SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 7 BY FATYMA SARDAUNA
SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 8 BY FATYMA SARDAUNA
Www.bankinhausanovels.com.ng
Idanu ta Ζara zarowa domin tabbatar mawa kanta cewa abun da tagani gaskiya ne, ko kuwa, gizo idanunta keyi mata.
Tabbas dagaske ne bawai gizo bane, hoton zanen fuskarta ne raΙau ajikin takardan. Hanunta na rawa haka ta durΖusa Ζasa, haΙe da sanya hanu ta sake ware takardan, tabbas itaΙince babu ko kokonto, zanen fuskarta ce kwance ajikin takardan, amma saboda tsananin kyawun da zanen yayi tamkar azahiri haka zaka gani, hanu tasanya ta shafi zanen, cike da fargaba haΙe da Ιaurewar kai.
Lallai yazama dole a gareta tanemo wanda yake aikata mata waΖ΄an nan abubuwan, kusan kwana uku yanzu kenan ana turo mata da saΖonni, bata kuma san daga waye bane.
Bata damu da ta duba sauran kayan dake cikin kwalin ba, ta tattara shi ta Ιoye acikin kayanta.
Zama tayi dirshan akan katifa tana mai da numfashi akai akai, sosai abun yabata mamaki, tabbas ko ma waye ne wanda yake bibiyarta ta tabbata yayi mata farin sani, amma kuma rainin hankalin yayi yawa, dole zataimawa tufkar hanci. Abun da ta Ζudurta kenan acikin zuciyarta domin iskancin yasoma isarta.
Ζarfe 6:30 na yammaci Dr Sadeeq yayi wa gidansu Zahrah tsinke, bayan yasha adon sa cikin riga da wando na shadda Ζ΄ar bugu mai kyau. Zama yayi acikin motarsa yana mai jiran fitowar Zahrah, domin kuwa yamata waya yasanar da’ita cewa gashi nan, a Ζofar gidansu.
Kafeta da idanu yayi domin kuwa bakaΙan ba tayi masa kyau, cikin shigar doguwar rigan dake jikinta, lallai Zahrah Ζarshe ce wajen haΙuwa dakuma kyau.
Fuskarta Ιauke da murmushi Zahrah ta Ζaraso wajen da motar tasa take fake. Tsayawa tayi ajikin motar, batare da ta buΙe tashiga ba. Ganin haka yasa Dr Sadeeq buΙe murfin motar yafito.
“Yau kuma aji ake jamin ne?” ya tambayeta cikin yanayin tsokana.
Ζan guntun murmushi tayi haΙe da juya idanunta. “Eh mana, ko bankai naja aji bane?” itama ta tambayesa cikin yanayi na shauΖi.
“Murmushi yayi haΙe da Ιage giransa sama “Kin isa har kinma wuce, ko bakisan cewa keΙin tamusamman bace?”
Hararan wasa Zahrah ta wurgamai haΙe da kawar da kanta gefe, batare da tace dashi komai ba. Haka take al’adar ta ne, bakoda wani lokaci take bada amsar tambaya ba, domin a cewarta shiru ma magana ne.
“Kona zagayo na buΙe miki murfin motar ne gimbiyata, saboda naga kamar bazaki iya ba ?” yafaΙi hakan cike da kulawa.
“A’a ba buΖatar hakan, ni dakaina ma zan iya” taΖare maganar tana mai buΙe murfin motar, haΙe da shiga tayi mawa kanta mazauni.
Shima komawa yayi cikin motar ya zauna. Bayan ya Ιaura duka idanunsa a kanta.
“Kinyi kyau sosai, fiye da ko yaushe” yafaΙi haka yanamai kashe idanunsa.
Ζanguntun murmushi Zahrah tayi “Nagode” tace dashi ataΖaice
Jinjina kansa yayi azuciyarsa kuwa cewa yayi “Lallai Zahrah tana da aji, duk da ta rasa Virginity Ιinta hakan baisanya ta zama wata sakaka da’ita ba, yanason mace wacce ta’iya takunta, wacce bata sakar baki tayita dariya like mental problem, wasu matan da zaran kace dasu sunyi kyau tofa take zasu wage baki suita ΖyaΖyata dariya, babu wani Ιan jan aji ba komai. nima shaida ce irin su Sister Munubiya idan kace dasu sunyi kyau ae har kyautan kuΙi zasu baka tsabar daΙi?”
STORY CONTINUES BELOW
Sake gyara zamansa yayi haΙe da dawo da nutsuwarsa zuwa gareta.
“Zaki’iya zama dani a ko wani irin hali Zahrah?”
Ya jefomata tambayar da bata tsammaci jinsa ba.
Cikin yanayin mamaki Zahrah ta dawo da kallonta garesa, haΙe da cewa “Banfahimci maikake nufi ba”
“Inanufin zaki iya rayuwa dani ako wani irin hali na tsinci kaina? sannan zaki iya yarda na haΙaku ku biyu na aura?” yakuma maimaita tambayar tasa.
Dummm haka Zahrah taji Ζirjinta ya buga, idan da badon kada yace ta rainasa ba, to tabbas da zatace dashi yasake maimaita maganar da yayi. Domin idan kunnuwanta sunjiye mata dai dai, to kuwa bata da amsar da zata basa, domin koda ta basa amsa zata iya faΙuwa, saboda balallai ta bashi amsa dai dai da abun da ya tambaya ba.
Idanunsa duka ya tsura mata, amsa kawai yakeson ji daga bakinta.
Kasa ce dashi komai tayi, domin kuwa haryanzu bata gama haΙa amsar da zata basa ba.
“Nasani dama ba lallaine ki amince ba, Hajiya na ta amince da aurena dake, amma kuma kamar yanda nafaΙamiki a baya, tun tuni akwai zaΙin da tayimin, takuma umarceni da na aureku duka biyu, shin zaki iya aurena a haka, zaki iya zama da wata a matsayin kishiyar ki?” yafaΙi hakan cike da zaΖuwan son jin amsa daga gareta.
Jikinta ne gaba Ιaya yayi sanyi, take taji zuciyarta ta karaya, batasan ya’ake zama da kishiya ba, haryanzu ita yarinyace, bakomai tasani na game da al’amarin duniya ba, tanaji a labarai irin illan da kishiyoyi suke mawa junansu saboda kishi, amma ita yanzu ba wannan bane a gabanta, makomarta na gaba take tunawa, shinya zata kasance?” ta tambayi zuciyarta…
“Kinyi shiru kice wani abu mana zahrah ko zuciyata zata daina bugawan da takeyi” Dr yafaΙi hakan cikin yanayin damuwa.
“Bazan taΙa Ζin aurenka ba, sai dai idan har kaine kace kafasa aurena, sai dai kuma inajin tsoro, bansan mene zai kasance dani gaba ba, dan Allah kada soyayyar matarka ta ruΙeka, ka wulaΖantani, banda wani madogari sai ALLAH sai kuma kai” taΖare maganar cikin rawar murya, yayinda idanunta sukayi rau rau dasu, alamar zasu zubda Ζwalla.1
Ajiyar zuciya mai Ζarfi ya sauΖe, haΙe da sakin Ιan taΖaitaccen murmushi. “Har abada kada kitaΙa tunanin zan wulaΖantaki Zahrah, inasonki da gaske bada wasa ba, namiki alΖwari zan kamanta adalci a tsakaninku, bazan juya miki bayaba insha Allah!” Doctor Sadeeq ya faΙi haka cike da lallashi.
Tuni idanun Zahrah suncika da Ζwalla, amma idan ta tuno cewa bata da zaΙi sai taji gwamma kawai ta daure zuciyarta, haka ta ta Ζaddaran take.
“Kada kiyi kuka kinji My Princess, ina tare dake ako wani lokaci, zankuma share miki dukkanin hawayenki nan bada jimawa ba namiki alΖawari”
Saurin maida hawayenta tayi haΙe da ΖaΖalo murmushin dole ta’aza akan fuskarta, wan nan damuwarta ne ita kaΙai, baikamata ace tabari Dr Sadeeq yagane ba, lallai tun yanzu yakamata ta zama mai juriya.
“Baffa yana gida kuwa?” Dr. Sadeeq ya tambaya.
Wasa da yatsun hanunta tashiga yi, haΙe da kaΙa masa kai alamar “Eh”
Kai yajinjina haΙi da cewa “Yanaga duk jikinki yayi sanyi? banace kada kisa damuwa a ranki ba” cikin kulawa yayi maganar.
Cike da shagwaΙa Zahrah ta langwaΙar da kanta gefe haΙe da turo Ιan Ζaramin bakinta gaba, “Nibansa damuwa a raina ba” tace haka cikin sanyayewar jiki.
Wani irin kallo maiΙauke da ma’anoni masu yawa Dr.Sadeeq yashiga yi mata, ji yake tamkar yajawota jikinsa ya rungumeta tsam acikin Ζirjinsa, saboda ako da yaushe idan yana tare da’ita wani irin feeling yakeji a jikinsa.
STORY CONTINUES BELOW
“Kije kimin sallama da Baffa inaso zamuyi magana”
“To” kawai tace dashi haΙi da buΙe murfin motar tafita. Dakallo kawai ya bita harta shige gida.
Tana shiga cikin gida ta iske Baffa yana ΖoΖarin fitowa daga Ιakinsa.
“Zahrah har kindawo? badai likitan yatafi ba?” Baffa yajeromata tambayoyi alokaci Ιaya.
“A’a baitafi ba Baffa, shine ma yace nace ma yana son magana dakai” Zahrah tafaΙi haka ga Baffa cikin girmamawa.
“To Allah yasa lafiya, yanzu kuwa zanje na sa mesa” ya faΙi maganar yana mai nufar hanyar fita daga gidan.
Zahrah kuwa Ιakinta takoma.
Sosai maganar Dr.Sadeeq yataΙa mata zuciya, bakomai take hangomawa kanta ba, sai yanda makomarta zai kasance acikin gidansa, tabbas ta tabbatar wacce zai aura, ba irin ta bane, tasan tana da galihu, saΙanin ita da take ko oho, sannan kuma dole zata ga banbanci daga Ζ΄an uwansa, haka ma Dr.Sadeeq Ιin dole zai banbantasu, saboda waccar zai sameta a budurwa, saΙanin ita da zai sameta ba’a budurwa ba, kukane yaΖwace mata mai sauti, cusa kanta cikin cinyoyinta tayi tashiga rera kukanta, har abada cutar da Zaid yayi mata bazai taΙa gushewa ba…..
“Alhmdlh masha Allah! haΖiΖa naji daΙin wannan magana taka Likita, lallai kacika mutumin kirki kuma mutumin Ζwarai, Allah yasaka ma da gidan Aljanna, kuma idan dai Zahrah ce kada kaji komai natabbatar itama tana Ζaunarka, saboda haka nabaka izini ka turo magabatanka, don mu tsaida magana,kuma maganar bayarwa nabaka Zahrah!” Baffa yafaΙi haka cikin farinciki, duk da kuwa cewa dama tun abaya yasan cewa Dr.Sadeeq yanason Zahrah, amma sake tabbatar masa da Dr. Ιin yayi yanzu, yasanyashi jin daΙi, domin shima yanzu burinsa shine ya inganta farincikin marainiyar Allah wato Zahrah..
Farinciki ne sosai yakama Dr.Sadeeq, yaji daΙin aminta dashi da Baffa yayi.
“Nagode da wannan dama da kabani Baffa, Allah yajiΖan magabata” Dr Sadeeq yafaΙa cike da girmamawa.
“Mune da godiya Likita, ai mu ba’abun da zamuce maka saidai fatan alkhairi” Baffa yafaΙa shima cikin jin daΙi, domin yasan Zahrah na auren Dr.Sadeeq wahalanta yaΖare da yardan Allah,saboda yana da tabbacin cewa Dr.Sadeeq zai bata kyakkyawan kulawa, duk da kuwa cewa Dr.Sadeeq Ιin yasanar dashi cewa ba Zahrah ita kaΙai zai auraba, yasanar dashi komai, kuma Baffa yayi na’am da hakan, saboda shi baimaga wani aibu acikin hakan ba, ai namiji mijin mace huΙu ne.
(Nima nace wannan gaskia ne, sbd haka duk me mace Ιaya ya Ζara??)1
Cike da farinciki Baffa da Likita sukayi sallama, yayinda Baffa yakoma cikin gida, ya kumace da Dr.Sadeeq zai turo masa Zahrah suyi sallama.
Tanajin Muryan Baffa a tsakar gida, tayi saurin share hawayenta, haΙe da miΖewa tsaye, domin har Baffa yafara ΖwaΙa mata Ζira.
Fuska cike da fari’a Baffa yace “Likita ke yake jira, zai tafi”
Sumi sumi haka Zahrah ta fice yayinda tabar Baffa yana gayamawa Inna abun da ya wakana tsakaninsa da Likita.
Tun fitowarta yake ta zabga murmushi, kallo Ιaya zakai mawa fuskarsa ka gane cewa yanacikin farinciki.
“Kitayani murna My Princess saura Ζ΄an kwanaki Ζalilan na mallake ki!” Dr Sadeeq yafaΙi haka cike da shauΖi.
Kunyane yakama Zahrah, don haka ta sanya duka hannayenta biyu ta rufe fuskarta, bayan ta ΖaΖalo murmushi ta aza akan fuskar ta..
“Baffa yabani daman naturo magabatana don asa mana ranan aure, kuma insha Allah, gobe magabatana zasu zo, za’asa ranan aurenmu nan bada jimawa ba, so sai ki shirya domin kin kusa zama amaryata!” yanayin yanda ya Ζare maganar kaΙai ya isa taΙa zuciya..
Kunyane yasake kama Zahrah, har batasan sanda murmushi mai sauti ya kufce mata ba, gaba Ιaya ta lura Dr.Sadeeq ya Ζosa da ayi aurensu bata kumasan dalilinsa nayin hakan ba..
STORY CONTINUES BELOW
“Kinyi shiru kodai bakya farinciki ne my princess?” yatambaya.
Ζan satan kallonsa tayi haΙe da sakarmasa murmushi mai tsayawa a zuciya.
Ζaran wayarsane ta katsesa daga kallonta da kuma zancen zucin da yakeyi. Ajiyar zuciya ya sauΖe ganin wacce take Ζiran nasa, maida wayar tasa cikin aljihu yayi batare daya Ιaga Ζiran ba.
“Dare yayi Zahrah kishiga gida, zamuyi waya, kikulamin da kanki ” yafaΙi hakan yana me ΖoΖarin shiga cikin motarsa.
