Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 5 BY FATYMA SARDAUNA

SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 5 BY FATYMA SARDAUNA

                 Www.bankinhausanovels.com.ng 

Dai dai ta Ι—aura hanunta kan handle Ι—in Ζ™ofar kenan, aka turo Ζ™ofar daga waje, cikin rashin sa’a Ζ™ofar ya bugeta a goshi, saurin ja da baya tayi haΙ—e da rumtse idanunta gam, ji takeyi tamkar ta shaΖ™esa ya mutu, ta tsani ganin kowani irin namiji ne a rayuwarta, musamman ma shi,domin kuwa yanayinsu yana ma ta shige da Zaid, kuma gani take tamkar kowani namiji irin halin Zaid garesa,,

“Ganinki tsaye anan yatabbatarmin cewa guduwa zakiyi, Miye ribarki a rayuwa idan kika gudu daga gaban i yayenki ? nasan duk inda zaki bazakiyi rayuwa mai kyauba, idan kika zaΙ“i tafiya can wata uwa duniya mai zaki tsinta? ina mai tabbatarmiki cewa babu wani abun da zaki tsinta sai, zallan takaici, dakuma Ζ™uncin rayuwa, zaman bariki kikeso kiyi? kokuwa zaman kanki kike so kiyi? ” da sauri taΙ—ago manya manyan idanunta dasuke cike tab da Ζ™walla ta watsa masa wani irin mugun kallo…

“Babu abun daya shafeka da rayuwata, idan naga dama nayi kowacce irin rayuwa ma baishafeka ba, duk ba kune kuka jefa rayuwata acikin matsanancin duhu ba, wallahi na tsani naji koda kalmar farkon sunan kune a cikin kunnuwana, ballan tana aΖ™ira sunan Namiji akusa dani, natsaneku! natsaneku!! ” wani irin kukane ya Ζ™wace mata maicin rai,

“Kacuceni Zaid! Kacuceni! natsaneka tsana mafi muni! mai nayi maka dana cancanci wannan sakamakon a wajenka? mai na aikata maka wanda yasanya ka cutar da rayuwata? bazan yafe maka ba Zaid! kacutar dani, karuguzamin duk wani buri nawa, ka tarwatsamin rayuwata, mai yasa saini kazaΙ“a maiyasa!!!” taΖ™are maganar cikin Ζ™araji da matsanancin kuka, tamkar wanda takama Zaid Ι—in a gabanta..

Wani irin mugun tausayin tane yaji ya daki zuciyarsa, haΖ™iΖ™a Zahrah abar tausayice, domin kuwa tanacikin wani hali wanda take buΖ™atar abokin rarrashi da kuma mai kwantar mata da hankali,,, juyawa kawai yayi yafice daga Ι—akin, domin kuwa jin kukanta yake har tsakar kansa.

Nurse yaturo tazo tayi mawa Zahrah alluran bacci, domin idan ba alluran bacci akayi mata ba yana da yaΖ™inin cewa kwana zatayi tana ruskar kuka..

Duk yanda yaso bacci ya Ι—aukesa, hakan ya gagara domin kuwa duk juyin da zaiyi wani irin matsanancin tausayin Zahrah ne ke cika masa zuciya, baisan wani irin tausayawa yake mawa Zahrah ba, amma tabbas yasan tausayinta da yakeyi, yayi Ζ™arfi a cikin zuciyarsa, da Ζ™Ζ΄ar dai yasamu ya yakice tunanin Zahrah, a cikin zuciyarsa ya samu yayi bacci, wanda rabin mafarkansa ya kasance na Zahrah ne…

Wanene Dr S.S. ?

Dr Sadeeq yakasance Ι—a na biyu a cikin gidansu, Alhaji KHABEER SARDAUNA shine mahaifinsa, Alhj Khabeer wanda ake Ζ™ira da Alhj Sardauna, mutum ne mai matuΖ™ar karamci da kuma kyautatawa na Ζ™asa dashi, hakan yasa talakawa suke matuΖ™ar sonsa, kasancewarsa Ι—an siyasa, Hajiya Habiba itace mahaifiyar Dr Sadeeq, mace ce itama mai tsananin karamci dakuma kyauta, tana da kyakkyawan hali wanda kowa yashaida hakan, Dr Sadeeq shine Ι—a na biyu a cikin gidansu, yanada yaya wacce ake Ζ™ira da Aunty Raliya, Aunty Raliya dai, tana aure ne a cikin garin Abuja, tana kuma zaune a unguwar Wuse Zone 2, bayan Dr Sadeeq a kwai Ζ™aninsa Samad, Samad dai baya zaune a Nigeria yana zamane a Australia, a can yake da karatunsa, tun Dr Sadeeq yanada shekaru 20, Allah yayiwa mahaifinsu rasuwa, mutuwar da ta matuΖ™ar girgizasu, amma babu yanda suka iya dole su Ι—auki dangana domin kowani bawa da kalan tasa Ζ™addaran.. yanzu tsawon shekaru biyu kenan Hajiya Habiba tana matsawa Dr Sadeeq, a kan cewa yafito da matar aure, amma abun yagagara, da anfara maganar aure sai abun yalalace, ko daga baya yace baison yarinyar, ko yace bata da nutsuwa, da haka dai magana zata Ι“alakuce,, yanzu ne Hajiyarsa ta hura masa wuta akan cewa lallai tabasa nanda kwana kaΙ—an yafito da matar aure dan bazata ci gaba da zuba masa idanu babba dashi ace bai aje iyali ba….

STORY CONTINUES BELOW

Washe gari..

Ƙarfe 3 da rabi na yamma Dr Sadeeq da kansa ya rubutawa su Zahrah sallama, domin ya fahimci cewa matuΖ™ar bai sallamesu ba, za a iya nemanta a rasa, bakuma zai so hakan ba.

Koda suka fito daga cikin asibitin, duk yanda yaso Zahrah tashiga cikin motarsa ya kaisu gida Ζ™iyawa tayi, dole haka yanaji yana gani suka tari mai taxi, baiyi Ζ™asa a guiwaba wajen shiga motar tasa ya rufamusu baya…

Suna isa bakin Ζ™ofar gida, idanun Zahrah ya sauΖ™a a dai dai wajen da Zaid yake faka motarsa kullum idan yazo, wani irin muguwar faΙ—uwar gaba taji, take kuma zuciyarta tayi rauni, kuka ne ya kuma Ζ™wace mata, da sauri tafice a cikin motar dagudu tanufi cikin gida,, saida Inna suka sallami mai taxi kafun suka lura da Dr Sadeeq dake tsaye a bayansu yana Ζ™arewa yanayin unguwar tasu kallo, “A’a Likita dama kana biye damune ?” Baffa ya tambaya washe da baki,,

“Eh Baffa ina biye daku, dama gani nayi yakamata ace nasan gidan saboda magungunan ta basu Ζ™areba, nakuma san basha zatanayiba matuΖ™ar ba’a tilasta mata ba”

“Ƙwarai kuwa likita ai taurin kai gareta, dole saida takurawa, to mushiga daga ciki mana ” Baffa yaΖ™are maganar yanamai yi mawa Dr S.S nuni da Ζ™ofar shiga gidan.. Baiyi musu ba haka yabi bayan Baffa suka shiga cikin gidan,

Inna ce ta baje masa wani Ζ™aton tabarma ya zauna akai, yayinda ta Ι—ebomasa ruwa a kofi ta aje mai.

Gyara zama Dr S.S yayi haΙ—e da cewa “Baffa inaso muyi wata magana ne idan har bazaka damuba “

“FaΙ—i maganarka kai tsaye likita, kada kaji wani shakku” Baffa yafaΙ—a yana mai dawo da hankalinsa ga Dr Sadeeq.

“Maiyasa bazaku kai case Ι—in Zahrah kotu ba? yakamata ace amatsayinta na marainiya a bimata haΖ™Ζ™inta, bai kamata ace wani Ζ™aton banza ya keta mata haddi ba, sannan kuma abarshi yaci gaba da walwala, inaga yakamata ayi wani abu akai” Dr Sadeeq yafaΙ—a cike da damuwa.

Nannauyar ajiyar zuciya Baffa ya sauΖ™e haΙ—e da jinjina kansa, cike da rauni yace “BazanΖ™i shawaranka ba likita, sai dai a gaskia bazan Ι“oye maka ba, hakan da kake so bazai samuba, domin yanda ka ganmu nan haka muke rayuwarmu, mu talakawa ne, cin yau da Ζ™yar na gobe da Ζ™yar, kuma maganan nan ma da nake maka, bansan wanene yayi mawa Zahrah fyaΙ—e ba, to ka ga kenan babu batun ma Ι—aukar fansa”

“Wanene ZAID ?” Dr S.S ya tambayi Baffa.

Washe da baki Baffa yace ” shine yaron da Zahrah ta amince dashi, yake zuwa zance wajenta, idan kuma bazaka mantaba ai nafaΙ—a maka shiΙ—in yaron kirkine, na tabbatar da cewa baisan haka yafaru da ita ba, da nasan dole zaizo” Baffa yaΖ™are maganar yana mai jinjina kai..

“Shine yayi mawa Zahrah fyaΙ—e !” Dr S.S yafaΙ—a murya a kausashe,

Gaba Ι—aya idanunsa Baffa ya zaro, alamar maganar ta dake shi, “Zaid fa kace likita !” Baffa yafaΙ—a cikin kaΙ—uwa,

“Ƙwarai kuwa domin kuwa jiya ta ambaci sunansa, nakuma ji da kunne na, amma tunda kace ba zaku kai case Ι—in kotu ba, bakomai ni zan wuce” Dr Sadeeq yafaΙ—a yana mai miΖ™ewa tsaye, bayan yaciro damin kuΙ—i ya a jewa Baffa kan tabarma,,

“A’a hadda Ι—awainiya haka likita? to to munagodiya!” Baffa yafaΙ—a cike da farinciki,

(hmm mai hali dai baya fasa halinsa)

“Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un! Malam hayaΖ™i, hayaΖ™i Malam a Ι—akin Zahrah !!” Inna tafaΙ—a cike da tashin hankali, ai da sauri Dr Sadeeq da baffa, suka nufi Ι—akin Zahrah’n wanda hayakin haryasoma cika tsakar gidan, dayake Ζ™ofar bata da wani Ζ™arfi duka Ι—aya Dr S.S yayi mawa Ζ™ofar Ι—akin tabuΙ—e, gaba Ι—aya Ι—akin yaturnuΖ™e da hayaΖ™i yayinda wuta kecin wasu kaya dake aje tsakiyar Ι—akin, gefe da kayan kuma Zahrah ce durΖ™ushe tana kuka, har wutan yakusa Ζ™arasowa gareta,

STORY CONTINUES BELOW

Cikin zafin nama, Dr Sadeeq yasanya hanunsa, ya janyeta daga tsugunnen da take, kai tsaye waje yafito da’ita, domin kuwa hayaΖ™in yasoma shiga cikin maΖ™oshinsu, Baffa da Inna kuwa ruwa suka Ι—ebo suka kashe wutan,

RiΖ™eta yayi gam yayinda ya kafeta da idanunsa da suka rune tsabar Ι“acin rai,

Baisan meyake damuntaba, rashin hankaline ko kuma sangartane baisaniba, yasan cewa tanajin ciwo a cikin zuciyarta, amma abun da take Ζ™oΖ™arin aikata mawa kanta, kama yake da taΙ“in hankali, Ζ™oΖ™ari yayi wajen danne zuciyarsa, haΙ—e da saisaita muryarsa, “Maiyasa Zahrah ? bazaki Ι—au Ζ™addaranki ba ?” yayi mata tambayar cikin tausasa murya, hawayene suke gudu haΙ—i da ambaliya akan fuskarta, gaba Ι—aya jitakeyi duniyar najuya ma ta, dawowanta gida yasake tada mata da mikin dake maΖ™are cikin zuciyarta, duk da kuwa dama cewa mikin bai wau ya kwanta ba ne,,

Saurin saketa yayi sakamakon Ζ™arasowar Baffa da Inna wajen, zamewa tayi aΖ™asa dabas tana mai sakin kuka,

Kallon Baffa Dr Sadeeq yayi, kafun Baffa yace komai Dr Sadeeq yace, “Baffa ni nawuce sai nasake zuwa “

“To Likita mun gode ka gai da gida ” Inna da Baffa suka haΙ—a baki wajen faΙ—a, da “To” kawai Dr Sadeeq ya amsa musu haΙ—e da sa kai yafice daga cikin gidan,

Kama hanun Zahrah Inna tayi suka zauna akan tabarma, cike da damuwa Inna tasoma cewa “Maiyake damunkine Zahrah ? sai kace akanki aka fa ra yin fyaΙ—e? gaba Ι—aya duk kinbi kinΙ—aga hankalinki, muma kin Ι—aga mana namu hankalin, a gaskia nida Baffanki munsoma gajiyawa da wannan halin naki, bayan kinso caka mawa kanki almakashi, likita ya hana, yanzu kuma Ζ™ona kanki kikesonyi, wai kina cikin hankalinki kuwa Zahrah?”

