Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

YAREEMA KHALEED CHAPTER 7

YAREEMA KHALEED






CHAPTER 7





*__________?* ko bayan da Nawwara ta Ι—aga abinda taji mahaifin nata ya faΙ—a ne ya Ι—aga hankalinta, da sauri kuwa ta faΙ—a Ι—akin Anty.
+

zaune gefen gado ta ganta ta rafaka uban tagumi, ta dafata tace, “mi Hajiya Saddiqa tace maki?”.

ai gaban Anty sai daya faΙ—i jin ambatar sunan Hajiya Saddiqa, bata taΙ“a sanin da shaiΙ—aniyar mace take mu’amala ba sai data nuna mata halinta, to kome zai faru da ita ai sai dai ya faru da ita amma bazata taΙ“a iya mu’amala da mace Ζ΄ar uwarta ba.

saΙ“o mai girma a wurin Allah, mai aikata shi Allah ya tsine masa, da sauri ta girgiza kanta tace da Nawwara, “babu komai tace dai zata je ta dawo”.

Nawwara tace, “oak, to Anty Baba ne ya Ζ™irani yace wai mu shirya yanzu yasa Yaya ya gama booking zamu wuce Ζ™asar Libya”.

a firgice Anty ta zaro ido dan zancen ba Ζ™aramin razana ta yayi ba, kamin tayi wani yunΖ™uri na magana suka jiyo Ζ™arar jiniya a harabar gidansu.

da sauri suka miΖ™e su duka suka fita, suna isa parlo suka ci karo da Hajiya a tsaye fuskarta da zallar Ι“acin rai

tana ganinsu ta bama Ι—an sandan dake tsaye umarnin ya sama Anty ankwa, take kuwa aka sanya mata ankawa.

rau-rau idanuwanta sukayi, zatai magana cikin tsawa Hajiya ta dakatar da ita da hannu tace,

“dakata karki ce dani komai, munafukar banza kawai maciya amana, muguwa, mai hassada da Ζ™yashi, toki sani makomarki bazatayi kyau ba, domin bazan taΙ“a yafe maki ba kuma bazan barki haka ba”.

tini Hajiya ta bawa Ζ³an Sanda umarni suyi gaba da ita zuwa airport.

*2Hrs 53Mints Letter.*

cikin wannan lokaci jirginsu ya sauka a Ζ™asar ta Libya, suna sauka motar data iso domin su ta Ι—aukesu zuwa masarautar ta Libya.

tin kamin a shiga gaban Anty ke faΙ—uwa, lokacin kuwa da sukai sallama cikin fada jinta tayi kaman tayi mene saboda kunyar data kamata.

Ζ™asa tayi da idonta ta kasa haΙ—a ido da mijinta, cikin tsawa Ζ΄an sandan dake tsare da ita suka ce ta zube gwiwonta Ζ™asa.

Hajiya na shigowa daga bayansu tace da Uncle Badamasi, “kai yau idan harni na haifeka na baka nono, to kamin na Ζ™ifta idona ka saki wannan makirar, ka mata cika biyu ranar data gama idda ka cikashe mata na ukunta”.

take kuwa ya kalla Anty da mugun tsanar halayyarta yace, “Asma’u na sakeki saki biyu”.

Rahinat na ganin Hajiya ta Ζ™wace daga hannun Khaleed daya wani damΖ™eta kawa ance za’a Ζ™waceta tayo wurinta da gudu ta rungumeta.

tsam itama Hajiya ta rungumeta tana hawaye farin ciki fal ranta, “Rahinatu kece”.

kai kawai Rahinat ta Ι—aga mata tana murmushi, tausayi ta bawa kowa na wurin tinawa da cewan fa da tana magana amma a sanadin muguwar Ζ΄aruwarta yau ta zama sai kallo.

