarta kamar ta shake sannan suka yiwa junansu ta’aziyya da kuma jajen abinda ya faru.
Kafin ta fito daga wanka a toilet din Safinan an kawo mata katon akwatin kayanta, sannan kuma an wadata su da abincin tarba kala-kala, sai da ta idar daga sallah bayan ta canja kaya ne sannan idonta ya iya kallon Aisha sosai, a lokacin Safinan ta fita don raka wasu kawayenta da suka zo yi mata ta’aziyya.
“Ishsh me ya same ki ne wai? Abinda ya faru ne yasa kika yi wannan ramar ko kuwa? Idanunki sun fada sosai.”
Aisha ta dago ta kalle ta daga kwancen da take sai kuma ta girgiza kanta.
“Babu komai Adda, ba muna waya ba? Na taba gaya miki wani abu ne? I’m fine.”
“I don’t buy that..” cewar Nadiyan.
“Idan a waya ne na yarda, amma banda yanzu da idona suke ganinki, da haka kike? Ko ba kya kallon fuskar ki ne a mudubi? Har baki fa kinyi.”
Sai ta taso ta zauna a gefen gadon ta take kwance ta kamo hannunta tace.
“Ishsh, ni fa Ζ΄aruwarki ce, yayarki guda daya a duniya, akwai wanda ya kamata ki gayawa damuwarki ne bayan ni? Bayan yanzu kina ganin Mama ma a kwance take.”
A lokacin sai duk wata dauriya da Aishan ke yi ta kwance, tulin abubuwan da ta dade tana dannewa a kirjinta suka wargaje, sai kawai ta fashe da kuka, wani irin kuka dake tasowa tun daga kasan zuciyarta.
“Adda dlwallahi bana jin daΙin auren nan, har dukana yake…”
“Subhanallah, shi Muhammad din?”
Cikin kuka Aisha ta sake daga kanta.
“Wallahi Adda tunda aka kai ni ban taba jin wani dadi ba, duk abinda nayi sai ya hantare ni yace wai siyar masa dani akayi saboda iyayena na son kudi, har su Daddy zaginsu yake, daga baya kuma sai ya fara dukana, Adda wallahi har fin Ζarfi yake min.”
“Innalillahi wa’inna ilahir raji’un…” Cewar Nadiyan.
Me ke faruwa a rayuwarsu ne? Me suka jawowa kansu ne? Wannan wane irin bala’i ne? Ace ita bata yi sa’ar aure ba sannan ga Aisha ma? Ba gwara ma nata an Ιauki shekaru ba? Amma Aisha duka-duka watanta nawa?
“Ζ³anuwansa suna da kirki, danginsa gabadaya suna mutunta ni, shine kawai daban Adda, kuma wallahi babu wanda zan tunkara a masarautar nan in gaya masa ya yarda. Munyi maganar da Mama kwanaki sai tace min wai zamu je wajen wani malami komai zai wuce, ni kuma bana son harkar bin wasu malamai shi yasa na daina gaya mata. Na daina gayawa kowa.”
Kafin Nadiya tayi magana, Hidaya ta tashi cikin Ιan kuka tana mutstsika idonta, don haka Aishan tayi saurin miΖewa ta Ιauke ta. Tana buΙe ido kuwa tace fitsari zata yi don haka tayi bandaki da ita, Nadiya tabi bayansu da kallo wani abu na Ζullewa a cikin Ζirjinta. A lokacin ne kofar Ιakin ta bude, Safina ta dawo. Ta shigo ta zauna a gefen gadon tana fadin.
“Adda baki ci abincin ba, kun sha hanya fa.”
Ta girgiza mata kai.
“Bar abincin nan kawai Safina, gaya min taΖamaimai me ya sami Mama wai?”
Safina ta dan yi ajiyar zuciya kafin tace.
“Tun jiya da daddare ne da aka kawo gawar Jakadiya Babba cewar sunyi hatsari wa ita da Sani direba a mota, ance dai Sanin bai mutu ba amma wallahi Adda ita baki ganta ba, gawar duk ta daddatse haka, ni ban ma iya kallonta sosai ba bayan na dawo, saboda na fita ne, to shigowata ne su Jakadiyan soro suke gaya min wai Mama tana ta wasu surutai bayan taga gawar, tana rantsewa wai ba Jakadiyan bace ita ta san Jakadiya bata mutu ba.
Da na shiga na same ta an riΖe ta tana ta rantse-rantsen cewa wai wallahi Yaya Farouq ma bai mutu ba haka ma jakadiyan, wai ita ta san tana nasara a komai kuma malamanta basu taΙa nuna mata wannan ranar ba. Adda maganganun da take fada wallahi ba zaki ce a hankalinta take ba, ina ta rokonta tayi shiru amma bata daina ba. Daga baya sai ta sarΖe a maganarta shikenan ta fara tari, sai kuma jini ya shiga fitowa, da yawa tana ta zubar dashi akan carpet.
Yaya Saif ne ya kira likita yazo wajen Ιayan dare ya mata allurar bacci don yace shi bai san me ya same ta ba. Dazu da safe aka binne gawar Jakadiyan, sannan wasu likitocin kuma suka Ζara zuwa suja duba Maman, ni dai ban tabbatar ba amma naji kamar Ιayan yace wai kwaΖwarta ce ta dan taΙu, shi yasa hankalina ya kara tashi, don ban san ya za’ayi jibi ba in aka kawo gawar Yaya Farouk.”
“Mama haukacewa tayi fa.”3
Kai tsaye muryar Aisha ta fito daga bayansu a lokacin da Safina ta rufe bakinta.
***
Lagos.
