Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

WATA MACE CHAPTER 3 BY SANA S MATAZU

WATA MACE CHAPTER 3 BY SANA S MATAZU

                   Www.bankinhausanovels.com.ng 

SAUYI.

Haihuwar Labiba ta kawo sauyi da yawa a rayuwar aurenta da Yusuf. Sossai zahirin hallayarta ta fito kowa ya sani. Muguwar Ζ™azantar data zame mata jiki ta bayyana. Ɗakinta baya zaunuwa saboda zauri ga Ζ™arnin miyau. Domin tana tashi daga bacci shi take soma tsartarwa a jikin bango. Tun yana kauda kai har ya zamana ya soma tankawa amma babu sauyi ko kaΙ—an sai ma izgilanci da rainin wayau data tsiri yi masa. Hakan ya asassa musu rabuwar Ι—aki kowa ya zamana yana da mallakinsa.

***

Duk abinda ya ke faruwa game da Ζ™azantar Labiba Amne ta sani sarai, amma bata taΙ“a kadda baki ta yi mata magana ba hasalima hakan ya yi mata yadda take so ko ba komai Yusuf zai Ζ™ara Ζ™untata da baΖ™in ciki. Watan Ummi goma a duniya Allah Ya sake bata rabon ciki, tabbas samuwarsa ta Ζ™ara asassa komai na rayuwarta. Iskanci kala-kala da an yi magana ta ce cikine. Tun ba ajin kansu har ya zamana iyayensu maza sun soma shiga cikin lamarin domin sassanci. Baba Ι“aure dai kodayaushe yana bayan Yusuf saΙ“anin mahaifinsa. 

***

A safiyar wata Asabar Yusuf ya tashi da sassafe. Nazira Ι—iyar Yaya Asabe da tazo musu hutu yasa ta kira masa Labiba ta tafi da Ι—an gudunta tana tsale. Tana shiga ta sameta a kwance kamar mataciyya. Kauda kai ta yi tana gunguni dan Nazira akwai rashin kunya. Ζ³ar Ζ™ara ta yi, wadda ta haddasawa Labiban farkawa, a tunzure take duban yarinyar da haushin tadata da ta yi. Nazira kuwa baya ta yi tana Ι—an turo baki. Tsittt! Kake jin sautin fitar miyan bakinta, bai sauka ko ina ba sai a bangon Ι—akinta. Nazira data shigo ta ja baya tana kyaΙ“e baki. Idanunta Ζ™ur a kan bangon da Addahrta ta zubar da miyan. Ɗauke kai ta yi tana yatsuna fuska. Karaf a kan idanun Labiba, ta maka mata harara,

“Dan ubanki ni kike kyaΙ“ewa baki?”

Ja da baya yarinyar ta yi tana zare idanu, domin tasan matuΖ™ar ta shiga hannunta mai Ζ™watarta sai ubangiji. Bata sami nasarar guduwa ba ta cafkota.

“Ba dake nake ba?”

Da sauri yarinyar ta toshe hancinta saboda hamammin bakinta daya doketa. Daidai lokacin da take kicin-kicin Ζ™wacewa Yusuf ya jiyosu ya tako zuwa Ι—akin badan ransa ya so. Sai dan sanin zata iya illata masa yarinya kafin zuwansa.

“Laby cikamin yarinya!”

Ya furta da fuskar shanu.

“Idan anka Ζ™i hwa?”

“Zan Ι—auki mataki fiye da tsamaninki!”

Kallon uku kwabo ta watsa masa, ta cuno baki tana karkata kai.

“Da anka yi man wanga tutiya, banda wannan lokaci kajiya”

Wani Ζ™ululu ne ya tokare masa maΖ™oshi, da Ζ™yar ya haΙ—iye miyan daya tattaro, bai san yaushe ne Labiba zata sauya ba? Ba haka ya ga KOWACE MACE na yi wa mijinta ba. Wai shin jarrabta siyanta ake da Labiba ta kwaso duk wasu makaman raini ta zuba akansa? Ba tare da ya tanka mata ba, ya juya ya kama hannun Ummi da Nazira da zumar su bar Ι—akin,

“Allah ka rabani da lusarin namiji!”

Saukar kalamanta kamar aradu cikin kansa, a fusace ya juyo ya watsa mata wani kallo muryarsa na rawa,

“Ba ki ji ya daΙ—in halinki ba, Ι—iyan boya kawai”

“Uwa taka ma ai tsattson boya ce..”