“Gaya mata dai Salame, domin nima nan nasoma gajiya da rarrashi, yanzu dakika Ζ™ona kayayyakin daya baki, shiΙ—in kika Ζ™ona ne? tambayanki nake shiΙ—in kika Ζ™ona ?” Baffa yafaΙ—a cikin faΙ—a faΙ—a, domin ya lura idan suka biyewa Zahrah tofa bazata taΙ“a daina yunΖ™urin kashe kanta ba..

Zuciyar Zahrah ne tasakeyin rauni, ” Allah sarki ni, komai nayi, ganin laifina suke, shin bancancanci rarrashi da kulawaba? fyaΙ—e akayimini amma hakan baiwani shiga jikin kowa ba, natabbata idan da iyayena suna da rai, to tabbas da bazasu taΙ“a kwantar da hankalinsu ba, kuma nasan dolene sai sun Ι—aukarmin fansa, bakuma zasu taΙ“a gajiyawa daniba, wayyo Allah na mutuwa tayi mini yankan Ζ™auna daku iyayena !!” maganar da Zahrah take faΙ—a kenan a cikin zuciΖ΄arta, hawayenta ne suka sake tsananta zuba, sai yau ta tabbatar cewa Maraici bashi da daΙ—i, sai yau tasake tabbatar da cewa Allah ne kaΙ—ai gatan ta, Zaid ya cuceta, yayi mata babban tabo wanda hargaban abada ba zata taΙ“a mantawa dashi ba, “maiyasa Zaid ?” tasake tambayar kanta bayan kuma tasan bata da amsa,,

Haka Inna da Baffa suka wuce Ι—aki suka barta zaune a tsakar gida tana tsiyayar hawaye, babu mai rarrashi.

TuΖ™in mota yake amma gaba Ι—aya hankalinsa yanaga yanda yabaro Zahrah, tsantsar tausayinta yakeji, yanason taimaka ma ta amma to tayaya? ta wacce hanya? duk alokaci Ι—aya ya tambayi kansa, wayarsa ce tasoma Ζ™ara alamar shigowar Ζ™ira, Zabba’u shine sunan dake yawo akan screen Ι—in wayar, Ζ™aΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya ya sauΖ™e haΙ—e da Ι—aukan wayar yakara a kan kunnensa,

“Cike da sangarta Zabba’u tayi masa sallama, amsa sallaman yayi a daΖ™ile haΙ—e da cewa “Ganinan zuwa” Ζ™it yakashe wayar haΙ—e da cillata kan kujeran mai zaman banza, shi sam baisan yanda zaiyi da Zabba’u ba, amma a zahirin gaskia Ι—abi’u da tarbiyanta basu masa ba,duk da kuwa cewa Ζ΄ar uwa take a garesa.

New York City

Tsaye yake agaban wani tangamemen cupboard paper, wanda yake liΖ™e ajikin wani abu kamar allo, sanye yake da 3 guater jeans, yayinda yabar gaba Ι—aya surar jikinsa a waje, kasancewar baisanya rigaba, babban abun Ι—aukar hankali ajikinsa shine lafiyayyun, 6 packs Ι—insa, dake kwance raΙ—a raΙ—a akan cikinsa, riΖ™e yake da wani dogon pen a hanunsa da’alama dai wani abu yake zanawa mai mahimmancin gaske,, Ζ™ayataccen murmushinsa yasake, haΙ—e da Ι—aukan glass cup Ι—in da wine Ι—insa ke ciki, yakai bakinsa, saida ya shanye duka wine Ι—in dake cikin kufin, kafun ya aje kofin kan wani Ι—an Ζ™aramin table dake kusa dashi,

STORY CONTINUES BELOW

Hanunsa yasanya akan kyakkyawar fuskar daya zana a jikin cupboard paper Ι—in, a hankali yashiga shafa zanen , hanunsa yakai dai dai saitin bakinta, haΙ—e da shafawa, idonsa Ι—aya yakashe haΙ—e da lasan laΙ“Ι“ansa,

“Kinkasa barina My Sugar Baby, maiyasa ? ” yayi tambayar yana mai tsare zanen dake jikin cupboard papern da ido,

“Bazaki amsaminba ko? fushi kike dani ko sugar baby na?”

Yasake tambayar wannan zanen dake jikin cupboard paper’n.

Murmushi yakumayi haΙ—e da matsawa daf da cupboard paper’n bakinsa yaΙ—aura adai dai kumatun ta yamanna mata kyakkyawan kiss, “Kikulamin da kanki kinji My Zahrah!!” yafaΙ—i maganar cikin shauΖ™i,, sai alokacin nalura ashe zanen fuskar Zahrah ne raΙ—au ajikin cupboard paper’n, bakaΙ—an ba kuma zanen yayi kyau,, kyakkyawan Ζ™yalle yasanya yarufe zanen, haΙ—e da Ι—aukar wayarsa yafice daga cikin Ι—akin…

Yana fita falo Abid dake tsaye tun Ι—azu yana zaman jiransa, ya saki tsuka, haΙ—e da cewa ” Wai don Allah maika tsaya yi ? tun Ι—azu fa kasan nakejiranka, amma ka shanyani “

Zama Zaid yayi akan kujera haΙ—e da jawo kwalbar wine Ι—insa, yashiga shan abunsa, ganin haka yasa Abid sauΖ™e ajiyar zuciya haΙ—e da girgiza kai, wato dai yau Ζ΄an halinne suka motsa, gaskia Zaid yanada wuyan sha’ani, bakoda yaushe kake gane gabansa da bayansa ba, duk da kuwa tsananin sabon dake tsakaninsu, amma shi kansa wataran idan Zaid ya juye tofa baya iya gane masa.

“Kana yawan shan wine Zaid, baka tunanin zata iya janyomaka matsala nan gaba ?” Abid ya tambaya cike da kulawa, domin kuwa, shi ko za’a kasheshi bazai iya shan rabin wine Ι—in da Zaid yakesha a rana ba,

“Maiyashafeka da shan wine Ι—ina ?sanin kankane natsani sa’ido ” Zaid yayi maganar cikin haΙ—e fuska,

Dariya Abid yayi, domin kuwa yanzu yatabbatar cewa Shu’umin cin nasa ne ya motsa, “Okay i’m sorry bazanΖ™ara ba, amma yakamata ace musauΖ™a Ζ™asa, babes Ι—in nan fa suna jiranmu ” Abid yafaΙ—a yana mai duba agogon dake Ι—aure a tsintsiyar hanunsa,

“Kaje kawai ka sallamesu, nikam bana ma buΖ™atar ganinsu, mata duk a bubbushe, ba wani diri mai burgewa, sai kace 1, kaje can kata fama idan zaka iya” Zaid yafaΙ—a cike da Ζ™uncin rai,

Dariya sosai Abid yayi, haΙ—e da tashi kawai yafita daga falon, gaba Ι—aya kwana biyun nan yarasa maiyake damun Zaid..

Abid na fita Zaid yagyara zamansa, haΙ—e da lumshe idanunsa, gaba Ι—aya fuskar Sugar Babynsa ne yake yimasa gizo a cikin idanun nasa.

Abuja Nigeria

Zahrah ce zaune akan Ζ΄ar yaloluwar katifarta, ta tanΖ™washe Ζ™afafunta, yayinda kanta ke kallon sama, ruwan hawayene kawai ke gangarowa daga cikin idanunta, kallo Ι—aya zakai mata wata irin muguwar tausayinta yadaki zuciyarka, domin kuwa wani irin muguwar rama ce ta bayyana a jikinta,1

Da sallama Khausar tashigo cikin Ι—akin, kamar daga sama haka Zahrah taji muryar aminiyarta ta wato Khausar, tana kai kallonta bakin Ζ™ofa taga Khausar Ι—in tsaye tayi turus,,

Ai dagudu Zahrah taje tafaΙ—a jikin Khausar, haΙ—e da sakin wani sabon kuka mai sauti, duk da cewa Khausar batasan abun dayake faruwa ba, amma tasan cewa ba lafiya Ζ™awartata take ba, kawai itama sai tafashe da kuka, hakanan taji wani irin tausayin Zahrah’n yacika zuciyarta, rungumeta tayi da kyau a jikinta, ko kaΙ—an Khausar batayi yunΖ™urin hana Zahrah kuka ba, saida Zahrah tayi kuka sosai, kafun ta tsagaita, a hankali take sauΖ™e ajiyar zuciya,, hanunta Khausar takama suka zauna akan katifar Zahrah’n,,

“Zahrah!” Khausar taΖ™ira sunanta cikin sanyin murya, Zahrah bata iya amsa mata ba, sai Ι—ago idanunta da suka kumbura suntum tsabar kuka, tayi ta kalli Khausar Ι—in,

Zaro idanu Khausar tayi, cike da tashin hankali tace “Zahrah maiyake faruwa ne, tun ranan nake Ζ™iran wayarki a kashe, nazo gida kuma bansamu kowaba, nazo yafi sau huΙ—u bana samun kowa acikin gidan, dan Allah Ζ™awata kifaΙ—amin maiyake faruwa ?” Khausar tayi maganar cikin damuwa.

“Rayuwata taΖ™are Khausar, yacuceni,ya yi mini babban illa, dakuma tabo wanda bazai taΙ“a gogewa ba, ya nakasamin rayuwata, ashe haka Ζ™addara zata zomin mummuna? nayarda cewa kowani bawa da’irin tasa Ζ™addaran amma ni tawa Ζ™addaran tafi takowa muni, danasan haka zata faru dani, dana roki Allah daya kasheni kafun yanzu na….” Saurin toshe mata baki Khausar tayi, cike da ruΙ—ani haΙ—i da tashin hankali, Khausar tace “Kada kiyi saΙ“o Zahrah, kinsani acikin duhu, kisanar dani maike faruwa dan Allah, gaba Ι—aya kinsani cikin tashin hankali !” Khausar tafaΙ—a cikin Ζ™osawa,

“Za..i..d yayi min fyaΙ—e Khausar !!!” Zahrah tafaΙ—a tana maisake rushewa da kuka,,

Tamkar anwatsamata ruwan zafi haka Khausar taji ajikinta, lokacin da maganan Zahrah yadaki dodon kunnenta, “Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un! FyaΙ—e fa kikace Zahrah ?” Khausar ta tambaya cikin matsanancin tashin hankali, lokaci guda hawaye suka shiga sauΖ™a daga cikin idanunta, take jikinta yayi sanyi laΖ™was,,

“Yacutar da rayuwata Khausar, ashe haka soyayya ta ke? rama alkhairi da cuta, ashe haka duniya take cike da azzaluman bayi? maiyasa yayi min haka Khausar? mainayi masa? yaruguzamin duk wani farincikin rayuwata, wayyo Allah na Khausar ki karΙ“i wuΖ™annan ki kasheni dashi ko da zansamu sauΖ™i da salama acikin zuciyata !!” Zahrah taΖ™are maganar tana mai miΖ™omawa Khausar wata wuΖ™a da ke aje gefenta,,

Matsanancin kuka Khausar tasanya, haΙ—e da jawo Zahrah jikinta, ta rungumeta Ζ™am, kuka suka shiga yi wiwi, babu mai lallashin Ι—an uwansa…

((Agaskia banson abunda wasunku sukemin,musamman masu cewa naΖ™ara musu yawan typing, inaso kusani cewa, banda wadataccen lokaci, inazuwa makaranta, inada miji, sannan kuma nima inada wasu uzururrukan, yakamata kuna hakuri, amma wasu har baΖ™ar magana su ke Ζ™oΖ™arin gayamin don kawai shekaran jiya nayi muku typing kaΙ—an, hmm wlhy kunbani mamaki, ni bana neman faΙ—a da kowa, saboda banΙ—auki duniya komai ba, shekaran jiya a matuΖ™ar gajiye nake saboda naje school, amma haka na lallaΙ“a nayi muku typing, a she duk da haka wasunku basu godeba, haka sukaita Ζ™ananan maganganu, wata har cewa take wai tagaji da wayon danake yi,koda yaushe sai nace na gaji, yes dole nagaji tun da dai ni ba engine bace, da za’ace bazan gaji ba, kuma ina da abubuwanyi. kuyi haΖ™uri my real fans na zage inata faΙ—a, wlhy raina ne yaΙ“aci wasu komai kamusu baka burgesu.

