SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 8 BY FATYMA SARDAUNA
SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 8 BY FATYMA SARDAUNA
Www.bankinhausanovels.com.ng
Yajima zaune a kan gadon nasa, gaba Ιaya kansa ya kulle yarasa meke damunsa, wai shin da gaske SO yake ko kuwa? anya kuwa yanaga zaman sa haka zai yi wu? zaifi masa kyau yanemi Abid domin shi ne kaΙai zai iya fayyace masa halin da yake ciki, tabbas shi koda son Zahrah Abid Ιin yace masa yanayi yanzu bazai musa masaba, idan kuwa har haka so yake to yana mawa Zahrah so me tsanani, saurin laluΙar wayarsa Ζirar Samsung dake kusa dashi yayi. Numbern Abid ya dannawa Ζira, bugu biyu Abid ya Ιaga Ζiran cikin muryan kasala yace “Mutumin ya akayi ne, ka katseni ina cikin holewata”+
“mcheeww aikin ka kenan cin Ζ΄aΖ΄an mutane, kana ina yanzu inaso muyi serious magana da kai” Zaid yafaΙi haka cike da zaΖuwa.
MiΖa Abid dake kwance shame shame a gado yayi haΙe da sakin daria, wai yau shi Zaid ke cewa baida wani aiki se cin Ζ΄aΖ΄an mutane, hmm ai duk iskancinsa shikansa yasan a ΖarΖashin Zaid yake, domin kuwa Iskancin Zaid me lasisi ne.
Cike da Ζuluwa Zaid yace ” Nifa bana Ζira ka kamin iskanci bane, da zaka tsaya kanamin dariya”
“Yi haΖuri mana nawan, maganartaka ce tabani dariya, zuwa anjima mu haΙu a Millinion Park ina fata de bawata matsala bace ta afku?”
Ζan yamutsa fuska Zaid yayi haΙe da duban agogon Rolex Ιin dake Ιaure a tsintsiyar hanunsa. “Shikenan to muhaΙu Ζarfe 5 na yamma banakumason kamin african time, 5 nacika idan bakazoba, bazan tsaya Ιata time Ιina wajen jiranka ba” yayi maganar cikin yanayi da yake nuna cewa ba wasa yake ba..
“Okay” kawai Abid yace haΙe da aje wayartasa yajawo babe Ιin dake kusa dashi, suka ci gaba da watsewarsu ko kunyar Allah dayake ganinsu basayi, Allah karabamu da ΖeΖashewar zuciya Ameen.
Zaid yana aje wayartasa yasanya hanu yashafi cikinsa, sai alokacin yake tuna rabonsa da yasanya abinci acikin cikinsa tun jiya da yammaci, amma saboda tsabar yashiga tension ko yunwarma bayaji, murmushi yayi tunowa da yayi da yanda yaji muryan Abid, dagajin yanda yaji yanayin muryartasa yatabbatar masa cewa holewa da mace Abid Ιin keyi, “hmmm Abid ba dama wajen iya latsa mace” yafaΙi haka a fili, shikamma rabonsa daya kusanci wata mace harya manta, shi yanzu ko mace ma yagani bata wani burgesa, yanzu idan zaiyi sex to badakowacce mace yakeso yayi ba, face Zahrah ita kaΙai yakejin cewa zai iya sauΖewa damuwarsa yanzu, itakuma kaΙaice zata iya basa gamsuwa Ιari bisa Ιari. MiΖewa yayi yanufi wajen fridge Ιin dake Ιakin nasa, fresh milk ya Ιauka haΙe da tsiyayawa a cikin glass cup, zama yayi yasoma sipping fresh milk Ιin a hankali, gaba Ιaya hankali da tunaninsa sunaga Zahrah, ko yanzu wani hali take ciki? Allah masani…
***
Sake narke masa murya tayi cikin shagwaΙa tace “Nide bance bana sonka ba, aikaima kasan inasonka, kawai de nakasa sakewa da kai ne har yau!” taΖare maganar tana me rausayar dakanta gefe tamkar yana ganinta..
Dr.Sadeeq dake zaune cikin luntsumemiyar kujeransa na office ya lumshe idanunsa haΙe da gyara zaman wayar akan kunnensa, sosai shagwaΙan Zahrah ke sauΖar mai da kasala acikin jikinsa, yayinda idan yaji muryarta yake samun nutsuwa a cikin zuciya da ruhinsa…
STORY CONTINUES BELOW
“To meyasa bakya iya sakewa dani ne My Princess, kinkuwa san irin sonda nake miki? inasonki Zahrah fiye da tunaninki, amma bazaki gane hakan ba, sai idan nasameki a matsayin matata, na tabbata nan da 3 weeks kinzamo mallakina daganan kuma zaki gaskata soyayyata a gareki!” yafaΙi maganar tasa cikin yanayi na shauΖi..
Saurin kulle idanunta tayi haΙe da sanya hanu tarufe fuskarta, saikace wanda take aga banshi, sosai maganarsa yasa taji kunya,, ta lura haka Dr.Sadeeq Ιin yake watarana baruwansa kansa tsaye yake faΙar maganar da zaisanya taji kunya.
“My Princess kinyi shiru” Dr.Sadeeq yafaΙi haka a kasalance.
Numfashi Zahrah ta fesar haΙe da sake yin Ζasa da muryarta cikin shagwaΙan daya zamemata sabo tace “Munyi magana da Baffa, yace ku kawo kayan lefen duk sanda kuka shirya kawai”
DaΙi ne yakama Dr.Sadeeq harsaida yakasa Ιoye murnarsa idan kuwa hakane to tabbas acikin satin nan zai sanar da Ζ΄an uwansa saisu shirya rananda zasu kawo kayan, shida zasuce yauma to tabbas da zaiso hakan.
“Naji daΙin maganarki My princess saboda haka kincancanci nabaki kyauta ta musamman, idan banzo da dare ba gobe zanzo insha Allah”
Murmushi kawai Zahrah tayi haΙi da cewa “Nagode amma kariΖe kyautarka bayanzuba”
“Meyasa?” yatambayeta cikin yanayi na Ιata fuska.
“Saboda hidiman da kakeyi yayi yawa, dan Allah kabari haka kaji!” taΖare maganar cikin yanayin shagwaΙa.
“Inde akan kine Zahrah bazan taΙa gajiyawa ba, zanyi wani aiki yanzu zanΖiraki anjima kinji princess Ιina!” yafaΙi haka cike da lallashi…..
Haka sukayi sallama cike da kulawa ga junansu, yanzu kam tagama aminta da Dr.Sadeeq insha Allah kuma idan ta auresa zata basa farinciki me Ιorewa, iyaka iyawarta…..
Sosai Zaid yashaΖa da irin yanda Abid yasanyasa agaba yaketa yi masa dariya,, tsuka Zaid yaja me tsayi haΙe da kawar da kansa gefe jiyake tamkar ya tashi ya rufe Abid da duka, idan banda iskanci taya zai sanyasa gaba yayi ta masa dariya bayan yagama jin matsalarsa…
Wani mugun kallo Zaid yajefawa Abid me Ιauke da tarin ma’anoni da yawa, ganin haka yasanya Abid saurin gimtse dariyarsa haΙe da kama hanun Zaid Ιin…
“Yi haΖuri Abokina, maganar ce tabani dariya”
Tsuka Zaid yakuma ja batare da yace komai ba…..
“Nafuskanci inda matsalanka ta dosa Zaid amma kuma nasan abune me wahala ka yarda da abun dazan faΙa ma”
“Bazaka gane yanda nakeji agame da’ita ba ne Abid, dakasan yanda nakeji a zuciyata da ka tausaya kasanar dani maganin matsala ta, kodai shine so Ιin da kake cewa?” Zaid yatambayi Abid cike da damuwa…
“Ζwarai kuwa Zaid wan nan shine SO, sai de naka SO’n ya banbanta da sauran soyayya’n, kai naka soyayya’r me tsanani kakeyi, wanda tariga da tajima acikin jikin ka batare da ka sani ba, ina da yaΖinin cewa tun farko Son Zahrah kake bawai sha’awarta ba kamar yanda ka Ιauka!” Abid yafaΙi haka da iyaka gaskiyarsa…
Nannauyar ajiyar zuciya Zaid ya sauΖe haΙe da sanya duka hannayensa ya dafe kansa wanda yake Ιan sara masa a hankali.. Tabbas yanzu kam ko yaso ko yaΖi dolensa ya yarda da maganan da Abid yafaΙa masa, domin kuwa idan har ba soyayya ba menene ke damunsa dayake sawa yakejin zafi a zuciyarsa? idan ba soyayya ba menene yake sanya tunaninsa hargitsewa da zaran yatuno Zahrah? idan ba soyayya ba menene yake sanya sa rasa sukuni da nutsuwarsa aduk sanda yatunanota kokuma yaganta? lallai kuwa soyayya baimasa adalci ba da bai sanar dashi kansa ba tun sanda yafarasa batare da yasani ba..
Idanunsa da sukayi jajur dasu ya Ιaga haΙe da maida kallonsa ga Abid “Inasonta Abid inasonta sosai!”
Waro idanu Abid yayi yana me kallon Zaid idan da ba Zaid Ιin ne da gaske a gabansa ba, to tabbas da sai yace badaga bakin Zaid wa Ζ΄an nan kalaman suka fitoba, yau Zaid da kansa yake cewa yakamu da son wata? lallai kuwa rayuwa tana shirin juyawa abokin nasa baya.1
STORY CONTINUES BELOW
MiΖewa Zaid yayi daga zaunen da yake haΙe da sanya hanu ya kwashe wayoyinsa dake kan Ιan Ζaramin table Ιin dake aje gabansu.
Kallonsa Abid yayi cike da mamakin ganin yanda lokaci Ιaya yanayin Zaid Ιin ya sauya.
“Inakuma zaka?” Abid yatambaya..
“Zanje gidansu Zahrah Abid, idanuna sun matsamin zuciyata har bugawa take Abid, ita kawai nakeson gani, idan har zata amince inaso ayau base gobeba koda Ζarfe Ιaya ne na dare a Ιaura mana aure da’ita” yanakai wa nan a zancensa yayi tafiyarsa.. Hangame baki Abid yayi yana kallonsa harya Ιacewa ganin idanunsa. Anyakuwa Zaid yana cikin hankalinsa? Kodai asiri yarinyar talakawan nan tayi masa ne? Abid yajerowa kansa waΖ΄an nan tambayoyin, bayan yasan baida amsa bai kuma da me basa amasar…
Zahrah dake zaune tana gudanar da assigment Ιinta, wani yaro yashigo cikin gidan nasu haΙe da kwaΙa sallama.. Amsa masa Zahrah tayi batare da taΙago kanta takalli yaron ba..
“Wai ana Ζiran Zahrah a waje” yaron yafaΙa yana me kallon Zahrah domin kuwa yasan cewa itace wacce aka aikosa yayi Ζiranta..
Sai alokacin Zahrah taΙago kanta ta kalli yaron, haka nan taji gabanta yafaΙi, to waye kenan yake sallama da’ita? ta tambayi kanta, wayarta dake kusa da’ita ta Ιauka haΙe da dubawa, 1 missed call tagani na Dr.Sadeeq, dayake wayartata a silent tasanyata shi yasa bataji Ζiran nasa ba, kenan shine yazo yaΖira wayarta bata Ιauka ba shiasa yaturo yaro. “Jekace inazuwa” ta bawa yaron amsa a taΖaice..
MiΖewa tayi haΙe da tattara takardunta tayi Ιaki. Mayafi taΙauka ta yafa akan kayan dake jikinta…
Tsaye yake ajikin motarsa yayinda yakifa kansa asaman motar yana me kaΙa key Ιin motarsa dake riΖe a hanunsa..
Kanta a Ζasa tafito daga cikin gidan tana me duba wayar dake hanunta. Tsayawa tayi cak bayan ta haΙe wani miyau dayazo me Ιaci ya maΖale mata a maΖoshinta.
Murmushi yasakarmata haΙe da soma takowa zuwa gareta..
Lokaci Ιaya idanun Zahrah suka sauya kala daga fari zuwa ja, juyawa tayi a fusace tanufi hanyar shiga gida, da sauri Zaid yasha gabanta haΙe da marairaice fuska cike da tashin hankali yasoma cewa….
“Dan Allah Zahrah kitsaya ki saurareni, dan Allah kada kimin haka Zahrah, inaso ki saurare…..” kasa Ζare maganar nasa yayi sakamakon kyakkyawan marin da Zahrah ta shimfiΙa masa akan kyakkyawar fuskarsa…
Cikin Ζuna da kuma zafin zuciya haΙi da raΙaΙi Zahrah ta haΙa yatsanta na tsakiya dakuma babbar yatsarta, ta kaΙa ade de fuskar Zaid duk da kuwa cewa yakerema tsayinta..
“Natsaneka tsana mafi muni, natsani jin kowani irin kalma ce da zata fito daga bakinka, wlh wlh nayi rantsuwa sau biyu, idan har ka sake naΖara ganin fuskar ka to zanyi maka abun da baka taΙa tunani ba!” cikin matsanancin Ιacin rai taΖare maganar tana me raΙan gefensa zata wuce, Zaid da zuciyarsa tariga da ta karye baiyi Ζasa a guiwa ba yasake shan gabanta.
“Kimin duk abun da kikeso Zahrah, zanfi jin daΙima idan akace kece zakiyi silan mutuwa ta, dan Allah ki saurareni mana Zahrah!!” yaΖare maganar cikin rawan murya…
Kuka ne ya Ζwacewa Zahrah me tsanani cikin muryan kukan tasoma cewa…..
“Miye laifina Zaid? Menene aibuna? shin wani abu na aikata maka da ka zaΙi cutar da rayuwata? ashe de ganganci ne don na Ιau soyayyata na baka? me yasa ka yaudareni Zaid? meyasa dole saini kazaΙi ka tozarta? Kacutar da rayuwata ka dasamin Ζunci a cikin zuciyata, wlh natsaneka Zaid, Idan har yaudara zata zamemaka abun ado mezaka amfana dashi acikin rayuwarka? Miye ribar aikata zina da fasiΖanci? Natsaneka Zaid! Natsaneka!! Bana fata Allah yaΖara haΙa fuskata da taka fuskar har gaban abada! Dan Allah kafita a rayuwata Zaid!!!” cikin matsanancin kuka taΖare maganar tana me durΖushewa Ζasa domin kuwa zuwa yanzu tsayuwa ya gagarewa Ζafafunta…
Idanun Zaid ne suka kaΙa suka zama jajur dasu tamkar wanda aka zuba musu jan barkono. gaba Ιaya jikinsane yasoma Ιari, shi Ιin ma durΖusawa yayi agabanta cikin murya me tsananin rauni yaΖira sunanta,, saurin Ιaga masa hanu Zahrah tayi alaman batason jin komai daga garesa..
