Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

WATA MACE CHAPTER 6 BY SANA S MATAZU

WATA MACE CHAPTER 6 BY SANA S MATAZU


                Www.bankinhausanovels.com.ng 

Look Ramlatu kinsan dai abinda ki ke be dace ba. Ta yaya na kai kuΙ—i gidanku amma kuma kina tsayawa da samari kuma dan cin fuska a gabana?”

“Dakata Kabir, ni fa allura ce acikin ruwa ta yaya zan tsaya ka yi min sakiyar da ba ruwa. Na sani ko Ζ™arya ka ke ba aurena zaka yi ba, sai na gama sakankancewa sannan in ji wuf ka fece!”

Wani miyau ya haΙ—iya yana jin kansa yana yi masa nauyi,

“Be san abinda ya ja shi ga auren Ramlatu ba, duk da zuciyarsa ce ja gaban kwaΙ—aitar da shi cewa ita ce ta dace da shi amma kuma yana ganin kamar ya yi kuskure”

Kallonta yake idanunsa jajjur, amma kuma wata shakkarta da be san dalilinta ba tana mammayeshi. Kamar wanda aka datsema baki ya kasa tanka mata haka ta juya tana girgije-girgije. Ƙasan ransa ya na jin kewar Zahidaht da komai nata.

“Shikenan Ramlatu ki faΙ—a ma su Baba ji bi za a zo batun saka rana kuma wata Ι—aya nake buΖ™ata!”

GuΙ—a ta yi tare da kai masa hug, “amma ka biyani wallahi”

Janye jikinsa ya yi yana takaicinta, sai dai ya gaza hanata shi gaba Ι—aya ma tsoronta yake ji dan wani kwarjini take yi masa.

***

Ζ³an kai amarya sun Ι—aukin hanyar Geza. Tafiya suke ba kama hannun yaro. Tun Labiba na ganin abin wasa ne har ta soma gajiya, ita da Tukur ya ce mata nan nan unguwar Maude za a kaita. Tazararta da gida kaΙ—an ne amma kuma ta ji sai lulawa ake. Gashi an Ζ™umsheta cikin mayafi ga zafi ana yi, ganin tafiyar ba ta Ζ™are ba ce yasa ta yayye rufin tana kallon yadda suke wuce hanya. Wani abu ne yake tokare da zuciyarta ganin da gaske Ζ™auyen Geza za a kaita. Bata manta ba, nan ne garin da Ζ™awarta Atine ta yi aure. Suka dinga yi mata dariya tun suna yara bare kuma yanzu? Tabbas ya yaudareta amma zata nuna masa kuransa. Sai dai wata zuciyar na gargaΙ—inta kan kadda fa Ζ™ilu ta jawo bau. Ba wannan ne matsalarta ba, ta ina zata fara rayuwa a Ζ™auyen nan da ko service me kyau basu da shi. Kennan da gaske Ζ΄an gidansu suke yi na cewar gidan ma da zata zauna na Ζ™asa ne? Da sauri ta girgiza kanta tana ayyana miliyan guda fa ta bashi ya zai kama mata gidan Ζ™asa?

Tunaninta ya katse daidai lokacin da suka ajiye motarsu a Ζ™ofar wani gidan Ζ™asa. Kasancewar akwai sauran rana bata Ζ™arasa faΙ—uwaba. Sossai ta ware ido tana kallon Ζ™ofar gidan. Ya sha shafe da farar Ζ™asa an mana irin tambarin nan na indomie da ake yi wa gidajen Ζ™asar Ζ™auyuka. Gabanta ya doka, tana saukewa Hajiya iyyah harara saboda mitar da take na taΖ™i rufe fuskarta. Bata damu ba, ta soma jan hannunta,

“Labiba fito mun kawo ki gidanki”

Hajiya Mawwadah ta maida dariyarta tana yin gaba, tare da cewa,

“ku sata ta yi basmallah ta saka Ζ™afar dama!”

“Angama Mamarmu”

Cewar Ade tana rangaΙ—a guΙ—a cike da shaΖ™iyanci. Su Yaya Amina da Maryam da Husnah kuwa  sakatotto suka yi dan dama su basu san dawan garin ba tunda basu zo jera ba. Duk surutan da ake a gida sun Ι—auka iya shege ne. Labiba kamar mutum-mutumi haka aka dinga janta. Ta dinga binsu kamar raΖ™umi da akala. Yuuuu! Yara suka yi dafifi a Ζ™ofar gidan suna shafa bango kamar sun ga wani sabon abu. Suka shiga gida sai Ζ™amshin Ζ™asa yake da yake anyi yayyafi kafin  su Ζ™araso.