Nadawo gareku sisters masu cewa Zahrah tasoma basu haushi sbd abubuwan da takeyi, yaka mata ace kufahimceta, bawai inabin bayan tabane, amma yana da kyau ku yi imagine akan ya mace za taji idan har akai mata fΖ΄aΙ—e?dole za taji matsanancin ciwo, acikin zuciyarta, kuma dole ne abun zai zama babban tabo wanda bazai taΙ“a gogewa acikin zuciyarta ba, saboda haka kuyi hakuri kuyi mata uzuri. Kuyi haΖ™uri nayi mistake, Ζ™awar Zahrah sunanta Husnah ne ba Khausar ba, kamar yanda nasa a page Ι—in baya, Husnah nakeson sawa, to bestyna saita tsayamin arai nasa sunanta,lol.)+

Kuka suka shugayi wiwi babu mai lallashin Ι—an uwansa, da Ζ™yar Husnah ta’iya tsagaita kukanta,haΙ—e da daidaita nutsuwarta, duk da cewa zuciyarta bata daina bugu ba, tamkar Ζ΄ar uwa ta jini haka ta Ι—auki Zahrah, saboda haka duk wani abu daya faru da Zahrah tamkar da ita yafaru, domin kuwa abokin kuka shi’ake gayawa mutuwa, wannan abotar tasu tasamo asaline tun suna yara, haka kuma sun Ζ™ulla abotansu cikin gaskia da yarda da juna,,1

“Bazance miki kidaina kuka ba, Zahrah domin idan nace miki haka, banyi miki adalci ba, sai dai zan sake tunatarmiki cewa akwai Sarkin sarakuna, mai tausayi ga bayinsa, mai amsa addu’an bayinsa, mai basu, mai kuma hanasu, shi ishashshene akan dukkan komai, yanaji,kuma yana gani, sannan kuma shi ya wanzar da faruwar haka a gareki, tunkafun ya halicceki ya tsara, cewa hakan zai faru a kanki, kada kiyi jayayya Zahrah, domin kuwa babu wani bawa a duniya daya isa ruguza tsarin Allah, Allah baya bacci, yanasane da wanda sukayi cuta, dakuma wanda aka cuta, zaifi kyau ki miΖ™a al’amuranki garesa, haΖ™iΖ™a nasan cewa abun da Zaid yayi miki, abune mafi matsanancin ciwo acikin rayuwar Ζ³AMACE, amma kashe kai, ko kice a kasheki banaki bane Zahrah, rungumar Ζ™addara ita tafi dacewa dake, haΖ™iΖ™a nasan cewa har gaban abada bazaki mantaba, amma inaso kiΙ—auki Ζ™addaranki, kimiΖ™awa Allah lamuranki, da sannu zakiga sakayya, ke ba jahila bace, da iliminki na addini dana zamani, saboda haka inaso kiyi amfani da wannan ilimin naki wajen Ι—aukar Ζ™addaranki hanu bibbiyu, kada kice na faΙ—i haka ne don banasonki, wlhy inasonki Ζ™awata, inajinki tamkar jinin jikina, kawai dai hakan shine mafita !!” Husnah tayi maganar cikin tsananin tausayawa, yayinda ruwan hawaye suka gama wanke fuskarta…

A hankali Zahrah taΙ—ago idanunta dasuyi jajur tamkar anwatsa musu garin barkono, ta kalli Husnah, sosai maganar Husnah yadaki zuciyarta, sai dai yazame mata dole shiga ƘUNCIN RAYUWA, da ace zata buΙ—ewa mutane Ζ™irjinta suga, cikin zuciyarta, to tabbas da tayi hakan, domin tasan duk wanda yaga ciwon dake mamaye da zuciyarta, to tabbas dole ne zai koka mata, domin kuwa wani irin danΖ™areren ciwone yabaibaye zuciyarta, wanda batasa ran zata warke har gaban abada,

” Ashe babban kuskurene Ι—aukar soyayya ka bawa wanda yafika? menene aibuna dan nafito a mace? me maza sukaΙ—auki mata ne? a she dan kana talaka shikenan kai bakomai bane? bakuma ka da Ζ΄anci? ya ketamin haddina da Ζ™arfin tsiya, yanunamin Ζ™arfi da kuma fifiko, duk dan kawai ina mace, maiyasa ya tsalleke dukkan mata yazo kaina nida banda kowa sai Allah? nayi masa kuka, nayi masa magiya, na roΖ™esa amma ya toshe kunnuwansa, yacire duk wani imaninsa ya cutar da rayuwata, kigayamin miye laifina dan nafita cikin hayyacina ? ki faΙ—amin shin bancancanci in haΙ—iyi zuciya in mutu ba, f…ya…Ι—…e fa yayi mini Husnah!!!” Zahrah tafaΙ—i maganar cikin matsanancin kuka,

STORY CONTINUES BELOW

Duk yanda Husnah taso ta sake danne zuciyarta kasawa tayi, kawai sai ta sake sakin kuka haΙ—e da rungume Zahrah Ζ™am acikin jikinta,

Saida sukayi kuka sosai, kafun suka soma sakin ajiyar zuciya, take zuciyar Husnah tayi sanyi, amma banda ta Zahrah, domin babu wani sanyi daya ragewa zuciyar Zahrah.

A hankali Husnah tashiga shafa bayan Zahrah, wacce haryanzu sheshsheΖ™an kuka take,

” Ki tsaida kukanki Zahrah, kuka baya maganin komai, sai dai ya sanyamiki ciwon kai, addu’a ita kaΙ—ai ce magani, nasanki Zahrah, inakuma da yaΖ™inin cewa baki kai kukanki ga Allah ba, kiji rani inazuwa ” Husnah tafaΙ—a tana me miΖ™ewa tsaye, kaitsaye ficewa tayi daga Ι—akin, yayinda Zahrah tafaΙ—a kan katifa taci gaba da kukanta,,,

Mintuna kaΙ—an Husnah tashigo Ι—akin hanunta riΖ™e da wasu magungunan da likita ya kawowa Zahrah, wanda takarΙ“o wajen Inna,,

Ledan da tashigo dashi ta jawo, haΙ—e da Ζ™arasowa wajen Zahrah, tamkar Ζ΄a da uwa, haka Husnah ta jawo Zahrah jikinta, cike da tausayi haΙ—i da rauni tace ” Kidaina kuka dan Allah Zahrah, kinga ko na tahomiki da abincin da kikafi so, Shinkafa da Kifi, Mom ce ta dafa ” Husnah taΖ™are maganar tana mai buΙ—e wni kula, wanda ta ciro a cikin ledan da tazo dashi,

“Nasan bakici komaiba, kuma koda nace kici ma, cemin zakiyi kin Ζ™oshi, amma dan Allah kici ko kaΙ—anne zanji daΙ—i Zahrah, baki da kowa sai Allah, amma kada kimanta nidake tamkar gudan jini muke, damuwarki damuwata ce ” Husnah tafaΙ—a tana mai zub da Ζ™walla,

Kallonta Zahrah tashigayi, take kuma zuciyarta ta karye, sai kawai tafaΙ—a jikin Husnah, tashiga sauΖ™e ajiyar zuciya,,

Cike da lallami Husnah tashiga bawa Zahrah shinkafa da kifin da takawo, duk dacewa maΙ—aci yafi abincin daΙ—i a bakinta, amma hakanan ta daure takeci, badon komaiba sai don Husnah tacancanci tayi mata komai a rayuwarta, itace mace ta farko data fara bata kyakkyawan kulawa wanda tunda abunnan yafaru da ita babu wanda yabata, sai likita..

Duk da cewa bata wani ci mai yawa ba, amma zaiyi mata amfani, domin kuwa cikinta yajima ba’asa mai komai ba a cikinsa,,

Husnah nagama bata abincin, ta Ι—auko musu Al’Qur’ani guda biyu, miΖ™awa Zahrah Ι—aya taΖ΄i, haΙ—e da buΙ—e mata fejin farko, cemata tayi su karanta a tare, duk da cewa da Ζ™yar muryarta yake fita amma sosai tayi Ζ™oΖ™ari wajen karanta Al’Qur’ani,n.

Babu abun da yagagari Allah, Al’Qur’ani littafine mai cike da tarin haske, yana wanke zuciyar maikarantasa, yanasanya nutsuwa ga ma’abocin karantashi, take Ζ™uncin dake maΖ™are acikin zuciyar Zahrah yasoma ragewa, sunacikin karatun wani irin bacci ya yi gaba da’ita,, take ta kwanta a wajen tahau bacci,,

Murmushi kawai Husnah tayi haΙ—e da Ι—aukar Al’Qur’ani’n, dake riΖ™e a hanun Zahrah ta aje gefe,

“Kayafe ma ta ya Allah! domin nasan tsananin tashin hankali da damuwa, su sukayi tasira a cikin zuciyarta, wajen mantar da’ita kai kukanta gareka!” Husnah tafaΙ—a tana mai kallon sama, gudun kada ta tashi Zahrah a bacci yasanya tasoma karatun nata Ζ™asa Ζ™asa…

((Ƙawaye: bawai nishaΙ—antarwa kaΙ—ai shine amfanin muba, mu mata ne, kuma mu Ζ™awayen juna ne, yana da kyau, mu Ζ™aunaci junanmu, tsegumi, Ζ™yashi, baΖ™inciki, hassada, duk banamu bane, kamar yanda akace ciwon Ζ΄a mace na Ζ΄a mace ce, yana da kyau muΙ—auki hakan da matuΖ™ar mahimmanci, du kanmu zamuso ace munsamu Ζ™awa kamar Husnah, to amma ta yaya zamu samu Ζ™awa kamar Husnah? dole ne mu tsarkake zuciyoyin mu, mudaina mawa junanmu Ζ™yashi da hassada, mudaina bawa junanmu mugayen shawara, mudaina zuga wasunmu sukai kansu zuwaga halaka, kada ki bata gurguwar shawara wanda zata cutar da’ita, wai don takawo kanta gareki domin kibata shawara, kada ki zugata akan cewa ta aika Ι“arna, idan har bazaki faΙ—a mata alkhairi ba, to kada ki faΙ—a mata sharri, dukanmu mata ne, kuma dukanmu zuciyoyin mu suna da rauni, ta yarda dake, saboda kunyi shekara da shekaru kuna tare, hakan yasa ta Ι—auki duk wani sirrinta ta zazzage miki, maiyasa tayi haka? saboda ta Ι—aukeki Ζ΄ar’uwa, tunda ta sanar dake duk wani sirrinta, mai yakamata kiyi? saiki riΖ™e mata amana, ki tsare mata sirrinta, amma saiki kaje ki ka tona mata asiri a wajen mutanen duniya, idan kikayi haka kincancanci a Ζ™iraki da suna Ζ™awa? maiyasa muka Ι“ata kanmu ? mukaraba kan abotanmu ? saboda bama iya riΖ™e sirrin juna, kuma bamaso kowa ya Ζ™aru, ko ya samu buΙ—i, saimu kaΙ—ai, yana da kyau muriΖ™e abotarmu da kyau, domin a matsayinmu na mata idan bamuyi abota da junan muba, da waye zamuyi? da maza? suda basusan yanda zasu magance mana matsalolinmuba, sirrin mace fa sai mace Ζ΄ar uwarta, please Sisters dan Allah muyi Ζ™oΖ™ari wajen gyara zuciyoyinmu, domin mukasance abokai na Ζ™warai, masu rufa asirin juna.))

STORY CONTINUES BELOW

Zaune yake a katafaren wajen shaΖ™atawa dake farfajiyar gidan, sanye yake da riga da wando na jamfa hadda hulansa, bakaΙ—an ba yayi kyau, kasancewarsa matashi mai jini a jika, sannan kuma dama akwai kyau Ι—in tubarkalla, Wayarsace Ζ™irar iphone Xs Max riΖ™e a hanunsa yana faman latsawa da dukkan alamu abu mai mahimmanci yakeyi, Ζ™amshin turarenta ne yafara cika hancinsa, a hankali yaΙ—ago kansa yakai dubansa zuwa gareta, sanye take da doguwarriga na atamfa wanda yakama jikinta sosai, yayinda ta saΖ™ala wani Ι—an Ζ™aramin vail a wuyanta, balaifi tayi kyau, tunda dama kyakkyawace.

cike da takun Ι—aukar hankali taΖ™araso wajen dayake zaune bakinta Ι—auke da sallama,

Amsa mata sallaman yayi yana mai Ι—auke idanunsa daga gareta, domin komai najikinta bayyane yake a fili.

Kujeran dake kusa dashi ta ja, ta zauna, cikin sauyawa murya amo tace, “Barka da zuwa Jarumi na”

Kai kawai yaΙ—aga mata alamar yaji, batare daya Kuma kallon taba, sake lanΖ™wasa murya tayi, takuma cewa “Yakamata mu’isa falon baΖ™i ai, sai nake ga kamar zaman mu anan baiyiba, kasan fa kai Ι—in maidaraja ne baidace ace nabarka anan ba” taΖ™are maganar tana mai kaΙ—a idanunta, alamar yanga.

“Inaganin nan Ι—in ma yayi ai basai munshiga ciki ba” Dr Sadeeq yafaΙ—a yana mai gyara zamansa,

Harara Zabba’u ta Ι“allamasa Ζ™asa Ζ™asa batare daya gani ba, a zuciyarta kuwa cewa tayi “Inbanda Allah yaΙ—igamin soyayyarka a cikin zuciyata, da mai zai sanyani tsayawa, har ka wulaΖ™antani “

Ɗago da kansa yayi ya kalleta, cikin muryan dakewa yace “Ni zan wuce “

“Haba Yaya Sadeeq maiyasa kakemin hakane wai ? ko minti 30 fa bakayi da zuwa ba, amma kuma kace zaka tafi ” taΖ™are maganar tana kwaΙ“e fuska tamkar wata Ζ™aramar yarinya, ko kaΙ—an kuma hakan baimata kyau ba, domin kuwa shekarunta ya wucewa abun da take Ζ™oΖ™arin yi, (wannan saimu nida bestyna jikar Hajiya sweet 19,lol)

Hanu yasanya a cikin aljihunsa yaciro kuΙ—i, aje mata yayi akan table Ι—in dake gabansu, haΙ—e da tashi tsaye yasoma tafiya,, ganin haka yasa Zabba’u daΙ—a Ι“ata fuska, cike da Ζ™uncin zuciya, tarufa masa baya.

