⚔️*🔥ƘARFE A WUTA🔥*⚔️
MALLAKAR AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
*Labarin ƙarfe a wuta, ƙirƙirarran labari ne, idan yayi kamanceceniya da rayuwar wani ko wata, arashi ne.*
Ban lamunci a juya mini littafi, ta kowace irin siga ba, sai da izinina❗
Page 1
Tsit ƙaton falon yayi, ba ka jin sautin komai, sai ƙarar
gudun AC.
Sai mutanen falon da suke tsaye sun yi cirko-cirko, kamar
masu jiran wani sakamako.
Wata matashiyar budurwa ce, durƙushe a kan gwiwoyinta,
fuskarta ɗauke da wani yanayi na tsantsar damuwa, da tashin hankali,
fuskarta tayi sharkaf da hawaye.
"Yanzu sakamakona kenan a wurinki? Irin wannan
sakamakon shi na cancanta daga gare ki ko?"
Cikin ƙulewa wata babbar mace ta ce "Dama wani sakamako
ka ke saka ran samu daga tsintaccaiyar mage? Ai ba za ta taɓa mage ba, abun da
na din ga ankarar da kai kenan, tun a shekarun baya, amma ka kasa ankarewa,
yanzu ta nuna maka ita ƴar kunama ce"
Budurwar ta yakice gumin da yake tsatstsafo mata, ba tare da
nadamar abubuwan da suke gudana ba a ƙasan ranta, a zahiri ta ce "Ba
mummunan sakamako bane ba, abun da ka tarbiyantar da ni a kai ne, gaskiya ita
nake tsaye a kai, bani da niyyar cutar da kowa a gidan nan, kowa aikinsa yake
yi, yakamata ayi mini adalci, ba a goyi bayansa a nuna ni ce nake kan ƙarya ba,
a bari nima na yi nawa aikin"
Cikin tsawa ɗaya matar ta ce "Har wata gaskiya ce da
ke.....
Dattijon ya ɗaga mata hannu ya ce "Ya isa haka, tashi
ki je, ba na ko son ganinki, ki je ki yi abun da ki ke ganin ya dace da
ke".
Cikin rauni da tashin hankali ta ce "Abba, ba ka son
ganina ka ce?"
"Eh mana, idan har ki na gudun ɓacin raina da fushina,
dole ki ba wa ɗan uwanki duk wani cikakken haɗin kai, domin gudanar da aikinsa
yadda yakamata"
Cikin matsanancin tashin hankali ta ce "Amma Abba ni
kuma menene makomata...? Yakamata a ji ta bakina Abba"
Bai tsaya sauraron mai za ta ce ba, yayi gaba zai bar falon.
Cikin matsanancin tashin hankali, ta riƙe ƙafarsa ta na fashewa da kuka.
"Haba Abbana, me yayi mini saura a duniya, idan har zan
rayu ka na fushi da ni, ka yi haƙuri zan yi abun da ka ce in sha Allah"
tuni hawaye ya cigaba da wanke mata fuska, tsantsar nadama da damuwa suka
mamayeta, ta din ga kuka da sheshsheƙa kamar ta shiɗe, amma ya fizge ƙafarsa ya
yi gaba.
Yana barin falon, tamkar mutanen falon za su cinyeta ɗanya,
haka suka yo kanta sa surutu, kowa da abun da yake faɗa.
Tashi ta yi tsaye, ta goge hawayenta, cikin ko in kula, ita
ma ta bi wata hanyar ta bar musu falon, cikin sigar kwa ci kanku.
Ɗakinta, ta shiga ta buɗe drower, ta fito da wasu takardu ta
zube su a kan gado, ta kunna system ɗin ta da take caji a gefen gadon, lokaci
guda kuma ta ɗauki wayarta tana dannawa.
Jin motsin mutum a bayanta, ya sanya ta waiwaya da sauri.
A tsaye ta ganshi bakin ƙofa, fuskarsa babu walwala balle
annuri.
Mayar da hankali ta yi, za ta cigaba da danna wayarta, ya
tako zuwa gabanta, ya tsaya ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Kin shirya
aikata abun da aka umarce ki ko kuwa?"
Cikin hanzari ta tari numfashin sa ta ce "Ban ce shirya
ba, kuma ba zan shirya ba, daga nan har gaban abada, ka fita ka rabu da
ni".
Cikin matuƙar mamaki yake bin ta da kallo, "Yanzu duk
kukan da ki ka yi, ƙarya ki ke yi kenan?"
A hasale ta ce "Ina ruwanka, idan ma kukan ƙarya ne ko
na gaske, ka yi aikinka in yi nawa, kar ka sake yinƙurin shigar mini aiki, idan
ba haka ba komai yana iya faruwa, wallahi ba zan fasa abun da na yi niyya ba,
idan kuma ka cigaba da takura mini, zan baka mamaki"
Hannu ya saka, ya ɗagota daga kan gadon ya ce "Menene
zai faru, wani irin mamaki zaki bani? Me zai faru nake son ki gaya mini. Kina
da hankali kuwa? Kin san doka amma kina taka ta yadda ki ke so? Da me ki ke
taƙama ne haka?"
"Doka ko? Ni iya takata na yi, kai kuma cin
zarafinta ka ke ƙoƙarin yi, ka ƙyale ni babu ruwanka da ni, ka yi naka aikin na
yi nawa duk wanda yayi galaba shikenan. Idan ka ga dama ka je ka sake gayawa
Abba abun da duk yayi maka a kaina, wallahi babu gudu babu ja da baya, ban fara
dan ina saka ran dainawa ba, ba tare da na yi nasara ba" hankaɗata yayi
kan gadon, yana wani irin huci, zuciyarsa na yi masa zafi, yayi wata irin ƙwafa
yana bin ta da kallo. Cikin hanzari ya fice ya bar mata ɗakin, saboda idan ya cigaba
da tsayuwa, zai iya yi mata abun da ba shikenan ba. Ta yinƙura ta tashi zaune
tana haki, tana kallon ƙofar da ya fita.
****
Tsaye take a gefen wani gini, tana ƙarewa harabar kotun ido.
Yadda aka cika harabar da manya da ƙananan motoci ne, ya sake tabattar mata da
manyan shari'oi za a gudanar a yau.
Ta din ga kallon agogon hannunta, tana kallon gate shigowa
harabar kotun.
Motar gidan yari ce ta shigo, aka yi parking ɗin ta, sai dai
tsayuwar motar babu daɗewa wata danƙareriyar motar, ta shigo harabar kotun.
A ƙalla an kai mintuna goma da parking ɗin motar, sannan aka
buɗe bayan motar, wata mata ta fito, sanye cikin coat.
Mutanen da ke harabar wurin, suka nufeta, wasu suka karɓi
jakarta, ana ta yi mata fadanci, cikin girmamawa.
"Ya Allah kai ne Allah, kai ne buwayi gagara misali,
Ubangiji da babu wani kafinsa, kuma babu wani a bayansa. Allah na san mutanen
nan sun fi ƙarfina ta ko ina, amma kaine abun dogaro na, na san ba za ka bani
kunya ba. Allah sun fi ƙarfina ka fi mini ƙarfinsu. Allah ka yi mini
kunfayakununka a kan shari'ar nan, hasken gaskiya ya shafe duhun ƙarya, duk da
ina da masu goya mini baya, amma Allah goyon bayanka nake buƙata" ta jima
a tsaye tana karanto addu'a, tare da yi wa Allah kirari.
A hankali ta furta "What a hectic trial, Ubangiji ka
iya mini" cikin nutsuwa, ta fara taka takalminta mai tudu, ta nufi shiga
cikin kotun, da takunta mai kama da na ƙasaita, shigarta ta lawyoyi tayi
matuƙar yi mata kyau, tana tunkarar ƙofar shiga, zuciyarta na tsananta
bugawa,tana fatan Allah ya shiga lamarin ta.
****
Ƙofar famfo kano state.
Ƙarfe goma saura mintuna goma na dare, tuƙi yake yi cikin
sauri, saboda yadda fasinjar da ya ɗaukko take azalzalar sa. Duk saurin da yake
yi, mita take yi masa, a kan ya ƙara gudu.
Yanayin kwalliyar da ta yi, cikin baƙin material, fuskarta
ta sha make-up, zai tabattar maka daga wurin biki take.
Ta kalli agogon hannunta, kamar ta fashe da kuka ta ce
"Mai napep, ka yi wa girman Allah ka yi sauri"
Ya ce "Wai dan Allah hajiya yaya ki ke so na yi ne?
Haba babata duk saurin da nake yi, ki yi haƙuri mana mu tafi a sannu".
A ƙule ta ce "Ban gane babarka ba, wani irin wulaƙanci
ne wata babarka, na yi maka kama da tsohuwa ne?"
Yayi murmushi ya ce "A'a, ai ku mata duk in da ku ke
iyaye ne... Katse shi ta yi ta hanyar cewa "kuma sai aka ce na haifi kamar
ka? Ai sai a bari na haifa tukuna, a yanzu na haifi kamar ka, ai tawa ta ƙare a
duniya. Ko yayarka ka ce mini ka cuce ni, balle babarka. Ni dai ka ƙara sauri,
yau na san kashina ya bushe, sai an yagalgalani da masifa a gida yau. Aikin
banza, ƙawayen amarya ƴan wahala, mun gama wannan wahalar a ɗauke ta a mota an
kai ta gidanta, mu muna fama a titi. Mu ma Allah ya kawo lokaci, ace ga miji ga
mota"
Ya waiwaya ya kalleta yana murmushi, a fusace ta ce
"Lafiya malam?"
"A'a Allah ya baki haƙuri".
Kafin su ƙarasa in da zata sauka, ta ciro masa kuɗinsa, su
na zuwa in da za ta sauka, ta miƙa masa, ta sauka tayi cikin layinsu da gudu a
kan takalminta mai shegen tsini, ko wahalar gudun ba ta ji.
Mayafinta da jakarta a hannu, ta tura gate ɗin ta shiga ta
na haki.
Wani matashin saurayi, yana tsaye a harabar gidan hannunsa
riƙe da waya, ya kalleta ya ce "Daga ina ki ke?"
"Biki" ta bashi amsa kai tsaye.
"Za ki ci ubanki kuwa, Major yana nan ido biyu, tun
ƙarfe takwas ya dawo yake tambaya ko kin dawo, gashi kin kashe waya ke ga
ƙwararriya"
Cikin ta yayi wata ƙara saboda tsoro "Allahumma inni
as'aluka afuwa wal afiya, yau na kaɗe" ta ƙarasa maganar tana nufar cikin
gidan.