Ɗakuna uku ne a gidan, Ι—aya ya Ι—auke kujerunta gaba Ι—aya da tv da fankar Ζ™asa Ox babbar sai firij Ι—inta. Ɗayan kuma ya Ι—auki gado da kwaba da mudubi. Sai kayan kicin Ι—inta da aka tsubesu a cikin Ι—ayar kwabar saboda babu kanta. Hasalima turaku uku ne na murhun dutse da aka yi da gini babba da Ζ™arami kuma ciki babu daΙ“e. Sai rumbun hatsi a tsakar gidan, daga gefe kuma buΙ—aΙ—Ι—an banΙ—akine. Tsakar gidan ya sha irin shafa nan me tafiyar mijici da ake yi a Ζ™auyuka da farar Ζ™asa. Labiba kasa jurewa ta yi ta warce hannunta tare da lallubar jakarta hannun Yaya Amina tana Ζ™oΖ™arin kiran Tukur amma kuma yaΖ™i Ι—agawa. Fashewa ta yi da kuka,

“Wallahi bazan zauna a wannan matsiyacin Ζ™auyen ba, ai ba haka muka yi da shi ba. Uw…sa ya yi da kuΙ—in da ya…”

Bakinta Hajiya Mawwadah ta buge tare da turata Ι—akin da gado yake, ba dan komai ba sai dan ganin yadda yara suka yi dafifi suna kallonta. Daga bayansu kuma mata ne zuga guda an zo tarar amarya. Suna zama kuwa matan na shigowa. Nan aka gaggaisa suka soma gabatar da kansu, matan kawunansa ne da kannansa sai kuma yayyansa mata uku. Dukkansu anan garin suke wasu ma suna maΖ™otaka da Labiban. A Ι—age take dubansu, tana yatsina duk ta gama Ζ™aguwa Tukur ya dawo ta sauke masa kwandon masifa na ha’intarta da ya yi ya kawota Ζ™auye. Lallai mutum mugun ita ce ne. Ƙanwar Tukur ce ta kasa haΖ™uri da duban da take musu, ta ga ko Ζ΄ar kunyar nan ma ta amare babu a gun amaryar tasu ta furta,

“mu dai ance mana matan birni basu da ta ido, naga kuma da alama irinsu aka kwaso masa!”

“Mene ne haka Magajiya”

Cewar matar Ζ™anin mahaifinsu Lantana tana umartar yara da su ajiye fantekun da suka zo da su. Nan da nan suka miΖ™e, Addeh ta cikasu da tukuicin dubu goma. Kamar su goyata haka suka fita suna murna. Sai dai da hanzari wasu suka zagaya suna kaiwa mahaifiyar Tukur tsegumin irin surukar da aka Ι—auko mata. Sossai ta shiga faΙ—a tana ba zata lamunta ba kasancewarta mace me zafi. Ana haka Tukur ya Ζ™araso, nan ta haushi da faΙ—a haΖ™uri ya dinga bata tare da nuna mata zai ja kunnan Labiban. Fita ya yi yana jinjina abinda ya faru duk da ya shiryawa haka domin ya san halinta amma ba zai juri Ζ™asΖ™antar da martabar mahaifiyarsa ba. YaΖ™in nasa ne._Suna da yatsan Ι—agawa su yi nuni wa shafin da Ζ™addara ta buΙ—ewa Ι—ayansu abisa kalmar sakaci. Amma kuma nasu yatsan ya kan zauna a Ζ™wantare wajen nuni wa nasu sakacin zuwa kalmar Ζ™addara. Idanunsu na da kaifi wajen hango kuskure duk Ζ™anΖ™antarsa. Amma suna zama makafi yayinda suka hango nasu kuskuren koda kuwa kusancinsu da shi ya kai sun shafa sun ji tabbacinsa._+

WAYE TUKUR?

Ita ce tambayar da Labiba taketa nanawata acikin zuciyarta. Domin gaba Ι—aya ta rikice. Ζ³an kai amarya kuwa tun suna Ζ™unshe dariyarsu har wasu suka soma yi a gabanta sai da Hajiya Mawwadah ta tsawatar musu. Ta kira Yaya Khamis ya fi sau shurin masaΖ™i amma wayarsa bata shiga hakama Amne. Ƙarshe ta ajiye girman kanta ta sa Husnah ta bincika mata aka tabbatar mata network Ι—in garin baya tafiya sossai sai cikin dare ko kuma ka zaga baya ka hau dutse.