“Banason nasake koda jin muryarkane Zaid, kafita a rayuwata, wai mekake nema dani ne? ko kana tunanin zan sake aminta da kai ne? hmmm kayi babban kuskure Zaid idan kuwa har haka kake tunani, zaifi maka kyau, kamanta dani kakuma manta da wacece ni, ni na barwa Allah cutarwan da kayi agareni, kuma insha Allah nasan zai Ιaukarmin fansa,, sai de inaso kasani cewa har abada bazan taΙa yafe maka ba, inaso kuma kada kamanta da cewar natsaneka !” a fusace ta faΙa cikin gida haΙe da banko Ζofar gidan nasu.
Tashi yayi daga durΖuson da yake haΙe da bin bayanta da kallo, gaba Ιaya zuciyarsa tagama karaya, wani irin abu yakeji ajikinsa yayinda kansa yayi masa wani irin masifaffen nauyi, zafi yakeji azuciyarsa irin sosai Ιin nan.
Zahrah kuwa zamewa tayi jikin Ζofar gidan nasu tasaki wani irin kuka me tsuma zuciya. Se yaushene zata warke daga raΙaΙi dakuma ciwon abun da Zaid yayi mata? ganinsa yasake tasomata da mikin daya Ζi warkewa tsawon lokaci acikin zuciyarta, maiyasa Zaid yazame mata bala’i acikin rayuwarta? kuka tashiga yi sosai da sosai…
Zaid kuwa daΖyar ya iya jan Ζafafunsa yanufi motarsa, kasa tuΖa motar tasa yayi, gaba Ιaya idanunsa duhu suke gane masa, tabbas bazai taΙa iya tuΖa mota yana a irin wan nan halin ba,, da Ζyar ya’iya laluΙa wayarsa yaΖira driver’nsa… Mintuna kaΙan drivern Zaid yazo ya wuce dashi….
Saida tayi kukanta son ranta har sai da taji kanta yasoma ciwo kafun ta tsagaita, haΙe da miΖewa daga jikin Ζofar tashige cikin gida, direct Ιakinta ta wuce ta kwanta numfarfashi kawai take sauΖewa, lokaci Ιaya zazzaΙi yarufeta, harsaida tajawo mayafi ta lulluΙi jikinta….
Sanda yashiga falonsa ko gani bayayi sosai, wani irin ciwo kansa ke masa me tsanani wanda yasanya idanunsa sukayi nauyi, da Ζyar ya’iya jan Ζafansa yashiga Ιaki, kalaman Zahrah ne sukeyi masa yawo acikin kansa,, yatsani jin kalmar tatsaneshi da take yawan faΙa Ιin nan, wlhy a gurinshi da ta faΙi wan nan kalman gwamma ta sharara masa maruka koda kuwa guda biyarne akan Ζuncinsa.. Ya yanke shawara da de yakasance a irin wan nan yanayin ya gwammace yafita daga cikin hayyacinsa idan yaso bayan wasu tsawon lokaci yadawo cikin hayyacin nasa,, wasu Ζwayoyin magani yaΙauko harkala biyu, wanda suke gusarwa mutum da hankalinsa, maganin suna da hatsari sosai hakan nema yasanya ba’a sai dasu a bayyane sai de a Ιoye, kuma suna mugun sa bacci sosai… Saida ya Ιalli guda uku uku daga jikin kowani sachet, kafun ya watsa maganin cikin bakinsa, wan nan karon ko ruwa baisha ba haka ya haΙiye magungunan, yanda kalaman Zahrah ke dawowa cikin kunnensa yafi komai Ιaga masa hankali, kwanciya yayi lamo akan gado yayinda yake Ζwato numfashinsa dake ΖoΖarin Ζwace masa da Ζyar. wani irin fusga numfashinsa yayi lokaci Ιaya kuma komai najikinsa ya sake…1
Zahrah kuwa zazzaΙine ya dirarmata me zafin gaske, wanda yasanya lokaci Ιaya jikinta yasoma Ιari ta fara rawan Ιari, har zuwa yanzu hawayenta bai tsaya ba. Zaid ya cuceta itakam duk irin Ζuncin daya jefata a baya bai ishe saba saida yakuma da wowa gareta, sai yaushene hawayenta zasu tsaya? sai yaushene zata samu farinciki ingantacce wanda babu algus acikinsa? tunda ta haΙu da Zaid Ζuncin rayuwarta yasoma, wani irin annoba Zaid yazame mata ne?…..Baki Labisat dake tsaye taturo gaba haΙe da Ιata fuskarta duk wai akan don Mom Ιinsu tace taΖira mata Zaid a Ιangarensa ne yasa take wan nan abun…
“Tsayuwan uban me kike bacewa nayi ki Ζiramin yayanki ba!” Mom tafaΙi haka cike da faΙa, ganin Labisat Ιin bata da niyar zuwa aiken datayi mata.
“Mom wlhy tsoro nakeji kada naje ya masifance ni!” Labisat tafaΙi haka cikin shagwaΙa.
Harara Mom tawurga mata bashiri Labisat takama hanyar fita daga cikin falon…
Aranta kuwa roΖon Allah take yasa idan taje kada ya masifanceta saboda shi abun faΙa baya masa kaΙan ko kaΙan, jiya jiya dawowanta daga boarding school amma Mom zata haΙata da masifan Yaya Zaid (Su yaya manya?)
Kusan sau huΙu Labisat tana knocking Ζofar daze kaita cikin falonsa, amma shiru ba amsa, hakan yasanya tatura Ζofar tashiga,, bakowa acikin falon sai daddaΙan Ζamshinsa dake tashi.. Direct Ζofar bedroom Ιinsa tanufa haΙe da soma knocking Ζofar,, jin shiru ne yasanya tashiga Ζiran sunan sa…
“Brother! Brother!” ko gyaran murya bataji yayiba balle tasa ran zai amsa mata, batama tabbatar yana cikin Ιakin ko baya ciki ba..
Gajiya tayi da knocking Ζofar ta juya tayi tafiyarta…
“Mom inaga fa kamar Bro bayanan domin nayita knocking door Ιinsa amma bai amsa ba”
“Tabbas yana cikin gidan nan Labisat domin kuwa tunjiya daya shigo baifita ba, har me gadi na tambaya naji ko yaga fitarsa amma yacemin tunjiya daya shigo bai fita ba, miskilancin nasa ne ya motsa, banaje dakaina nasa mesa nikam ae be isa yanunamin halin Ζyaliya ba” Mom tafaΙi haka tana me miΖewa tsaye daga zaunen da take..
Itama Ιin de knocking tayi masa haΙe da Ζiran sunansa amma shiru bai amsata ba, hakan yasa ta murΙa handle Ιin Ζofar ta kutsa kanta ciki bakinta Ιauke da sallama..
Tsuka Mom taja sakamakon ganinsa da tayi kwance akan gado yayi ruf da ciki, lallai ma wato iskancine ya hanasa amsa mata, da fari hartayi zaton ko baya gidan ne..
“Zaid!” taΖira sunansa cikin kakkausar murya… Ko motsawa baiyi ba balle tasaran ze amsa mata..
Kafeshi da idanu tayi tana me nazartarsa, a iya saninta da Zaid baya bacci a irin wan nan lokacin, impact ma shiba mutum bane ma’abocin yawan bacci ba’a bisa Ζa’ida ba, idan kuwa harda gaske baccin yake to baya rasa Ιayan biyu kodai baida lafiya ko kuma yayi halin nasa nashan Ζwayoyi, “Sai yaushene Zaid ze san ya girma? sai yau shene zai dena nuna rashin damuwa da lafiyarsa?” tajeromawa kanta waΖ΄an nan tambayoyin, “HaΖiΖa Zaid Ιanta ne amma ita kanta har yau batasan wani irin haline da shi ba, shi mutum ne me nuΖu nuΖu bakoda wani lokaci ne kake sanin gaba da bayansa ba, haka nan yake bakomai ne zaka masa Ζa burgesa ba yanada wani shegen shu’umin hali saide kawai Allah yashirya mata shi”…
STORY CONTINUES BELOW
A hankali tashiga takawa zuwa gaban gadon nasa..
Idanu Mom tasake warowa waje, tabbas idan de idanunta de de suka gane mata to kuwa Zaid baya numfashi, domin babu wata alamar da take nuna akwai nunfashi a tattare dashi saboda ko cikin sa baya motsawa, alama ta baya shaΖan numfashi kenan..
Hanunta takai setin hancinsa ko da zataji Ιumin numfashin sa.
Salati Mom tasa haΙe da dafe Ζirjinta, sakamakon wani irin bugawa da taji zuciyarta tayi.
“Zaid!Zaid!” Mom tashiga Ζiran sunansa cikin tashin hankali haΙe da soma jijjigasa.
Hawayene suka shiga bin Ζuncin Mom bashiri ta fita daga Ιakin, direct Ιangaren Alhaji Ma’aruf ta nufa saboda yana gida baikai ga fita office ba..
“Alhaji! Alhaji! katemaka wlhy Zaid baya numfashi zo muje ka gani, katemakeni kada na rasa Ιana mafi soyuwa a gareni!!” gaba Ιaya cikin tashin hankali Mom keyimawa Dad bayani..
Mamaki haΙi da al’ajabi ne yakama Alhaji Ma’aruf amma de yanzu balokacin tambaya bane gwamma yabita yaga meke faruwa da Zaid Ιin….
Shima sosai ya tsorita kuma hankalinsa yatashi daganin Zaid yashe a gado baya numfashi sai kace gawa…
Da Ζyar Abba ya’iya sungumarsa yasanyasa a mota, abunka da ΖaΖΖarfa kuma ma’abocin yin gym shiasa jikinsa yake ko ina a murΙe, san nan kuma me Ζaramin Ζarfi bazai iya Ιaga sa ba, Dad Ιin ma saida temakon Mom ya iya Ιagasa… Daga Mom har Labisat hankalinsu amatuΖar tashe yake haka suka shiga mota suka rankaya zuwa asibiti…
Direct Emergency aka kai Zaid cikin gaggawa likitoti suka shiga basa temakon gaggawa…
Jigum jigum haka Abba da Mom sukayi a wani Ιan corridor dake kusa da Ιakin da aka kai Zaid, iya Ζololuwar tashin hankali sun shigesa, kuka kawai Mom da Labisat keyi, kasa koda rarrashinsu Alhaji Ma’aruf yayi domin shima da akwai hali da kukan ze sanya ko da zaiji sassauci a cikin zuciyarsa…
Likitotin nan sunci baΖar wahala kafun da taimakon Allah suka samu suka daidai ta numfashin Zaid. Haka suka fito suna sharce gumi…. Kallon Alhaji Ma’aruf Ιaya daga cikin Doctors Ιin yayi haΙe da cewa “Ranka ya daΙe muje office” ΖoΖarin binsu Mom tasomayi Alhaji Ma’aruf yaΙaga mata hanu alamar tajirasu….
Handkerchief likitan nan yaΙauka ya Ζare share gumin dake tsatstsafawo akan goshin sa..
Ganin haka yasa Abba cike da tashin hankali yace “Yade Dr.Bilal meke faruwa ne, dan Allah kada kafaΙamin wani mummunan labari!”
Jinjina kai Dr.Bilal yayi haΙe da kallon Dad. “Kwakwantar da hankalinka Alhaji zuwa yanzu komai ya daidaita munshawo kan matsalan”
Nannauyar ajiyar zuciya Dad yasauΖe haΙe dayin hamdala acikin ransa…
Sake gyara zama Dr.Bilal yayi haΙi da cewa “Sai de kuma agaskia bazan Ιoye maka ba Alhaji Ιan ka yana cikin matsala wanda yake gab da rasa rayuwarsa matuΖar baikiyayewa kansa shan Ζwayoyi masu mugun haΙari ba, baya ga haka kuma idan har ya cigaba dashan giya nan da Ζ΄an kwanaki tofa sai de kuma abun da Allah yayi!”
Yanzukam Dad ne yashare gumi ba Dr.Bilal ba, domin kuwa a iya tsawon rayuwarsa baitaΙa sanin Zaid nashan wasu Ζwayoyi masu bugarwa ba, yade san da ya nashan giya amma kuma atunaninsa yajima da dena shan giyan.
“Bangama fahimtarka ba likita, naji kace Ζwayoyi na bugarwa, kana nufin shiΙin ne yakeshan Ζwayoyin bugarwa?” Dad yatambayi Dr.Bilal cike da son sanin Ζarin haske akan batun..
“Wato a iya bincikenmu mungano cewa akwai wata Ζwaya me haΙarin gaske da yakesha lokaci zuwa lokaci, wanda kuma haΙarin Ζwayar yana da matuΖar yawa, bazanyi mamakin a ina yasamu Ζwayan ba, saboda nasan shiΙin isashshene, saboda Ζwayar ba ako ina ake samunta ba, a Ζa’ida ma anhana shigo da Ζwayar nan gida Nigeria, kawai de rayuwar yanzune da ta zama sai a hankali, zai iya yuwuwa kuma ba anan yake sayan Ζwayan ba daga can waje yake shigowa da abarsa, sai de kuma wan nan duk bashine damuwar ba, idan har ya cigaba da shan wan nan Ζwaya to ina me tabbatar maka da cewa zai iya rasa ransa ako da yaushe, duk da kuwa dama munsan mutuwa tana kan kowa yanzu ko anjima, amma tabbas kiyayewan shine yafi, san nan kuma giya tayi masa mummunan illa saboda tasamu mafaka acikin cikinsa, wataΖila yamai da ita ruwan shansa ne, amma kuma duk hakan ba wani babban matsala bane idan har ze kiyaye to da taimakon Allah komai zezo masa cikin sauΖi!”
STORY CONTINUES BELOW
Salati Alhaji Ma’aruf yayi a bayyane haΙe da sanya hanu yazame hular dake kansa, ashe bayan giya hadda wata tsinanniyar Ζwaya me haΙari Zaid yake sha? anya kuwa Zaid yanada cikakken hankali? shin wani irin haline haka da Zaid? amma babban abun tambayar shine laifin waye acikinsu, laifinsune su iyayensa kokuwa laifinsa ne shi kansa Zaid Ιin?