Jifa ya kai mata da takalmin Ζ™afarsa, ya kuwa yi nasarar samunta a bakinta. Ta Ζ™walla Ζ™ara tana riΖ™e wajen. Take leΙ“Ι“en ya fashe kafin ajima ya kumbura ya yi suntum da shi. Ta kuwa shiga surfa masa zagi ta uwa ta uba, ganin idan ya biye mata sai ya iya yi mata dukan da zai nakasata ya sa ya fice da niyyar bar mata gidan gaba Ι—aya. Nazira da take riΖ™e da Ummi tana kuka ta yi sakare tana kallonsu. Farga ya yi da yarinyar ya juya kawai ya fita gudun yin abin kunya.

***

Cikin Labiba na Ζ™ara girma Ζ™azantarta ta Ζ™aru fiye da baya. Nazira da take tayata aiki ta tattara kayanta ta gudu saboda masifarta. Cikinta na gab da haihuwa gwamna mai ci ya bawa Baba Ι“aure kwangilar gina babbar kasuwar da ta kasance a tsakiyar garin sakwato. Wadda ta haΙ—a kowane nau’in kaya na kasuwanci. Kasuwa ce da aΖ™ala ba a kasaraba aka yi itifaΖ™in zata ci naira miliyan Ι—ari da hamsin da Ι—oriya. Sossai wannan kwangila ta fito da martabar duk wani Ι—an cikin *ƊAN SAƁALO ESTATE.* Nan da nan Baba Ι“aure ya soma gudanar da gwangilar cike da Ζ™arfin guiwa.

Yusuf na Ι—aya daga cikin ma’aikatan da aka Ι—auka, kuma yana cikin waΙ—anda aka ba wa babban matsayi a wajen. Safiyar da zai fita aikin haka suka rabu da Labiba da zagi uwaka ubanka kare baya ci ba. Ji ya yi kamar bazai fita ba saboda Ι“arin rai.

Tunda ya bar gidan kansa ya ke ciwo, ga jiri da yake Ι—ibarsa lokaci-lokaci. Haka ya daure ya tuΖ™a machine Ι—insa har zuwa inda ya ke san zuwa. Aharabar ma’aikatar da ake gudanar da kwangilar da wan mahaifinsa ya karΙ“a ta gina babbar kasuwar MARWAKH ya samu ya yi matsuguni. Tun daga nesa ya hango Baba Ι“aure yana zagaya wajen, ya zuba masa idanu, tsoho mai karamci da sanin ya kamata. Tarin dukiya bai Ι—ora masa girman kai ba, kamar yadda Ι—iyarsa ta Ι—orawa kanta. Sau tari yana jin kamar ya saki Labiba ya huta, sai dai kullum yana tuna karamcin mahaifinta da kuma furucin mahaifinsa,

“Labiba Ι—iyatawa ce, ni naka Ι—aurama aure da ita. Amanatata naka baka, ni zaka duba ba ita ba!”

Ajiyar zuciya ya saki, ya taka akan duga-dugansa, daf da yayan mahaifin nasa ya Ζ™arasa tare da rusuna ya gaisheshi. Daga bisani ya cire rigarsa ya saka ta ma’aikata kamar kowa. Cikin hanzari ya shiga sahu, aka soma loda masa suminti a kwano yana Ι—auka kamar kowa. Nauyin sumintin ya danΖ™arar da dogon wuyansa, har ya bada wata Ζ™ara Ζ™as! Cije laΙ“Ι“ansa ya yi yana jin Ι—aci a Ζ™asan ransa, sai dai kuma wata zuciyar na tuna masa,

“da haka kowa ke mallakar gumin hallak!”

A haka suka shari awa huΙ—u suna aikin gini, wasu na Ι—aukar bulo, wasu na kwaΙ“in suminti wasu kuma na Ι—aukar kwaΙ“in suna kaiwa masu dasa harsashin gini. Nan da nan suka ci Ζ™arfin aikin domin sun kai kimanin su Ι—ari da hamsin. Sallah da cin abinci kaΙ—ai ya ke tsayar da su. A haka suka kammala. Daga bisani suΖ™a soma bi layi sahu-sahu ana rarrabamusu haΖ™Ζ™insu na ranar. Kowannansu da naira dubu uku ya tashi.

Hannu yasa ya karΙ“i nasa kason, farin ciki na zaga zuciyarsa. Idannunsa na kan kawun nasa, yana yaba hallayar dattijon har gobe. Tabbas samun irinsa sai an tona. Ba kuma shi kaΙ—ai ba da yawansu sai sun yi godiya bayan sun karΙ“i kuΙ—in, ba don komai ba sai don karamcin shugaban nasu. Sau tari idan sun yi aiki irin wannan na kwangila ga su kuma da yawa, maimakon a basu dubu Ι—aya da Ι—ari biyar ko dubu biyu na yini da aka sani ana biyan kowane magini. Wato raba kuΙ—in biyu da wasu suke yi, suna yi musu tinΖ™ahon suna da suna da yawa shi yasa aka rage farashin. Shi baya yin haka.