Gidan Mubarak.
10:15Pm.
“Ya Allah! Na manta.”
Cewar Khadija a lokacin da take ΖoΖarin hawowa kan gadon baccinsu bayan ta canja cikin kayan bacci.
“Me ya faru, Mubarak ya tambaya daga kwance yana danna Tab a hannunsa.
“Ban buΙe windon Ιakin su Hanan ba wallahi, tun da safe da zamu je asibiti dana rufe.”
Ta fada tana ΖoΖarin miΖewa, sai yayi saurin kamo hannunta.
“Dawo ki zauna, kin gaji, bari inje.”
Tayi murmushi mai fadi.
“Awwn nagode sosai King, A dawo lafiya.”
Ta faΙa tana komawa da baya ta fada cikin laushin gadon. Mubarak ya ajiye tab Ιinsa yana dariya sannan yayi hanyar kofa, ya fito daga Ιakin ya biyo hanyar korido zuwa wani koridon da zai kaishi ga hanyar Ιakin yaran, har ya wuce Ζofar wani toilet a farko sai kuma yaga Ζofarsa slightly a buΙe, saboda ya dawo da niyyar jawo ta ya rufe a lokacin da maganganun dake fitowa daga cikin suka shiga kunnensa.
“Kar ki damu Naja, ai ni na raina komai yanzu, da ace ma naga yarinyar tun farko me zai sa mu hayo Ζ΄an bindingar nan har a sami wannan akasin?”3
Muryar ta kyalkyale da dariya cikin wayar da take yi sannan tayi magana ta gaba.
“Wallahi Naja, abinda nake shirin yi ko wani Ζaramin shaidan sai ya faΙa tarkona balle kuma wani Madaki, ai ki bari kawai ni naga abinda na gani, don haka dole ne in mallaki gayen nan ko me za’ayi wallahi, wallahi!”3
Muryar Salwa tar! Ta rantse ta kuma rantsewa a cikin kunnen Mubarak!13
***Mubarak yasa hannunsa ya tura Ζofar banΙakin a hankali, katakon Ζofar ya bada wata Ζara ta katako irin Ζiiiii Ιin nan, Ζarar da ta shiga kunnen Salwa tasa ta juyo da wani irin sauri mai haΙe da fargabar data haska tar a cikin idonta.1
A lokaci guda kuwa wayar hannunta ta sulale ta daki dandaryar tiles Ιin banΙakin, ta rikice kuma diririce tana kallon Mubarak Ιin da nasa idon da ke haskawa da wani irin Ιacin ran daya haddasa kalarsu canjawa.1
Tasa hannu ta dafe gefen sink Ιin tana jin kamar zata fadi sai kuma ta sake shi ta shiga takawa baya a hankali tana cigaba da kallonsa haΙe da girgiza kai cikin amsar da ba’a tambayeta ba. Mubarak ya haΙe hannayensa biyu yayin da yake kallonta da idanunsa da a yanzu suka rikiΙe suka kaΙa jazur!
“Wane Madakin kike cewa zaki mallaka?”
“Yaya… Ba wai ni bace, kawai… Kawai tunani nayi…”
“Cewa nayi dan ub*nki wane Madaki kike cewa zaki mallaka?”
Sai da ta zabura saboda yadda Ζarar tsawar daya daka ta karaΙe bangwayen toilet Ιin. Ta cigaba da girgiza kanta hannayenta na rawa, saboda Allah ya sani tunda take a rayuwarta baza ta taba cewa ta taba sanin wannan kalar ta Mubarak ba, a kullum shi wanta ne mai fahimta da kuma yi mata uzuri a lokacin da kowa kr Ζalubalantarta, amma a yanzu fuskarsa tamkar na wani zaki ne dake shirin yunΖurowa ya keta ta…
“Ke kika sa aka harbe shi?”
Wannan karon muryarsa na karkarwa alamun tsananin Ιacin ran da yake son daurewa. Salwa ta cigaba da girgiza kanta tana Ζara yin baya har sai da ta dangana da bangon karshe.
“Wallahi tallahi Yaya Ζawata ce tace…” Sai kuma Ζaryar ma ta ruguje ta rasa me zata kamo ta fada.1
A lokacin ne Khadija ta Ζaraso cikin wani irin sauri hannunta damΖe da da tsakiyar top Ιin data Ιora akan siririyar rigar baccinta, Ζarar tsawar da Mubarak ya daka ce ta fito da ita ba shiri a firgice.
“Me ya faru Daddy? Me nene?…”
Ta tambaya a ruΙe tana kallon yanayin Mubarak Ιin da ita kanta bata taba gani ba tsawon zamansu. Sai kuma ta juya cikin banΙakin ta kalli Salwa da jikinta ke faman faman karkarwa cike da tsananin tsoron dake haskawa a idanunta.
“Wallahi Yaya, wallahi tallahi… Na rantse ka saurare ni, ka tsaya, ka tsaya, ka tsaya kaji…”
Cewar Salwan cikin ihu a lokacin da Mubarak yayo cikin toilet din, wayarta data fadi a kasa ya tsugunna ya Ιauka sannan hannayensa biyu ya Ιalla ta gida biyu da wani irin Ζarfi ta tsakiya.
Har a lokacin Salwan ihu take tana roΖonsa cewa ya tsaya zata masa bayanin komai.
“Mubarak me nene wai? Me tayi? Dan Allah ka saurara tunda tace ka tsaya…”
Mubarak bai saurari Salwan ba balle Khadija, ya Ζarasa ya damΖo hannayenta duka biyu a lokacin da ta Ζara rikicewa ta shiga ΖoΖarin tirjewa tana Ζara roΖonsa amma karfinta da nasa ba daya bane, ya jawo ta yana mai ture Khadija dake tsaye a kofa tana ΖoΖarin riΖe shi gefe sannan ya cigaba da jan ta suka fita daga toilet Ιin.
