Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 11 BY FATYMA SARDAUNA

SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 11 BY FATYMA SARDAUNA

                     Www.bankinhausanovels.com.ng 

Tsayawa yayi yana me Ζ™arewa gate Ι—in kallo, idan da zaibi son zuciyarsa ne, to tabbas da shiga cikin gidan zaiyi, amma kuma saidai wata zuciyar tana gargaΙ—insa da kar ya shiga cikin gidan, bawai kuma don yanajin tsoro ba, kawai dai yana me tausayawa kansa ne, yasan idan yaga Zahrah dole sai ciwonsa yasake motsawa, duk da yanzun ma bawai ciwon nasa ya kwanta bane, komawa yayi cikin motarsa yazauna, haΙ—e da Kifa kansa akan steering motar, lumshe idanunsa yayi sai kawai ga hawaye suna fitowa daga cikin idanun nasa, wai yau shi Zaid ke kuka akan mace, lallai rayuwa

juyawa take, gashi shikam tajuyo masa da saΙ“anin tunaninsa… Ƙarar motar dayaji shi yasanya sa Ι—ago kansa yakai kallonsa wajen gate Ι—in gidan, ko ba a faΙ—a masa ba yasan motar RIVAL ce (wai Dr.Sadeeq ne rival Ι—in nasa) balle ma kuma yagansa acikin motar, wani irin abune yazo ya tokarewa Zaid maΖ™oshinsa, baΖ™inciki, haushi, takaici, da kuma tsanar doctor ne duk suka haΙ—e masa waje guda. Ji yake kamar yafita acikin motar yaje ya shaΖ™o sa kozaiji salama acikin ransa.. Har motar doctor tashige cikin gidan bai Ι—auke idanunsa akan gate Ι—in ba, da sauri ya rumtse idanunsa lokacin da motar tagama shigewa cikin gidan aka kullo gate Ι—in gidan, da Ζ™arfi ya danne lips Ι—insa haΙ—e da buga steering motar, yanaji yana gani wani zai yi masa rayuwa da Zahrah’nsa. “Yanzu Allah ne kaΙ—ai yasan shigarsa mezaiyi mata, wata Ζ™ilama rungumeta zaiyi, wataΖ™ila kuma har kiss zaice zaiyi mata” wata zuciyar tafaΙ—a masa haka. Da Ζ™arfi ya shiga dukan steering motar, yana me jijjiga kansa, Ζ™waΖ™walwarsa bazata iya Ι—aukar masa wannan tashin hankalin ba, jiyake komai na duniyan nan najuya masa, Allah yasa abun da zuciyarsa ta faΙ—a masa bahakanne zai kasance ba, bazai taΙ“a iya jurewa ba, hanunsa ya Ι—aura adaidai saitin zuciyarsa haΙ—e da sake rumtse idanunsa, zafi yakeji haΙ—e da zogi acikin Ζ™irjinsa, da Ζ™yar ya’iya tada motar ya cillata kan titi a zafafe, gudu sosai yakeyi akan titi babu ruwansa da waΖ΄anda suke gabansa ko suke bayansa, idanunsa sun rufe sosai.. Ikon Allah ne kawai yakawoshi gida, amaimakon yawuce Ι“angarensa sai ya wuce Ι“angaren mom Ι—insa..1

Hajiya Safara’u ce tsaye agaban dinning table tana shirya abinci, batare da sanin shigowarsa ba saiji tayi anrungumeta ta baya, Ζ™amshinsa kaΙ—ai taji tagane cewa tilon Ι—anta ne, mamakine tsantsa ya bayyana akan fuskarta yaushe rabon Zaid yazo ya rungumeta haka? kansa ya Ι—aura akan wuyanta haΙ—e da sauΖ™e ajiyar zuciya, wani abu me Ι—umi da taji yana sauΖ™a akan wuyanta ne yasanya tayi saurin juyowa garesa, batayi mamakin ganinsa ahaka ba amma Ζ™warai tayi mamakin ganin yanda hawaye ke zuba daga cikin idanunsa.

STORY CONTINUES BELOW

“Zaid!!”

taΖ™ira sunansa cike da tsananin mamaki haΙ—e da tashin hankali.

Jajayen idanunsa ya Ι—ago ya kalleta haΙ—e da sake rungumeta.

“Mom nakasa jurewa, bazan iyaba, please ki ciremin soyayyarta acikin zuciyata, koda zan samu nutsuwa na minti Ι—aya acikin ruhi na!” cikin matsanancin rauni yake maganar gaba Ι—aya yazama abun tausayi yadawo saikace yaro Ζ™arami..

Ahankali Mom take shafa bayansa haΙ—e da jinjina kanta, tabbas da ace akwai yanda zatayi da ta cirewa Zaid soyayyar Zahrah acikin zuciyarsa, bazata iya jure ganin hawaye da kuma damuwar Ι—anta ba.

Kamasa tayi suka zauna akan kujera, kansa yaΙ—aura akan cinyarta yayinda ita kuma take shafa tarin sumar dake kansa .

“Nakanji ciwo acikin zuciyata idan naganka kana kuka Zaid, bansan wani irin soyayya kakeyiwa Zahrah ba, amma kuma bamu da yanda zamuyi Zahrah matar wani ce yanzu” Mom tafaΙ—i haka cike da lallashi.

“Mom ki taimakeni, zafi nakeji acikin zuciyata, yanzu kenan bazan sameta ba? shikenan har abada saidai naΖ™are rayuwata a haka babu ita? bazai yiwuba Mom, dana sani tun farko daban yaudareta ba, dana sani tun farko dana aureta, duk nine najawa kaina ni da kaina na haramtawa kaina ita, nasan dabanyi mata fyaΙ—e ba dayanzu na sameta, nine fa nayi mata fyaΙ—e mom, meyasa nayi haka mom? kaicona yau nayi danasanin yi mata fyaΙ—e da nayi fiye da ko yaushe!” yafaΙ—i haka yana me sake fashewa da kuka kamar yaro..

Mamaki haΙ—i da ruΙ—ani dakuma tsantsar kaΙ—uwa su suka bayyana akan fuskar Mom, kallonsa kawai takeyi zuciyarta na tafarfasa.1

“Kana da hankali kuwa Zaid? FyaΙ—e fa kace, anya kuwa Ζ™waΖ™walwarka bata fara taΙ“uwa ba?”

Sai yanzu yatashi daga kan cinyarta, bayi da wani zaΙ“i wanda ya wuce yafaΙ—awa Mom Ι—insa gaskiya…

“Ban haukace ba Mom, dagaske ne nine nayi mata fΖ΄aΙ—e, nine nan na tozarta rayuwarta, nine nan na fara gurΙ“ata mata rayuwa, na rabata da farincikinta da duk wani jin daΙ—inta, narufe idanuna naketa mata haddinta alokacin da take tsananin buΖ™atar taimakona, nayi mata fyaΙ—e mom nabiye son zuciyata nasan ban kyauta mata ba amma kuma babu yanda zanyi ne yazama dole……”2

Tassssss haka mom ta Ι—aukesa da wani irin lafiyayyen mari, marin daya matuΖ™ar firgitasa ya Ι—aiΙ—aita tunaninsa, tundayake yataso yayi wayo mahaifiyarsa bata taΙ“a sanya hanu ta mareshi ba sai yau, kai koda tsawa me Ζ™arfi bata taΙ“a yi masa ba, bakinsa ya hangame haΙ—e da sanya hanunsa akan Ζ™uncinsa inda ta maresa yana kallonta.

Itakanta mamakin marin datayi masa take, sai dai kuma ranta amatuΖ™ar Ι“ace yake..

“Kayi mata FyaΙ—e? kacuceni Zaid, bantaΙ“a tunanin zaka iya aikata wannan rashin imanin ga wata Ζ΄a mace ba arayuwa, meyasa? meyasa? idan aure kakeso meyasa bakayiba? kahalakar da rayuwar Ζ΄ar mutane, kaicon wannan gurΙ“ataccen halin naka, tabbas yanzu na yarda alhaki ne kawai ke bibiyarka, idan kuwa hakane to wallahi baka ga komai ba arayuwarka, niba azzaluma bace kuma bana zama inuwa Ι—aya da mutum meyin zalunci, bansan zuciyarka tayi tauri harhaka ba, dahar kake tunanin aurenta, nayi danasanin tura mahaifinka nemamaka aurenta, ashe kai macucine agareta azzalumi, taya kake tunanin zata amince dakai?” kanta tashiga girgizawa haΙ—e da juyawa ta nufi matattakalan dake cikin falon ranta amatuΖ™ar Ι“ace, sam batasan abun da Zaid ya aikata ga Zahrah ba sai yanzu, lallai da ita da kanta zata Ι—aukawa Zahrah mataki.1

Zaid kuwa har Mom tagama haura step Ι—in dake cikin falon, bai Ι—auke idanunsa akanta ba, mamakine ya lulluΙ“esa matuΖ™a, sake shafa kumatunsa yayi inda mom Ι—in ta zabga masa mari, baitaΙ“a ganin Ι“acin ran mahaifiyarsa irin nayau ba tun dayake. MiΖ™ewa yayi yawuce Ι“angarensa shi dai idan za amaresa sau million a basa Zahrah to bazai taΙ“a damuwa ba..

6

STORY CONTINUES BELOW

Mom kuwa tana shiga Ι—aki wayar Dad taΖ™ira tasanar masa komai, Ι“acin ran da Mom tashiga kaΙ—anne akan wanda Dad ya tsinci kansa aciki, lallai Zaid yamaidashi mutumin banza, dayasan haka tafaru tsakaninsa da Zahrah da baije ne ma masa aurenta wajen Baffanta ba, wannan ma ai rashin ta ido ne, amma zaiyi maganinsa ne, jibi jibin nan zai Ι—aura masa aure kuma dolensa ne yazauna da matar, hukuncin da Dad ya yankewa Zaid kenan.4

*****

Tun jiya suka koma makaranta amma bata samu daman zuwa ba, doctor da kansa yace ta bari sai yau… BuΙ—e Ζ™ofar Ι—akin tayi ta fito, dagani sauri take, ta shirya tsab cikin riga da zani na atamfa ta rufa jikinta da wani Ζ™aton mayafi me Ι—an kauri..

Kallonta yakeyi sosai, take yaji wani irin kishinta ya lulluΙ“emai zuciya, duk da ba wani kwalliya tayi sosai ba, amma shikam baijin zai barta tafita ahaka, kishi yake wani ya ganemai fuskar mata, ganin yanda yake kallonta ne yasanya taΙ—an shagwaΙ“e fuska haΙ—e da karyar da wuyanta gefe, don daganin yanda yake kallonta tasan akwai magana abakinsa.2

“Banjin zan barki kifita a haka, maza je ki Ι—auko hijab kisanya” yafaΙ—i haka cikin dakiya da’alama babu wasa a lamarin nasa. Bata musa masa ba ta koma Ι—aki, hijab ta Ι—auka ta sanya wanda ya tsaya iyaka guiwarta, tana fitowa yasake kafeta da idanu, har yanzun ma dai baijin zai iya barinta tafita ahaka, gaba Ι—aya ma shi kullum gani yake tana Ζ™ara yi masa kyau, nana gaba kaΙ—an zai hanata fita ne ma kwata kwata.

“Dan Allah yanzu kam kabarni natafi kaga fa zanyi latti!” tafaΙ—i haka cikin shagwaΙ“a.

Marairaice fuska yayi haΙ—e da sanya hanu yashafi sajen dake kwance akan Ζ™uncinsa, ba tare dayace komai ba yamiΖ™e tsaye yanufi hanyar fita daga cikin falon, ganin haka yasa itama ta rufa masa baya da sauri…

Tafiya suke amma yaΖ™i cewa da ita komai, kallon yanda ya haΙ—e fuska tayi, sai kawai tasaki dariya, wai ahakan shi fushi yakeyi da ita, sam yanayin fushi bayayi masa kyau akan fuskarsa.

“Meyasa bazaka kulani bane wai? idan makarantar ne bakaso sai ka maidani gida, amma kadaina fushi bakayin kyau kwata kwata idan kana fushi” tafaΙ—i haka tanaΙ—an dariya.3

Sai alokacin ya juyo da kansa ya kalleta. “Ni ba fushi nake ba” yafaΙ—i haka cikin cushewar murya.

Murmushi kawai tayi batare da ta sake ce dashi komai ba, saima kwantar da kanta da tayi ajikin kujeran motar tana kallon yanda mutane suke ta hada hadan su.

A dai dai inda yake ajiyeta lokutan baya yauma anan yayi parking motar tasa, buΙ—e murfin motar tayi zata fita, da sauri ya riΖ™o hanunta, juyowa garesa tayi tana Ι—an murmushi, shima murmushin yayi mata haΙ—e da matsowa daf da ita, kiss ya manna mata akan kumatunta haΙ—e da cewa

“Ki kulamin da kanki”

Tsadadden murmushinta tayi masa haΙ—e da jinjina kanta alamar zata yi yanda yace. Sai da yaga shiganta cikin hall Ι—in da zasuyi lecture kafun ya ja motarsa yabar haraban makaranta baki Ι—aya..

Tana shiga cikin hall Ι—in suka Ι—inke ita da Husnah sukaita hira, kafun lecturer yashigo….