Cikin sanɗa ta shiga falon, sai dai tana shiga, ta fara
tozali da dattijon zaune a kan kujera 3 seater, ya sanya ƙofar shigowa falon a
gaba, da gani babu tambaya ta san ita yake jira.
Tsayawa tayi ƙyam da takalmanta a hannu, da jaka da mayafi,
kamar ta juya da gudu ta koma.
"Daga ina?" Yayi mata magana cikin dakakkiyar
muryarsa.
Cikin rawar murya ta ce "Abba, wurin biki"
"To juya ki koma in da ki ka fito"
"Ai an tashi" tayi maganar kamar ta fasa ihu, dan
tuhumar Abba babu daɗi.
"Dama haka mu ka yi da ke? Ki fita ki je ki yi zamanki?
Ki dawo mini gida bayan goma, sai ka ce ki na zaman kanki?, koma ki kwana a in
da aka yi bikin"
"Dan Allah Abb.."
"Get out, kar ki kuskura ki yi mini magiya. Duk gidan
nan babu mai bani ciwon kan da ki ke bani Arfa, koma in da ki ka fito ba ki da
wurin kwana a cikin gidan nan yau" da gudu ta juya ta fita saboda tsorata
da ta yi.
Ta koma harabar gidan, a ƙasan zuciyarta ta ce "Na
shiga uku, ni ake kora kamar wata karya, yanzu idan gidan mijina ne, ba sai dai
ya gama bala'in in shige ɗaki na bar shi ba..
Ba ta gama tsinkewa da lamarin ba, sai da major ya kulle
babbar ƙofar shiga cikin gidan.
Ta zube kayanta, ta tafi famfon harabar gidan, ta dinga
wanke fuskarta, ta wanke kwalliyar fuskar gaba ɗaya, ta koma ta zauna jiran
tsammani ko Allah zai saka Abba ya buɗe mata ƙofa.
Samarin gidan suka fara fitowa daga BQ, suna shimfiɗa a
harabar gidan, za su yi kwanciyar zafi. Sai wulaƙanci suke yi mata, suna yi
mata Allah ya ƙara, suna kyararta, kamar wadda ta aikata wani gagarumin abun
kunya.
Ganin ba ta da mafita, ta laluba ta samo tabarma ta shimfiɗa,
ta yi kwanciyarta dan a gajiye take sosai.
Tsakar dare, ta yi juyi, ta ji babu kowa a kan gadon sai ita
kaɗai, mamaki ya kamata, ta kalli agogon wayarta, biyu da rabi na dare.
Tasowa ta yi ta fito nemansa, sai dai ga mamakinta, ta tarar
da shi a ventilation ɗin saman bene, ya zauna a kan kujera ya saka harabar
gidan a gaba, hannunsa riƙe da ɗan ƙaramin Alqur'ani yana karantawa.
"Lafiya dai?" Tayi maganar cikin mamaki.
Ya waiwaya ya kalleta ya ce "Lafiya ƙalau"
"Amma me ka ke yi a wurin nan, a wannan uban daren? Na
zata tuni ka kwanta, na fito na duba falo baka nan"
Cikin ko in kula ya ce "Kar ki damu, ki je ki yi
kwanciyar ki, Arfat ke punishment"
Cikin takaici matar ta ce "To ta na punishment, sai
kuma kai ka zo nan ka zauna, ka hana idonka bacci?"
Yayi murmushi ya ce "Ko na kwanta ba zan iya rintsawa
ba, ki yi kwanciyar ki kawai" tamkar ta yi tsaki, haka ta wuce shi ta
ƙyale shi, tama tunanin yaushe ƙarshen wannan lamarin zai zo?.
Haka ya kwana a zaune, yana gadin harabar gidan, duk wanda
yayi juyi cikin mazan nan, yana kallon shi.
Yana ganin yadda Arfa ke ta juyi, sauro ya dame ta, sai da
ya ji tamkar ya sauka ya samu abu ya rufe ta, amma ya ƙyale ta.
Asubar fari, ya yi alwala, ya sauka ƙasa domin tafiya
masallaci.
Samarin na jin takunsa, suka din ga tashi, idan ba haka ba,
ya tashi mutum da carbi.
Ya na zuwa in da take kwance tana bacci, ya tsula mata carbi
a ƙafafuwanta.
A razane ta tashi tana rarraba ido.
Bai ce mata uffan ba, ya yi gaba ya fice.
Tana ganin ya fita, ta tattara komatsanta, ta shiga cikin
gidan, sai soshe-soshe take yi, saboda uban sauron da ya cije ta.
Cikin ɗakinta ta shiga, ta watsar da jakarta da sauran kayan
a kan gadonta, ta jona wayarta a caji.
Ta tuɓe kayanta daga ita sai underwear. Wata matashiyar
budurwa da aƙalla za ta ɗan girmewa Arfa ta fito daga banɗaki, ta kalle ta, ta
ce "Arfa, ke kuwa a ina ki ka kwana? Har sha ɗayan dare ba ki dawo
ba" banza tayi mata, ta taho fuuu ta kusa bangajeta, ta shiga banɗaki. Ta
girgiza kai kawai ta shimfiɗa sallaya.
Da ƙyar ta yi sallar asuba, sai soshe-soshe take yi, tana
idarwa ta ɓingire ta hau bacci a wurin.
Sosai take baccinta, dan ta gaji sosai, ga baccin jiya sam
bai yi mata daɗi ba.
"Nabila!Nabila!!"
Tsaki tayi tare da jan "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un, menene, wannan wane irin kira ne dan Allah?"
"Abba ne ya ce, ace miki yana fatan kin ajiye aiki ne,
da ki ka kwanta kina bacci haryanzu ba ki fita ba"da sauri ta buɗe idonta,
gaba ɗaya ta manta yau Monday.
Kamar korarriya ta tashi, ta afka banɗaki, a gurguje ta
wanke bakinta, tayi wanka, ta fito ta shafa mayuka, da turaruka ta shirya cikin
uniform.
Ta saɓa coat ɗin ta a kafaɗa, ta ɗauki jakarta ta goyo, ta
sanya takalminta, tayi waje tana kunna wayarta.
Ta shiga kitchen, ta buɗe fridge ta ɗebi lemuka ta zuba a
jakartab, da abun da ta ajiye da wanda ba ta ajiye ba, duk ta kwasa ta zuba, ta
zuge jakar ta fito falo.
A falon suka yi karo da wata matashiyar mata, matar ta kalli
Nabila ta ce "Ma'aikaciya ko mahaukaciya, kalleki kamar korarriya Nabila,
zaki fita aiki amma ki ka kwanta ki na kwasar bacci abinki".
Nabila ta ce "Anty, the whole barrister ki ke cewa
mahaukaciya?"
"Yo banda shirme, kalleki kamar an hankaɗoki, ke wannan
wane nutsatstsen ne ma zai ce ki tsaya masa shari'a?"
Nabila ta ce "I will fill a lawsuit against you, what
you did is deformation of character, the whole barrister Anty ki ka zaga"
"Wuce ki tafi kafin na make ki ni? Idan suka kore ki
daga wurin aikin, ai kya nutsu" Nabila ta sake kwasa da gudu a kan
takalmanta kamar ba budurwa ba.
Mai aikinsu ta tarar a famfon harabar gidan, tana
wanke-wanke.
"Shalelen Abbanta, yau kamar kin makara"
Ɗaga mata hannu kawai Nabila ta yi, kowa ya ganta sai yayi
magana, ta kalli hanyar benen Abba, kamar ta je ta gaishe shi, amma ta fasa ta
san yadda ta makaran nan, sai ya zaunar da ita yayi mata faɗa, ga laifin jiya
ga na yau, kuma ta san sai ya haɗa har da na waccan shekarar yayi mata, dan
haka tayi wuf ta fice waje.
Duk irin vibration ɗin da wayarta take yi, ba ta ɗaga ba sai
da ta zauna a cikin adaidaita sahu, sannan ta ɗaga kai wayar kunnenta.
"Wai Nabila wani irin wulaƙanci ne, nake ta kiranki ki
ka ƙi ɗagawa?"
Nabila ta ce "Ke ban son tijara, kin wuce aiki
ne?"
A fusace mai maganar ta ce "Ban sani ba"
Nabila ta yi dariya ta ce "Sorry masoyiyya, ki fito
titi gani nan" tafiyar mintuna sha biyar suka yi, suka iske wata
matashiyar budurwar a titi, sanye cikin doguwar rigar abaya, ta kama adaidaita
sahun ta shiga tana hararar Nabila.
"Sorry sumy, kar ki fashe dan Allah"
"Wallahi kin fusata ni Nabila"
"Shiyasa na ce ki yi haƙuri ai, ya gidan ya su
mama?"
Sumayya ta ce "Suna lafiya ƙalau, meyasamu fuskarki? Na
ga kamar ƙuraje"
Nabila ta rausayar da kai ta ce "Ke bari, the whole me,
jiya Abba ya saka na kwana a haraba, sauron nan na cikin flowers suka yi idi a
kaina"
Sumayya ta waro ido ta ce "Wai da gaske?"
"Zan yi miki ƙarya ne? Wallahi dattijon nan ya ce wai
na koma in da na fito ya rufe ƙofa. Aikuwa na din ga tsinewa amaryar nan, na
baro ta a gidanta cikin nishaɗi da farinciki, ni kuma na afka tashin hankali,
kamar ni degree holder, Abba ya rufewa gida. Yanzu dan Allah da a gidan mijina
ne, da ba sai dai yayi masifar ya gama ba, babu wanda ya ji ya gani? Ai Abba ya
tozarta ni jiya. Sai so ake a ga fuska a tuhume ni, ko ayi mini rashin mutunci
a gidan nan, kin san gidanmu Allah ya wadata mu da munafukai, ni kuwa na haɗe
rai"
Sumayya ta ce "Allah ya ƙara, ke uwar gwaninta, har da
kai amarya, banda uban anko da ki ka yi mata. Ina mai tabattar miki ke da
ganinta ta tako gidanku, sai wani ikon Allah"
Nabila ta ɗan yi shiru ta ce "Ku ma fa haka ne, kin san
wani abu, ba hassada nake yi wa amira ta yi aure ba, amma kalli na fita kyau
fa, na fita komai amma amira ta shige daga ciki, ohh ni Nabila, duk kyan nan da
dirin nan yadda ki ka san na je na haye kan high table ɗin nan ayi da ni ranar
dinner. Ba ma wannan ba duk wannan gayun da kwalliyar ban yi saurayi a bikin
nan ba"
Sumayya ta ce "Ki je ki ɗorawa ranki jarabar son aure,
ki ƙi focusing a kan career ki, ni ko a jikina na san lokaci ne, kuma tun da ba
yawon iskanci nake ba, duk wadda ta yi mini gorin aure sai na ci ubanta,
shekarun namu nawa ne duka da za a addaba mana"
Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Ba haka ba ne
Sumayya, we have a different backgrounds, ke kin san me nake nufi, wallahi
ƴanci nake so Sumayya, ko ta halin ƙaƙa"
Sumayya ta ce "Kar neman ƴanci ya kai ki ga halaka, duk
ina samarin naki ne to?ba wanda zaki tsayar?"