Murmushin dole Zahrah tayi haΙe da yi masa saida safe, tajuya ta nufi cikin gida, hakanan taji wani iri a zuciyarta duk da batasan me yasa baiΙaga Ζiran da ake mai ba, amma tana da yaΖinin cewa matar da zai aura tare da itane ta Ζirasa. Saurin kawar da tunanin tayi aranta, domin tuna hakan ma bashida amfani a gareta.
Washe Gari….
Kamar yanda Dr.Sadeeq yafaΙa hakanne ya kasance da da dare bayan sallan magriba Baffa Amadu shida amininsa suka zo gidansu Zahrah don tambayan aurenta, balaifi Baffa yayi musu tarba mai kyau, sunkuma ji daΙin hakan, duk da sun lura cewa suΙin basuda wani Ζarfi, ma’ana arziki…
Magana ta fahimta akayi tsakanin Baffa da kuma Baffa Amadu, a taΖaice dai Baffa yabasu auren Zahrah, yayinda sukuma suka Ιau alΖawarin cewa a cikin satin za’akawo kayan tambaya dakuma na lefe, daga nan sai asa ranan aure, amma basason auren ya Ιau lokaci, saboda rana Ιaya suke so ayi dana Salima.. Da to kawai Baffa ya amsa musu domin shi baida wani abun cewa banda hakan, sai dai a Ζasan zuciyarsa tunani yake taya zai samu kuΙin da zaiyi mawa Zahrah kayan Ιaki, domin dai bayanda za’ayi ace anyi aure ba kayan Ιaki… Haka dai sukayi sallama cike da mutun ta juna…
Baffa ne Zaune akan tabarma ya yi jigum bakomai ke damunsa ba, kamar sha’anin auren Zahrah, Allah yasani ko abincin da za’aci abikin bai tanada ba, balle wata uwa uba kayan Ιakin da za akaita dashi..
“Wai tunanin mekakeyine haka tun Ιazu?” Inna dake zaune gefensa ta jefo masa tambaya.
“Ba dole nayi tunani ba Salame, kinga dai yau iyayen yaron nan Sadeeq suka zo, kuma da duk kan alama basa so aja auren nan yakai wani lokaci, kin kuma san halin dai da muke ciki na rashin kuΙi”
“Yo dama akan wannan kake Ιaga hankalinka? hmm Malam kenan to ai ni banga abun Ιaga hankali anan ba, ca nake shi Sadeeq Ιin yasan duk halin da muke ciki, kuma shi yakawo kansa yace ya na so, bawai mu makai masa dole ba, saboda haka malam ka kwantar da hankalinka, Zahrah ya nema kuma Zahrah’n zamu bashi” Inna tafaΙi haka da’iyaka gaskiyarta…
Kallon Inna kawai Baffa yayi haΙe da girgiza kansa, yasan ma koda yayi ΖoΖarin fahimtar da’ita to fa bazata fahimta ba.
***
“What? Mom cewa fa kikayi wai bani kaΙai Sadeeq zai aura ba, anya kuwa Mom kinji abun da Hajiya Habiba tafaΙamiki da kyau?” Salima tatambayi mahaifiyarta Hajiya Furaira cike da mamakin jin abun da mahaifiyarta tace da’ita..
“Abun da na faΙa miki shi naji daga bakin Hajiya Habiba, Salima kicire Sadeeq a ranki, domin kuwa aurenki dashi bazai taΙa yiyuwa ba, da raina dakuma hankalina bazan taΙa bari Ζ΄ata taje kan kishiya ba!” Hajiya Furaira tafaΙi haka cikin Ιacin rai..
Kuka ne ya Ζwacemawa Salima cikin muryan kuka ta soma cewa “Wani irin cin amana ne wannan mom, sai da maganar aurena dashi ta kankama sannan wata banzar magana zata Ιullo, wallahi bazan haΖura da shi ba, bakuma zan taΙa zama da wata a matsayin kishiyata ba, dole ne Sadeeq ya aureni ni Ιaya batare da wata ba, bazan iya jure rashin saba Mom, dan Allah kiyi wani abu” Salima ta Ζare maganar cikin shaΙe shaΙe da hawaye.
“Mekikeso nayi Salima? so kike naje na basu haΖuri akan su sa Sadeeq ya aureki ke kaΙai? ko ko sokike na zubar miki da Ζima daΖuma Ζ΄ancinki? Hajiya Habiba Ζ΄ar uwatace kuma Ζawata, bantaΙa tunanin haka daga gareta ba, amma bakomai, zanyi maganin abun, kuma ni banzauna da kishiya ba, Ζ΄a tama bazata zuana da kishiya ba, wannan alΖawarine na Ιaukar mawa kaina” still cikin Ιacin rai Hajiya Furaira take maganan…
STORY CONTINUES BELOW
Cikin matsanancin Ιacin rai Salima ta juya ta koma Ιakinta, ji takeyi zuciyarta na tafarfasa, kamar ita ace ta haΙa miji da wata, sam bazai yi wuba, lallai ko da mahaifiyarta bazatayi wani abu ba yakamata ace ita tayi, wayarta da mayafinta ta Ιauka, a fusace ta fice daga Ιakin nata, tana son Sadeeq tun ba yau ba, zata kuma iyayin komai akan sa.
Ζangaren Dr Sadeeq kuwa tuni yasoma haΙa mawa Zahrah kayan lefe, sosai yake iya ΖoΖarin sa wajen ganin yasanya duk wani abu da yasan zai burge Zahrah.
Ζangaren Hajiyarsa da Aunty Raliya kuwa, sam basu wani damu da auren ba, hakanne ma yasa suka tura masa aniyarsa, su dai sunfi bada Ζarfi wajen ganin Salima tasamu abun da take so, yayinda Hajiya Furaira ta kafe kan cewa Ζ΄arta bazata auri Sadeeq ba matuΖar ba’a fasa aurensa da Zahrah ba, ranta bai Ζara Ιaci ba ma, sai da taji labarin cewa Zahrah Ζ΄ar talakawa ne, sannan kuma bata da wani galihu, ai take ranta yaΖara Ιaci, tace sam bata amince ba, yayinda Salima kuwa ta kafe akan cewa lallai sai ta ruguza auren da Dr.Sadeeq yake nema bayan nata.
Gaba Ιaya Zahrah ta ruΙe, zuwa yanzu wanda yake turo mata saΖo ya uzurawa rayuwarta, a yanda ta fahimta shine duk inda tayi yana biye da’ita, wani babban tashin hankali daya kunnu mata shine, sabbin saΖonnin da yafara turo mata a cikin wayarta, tagama iya hasashenta ko zata gano a ina yasamu number’n ta amma takasa samun daman sanin inda yasamu number’nta, gaba Ιaya yanzu salon saΖonnin nasa sun sauya salo, domin kuwa yanzu saΖon kalamai yaΖe turo mata masu daΙi, wanda kuma duk rabin saΖon yaba kyawunta yake, babban abun daya Ζara ruΙata shine irin maΖudan kuΙaΙen dayake turomata ta waya. sannan kuma idan ta gwada Ζiran number’n da yake turo mata saΖo dashi, bata samu domin da zaran taΖira wayan za’ace mata a kashe wayar take, hakan yasa tafara tunanin cewa kodai gamo tayi…
Ζan Ζara wayarta tayi alamar shigowar saΖo, take taji gabanta yafaΙi, zuwa yanzu har tsoro take taji wayarta tayi Ζara, domin kuwa tasan idan har wayanta tayi Ζara to ko Ζiran Dr.Sadeeq ko kuma saΖon mutumin da batasan shiba…
Number’n nan ce dai, da aka saba turo mata saΖo dashi, yauma saΖonne aka kuma turowa..
_Tunaninki ya hanani sukuni My Zahrah, ina fatan dai kina lafiya, ina kuma fatan zuwa yanzu kindaina tsoro da kuma mummunan tunanin da kikeyi akaina, kina da kyau My Zahrah, komai naki me kyau da burgewa ne._
Abun da saΖon ya Ζunsa kenan.
Zahrah ta karanta saΖon nan yafi sau biyar, kwata kwata ta kasa fahimtar abun da saΖon yake nufi.
Saurin yin Deleting saΖon tayi haΙe dayin switch off Ιin wayar tata, bazata taΙa yarda wan nan mai saΖon ya haukata mata tunanin ta ba, yazama dole a gareta ta sanja layi.. Kwanciya tayi lamo tana mai addu’an Allah yasa bacci ya Ιauketa. domin bacci ne kaΙai zai kawo mata sauΖi a zuciyarta.
Zaune suke dukansu a Ιan madai dai cin tsakar gidan nasu, domin dama idan dare yayi sukan zauna a tsakar gida su Ιan taΙa hira, haka al’adarsu take..
Wani yarone yashigo cikin gidan bakinsa Ιauke da sallama, haΙa baki sukayi wajen amsa masa sallaman.
“Wai ana sallama da mai gidan nan” yaron yafaΙa.
“To kace inazuwa” Baffa yafaΙi haka yana ΖoΖarin miΖewa tsaye.
Kusan tare suka fita shida yaron sai da Baffa yaji wani irin faΙuwar gaba sakamakon wasu irin danΖara danΖaran motoci guda biyu da yagani fake a Ζofar gidansa.
Ja Baffa yayi ya tsaya turus yana me mamakin ganin waΖ΄an nan rantsatstsun motocin a Ζofar gidansa, “Allah yasa da alkhairi suka zo” Baffa yafaΙi haka a cikin zuciyarsa.
BuΙe murfin motar Alhaji Ma’aruf yayi haΙe da sako Ζafarsa waje.
Sake waro idanu Baffa yayi haΙe da kafe Alhaji Ma’aruf dake ΖoΖarin fitowa daga cikin mota da ido.
Fuska cike da annuri Alhaji Ma’aruf ya Ζaraso wajen Baffa, haΙe da miΖa masa hanu alamar su gaisa.
Cikin Ιari Ιari Baffa ya Ιago hanunsa haΙe da miΖamawa Alhaji Ma’aruf suka gaisa.
“Inafatan kaine ma mallakin wannan gida, kuma Baffa ga Zahrah?” Alhaji Ma’aruf ya tambaya.
Saida Baffa yaji zuciyarsa tayi tsalle sakamakon jin an ambaci Zahrah, Allah yasa ba wani abun Zahrah tajawo musu ba.
“Eh nine ranka ya daΙe, Allah yasa lafiya?” cikin dar Ιar Baffa yafaΙi hakan.
Murmushi irin nasu na manya Alhaji Ma’aruf yayi haΙe da kallon Baffa…”Nazo da magana mai mahimmanci, inaga zaifi kyautuwa kabiyoni cikin mota mu tattauna, don maganar bata tsaye bace”
Kallon Alhaji Ma’aruf Baffa yashiga yi, haΙe da excort Ιin da suke bayan Alhaji’n, tabbas Alhaji Ma’aruf baiyi masa kama da irin mugayen mutanen nan ba, domin daga ka gansa zaka fahimci cewa dattijon arziki ne, hakanne yasa Baffa bai musa masa ba, yabisa zuwa mota..
Acikin mota kuwa bayan sun sake gaisawa, Alhaji Ma’aruf yayi gyaran murya haΙe da cewa…
“Sunana Alhaji Ma’aruf, kasancewar dare ne yasanya ka kasa shaida fuskata, domin ni ba Ιoyayyen mutum bane. Nazo gare ka ne domin nemawa Ιana Auren Ζ³ar Wajenka Zahrah, ina fatan bazaka watsa mini Ζasa a ido ba”…….Shirune yashiga tsakanin Baffa dakuma Alhaji Ma’aruf, bakomai ne kuma yasa hakan ba face nazari da Baffa yashigayi, lallai wannan abu da mamaki yake, neman aure mace Ιaya duk alokaci guda.+
“Naji kayi shiru, Allah yasa dai ba wata matsala bace ta faru” Alhaji Ma’aruf ya faΙa, domin ko kaΙan baya fatan wani abun da zai zo ya gifta har ya katsewa Zaid cikar burinsa..
Gyara zama Baffa yayi haΙe da sauΖe ajiyar zuciya..
“A gaskiya Alhaji bazan Ιoyemaka ba, yanzu haka na bada auren Zahrah ga wani, wanda kuma tariga da ta aminta dashi, sai dai bazan yi saurin yanke hukunci ba, idan har Zahrah ta aminta dashi Ιan wajen naka, shikenan, saboda ni bazan mata dole ba, duk wanda takawo tace shitake so, to shi zan aura mata, amma kuma a iya sanina babu wani wanda yake zuwa wajenta, bayan likita’n dana bashi aurenta, sai dai kuma bansan shi Ιan wajen naka a ina yaganta har yaji yanada burin aurenta ba”
Ζan jim Alhaji Ma’aruf yayi haΙe da sauΖe ajiyar zuciya. Lallai yakamata yayi duk abun da zaiyi, domin shikansa yanaso Zaid yayi aure, amma kuma yasan cewa nema cikin nema haramunne, tunda gashi har shi Baffan yarinyar ya ri ga daya shaida masa cewa yabada auren yarinyar ga wani, yazama dole suyi haΖuri kenan.
“Naji maganarka Malam Hayatu, nakuma gamsu, amma bayar da aurenta ga wani, ae bashi yake nufin anΙaura aurenta ba, koda yaushe ra’ayin mutane yana iya sanjawa, saboda haka zanbaka dama kayi tunani mai kyau” Alhaji Ma’aruf yafaΙi haka bayan yaciro wasu maΖudan kuΙi a cikin aljihun rigarsa ya Ιauramawa Baffa akan cinyarsa..
Ware idanu Baffa yayi sakamakon ganin maΖudan kuΙin da Alhaji Ma’aruf yaΙaura masa akan cinyarsa, badai yana nufin duk nasa bane.
Murmushi irin na manya Alhaji Ma’aruf yayi haΙe da cewa “Kada kadamu bawai nabaka kuΙinnan bane,don ka bawa Ιana auren Ζ΄arka ba, nabaka ne kawai saboda shi meyin alkhairi ako da yaushe baya rasawa”
Cikin sanyin jiki Baffa yayi masa godiya haΙe da buΙe murfin motar yafita, zuciyarsa cike da Ιunbin mamaki…
Baffa na fita daga motar Alhaji Ma’aruf yamawa driver’nsa umarni akan cewa su tafi, aikuwa ba Ιata lokaci drivern yatada mota..