Ƙarfe biyar na yamma suka kammala duk wani lecture Ι—in da suke dashi, har bakin motar doctor Ι—in Husnah ta rako ta..

ƘoΖ™arin janta da hira yake amma tayi masa shiru, saboda gaba Ι—aya agajiye take, dolensa shima ya Ζ™yaleta harsuka isa gida.

Da ruwan Ι—umi tayi wanka, tana fitowa ta zura wata riga doguwa marar nauyi ajikinta, haΙ—e da faΙ—awa kan gado, numfashi kawai take sauΖ™ewa na gajiya, mintuna kaΙ—an bacci Ι“arawo ya saceta, koda Dr.Sadeeq ya shigo yasamu tana bacci baiyi yunΖ™urin tashinta, falo yakoma yayi zamansa….

*****

Bayan kwana uku.

Yau kusan kwanansa uku kenan a guest house Ι—insa yake kwana, gaba Ι—aya abubuwan duniyane suka haΙ—u sukayi masa yawa, bayacin abinci a iya tsawon kwanakin nan, gashi ciwonsa ya dawo sosai, daga zaran yayi tari sai jini, magungunan nasa ma yadaina sha, addu’a yake Allah yasa wannan ciwon nasa yazamo ajalinsa ko zai samu sauΖ™in raΙ—aΙ—in dayakeji acikin zuciyarsa…2

STORY CONTINUES BELOW

Horn Ι—in motarsa yake dannawa a Ζ™ofar gidannasu kamar zai tashi sama, da sauri me gadi ya wangale masa gate Ι—in gidan ya tura hancin motarsa ciki, ko kyakkyawan parking baiyi ba, haka yafito daga cikin motar yanufi Ι“angarensa, yana shiga falonsa yasoma Ζ™oΖ™arin cire rigar jikinsa, dai dai lokacin wata Ζ΄ar mata shiyar budurwa ta buΙ—e Ζ™ofar Ι—akin dake kusa da bedroom Ι—insa ta fito, tsananin mamakine yakashe Zaid, kallon tuhuma kawai yake aika mata dashi.

Yanda ta gansa sai da taji gabanta ya faΙ—i amma dayake dama tayi masa farin sani yasanya taΙ—an wayance haΙ—e da sakar masa murmushi..

Kallonta yakeyi daga samanta har Ζ™asanta, “wace Ζ΄ar iska ce haka da har tasamu daman shigo masa Ι“angarensa har da kuma kutsawa cikin Ι—aki?” tambayar da yayiwa kansa kenan.1

“Wacece ke? Uban waya baki daman shigomin Ι—aki?” ya tambayeta murya a kausashe.

Sai da taji tsoro amma kuma hakan bai hanata bayyana murmushi akan fuskarta ba. Wani Ζ™ululun takaici da baΖ™incikine suka cika zuciyar sa, badon komai ba sai don murmushin dayaga tanayi masa.

“Dan ubanki bamagana nake miki ba!” ya kuma faΙ—a cikin tunzura.

Yanzu kam ta tsorata dashi sosai da sauri ta juya zata koma cikin Ι—akin, taku Ι—aya yayi ya fincikota, yana juyo da ita ya bata kyakkyawan mari akan fuskarta wanda ya sanyata fasa wata uwar Ζ™ara, sosai zafin marin ya ratsata..

“Bazaki faΙ—amin mikikeyi a cikin Ι—akin nan bako dan ubanki, inaga sainaci uwarki tukun zakimin bayani, banza me kama da fara!!” yafaΙ—i haka yana me Ζ™oΖ™arin zare belt Ι—in dake jikin wandonsa, da’alama dai so yake ya jibgeta.4

“Kada ka kuskura ka taΙ“a ta inagaya maka idan bahaka ba ranka zaiyi mummunan Ι“aci!”

Muryar Dad da shigowarsa kenan yakaraΙ—e gaba Ι—aya falon, aΖ™ufule Zaid yajuyo yana kallon mahaifinnasa.

“Dole ne zan daketa matuΖ™ar bata ficemin acikin Ι—aki ba, taya ma zakubar wata kucaka tashigomin Ι“angarena, dubeta fa Ζ™azama da ita, wata ballagazar mata, kunfi kowa sanin bana buΖ™atar Ζ΄ar aiki, me yasa to zaku Ι—aukarmin? kurasa ma wacce zaku kawomin amatsayin Ζ΄ar aiki sai wannan baΖ™ar yarinyar!” Zaid yafaΙ—i haka yana me nuna ta cike da Ζ™yama.4

“Ba Ζ΄ar aiki bace matarkace, kuma wallahi kada kasake kace zaka saketa nafaΙ—a ma!” Dad Ι—insa yafaΙ—i haka cikin Ι“acin rai, baijirayi me Zaid Ι—in zaice ba yasakai yafice daga cikin falon..1

Tsananin tashin hankali ne ya bayyana akan fuskar Zaid, kalaman Dad Ι—insa sunyi matuΖ™ar sanyasa cikin mamaki.

“Matata?”

tambayar da ya yiwa kansa kenan, sake kallonta yayi, tana nan tsaye sai raba idanu take kamar mayya, dagani a matuΖ™ar tsorace take..

“Da gaskene abun da Dad Ι—ina ya faΙ—a?” yayi mata tambayar babu alaman wasa akan fuskarsa.

Kanta ta jinjina masa alamar “Eh”1

Wannan wani irin cin fuskane Dad Ι—insa yayi masa? aure batare da saninsa ba auren dole fa kenan? ae kuwa yau zataci ubanta ne, matsowa yashiga yi daf da ita hanunsa yasanya ya damΖ™i gashin dokin da akayi mata kitso dashi, yawun dake cikin bakinsa ya tofa mata akan fuskarta, cike da tsananin takaici ya tureta gefe, take ta Ζ™walla Ζ™ara domin kuwa kan table na glass tafaΙ—a daya tureta, baiko saurareta ba ya shige cikin bedroom Ι—insa, yanashiga cikin bedroom Ι—in ya buΙ—e cikin fridge Ι—insa ya Ι—auΖ™o kwalbar alcohol me matuΖ™ar sanyi, da Ζ™arfi ya Ι“alle murfin alcohol Ι—in yakafa kwalban abakinsa, saida yasha fiye da rabi kafun yayi wurgi da kwalban gefe, wani irin haushin kansane yakamasa, baisan da yaushe yaΙ—au kwalbar giyan yakai bakinsa ba, yanaso yadaina aikata duk wani abu dayasan Zahrah bataso amma kuma yau baida wata mafita wacce ta wuce nashan alcohol Ι—in, takaicine yasake cika masa zuciya, duk waccar shegiyar yarinyarce tasa sa shan alcohol Ι—in don haka dole itama sai ya horata, yanzu idan Zahrah tasan yasha alcohol bazata taΙ“a jin daΙ—i ba.. Ɗaukar sauran alcohol Ι—in yayi yafice zuwa falo, tananan Ζ™udundune ajikin kujera sai maΖ™yarΖ™yata takeyi, matuΖ™ar tsoron Zaid takeyi, ko yanzu dataga fitowarsa saida gabanta yafaΙ—i..3

Direct wajen da take zaune ya nufa, gashinta yakuma damΖ™owa haΙ—e da jawota zuwa tsakiyar falon, bakinta yakamo da hanunsa ya matse haΙ—e da tura mata kwalbar giyan acikin bakin nata, kuka take tana girgiza kanta amma yaΖ™i sakinta, adole wai saitasha alcohol Ι—in, cikin rashin imani irin na Zaid haka ya danne yarinyar mutane ya Ι—ura mata giya acikinta da Ζ™arfin tsiya, sai da yatabbatar ragowan giyan dake cikin kwalbar yajuyemata shi acikinta kafun ya hankaΙ—ata gefe, ganin yanda take kuka kamar ranta zaifitane, yasanyasa fashewa da dariyan mugunta, lokaci guda kuma ya tsume haΙ—e da kawar da kansa gefe, miΖ™ewa yayi yafice daga cikin Ι—akin, azuciyarsa yace “anjima kaΙ—an wanka zanmiki da ruwan Ζ™anΖ™ara dan ubanki…..

“Kuka sosai  Afra keyi, wani irin miji ne haka iyayenta suka aura mata? duk da cewa da amincewa da kuma yardanta akayi mata auren, amma sam bata tsammaci mugunta da shuΙ—ewar hankalin Zaid har yakai haka ba, tun da take arayuwarta bata taΙ“a kwatanta koda shan codine bane ballantana uwa uba giya,   iskancinta baije can ba, duk da cewa itama tana da  nata wayewar.     Wani irin amai tashiga kwarawa atsakiyar falon,  lokaci Ι—aya ta harar da duk wani abu dake cikinta, jingina bayanta tayi da jikin kujera tana me da numfashin wahala..1

Zaid da shigowarsa falon kenan, yayi saurin toshe hancinsa haΙ—e da kawar da kansa gefe cike da bala’i yace

“Ke dan ubanki duk girman gidannan kirasa inda zakiyi amai sai a cikin falon nan?  ki share wajennan yanzu kafun infito kokuwa idan nafito nasamu baki shareba nasa ki lasheshi yakoma inda yafito, Ζ™azama kawai, wai ahakane zanyi rayuwa dake mcheeww!” cikin Ι“acin rai yaΖ™are maganar haΙ—e da shigewa cikin Ι—akinsa..

Jikin Afra na rawa ta Ι—auko moper tashigayin mopping Ι—in wajen, Ζ™aramin aikinsa ne idan har yadawo yasamu bata gyara wajen ba yasata ta lashe aman, tabbas tasan zai iya, yau kaΙ—ai tafuskanci cewa shiΙ—in tsananin mugu ne, wanda babu kamarsa, tana gama gyara wajen ta gudu cikin Ι—akin da aka sauΖ™eta, Ι—akin dake kusa da nasa, tanashiga Ι—akin ta murza key, haΙ—e da faΙ—awa kan gado, tasaki wani irin kuka,  danasani kawai takeyi acikin ranta,  itafa tayarda ta auri Zaid ne saboda dama tuncan yana matuΖ™ar kasheta aduk sanda tagansa sai taji inama dazai zamo nata, sannan kuma gayen akwai kuΙ—i uwa uba aji, duk da cewa ita Ι—inma babanta me kuΙ—i ne amma baikai na baban Zaid  dashi kansa Zaid Ι—in ba,   lokacin da babanta yazo mata da maganan auren Zaid, daΙ—ine yakusa kasheta ganin irin damar da Allah yabata, ashe bata saniba gidan mutuwa takawo kanta, ita da har jinkanta tasomayi, har Ι—agawa takeyiwa Ζ™awayenta, ita adole ta auri namijin duniya, batasan cewa wahala zata ruska ba, ta Ι—auka cewa holewa zatayi,  harta fara tunanin Ζ™asashen da zata sasa yakaita, sai gashi haΙ—uwarsu ta farko ma da lafiyayyen mari ya tarbeta…8

Zaid kuwa yana shiga cikin Ι—akinsa yafaΙ—a kan gado haΙ—e da lumshe idanunsa, kansa ne yake matuΖ™ar sara mae, tun jiya yakejin ciwon kan, amma yau abun ya tsananta sosai,     wata tsuka yaja me sauti, haΙ—e da sake gyara kwanciyarsa, shi wannan auren ma da aka laΖ™aba masa kaΙ—ai ya isa Ζ™ara masa ciwon kai, shiba yaro ba, shiba bagidaje ba amma ankama anyi masa auren dole…

******

Tsaye take agaban dinning area, ta kafesa da manya manyan idanunta, yayinda shikuwa baimasan tana kallonsa ba, hankalinsa gaba Ι—aya yana ga agogon dayake Ζ™oΖ™arin Ι—aurawa a tsintsiyar hanunsa..   Bakomai yasa take kallonsa ba, face kyawun da taga yayi mata,  shadda ne milk colour ajikinsa Ι—inkin riga da wando, rigar ta tsaya iyaka guiwarsa, yayi kyau sosai yasha hularsa light brown wanda taΖ™arawa kwalliyartasa kyau..  Yana Ι—ago kansa suka haΙ—a idanu, da sauri ta kawar da idanunta daga kansa, haΙ—e da sunkuyar da kanta Ζ™asa.

Murmushi yayi haΙ—e da takowa yaΖ™araso inda take, hanu yasanya ya rungumota ta baya.

“Namiki kyau ne haka kiketa kallo na?” yatambayeta yana me shaΖ™an daddΙ—an Ζ™amshin jikinta.

STORY CONTINUES BELOW

Ɓata fuska tayi haΙ—e da cewa

“Namiji kuma dama yana kyau ne idan yayi kwalliya?”

Dariya maganar ta ta ta basa, juyo da ita yayi yazamana suna fuskantar juna.   

“Eh mana bakisan maza sun mafi mata kyau ba?”  ya faΙ—i haka yana me Ζ™arewa fuskarta kallo.

Idanunta ta waro haΙ—e da  cewa “Maza sunfi mata kyau? cab aikuwa nidai baka fini kyau ba”

Dariya yayi haΙ—e da Ι—an jan hancinta.