Nabila ta yi tsaki ta ce "Bar matsiyata, daga ƴan
wahala sai ƴan iska. Sai dai duk wanda ya zo hannuna sai na ci rabona ayi
baran-baran. Na daina wahalar son mutum, daga ƙarshe yayi breaking heart ɗina,
ya ci bulus. And also haryanzu ban samu spec ɗi na ba kin dai gane"
Sumayya ta ce "Au ke yanzu har wane zaɓe-zaɓe ki ke
yi?"
Nabila ta ce "To ana raba mai rai da motsi ne? Iya wuya
akwai abun da zuciya take so, kuma ni na fi son namiji mai kumari sosai. Irin
wanda zaki ganshi ingarman namiji mai cikar zati. Beside fuskar namiji ba gemu,
ai sunansa sumayya, ni kuma daga dattijai, sai marasa gemu, sai kuma ƴan
wahala, ni matashi nake so, ba kuma yaro ba"
Sumayya ta ce "Au sunana ne ma abun kwatancen iya
shegenki ko, to ki je dan kanki. Mai napep zan sauka a nan, za ta baka kuɗin"
Nabila ta ce "Ke uban waye ya ce miki ina da kuɗi?"
Tuni Sumayya ta sauka, ta bar Nabila.
Nabila ta yi ƙwafa ta ce "Zamu haɗu ne, zaki ga
wulaƙanci".
***
A hankali yake buɗe jajayen idanunsa, a lokaci guda kuma
yana lumshe su, tamkar mai shirin yin bacci. Sai mirgina kansa yake yi, yana
sake lumshe manyan idanunsa da suka koma jajaye matuƙa.
Tamkar an jefo shi, haka ya faɗo ɗakin, yana rarraba ido.
A hankali ya ɗaga kai ya kalli wanda ya shigo ɗin, ya mayar
da kansa ƙasa ya sunkuyar.
"Allah ya taimaki oga..." Bai amsa ba kawai ya buɗe
tafin hannunsa ya miƙa masa.
Wata baƙar leda ya ciro, ya ɗora masa a hannun, sannan ya ce
"Sai dai Oga ba a samu da yawa ba, ƴar kaɗan ce, cinnaku sun yi wa kasuwar
ƙawanya, shiga da fitar kaya na bayar da wahala, da ƙyar na samu wannan wurin
wani ɗan inyamura, ina ga wuri zan canza, saboda kamar ana son yi mini
cune".
Bai ce masa uffan ba, ya kwance ledar, ya fito da kwalin
wata allura pack guda, mai ɗauke da ampoule na allura guda goma.
Sirinji lamba biyar ya ɗauka, ya din ga fasa alluran yana
zuƙa, sai da ya cika sirinjin, sannan ya miƙe hannunsa.
Ya ɗaga kansa ya kalli matashin da ya kawo masa allurar, bai
ce masa komai ba, matashin ya bar ɗakin.
Ya mayar da idonsa kan hannunsa, ya yana kallon jijiyoyin da
suka kwanta ɗoɗar a ƙarƙashin fatarsa, suka yi ruɗu-ruɗu, manya da ƙanana.
Ya dubi guda ɗaya, ya huda ta da sirinjin hannunsa, ya fara
bawa kansa allurar sannu a hankali. Sai da ya zuba ta duka, sannan ya yi jifa
da sirinjin, ya sunkuyar da kansa ya na jiran Sakamakon hukuncin da ya ɗauka.
Sai dai kusan mintuna goma sha biyar, bai ji abun da yake so
ba, sai wani irin nauyi da kansa ya ƙara, idonsa ya din ga yi masa yaji, ya
rintse idanunsa amma bai ji alamar abun da yake so ba.
Abu kamar wasa kansa ya din ga wani irin sarawa, ƙirjinsa
yana zafi. Ya dafe kansa da hannunsa bibbiyu yana jujjuyawa tare da rufe
idanunsa.
Ihu ya fara yi iya ƙarfin sa yana taƙarƙrewa, yana girgiza
kansa, saboda yadda yake jin kansa tamkar zai yi bindiga.
Da gudu suka shiga ɗakin, suka fara ƙoƙarin danne shi, amma
ya yi ihu ya watsar da su baki ɗaya ya cigaba da kururuwa.
Ayshercool.
08081012143
⚔️*ƘARFE A WUTA*⚔️
MALLAKAR AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Arewabooks ayshercool7724
Watpad ayshercool7724
2
A ƙalla sun kai ƙarti uku majiya ƙarfi, suka riƙe shi, amma
sai ƙoƙarin watsar da su yake yi, ga wani irin gurnani yana yi, kamar
mahaukacin zaki.
Da ƙyar suka haɗu suka kai shi ƙasa, suka daddane shi yana
cigaba da ƙoƙarin watsar da su ya tashi.
Ɗaya daga cikinsu da yanayin kamanninsa ya bayyana, ƙarara
shaye-shaye ya huda shi, saboda yadda laɓɓansa suke baƙi ƙirin, ga wani irin
ƙaton tabo a gefen fuskarsa.
A hankali yake ɗan dukan bayansa cikin sigar rarrashi yana
faɗin "Easy maza, easy, mun san ka na cikin damuwa da raɗaɗi, amma hakan
ba mafita bane ba, ka yi haƙuri muna tare da kai ɗari bisa ɗari iya wuya"
ya cigaba da maganar yana rarrashin sa.
A hankali jikinsa ya saki, ya daina gurnanin da yake yi, ya
lumshe idanunsa, ya rufe su, tamkar mai bacci. Sai da suka tabattar ya yi
relaxing, sannan suka ɗaga shi.
Major ne tsaye a gaban mudubi, yana ƙara kintsa jikinsa
kamar wani matashi, ba dattijo ba, uwargidan sa na gefensa tana taimaka masa
yana shiryawa, Ba tare da ya kalle ta ba ya ce "Arfa kuwa ta tafi
aikin?".
Ta yamutsa fuska ta ce "Ta ga dama ta tafi"
Ya jinjina kai ya ce "Punishment ɗin da na yi mata
jiya, shi ya hana ta zo ta gaishe ni yau kenan,'? zan gamu da ita ne idan ta
dawo".
"Dan girman Allah major ka ƙyale sabgar yarinyar nan,
sai ka ce itakaɗai ce ƴa a gidan nan, komai ita su duk sauran ba ƴaƴa bane ba,
da ba ka damu da lamarinsu ba?" Kallon da yayi mata ne ya sanya ta yin
shiru, tare da sunkuyar da kai, bai sake ce mata komai ba, ya ɗauki mukullin
motarsa ya fice.
Cike da takaici ta sauka daga benen, ta fito main falon
gidan tana mita.
"Yaya ya dai? Meyafaru ne?" Duk da ba ta kasance
mai sakarwa abokan zamanta fuska ba, amma haka kurum ta tsinci kanta da gaya
mata abun da ya faru saboda takaici.
"Major ne mana, gaba ɗaya ya tattara hankalinsa a kan
yarinyar nan, kamar itakaɗai ce ƴa a cikin gidan nan, jiya kwana na ne, amma a
barandarsa ya ƙare kwanan jiya, wai yana gadinta, abubuwan nan sun fara
isata"
Ɗayar ta taɓe baki ta ce "Ai ni na gaji, na zuba ido su
ƙarata, abun da ba jiya aka fara ba, ba yau ba".
Anty, wadda take ta uku, da take karyawa, duk da ba da ita
suke ba ta ce "Amma dai an yi abun kunya, kishi zan ce ko baƙin ciki da
ƴar cikinku"
A fusace Uwargidan major, da ake cewa Mama ta ce
"Asiya, da ni ki ke ko wa?"
Anty ta ce "Duk wanda ya tsargu, sai menene dan ya nuna
mata kulawa ta musamman, duk kulawar da yake bawa sauran yaran bai isa ba? Ƴaƴa
nawa ne a gidan nan, kowanne ya na bashi kulawa dai-dai da buƙatarsa ne, amma
da yake kishi ya zame muku bala'i, mussaman ma ke, da kowa ma yi ki ke, kin fi
mu daɗewa da shi, amma haryanzu ba ki san halinsa ba"
Mama ta ce "Ba zan yi musayar yawu da ke ba ƙanwar
bayana, dan ba ki isa ba, da wanda ya ajiye ki zan yi".
Anty ta ce "Idan ma ƴar cikinki ce, matsayinmu ɗaya
matan major, kuma ni gaskiya nake faɗa" haka suka cigaba da ƴan faɗace-faɗacen
su na kishi.
Nabila kuwa da wasu lokutan a kan yi mata laƙabi da Arfat,
tana zaune a katafaren office, itakaɗai sai aikin danna waya take yi, cikin
nishaɗi kamar babu wani abu da yake damunta.
Knocking ɗin ƙofar office ɗin aka yi, ta bayar da izinin a
shigo.
Nabila suka gaisa da matar ta ce "Nabila ko?"
Nabila ta jinjina kai ta ce "Eh"
"Ki zo Barrister yana kiranki"
"Wane barrister?"
Matar ta ce "Director. Dama ina son in yi miki magana.
Kin ga wurin nan babbar organization ce, da muke dealing da mutane daban-daban,
especially manyan mutane. Yana da kyau ki jajirce director baya son ragwanci ko
harkar ko in kula da aiki, sai ku samu saɓani"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Na gane, na kuma fahimta
na gode sosai" matar ta jinjina kai ta fita.
Nabila ma tashi ta yi, ta fita ta tafi office ɗin da ake
nemanta.
Ta tarar da shi da wani babban mutum a zaune a office ɗin
sa, ta gaishe su cikin girmamawa sannan ta kalli Director ta ce "Sir
gani"
Ya kashingiɗa ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Nabila,
what is actually wrong with you ne?"
Cikin mamaki ta ce "Ni kuma? Me na yi sir?"