“HaΖiΖa dukansu suna da laifi, amatsayinsu na iyaye basu wani tsaya sunbawa Zaid kyakkyawar kulawa ba, kuΙi kawai suka sake masa haΙe da turasa makaranta har wata uwa duniya, amma duk da haka bekamata ace yakasance haka ba, idan su basa lura da al’amuransa shi Ιin mahaukaci ne da be san dede ba? tabbas yasan shiyake da alhakin kulawa da tarbiyan Zaid tunda shine yaΙaukosa daga wajen Mahaifiyarsa yadawo dashi America kusa dashi, tunda suke America bai taΙa tsayawa da kyau yakula da wani irin rayuwa Zaid Ιin keyi ba, shide kawai yabuΙe masa bakin aljihu yana ganin hakan shine gata, Ζwarai mafiyawancin iyaye ayanzu sunfi bada kulawarsune ga Ζ³aΖ΄a mata, yayinda Ζ΄aΖ΄ansu maza kuwa ko oho, duk wata kyakkyawar tarbiya Ζ³aΖ΄a mata ake ΖoΖarin koyawa, yayinda Ζ³aΖ΄a maza kuwa suka zama hoto, aganin iyaye komiye Ιa namiji yayi adone bakamar Ζ΄a mace ba, tabbas hakane duk abun da Ιa namiji yayi adone bakamar mace ba, amma hakan bawai yananufin shi Ιa namiji abarsa sakaka haka bane batare da annuna masa kulawa ba, shi namiji a koda yaushe ana ganin zai iya kula da kansa, amma yana da kyau ana nuna masa kulawa ana kuma jansa ajiki kodan yasamu inda zena faΙan damuwarsa, kowafa yanason yasamu tarbiya me kyau daga Namiji har mace, saboda haka yazama lalle iyaye su tashi tsaye wajen kulawa da Ζ΄aΖ΄ansu maza saboda ba mata ne kaΙai suke buΖatan kulawa ba harsuma maza suna buΖata……
Dr.Bilal ne yakatse Dad daga tunanin da yafaΙa me zurfi tahanyar cewa da yayi dashi. “Zaid yana buΖatar hutu saboda haka sai nan da 4 hours kafun su samu ganinsa”
Jiki ba Ζwari haka Dad yafito daga office Ιin yanufo inda su Mom ke tsaye suna sharce hawaye..
“Yaya de Alhaji me likitan yacema?” Mom tatambaya cike da damuwar son sanin wani hali Ιanta yake ciki..
“Kada kidamu, ku kwantar da hankalinku jikinsa da sauΖi zuwa anjima kuma insha Allah zamu samu ganinsa yanzu likita yace yana buΖatar hutu ne, to dole zamu barsa yaΙan huta” Dad yaΖare maganar yana me kamo duka hannayen mom alamun rarrashi..
Hamdala Mom tayi haΙe da sauΖe ajiyar zuciya
Sake kallon Dad tayi cikin yanayi na tuhuma tace “Meyasanya naga fuskarka Ιauke da tashin hankali me tsanani Alhaji?”
Murmushin dole Dad yanemo ya ara akan fuskarsa bayason faΙa mata wan nan maganar yanzu yafiso saisun samu nutsuwa sunkoma gida tukunna, sai de kuma abun da shi besani ba shine tafikowa sanin cewa Zaid yanashan giya, saboda tasha kamasa acikin maye yayi mankas, san nan kuma tajima da sanin cewa yanashan Ζwayoyi, sede abun da bata sani ba shine haΙarin da Ζwayoyin suke Ιauke dashi….
********
Haka Zahrah tawayi gari yau da zazzaΙi sede duk da haka bata nunawa kowa cewa bata da lafiya ba, sede kuma idanunta sun kunbura sakamakon kukan da taci ta Ζoshi a daren jiya..
Haka de tashirya kanta tsab don zuwa makaranta amma kowa yaganta yasan bata da wani isashshen kuzari a tattare da’ita,, ko abun kari bata tsaya taci ba haka ta fice a gidan nasu….
********
“Kuka bazai taΙa yimiki maganin komai ba Zahrah, tabbas nasan kinajin raΙaΙi a cikin zuciyarki amma zuwa yanzu yakamata ace kimanta da baya kifuskanci gaba, aure zakiyi yanzu babu amfani kicigaba da sanya kanki cikin Ζunci!” Husnah tafaΙi haka ga Zahrah cikin yanayi na tausasawa, kasancewar duk wunin yau Ιin da sukayi amakaranta bata gane kan Ζawarta ta ba…
Hannayen Husnah duka Zahrah takama haΙe da kallonta. Cikin murya me rauni tasoma cewa…..
“Ni kaina inaso naganni cikin farinciki Husnah, amma nasan hakan bazai samu ba matuΖar Zaid yana raye a doron Ζasa, koda ma ace baya raye nasan bazanyi farinciki ba Husnah saboda yariga daya gama lalatamin rayuwa, bana tunanin cewa akwai wani namiji da zaiyi Ιokina idan ya aureni? Shifa budurci wani abune me matuΖar mahaimmanci a rayuwar Ζ΄a mace Husnah, babu wani mutumci dakuma karamci wanda ya wuce mace takai budurcinta Ιakin mijinta, mafi ganganci da kuskure da mace zata aikata kafun aurenta shine ta yarda ta bawa wani kyautar budurcinta, mata irina suna da yawa Husnah wa Ζ΄anda aka mawa fyaΙe aka Ζwaci budurcinsu da Ζarfin tsiya, san nan kuma akwai waΖ΄anda maza suke ruΙansu da kuΙi ko kuma da soyayya harsu yi nasaran rabasu da budurcinsu, san nan akwai kuma wanda dan kansu suke bada kyautar nasu budurcin ga wani daban, rasa budurci abune me matuΖar ciwo Husnah musamman ma ga iri na wanda aka mawa fyaΙe, Yawancin maza suna fatan idan sunyi aure su samu matansu da cikekken mutumcinsu, inde kuwa har a matsayin budurwa suka aureta, haΖiΖa akwai wata soyayya dakuma girmamawa dake shiga tsakanin mace da mijinta matuΖar takawomasa budurcinta Ιakinsa, saΙanin haka kuwa shike hargitsa tunanin namiji, shike jagulawa mace zaman aure’nta, koda ace ya yarda Ζaddarane hakan amma tabbas wani lokaci abun zaina masa ciwo, duk da nasan cewa Dr.Sadeeq yasan komai daya faru dani, amma duk da haka tabbas nasan duk randa yakusanceni saiyaji ciwo acikin ransa, saikuma yaji wani abu saΙanin tunaninsa, shi a yanzu yana ganin cewa hakan bakomai bane, amma kuma hakan komai ne bakuma ze gane hakan ba sai randa ya aureni yakuma nemi dana basa haΖΖinsa na aure,, wan nan ranan nake gujewa kaina Husnah bansan ina zan tsoma kai da zuciyata ba amma nabarwa Allah komai!!” gaba Ιaya hawaye sungama wankewa Zahrah da Husnah fuska, lalle kuwa wan nan itace mummunar Ζaddara wand ba’a taΙa mantawa da’ita,, rungume Zahrah Husnah tayi cike da tsananin tausayin Ζawarta ta,,, tabbas duk abun da Zahrah tafaΙa gaskiya ne kai budurci Ιakin miji yafi komai daΙi a rayuwa saboda ko ba komai zaiΖara muku danΖon soyayya dakuma mutunta juna, duk da cewa Zahrah ba’asonta tarasa budurcinta ba amma kuma tabbas kamar yanda Zahrah ta faΙa hakan yake dolene Dr.Sadeeq zaiji zafin abun sosai aduk ranarda kusantar farko tashiga tsakaninsu, amma kuma babu wanda ya isa ya tsallakewa Ζaddararsa…..
STORY CONTINUES BELOW
Hawayenta tasanya hanu tashare kafun tashiga sharewa Zahrah ma nata hawayen,,,,
“Ki kwantar da hankalinki Zahrah komai zai zo cikin sauΖi insha Allah taso muje musamu ruwa muwanke fuskarmu ko”
Ba musu Zahrah ta tashi tsaye Husnah takama hanunta suka nufi wajen da sukasan zasu samu ruwa……
***********
Jigum haka su Dad dake tsaye agefen gadon Zaid sukayi, yanzu awa 5 kenan suna irgawa batare daya buΙe idanunsa ba, gashi kuma 4 hours likita yace musu zaiyi….
Babban yatsar Ζafansane tasoma motsawa kafun idanunsa da sukayi nauyi suka soma buΙewa a hankali,, da sauri Dad Ιinsa yaΖaraso jikin gadon yanayi masa sannu…
ΖoΖarin tashi zaune yasomayi da sauri Dad Ιinsa yamaidasa ya kwanta “Ba sai ka tashi ba Zaid yakamata kabari kaΙan wastsake tukunna kafun kasoma yunΖurin tashi”
Ζan yamutsa fuska Zaid yayi haΙe dabin ledar ruwan da aka Ιaura masa da kallo.
Dai de lokacin Labisat suka shigo ita da Dr.Bilal domin dama Mom naganin Zaid Ιin yabuΙe ido tace da Labisat tayi mata Ζiran Doctor…
Ζ³an gwaje gwaje Dr.Bilal yayi masa haΙe dayi masa wasu Ζ΄an tambayoyi, ko motsawa bakin Zaid beyiba balle Dr.Bilal yasa ran samun amsa, ganin haka yasa Dr.Bilal yin murmushi batun yauba yasan Zaid Ιin saboda haka shirun da Zaid Ιin yayi masa bawani abu bane daya kamata ace yadamu ba,, kallon Dad Dr.Bilal yayi haΙe da cewa
“Ko yanzu idan kuna buΖatar sallama se a baku saboda babu wata damuwa, se daifa a kiyaye kamar yanda na faΙa”
Kai Dad yajinjina haΙe da cewa “Shikenan Doctor insha Allah za’a kiyaye, muje sai nakarΙi takardan sallaman ko” Dad da Dr.Bilal suna fita Zaid yatattaro duka wani kuzarinsa dayayi masa saura yamiΖe tsaye, kafaΙun Labisat dake tsaye kusa dashi ya kamo haΙe da Ιaura hanunsa akan kafaΙan nata suka nufi hanyar fita daga Ιakin, domin kuwa koda Dr.Bilal be basu sallama ba tabbas bazai Ζara 1 hour a cikin asibitin ba…
Yana riΖe da kafaΙan Labisat harzuwa cikin mota, shida Labisat mota Ιaya suka shiga, yayinda su Dad da Mom suka shiga wata motar wanda duk su sukazo da ita… Direct gida suka nufa
Idanunsa gaba Ιaya suna a lumshe yayinda yajingina bayansa a jikin kujeran motar wanda yake zaune akai.
Ζan satan kallonsa Labisat tayi hakanan taji wani irin mugun tausayin Ιan uwan nata ya kamata, tabbas basuyi wani shaΖuwa da yayan nata ba amma tafuskanci cewa yanacikin damuwa, takuma tabbatar da cewa sanadin damuwarne ma har ya kaisa ga kwanciya a asibiti, to wan nan wace irin damuwace yayanta yake ciki haka? tabbas zataso sanin damuwar dake damunsa saboda tana matuΖar son Ιan uwan nata bandashi batada wani Ιan uwa dasuke uwa Ιaya uba Ιaya shikaΙaine yayanta kuma garkuwanta……
Koda suka isa gidama Labisat ce tarakasa har Ιangarensa,, zama yayi akan kujera haΙe da jawo wani Ιan Ζaramin table Ιin dake tsakiyar falon yaΙaura Ζafafunsa akai..
“Yaya mezan kawo maka, yakamata kasa wani abu acikin ka!” cike da Ιar Ιar Labisar tafaΙi maganar saboda tasansa sarai ba’a iyarmasa yanzu saiya saceka..
“Friedrice” yafaΙa a taΖaice batare kuma daya buΙe kyawawan idanunsa dasuke a lumshe ba..
Jiki na mazari haka Labisat ta tafi kawo masa friedrice Ιin dayace, domin kuwa dama agidan nasu ba a rasa friedrice..
Mintuna kaΙan tadawo hanunta Ιauke da Ζaton tire hadda plate Ιin yankakkun kayan marmari akan tire Ιin,, adede gabansa ta ajiye tire Ιin haΙe da Ιaukan plate ta buΙe kulan da friedrice Ιin ke ciki ta zuba masa.
“Yaya gashinan na kawo” tafaΙa tana me tura masa plate Ιin friedrice Ιin gabansa.
Ganin da tayi bece da ita komai ba yasanyata miΖewa sumu sumu tafice daga falon nasa…
STORY CONTINUES BELOW
Jawo plate Ιin yayi gabansa yasoma tsakuran abincin yanaci kaΙan kaΙan duk da kuwa bawai buΖatar abincin yakeyi ba adole kawai yakeci… Lomansa huΙu ya aje spoon Ιin dake hanunsa haΙe da jawo plate Ιin yankakkun kayan marmarin dake gabansa yasoma sha, sai alokacin yasoma jin daΙin bakinsa, amma da kwata kwata bayajin ΙanΙanon komai,, fruits Ιinma baiwani sha me yawaba haka yature yakuma maidakansa yajingina da kujera,, idan akwai abun dayake Ζauna dakuma muradin gani yanzu arayuwarsa baiwuce Zahrah ba, dole yaje gidansu ayau Ιin koda kuwa idan yaje zata Ιauki wuΖa ne taluma masa a cikinsa…..
Yauma de kamar kullum Zaune take a tsakar gidan nasu, kwanon abincine aje agabanta tana tsakura da kaΙan kaΙan tana kaiwa bakinta domin kuwa haryanzu bata wani jin daΙin jikinta..
Inna ce zaune daga gefenta tana ta ΖoΖari wajen ganin ta seta tashan radion ta..
Wani yarone yayi sallama yace wai ana Ζiran Zahrah,, “Jekace tanazuwa” Inna tahanzarta faΙa, har yaron yakama hanyar fita daga gidan, Zahrah ta tsaidasa haΙe da cewa “Kace bazata zo ba”
Hangame baki Inna tayi tana kallon Zahrah “Bazakijeba fa kikace?”
“Eh Inna dan Allah kuma kada kitambayeni dalili” tayi maganar tana me langwaΙar da kanta gefe.
Harara Inna ta watsa mata haΙe dayin tsuka baΖin ciki kawai Zahrah’n takeyi mata wayasani ma ko wanda ke Ζiran nata da alkhairi yazo…
“Wai Bazata zoba” yaron nan yafaΙawa wanda ya aikosa.
