Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

WATA MACE CHAPTER 2 BY SANA S MATAZU

WATA MACE CHAPTER 2 BY SANA S MATAZU

                   Www.bankinhausanovels.com.ng 

Kamar yadda me karatu ya sani a baya, Yusuf Ι—a ne ga Baba Ɗangaladima, abin soyuwa ga kowa tun yana Ζ™arami haka har girmansa. Sai dai Yusuf ba shi da nasibi akan komai. Duk Ζ™aunar Baba Ι“aure na Yusuf ya yi zurfin karatu abin ya faskara. Sau biyar yana faΙ—uwa jarrabawar gama secondary Ζ™arshe dai sai Jawwad ne ya zana masa. Shi ma ba asami wani abin kirki ba. Hakan yasa Baba Ι“aure ya ja shi jikinsa ya Ι—orashi harkar kwangilolinsa. To shi ma dai tana kasa tana dabo. Yau riba gobe faΙ—uwa, babu wani cigaba da aka samu. Daga faΙ—uwa sai ayi aiki a sami matsala. Gona kuwa ko ya noma ba a samun abin kirki. Akasari ma

Ζ™wari ne suke cinye shukar tun kafin ta yi nisa. Tun abin baya damunsu har ya soma damunsu. Kowa a zuri’arsu yasan da wannan TAMBARI a tare da Yusuf.

Gori daga shi har mahaifiyarsa suna shan sa, sai dai kasancewarsu mutane masu haΖ™uri ko Ι—aga kai basa yi bare su tanka. Tun ana yi a bayan idanunsu har ya kai ana yi gabansu. Sai ya zamana Yusuf ya soma ja baya da Baba Ι“aure sossai. Ya sha ganinsa idan zai fita yana sa yara nemansa haka zai laΙ“Ι“e saboda mudun suka fita tare abu ne mawuyaci bai bashi kwangila ba, kuma ba a samun nasara sai faΙ—uwa shi yasa ya zaΙ“i nisa da shi fiye da kusancinsu. Ya fi ganewa ya fita ya yi buga-bugarsa kamar ba Ι—an cikin Ι—an saΙ“alo estate ba. Bai cika shiga cikin Ζ΄an uwansa samari ba, rayuwarsa ya ke yi shi kaΙ—ai. Kama daga kan dako, aikin gini koyon Ι—inki babu wanda ba ya yi, duk kuma abin da ya samu yakan yi Ζ™oΖ™arin ya raba ya siyi wani abu ya kai cikin gidan. Wannan na Ζ™ara masa martaba da mutuntaka sossai a idanun masu mutuntakar gida.+

***

Zahidah Ι—iya ce a gidan Baba Ι“aure. Yarinya ce mai tsanin natsuwa da haΖ™uri ga sanin yakamata. Akasarin rayuwarta tafi yinta ne Ι“angaren Baba Ɗangaladima wajen Hajiya Hauwa. Ko kuma gidan surukarta Yaya Amina matar Adam babban Ι—anta. Hakan yasa suka shaΖ™u matuΖ™a da ita, hakama Yusuf akwai shaΖ™uwa tsakaninsu. Tana da kaifin Ζ™waΖ™walwa sossai ga wayau da kuma girmama manya. Hajiya Hauwa ta sha hasashen a haΙ—a auranta da Yusuf kamar yadda aka saba haΙ—a auratayya a danginsu. Sai dai da yake yanzu zamani ya ja, sukan bari yaran su haΙ—a shekaru shatakwas cif lokacin sun kammala karatun gaba da primary. Badomin komai ba sai dan Ι“arakar da suka soma samu na shigowa cikin ahalin na dojewar wasu a wajen haΙ—in. Alla bashi sai yaran su haΙ—a kawunansu da kansu,  su kuma su aurar dasu amma babu batun ka aure wata a waje. Su kuma mazan lokacin ko sun gama karatu ko suna dab da gamawa.

Wannan sauyi da aka samu Ζ™warai shi ya daΖ™ilar da burinta na son a haΙ—ata da Yusuf. Zahidah mace ce mai Ζ™ulafuci, idan tasa abu aranta sai Allah. Shiyasa kaf sa’aninta ta rugasu kammala karatunta na gaba da primary. Tsabar Ζ™oΖ™arinta, bata isa zana jarrabawa ba, aka yi mata jumping (tsalake). Haka kuma ta haΙ—a saukarta hadda. Tana da burin cigaba da karatu sossai. Kowa ya son burinta, dan da ya wa agidan sukan yi mata laΖ™abi da *Ζ³AR BOKO*. Kuma takan amsa kai tsaye ba tare da shakka ba, domin tasan akwai tsarin cigaba da karatu bayan aure acikin zuri’arsu.

Mace ce mai tsanin tsafta da son kwaliya, Ζ™unshi kafin wani ya disasshe anyi mata wani. Saboda zaryar gidan Ζ™unshi ta koyi yankan salatif kala-kala wanda har ya zame mata sana’a kuma take samu da shi matuΖ™a. Dan ko a iya cikin zuri’arsu kuΙ—in da ta ke samu da salatif Allah Ya yi yawa da su. Wasunsu na ganin kamar wahalar banza take yi, amma ita kaΙ—ai take sanin nishaΙ—in da take ji a tare da ita idan tana aikinsa. Domin ta haΖ™iΖ™ance zana shi baiwa ce kuma wanda ubangiji ya so yake bawa. Dan haka tun abin yana damunta har ya bar damunta. Masu manyan sana’ar da yawa sun sha zuwa wajanta rancen kuΙ—i, takan yi murmushi idan ta tuna su ne gaba wajan kushe hikimarta.