Haka kuma Ι—abi’ar sauya ma’aikata a washegari baya yi. Wanda akasari haka Ζ΄an kwangila suke yi, in ma dai waΙ—anda suke da hanya ko kuma in baka yi sammako ba a Ι—auki wasu a yi maka tinΖ™aho da cewar aikin kwangila babu jira. Akasari maginan da suke aikin kwangila suna fuskantar wannan matsin na ragin haΖ™Ζ™insu, ga hantara da kyara daga shugabaninsu. Ga kuma fitar sassafe gudun a sauyasu da wasu. Wsu na jurewa hakan kasancewar rashin aiki da ya yawaita, duk wajen da ake aikin kwangila irin na gini baya rasa matasa masu zuciyar nema a wajen. In ma sun san wani, in ma kuma haka siddan su zo neman dacewa dan samun hasafi.

Sai dai shi nasa fanin ba haka bane, Baba Ι“aure akwai karamci, mutanan da ya soma aiki da su, har agama da su yake aiki. Kuma yakan ninka musu kuΙ—in aikinsu tare da tunatar da su muhimmancin wadata iyali. Shiyasa duk wajan da ake aikinsa zaka ga tururuwar matasa.

Da murna da komai Yusuf ya wuce gida, a hanya ya tsaya ya siyi shinkafa kwano Ι—aya ta hausa, sai shinkafar tuwo rabin kwano saboda yasan Labiba na Ζ™aunar wainar shinkafa.  Ummi da Nazira kuma ya siya musu alawa da biscuit da bobo. Wasai ya ke jin ransa ko ba komai ya fi Ζ™arfin gidansa. Duk da Ζ™asan ransa yana jin takaicin yadda suminti ya yi masa kanta a hannu tare da maida fatar hannun nasa me kausji da wani irin tauri na ban mamaki. Haka Ζ™afafunsa tafin Ζ™afar duk ya tsattsage duk kular da yake bata da man kaΙ—anya. Duk wannan takaicin be hanashi yin walwala ba saboda ya siyi abinda za su ci. Sai dai tun daga bakin Ζ™ofa gabansa ya soma faΙ—uwa. Kafe machine Ι—insa ya yi, tare da yin shahadar Ζ™uda ya shiga. Take idanunsa suka sauka akan yanyyamun Ζ™udan da suka cika mazubin kashin yara. Da sauri ya Ι—auke kai, zuciyarsa kamar ta fito dan takaici. Tana zaune a can gefe, daga ita sai Ι—aurin Ζ™irji, ga mangwaro take sha. Ummi na kwance a Ζ™asa bako riga Ζ™uda na binta. Ga hannunta a baki tana sha, bisa dukkan alamu yunwa ta ci ta cinyeta. Da gudu ya nufoshi,

“Abba sannu da zuwa!” Sauban yaron Yaya Adamu ya faΙ—a yana Ι—aneshi. Shafa kansa ya yi, yana jin Ζ™uncinsa na raguwa. Babu suturar kirki a jikinta bare kuma yasa ran za ta sakawa Ummi. Ya sake kallon Sauban yaron ya bashi sha’awa tsaf da shi. Hannunsa ya riΖ™e sossai cikin nasa.

“Saubahn ina Mamanka?”

Mtsss! Tsakin Labiba ya shiga kunnuwansa, ta miΖ™e yuu! Ƙudaje kuwa suka ce sallamu alaikum. Ɗauke kai ya yi. Ya soma Ζ™arewa tsakar gidan kallo. Ya ma rasa ta ina ne zai soma. Allah Ya yi shi da mugun tsafta. Dan haka ya zage ya gyara ko’ina tsaf duk da gajiyar daya kwaso. Bai nufi Ι—akin girki ba, gudun ganin abinda zai iya sa shi amai. Ummi ya kama ya yi mata wanka, ya kaita Ι—akinsa wanda yake fitar da Ζ™amshi mai daΙ—i. Daga bisani ya yi dabarar dafa musu indomie suka ci tare da ita, nan da nan ta ware tana Ι“angala dariya sai ta Ι“ingire ta kama bacci. Sai da ya mula sannan ya nufi Ι—akinta. Tana zaune kai babu Ι—ankwali ga tulin kayan wanki, zauri kuwa ba a magana kamar banΙ—akin Ζ΄an makaranta. Shinkafar ya miΖ™a mata da sauran canjin, ta karΙ“a a lallace.