Waro idanu Zaid yayi maganar ma shi dariya taso basa, amma a irin wan nan yanayin dayake ciki bayatunanin zai iyayin dariya…
“Wayene yacema bazata zo ba?” Zaid yatambayi yaron.
“Ita da kanta” yaron yabasa amsa domin kuwa shiΙin Ιan maΖotansu ne saboda haka yasan Zahrah’n.
Kai Zaid yajinjina haΙe da cije laΙΙansa,, Allah sarki rayuwa babu yanda bata juyawa mutum, amma in banda haka wai yau shine a wata ΖasΖantacciyar unguwa kuma Ζofar gidan su mace yakuma aika tace bazata zo ba, shine fa Zaid Ιin da har gobe Ζ΄an mata suke rushing akan sa, to amma meyasa haka takasance dashi?” ganin da yayi yaron nashirin tafiya ne yasanya yace “Kaje kace injini nace tayi haΖuri tafito” bamusu yaron yakoma yakuma faΙi saΖon da akabasa umarnin yafaΙa..
Tsuka Zahrah taja haΙe da tashi tsaye “Kaje kace wai inji Zahrah kozai mutu a tsaye baza ta zoba” tanakaiwa nan azancenta tayi wucewarta Ιaki..
Abunda Zahrah tafaΙa shi yaron nan yazo ya sanarwa Zaid, kuΙi Zaid yaciro a aljihunsa 1k yabawa yaron dafari yaron yatsorita yaΖi amsa, amma Zaid yatilasta masa saida ya amsa, haka yaron yatafi yana murna…
Motarsa yabuΙe yashiga yayinda yakifa kansa a steering motar meyasa soyayya zata masa haka, idanunsa Zahrah kawai suke son gane masa tabbas yau bazai taΙa iya runtsawaba matuΖar baiga Zahrah ba, yana mawa Zahrah wani irin mugun so me tsananin zafi.. Jan motarsa yayi yakoma ΖarΖashin wata bishiya tayanda bakowa zai lura da cewa yana wajen ba, yaΖudurta aransa cewa koda zai kwana a wajen ne bazai gusa ba harsai idanunsa sun mai tozali da Zahrah….
Bayan awa Ιaya
Zahrah ce tafito daga cikin gidan nasu sanye da wani siririn mayafi wayarta ce riΖe a hanunta se kuma wani littafi. Zaid dake zaune cikin motarsa yana ganinta ya sake waro idanu haΙe da sauΖe ajiyar zuciya me Ζarfi, jiyakeyi tamkar yaje ya ΙauΖota can caΙak yatafi da ita… Yana kallonta tayi shigewarta wani gida dake kusa da nasu gidan.. Bayan kamar mintuna 8 da shiganta gidan yaga takuma fitowa da sauri yabuΙe murfin motarsa daniyar Ζarasawa gareta sai de kuma ko taku biyu baiyiba tashige cikin gida ko ganinsa ma ita batayi ba, haushine yasanyashi buga tayar motarsa da Ζafarsa, haka yakoma yayiwa motarsa key haΙe dayin reverse yabar unguwar tasu cike da Ζuncin rashin samun daman yi mata magana da be yiba, amma de yaji sanyi sosai a zuciyarsa daya ganta…
*********
Yau tunsafe Zahrah tashiga busy hidama kawai sukeyi ita da Husnah domin kuwa yaune ranar da Dr.Sadeeq yace mata za’a kawo lefenta,, yanzuma daga shopping suke sunje sun sayo kayan drinks da kuma su snacks wanda za’abawa baΖi. Zama sukayi akan tabarma suna me da numfashi saboda sungaji sosai,,, kallon Zahrah Husnah tayi haΙe da sakin murmushi.
“Ζawata nifa yau daΙi nakeji jinake tamkar ma nice za’a kawowa lefen” dariya Zahrah tayi haΙe dacewa “To aike kince bayanzu zakiyi aure ba saikin gama school gashi Nuruddeen yana tsananin son kuyi aure amma ke kinΖi”
“Hmm ai zan masa maganane yaturo kawai domin ni mafa yanzu dagaske auren nakeso nagaji da rungumar pillow idan nazo bacci” Dariya suka sanya su dukansu hadda tafawa, “Allah yashiryeki Husnah” Zahrah tafaΙa tana dariya.. Haka de sukaci gaba da Ζ΄an hirarrakinsu irin na Ζawaye……….
Ζarfe biyar dai dai wasu rantsa rantsan motoci suka soma tsayuwa a Ζofar gidan su Zahrah duk macen da tafito acikin motar sai kaga tana yatsuna fuska haΙe da soma Ζarewa wajen gidansu Zahrah kallo, motocine kusan guda goma sha biyu suka kawo kayan lefen ahankali aka shiga fito da akwatuna ana shiga dashi cikin gidan su Zahrah.. Fuska babu yabo ba fallasa haka matan nan suka soma shiga cikin gidansu Zahrah,,,,, da fari’a Inna da tawagarta suka tarΙi mutanen haΙe da basu wajen zama, haka suka zauna wasu daga cikinsu suna yatsuna fuska kamar wanda akace su zauna akan kashi…
“Sannunku da zuwa lale marhaba” Wata mata maΖociyar su Zahrah tafaΙa ga matan da suka kawo lefen. Amma kuma daΖyar aka samu biyu daga cikinsu suka amsa mata..
Akwatuna ne harguda shabiyu aka jibge akan wata tabarma dake shimfuΙe,, su Inna ne suka fara Ιagawa matan da suka kawo lefen gaisuwa ciki ciki suka amsa musu cike da isa,,,,, Aunty Raliya ce ma tayi Ζarfin halin cewa “Ga kayanan munkawo Allah yasa ayi bikin a sa’a, Allah kuma yasa asamu kyakkyawar zuri’a” dagajin yanda tayi maganar kaΙai ya isa ya tabbatarmaka cewa kalaman ba anyi su bane cikin daΙin rai,,, da Ameen kawai su Inna suka amsa musu,,, kuΙi Aunty Raliya taciro acikin jakarta bandir Ιin Ζ΄an dubu dubu har na dubu Ιari ta Ιaura akan wani akwati haΙe da kallon Ζ΄an uwanta tace “Muje ko” dukansu miΖewa sukayi suka nufi hanyar waje,,, yayinda Inna tasa yaran maΖotansu suka kwashi kayan tarban baΖin da suka musu aka kai musu cikin mota, maman Badi’a Ιaya daga cikin maΖotan su Zahrah ita tazari dubu hamsin daga cikin kuΙin da suka aje tabawa Ζ΄arta Badi’a tace takaiwa matan dasuka kawo lefen,,, dawowa da kuΙin Badi’a tayi tace ae sun riga da sun tafi koda tafita Ζurar motarsu kawai tagani,,, “To suko wasu irin mutanene haka ae ba haka akeyi ba, ko fa kayan basu tsaya sun nuna mana ba saikace wanda suke akan Ζaya” Maman Badi’a tafaΙi haka cike da mamakin hali irin na matan da suka kawo lefen,,, washe da baki wata mata daga cikin gayyar Inna tace “Kai amma kuwa Zahrah tayi goshi kuga kayafa kamar wanda za a buΙe kanti” ae kuwa basusan cewa Zahrah tayi goshi ba saida suka soma buΙe akwatunan,, kowanni akwati shaΖe yake da kaya nagani na faΙa,, take Inna tasoma rangaΙa guΙa hadda rawan murna…….Hayaniya haΙi da guΙan da su Inna keyi shiyayi sanadiyar janyo hankalin Zahrah dakuma Husnah da suke zaune a Ιakin Zahrah sunyi muΖus,,,,+
“Ke nifa tashi zanyi naje nabawa idanuna abinci, dan wlh bazan iya zama aΙaki kamar wata sabuwar amarya ba, ke dai da zaman yazamemiki dole saiki ta fama” Husnah tafaΙi haka tana me miΖewa tsaye daga zaunen da take,,, murmushi kawai Zahrah tayi mata haΙe da binta da kallo hartafice daga cikin Ιakin…
Hamdala Husnah tayi haΙe da nunatsantsar farincikinta alokacin da idanunta sukai mata tozali da kayan lefen Ζawartata,,,, lallai Dr.Sadeeq yayi ΖoΖari domin kuwa naira tayi kuka, koda kyawun akwatunan aka barka sun isa sanyaya maka rai, balle kuma aje ga kayan ciki masu kyau da tsadar gaske, wan nan shiyasake tabbatar mata da cewa Zahrah bazatayi kuka ba idan ta auri Dr.Sadeeq, saboda me sonkane kaΙai zai iyayin komai dayasan zai faranta maka rai….
Duk yawan atamfofin dake cikin akwatunan nan saida su Inna suka irgesu kaf, turame hamsin banda su laces haΙi da shaddodi dakuma dangin su materials,, Ιangaren dogin riguna ma akwati guda aka cika dasu, sosai kuma yasaki bakin aljihunsa wajen zaΙo masu kyau da tsada,, haka Ιangaren sarΖokima komai yaji domin kuwa kaf cikin sarΖoΖi da Ιan kunnayenta babu wani mai sauΖin kuΙi acikinsu gwala gwalanta har guda uku,, san nan kuma Ιanagaren jaka da takalma ma yayi ΖoΖari sosai, domin kuwa kusan kowani kaya yanada jaka da takalmi hadda mayafinsa,, wajen kayan shafa ma yayi ΖoΖari sosai wajen fidda naira yasai kayan shafa Ζ΄an yayi masu kyau duk da kuwa yasan cewa ita ba gwanar kwalliyan fuska bace…
“Gaskiya kaya yayi kyau yarinya tayi goshi, ai wan nan kayan ko Ιiyar babban attijiri sai haka” Maman Badi’a tafaΙi haka bayan taΖarewa wani haΙaΙΙen leshi dake riΖe a hanunta kallo wanda a Ζalla kuΙinsa zai kai 50k,,,
“Ζwarai kuwa yarinya tayi goshi Maman Badi’a ai dama tuntuni nasan fiye da haka ma sai yafaru, ga kaya kan nan harda nasadakarwa!” Inna tafaΙi haka cikin murna…
Wata dake zaune kusa da Inna tace “wan nan haka yake muma dai Allah yabawa namu Ζ΄aΖ΄an mazajen aure masu Ζashin arziki”
Duka matan suka haΙa baki wajen cewa Ameen domin kuwa babu wacce zataΖi ace Ζ΄arta ce tasamu wan nan kayan more rayuwan….
Sai kusan magriba matan dasuka karΙi lefen Zahrah suka soma tafiya, bayan Inna ta yaga musu wani abu daga cikin dubu hamsin Ιin daya rage,, haka suka tafi suna mata godiya suna kuma zuba santin kayan domin kuwa koda maΖiyin Zahrah ne yaga wan nan uban kaya da Dr.Sadeeq yayi mata tabbas dole sai ya jinjina abun…..1
Lokacin da Zahrah taga irin yawan kayan lefen da Dr yayi mata kasacewa komai tayi, sosai abun yabata mamaki domin kuwa bata taΙa zaton zai Ιarnata dukiya mai yawa harhaka wajen yi mata lefe ba, bayan kuma yasan cewa ita ba cikakkiyar budurwa bace,,, sai de taΖudura aranta cewa zata faΙa masa kayan sunyi yawa……
STORY CONTINUES BELOW
Gidansu Doctor…
“Gaskiya da sake Hajiya, yakamata a dakatar da wan nan batun auren na Sadeeq da yarinyar nan, kinkuwa ga gidansu Hajiya? wlhy ko suminti babu a tsakar gidansu zallan turbuΙin yashine, kallo Ιaya zakai musu kafuskanci cewa suΙin faΖara’une basu da komai, kwata kwata ma Sadeeq baisan inda zaije ya nemo aure ba domin a wan nan gidan bana tunanin akwai wata halitta da zata burge wani Ιa namiji acikinsa, kawai dai ni inaga ma asiri sukayi masa wlhy, amma bacin haka banjin dakansa zaije neman aure wan nan gidan!” Auntie Raliya ce ke faΙan haka cikin Ιacin rai…..
Ajiyar zuciya Hajiya tayi cikin Ιacin rai tace “Hmmm Raliya kenan aeni ban isa hana wan nan auren ba ko kinmanta cewa har Ζarana wajen Baffan ku Sadeeq yakai akan naΖi amincewa da aurensa, ni yanzu baruwana acikin lamarin aurensa ko mai ya jajiΙowa kansa shiya sani”
Ζwafa Auntie Raliya tayi haΙe da sakai tafice daga cikin Ιakin Hajiyar, harga Allah ita sam batason wan nan auren da Sadeeq zaiyi, yarasa ma wacce zai kwaso musu sai wacce wani ya haiΖewa a waje san nan kuma Ζ΄ar talakawa futuk…
Auntie Raliya tana fita falo Ζawayenta da ta gaiyato suka kai lefe tare, sukayi caaa akanta kowacce tana ingizata akan cewa tasa afasa auren domin kuwa sam ajin Sadeeq yagirmewa neman aure a wan nan gidan matsiyatan,,, take kuwa Auntie Raliya tahau kan zancen tazauna dabas, takuma Ζuduri aniyar lalata zancen auren abune me sauΖi kuma dakanta zataje ta kwaso kayan lefen Ζanin nata……..
1
Ζata fuska Zahrah tayi haΙe da tunzuro Ιan Ζaramin bakinta gaba cike da shagwaΙa tace “Dagaske nake faΙa maka kayan lefen nan sunyi yawa, ko Ιazu dawowan Baffa daya gani shima haka yace, kuma kafasan ba kyau yin wasa da dukiya” taΖare maganar tana me langwaΙar da kanta gefe.
Murmushi Dr.Sadeeq yayi haΙe da kwantar da bayansa ajikin kujeran motar dayake zaune akai kana ya lumshe gajiyayyun idanunsa, sautin muryarta nayi masa daΙi sosai…
Shirune yashiga tsakaninsu har na tsawon minti Ιaya.
“Duk abun da mayi miki kin can can ci haka daga gareni ne Zahrah, dan Allah kibar maganar yawan lefen nan, ni banga wani yawa da sukayi ba, naso ma nayi miki wanda yafi wan nan to abubuwane sukai min yawa, amma kin wuce haka a wajena, kuma kinsan ku biyu ne” yafaΙi haka yana me kafeta da idanunsa..