  Abin ya bata mamaki dama akwai irin waΙ—anna Ζ™auyukan a cikin garinsu? Ta dai ji ana faΙ—ar garin geza amma bata taΙ“a zuwa ba, hasalima akwai gonakin mahaifinsu a garin waΙ—anda bayan rasuwarsa duk aka saidasu. Amma bata taΙ“a tunanin haka Ζ™auyen yake ba. Tana yawan ganin Ζ΄an garin sun kawo tallan gyaΙ—a me gishiri cikin Sakwato. Yanayin yadda suke wajen rashin tsafta ga rashin kunya da raina mutane, uwa uba rashin wayewa. Duk bata Ι—auki lamarinsu da zafi ba, ta Ι—auka kawai abu ne irin na Ζ΄an tallah musamman a shigarsu.

***

Tukur shi ne cikakken sunansa. Matashi ne me kimanin shekaru talatin cif, amma matsi da Ζ™uncin rayuwa ya takureshi waje Ι—aya Ι—an firit da shi kamar Ι—an shekara ashirin da Ι—oriya. Yana da faΙ—in Ζ™irji da kuma Ζ™aton kai ga tagomashin tsagun magge a gefan bakinsa.

  Su takwas mahaifinsu ya mutu ya bari, babu wanda ya sami tagomashin karatun boko saboda rayuwar yau da gobe. Yayarsu Hajara sai Katume da Tsahare da kuma Indo. Duk suna aure anan Geza da Ζ΄aΖ΄ansu. Tukur shi ne na biyar sai Auwala da Isuhule daga nan sai autarsu Mero data rage ba ayi mata aure ba.

  Auwala direba ne Lagos yake zuwa. Isuhule kuwa manomine. Sai Tukur da ubangiji ya taimakeshi aka turashi garin Sakwato almajiranci. Anan ya sami karatu na izzuf talatin cif daga nan ya faΙ—a buga-bugar rayuwa. Allah ya bashi nasibi kan gyaran takalma da kuma facinsu.

  Kasancewarshi babba cikin maza Ζ΄an uwansa be bashi damar yin aure da wuri ba, duk kuwa da gorin da ake masa na Ζ™annansa duk sunyi aure har ma da yara biy-biyu Isuhule da Auwala. Badan komai ba sai dan yadda yake tunanin sana’arsa ba zata Ι—aukeshi da iyalinsa ba amma a ransa yana son ya raya suna.

  Haka abokansa babu wanda be aure ba. Lokacin da ya riski dami a kala game da Labiba ba Ζ™aramin farin ciki ya yi ba, koba komai lokaci ya yi da shi ma zai raya gori. Ya kuma ci alwashin ko zata  yi hauka ba zai saketa ba. Musamman da ya ga gidan data fito.

  Ya godewa Allah da ya sa duk dabarar da ya haΙ—a babu wanda ya fuskanceshi ita Labiba na Ι—aukar Khamis ne ya turoshi shi kuma Khamis na Ι—auka Labiba ce ta aikoshi. Ko Jawwad sai ranar Ι—aurin aure suka haΙ—u shi ma sama-sama kuma be wani tsaurara bincike ba da jin cewar Labiba ya aura. Hasalima shi ta kansa yake sakammakon kamuwa da cuta me karya karguwar jiki.

   Mahaifiyarsu Baba Harira mace ce me faΙ—an gaske, bata son raini. Tana sana’ar gasarar koko da wainar gero da safe. Da rana kuma tana taliyar hausa da manja da awara. Haka kuma tana sana ar saida mai da Ζ™uli-Ζ™uli. Tun suna yara sana’arta kenan.

  Baba Harira tafi kowa takaicin rashin auren Tukur, da kanta ta sha nema masa auren Ζ΄aΖ΄an abokanta sai ya doje. Hakan yasa ya daina zuwa gidama gaba Ι—aya sai dai ya yi musu aike. Gidansu  Tukur babban gidane me wadatar Ι—akuna, matan Ζ™annansa da Ζ΄aΖ΄ansu duka a haΙ—e suke da mahaifiyarsu. Sai dai katanga da ke nuna Ι“angaren wancan da wannan amma Ζ™ofa Ι—aya ce ta shiga gidan.