Ya gyara zamansa ya ce "Anya ke ki ke son zama lawyer
ko choice ɗin major ne? Tun da ki ka zo wurin nan you don't care, sai dai ki
zauna ki danna waya, ki yi ciye-ciye, sai kwalliya. Bama kya shiga cikin
ma'aikatan ki ga yadda ake aiki, balle mu ga gogewarki, mu faa tura ki trials,
dama zuba miki ido na yi amma na ga baki san zuru ba" Nabila ta yi shiru
ta sunkuyar da kanta ƙasa.
"Ina buƙatar ganin canji a tare da ke, idan ba haka ba
na fara kai ƙarar ki wurin Major, yanzu muna da client da yake son yin apeal, a
kan wata shari'a da wasu mutane suka kai ƙararsa. Ki je na saka ki a team ɗin
su barrister Habib, ki je ku tattauna yadda za ayi handling case ɗin. Effort ɗinki
shi zai sanya na baki manyan cases to help your career"
Ta risunar da kai ta ce "Ok sir" ta juya ta fara
tafiya, sai dai mutumin da tarar a office ɗin, ya bi bayanta da kallo yadda
ƙugunta ke juyawa, cikin skirt ɗin kayan jikinta.
Office ɗin Barrister Habib ta je, aka sanar da ita suna ɗakin
sirri, dan haka kai tsaye can ta wuce.
Ta tura ƙofar ta yi sallama, suka amsa mata, ta nemi wuri ta
zauna.
Barrister Habib ya ce "Kin ga damar zuwa kenan?"
Wani irin kallo ta yi masa, amma ba ta ce komai ba, su kuma suka cigaba da abun
da suke yi.
Shari'a ce a kan wani attajirin mutumin ya karɓe gonakin
wasu ƴan ƙauye, ya basu diyya ya fara ginin kamfanin sarrafa shinkafa, sai dai
suka yi ƙararsa diyyar da ya biya su, ta saɓawa yarjejeniyar da suka yi da shi,
dan sam bai kai darajar gonakinsu ba. Ganin ba su da galihu, ya sanya bai damu
da ƙarar da suka kai shi ba, sai da aka yanke hukuncin ya biya su, sannan ya ce
zai yi apeal.
Mamaki ya cika Nabila, irin maƙudan kuɗin da ya biya law
firm ɗin su, a bashi lawyoyi su kare shi, ya isa ya ƙarawa mutanen nan, ya biya
su haƙƙoƙin su.
Nabila dai ta yi zuru da ido, tana kallon yadda ake harhaɗa
hujjoji na halal da na haram, domin mutumin yayi nasara a kotu.
Baƙin ciki da takaici suka isheta, sunan ƙauyen da abun ya
faru kawai ya isa ka gane cewar masu ƙaramin ƙarfi ne. Dan galibi mutanen
karaka da Allah suka dogara, da harkar noma suka dogara.
Tashi ta yi tsaye ta ce "Excuse me please, na fara jin
yunwa lokacin cin abincina yayi"
Duka lawyoyin da shi kansa client ɗin suka ɗago suka
kalleta.
Habib ya ce "Ana tsaka da aikin?"
Ta basar ta ce"Am sorry, am having a chronic ulcer, za
a iya samun matsala, idan na cigaba da zama" daga haka ta ɗauki jakarta ta
fice, tana mitar ba zata zauna a ƙulla wannan sharrin da ita ba, ranar lahira
ta shiga uku.
Ta koma office ɗin ta, ta yi alwala tayi sallar azahar, ta
je ta samu Director ta sanar masa da tana da uzuri ta na son ta tafi, yayi mata
iznin hakan.
A hanya ta tsayar da mai napep, suka ɗauki sumayya, sannan
suka tafi.
Ta kalli Sumayya ta ce "Sumy, meyafaru ne? Na ga kina
wani ɓata rai"
Sumayya ta yi tsaki ta ce "Haushin kaina nake ji, da na
karanci aikin jarida Arfa"
Cikin mamaki ta ce "Amma meyasa, na ga shi ne zaɓinki?"
"Wallahi duk ya fita daga kaina, hira aka yi da
honorable Indabo, wai an yi borehole a ƙananan Hukumomin da yake wakilta, an
raba kayan makaranta ga ɗalibai. An kai bencina makarantun firamare da na
islamiyyu. Last week aka ce na je na tattauna da al'umman local government ɗin,
na je ni ban ga ayyukan da aka yi ba, na tattauna da mutanen ƙananan hukumomin,
sun ce ba ayi musu ba. Na kai recording ɗin, aka saka, wai lawisa ba ta
tantance shirin ba, ba ta sani ba aka saka, kin ga cin mutuncin da aka yi mini,
wai zan lalata musu business wai sai na je na samo mutanen da zan yi hira da
su, su ce eh an yi ayyukan su yi godiya alhalin ba ayi ba. Na zama maƙaryaciya
kenan me zan ce wa Allah? Wai har da idan ban yi wasa ba, sai honorable ya saka
an ɗaure ni"
Nabila ta ce "Ikon Allah, ashe duk kanwar ja ce sumy,
yo nima hakan take ai, wani tasonon Alhaji ne ya zo yayi kirim a kan kujera
kamar damin doya, ya biya uban kuɗi wai za a kare shi, ya cuci talakawa ko
kunya bai ji ba, kuma director ya sakani a team ɗin lauyoyin, ni dai ba zan yi
ba wallahi, sai dai ya yi ta gaya wa Abban. Haka kurum a cuci mutane ka je ka
cewa Allah me?"
"Wallahi Nabila, ba ki ji zuciyata ba, yanzu sai dai na
je na tara maƙwabta na yi hirar ƙarya da su, a zo a sake sakawa, kuma wai sai
na rubuta takardar ban haƙuri, ki ji fa"
Nabila ta ce "Tirƙashi, wai ya ɗaure ki, to ya ɗaure ki
shi ma ya hau da ɗaurin Allah " Haka suka cigaba da tattaunawa, har suka
isa in da sumayya za ta sauka.
***
Cikin tsananin tashin hankali, yake magana, kallo ɗaya zaka
yi masa ka san hankalinsa a matuƙar tashe yake.
Ya daki teburi ya ce "Kwamishina, dole fa ku nemo yaron
nan, dole ku mayar da hankali a nemo shi a duk in da yake a ƙasar nan"
Mutumin da yake zaune cikin kakin ƴan sanda ya ce
"Honorable, ka kwantar da hankalinka, aikinmu baya buƙatar garaje da
gaggawa, sai mun bi a sannu"
"Haba Cp, wane irin bi a sannu? Rayuwata na cikin
hatsari, yayi iƙirarin kashe ni, dole fa a nemo yaron nan, ko be kashe ni ba,
idan ya buɗe bakinsa yayi wata magana a kaina kashina fa ya riga ya gama
bushewa, na san fa waye yaron nan ciki da bai"
Cp ya gyara zamansa ya ce "Amma honorable, wace irin
yadda ko alaƙa ce tsakanin ka da yaron nan, da har ya sanka haka, zamansa a
gari yake barazana a gareka"
Tsaki mutumin yayi ya ce "Kai har ka tambayi alaƙar da
ke tsakanin ɗan siyasa, da tantirin ɗan daba, ɗan iska? Ku nemo shi dillalin
wiwi ne, da hard drugs. Da kun ganshi ma kawai a harbe shi, kuma a tuhumi
controllern gidan yari, a kan dalilin sakinsa, bayan ko shari'a ba ayi masa ba
tsawon lokaci"
Ɗan sandan ya jinjina kai ya ce "Shi controller ya ce
court order ya karɓa"
"Ni dai ka yi mini wannan taimakon a nemo shi da
gaggawa, dan yana cikin garin nan, tun da ga ayyukan ta'addanci yana ta yi
yadda ya ga dama".
CP ya ce "In sha Allah, ka kwantar da hankalinka za ayi
duk mai yiwuwa, zan nemi zaƙaƙurai daga cikin mutanenmu, da suke dealing da
criminal cases, very soon zai zo hannu, DSP Nasir na san zai yi abun da ya dace
in sha Allah"
"Yauwwa to shikenan, ko dai sanarwa za ku yi, ace duk
in da aka gano shi a kamo shi, an sake shi ba bisa ƙa'ida ba"
Da sauri ya ce "No ai ba haka aikin tsaro yake ba, ai
wannan abun kunya ne ga hukumominmu, yanzu sanin in da yake shi ne babban
target ɗinmu, dan yaron yana da wayo sosai, na bibiyi record ɗin sa, sai an yi
taka tsantsan sosai wurin kama shi, sai an yi amfani da dabarun aiki, hatsabibi
ne sosai"
"To ayi ƙoƙarin hakan dan Allah".
***
Gudu-gudu sauri-sauri ta ƙarasa gida, saboda azababben
fitsarin da ya cika mata mararta, tana zuwa ɗaki ta watsar da komai a kan
gadonta, ta shiga banɗaki.
Sai da ta gama fitsarin, ta ji iska na shigarta, tayi wanka
ta fito, ta tattare kayan da ta watsar, ta samu riga ta shan iska ta saka, ta
shafa turare ta fita.
Kitchen ta shiga dan zuba abinci, ta ci karo da fate-faten
wake a cikin food flask ɗin ta. A ƙule ta ja uban tsaki, ta fito babban falo
kamar ta fashe da kuka, ta hau ƙwalawa mai aikinsu kira.
"Baba magajiya!"
Daga can wani sashen ta amsa da "Na'am, Arfa gani
nan"
"Na ga faten wake yau?"
"Eh, umarnin Hajiya babba ne, ita ta ce ayi faten
wake".
Cikin ɗaga murya arfa ta ce "Amma dai an san ba na ci
ko? Kin dafa mini wani abun ne?"
Magajiya ta ce "Wallahi har na ɗaukko doya na fara
frayewa, na ɗan dafa miki, na soya miki miya, aka kuma sakani aiki".
Nabila cikin kwakwazo take masifa "Saboda tsabar an
tsane ni, so ake na mutu a huta, in je aiki in dawo a kasa ajiye mini abinci,
sai a dafa abun da ba na so"
"Ke Nabila meye haka ne, hajiya ce ta bayar da umarnin
hakan, ki shiga kitchen ki dafa wani abun mana" Nabila ta kalli Yaya Sauda
ta ce "In je in dawo yanzu, sannan in shiga kitchen in hau girki, bari in
je in sha faten waken, duk abun da ya same ni, ku kuka kasheni, ai kun san
likita ya hana ni cin wake"
"To ki je ki ci ɗin mana, idan kin mutun sai ne? Banda
gulma amma ai ki na cin ƙosai da shinkafa da wake, ko duk su ba waken bane
ba"
Kamar ƴar goye, Nabila ta din ga zirarar da hawaye ta na
bala'i.