“Ka fanshi kanka da…”

Kafin ta Ζ™arasa idanunta suka nuna mata shinkafar gida, Ζ΄ar hausa. Wata ashariya ta Ζ™undumo ta maka masa tare da tattara shinkafar ta jefa masa. Bata sauka ko’ina ba sai kan fuskarsa. Ta tarwatse a tsakar Ι—akin. Take ya soma bin shinkafar da idanu, kwanyarsa na lissafomasa tarin wahalhalun da ya sha wajan samar da ita. Komai ya shiga zuwar masa daki-daki kamar a lokacin ya ke aikin. Zuciyarsa ta Ζ™untata matuΖ™a karon farko ya ji yana muradin sauke fushinsa akan Labiba tun auransu. Kyawawwan maruka guda uku ya shimfiΙ—a mata akan fuska, yana huci ya nunata da yatsa,

“Zan juri komai Laby amma banda wulaΖ™anta Ζ™umajina!”

Daga haka ya fice ya bar mata Ι—akin tana kuka da Ι—ura masa ashariya kamar Ι—iyar maguzawa. Ashariya ta shiga auna masa kwano-kwano. Hajiya Hauwa dake kwance a kabari, ta dinga ambata tana Ι—urawa zagi. Gani ya yi ba zai iya juraba ya zage kwanji ya jibgeta son ransa. Ai kuwa da himma ta tattara ta nufi gida. Amne ta dinga surfa ruwan bala’i ta kuma yi rantsuwa duk ranar da ya kuma dukkan mata Ι—iya to yayyunta zasu rama mata.

Baba Ι“aure ne ya nuna mata bata isa ba, ya kuma ja kunnan Labiba da kakkausar murya kan zagar masa iyaye. Tare da yi wa Yusuf Ι—in nasiha mai ratsa jiki kan haΖ™uri da iyali. Nauyinsa ya koma ji sossai, saboda me doki ne ya koma kuturi shi da ya kamata ace ya tsayawa Labiba amma shi yake goyon bayan Yusuf. Ƙima da mutuntakarsa sai ta kuma Ζ™aruwa a idsnunsa dama dangi baki Ι—aya. Tun daga lokacin Labiba ta shiga fefan dangi, aka watsata. Da anga kina Ζ΄ar rashin kunya ga miji za a soma dangantaki da ita, har abin ya soma zama abin fitina cikin ahalin.Baba Ι“aure ya tashi haiΖ™an, wajen gudanar da aikin kwangilarsa. Ba’a Ι—auki wata biyu ba gaba Ι—aya birni da kewayen garin suka san da mashahuriyar kasuwar. Saboda yadda ginninta ya soma fantsama ko’ina ka zauna batun ake yi. Wani abin burgewaa sisi bai karΙ“a ba na aikin ya ce sai ya kammala. Wannan ya Ζ™ara masa Ζ™ima da martaba a idan gwamna sossai.

A Ι“angare guda kuma Ζ΄an adawa nata Ζ™oΖ™arin dakusar da hoΙ“asarsa, amma kuma Allah bai basu ikon yin nasaraba. Cikin watanni Ζ™alilan aka kammala ginin kasuwar, gwamna ya haΙ—a gagarumin taro tare da karrama shi da wasu cikin makusantansa. Aka bashi lambar girmamawa tare da yabawa aikinsa. Sai dai kuma kamar yadda gwamna ya buΖ™ata shi ne, ya zo gida ya amshi kuΙ—in aikin kwangilarsa ba za a bashi su gaban bainar jama’a ba.

Haka taro ya tashi farin ciki cike da zuΖ™atan makusanta. Yusuf kansa yana cikin masu farin ciki, domin ba kaΙ—an ba ya dama a wannan kwangila ya samu daidai gwargwado haka duk wani matashi dake kewayen unguwar dama cikin estate Ι—insu.

Bayan sati biyu a safiyar Littinin Baba Ι“aure ya yi wa iyalansa sallama. Ya shirya ya tafi karΙ“o haΖ™Ζ™insa kamar yadda aka buΖ™ata. Sai dai tun safe har zuwa magarba babu shi babu labarinsa, hakama wayoyinsa basa shiga. Amne ce ta soma ankarar da mutanan gidan halin da ake ciki, domin ita Ι—in mace ce mai kulawa da lamarin mijinta. Tunda ya tafi take bibbininsa a waya, balantana kuma da take tunanin kuΙ—i zai amso ko banza tana da kaso mai tsoka. Saidai bata samun wayar, tun abin yana cinta ita kaΙ—ai har ta fito ta nunawa mutanan gidan wayarsa fa bata shiga. Nan fa hankula suka soma Ι—agawa aka shiga cuku-cukun neman ina ya tsaya. Sai dai kash duk iya Ζ™oΖ™arinsu babu labarinsa. Kafin wayewar gari labarin Ι“atan Baba Ι“aure ya kewaye cikin ahalin baki Ι—aya.