Saida suka Ιacewa ganinsa kafun Baffa ya iya Ιauke idanunsa daga kansu, kuΙin dake hanunsa yashiga juyawa, “Lallai wannan mutumi yanada ihsani, amma kuma yazo da babbar magana, da ace yanada dama to da a yanzu yabawa Ιan Alhaji Ma’aruf Ιin auren Zahrah, to saidai kuma yanzu ya saduda, sakamakon wa’azi mai tsoratarwa dayaji akan cutar da maraya, da kuma irin azabar da za’amawa mai cutar da maraya, tundaga wannan lokacin yaΖudurta aransa cewa bazai sake cutar da Zahrah ba, yanzu ma dolensa zai bata zaΙi, domin ita zatayi zaman auren ba shiba…
Yanashiga gida Inna da takasa zaune takasa tsaye, ta Ζaraso wajensa da sauri tana me cewa “Lafiya naga ka jima, har nafara jin tsoro naΙauka irin mutanen nan ne masu garkuwa da mutane suka kamaka, domin na leΖa naga wasu fankama fankaman motoci a waje”
STORY CONTINUES BELOW
Harara Baffa ya wurgamata, haΙe da jan tsuka “Bazaki taΙa sanja halinki ba ko Salame, wato ke dai koda yaushe kai da kuma idanunki sunaga Ζofar gida, kullum cikin leΖe kike, wato dai har dare ma yanzu leΖe kikeyi, Allah ya kyauta” yafaΙi haka yana mai nufar hanyar Ιakinsa…
Fuska Inna ta Ιata haΙe da kafe aljihunsa da idanu, domin kuwa tuni idanunta sun Ζyallaro mata tudun da aljihunnasa yayi, Ζwafa tayi haΙe da rufa masa baya, koma mene sai
taje taganema idanunta, idan ma abuncine aci da’ita..
Sake gwalo idanu Inna tayi, ganin kuΙin da Baffa ya’aje akan gadonsa, “Malam kace farar fita kayi, a shema baΖin arziki ne, nayi musu mummunar fahimta, ae irinsu muke fatan suta zuwa” washe da baki ta Ζare maganar…
“Akwai matsala Salame, amma jeki Ζiramin Zahrah” Baffa yafaΙa bayan yayimawa kansa mazauni, a bakin gadonsa.
“Yanzu kuwa” Inna tafaΙa tana me fita daga Ιakin..
Zahrah ce zaune akan gadonta, game take bugawa a cikin wayarta, da’alama dai game Ιin yayi mata daΙi, domin kuwa ita kaΙai sai murmushi take.
Inna ce tashigo cikin Ιakin haΙe sa shaida mata Ζiran da Baffa keyi mata, haka nan taji gabanta yafaΙi. Tare suka fito da Inna, dukansu suka Ιunguma zuwa Ιakin Baffa’n…
Gyara zama Baffa yayi haΙe da maida kallonsa ga Zahrah, wacce ta duΖar da kanta Ζasa.
“Bayan Likita akwai wani wanda kikasan yanasonki, ko kuma kika basa dama ya turo magabatansa wajena?” Baffa yatambayeta cike da kulawa.
“A’A Baffa bana mu’amala da kowa sai likita, bankuma bawa kowa izinin zuwa wajenka ba” tafaΙi haka cike da girmamawa, duk da kuwa cewa kanta ya Ιaure da jin tambayar da Baffa’n yayi mata…
Kai Baffa yajinjina haΙe da cewa “Ζiran da akai min Ιazu wani ne yazo nemawa Ιansa aurenki, shine nayi tunanin ko kinsan da zuwansa”
Wani irin bugawa Zahrah taji Ζirjinta yayi, har batasan sanda ta Ιago da idanunta ta kalli Baffa ba.
Baffane yacigaba da cewa “Bansan ko su Ιin suwaye bane, amma ban Ιoyemusu komai ba, nasanar dasu cewa nabada aurenki ga wani, amma mahaifin yaron yace yabani lokaci nayi tunani, saboda hakane ma naΖiraki domin ni bazan miki dole ba, zanbaki dama ne ki zaΙi wanda kikeso”
Take idanun Zahrah suka kawo Ζwalla, sakamakon jin wani baΖon al’amari dayake shirin kunno kansa cikin rayuwarta.
“Kinyi shiru, ki kwantar da hankalinki bazan miki dole ba Zahrah, kema kina da Ζ΄an ci, zan kuma baki Ζ΄ancin ki, sai dai abun da nakeson sani shine wanene yaron nasa, saboda bai yiwuwa a haΙaki aure da wanda bamusani ba, amma idan ke kinsan sa shikenan ba damuwa”
“Bansan saba Baffa, kuma ma koda nasansa bazan aminta dashi ba, saboda idan nayi haka ban yi mawa Dr.Sadeeq adalci ba” Zahrah tafaΙi haka cikin sanyayewar murya…
“Adalci, kaji shirmen banza don Allah Malam, wani adalcine yarage miki, wanda yawuce ki kai kanki cikin arziki kicisa yanda yakamata, saidai ko inkuma baΖin ciki kike mana”
Inna ta tsomo bakinta cikin maganar batare da angayyaceta ba…
“Tashi kije Zahrah, idan suka sake zuwa zan sanar dasu cewa hakan da sukeso bazai yi wuba” Baffa yafaΙa, yana mai wurgamawa Inna harara..
Cikin rashin Ζwarin jiki haΙe da Ιaurewar kai Zahrah tabar Ιakin.. Haushin Zahrah da Baffa ne yacika zuciyar Inna, amma ganin yanda Baffa yahaΙe fuska bai bata damar yin Ζorafi ba yasanya itama tafice daga Ιakin tana me Ζananan maganganunta wanda ita kaΙai tasan metake cewa..
Zama Zahrah tayi jigum haΙe da zurfafa tunanin ta, ba’abun dake bata mamaki da Ιaure mata kai, kamar neman aurenta da Baffa yace anzo anyi, “To waye zai zo neman aurenta batare da saninta ba? batare da ta kuma sanshiba, lallai koma waye baisan meyafaru da’ita ba, domin tasan daya sani, da baiyi gigin turo magabatansa nema masa aurenta ba” Haka dai tayita saΖawa da kuncewa har bacci ya Ιauketa……
STORY CONTINUES BELOW
Cike da tsananin mamaki Zaid yake kallon mahaifinsa, sakamakon ji da yayi mahaifin nasa nacewa “Wai anbada auren Zahrah’nsa ga wani” ” Anya kuwa gidan su Zahrah Dad Ιinsa yaje? kodai yayi mistake ne yaje wani gidan amadadin nasu Zahrah?” duk wannan tambayar kansa ya mawa.
“Inaga zaifi kyautuwa kanemi wata My Son, domin kafasan nema cikin nema haramunne” Alhaji Ma’aruf ya faΙa yana me kallon Ιan nasa.
“Inaga ba gidansu kaje ba Dad,
domin ni nasan Zahrah tawace, baza’a bawa wani ita ba bayanni” Zaid yafaΙi haka bayan yayi sipping holandia milk Ιin dake aje cikin glass cup Ιin dake gabansa.
Kallon mamaki Alhaji Ma’aruf, yashiga yi mawa Zaid, sakamakon jin abun daya faΙa.
Baisan me yake shirin faruwa da Ιansa ba, amma tabbas ya hango wata irin soyayya acikin idanun Zaid Ιin me matuΖar zafi, wanda Zaid shikansa baisan da’ita ba…
“Akwai matan aure dayawa Zaid, zaifi kyau ka zaΙi wata, koda a cikin Ζ΄an uwankane” Alhaji Ma’aruf yafaΙi haka cikin lallashi.
Murmushi kawai Zaid yayi haΙe da kallon mahaifin nasa…
“Kai mahaifinane saboda haka bana iya Ιoye maka komai, a gaskiya banjin zan iya zama da wata daban, idan ba Zahrah ba, zanyi komai da kaina kawai” yafaΙi haka yana me miΖewa tsaye… Da kallo kawai Alhaji Ma’aruf yabi sa dashi har ya fice daga cikin falon nasa. Ajiyar zuciya yayi haΙe da cewa “wataΖila idan kuΙi na magani, to zasu maya Zaid, ta hanyar samo masa auren Zahrah”
(hmm bakomai ake nema a samu ba, bakuma komai kuΙi yake iya saya ba)
Kai kawo Zaid yashigayi a tsakiyar tankamemen aljannar duniyar falonsa, gaba ΙaΖ΄a yarasa me yake masa daΙi, shin maganar da Dad Ιinsa ya faΙa masa cewa anbada Zahrah, gaskiya ne kokuwa Dad Ιinnasa ne yayi mistake wajen gano gidan su Zahrah, dudduniya babu wani mahaluΖi daya isa yimasa shamaki da muradinsa, lallai lokaci yayi daya kamata ya bayyana kansa gareta, baidamu da yanda zata Ιaukesa ba, shidai burinsa kawai shine ya mallaketa amatsayin matarsa, lallai yanzune zai gudanar da babban takunsa, sannan kuma yazama dole yagano bayanshi wayake bibiyan Zahrah, har ake yunΖurin aura masa ita, dole yagano wannan, domin yayi imani cewa Zahrah tasa ce…
***
Fitowarsu daga lecture kenan, wayarta tayi Ζara alamar shigowar saΖo,, ko kaΙan batayi mamaki ba, domin zuwa yanzu tasaba da saΖonnin da’ake turo mata batakuma san waye yake mata hakan ba.
Ajiyar zuciya ta sauΖe bayan ta gama karanta saΖon, yau madai kalamaine masu tsayawa a zuciya, Ιoyayyen mutumin nata Ζ΄arubuta mata, sai dai kuma duk sanda ya turo mata da saΖo, idan takaranta kalaman sukan tsaya mata arai suna kuma yawan yi mata yawo a ΖwaΖwalwarta, koda sau Ιaya ne bata taΙa tunanin mayar masa da amsa ba, amma hakanan taji yau tanason tambayarsa ko shiΙin waye.
“Waye kai?” Abun da tarubuta tatura masa kenan.
Zaid dake kwance cikin wata luntsumemiyar kujera yana sipping wine yaji wayarsa tayi Ζara alamar shigowar saΖo, Ιaga wayartasa yayi yaduba, murmushinsa me kyau yayi bayan yagama karanta tambayar nata..
“Kinason ganina?” shima yamayar mata da tambaya, tahanyar tura mata saΖo.
Zahrah na karanta saΖon tasoma typing kamar haka….”Mezai hana idan zaka bayyana kanka” tana gama rubutawa tayi sending..
“Kishirya ranan friday 8:00 pm zankawomiki ziyara, ina fatan zakiji daΙin ganina, sannan zan taho miki da kyakkyawan surprise” yana tabbatar da cewa saΖon ya isa zuwa wayarta, yayi switch off na wayarsa, sake gyara kwanciyansa yayi ajikin kujeran, haΙe da lumshe idanunsa, jiyake mararsa tana yi masa ciwo, kusan kwana uku kenan da yake fama da wannan ciwon maran, hakan kuma yasamo asali ne da wata irin sha’awa da ta damesa, sai alokacinne ma yake tuna cewa yajima baiyi sex ba, lallai akwai abun da yake damunsa, Zaid Ιin da baya iya kwana Ιaya baiyi sex da mace ba, wai shine yanzu yake iya kwanaki batare da yayi sex ba, shida mace Ιayama bata isan sa, amma sai gashi, yau Ιayan ma, yakasa nutsuwa yakusanceta, lallai yanzu kam yayarda da cewa akwai abun dake damun jiki da zuciyarsa….
Ζan jim Zahrah tayi bayan tagama karanta saΖon nasa, idan bata mantaba yau Tuesday kenan saura kwana biyu jumma’a tayi, lallai tanaso taga wanene wannan wanda yaΙau lokaci yan Ιata tunaninta, ta wani Ιangare na zuciyarta kuwa, ji takeyi tamkar akwai wani gagarumin abu dazai faru da’ita, yayinda idan ta tuna aurenta da Dr.Sadeeq saitaji ta zama wani iri da’ita, bakuma aurenta da Dr. Ιinne bataso ba, a’a kawai dai tanaji ajikinta kamar basu dace da juna ba ita dashi…
Dariya sosai Salima tashiga yi, sakamakon labarin da Ζawarta kuma aminiyarta Laura tabata yanzun. Wani irin daΙi taji haΙe da sanyi acikin zuciyarta, gaba Ιaya labarin Zahrah Laura ta kwashe ta sanar da Salima, wanda Laura ta samo asalin labarin Zahrah ne daga bakin wata Asma da take unguwarsu Zahrah’n kuma har school Ιinsu Ιayama da Zahrah..
“Dama akan sauran wani Doctor yake wulaΖantani hadda jamin aji, hmm lallai kuwa bazanyi kishi da mai aji bama ballentana marar aji” Salima ta faΙi haka cike da kunfar baki…
“Ae magana taΖare Salima, kamar yanda na faΙamiki, tashi kawai zamuyi muje hargidansu, muci mata mutunci mukuma gargaΙeta da tafita hanyar Doctor Sadeeq” Laura tafaΙi haka cike da son zuga Salima.
“Gaskiya ne nima ina bayan maganarki Laura” wata wacce take zaune gefen Laura ta faΙi haka, tana me taΙe baki..
Kallonta Salima tayi haΙe da cewa “Shiyasa nake sonki Ζawata, bakida wasa, wajen sawa ayi rashin mutumci, idan kinshirya muje gidan nasu yanzu, domin akan Doctor sai inda Ζarfina ya Ζare” Salima tafaΙi haka tana maitashi daga zaunen da take.
Motar Salima suka shiga su duka ukun yayinda Laura ke tuΖasu, domin itace jagoran tafiyan kasancewa har gidansu Zahrah ta sani, saboda tasa Asma ta nuna mata….
Zahrah ce zaune a tsakar gida bisa kan tabarma, kwanon abincine aje a gabanta, gaba Ιaya ta kasa tsayawa taci abincin yanda yakamata domin kuwa yau Thursday gobe ne kuma haΙuwarsu da mutumin dayake Ιoye mata kansa, duka nutsuwarta baya gareta, hakanan takejin babu alkhairi a haΙuwarta da mutumin…
Wani irin bangaja da aka mawa Ζofar gidansu shiyasanyata Ιago kanta takai kallonta zuwaga Ζofar gidan nasu..
Wasu tsalan tsalan Ζ΄an mata su uku ta gani, tsaye ko wacce ta kafa makeken glass akan idonta, yayinda suke taunar cingam cike da iyawa haΙi da salo……Baki da hanci Zahrah ta sake tana kallon waΖ΄an nan Ζ΄an matan da suke tsaye suna me yimawa cikin gidannasu kallon wulaΖanci haΙe da Ζyama..+
Cire glass Ιin dake idanunta Salima tayi, haΙe da watsamawa Zahrah wani irin kallo mai Ιauke da mugun tsana, cike da Ζyama ta furzar da yawu, haΙe da kallon Laura “Itace wan nan?” Salima ta tambaya tana me nuna Zahrah da hanunta cike da taΖama.