STORY CONTINUES BELOW

***

Jawwad shi ne kaΙ—ai Ι—a namiji a gidan Baba Iro. Baba Iro kaf Ζ΄aΖ΄ansa mata ne, ya yi aure-aure ya kai goma domin Allah Ya bashi Ι—a namiji amma duk matan da ya aura basa rufe wata goma suke haihuwa. Sai dai kash babu wadda ta haifa masa burinsa sai Ζ΄ar uwarsa Sadiya. Wadda kafin ya karΙ“i auranta an sha Ζ™warbai da shi. Lokacin da ta haifi Jawwad babu irin Ι“arnar kuΙ—in da bai yi ba. Sadiya tana takaicin yadda Ζ™iri-Ζ™iri ya ke nuna ya fi son Ι—a namiji akan mace. Duk da kasancewar Jawwad ya taso a tsakiyar mata Ζ΄an uwansa hakan bai hanata Ζ™oΖ™arin bashi kyakkawar tarbiya ba. Sai dai kuma mahaifinsa ya Ι“ata komai ta yadda ya dinga fifitashi kan komai a kan Ζ΄an uwansa. Duk wata kaddara da ya mallaka tun Jawwad na Ζ™arami ya maida sunansa akai.

Duk inda zashi to tare da shi yake tafiya. Ζ³an uwansa sun sha nuna masa kuskuran abinda yake yi amma Ζ™arshe da faΙ—a suke rabuwa. A haka yaro ya tashi a sangarce, babu kwaΙ“a babu harara. Jawwad Matashi ne mai jini a jika kuma Ι—an Ζ™walisa.  Sai dai tun tasowarsa fitinanne ne baya jin magana. Tun yana shekara goma sha takwas ya Ζ™ware a bin mata da kuma tare yara a hanya yana Ζ™waΖ™Ζ™ularsu. Wannan kowa ya san shi da wannan TAMBARIN a zuri’arsu. A silarsa iyayansu suka so dawo da al’adar aurar da yaransu suna shekaru goma takwas maza amma hakan bai samu ba. An yi masa aure ya kai sau uku amma kuma baya shafe wata biyu da matan yake sakinsu. Hakan yasa aka haΖ™ura aka zuba masa ido ana binsa da addu’a domin sun haΖ™iΖ™ance duk zuri a sai a sami wari guda.

***

Kabir ya fito ne daga zuri’ar Baba Muttaka Ι—an uwargidansa ne Hajiya Fure. A zuci fir’una a fuska Musa kenan. Kafatanin hallayar Jawwad irin ta Kabir ce sai dai kuma ga wanda ya san baΙ—inin Kabir kenan ga wanda yasan zahirinsa kuwa ba zaka taΙ“a cewa yana da wani aibu ba. Yana da suffar kamala sossai, akwai shi da iya taku da nutsuwa ga tausassa kalamai. Idan yana magana da kai dole ka ji ya burgeka, duk wani salo na tausasawa ya sani. Allah ya bashi kaifin fikra da balagar harshe. Shi yasa Ζ΄an mata da yawa suke rubibinsa. Akwai masu kuka akansa.

***

Labiba, Ι—iya ce ga Baba Ι“aure kuma ita ce Ζ™arama a gidan cikin mata, sai dai mace ce me ji da kanta. Ζ³ar Ζ™walisa ce ta Ζ™in Ζ™arawa. Bata da kunya ko kaΙ—an, bata ragawa na sama da ita haka ma Ζ™ananun dake Ζ™asanta. Yanzu yaro zai mata abu bako kunyar idon mahaifiyarsa zata kwafΙ—eshi. Gata gaΙ“uwa ko kusa bata iya magana ba, duk yadda tazo bakinta haka zata furzota ba tare data taunata ba. Ba namiji ba hatta mace Ζ΄ar uwarta takan jinjina wautarta idan ta yi wata maganar. Bata ganin kowa da gashi musamman yadda take la akari da mahaifinsu ne ginshiΖ™in *ƊAN SABALO ESTATE*. Sangarta take zubawa son ranta kuma mahaifiyarta na Ι—aure mata Ζ™ugu.

Labiba baΖ™a ce amma kuma ta kwaso kyawun mahaifiyarta wadda ta kasance Ζ΄ar asalin garin sumalia. Tana da kyawu daidai gwargwado. Ga kuma cikar hallita. Duk wata budurwa mai ji da kanta a estate Ι—insu bata kama Ζ™afarta ba. Duk gayun Labiba bata san idan ta cire kaya ta sauya ta Ι—auke ba, mahaifiyarta ko kuma yaran da ake riΖ™o a Ι—akinsu sa’aninta wanda Ι—akin kwanansu Ι—aya su suka san wannan hidimar. Bata san ta yi kwaliyya ta kwashe kayan data yi amfani da su ba. Bata san ta ci abinci ta Ι—auke kwano ba.

Tun suna kai Ζ™ara har suka haΖ™ura domin Amne bata goyon bayansu. Haka batasan wanke kai ta yi kitso ba, zadai ta kimma acuci akanta yana sumbuΖ™a wari ba damuwarta bace domin zata buleshi da turare. Babu tazara tsakaninsu da Zahidah sa’anin juna ne. Sai dai kowa hidimarsa yake, idan sun haΙ—u to anzo taron cikin gida ne ko kuma islamiyya domin Zahidaht bata son raini ko kaΙ—an. Bayansu akwai Ζ΄an mata shida masu irin shekarunsu. Husnah, Amira da Maryam  da MashiΙ—a da Zuhuriyya sai kuma Kamila.

***

Kwanci tashi babu wuya wajen ubangiji, Ζ™arshan shekara na gabatowa haka kuma batun shirya-shiryan aurar da Ζ΄an matan *ƊAN SAƁALO ESTATE* ya soma kankama. Ko wace nada zaΙ“inta in ka Ι—auke Zahidaht da Labiba. Haka ma matasan kowa da zaΙ“insa idan ka Ι—auke Kabir da Yusuf da kuma Jawwad. Wanda Jawwad da Kabir ana dakon fitowar jarrabawarsu ne, da suka zana ta zangon karatunsu na biyu. Awannan lokacin da yawa basa lissafi da Jawwad a auran saboda bama shi da wadda take sauraronsa cikin zuri’arsu. Kasancewar a lokacin ya saki mata guda biyu, Ι—aya Ι—iyar Baba Khamis Ι—aya kuma Ι—iyar Baba Muttaka. Wanda abin har ya so taΙ“a zumuncinsu. Kasancewar duk matan da ya saki na baya sun yi aure amma waΙ—anan sai auran nasa ya zame musu TAMBARI kwata-kwata babu mai sha’awar auransu cikin zuri’ar.