“Nafiki kyau sosai ma, nifa banasa jan baki, bana shafa powder, bana sa kwalli, bana kumayin jagira, haka kuma bana wani shafa mai wanda zai sa fatata tayi kyau, komai nawa daga Allah ne, ku kuma mata kullum cikin shafawa da gogawa kuke, kinga kenan dagaske munfiku kyau” yafaΙ—i maganar yana me Ι—an Ζ™ara fito da idnunsa waje.

Duk da tana cikin fushi, amma sai da tayi dariya.  

“KafaΙ—i komai ma, amma nidai bazan yarda cewa  wai kafini kyau ba”

tafaΙ—i haka tana me Ζ™oΖ™arin zame jikinta daga cikin nasa. 

Sake riΖ™eta yayi gam haΙ—e da cewa

“Dagaske namiki kyau? naga har wani kishi na kike”

Ɗan Ζ™aramin bakinta taturo gaba haΙ—e da shagwaΙ“e fuskarta.

“Idan nayi kyau kaima baka barina nafita, to me yasa kai kakeson yin kyau ako da yaushe? kana tunanin bazanji haushi bane idan wata ta kalleka!” kafun taΖ™are maganar ma tuni idanunta sun soma kawo ruwa.

“Eh kumafa hakane, harma kintunamin, akwai wata kuwa a asibitin mu, kullum saitace namata kyau, sannan kuma saitace wai ina matuΖ™ar burgeta, gaskiya nima kuma tana burgeni dan a Ζ΄an kwanakin nan harma na fara tunaninta, to mezakice akanta?” yaΖ™are maganar yana me Ι—aga mata giransa Ι—aya.

Baki kawai tasake tana kallonsa yayinda wani malolon baΖ™in ciki ya tokare mata zuciya. Da Ζ™arfi ta soma turesa tanason Ζ™wace jikinta daga nasa.   2

Ganin haka yasanya yasake riΖ™eta  da kyau haΙ—e da cewa

“Mekikeyi haka?”

“Kafi kowa sanin abunda nakeyi,  inatunanin tsayuwan da kakeyi anan kana Ι“ata lokacin kane, domin wacce kake muradi tanacan tana jiranka, koba don itane kayi kwalliyar ba? ai bana tunanin ni inada wani amfani a wajenka, ka sakeni kaje tayaba kwalliyar taka banaso na Ι“ata bata gani ba.”

Dagajin yanda take maganar kasan kishine tsantsa kecinta, domin kuwa har hawaye sun gangaro daga cikin idanunta..

Dariya sosai yashiga yi batare daya sake ta ba.2

“Kasakeni nace, ai nasan baka buΖ™ata ta!” tafaΙ—i haka tana me yunΖ™urin Ζ™wace hanunta dake cikin nasa.

Da Ζ™yar ya iya tsagaita dariyan   nasa, yashiga dubanta da kyau, yasani dama da sannu zuciyar Zahrah zata nutsa acikin Ζ™aunarsa sosai, gashi kuma yafara ganin alama tunda har kishinsa ya bayyana acikin idanunta..

Fuskarta yatallafo da tafukan hanunsa haΙ—e da sanya bakinsa yashiga lashe hawayen dake fitowa daga cikin idanunta.

“Bazan iya jure ganin matata tana kuka ba, ki kwantar da hankalinki kinji me daΙ—i na, babu wata mace da ta isa Ζ™wace miki doctor Ι—inki,  ketawace ni ma kuma naki ne,  babu wata kuma danake tunani bayanke kiyarda dani!!” yafaΙ—i maganar cikin lallausan murya yana me Ζ™ara riΖ™e fuskarta acikin tafukan hanunsa. 

Ajiyar zuciya ta sauΖ™e wanda harsaida ya bayyana afili, har cikin ranta taji daΙ—in maganganunsa, amma kuma afili bata nuna  hakan ba, Ζ™oΖ™arin Ζ™wace kanta daga jikinsa tacigaba dayi.

“Nine bakyaso ko? shikenan tunda bakyaso nariΖ™eki” yafaΙ—i haka yana me sake ta yanufi hanyar fita daga cikin falon.  Da sauri ta je ta rungumesa ta baya, wani murmushi yayi haΙ—e da juyowa  gareta yazamana suna fuskantar juna.

STORY CONTINUES BELOW

“Dan Allah kada ka Ζ™aramin irin wannan wasan, gashi duk kasa ma naji natsani komai!” tafaΙ—i haka a shagwaΙ“e.3

Murmushi yayi mata haΙ—e da sanya hanunsa yaΙ—anja kumatunta. 

“Bazan sakeba, kiyi haΖ™uri kinji me daΙ—i na!”

Da sauri ta cusa kanta   acikin Ζ™irjinsa haΙ—e da sanya hanunta ta  mintsineshi acikinsa.  Da Ι—an Ζ™arfi yace “Ahhhshhhh!”

Dariya tayi masa haΙ—e da yi masa gwalo ta wuce zuwa dinning domin dama abinci take haΙ—awa.

Biyota yayi kan dinning table Ι—in suka shirya abincin atare,  acikin plate Ι—aya sukaci abinci, gaba Ι—aya yanzu doctor yagama shagwaΙ“ata abinci ma shiyake bata abaki, har sai ta Ζ™oshi,   tana ajiye cup Ι—in ruwan dake hanunta, ta Ι—an saci kallonsa, ta lura tun Ι—azu yaketa kallonta.

“Kaima nayi maka kyaun ne, kaketa kallona haka?” ta tambayeshi.

Murmushi yayi mata haΙ—e da cewa

“Ae ni dama kullum kinamin kyau,  ke mai kyauce ai ako da yaushe, amma kuma…” baiΖ™arisa maganar dake cikin bakin nasa ba yayi shiru.

“Amma kuma me?” ta tambayeshi da sauri domin atunaninta ta zaci zaice amma bata masa kyau sosai ne.

“Amma bakyason bani abun daΙ—i na, please yau ki tausayamin kinji, bazan iya bacci bafa yau idan baki bani ba!” yafaΙ—i haka cikin sigar shagwaΙ“a haΙ—e da Ι—anyin Ζ™asa Ζ™asa da muryarsa.1

Maganganunsa kunya suka bata da sauri ta sanya hanunta ta rufe fuskarta,   jawota jikinsa yayi haΙ—e da sanya bakinsa adai dai saitin kunnenta cikin muryar raΙ—a yace

“Bazan iya jurewa ba Zahrah, inaso akullum kina bani kanki sau ba adadi, inason kasancewa tare dake ako wani lokaci” bakinta yashafo da hanunsa haΙ—e da lumshe idanunsa.   “Nayi missing waΖ΄annan lips Ι—in amma yau zanyi musu sucking na musamman har ma….” bata jirayi jin Ζ™arshen zancen nasa ba ta ruga da gudu zuwa cikin Ι—aki, bazata iya cigaba da sauraran waΖ΄annan manya manyan kalaman nasa ba. Murmushi kawai yayi haΙ—e da miΖ™ewa yafice daga cikin falon, dama sabiti zaije.

Tanajin fitar motarsa acikin gidan ta sauΖ™e ajiyar zuciya haΙ—e da lumshe idanunta, kwanciyarta ta gyara, tana me tuno kalamansa,    itakanta tana tsananin son taji ta ajikinsa, musamman idan fatarsu ta haΙ—e waje guda hakan na haifarmata da wani irin yanayi me daΙ—in gaske,  kallonta ta mayar ga agogon bangon dake kafe acikin Ι—akin.   Ζ˜arfe 11 na rana yau take da lecture saboda haka tana da Ι—an sauran lokaci, domin yanzu Ζ™arfe 10 ma batayi ba, wani English Novel  mesuna  ( Just A Friend)   tajawo haΙ—e da buΙ—e chapter’n da take ta soma karantawa, agurin wata Ζ΄ar class Ι—insu ta karΙ“o  shi.

****

Ƙarfe 4 na yamma dai dai suka fito daga cikin lecture Ι—insu wanda shine na  Ζ™arshe a  wannan ranan, direct library ta nufa saboda akwai wani littafi da takeson dubawa, kasancewar akwai assigment Ι—in da aka basu, idan ta samu littafin kuma sosai zai taimaka mata wajen yin assigment Ι—in cikin sauΖ™i.     Gaba Ι—aya hankalinta naga littafin da take dubawa, sam bata damu da mutanen dake wajenba kasancewar kowa karatu kawai yakeyi.   Tana zaro littafin daga ma’ajinsa ta saki murmushi,  juyawa tayi daniyar tafiya idanunta suka sauΖ™a akan shi, waro manyan idanunta waje tayi haΙ—e da sakin littafin yafaΙ—i Ζ™asa.   Jikinta ne yaΙ—auki rawa da sauri ta tsugunna ta Ι—auki littafin haΙ—e da nufar hanyar waje, tsabar sauri har Ζ™afafunta harΙ—ewa suke,  batayi auneba saiji tayi ta buge mutum, da sauri taΙ—ago don ganin waye ta buge, shiΙ—inne dai tsaye a gabanta yana me kallonta da jajayen idanunsa, da sauri taja baya, haryanzu jikinta rawa yake kamar wacce taga mutuwarta.1

“ZAHRAH!”

yaΖ™ira sunanta cikin wata irin murya me matuΖ™ar rauni.

Kusan mintuna uku takasa amsa masa da Ζ™yar ta iya motsa bakinta,

“I..na..da au..re” 

shine kalaman da suka fito daga cikin bakinta awawware batare kuma da ta shiryawa fitowar kalmomin ba.

Rumtse idanunsa yayi haΙ—e da dunΖ™ule hanunsa. Cikin murya me Ι—aci haΙ—e da bushewar maΖ™oshi yace 

“Nasani!”1

Bazata iya jurewa ganinsa ba da sauri ta bi ta wata hanyar ta wuce da gudu, ko takan littafinta daya kuma faΙ—uwa batayi ba.

Bayanta yabi da kallo haΙ—e da tsugunnawa yaΙ—auki littafin, juyawa shima yayi yafice daga cikin library Ι—in. Sai dai ko daya fito,  ko Ζ™yallinta bai gani ba.

Zahrah kuwa tana fitowa daga cikin library Ι—in direct wani Ι—an corridor wanda mutane basu cika yawan bi ba tanufa, kaitsaye ta tsinci kanta awani fili wanda bakowa acikinsa sai shuke shuke,  zama tayi akan wani benci dake wajen, haΙ—e da fashewa da kuka,  tashiga ukunta itakam, wannan wace irin jaraba ne, meyasa Zaid bazai barta ta huta bane,  jitayi lokaci Ι—aya Ζ™irjinta yayi mata nauyi kamar anΙ—aura mata gungumen dutse, wayarta dake ringing ta kalla,  Dr.Sadeeq ne ke Ζ™ira amma bazata iya Ι—agawa ba, ahalin da take ciki yanzu ma batasan me zata ce masaba idan ta Ι—aga.  Da Ζ™yar ta’iya tashi tabi ta Ζ™ofar baya tafice daga cikin makarantar gaba Ι—aya, tana fita ta tare me taxi haΙ—e da gaya masa inda zai kaita, ko ciniki basuyi ba ta faΙ—a cikin motar haΙ—e da ce masa yaja suje.

Yana kawota Ζ™ofar gida ta basa kuΙ—insa haΙ—e da ficewa acikin motar ta kutsa kanta cikin gidanta.

Bata damu da duhun dake cikin Ι—akin ba  haka ta faΙ—a kan gado ko mayafin dake jikinta bata cire ba..  ZazzaΙ“ine me zafin gaske ya rufeta alokaci guda..1

Zaid kuwa yana fita daga cikin library Ι—in direct wajen da motarsa ke fake ya nufa, buΙ—e murfin motar yayi, ya shiga ya zauna, kifa kansa yayi akan steering motar yana mejin zafi da raΙ—aΙ—i na ratsawa har cikin Ζ™waΖ™walwarsa,   akaro nafarko daya yardarwa kansa cewa zai haΖ™ura da Zahrah kenan, tabbas yazama dole ya yi haΖ™uri da ita koda kuwa hakan nanufin mutuwarsa ne,   yau Zahrah da bakinta ta faΙ—a masa cewa tana da aure, maganar dayajita tamkar anwatsa masa tafasheshshen ruwan zafi,   bayajin zai iya yin rayuwa idan babu Zahrah, amma kuma ayau yaΙ—aukarwa kansa alΖ™awarin cireta acikin zuciyarsa, duk da yasan hakan zai zamo kamar yaudaran kansa ne yakeyi, amma kuma dole zai jarraba….3

****

Cikin matsanancin tashin hankali Dr.Sadeeq yadawo gida, yaje makarantar su Zahrah yanemeta sama da Ζ™asa bai ganta ba, gashi yaΖ™ira wayarta bata Ι—auka ba daya Ζ™ara Ζ™iranta kuma yaji wayar akashe, hankalinsa atashe yake sosai, yana shigowa cikin Ι—akin yadanna madannin Ζ™oyin wuta take haske ya gauraye gaba Ι—aya Ι—akin, wani irin ajiyar zuciyar dabai taΙ“a yin irinta ba ya sauΖ™e, haΙ—e da lumshe idanunsa, da sauri yaΖ™araso gareta haΙ—e da sona Ζ™iran sunanta, jin shiru bata amsa saba yasanya yakai hanunsa jikinta, zafi zau yaji jikin nata, take tausayinta yakamasa, shidai yasan hakanan Zahrah bazata dawo gida bata jirasa yazo ya Ι—auketa ba, sannan kuma haka nan bazata kashe wayarta ba.  Zama yayi akan gadon haΙ—e da Ι—agota ya kwantar da’ita ajikinsa.  Mayafin dake jikinta ya zare haΙ—e  da sanya hanu yashiga shafa kumatunta.1

 “Zahrah!” yakuma Ζ™iran sunanta cikin sassanyar murya.