“Yaya dan girman Allah kayi hakuri, ka tsaya kaji, wallahi ban san shi zasu harba ba…”4
RoΖonsa take yi tana magiya yayin da take juyawa tana kallon Khadija dake bin bayansu kamar mai neman taimako, suka isa har falo kuma anan din ma bai tsaya ba, gadan-gadan ya nufi hanyar Ζofa da ita bayan ya suri wasu tarin muΖullai da suka haΙa har da na motarsa akan dan center table Ιin dake falon.
“Mubarak ina zaka kaita? Fita zaka yi? Ζarfe goma fa ta wuce… Ina zaka je a daren nan…?”
Khadija.
STORY CONTINUES BELOW
“Dan girman Allah Yaya… don darajar Allah ka tsaya, ka saurare ni… Wallahi tallahi ba shi nace su harba ba… Yaya…”
Salwa.
Mubarak ya buΙe Ζofar gidan yana mai cigaba da jan Salwa wadda ke sanye da doguwar riga ta atamfa da kuma Ιaurin baΖin mayafi akanta, yana jin yadda take cigaba da ΖoΖarin tirjewa tana ΖoΖarin zubewa a Ζasa amma yasa dukkan Ζarfinsa ya hana ta, zuciyarsa ta riga ta kai bango kuma idanunsa sun rufe in banda wani baΖin hayaki da baΖin tiriri ba abinda yake gani a idanunsa kuma yake ji a cikin Ζirjinsa.1
Daga shi har ita babu mai takalmi a cikinsu ya buΙe motarsa bayan ya zube sauran muΖullan a Ζasa, Khadija ta biyo su har jikin motar tana Ζara roΖonsa da bashi hakuri akan taΖamaimai abinda bata sani ba, amma bayan ya buΙe gidan gaba ya tura Salwan da ta shiga da Ζyar kallonta kawai itama yayi tasha jinin jikinta musamman da ta tuna kayan dake jikinta, ta koma can kan porch Ιin falon da sauri tana cigaba da kallonsu a rikice, Mubarak ya zagayo ya buΙe motar ya shige yayin da a lokacin Aliyu daya farka ya fito shima, cike da nasa mamakin shima ya tsaya kusa da mahaifiyarsa yana kallon yadda motar ta tashi da wani irin sauri ta nufi gate inda maigadi ke ΖoΖarin buΙewa.
A cikin motar ba abinda ya canja, Salwa magiya take yi tana cigaba da roΖar Mubarak Ιin da baya ko jinta, idanunsa jazur na manne akan titi yayin da huci ke faman fita daga hancinsa, tun tana zaune a kujerar har sai da ta tsugunna a Ζasa tana cewa.
“Yaya don darajar ma’aikin Allah ka saurare ni, wallahi ba shi nace a harba ba, mistake suka yi, nima ba zan taΙa so in yi wani abu da zai taba shi ba, kuma abinda kaji ina cewa ba akansa zanyi ba…”
Ina! Mubarak baya ko jinta, tituna kawai yake ratsawa yana bi ta tsakanin motocin da fitilar danjarsu ke Ζara Ζawata nasa jan idon. Kuma duk tarin magiyar da Salwa ke yi, babu ko Ιigon kwalla a idanunta, tunaninta ne kawai ya rikice amma karfin ruΙanin nata bai kai ga fitar hawaye ba sai a lokacin da ta ji tayoyin motar sun ja birki alamun an iso inda Ζaddarar da take shirin fuskanta take, a lokacin da idanun ta suka juya da wani irin sauri yayin da ta dafo saman dashboard Ιin gabanta ta Ιago daga tsugunnen da take, a lokacin da duk da Ζarancin haske a harabar wajen idanun nata suka gane mata kalar fentin ginin dake gabansu.
Yellow.
Blue.
Green.
Police station!5
***
09:00 AM
VoilΓ‘ Private Hosital, No 1388 Gyari Park.
Jidda ta murΙa handle Ιin Ζofar Ιakin a hankali da niyyar shiga, a hannunta wannan basket Ιin ne mai kyau da su Khadija suka kawo da kwanuka a ciki. Jiya duk da ta saΙa murafan sai da wasu daga cikin abincin suka Ιan canja Ζamshi saboda haka yanzu ta tattara su ta kaiwa masu gadi a can bakin gate, suna ta godiya kuwa suka karba, itama har sai da yawunta ya tsinke a lokacin da suke juye wani farfesun nama cikin kwanukansu, amma ya zata yi ne, Madaki ya riga yace shi ba zai ci ba don haka kawai itama sai taji Ιan shakkar ci tunda dama tun farko ba ita aka kawowa ba.2
A lokacin da ta fita kuma baya Ιakin, don tun Ζarfe takwas da Ζ΄an mintuna da aka gama masa dressing Ιin safe, yabi Nurses din da cewar zai je wajen likitan da file Ιin da ke hannunsa don su tattauna wani abun, wani abun da take ganin kamar akan zancen tafiya Kiyari ne kamar yadda ya faΙa mata jiya, ya faΙa a kunnenta…
Wani abu da har yanzu ta kasa ganewa kenan, ta kasa gane yana nufin zai maida ita ne gaba Ιaya in sun je a can zai rabu da ita shi ya dawo ko kuwa? Don da alama ya gama a yanzu ya kammala zargin da yake akanta, kuma duk da ta san dai saboda rasuwar yayi zancen tafiyar amma bata sani ba ko zaiyi amfani da damar ne ya jefi tsuntsu biyu da dutse Ιaya.