"Kar Allah ya sa ki ci abun da aka dafa, kya mutu da
yunwa agola ƴar wahala".
Cikin tsananin fusata Nabila ta ce "Tun da dai ba
shegiya ba ce ni da ubana, ai da sauƙi"
Cikin son kunna Nabila, Sauda ta ce "Meye marabarki da
mara uban?"
Baba magajiya da ke tsaye ta ce "A'a Sauda, dan Allah
kar ayi haka, ke fa babbace"
Sauda ta ɗaga mata hannu tare da cewa "Babu ruwanki, ki
wuce ki ƙarasawa mama aikinta. Ke kuma ki tsaya ki cigaba da hauka, banda samun
wuri ina na taɓa ganin agola da miƙe ƙafa".
"Ai gara ni, agolar ce, kuma iya wuya ni ƴar gari ce,
ba baƙuwar haure ba, jikar yarabawa. Kuma ni ba dan albarkacin ubana ba,
wallahi da na daɗe da barin gidan nan, gara na je na kama gida na yi zaman
kaina, iyaka ace ina zaman kaina, ba ɗan iskan da zai takura mini"
Sauda ta tsaya ta ce "To ki je ki kama ki yi zaman kan
naki mana, ke dama banda Abba a tsaye yake a kanki, ai ƴar zaman kantan za ayi,
kuma ƴar gagara".
Nabila ta buɗe baki za ta yi magana, suka ji gyaran muryar
Abba, daga saman bene. Tuni idon Nabila yayi jawur, saboda kuka da ɓacin rai.
Ya ce "Magajiya" cikin sauri ta ce "Na'am
ranka ya daɗe"
"A gabanki kina tsaye yaran nan suke faɗa? Ki ka kasa
tsawatar musu?"
Ta risuna ta ce "Tuba nake ayi mini afuwa".
Sauda ta ce "Wallahi Ab...." Ya dakatar da ita ya
ce "Ban tambaye ki ba, kukan me ki ke yi ke kuma?" Yayi maganar yana
kallon Nabila.
"Faten wake aka yi, ba a dafa mini komai ba, kuma yunwa
nake ji"
Ya ce "Wannan abun kawai shi ne abun kuka kuma? Ke a
rayuwarki ba zaki taɓa girma ba kenan?" Tayi shiru tana sheshsheƙar kuka,
kukan da yake jin sa har zuciyarsa.
"Magajiya, ko aikin wa ki ke yi, ki ajiye ki sama mata
abun da za ta ci, ba biyanki nake dan a farantawa wani a ɓatawa wani ba, duk
ƴaƴana nawa ne, babu banbanci a tsakaninsu"
Ta risuna ta ce "In sha Allah Alhaji, za a kiyaye"
"Ke kuma, ki cigaba da faɗa da yayyenki, zaki ga yadda
zan yi da ke. Kuma na gode da furunciki Arfa, zaki yi zaman kanki ko? Tun ina
raye ki ke wannan iƙrarin, ranar da na mutu ban san me zaki aikata ba, kin
kyauta" bai tsaya jiran me za ta ce ba, ya wuce ya koma ɗakinsa.
Sauda ta yi wa Nabila gwalo, Nabila ta ce "Ai ke
yakamata na yi wa gwalo, ni na yi nasara, tun da an ce a ajiye aikin babarki
ayi nawa, banza ƙatuwar kwabo" Nabila ta wuce ɗakin su, tana tunanin ko
dan wannan tijarar, ya isa tayi fatan tayi aure ta bar gidan nan.
***
Ɗan siririn matashi ne dogo, wankan tarwaɗa, sanye da kakin
ƴan sanda, da ɗan hanzari yake bin wata doguwar baranda, wadda ta sa da shi da
wata ƙofa.
Ya buɗe ya shiga da sallama, ya sarawa wanda ya tarar a
cikin ofishin, wanda da gani babu tambaya, ka san babba ne sosai a cikin
rundunar jami'an tsaro, duba da yanayin ranks ɗin da ke maƙale a kafaɗar
uniform ɗin sa, da kuma haɗuwa da tsaruwar office ɗin na sa.
Ya ƙame tare da sarawa mai office ɗin, ya yi masa alama da
ya zauna.
Ya zauna tare da sake gaida wanda ya tarar a office ɗin, da
uniform ɗin sa ke ɗauke da sunan ACP Solomon wada.
ACP wada ya kalli matashin ya yi murmushi ya ce "CSP
Nasir Yusuf"
Nasir ya waro ido ya ce "Wane ni Yallaɓai, Dsp ɗin
dai"
"Au Csp ɗin ne ba ka so? Ba abun mamaki ba ne ba, ka ji
gobe kai ne Cp na garin nan, kai koma IG gaba ɗaya"
Nasir yayi murmushi yana sunkuyar da kai.
"Ƙwazon mutum babu in da ba ya kai shi, kuma kar ka yi
mamakin ƙwazonka ya kai ka in da ba ka zata ba. Yanzu ba karatunka da kuma
ƙwazon ne ya kawo ka matakin da ka ke yanzu ba?"
Ya jinjina kai ya ce "Haka ne ranka ya daɗe".
Acp Wada ya ce "Good, wani aikin za'a sake baka, wanda
mu ke buƙatar sa da gaggawa, direct order ce daga Cp,ya kuma ce a jinjina maka
aikin office ɗin ka yana kyau"
Nasir ya tattara hankalinsa ya ce "Ok sir, na gode
sosai"
Solomon wada ya ce "Nasir, idan ka mayar da hankali
yadda ake so, ka gudanar da aikin nan, za ka samu cigaba a aiki sosai da
sosai"
Cikin girmamawa ya sake cewa "I will do my best in sha
Allah".
"Good" ya ɗaukko wani file ya ajiye masa, sannan
ya ce "Kwanakin baya, akwai wani ɗan daba, da ya addabi garin nan, kai ɗan
garin nan ne za ka fi ni sani, wai shi Aminu ana yi masa laƙabi da viper.
Shekarun da suka gabata yana tsare, sakamakon laifin da ya
aikata, kafin kwatsam mu samu sanarwar cewa an sake shi. So bayan sakin nasa,
akwai kokwanto a cikin sakin da aka yi masa ba bisa ƙa'ida ba ne ba, duk da
controllern gidan yari ya ce order aka bashi ya sake shi, bayan fitowarsa ya
cigaba da aikata miyagun laifuka a ɓoye, na sayar da miyagun ƙwayoyi tare da
ƙyanƙysar sabbin ƴan daba, da suka hana jama'a zaman lafiya a garin nan, wanda
yaƙi da wannan a ƙarƙashin kulawar office ɗin ka yake, a zone ɗin. Abun da muke
so da kai shi ne, Aminu ya shigo hannu, ko ta halin ƙaƙa."
Nasir ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Ok sir, tabbas
cases na dillancin ƙwayoyi da harkar daba, yana ƙara ta'azzara, amma laifin me
yayi aka kai shi kurkuku? Kuma ya aka yi, aka sake shi ba bisa ƙa'ida ba?"
"Wannan ba huruminka bane ba, duk ba shi ne a gabanmu
ba, kamo yaron shi ne abun da muka saka a gaba, wannan abun da ya shafi shari'a
ne, ɓarnar da yake aikatawa ta yi yawa. Kuma a zone ɗin ka yaransa suka fi
yawa, dan haka ka je ka yi iya ƙoƙarin ka a kai. Yabawa da nustuwarka, da
jajircewar ka ya sanya muka baka aikin nan, ina nan ina saurarenka, ba a
buƙatar ɓata lokaci. Ka je ka duba file ɗin a tsanake, akwai sauran
informations da za su taimaka maka wurin kama yaron, da duk wani record na
criminal acts ɗin sa yana ciki. Nan da gobe in Allah ya kaimu zaka dawo mini da
file ɗin. ba na buƙatar kuma ka yi wani abu sama da haka, kar ka ƙetare iyakar
da na gindaya maka".
"Ok sir, i will do mai best in sha Allah" ya ɗauki
file ɗin, tare da sake sara masa ya fita.
Ɓangaren Nabila kuwa, al'amuranta ba a samu sauyi ba, dan
duk shari'ar da ba ta yi mata ba, ba za ta mayar da hankali a kai ba.
Director kuma ya bar ta ne, saboda mutuncin mahaifinta Major
Yusuf da yake gani, mutum ne na gari kuma akwai tarin alkhairai da ya yi masa,
shiyasa ya ƙyale Nabilatake cin karenta babu babbaka.
Nabila gaba ɗaya wasu lokutan sai ta ji tana danasanin
karantar ɓangaren shari'a, yadda wasu abubuwan suke gudanawa sam ba sa yi mata
daɗi.
Hausawa suka ce sai hali ya zo ɗaya ake abota, ɓangaren
ƙawarta sumayya ma haka, kusan ƙalubale ɗaya suke fuskanta, dan har gara ma
Nabila tana da alfarma a wurin na ta aikin, Sumayya kuwa na ta babu sani babu
sabo.
Yau ganin motar Abba a gida bayan ta dawo daga aiki, ya
sanya ta fuskanci yana gidan, dan haka da ta zuba abincinta, sai ta hau saman
benensa.
A falonsa ta tarar da shi da Yaya Nasir, suna magana, da
alama magana ce mai muhimmanci suke yi, sai dai yayi shirin fita.
"Abba sannu da gida" "Yauwwa" ya amsa a
taƙaice.
Sai dai ta na zama ya tashi ya yi wa Nasir sallama, ya fita
ya bar falon.
Nasir ya galla mata harara.
A shagwaɓe ta ce "Dsp me na yi ne? Kwana biyu duk Abba
ya canza mini, kai ma kuma kana hararata"
"Ba dole ya canza miki ba, duk kin gallabi kowa a gida,
bayan na dawo daga kaduna ake gaya mini wai kin je biki kin yi dare, ƙarshe a
haraba ki ka kwana yayi punishing ɗin ki, ba ki zo kin bashi haƙuri ba. Law
firm ɗin ku director ya kawo masa ƙara, daga danna waya sai kwalliya ki ka iya,
ba kya son aiki, yayi ta bashi haƙuri ya ce a kula da ke a koya miki aiki, ko
ba a biya ki ba, shi zai din ga biyanki salaryn. Kwatsam jin kunnensa ya ji ki
na cewa ba dan shi ba, zaman kanki zaki yi, kin san kwana nawa ya ɗauka ba ya
bacci saboda wannan maganar da ki ka yi? Duk cikinmu babu wanda Abba yake
lelensa kamar ke, amma sai ba shi kunya ki ke ko ta ina?"