Kabir kuma yana Ι—aya daga cikin waΙ—anda gwamnan dake ci alokacin, ya nemi alfarmar a barshi ya tafi Ζ™aro karatu. Baba Ι“aure bazai iya karya wa gwamna bille ba, abokinsa ne tun yarinta hakan yasa ya amince da buΖ™atarsa ya tara sauran Ζ΄an uwansa suka yi shawara aka haΙ—a da Jawwad aka biya masa suka tafi. Karon farko da wani matashi wanda bai taΙ“a aure ba a zuri’ar ya tafi Ζ™aro karatu, kuma ba cikin Sakwwato ba Ζ™asar waje. Daidai lokacin da ake shirin aurar da Ζ΄an matan gidan su kuma sun zo gida ne hutun jarrabawa. Iyaynsu kuma suka yanke a dakata jiran jin yadda sakkamakon ya yi kyau, alla bashi sai a Ι—aura auren su juya da matan.

Wannan fifiko da suka samu ya Ζ™arawa Jawwad da Kabir girman kai da kuma samun wani fili a zuΖ™atansu na cewa su Ι—in sun kai. A Ι—age suke kallon kowa, sun raina da yawa cikin matasan gidan musamman Yusuf. Babu yadda Jawwad da Kabir basu gwada hikimarsu ba, ko Labiba zata amince da buΖ™atarsu domin suna ganin su suka dace da Ζ΄ar Ζ™walisa irinta amma ta shafawa idonta kwalin audi ta nuna bata san suna yi ba. Ɓangaren Jawwad dama shi soyayyar zamani yake biΙ—a, daya ga ba fuska sai ya haΖ™ura. Shi kuwa Kabir zahiri da gaske yake son auranta shi ma dai babu fuska dole ya haΖ™ura.

Daga gefe guda kuma, Zahidaht ta makance akan soyayyar Kabir, ba dan komai ba sai dan tunaninta shi ne daidai da ita. Ɗan gayu ga Ζ™walisa ga kuma ilmi. Koba komai zai tuntuΙ“awa mafarkinta tabbata na cigaba da karatu. Sai dai ta kasa tunkararsa koda wasa, domin baya wasa dasu kwata-kwata. Tun ana zunΙ—enta a gida taΖ™i fitar da tsayayye, duba da yadda Salihu yake sonta har aka soma yasar musu da habaici a tsakar gida ita da mahaifiyarta. Hankalinta ya tashi matuΖ™a, musamman da mahaifiyarta ta soma sakata a Ι—aki tana nuna mata ta rufa mata asiri ta karΙ“i tayin Salihu. Sossai ta shiga damuwa, zuciyarta ta soma aminta da karΙ“ar Ζ™udurin mahaifiyarta kodan sama mata natsuwa.

Ɓangaren Yusuf kuwa baya kula kowace mace cikin ahalinsu da sunan so, yana ganin wace ce zata so shi a hakansa? Hakan yasa koda wasa bai Ι—orawa kansa kula *WATA MACE* cikin zuri’arsu da sunan soyayya ba, in ka Ι—auke gaisuwar mutuntaka. Hakama mahaifiyarsa tana goyon bayansa. Mace Ι—aya ce ya ke hango nutsuwarta ta kwanta masa, sai dai koda wasa baya tunanin zata karΙ“i tayinsa shi yasa ya haΖ™ura.

Gaba Ι—aya ya maida hankalinsa ne ga sana’ar hannu da kuma nacin karatun al-Ζ™ur’ani. Kaf zuri’arsu babu mai baiwar karatunsa, shi yasa ya ware aji guda na Ζ™anannun yara masu rasowa yana koyar dasu Ζ™ira’a. Kuma alhamdullilah, duk wata gasa ta karatu acikin garin Sakwato matuΖ™ar aka Ι—auki yaran da yake koyarwa to *ƊAN SABALO* sukan yi nasara. Ya goge a fannin sanin alΖ™ur’ani da Ζ™a’idojinsa.Safiyar wata Asabar garin Sakwato an tashi da wani irin muku-mukun sanyi. Labiba na Ζ™unshe cikin lallausan bargonta, gaba Ι—aya Ζ΄an Ι—akin da suke kwana tare sun farka, wasu na Ι—akin girki wasu kuma na cikin gida. Wasu kuma da yawa suna islamiyya. MiΖ™a ta yi tare da sako Ζ™afaffunta Ζ™asa, Ι—an turo baki ta yi ta yatsina fuska. Kai tsaye banΙ—akin Amne ta shiga, cikin mintun ta fesa wankanta tare da wanko baki ta fito tana taku Ι—ai-Ι—aya. Sai da ta shari lokaci wajen shiryawa daga bisani ta fito babban fallo. Bata sami kowa ba hakan kuma bai dameta ba, duk da tasan ta karya dokar zuwa islamiyya haka ta kaΙ—a kai ta tafi bayan ta karya kumalo.

Tana gab da shiga makarantar gabanta ya yanke ya faΙ—i, ba dan komai ba sai dan tunawa da yau kowace rana ce. Ilai kuwa tana saka Ζ™afa cikin makarantar ta haΙ—a idanu da mahaifinta. Harara ya wurga mata ta sune kai Ζ™asa domin tasan laifinta. Ita shaf ta manta yau ne Ζ΄an ajin Zahidaht da kuma ajin Yusuf suke gwajin gasar karatu, Ζ™a’idar islamiyyar ne duk Ζ™arshan wata sukan shirya gasar karatu daga wannan aji zuwa wannan aji. Ajin da ya yi nasara zai kara da dukkan ajujjuwan idan ya yi nasara shi ne ajin da zai jagoranci estate Ι—insu a gasar da suke fita ta Ζ™arshen shekara. Da babu abin da zai sa ta shigo makarantar ma, saboda tasan rana irin wannan tana haΙ—a duk wani uba na cikin zuri’arsu. LallaΙ“awa ta yi zata zauna sai jin sautin muryar mahaifinta ta yi,

“Yusufa ga Labiba can yi mata bulala!”