STORY CONTINUES BELOW
Taso tayi masa wannan tambayar Tun jiya amma Ζiri-Ζiri ta kasa, bata taΙa sanin cewa a duniya akwai wani abu da zai sa bakinta ya mutu ba sai jiyan, wannan lokacin da babu abinda take iya ji a hancinta sai Ζamshinsa, wani Ζamshin turare mai sanyi daya haΙu dana fatarsa ya cika kanta, sannan Ιumin jikinsa kuma kusan gabaΙaya ya zagaye nata saboda yadda ya sunkuyo da fuskarsa daidai kunnenta, tata fuskar ta shige cikin wuyansa.3
Bata taΙa jin wani abu irin haka ba, zuciyarta ta rabu gida biyu a lokacin, tana jin kamar ta kara matsawa ta shige jikin nasa tana kuma jin kamar ta janye ta bar gadon ma bakiΙaya, data rasa me zata yi sai kawai ta haΙe nata jikin waje Ιaya, ta dunΖule hannunta akan Ζirjinta, na Ζafa kuma ta dunΖule su a cikin tafin Ζafar ta. Kuma babu wanda ya sake magana a cikinsu har sanda ya janye fuskarsa ba tare da ya sake tambayar amsarta ba, kuma a haka daren ya wanzu zuwa sanda bacci ya Ιauke su, hannunsa riΖe da nata cikin bargon nan har aka Ζwalla kiran sallar asuba…
“Zuwa nan da 12 insha Allah komai zai zama ready, bari in tafi da waΙannan.”
Muryar wannan Nurse Ιin Namiji ta shiga kunnen Jidda a lokacin da ta tura Ζofar Ιakin ta shiga ciki. Yana tsaye a gefen gadon rike da wasu takardu da kuma dan tray Ιin dake Ιauke da magunguna yayin da Madakin ke zaune daga gefe ya zuro Ζafafunsa Ζasa da alamun magana suke yi har yanzu, don Nurse Ιin shi ya raka shi gurin likitan da yace za shi Ιazu.
“Bari inje, zuwa 12 Ιin idan ya shigo I’ll contact you as soon as possible insha Allah.”
Cewar Nurse Ιin yana mai tahowa wajen Ζofar inda Jiddan ke tsaye, sai da yazo dab da ita sannan tace ‘Sannu da aiki’ ya amsa da ‘Yawwa’ har da Ιan guntun murmushi sannan ya fita.
Tana juyowa idanunta suka haΙe dana Madaki dake kallonta daga inda yake zaune, Ya ilahy! Idanun nasa a lumshe suke har yanzu kamar maganin baccin nan bai gama sakinsa ba, babu shiri wani abu ya zarce maΖogwaronta a lokacin da ya Ιago hannunsa ya miΖo saitinta alamun tazo.
Babu yadda zata yi, in tace ba zata ba ma zuciyarta ba zata barta ba, saboda haka ta Ζarasa a hankali basket Ιin nan riΖe a hannunta, ai kuwa kamar lokutan baya tana zuwa daidai tsawon hannun nasa ya naΙe yatsunsu waje daya sannan ya jawo ta dab dashi sosai.
“Kin tashi lafiya?”
Sun gaisa fa, Ιazu kafin ya fita, sakewa zasu yi? Ta ayyana hakan a zuciyarta kuma maimakon ta amsa sai itama tace.
“Yaya jikin naka?”
“Alhmdlilah, da sauΖi sosai.”
A can Ζasar maΖoshinsa zancen ya fito, Adam’s apple Ιin sa na motsawa sama da Ζasa a hankali, sai ya kalli basket Ιin hannunta sannan yace.
“Har wanke plates Ιin suka miki?”
Ta girgiza kanta, haka yasa yaji ratsawar numfashinta akan fuskarsa.
“A’a ni na wanke da kaina, a wani fanfo anan baya.”
Fanfon dai da aka hana ta alwala jiya, kuma tana sane yau ma ta koma, da zummar duk wanda ya mata magana tace ai kuΙi suka biya ba kyauta suke zaune a asibitin ba kuma ruwa ma ai dukiyar Manzon Allah ce don haka fanfon bana kowa bane. Sai gashi har ta gama ta fito Allah bai kawo mai tanka mata ba.2
Madaki ya gyada kansa yana motsa yatsunsa cikin nata kamar mai son Ιauko wani abun kafin ya sake magana.
“Me zamu ci kenan mu?”
Tamabayar ta rungume zuciyarta amma sai tayi ΖoΖarin ture ta, ta sake haΙiye yawu a bakinta sannan ba tare da ta Ιago ta kalle shi ba tace.
“Idan ka kira Baba Saminun ya kaini gida sai in dafo maka duk abinda kake so qarfin.”
STORY CONTINUES BELOW
Sai ya girgiza kansa shima.
“Ba inda zaki koma ki dawo, tare zamu tafi, sunce zuwa 12 likitan da zai sallamenin zai Ζaraso.”
Sai a lokacin ta Ιago ta kalle shi.
“Da gaske? Baka warke ba fa, Kwana biyu kawai?”
“Na warke mana, idan ban warke ba ta yaya zamu tafi Kiyari gobe?”