Cikin sanyin jiki, da tashin hankali ta ce "Innalillahi
wa Innalillahi raji'un, ban zaci ran Abba zai ɓaci har haka ba, to kuma ba ka
bashi haƙuri a madadina ba? Yaya sauda ce fa take ce mini agola, ni kuma ba na
son na gaya masa. Ba na son fushin Abba, dan Allah ka tayani ba shi haƙuri.
Maganganun Sauda ne suka ɓata mini rai, na yi dana sanin abun da na faɗa, amma
dan Allah Yaya Nasir ka bashi haƙuri"
Ya girgiza kai ya ce "No ni ba ruwana"
Kuka ta saka masa tana cewa "Wallahi ba zan ci abinci
ba, sai yanzu na ji maganar da na yi, ta yi nauyi ban san abba zai ji ba"
"Kin ga ya isa, kar ki saka ciwonki ya tashi na shiga
uku, ya mayar da fushin da yake yi da ke kaina" ai kamar ya sake
tinzirata, ta cigaba da sheshsheƙar kuka.
Cikin tsawa ya ce "Ke wai dan ubanki meye haka? Am i
your mate, ba magana nake yi miki ba?" Sai da ta razana, amma hakan bai
saka ta daina kukan ba.
Ya zuba mata ido, Nabila tun asalinta tun tana yarinya take
fama da taurin kai na tsiya, yanzu ko dukanta zai yi, ba za ta daina kukan da
take yi ba, balle ma yanzu ba wannan dan ta girmi duka. Har mamakinta yake yi,
ƙatuwar budurwa ta kammala degree, kusan shekara ashirin da huɗu amma tana abu
kamar yarinya ƙarama. Tsaki yayi, ya tashi shi ma ya fice, ya ƙyale ta, ta ci
uban kukanta, ta kwanta a kusa da flask ɗin Abincinta ta hau baccin gajiya.
A tsanake Nasir yake duba file ɗin da aka bashi, a kan Aminu
viper, da aka ce lallai ya kamo.
A record ɗin da ya duba, ya gano zuwan Aminun gidan yari, ba
sau ɗaya bane ba, a kan mabanbanta laifuffuka da suke da alaƙa da harkar daba,
da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi.
Sai dai abun da ya ɗaure masa kai, ba a shigar da dalilin da
ya sanya, aka kai shi prison na ƙarshe ba, an dai nuna ya aikata wani babban
laifi ne, da ga cikin manyan laifuka da bai kamata daga lokacin faruwar abun
zuwa yanzu ace an sake shi ba, haka zalika an cire wasu abubuwa masu muhimmanci
da yakamata ace ya gani a cikin file ɗin, sannan ga shi solomon Wada ya yi masa
umarni da ya yi amfani da iya abun da aka bashi.
"To menene dalilin haka?" Ya tambayi kansa, a
lokacin da kan na sa ya ƙara ɗaurewa.
Sake duba file ɗin yayi yana tunani, kamar ya taɓa duba wani
case, makamancin record ɗin da yake cikin file ɗin, sai dai kamar sunan ba haka
yake ba.
"Aminu Viper" ya sake maimaitawa.
Ayshercool.
08081012143
⚔️*ƘARFE A WUTA ⚔️
AISHA ADAM AYSHERCOOL
3
Sama-sama Nabila ta ke jin hayaniya a kanta. Amma ta ƙi
motsawa.
"Ke Arfa" yayi maganar yana riƙe hannunta.
Tashi ta yi zaune tana buɗe idonta a kan Abba, a sanyaye ta
ce "Abba ka dawo?"
"Na dawo, tun da na tafi ki ke kwance a nan, ko abincin
ba ki ci ba?"
"Abba Yaya ne ya ce kana fushi da ni, dan Allah ka yi
haƙuri ba zan sake ba"
Major ya ce "Eh ya kira ni ya gaya mini, na haƙura
tashi ki wanke fusarki ki zo ki ci abincinki" ta tashi ta shiga banɗakin
falon, ta wanke fuskarta, ta zo ta zauna ta saka spoon ta fara cin abincin.
Ya numfasa ya ce "Rashin ji ne, ya yi miki yawa arfa,
duk yadda na so na yi haƙuri sai kin ƙure ni, ban bi daɗin abun da kunnuwana
suka jiye mini ba, kina iƙrarin zaki yi zaman kanki"
"Abba ka ce fa ka haƙura, ba zan sake ba"
"To shikenan na ji, ci abincin"
Umma tayi sallama da flask ɗin shayi, matarsa ta biyu,
kasancewar yau girkinta ne.
Ta zauna a kusa da shi, ta haɗa masa tea, ya karɓa yana sha
ya na yi wa Nabila hira, kamar bai yi fushi da ita ba, har ta ɗan ware.
Kiran sallar magariba ne, ya sanya ta tashi ta bar ɗakin,
dan umma ta ji haushin zaman da Nabila ta yi, ita kanta Nabila ta so ba su
wuri, amma Abba ya cigaba da jan ta da hira.
Da ya dawo daga sallar magariba, kai tsaye ɓangaren mama ya
wuce, tana zaune a falonta, da Sauda su na kallon tv.
Gyaran murya yayi, sannan yayi sallama, suka amsa suna yi
masa sannu da zuwa.
Ba tare da ya amsa ba ya kalli Sauda ya ce "Sauda nan
gidan waye?" Ta ɗan yi turus tana kallonsa.
"Ki amsa mini"
"Gidanka ne Abba"
Ya ce "Masha Allah, idan ba zaki iya zama da ni, da
tsarina ba, ko ki koma gidan tsohon mijinki, ko kuma ki fitar da miji ki yi
wani auren"
Cikin damuwa Mama ta ce "Major me yayi zafi haka?"
"Baƙar aƙidar ki, da ta ara ta yafa, ba zan lamunta ba.
Kun sani ba na ɗaukar duk wani abu da ya shafi Nabila da sauƙi, yadda na yi
mata shamaki, da wanda ya zama katangar rayuwarta, dole na tsaya tsayin daka,
na kula da ita kamar yadda na yi alƙawari. Ba zan lamunci a cigaba da wulaƙanta
mini ƴa ba, har ta fara iƙirarin za ta yi zaman kanta. Babu wani ɗa da ya fi
Nabila a cikin gidan nan, idan ki ka sake ce mata agola, to zaki fita ki bar
mini gida ki nemi wani uban".
Cikin takaici mama ta a ce "Amma da kunnenka ka ji ta
faɗa mata haka? Ka san dai makirci irin na yarinyar nan ko?".
"Kunnena ne ya jiye mini, ko zan yi mata ƙarya
ne?"
Suka yi tsur-tsur baki daya.
Ya ja guntun tsaki ya bar falon.
Yana fita sauda ta ce "Mama dan Allah sai yaushe Abba
zai daina fifita yarinyar nan a kanmu, tun da aurena ya mutu bai taɓa yi mini
gori ba sai yau, saboda ita?"
"Ba ke kaɗai ba, ni kaina yadda ki ka san na yi mata
kucciya, duk ita ce matsalar gidan nan, amma zan kawo ƙarshen komai da kaina,
ki bar ni da su".
Nabila kuwa na ɗakinta, itakaɗai, tana duba document ɗin
shari'ar da director ya saka aka ba ta, sai dai gaba ɗaya ba ta da intrest a
kan shari'ar, da ta gaji ma, ajiyewa ta yi ta hau waya da saurayi.
Wata matashiyar budurwa ce ta shigo ɗakin ta ce
"Wallahi Nabila abun da ki ke yi ba kya kyautawa"
Nabila ta ɗan kalli Asiya, ta katse wayar ta ce "Da na
yi me?".
"Kin saka Abba ya yi wa mama da Anty sauda kaca-kaca
saboda ke, sai da Anty sauda ta yi kuka".
"To ai cewa zaki yi, Abba bai kyauta ba ni meye nawa a
ciki?"
"Amma ke ki ka gaya masa ta ce miki Agola, bayan yayi
musu mu ma ya iskemu a babban falo, ya yi ta yi mana faɗa".
Nabila ta ce "Ashsha, ai kin san ni bana kai ƙara, ko
dai na ɗauki mataki, ko kuma Allah ya saka mini da gaggawa"
Asiya ta ce "Ai shikenan, kowa yayi na gari
kansa".
Nabila ta ce "Allah ya yaye miki Aisya, ke ma fa matar
nan idan ta tashi karta miki wulaƙanci, ba saurara miki take yi ba, daga ke har
umman, amma ku yi ta bin ta kamar wata shugaba, ni dai ba mai takani ban ɗaga
ƙafar na karya ba"
"A'a ai ke ki ka ce, ke ki na da ma dogara"
Nabila ta yi tsaki, tare da furta "Allah ka aurar da ni
na huta da wannan kacaniyar gidan, Ya Allah dogo mai gemu" ta fita daga ɗakin
tana addu'a.
Bayan kwanaki takwas.
A tsaye yake ƙyam, kamar ƙofa, kasancewar in da yake a
tsayen ba a iya ganinsa sosai saboda duhu, sai dai inuwarsa ta nuna dogon
mutum, kakkaura.
Ya ɗauki ɗankwali, ya ɗaure kansa da shi, tare da naɗo ɗankwalin
ya rufe fuskarsa sai idanunsa kawai ya bari a waje.
Ya laluba hannunsa, ya ɗaukko wata irin doguwar wuƙa, ɓangare
ɗaya zarto, ɗaya kuma kaifi, ga ta da uban tsini, a ƙalla za ta yi kamu uku, ya
ɗaga rigarsa ya soketa.
Ya sake ɗaukar wata ya soke a jikin wandonsa.
Yanayin takun da yake kawai, ya isa ya tabbatar daƙaƙarfa
ne, saboda yadda ƙasa ke amsa takun nasa.
Bayan wasu awanni, duhun dare ya ƙara yi, sahu ya ɗauke, sai
haushin karnuka ko ina.
A ƙofar wani gida ya tsaya, ya din ga waige-waige, ya
tabattar da babu kowa. Tamkar ɗan biri, haka ya cafke katangar gidan ya dira
ciki.
Ya saka mukulli, ya buɗe wata ƙofa a cikin gidan da duk ta
yi ƙura, ya buɗe ta ya kutsa kai ya shiga ciki.
Tsayawa yayi ya kunna fitilar wayarsa, yana haske ɗakin,
take ya ji wani abu mai tsananin ɗaci ya fara kaiwa da komowa a ƙirjinsa, ya ji
numfashin sa na barazanar barin ƙirjinsa.
Jikinsa ne ya fara rawa, ya ji tamkar hankalinsa zai gushe,
ya durƙusa a wurin yana wani irin haki, cike da wani yanayi na mai shirin fita
hayyaci.