Da hanzari ta Ι—ago kanta, gaba Ι—aya sai ta muzanta yadda idanun sa’aninta na yawo a kanta. Har ta hango Husnah Ι—iyar Baba Mu’az da Maryam suna Ζ™unshe dariya. Wani takaici ya kamata, kwata-kwata ta tsani abinda zai muzantata cikin sa’aninta. Ga mamakinta sai ta riski sautinsa cikin sanyin da ya zame masa Ι—abi’a,

“Baba ai Labiba bata makara, ayi mata uzuri”

Sai ya Ι—auke kai ya cigaba da abinda yake yi, kamar ba shi ya yi furucin ba. Gaba Ι—aya kuwa su Husnah suka rakashi da idanu suna mamakinsa. Saboda sun sa yadda take kayawa tsakaninsa da ita matuΖ™ar ya daketa shi yasa ma ya sahalewa kansa dukan nata.

“Bani bulalar!”

Ya furta a fusace, jiki a sanyaye ya miΖ™a masa, da kansa ya taso har inda take ya yi mata bulala goma, lafiyyayu. Tun tana daurewa har ta soma kuka don ta tsani duka. Ai kuwa filin wajen ya yi Ι—if ana jin shassheΖ™ar kukanta. Sai ajiyar zuciya take saki. Daidai lokacin Kabir da Jawwad suka Ζ™araso wajen, akan idanunsu aka yi komai har gwalo ya yi mata da suka haΙ—a idanu da shi.

Iyayyen suka shiga gaisarwa Ι—aya bayan Ι—aya, har suka zo kan Baba Ι“aure idanunsa akan Jawwad ya sha aski irin wanda ake kira hana sallah. Ga uban zanzaro da Ζ™aramar riga iya Ζ™ugu. Kabir kuwa shigar shadda ya yi da hula zanna bukar suna taku Ι—aiΙ—ai. Yana shirin tanka musu ne daga gefe kuma cikin taro, aka gabatar da Zahidaht domin gabatar da buΙ—e taro da karatun alΖ™ur’ani. Wannan dalili ya dakatar da Baba Ι“aure daga Ζ™udurinsa na hukunta kowannansu, sai dai ya Ζ™uresu da idanu yana ajiye kowanensu a hukuncin da ya ke hangen ya dace da shi ciki kuwa hadda Zahidaht da sautin karatunta ya dira a kunnunwansa cikin taushi da nutsuwar murya.

Ɓangaren Labiba kuwa, bayan ta gama shan kukanta duk fuska ta dame da kwaliya. Da mamaki ta dinga satar ajiye kallonta a saitin Yusufa, ba yau ba ya saba tareta a makara ya yi mata alfarma ba wai saboda wani abu ba. A rayuwar Yusuf ya tsani ya daki yarinya ta tafi tana yi masa Ζ™unΖ™uni. Ita kuma Ι—abi’arta kenan, duk da cewa bashi da zafi kan sauran Malam amma ya salaΙ—ewa kansa dukan Labiba tunda ya fahimci bata da kunya. Amma bata taΙ“a kawo zai tsallake umarnin mahaifinta a kanta ba. Kanta a Ζ™asa har aka gama taron baki Ι—aya, Ζ΄an ajin Yusuf ne a kan gaba sai kuma na Zahidaht da suke bi musu baya.

Ba a tashi taro ba, sai da Baba Ι“aure ya sami matsaya kan hukuncinsa. Ya kuma yi na’am da hakan, karon farko da yake ji aransa zai karya dokar da suka gindaya a zuri’artasu. Iyaye da dama sun yi jawabi mai Ζ™ayatarwa, tare da nuna jin daΙ—i da kuma godiyarsu ga Yusuf. Daga bisani aka sallami kowa tare da kyaututtuka ga Ι—aliban da suka yi nasara. Sai kuma sanarwar Ζ™arshe ta taron family da za a gudanar bayan azahar.

Jiki a sanyaye Labiba ta miΖ™e zuwa cikin gida, bata yadda ta jera da sa aninta ba, tunda yau sun sami abinda suke so kanta. Da Kabir ta soma karo,

“Su Laby manyan mata!”

Ya furta yana dariyar shaΖ™iyanci, sunan da yake kiranta da shi kennan, kuma yara da manya sun kama, wasu kan ce Yaya Laby, wasu Anti Laby wasu kuma Laby Ι—in kai tsaye. To ita ma dake uwar iyayi ce sai take amsawa duk da Amne na masifar sunan. Bata biye masa ba ta yi gaba abinta. Sai dai kuma tana shiga babbar mahaΙ—ar shiga gidan ta sami su Husna ana hira da shewa, ana ganinta kuma aka yi Ζ™usu! Bata raba Ι—ayan biyu da ita suke, Ι—auke idanu ta yi ta hangi Zahidah na sawa Yaya Amina Ζ™unshi ta Ζ™arasa,

“Kai ya yi kyau! Zeedat zaki yi min ni ma?”

Ta furta tana tsaresu da idanu,

“Laby baki da kunya wallahi, ko ki gaishe ni kin wani tsayamana akai”

Ade ta furta tana zare idanu, yaya Asabe ta yi murmushi tana auna gajen haΖ™uri irin na matan yayyun nasu. Shiyasa duk Labiban ta bi ta rainasu bare kuma Amne na Ι—aure mata Ζ™ugu. Ilai kuwa, yaya Asaben kaΙ—ai ta gaisar, don duk tsaurin idonta tana raga mata, bata wasa da yaro gata da kyauta abin da bai rufe mata ido ba. Sai ma juyawa da ta yi, tana Ζ™ara nanatawa Zahidaht zata yi mata Ζ™unshi, ita ma dake Ζ΄an miskilancin na kanta kai kawai ta Ι—aga mata. Be dameta ba, ta wuce tana jin yadda suke mata cari. Tana shiga ta sami Hajiya Muwaddah da Amne na haΙ—e kayan da za a raba wajen taro na ci.