“Na’am!” ta amsa masa cikin wata irin murya, dagaji kasan tanajin jiki.

Kanta yashiga shafawa ahankali, zuge mata zip Ι—in rigar dake jikinta yayi, haΙ—e da cire  rigar gaba Ι—aya daga jikinta, kwantar da ita yayi akan gado, kana ya  nufi wajen da Ι—an Ζ™aramin drawer Ι—insa ke aje,  maganin da zai  sauΖ™ar  mata da zazzaΙ“i cikin gaggawa yaΙ—auko.

Dakansa ya lallaΙ“ata tasha maganin, abun gwajinsa ya Ι—auko yashiga gwadata, cutar dayaga tana damunta shiyayi matuΖ™ar Ι—aga masa hankali, wani irin zufane yashiga keto masa.

“Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un!!”1

kawai yake ambata acikin zuciyarsa,  duk sanyin A.C’n dake cikin Ι—akin  amma Dr.Sadeeq gumine ke tsastsafowa daga jikinsa.

“Taya akayi Zahrah takamu da wannan ciwon?” tambayar dayake tayi mawa kansa kenan…..Hanu yasanya akan goshinsa ya share zufan dake tsastsafo masa. Tashi yayi tsaye haΙ—e da tattara kayan aikin nasa ya ajiye a gefe. Direct bathroom ya shiga haΙ—e da sakar mawa kansa ruwa….+

Tun shiga wankansa har kawo yanzu da ya fito yake shirya kansa tanajin sa,amma idanunta alumshe suke kamar meyin bacci.

Zama yayi akan gadon haΙ—e da Ι—agota ya jawota zuwa jikinsa, kanta ya kwantar akan Ζ™irjinsa haΙ—e da soma shafa bayanta a hankali, still Ι—aya hanunsa yasanya yana me shafa gashin kanta.

Cikin murya me Ι—auke da nutsuwa ya soma cewa.

“Meyasa haka Zahrah? me yasa kika zaΙ“i Ζ™untatawa kanki? tun bayauba nasha faΙ—a miki cewa ki daina yawan sanya kanki cikin damuwa, na faΙ—a miki kirage yawan tunani, har acikin zuciyata inamiki wani irin so wanda bansan iyakacinsa ba, bana so nagan ki cikin damuwa, ganin farincikin ki yafiyemin komai aduniyarnan, kinkuwa san meke damunki yanzu? damuwar da kike yawan sanya kanki aciki tahaifar miki da matsala wanda baikamata ace yarinya Ζ™arama kamarki tana Ι—auke da wannan ciwonba, mekika nema kika rasa aduniyar nan? banaso ki Ι“oyemin komai inaso kifaΙ—amin shin azamana dake ina cutar dake ne? ko kuwa inayi miki wani abu wanda ba kya so ne?”

Kanta tashiga girgizawa alamar “A’a” tuni hawaye sungama wanke mata fuska.

“To idan dai har hakane yakamata ki faΙ—amin damuwarki koda nima zanji sauΖ™i acikin zuciyata”

yafaΙ—i haka a gareta cikin tausasawa.

Kuka ta fashe dashi haΙ—e da sake rungumeshi cikin kukan tace.

“Nakasa daurewa ne, nakasa daure zuciyata, idan dai yana cikin wannan duniyar bazai taΙ“a barina ba, bazai barni ba harsai yakasheni sannan zai huta, naso namanta dashi amma nakasa, bansan meyasa ba kullum zuciya ta me rauni take kasancewa akansa, dan Allah kayi haΖ™uri banfaΙ—i haka agareka don na Ι“ata ranka ba, kawai dai nafaΙ—i abun dake zuciyata ne!” taΖ™are maganar tana sheshsheΖ™an kuka..

Rumtse idanunsa yayi haΙ—e da cije laΙ“Ι“ansa, dama yasani duk duniya damuwarta bazata wuce akansa bane yajima da sanin wannan. Ɗagota yayi daga jikinsa yazamana suna fuskantar juna. Cikin wata irin murya yace..

“Ba iya miji bane ni agareki, ni Ι—an uwa ne wanda baki da kamarsa, najima da sanin cewa har yanzu Zaid yana cikin rayuwarki, nasan Inasonki so me tsanani, sai dai kuma duk irin soyayyar danakeyi miki Zaid yafini sonki, da ace zan iya to da najima da mallakawa Zaid ke amma bazan taΙ“a iyawa ba Zahrah nima masoyinki ne na haΖ™iΖ™a kamar yanda Zaid yakejin bazai iya rayuwa ba idan babuke, haka nima nakeji ajikina, batun yauba nasan Zaid yana nan kwance aΖ™asan zuciyarki, bana yaudaran kaina nakan faΙ—i abu ne aduk yanda natsaya na fahimceshi, koda kuwa abun dana faΙ—a bazasuyimin daΙ—in ji acikin kunnuwa naba, duk da kuwa nina faΙ—esu, bana Ι“oye gaskiya saboda biyan buΖ™atar kaina”

KafaΙ—unta yakama da duka hannayensa. Ci gaba yayi da cewa

“Yanzu zanyi miki magana ne a matsayina na mijinki kuma wanda yake sonki, har yanzu duk da na aureki kina aΖ™arΖ™ashin ikona bazan taΙ“a takuramiki ba, inamatuΖ™ar son farincikin ki, idan har kinaji ajikinki cewa bazaki iya rayuwa ba idan babu Zaid shikenan zan iya…..” rumtse idanunsa yayi da Ζ™arfi ya kasa Ζ™arasa maganar, da sauri ya miΖ™e yafice daga cikin Ι—akin.3

STORY CONTINUES BELOW

Zahrah wanda tun fara maganarsa tayi saroro tana kallonsa, tana ganin ficewarsa ta fashe da kuka.

“Me doctor yake shirin cewa? badai zai haΖ™ura da ita ba?” tambayar da tayiwa kanta kenan, sam haka bazai taΙ“a yiwuwa ba, wace irin banzace ita? taya ya zata iya jure rashin masoyi kamar doctor Sadeeq? kuka tashiga rerawa me tsuma zuciya, kaiconta tunda dai harta bari Dr.Sadeeq ya iya sanin sirrin dake cikin zuciyarta, yanzu da wani idanu zata kalleshi bayan yasan cewa akwai son wani maΖ™are acikin zuciyarta? lallai koda ace Zaid ubantane yakamata tayi Ζ™oΖ™arin mantawa dashi….3

Dr.Sadeeq kuwa yana fita daga Ι—akin falo yanufa, yanazuwa ya buΙ—e fridge haΙ—e da Ι—aukan goran ruwa yakafa a bakinsa, saida yasha ruwan fiye da rabin gora kafun ya kai goran Ζ™asa, ajiyar zuciya kawai yake sauΖ™ewa akai akai.

“Meyake shirin aikatawa ne haka?” yatambayi kansa. Girgiza kansa yayi haΙ—e da ware idanunsa, idan yace zai iya rabuwa da Zahrah to yayi Ζ™arya, amma kuma idan yazamana bashine zaΙ“in ranta ba, to fa tabbas yazama dole ne yarabu da ita, badon kowaba saidon samun ingantaccen farincikinta, yasani shima abune me wahala ya iya jure rashinta, amma kuma itama yakamata aduba zuciyarta, yakamata tasamu abun da takeso.

key Ι—in motarsa dake aje kan Ι—an Ζ™aramin stull dake falon ya Ι—auka haΙ—e da sakai yafice gaba Ι—aya daga cikin falon, motarsa yashiga ya fice daga cikin gidan, bayajin zai iya zama acikin gidan gaba Ι—aya zuciyarsa a dagule take..

Zahrah kuwa tanajin alamar fitansa daga cikin gidan tasake fashewa da kuka, duk da kuwa zafin zazzaΙ“in dake damunta. Kuka tayi sosai amaimakon zazzaΙ“in nata ya ragu sai gashi ya Ζ™ara hawa, to taΖ™i tabar zuciya da Ζ™waΖ™walwanta su huta…2

****

Da Ζ™yar ya iya kai kansa gida, tsabar yana acikin wani irin yanayi har idanunsa soma rufewa sukayi, yazamana duhu duhu kawai yake gani, hanunsa dafe da saitin zuciyarsa yafito daga cikin motar, taku biyu yayi duhu ya mamaye duka idanunsa take wani irin juwa ta Ι—ebesa saigashi yashe a Ζ™asa bayako da numfashi, da gudu ma aikatan gidan sukayo kansa suna Ζ™iran sunansa

“Oga! Oga!!”

Oga baimasan sunayi ba, wani daga cikin masu bawa flowers ruwa ne ya ranta aguje yaje yasanarwa Mummy dama Dad na nan atare suka fito amatuΖ™ar ruΙ—e.1

Ganin da suka mawa Zaid yashe a Ζ™asa yafi komai Ι—aga musu hankali, da taimakon ma’aikatan wajen Dad yasanyasa amota direct suka wuce asibiti Mom sai kuka take.

Emergency aka karΙ“esa, Lallashin duniya Dad yayimawa Mom akan tayi shiru ta daina kuka amma taΖ™i, duk da cewa tana fushi dashi amma bata Ζ™aunar taga ko taji wani abu yasameshi, yanzu idan akace ya mutu yazatayi da rayuwarta?

Sama da 1 hour likitoti suka kwashe akansa suna bashi taimakon gaggawa. Ɗaya daga cikin likitotin ne ya kalli Dr.Bilal haΙ—e da Ι—aga masa kai alamar wai Zaid Ι—in babu rai ajikinsa. girgiza kai Dr.Bilal yayi alamar bai yarda cewa babu rai ajikin Zaid Ι—in ba..

Hmmm likitotin nan sunsha matuΖ™ar wahala kafun suka samu numfashin Zaid ya dawo dai-dai. Dukansu haka suka fito suna gumi domin kuwa da fari harsun cire rai dashi, sun Ι—auka dagaske ya mutu.

Da gudu gudu sauri sauri Dad yataho wajen Doctor Bilal, hanun Dad Dr.Bilal yakama suka wuce office Ι—insa…..

“Yajikin nasa doctor? dan Allah kafaΙ—amin wani hali yake ciki a yanzun?” Dad yatambayi Dr.Bilal cikin yanayi na matuΖ™ar ruΙ—ewa.

“Ka kwantar da hankalinka Alhaji, yau Zaid ya hau matakin Ζ™arshe wanda da taimakon Allah muka samu da Ζ™yar muka shawo kan matsalan, amma bazan taΙ“a Ι“oye maka ba idan har yasake shiga cikin yanayi irin wannan to fa tabbas wata Ζ™ila saidai haΖ™uri, ba’aja da ikon Allah amma kuma fa da matuΖ™ar wahala idan zai sakeyin numfashi, dama wannan shine matakin Ζ™arshe kuma gashi yakawosa idan irin haka tasake faruwa kuma to saidai dukanmu muyi haΖ™uri, haka Allah dama yake abunsa, duk wani me rai mamaci ne, koda ciwo ko babu ciwo, watarana dole mutum saiya mutu idan lokacinsa yazo, haka kuma gaba Ι—aya zamu zama tarihi, saidai aba da labarin mu kamar yanda aka bamu na waΖ΄anda suka shuΙ—e kafun zuwanmu iyaye da kakanninmu kenan!” Dr.Bilal yafaΙ—i haka yana me tattara nutsuwarsa ga Dad.

STORY CONTINUES BELOW

Gumi kawai Alhaji Ma’aruf ke sharewa sai ambatan

“Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un!” yakeyi gaba Ι—aya ji yayi duniyar tayi masa nauyi.

“Doctor menene mafita?” Dad yatambayi Dr.Bilal cikin sanyayewar guiwa.

“A yanzu kam dai bamu da mafita Alhaji Ma’aruf, sai dai mujira muga me Allah zaiyi, wataΖ™ila Zaid zai iyakaiwa kwana uku batare daya farka ba, wataΖ™ila kuma ko nanda kwana biyu ya farka, amma yazama dole ku kula dashi, yanzu bakamar da bane, yanzu abu kaΙ—an na Ι“ata masa rai zuciyarsa zata hau zafi, sannan kuma idan ya yawaita yin tunani to fa akwai babbar matsala, yazama dole ku tsaya akansa ku lura, akwai magungunan dazan rubuta muku, idan yatsaya akansu insha Allah zasu taimaka masa sosai.”

Sai alokacin Alhaji Ma’aruf ya Ι—anji sanyi acikin ransa.

“Nagode Ζ™warai Dr.Bilal kuma Insha ALLAH zamu kiyaye sosai!” Dad yafaΙ—i haka yana me miΖ™ewa tsaye. Musabaha sukayi da Dr.Bilal kafun ya fice acikin office Ι—in.