Jidda ta cigaba da daurewa kallonsa mamaki na sauka akan fuskarta, dama abinda yaje yi wajen likitan kenan? Takura musu yayi su sallame shi don suyi tafiyar gobe? Ita fa har ga Allah bata gama tsaida zuciyarta akan tafiyar nan ba, tana masifar son ganin su Baddo amma kuma ta san tafiyarta baya nufin dawowarta, shi yasa take so sai ta gama tsaida zuciyarta waje Ιaya tukunna, sai ta gama sallama da duk abubuwan data san ta fara sabawa dasu.1
“Saboda zuwa Kiyari zamu tafi baka gama warkewa ba?”
“Na gaya miki na warke.”
Jidda ta sake girgiza kanta.
“Baka warke ba, aiki fa aka maka a wajen, kuma kwana biyu kenan kawai.”
“Kin iya naushi?”3
“Me?”
Tambayar tazo mata babu zato, don ba amsar da tayi tsammani bace.
“Ki gwada, ki naushi ciwon yanzu, zan tabbatar miki na warke.”
Madaki ya faΙi hakan ne kawai don tayi tunanin cewa ya fara warkewa ba wai don shi kansa ya yarda da Ζarin jikinsa ba, sai dai da gaske bai san halin Jidda ba, don kallonsa tayi na wasu Ζ΄an sakanni kafin ta sunkuya ta ajiye basket Ιin hannunta, kuma Ιagowar da zata yi kawai yaga hannunta na dama a dunΖule alamun da gaske naushi nasa zata yi, don haka a lokaci guda ya saki Ιaya hannun nata ya kamo shi sannan ya jawo ta jikinsa gabaΙaya.6
“I’m just joking, ya ilahi ke baki san wasa ba?”5
Ya faΙa a daidai fuskarta yayin da ya zaunar da ita akan cinyarsa, Jidda bata ce komai ba don da gaske tayi niyyar dukan nasa, ko bada karfi ba idan dai ta fama ciwon watakila ba lallai a sallame shi yau Ιin ba.2
“Ko ciwon nan zai dawo sabo, we’re leaving this place yau, saboda haka ni da ke kawai zaki Ζara bari da jinya.”
Ya faΙa a hankali daidai gefen fuskar tata, Ζamshin toothpaste Ιin bakinsa na busawa akan fatarta, a lokaci guda jikinta ya Ιauki dumi kamar an Ζyasta ashana daga tafin Ζafarta, kuma kafin tayi wani yunΖuri Madaki ya manna leΙΙensa akan kumatunta na gefensa sannan muryarsa ta fito akan fatarta…3
“Kin iya dressing ai ko…?”
A lokaci guda wani abu tamkar wuta ya sake tafiya zuwa Ζarshen kowacce jijiya ta jikin Jidda, yana Ζara rura Ιumin da jikinta ke Ιauka, ita bata san wannan abin ba, bashi ma da suna a ΖwaΖwalwarta balle har ta iya fassara ma’anarsa.
“… Sun ce ko na tafi dole sai ana yiwa wajen dressing..”
Ya Ζara faΙa leΙΙensa na sliding akan fatarta, a wannan lokacin duk yadda Jidda ta kai ga dunΖule yatsun Ζafarta sai da duk wata nutsuwarta ta wargaje, ta kasa cigaba da daurewa komai saboda haka bata san sanda ta juya da wani irin sauri ta cusa kanta a gefen wuyansa ba cikin neman sauΖi, hannyenta duka biyu na dunΖule akan Ζirjinsa…2
A lokacin ne kuma Ζofar Ιakin ta buΙe, waΙannan Nurses Ιin na lab suka shigo har su biyu, Ιauke da kayan test Ιin da zasu yiwa Madakin don a fitar da result na Ζarshe kafin zuwan likitan da zai sallame shi.3
Kalaman ‘Booked for Honeymoon’ suka tabbata a zuciyar Ιaya daga cikinsu.1
***
“Why are you not picking my calls? Tun safe nake kiranka.”
STORY CONTINUES BELOW
Madaki ya faΙa a cikin wayar da yake yi tsaye daga wata baranda a harabar asibitin, yayin da yake hango motarsa a can gaba, inda Jidda ke ta ΖoΖarin harhaΙa kayan flask Ιin nan daga baya yayin da Baba Saminun da zai yi driving Ιin su ke tsaye a waje daga bakin Ζofar zaman direba. An riga an sallame shi tun dazu bayan likitocin sun kafa masa wasu Ζ΄an sharuΙa da shi bai gansu a matsayin Ζalubale ba kamar yadda suka nuna a farko sanda ya nemi a sallame shin.
A yanzu shi suke jira kawai su tafi amma haka kurum sai yaji kamar baya son fita daga asibitin ba tare da ya samu Mubarak ba, don tun safe yake kiransa a waya amma bata ko shiga balle har yasa ran za’a Ιauka. Don haka dole ya tashi Habibu a tsaye wanda yake office yayi roaming file Ιin Mubarak Ιin na aiki a computer office Ιin sannan aka samo nambar matarsa Khadija.
Wadda itama bayan ta Ιauka, da kyar ta iya haΙa shi da Mubarak Ιin bayan ta gama inda-indar da bai fahimta ba.
“I’m sorry wayar tana kashe ne, yaya jikin naka?” Muryar Mubarak Ιin ta amsa daga cikin wayar.
Madaki ya Ιan haΙe girarsa alamun nazari kaΙan saboda jinsa da yayi kamar mara lafiya.
“An sallame ni, kai kuma me ya same ka?”
“Kuma ka tabbata zaka iya tafiyar nan a haka?” Mubarak Ιin ya tambaya shima, don ya riga ya san dalilin da yasa aka sallame shin.
“Zan Ζokarta insha Allah don dole ne inje, and why are you not here? Yau Lahadi fa? For God’s sake we should fight this together in kaga da yadda suka yi discharging Ιina.”