Zama ta yi ta jefa hannu a robar cake ta hau tauna tana lumshe idanu, bata tantama wannan aikin Mamarsu Yusuf ne, shi yasa kullum take dakon zuwa gaisheta da safe ko ba komai takan fito da tsabarsu tunda sana’arta kenan kuma ta Ζ™ware sossai. Kamar an mintsineta ta turo baki, ta hau bawa Amne labarin abin da Babansu ya yi mata. Ai kuwa Amnen ta shaΖ™a, amma tasan ko giyar wake ta sha ba zata ce don me ba. Sabida ita kanta ya sha jan kunnanta kan makarar Labiba, duk cikin sa aninta ita kaΙ—ai ce bata yi sauka ba, saboda fashi da latin islamiyya. KaΙ—a kai kawai ta yi, Hajiya Muwwadah ta yi Ζ™wafa,

“Ina ma Yusufan ya bugeki da yagane!”

“Mama ai shi yana da kirki, ni ba ya dukana ba fa ko makara na yi a islamiyya. Shi kam matarsa ta huta wallahi yana da sanyin hali”

Karaf! Sautin maganar ya sauka akan kunnuwan Baba Ι“aure. Ita kuwa Laby tana furta hakan ta miΖ™e tana Ζ™oΖ™arin shigewa cikin Ι—akinsu, duk suka rakata da idanu.+

***

Gaba Ι—aya Ι—akin taron cike yake da ahalin gidan, Husnah da Maryam da Zahidah su ne suketa kujuba-kujubar gyara yaran da suka Ζ™i zama. Can Maryam da ta fisu rashin haΖ™uri ta ja Ζ™wafa tare da taune gefan bakinta,

“Wai ku mu kaΙ—ai zamu yi aikin nan ne, ina ce hadda Laby Baba ya haΙ—amu. Ita wata fi ne da duk lokacin da aka samu aiki sai ta noΖ™e?”

Zahidaht ta murmusa, tare da dafa kafaΙ—arta,

“DaΙ—ina da Maryam ragon azanci. Shin idan mun yi faΙ—uwa muka yi? Ita fa taga zata iya kowa da kiwon da ya karΙ“eshi. So hurry up mu yi abin da yake gabanmu”

Bata da yadda zata yi tunda Zahidah ta furta hakan, koba komai gaba take da ita. Kuma basu da tsarin raina nagaba cikin ahalinsu. Dan haka ta cigaba da aikin amma tana yi tana Ζ™unΖ™uni. A haka wajen ya kammala kowa ya hallara. Iyayye da jikoki da Ζ΄aΖ΄a babu wanda babu. Duk wurin da ka wulga hayaniya ce tare da tashin muryoyi ana hirar zumunci. Baba Ι“aure ne ya Ι—auki abin magana tare da yin gyaran murya, gaba Ι—aya wurin ya yi tsit!

Godiya ya soma yi ga ubangiji, daga bisani ya faΙ—i irin nasarorin da ahalin ya samu daga kowane Ι“angare. A hankali har ya gangaro kan maΖ™asudin taruwarsu, wato batun aure. Kowa ya nutsu ya kasa kunne yana sauraron bayaninsa, masu murna na yi akasin hakan kuma dai yana cikin ransu. Maganar daya furta ce ta Ι—auke jin wasu daga cikin mazauna wajen na Ι—an lokaci,

“Mun yanke zamu haΙ—a Yusuf da Labiba aure, Jawwad da Khamisa, da kuma Zahidaht da Kabir”

Dum! Sautin ya sauka a kunnuwansu, da fari kalon-kalo aka soma yi tsakanin, Amne da Hajiya Muwwadah. Haka ma tsakanin Yusuf da Ummunsa sai Labiba da take ji kamar almara. Wani irin yanayi ta sami kanta, ita ba farin ciki ba ita ba takaici ba. Haka dai tsaka tsaki, kafin daga bisani zuciyarta ta soma wassafo mata wasu cikin kamalolin Yusuf Ι—in. Sai ta sami kanta da sakin murmushin da ita kaΙ—ai ta san manufarsa. Ɓangaren Zahidaht kuwa, farin ciki ne ya mammateyeta tako’ina jinta take a duniyar sama. Gaba Ι—aya wajen ya Ι—auki kaburburi ana nuna jin daΙ—i,

“Alhaji ina da magana!”

Cewar Amne tana haΙ—e girar sama da Ζ™asa, ba ta saurareshi ba ta ci gaba,

“A tarihin wannan zuri’a kowa ya santa da auren zumunci amma kuma kowa ya san cewa auran na Ζ™uluwa ne bisa ra’ayin ma’auratan. Ta ya ya lokaci guda zaka dawo mana da shuΙ—aΙ—Ι—an tsarin da mun riga mun kawar da wanzuwarsa”

“Ƙwarai kuwa Hajiya Amne wannan abu dubawa ne, an tambayi yaran?”

Cewar Hajiya Muwaddah tana murmushin mugunta, duba da yadda taga kowa na bin Amnen da idanu. Dama haka ta saba ta hankaΙ—ata ta magantu akan kowace muΖ™ala ta gidan ita kuma tana daga gefe tana rura wuta. Baba Ι“aure kansa ya Ι—aure, a zuciyarsa ayyana ya aka yi rainin da matarsa ta yi masa ya kai haka? Har ya gindaya hukunci ta fito tana addawa da hakan. Lallai a wannan karon zai nuna mata so ba ya hana hukunta masoyi.

Ƙanannun maganganu ne suka soma tashi, Ζ™us-Ζ™us musamman Ι“angaren Kabir fiffiΖ™a ya soma yi yana baya son Zahidaht. Abin da ya haifar mata da faΙ—uwar gaba mai tsanani, tare da soma tunanin wace irin rayuwa zasu yi tare. Domin ta san tunda Baba Ι“aure ya furta, to fa ba fashi sai wani hukunci na ubangiji.

“Yusuf!”

Baba Ι“aure ya kira sunansa, murya a kausashe ga kuma Ι“arin ran daya gaza Ι“oyuwa a muryar tasa. Hakan yasa kowa ya shiga taitayinsa,

“Na’am Baba”

“Zaka iya auren Ι—iyata labiba?

Ya furta yana kafeshi da idanu take jikinsa ya yi sanyi, yana jin wani irin rauni yana kewayashi. A karon farko mutumin dake Ζ™umaji kullum wajen taimakon rayuwarsa yana neman alfarma mai matuΖ™ar wuya gareshi. Ya sani bashi da matsala da mahaifansa, haka karan kanshi zai iya karΙ“ar komai daga baban nasa amma kuma zuciyarsa ta fi tafiya kan tunanin Labiba da Amne fa?