Mai gadi na buΙ—e masa gate yafice da motarsa, Zabba’u naganin fitansa, tasaki tsuka cike da takaici, wai ace kamar ita babbar yarinyar da maza suke mararin samunta, amma wai ita wani ke wulaΖ™antawa, kwashe kuΙ—in da ya aje mata akan table tayi haΙ—e da sakai tayi shigewarta gida…

Zahrah kuwa ba’ita tafarka daga wannan baccin da takeyiba, sai Ζ™arfe 6 na yamma, lokacin anata Ζ™iraye Ζ™irayen sallan magriba, har zuwa lokacin kuma Khausar tananan bata tafi ba,,1

Koda ta tashi a baccin, ji tayi gaba Ι—aya tayi sakayau da’ita, a cikin kaso Ι—ari na Ζ™unci da damuwarta, babu kaso talatin, Allahu Akbar haΖ™iΖ™a karatun Al’Qur’ani warakace ga duk wani damuwar zuciya, harma da ta rayuwa.

Matsowa kusa da’ita Husnah tasakeyi, cike da tausasawa takama duka hannayenta biyu,

“Bazan gajiya da faΙ—a miki ba Zahrah, yin imani da Ζ™addara mai kyau ko marar kyau, shi’ake so ga ko wani musulmin Ζ™warai, kuma Allah baya Ι—aurawa bawa abun da bazai iyaba, idan kika Ζ™ara haΖ™uri ki kaΙ—au Ζ™addaranki, to ina mai tabbatarmiki da zaki samu kyakkyawan sakamako awajen ALLAH, haΖ™iΖ™a nasan Zayd ya cutar da rayuwarki, amma Allah bazai barshi ba, da sannu Allah zai saka miki,kimin alΖ™awari bazaki na yawan kukaba, sannan bazakina yawan damuwa ba, duk da nasan hakan abune mawuyaci, amma idan kika daure zaki iya, sannan kuma kuka baya maganin damuwa, karatun Al’Qur’ani kaΙ—ai zaki riΖ™a, insha Allahu damuwarki zata gushe, sannan kuma, kinyi kuskure Zahrah kinbari tarin damuwar da kika shiga, ya hanaki kai kukanki ga Allah, kin manta shine maikowa mai komai, dan Allah Zahrah kimin alΖ™awarin cewa zaki rage sanya kanki a damuwa, duk sanda wani tunani yake shirin zuwa miki, to ki gaggauta Ι—aukan littafi mai tsarki, ki karanta hakan zai sanyamiki nutsuwa !!” Husnah tayi maganganunta cikin lumana dakuma son sawa Ζ΄ar uwarta Ζ™warin guiwa,,

“Bansan mai zance miki ba Husnah, amma haΖ™iΖ™a kinwuce Ζ™awa ke Ζ΄ar uwace, kuma koda a cikin Ζ΄an uwanma keΙ—in ta da bance, namiki alΖ™awari cewa zan maid komai nawa ga Allah, haΖ™iΖ™a rayuwata tana cikin Ζ™unci da kuma baΖ™in ciki, amma nasan babu a bunda yagagari Allah, kuma da sannu rayuwata zatayi haske, duk da banda tabbacin hakan !” Hawayene kawai ke tsiyaya daga idanun Zahrah, domin sosai takejin ciwon abun da Zayd yayi mata, yanzu tayarda cewa dama haka Allah yatsara mata, kuma zata rungumi Ƙaddaranta, har Allah yakawo ma ta mutuwarta,, amma dudduniya bata taΙ“a jin matsanancin tsana ga kowa ba bayan Zayd,,

Sosai Husnah tabawa Zahrah shawara masu amfani, wanda zasu taimaka wajen cireta a damuwa,, saida akayi sallan Isha kafun driver’n gidan su Husnah yazo ya Ι—auketa…

Tiryan tiryan Baffa ya Ι—ebi Ζ™afa, har ofishin Alhaji Umar, gaba Ι—aya abun da yafaru da Zahrah, Baffa ya kwashe ya faΙ—a masa, bakaΙ—an ba hankalin Alhaji Umar ya tashi, domin kuwa shi Zahrah tamkar Ζ΄a yaΙ—auketa, saboda mahaifinta yayi masa taimako sosai, cikin faΙ—a da hargowa Alhaji Umar kecewa zai kai case Ι—in koto, saurin dakatar dashi Baffa yayi, haΙ—e da yagyara zama, ban baki Baffa yashiga yi wa Alhaji Umar, akan cewa kada yakai case Ι—in kotu, domin kuwa yaron yafi Ζ™arfinsu, sannan kuma idan har aka kai case Ι—in kotu, tofa sunan Zahrah ne zai sake Ι“aci, wanda basusan an ma ta fyaΙ—e bama zasu sani, sannan kuma zata rasa mijin aure, domin wasu zasuce ba fyaΙ—e aka mata ba, ita takai kanta, kuma dole su zasukwan a ciki, domin basu da kuΙ—i, a yanzu yanda rayuwar duniyar nan take, mai kuΙ—i shine sarki, kuma mai kuΙ—i shi kaΙ—aine mutum, haka wasu suka Ι—auka, ko shari’a ake mai kuΙ—i shiyake nasara,, sosai jikin Alhaji Umar yayi sanyi, domin kuwa tabbas maganganun da Baffa yafaΙ—a haka yake, kuma yasan duk kuΙ—insa bai isa yaja da wanda suka fisa ba, domin shi Ι—an Ζ™aramin mai arziki ne akan wasu…

((Sau dayawa akan cutar damu Ζ΄aΖ΄an talakawa, amma bamu isa mu kai Ζ™ara ba, mune da gaskia, amma mu’ake bawa rashin gaskia, maiyasa ? saboda mu bamu da kuΙ—i, wanda bashi da kuΙ—i kuma ba mutum bane a wajenku ko? anacin zarafin Ζ™ananan yara dakuma Ζ΄an mata, amma ba a iya Ι—auka musu mataki, saboda kawai wanda suka aikata abun masu hanu da shuni ne, mukuma an maidamu ko’oho, Allah sarki Allah ka’iyar mana, kabimana haΖ™Ζ™inmu gaduk wani wanda yazaluncemu Ameen.))A hankali yake tafiya da motarsa har yakawo Ζ™ofar gidan, dai dai tsayawur motar tasa, Baffa ya fito daga cikin gida.+

cikin hanzari ya Ζ™araso inda motar Dr Sadeeq Ι—in ke fake, “A’a likita kaine da yammacin nan haka ?” Baffa yafaΙ—a fuska cike da annuri,

“Eh wlh nine Baffa, tun safe naso zuwa, to aikine yayimin yawa ” Dr Sadeeq yafaΙ—a yana mai Ζ™oΖ™arin fitowa daga cikin motar tasa.

“To muje nayi maka iso zuwa cikin gidan ko, aikuwa mutumiyar taka tanacan ta kulle kanta a Ι—aki, tana karatu “

“Karatu kuma Baffa? badai ta dawo normal ba ?” Dr Sadeeq ya tambayi Baffa cikin sakin fuska, domin har yaΙ—anji sanyi a cikin zuciyarsa daga jin maganan Baffan,

“Ƙwarai kuwa likita, ai yanzu duk wannan hargowan kukan ta dainashi!” Baffa yafaΙ—a dai dai sanda suka kawo cikin gidan,

Da fari’a Inna ta tarbi Dr Sadeeq, haΙ—e da baje masa tabarma a Ι—an madaidaicin tsakar gidan nasu, shima cike da mutum tawa ya gaida ta.

Bayan sun gama gaisawanne yake tambayar ko Zahrah tana shan magungunanta ?

Take Inna tace yabiyota tayi masa iso zuwa Ι—akin Zahrah’n,

Ba musu yabi bayan Inna duk da cewa yasan hakan baidace ba, amma bayida wani zaΙ“i sai hakan, domin kuwa shima yanason ganinta.

Zaune take akan katifa, yayinda hanunta ke Ι—auke da wani Ι—an Ζ™aramin Al’Qur’ani, tana karantawa Ζ™asa Ζ™asa, a hankali taΙ—ago kanta jin muryar Inna abakin Ζ™ofar shigowa Ι—akin nata,

“Shigo mana likita ” Inna tafaΙ—a tana mai wangale Ι—an yalolon labulen Ι—akin,

Yanashiga cikin Ι—akin, Zahrah tamiΖ™e zumbur daga zaunen da take, take jikinta yasoma rawa,

Ganin yanda yanayinta ya sauya alokaci Ι—aya, yasa Dr Sadeeq tsayawa cak a inda yake, yana mai Ζ™are ma ta kallo, kallo Ι—aya yayimawa idanunta, yafahimci cewa tayi kuka, take yaji ba daΙ—i a zuciyarsa.

“Zahrah!” yaΖ™ira sunanta cikin muryar nutsuwa,

Kasa amsa masa tayi saima kau da kanta gefe da tayi tana mai rumtse idanuwanta, domin kuwa sosai Likitan yake mata yanayi da Zaid.

Cikin muryar nutsuwa ya kuma cewa “Kifito waje inason magana dake”

Yanakai Ζ™arshen zance’nnasa, yajuya yafice daga cikin Ι—akin.

Tunyanasa ran fitowar Zahrah hardai yacire rai domin kuwa babu alaman zata fito Ι—in.

Daga Ζ™arshe dai kayan marmari da kuma sauran magungunanta da ya taho mata dashi, sai Baffa ya bawa yace a bata, don yafahimci batason damuwa, kuma yafuskanci cewa tana matuΖ™ar tsoronsa, baikuma san dalilin hakanba.

STORY CONTINUES BELOW

Tanajin Ζ™aran tafiyar motarsa ta sauΖ™e nannauyar ajiyar zuciya, hakanan duk sanda ta kallesa takejin faΙ—uwar gaba, shigowar Inna cikin Ι—akin shiyayi sanadiyar katsuwar tunaninta,,

Ƙatuwar ledan da Dr Sadeeq yakawo, wanda yake cike da kayan marmari Inna ta aje mata haΙ—e da watsamata harara gami dayin tsuka tafice daga cikin Ι—akin, domin yanzu gaba Ι—aya tsananin haushin Zahrah’n takeji.

Ko kallon ledan Zahrah batayiba ballantana ta duba miye a ciki, domin itakam yanzu anshata kuma haryanzu bata warke ba, don haka babu wani Ι—a Namiji daya isa yasake yaudaranta, babu kuma wani Namiji da zata sake amincewa dashi a iya tsawon rayuwarta, tasan cewa ingancin rayuwarta yariga dayagama Ζ™arewa, domin kuwa tasan cewa babu wani namiji dazai aureta, bayan yasan cewa Zaid yariga da ya gama keta mata rigan mutumcinta.

New York City

Gudu sosai motar tasa keyi akan titi tamkar zai tashi sama, yayinda jami’an tsaron dake tsaron titi suke tayi masa magana amma bayako sauraransu, kai tsaye katafaren gidansa dake cikin New York Ι—in ya nufa, tundaga fitowarsa acikin motar zaka gane cewa a matuΖ™ar buge yake domin kuwa sai haΙ—a hanya yake gakuma zungureriyar kwalbar giya dake riΖ™e a hanunsa, yana shiga cikin katafaren falonnasa, yafaΙ—a kan kujera, haΙ—e da lumshe idanunsa,

“MY ZAHRAH!!” yaΖ™ira sunanta cikin wani sweetness voice Ι—insa, sannan kuma cikin yanayi mai nuni da cewa mutum yana cikin shauΖ™i,, da Ζ™yar ya iya miΖ™ewa yakai kansa zuwa Ι—aki, yanashiga cikin bedroom, kaitsaye ya wuce bathroom saida ya amayar da gaba Ι—aya giyan da yasha, kafun yasamu nutsuwa, amma duk da haka mayen giyan bai sake sa ba.

BuΙ—e drowern sa yayi, haΙ—e da fiddo wani irin Ζ™aton hoto wanda gaba Ι—ayansa aka rufesa da glass ma’ana akayi masa gidan glass, ba hoton kowa bane face hoton kyakkyawar fuskar Zahrah tana murmushinta mai burgewa.

Murmushi yayi haΙ—e da mannawa hoton kiss, cikin unique voice Ι—insa yace “Inakewarki My Zumata, haΖ™iΖ™a keΙ—in ta da bance, verysoon inanan dawowa gareki, har yanzu sha’awarki bata sakeni ba, banΖ™oshi dake ba babyna, kikulamin da kanki kinji Sweet Zahrah na!!” yaΖ™are maganar cike da tsananin shauΖ™i, domin kuwa wani irin feelings yakeji a ga me da Zahrah’n, yarasa maiyake damunsa akan Zahrah, aΖ™a’idansa idan yayi sex da mace sau Ι—aya, to baya sake waiwayanta harsai idan ita tawaiwayesa, nan ma saiyaga dama ya amsa tayinta, amma yau gashi yana mugun kewar Zahrah saboda yasha zumanta mai daΙ—in Ι—anΙ—ano, haryanzu baisan menene so ba, sha’awa kawai yasani akan haka kuma ya dogara.