Murmushi kawai Zahrah tayi haΙe da kawar da kanta gefe, sam bataso idan yana kallonta itama ta kalleshi saboda takanjin nauyinsa awasu lokutan,, amma kuma hakanan taji kalmar dayace su biyu ne yaΙan sosa mata rai, wato idan ma ta manta to yatuna mata…
Wani murmushin Dr.Sadeeq yakumayi sakamakon ganin yanda fuskarta ya Ιan sauya lokaci Ιaya yakuma san maganarsa ce batai mata daΙi ba, dama kuma yafaΙi hakanne don yagane cewa tana kishinsa ne ko a’a….
“Bansan wani irin daΙi da kuma farinciki zan tsinci kaina ciki ba aduk sanda wannan ranar taruskeni, amma kuma da zanfi kowa jin daΙi idan har Allah ya gwadamin wannan rana!” yafaΙi haka cikin shauΖi, dason kawar da wancen zancen nasu..
Cike da mamaki Zahrah taΙan saci kallonsa haΙi da cewa “Wace rana ce wan nan?”
“Ranar da zaki zamo mallakina, ranarda za’akawomin ke Ιakina amatsayin matata ta sunna, ranar da zan kwana ina kallon wannan kyakkyawar fuskar taki babuko Ζyafta ido”
Kunyane yakama Zahrah wanda haryakaita ga cusa kanta tsakankanun cinyoyinta, sautari Dr.Sadeeq yakan faΙi abubuwan da suke sanyawa takejin kunyarsa sosai…
Murmushi Dr.Sadeeq yayi haΙe da sake kwantar da jikinsa akan kujeran motar,,,, yana matuΖar son komai na Zahrah ciki kuwa hadda wan nan kunyar nata, tun asalinsa yanason mace me kunya, sai gashi kuma yanzu Allah yabasa, sai de kuma yasan nan gaba kaΙan zaisha fama da’ita saboda idan sunyi aure yasan wan nan halin nata na kunya zatai ta gwadamasa.
STORY CONTINUES BELOW
Kallon agogon dake Ιaure a hanunsa na dama yayi.
“8:30pm” yafaΙa a bayyane kana yadawo da kallonsa ga Zahrah wacce har yanzu bata Ιago kanta ba.
“Shikenan to tunda dai kunyana kikeji ni zantafi naga dare yasoma yi” yafaΙi haka adai dai lokacin da yake ΖoΖarin Ιaura sit belt ajikinsa..
Sai alokacin taΙago kanta amma bata yadda ta kallesa ba,, “Sai da safe” tafaΙi haka tana me ΖoΖarin fita daga cikin motar domin dama taΖosa yace mata zaitafi saboda tagaji da zaman motan gashi tana da assigment kuma gobe zasuyi submit Ιinshi, san nan kuma tana buΖatar kasancewa ita kaΙai domin tattaunawa da zuciyarta a game da sabon al’amarin dayake shirin kunnu mata kai….
Kansa yajinjina haΙe da cewa “Dama so kike natafi ko?”
Murmushi tayi masa kana taΙan girgiza kan ta alamar a’a, cikin murya me sanyi tace “Bahaka bane kawai de nafara jin bacci ne”
Kansa yakuma jinjinawa cike da gamsuwa haΙe da juyawa baya yaΙauΖo wata farar leda dake aje kan kujeran gidan baya na motar.
“Idan Allah yakaimu da safe zanΖiraki ina fata zakiyi bacci me daΙi” yafaΙi maganar yana me miΖomata ledan dake riΖe a hanunsa…
ShagwaΙe fuska Zahrah tayi haΙe da marairaice manya manyan idanunta da suke sauΖar masa da kasala aduk sanda ya kallesu,, “Gaskiya ni dai a’a nagaji da wayon da kakemin, kuma tun ba yauba na faΙa ma hidiman dakakemin yana yawa!”
Lumshe idanunsa yayi haΙi da buΙesu alokaci guda, idan yanaganin irin wan nan shagwaΙan nata to tabbas zata iya zautar dashi lokaci Ιaya, yafice a hayyacinsa, domin shi shagwaΙan mace nasanyawa yaji feeling ajikinsa sosai,, cikin murya me sanyi yace “Kiyi haΖuri ki ΖarΙa kinji princess Ιina, kinga ba kyu maida hanun kyauta baya!”
Sake turo baki tayi haΙe da kwaΙe fuska, abun mamaki sai taga shima ya marairaice mata fuska kamar wani Ζaramin yaro,, “Please!” yafaΙa cikin muryarsa da tayi Ζasa sosai..
Dole babu yanda ta’iya haka tasanya hanu takarΙi ledan haΙe dayi masa saida safe tafice daga cikin motar,,, yanaganin shigewarta cikin gida yasaki murmushi haΙe da sanya hanu yashafi sajen dake kwance akan Ζuncinsa, key yayi mawa motar haΙe dayin reverse yabar unguwar tasu. Yana tuΖi amma shikaΙai yaketa zuba murmushi, aduk sanda yake tare da Zahrah yakansamun kansa cikin farinciki da nishaΙi, tabbas yanayimawa Zahrah so me tsanani…..
Zahrah kuwa tana shiga cikin gida direct wajen da Inna ke zaune tanufa, ΖoΖarin zama tasomayi haΙi dayimawa Inna sannu da gida.
Washe da baki Inna ta amsa mata bayan ta kafe Zahrah da’ido, Allah Allah take taga menene acikin ledan da Zahrah ta shigo dashi..
Dariyane ya Ζwace mawa Zahrah sakamakon ganin yanda Inna ta tsareta da’idanu tamkar wata mayya.
“Dariyan uban me kike? banson shashanci wallahi” Inna tafaΙi haka ga Zahrah a hasale, ganin bata da shirin buΙe ledan…
Hannayenta tasanya ta toshe bakinta haΙe dasoma ΖoΖarin shanye dariyar ta.
Ledan da tashigo dashi ta buΙe tasoma dubawa gasassun kajine manya guda biyu sai kuma sauran kayan ciye ciye kamar su snacks dakuma chocolate,,
Ledan da kajin ke ciki ta ciro ta miΖamawa Inna ae kuwa hanun Inna har rawa yake lokacin da tazo karΙan ledan tsabar kwaΙayi.
Fari’ar Inna ne yasake yawaita sakamakon ganin kaji da tayi, babu wani Ιata lokaci ta yago cinyar kaza Ιaya takai bakinta,, tsabar daΙin kazar saiga Inna tana lumshe idanu haΙi da jijjiga kai.
Murmushi kawai Zahrah tayi haΙe da Ιaukan sauran kayan tawuce Ιakinta yayinda tabar Inna tayi pieces tana cin kaza hadda rausayar da kai gefe alamar daΙinta takeji….
STORY CONTINUES BELOW
Jigum tayi haΙe da sake takurewa waje Ιaya akan Ζ΄ar katifartata,,, tabbas Dr.Sadeeq yacancanci ta sadaukar masa da duka soyayyarta ko dan saboda halaccin da yayi mata a rayuwa, bazatace batasan menene so ba, itacema zata ba da labari akan so, domin ta ΙanΙana zafinsa me matuΖar Ιaci da dafi,, idan tace Dr.Sadeeq baya burgeta tayi Ζarya, haka kuma idan tace Dr.Sadeeq baida abubuwan burgewa ajikinsa da zasu sa mace tasosa nan ma tayi Ζarya? tabbas Dr.Sadeeq baida wani makusa daga halayya Ιabi’a harma da surarsa yacika cikakken namiji, amma babban abun dake damunta shine batajin tsananin soyayyarsa acikin zuciyarta, bawai tana Ζinsa bane, kawai de zafin soyayyar tasa ne bataji a jiki da zuciyarta, ba kamar yanda taji na Zaid ba,, ada batajin soyayyar Dr.Sadeeq acikin zuciyarta amma ayanzu tayi ΖoΖari wajen ganin takoyawa zuciyarta sonsa, takuma yarda cewa zata iya zaman aure dashi domin baida wani makusa atattare dashi wanda zaisa a Ζisa, murmushine yasuΙuce mata sakamakon tunowa da tayi da irin kallon dayakeyi mata Ιazu, tabbas ya iya nuna soyayyarsa a fili, abu Ιaya ne ajikinsa wanda yake Ιaukar hankalinta, shine Ζwayar idanunsa, duk da cewa shi Ιin namiji ne amma yanada idanu masu kyau wanda zasu sanya maka nutsuwa aduk sanda ka kallesu, hakan yasa ako da yaushe takeson kallon cikin idanunsa amma bata iyawa saboda kunya….. Tunanin Zaid ne yakutso kansa cikin zuciyarta harsai da taji faΙuwar gaba,, “Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un!” shine abun da tashiga nanatawa acikin zuciyarta,, wannan wani irin bala’i ne? tunda Zaid yashigo cikin rayuwarta shikenan kuma komai nata ya ruguje, lallai itakam taΙaukeshi amatsayin annoba wanda gani da jinsa babu alkhairi …..1
Yau Kwanansa Ιaya da wuni Ιaya cur baisanya ko wani irin abinci abakinsa ba, sai ruwan giya dayake ta kwankwaΙa ba dare ba rana,, damuwa ce tayi masa mugun yawa abubuwa gaba Ιaya sun caΙemasa, kallo Ιaya zakai masa kafuskanci cewa yanacikin halin damuwa, domin kuwa lokaci Ιaya ya zabge rama ta bayyana kanta ajikinsa, yayinda manya manyan idanunsa suka sake fitowa waje,, wani irin zafi zuciyarsa keyi masa, baisan da yaushene kuma ta yaya yakamu da soyayyar Zahrah me tsanani haka ba, tunjiya yarasa nutsuwarsa a sakamon labari dayaji daga bakin wanda yasanya yana kulamasa da shiga da ficen Zahrah, inda yasanar masa cewa ankawowa Zahrah kayan lefe, iya Ζololuwar tashin hankali Zaid yashiga dajin wannan magana, sam be shirya wa rasa Zahrah ba saboda rasata dai dai yake da rasa rayuwarsa gaba Ιaya, akuma yanda yakejin matsanancin sonta a cikin zuciyarsa zai iya sadaukar da komai nasa gareta, ko da kuwa ransa ne…
Yanzuma zaune yake yatusa wani Ζaton hoton zanen fuskarta daya zana a daren jiya a gaba yana kallo, saboda tsabar kyawun da zanen yayi idan kagani bazamakace zane bane…
Idanunsa dake kan idanunta na cikin zanen ne suka kaΙa sukai jajur dasu. Saiyanzu yakejin tsanar kansa dakuma tsanar wannan banzan halin nasa, sai yanzu yake tsananin danasanin abun daya aikatawa Zahrah, haΖiΖa yasan cewa ya zalunci Zahrah ya cutar da’ita ya lalata mata rayuwa, kuma hakan da yayi mata shiya nisan ta masa ita, wani irin tsana ne Zahrah tayi masa haka? shin tasan irin zafi dakuma raΙaΙin dayakeji akanta kuwa? yadaina cin abinci tasanadiyar ta, wannan yasa ulcer tayi masa mummunan kamu, gakuma soyayyarta da ta sanya masa ciwo a zuciya,, ta wani Ιangare kuma yana fama da wani matsanancin ciwon kai wanda dashi yake kwana yake kuma tashi, cikinsa kuwa tamkar anhura masa wuta haka yakeji aciki,, hanu yasanya yashafi zanen fuskartata, tabbas idan baisamu Zahrah ba bazai taΙa iya cigaba da rayuwa ba,,, abun da Zaid baisani ba shine tuni ruwan hawaye sun cika idanunsa gangarowa kan fuskarsane kawai da basuyi ba, zumbur haka yamiΖe tsaye haΙe da zura silifas Ιinsa ko wayoyinsa bai tsaya Ιauka ba, haka yafice daga cikin Ιakin nasa….
Yana fita compound Ιin gidan nasu driver’n sa yaΖaraso garesa da sauri,,,, “Oga fita zamuyi ne?” driver’n yatambaya cike da girmamawa,, kai kawai Zaid ya Ιaga masa alamar “eh” jikin driver’n na rawa yace “Oga da wacce motar zamu fita?”
Cike da Ζosawa Zaid yace “Kowacce”
Driver yayi mamaki sosai dajin maganar Zaid domin yasan idan dai har fita Zaid Ιin zaiyi to sai yazaΙi motar dayakeso amma kuma sai gashi yau yace kowacce.. Wata haΙaΙΙiyar baΖar benz driver’n yatuΖo daga cikin parking space zuwa inda Zaid ke tsaye ya harΙe hannayensa acikin aljihun wandon track suit Ιin dake jikinsa..
Zaid nashiga cikin motar driver yabawa motar wuta yayinda me gadi ya wangale musu gate suka fice daga cikin gidan…..
Baffa ne zaune akan dakalin Ζofar gidan yana me latsa Ζ΄ar Ζaramar wayarsa, zaman da yayi Zahrah yake jira ta dawo daga aiken da yayi mata,, daf dashi motar tayi parking, hakan yasa Baffa ya kafe motar da’ido don ganin wanene zai fito daga ciki…
A hankali Zaid yabuΙe murfin motar yafito, kallonsa Baffa yashigayi daga sama har Ζasa saboda sarai yagane shine Ιan iskan me kuΙin da yamawa Zahrah fyaΙe, saida Baffa yagama Ζaremasa kallo kafun yakawar da kansa gefe…
Da sallama Zaid yaΖarasa wajen Baffa,, ciki ciki Baffa ya amsa masa sallaman, durΖusawa Zaid yayi haΙe dayin Ζasa da kansa cikin murya me sanyi yace “Kagafarceni Baffa, nasan ban kyautaba amma dan Allah kada ka hanani auren Zahrah, wallahi a yanda nakeji idan bansamu Zahrah ba mutuwa zanyi!”
Baki Baffa yasake yana kallon Zaid, namiji har namiji amma wai yana cewa idan bai auri Zahrah ba mutuwa zaiyi kuji iskanci fa,,
Sake Ιago kansa Zaid yayi haΙe da watsawa Baffa jajayen idanunsa, “Wlh Baffa yanzu da gaske nake aurenta zanyi, kada kace zaka hanani ita dan Allah, wallahi Zahrah tana da matuΖar mahimmanci acikin rayuwata!”
Yanzukam kallon tsab Baffa yashiga yi masa saida yaΙauki kusan minti biyu yana kallon Zaid Ιin kafun yaΙan nisa haΙe da cewa “BantaΙa tunanin kana da idanun da zaka dawo ka kallemuba, amma sai gashi kadawo kana kallona har kuma kana roΖona dana baka auren Zahrah, idan da kanasonta tunfarko mai yasa baka aureta ba kalalata mata rayuwa? ni bazance maka komai ba saide ince munbarka da Allah saboda bamu da yanda zamuyi dakai, amma kuma kasani bazan baka auren Zahrah ba harsai da amincewarta, idan har tace ta amince zata aureka shikenan nime iya baka aurenta ne” Baffa yana kaiwa nan a zancensa yatashi yayi shigewarsa cikin gida.. Da Ζyar Zaid ya’iya tashi ya zauna akan dakalin da Baffa yatashi hannayensa duka biyu yasanya ya dafe kansa dake yi masa nauyi kamar ze faΙo Ζasa…..