“Idan baka ra’ayinta babu tursassawa tsakaninmu. Kaima Ι—ana ne kuma mafi soyu ba gareni. Zan iya jurar kowane sauyi daga gareka…”

Ya Ζ™arasa murya a raunane, domin ya gama karantar saΖ™on dake cikin zuciyar Yusuf Ι—in, yadda yake ganin kaf ahalinsu babu mai iya Ι—aukar tarangahomar Ι—iyar tashi guiwarsa a sanyaye take da gazawar wanda ya ta’alaΖ™a da burinsa gareshi.

“Baba ka yi haΖ™uri bazan iya…!”

Ɗas! Ɗas!! Ɗas!!! Gabansa ya tsananta faΙ—uwa sakammakon haΙ—a idanu da mahaifiyarsa.Baba ka yi haΖ™uri, ba zan iya musu bisa umarninka ba. Ko da baka bani umarni ba Labiba Ζ΄ar uwata ce!”

Gaba Ι—aya wajen ya Ι—auki kabbara, jikin Baba Ι“aure har tsuma yake tsabar farinciki. Labiba kuwa ji ta yi kamar an Ι—aureta da sassari, me kalaman Yusuf suke nufi, yana nufin sonta yake yi ko kuma manna masa aka yi?”

“Labiba kina son Ι—an uwanki?”

Muryar Baba Ɗangaladima ta ratsa cikin tunaninta, kanta a Ζ™asa bakinta ya yi nauyi. Ba zata taΙ“a iya kunyata mahaifinta ba duk rashin kunyarta. Sai kawai ta gyaΙ—a kai, wata irin ajiyar zuciya mahaifin nata ya sauke. Haka ma Zahidaht dai ta amince duk da tana tararrabin amsawar Kabir. Amma ga mamakinta koda aka tambayeshi kai tsaye ya amsa da yana sonta. Ta yi mamaki Ζ™warai da gaske. Shi kuwa Kabir ya amsane, ganin Laby ta kuΙ“ce masa kadda ya yi biyu babu kuma Zahidaht dai ba baya ba. Haka taro ya tashi rayukan wasu a daΙ—aΙ—Ι—e wasu kuwa sai ikon Allah.

Ba Ζ™aramin Ι“aci ran mahaifiyar Labiba ya yi ba, ga kuma Ζ™awarta na Ζ™ara ingizata. Tunda ta shiga gida take kai kawo tsakanin falo da cikin Ι—aki. A haka Labiba ta risketa, idanunta Ζ™ur a kanta tanata huci. A zuciye ta kai hannu ta damΖ™eta,

“Me yasa kika amince Labiba? Kinsan kuwa me ki ka aikata? Ki rasa wanda zaki aura duk taron samarin gidan nan sai wanda bai san ya tsinanawa kansa komai ba?”

“Amne ba zan iya kunyata mahaifina ba gaskiya, shi ma Yusuf Ι—in ai baya ra’ayina daga dukkan alamu, amma kuma ya kasa kunyata Abbana sai ni da ya haifa?

“Allah Ya yi miki albarka Labiba”

Muryar mahaifinta ta ratso kunnuwanta, dukkansu suka juya domin basu san shigowarsa ba sai sautin muryarsa. Ya ci gaba,

“Sa’adatu wallahi baki isa ki Ι“atamin rai akan auran nan ba, kin ji na rantse zan iya sahale naki auren da shikka uku Ζ™warara matuΖ™ar wata Ι“araka ta taso. A yanzu dai na gamsu Labiba ta haifu, dan haka duk wata Ι“araka da zata taso a nan gaba dake zan koka!”

Ficewa ya yi ba tare da ya tanka mata ba. Jiki a sanyaye suka wuce Ι—akunansu. Kwana Amne ta yi tana tunanin mafita, sai dai kuma furucin mijin nata ya Ι—aga mata hankali. Basu taΙ“a irin haka da shi ba, dan haka ta haΖ™ure zata bishi yadda yake so kafin ta sami mafita.

Furucinsa ya zauna mata a zuciya Ζ™warai. Bisa wannan dalili ne ya sa gaba Ι—aya ta Ι—auki Ι—amarar saki jiki a gudanar da sha’anin bikin ba tare da ta nuna bata so ba. Sai dai a Ζ™asan ranta bata da maΖ™iyi sama da Yusuf Ι—in. A gefe guda kuma Hajiya Muwaddah na Ζ™oΖ™arin zugata amma taΖ™i bata fuska kwata-kwata. Shi ma Ι“angaren Kabir duk tunaninsa ya gaza gano makusar Zahidaht, tako’ina mace ce ta tserewa sa a. Dan haka ya tattara ya haΖ™ura ya rungumi auren gadan-gadan, tare da nuna mata tsantsar kulawar data mantar da ita AUREN HAƊI za’ayi musu.

Yusuf ne dai kadaran-kadahan baya shigewa Labiba, ba kuma ya wasarerre da ita. Sossai Labiba ta saki jiki ta Ζ™ara fuskantar Yusuf Ι—in, sai ta ga ya yi dai-dai da ra’ayinta. Haka aka gudanar da biki hankali kwance, Kabir ya cale da amaryarsa ya cigaba da karatunsa haka ma Jawwad.

***

Zaman Labiba da Yusuf zamane me armashi, domin dai ta sameshi yadda take buΖ™ata fiye ma da tsamaninta. Duk wata hidima ta gida tare suke yinta, haka zai gama ya fita buga-bugarsa ya samo kuΙ—insa. Babu Ζ™yashi ko nawa zai samo to zasu Ζ™are ne a hidimar Labiba.+

Labiba ta sami yadda take so, tana burin auren miji bawan mace. Uwa uba kuma Yusuf mutum mai haΖ™uri, ga kawaici da kuma tsanin tsafta komai take so yana koΖ™arin yi mata shi koda kuwa ransa baya so. Ita ma kuma ta ajiye son jikinta, gidanta Ζ™was-Ζ™was irin na amare musamman idan yamma ta yi haka zata kunna tsintsiyar Ζ™amshi ya yi ta tashi. Kwanakin amarcinsu sun kafa tarihi mai girma a rayuwarsu, tare da alΖ™awarurruka wanda suka fi yawa sune yadda zasu kula da yara idan Allah ya basu.