Haka Bacci yaΙ—auki Zaid yanata sambatu irin na mashaya yayinda yake rungume da hoton Zahrah akan Ζ™irjinsa, yana ji tamkar Zahrah’nce dakanta ya runguma a Ζ™irjinsa.

Washe gari bashine yatashiba sai Ζ™arfe 9 na safe, salati yasoma yi cike da Ζ™uncin rai, sam baisan maiyasa yake makara sallan asuba a kwana biyunnan ba, ( Nace Saboda Zina bata haΙ—uwa da ibada ) daΖ™yar ya’iya tashi yashiga bathroom domin gaba Ι—aya jiyake jikinsa na masa ciwo,gashi kuma baida time Ι—in da zaiyi gym, wanka yayi cikin mintuna Ζ™alilan, fitowa yayi sanye da rigan wanka ajikinsa, agurguje yamurza lotion ajikinsa haΙ—e da sanya hand dryer ya busar da gashin kansa, wata baΖ™ar jallabiya yasanya haΙ—e da nufar inda darduma ke shumfuΙ—e, yatada kabbaran sallah, ko kunya bayaji.

(Tir da hali irinnaka Zaid, sallah da rana faΙ—e faΙ—e Allah yashirya)

Yana idar da sallah, ya buΙ—e ma’adanan clothes Ι—insa haΙ—e da zaro wasu riga da wando masu matuΖ™ar kyaun gaske, koda yasanya kayan sosai suka amshi jikinsa kasancewarsu masu kalar fari, daga takalmi, belt harzuwa agogon dake Ι—aure a hanunsa kalar maroon garesu, haΙ—aΙ—Ι—iyar rigar suit maroon colour yaΙ—aura akan kayannasa, take yafito a asalin Zaid Ι—insa, wato Abundance, Increase, Increment, Superabundance, Addition, Excess, Surplus, haΖ™iΖ™a Zaid kyakkyawane kuma cikakken namiji da ya isa Ι—aukar hankali ko wacce irin mace ce afaΙ—in duniyar nan, haΖ™iΖ™a Zaid yana da kyakkyawar sura irinta cikakkun maza, haka kuma yanada matuΖ™ar burgewa abubuwan da Zaid kedasu naburgewa suna da tarin yawa, tamkar yanda ma’anar sunansa ke da tarin yawa, shikansa yasan yayi kyau sosai, babu kuma abunda ke tashi a jikinsa sai tashin Ζ™amshi mai sanya nutsuwa da kuma sanya shauΖ™i,

STORY CONTINUES BELOW

Al’adarsa ce kullum kafun yafita saiya bawa hotonta kyakkyawan sumba (kiss), to yauma hakance takasance domin wannan hoton nata yaΙ—auko, ya manna mawa kiss, haΙ—e da maidashi ya aje, kaitsaye yafice daga cikin Ι—akin, ko sauraran kayan breakfast Ι—in da aka aje masa akan derny table baiyi ba yasakai yafice daga cikin Aljannar duniyar falon nasa,, yana fita yashiga cikin motarsa, kai tsaye yawuce babban hotel Ι—in dazasu gudanar da meeting, domin yau sunada gagarumin meeting, zuwa yanzu gaba Ι—aya duk an hallara a wajen shikaΙ—ai kawai ake jira, domin shida ma’aikatansa ne zasuyi meeting Ι—in.

Nigeria

Yau kimanin sati guda kenan tunda Dr Sadeeq yazo baisake zuwaba, Ι“angaren Zahrah kuwa sosai takesamun sauΖ™i acikin zuciyarta, sakamakon karatun Al’Qur’ani da tariΖ™e babu dare ba rana, zuwa yanzu ta dangana komai nata ga Allah, tasan ko ba daΙ—e ko ba jima zai bi mata haΖ™Ζ™inta.

Zaune take a tsakar gidannasu tazuba uban tagumi, amma a zuciyarta karatu takeyi, Inna ce kishingiΙ—e a gefenta, tana koran sauron dasuka addabeta kasancewar dare yasoma rufawa domin kuwa har an idar da sallan magriba,,

Baffane yashigo cikin gidan fuskarsa Ι—auke da fari’a, Inna ce kawai ta amsa masa sallaman da yayi, kallon Zahrah yayi haΙ—e da cewa “tashi ki Ι—auko hijabinki likita na jiranki a waje”

Wani irin mummunan faΙ—uwa gabanta yayi, domin dudduniya a yanzu babu abun da zai Ι—aga mata hankali kamar ace wai wani naΖ™iranta a waje, sam itakam tagama cire Ζ™auna da sake zuwa Ζ™iran wani, bata Ζ™aunarma koda sake fita waje ne,

“Wai ba magana nakeyimiki bane Zahrah kin shareni kuma bayan kinajina!” Baffa yafaΙ—a cikin faΙ—a faΙ—a,

Kuka Zahrah tafashe dashi haΙ—e da Ι—ago idanunta, ta kalli Baffa cikin muryan kuka tace “Baffa kataimakeni dan Allah, wallahi banso wani abu yasake faruwa da rayuwata !! “

“Ikon Allah, Malam kajita ko zata sake Ι“arar mana da daman da muka samu na biyu, saikace akanta aka fara yin fyaΙ—e!” Inna tafaΙ—a cikin Ι—aga murya,,

Da gudu Zahrah tajuya ta shige cikin Ι—akinta haΙ—e da faΙ—awa kan gado tashiga rera kuka mai sauti, itakam batasan yanda zatayi da rayuwarta ba, batasan wasu irin iyaye bane Baffa da Inna, son zuciyarsu tayi yawa, kansu kawai suka sani, anya kuwa zasu rabauta da rahamar Allah ? cutar da maraya abune wanda ba kyau, kuma sunsani amma suke take saninsu, “Ya Allah kataimakeni !” tafaΙ—a cikin muryar kuka,

“Banni da’ita Salame nida itane, ai inbazata fita ba shi zaishigo cikin gidan ” Baffa yaΖ™are maganar yana mai nufar Ζ™ofar fita daga gidan.

Dr Sadeeq ne tsaye a jikin motarsa yasha sky blue Ι—in shadda sai tashin Ζ™amshi yake,

Baffa yafito fuska a sake kai tsaye yanufeshi, “Yauwa likita ka’iso saikuyi maganar acikin gida ko, kasan mutumiyar taka sai a hankali” Baffa yafaΙ—a still washe da baki, like namesake Ι—ina (fatiwasha lol), ba musu Dr Sadeeq yarufa masa baya suka shiga cikin gidan.

Yauma dai a tsakar gidan yazauna duk da cewa babu yawancin haske a tsakar gidan amma akwai hasken farin wata.

“Wai Zahrah bazaki tashi kije bane, nacemiki gashi yashigo har cikin gida, dan Allah Zahrah kada ki watsamana Ζ™asa a ido, kidubi girman mutumcin dayayi miki sanda kike ciwon hauka kitashi kije ” Inna tafaΙ—a cikin lallami.

“Ciwon Hauka kuma Inna?” Zahrah ta tambaya cike da mamaki domin dai ita a saninta batayi wani ciwon hauka ba,

“Ƙwarai kuwa kedai tashi kije kawai” Inna ta faΙ—a still cikin lallami, bawai don tasoba haka tasanya hijab haΙ—e da ficewa daga cikin Ι—akin.

Tun fitowarta a cikin Ι—akinnata ya kafeta da idanunsa, har taΖ™araso can gefe dashi ta zauna, haΙ—e da takurewa waje Ι—aya tana matsan Ζ™walla,

“Saiyaushe zaki daina kuka ne?” Dr Sadeeq yatambaya cikin tattausar murya,

STORY CONTINUES BELOW

Shiru tayi bata amsa masa ba domin jin kalamansa take tamkar zuban narkakken dalma acikin kunnuwanta,

“Matsowa yayi gaf da ita, har tana iya jiyo Ζ™amshin turarensa, babu wani tsoro kokuma Ι—ar ya sanya hannayensa akan kumatunta yashiga share ma ta hawaye, sosai jikinta yaΙ—auki rawa domin tayi matuΖ™ar tsorata da hakan,

“Banason kukanki Zahrah, nasani dole kina buΖ™atar ayi miki uzuri, kinajin ciwo da damuwa a cikin ranki, kuma kinada buΖ™atar kyakkyawan kulawa, kidaina min kallon wani bare kokuma na daban, kiyi mini kallon Ι—an uwanki, wanda zaki iya gayawa damuwarki, inaso kifaΙ—amin duka damuwarki kinji Ζ™anwata, nasan zakiji sanyi idan kika faΙ—i ko kaΙ—anne daga cikin damuwarki !!” Dr Sadeeq yayi maganar cikin lallashi dakuma tausasawa,

Kuka takuma sanyawa mai sauti, domin kuwa tabbas abun daya faΙ—a Ι—in hakanne, tana buΖ™atar mai kulawa da’ita, tana buΖ™atar Ι—an uwa mai Ι—aukar damuwarta, saurin Ι—ago da kanta tayi ta kallesa, sakamakon jin hannayensa da tayi akan nata,

Kai ya jinjina mata batare da yace da ita komaiba, yana kallonta tayi kuka harta Ζ™oshi, a hankali take sauΖ™e ajiyar zuciya, kofin ruwan dake gefensa ya Ι—auka, haΙ—e da kawai bakinta, babu musu taΙ“uΙ—e baki ta soma sha, domin kuwa yanda zuciyarta ta bushe tana buΖ™atar ruwan,, saida tasha fiye da rabi kafun ta tsagaita da shan ruwan, sosai taji zuciyarta tasoma dawowa daidai nutsuwarta kuma yasoma sauΖ™a,,

“Yaushe zaki koma makaranta ?” Yajefomata tambayar kansa tsaye, kallon mamaki tabisa dashi, domin kuwa ko a wasan mafarki bata sake kawo sake zuwa makaranta acikin zuciyarta ba, itakam ai duk wani farinciki yawuce mata,

“Kada ki yarda da abun da zuciyarki takecewa, ba’akanki aka faraba, haΖ™iΖ™a abune mai ciwo amma idan kika daure zuciyarki, zaki iyayin rayuwar farinciki kamar kowa” Dr Sadeeq yafaΙ—a cike da son Ζ™arafafa mata guiwa,

“Kada kayi Ζ™oΖ™arin yaudarana domin kuwa sam banda wani sauran farinciki, yaruguzamin duk wani burina, to yanzu inaso kasanar dani shin menene amfanin karatuna bayan zuciyata cike take da Ζ™unci? kuma miye amfanin farincikina bayan rayuwata ke waye take da duhu ?, zanfaΙ—ama damuwata domin nayarda dakai, inajin ciwo mai zafi a zuciyata bankuma san ranan warkewarsa ba, shin maiyasa zaka ce nayi farinciki bayan kasan cewa bazantaΙ“a samuba ?”

Ɗan gajeren murmushi yayi haΙ—e da matse hannayenta gam acikin nasa, “Saboda inada yaΖ™inin baki farinciki mai Ι—orewa, amma saikin daina sakanki a damuwa “

Wani irin kallo tawatsa masa wanda yake nuni da cewa tana buΖ™atar Ζ™arin haske akan maganganun nasa.

“Zahrah ke yarinyace mai Ι—auke da tarin Ζ™uruciya, kinaga yadace kibar rayuwarki tatafi a haka ?”

Dr Sadeeq yatambaya yana mai kafeta da idanu.

“Haka Allah yatsaramin, BAZAN BUTULCE BA, yadda da Ζ™addara yana da kyau, NAYARDA DA ƘADDARA TA, saidai kuma bazan mantaba har abada, babu mai aurena, babu kuma mai tallafawa rayuwata, zanΖ™are rayuwata acikin Ζ™unci, idan har kaΙ—aukeni Ζ΄ar uwa kamar yadda kafaΙ—a, to inaso ka yi tunani shin wacce ta tsinci kanta acikin mummunar Ζ™addara irin tawa akwai sauran farinciki da yarage mata?, ni yarinyace haryanzu bangama sanin rayuwaba, amma tabbas nasan mai kyau dakuma marar kyau, saboda haka rayuwata a gurΙ“ace take, yariga daya ruguzata, bakuma zata taΙ“a kafuwa ta tsaya da Ζ™afafunta ba har abada, BANI DA ZAƁI likita amma akwai Allah ya isarmin komai!!” gaba Ι—aya hawaye yagama wanke mata fuska, wannan karan ba iya zuciyarta bace tayi rauni hadda tashi zuciyar, lallai Ζ™addaran Zahrah mummuna ce, amma kuma yazama dole yatsaya yakawar mata da duk wani duhu dake rayuwarta shi mai iya dawo mata da farincikin tane idan harzata amince, amma yasani Zahrah ta yanke Ζ™auna gaduk wani Ι—a namiji,

“Likita ga abinci ko” Inna takatsemusu tunanin da sukeyi su dukansu.