  Girki a cikin gidan ake basa raba tukunya, sai dai idan an gama Baba Harira ta rarraba. Idan kana san ganin fushin Baba Harira ka taΙ“a Mero auta, tabbas ranar zaka ga fushi da sababi dan haka surukanta suke shakarta kuma suna taka tsantsan da ita. Ƙiri-Ζ™iri mijinki zai siyo miki abu, koda ya bata nata ta taka Ι—akinki ta Ι—auki naki ta haΙ—a biyu. Idan kinyi magana ta ce yayanta ne ya siya kuma Baba ta goya mata baya.

Kwatsam Tukur ya zo mata da batun zai auro Ζ΄ar birni ya kawota nan, abin ya Ι—aure mata kai amma bata hanashi ba a saninta Ζ΄ar birni da hankalinta bata zama a garin nan. Domin su kansu suna fatan yaransu in sun fita talla su samo na cikin gari su aura dan har murna ake zo ma uwa idan Ζ΄arta ta samo Ι—an cikin Sakwato.

  Amma ba a Ζ™wacewa yaro garma dan haka ta yi masa fatan alkhairi. Tun a wajen haΙ—a lefe suka soma haurawa, a cewarta ya tsawala amma sai ya nuna mata Ζ΄ar babban gida ce. Data turkeshi kan ina ya sami kuΙ—i be Ι“oye mata komai ba amma ya nuna mata shi fa ba AUREN MANUFA zai yi ba in ya aureta ya aura kenan. Sossai ta goya masa baya, domin ta tsani masu yin irin auren da ya faΙ—a mata tana danganta hakan da yi wa ubangiji shisshigi a lamuransa.

A wajen fitarwa da Labiba sashi ma sai da suka haura, domin kaf surukanta Ζ™ofarsu na ciki amma ya nuna mata na kwana biyu ne. Dan haka Ζ™ofa biyu aka yi Ι—aya tana cikin gida Ι—aya na waje.

***

Washegari Baba Harira ta sa aka damawa Ζ΄an kawo amarya koko, ya ji gasara ya yi kirtif ga kuma wainar gero da tasha Ζ™uli da man Ζ™uli ziryan aka yanka albasa akai. Sai aka Ι—ora musu farar alawa akai madadin sakari. Biredin da ya siyo musu kuwa ta rabawa jikokinta acewarta Labiba ta ja musu. Sai dai ga mamakinsu tsaf Ζ΄an kai amarya suka lamushe waina da koko suna santi. Hakan ya ragewa Baba Harira haushin Labiba koba komai ta ci albarkacin danginta. Sai dai Labiba Ζ™irΖ™iri taΖ™i ci taΖ™i sha sai da Hajiya Mawwadah ta aika ango ya samo mata tea da biredi da Ζ™osai. Haka ta ci tana yatsina, su dai da ido suke binta suna ganin dole ta sauko.

Da zasu tafi har gida suka shiga suka yi wa Baba Harira godiya suka rabu kowa ransa wasai. Sai lokacin Labiba ta Ζ™ara raina kanta. Kuka take wiwi tana riΖ™e Husnah ita ma Husnahr Ζ™wallar tausayinta take sharewa Yaya Amina kuwa ta kasa cewa komai. Da Ζ™yar da siΙ—in goshi suka Ι“amΙ“are suka shiga motocin Ɗan saΙ“alo estate suka nufo cikin Sakwato.

  A mota gaba Ι—aya sunyi Ι—if suna jimamin wace rayuwa Labiba zata yi?

***

Lokacin da labari ya je kunnan Amne game da garin da aka kai Labiba kamar zata yi hauka. Tasa Khamis ta yi agaba ta dinga surfa masa zagi ta uwa ta uba. Abokan zamanta kuwa banda dariya babu abinda suke yi mata. Su Yaya Amina ne kaΙ—ai masu tausarta hatta Hajiya Mawwadah ta kware mata baya. Khamis kansa ya shiga tashin hankali sai yanzu ya soma tunanin yadda auran ya kasance, yana tunanin duk da zaman Ζ™arantace ne amma wace rayuwa zata yi?

***

Labiba amarya kuwa, bayan tafiyar danginta ta fito ta zazzaga gidan, babu laifi kayanta sun haska gidan dan tana kallon yadda Ζ΄an Ζ™auyen suke shasshafasu suna kallon fuskarsu a jikin mudubi.

Abu Ι—aya ya burgeta da garin ba a cika Ι—auka wuta ba. Koba komai ta samu ta cajin yin karatun novel da yin game. Sai da ta gama zaga gidan tsaf sannan ta lura da Ζ™ofar da ta zamo mahaΙ—arsu. Jim ta yi kamar zata buΙ—e sai kuma ta Ζ™yale.