Wata Ι—aya biyu uku, a hankali ya soma fuskantarta. Gaba Ι—aya malalaciya ce bata san aiki, ga shi kowace magana ta faΙ—o bakinta to zata yaΙ“a masa ba tare da la’akari da yanayinsa ba. Cikin wata biyar da auransu kayan Ι—akinta sun fita daga hayyacinsu. Ɗan wanka da kwaliya da Ζ™amsassa gidan da take yi duk ta watsar dama na marmarine. Haka Yusuf ya dinga Ζ™oΖ™arin gwada mata kuskuranta, abin da ya soma haifar musu da saΙ“ani kenan.

***

Kwanci tashi babu wuya wajen ubangiji. Suna shekararsu ta farko da aure ne al’amura suka soma ja baya. Bikinsu dama kafin azumine aka yi, basu da matsalar abinci sakammakon kayan gararta ga kuma kayan azumi da aka rarraba a ahalin nasu. Haka suka yi sallah kashirΙ“an cikin wadata ga Ι—inkuna da Yusuf ya zuba a sallar ya samu kuΙ—i sossai. A haka suka gangara babbar sallah ma ya yi Ι—inkuna babu laifi. Bayan sallah ne al’amuran suka soma ja baya, samunsa ya ragu sossai babu Ι—inki sai ya koma harkarsa ta leburanci. Kwatsam ciki ya bayyana a jikin Labiba, ita da shi gaba Ι—aya sun yi murna, haka suka dinga rainon abinsu. Da daΙ—i babu daΙ—i Yusuf yana Ζ™oΖ™arin faranta mata.

Tunda ta sami ciki ya hanata wanki, shi yake wanke musu kaya duka ya share gida ita kuma ta ji da hidimar girki duk da cewa idan ta dafa ba samun ciyuwa yake wajantaba. Matsalar da suka soma fuskanta gaba Ι—aya Labiba ta Ζ™ara Ζ™azancewa, ko ina zubar da miyau take yi, sai ya zamana Ι—akinta baya zaunuwa saboda Ζ™arni. Ga rainuwa ta masifa, komai ya kawo a wulaΖ™ance take karΙ“a tana mita. Baya ko Ι—aga kai ballantana ya nuna mata ya damu. Musamman da ya lura da yanayin da take ciki. Duk wata kulawa data dace da mai irin lallurarta yana Ζ™oΖ™ari sossai a kanta.

Ƙazantarta na damunsa musamman shi gwanin tsafta, haka zai zage ya gyara ko’ina. Ya sa turare amma kafin sati komai wajen zamansa daban. Ba ruwanta da idan ta cire kaya ta Ι—auke. Wasu lokutan hadda masu lema, sai Ι—akin ya dinga warin ruma. Haka ya yi ta yi mata uzuri, la’akari da masu juna biyu kan tsinci kansu a yanayin da ya fi natama. Dan haka ta miΖ™e Ζ™afa tana zuba taΙ“ara son ranta.

Cikin ikon Allah cikinta ya shiga watan haihuwa mahaifiyar Yusuf ta rasu. Mutuwar data girgiza kaf ahalinsu domin Hajiya Hauwa’u mace ce mai yakana. Bayan makoki da sati uku Allah Ya sauki Labiba lafiya ta sami Ι—iya mace. Ai kuwa murna wajen Yusuf kamar ya goyata, ranar suna yarinya ta ci sunan Hajiya Hauwa suke kiranta da suna Ummi. Baba Ι“aure da Baba Ɗangaladima basu bar Yusuf ya kashe taronsa ba, komai su suka yi tun daga hidimar haihuwar har zuwa ragon suna. Anyi suna da kwana biyu, Labiba ta dawo gida wanka. Amne ta zage ta kula da ita yadda ya kamata. Ummi yarinya mai haΖ™uri da saurin shiga rai, kowa na Ζ™aunarta kodan dattakon kakkaninta da mahaifinta. Kullum Baba Ɗangaladima kafin ya fita sai ya leΖ™o ya ganta, da tsokana da komai zai ce,

‘Ku kawomin akori kishiya!”

Amne kan ce,

“Kakanin zamani da babu kunya a idanunsu, sun iya biyo jikanya”

Duk da yasan shaguΙ“e take masa, yakan maida abin a wasan dare domin cikar mutuntaka. Takai ta kawo tsegumi kala-kala cikin gida, tun wasu na mitar rashin kawaici, har suka sa idanu. Sunan a kori kishiya ya so yin tasiri ga Ummi sai da Labiba ta nuna jan ido sossai sannan aka daina faΙ—a.

***

ZAHIDA.

Zahidaht kuwa zaman nasu ba acewa komai, domin dai satinsu huΙ—u ta soma fuskanta asalin waye Kabir. Bata taΙ“a sanin halinsa haka yake ba, ta shiga nadama mara iyaka daga bisani ta rungumi Ζ™addara tana yi masa addu’a.

Matsala ta farko da suka soma fuskanta, maganar karatu da ta yi masa. Nan ya sawa idonsa kwalin Audu ya nuna be son batunba, tun suna yi ita su kaΙ—ai magana har kunnanan Baba Ι“aure amma ya Ζ™yirmushe ya ce bazata yi ba. Tilas tana ji tana gani ta haΖ™ura. Bata da aiki sai zaman gida kamar me gadi. Ganin zaman bazai mata ba yasa ta soma saida kayan gargajiya, wanda Yaya Asabe ke mata aikinsu ana turamata Ζ™asar da suke tana saidawa. Su kuka, daddawa kayan Ζ™amshi da sauransu har ma da lalle da salatif. Akan zuzzubasu cikin roba, tare da mana tambarin sunanta da addreshi. Ai kuwa nan da nan ta yi sabo da mutane irinta Ζ΄an asalin nijeriya, idannunta suka Ζ™ara buΙ—ewa tana fuskantar rayuwa yau da gobe. A irin haka ta gano mijinta manemin matane ta hanyar wata mai siyan kayanta Ζ΄ar bariki kuma mashayi.