Baba Ɗangaladima ya fi kowa shiga tashin hankali, sai dai ya fi kowa nuna musu dauriya domin shi mutum ne mai kawaici. Sai yamma suka sami zuwa wajen gwamna sai dai abin tashin hankalin an basu tabbacin bai zo ba. Tashin hankali wanda ba a samasa rana. Wannan ahali sun ga tashin hankali koke-koke kuwa babu yara babu manya. Haka suka dawo guiwa a sage duk da kwantar musu da hankali da gwamnan ya yi tare da alΖ™awarin sa wa a bincika. Kwana Ι—aya biyu uku, babu wani sauyi, ba bu shi babu dalilinsa.

Ta Ι“angaren gwamna ma kuma duk Ζ™oΖ™arinsu babu wani cigaba sai ban haΖ™uri da yake wa iyalan. Addu’a kuwa basu san iyakar wadda suka yi ba, suka saka aka yi. Hakama mutanan gari kowa yana nuna alhininsa. Kwanansa biyu da yini aka kira wayar Baba Ɗangaladima tare da buΖ™atar maΖ™udan kuΙ—i kan za a badashi ko kuma zuwa washegari a sami gawarsa. Sossai hankalinsu ya tashi, domin bada kuΙ—in da aka buΖ™ata tamkar durΖ™ushewar ahalinsu ne domin gaba Ι—aya dukiyarsu bata gaza hakan ba. Haka suka shiga cuku-cukun samun kuΙ—in amma abu ya faskara. Koda labari ya isa ga kunnan gwamna sai ya buΖ™aci su barshi da alhakin hakan. Sun ji daΙ—i karamcinsa sossai da sossai. Abinka da aikin gwamnati, ba zasu ce ga yadda aka yi ba, su dai sun wayi gari suni ganshi an kawoshi har Ζ™ofar gida da asuba a wata baΖ™ar mota aka tafi.

Ζ³an uwa sun cika da murna da farin ciki musamman da ya kasance lafiyarsa Ζ™alau, babu wani rauni tare da shi. Kwana biyu Ζ΄an uwa na jelar zuwa ganinsa, aranar kwana na uku ne suka tashi da tashin hankali sakammakon jikinsa da ya rufe da zazzaΙ“i sai kuma Ζ™afaffunsa da ya zamana basa motsawa ko kaΙ—an. Babu jinkiri aka wuce asibiti da shi, binciken farko likitoci suka tabbatar da an yi masa allurane mai nakasa gaΙ“oΙ“in jiki daga nan kuma sai kisa. A bayanin nasu sun tabbatar da zasu yi iya Ζ™oΖ™arinsu wajen dakatar da allurar, gwamna kansa ya shiga tashin hankali domin yana da yaΖ™inin don a Ι“ata sunansa a ka yi.

A ranar ya soma cuku-cukun nema masa visa domin tafiya egypt, cikin kwana biyu zuwa uku aka kammala komai. Tare da Baba Ɗangaladima aka tafi, kwanansu biyu dai jiki ya Ζ™i daΙ—i aranar kwana na uku ya amsa kiran mahallicinsa.

Iya tashin hankali ahalin sun shiga, haka aka yi cuku-cukun Ι—auko gawarsa zuwa gida nijeriya wadda ta shari tsawon kwana biyar da clearing da komai suka iso tare da rakiyar tawagar amintattun gwamnati. Cincirindon mutane ba a cewa komai saboda tsabar yawansu. Da Ζ™yar motocinsu da ambulance Ι—in da aka turo daga wani asibitin gwamnati wadda ta Ι—auko shi suka iya wucewa. Bawan Allah mai halin gaskiya da amana ko da rai ko babu yana cikin zuΖ™atan mutane. Koke-koke kawai ake ji yayin da Ζ΄aΖ΄ansa da kansu suka Ι—auki gawar mahaifinsu zuwa cikin gidan domin haΙ—a shi. ZuΖ™ata sun raunana matuΖ™a a wannan rana. Hajiya Amne da abokan zamanta sun zabge lokaci guda. Surukan gidan da jikoki ne ke iya taΙ“uka wani abu, suma Ι—in a sanyaye. An shirya yin jana’izar ana idar da sallar azahar saboda Ζ΄an uwa da abokan arziΖ™i na nesa da suka roΖ™i alfarma.

Baba Ɗangaladima baya iya ko magana, haka ma Yusuf Labiba kuwa sumanta uku tana farfaΙ—owa. Hakan ya jaza mata naΖ™uda gadan-gadan a ranar ta haifi cikin jikinta, yaro Ι—an firit da shi bakwaini. Haka aka yi masa sutura aka sadashi da makwancinsa na gaskiya. Ba wani zama aka sake yi ba, tunda anyi na baya. Har zuwa lokacin Labiba na sashin mahaifiyarta bata koma gidanta ba. Ζ³usuf kuwa bai bi ta batunba, ganin har lokacin mutuwar bata gama sakin ahalinsu ba.