*****

A daddafe ta tashi tayi sallan isha. Tana kan sallayan bata tashiba yashigo cikin Ι—akin, idanunta ta zuba masa, bada kayan da yafita ya dawo ba, yanzu rigane da wando na jeans ajikinsa, kallonsa takeyi kamar wani wanda bata taΙ“a ganinsa ba, shima kallonta yayi haΙ—e da yi mata murmushi, ya wuce cikin bathroom, mintuna kaΙ—an yafito daga cikin bathroom Ι—in.

“Kizo kici abinci” yana faΙ—a mata haka yafice daga cikin Ι—akin.

Wani irin kunyan sa ne yaka mata, amma kuma babu yanda zatayi, abundake cikin zuciyarta ta faΙ—a.

MiΖ™ewa tayi sumi sumi ko hijab Ι—in dake jikinta bata cire ba ta fita zuwa falo.2

Zama tayi akan sofa kusa da inda yake zaune, haΙ—e da takure jikinta waje Ι—aya, shawarma ne da gasashshen kifi (roasted fish) ya sayo musu, tura mata plate Ι—in yayi gabanta.

“Kici sai kisha magani” yafaΙ—i haka fuskarsa Ι—auke da Ι—an murmushi, kallonsa tayi kamar zatace dashi wani abu kuma saita fasa tasoma cin abincin da kaΙ—an kaΙ—an. Shikuwa sannu a hankali yake sipping country yoghurt Ι—insa yana me kuma latsa wayarsa.

Haka suka zauna shiru babu me cewa da Ι—an uwansa Ζ™ala.

Tana kammala cin abincin ya bata wasu magunguna daya shigo dasu, babu musu ta amsa tasha. Ganin yatashi yabar falonne yasanya itama ta tashi ta koma Ι—aki, wanka tayi kana ta fito ta sanya wata sleeping gown wacce ta tsaya iyaka cinyarta, ko guiwa bata Ζ™arasa ba, sosai rigar tayi mata kyau ta kuma fito da farar fatarta fili, dogon gashinta ta kama ta tubke a tsakiyar kanta haΙ—e da Ι—aureshi da ribbon, turarenta me daΙ—in Ζ™amshi ta shafa, tana nan tsaye a cikin Ι—akin yaturo Ζ™ofar Ι—akin yashigo.

Wani irin yawu ya haΙ—iye a maΖ™oshinsa, sanda idanunsa sukayi masa tozali da ita, sosai tayi kyau acikin rigar, ga fararen cinyoyinta sun bayyana kansu a fili, da Ζ™yar ya iya daure zuciyarsa, murmushi kawai yayi mata haΙ—e da kawar da kansa gefe, shi kaΙ—ai yasan me yakeji acikin zuciyarsa, yana tsananin kishin matarsa, kamar yanda yake tsananin sonta.

Kan gado ta koma ta kwanta, agogon hanunsa yacire haΙ—e da cire rigarsa, 3 guater jeans yasanya..

Zama yayi a gefen gadon haΙ—e da jawo laptop Ι—insa yasamo dannawa, dama yanada ayyukan da suka masa yawa yanaso ya Ι—an ragesu, bayaso ya kwanta shiru tunani ya damesa.

Hanu tasa ta share hawayen dake fitowa daga cikin idanunta.

“fushi Dr.Sadeeq yakeyi da ita kenan?” tambayar da take ta yiwa kanta tun Ι—azu kenan, bazata iya jure fushinsa akanta ba, duk da baifito ya nuna mata hakan afili ba, amma duk wasu alamu sun nuna hakan, bayason yi mata magana me tsawo sannan kuma baya sake mata kamar yanda ya saba, idan tabarsa haka batayi masa adalci ba, ayanzu bata da wani wanda ya wuce mata shi, shi Ι—inne dai komai nata, bazata iya Ι—aukar fushinsa akanta ba.9

STORY CONTINUES BELOW

Aikinsa yake cikin nutsuwa amma kuma gaba Ι—aya tunaninsa akanta yake, ba abun dayafi damunsa kamar cutar hawanjini dake da munta, yasani sarai cutar hawan jini bata da kyau tana cutarwa sosai, musamman ma ga yarinya kamarta hakan yasa yake tsananin tausayinta.

Baizataba saiji yayi ta rungumeshi ta baya, haΙ—e da Ι—aura kanta akan wuyanshi, me makon tace wani abu sai kawai ta fashe masa da kukan shagawaΙ“a.

Lumshe idanunsa yayi har a cikin zuciyarsa bayason kukanta idan tana kuka hankalinsa tashi yake.

Jawota yayi ta dawo gabansa.

“Menene?” yatambayeta yana me Ι—ora idanunsa akanta.

“Bazan iya jure fushinka ba, dan Allah kayi haΖ™uri wallahi inasonka banason kajuyamin baya, banda kowa sama da kai, idan kajuyamin baya bansan yanda rayuwata zata kasance ba, kayi hakuri kaji!!” kuka take sosai alokacin da take faΙ—ar maganar.1

Wani irin sanyine yaji yana ratsa zuciyarsa kalmar “Wallahi tana son shi” da ta faΙ—a yafi komai da Ι—aΙ—a masa rai, yaji daΙ—in maganar sosai, amma sai ya dake bainuna mata hakan afili ba.

“Ni nace miki ina fushi dake ne?” abunda yatambaya kenan.

Da sauri tashiga kaΙ—a kanta alamar “Eh”

Cike da mamaki yace “yaushe nace haka?”

“Kaine kake bani abinci abakina harsai na Ζ™oshi, amma yau turamin abincin gabana kayi kace naci ni kaΙ—ai, sannan tunda kafita baka dawo gidan nan ba, gashi kazo baka kulani ba saima laptop Ι—inka daka fara latsawa, kasabarmin bazan iya jurewa ba, dan Allah kada kayi fushi dani naroΖ™eka, bazan iya samun nutsuwa ba matuΖ™ar baka tare dani, bazan iya zama dakowa ba bayan kai, inasonka sosai!”

Tunda ta fara maganar yake kallon Ι—an Ζ™aramin bakinta hartakai Ζ™arshe.

Jawota yayi jikinsa, haΙ—e da sake lumshe idanunsa, sun kai kusan mintuna uku a haka, babu wanda yasakeyin magana kafun ta Ι—ago kanta daga cikin Ζ™irjinsa. BuΙ—e idanunsa yayi ya sauΖ™esu acikin nata, kallon juna sukeyi cikin wani irin yanayi me wuyar fassaruwa, ahankali ta matso da fuskarta daf da tashi haΙ—e da lumshe idanunta, bakinta ta buΙ—e ahankali ta Ι—aura harshenta akan lips Ι—insa, jiyayi kamar anjona masa shocking ajikinsa, ahankali ta tura harshenta cikin bakinsa tana me yawo dashi, kasa jurewa yayi cikin hali na zaΖ™uwa ya kama harshenta yashiga tsotsa.. Sosai suke kissing Ι—in junansu, numfashinsu har Ζ™oΖ™arin Ζ™wace musu yake. Igiyar dake gaban rigarta yaja take rigar ta buΙ—e ta gaba, sake lumshe idanunsa yayi haΙ—e da fitar da wani irin numfashi me sauti alokacin da idanunsa suka sauΖ™a akan breast Ι—inta, kansa ya cusa acikin Ζ™irjinta yana kai mata kiss tako ina.. Cikin mintuna Ζ™alilan Dr.Sadeeq da Zahrah suka fice a cikin hayyacinsu babu ma kamar doctor, gaba Ι—aya idanunsa sun rufe numfashi kawai yake fitarwa ta bakinsa… Soyayyar su tayau ta da bance, yau tsantsar soyayya ya gwada mata wacce tasa ta manta komai acikin duniya har batasan sanda hawaye suka gama wanke mata fuska ba, shi ma kansa yau yazautu da tsananin kulawan data basa, ita kanta mamakin yanda yake shiΙ—ewa akanta take, sai dai kuma idan ta tuno cewa ko wacce mace da irin baiwar da ALLAH ya mata saitaji sanyi acikin ranta, ko a iya nan aka tsaya, zata ta godemawa ALLAH …

Cike da shagwaΙ“a ta ture kanshi dake kan breast Ι—inta. “So kake ka ciremin nipples Ι—ina ne wai?”

Duk da haryanzu yana acikin magagin duniyar daΙ—in dayashiga bai sake saba amma saida yayi dariya.

“Dama Nipples yana fita ne?” shima yatambayeta cike da mamaki, domin a iya tsawon rayuwarsa shi bai taΙ“ajin inda akace nipples yafita daga jikin breast ba.

“To bakai bane tun Ι—azu fa kaketa sha, kuma zafi yakemin!” araunace tafaΙ—i maganar.

“To ba nipples din bane yace yana sona!” yafaΙ—i haka yana me kwaikwayon yanayin maganarta.

Dariyane yakamata sosai, da Ζ™yar ta samu ta zame hanunsa dake kan breast Ι—in nata, tana Ζ™oΖ™arin tashi yayi saurin kamota ya kwantar da ita, kwanciya yayi asamanta haΙ—e da sakarmata duka nauyinsa.

Ɗan Ζ™aran wahala tasake haΙ—e da lumshe idanunta.

“Ina da nauyi ne? ke Ι—azu da kika hau kaina ai bance kina da nauyi ba”

“To ae Ι—azu banice na hau kanka ba kaine ka Ι—aukeni ka Ι—aurani akan ka batare da nace inaso ba”

“To amma dana Ι—auraki wayace ki sakemin duka nauyinki harma da kama min…..”

Da sauri ta sanya hanu ta toshemai baki bataso ya faΙ—i abun da tayi masa, ita kanta batasan tayi masa haka ba alokacin tana wata duniyarne na daban. (Khair uwar gulma harkin baza kunnuwa kiji metayi ko, to bazakiji ba nima banji ba balle ke?)1

“INASONKA!!!” Zahrah tafaΙ—a cikin wata irin murya me Ι—auke da tsananin shauΖ™i.

“Nima INASONKI!!!” shima yafaΙ—a cike da tsananin Ζ™auna, wani irin kallo sukayiwa junansu, cike da sha’awar juna suka sake haΙ—e bakinsu waje Ι—aya…….

(Zahrah da Doctor fa sun zama one love ga soyayya ga jaraba, doctor ya koya mata?)Kwanansa biyu acikin asibitin kafun ya samu ya dawo cikin hayyacinsa, sai dai kuma tunda ya dawo hayyacinsa baice da kowa komai ba, ko su Dad Ι—insa da sukeyi masa ya jiki, da kai kawai yake amsa musu, shikaΙ—ai yasan meyakeji acikin jiki da zuciyarsa.+

Zaune yake akan gadon asibitin yayi jigum, babu wani abu dake yi masa daΙ—i acikin duniya,  Matakin daya Ι—aukarwa zuciyarsa yayi masa tsauri sosai, a haΖ™iΖ™anin gaskiya yasan yaudaran kansa yake, cire soyayyar Zahrah acikin zuciyarsa, ba abu bane me sauΖ™i, yana sonta so sosai, so irin wanda ba a misaltashi,  so ne dayakai Ζ™ololuwa, ko ina acikin zuciyarsa tambarine na Ζ™aunarta, rumtse jajayen idanunsa yayi haΙ—e da sanya haΖ™uransa ya ciji laΙ“Ι“ansa, dai dai lokacin aka turo Ζ™ofar Ι—akin aka shigo, ko kallon bakin Ζ™ofar baiyi ba, balle yaga waye ne yashigo cikin Ι—akin.

Turus haka Afrah taja ta tsaya tana me Ζ™aremasa kallo,  mugun tsoronsa takeji, yanzuma Momynsa ce tace tazo ta duba ya jikin nasa shiyasa ta shigo, amma da bazata shigo ba.   Karambani irin na Afrah yasanya taΙ—an matsa kusa dashi cikin murya me sanyi tace.

“My Dear yajikin naka?”3

Da sauri ya buΙ—e jajayen idanunsa ya watsa mata su, take jikin Afrah ya soma rawa, tsananin tsanarta tahango acikin Ζ™wayar idanunsa,  yanayin yanda taga idanunsa sunyi ja shi kaΙ—ai ya isa firgita mutum, da sauri ta juya tafice a Ι—akin,  zuciyarta cike tab da sabon tsoronsa, gani take kamar zai tsaidata ya jibgeta, aitana tsintar kanta a wajen Ι—akin tashiga sauΖ™e ajiyar zuciya akai akai…

Shikuwa idanunsa ya maida ya rufe, wani irin Ι—aci yakeji acikin maΖ™oshinsa, yayinda ransa yakai Ζ™ololuwa wajen Ι“aci, hakanan shikam Allah ya Ι—aura masa tsanar yarinyar dako sunanta ma baisani ba, anzo anwani Ζ™aΖ™a ba masa ita amatsayin mata.       “Shegiya me Ζ™ananan idanu, daganinta munafukace” yafaΙ—i haka acikin zuciyarsa, jingina kansa yayi da bango, yaci gaba da tunanin yanda zai samawa rayuwarsa salama…5

*****

Gyara zama Husnah tayi  haΙ—e da miΖ™a duk wata nutsuwarta ga Zahrah.

“Kina mamakina ko Husnah? nasan dole dama zakiyi mamaki, amma kuma idan kika yi tunani me kyau tawani wajen baizama abun mamaki ba”

Zahrah tafaΙ—i haka da iyaka gaskiyarta, saboda ita yanzu tama daina mamakin kanta kwata kwata.