(… Me yasa baka shigo ba? Yau lahadi fa? Tare ya kamata ace munyi fafutukar nan, in kaga da yadda suka sallame ni.)2
Daga tsallaken Mubarak ya cije leΙΙensa na Ζasa da Ζarfi, ya cusa yatsunsa cikin gashinta har zuwa Ζeya sannan ya sunkuya ba tare da ya cire hannun ba, Allah ya sani da kyar ya karΙi wayar a yanzu da Khadija ta kawo masa, sai da ta nuna masa fuskar screen Ιin tare da lokacin kiran dake tafiya akai sannan a fili tace ‘Madaki ne ke son magana da kai..’ don haka bashi da zaΙi dole ya karΙa Ιin.
Amma har ga Allah bai so fuskantarsa a yau ba, musamman wannan lokacin da ko rana bata gama buΙewa ba, awanni basu shuΙe ba daga sanda ya riga yaji wani abu daya gigiza zuciyarsa fiye da duk wani hali daya taΙa shiga a rayuwarsa, don ko a lokacin da iyayensa suka rasu bai wani gama mallakar hankalinsa sosai ba balle ace yaji zafin da yafi haka.
Madaki abokinsa ne da ya dade da juyewa ya zama Ιan uwa, ya taimake shi fiye da duk wani taimako daya da wani Ιan adam ya taΙa yi masa a duniyar nan, ubangiji ya Ζaddara samun duk wata darajarsa a duniya ne ta silar Madaki, babu wani abu koda makamancin allura ne da zai iya warewa a cikin dukiya da nasararsa yace wai babu sunan Madaki a silar samunsa, komai da ya samu ta hanyarsa ne, komai da ya zama ta dalilinsa ne, wani mutum ne shi da yake ganin inda ana iya Ιora wani a gurbin iyaye tsaf zai iya cike wannan gurbin nasa da Ibrahim Madaki.
Amma ace wai an wayi gari saboda wani shashancin banza da shirmen mahaukaciyar kwakwalwar Salwa ta sanya an harbe shi, harbi da bindiga wanda da yayi kuskuren wucewa gefen kafaΙarsa da shikenan yanzu ta kashe shi saboda wani mahaukacin hasashenta na ganin cewa zata mallake shi, A tunaninta yau ko ita tafi kowacce mace hankali a duniyar nan zai taΙa bari Madaki ya aureta ne? Wato ya Ζare rayuwarsa a ΖarΖashin su bai amfani wasu da komai ba kenan saboda su kaΙai ne mutane…3
Ya riga ya rantse ya kuma rantsewa da Allah sai ya hukunta ta daidai gwargwadon yadda ba zata sake kwatanta irin wannan tunanin akan wani ba nan gaba, haka ya faΙa a lokacin daya shigar da ita cikin police station din nan tana magiya tana bashi hakuri amma bai ko saurare ta ba yace da Ζ΄an sandan so yake a tuhume ta saboda tayi ΖoΖarin kashe wani, so yake ta faΙa musu gaskiya akan duk abubuwan da ta daΙe tana shiryawa in yaso ko karyata suka yi daga baya ya biya a kaita asibiti.
STORY CONTINUES BELOW
Ya dade yana mata uziri, ya daΙe yana goyon bayanta akan abubuwa da dama, kallonta yake a kodayaushe da wannan tausayin na cewar bata taΙa sanin Ιumin mahaifiya ba don a sanadiyar haihuwarta ta rasu, yana tausayin wannan kewar rashin uwar data taso dashi shi yasa bai taba barin zuciyarta taga aibunta ba, amma a yanzu komai ya buΙe akan idanunsa, wancan tunanin nasa akanta ya ruguje, kuma a karo na farko ya yarda da abinda yayarsu ke yawan gaya masa cewar ‘Salwa bata da hankali Mubarak, Ina kokwanton idan da imani ma a kasan zuciyarta..’
A yanzu zuciyarsa ta yarda da hakan, don kuwa babu wani mai imanin da zai hallaka wani don cikar burinsa kaΙai, shi yasa ya rantse ya kuma rantsewa cewar sai ya hukunta ta da wani hukunci da duk yadda zuciyarta ta kai ga ΖeΖashewa sai tayi laushin da zata fahimci kuskurenta Ζiri-Ζiri.
Don haka a yanzu fama kawai yake da kansa na irin kunyar Madakin da zai Ιauka duk ranar da ya fahimci abinda ke faruwa, da kuma kunyar Ζ΄ar talikai yarinyar da bata ji ba bata gani ba. Ya san tun a ranar Madaki zai iya fahimtar cewa yana zargin yarinyar nan don ko daga yadda ya amsa gaisuwarta ba kamar yadda ya dace bane a yadda yake son ganin nata a baya, amma da yake shi yafi adalci da daurewa zuciya sai bai ce komai ba, kuma bai nuna ba har a yanzun da ya kira yake cigiyarsa.
Ba tare da ya Ιago daga sunkuyawar da yayi ba, Muryarsa ta fito a hankali tana shiga cikin wayar.
“Wallahi bana jin daΙi ne, kuma ma dai wani abu ne ya taso min unexpected.”
Madaki ya kaΙa kansa.
“To Allah ya warware mana, but gaskiya we have to meet kafin goben don jirgin Ζarfe takwas nayi booking, Ina son in sami jana’izar ne tunda Saifudeen yace min wajen 11 ake saka ran kai shi, and also there’s something we need to talk about. (… akwai abinda zamu tattauna.)”