“Eh itace Ζ΄ar matsiyata” Laura ta faΙa tana yanatsina fuska.
“Lafiya kuwa bayin Allah? su waye ku? Zahrah ko kinsan sune?” Inna da fitowarta a Ιaki kenan ta tambaya, Tana me mamakin ganinsu haΙi da aljabi.
“Ba alkhairi bane ya kawomu, saboda baku kai matsayin da zamuzo muku da alkhairi ba, sunana Salima, nazone domin najawa wannan matsiyaciya kuma karuwar Ζ΄ar taku kunne, koda wasa Doctor Sadeeq basa’an aurenta bane, saboda yawuce ajin macen da taraba mutuncinta a titi” takawa taci gaba da yi cikin isa harta Ζarasa gaban Zahrah, da ta kasa ko motsi… “Banzo danna cutar dake ba, amma tabbas idan kika sake nakuma dawowa cikin gidan nan to zanyi miki babban illa, rabuwa dashi zai fi miki, idan kuma kika Ζi, hmmmm zakisan cewa bakin rijiya bawajen wasan makaho bane, bake kaΙaiba, hatta tsohon da yake riΖe dake sai ya ΙanΙana” Salima tana kai Ζarshen zancen nata tamaida glass Ιin ta dake riΖe a hanunta, haΙe da kallon su Laura “Muje” tace dasu, babu musu kuwa suka rufa mata baya, suna tafiya suna kareraya…
Tamkar statue haka Zahrah tayi ΖasaΖe tana kallonsu, harsuka fice daga cikin gidan.
Sallallami Inna tashiga yi haΙe da tafa hannuwanta duka biyu, “Lallai kuwa wa Ζ΄an nan Ζ΄an iska masu jajayen fuskar suncika marassa ta’ido, rashin kunya har cikin gida” Inna tafaΙi haka cike da mamaki.
Kai kawai Zahrah ta girgiza, haΙe da jawo kwanon abincinta ta ci gaba da ci, batare da ta tankawa Inna da take ta ΙaΙatu ba,, sai dai kuma sosai maganganun Salima suka daki zuciyarta, har wani Ιaci takeji a cikin maΖoshinta.. Tura abincin takeyi amma jinsa take tamkar maΙacin dayafi kowanne Ιaci, har wani zafi takeji a Ζirjinta. Tana gama cin abincin, ta kora da ruwa, haΙe da tashi kai tsaye tanufi Ιakinta.
“Karuwa” sunan da Salima taΖirata dashi yafiye mata komai ciwo, tunda take a duniya ba’a taΙa Ζiranta da sunan karuwa ba, sai a yau Ιin, wasu irin zafafan hawayene taji sunshiga gangarowa daga cikin idanunta, durΖushewa tayi a Ζasa haΙe da soma rusa kuka, filla filla kalaman da Salima ta faΙa mata suke dawowa cikin kanta, koda wasa bata taΙa tunanin za’afaΙi kalma na Ιatanci masu muni irin haka akan ta ba.
“Kacuceni Zaid, Kacuceni, me yasa ka aikata haka agareni, shin koda sau Ιaya ne bakayi tunanin yanda rayuwata zata kasance ba, bazan taΙa yafe maka ba Zaid har kuwa nakoma ga mahaliccina” cikin kuka ta Ζare maganar, domin kuwa sai yau tasake tabbatar da cewa Zaid ya cuceta, takuma Ζara jin matsanancin zafi dakuma ciwo akan fyaΙen da Zaid yayi mata.. Abu kamar wasa haka Zahrah tayita kuka tamkar ranta zai fita, sai gashi cikin mintuna Ζalilan ciwon kai yakawomata ziyara, wanda har sai da yakaita ga kwanciya.. Ζiran Dr.Sadeeq ne yashigo cikin wayarta amma tanaji tana gani takasa picking call Ιin har wayan ta tsinke, taΖi Ιaga wayan ne kuma don bataso yafahimci cewa tana cikin damuwa. Wani Ζiran nasa ne kuma yasake shigowa, still dai har wayan ta katse, Zahrah bata Ιauka ba, domin har yanzu bata dawo cikin nutsuwarta ba.. Ζira na uku ne yakuma shigowa cikin wayarta ta, ΖoΖari tayi wajen Ιoye damuwarta haΙe da Ιaukan wayar ta kara akan kunnenta..
STORY CONTINUES BELOW
Ajiyar zuciya Dr.Sadeeq yasauΖe sakamakon ji dayayi ta Ιaga wayan.
“Wani irin laifi me girma na’aikata haka da aka Ζi amasa wayata?” Dr.Sadeeq yatambaya.
Cikin sanyin murya Zahrah tace dashi “Bana kusa ne shiyasa”
Wata ajiyar zuciya yakuma sauΖewa cike da kulawa yace “Naji muryarki ta sauya ina fata dai kina halin lafiya?” cikin kulawa ya Ζare maganar.
“Lafiya Ζalau” tabasa amasa a taΖaice.
“Yakamata nazo muyi magana domin inaso nasan irin shirye shiryen da zakiyi, idan lokacin auren mu ya gabato, kinsan yakamata ace anfarayin komai akan lokaci, yanzu ina tuΖi ne idan na tsaya zanΖiraki”
“To” kawai ta’iya cewa dashi, har ya katse Ζiran.
Tanacire wayar akan kunnenta saΖo yashigo cikin wayar.
“Nakan ji wani iri a jikina idan har kina cikin wani irin yanayi, ki daina sa kanki a damuwa, saboda zaki iya cutar da zuciyarki, nikuma bazan so haka ba, saboda kece muradina” abun da saΖon yaΖunsa kenan..
Tsuka Zahrah tayi bayan tagama karanta saΖon, haΙe da kashe wayarta ta baki Ιaya, jira take kawai Allah yakaita gobe taga wayane yake raina mata hankali haka, daga goben kuma zata takamawa komaye birki, domin kuwa ko ma wayene bazai taΙa burgeta ba, zuwa yanzu babu wani Ιa Namiji da zaiyi tasiri acikin zuciyarta.
Zaid ne kwance akan makeken gadonsa wanda yasha bedsheet na alfarma, kwanciyar nan yayi irin wanda ba kyau, wato rufda ciki, wata doguwar takarda ne riΖe a hanunsa, wanda take Ζunshe da duk wani abu daya Ζunshi Dr.Sadeeq daga kan sunansa aikinsa har zuwa mazauninsa, dakuma a halinsa, kyakkyawan bincike Zaid yasa a kayi masa akan Doctor Ιin, saboda a cewarsa babu wanda ya’isa ya shiga huruminsa, saboda Zahrah tasace shi kaΙai, saboda haka dole ne zaitakawa Dr.Sadeeq birki..
Murmushine ya bayyana akan fuskarsa bayan yasanya duka hanunsa biyu ya shafi sajen dake kwance akan fuskarsa,, shi kansa yaΖosa gobe tayi yaga Zahrah’n sa, duk da kuwa cewa yana biye da duk wani shiga da ficenta, amma kwata kwata baya gajiyawa da ganinta, sam baisan meke damunsa ba, zuwa yanzu yafara kokonto dakuma tunani anya ba wannan abun da yakeji shi ake Ζira soyayya ba kuwa? Idan kuwa harda gaske abun nan da yakeji a game da Zahrah shi ake Ζira soyayya, to tabbas yakamu da so matsananci, sai dai kuma bayida ikon tabbatarwa kansa cewa so yake, hakanne ma ya hanasa gane wanni hali yake ciki, ko da wasa bai taΙa tunanin cewa Zahrah zata Ζisa ba, saboda haka ako da yaushe cikin Ζarawa kansa Ζwarin guiwa yake….
FRIDAY
Rana bata Ζarya, ranan yau ta kasance Friday kuma yaune Ζoyayyen mutumin ta yayi mata alΖawarin baiyana kansa gareta, sai dai kuma baΖon al’amarin da ta wayi gari dashi yasoma tsinkar mata da zuciya, haΙe da sanyayewar jiki, domin kuwa yau ta tashi tana me jin faΙuwar gaba, haΙe da bugawan zuciya da akai akai, hakan kuwa baΖaramin tsoro yajefata ciki ba, saboda bata taΙa mantawa irin wannan faΙuwar gaban ta dinga ji a ranan da mummunar Ζaddaranta zata rusketa,, sai dai kuma babu abun da yagagari Allah, don haka ta shiga yin addu’o’i acikin zuciyarta, saboda ta samu salama..
Ζarfe Uku na yammaci de de suka fito a lecture’n Ζarshe da suke dashi na wannan ranan, gaba Ιaya sukuku haka ta wuni a cikin school Ιin, Husnah tayi tambayan har ta gaji, akan ta faΙa mata meke damunta amma tace ba komai, to me zatace mata? ita kanta batasan meyake damunta ba.
Su Husnah ne suka kawota har Ζofar gida, saboda yanzu Dr.Sadeeq aiki yamasa yawa sosai, ga aikin office ga kuma hidiman hada hadan biki, gaba Ιaya baya samun isashshen lokaci, hakan yasa idan sun tashi a school take shiga motar da ake zuwa Ιaukar Husnah su sauΖeta a gida…
Tun azaure take ta kwaΙa sallama harta shigo cikin gidan nasu, amma babu wanda ya amsa mata, hakan yasa ta tabbatar cewa bakowa acikin gidan, har Ιaki ta leΖa amma babu Inna babu alamarta, saboda haka kai tsaye ta wuce Ιakinta. Zama tayi jigum tamkar wacce aka mawa mutuwa, fargaban haΙuwa da Ιoyayyen mutumin nan take, hakanan takeji dama bata nemi ganinsa ba, saboda gaba Ιaya jikinta yagaya mata babu alkhairi a haΙuwarsu, sai dai kuma babu yanda ta’iya tunda ya tabbatar mata da cewa yau Ιin zaizo, ganin da tayi tunani na shirin damunta, yasa ta Ιauko alΖur’ani mai girma tasoma karantawa, saboda hakan yana sauΖar da salama sosai acikin zuciyar wanda yake cikin Ζunci da fargaba….
STORY CONTINUES BELOW
Tana kai sujjadar Ζarshe ta sallan isha tafashe da wani irin kuka me tsuma zuciya, hakan yafarune kuma saboda ta kasa control Ιin kanta, sosai faΙuwar gaban da takeji yake tsanan ta aduk bayan wasu mintuna.. Cikin kuka tasamu ta sallame sallan isha Ιin, bayan ta gama faΙawa ALLAH buΖatunta, tana me kuma neman sauΖi a garesa, idanunta da suke cike da hawaye ta Ιaga haΙe da maida kallon ta ga yagalgalellen agogon bangon dake Ιakin nata, Ζarfe bakwai da arba’in, saura mintunan da basufi Ashirin ba yaΖaraso kenan, domin Ζarfe takwas yace mata zai zo…
Bugawan da agogo yayi 8:00 pm, yayi dai dai da bugawar zuciyar Zahrah, har saida taji cikinta yabada wani sauti. Kallon agogo takumayi akaro na barkatai, bazata iya tantance me takeji ajikinta ba, tsoro ne kokuma ruΙewa ne, takasa banbancewa.
Idanun Zahrah nakan agogo har Ζarfe takwas da minti biyar, ko Ζyafta idanun ta batayi ba, azahiri agogon take kallo, amma a baΙini ba da idanunta take kallo ba, da ΖwaΖwalwarta take gani, kallon agogon kawai take amma bata fahimta saboda tunaninta ba a kansa yake ba.
SaΖone yashigo cikin wayarta, wanda yayi dai dai da kusan Ιaukewar numfashinta.
“InaΖofar gidan ku” bakinta na rawa haka takaranta saΖon saikace wanda aka turomata saΖon ranar mutuwarta.
Takai kusan minti huΙu tana sake maimaita karanta saΖon, sai kace wanda aka yo saΖon da wani harshe bana hausa ba, idan kaga yanda take karanta saΖon zakai tunanin bata iya hausa bane, kokuma bata gane abun da saΖon yake nufi ba, bakomai yasa hakan ba kuma face tsoro da taji ya daki zuciyar ta, yayinda gabanta yatsananta faΙuwa, tabbas wannan faΙuwar gaban bana haka kawai bane, lallai dole akwai abun da zai faru da ita, amma kuma yazama dole taje taga wanda yake turomata saΖonni, hanunta na rawa haka ta Ιau hijib Ιinta ta sanya, da Ζyar take iya jan Ζafanta ta fita daga Ιakin…
Inna ta iske zaune a tsakar gida, tana jin radio, “Inada baΖo a waje Inna” Zahrah tafaΙa cikin wata irin murya me rauni. Yanayin yanda Inna taji muryan Zahrah yasanya ta Ιago da kanta ta kalle ta, “Lafiyanki kuwa, meke damunki?” Inna tatambaya cike da mamakin yanda taga jikin Zahrah a sanyaye.
“Babu komai Inna” Zahrah tafaΙi haka tana me nufar hanyar Ζofar fita daga gidan..
Kasancewar akwai wadataccen haske a Ζofar gidan nasu na Ζoyayen wuta wanda maΖotansu suka kukkuna hakan yasa wajen baida duhu, zaka iya hango duk wanda ke tsaye dakuma wanda ke tsugunne, kai harma wanda ke kwance zaka iya ganinsa.
Bugun zuciyarta ne yaΖaru yayinda Ζafofinta suka soma yi mata nauyi, wani mutumi tagani tsaye ajikin wata mota da ta amsa sunanta mota, sai dai kuma yajuya baya, saboda haka bayansa kawai take iya hangowa, sanye yake da wandon jeans black dakuma black Ιin riga sannan kuma akwai hula irin fosin kaf Ιin nan akansa. A hankali take taka Ζafafunta dasuka mata nauyi tanufi inda yake tsaye, yayinda ta sanya hanunta ta cikin hijab Ιinta ta dafe Ζirjinta da takejinsa kamar zai daka tsalle yafito waje..
Abu na farko daya fara hargitsa mata Ζwakwalwa bayan ta isa gareshi shine fitinannen Ζamshin turarensa wanda har gaban abada bazata taΙa manta wan nan Ζamshin ba, wani irin killer smile Zaid yayi bayan yatabbatar da cewa ta karaso gab dashi, fuskarsa Ιauke da murmushi ya juyo zuwa gareta, haΙe da sanya hanunsa ya cire hular dake kansa, take kyakkyawar fuskarsa ta bayyana, wacce take Ιauke da murmushi.