Da rana aka aiko Mairo ta kawo mata gero da wake, Ζ™erere ta tsaya mata aka kamar wata sa’arta bayan ta dire kwano. Bayanta kuma Ζ™awayenta ne da suke dafifin leΖ™a Ι—akin Labiba suna kallon firij. TaΖ™aici ya kamata, ta tsaya kawai tana kallonsu kafin ta gama yanke abin yi Mairo ta buΙ—e firij ta rarraba musu pure water. Ta zarce ta Ι—auki kwalbar turaren data gani gefan kujera.

   “Ina so!”

Ta furta cike da ko in kula, daga bisani ta ba wa abokanta umarnin su tafi. Fuu! Labiba ta miΖ™e ta bi bayansu. Janyo kwalar rigar Mairo ta yi tana huci,

  “Bani kayana!”

  “Na hana ai yayanmu ne ya siyo..”

  “Da kuΙ—in uwarki ya siy…”

Wani wawwan ihu Mairo ta tsalla, wanda ya janyo hankalin mutan gidan suka shiga rige-rigen nufo sashin. Kafin Labiba ta yi aune sun soma tuttuΙ—owa ta Ζ™ofar da ta dinga tunanin ta me ce ce.

“Wallahi baki isa ki zagarmun Innarmu ba. Ƙarya nayi ba shi ya siya ba?”

  Ta faΙ—a tana cakumar wuyan Labiban wadda mamaki da takaici sun hanata kataΙ“us. Daidai Ζ™asawowar Baba Harira tana tambayar ba asi, caraf sai Mairo ta Ζ™ara kukanta tana faΙ—in,

“Innarmu zaginki ta yi…”

“Zagi?”

Sauran matan suka haΙ—a baki wajen faΙ—a,

“ke kuma taki tarbiyar kenan daga zuwanki jiya?”

Wata Ζ΄ar tsamurmura ta faΙ—a, kafin su farga sai ga Tukur kamar anjehoshi.

“Lafiya Inna? Ke dalla malama sakar mata wuya!”

Ya faΙ—a yana watsawa Mairo harara. Da hanzari ta saketa. Matan kuwa da Ι—ai Ι—aya suka soma zare jiki saboda sun san halinsa.

“Ke Ladiyo me ya faru..”

Mairo ta yi caraf,

“Innarmu amaryarka ta zaga..”

“ban tambayeki ba suda!”

Tiryan-tiryan Ladiyo ta faΙ—i gaskiyar abinda ya faru, duk da hararar da Mairo ta ke antaya mata. Juyowa ya yi tare da nunata da yatsa ya shiga watsa mata kashedi. Sum-sum ta ja tawagar Ζ™awayenta suka fita. Sai lokacin ya dubi Inna yana sassauta murya kansa a Ζ™asa,

“Dan Allah Inna kadda ki biye zancen yaran nan su hanaku zama lafiya. Labiba dai Ζ΄ar ki ce kamar ni…

“Dakata min Tukur ni ma a gabanta zamu yi magana da kai?”

  Ta faΙ—a tana tsattsareshi da idanu. Kai ya girgiza jiki a sanyyae baya san fitina ta soma tashi tsakaninsu, yasan Innarsa kuma ya san labarin Labiba tabbas ya kamata ya yi wani abu..Fuu! Ta juya ta nufi sashinta. Labiba ta bi su da idanu kawai tana jinjina lamarin.

***

Sati uku da kai Labiba Ζ™auyen geza, gaba Ι—aya hankalinta ya tashi. Tukur ya rantse mata ya maya babu saki tsakaninsu. Kuma ya gayamata dalilinsa na auranta da hanyoyin da ya bi. A ranar ta kira Yayanta ta faΙ—a masa komai. Shi kansa ya girgiza amma babu yadda zai yi, in ya yi wani yunΖ™uri tabbas iyayansu zasu fahimci manufarsu ba kuma ya san ta Ζ™ara wani laifin kan na baya. Dan haka hankali ya kwantar mata tare da nuna ta yi haΖ™uri kawai ta rungumi Ζ™addara.

  Ɓangaren Amne ma dai hakane, amma zuciyarta na cike da danasani da takaicin yaudarar da aka yi musu.

Labiba fa ta shiga tsaka me wuya, da fari ta soma zuba rashin mutunci sai dai mutanan gidan suka nuna mata sun fita gogewa. Mairo kaΙ—ai ta isheta ciwon kai. Haka zata jawo yara ta kunna kallo, ta Ι—aura Ζ™anΖ™ara ta saka a firij dinta wai ta saidawa idan kuma ta hana Baba Harira ta tsefet tsaf ta uwa ta uba.