Mubarak ya Ιago da kansa a lokacin yana kallon Khadija data shigo da wani tray na kayan breakfast Ιin da da bai bata damar kawowa ba tun Ιazu.
“Insha Allah Mdee, zan shigo wajen yamma.”
“Ka nemi Nasiru ku taho tare, akwai takardun da zan bashi don watakila zuwa wednesday Jack na HRS zai iya shigowa ya karΙa, tunda kaga kaima may be zuwa wednesday Ιin zaka shigo.”
“Insha Allah.”
Mubarak Ιin ya amsa yana karΙar plate Ιin soyayyen Ζwai da chips wanda Khadija ke miΖo masa.
A Ιangaren Madaki kuwa yana sauke wayar, idonsa ya sake kaiwa kan Jidda wadda ta fito daga motar a yanzu ta tafi kan wata baranda dake gefe, inda wata mata ke ta fama da wasu Ζananan yaranta, akwai babba da bai fi shekaru uku ba sai kuma Ζ΄an biyu mace da namiji dake ta faman kuka yayin da take ΖoΖarin haΙa musu abincinsu, babban kansa bashi da wayo don Ζannen nasa na kuka amma yana kara jan mayafin Maman alamun shima da abinda yake so. Macen ce riΖe a hannun Jidda sai jijjiga ta take yi tana busa iska kaΙan a kunnenta yayin da Maman ke jijjiga Ιayan tana kuma cigaba da haΙa musu abincin.
A lokaci guda yaji kamar bugun zuciyarsa ya Ιan Ιauke kaΙan sannan kamar iska ta Ιauke a Ζirjinsa, bai taba ganin mace kamar ta da bata dauki kanta komai ba irin Jidda, don daga yadda take jijjiga yarinyar tana kuma kokarin yiwa babban magana na nesa zai rantse cewar ita kanwar matar ce tare suka zo ba wai taimaka mata kaΙai ta tsaya yi ba.
Ba zancen aiki kaΙai yake son yiwa Mubarak a yau ba, har da zancenta, yana so ya gaya masa cewar ya fahimci kyawawan halin yarin yar nan kuma zuciyarsa ta ture dukkan wani zargin da yake akanta, A yanzu gani yake kowacce irin Ζaddara ce ta haΙa shi da ita mai kyau ce don baya tunanin inda ba’ayi hakan ba a duk sanda ya tashi yin aure a rayuwarsa zai iya haduwa da mace mai saukin kai da tsaftatacciyar zuciya irinta, komai da take yi a rayuwarta hakika ne daga zuciyarta, bata da riΖo ko kaΙan balle kuma mugunta.
STORY CONTINUES BELOW
A Ιan zaman da yayi da ita wannan halin nata shi ya canja kaso mafi yawa na tunanin da yake dashi akanta ba wai bincikensa ba, kuma hakan ne a yanzu ya haddasa wani abu kamar Ζaunarta a zuciyarsa, tunda dama zuciyar fanko ce bata taΙa sanin wani abu makamancin haka ba, a kullum yana danne dukan wani emotion da feelings Ιinsa ne a Ζasan ciwonsa, yana gayawa zuciyarsa dake da rauni cewar ba zai iya raba ta da kowa ba, tasa ce shi kaΙai daga shi sai ciwon nasa.
Amma a yanzu gani yake kamar ma bashi da control da zuciyar sai iya inda ya rage Jidda bata mamaye da kyawawan halayenta ba wanda dashi yake son cimma burinsa na son canja duniyarta itama ya koya mata wata sabuwar rayuwa da tafi wadda su duka biyun suka taso a ciki, so yake ya inganta zamansu, ya samar da wani farin ciki a zuciyoyinsu ta yadda ko da ciwonsa bai bashi isashiyar dama ba aΖalla zai san cewa bayan ibada, bai Ζare rayuwarsa aiki kawai ba.
Kallonta yake tana ta jijjiga Babyn wadda a yanzu tayi shiru alamun ta haΖora, daga zaune a kujerun gefe kuma Maman na bawa Ιaya namijin abinci, a Ιazu ba don shigowar Nurses Ιin nan ba, yaso aiwatar da wani abun da zai fara fahimtar da ita manufarsa akanta, zai sa ta fahimci cewa a yanzu tana daya daga cikin abubuwa mafi muhimmanci a rayuwarsa kuma zai kare ta da dukkan iyawarsa, amma akace wai sannu sannu bata hana zuwa…
A lokacin ne kuma ta juyo ta kalle shi, wani kallo da ya Ζara nauyin iska a Ζirjinsa yayin da murmushin leΙΙenta kuma ya yanke shigar iskar ma baki Ιaya, ba mummuna bace kuma bata da wani shahararren kyau ya sani, sai dai a idanunsa tafi kowacce mace a daraja da Ζima a rayuwarsa.
“Ka gama?” Motsin fatar bakinta da kuma alamar da tayi da hannunta yasa ya fahimci me take nufi tun daga can.
Sai ya Ιaga mata kai idanunsa na nazarin yadda hasken ranar na Ζarfe Ιaya ke dallare fuskarta yana Ζara Ζawata masa kammaninta da kuma tsarin halitta, wannan karon bata yi magana ba, da hannu tayi masa alamar komai cikin wani Ιan dogon sentence.
“Dan Allah. Ka jira. Minti Ιaya. In bata. Babyn.”
A hankali wani Ιan guntun murmushi yayi playing akan leΙΙensa ba yayin da wayar hannunsa ta shiga Ζara alamun shigowar kira. Sai dai bai Ιaga ba balle ya daina kallonta, itama shi Ιin take kallo kamar tana jiran amsarsa, yayin da a tasa zuciyar tunani yake daki-daki na yadda zai fara fahimtar da ita manufarsa akanta, me Mubarak yace ne?