Ι“angaren Raihana ma tana ganin Anty ta taso da gudunta tayo wurinta tana kiran,

“Umma na mai jin Ζ™aina, ki bar zubda hawaye matsawar ina raye babu wanda ya isa yay maki wani abu wai shi Ι—aukan hukunci saboda baki da hakkin kowa”

“ni ba mahaifiyarki bace Raihana kamar yanda na faΙ—a maki, duk labarin dana karanta maki Ζ™arya ne gaibu ne, babu wani abu Ι—aya daya faru daga ciki, tabbas Ι—aya nake sanar maki dashi cewan waΙ—an can sune iyayenki na gaskiya kaman yanda na shaida maki, amma sam zancen sun sai daki Ζ™aryata ne, zance ne da shiri na son zuciyata”.wata muguwar damΖ™a Raihana ta bawa kafaΙ—ar Anty, jijjigata ta hauyi kawa ta sami reshe, manyan idanuwanta ta firfito mata dasu waje, numfashi mai zafi take sauke mata aka tana huci, yanayin data koma ya tsorata Anty dan sai ta ganta kawa aljana ko wata horo.
+

cikin in-ina tace da ita, “kika ce mene? kika ce mene?, ina tambayarki kin min shiru kika ce mene?, dama sharri kika haΙ—a domin ki rabani da iyayena?, kikai wa iyayena Ζ™arya”.


duk maganar da take a tsawace take mata su tana wani jijjigata, kan kowa na wurin ya ankare cikin zafin nama Raihana ta Ι—aga hannu ta ware zara-zaran yatsunta ta bawa Anty tas tas a fuska.

“ki gaya min duk dalilin shirinki na yin haka?, ki faΙ—a min dalilinki na sanya rayuwata cikin wahala bayan ina da gata”.

ta faΙ—a tana maΖ™ure wuyan Anty, tana soka mata farcinanta zaΖ™wa-zaΖ™wa.

kakari Anty ta fara ,tini aka taso aka yo kan Raihana ana Ζ™oΖ™arin Ζ™watarta amma kawa wata namijin zaki sai data watsar da kowa Ζ™asa.

“zaki gaya min ko saina feΙ—e ki”.

tai maganar cikin Ζ™araji tana nuna Anty da wuΖ™ar data warta hannun wani dogari.

“kiyi haΖ™uri ,wallahi son zuciya ne, hassada duk ita ta jazamin, na kasance tin auren Sa’adatu da Abdullahi nake baΖ™in ciki ,haka kawai nake Ζ™inta bata re data min wani laifi ba, saboda ta kasance mace mai farin jini kowa sonta yake, haka dangin mazajenmu duk sunfi sonta, shiyasa ni kuma na tsaneta, lokacin data haifi Ζ΄an biyu ji nayi kamar na kasheta saina kasa samun wannan damar shine kamin ta farka Abdullahi yazo nazo na saceki nai replacing da wata gawar jaririya dana sato, kema so nayi na kasheki sai Allah bai bani wannan damar ba, shine na bada rainonki har kika girma nai maki wannan karatun Ζ™aryar, amma wallahi iyayenki mutanen arziΖ™i ne….”

ai bata Ζ™arasa ba Raihana ta soka mata wuΖ™ar dake hannunta take jini ya shiga shatata.

salati kowa ya saka aka mimmiΖ™e tsaye.*__________?* Khaleed ne ya miΖ™e da sauri ya isa wurinta, yana zuwa yay saurin Ζ™wace wuΖ™ar da take neman sake daΙ“awa Anty, yanda take huci shima haka yake huci, wani fincikarta yayi daga kan Anty yay cilli da ita gefe guda
+

“Arrest her”.
mai martaba ya faΙ—i yana daga kan kujerar mulkinsa a zaune.

take aka Ι“ama Raihana handcuff a hannu, hawaye kawai take zubarwa tana bin Rahinatu da mahaifanta da kallo, dana sanin abubuwan da tayi kawai take,soyayyarsu da Ζ™aunarsu gami da tausayinsu lokaci Ι—aya sukai wa zuciyarta mugun kamu,shin ta inama zata fara neman yafiyar Rahinatu.