Inna tana aje abincin tajuya tashige cikin Ι—aki, kallonsa yamaida kan Ι—an Ζ™aramin bakinta dake bushe, sannan yakuma maida kallonsa kan idanunta, a matsayinsa na mutum mai karantar yanayin Ι—an adam, take yakaranci halin da take ciki, bayajin yunwa ko kaΙ—an domin saida yaci abinci kafun yafito, amma saboda dalili Ι—aya yasa yajawo kwanon abincin gabansa, shinkaface Ζ΄ar gida jalof, ko mai batajiba ballantana albasa, amma haka ya share, yakai loman abincin cikin bakinsa, taunawar farko yaci karo da dutse amma haka dolensa ya basar (readers likitafa yagamu da girkin manya Inna, lol?).

“Zo muci” yafaΙ—a a taΖ™aice,

Saurin kallonsa tayi haΙ—e da girgiza kanta, domin ita yanzu abinci baya gabanta, damuwarta ma abincine a wajenta,,

Babu alamar wasa akan fuskarsa kaitsaye yanufi bakinta da hanunsa wanda yake Ι—auke da Ζ™wayoyin shinkafa domin da hanu yakecin abincin,,

SaΖ™are haka tayi tanakallonsa domin wannan shine karo na farko a rayuwarta da wani Ι—a Namiji ba muharraminta ba ya taΙ“a yunΖ™urin bata abinci a baki,

Kai tagirgiza masa alamar bataso haΙ—e da kawar da kanta gefe,

“Kinaso muyi faΙ—a kenan, kuma hakan nanufin baki Ι—aukeni Ι—an uwaba, nasan wunin yau bakisa komai a cikin kiba, sbd haka banason gardama, idan kuwa kikace bahaka ba, to akwai alluran da na taho da’ita, yanzu sainasa Baffa da Inna su riΖ™emin ke na yi miki har guda uku!! ” yaΖ™are maganar in a serious tone, aikuwa ya faΙ—ar mata da gaba domin kuwa tsoron alluran da takeyi haryazarce tunanin mutane, “Haaaa” Dr Sadeeq yafaΙ—a still yana kusanta hanunsa ga bakinta, tamkar dai za abawa Ζ™aramin yaro abinci.

“Basaikabani ba zan iya ci!” Zahrah tafaΙ—a cikin raunanniyar muryarta,

“To ci ingani” Shima yafaΙ—a yana mai turo mata kwanon abincin gabanta, ahankali ta sa hanu ta tsakuri abincin, tamkar wacce akace ta tsakuro garwashin wuta da hanunta, daΖ™yar ta iya buΙ—e baki ta kai loman abincin bakinta, murmushi yayi haΙ—e da sanya hanunsa acikin kwanon abincin yasoma ci, duk da cewa ba daΙ—in abincin yakejiba, adole Zahrah take kai loman abincin bakinta bayanda ta’iyane kawai,,

Lomanta huΙ—u ta soma kwarara amai a wajen tamkar zata amayar da Ζ΄aΖ΄an hanjinta, miΖ™ewa tayi daga tsugunen da take domin tasoma Ι“ata jikinta da amai, aikuwa wani irin jiri ne ya Ι—e beta take ta faΙ—a kan Dr Sadeeq dashima yake yunΖ™urin tashi tsaye,, gaba Ι—aya yatarota tafaΙ—a cikin Ζ™irjinsa, yayinda aman dake jikinta ya gogu ajikin kayansa,,

Da sauri su Inna da Baffa suka Ζ™araso wajen domin tundaga Ι—aki sukejin Ζ™aran amannata, “Lafiya likita maiyasameta kuma ?” duka suka tambaya cikin Ζ™osawa, da’alama dai sungaji da lamuranta.

” Bakomai inaga olsa (ulcer) ce kawai ke damunta ” Dr Sadeeq yafaΙ—a yana mai Ζ™oΖ™arin shimfiΙ—eta a akan tabarman da suke zaune,

Saidai gaba Ι—aya ba Ζ™arfi a jikinta, saboda haka duk ta narkemasa a cikin jiki, yayinda shikuwa zuciyarsa ke tsananta bugawa, addu’a yake a zuciyarsa Allah yasa ba abun da yake zargi bane ke damun Zahrah idan kuwa abun da yake zargine tabbas babban tashin hankali na gaba…

(Wani tashin hankali munbanu readers ?, Allah yasadai bacikine da ita ba, da Zaidu ya yi aiki mai tsada ? )A hankali Doctor ya kwantar da ita, cikin sanyin jiki yanufi motarsa don Ι—auko jakarsa ta aiki, domin dama daga office yake yabiyo tagidannasu,, Allah yasa ba abun dayake hasashe bane yake shirin faruwa, lallaiko idan har ya zamana Zahrah ciki ne da ita, to fa shikansama yashiga tashin hankali, bawai ita kawai ba, domin yasan Ι—an guntun tsarin daya shirya rugujewa zaiyi, to ina kuma ga Zahrah wacce bata gama warkewa daga ciwon dake jikinta ba, kuma ace taΖ™ara faΙ—awa cikin azabar wani ciwon, tabbas yasan tashin hankalin da zata shiga sai ya take wanda tashiga a baya,, jiki a saluΙ“e haka Dortor Sadeeq yadawo cikin gidan, zuwa lokacin har Inna ta Ι—auketa takaita cikin Ι—aki.1

Tana kwance akan Ζ΄ar katifarta, sai faman sauΖ™e numfashi take a hankali, dagani kasan aman da tayi ya galabaitar da’ita sosai, zama yayi gaf da’ita, haΙ—e da kama hanunta, lokaci guda yaji jikinta yaΙ—au zafi sosai, kayan aikinsa dake cikin jakarsa ya ciro ya fara yi mata Ζ΄an gwaje gwaje,

Wata irin Ζ™aΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya Dr Sadeeq ya sauΖ™e sakamakon gano abun dake damun Zahrah da yayi, duk da cewa baiyi mata gwajin ciki ba, amma a iya Ι—an bincikensa da yayi ya gano cewa bata Ι—auke da ciki, ulcer ce kawai tayi mata mummunan kamu, sakamakon yunwa daya samu mazauni acikin cikinta.1

Kallonsa yamaida kan Baffa haΙ—e da cewa ” Bawani babban damuwa bane ulcer ce, yanzu zanje na Ι—auko wasu allurai a asibiti sainazo nayi mata, insha Allah komai zaiyi dai dai”

“To likita Allah yayi albarka muna godiya sosai !” Baffa yayi maganar cike da yabawa Ζ™oΖ™arin Dr Sadeeq.

MiΖ™ewa Dr Sadeeq yayi haΙ—e da sakai yafice daga cikin Ι—akin, yana fita su Inna ma suka mara masa baya.

Kwanciya tayi lamo tamkar wacce ruwa ya Ζ™are mawa a jiki, gaba Ι—aya jinta takeyi bata da kuzari, gawani irin zafi da Ζ™una da Ζ™irjinta keyi mata,,

Koda Dr Sadeeq ya Ι—auko magunguna da Alluran da yakamata ace yayi mata, sai da ya biya ta wani katafaren wajen sai da kayan marmari yasaya mata dangin su apple da su inabi hadda abarba, bai tsaya anan ba hadda fresh milk saida yabiya ya saya, gudu yashiga sharawa akan titi, burinsa Ι—aya shine yaje yabata taimako mai kyau, sosai yakejin tausayinta, saboda ta cancanci a tausaya mata, daga wani Ι“angare na zuciyarsa kuwa idan yatuno da cewa ba ciki bane da’ita, sai yaji wani irin sanyi da nishaΙ—i na ratsa zuciyarsa, wanda ya alaΖ™anta hakan da cewa bayason tasamu ciki saboda zata sake shiga wani hali marar daΙ—i. (kuji shifa? wai hakane reaΙ—ers?)

Mintuna Ζ™alilan ya iso Ζ™ofar gidannasu.

Koda yanemi Inna da tayi masa iso zuwa Ι—akin Zahrah’n, cewa tayi yashiga kai tsaye ai anzama Ι—aya su yanzu Ι—an uwa suka Ι—aukeshi (hmm)

Yanda ya barta haka yataradda ita sai dai yanzu idanunta a lumshe suke, “Zahrah!!” yaΖ™ira sunanta dai dai lokacin da yake Ζ™arasawa kusa da’ita.

A hankali ta buΙ—e idanunta tasauΖ™esu a kansa, Ι—an guntun murmushi yayi mata, wanda yasanya gabanta mugun faΙ—uwa, domin kuwa murmushin nasa yatuna mata da murmushin Oga Babba (ZAIDU manyan maza, lol), take taji wani irin abu ya toshe mata maΖ™oshi, yayinda zuciyarta tayi Ζ™unci.

STORY CONTINUES BELOW

Aje Ζ™atuwar ledan dake hanunsa yayi, haΙ—e da zama akan katifarta ta, “Tashi ki zauna” yafaΙ—a yana mai kafeta da ido, kai kawai ta girgiza masa alamar bazata iya tashi ba, ajiyar zuciya ya sauΖ™e, haΙ—e da kamo hannayenta duka biyu ya Ι—agota zaune, duk da cewa yana matuΖ™ar jin shock idan yataΙ“a jikinta, amma babu yanda zaiyi dole hakan shine mafita.

Ledar daya shigo da’ita ya buΙ—e, haΙ—e da Ι—auko apple guda Ι—aya ya miΖ™a mata, kallonsa kawai tayi haΙ—e da kau da kanta gefe,

“Magani bazaiyi aiki a jikinki yadda ya kamata ba, harsai kinci abinci, idan kuwa kikasha magani bakici abinci ba zai wahalar dake sosai, dan Allah banason gardama Zahrah, nasan kuma kema kina buΖ™atar abinci, don haka ki karΙ“i apple Ι—innan kici, ciwon ulcer bazai taΙ“a sake kiba matuΖ™ar kina zama da yunwa!!” yaΖ™are maganar cikin lallashi.

Ɗan Ζ™aramin bakinta taturo gaba haΙ—e da Ι“ata fuska, sam batason cin wani abu daga garesa, amma yana Ζ™oΖ™arin tursasata dole, kuma yayi gaskia dayace tana buΖ™atar abinci, tabbas ita kanta tasan tana buΖ™atar abinci.

“Yauwa Zahrah nasan dama keΙ—in maijin magana ce, karΙ“a kici ko!” yaΖ™are maganar yana mai marairaice fuska, haΙ—e da kusanto da apple Ι—in dai dai saitin bakinta.

Hanu tasa ta karΙ“i apple Ι—in, a hankali take gutsuran apple Ι—in kamar mai gutsuran magani, duk da kuwa cewa taji test Ι—inshi a cikin bakinta,, tana cinye apple Ι—in ya miΖ™o mata goran fresh milk mai sanyi.

“Ungo wannan ma ko kaΙ—anne kisha, nasan zai taimaka kuma idan kika sha bazanmiki allura ba!”

Saurin kallonsa tayi, don tabbatar da abun da ya faΙ—a, aikuwa idan dai har bazai yi mata allura ba idan tasha, to lallai zatayi Ζ™oΖ™ari tasha Ι—in,

“Ka tabbata bazakamin alluraba idan nasha?” tafaΙ—i maganar a sangarce, cikin kuma yanayi na marar lafiya,

“Bazan miki allura ba Zahrah, idan dai harkika sha, kuma koda zan miki ma kaΙ—an zanmiki kuma bamai zafi ba!” yaΖ™are maganar yana murmushi.

Take tasake turΙ“une fuska haΙ—e da turo baki.

“Nifa wasa nake miki bawata allura dazan miki !” Dr Sadeeq yafaΙ—a yana dariya Ζ™asa Ζ™asa.

KarΙ“an goran fresh milk Ι—in dake hanunsa tayi, haΙ—e da kafa kanta tasoma sha, tun asalinta ita mai son madara ce, haka kuma fresh milk yana Ι—aya daga cikin abubuwan da takeso, sabo da haka sosai tasha har saida taji cikinta yacika, take kuma Ι—an kuzari yasoma dawo mata, miΖ™o masa goran tayi alamar taΖ™oshi,

“Kishanye duka” yafaΙ—a a taΖ™aice,

“A’a naΖ™oshi” itama tabasa amsa ataΖ™aice,

“Okay to mai kikeson ci yanzu kuma?” yatambaya yana mai tsareta da idanu.

“Babu” ta basa amsa a taΖ™aice,

Kansa kawai yajinjina haΙ—e da Ι—auko drugs Ι—in daya taho mata dasu yasoma Ι“arewa yana bata, sai ta rufe ido haΙ—e da Ζ™anΖ™ame jiki sannan take iya sha, shiko dariyama take basa, bai taΙ“a ganin mai tsoron allura da magani kamarta ba.

Yana gama bata maganin yace ta kwanta, batayi Ζ™oΖ™arin musa masa ba, ta kwanta domin kuwa kafun yace mata kwantan, idanunta harsun fara rufewa,, “Zahrah!” yaΖ™ira sunanta, shiru babu amsa kuma bata ko motsaba sai idanunta da suke buΙ—ewa suna rufewa a hankali, da’alama dai yabata wani magani ne mai matuΖ™ar kashe kuzarin jiki.