… Ka san hanyoyin ka fa…
***
Kiyari.
Fadar Mai Martaba.
04:30 Am.
Lafiya maigidan bawa da baiwa
Lafiya dubu jiran mutum Ιaya
Lafiya Adalin sarki
Lafiya gagara gasa
Hifzullahi na Allah
Kanzullahi basasa
Amin Alfanda
Amin mai nasara
Amin zullillahi…
Wannan kirarin shi ke tashi daga bakin fadawa a lokacin da Sarki ya dawo daga masallacin sallar la’asar ya dawo cikin faΙarsu domin cigaba da karΙar gaisuwa daga tarin al’ummar dake ta tururuwa a masarautar, duk da cewar har a yau ba’a kawo gawar ba, Saifudeen tare da wasu daga cikin Ζ΄aΖ΄an Ζannensa sun tafi tun a jiya kuma a Ιari da akayi waya dasu safe since an gama duk wasu cike-cike da komai har ma an basu gawar kuma zasu taho da safe, wanda a agogon Nigeria ya kama karfe uku kenan na dare. Don haka aka sanar da jana’izar da misalin Ζarfe goma yadda duk daΙewa zuwa sha Ιaya an kammala komai an kaishi.
Sarki Ahmad Uba Kamsusi ya san cewa shi shugaba ne, mai dauke da nauyin dubunnan al’umma a kafaΙunsa, wanda ba yau ya saba Ιaukan hakan ba, yana riΖe da wannan nauyin tsawon shekaru amma duk tsawon wannan lokacin bai taba jin nauyin hakan a tattare dashi ba sai a cikin kwanakin nan, sai a yanzu da hankalinsa yake a mutukar tashe yake ganin cewa rayuwa ta juyo dashi da kuma iyalansa zuwa wani Ιarin nata mai tsananin duhu, don ko a jiya da su Nadiya suka zo yi masa ta’aziyya sai da ya fitar da Ζwalla a idanunsa bayan fitarsu duk yadda yaso ga daurewa.
A baiyane yake cewa dukkaninsu suna cikin tashin hankali da zuciyoyinsu ne kadai zasu iya fassarawa, don babu wani abu a duniya da yafi rashin Ιan uwa da kuma mahaifi, Farouk ya tafi, Fulani bata mutu ba amma gangar jikinta ce kadai a raye, babu wannan Hafsatun da take uwa kuma mata a wajensa, ya fahimci hakan tun daga lokacin da ta fara sambatu a gabansa kafin ma a kawo gawar Jakadiyarta abubuwa su Ζara rincaΙewa.
Halin da ta shiga kamashonta ne, laifinta ne, kuma ta riga ta gama tonawa kanta asiri a gaban kowa, ta fallasa asiri da ya daΙe a Ιoye, abinda aka daΙe ana tsegunta masa yana turewa, yana ganin haddasa ce kawai daga makiyanta, yana ganin Hafsatun da ya sani ba zata aikata haka ba. Sai gashi a yau komai ya kwance, kuma bahaushe yayi gaskiya da yace rana dubu ta Ιarawo, daya tak! ta mai kaya, a yanzu anzo gaΙar da Fulani zata karbi sakamakon duk wani abu da ta daΙe tana shukawa, kuma a yanzu duk wanda ke karkashin alhakin ta lokacin sakayyarsa ya fara kenan don har yanzu ma ba’a san takamaiman abinda ya same ta ba.
Saboda bayan ta farka daga baccin da ta dade tana yi a kasan allurai ne sai kuma aka zo masa da bayanin cewa bata iya tashi kwata-kwata ko magana, don haka a yanzu aka kira likitoci suka shiga Ζara duba ta, wanda bayanin hakan ne a yanzu Galadima ya shigo dashi kamar yadda likitocin suka shaida masa.
Sarki ya gaishe ka, kogin gabas maci yammawa,
Sarki ya amsa mai ado da kurar doki,
Lafiya dai Galadima jakadan Sarki…
Fadawa suka rufe da kirari a lokacin da Galadiman ya shigo ya durΖusa a gaban mai martaba, bayan yayi gaisuwar ne kuma sai ya Ιago ya kalle shi da zummar ya sallami dogarawan kafin ya shaida masa bayanin da yake tafe dashi, amma ga mamakinsa Sarkin kallonsa yayi shima sannan ya buΙe baki yace.
“Ina sauraren ka Galadima.”
Saboda haka sai ya taso ya matso a hankali daidai saitin kujerarsa sannan ya ajiye wani file mai Ιauke da bayanin dukkan wasu gwaje-gwaje da likitocin suka gabatar. Kansa a sunkuya yace.
“Kamar yadda suka shaida min ranka ya dade bayan sun kammala dukkan binciken su sun gano cewar Fulani tana dauke da matsalar ΖwaΖwalwa ne wanda since za’a iya magance shi cikin Ζananan lokaci in har ba’a bari ya cigaba da tasiri ba.”
Sarki ya gyada kansa, Galadima ya sake gyaran murya sannan ya sauke muryarsa ya fadi magana ta biyun, magana ta karshe kuma magana mafi girma kwatankwacin labarin rasuwar Umarul- Faruk.
“A bincike na biyu kuma ranka ya dade, sun ce ta kamu da cutar Ιarin jiki koma fiye da rabi ranka ya daΙe don idanunta ne kawai ke iya motsi a duk jikin nata!”5
***
Post a Comment for "ZANEN DUTSE CHAPTER 5 BY AISHA-SHAFIEE"