Da Ιan sauri take tafiya tana latsa wayanta burinta kawai shine taganta acikin gida, duk sanyin da akeyi yau yagama ratsata, saboda haka take Allah Allah ta’isa gida.. sam bata lura da akwai mutum a Ζofar gidan nasu ba dan hankalinta gaba Ιaya nakan wayartata…
“Zahrah!” taji anΖira sunanta da murya wacce bazata taΙa mantawa da’ita ba a iya tsawon rayuwarta…
Ja tayi ta tsaya haΙe da maida kallonta inda taji sautin muryar tafito,, tabbas kuwa ba gizo kunenta keyi mata ba shiΙinne dai, kallonta yashigayi da idanunsa wanda suka zama jajaye, itama tsayawa tayi tana kallonsa, a wannan karon kam babu alamar wasa kokuma tsoronsa akan fuskarta,, kallonsa takeyi ido cikin ido…
“Dan Allah Zahrah ki saurareni, wallahi inasonki inamiki so me tsanani, inamiki soyayyar da babu wani wanda zaiyi miki shi a duniyar nan, meyasa bazakisoni ba Zahrah? Inasonki, Inasonki, Inasonki da duka zuciyata, dan Allah kiyarda muyi aure Zahrah!” cikin rauni yaΖare maganartasa saikace ba jarumin namiji ba…
Kallonsa Zahrah tashigayi tundaga Ζasan sa harzuwa samansa, wani irin murmushi tayi masa wanda ita kaΙai tasan ma’anarsa,,, “BantaΙa tunanin zaka iyayin wannan jarumtar ba, Ζwarai kayi ΖoΖari dahar ka iya tunkarana da wannan maganar, sai de kuma tun awancan lokacin na faΙamaka kafita a rayuwata, idan duka mazan duniya zasu Ζare na gwammace na mutu babu aure dana aureka, ka kalleni da kyau bancancanci zama matar mazinaci kuma Ιangiya ba, niba irin matan nan bane da yacancan ci fasiΖai irinka su samuba, natsaneka Zaid tsana me tsanani, wlhy danaga ranar da zan zamo matarka gwamma acemin naga ranar mutuwa ta, katafi kawai Zaid kaje nabarka da Allah, kuma inaso kasani cewa yau Ιin nan za’a tsaidamin ranar aurena da wanda zuciyata ta aminta dashi, wanda yake kamili me tsoron Allah, shi ba kamar kai bane Ιan giya!” tanakaiwa nan azancenta tajuya daniyar shigewa cikin gida…
Dasauri Zaid ya kamo hanunta haΙe da jawota da Ζarfi tafaΙa cikin jikinsa, dai dau lokacin ne kuma motar Dr.Sadeeq taΖaraso wajen….Saurin turesa tayi haΙe da hankaΙasa gefe da iya Ζarfinta ta Ζwace jikinta daga nasa, wani irin mugun kallo tashiga yimasa haΙe da tofar da yawu aΖasa, da ace wulaΖanta Ιan adam abune me kyau to tabbas da akan fuskarsa zata tofa wan nan yawun ko hakan zai sanya ya gamsu da irin tsantsar tsanar da takeyi masa.
“Banafatan na sake haΙa jikina da wan nan Ζazamemmen jikin naka mai Ιauke da tarin najasa!” cike da tsananin Ζyamata Zahrah ta faΙi haka ga Zaid haΙe da juyawa tanufi hanyar shiga gida..+
“Koda kuwa na daina aikata zina nakuma daina shan giya?” Zaid yafaΙi haka cikin dakakkiyar muryarsa…
Cak ta tsayawa daga tafiyan dakeyi, sosai maganar tasa ta daki zuciyarta..
A hankali yashiga takowa zuwa inda take saida yazo gaf da’ita kafun ya tsaya……. ” I promise to leave all my bad habit if you wish to marry me, I love you Zahrah, trust me for the sake of God, i will not hurt you!” gaba Ιaya muryarsa tayi rauni dagajin muryartasa kasan cewa yana cikin matsanancin damuwa…1
Idanunta da suka kawo ruwa ta Ιago ta watsa masa su,,,,, Shi Ιin ma kallon ta yakeyi da idanunsa wanda suka zama tamkar an watsa musu garin barkono,, sun Ιauki tsawon mintuna biyu suna kallon juna kafun da ga bisani Zahrah tajuya ta shige cikin gida, ko sake waiwayosa batayi ba yayinda yashiga Ζiran sunanta amma bata amsa masa ba harta shige cikin gida, because tagaji da wannan Ιan iskan yaudaran nasa, yanzukam bazata iya Ιauka ba….
Iskan dake cikin bakinsa ya fesar haΙe da meda duka hannayensa cikin aljihun wandonsa, cikin sanyin jiki haka yakoma cikin motarsa driver yayimawa motar key suka Ιauki hanyar fita unguwar batare da sun kula da Dr.Sadeeq dake zaune cikin motarsa ba…
HaΖoransa ya sanya ya danne laΙΙansa na Ζasa komai daya faru akan idanunsa ya wakana sai de baijiyo magan ganun da suka shiga tsakaninsu ba,, wani irin Ιaci yaji maΖoshinsa nayi, iya matuΖa Ιacin rai yashigesa, bakomaine yafi komai Ζona masa ransa ba kamar yanda yaga Zaid yajawo Zahrah jikinsa, hakanan yaji wani irin mugun kishi ya turnuΖe masa zuciya,, babban abun dayafi Ιaga masa hankali shine yanayin daya hango fuskar Zahrah, tabbas yafuskanci wani Ιoyayyen abu daga gareta,,, key yayi mawa motarsa cikin Ζunan rai yayi reverse haΙe da barin Ζofar gidan nasu batare da ya aika ayi masa Ζiranta ba..
Zahrah na shiga cikin Ιakinta ta durΖusa a Ζasa haΙe da fashewa da wani irin kuka me tsuma zuciya kaicon zuciyarta da ta so mata namiji irin Zaid, ashe da gaske shiΙin mazinaci ne tunda gashi da bakinsa yafaΙa, kuka tashiga yi tamkar wacce aka sanarmawa da ranar mutuwarta, yayinda wani abu yataso ya tokare mata Ζirji wanda batasan komenene shi ba kamar yanda batasan kukan me takeyi ba…
Driver yana parking motar Zaid yace yafita ya bashi waje, aikuwa babu musu driver’n yafita daga cikin motar….. Kansa ya kafa ajikin kujera haΙe da fidda wani irin zazzafan numfashi ta bakinsa, zuwa yanzu kam bazai iya jurewa ba, sam bazai iya jure raΙaΙi dakuma azaban soyayyar Zahrah dake damunsa ba, tabbas da ace zai iya to da yayi iya ka ΖoΖarinsa wajen ganin ya yakice soyayyarta acikin zuciyarsa amma hakan bazai yiwuba domin kuwa duk kowani kwanan duniya soyayyarta Ζara ninkuwa takeyi acikin zuciyarsa, zuwa yanzu soyayyar Zahrah babu inda bata ratsa acikin jikinsa ba,,,, a Ζalla yakai kusan 30 minute acikin motar yana saΖawa da kuncewa, da Ζyar ya’iya fitowa daga cikin motar kai tsaye yanufi babban parlour’nsa dake cikin guest house Ιin nasa, domin kuwa daga gidan su Zahrah guest house Ιinsa suka yiyo….
STORY CONTINUES BELOW
Yana shiga cikin falon ya faΙa kan doguwar kujera haΙe da lumshe kyawawan idanunsa, kansa ne ke saramasa yayinda juwa ke Ιibansa, lallai yazame masa dole yasamawa kansa mafita, yazama dole yafarka daga wannan mafarkin daya keyi tabbas al’amuransa a yanzu suna masa kama da al’amara,, tabbas yana buΖatar samun relief daga damuwar dayake ciki, amma sai dai babu amfanin shangiya a yanzu domin kuwa koda yashama bata basa wani relief Ιin da ya kamata, miΖewa yayi yashiga cikin Ιakinsa, kai tsaye wani Ιan drower yanufa haΙe da buΙewa, hanu yasanya ya Ιauko wata wayarsa Ζirar techno phantom 9 wanda dama yana ajewane saboda rana irin haka, kasancewar baifito da wayoyinsa ba duk yabarsu a gida,, yana kunna wayar ya laluΙo wata lamba haΙe da turawa lambar text message, yana ganin alamar saΖon ya isa inda yakeson yaje yayi switch off Ιin wayar haΙe da maidata inda ya Ιaukota kwanciya yayi akan makeken gadonsa wanda yasha shumfuΙa ta alfarma, cusa kansa yayi cikin pillow haΙe da soma fitar da numfarfashi akai akai….
A hankali taturo Ζofar Ιakin wanda kafun ma tashigo tuni Ζamshinta yarigata shigowa, sanye take da jan wando pencil wanda yayi matuΖar bayyana kyakkyawar surar jikinta yayinda rigarta yakasance baΖa me kyau, rigan irin masu faΙin wuyan nan ne hakan ne yasanya manya manyan breast Ιinta bayyana kansu tasaman rigar,, takalmine me uban tsini a Ζafarta yayinda ta tufke dogon gashin kanta da jan ribbon kalan wandonta,, kallo Ιaya zakayi mata kafahimci cewa wayayyar macece Ζ΄ar duma, shigarta kaΙai ya isa yabayyana maka ainihin ko wacece ita, saboda bashigane da mata masu mutumci sukeyi su fita ba kamar yanda ita tayi, domin kuwa ko Ιan kwali babu akanta, wani irin murmushine kwance akan fuskarta dake nuna alamar cewa tana cikin farinciki,, lumshe idanunta tayi haΙe da buΙesu alokaci guda, kallon surarsa kaΙai ya isa sanya mata nutsuwa, tajima tana tsumayi da kuma fatan Allah ya sake Ιaurata akansa, harta cire rai saikuma gashi yau shi da kansa ya gayyatota, lallai zata iya cewa a rana irin ta yau tafi kowa sa’a..
Duk da yaji Ζamshin turarenta acikin hancinsa hakan baisanya yaΙago kansa ba,,
Cikin taku irin na matan da suka goge wajen iya Ιaukar hankalin Ιa namiji tashiga takowa har zuwa inda yake kwance ya yinda juyawa Ζofa baya…
Hanunta tasanya a bayan wuyansa haΙe da soma shafawa a hankali,, cikin wata murya me sanyi dajan hankali tace “Man!”
Shiru yayi bai amsa mata ba, duk da kuwa cewa yanajinta,,, ganin bai amsa taba yasanya tayi murmushi haΙe da cire takalman dake Ζafarta ta hawo kan gadon,, bakinta ta sanya adai dai saitin tsakiyar bayansa tashiga tsotsa haΙe da shafa bayan wuyansa a hankali,,,, wani irin zubawa Zaid yaji tsikar jikinsa tayi, adai dai sanda take ΖoΖarin nuna masa wani sabon salo…. “Meenal!” yaΖira sunanta da wata irin murya wacce ta riga da ta cushe..
Murmushi Meenal tayi haΙe da mirginowa ta dawo gabansa suna fuskantar juna, lumshe idanunta tayi alokacin da tayi arba da kyakkyawar fuskarsa, wallahi tana matuΖar son Zaid komai nasa me kyaune daga ciki har waje, ba abunda yake Ιaukar hankalinta akan fuskarsa kamar wannan kyakkyawan sajen nasa dayake shan gyara da mayuka masu kyaun gaske..
“Nayi kewarka Man, ashe de kaima kayi kewata? katafi ka barni da tunanin daΙin da kajiyar dani, wanda har rana me kamar ta yau babu wani Ιa namiji da yajiyar dani kwatan kwacin wannan” Meenal taΖare maganar cikin yanayi na shagwaΙa haΙe da sake matsowa tashige cikin jikinsa,, Ιan guntun murmushi yasakar mata haΙe da soma Ζarewa fuskarta kallo, Meenal kyakkyawar yarinyace wanda kyawun nata kuma yazama na Ιan maciji, domin kuwa Meenal tantiriyar Ζ΄ar iska ce kuma cikakkiyar mazinaciya wanda idan ta kafamawa namiji Ζahon zuΖa duk nuΖu nuΖunsa sai ta jefasa cikin raminta, sai dai idan kuma shiΙin ya kasance gwaska na gasken gasken, tofa nan ne zasu dai dai ta, kamar dai Zaid da ta buga ta rawa yaΖi faΙowa raminta, domin kuwa shi Ιin ma Ιan iskane me lasisi san nan kuma gwaska ne me zaman kansa, wannan yasa Meenal takasa turasa a cikin raminta..
Hanu Meenal tasanya akan faffaΙan Ζirjinsa tashiga shafawa haΙe da cusa kanta acikin wuyansa cike da Ζwarewa take manna masa kiss,, tamkar wata mayya haka take sake shigewa cikin jikinsa..