Jikinta ne yaΙauki rawa yayinda idanunta suka Ζara buΙewa take numfashinta yasoma ΖoΖarin Ζwacewa, zuciyarta tashiga duka, Ζafafunta suka Ζage waje Ιaya, yayinda hawaye suka dinga fitowa daga idanunta tamkar anyi ambaliyan su.
Kallon yanda jikinta yake rawa Zaid yayi haΙe da dawo da kallonsa kan fuskarta jefa idanunsa yayi cikin nata. “ZAHRAH!” yaΖira sunanta da wata irin murya me sanyi, sakamakon ganin da yayi kamar cewa bata cikin hayyacinta…
“ZAHRAH” yasake Ζiran sunanta, de de lokacin ne kuma numfashin ta yashiga gudu yana neman Ζwace mata, aikuwa kasa fusgo numfashin nata tayi, lokaci Ιaya numfashinta yayi nasaran fita daga jikinta, take ta yanki jiki tafaΙi warwas a Ζasa, cikin mugun tashin hankali Zaid yayi kanta, haΙe da sanya hannayensa duka biyu ya Ιagota zuwa jikinsa, sunanta yashiga Ζira cikin tashin hankali dakuma ruΙewa, a matuΖar firgice ya sanyata acikin motarsa haΙe da shiga cikin motar da wani irin gudun gaske Zaid yafigi motar ya cillata kan titi… Gaba Ιaya ya ruΙe wani irin gudu yake shararawa baburuwansa da wanda ke gabansa ko bayansa, gaba Ιaya ya ruΙe sunan Zahrah kawai yake ambata, Allah yasa ba zuciyarta ta haΙiya ba..
STORY CONTINUES BELOW
Matsanancin gudun da Zaid yakeyi har ya wuce hankali, da wani irin gudu yashigo cikin asibitin yayin da ya Ιauko Zahrah caΙak a hanunsa tamkar wata Ζ΄ar tsana, haka yashigo da’ita cikin asibitin, ganin haka yasa Doctors sukayo kansa da sauri, hankalinsa a matuΖar tashe ya miΖa ta ga doctors sukayi emergency da’ita kai tsaye.. Taimakon gaggawa likitoci suka shiga bawa Zahrah domin kuwa bako maine ya haifar mata da Ιaukewar numfashin ba, face razana dakuma tsananin firgita haΙi da tsoro da suka rusketa alokaci guda, sannan yanayin yanda zuciyarta ke bugawa, yawuce mizani, idan har zuciyar tata tacigaba da bugawa da sauri sauri haka, tofa lalllai rayuwar Zahrah tana cikin haΙari…
(Niko nace idan Zaid yakashe mana Zahrah zamuci …. ko fans?)1
Iya ruΙewa Zaid ya ruΙe yakasa koda zamane, damuwarsa Ιaya shine Doctors Ιin da suke kan Zahrah, su sanar dashi meke faruwa, lallai idan har Zahrah tasamu wani matsala, to bazai taΙa yafewa kansa ba, sannan kuma babu uban da ya’isa yazauna lafiya, matuΖar likitocin nan suka kasa shawo kan matsalan Zahrah..
Kusan minti talatin likitocin nan sukayi suna ΖoΖarin shawo kan numfashin Zahrah, cikin ikon Allah kuwa sun samu komai yayi dai dai sai dai dole tana buΖatar hutu kodan zuciyarta ta samu salama…
Suna fitowa Zaid yayi kansu, gaba Ιaya idanunsa sun kaΙa sunyi jajur dasu.
Kallonsa Ιaya daga cikin manyan likitocin dasuke kan Zahrah yayi haΙe da dafa kafaΙunsa, “Ka kwantar da hankalinka, komai yayi dai dai, yanzu biyoni office Ιina”
Ba musu balle girman kai Zaid ya bi bayan liikitan.
Kasa zama akan kujeran da Dr Ιin yabasa yayi, babban damuwarsa shine yasan wani hali Zahrah take ciki.
“Nace ka kwantar da hankalinka, kazauna saimuyi magana ko” likitan yafaΙa yana me nuna masa kujera..
“Kaga Doctor bazamane yadameni ba, babban damuwana shine nasan wani hali take ciki” Zaid yafaΙi haka cikin damuwa..
“Zan faΙama ko wani hali take ciki, amma dole sai ka zauna”
Badon Zaid yasoba haka yazauna akan kujera haΙe da sanya duka hanunsa ya dafe kansa.
“Bawani babban abubane yake damunta, akwai abun da yafirgita ta ne, kuma dama anasamun irin haka, sau da dama firgici da tsoro, yakansa mutum yasamu Ιaukewar numfashi naΙan wasu daΖiΖu, amma idan tadawo hayyacinta komai zaidawo dai dai, sai dai kuma tana buΖatar hutu sosai, saboda haka bayau zaku samu sallama ba, dole sai kunjira zuwa gobe da safe, saboda yanzu haka akwai alluran damuka mata kuma suna sa bacci sosai”
Ajiyar zuciya me Ζarfi Zaid ya sauΖe, saboda jin bayanan Doctor da yayi, sun sauΖar masa da nutsuwa “Amma dole sai anan zamu kwana? me zai hana kabani ita mutafi gida, idan yaso saitayi baccinta acan” Zaid yafaΙi haka fuskarsa Ιauke da damuwa.
Murmushi Doctor yayi haΙe da cewa “Hakan bazai samu ba, saboda zata iya farkawa da kowani lokaci, bamu kuma san a wani hali zata tsinci kanta ba, bayan ta farka, saboda haka zamanku anan Ιin zaifi amfani” Doctor yafaΙi haka cike dason gamsar da Zaid.
Kai kawai Zaid yajinjina haΙe da kallon Doctor “Zan’iya ganinta kuwa? sannan kuma inaso akaita Ιaki na musamman konawane kuΙin Ιakin zan biya”
“Wannan ba’abun damuwa bane, zamu kaita Ιaki na musamman sannan kuma zaka iya ganinta, bana Ζira nurse sai a sanja mata Ιaki daganan saikaje ka ganta ko” Dr yafaΙi haka bayan yakara waya akan kunnensa. Cikin mintuna Ζalilan aka sanjawa Zahrah Ιaki inda aka kaita Ιaki na musamman.
Zaid ne tsaye akanta yana me Ζare mata kallo, karo na farko kenan daya farajin wani irin matsanancin tausayin ta acikin zuciyarsa, haΙe da wani shauΖi mai fisgar zuciya. A hankali yaΖaraso dab da gadon nataz haΙe da ranΖwafo da kansa dakuma Ζirjinsa zuwa gaf da’ita, lumshe idanunsa yayi haΙi da kai bakinsa gefen kumatunta ya yi mata kiss, haΙe da sa hanu yashafi gefen fuskarta, “I’m sorry Zahrah!” yafaΙi haka acikin maΖoshinsa. Karo na farko kenan a rayuwarsa daya soma bawa wata mace haΖuri.. Zama yayi a bakin gadon, haΙe da kama hanunta na dama yasanya acikin nasa hanun, a hankali yake murza hanunta haΙe da lumshe idanunsa.
Abu kamar wasa hankalin Inna ne yasoma tashi ganin Zahrah ta kwashe sama da awa Ιaya, a waje batare da ta shigo gida ba, gashi ta leΖa waje bataga ko da me kamannin Zahrah bane, kasa zama inna tayi gaba Ιaya hankalinta a tashe yake, Baffa ne yashigo cikin gidan bakinsa Ιauke da sallama, ko amsa sallaman nasa Inna batayi ba tayo kansa tana cewa “Yau wa Malam gwamma da ka dawo, ko ka haΙu da Zahrah a waje kuwa?”
“Zahrah kuma, ina Zahrah’n take?” Baffa yatambaya cike da mamaki.
Nan Inna tashaida masa cewa tunΙazu tafita bata dawo ba,bayan tasanar mata cewa wani ne yaΖira ta a waje.
Take hankalin Baffa yatashi, domin kuwa Zahrah bata taΙa irin haka ba, har maΖota ya aika ko taje amma aka ce masa bata zoba, take Baffa da Inna suka zuba tagumi, sun marasa ta ina zasu fara, Inna cema takawo shawara akan cewa aΖira Doctor Sadeeq koshine yazo ya Ιauketa, aikuwa Baffa yayi na’am take yadannawa number’n Dr.Sadeeq Ζira, bugu biyu Dr.Sadeeq yaΙaga wayan,, shima bakaΙan ba hankalinsa yatashi jin dayayi cewa wai su Baffa basuga Zahrah ba, ae take yashiga motarsa yataho gidansu Zahrah’n duk da cewa dare yayi…
Kallon agogon hanunsa Zaid yayi a karo na barkatai, Ζarfe 10 na dare kenan, ajiyar zuciya ya sauΖe akaro na uku, haΙe da furzar da iska a bakinsa, kallonsa yakuma mayarwa ga Zahrah, wacce take ta sharan bacci, hakanan yatsinci kansa da sakin murmushi mai sauti, komai na Zahrah me kyaune, tafiyin kyau ma idan tana bacci.
Zama yayi akan wata kujera dake kusa da gadon haΙe da jingina bayansa da jikin bango, lumshe idanunsa yayi tare da cije laΙΙansa sai yanzu Ζ΄ake tunanin ya makomarsa zai kasance idan Zahrah tafarfaΙo, domin kuwa ya hango muguwar tsanarsa acikin idanunta.Lokaci Ιaya hankalin Dr.Sadeeq yayi wani irin mummunan tashi, take ΖwaΖwalwar kansa tashiga charge, a iya tsawon sanin da ya yi mawa Zahrah, ita ba mace bace meson fitar dare, balle har tayi nisa da gida, sai dai kuma abun mamaki gashi yau annemeta an rasa, bayan ko Ιazu suna tare a waya shida ita, baikuma ji wani sauyi a tattare da’ita ba, sai dai kawai muryarta da yaji cikin sanyi. “To ina Zahrah taje?”
Yayi mawa kansa tambayar da bayi da amsa.. “Kodai Zahrah tayi hakane don batason aurena da’ita?” yakuma tambayar kansa, sai da zuciyarsa ta buga, shi kansa yatambayi kansa abun daya faΙar masa da gaba, kai amma Zahrah bazatayi haka ba, saboda ita da kanta ta tabbatar masa cewa ta amince da auren sa, saboda haka bazata bar gida saboda batason auren sa ba..
Kallonsa yamaida ga Inna wacce tayi tsuru tsuru da ido tamkar wata munafuka…”Da tazo fita bakiga wani alaman damuwa ko tashin hankali akan fuskarta ba?” Dr yatambaya cike da kulawa.+
“Ζwarai kuwa da damuwa tafita, saboda kwana biyun nan gaba Ιaya da damuwa take wuni sakamakon waΖ΄ansu tsinannun Ζ΄an mata da suka zo, acewar Ιaya daga cikin su wai ita zaka aura Samira take ko Salma oho, haka nan suka zo hargida suka zagemu kaf, tamkar ma zasu mana luguden duka, to tundaga tafiyarsu dai take fama da Ζuncin rai har kawo yau, Allah dai yasa ma basune sukai mata wani abun ba” Inna tafaΙi haka cike da jimami..
Cike da mamaki Dr.Sadeeq yace “What Salima tazo har gidan nan taci muku mutunci?”
“Ζwarai kuwa ashe dagaske kasanta, tabbas haka tace sunanta wai Salima, ita da waΖ΄ansu masu ΖoΖaΖΖun fuska, kamar an gasa nama”
Hanu Dr.Sadeeq yasanya yadafe kansa, lallai idan de har Salima bata ji kunyar zuwa ta zagar masa abar sonsa ba, to tabbas shima bazaiji kunyar zuwa har gidansu yaci mata mutumci ba, Uwa mahaifiyarsa kaΙai ze iya Ιagawa Ζafa akan Zahrah, amma duk wacce tace zata ci mutumcin Zahrah tofa shima zaici nata mutuncin, lallai yakamata ne yafara nemo inda Zahrah take kafun yasan matakin da zai Ιauka akan Salima. Sake dialing number’n Zahrah yayi amma still ce masa ake wai wayar akashe take, tun Ιazu yake Ζiran wayar anacemasa akashe wayarta ta take.. Tunanin Ζiran abokinsa inspector Adam ne ya faΙo masa, saboda yalura lamarin dole sai anshigo da hukuma ciki, tunkan suyi sake lokaci ya Ζure musu. Nan yashiga dialing Number’n inspector Adam amma har wayar ta katse bai Ιauka ba, sake Ζira yayi amma still bai Ιauki wayar ba, tsuka Dr.Sadeeq yayi haΙe da maida wayarsa cikin aljihunsa….
Asibiti
Sai yanzu tunanin halin da iyayen Zahrah zasu shiga yafaΙo masa arai, tabbas yakamata ne yasanar dasu halin da ake ciki, wayarsa yaΙauka haΙe da soma rubuta saΖo, domin bayason wayar da zaiyi yatashi Zahrah a baccin da takeyi, saboda haka gwamma yatura saΖo,a ganinsa hakan zaifi… wata number yaturawa saΖon, batare da yajira amsar da wanda yaturawa saΖon zai basa ba, ya maida wayarsa cikin aljihu…..
Dr.Sadeq ne yadubi Baffa dake a halin damuwa. “Banaje nasanarmawa Ζ΄an sanda, akwai abokina inspector, inaga kawai gwamma naje gidansa na sanar dashi abunda ke faruwa, ina ga zaifi akan tsayuwan damuke” yafaΙi maganar yana me duba agogon dake Ιaure a tsintsiyar hanunsa, Ζarfe sha Ιaya na dare kenan agogon sa yanuna masa..
STORY CONTINUES BELOW
Sallaman da sukaji ana kwaΙawa a Ζofar gidan ne yaΙauki hankalinsu, ae ba shiri Baffa da Dr. Sadeeq suka Ιunguma zuwa Ζofar gidan, Inna ma ba’a barta a baya ba ta rufa musu baya.
Wani mutumi me shigar cute baΖaΖe suka gani tsaye a bakin Ζofar gidan, yayinda yarufe idanunsa da tabarau, da ganinsa dai zaka gane irin body guard Ιin nan ne.
“Waye kai?” Dr.Sadeeq yatambaya yana me Ζaremasa kallo.
“SaΖo aka bani nasanar daku cewa Zahrah bata da lafiya, yanzu haka tana asibiti..” baikai ga idar da zancen nasa ba, Dr.Sadeeq yace “Meyasameta sannan kuma a wani asibiti take?” duka tambayar yayisune alokaci Ιaya, kuma
cikin ruΙewa..
“Zaku iya biyoni muje” Body guard Ιin nan yafaΙa yana me nufar wajen da motar da yazo da ita ke fake.