bayan an fita da Anty Asma’u zuwa asibiti aka samu hayaniyar dake fada ta tsagaita, mai martaba ya buΖ™aci da a kawo masa biro da takarda, miΖ™o masa akai yay rubutu ajiki kana waziri ya miΖ™a hannu ya amsa.

abinda ke jikin takarda ya fara karantowa bayan yace saΖ™o daga mai martaba,
“wannan kotu tana buΖ™atar da a kamo mata waΙ—an nan mutane, Baheer Suhail Albanna, Dameer Suhail Albanna,Salman Suhail Albanna,Abid Suhail Albanna da Yasmeen Suhail Albanna”.

baki Ι—ayansu acikin minti uku aka gabatar dasu gaban mai martaba, kowanne cike da kunya da dana sani banda Sultan Dameer wato mahaifin Raihan.

ba wani Ι“ata lokaci Mai martaba ya yanke masu hukunci.

“haΖ™iΖ™a kunyi kuskure mafi girma, laifukanku suna da yawa Ζ™warai, dan ku Ζ΄aΖ΄ana ne hakan bazai hana ni yanke maku hukunci mai tsauri ba, tambayar da zanyi maku shine wane yay kisan wannan gawar?”.

shiru sukai dukkaninsu ba wanda yay magana, har saida yay sau uku tukunna Abid da shine Ζ™arami ya buΙ—i baki yayi magana cike da tausayin mahaifin nasu, dan yanayinsa kawai ya nuna yana cikin Ζ™unci ,takaici, gami da kunyar abinda Ζ΄aΖ΄an cikinsa sukai duk a saboda kujerar sarauta

“ΩƒΨ§Ω† ΨΆΩ…ΩŠΨ± Ω‡Ωˆ Ψ§Ω„Ψ°ΩŠ Ω‚ΨͺΩ„Ω‡.”

Khulaid ne ya nemi izini da abashi damar yin magana.
aka bashi ya miΖ™e ya bada wani flash, aka soka jikin laptop, take dukkanin abubuwan daya faru na sirrin tattaunawar su Dameer ya bayyana aciki.

su kansu mamaki sukai sose, taya akai har aka sami wannan, Khulaid yace saboda wannan rana yay Ζ™oΖ™arin yaga yana bibiyarsu domin samun hujja.

Waziri yay gyaran murya yace, “bisa wannan taΖ™aitattun hujjoji da kuma shaidu da suka gabata a gaban wannan fada da kuma al’umma, muke fatan kotu zasu saurari irin hukuncin daza’ai ma waΙ—annan azzalumai, bisa ga cutarwar da suka yima Ι—an gatan wannan masarauta wato *SULTAN AYAN* na Ι—ora masa laifin da baiji ba bai gani ba, sannan kuma suka nemi da suga sun cutar da wannan masarauta domin amsar kujerar mulki d akuma gawar Ι—aya daga cikin jakadan da suka kashe”.


STORY CONTINUES BELOW

Mai martaba yace a janye Dameer gefe, su kuma duk a sanya masu ankwa aje a Ι—auresu a gidan kaso, zasuyi rayuwa ta tsawon shekara 40 aciki kana a fito dasu.