   Ranar girkinta kuwa babu me taimaka mata, saboda ita ma bata taya kowa. Inda Allah ya taimaketa kwana biy-biyu ne zagayowar girki dan haka tana samun hutu na kwana huΙ—u. Tuwon dare sunayin kwano uku, saboda dumammen safe kuma shi za a kuma ci da rana wata rana sai dai idan muguntar Baba Harira bata tashi ba. Tukur ya so nuna mata gata Ζ™warai amma mahaifiyarsa na hanawa, amma duk da haka yana yi a sace. Duk yadda taso ta yi masa rashin kunya tana shakkar mahaifiyarsa don bata Ζ™yalewa. Tun a satin farko da ta nuna masa Ι—anyen kai ta yo waje kan karΙ“ar haΖ™Ζ™insa ta gane wacece surukarta. Dan sunkutukum ta Ι—auketa ta a kafaΙ—a ta maida ita Ι—akin tare da saka kwaΙ—o ta yi tafiyarta.

  Da safe sai goma da rabi ta buΙ—eta, bayan tun asuba ta buΙ—ewa Ι—anta Ι—aki. Lokacin data fito kuma ta sa facalolinta suka dinga yi mata dariya da habaici tana gudun miji. Tun daga lokacin ta kiyayi matar dan bata son raini. Ita kuma a duniya ta tsani Ζ™asΖ™anci. Yanzu gaba Ι—aya tunaninta ya tafi ne kan yadda Ι“ale auran cikin ruwan sanyi.

Amma kuma Khamis ya tabbatar mata badai gidansa ba matuΖ™ar ta kaso auranta. Wajen Amne kuma bata ga fuskar hakan ba. Babban takaicinta duk wasu kuΙ—i nata ta wasarairai da su. Kaya ta yi masu mugun tsada ga shi ta Ζ™are a Ζ™auye. Ko kayan kicin kuΙ—in da ta kashe suna da ya wa, da fari ta soma tunanin ta fitar da su ta siyar amma kuma tasan karya mata su za ayi. Duk wata kaddara tata ta rasa inda suka yi dan sai yanzu ta farga da cewa ta yi Ι“arnar kuΙ—i ba kaΙ—an ba. Gidan da Yusuf yake ciki kawai ya rage mata sai tsirarun kuΙ—i wajen Khamis.Tun auransu da wata biyu ya fuskanci ta soma tu’amli da maganin hana Ι—aukar ciki, da fari ya maida abin na marmari amma dag bisani sai ya fuskanci da gaske take bata buΖ™atar haΙ—a zuri’a da shi. Duk yadda ya fahimtar da ita hakan ta gaza fuskantarsa, hasalima dalilin hakan suka shafe sati uku suna gaba. Ƙwarai yana buΖ™atar haihuwa amma babu yadda zai yi ya turasasa Ramlatu. Da farko bambami ya soma, daga bisani ya ga ba ci ya koma lallashi. Ƙarshe dai tsada suka yi kan zai dinga biyanta dubu goma duk wata domin kadda ta sha maganin . Babu ja ya amince saboda haihuwar ce muradinsa a yanzu. Sun yi wannan yarjejeniya da wata Ι—aya kwatsam safiyar yau yana shirin fita aiki Allah ya nuna masa kwalin maganin da ta sha ta bari kan mudubi. Ƙwarai ransa ya Ι“aci har wani Ι—aci ya ke ji. Kai tsaye fallo ya nufo yana Ζ™walla mata kira.

Zaune take tana dana wayarta, bata amsa ba har ya  Ζ™araso inda take. Wayar ya warce tare da wurgata kan kujera.

“Ni zaki munafunta Ramlatu, ba tsada muka yi dake ba?”

Ya furta yana kanga mata kwalin maganin a fuska. Ta razana amma da yake Ζ΄ar duniya ce sai ta maze. Jijjigata ya yi yana huci kamar mahaukacin kare. A zuciye ta ingijeshi, abinda da Ζ™arashen maye sai ya yi taga-taga zai faΙ—i ya cize. Wannan dmaar ta samu ta nufoshi da dukkan Ζ™umajinta. Masifa ta shiga surfa masa kamar ta ci babu duk da tana jin Ι—ar a Ζ™asan ranta. Ganin ya nufota kamar zai daketa ya sa ta gyara tsayuwarta. Yana Ζ™arasowa ta tattara duk wani Ζ™arfi nata ta cakumi kwalarsa.