Hayaniya ya fara jiyowa a waje, hakan ya saka shi miƙewa
tsaye babu shiri.
Cikin sauri ya fito daga ɗakin, ya kama katanga, ya leƙa,
sai dai yana leƙawa ya ga ƴan ƙato da gora da miyagun makamai, sun fara taruwa
a kewayen gidan, kasancewar akwai hasken farin wata, kuma akwai hasken ƙwayayen
solar hakan ya bashi damar ganin makaman da suke hannun su.
Babu tsoron komai, ya haye katangar, ya hau saman roofing
gidan, ya dira ta wani ɓangaren, jin sautin dirarsa, ya sanya suka rufa masa
baya, ta in da suke jiyo sautin gudunsa har da karnuka su na kururuwar a tare.
Sai dai duk da wannan ƙira da Allah ya yi masa, ta siffar
ƙarfi ba ya jin nauyin jikinsa, ya din ga dukan ƙasar da dukkanin nauyin
jikinsa, ba su ankara ba, ya ɓace musu ɓat kamar walƙiya.
A bakin titi suka tsaitsaya suna haki, su na mayar da yadda
aka yi.
Ɗaya daga cikin su ya ce "Anya yaron nan, ba da layar
zana yake amfani ba?"
"Ba wata layar zana, tsohon hatsabibi ne kawai, ni na
yi mamaki ma da ya gudu ai, da da ne fa, wallahi sai ya illata ku kan ya gudun.
Ai kamar yadda na gaya muku ne, da na ji alamun ya zo, zan kira ku a waya na
sanar muku, ai ba zan sake sukuni ba sai ya je hannu, na za ta ma zaku kira ƴan
sanda ne"
Ɗaya daga cikin jami'an sintirin, ya ce "Ko zamu kira
ƴan sanda, mu yakamata mu fara huɓɓasa mu kama shi, sai mu miƙa musu shi,
wannan gudun nasa yaushe muka kira ƴan sanda ma"
"Amma duk da haka, yakamata su san yana zuwa ai"
Shugaban su ya ce"Muddin suka sani, canza taku zai yi,
ba zai sake zuwa ba".
Malam lawan da gidan sa ne a jikin gidan da yake zuwa ya ce
"In ji wa? Ba zai taɓa iya daina zuwa gidan nan ba, yadda ka san ya binne
asiri a ciki, kodayeke sai ta yiwu ma asirin ya binne, wannan hatsabibancin
nasa akwai lamarin sihiri a ciki, amma zan cigaba da saka ido, da ya zo zan
kuma kiranku"
"To shikenan malam lawan mun gode, yanzu ka koma gida,
bari mu koma bakin aiki, ko kuma a raka ka ne?"
"Ahha haba, kamar ba namiji ba, ba wani abu bari na
koma, ai ya riga ya gudu" Suka yi sallama ya nufi layinsu.
Sai dai yana daf da ƙarasawa gidansa, kawai ya ji an yi ball
da shi, kasancewar sa ɗan ƙaramin mutum, sai jin sa yayi, ya yi sama ya dawo
ƙasa kamar wani karmami. Ya tashi a gigice yana zaton ko gamo yayi da aljani,
ya hau waige-waige.
Haske shi ya yi da fitila, sannan ya ce "Kwana da yawa
malam lawan, tsohon butulu, da na ƙyale ka ban yi maka komai ba, shi ne ka
cigaba da yi mini bita da ƙulli?"
Cikin kwakwazo, da tsananin razani ya ce "Na tuba, na
bi Allah na kuma bi ka, dan Allah" kan ya ƙarasa, ya karya shi ɓaras, ta
hanyar saka ƙafa, ya yi masa wani irin duka a ƙafarsa ɗaya.
Malam lawan ya a kurma ihu, cikin tsananin zafin nama, ya
cire hular kan malam lawan,, ya tura masa a baki, sannan ya ciro wuƙar ƙugunsa
ya yanke shi a damtsensa, aikuwa jini ya ɓalle.
Ya durƙusa a gaban sa ya ce "Yanzu ai ka ji daɗin bayar
da rahoton zuwana, ragon maza kawai" ya tashi tsaye ya ja da baya ya ɓace
a cikin duhu, ya bar shi a mawuyacin hali, ga karaya ga yanka, gashi kuma ya
toshe masa baki.
Ko da ya koma gidansa da yake zaune, ciro wuƙar da ya yanki
malam lawan yayi, yayi jifa da ita. Ya tsaya yana haki, abun da ya yi alƙawarin
dainawa, yau ya yi, ya zubarwa da wani jini.
Ya dafe kansa yana huci cikin tsananin damuwa.
**
Yau sumayya ba ta haɗa tafiya da Nabila ba, dan da wuri
sosai ta fita, za ta shiga asibitin murtala ta duba wata yayar babansu da aka
kwantar a emergency, za ta kai musu abinci.
Su na tafe da mai adaidaita sahu, ta hango mutane na ta
shiga su na fita a wani layi, duk da lokacin gari bai gama hasken da za ace,
mutane suna wannan tururuwar ba.
Da sauri ta tsayar da mai baburin, ta biya shi kuɗinsa,
ta sauka, ta nufi layin da mutane ke shiga su na fita.
Wurin duk babu mata, sai maza, amma hakan bai hanata kutsawa
da son gano abun da yake faruwa ba.
Tsayawa ta yi ta tambayi wani magidanci, abun da yake
faruwa. Ya sanar da ita, gawar wani yaro aka tsinta, a bayan maƙabartar
unguwar, an yanke masa al'aura da wasu sassa na jikinsa.
Jikinta na tsuma ta cigaba da kutsawa tana faɗin "Ku
matsa, ni ƴar jarida ce" tare da nuna musu id card ɗin ta.
Ta ɗaɗɗauki hotunan yaron, sannan ta tsaya tattaunawa da
mutanen da suka fara zuwa su ka tarar da abun.
Sai kiranta ake yi a waya, ana jiran ta kai abinci, amma sai
da rana ta ɗaga sosai, aka gama komai ƴan sanda suka zo, sannan ta yi shirin
tafiya, shi ma sai da ta karɓi lambar wayar wani ɗan sanda, da zimmar zai din
ga ba ta update na sakamakon binciken da za su yi, a kan gawar.
Ko da ta je asibiti ta sha faɗa,na rashin kai musu abinci da
wuri, ko a jikinta, saboda ta samu rahoto, dan haka tana ajiye musu abincin, ta
yi waje.
Sai dai ba ta fito daga emergency ba, ta din ga jin ihun
wani babban mutum, kamar mara gaskiya, haka ta koma tana leƙawa ta ga abun da
yake faruwa.
Magidanci ne, ake yi masa ɗinkin wani uban yanka a
damtsensa, jikinsa yayi kaca-kaca da jini, duk da ana ta yi masa allaurar kashe
zafi, amma sai ihu yake yi.
Babu neman izni, ta afka ciki ta ce "Sannu bawan Allah,
ka yi haƙuri Allah ya baka lafiya, ka daure"
Duk sauka waiwayo su na kallonta, har da ma'aikatan, mutumin
ya ce "Na gode sosai"
Ta ƙara matsawa ta ce "Amma hatsari ka yi ne? Kodayeke
wannan ai yankan makami ne ba hatsari ba"
Ya ce "A'a wani ɗan daba ne, ya sare ni jiya cikin
dare, dama hukuma ta daɗe ta na neman sa"
Sumayya ta gyara tsayuwarta ta ce "Subhanallah, bawan
Allah a wace unguwa ce haka? Ko rigima ku ka yi da shi ne?" Ƙanin malam
lawan da yake tsaye a wurin, a fusace ya kalli sumayya ya ce "Dalla malama
fita, mutum yana fama da kansa, kin zo ki na yi masa wasu surutan banza"
Ta ce "A'a Allah ya baka haƙuri, ka sani ko akwai wani
taimako da zan iya yi masa. Kalli saran da aka yi masa fa, idan ba za ka damu
ba, zan naɗi muryarka, mu saka a radio, ko Allah zai saka, hukuma su bi maka
haƙƙinka, barin su da ake yi suna cin bulus ya sanya suke cigaba da ɓarna".
Malam lawan ya ce "Ke rufawa kanki asiri, hatsabibanci
da ta'addanci yaron, ya wuce tunanin ki"
Sumayya ta zaro wayarta, za ta yi magana, sai ga wasu mutane
guda biyu sun shigo da wani kaki a jikinsu, da ba ta san na menene ba, suka
mayar da ƙofar ɗakin suka rufe.
Malam lawan ya kalle su, ba su ne ƴan sandan da aka kirawo
suka tsaya masa, likitoci suka zo kansa ba ne.
Sumayya ta yi tsilli-tsilli da ido, ɗaya ya ƙirga
mutanen da suke cikin ɗakin, da likita ɗaya, nurse ɗaya, sai ƙanin malam lawan
da sumayya. Dan duk maƙwabtan da suka kawo shi, sun tafi wurin sana'oin
su. ya ce "Ku biyar ne a ɗakin nan, idan ka sake mu ka ji labarin
sunan wanda ya yi maka wannan raunin, to za ka maye gurbinsa da ya bari na
gidan yari, dan haka ka ja bakinka ka yi shiru".
Sumayya ta ce"Ban gane ba Yallaɓai, mutum mai laifi
kuma ace kar a faɗi waye? Ba ka ga irin illar da aka yi masa ba ne, ga karaya
ga rauni, da ya kashe shi fa?"
Ya ba ta amsa da "Da ya kashe shi, bakinki zai iya
sakawa, ki ɗauki hukuncin da za ayi masa na kisan" daga nan suka juya suka
fice.
Mamaki ya mamaye sumayya, ta ce "Kai kuwa bawan Allah,
waye wannan shi kuwa, da har jami'an tsaro masu kaki, za su hana bayyana
laifinsa, ana sane aka ƙi kama shi kenan?"
Malam lawan ya ce "Ba zaki ja mini masifa ba, ki fita
ki bar wurin nan, na ji da masifa ɗaya, bayan ɗinkin nan a karye nake
wallahi"
Cikin tsananin naci, da son samun rahoto, ta kwantar da
murya za ta lallaɓa shi, ta samu labari, amma da likitan da ƙaninsa suka koreta
daga ɗakin.
Fitowa ta yi, tana ta mamakin abun da ya faru, yaya za ayi
hukuma ta bawa mai laifi kariya, wane irin abu ne haka?.
Ba ƙaramar makara ta yi ba, amma tunanin abun da ya faru, ya
fi ɗaure mata kai.