“kai kuma Dameer kaida kayi kisa to ka sani a muslunci wanda ya kashe a kasheshi, dan haka za’a horaka tsawon shekara guda agidan Yari kana daga bisani a akaita maka abinda ka aikata”.

sannan Waziri yaci gaba da cewa, “bayan yanke hukuncin waΙ—an nan bayin Allah, yanzu hukunci zai koma kan Raihana bintu Abdullahi wadda tayi mummunan *ƘAZAFI* akan *SULTAN AYAN*, bisa shaida data gabata zamu bi hukunci ta hanyar da Addinin musuluci da shari’a ta tanada ga duk wanda yay *ƘAZAFI* ,kamar yanda Allah maΙ—aukakin sarki ya faΙ—a acikin qur’ani mai girma cikin suratul nur aya ta huΙ—u zuwa biyar, kamar yadda nassi ya tabbatar wanda yay Ζ™azafi yana da hukunci bulala tamanin, a don haka yanzu za’ai wa wannan yarinya bulala tamanin agaban al’umma domin su zama shaida na cewan an yanke hukunci kamar yanda Ubangiji ya umarta”.

ana gama faΙ—in haka Raihana ta zube gwiwoyinta Ζ™asa tana mai kuka sose, zuciyarta take ji tamkar ta fito waje.

sose itama Rahinatu dake jikin Hajiya take kuka, haka zalika Ammi ma kuka take, bazata iya kallon wannan hukunci ba dan haka ta sauke kanta Ζ™asa kan cinyar Abbi.wata sharfaΙ—eΙ—iyar dorina aka shiga laftawa Raihana, tin tana juriya har ta kasa, ihu take zundumawa sose tana roΖ™on ai mata afuwa, ba’a Ζ™yaleta ba sai da aka hattama wannan bulala guda tamanin ajikinta, farar rigar uniform Ι—in prison dake jikinta duk jini ya Ι“ata sakamakon fashewar da jikinta yayi. +

bayan an gama mata kotu ta kuma shaida cewan zata tsare Raihana acikin gidan yari na tsawon watanni biyu domin bata horo mai tsanani duba da irin abubuwan data aikata.

daga nan mai martaba yay bayani da kansa akan tsayawa a tabbatar da bincike kamin yanke hukunci, domin ita kanta wannan masarauta a yanzu tana dana sanin abinda ta aikata a baya, domin data tsaya tayi bincike da duk haka bata faru ba


bayan gama gabatarwar bayanai daga bakin mai martaba, aka Ι—auka su Sultan’s akai gaba dasu.

gabansu Ammi Raihana ta zube , tana kuka take neman yafiyarsu akan abinda ta aikata masu, sannan ta dawo gaban Rahinatu ta rungumeta tsam jikinta, kuka suke duk su du, roΖ™onta take da magiya cikin yanayi mai ban tausayi tana cewan ta yafe mata abinda tayi mata na cutarwa.

“na yafe maki 2win sis, dama tin a lokacin dana fahimci ke jinina ce na yafe maki”.

“na gode sose, sannan dan Allah ina roΖ™on ki tayani neman yafiya wurin mijinki shima ya yafe mani Ƙazafin dana masa, domin na jefe rayuwarsa acikin Ζ™unci”.

sakin juna sukai Rahinat ta maida kallonta ga Khaleed, harara ta watsa masa, gabansa tayi tattaki taje ta tsaya, da yaran kurmaye take masa magana akan ya yafe ma Raihana.

yanda take bayanin ya daki zuciyarsa, bai san lokacin daya rungumota jikinsa ba yana kaΙ—a kansa idonsa a runtse.

“duk abinda kike so shi nake so, idan kin yafe mata na yafe mata, kece mai controllng Ι—ina so you dont have to ask me”.

ya Ι—ago da fuskarta yana kallo idansa jawur yace, “Angel kiyi magana mana”.

fincikewa tayi taje gaban Raihana dake kallon Khaleed, wadda daka kalli irin kallon da take masa kaga kallo mai cike da soyayya.

murmushi Rahinatu tayi ta kamo hannunta da suke cikin ankwa, takardar data yi rubutu akai ta bata ta karanta.

zaro ido Raihana tayi bayan ta gama karantawa tana duba Rahinatu tna kaΙ—a mata kai, wannan abu ne da bazai yiwu ba kar muyi haka dake.