STORY CONTINUES BELOW
Lumshe idanunsa yayi haΙe da cusa hanunsa cikin sumar kanta,, take yasoma sauΖe ajiyar zuciya akai akai domin kuwa gani yake tamkar Zahrah ce kwance haka a jikinsa,, idanu Meenal ta kafesa dashi cike da mamakin irin sauyawan da yayi, nafarko ta hango tarin damuwa acikin idanunsa yayinda na biyu kuma ta hango wani abu mai Ιaure kai acikin idanunsa,,, “Man!” taΖira sunansa cikin wata irin murya, idanunsa kawai ya jefa acikin nata idanun batare da yace da’ita komai ba,, dama haka takeso burinta shine yaΙaga kyawawan idanunsa ya kalleta,, take ta sauya salon nata kallon ta marairaice idanunta,, fuskarta ta matso daf da tashi fuskar lokaci Ιaya tasoma ΖoΖarin haΙe bakinsu waje Ιaya, kamar koda yaushe Ζin aminta da hakan yayi da sauri ya kawar da kansa gefe, saboda hakan baya daga cikin tsarinsa haΙa miyau da matan bariki, domin babu abu mafi saurin sanya shaΖuwa kamar haΙakar yawun baki, sosai kiss yake sanya shaΖuwa a tsakanin masu yinsa, domin haΙuwar yawun bakuna biyu wani sinadari ne na musamman,,,, bata damu ba domin dama tasansa bayawa mace kiss batakuma san dalilinsa na hakan ba, wan nan kuma ita duk ba damuwarta bane matuΖar zai kusanceta to zatafi kowa farinciki,,,,, hanunta ta sanya akan mararsa tashiga shafawa a hankali haΙe da Ιaura bakinta akan nipples Ιinsa, jawota yasakeyi jikinsa bayan ya cire mata Ζ΄ar Ζaramar rigar jikinta, kansa ya cusa acikin Ζirjinta yana me shaΖar Ζamshin turarenta, haΙe da sanya hannayensa a bayanta yasoma shafawa a hankali,, take Meenal tasoma sauΖe numfashi akai akai dama Ζiris take jira saboda akunne take Ζwarai… Lokaci Ιaya Meenal tarikice wasu irin salo take gwadawa Zaid masu sanya mutum ya fita a hayyacinsa, yayinda shima yagama ruΙata da nasa salon har saida yakusa sanyata shiΙewa,, amma kuma wani abun mamakin shine yanayin hakan ne cikin wani irin yanayi wanda baisan dame zai Ζira sunan yanayin ba, kwata kwata baijin wani abu mai suna sha’awa a jikinsa duk dakuwa irin romancing Ιinsa da Meenal keyi, lumshe idanunsa yayi haΙe da jawota yadawo da ita Ζasansa aniyarsa shine ya kusanceta amma kuma sai yaji zuciyarsa tashiga bugawa da sauri sauri yayinda Zahrah tashigo cikin ransa ta tsaya cak, take idanunsa suka haskomasa irin kallon tsanan da tayi masa Ιazu, nan danan yaji komai yafice masa arai, da sauri ya ture Meenal gefe haΙe da sanya hanu ya dafe kansa da yayi masa nauyi, da wani irin kallo Meenal da takai Ζololuwa wajen sha’awa ta bisa, meye haka yakeyi? badai halin nasa na wulaΖanci zai gwada mata ba? idan kuwa hakane Zaid yacuceta, saida yagama jefata acikin masifaffiyar sha’awarsa san nan yajuya mata baya, hanu tasanya ta rungumosa ta baya haΙe da soma goga masa breast Ιinta akan bayansa “Meke damunka Man? kada kabari damuwa ya hanaka jin daΙin rayuwa please” tafaΙi haka cikin narkakkiyar murya, hanunsa yasanya ya zameta daga jikinsa wani irin haushinta ma yake ji, miΖewa yayi direct ya wuce toilet Ιinsa ko waiwayota baiyi ba, baki sake haka Meenal tabisa da kallo harya shige cikin toilet Ιin,, kuka ta fashe dashi haΙe da matse cinyoyinta, tsakani da Allah take kuka domin kuwa iyaka cuta a wajenta shine abun da Zaid yayi mata…
Zaid kuwa yanashiga bathroom ya zame wandon dake jikinsa haΙe da nufar inda babban bathtub Ιin wankansa yake, ruwa ne me kyau da tsabta acikin bathtub Ιin, amma duk da haka saida ya zubar yakuma taran wani ruwan, turaren wankansa me daΙin Ζamshi ya sanya a cikin ruwan haΙe da shiga cikin ruwan ya kwanta a hankali,, lumshe idanunsa yayi haΙi da jingina kansa, zafi yakeji adai dai saitin zuciyarsa, tabbas yanaji ajikinsa cewa akwai abun da zai faru dashi bayan wanda yake faruwa dashi yanzu, “wace irin soyayya ce haka yake yiwa Zahrah me zafi?” tambayar da kullum sai yayimawa kansa kenan, lallai yau yasake tabbatar mawa kansa cewa yazama mutum me rauni, A she dama akwai wata rana da zai iya kasancewa haka? yaΖira Meenal ne don taΙebemasa kewa yakuma samu ya rage tarin sha’awar dake damunsa, domin kuwa har wani ciwo yakeji mararsa nayi masa, amma kuma sai gashi ya kasayin komai da Meenal, ashe ba Meenal Ιin bace muradinsa Zahrah ce, haΖiΖa yasake yardarwa kansa cewa abunda kake so shi yake wahalceka sannan kuma yasake tabbatar mawa kansa cewa ΖAUNA guda Ιayane tal aduniya, SO ne kawai yake da yawa, amma Ζauna Ζaunace,, kafun yaΖira Meenal yayi tunanin cewa idan tazo zata gusar masa da damuwarsa, sai kuma bayan tazo yaga ashe bazata iya ba, ashe yin sex da shan giya basune maganin damuwarsa ba, Zahrah har lau itace maganin damuwar sa,, anya kuwa zai warke daga damuwar nan tasa?
STORY CONTINUES BELOW
Yajima acikin bathroom kafun yayi wanka yafito jikinsa sanye da farar rigar wanka,, kallonsa ya maida kan gado inda yabar Meenal don ganin wani hali ta ke ciki domin kuwa sarai yaji kukanta lokacin dayake cikin bathroom,, dariyane taso Ζwacemai sakamakon ganin Meenal da yayi takure a can Ζarshen gado tana bacci, yayinda ta cusa hanunta na hagu a Ζasanta, sarai yasan Meenal jarabebbiya ce yanzu haka fingering tayi don samawa kanta relief, abun da yafi tsana kenan wato mutum yayi amfani da kansa don biyan buΖatarsa, amma kuma wannan halin Meenal ne,, kai kawai ya girgiza haΙe da nufan gaban dressing mirror Ιinsa, vaseline yashafa ajikinsa kasancewar garin ana Ιan yanayi na sanyi, saida ya feshe jikinsa da body spray kafun yasanya kayansa riga da wando na jeans masu kauri, sosai kayan sukai masa kyau, kuΙaΙe yaciro a cikin drower Ιinsa ya ajiye a kusa da Meenal daketa sharan bacci, kana yayi ficewarsa daga Ιakin, direct bai zarce ko inaba sai compound Ιin gidan, yanzu kam shida kansa yakeson yayi tuΖi, don hakane ma yazaΙi BMW blue colour amatsayin wacce zai fita da ita….
Dr.Sadeeq
Duk yanda Dr.Sadeeq yaso samawa kansa nutsuwa hakan yagagara domin kuwa sam zuciyarsa bata amince da zuwa wajen Zahrah da Zaid keyi ba, duk da yau yafara ganinsa aΖofar gidan su Zahrah’n amma jikinsa ya basa cewa ba yaune zuwansa na farko ba, amma bakomai zaiyi maganin abunne zai nisanta Zahrah da Zaid nisantawa me tsanani kuwa, da wannan tunanin bacci ya Ιaukesa…
Washe Gari.
Dasassafe Zahrah ta shirya tayi tafiyarta makaranta sai dai a ranta tana mamakin rashin Ζiranta da Dr.Sadeeq yayi, rabonta dashi tunjiya da yamma sunkuma rabu dashi akan cewa zai Ζirata sai gashi kuma har zuwa yanzu bai Ζirata ba, uzuri tayi masa akan cewa ko aikine yayi masa yawa domin tasan hakanan Dr.Sadeeq bazaiΖi Ζiranta ba…
Tana tafiya ba jimawa motar Dr.Sadeeq ta tsaya a Ζofar gidan nasu, fitowa yayi daga cikin motar yasha adonsa cikin blue Ιin shadda sosai kuma yayi kyau,, yaro ya aika cikin gidan yace yace ana sallama,, bajimawa yaron daya aika yadawo ya shaida masa ance me gidan yana fitowa…. Washe da baki Baffa yaΖaraso wajen Dr.Sadeeq dake tsaye ” Maraba da Likita, dama kaine ai da kashigo ciki amma ka tsaya a waje sai kace wani baΖo”
Murmushi Dr.Sadeeq yayi cike da girmamawa ya sunne kansa Ζasa haΙe da durΖusawa ya gaishe da Baffa,, fuska cike da fari’a Baffa ya amsa gaisuwan,,,
“Aikuwa kayi rashin sa’a domin kuwa mutumiyar taka bata jima da fita a gidan ba, tatafi makaranta ko karyawa bata tsaya tayi ba, amma ina ga zaifi kyau mushiga daga ciki ko”
“A’a Baffa nan Ιin ma yayi, dama wajenka nazo ae”
“To to masha Allah, saimu zauna ae ko abisa dakalin nan” Baffa yaΖare maganar yana meyi mawa Dr.Sadeeq nuni da dakalin Ζofar gidan.
Duk yanda Baffa yaso Dr.Sadeeq ya hau kan dakalin su zauna Ζiyawa yayi, domin kuwa Baffa surikinsa ne baidace ace sun zauna gaf da juna ba kodan saboda kara da matuntawa,,
“Shikenan to tunda dae kaΖi zama, inajinka Allah yasa dai lafiya?”
Kansa yaΙan sosa haΙe da sakin murmushi “Lafiya Ζalau Baffa dama akan maganan aure nane da Zahrah…” sai kuma yayi shiru ya kasa Ζarasa maganar dake cikin bakinsa, gani yake tamkar idan yafaΙi maganar kai tsaye Baffa zaice masa yayi gaggawa ko kuma yace yayi rashin kunya…
“Ka kwantar da hankalinka Likita kafaΙi duk wani abu dake ranka” Baffa yafaΙi haka ga doctor Ιin..
“Am dama…dama inaso ne kabani izini nasake turo magabatana dan sukawo sadaki san nan kuma a tsaida ranar aure”
“Alhmdlh to ai wannan abun farinciki ne Likita, wannan ae bawani abun damuwa bane, nabaka dama ka turosu aduk sanda kakeso, sai de kuma zakaΙanyi haΖuri, saboda zansa lokacin da Ιan tsayi saboda kasan ba a yin aure kai tsaye haka dole sai anΙanyi mawa yarinya sayayya, ina fata hakan bazai sosa ranka ba?”
Murmushin jin daΙi Dr.Sadeeq yayi haΙe da cewa “Naji daΙi sosai Baffa, amma kuma maganar sayayya basai kun wahalar da kanku ba, domin zuwa yanzu gidan da zamu zauna baya buΖatan komai, saboda haka don Allah kada kusa kanku a wahala”
Murmushi Baffa yayi haΙe da cewa “Ζwarai mungode da wannan ΖoΖarin naka, amma sai de nace kayi haΖuri, duk da cewa mahaifin Zahrah baya raye ni Ζaninsa ina raye kuma niΙin ma ubane a wajenta, zan yi amfani da Ιan abun da nake dasu wajen ganin namata kayan Ιaki iya dede Ζarfina, kamarde yanda kowani uba keyiwa Ζ΄arsa, wannan shine kaΙai gatan da zamu iyayi mata a yanzu” Baffa yafaΙi haka da iyaka gaskiyarsa..
Ajiyar Zuciya Dr.Sadeeq ya sauΖe, haΖiΖa shi Zahrah kawai yakeso bawai wani abu na daban ba, kuma shi baiso akawota da komai, domin musamman ya ware mata Ιangarenta, kuma tuni yabawa wani abokinsa me saida furnitures a Dubai order akan akawomasa setin kujeru dakuma gado harma da duk wani abu wanda yasan zai Ζawata Ιaki,, amma tunda yaga Baffa yadage akan cewa shima zaiyi iya nasa ΖoΖarin shikenan zai ware wani Ιaki na da ban idan yaso sai a sanya kayan da Baffan yayi mata acan,,, cike da mutuntawa Baffa da Dr.Sadeeq sukayi sallama….
Baffa na shiga gida ya kalli Inna dake zaune,, “Salame inajin fa tafiyana yola yagabato idan banje jibi ba to zanje gata insha Allah”
Fuska Ιauke da mamaki Inna ke kallonsa, “Yola kuma Malam?”
“Ζwarai kuwa, kinga fitana Ιin nan to yaron nan ne Sadeeq yazo min da maganar cewa inbasa dama yaturo magabatansa don sukawo sadaki akuma sa rana, to ni dai nace yaturosu duk sanda yakeso, yanzu dole zanje yola insanya fili dakuma gonan nan namu na gado a kasuwa idan aka siya intarkata kuΙin nan nasamu nasaiwa yarinyarnan kayan Ιaki dakuma kayan aikace aikace kamar de yanda kowani iyaye kemawa Ζ΄arsu dan baiyiwuwa ace mu miΖata haka”
Ajiyar zuciya Inna tasauΖe haΙe da gyara zama ” Duk naji batunka Malam, amma kuma mezai hana kabar shi mijin nata yayi mata komai, ae naga yana da halin da zai iyayi mata fiye da wannan ma”
Murmushi kawai Baffa yayi shi kam tun ba yau ba yasan cewa bakoda yaushe ne Inna take gane karatun da’ake biya mata ba, don haka baiΖara cewa da’ita komai ba yawuce Ιakinsa, domin yasan kozai shekara a wajen yanason ganar da’ita tofa bazata fahimcesa ba,,, Inna kuwa baΖin ciki ne yakamata ina ma laifin yace zaiΖara jari da kuΙin, sai yace wani wai zai siyawa Zahrah kayan Ιaki,, haka taita Ζananun maganganunta babu maijinta ma balle yatanka mata……
Da yamma Dr.Sadeeq yaΖira Baffa yasanar masa cewa Baffansa zaizo da dare donsu tsaida magana, duk da cewa Baffa yayi mamakin sauri irin na Dr.Sadeeq Ιin amma saiya share yace Allah yakawosu lafiya,,
Hargida Baffa yaje yasanarwa Alhaji Umar abun da Dr.Sadeeq yace, kuma dama Alhaji Umar Ιin tuni yasan da maganar saboda duk abun da yafaru Baffa yanazuwa ya sanarmasa har kawo lefen da akayi ma Baffa yasanar masa,, sosai Alhaji Umar yayi murna yakumace zaizo gidan Baffa’n da dare a ΖarΙi baΖin dashi……
Kamar yanda Dr.Sadeeq yafaΙa hakane yakasance domin ana idar da sallan Isha Baffa Amadu da wani shaΖiΖin amininsa suka zo gidansu Zahrah,, sosai Baffa da Alhaji Umar suka musu tarba na mutunci,, zama sukayi haΙe dayin magana ta fahimtar juna, nan Baffa Amadu ya miΖa sadakin Zahrah ga Baffa naira dubu Ιari (100,000) bawani Ιata lokaci Baffa yasanya lokacin aure wata Ιaya, aikuwa take kowannensu yacika da farinciki haka sukayi sallama cike da girmama juna……
.Idan kin gama rubuce rubucen banzan naki kije Baffan ki nanemanki!” Inna tafaΙi haka aΖufule, ko jiran amsan da Zahrah zata bata batayi ba tayi ficewarta acikin Ιakin,,, da kallon mamaki Zahrah tabi bayan Inna wai meke faruwane tun dawowarta amakaranta tafuskanci cewa ran Inna a matuΖar Ιace yake da’ita, domin kuwa ko abincin rana Inna batayi mata tayi ba, kamar yanda ta sabayi mata kullum, to koma dai menene Allah yasa bawani abu bane me zafi… Tattara books Ιin dake gabanta tayi haΙe da miΖewa ta sanya hijab a jikinta kana tafice daga cikin Ιakin…..+
Da sallama Ιauke a bakinta takutsa kanta cikin Ιakin Baffan nata,, zama tayi akan tabarman dake shimfuΙe a tsakiyan Ιaki, haΙe dayi mawa Baffa barka da gida,, fuska Ιauke da fari’a Baffa ya amsa mata..