Ranar ta yi kuka ba kaΙ—an ba, babu wanda ta sanarwa sai Yaya Asabe, ita kuma ta fututtuke kan ta baro Ζ™asar domin ba zata zauna da fasiΖ™i ba. Sai dai kuma Ζ™iri-Ζ™iri ta nuna mata ba zata iya fuskantar iyayensu da mummunan labari ba. Kuma tana son mijinta zata iya zama da shi ta yi masa addu’a. Yaya Asabe ta Ζ™ulu matuΖ™a, tana son Ζ™watarwa Zahidaht Ζ΄ancinta sai dai ta lura so ya rufe mata idanu. Ta ciza ta hura amma ta Ζ™eΖ™ashe Ζ™asa ta Ζ™i karΙ“ar batun. Hakan yasa ta watsar da sha’aninta tare da yi mata gargaΙ—i kan nan gaba kadda ta nemi taimakonta kan matsalarsa. Ta kuwa amince da hakan Ι—ari bisa Ι—ari.

Sai dai tako’ina bata jin daΙ—in zama da shi. Zai shawo giyarsa idan ta gaya masa Ζ™arya ya naΙ—a mata duka. Hakan ba zai hana idan ta tashi ta kyautatta masa ba. Ya zageta ya hantareta kuwa ba komai ba ne, amma murmushi ne aikinta tare da furta,

“Na gode mijina!”

Kabir mugune sossai, ba shi da mutunci ga izgilanci da nuna kowa ba kowa bane. To itama Khamisa kusan duk matsalar Ι—aya ce. Haka take Ζ™oΖ™arin danewa sai dai ta zo gun Zahidaht ta ci kukanta. Wani lokacin KUSKURAN WASU IYAYEN take gani, sun san halin namiji su Ι—auki nutsatsiyar Ι—iya su bashi kawai dan taΖ™amar cewa mace zata saitashi. Ita a rayuwarta bata taΙ“a ganin an Ι—auki mace mara ji ba an bawa namiji, da sunan wai zai saitata. Hasalima gudun auransu ake koda kuwa cikin dangine amma namiji sai ka riskeshi da tarin guma-guman aibu sai ace duk abin da ya yi ADO NE.

Tana mamakin yadda laifi yake zama ADO! A saninta duka tabo sunansa tabo wala ga mace wala ga namiji. Sau tari Zahidaht ita take kwakkwafarta domin shi iskanci nasa ya wuce na Kabir gida yake komai gaban idanunta. Sai dai kuma, matsalar da aka samu Khamisa mace ce mai zurfin ciki da saka abu a rai. Gata da san a kula da ita kamar me, dan haka ta matsawa kanta da damuwa sossai.

A hankali ciwo ya soma cin Khamisat, kafin a farga ya ci Ζ™arfinta. Sau biyu tana yin Ι“ari saboda damuwa da tunani, asibiti sun yi iya bakin Ζ™oΖ™arinsu wajen nuna mata illar abin da take yi amma a banza haka ma Ζ΄ar uwarta. Damuwar data sawa ranta, ita ta haifar mata da ciwon zuciya ta mutu farat Ι—aya. Tabbas mutuwarta ta taΙ“a iyayyensu, musamman da suka sami labarin abin da ya yi sanadin mutuwarta. Daga wannan lokaci suka sallama Jawwada, ba kuma su yi tunanin bincikar Kabir ba domin zahirinsa ya gamsar da su.

Mutuwarta ta sukurkuta Zahidaht Ζ™warai, sai ma ya zamo sillar asassa damuwarta domin Jawwad dai gidansu ya dawo da zama kacokan kuma aciki ya cigaba da gudanar da rayuwarsa yadda ya saba. Bata da ikon magana, Kabir zai ci mutuncinta. Haka ta cigaba da haΖ™uri da daΙ—i babu daΙ—i. Komai ta yi a hantare. Babu yadda bai yi da ita ba akan ayi mata allurar hana Ι—aukar ciki taΖ™i amincewa. Hakan yasa yake amfani da wani mai duk lokacin da zai kusanceta. Wanda matuΖ™ar akwai ciki jikinta to kuwa a daren take Ι“arinsa. Ba tare data ankare ba, cikin shekara guda da auransu Ι“arinta biyar.

Tilas aka yi mata Ι—aurin bakin mahaifa saboda tana neman samun matsala. Lokacin da ta sami labarin haihuwar Labiba kamar ta yi hauka. Kwata-kwata bata san cewar Kabir ne yake mata bita da Ζ™uli ba. Sai baΖ™ar izaya da yake mata kullum. Tana da son Ζ™ananun yara haka zata bi constomer Ι—inta ta yi ta yi wa yaransu kyautar kayan wasa.

WulaΖ™anci dai ba kama hannun yaro, tun tana daurewa har ya zamana ta soma yunΖ™urin barin gidansa. Sai dai bata da me goyon bayanta. Yaya Asabe ce dama maogararta kuma bata bata dama ba tun farko. Sai yanzu take hango KUSKURANTA da a baya ta Ζ™i amincewa da Ζ™uduri yayartasu. Sai dai kuma kash, a wannan lokacin bata da me goyon bayanta. Domin dai Yaya Asabe nuna mata ta yi ta je ta yi haΖ™uri, haka kowace mace take yin haΖ™uri da mijinta. In ta samu wannan, ba lalai ta sami wannan ba. Babban abinda ya ke Ζ™ara dakusar da ita kuwa, ganin cewa da wuya ka ga a zuri’arsu wata ta kawo karar miji. Wannan na sarar da guiwarta matuΖ™a. Kabir kuwa sai abin da ya yi gaba. Musamman da ya kasance makarantarsu ana damawa da shi, akwai kwanya shi ne first class dan haka Ζ΄an mata binsa suke ba shi ne yake binsu ba uwa uba ga kyau tsayayyen namiji ne.

Post a Comment for "WATA MACE CHAPTER 2 BY SANA S MATAZU"