abinda ta rubuta mata shine, _daga wannan lokaci na sadaukar maki da soyayyata 2wins, ke mai son Khaleed ce ni kuma ayanzu mai Ζ™insa ce, dan haka zuwa lokacin da zaki fito a prison Sultan na nan yana jiranki, Rahinatu na mallaka maki shi ya zama naki har abada._

lokacin da aka Ι—iba masu ne ya cika, dakawa da Ζ΄an sanda sukai gaba da ita zuwa gidan kaso.

adu’a akai sarki ya sallami kowa, jama’a duk suka watse, sarki ma ya tashi ya wuce cikin gida, wurin dai ya rage daga su Ammi sai Khaleed.

Khaleed ya nemi kujerar dake kusa da Hajiya ya zauna, kallonsa Hajiya tayi tasa yatsa ta dungure masa kai.

Ζ΄ar dariya yayi yace, “sai yaushe zamu wuce?”.

“sirikina na gode maka, kayi Ζ™oΖ™ari sose da kayi bincike cikin Ζ™anΖ™anen lokaci har ka gano kan wannan Ζ™ulallen al’amari, banyi tinanin zan iya Ζ™yaleka batare dana yi shari’a da kai ba sai sanda ka kirani kake shaida min bayani akan komi, lalle kai mai Ζ™aunar Rahinatu ne ba maΖ™iyinta ba, halin da aka sanya ka shi yasa ka tsaneta, yanzu ya kamata mu tashi mu tafi domin na Ζ™agu Rahinatu ta sami lafiya”.


Hajiya ta kirayi Rahinatu, ta shaidawa su Abbi cewan su zasu wuce egypt aima Rahinatu aikin maΖ™ogaro domin a cire mata wannan abu da suka sanya mata.Uncle Badamasi su Nawwara suka Ζ™irashi suna kuka akan Antynsu, yace shi ba ruwansa babu wani abu da zaiyi akai.
+

suka kira Abbi suka faΙ—a masa shima yace bazai taimaki maΖ™iyiyarsu ba.

jin haka Ammi ta zabari jiki tabi bayansu zuwa asibiti, tana zuwa ta tadda har anma Anty Ι—inkin wurin da Raihana ta daΙ“a mata wuΖ™a, tana kwamce akan gado tana ta kuka.

Ammi tace wallahi duniya da lahira ta yafe mata, ta manta da faruwar komai, Allah ma muna masa laifi mai girma kuma ya yafe mana.


Anty tayi ta mata godiya.

*2hrs 27mints letter.*

saukar jirgin su Hajiya a Ζ™asar ta Egypt.

Cleopatra Hospital, shine asibitin da suka wuce domin aima Rahinatu aiki, ba Ι“ata lokaci aka shiga da ita surgery.

a wanni biyu kacal aka Ι—auka likita ya fito yay ma su Hajiya congrat domin an samu nasaran aiki.

da gudu Hajiya ta faΙ—a Ι—akin cike da murna, tana zuwa ta tsaya tana kallon Rahinatu dake dariya, tace, “Hajiyata”.____?* rungume suke tsam da juna cike da tsantsar farin ciki.
+

Kakus sai tattaΙ“ata take kawa Rahinat ta koma sabuwar halitta.

“Jikalle yanzu dai ina fatan Ζ™alau kike ko?”.

tana Ζ™ayataccen murmushinta data saba tace, “ehhh Kakus Ι—ina, sai dai Ι—an zafi kaΙ—an da wuyan nawa ke yi mani amma likitan yace zai warke a hankali idan ina shan magani”.

“to Alhmdl Allah ubangijin girma ya Ζ™ara maki lafiya, wannan yarinya kinsha wuya”.

“ai Kakus aka ce dama bayan wuya sai daΙ—i, yanzu ba gashi daga ni har Y Raihana’n komi ya wuce mana ba”.

“haka ne kam, itama yanzu tana fitowa a prison zata Ι—an-Ι—ani jin daΙ—in rayuwar da bata yi ba har ta iya cutar dake akai”.