Kallon su Baffa Dr.Sadeeq yayi haΙe da cewa su shigo motarsa subi bayan body guard Ιin, hakan kuwa akayi motar Dr.suka shiga yayinda Dr.yashiga bin bayan motar body guard Ιin. Gaba Ιaya ba acikin nutsuwarsa yake driving Ιin ba. Fargabane cike a zuciyarsa, bayi da wani buri da yawuce yaga Zahrah, yakuma ji meke damunta, har aka kawota asibiti batare da sanin su Baffa ba..
Suna shiga cikin asbitin wannan body guard Ιin ya kalli Dr.Sadeeq haΙe da cewa ya biyosa ciki, su Inna kuwa su jirasa, da su Inna sunso Ζi, amma sai Dr. Sadeeq yace su yarda su jirasu anan Ιin, badon su Inna sun so ba, suka tsaya daga waje… Suna shiga cikin wani corridor guard Ιin yaciro wayarsa, haΙe da karawa akan kunnensa.
“Oga na faΙa musu sunma biyoni, yanzu haka munatare da wani inazaton Ιan uwanta ne, iyayenta kuma suna waje” Abunda Body guard Ιin yafaΙa kenan cike da girmamawa.
Tsuka Zaid yayi sakamakon jin abunda guard Ιin nasa ya ce, shirmen banza, cewa yayi yafaΙamusu bawai ya taho masa dasu ba, to yanzu dayakawosu ina zai sasu, wata tsukan yakuma yi, haΙe da sakai yafice daga cikin Ιakin bayan ya sake rufe Zahrah da bargo..
Cakume kwalan guard Ιin nan Dr.Sadeeq yayi cike da Ιacin rai yace “Bamason iskancin banza kace tana asibiti bata da lafiya, gashi munzo kuma kana ΖoΖarin raina mana hankali, wlh idan wani abu yasameta saina Ιaureka” Cikin Ιacin rai Dr.Sadeeq yafaΙi maganan domin kuwa yulura guard Ιin nema yake ya raina masa hankali….
“Idan har ka’iya Ιauresa, to tabbas zan iya yarda na Ζiraka da suna jarumi !!” muryar Zaid takaraΙe wajen, wanda yake Ζarasowa garesu cikin takunsa na isa..
Kallon Kallo aka shigayi tsakanin Zaid dakuma Dr.Sadeeq, wanda kowannensu da irin manufar tasa kallon.
Sama da 5 minute Zaid da Dr.Sadeeq suka Ιauka suna kallon juna, Zaid nayimawa Dr.Sadeeq kallon tsana, yayinda Dr.Sadeeq kuma kemawa Zaid kallon tuhuma, haΙe da son sanin koshi waye…
Kallon guard Ιin nan Zaid yayi haΙe da taΙe bakinsa cike da isa yanuna Dr.Sadeeq haΙi da cewa “Wan nan kuma waye?” yayi tambayar cike da rainin hankali, yana me Ιage kai sama bayan yajefawa Dr.Sadeeq wani irin kallo..
“Hmm ba buΖatar kasan koni Ιin waye, kai de zaifi kyau kasanardani ko kai waye, amma shishshigi baikamace kaba, saboda bakayi kama da me kula da lafiya ba, kafi kama da masu shiga inda ba’a buΖatarsu” Dr.Sadeeq yafaΙi haka shima yana me Ιauke kansa daga kan Zaid.
Murmushi Zaid yayi haΙe da kallon Dr.Sadeeq daga sama har Ζasa. Kansa kawai ya girgiza “Lallai bana buΖatar kowa, kasan yanda zakayi dasu” Zaid yafaΙi haka ga Guard Ιinsa, haΙe da juyawa yanufi Ιakin da aka kwantar da Zahrah, lokacinsa bana me aikin duba lafiya bane, lokacinsa muhimmine kuma sai me mahimmanci yake bawa…
Hasala Dr.Sadeeq yayi lokaci Ιaya yaji zuciyarsa tana masa zafi, yana da sauΖi amma watarana abu kaΙan ke Ιata masa rai, a zuciye ya juya yafice daga cikin asibitin.. Su Inna dake tsaye a harabar asibitin suna ganinsa sukayo kansa da sauri suna tambayarsa ko Zahrah tana lafiya?
STORY CONTINUES BELOW
Kasa amsa musu yayi saima cewa da yayi, su shiga mota su yasauΖesu a gida… Bayanda suka iya haka suka shiga cikin motar jiki a sanyaye, saboda sunga gaba Ιaya fuskar Dr.Sadeeq Ιin Ιacin raine shumfuΙe akanta, kenan akwai abun dake faruwa.. Da wani irin gudu yaja motar suka fice daga haraban asibitin…
Gyara zama Baffa yayi haΙe da kallon Dr.Sadeeq wanda da’alama tunaninsa baya jikinsa.
“Meyake faruwa ne Likita? kashiga kakuma fito da Ιacin rai, ina Zahrah’n takene me yasameta?” cikin damuwa Baffa yayi tambayar domin shi gaba Ιaya kansa ya kulle.
Daure zuciyarsa yayi haΙe da cewa “Tana nan lafiya, gobe da safe zamu zo mu Ιauketa”
Ajiyar zuciya Baffa yasauΖe me Ζarfi yagodewa Allah da ba wani abun bane yasamu Zahrah, to amma ae da anbarsu sun ganta…
A Ζofar gida Dr.Sadeeq ya sauΖesu haΙe dayi musu saida safe yaja motarsa yayi gaba..
Suna shiga gida Inna ta kalli Baffa haΙe da cewa “Anya kuwa Malam bakaganin cewa akwai matsala?”
“Bawai gani nakeba, tabbas ma nasan akwai matsala Salame, sai dai fatana Ιaya shine Allah yatsare Zahrah, amma tunda Likita yace gobe da safe zamu koma asibitin, saimu jira zuwa goben idan Allah yakaimu”
“To Allah yakaimu” Inna tafaΙa jiki a sanyaye… Da “Ameen” kawai Baffa ya amsa.
Kamar yanda Zaid ya kwana a zaune, haka Dr.Sadeeq yakwana juyi, gaba Ιaya kansa ya kulle, yarasa meke faruwa, baisan waye wannan gayen ba, amma tabbas yaji tsanarsa fiye da misali, amma babban abun tambayar shine me yasamu Zahrah har aka kawota asibiti? sannan kuma meke tsakaninta da wannan mutumin? tambayar dayake buΖatar a amsa masa kenan, amma babu wanda zai amsa masa, tambayar da ta kuma hanasa bacci kenan…
Ζarfe bakwai na safe Zaid yasa aka turo masa nurses guda biyu, suka zo dankula da Zahrah, saboda yana buΖatar yaje gida yayi wanka…..
Tamkar amafarki haka fyaΙen da yayi mata yasake dawowa cikin idanu da ΖwaΖwalwarta, wani irin nishi tayi haΙe da sakin Ζara mai sauti, lokaci guda kuma ta ware idanunta da suka cika tab da Ζwalla, da sauri nurses Ιin nan sukayo kanta.
Kallon Nurses Ιin tashiga yi, haΙe da soma Ζaremawa Ιakin da take ciki kallo, tabbas idan ΖwaΖwalwarta bata juye ba, zata iya cewa nan Ιakin asibiti ne sannan kuma waΖ΄an nan dake tsaye a gabanta nurses ne.
“Barkanki da tashi, me kike buΖata yanzu a kawomiki?” Ιaya daga cikin nurses Ιin nan ta tambayi Zahrah cike da kulawa…
“Idanunta dasuke zubar da ruwan hawaye, ta Ιaga ta kalli nurse Ιin haΙe da girgiza kanta alamar batason komai.
Hanun nurse Ιin takamo duka biyu haΙe da fashewa da wani irin kuka me ciwo, da’alama wani abu takeson faΙawa nurse Ιin.. Dai dai lokacin aka turo Ζofar Ιakin aka shigo, Zaid ne yasha adonsa sai zuba Ζamshi yake.
Tsayawa yayi cak daga bakin Ζofar sakamakon ganin yanda Zahrah take kuka..
“Me kukayi mata?” yajefawa nurses Ιin tambaya cikin yanayi na rashin yarda dasu.
“Bamuyi mata komai ba,ranka ya daΙe tashinta kenan tasoma rusa kuka” su duka biyu suka haΙa baki wajen faΙan maganar…
Tamkar wanda aka zuba mata narkakken dalma haka taji sauΖan kalamansa acikin kunnuwanta, rumtse jajayen idanunta tayi, ji takeyi tamkar zuciyarta zata faso Ζirjinta ta fito.
A hankali Zaid yasoma takawa zuwa gare ta.
“Zahrah” yaΖira sunanta dai dai lokacin daya Ζarasa kusa da’ita.. Tunkafun yagama rufe bakinsa yaji sauΖan wani irin gigitaccen mari akan Ζuncinsa, kafun ΖwaΖwalwarsa tagama tantance masa abun dake faruwa, yakumajin sauΖar wani marin aΙaya Ιangaren hagu na kumatunsa..
STORY CONTINUES BELOW
Kasa koda motsawa yayi saima hangame bakinsa da yayi haΙe da zaro idanu yana kallonta,, Gaba Ιaya marukan nan Zahrah ce ta shararawa Zaid akan fuskarsa..
Yanayin yanda idanunta sukayi ja kace barkono ko attarugu aka watsa mata a ciki.
“Kazone ka sake cutar dani? to gani kacutar dani, gani nace ka cutar dani!!” tafaΙi haka da wani irin tsawa..
Cikin matsanancin kuka Zahrah tasanya hannayenta duka biyu tashiga dukan sa, tako ina Zahrah ke kai masa duka tana kuka, ganin hanu bazai wadarta ba yasanya ta sanya bakinta, tashiga cizonsa a Ζirjinsa, hakama bai mata ba saida ta Ιauki wani Ζarfe dake kusa da’ita tashiga kwaΙa masa a jikinsa tana kuka me tsuma zuciya… Haka Zaid ya tsaya tamkar gunki Zahrah na cizo da yaΖushinsa, gakuma dukan da take kai masa, amma yakasa yi mata komai, yakuma kasa koda motsa hanunsa ne.. dai dai lokacin su Dr.Sadeeq suka shigo cikin Ιakin, turus suma sukayi sakamakon ganin abunda ke faruwa.
“Kasheni zaifi maka sauΖi aduniyar nan, akan ace kabarni da raina, natsaneka, dan Allah ka kasheni!!” Abun da Zahrah ke faΙa kenan tana kuka. Kowa a wajen tsayawa yayi yana kallon ikon Allah, bakomai ke tashi a Ιakin ba face kukan Zahrah, tun tana dukansa da’iya Ζarfinta har Ζarfin nata yasoma Ζarewa a hankali ta sulale zuwa Ζasa, saboda kuka har shiΙewa take…
“Zahrah” Dr.Sadeeq yaΖira sunanta, cikin wata irin murya.. Jin muryan Dr akunnenta yasa taΙago kanta, tana ganinsa tsaye tatashi a guje haΙe da nufar inda yake da sauri tafaΙa cikin jikinsa haΙi da rungumesa Ζa Ζam,wani sabon kukan kuma ta sanya, haΙe da soma buga kanta akan Ζirjinsa..
Duka hannayensa shima yasanya ya rungumeta..
“Wayeshi?” Dr. Sadeeq yayi mata tambayar acikin kunnen ta..
“Shine wanda yaruguzamin rayuwata, shine yarabani da budurcina, shine yayi sanadiyar lalacewar farinciki na!!” Zahrah ta bashi amsa cikin matsanancin kuka, muryarta ko fita batayi da kyau tsabar kuka…
Iya kaΙuwa Dr.Sadeeq ya kaΙu dajin cewa wai wanda yayiwa Zahrah fyaΙe ne tsaye a gabansa, kallon tsana Dr.Sadeeq yashiga yi mawa Zaid..
Zaid kuwa tuni idanunsa sun rune sun zama jajur dasu, jikinsa har rawa yake, koda sau Ιayane baiji zafin duka dakuma marin da Zahrah tayi masa ba, babban abun da yayi masa zafi, shine yanda Zahrah taje jikin wani ta lafe. Tun da yake a rayuwarsa baitaΙa jin abun da yaji a yau ba… Takowa yashiga yi harzuwa inda suke tsaye ita da Dr.Sadeeq, hanunsa yaΙaga domin ya ciro Zahrah daga jikin Dr.Sadeeq. Da sauri Dr.Sadeeq ya tura Zahrah bayansa, haΙe da damΖe hanun Zaid wanda yakawo daniyar taΙa Zahrah..
“Babban kuskuren da zakayi a rayuwarka shine kayarda hanunka yasake taΙa jikinta, kayi na farko yakuma isheka, saboda haka ka kiyaye! ” Dr.Sadeeq yafaΙi haka cikin matsanancin Ιacin rai…
Hanun Zahrah yakama haΙe da janta suka fice daga cikin Ιakin, da sauri su Inna ma suka rufa musu baya, saurin dafe saitin zuciyarsa Zaid yayi, wanda yakeji tamkar zatayi tsalle ta fito waje.. Jingina bayansa yayi da bango haΙe da lumshe idanunsa.. Zafi yakeji a Ζirji dakuma zuciyarsa, take wani irin ciwon kai da zazzaΙi me zafi suka sauΖar masa alokaci guda..
Dr.Sadeeq dakansa yasanya Zahrah a mota, wacce har yanzu kuka take, ataΖaice dai tsabar kuka numfashinta har Ιaukewa yake…. Saboda tsabar gudun da Dr.Sadeeq keyi cikin mintuna Ζalilan suka isa gida, kowa acikinsu yana cikin tashin hankali. Inna ce takama Zahrah takaita Ιakinta. Bayan minti kaΙan Inna tafito daga Ιakin Zahrah da sauri. “Likita temaka numfashinta yana shirin Ιaukewa, taΖi daina kukan” Inna tafaΙa a ruΙe.
Dr.Sadeeq yana shiga Ιakin yace inna tabasa ruwa, aikuwa mintuna kaΙan Inna takawomasa ruwa, cewa yayi Inna taΙan basu wuri bamusu Inna tafita a Ιakin…1
Ιago Zahrah Dr.Sadeeq yayi haΙe da kai kofin ruwan bakinta, sosai tasha ruwan, take ta soma sauΖe ajiyar zuciya, amma still hawaye na gangara akan fuskarta..
Idanunta dasukayi luhu luhu saboda kuka ta Ιago dasu takalli Dr.Sadeeq, saikuma tasake fashewa da kuka, haΙi da faΙawa cikin jikinsa tarungumesa Ζam, hanunsa duka biyu yasanya shima ya rungumeta, a hankali ya shiga hura mata kunnen ta, saboda hakan zai sa taΙan samu relief, koba komai kukan nata zai tsagaita. Har tsakiyar kansa yakejin kukanta.