“Dole ne zanyi mamakinki Zahrah, wani irin so ne haka kikeyiwa   wanda ya tozarta rayuwarki?  bazan tuna miki abun da Zaid yayi miki ba, saboda na tabbata har kikoma ga Allah  bazaki daina jin ciwon abun da Zaid yayi miki acikin zuciyarki ba, a gaskiya bana ma tunanin kinacikin hankalinki Zahra, saboda baidace ace kina da aure akanki, kuma kina zancen wani daban ba mijin kiba”  

Husnah tafaΙ—i haka cikin yanayi dake nuna ranta ya Ι—an Ι“aci da jin kalaman Zahrah.3

Wani irin murmushi Zahrah tayi haΙ—e da sanya hanunta akan kafaΙ—an Husnah.

“Nasan dole zakiji haushina Husnah, amma kafun ke kiji haushina ninafara jin haushin kaina, ada nayi tunanin cewa banda hankaline, amma daga baya nagane cewa  so so ne,  kinsani nima kuma nasani so bayashawartarka kafun yashiga zuciyarka, so baruwansa da anzalunceka ko kuma kazalunta, shidai so so ne a kullum haka yake baya tambayarka shawara idan zai saka ka aikata wani abu, hakanan baya kuma sanjawa, shi Ι—inne dai akullum akuma ko da yaushe yana nan,        nasan Zaid yacutar dani,  amma kuma ina matuΖ™ar jin tausayinsa acikin zuciyata,   tabbas da ace inada iko ko wani hali dana sanjawa Zaid rayuwarsa nasan Allah zai bani lada” Zahrah taΖ™are maganar tana me cije laΙ“Ι“anta.1

STORY CONTINUES BELOW

Kallon baki da hankali Husnah tashigayiwa Zahrah.

“Ki sanja masa rayuwa fa kikace, anya kuwa kina cikin hankalinki Zahrah?” Husnah tafaΙ—a cike da mamaki.

“Inacikin hankalina Husnah ban haukace ba, ada nima nayi tunanin ko na haukace ne,sai kuma nagane bahaka bane”    hanunta ta Ι—aura akan  hanun  Husnah..

“Zaid bai taΙ“a tunanin haka zata kasance dashi ba Husnah, yayimini fyaΙ—e ne bisa bin  umarnin  zuciya dakuma gangar jikinsa da yayi,  yamin fyaΙ—e ne saboda yanaji ajikinsa cewa sha’awata ce ke damunsa, Allah ba azzalumin kowa bane saidai wanda yazalunci kansa,  ada nayi kuka sosai Husnah, nayi nadaman sanin Zaid acikin rayuwata, sannan kuma naji Ζ™unci da ciwon abun da ya aikata a gareni,  ada inatunanin cewa fyaΙ—en da Zaid yayi mini yatashi abanza, saboda banida wani wanda zai tunkaresa, har yaΖ™watarmin haΖ™Ζ™ina a wajensa…”   Ι—an tsagaitawa da maganar tayi haΙ—e da sakin wani murmushi,  cigaba tayi da cewa.1

“Nasani ko badaΙ—e ko bajima Allah zaimin sakayya, amma kuma bansan tawani hanya zai saka minba,  ashe tahanyar da Zaid yabi ya yaudareni ta hanyar Allah zai sakamin, kinsan wace hanyace?”   Zahrah ta tambayi Husnah.

Cike da zaΖ™uwa Husnah ta girgiza kanta alamar  “A’a”

“SO! naso Zaid so me tsanani, shine namijin dana fara bawa soyayyata tunda nazo duniya, haka kuma shine namijin da na aminta dashi Ι—ari bisa Ι—ari, bantaΙ“a tunanin cewa ze iya rumtse idanunsa yaketamin haddina cikin rashin tausayi da imani, hadda wulaΖ™anci ba,  nayi kuka harnagaji alokacin da Zaid ya lalatamin rayuwata,   Zaid yayi amfani ne da soyayyar da nakeyi masa wajen cutar dani,   Allah daya tashi sakamin Sai yasanya masa soyayyata me tsanani acikin zuciyarsa, yakuma nesantashi dani,  tsananin soyayyar da Zaid kemin shine sakayyar da Allah yayimini,  sannan kuma alhakina, na bibiyarsa sosai,        Zaid yana sona, son da bazaiyi mishi amfani ba, nayi masa nisa tayanda bazai iya samuna ba,  inada tabbacin cewa ayanzu yana cikin tsananin halin nadama wacce bazata amfaneshi da komai ba”

Ɗan numfasawa Zahrah tayi haΙ—e da duban Husnah. 

“Kina ganin Zaid yacancanci samun mace mai hankali da nutsuwa, wacce zata gyara masa rayuwa ko a’a?”  ta tambayi Husnah.

Harara Husnah ta wurga mata haΙ—e da taΙ“e bakinta…   

“Mazinaci, fasiΖ™i, Ι—an giya, ta’ina ya dace da mace me hankali da nutsuwa, ae sai dai ko yasamu wata daga cikin karuwan Ζ΄an matansa ya aura, sai su Ζ™are rayuwarsu a haka, amma wace me hankalince zata yarda ta aureshi”  Husnah tafaΙ—i haka da iyaka gaskiyarta.5

Murmushi me ciwo Zahrah tayi haΙ—e da cije laΙ“Ι“anta, kanta ta girgiza kana tace….

“Zaid bai cancanci zama da karuwaba Husnah”

Dasauri Husnah takalleta haΙ—e da cewa.

“Meyasa kikace haka?”

“Sauyin rayuwa yake buΖ™ata, dole yana da buΖ™atar wacce zata tsaya akansa ta basa kulawa, zuciyata tanayimini wani hasashe na daban”     Zahrah tafaΙ—i haka tana me kafe Husnah da idanu.

Harara Husnah takuma wurgawa Zahrah haΙ—e da taΙ“e baki,  cikin takaici tace.

“Amma dai kinsan mazinaci sai mazinaciya  Ζ΄ar uwarsa ko, taya zakina haΙ—a kamilar mace da wani taΖ™adarin Ι—an iska Zaid, cab hmm gwamma ma kisake tunani, me kuma zuciyarki take hasasho miki akan sa?” Husnah ta kuma tambaya.

“Kece zaki iya Husnah, banda wata wacce ta wuceki, banda wata Ζ™awa sama dake,  amma bansan yazaki Ι—au abun ba amma nasan…..”3

“Mekike son cewane wai Zahrah? naga kinata wani kwalo kwalo, ki faΙ—i abun da kikeson faΙ—i kai tsaye”   Husnah tafaΙ—i haka ta hanyar katse Zahrah daga maganganun da takeyi.

STORY CONTINUES BELOW

“Ke yakamata ki auri Zaid Husnah, ko saboda nima, zaki samu lada sosai ba Ι—an kaΙ—an ba….”4

Cikin tsananin mamaki  Husnah tamiΖ™e tsaye daga zaunen da take, wani irin kallo tashiga yimawa Zahrah, cikin wata irin murya dake Ι—auke da tsananin Ι“acin rai da takaici tace.

“Ni” tanuna kanta da Ι—an yatsarta.  “Allah ya sauwaΖ™emin, bantaΙ“a tunanin zaki zomin da irin wannan zancen ba Zahrah, ashe dama bakyasona, bakya Ζ™aunata?  nagode Ζ™warai da kikanunamin hakan adai dai wannan gaΙ“an,   amma inaso kisani idan mafarki kikayi cewa ni Husnah na auri Ι—angiya mazinaci to kigaggauta yin sadaka!”  taΖ™are maganar cike da Ι“acin ran abun da Zahrah ta gaya mata…

Haka Husnah ta suri jakarta tayi tafiyarta Zahrah naΖ™iranta ko waiwayowa batayi ba, balle ta tsaya sake sauraranta.1

Jingina bayanta tayi dajikin wata bishiya wanda suke zaune a Ζ™asanta,  wasu siraran hawayene suka gangaro takan kumatunta.

“Kowa kallon mahaukaciya yakeyi mata, to sai yaushene wasu mutanen zasu gaskata cewa soyayya ba Ζ™arya bane? sai yaushene wasu mutanen zasu gane cewa ita soyayya babu ruwanta da illa ko aibin mutum? menene laifinta don taji tausayin Zaid? So baΖ™arya bane, kuma duk inda so yake akwai tausayi, haka kuma akwai tsananin sha’awa.”      Ƙaran wayartane ya katse mata tunanin da takeyi,  dasauri ta share hawayenta haΙ—e da Ι—aukar wayar takara akan kunnenta..3

“To” kawai naji tace haΙ—e da jefa wayarta ta acikin jaka, tashi tayi daga inda take zaune haΙ—e da gyara mayafinta,   jakanta ta Ι—auka ta nufi inda Dr.Sadeeq ke jiranta. 

 

Tun daga nesa daya hangota yaketa zuba murmushi, komai na Zahrah’nsa me kyaune, tafiyanta ma kaΙ—ai abun Ι—aukar hankali ne, duk da cewa ba dagangan take hakan ba, haka asalin takunta yake Ι—auke da nutsuwa, bawai ita ta Ζ™irΖ™iri hakan saboda burgewa ba.6

BuΙ—e murfin motar tayi ta shiga bakinta Ι—auke da sallama,   lumshe idanunsa yayi haΙ—e da kamo hanunta yasanya acikin nasa hanun cike da nutsuwa yake murza Ζ΄an yatsunta.

“Nayi missing wannan kyakkyawar matar, nayi missing wannan kyakkyawar fuskan, haka kuma nayi missing wannan daddaΙ—an jiki me laushin, nakumayi missing wannan tausassun laΙ“Ι“an masu daΙ—in sucking,  kuma ma nayi missing wasu abubuwana wanda suke sani  nishaΙ—i  sosai  suke kuma..”  da sauri tasa hanu ta toshemasa baki haΙ—e da shagwaΙ“e masa fuska..

“Ni dai dan Allah kayi shiru!” tafaΙ—i haka a sangarce.

“Ni dai gaskiya naΖ™i wayon bazanyi shiru ba saina Ζ™arisa!”  yafaΙ—i haka cikin yanayi na  kwaikwayon maganarta.

Ɗan Ι“ata fuska tayi haΙ—e da sanya hanu ta shafi Ι—akalallen cikinta. 

“Yunwa nakeji sosai fa, rabona da abinci tun breakfast”

Ɗan waro kyawawan idanunsa dake Ι—aukar hankalinta waje yayi. 

“Meyasa kikeson barin kanki da yunwa ne?  kinsan fa bazan yafe miki ba idan har kika cutarmin da unborn Ι—ina” yayi maganar yana me kafeta da idanunsa.

Zaro idanu Zahrah tayi haΙ—e da kai hanunta kan cikinta da sauri, ta shafa wai ko zataji tudu.

“Unborn fa kace? badai ajikina ba?” tayi tambayar cike da zaΖ™uwar jin amsarsa da alama taΙ—an tsorata da kalaman nasa.

“Yes Unborn  Ι—ina dana sa miki daren jiya mana, banaso wani abu yasameshi seriously!”

Wani Ζ™aΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya ta sauΖ™e haΙ—e da jingina bayanta da jikin kujeran motar, gaba Ι—aya ya faΙ—ar mata da gaba.3

“Ita da take tsananin tsoron haihuwa, tun yanzu yafara mata wani zancen unborn”   tafaΙ—i  haka acikin zuciyarta..

“Ya naga duk kin wani firgice ne haka, bakyason baby ne?” yatambayeta adai dai lokacin da yake tada motar.

STORY CONTINUES BELOW

“A’a”   kawai tafaΙ—a murya a sanyaye.  Baice da ita komaiba yaja motar suka fice daga cikin makarantar…

Direct wani hotel suka nufa don cin abinci, a cewarsa bazai iya haΖ™uri har sukoma gida batare da tasawa cikinta wani abuba.1

Bata iya cin komai acikin hotel Ι—in ba, sai pepper meat da kuma kunun aya kawai.. Koda suka koma gida tuni bacci ya cika idanunta, kwana biyunnan sosai take ebo gajiya amakaranta,  da ta dawo kuma tayi wanka shikenan sai bacci.     Yaukam basu dawo da wuri ba sai gab da magriba, saboda haka bata ba bacci…    Wanka tayi da ruwan Ι—umi take taji gajiyan yasauΖ™a daga jikinta..1

“dogon wando na  pencil jeans ta sanya ajikinta, sai kuma wata riga wacce tsayinta yakawo har gaba da guiwanta, gefe da gefen rigan atsage suke har wajen ciki, gaban rigar kuwa akwai aninaye masu kyau, rigace me kyau irin wacce ake Ζ™ira da  shirt gown (my favorite)   sosai rigannan tayi mata kyau ajikinta yayinda hips Ι—inta kuwa suka bayyana afili,  kasan cewar rigar nada tsagu ta kowani Ι“angare dama da hagu,  batayi Ζ™oΖ™arin kame dogon gashinta ba, tazura lufaya haΙ—e da hawa kan sallaya ta gabatar da sallan magriba.

Tana idar da sallan ta miΖ™e haΙ—e da fita zuwa falo.     BuΙ—e Ζ™ofarta yayi daidai da shigowansa cikin falon, shima dawowarsa kenan daga masallaci.