Rahinat tasa hannu ta danna idonta dan mayar da Ζ™wallar data taru, ta duba Kakus tace,

“Hajiya na tausayawa Y Raihana halin data tsinci kanta, wai Hajiya har mai muka yima Anty Asma’u a rayuwa da bata son ganinmu cikin farinciki take mana hassada?”.

“to Jikalle koma mene ai a gabanki tayi bayani kuma duk kinji, ba kiga shi Khaleed Ι—in mai gaba Ι—aya ma so akai a kasheshi shi da iyayensa”.

cikin zuciyarta tace, _to ni ina ruwana da wani Khaleed,can tasu damuwar._

a fili kuma tace,

“Allah ya kyauta kuma ni na yafe mata komai ta mani Allah ya yafe mu baki Ι—aya, itama Y Raihana Ι—in zance mata ta yafe mata, amma dai Kakus Anty’n tana nan ko, wuΖ™an da Y Raihana ta daΙ“a mata bai haifar da wani matsala ba ko?”.

“umm toni ina na sani, ni dama hankalina naga lafiyarki ita ne nake so kuma kin samu yanzu hankalina ya nutsu ya kwanta, komi na farin ciki na zai dawo”.

ta kuma shafo fuskar Rahinatu tace, “yanzu mai kike son ci?”.

“Tsire lafiyayye da kuma fura”.
tai maganan tana Ι—aga manyan idonta waje.

“an gama Sarauniya yanzu zaki ci ki Ζ™oshi kuwa, bari naje na dawo”.

ta kamo hannun Hajiya dake Ζ™oΖ™arin miΖ™ewa tace, “sarauniyan wa?”.

“sarauniyan Hajiyanta mana,sarauniyan kuma Abbi da Amminta”.

Ζ΄ar dariya tayi ,Hajiya ta miΖ™e da hanzari ta fita, koda taje Ζ™ofa kallon Khaleed tayi wanda tin Ι—azu yake tsaye yana kallon, kai kawai tayi ta girgiza kai ta wuce tana murmushi duba da yanda ya Ζ™urawa Rahinat ido bako Ζ™iftawa.

STORY CONTINUES BELOW

Rahinat kuwa na Ι—ago da idonta ta kalla Ζ™ofa taga Khaleed take tai kicin-kicin da fuska ta Ι“ata rai.

hakan da tayi ba Ζ™aramin Ζ™arawa fuskar tata kyau yayi ba, ajiyar zuciya ya sauke ya zare hannunsa daga cikin aljihun wandon jeans Ι—insa, sannan ya nufeta yana ta fitar da azababben murmushi mai kyau.

yana zama kan gadon gefen kusa da ita tayi saurin kauda fuskarta gefenta.kansa ya Ι—an barΖ™ala kana ya kewaya hannunsa ta Ζ™ugunta, a hankali yake kewayawa yanda bazata ji bare tai yunΖ™urin hanasa, jin saukar hannunsa a shamulokin cikinta yasa tayi wani zillo har tana haΙ—awa da Ζ΄ar shaΖ™uwa.
+

kwantar da kansa yayi saman kafaΙ—arta yana goga fuskarsa a hankali.

cikin cool voice nasa yake rera waΖ™a a hankali hannunsa kuma yana shafa cikinta da wani irin salo.

“Am so lonely broken Angel,am so lonely listen to my heart,you,you are the one i miss so much”.

tsaki ta buga ta ture kansa a kafaΙ—ar tata sannan tasa hannu tai ball da hannunsa dake cikinta.

a Ι—an shagwaΙ“e ya yunΖ™ura zai kuma yin jikinta ta Ι“ata rai sose ta miΖ™e zata bar Ι—akin yay saurin fizgota ta faΙ—o jikinsa,gudun karta miΖ™e ya kewayeta da hannayensa gaba Ι—aya a faffaΙ—an Ζ™irjinsa.

sai da tasan yanda tayi ta tattaro Ζ™arfi a kiciniyar da take ta Ι“alle hannun nasa ta Ζ™wace ajikinsa.