Tsawon mintuna 15 yakai yana hura mata kunne, a hankali tasoma rage sautin kukan nata, bayan kamar mintuna 5 yajita shiru, sai sauΖar numfashinta da yake ji akan Ζirjinsa akai akai..
Yana duba fuskarta yaga tayi bacci, hawayene yaji suncika masa idanu, tabbas Zahrah taga Ζaddara a rayuwarta, wani irin tausayinta yakeji me tsanani, tabbas idan ya aureta zai yi iya ΖoΖarinsa wajen ganin ya mantar da ita duk wani damuwa da tshin hankalin da ta tsinci kanta ciki, zai kuma yi iyaka ΖoΖarinsa wajen ganin yabata farinciki me Ιorewa.
A hankali ya kwantar da’ita, haΙe da sanya hanu ya gyara mata dogon gashinta da ya rufe mata fuska. Yajima yana kallonta kafun daga bisani ya tashi yafita daga cikin Ιakin…
Zaune yasamu Baffa da Inna a tsakar gidan sunyi jigum. Yana fita suka tsaresa da ido da’alama bakinsu Ιauke yake da tarin tambayoyi..
Ajiyar zuciya ya yi haΙe da cewa “Tasamu bacci, kada ayi wani abu da zai tasheta, ni zan wuce office anjima zandawo”
Har bakin motarsa Baffa yarakasa bayan sun tattauna wata magana me mahimmanci….
Zaid ne zaune a cikin falon sa dake guest hause Ιinsa, kallo Ιaya zakai masa kafahimci cewa yana cikin tashin hankali, kwalaben giyane zube a gabansa, guda uku daga cikin kwalaben duk ya shanye giyan dake a
cikinsu, ba abun dake gigita masa tunani da ΖwaΖwalwa kamar yanda Zahrah ta nunamasa tsana a fili Ζarara, kallonsa yakai ga hanunsa na dama wanda yake fidda jini, bakomai yajawo hakan ba face Ζarfen da Zahrah ta kwaΙa masa akan hanun,, runtse idanunsa dasuka kaΙa sukai jajur yayi, haΙe da cije laΙΙansa, wani irin zafi yakeji acikin zuciyarsa a duk sanda idanunsa suka hasko masa lokacin da Zahrah taje ta faΙa Ζirjin Dr.Sadeeq, jiyake kamar ya kurma ihu, ko zai samu salama acikin zuciyarsa…. Ahankali yamiΖe tsaye haΙe da nufar Ιakinsa, Da Ζyar yake iya tafiya, saboda abuge yake mankas, kai tsaye Ιan Ζaramin drowern dake kusa da gadonsa yanufa, wani tablet yaΙauko haΙe da Ιarewa kusan guda takwas ya watsa a bakinsa, haΙi da korawa da ruwan swan… FaΙawa kan gado yayi yana me rumtse idanunsa, “Natsaneka” shine kalmar da tafi Ιaga masa hankali aduk cikin kalaman da Zahrah ta faΙa masa. itace kuma kalmar da takeyi masa yawo acikin kansa, cikin wani irin yanayi Zaid yatashi tsaye haΙe da nufar wajen da yake aje kayan shafansa, watsi yashigayi da duk wani abu dake kan dressing mirror Ιin nasa, lokaci Ιaya yayi buji buji da Ιakinsa, yayinda ya fasa gaba Ιaya kwalaben turarensa, har sai da wasu kwalaben suka yankesa a hanu da Ζafarsa, amma don tsabar baΖin kishi ko zafi baiji ba, idanunsa Zahrah kawai suke hangomasa kwance a Ζirjin Dr.Sadeeq. Lokaci Ιaya yaji wani irin juwa ta Ιebesa, harsai da yariΖe bango, a daddafe yaΖa risa kan gadonsa ya kwanta, ji yayi kansa yasoma juyawa, yayinda idanunsa suka soma rufewa, yasoma ganin komai bibbiyu, cikin mintuna Ζalilan idanunsa suka rufe ruf…..Ba’itace ta farka ba sai wajen Ζarfe Ιaya na rana..+
A hankali take ware manya manyan idanunta da suka kaΙa suka zama jajur dasu, ba tun yanzu ta farka ba, kawai dai Allah ne be bata daman buΙe idanun nata ba sai yanzu. Tun farkawarta kuwa take cikin tsanani da kuma mamakin mutum mai taurin zuciya irin Zaid, lallai shiΙin yacika Ιan iska kuma shu’umi, duk da irin girman laifin da ya aika ta mata, hakan baisanya yaji Ιar ko kuma shakkan tunkarar ta ba, lallai shiΙin acikin Ζ΄an iska ma daban yake,, haka nan taji gaba Ιaya zuciyarta ta ΖeΖashe takuma bushe, lallai tunda ya nuna mata shiΙin babban Ιan iska ne yakamata ace itama ta nuna masa iyakar iskancinsa, tunda har baiji kunyar tako Ζafa yazo gareta ba, to tabbas itama yakamata tacire kunya, wajen ganin ta koya masa hankali… Sai dai kuma kome zatayi bazata huce ba, saboda iyaka kuma maΖurar cuta Zaid yayi mata, ya mata illa dakuma tabon da bazata taΙa mantawa ba, harta koma ga mahaliccinta kuwa, Zaid ne ya surka mata farincikinta da wani irin mummunan baΖin duhu, ya katse mata jin daΙi da kuma walwalanta, ya lalata mata rayuwa a rana Ιaya, ya ruguza duk wani buri da fatanta, ya gwada mata Ζarfi ya amshi budurcinta cikin yanayi na tozarci, me yafi wan nan ciwo a rayuwar Ζ΄a mace? tasan Ζiyayya amma kuma zafin Ζiyayyar da takeyi mawa Zaid na daban ne, tabbas idan da kisan kai yana da kyau a addinance to haΖiΖa ba abun da zai hanata kashe Zaid san nan kuma itama ta kashe kanta, saboda Ζuncin da ya mamaye zuciyarta ba’irin Ζuncin nan bane da yake fita, lallai Ζuncin zuciyarta dawwa memme ne, sai dai kawai ta roΖi Allah daya sassauta mata…..
Hawayen da suka fito daga cikin idanunta suka gangaro ta gefen kumatunta ta sanya hanu ta share haΙe da miΖewa zaune, babu amfanin Ιata hawayenta wajen fiddasu, yanzu lokaci yayi da shine yakamata yayi kuka ba ita ba. Kayan jikinta tashiga cirewa, haΙe da Ιaura zani akan Ζirjinta kana ta sanya lufaya….
Tana fitowa daga cikin Ιakin nata, Inna ta kalleta haΙe da cewa.
“Yauwa Zahrah kintashi ko? ya Ζarfin jikin naki de?” alokaci Ιaya Inna tajero mata duka waΖ΄an nan tambayoyin..
“Eh Inna na tashi, ko zan samu ruwan zafi inaso nayi wanka ne, gaba Ιaya banajin daΙin jikina, gashi ina so naje gidan su Husnah” tafaΙi maganar tana me Ιan rumtse idanun ta, saboda wani juwa da taji yana ΖoΖarin Ιibanta..
“Kinkuwa ci sa’a yanzu na Ιaura ruwan abincin rana, gashi can inaga yama tafasa saiki Ιiba, amma idan kin Ιiba ki Ζaramin ruwa acikin tukunyar” Inna tafaΙi haka tana meyi mata nuni da tukunyar abincin dake Ιaure kan murhu…
Sosai taji daΙin jikinta sakamakon wanka da ruwan zafi da tayi, bayan ta idar da Sallan Azahar ne, tayi mawa kanta mazauni akan katifarta haΙe da Ιaukan jakar kayan kwalliyanta, mai kawai tashafa sai kwalli da ta zizara a cikin idanunta, ko powder bata shafa ba…
Doguwar rigar atamfa irin me sauΖin kuΙin nan tasanya ajikinta, haΙih da Ιaura hijab akan kayan nata mai kalar blue, yakumayi shige da atamfarta saboda shima atamfar kalan blue ne dashi (shuΙi). Me kyau de me kyaune ko a yaya kuwa, duk da batayi kwalliya ba kuma fuskarta a kumbure take saboda kuka, amma hakan bai hana kyawun fuskarta bayyana ba….
STORY CONTINUES BELOW
Kallon Inna dake ΖoΖarin sauΖe tukunyar abinci Zahrah tayi, tana me gyara zaman lufayar jikinta tace.
“Inna ni zan je gidansu Husnah, zuwa yamma zandawo insha Allah”
“Wani irin maganar zuwa gidansu Husnah kuma Zahrah? inace Ιazu Ιazun nan muka dawo dake daga asibiti, har kin yi sauΖin da zaki soma fita yawo?”
(Su Inna anfara soyayya da Zahrah fans, lol)
“Kada ki damu Inna yazama dole ne naje, amma bazan jima ba zandawo, dan Allah kada ki hanani zuwa Inna!” Zahrah ta faΙi haka cikin yanayi na nuna zaΖuwa.
“Shikenan tunda kin matsa, ai de kya tsaya kici abinci, idan yaso saiki tafi”
“A’a Inna banajin yunwa yanzu, idan nadawo zanci” takai Ζarshen zancen nata tana me nufar hanyar fita daga cikin gidan. Da kallo kawai Inna tabita harta fice daga gidan…
Tsayawa tayi tana kallonsa cike da mamaki, yayinda shima kallon nata yake cikin yanayi na mamaki…
Giransa Ιaya ya Ιage haΙe dayin murmushi…. “Ashe ma kinyi sauΖi, dana sani da ban bar aikin da nakeyi nazo duba kiba ae” Dr.Sadeeq yafaΙi haka yana me takowa zuwa wajen da take tsaye.
Kunyarsa ne taji yakamata, sakamakon abun da yafaru Ιazu a tsakaninsu, wato rungumarsa da tayi, wanda tasan hakan ba abu bane me kyau haramunne, mace ko namiji su taΙa mutumin da ba muharrami’n su ba, duk da cewa ba’acikin hayyacin ta ta rungumeshi ba, amma tabbas hakan bai dace ba…
“Yade naga kina wani sunkuyar dakai kamar amaryar da aka kaita Ιakin mijinta” Dr.Sadeeq Ζ΄afaΙi haka cike da zolaya.
Sai alokacin ta’iya Ιago kanta ta aika masa da
hararan wasa,,,,, ” Yaushe kazo? kuma me yasa ka tsaya anan baka shiga cikin gida ba?”
“Ummm banjima da zuwa ba, dama inaso amin sallama dake ne, kinga bai dace ace koda yaushe ina shiga cikin gidanku kai tsaye ba, amma sai kuma naga kamar keΙin sauri kike zaki unguwa ko?”
YaΖare maganar yana me leΖa fuskarta wanda ta sunkuyar da ita Ζasa.
Wasa da yatsun hanunta tashiga yi, haΙe da sanya haΖorinta na sama taΙan datse leΙenta na Ζasa..
“Yajikin naki?” yatambayeta don yaga bata daniyar basa amsan abun da yatambaya.
“DasauΖi, dama ni lafiyata Ζalau” tabasa amsa a ta Ζaice..
“Eh hakane kuma dama kinsan wani lokacin, idan lafiya tayi mawa mutum yawa, takan iya sawa ya kwanta a gadon asibiti”
Saurin kallonsa tayi sakamakon jin abun da yace, “Lafiyan?” ta tambaya cike da mamaki.
“Eh itafa lafiyan, to baga example akan ki ba” yanayin yanda yayi maganar kaΙai ya’isa ya tabbatar maka cewa zolaya ne kawai ke damunsa..
“Hmm” kawai Zahrah tace haΙi da Ιan satan kallonsa, aikuwa karab suka haΙa idanu, saurin Ιauke nata idon tayi.
Hmm yalura sarai kunyarsa takeji, kuma shiΙin ma kusan hakanne, kawai de dauriya dakuma shariya yafita, shiyasa ya share abun, amma shikansa yasan cewa ya aikata ba dai dai ba, saboda da ta rungumesa baikamata ace yabiye mata ba, kamata yayi ace ya ΙanΙareta daga jikinsa, sai de kuma babu yanda ya’iya saboda alokacin tana cikin halin buΖatar taimako, kum san nan shi be rungumeta don yaji daΙi ba.
“Inazakije ne haka, da rana tsaka?” yajefo mata tambaya…..
“Gidan su Husnah zani” ta basa amsa a taΖaice, saboda ba da kowani lokaci tacika son dogon magana ba…
“Shikenan muje saina kaiki, domin kinsan samun abun hawa zaimiki wahala, saboda rana tayi sosai”
Kallonsa tayi naΙan sakanni, kafun ta rausayar da kanta gefe cikin yanayi na shagwaΙa tace “Dama kabarni, koda Ζafana ai zan iya zuwa, idan har bansamu abun hawa ba, balle ma nasan zan samu”
STORY CONTINUES BELOW
“Da gaske zaki iya takawa da Ζafa daga nan har gidansu Husnah? to shikenan tunda zaki iya, zaimafi kyau ki taka da Ζafan, saboda kisamu ki Ιan rage wan nan Ζiban dakika haΙa, gaba Ιaya duk yasa kin yi muni, kin zama wata super mama dake” yafaΙi haka yana me Ζare mata kallo.
Waro idanu Zahrah tayi haΙi da soma kallon kanta, wai tayi Ζiba, takuma zama super mama.
Take idanunta suka yi raurau dasu, yayinda ruwan hawaye ya soma cika cikin su, “ashe da gaske tayi Ζiba bata sani ba? gashi harya fara goranta mata, to me yasa ita bataganin Ζibanta?” tatambayi kanta…
Dariya Dr.Sadeeq yasanya domin kuwa yalura tayarda da maganarsa, shikuwa wasa yake mata, bawai dagaske tayi Ζiban bane, gashi har tana ΖoΖarin yin kuka, shikam ya lura gaba Ιaya kuka baya bata wahalar yi, hawayenta a maΖale suke, mintuna kaΙan saikaga sun tsiyayo”
“Kintsorata ne dan nace kinyi Ζiba? hmmm nan gaba kaΙan zakiyi bindiga ki fashe saboda tsabar Ζiba”
Sake waro manya manyan idanunta tayi zuwa yanzu kam har Ζwallan cikin idanunta sun gangaro akan fuskarta….
“Au kinfiso ki kumbura ki fashe Ιin kenan?” yatambayeta yana me danne dariyar da ta taso masa…
Kai ta girgiza masa alaman “A’a”
“To kinaso na faΙamiki me zakiyi wanda zaisa bazaki fashe ba?”