Gyara zama Baffa yayi haΙe da cewa “Bakomai yasa nayi Ζirankiba sai dan na sanar dake abun dayake faruwa sannan kuma na danΖamiki haΖΖin ki a hanunki, yau da safe yaron nan likita yazo yasameni akan cewa zaituro magabatansa don sukawo sadakin ki, nakuma bashi dama, to yanzu dai sun riga da sun danΖamin sadakin ki a hanuna saboda haka ga abunki naira dubu Ιari ne cus nakine halak malak” Baffa yaΖare maganar yana me miΖa ma Zahrah maΖudan kuΙin dake hanunsa….
Gaba Ιaya jitayi jikinta yayi sanyi laΖwas gaba Ιaya duk wani kuzarinta ya gudu, hakanan taji wani iri a cikin zuciyarta.
“Ki karΙa mana Zahrah” Baffa yafaΙi haka ganin da yayi ko Ιago kanta takasa yi.
Girgiza kanta ta shigayi a hankali cikin muryarta me sanyi tace “Duk abun da ka yanke a gareni Baffa dai dai ne, amma maganar sadaki ka riΖe a wajenka, saboda ko kabani babu abun da zanyi dasu!” taΖare maganar cikin ladabi.
“A’a Zahrah ki karΙi abunki haΖΖin kine, saboda haka nima babu abunda zanyi dashi ki karΙi abunki saiki adana a wajenki, idan kuma wani abu zaki saya saiki saya, amma kada kiyi almubazzaranci dasu, zaifi kyau kisaya abu me mahimmanci wanda zai amfaneki yanzu ko gaba” maganar da tafito daga bakin Baffa kenan.
Shiru Zahrah tayi ita tama rasa yanda zatayi gaba Ιaya yanayinta yasauya, cikin sanyin jiki Zahrah tasanya hanu ta karΙi sadakin nata a hanun Baffa bawai dan ranta yasoba sai dan Baffa ya matsa akan cewa saita karΙa..
“Yauwa kinga idan kika riΖe abunki a hanunki ae yafi ko, sai kuma maganar sa rana, nasa nanda wata Ιaya, ai inaganin hakan yayi domin kafun lokacin insha Allah mungama iya ΖoΖarin da zamuyi wajen sayan Ζ΄an kayayyakin Ιaki”
Wannan magana ta sa rana yafi komai rugaza mata zuciya, fiye da maganan sadaki, haka nan taji faΙuwar gaban da takeji ya tsananta,, amma haka tayi mawa Baffa sallama cikin sanyin jiki tanufi Ιakinta…
Zama tayi akan katifarta haΙe da rumtse idanunta, take hawaye suka shiga fitowa daga cikin idanunta suna gudu akan fuskarta,, shikenan yanzu saura mata wata Ιaya tazamo matar aure? tambayar da tayiwa kanta kenan, bazata iya faΙan wani irin yanayi ta tsinci kanta aciki ba, fargaba ne ko kuma tsoro ne shine abun da bata sani ba,, idanunta ta buΙe haΙe da maida kallonta ga kuΙaΙen dake riΖe a hanunta,, tsurawa kuΙin idanu tayi tamkar mai son gano wani abu ajikin kuΙin,, hawayene suka kuma Ιalle mata, batasan dawani idanu zata kalli Dr.Sadeeq ba, shi wani irin mutum ne? yasani Ζwarai cewa ita ba cikakkiyar budurwa bace da ita da bazawara duk Ιaya suke, amma kuma shine ya cire maΖudan kuΙaΙensa yabada amatsayin sadakinta alhali kuma farashinta baikai haka ba, ita ba irin matan nan bane dasuka dace a sayesu da tsada har haka ba, domin kuwa acikin abubuwa goma da zasu Ζara farashinta babu kaso tara, saboda haka bata cancanci wannan sadaki ba,, hanu tasanya ta share hawayenta, haΖiΖa bazatace batason Dr.Sadeeq ba amma kuma batajin son nasa acikin jini da jikinta, amma hakan bawai wani abu ne da zaisanya taΖi aurensa ba, domin shi ne ma mutum na farko aduniya daya cancanci ta aura, kodan halaccin daya gwada mata a rayuwa…. Cikin wata jakarta tasanya kuΙin sadakin nata, haΙe da dawowa ta kwanta akan katifarta, bazama ta iya Ζarisa assigment Ιin nata ba domin kuwa gaba Ιaya yanayinta yasauya damuwa ta bayyana a tattare da’ita,, da Ζyar ta iya jawo wayarta taΖira Husnah ta sanar mata da duk wani abun daya faru,, daΙine ya kama Husnah sosai take ta hau farinciki haΙe da cewa gobe zatazo yakamata su fara shirye shiryen biki tunda wuri, domin wata Ιaya bawani lokaci ne me tsawo ba idan har darai da kuma lafiya…
STORY CONTINUES BELOW
*****
“Kiyi kuka da kyau Saleema amma kuma kozaki mutu bazaki auri Sadeeq ba matuΖar bai fasa auren da zaiyi da waccar Ζ΄ar ΖasΖantattun mutanen ba, ni bazan iya haΙa iri da jinsin matsiyata ba!” Abunda Hajiya Habiba take faΙa kenan cikin Ιacin rai.
Ζago kai Saleema tayi takalli mahaifiyarta ta fuska caΙa caΙa da hawaye, cikin muryar kuka Saleema tasoma cewa ” Wlhy inasonsa Mom kuma bazan taΙa iya auren wani bayan shiba, nidai na amince zan aureshi a haka, idan yaso bayan auren sai nasan yanda zanyi naΖori ita yarinyar”
Kallon ke shashasha ce Hajiya Habiba tashiga yi mawa Saleema, cike da baΖin ciki taja tsuka haΙe da watsawa Saleema’n harara “Nibansan yaushe zuciyarki ta mutuba wlhy Saleema, ashe ke baki da hankali? to nifa kisani nagama maganata aure da Sadeeq ne anfasa, kuma suzo su kwashe lefensu bama buΖata, domin kuwa kamarni Hajiya Habiba bazan lamunci cinfuskaba, saboda abunda suke shirin yi yanzu cin fuskane a gareni” fuuuu haka tayi wucewarta sama, tabar Saleema tana ta ruskar kuka, saikace wanda akace ubanta ya mutu….
****
Baffa na zaune a wajen sana’arsa wasu maka makan motoci guda biyu suka faka adaf dashi.. Sosai yayi mamakin ganin Alhaji Ma’aruf yakuma dawowa garesa a karo na biyu, wanda ko kusa baiyi tunanin haka ba..
Bayan sun gaisane Alhaji Ma’aruf ya nisa haΙe da cewa “Nasan zakayi mamakin dawowata gareka Malam Hayatu, sai de kuma me nema baikamata ya gajiya ba”
Ajiyar zuciya Baffa yasauΖe haΙe da tattaro duka nutsuwarsa yadubi Alhaji Ma’aruf…
“Bazan taΙa Ιoyemaka ba Alhaji, kamardai yanda nafaΙa maka afarko yanzu ma hakane, domin maganan da nakeyi maka yanzu ma jiya aka kawo sadakin yarinyar, saboda haka sedai nace kawai kuyi haΖuri”
Kai Alhaji Ma’aruf yashiga jinjinawa, zuwa yanzu dolensa zaibawa Zaid haΖuri akan cewa yayi haΖuri yacire yarinyar aransa, domin kuwa idan ba wani ikon Allah ba to babu alamun cewa Zaid zaisamu auren yarinyarnan Zahrah..
Haka Baffa da Alhaji Ma’aruf suka rabu, bayan Alhajin yayi mawa Baffa alkhairi maiyawa, amma sam wannan karon Baffa yaΖi karΙa yace bai buΖata, duk yanda Alhaji Ma’aruf yaso Baffa ya amshi kuΙin hakan bai samu ba,, haka Alhaji Ma’aruf yayimawa Baffa sallama shida tawagar body guard Ιinsa suka bar wajen, sam Alhaji Ma’aruf baiji daΙin hakan ba, yaso ace Ιansa yasamu abunda yakeso…..
Cike da tsananin damuwa Alhaji Ma’aruf ke kallon Zaid dake zaune a Ζasa yayi shiru, gaba Ιaya ya sanja, komai nasa yazama sanyi sanyi, ga alamomin damuwa da suka bayyana kansu a jikinsa, baisan wani irin masifaffen soyayya Ιannasa ya kamu dashi ba, baimasan taya ya Zaid zai Ιauki maganar da zai faΙa masa ba, amma dai yazama dole yafaΙa masa gaskiya amatsayinsa na mahaifinsa.
“Zaid!”
Alhaji Ma’aruf yaΖira sunan Zaid murya a tausashe.
“Na’am Dad” Zaid ya amsa murya Ζasa Ζasa.
“Inaso kabani hankali da nutsuwarka, dan Allah Zaid ka kwantar da hankalinka, nasani kuma kaima kasani nema cikin nema haramunne, kacire wannan yarinya acikin zuciyarka domin kuwa yau naje nasamu shi Baffan nata, yakuma shaidamin cewa a halin yanzu har ya karΙi sadakinta, saboda haka zaifi kyau kacireta a zuciyarka, kanemi wata nasan babu wata mace da zata Ζika”
Tamkar wanda Dad Ιin ya watsa masa ruwan zafi haka yaji sauΖar maganganun mahaifinsa acikin kunnuwansa, da sauri yaΙago jajayen idanunsa ya watsawa mahaifin nasa su,, bakinsa na rawa yace “AnkarΙi sadakinta kuma Dad?”
“Ζwarai kuwa Zaid abunda Baffan nata yafaΙamin kenan, shiyasa nace ka cireta a ranka”
Kai Zaid yashiga girgizawa,,,,, “Bazai taΙa yiwuwaba Dad, wlhy wani bazai taΙa auran Zahrah ba matuΖar ina numfashi acikin duniyar nan, inasonta fa Dad meyasa bazaku gane hakan ba? bazan iya cigaba da rayuwaba idan har babu Zahrah a gareni, nasan laifinane Dad, amma duk da haka bai dace a hanani Zahrah ba, saboda inasonta inamata wani irin so me tsanani please Dad niko yanzu dan Allah a Ιaura mana aure idan yaso daga baya ni na amince zan shawo kanta, nasanma tana sona har yanzu, kuma nasan daga baya zata yafemin abunda nayi mata!”
Cike da tsananin mamaki Dad ke kallon Zaid wanda gaba Ιaya ya ruΙe alokaci Ιaya, anya kuwa ba aljanune suka shiga jikinsa ba ? Dad yatambayi kansa cike da tsananin mamaki, domin kuwa sam Zaid ba haka yake ba, shi mutum ne me nuΖu nuΖu amma kuma wani babban abun mamaki shine yauga Zaid nan yana faΙin wai bazai iya rayuwa ba idan babu wata,,
“Zaid!” Dad yakuma Ζiran sunansa cike da tausayawa domin shikam baitaΙa ganin soyayya irin wannan ba…
Zaid bai iya amsawa mahaifinnasa ba, saide idanunsa daya Ιago ya kalli Dad Ιinnasa dasu.
“Zaid ka kwantar da hankalinka, ba ita kaΙai bace mace a duniyar nan akwai mata da yawa, kana da Ζ΄ancin da zaka zaΙi duk irin macen da kake so” Dad yafaΙi haka ga Zaid cikin lallami…
“Idan ni inada Ζ΄anci ita kuma dana cuta fa? nacutar da ita Dad cuta mafi muni, na zalunceta, banda wata hanya dazanbi na goge laifina a wajenta, sai ta hanayar aurenta, dan Allah Dad kayi wani abu, bazan iya jure rashin Zahrah ba!” yanzu kam har Ζwalla suncika idanun Zaid batare daya sani ba. (hmm so mugun wasa)
MiΖewa Zaid yayi daga zaunen da yake haΙe da sa kai yafice daga cikin falon Dad Ιin nasa, da kallo kawai Dad yabisa dashi harya fice, baisan me yake shirin faruwa da Ιan nasa ba amma ae so ba hauka bane…..1
Zaid yana fita daga Ιangaren Mahaifinsa direct part Ιinsa yanufa, idanunsa gaba Ιaya sun rufe yayinda kansa ke matuΖar sara masa, sam bazai iyaba, bazaitaΙa iya jure rashin Zahrah ba, lallai yazama dole yakuma yarda da shawaran da zuciyarsa ta basa,, tabbas yazama dole ya kusanto Zahrah zuwa garesa koda kuwa hakan zai jawo faruwar abubuwa masu tarin yawa…key Ιin motarsa ya Ιauka yafice daga cikin Ιakin, gaba Ιaya zuciyarsa ta bushe babu wani abun dayayi saura aciki banda tsananin soyayyar Zahrah…..
Da wani irin mahaukacin gudu Zaid yafigi motarsa yafice daga cikin gidan saura kaΙan yabitakan me gadi daya wangale masa gate, Allah ne ya ta Ζaita Me gadin yayi saurin matsawa gefe, domin kuwa ko gama buΙe gate Ιin baiyi ba Zaid yayi yo kansa….
TuΖi yakeyi amma kuma kwalbar giya ne riΖe a Ιayan hanunsa yana sha, jinkansa yake gaba Ιaya yana juyawa, yayinda zuciyarsa keyi masa zafi, idanuwansa Zahrah kawai suke hango masa, batare da Zaid yakulaba motarsa tayi karo da wata babbar mota, take motar tasa ta Ιagu sama haΙe da faΙowa Ζasa sannan kuma tashiga gungurawa kan titi, batare da Zaid dake cikin motar ya tsira ba…..
Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 8 BY FATYMA SARDAUNA"