“Waw!!!  Kinyi matuΖ™ar yin kyau sosai fiye da kullum” yafaΙ—i haka  yana me ware mata duka hannayensa alamar tataho zuwa garesa..

Wani irin sanyin daΙ—i taji acikin zuciyarta lokacin da taji kalamansa, babu musu ta Ζ™arasa  garesa haΙ—e faΙ—awa cikin Ζ™irjinsa.

Kansa yaΙ—aura akan wuyanta haΙ—e da sanya harshensa yasoma yawo dashi yana lashe fatar wuyanta. Hanunsa ya Ι—aura adai dai kan hips Ι—inta,   cike da zolaya yace.

 

“Barin taΙ“a naji ko ciko akayi, anaso a yaudareni”

Dariya ne yakamata. Cewa tayi

“Allah ya sauwaΖ™e inyi cikon hips, taΙ“a da kyau kaji hips Ι—ina ne da Allah yaban bawai soso ba”

Shima dariya yayi haΙ—e da sake matseta acikin jikinsa.

“Nasani to ko kema kina Ι—aya daga cikin mata masuyin cikon hips Ι—in tunda ai naga mata sunayi sosai”3

Da sauri ta Ι—ago ta kallesa lokaci guda ta Ι“ata fuska.

“Wato mata kake kallo sosai idan kafita ko? harkasan ana cikon hips, hmmm thank you”  tafaΙ—i haka tana me Ζ™oΖ™arin zare jikinta daga nashi..

Da sauri yasake matseta ajikinsa haΙ—e da tausasa muryarsa.1

“Tuba nake madam, amma nisam mata basa gabana, inadake mezanyi da wata kuma daban, ke kaΙ—ai ce kinkuma isheni,  amma kinsan ba abun mamaki bane dan nasan hakan, saboda  yanzu hakan ya yawaita sosai, wasu mata basa haΖ™uri da surar da Allah yayi musu, dole wai sai sunyi ciko, inakaranta labarai, ina kuma gani a Instagram,  amma kema kinsan baruwana da duk wata mace ina da me daΙ—ina mezanyi da wata me Ι—aci!”  yafaΙ—i haka cike dason shagwaΙ“ata.2

Aikuwa take ta hau dariya sosai taji daΙ—in kalamansa, amma kalman me Ι—acin nan yabata dariya sosai, ko wace macece me Ι—aci oho.  

(Please maza kuna faΙ—awa matayenku kalamai masu daΙ—i, koda ita Ι—in bata da wani kyau, ka hure mata kunne kace ai ita kyakkyawace, wallahi zataji daΙ—i sosai, kai inda halima kadinga Ζ™iranta da sunan me daΙ—i??wallahi yanzun sai gaka ranta yayi fari Ζ™al, kuma always zakaga tana cikin farinciki, wayyo wayaga anΖ™ira su O’O da sunan me daΙ—i, ai nasan sai sunkusa sumewa  saboda daΙ—i???)2

Zama sukayi akan kujera haΙ—e da jawota ya Ι—aurata akan cinyarsa, kansa yacusa acikin Ζ™irjinta,  bayan ya Ι“alle aninayen dake jere agaban rigarta,  sosai Ζ™amshin dake fitowa acikin Ζ™irjinta yake yi masa daΙ—i, yanason Ζ™amshinta, domin kuwa yana sa masa nutsuwa sosai. 

Lumshe idanunta tayi, tana mejin daΙ—in kissing Ι—inta da yakeyi a Ζ™irjinta, hanunta ta sanya acikin gashin kansa tana  yamutsawa a hankali.      Ƙaran wayarsane yakaraΙ—e musu kunnuwansu, akasalance Dr.Sadeeq ya jawo wayartasa batare daya duba wanda ke Ζ™irannasa ba ya kara wayar akan kunnensa.    Waro manyan manyan  idanunsa waje yayi haΙ—e da cewa

“Dagaske kake?” 

Banji me wanda yaΖ™irasa a wayar ya faΙ—a masa ba saiji nayi kawai yace

“Okay ganinan fitowa.”

Kallonsa Zahrah tayi,  tanameson jin Ζ™arin bayani daga bakinsa.

“Lumshe mata idanunsa yayi haΙ—e da Ι“uΙ—esu  alokaci guda.

“Friends Ι—inane sukamin surprise wai suna waje, banaje na shigo dasu, please mintina kisanja wannan kayan kinji, ina kishinki sosai banason kowa yakallemin ke!” yaΖ™are maganar yana wani lumshe idanu, domin kuwa cike yake da shauΖ™inta.

Murmushinta me kyau tayi masa haΙ—e  da tashi daga kan cinyarsa tana cewa.

“Yanzu kuwa zan sanja kayan.” 

Ɗaki ta wuce shikuma yayi waje don shigo da abokansa.

Zama tayi akan gado bayan ta sanja shigarta zuwa riga da sket na material marar nauyi takuma yane jikinta da mayafi,      tanajin hayaniyansu acikin falon.

“Maza kenan wai nan su fa taΙ—i suke, amma kuma yawancin zancen nasu kama yake da musu” tafaΙ—i haka acikin zuciyarta.    Bata ida zancen zucin da take ba,  Dr.Sadeeq ya shigo cikin Ι—akin.

Hanunta yakamo haΙ—e da kai mata sumbata a goshinta.

 

“Ko wani irin kaya kika sanya sai sunyi miki kyau, kyau ajininki yake  Ζ΄an mata na!”  yafaΙ—i haka yana me Ζ™are mata kallo.

“Ζ³an mata kuma?” ta tambayeshi tana Ι—an murmushi.

“Eh mana Ζ΄an matace ke a wajena ae har gobe, kuma ke sabuwace a wajena, tunda har yanzu bangama lashe zuma na ba”  yafaΙ—i haka yana me kashe mata idanunsa Ι—aya.

Kunyansane ya kamata,  amma babu yanda ta iya shidai duk irin kalamansa kenan.

“Ki kawowa baΖ™inmu drinks kinji”

“To” Kawai tacemai.

A tare suka fita ita tayi hanyar kitchine shikuma yayi cikin falon..

Hanunta Ι—auke da wani Ι—an madaidaicin trey wanda ke Ι—auke da kayan drinks da kuma Ζ΄an madaidaitan glass cups tafito daga cikin kitchine Ι—in,       kanta aΖ™asa tanufo cikin falon saida takawo cikin falon kafun ta Ι—ago kanta fuskarta Ι—auke da Ι—an murmushi,     wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, lokaci guda idanunsu ya sauΖ™a acikin na juna, take ta saki trey Ι—in dake hanunta yafaΙ—i Ζ™asa, Ζ™aran faΙ—uwarsa yajawo hankalin gaba Ι—aya waΖ΄anda suke cikin falon……Da sauri Dr.Sadeeq yataso ya taho gareta, durΖ™usawa yayi yashiga tayata tattare wajen, saboda har wasu daga cikin cups Ι—in dake kan tray Ι—in sun face. Bisa tsautsayi ta zo Ι—aukan wani fasashshen cup kwalba ya caketa a Ζ΄ar yatsar hanunta, take ta saki wani Ι—an Ζ™aramin Ζ™ara, cike da kulawa Dr.Sadeeq yace.+

“I’am sorry kibi a hankali, muga hanun yayi jini ne?” yaΖ™are maganar yana me kama hanunta wanda kwalban yasoketa.

Murmushin Ζ™arfin hali tayi haΙ—e da cewa

“Yayi jini amma baso sai ba” hanunta Dr.Sadeeq yakama yashiga hura mata iskan bakinsa ahankali, yama manta da cewa basu kaΙ—ai bane a cikin falon.

“Sannu amaryarmu, munsa kin yanke da Ζ™walba ko, i’am really sorry” wani daga cikin abokan Dr.Sadeeq yafaΙ—i haka yana Ι—an murmushi.

Murmushi itama ta Ζ™aΖ™alo haΙ—e

da girgiza kanta, alamar

“bakomai”

“Tashi ki gaishesu sama sama ae duk sune silar jin ciwonki” Dr.Sadeeq yafaΙ—i haka yana me miΖ™ar da ita tsaye.

Ɗan matsawa tayi wajen da suke zaune tashiga gaidasu cikin sassanyar murya, amma bata yarda ta kalli inda yake ba, shima kallo Ι—aya yayi mata ya sadda kansa Ζ™asa, “ItaΙ—ince dai duk da taΖ™ara kyau hakan baihanasa ganeta ba” yafaΙ—i haka acikin zuciyarsa, zuciyarsa ne ke ingizasa daya Ι—aga idanunsa ya kalleta, amma kuma yaΖ™i bin umarnin zuciyartasa saboda yasan hakan baidace ba.

Dr.Sadeeq dakansa yakawo musu wani drinks Ι—in ita kuwa ta wuce Ι—akinta..

Zama tayi akan gado haΙ—e da sauΖ™e wata irin ajiyar zuciya me Ζ™arfi, bazata taΙ“a manta wannan fuskarba, tabbas shine.

“To meya kawo JABEER gidanta kuma? kodai shima abokin doctor Ι—in ne?”

tayi mawa kanta duka wa Ζ΄annan tambayoyin, ganin da tayi cewa tunani bazai fishsheta bane, yasa ta miΖ™e ta Ι—auko Ι—an Ζ™aramin Al’Qur’ani’n ta tashiga karantawa a hankali…

Yanashigowa cikin Ι—akin yajingina bayansa da jikin Ζ™ofa haΙ—e da sauΖ™e ajiyar zuciya.

Kallonsa tayi haΙ—e da Ι—an sakin murmushi.

“Yadai sai kace wanda yayi gudu?”

“laifine idan nayi gudu dan nazo naga matata?” shima yatambayeta yana me tsareta da idanunsa.

“A’a, amma ae abun bana gudu bane, tunda dai batashi sama zanyi ba inanan tare dakai” tafaΙ—i haka tana me gyara zamanta.

Takowa yayi yaΖ™araso gareta, zama yayi gab da ita haΙ—e da Ι—aura kansa akan wuyanta.

“Ya hanun naki?” yatambaya yana me Ζ™oΖ™arin kamo hanun nata wanda taji ciwo dan ya duba.

“Da sauΖ™i bayama min zafi sosai”

Iskan bakinsa ya hura ahanun kafun yaΙ—ago ya kalleta.

“Amma nayi mamaki Ζ™warai da abun daya faru Ι—azu, ko dai tuntuΙ“e kikaji ne?”

STORY CONTINUES BELOW

Da sauri ta shiga kaΙ—a kanta. “Bankula da gabana bane alokacin danake tafiya shine kawai na buge da kujera” batasan sanda ta mulmulo wannan Ζ™aryan ta rantaΙ“a masa ba.

Kansa ya jinjina haΙ—e da sanya hanunsa ya rungumota zuwa jikinsa.

“Nagodewa Allah ma dayasa bakece da kanki kika faΙ—i ba, tray ne kawai ya faΙ—i, da bansan inda zansa kaina ba” yafaΙ—i haka yana me shafa gashin kanta da hanunsa.

Ɗan shirune yashiga tsakaninsu kowannensu da abunda yake saΖ™awa acikin ransa, tabbas bazata iya haΖ™ura ba sai ta tambayeshi waye Jabeer agareshi, to amma tace masa me? tace masa me ya haΙ—asa da Jabeer tsohon saurayinta ko kuma me? bari dai tayi masa wani wayon, tafaΙ—i haka acikin ranta…

Ɗan sake gyara zamanta tayi haΙ—e da cewa. “Amm wai duka waΖ΄annan abokanka ne?”

Murmushi yayi batare daya Ι—ago ya kalleta ba yace “Eh”

Kanta ta jinjina haΙ—e da sake cewa “Dukansu fa nake nufi”

Murmushi yakumayi saidai a wannan karon ya Ι—ago idanunsa ya kalleta.

“Eh dukansu abokaina ne, meya faru?” yatambayeta yana me tsareta da idanunsa..

Murmushi ta Ζ™aΖ™alo haΙ—e da cewa

“Babu ko mai kawai dai naga sunyi yawa ne, kuma naga wasu daga cikinsu banga fuskokinsu a wajen bikinmu ba shiyasa”

“Ae mu maza ba irinku bane munfiku yawan jama’a, wasu daga cikinsu basu samu daman zuwa bikinmu ba shiyasa bakisansu ba, kamar Jabeer baisamu halattaba saboda baya Nigeria yana Polland yana karatu, kuma baijima da dawowa ba, sauran kuma wani uzururruka ne suka hanasu zuwa, kinsan maza da sabgogi” yafaΙ—i haka yana me sake kwanciya acikin jikinta.

Yanzu tasamu amsar da takesonji cikin sauΖ™i, kenan dama Jabeer baya Nigeria ne shiyasa bainemeta ba, da sauri ta yi watsi da tunaninsa haΙ—e da Ζ™oΖ™arin zame Jikinta daga cikin nasa jikin.

Ƙara rungumeta yayi batare daya bata daman tashi ba, kallon cikin Ζ™wayar idanun juna suka shigayi, kallon tsananin SO Dr.Sadeeq keyi mata, yayinda ita kuma nakasa fassara wani irin kallo takeyi masa, na Ζ™auna nane ko na SO oho, Lumshe idanunsa yayi haΙ—e da buΙ—esu alokaci guda, yanayin yanda taga idanun nasa sun mareraice shiyasanya taji tsikar jikinta ya tashi, aduk sanda ta kalli cikin idanunsa takanji wani abu na ratsa har cikin Ι“argonta, hakanne ma yasa bata Ι—aukan lokaci me tsawo tana iya kallon cikin idanunsa, sosai idanunsa keyi mata kyau.