Mutuwarsa ta sanyaya jikin ahalinsu da dama. A  kuma lokacin ne Zahidaht ta zo ita da Kabir da Jawwad kuma a wannan zuwane ta tubure kan bazata koma ba. Duk da cewar iyayan nasu basu tambayeta dalili ba, amma kuma ramarta ta matuΖ™ar tsoratasu. Ta Ζ™anjame kamar ba wace ta bar nijeriya ba. Kowa ya goyi bayanta, da aka matsa mata da san sanin dalili sai ta nuna musu ta fison kusanci da ahalinta ne. Mahaifiyarta kam bata yadda ba, binta kawai take da ido tana fatan ta sami sararin keΙ“ewa da ita.

Dole Kabir yana ji yana gani ya haΖ™ura ya barta, sai dai bisa turasassawar mahaifansu ya soma neman transper domin fara aiki a Ζ™asarsa sakammakon ya kammala karatunsa har ya soma aiki. An yi cuku-cukun karΙ“ar transper zuwa Ζ™arshan shekara ya tattara ya dawo. Dawowarsa yasa ya rage yi mata abubuwa da yawa saboda idanun yan uwa. Sai dai kuma ta yi nadamar  dawowawarsu gaba Ι—aya, domin  sai da ta zama Ζ™ofar data bashi lasisin Ζ™untata rayuwarta. Ta hanyar kisan mummuΖ™en da yake yi mata.Yusuf ya yi wa Labiba abin da bata taΙ“a zato ba, ranar data cika sati aranar ya yanka Ζ™aton ragonsa ya kuma shaidawa duniya ya maidawa Ι—ansa sunan Baba Ι“aure. Kowa ya yi matuΖ™ar farinciki musamman Amne, nan da nan wasu suka soma kiran yaron da suna Khalifa. Wasu kuma Yusuf takwaran Yusuf Ι—an Yusuf jikan Yusuf, amma kuma masu kiransa Baba baure sun fi yawa. Sai dai Labiba ta fututtuke tace Khalifa sak za a kira mata Ι—a.

Kwanci tashi mutuwar ta bi jikinsu gaba Ι—aya, sai dai alhini irin na sabo. Amma banda Baba Ɗangaladima dan shi kamar zuΖ™arsama ake kullum cikin rama. Haka su Yusuf zasu tasashi gaba su yi ta bashi baki.

Lokacin da Labiba ta koma gidanta sai ya zamana Ζ™azanta ta Ζ™aru, da an yi magana ta hau zuba rashin kunya tana faΙ—in ba a tausayinta ba a ganin gwarnai ta yi. Tun Yusuf na kauda kai har ya soma kai Ζ™ararta wajan mahaifinsa. Saidai kullum bayan Labiba yake bi, bawai dan wani abu ba, sai dan tuna cewa kadda dangi su ce Ζ™asa ta rufewa mahaifinta idanu ana yi mata badaidai ba.

Shi kuma duk Ζ™anΖ™antar laifi idan ya aikata mata, zata kira Amne da Khamis ta shirya Ζ™arya da gaskiya su kirashi ba tare da jin ta bakinsa ba su ci mutuncinsa son ransu. Yusuf sarkin haΖ™uri sai dai ya bada haΖ™uri, amma kuma abin na cin ransa gaba Ι—aya ya zabge ya rame. Ga wata uwar Ζ™asumba da ya ajiye, haka kuma fatarsa ta Ζ™ara duhu idanunsa sun zurma ciki sossai sun fidda wani kogo daya Ζ™ara fito da aihinin sirrintakar hancinsa.

Cikin Ζ™anΖ™anin lokaci raini mai Ζ™arfi ya shiga tsakaninsa da Labiba, bata shakkar ta zageshi a gabansa hakama gaban abokansa da Ζ™awayenta. Har abin tinΖ™aho ya zamo mata sai yadda ta ke so ake yi agidan. Abinci idan ya kawo mata Ζ΄ar hausa ba zata dafa ba, idan kuma Ζ΄ar gwamnati ce to ba zata girka mai daΙ—i yadda zata yi armashi ba. Hasalima abinci Ζ™arshansa babbakewa cikin tukunya musamman data soma chats ya zamana yana Ζ™ara Ι—auke mata hankali. Sangarta kala-kala, wandunan kashin yaro kuwa bata wankewa sai sun taru ta kule a leda ta watsar a bola. A haka Khalifa ya shekara Ι—aya da watanni Ummi kuma nada shekaru biyu da watanni.

***

MUSABABI.