Dariya yayi Ζ™asa Ζ™asa haΙ—e da cewa “Yarinta da daΙ—i”

zuΖ™a zuΖ™an alluran daya taho dasu guda biyu, yaciro acikin ledan haΙ—e da haΙ—a komai da komai wanda ya kamata,

RiΖ™e alluran yayi a hanunsa haΙ—e da mai da kallonsa ga Zahrah wacce take kwance lamo, a hankali yasanya hanunsa ajikinta haΙ—e da juyata, saida ya rumtse idanunsa shima kafun ya’iya yi soka mata alluran, yana gamawa ya juyata Ι—aya gefen ma yayi mata, sosai taji zafin alluran amma bata da bakin magana, sai dai hawaye da suka soma gangara daga cikin idanunta.

STORY CONTINUES BELOW

“kiyi haΖ™uri Zahrah Ζ΄an mata, dolece tasa namiki alluran, inaso naga kinsamu lafiya ne!” Dr Sadeeq yafaΙ—i maganar cikin tausasa murya, bayan yashare mata Ζ™wallan dake sauΖ™a a gefen fuskarta, miΖ™ewa yayi tsaye haΙ—e da sakai yafice daga cikin Ι—akin, bayan yatattara kayan aikinsa.

Bai taradda Inna a tsakar gida ba sai Baffa, don haka a gurguje yayi masa sallama, yatafi sbd dare yasoma rabawa.

Ɓangaren Zahrah kuwa tun kafun Dr Sadeeq yafita bacci yayi awon gaba da’ita, domin daga magungunan har alluran da yayi mata suna saka bacci.

A hankali yake tuΖ™in motar tasa, fuskarsa cike take da annuri, Situation Ι—in Zahrah kawai yake tunawa, sosai komai nata yake burgesa, musamman ma tsoronta, hakanan yakejin kansa cikin nishaΙ—i idan yana tare da’ita, baikumasan dalilin faruwar hakanba.

Koda ya yi parking motarsa kai tsaye Ι“angaren mahaifiyarsa ya nufa, domin yau ko gaisawa basuyi ba ya fice daga gidan,

Koda yashiga falonnata bai isketa ba, don haka kaitsaye yanufi bedroom Ι—inta domin yanada yaΖ™inin cewa zai taradda ita acan.

Knocking Ζ™ofar bedroom Ι—innata yashigayi a hankali, jin knocking Ι—in ya tsananta ne yasa taba wa mai knocking Ι—in umarnin shigowa, domin dama tana da yaΖ™inin cewa shiΙ—inne kasancewar taji Ζ™aran shigowar motarsa cikin gidan.

Zaune ya’isketa akan sallaya, da’alamu idar da sallan nafilanta kenan.

HarΖ™asa ya durΖ™usa ya gaidata cike da girmamawa, cikin sakin fuska itama ta amsa masa gaisuwarsa haΙ—e da cewa ” Ina kashigane yau tunsafe ?”

Ƙeyarsa yashiga sosawa a hankali, yayinda fuskarsa ke Ι—auke da Ι—an murmushi.

” Am Hajiya aikin office ne ya Ι“oyeni, dana tashi kuma sai na biya ta gidansu Zahrah domin duba jikinta, to danaje sai nasamu batajin daΙ—i !” ya faΙ—i maganar fuskarsa Ι—auke da alamar damuwa.

“Gidansu Zahrah kuma Sadeeq ?, to Allah ya sauwaΖ™a, a kwai a binci, a derny saika Ι—ebi iya yanda zaka iyaci, domin daganinka bakasa komai a cikin ka ba” Hajiya tafaΙ—i maganar cike da kulawa,

“To Hajiya zanci insha Allah” yaΖ™are maganar yana me miΖ™ewa tsaye, sallama yayiwa mahaifiyartasa kafun yasakai yafice daga cikin Ι—akin.

Yana fita Hajiya tasaki Ζ™wafa haΙ—e da cewa

“Nasan maganinka aure zanyimaka ko da baka shiryaba, natabbatar hakan zai sa ka rage yawan kaiwa dare a waje, kullum kai baka da hutu aiki tamkar engine, duk kuma rashin iyali shiya jawo hakan “.

Yana isa Ι—akinsa yasoma rage kayan jikinsa, Ι—an Ζ™aramin towel ya Ι—aura haΙ—e da faΙ—awa bathroom yasakar mawa kansa shower, cikin zuciyarsa kuwa cunkushe take da tarin tunanuka kala kala, haΖ™iΖ™a yasan cewa yana buΖ™atar mace akusa dashi, domin dai shiba dutsi bane da zai zauna haka Ζ™iΖ™am ko da yaushe, dole yana buΖ™atar wacce zata na taimakawa wajen enjoying life Ι—insa, tun ba yauba yagane cewa yana Ι—aya daga cikin maza masu yawan buΖ™ata, amma kuma sosai yake Ζ™oΖ™ari wajen shan pills wanda zasu sama masa relief, a gurguje yayi wankan yafito, wata brown Ι—in jallabiya mai kyau yasanya bayan yatsane ruwan dake jikinsa, kulan abincin daya Ι—auko a falon Hajiyarsa yajawo haΙ—e da buΙ—ewa, jallof Ι—in shinkafa ne sai coslow, kaΙ—an ya tsakura a cikin plate yasoma ci, gaba Ι—aya tunanin Zahrah yacika masa zuciya wani irin feeling yakeji a kanta, idan yatunota sai yaji nishaΙ—i ya sauΖ™a acikin zuciyarsa, yanason komai nata, idan tana kuka tanayimasa kyau sosai, haka ma idan ta kwaΙ“e fuska bakaΙ—an ba take kyau, gaskia tana da abubuwan burgewa da yawa, da tunaninta yasamu ya kammala cin abincin duk da cewa baiwani ci mai yawa ba, saida yafita ya Ι—anΖ΄i exercise kafun ya dawo ya kwanta, domin a matsayinsa na likita yasan illan dake cikin kwanciya daga cin abinci..

Washe gari

Alhamdulillahi tatashi da Ζ™arfi a jikinta, sai dai Ι—an abun da baza a rasa ba, tun tashinta da haushinsa ta tashi, domin jiya tanaji tana gani haka ya yaudareta yayi mata allura, bayan yagama kashe mata jiki da Ζ™wayoyin da ya bata, don haka bakinnan a Ι—ane yake ita adole tana fushi da likita.

Kasancewar yau Asabar babu aiki, yasanya bai tashiba harsai 9 na safe, wanka yayi yashirya cikin kaya masu kyau haΙ—e da baΙ—e jikinsa da daddaΙ—an turare, motarsa yanufa direct bayan yafito daga Ι“angaren Hajiyarsa, JABI LAKE yanufa inda yayiwa Zahrah siyayya sosai.

(hmm readers kunaga zaΖ™ewar doctor batayi yawa ba kuwa ?)

Yaukam har zauren cikin gidan yashiga anan yatsaya yasoma kwaΙ—a sallama, Cike da zumuΙ—i Inna dake zaune a tsakar gida tasoma amsa sallaman nasa, domin tasan bazai shigo hanu rabbana ba, sauran kayan maΖ™ulashen da yasa yawa Zahrah jiyama ita tacinyesu.

“Iso mana likita, ai dakazo kawai ka iso, bawani nuΖ™u nuΖ™u nanma fa gidan kune !!” Inna tafaΙ—a fuska a sake,

Ɗan murmushi kawai Dr Sadeeq yayi haΙ—e da Ζ™arasa shigowa cikin gidan, akan tabarma ya zauna kamar koda yaushe,

Yana zama Zahrah tafito daga cikin banΙ—aki, daga ita sai Ι—aurin zani a Ζ™irji sai kuma Ζ΄ar Ζ™aramar lufaya dake jikinta, kallo Ι—aya zaka mata kasan cewa daga wanka take, saurin Ι—auke idanunsa yayi daga gareta, yayinda ita kuma tayi saurin sunkuyar da kanta Ζ™asa, sam bata zaci ganinsa ba awannan lokacin. Sumi sumi haka ta raΙ“a tashige cikin Ι—akinta.

Bayan sungama gaisawa da Inna ne ya yayi shiru haΙ—e da sunkuyar da kansa Ζ™asa, sarai Inna tasancewa wajen Zahrah’n yazo don haka kai tsaye tace masa yashiga yasamu Zahrah’n aciki.

Shikam harga Allah bayason shiga Ι—akinta, domin kaΙ—aituwar mace da namiji a waje Ι—aya hatsarine, amma ya ya’iya tunda yalura cewa iyayen riΖ™onnata Ζ™aramin tunani garesu.

Tsaye take atsakiyar Ι—akin, saka rigarta kenan ko zip Ι—in rigarma bata gama jaba, jin sallamansa yasa tayi saurin dawo da kallonta bakin Ζ™ofar, harta fara zaton ko kunnenta ne yaji hakan ba sallamarsa bane, sai kuma taga yashigo cikin Ι—akin, da sauri ta matsa jikin bango ta manne bayanta, domin gaba Ι—aya bayanta a waje yake,

“Uh sorry nashigo kinasa kaya ko” Dr Sadeeq yafaΙ—a yana mai kallonta.

Harara ta gallamasa haΙ—e da turo bakinta gaba, dagani kasan fushi take.

Dariya yasanya harsai da fararen haΖ™waransa suka bayyana,

“Fushi kikeyi dani ko?, to ai balaifina bane, dolece tasa nayi miki alluran don ki samu sauΖ™i, yanzuma kuma wasu alluran nazo nayi miki” yafaΙ—a yana gimtse dariyarsa.

Kuka Zahrah tasanya haΙ—e da sake matsewa ajikin bango,

“Dan Allah kada kamin, banason allura kataimakeni!” tafaΙ—a cikin muryar kuka da tsoro.

“Shiiii kada kitaramana jama’a madam, ni ba allura zanmiki ba wasa nake miki ” Dr yafaΙ—a yana mai Ι—aura yatsansa Ι—aya akan laΙ“Ι“ansa alamar tayi shiru.

“Ni bazansake yarda dakai ba, ai jiyama cewa kayi ba allura zakaminba, amma kuma shine kabani wani abu nasha kamin, ni bazan sake yarda dakai ba!” Zahrah tafaΙ—a tana matsar Ζ™walla daga idanunta.

“Hahhh to ya’isa haka yanzu kam dagaske ba allura zanmiki ba, juyo na jamiki zip Ι—in kinji Ζ΄ar Ζ™aramar Ζ™anwata !” Dr Sadeeq yafaΙ—a cikin tsokana,

“Dan Allah kafita banaso, zanzo na sameka, domin ni ba wani namiji da zai sake taΙ“amin jiki ehe !” Zahrah ta faΙ—a cike da shagwaΙ“a.

Wani irin zubawa tsikar jikinsa yayi, domin yanayin yanda tayi maganar kaΙ—ai ya isa sanya jarumin namiji faΙ—awa cikin wani yanayi,

(Hahhhh likita bokan turai, to Zaid ma yafaΙ—a a wani hali, balle kai da bakasan salon mace ba ?)

Nannauyar ajiyar zuciya Doctor ya sauΖ™e, haΙ—e da zura hannayensa a cikin aljihun wandon sa, “Shikenan to tunda kince haka, na baki two minute kacal kisameni a waje, idan kuwa bakifitoba zan dawo na sake iskeki, kuma wlh sai na danneki na jamiki zip Ι—in da Ζ™arfin tsiya” dagajin yanda yayi maganar kasan cewa tsokana ce kawai.+

Kai kawai ta iya jinjina masa alamar cewa taji zata fito Ι—in,

Ɗan gun tun murmushi Dr yayi haΙ—e da sakai yafice daga cikin Ι—akin.

Yana fita ta sauΖ™e nannauyar a jiyar zuciya, haΙ—e da sanya hanunta a bayanta, taΖ™arasa jan zip Ι—in rigarta, zunbuleliyar hijabinta ta zura akan rigar haΙ—e da ficewa daga Ι—akin, saboda tasan idan bata je bama tabbas zai biyota.

Zaune ta iskesa a cikin rumfar dake barandar gidan nasu, can gefe dashi ta zauna haΙ—e da kawar da kanta gefe domin kuwa ta lura gaba Ι—aya idanuna akanta suke,

“Banason wasa matso kusa kisha maganinki !” yafaΙ—a babu alamar wasa akan fuskarsa.

Ɗan Ζ™aramin bakinta tacunno gaba haΙ—e da sake Ι“ata fuska, Allah ya sani ta tsani magani sosai da sosai, batama so ayi mata ko da zancen magani ne.

Batare da ya sake ce da ita komaiba yashiga Ι“allo Ζ™wayan maganin daga jikin tablet Ι—insu, yana sawa a hanunsa, har sai da yagama Ι“are iya wanda zatasha a yau Ι—in, miΖ™o mata maganin yayi haΙ—e da bata goran ruwa,

Fuska a daΖ™une haka ta karΙ“i magananin saida ta rumtse idanunta sosai kafun ta iya haΙ—iye maganin, gashi dama irin magani mai Ι—acin nan ne,

“Kishirya next week zaki koma makaranta ” Dr Sadeeq ya faΙ—a yana mai latsa wayar da dake riΖ™e a hanunsa, bakuma alamar wasa akan fuskarsa.