ShaΖ™ar data kaiwa wuyansa ita tafi komai bashi mamaki, zuciyarsa ta zo iya wuya. Ya Ι—aga hannu zai kwaΙ—a mata mari, kamar wanda aka jonawa shocking sai ya janye. Ya yi wa kansa alΖ™awarin ba shi ba dukkan mace. Yana tuna silar rasuwar Zahidaht ya kan ji ya tsani kansa, tabbas ba zai sake wannan gangancin ba. Kallonsa ta yi sheΖ™eΖ™e,

“Wai Kabir da dukana zaka yi, to me ya hanaka ka dakeni?”

Shiru ya yi mata yana huci, ga hannuwanta _still_ a wuyansa ta gaza sakinsa. Jijjiga jiki ta soma yi,

“haihuwa ce da kai na ce ba yanzu ba,ka barni in yi sha’anin rayuwata. Ko zan haihu sai na mori Ζ™uruciyata ballantana kuma ni ba sakarya ba ce da zan yadda in haihu da mutum irinka. Wallahi ba zan haifi ‘ya’ya a dinga kawomunsu an bi su an Ζ™waΖ™waleba!”

Kamar saukar aradu ya ji shigar kalamanta, jikinsa ya yi mugun sanyi. Zuciyarsa ta matse da wani irin yanayi. Tabbas sai yanzu ya ke Ζ™ara danasani da takaicin rayuwarsa ta baya, be taΙ“a hango abinda Ramlatu ta faΙ—a ba duk da yasan ta faΙ—a ne domin kare kanta. Murya a raunane ya furta,

“sakarmun wuya!”

Ita kanta ya bata tausayi ganin yadda kalamanta suka illatashi lokaci guda. Amma Ζ™asan ranta tana jin wannan shi ne makamin yaΖ™arsa ta huta kawai. In ya ga ba zai iya ba ya sauwaΖ™e mata. Wayarta ta Ι—aga ta dana kira, ta bishi da idanu ganin ya dafa bango yana bi har ya kai Ζ™arshan fallon ya fice. Tsuka ta ja tare da furta,

“Adijee na gama da batun Man fa, na samo hanyar hukuntashi”

Daga can Ι“angaren aka furta”ke fa kwalba ce wallahi”

Ba ta bata amsa ba, suka koma wata hirar da ban.+

***

Labiba ganin babu sarki sai Allah ya sa ta saki jikinta ta soma fuskantar rayuwar da ta riska. Ta karΙ“i duk wani sauyi da ta samu acikin rayuwarta illa abu biyu zuwa uku. Baba Harira dai tsakaninta da ita mutuntawa ce, haka ma facalolinta tuni ta taka musu birki kan izgilanci da suke yi mata kuma Tukur ya mara mata baya. Hakan ya sama mata sauΖ™i sossai. Tsakaninta da su gaisuwa sai in ta fito girki sun haΙ—u wanda babu wanda yake taimaka mata. Hakan kuwa ba Ζ™aramin naΖ™asu ya ja mata ba, duk ranar girkinta sai ta yi zazzaΙ“i sabida bata da mataimaki.

Mairo ma tuni ta dakatar da ita, duk masifarta da ta Baba Harira sun haΖ™ura sun sa mata ido domin ta Ζ™eΖ™ashe Ζ™asa ta hana Mairo Ι—aukar mata ko tsinke. Idan sun yi magana amsarsu ita ce guminta ne bana Ι—an uwansu ba. Jin hakan ya kan sa guiwoyin Baba Harira yin sanyi domin tana gudin asan AUREN MANUFA Ι—anta ya yi a saka shi a bakin duniya. Dan ta lura Ζ™warai Labiban tere take san yi musu. Wnda tana da yaΖ™inin matuΖ™ar Ζ™addara ta ratso ya saki Labiban babu me bashi auren Ι—iya a garin dan haka suka shafa mata lafiya.