A haka zamansu ya miΖ™a, sai dai yau da gobe taΖ™i gaban wasa. Duk Ζ™umbiya-Ζ™umbiyar Yusuf sai da dangi suka fahimci baya jin daΙ—in zama da mstarsa. Saida ya zamana babu wanda bai san matsalarsu ba. Duk inda aka zauna taro manya ciki kan Ζ™oΖ™arin bata shawara, musamman kan Ζ™azanta amma Ζ™arshe sai dai ta zagesu tas ta Ζ™ara gaba abinta. Cikin tsakanin aka yi musu rabon gadonsu, dukiyar da aka samu ta girgiza mutane da dama, basu taΙ“a tsamanin dukiyar mahaifin nasu takai hakanba.

Kowace Ι—iya mace saida ta tashi da naira miliyar arba’in da gida guda Ι—aya banda kadarori. Shi kansa Baba Ɗangaladima abin ya shallake tunaninsa, bai taΙ“a kawo Ι—an uwansa ya kai haka ba. Su Khamis nan da nan aka shiga faccaka da kuΙ—i, masu wayau ciki suka kafa sana’a wasu kuma suka shiga sharholiyarsu yadda suka ga dama.

Zahidaht na Ι—aya daga cikin waΙ—anda suka bada dukiyarsu a juya musu, Ζ™warai taso bawa Yusuf ya juya mata domin shi ne koma baya acikin ahalinsu amma mahaifiyarta ta fututtuke ta nuna bata lamunta ba. Sai dai hakan baisa ta fasa niyyarta ba, a Ι“oye ta siya masa sababbin kekuna aka gyara shagon dayake haya aka zuba masa su. Tare da bashi naira dubu hamsin ya kafa jarin kayan Ι—inki a shagon. Ranar ya yi kuka irin wanda bai taΙ“a yi ba, ta kuma roΖ™i alfarmar ya zama sirri daga ita sai shi da mahaifinsa da yaya Asabe suka sani. Sauran kuΙ—in kuma ta dunΖ™ule ta miΖ™asu ga mijin Yaya Asaben ta ce ya juya mata, anyi takarda da shaidu da komai kuma gaban jagororin gidan.

Wannan abu data yi ya Ζ™untata ran Kabir kamar ya yi hauka, domin shi ya baje sai lallaΙ“ata yake yi, salon kulawa kala-kala yana tsarin ta gama zuwa hannu har mota sai ta siya masa. Aikuwa ranar data miΖ™a dukiyarta ga Yaya Adam kaΙ—an ne bai yi hauka ba, ga Jawwad na Ζ™ara tunzurashi. Ranar yini suka yi a club ya sha syrup ya yi tattul ya nufo gida, duka ya yi mata na fitar hankali tare kyakkyawan gargaΙ—i kan ta amso kuΙ—in amma ko a Ζ™afar silifas Ι—inta kuma ba wanda ta kai wa Ζ™ara. Ta yi alΖ™awarin tunda Yaya Asabe bata goyi bayanta ba, ba zata taΙ“a buΙ—e baki takaiwa wani Ζ™ararsa ba. Duk ranar da ubangiji ya nufa zasu fuskanci wa suka bata matsayin miji to zasu fuskanta ba tare da takai Ζ™ara ba. Ƙila hakan ya ankarar da su KUSKURAN da suka tafka daga su har ita. Musamman data ga yadda lamarin Labiba da Yusuf yake tafiya sai ya Ζ™ara mata Ζ™arfin guiwar cewa, ko ta kai Ζ™ara dai bayan Kabir za a bi.

Ɓangaren Labiba kuwa, duniya sabuwa dal gareta, gidan da suke zaune ciki nan ne ya zama gadonta. A ranar da aka mallakamata shi a ranar ta tsira Yusuf ya bata takardunsa domin suna hannunsa. Fes ta ke jin ranta. Cikin Ζ™anΖ™anin lokaci ta dinga wasa da dukiya. Gwala-gwalai ta siya, a je gidan biki a yi ta iyayi ana Ι—aga kai. Ta sake kayan Ι—aki biy biyu, wato ya zamana two bedroom. Sai dai kayan basu je ko’ina Ζ™azanta ta nakasusu, musamnan da ya kasance na dubai ta saka. Su kuwa suna buΖ™atar kulawa. Haka kayan kallo da duk wasu nau’in kayan amfanin gida ta sauyasu kamar wata amarya ga danΖ™areriyar waya.

Ƙawaye kansu sababbi ta sake Ζ΄an yayi. Ganin tana Ι“arnar kuΙ—i ne, Amne ta Ζ™wace kuΙ—inta ta damΖ™awa Khamis yayanta aka soma juya mata da yake harkar gwala-gwalai yake yi. Kwatsam Zahidaht ta je mata da shawara kan me zai hana ta ba wa Yusuf kuΙ—inta ya juya mata, ranar da uwaka ubanka suka rabu. Har tana goranta mata me ya hana ita ta ba nata mijin tata dukiyar? Wannan abu ya ba ta mamaki Ζ™warai da gaske, domin me Ι—aki shi ya san inda yake masa zuba. Ta sha alwashin badan alΖ™awarin da ta yi wa zuciyarta ba, da sai ta bambancewa Labiba tazarar dake tsakanin Kabir da Yusuf.