Saurin dawo da kallonta garesa tayi, haΙ—e da girgiza kanta, “A gaskia ni bazan sake komawa makaranta ba !” Zahrah tafaΙ—a cikin Ι“ata rai,

“Maiyasa ? ” Dr Sadeeq ya tambaya kai tsaye.

“Saboda babu amfanin hakan, ana karatune don a inganta rayuwa, to nikuma tawa rayuwar tajima da rugujewa, mai yasa zanΙ“ata lokacina wajen gyara abun da bashi da kyau, bakuma zai gyaruba, na haΖ™ura da komai zanjira mutuwata kawai !” Zahrah taΖ™are maganar cikin yanayi mai nuni da cewa zuciyarta tagamayin rauni,

” Idan ginin gida ya ruguje, Ζ™oΖ™ari ake a sake gyarasa, akuma sabuntasa har yafi nada Ι—in daya ruguje kyau, da kuma Ζ™awatuwa, shin kinsan maiyasa ake yin hakan? ” Dr Sadeeq ya tambayeta bayan yamai da gaba Ι—aya nutsuwarsa gareta.

“A’a” tafaΙ—a a taΖ™aice.

“Saboda yanada matuΖ™ar amfani gamasu shi, sannan kuma yana da kyau idan karasa dama ta farko, kasake neman wata damar, domin sau dayawa anasamun nasara ne a gaba, bawai a farko farko ba, idan kika ci gaba da kashewa kanki Ζ™argin guiwa, to zuciyarki zata zama mai tsananin rauni, babu amfani idan kikace bazaki inganta rayuwarki ba, amma inaso kisanar dani fa’idan yin hakan, nuna kin yarda da Ζ™addara yana Ι—aya daga cikin mantawa da komai, idan kika zauna a gida, bazaki taΙ“a samun cigaba ba, nasan abun da Zaid yayi miki har yau yana cikin zuciyarki, kuma inada tabbacin cewa idan kinsamu wadataccen ilimi nan gaba, zaki iya yaΖ™i da azzalumai irin su Zaid, please Zahrah kada kicemin a’a, nayi hakanne saboda samamiki sauΖ™i, da kuma cireki a kaΙ—aici !” Dr Sadeeq yaΖ™are maganar cikin muryan tausasawa, dason Ζ™ara mata Ζ™arfin guiwa.

STORY CONTINUES BELOW

Hawayen da suka shiga ambaliya akan fuskarta ta sanya hanu ta share

” Yar zuwa yau banajin akwai wani sauran farinciki daya ragemin a gaba, da wani ido mutanen duniya zasu kalleni? wasu zasu Ι—auka cewa ni nakai kaina garesa, wasu zasumin dariya wasu ko zasumin Allah ya daΙ—a, babu wani namiji da zai tunkareni da sunan soyayya, rayuwata a yanzu tana gudana ne tamkar ruwan shayin da aka sa ma sa lipton amma ba asanya sugar da madara acikin saba, dan Allah kada ka matsa akan cewa lallai saina koma…..”

“Ya’isa haka Zahrah, banason yawan gardama, shin bazakiyi Ζ™oΖ™ari ki inganta rayuwarki ba? haΖ™iΖ™a Zaid yacutar dake, amma hakan bawai yana nufi ya Ζ™arar da rayuwarki bane baki Ι—aya, matan da akamawa fyaΙ—e suna da yawa a duniyarnan, amma kuma hakan bai sa sun tauyewa kansu wani nau’i na jin daΙ—in rayuwarsu ba, ke mai yasa bazaki yi haka ba ? inaso ki manta da komai, kuma daga yau Ι—innan nagama maganata, next week zaki koma school insha Allah, tun yanzu saiki fara shiri !” Dr yafaΙ—a fuskarsa babu alamar wasa.

Aikuwa yanayin yanda taga fuskar tasa a Ι—aure tamau yasa takasa ce dashi komai, hakanan yake mata kwarjini a cikin idanunta.

MiΖ™ewa yayi tsaye, haΙ—e da cewa “Kibiyoni waje inason muyi wata magana”

Saurin kallonsa tayi, domin ita rabonta da fita waje tun randa mummunar Ζ™addaranta ya rusketa, wanda kuma da bazata taΙ“a mantawa ba.

Jiki a saluΙ“e haka ta rufa masa baya, suna zuwa bakin motarsa taja ta tsaya, haΙ—e da sake tamke fuska.

Murfin Ζ™ofar mai zaman banza ya buΙ—e haΙ—e da fiddo wata Ζ™atuwar leda,

” Idan har kika kumamin musu to tabbas zamu Ι“ata dake, sannan kuma wlh allurai shida zan danneki na miki da Ζ™arfin tsiya bandamu ba koda ma sun karye a cikin jikinki, ke kikaso!” Dr Sadeeq yafaΙ—a cikin tsare gida, yayinda yake miΖ™o mata zungureriyar ledan dake hanunsa.

“Dan Allah kayi haΖ™uri kada kamin allura, amma a gaskia ni baxan iya karΙ“an komai daga gareka ba, ni bazan sake karΙ“an abun kowa ba, domin kuwa da haka Zaid yasamu ya cuci rayuwata yasamin babban tabo mai wahalar gogewa!” Zahrah tayi maganar cike da tsoro da kuma Ζ™unan zuciya.

“Alluran dai kikeso kenan, shikenan bana Ι—aukosu dama nazo dasu kusan guda goma” Dr Sadeeq yafaΙ—a yana mai niyar sake buΙ—e murfin motar.

A tamanin Zahrah ta ruga zuwa gida,

Dariya sosai Dr Sadeeq yashigayi, sosai yarintar Zahrah yake burgesa, haΖ™iΖ™a Zahrah yarinyace, domin kuwa kallo Ι—aya zakai mata ka fuskanci cewa tsananin yarinta na damun ta sosai, akan allura gaba Ι—aya ta ruΙ—a kanta.

Baiyi yunΖ™urin komawa cikin gidan ba, sai neman wani yaro yayi yabasa ledan yace ya kai cikin gidan, shikuwa key yayi mawa motarsa yayi tafiyarsa.

Zahrah kuwa tana shiga cikin gidan kaitsaye Ι—akinta tawuce haΙ—e da banko Ζ™ofar ta rufeta gam, faΙ—awa tayi kan katifarta tana mai sauΖ™e a jiyar zuciya, ko da taji Ζ™aran tashin motar Dr Sadeeq Ι—in, wani sanyi taji a cikin zuciyarta, haka kawai yazo ya zurkuΙ—a mata wannnan maka makan alluran nasa, ai wlh bata saΙ“uwa…..

*New York City*

Kwance yake akan makeken gadon sa, daga shi sai Ι—an wani 3 guater jeans, yayin da ya ware Ζ™afafunsa, duk da cewa akan gado yake, amma saboda tsabar iskanci irin na Zayd sanye yake da takalma (toms) aΖ™afarsa, yayinda hanunsa ke riΖ™e da wata zungureriyar kwalbar giya, gefensa kuwa wata kyakkyawar baturiya ce kwance tsirara bako Ι—igon abun rufa tsiraici a jikinta, daganinta kasan irin cikakkun Ζ΄an iskan nanne, gaba Ι—aya ta tsare Zaid da idanunta, sai wani lasan baki takeyi tamkar tsohuwar mayya, bakomai yasa hakan ba, face yanda gaba Ι—aya ta gama kwaΙ—aituwa da Zaid Ι—in, amma kuma yaΖ™i amincewa ya kusanceta, gaba Ι—aya wani irin muguwar sha’awarsa takeji, duk kuwa yanda ta nu namasa zallan karuwancinta a fili, yaΖ™i kusantar ta, saima sake je fata cikin kogin sha’awa da yayi,

Zaid kuwa da gangan yaΖ™i kusantarta, domin yanzu tsagwaran iskanci yake ji dashi, sai ya Ι—auko mace yagama Ζ™waΖ™uleta, yabarta batare da yayi sex da’ita ba, wayarsace tasoma Ζ™ara alamar shigowar Ζ™ira, har Ζ™iran ya katse Zayd bai ko kalli inda wayar take ba balle yasan wake Ζ™iransa,,

Cike da salo irin na Ζ΄an bariki wanda ta yarda cewa idan hartayi masa zai kusanceta, ta sake matsowa daf dashi, a hankali ta zura hanunta acikin 3 guater jeans Ι—insa, haΙ—e da soma shafa kan mararsa a hankali, yayinda Ι—aΖ΄an hanunta ke kan faffaΙ—an Ζ™irjinsa tana shafawa slowly, ta yadda zaiji abun har tsakiyar kansa, cike da Ζ™warewa tashiga murza ….

A hankali yaΙ—ago idanunsa da suka soma sauya launi ya sauΖ™esu akan baturiyar, ai kuwa yayi kyakkyawan gani, domin kuwa fuskar Zahrah yagani ta bayyana akan ta baturiyar, bakomai yasa hakan ba face giyar da yasha da tasoma yi masa aiki, da Ζ™arfin gaske yajawo baturiyar jikinsa, haΙ—e da matseta Ζ™am a Ζ™irjinsa, take jikinsa yasoma Ι“ari,lokaci Ι—aya yashiga bata kyakkyawan romance wanda yasanyata tafara nishin daΙ—i.

Gaba Ι—aya baturiyar nan tadawo masa Zahrah acikin idanuwansa, baisan sai yaushene matsanancin sha’awar da yakemawa Zahrah zata sake saba, a kullum a ko wani daΖ™iΖ™a sha’awar Zahrah sake ninkuwa masa takeyi acikin zuciyarsa,

Hmmm duk jaraba irin ta wannan baturiya yau fa sai dai ta haΖ™ura, domin kuwa Zaid tun kan abunnasa yagama shiga jikinta, yayi saurin tureta gefe, wani irin masifaffen Ι“acin raine yazo masa, Ζ™arya ne yasani ba Zahrahn sa bace wannan, sharrin giyane kawai, idan har giya zata iya sanyawa yaga fuskar wata a matsayin Zahrah, to bata isa sawa Ι—anΙ—anon wata yakasance tamkar na Zahrah’nsa ba, Zahrah da ban take komai nata na dabanne, cikinta a cike yake, bakamar sauran matan dayake mu’amala dasu ba, wanda su gaba Ι—ayansu a wage suke daga ciki har waje, ita kuwa Zahrah daga ciki har waje a haΙ—e take, bakomai yasanyashi ture baturiyar nan gefe ba face jinsa da yayi ya faΙ—a zuruf tamkar anzura Ζ™wallo a raga, bathroom ya wuce kaitsaye yasakarmawa kansa shower.

Itakuwa mayyar baturiyar dolenta ta maida Ι—an fingilan rigarta ta fice daga cikin Ι—akin, cikin matsanancin sha’awa, Zayd ya jangwalo mata bala’i.

Zayd kuwa a daddafe yayi wanka, domin kuwa wani irin ciwo marar sa ke yi, koda yafito a wankan a daddafe yasha tea da lamon tsami, kwanciya yayi lamo yana mai sauΖ™e numfashi akai akai, lallai yazame masa dole yakoma Nigeria kodan Zahrah ma, yazame masa dole yakomawa Zahrah domin kuwa bazai zauna sha’awarta ta kashe shi ba, amma ya Ι—au alΖ™awarin cewa wannan karon bazai mata da Ζ™arfi ba, lallaΙ“ata zaiyi tabasa kanta cikin sauΖ™i, da wannan tunanin bacci yayi awungaba dashi,

(Hmmm ayi bacci lafiya Zaidun Munubiya,lol).

Nigeria.

Yaune ranar da Dr ya shaidawa Zahrah cewa zata koma makaranta.

Don haka tun tashinta, tatashi tanajinta wani iri, gaba Ι—aya ji take gabanta na faΙ—uwa, hakanan take tsarge, gani take tamkar kowa yasan maiyafaru da’ita, a daddafe tayi wanka, wata simple gown tasanya ajikinta, wanda bata da ado ko kaΙ—an, wata Ζ™atuwar lufaya ta zura wanda tsawonsa ya wuce guiwarta. Jin maganarsa a tsakar gidan, yasa taji Ζ™irjinta ya Ι—an buga kaΙ—an, cikin rashin kuzari tafito daga cikin Ι—akin.

Kamar yanda yayi mata kyau, haka shima yaga tayi masa kyau, duk da cewa babu Ι—igon kwalliya akan fuskarta.

“Muje ko!” YafaΙ—a a taΖ™aice, saurin ja da baya tayi haΙ—e da girgiza kanta, domin kuwa ko karen hauka ne ya cijeta, bazata yarda ta shiga motarsa ita kaΙ—ai ba.

“Muje Baffa na jiranmu a waje” Dr Sadeeq yafaΙ—a domin yaga alamar a tsorace take,

Ajiyar zuciya mai Ζ™arfi ta sauΖ™e haΙ—e da bin bayansa, domin kuwa tuni yariga da yayi gaba.

Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 5 BY FATYMA SARDAUNA"