Babbar damuwarta yanzu shi ne muguwar kazantar Tukur, tun lokacin da ta yi karatun ta nutsu kan rayuwarta ta baya ta fuskancu Ζ™azanta da wasu Ι—abi’unta suka ja mata barin gidan Yusuf ta Ι—auki Ι—amarar gyara kuskuranta. Komai nata tsaf yake abin sha’awa. Sai dai ga Tukur abin ba haka bane. Tukur cikakken Ζ™azami ne na bugawa a jarida. Ya kan shafe kwana biyar be yi wanka be yi brush ba. Hakan yasa haΖ™oransa suke yalaye shar da su babu kyan gani. Har mamaki take yi me yasa bata kula da duk wannan ba KAFIN AURE amma Ζ™addara ta tiga fata. Kaya kuwa sai ya yi sati yana maimaita saka m

su kuma ya zo ya cusa mata cikin kwaba, kusa da wankaku su yi ta tashin tsami. Fason Ζ™afarsa kuwa kullum cikin janye mata zanin gado yake yi. Ta yi masifar ta yi lalashin ya kan rage akan da amma har lokacin be gamsheta ba.

***

Yusuf kam sai sambarka, arziki ya ninka na da. Allah ya sa masa albarka, bayan gidan youghurt da ya buΙ—e yanzu yana da wajen kiwon kaji da kuma raguna. Shi kansa har mamaki yake yi. Haka kuma be yi Ζ™asa a guiwa ba wajen tallawa dangi da Ζ΄an uwa. Kowa nasane be ware ba, hidimar abinci da sutura duka ya Ι—aukewa mahaifansa. Su Khamis duk sai suka raina kansu, Ι—aga kai da Ι—agawar da sukewa dangi sai ta tashi a babu. Babu wanda zai buΙ—e baki be kira mutuntakar Yusuf a dangi ba. Ya zamo wani tauraro me haskawa. Matarsa kuwa ta zamo abar kwatance domin ita take Ζ™ara goya masa baya kan dukkan hidimar danginsa. Da jiki da zuciyarta tana tare da shi. A yanzu haka tana Ι—auke da ciki wanda suke sa ran haihuwarsa yau ko gobe. Duk wata siyayya ya gamata. Wasu lokutan tasa kayan babyn yake a gaba yana kallo, wani lokacin ya yi kuka wani lokacin ya yi dariya. Yana tuna Ι—iban albarkar Labiba a lokutan haihuwarta da bashi da karfin siyan komai.

***

Da gudu yaran suka shigo, tana zaune ta miΖ™e Ζ™afa saboda nauyin da cikinta ya yi mata tana dubansu. Murmushi ya suΙ“uce mata ganin yadda suke zaga fallon suna dariya. Da alama Khalifa na san karΙ“ar teddyn Ι—in hannun Ummi ne. Daidai lokacin mahaifinsu ya yi sallama bayansa yaya Amina ce da nata yaran. Da gudu Ummi ta tafi ta rungumeshi,

“Abba ka ga Khalifan Mommah ko”

“A’a fa Ι—iyar Abba ke kika taΙ“amun yarona”

Cewar Shukura tana murmushi, Ζ™arasawa suka yi gaba Ι—ayansu ta yunΖ™ura tana gaishe da yaya Amina. FaΙ—a ta soma yi mata kan mene zata takura kanta ta ce sai ta sunkuya bayan ta yi nauyi. A kunyace ta Ι—auke kai tana murmushi, ita ma murmushin ta yi Ζ™warai halin yarinyar na burgeta. Sai yanzu ta sake gasgata cewar Yusuf ya yi mata.

Hirar zumunci suka shiga yi, Shukura ta miΖ™e ta kawo mata abin motsa baki sannan ta basu guri su gana da Ι—an uwanta bayan ta yi dabarar janye yaran. Wannan Ι—abi’a tata ta Ζ™ara mata Ζ™ima a idanun dangi da yawa. Duk yadda kuka saba da ita matuΖ™ar ta kula wajen Yuauf suka zo to kuwa zata basu waje su yi uzurinsu. Musamman yanzu da ya kasance Yusuf Ι—in ya zama babban Ζ™arami a cikinsu. BuΙ—i da wadata sai Ζ™aruwa suke yi a harkokinsa. Mutane da ya wa na ganin shi ya maye gurbin mahaifin Labiba acikin zuri’arsu saboda yadda harkokin kuΙ—i suke zuwar masa da nasara.

Amne kanta ta shiga nadama da danasani, duk wata hidima ta gidan shi ne kama daga kan cimma zuwa sutura. Sau tari idan aka shiga taro har shaguΙ“e ake yi mata cewar Ι—iyarta me Ζ™ashin tsiya ce gashi nan daga rabuwarsu Yusuf ya zama wani abu. Ira-iran wannan kalaman kansa mata jin Ζ™yamar shiga dangi, sossai take dana sanin raba Labiba da gidan auranta.

Post a Comment for "WATA MACE CHAPTER 6 BY SANA S MATAZU"