“Baby bacci nakeji!”

yafaΙ—i haka cikin murya me sanyi, yana me sake lumshe idanunsa.

“Ɓacci a wannan lokacin? Yanzu fa lokacin sallan isha ne”

ta faΙ—i haka cike da mamakinsa, tasan dai shiba mutum ne dayake da saurin bacci ba.

Hanu yasa yaΙ—an murza idanunsa, kansa kawai ya kaΙ—a mata batare dayace da ita komaiba yakoma jikinta ya kwanta. Yana lumshe idanunsa ladanin masallacin kusa da gidansu yasoma kwaΙ—a Ζ™iran sallah’n Isha. Jiki babu Ζ™wari haka yayi alwala yawuce masallaci..

Koda ta idar da sallah batayi yunΖ™urin tashi akan sallayan ba, zama tayi tana me rero karatun Al’Qur’ani ahankali.

Yana shigowa ta rufe Al’Qur’ani’n domin dama takai Ζ™arshen suran da take karantawa.

Direct bathroom ya wuce, tanajin Ζ™aran ruwa tasan wanka Ζ΄akeyi.. Bawani jimawa sosai yafito daga shi sai towel Ι—aure aΖ™ugunsa, kallo Ι—aya tayi masa ta Ι—auΖ™e kanta, har yau bata iya jure ganinsa a haka, tashi itama tayi ta wuce bathroom Ι—in donyin wanka.

Dogon wandon jeans kawai ya sanya ajikinsa haΙ—e da feshe jikinsa da turarensa me daΙ—in Ζ™amshi.. Kwanciya yayi lamo agadon haΙ—e da lumshe kyawawan idanunsa.

STORY CONTINUES BELOW

daga ita sai wani Ι—anΖ™aramin towel tafito Ι—aure ajikinta, yanzu kam bata wani jin kunyarsa sosai, tana iya fitowa gabansa a haka, sai dai idan taga ya kafeta da idanu, sai taji gaba Ι—aya tayi wani irin da ita. Kallonta yayi yakuma sake lumshe idanunsa, yayi imani idan yaci gaba da kallon wannan haΙ—aΙ—Ι—iyar surar tata zata iya zautar dashi.

Turare kawai ta shafa ajikinta, ko sleeping dress batasanya ba, yau kuma da towel takeson kwana, kashe musu wutan Ι—akin tayi ta kunna musu na bacci, wanda bashida haske sosai.

A maimakon tanufi gefensa ta kwanta, sai ji yayi ta haye kansa.

“Wayyo mama lutiya zata karyani!” yafaΙ—i haka aΙ—an shagwaΙ“e.

Sake sakar masa duka nauyinta tayi akansa, haΙ—e da cusa kanta cikin wuyansa.

“Kai nauyinka baisa na karye ba sai nine zan karyaka, ko kamanta kafini nauyi” taΖ™are maganar tana me manna masa wani irin hot kiss akan wuyansa.

Lumshe idanunsa yayi sosai yaji kiss Ι—innata ya ratsa shi.

“Wai yaushe kika zama haka ne princess?” yatambayeta, don harga Allah kwana biyun nan yana mamakinta.

Cikin rashin fahimtar maganan nasa tace “Bangane ba”

“Naga ne kindaina jin kunyana, sannan kuma nima da nake da kunyan nema kike ki lalatani ki maidani marar kunya”

Cizo takaimasa akan Ζ™irjinsa, wanda yasanya sa sakin wata Ζ΄ar Ζ™ara.

Yana dariya yace

“To Ζ™arya nayi ai gaskiya nafaΙ—a, yanzu bakyajin kunyana ko kaΙ—an, har kaya kike cirewa a gabana…”

Wani cizon takuma kaimasa batare da ta bari yaΖ™arisa abunda yakeson faΙ—a ba, da sauri yatureta takoma Ζ™asansa shikuma yazama yana samanta, yayi mata rumfa da kirjinsa, duka hannayenta yakama yariΖ™e acikin nasa.

Cikin dariya ta soma Ζ™oΖ™arin Ζ™wace kanta daga jikinsa don talura cizon da tamai yakeson rama wa.

“Dan Allah kayi haΖ™uri bazan Ζ™araΙ“a!” tafaΙ—i haka aΙ—an tsorace dan ta lura dagaske cizonta zaiyi.

“Ae babu maganar haΖ™uri yarinya, aΖ™irji kika cijeni, nima kuma dan haka aΖ™irjinki zan cijeki” yafaΙ—i haka yana me warware towel Ι—in dake jikinta.

Cikin dariyan data kasa hanashi fitowa tashiga yi masa magiya amma yace sam shi sai ya rama.

Yana Ι—aura bakinsa akan Ζ™irjinta, tayi shiru lokaci guda ta shiga sauΖ™e ajiyar zuciya akai akai, harwani lumshe idanunta take tsabar daΙ—in abun da yakeyi mata da takeji, shikuwa dagangan yayi mata haka so yake ya tsokalota sai yayi mata wayo yayi baccinsa, hanunta tasanya ta Ι—ago kansa, wani irin kallon tayi masa wanda ya rikirkitasa, bakinsu ta haΙ—e waje Ι—aya, atare suka soma sucking lips Ι—in juna, shida yake shirin mata wayo sai gashi ya susuce alokaci Ι—aya, har yazo yafita Ι“uΖ™ata….. Bargo yaja ya rufe musu duka jikinsu, yana kwance akanta bacci me daΙ—i ya Ι—aukesu…..

*****

*_ZAID_*

Tunda aka sallamosu daga asibiti baice da kowa Ζ™ala ba, haushin kowa yakeji, tuΖ™uΖ™in baΖ™in ciki zuciyarsa keyi masa, ji yake yatsani kowa, bayamaso wani yashigo cikin lamarinsa..

Zaune yake a cikin falonsa, dagashi sai 3 guater jeans ko riga baidashi duk da kuwa irin sanyin da ake busawa a gari amma shi haka yake zaune a tuΙ“e, bawai kuma don bayajin sanyinba taurin kai dana zuciya ne kawai irin nasa ya hanasa suturta jikinsa.

Ƙafansa nakan rug yayinda kansa ke kalllon sama ya lumshe duka idanunsa, sake muskutawa yayi akaro na barkatai, haΙ—e kuma da Ζ™ara Ζ™anΖ™ame idanunsa da suke a lumshe, waishi adole so yake yayakice tunanin Zahrah acikin zuciyarsa, amma duk yanda yaso cire tunanin nata acikin ransa ya kasa, hanu yasa ya Ι—an bugi kansa da Ζ™arfi, dai dai lokacin Afrah tafito daga cikin Ι—aki daga ita sai wata Ζ΄ar Ζ™aramar riga dake sanye ajikinta, ko guiwarta rigan bata wuce ba.

Wani irin Ζ™amshin turaren dayaji acikin hancinsa ne yasanya sa buΙ—e idanunsa, ya watsa su akanta, kallonta yashigayi daga sama har Ζ™asa. “gatanan dai kamar wata Ζ΄ar kaza amma shegiya sai fitinan tsiya” yafaΙ—i haka acikin zuciyarsa, saboda ya lura kanta yana rawa, nema take ta shigarmai rayuwa taΖ™arfin tsiya, kuma zaiyi maganinta ne.

Afrah kuwa zuciyartane tashiga dukan uku uku, tsoronsa ne yasake shiganta bama kamar yanda taga idanunsa sun juye sunyi jajur dasu, harta juya zata koma Ι—aki, saikuma ta tuno da shawarar da Ζ™awarta Asma ta bata, Asma tace mata ” Zaid Ι—an duniya ne yanason mata sosai, saboda haka tayi duk yanda zatayi ta shawo kansa ta hanyar nuna masa surarta a fili, idan ta nuna masa bata da kunya zasu dai dai ta” tunowa da waΖ΄annan kalaman na Asma yasa Afra taji tasamu Ζ™warin guiwa.. Sanja takunta tayi zuwa wani salo da ban, direct wajen dayake kishingiΙ—e ta nufa tana me motsa kowani gaΙ“a dake jikinta.

Bai taΙ“a yin zato ba saiji yayi Afra tafaΙ—o cikin jikinsa kamar wacce aka jefo, baikai ga buΙ—e idanunsa ba yaji ta saki wani irin munafukin Ζ™ara..

“Wayyo Allah Ζ™afa ta honey kataimakeni na karya Ζ™afa ta” abun da Afrah ke faΙ—a kenan cikin iyayi.

Wani irin kallon takaici Zaid keyi mata, waishi zata gwadawa bariki, tafaΙ—o kansa da gangan sannan kuma tana yi masa ihun banza wai yataimaketa.

Da sauri yasake maida kallonsa gareta alokacin da zuciyarsa ta Ζ™itsa masa wani abu akanta.

“Tabbas hakanne ma, sai yanzu yasake lura da ita, amma ba ya gwadata ya gani” yafaΙ—i haka acikin zuciyarsa..

Da Ζ™yar ya iya buΙ—e bakinsa yaΖ™ira sunanta “Afrah”

Dasauri Afrah dake yashe aΖ™asa tana kukan Ζ™arya ta Ι—ago kanta tana kallonsa jin da tayi yaΖ™ira sunanta. “Kodai Target Ι—ina yafara aiki ne?” ta tambayi kanta .

“Ba Ζ™iranki nake ba da bazaki amsa minba!” yafaΙ—a murya aΙ—an kausashe.

“Kayi haΖ™uri honey Ζ™afa ta ce kemin zafi shiyasa” tafaΙ—i haka cikin yanayi na shagwaΙ“a tana wani yayyarfe hannu, ita adole so take ya faΙ—a cikin tarkonta.

Cike da tsananin takaicin Ζ™iransa da sunan honey da takeyi yasanyasa rumtse idanunsa da Ζ™arfi, ji yake kamar yaje ya shaΖ™eta bazai saketaba harsai yaga bata numfashi, amma akwai abun da yakeson ganowa a tattare da ita dolensa saiya daure.

“Zo muga me yasamu Ζ™afartaki”

Jiki na rawa Afrah ta matso garesa dama haka takeso yace, tana matuΖ™ar so taganta akusa dashi, haΙ—a jiki dashi kuma shine burinta batun yau ba.

Hanu yasa ya kama Ζ™afarta ta, a hankali yashiga shafawa cike da wani irin salo, wayyo Allah Afrah dama haka takeso, ita kanta batasan sanda ta lumshe idanunta ba, wani irin daΙ—i takeji acikin jikinta, “Gaskiya shawarar Asma tayi aiki” tafaΙ—i haka acikin zuciyarta, cigaba yayi da shafa Ζ™afannata ahankali harzuwa wajen cinyoyinta, tuni ta narkemasa ajiki taΖ™ara kusanto da kanta garesa, hanu tasanya akan faffaΙ—an Ζ™irjinsa tashiga shafawa ahankali, duk iskanci irin na Zaid saida ya tsaya yana kallonta, tabbas yanzu ya gano abun dayakeson ganowa atattare da ita, wani irin baΖ™inciki da Ι“acin raine suka tokare masa maΖ™oshinsa.

“Hakan da Afrah keyi masa alamace dake nuna ita babaΖ™uwa bace a harkan tasan namiji kenan kome?” tambayar da yake tayiwa kansa kenan, shiba Ζ™aramin Ι—an iska bane, yanda Afrah keyi masa alama ne dake nuna cewa tasaba irin haka da wasu mazan. “Kenan ita Ζ΄ar iska ce?” still yakuma tambayar kansa. Hanunsa yasanya ya damΖ™i gashinta haΙ—e da miΖ™ar da ita tsaye, da fari ta Ι—an tsorita amma ganin irin kallon dayakeyi mata yasa taΙ—anji sanyi acikin ranta, ganin sunnufi hanyar Ι—akinsa yasa ta shiga sakin murmushi, daΙ—i taΖ™eji yau Allah zai cika mata burinta..

Suna shiga cikin Ι—akin yasanya hanunsa da Ζ™arfi ya yaga Ζ΄ar fingilan rigar dake jikinta, take komai nata ya bayyana, hankaΙ—ata yayi kan gado haΙ—e da soma yunΖ™urin zare belt Ι—in dake jikin wandonsa,, idanu Afrah ta zaro waje amatuΖ™ar tsorace, bata taΙ“a tsammanin haka daga garesaba ta Ι—auka kasheta zaiyi da soyayya amma meyake shirin yi matane haka “Dukanta zaiyi ne ko kuma turmusheta zaiyi batare dayatsaya sunΙ—anyin romancing juna ba?” waΖ΄annan tambayoyin sune suka cika zuciyarta fal…

(Me Zaid yakeyi hakane? hahhhh da’alama dai yau amarci za’aci agidan Baba Zaid, team Zaid karkuyi nisa saboda nan gaba kaΙ—an Zaid zai buΖ™aci taimakonku, yayinda komai ya wakana tsakaninsa da amarya, inaga dole saikun shigo cikin lamarin?)

Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 11 BY FATYMA SARDAUNA"