“tashi ka fita tinda ba wurin zamanka bane”.

tayi maganar da Ζ΄ar Ζ™aramar muryarta ita alalen dole da faΙ—a tayi, wani ko ya jita ma ce zai shagwaΙ“a take bama faΙ—a ba.

“ka tashi ka Ι“ace min a waje nace”.

shima kwai-kwayon yanda tayi Ι—in yayi yace, “uhmm uhmm idan naΖ™i fa Angel nah”.

haushi sose ya Ζ™ara bata, tana baΖ™in cikin wannan sunan da yake kiranta dashi.

“karka sake kirana da wannan stupid name Ι—in naka,asalin sunana ma ka faΙ—i bazan yafe maka ba, kuma nayi niyyar fita na baka wurin amma yanzu na fasa tinda wuri nane ba nake ba, Allah idan baka tashi ka fita ba saina cijeka”.

ta Ζ™arashe maganar kamar zata yi kuka.

Ya Allah,wani Sonta da Ζ™aunar ta ne suka Ζ™ara yiwa zuciyarsa dirar mikiya, sai daya lumshe idonsa kamin ya buΙ—e ya Ι—ora Ζ™afafunsa kan gadon,akan pillow ya jingina kansa kana ya naΙ—e hannayesa a Ζ™irjinsa, jinsa kusa da ita a zabure ta miΖ™e ta sauka Ζ™asa,waigo da kai yayi ya zuba mata narkakkun idanuwansa yana mai jin kawa ya haΙ—iyeta saboda tsan-tsar Ζ™aunar da yake mata.

Murmushi yayi yace da ita, “Angel nah mi yasa kike kora na, idan kin koreni a wajen ki ina zani bayan kin san zuciyata bata da kowa sai ke?”.

“tambaya ta ma kake, to oho?”.

ta basa amsar tana galla masa harar tana duban wani gefen.

ganin da gaske dai take da azama ya sauko daga gadon yaje gabanta ya tsaya,duka tausassun hannayenta ya kamo ya sanya cikin Ι—umammun nashi.

still fuskarta na kallon wani gefen guda, ta fizge a riΖ™on ta Ι—an ja da baya.

“Hayatee nah kina so na mutu ko?”.

kalaminsa ya sanya tai saurin runtse idonta.

ya sake matsawa gab da ita yasa hannu a haΙ“arta ya juyo da fuskarta tana facing nashi amma idonta a Ζ™asa.

“am asking you ki amsa mani, kina so na mutu ko?”.

“zanfi kowa farin ciki idan hakan ya kasance domin kana nema ka addabi rayuwata wanda ni kuma bana so”.kauda kai yayi da sauri, kamar zai mata kuka yace mata, +

“kina so kice min kin daina sona yanzu?”.

tambayar da yayi mata babu shiri ta Ι—ago manyan idanuwanta masu daΙ—a narkar masa da zuciya ta watsa masa su.

cikin idonsa take kallo tace, “ai ba daina sonka kaΙ—ai nayi ba, har kai kanka bana so ba kuma na Ζ™aunar gani da duk wani abu daya dangance ka, Khaleed ko acan baya dana so ka *ƘADDAR SO* ta afka mani, amma a yanzu babu wata Ζ™addara makamanciyarta da zata kuma samuna, idan kana tinanin cewar har yanzu ina sonka ko kuma zan so ka anan gaba, to kayi gaggawar farka daga dogon barcin da kake domin abu ne da bazai taΙ“a yiwu ba, Khaleed ina so na faΙ—i maka ka daina bibiyata ka barni na buΙ—e sabon shafi n afara rayuwar soyayya….”.