Dasauri ta ΖaΙa kai alamar tanaso yafaΙa mata…
“Yauwa Ζ΄ar gari ashe de kema bakyaso ki fashe, to abu Ιaya zakiyi wanda shizai hanaki fashewa, kinga de ni likita ne ko? nakumayi zurfi cikin karatun likitanci, saboda tsabar zurfin da nayi ina karatune ma yasanya nagano cewa idan mutum yacika matsantawa kansa da damuwa da kuma yawan koke koke to yakan iya kumbura kamar de yanda kikayi yanzu, daga nan kuma bayan kamar 1 week shikenan sai dai yayi bindiga yafashe fush, shikenan kuma sai de wani bashi ba, kinaso haka ta faru dake?” yafaΙi haka yana me zura mata manya manyan idanunsa.
“A’a” tabashi amsa cikin murya me sanyi, domin kuwa a haΖiΖanin gaskiya ta yarda da kalamansa, ko kaΙan bata gano cewa shiya shirya abunsa ba. take fargaba ya Ιarsu a zuciyarta….
Wata irin dariyane takama Dr.Sadeeq amma kuma ba halin yasaki dariyar tasa, dolensa ya danne ta matuΖar yanaso Zahrah ta gamsu da bayanan sa hundred percent,,, lallai yau yaΖara tabbatarwa kansa cewa Zahrah yarinyace kuma yarinta na damunta, amma inbanda haka ta’ina ta taΙa jin ance mutum ya yayi bindiga yakuma fashe da ransa.
Gyara tsayuwarsa yayi haΙe da cewa “To yanzu de zaΙi ya rage gareki Yarinya, ko ki daina kuka ko kuma ki fashe, saboda haka zaki biyoni muje ne ko kuwa a’a nayi tafiyata?”
“Zanbika” tafaΙa cikin muryar tsoro saboda gaba Ιaya kalaman likita sun rikitata…
Murmushin gefen baki Dr.Sadeeq yayi haΙe da juyawa yanufi wajen motarsa, yana me danne dariyarsa…
Zahrah kuwa tamkar wacce Ζwai yafashewa haka ta bi bayansa.
Saida suka hau titi kafun yajuyo da kallonsa gareta, gani yayi tayi jigum da’ita, da’alama tunani takeyi….
“Amma nace miki yawan sakai a damuwa shike sa mutum ya fashe ko? hala don ba Ιangaren likitanci kike karanta ba shiyasa bakisan da hakan ba”
Kallonsa tayi haΙe da ΖwaΙe fuska, cikin murya me sanyi tace “Ni ae yanzu bawai a damuwa nake ba, kawai de ina kallon hanya ne” ….
Kansa ya jinjina haΙe da cewa tayi masa kwatancen gidansu Husnah’n domin shi basani yayi ba….
A dai dai Ζofar gidan su Husnah ya tsaida motar tasa, haΙe da dawo da kallonsa ga Zahrah wacce ke ΖoΖarin buΙe murfin motar tayi ficewarta…
“Da yaushe zaki koma gida?”
STORY CONTINUES BELOW
Ζan jim tayi kana tace “Ko zuwa bayan la’asar ma, irin Ζarfe biyar Ιin nan haka” yanayin yanda taΖai Ζarshen zancen nata tana me juya kyawawan idanunta, shi ya shagaltar dashi har ya tsaida idanunsa akan ta, sosai takeyi masa kyau idan tana juya idanunta, ya kuma lura cewa hakan al’adarta ne, idan hartana magana, to takan juya idanunta masu kyawun gani, musamman idan maganar tazo Ζarshe..
“Ya de?” Zahrah ta tambayeshi sakamakon ganin da tayi yakafeta da idanunsa..
“Babu, kikulamin da kanki kinji, zan zo na Ιaukeki idan 5 Ιin tayi, inafata babu wata matsala?” yatambayeta cike da nuna kulawa.
Murmushinta me kyau tayi masa haΙe da cewa
“Babu wata matsala”
Yana kallonta tabuΙe Ζaramar Ζofar dake jikin gate Ιin gidan su Husnah tashige… Yana tabbatar da shigewarta yayiwa motarsa key haΙe dayin reverse yaΙauki hanyar asibitinsu, saboda dama aiki yabaro yazo gareta, to yazaiyi tunda tazama wani Ιangare na jikinsa…
Da matuΖar farinciki Husnah ta rungume Zahrah tana mejin daΙin ziyarar bazata da Zahrah’n takawo mata, saboda bata faΙa mata zata zoba. Bayan Zahrah ta gaisa da Momyn Husnah ne, suka rankaya zuwa Ιakin Husna’n,,, ba Ιata lokaci Husnah ta cikawa Zahrah gabanta da kayan ciye ciye dasu drinks.
“Naji daΙin zuwanki sosai Ζawata, kamar kuwa kinsan ina kewarki, jiyafa har mafarkin ki nayi, da safe naΖira wayarki kuma najita switch off, ina fata dai kina lafiya?”
Hijabin dake jikinta ta cire haΙe da cewa “Lafiya amma ba sosai ba”
Da sauri Husnah ta dawo da kallonta ga Zahrah
“Meyafaru dear?” Husnah tatambaya cike da kulawa.
Kallon Husnah Zahrah tayi na tsawon minti guda….
“BabuΖatar tuna abun da yafaru Husnah, saboda kinsan inada raunin zuciya, tuna abun zai iya sake jefani cikin wani hali”
Damuwane ya bayyana Ζarara akan fuskar Husnah haΖiΖa tamkar Ζ΄ar uwa ta jini take kallon Zahrah saboda haka duk wata damuwa ta Zahrah damuwar tace itama.
“Zaki iya Ιoyewa kowa damuwarki amma bandani Zahrah, sai de kuma babu amfanin takuraki akan cewa lallai sai kin sanar dani, saboda bansan wani hali zaki samu kanki aciki ba bayan kin faΙamin”
Dafa kaΙan Husnah Zahrah tayi haΙi da daure zuciyarta…
“Nasake haΙuwa da…. da….wanda ya yimin fya…….” kasa Ζarasawa tayi saikawai tafashe da kuka.
Ko bata Ζarasaba Husnah tafahimci me Zahrah take nufi.
Cike da tashin hankali Husnah tasoma salati…
Sake jawo Zahrah jikinta tayi haΙi da rungumeta….”Ki daina kuka, yanzu ba lokacin kuka bane Zahrah, kinmaci abinci kuwa ?” Husnah ta tambayi Zahrah cikin kulawa…
“Banajin yunwa Husnah!” Zahrah tafaΙi haka cikin shaΖewar murya, wani yunwa zataji ita da take cikin bala’in sake ganin Zaid…
“Kinsan de ba kyau zama da yunwa ko, kinga yau ni namayi abincin dakaina, bana zuba mana muci tare, kuma dan Allah kada kicemin a’a”
Babu yanda Zahrah ta’iya dole tabiyewa Husnah taci abinci, gaba Ιaya Husnah se zuba take tamkar kurna, takasa yin shiru koda na minti biyu ne, tayi hakanne kuma saboda ta gusarwa da Zahrah da muwarta, daga Ζarshe de har game, Husnah ta jona musu a tv suka buga, sosai kuma hakan ya Ιebewa Zahrah kewa….
Tare sukayi sallan la’asar daga nan kuma Husnah ta Ιebi Zahrah, suka tafi shoprite, dangin su ice cream da chocolate suka jida, daga nan sukayo gida.
Kamar yanda yafaΙa Ζarfe biyar da minti Ιaya dai dai ya Ζaraso Ζofar gidansu Husnah.. Ζiran Zahrah yayi a waya ya tabbatar mata cewa yana Ζofar gidan su Husnah….
STORY CONTINUES BELOW
Zahrah na ajiye wayarta Husnah ta kalleta haΙe da kashe mata ido Ιaya.
“Ζawata tazama Ζ΄ar soyayya, sosai yanayin soyayyarku da Man Ιin nan yake kasheni, kinfasan gayen naki ya haΙu over, da badan ke bace danayi snatching Ιin sa!” cike da zolaya Husnah ta faΙi maganar…
Dariya suka sanya su dukansu, haΙe da rungume juna.
Har bakin motar Dr.Sadeeq Husnah ta raka Zahrah, bayan Momyn Husnah ta cikawa Zahrah leda da dangin su turare dakuma kayan shafa hadda kyautar wani haΙaΙΙen leshi, sosai Zahrah tayi godia, hakan kuma yana Ιaya daga cikin abubuwan daya sanya bata son zuwa gidansu Husnah, saboda idan dai tazo tofa sai mahaifiyar Husnah tayi Ιawainiya da’ita wajen bata kyautan kayayyaki masu kyau da tsada…
Harsaida Husnah taga tashin motar su Zahrah kafun takoma cikin gida…
“Kinsamo abun daΙi shine kokimin tayi ko?” Dr.Sadeeq yafaΙi haka ga Zahrah wacce ta Ιaura ledan sayayyar da sukayi a shoprite ita da Husnah akan cinyarta…
“Murmushi me sauti tayi haΙe da cewa “Ba’abun daΙi bane, kayan shafa ne”
“Um um ni banyarda ba, kitaimaka kiban ko chocolate Ιaya ne, naci yunwa nakeji, yau duk banci abinci ba” yaΖare maganar yana me shagwaΙe fuska, sai kace wani Ζaramin yaro…
Dariya Zahrah tayi haΙe da satar kallonsa “wai ma ya’akayi yasan cewa acikin ledar hanunta akwai chocolate?” ta tambayi kanta.
“Kina mamakin ya’akayi nasan cewa a ledarki akwai chocolate ko?, ai ba abun mamaki bane, tunda nasan shiΙin favorite Ιin ki ne” yafaΙi haka cikin yanayin shauΖi, amma still idanunsa naga titi..
BuΙe ledar tayi taciro wani chocolate mai kyau da daΙi kusan yafi kowanne ma daΙi acikin sauran chocolate Ιin da ta saya, ta miΖa masa haΙi da cewa “Ga wan nan amma bazan iya baka kyautarsa duka ba, saboda haka kaci rabi kabarmin rabi”
Saurin kallonta yayi fuskar sa Ιauke da murmushi… ” NaΖi wayon, idan har kinaso na karΙa saide kibani kyautansa duka”
Turo Ιan Ζaramin bakinta tayi gaba, haΙe da noΖe kai alamar hakan bazai yiwuba, kallon bakin nata yayi, harsai da yaji tsikar jikinsa Ζ΄a zuba, hmmm lallai idan ya auri Zahrah, zai tsotse wan nan Ιan Ζaramin bakin nata ne yanda ya kamata?…
“Kici chocolate Ιinki ke kaΙai nikam na gode” yafaΙi haka a taΖaice domin dama wasa yake mata baci zaiyi ba, shi da yake fama da ciwon ciki idan yaci chocolate kuma yake nan?
Lokacin da suka iso gida biyar da rabi har ta gota… kallon Zahrah Dr.Sadeeq yayi haΙe da Ιan nisawa.
“Nagama haΙa miki kayan lefe da kuma sauran abun da suka dace, wace rana kikeso a kawo?”
Saurin Ιaga idanu tayi ta kallesa jin abun da yace.
Idanunsa Ιaya ya kashe mata, wanda yasanya taji gabanta yafaΙi, saboda a wajen mutum Ιaya ta saba ganin irin wan nan kashe idon, kuma shi hakan yazame masa al’adarsa ne, bakowa bane kuma face ZAID.
“Zamuyi waya” Zahrah tafaΙi haka don son kawar da tambayar tasa, saboda a yanzu bata da amsar da zata basa..
Ajiyar zuciya ya sauΖe haΙe da dafa steering motar da duka hannayensa biyu. “Shikenan idan kin nutsu zan Ζiraki” yafaΙi haka cikin sanyin murya..
Murmushi tayi masa irin me tsayawa a rai Ιin nan, kana tabuΙe murfin motar tayi ficewarta, sai de batare da yasani ba, ta aje masa wan nan chocolate Ιin…
Bayan kamar 2 minute da shiganta cikin gida yaja motarsa shima yayi tafiyarsa…
*ZAID*
Tunda yasha wan nan Ζwayoyin baisan inda kansa yake ba harsai Ζarfe uku na yammaci,, ko da ya buΙe idanunsa ji yayi duniyar na juya masa, amma haka adaddafe ya shiga bathroom yayi wanka haΙe da Ιauro alwala, sai yanzu zaiyi sallan Azahar don tsabar asara, gashi har la’asar ma takawo kai….
Yana idar da sallan azahar ya miΖe daga kan sallaya haΙe da zura slipper Ιinsa yafice daga Ιakin… Kai tsaye masallacin jikin gidansu yanufa don gudanar da sallan la’asar wanda ake Ζira yanzu.. Ko a cikin masallacin mutane sai mamakin ganinsa suke saboda abune mawuyaci ka gansa a masallacin da wan nan time Ιin, yafi yawan zuwa sallan isha ko asuba, amma banda azahar da la’asar saboda a wan nan lokacin ma kwata kwata baya gida, sai de yayi sallah a wani wajen. Baidamu da kallon da mutane suke masa ba, yana idar da sallan sa yatashi yayi shigewarsa cikin gida…
Tsab yagama shirya kansa cikin Ζananan kaya, riga da wando na blue jeans wanda suka matuΖar amsar jikinsa. Ba abun da yake sai tashin Ζamshi.
Zama yayi abakin gadonsa haΙe da sanya hanunsa duka biyu ya dafe kansa dake yi masa ciwo kaΙan kaΙan,, wani irin sabon al’amari yakeji a cikin zuciyarsa, baisan da wani suna ze Ζira abun ba, amma tabbas jiyake zuciyarsa na azalzalarsa akan Zahrah, san nan yanajin cewa itace muradinsa, saurin buΙe idanunsa da ke lumshe yayi sakamakon hasko masa marukan da Zahrah ta sharara masa akan fuskarsa da sukayi, hanunsa yakai kan Ζuncinsa ya shafa haΙe da sakin murmushi, tunda yake a a rayuwarsa wata mace banda mahaifiyarsa bata taΙa kai hanunta jikinsa da sunan duka ba ballan tana har akai ga mari, sai gashi yau, Zahrah ta shararamasa lafiyayyun maruka harguda biyu akan fuskarsa, takuma haΙa masa hadda duka, amma ko kaΙan baiji zafin abun ba, anya kuwa shine? kodai an musanyashine bai sani ba? meke damun ΖwaΖwalwa da zuciyarsa ne? shine Zaid kuwa? Yajerowa kansa waΖ΄an nan tambayoyin….
Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 7 BY FATYMA SARDAUNA"