A taΖ™aice dai Labiba sai ta miΖ™e Ζ™afa ta sake sabon zubin rashin mutunci. Girki bata yi saita ga dama, take away take yi ita da yaranta. Hidimar dangi kuwa idan ana yi matuΖ™ar bata Ζ΄an Ι—akinsu bace sai ta mula take zuwa. Yusuf ya zame mata hoto bashi da Ζ΄ancin tsawatar mata zata ci zarafinsa, agaban Ζ΄aΖ΄ansa. Tun Ummi bata fuskanta har ta soma fuskanta domin ta yi wayau ta shiga shekara ta biyar Khalifa kuma huΙ—u. Idan ta zauna a waje sai ka ji tana,

“Ummunmu tana sa babanmu kuka!”

Idan yaro ta samu suke wasa sai dai ka ji tana tambayarsa,

“Mamanka tana sa babanka kuka?”

Haka ma idan babbane ba take masa wannan tambayar. Ranar data yi wa Nazira tambayar a gaban Yaya Asabe ba Ζ™aramin kaΙ—uwa Yaya Asaben ta yi ba. Ta ja Labiba ta dinga yi mata faΙ—a tare da nusar da ita KUSKURAN da take aikatawa na yin komai gaban yara. Ta nuna kamar ta ji, amma koda suka dawo gida mugun duka ta yi wa Ummin wanda ya fusata mahaifinta ya zage Ζ™arfinsa ya naΙ—a mata nasa dukan. Ai kuwa ta ji jiki matuΖ™a.

***

Kamar yadda muka sani a al’ada Ζ™aratowar azumi kowane magidanci yana hoΙ“Ι“asa a gidansa. Hakama Yusuf ya kasance mai tsayuwa tsayin daka wajen ganin ya wadata gidansa, sai dai wai a banza man kare in ji Ζ΄an magana. Ko kaΙ—an bai Ι—aΙ—a Labiba da Ζ™asaba hasalima a raine ta karΙ“i kayan. Har aka yi azumi huΙ—u biyar zuwa goma bai san samun abin buΙ—a baki daga gidansa ba, sai dai Asiya yarinyar da yake haya a shagon gidansu tana Ζ™oΖ™arin kawo masa kunu Alla bashi shi kuma yana siyen Ζ™osai da dabino. Sossai yake mutunta Asiya da mahaifiyarta bisa karamcinsu.

Lokacin da aka shiga hidimar sallah sai ya zamana aiki ya soma rincaΙ“ewa Yusuf, Ι—inkuna sun soma yi masa yawa baya samun dawowa da wuri, amma abin takaici duk lokacin da zai dawo sai ya samu ta garΖ™ame gida da sakata. Idan ya yi magana kai tsaye zata ce,

“Gidanka ko nawa?”

Tun ba ajin kansu game da hakan har ya kai ga ya kai Ζ™ararta, sai dai ga mamakinsa kadda baki Baban nasa ya yi ya tambayeshi,

“Yusuf tun nawa ka ke fita?”

Ya bashi amsa da cewar,

“Baba asuba ne”

“Ka dawo nawa”

Sai da ya yi jim, sannan ya amsa,

“Ina kai biyu saboda yanayin aikin namu!”

Kai tsaye mahaifin nasa ya maida dubansa kanta,

“Labiba Ζ™arfe nawa ki ke so ya dawo?”

Babu kunya ta amsa,

“ko bai sha ruwa gida ba Baba kadda dai ya wuce tara!”

“Yusuf”

Mahaifinsa ya kirashi da kaushin murya, ya amsa kansa a Ζ™asa yana jin wani irin raΙ—aΙ—i da Ι—aci tun daga Ζ™asan zuciyarsa,

“daga yau idan ka wuce tara a waje Labiba zata rufe gidanta!”

Ɗas! Gabansu ya faΙ—i su duka, Labiba maimaita kalmar take cin ranta,

‘Gidanta! Gidanta!! Gidanta!!!’

Tana ji kamar Baban magana ya faΙ—a mata, amma suita dake tare da yi masa godiya suka nufi gida. Tun daga wannan rana Labiba ta sake samun lasisin cin fuskar Yusuf son ranta. Haka aka kusa gama azumi gaba Ι—aya yana kwannan shago, ya zamana tun kafin maΙ—inka su soma kwanan shago shi ya soma. Saboda idan ya dawo, sai ya shefe mintuna sittin yana bugu da kiran waya amma ba zata ko Ι—aga ba. Kuma ba zata buΙ—e masa ba.

Post a Comment for "WATA MACE CHAPTER 3 BY SANA S MATAZU"