“dani ba”.
yace da ita yana kallonta cikin ido kaman yanda ita Ι—in ma ke kallonsa.

“ko mai kama da kai bana fatan Allah ya Ζ™ara haΙ—ani rayuwa dashi bare kuma kai, kai Khaleed idan baka sani ba yanzu ka sani a duk duniya idan da wani abu da zuciyata ta tsana to ya biyo bayanka, wallahi bana sonka bana sonka ko kaΙ—an…..”.

sam bai jin zai iya jurema jin sauran kalamanta dake masa zafi cikin zuciya, hakan yasa yay saurin haΙ—e bakinsa da nata wuri Ι—aya,cikin wani salo na daban yake kissing nata.

duk yanda taso ta Ζ™wace ta kasa har sai da ta samu dabarar da ta danΖ™ara masa cizo a leΙ“e babu shiri kuwa ya sakar mata baki.

yatsansa yasa yana shafa wurin da har jini ya Ι—an fito dan ba Ζ™aramin cizo tai masa ba.

halshensa yasa yana lasar leΙ“en nasa daya gama jiΖ™ewa da yawun bakinta, ya shaΖ™i doguwan iska gami da sauke dogon numfashi kana ya lumshe idonsa ya buΙ—e yana kallonta yace,

“so sweet more than honey”.

tsukar da tayi har cikin dodon kunnensa, duΖ™awa tayi ta Ι—auka Ι—an kwalinta daya saΙ“ule mata, Ζ™walla duk ta tarar ma idonta amma dan kar tai kuka a gabansa ta dake, raΙ“awa tayi ta gabansa tana watsa masa harara mai cike da ban haushi.

kamin ta kai Ζ™ofa taji shi ya rungumota ta baya ya tsamke ta tsam sai faman hura mata iska yake a wuyanta daya saΖ™alo kansa.

“Hayatee (Rayuwata), ki daina wannan fishin naki dan Allah ban sonsa, in kika ci gaba zaki rasa ni”.

kamin tayi magana Hajiya ta turon Ζ™ofan ta shigo, turus tayi daga inda take ta riΖ™e haΙ“a.

“ahhh lalle sannu mara kunyan zamani”.

tace da Khaleed tana kallonsa.

sam ganin Hajiya ko maganan da tayi baisa ya saki Rahinatu ba sai ma Ζ™ara matse jikinsu da yayi yana murmushi.

Hajiya ta cire takalimin dake Ζ™afarta tayo kansa zata Ζ™wala masa yay sautin juyar dasu, da sauri Rahinat ta sauke kanta Ζ™asa dan saura Ζ™iris akanta.

“sannu fitsararre, ai sai ka bari idan mun bar asibitin kayi iya shegen naka, amma anan ko bani ba likita zai iya shigowa, ba kowa zaka bari da kunya ba sai ita”.

“Hajiya kice ya sake ni”.

“to kaji ka sake ta”.

ya saki Rahinat kans aΖ™asa yana sosa gashin girarsa.
Hajiya ta harare shi tace, “kamin kayi min abin kunyar daya fi wannan Ζ™wamma mu tarkata mu tafi tinda dai lafiya take, sai kaje ka mana booking”.

Rahinat tayi tsalle ta dire ta doki Ζ™afa a Ζ™asa tace, “Allah Hajiya indai tare dashi zamu tafi sai kuyi tafiyanku ni na taho ko a Ζ™asa ne”.

zaro ido waje yayi jin abinda tace, ya matsa daga kusa da ita yace da Hajiya,

“manatun amana,ki kula min da ita sose da sose,irin sose Ι—in nan fa Hajiyata, zanyi gaba sai kun taho”.

Hajiya ta mangare shi tace, “bazan kula da ita ba Ι—in mara kunya”.

yana Ζ΄ar dariya ya fice a Ι—akin bayan yay ma Rahinat blowing kisss.

Post a Comment for "YAREEMA KHALEED CHAPTER 7"