***
Sannu a hankali yake yi wa kansa allura, yana yi yana fatan
samun abun da yake so, a hankali ya gama ɗurawa jijiyarsa ruwan allurar da yake
fari tas a cikin sirinji, bayan ya kammala tsaf ya fara jin kansa yana yi masa
nauyi.
Take idanunsa suka yi mitsi-mitsi, ya soma lanƙwasa kansa,
yana jin idanunsa kamar za su fito waje, suna yi masa yaji, a haka ya kunna
sigari, ya kashingiɗa, ya na bawa sama hayaƙi,yana jin yadda jikinsa ke son
bijirewa aikin allurar.
Wayarsa ce ta fara vibrating, ya miƙa hannu, ya ɗaukkota ya
duba, yana zaton ko a cikin yaransa ne, sai dai ya ga private number ce.
Har zai ƙi ɗagawa, sai kuma ya ɗaga ya saka a kunnensa, amma
bai yi magana ba.
Daga cikin wayar aka ce, "Meyasa ba ka gajiya da neman
magana ne? A wannan karon ma sai da ka saka na yi abun da na goge ɓarnar da ka
yi, yakamata ka nutsu Aminu"
Ya saki hayaƙi, tare da ɗan kaɗe tokar da sigarin ta tara,
sannan ya ce "Waye kai? Sannan waye ya saka?"
Mutumin yayi dariya, ya ce "Mutum mai ba ka kariya,
domin cimma nasa muradin, yakamata ka sauƙaƙa mini aiki, ka daina aikata
abubuwan da za su din ga barin trace a kan ka".
"Ka yi muguwar kasadar ƙoƙarin cimma burinka da mutum
irina, kar ka manta viper ake yi mini laƙabi da shi, macijin da ya fi kowanne
hatsari, idan ka bari na sare ka, ka gama yawo" yana gama maganar ya
cillar da wayar, ya ɓata fusaka kamar ya fashe da kuka.
Cikin fusata ya ce "Ni again? wani ya kuma amfani da
ni? Impossible zan watsa dafina a in da ya dace da in da bai dace ba, sai na
tabattar da danganawa ga kunyar ƙarshe, ko da kuwa za ayi mutuwar kasko"
ya yinƙura da nufin ya tashi tsaye, amma ya kasa sarrafa gangar jikinsa, hakan
ya tilasta masa komawa ya nemi wuri ya kwanta.
Duk da irin faɗan da sumayya ta sha a wurin aiki a kan
makara, bai dame ta ba, jikinta sai tsuma yake saboda ta zo da rahotanni masu
muhimmanci da ɗaukar da hankali.
Ofishin head of news ta je, ta shiga da sallama.
Matar ta ɗago ta amsa mata da ƙyar, ta ƙarewa sumayya kallo,
ta ce "Yanzu ne lokacin shigowa aiki ko? Gaba ɗaya yaran yanzu ba kwa ɗaukar
aiki da muhimmanci, kodayeke karatun ma ba wani na kirki ku ka yi ba, duk da
satar amsa ku ke gamawa. Ki shiga hankalinki kafin na kai maganar nan wurin
MD"
Sumayya ta risuna ta ce "Afuwan anty, in sha Allah ba
zan sake ba, na samu wasu rahotanni ne masu muhimmanci, da ya san na tsaya a
hanya, shiyasa na makara na kawo miki a tantance ne ko za a saka su a
news"
A yamutse matar ta ce "Na menene" cikin farinciki
da jin ƙwarin gwiwar ta yi abun arziki ta fara da gaya mata abun da ya faru a
asibiti.
Amma matar sai cewa ta yi"Amma ba ki da hankali ko? Ta
yaya zamu saka wannan shirmen a news?"
"Anty ai a rahotanni, ko a janyo hankalin hukuma....
"Dalla yi mini shiru, business mu ke yi a nan mu, ke fa iyayinki da rawar
kanki yayi miki yawa sumayya. Meye hujjarmu idan aka tsutsiye mu, cewar hukuma
na ɓoye mai laifi?"
Sumayya ta ce "Wallahi a gabana aka yi, mutumin yana
nan a emergency"
"Kin ga idan ba ki da abun faɗa, fita ina da abun
yi"
Sumayya ta yi iya ƙoƙarin ta, ta danne abun da yake taso
mata na fushi ta ce "To shikenan, sai kuma akwai abun da na gani, ina kan
hanyar tahowa nan, a nan wajen gari, an tsinci gawar yaro an cire masa wasu
sassan jikinsa".
"Almara kenan, wa zai yadda da wannan zancen?"
"Ba zance ba ne ba, na yi recoding ɗin maganar wasu
daga mutanen da suka fara cin karo da abun".
"Sumayya, ba irin wannan labaran mu ke buƙata ba dan
Allah, je ki su murtala sun fita neman rahotanni, ki din ga kawo sensitive
abubuwa"
Summaya ji tayi wata irin ashar na kai komo a wuyanta, da
take ƙoƙarin narkawa matar nan, ta rasa abun da ta yi mata, haka kurum ta tsane
ta. Ta yi ta kyararta ba ta son ta ga tayi wani abu na cigaba.
Sumayya ta fice daga office ɗin kamar ta yi kuka, ta koma
reception ta nemi wuri ta zauna.
Ba uwar da ta tsinana a aikin yau, tun da head of news
department ta yi mata wulaƙanci.
Kasancewar a makare ta je, ya sanya lokaci yayi gudu,
Lawisa, wato head of news ɗin, ta din ga shiga tana fita, ta na kaiwa tana
komowa, idan ta kalli in da Sumayya take sai ta haɗe rai.
Wannan karon bayan ta fita, a tare suka shigo da managern
director, sai karairaya take yi masa, tun da ya shigo ma'aikatan suke ta gaishe
shi.
Ban da sumayya da ɓacin rai ya saka ta cika ta batse.
Sai da yayi gyaran murya ya ce "Wannan ba sabuwar staff
ɗin mu ba ce? Ya na ganki a nan? Wane department aka kai ta ne?"
Lawisa ta yi caraf ta ce "Sir ba ta da ƙwarewar aiki ne
haryanzu, ana ɗan nunnuna mata aiki ne, kafin ta gama gogewa".
Ya ce "Ok, babu laifi" sumayya kamar ta kwaɗawa
lawisa mari, a fusakarta da ta sha uban bleaching, duk tayi taruwar jini.
Ta daure ga gaida MD, sannan suka wuce gaba.
Tsaki Sumayya ta ja, tana duba wayarta.
Sai dai jin sallamar Nabila a reception ya sanya ta ɗago da
sauri tare da amsa mata.
"Ya na ganki a nan?"
Nabila ta ce "Ke baki iya karrama baƙo ba ko?" Ta
tsaya suka gaisa da admin ɗin da ke reception, sannan ta ƙarasa kusa da Sumayya
ta zauna.
"Arfa, ya na ganki yanzu ne? Lokacin tashi daga aiki
bai yi ba?"
"Kema ya na ganki a nan kamar mara galihu, ke baki da
office ɗin da zaki zauna ne? Ki zo chambermu ki ga ofishin da aka bani hajiya,
kamar wata sarauniya"
Sumayya ta ce "Eh ofishin da baki damu da aiki ba ko,
sai sun dawo da ke gadin chamber tukuna".
Nabila ta yi dariya ta ce "Kin san wani abu, wai nan
aikena aka yi, zan je na lallaɓa na zo da wata mata, ko in tattauna da ita,
sannan in je shagari firm, zan haɗu da wani lawyer, kuma ni wallahi kaina ciwo
yake yi"
Sumayya ta kalleta ta ce "Ba zaki ba kenan?"
"Ai faɗa ma ɓata baki ne, sumayya wurin nan naku mai
kyau, tashi ki rakani na zaga" duk da ran sumayya babu daɗi, amma ganin
Nabila ya sanya ta jin sanyi a zuciyarta.
Suka shiga zazzagawa, ta kaita news room, sai dai su na buɗewa
suka tarar da MD da lawisa a ciki, suna aiki.
Sumayya ta risuna ta ce "Am sorry sir, ban san ku na
ciki ba, Arfa mu je ki ga....
"A'a tsaya mana na ga nan ɗin, Nabila ta shiga cikin
fara'a ta ce "Yallaɓai ina wuni?"
Shima cikin fara'ar ya ce "Lafiya ƙalau, ya ki
ke?"
"Lafiya lau sir, ina fatan ba zan takura muku ba, ina
son sanin abubuwan da ban sani ba a rayuwata, mussaman wanda ba field ɗina ba,
sister ina wuni?" Tayi maganar tana kallon lawisa da ta yi bala'in haɗe
rai.
Lawisa ta takurawa Sumayya ne, saboda tana ganin ƴar gayu
ce, ga ta baƙa amma baƙinta mai kyau ga ƙwazo, tana gudun ta ƙwace mata
matsayin ta, kuma ita bazawara ce, a da a wurin babu wanda ya kaita gayu a
wurin, amma yanzu sumayya ta fita.
Yanzu kuma ga Nabila, ita da take da hasken fata ma sosai.
Nabila ba ta san lawisa ta amsa ko ba ta amsa ba, ta ja
kujera ta zauna, tana yi wa MD tambayoyi, a kan abubuwan da suke cikin news
room ɗin.
Lawisa ta ƙulu,ta din ga harar Nabila, amma ko a jikinta,
ita kanta sumayya sai da haushi ya kamata abun da Nabilan take yi.
Nabila ta ce "Yallaɓai, ko zaka saka mini lambarka,
idan wani abu ya kama na aiki, zan iya taimakawa i am barrister Nabila
Yusuf"
Ya ce "Wow, what a very young and beautiful barrister,
kin zama lawyer da ƙananan shekaru, ya karɓi wayar Nabila, ya saka mata
lambarsa, ta tashi ta yi musu sallama.
Sumayya kamar ta yi bindiga, su na fita ta din ga ɗurawa
Nabila ashar, a kan abun da ta yi, tare da gaya mata alaƙar Lawisa da kuma MD.
Nabila ta ce "Sumayya, dan Allah kar ki ɓoye mini, idan
yana da kuɗi na ci rabona, na ga zai yi son mata"
Ganin Nabila na neman mayar da ita mahaukaciya, sai ta canza
maganar.
"Ke kin san menene? wai ni zan kai rahoto har kashi
biyu, sakaryar matar nan ta ce ba za a saka ba, wai ba sa buƙatar irin wannan
labarin, MD ya tambayi me nake yi a reception ba na aiki, wai ta ce masa ban
iya aiki ba, na rasa uban da na tsare mata ta tsane ni, dama ni na samu damar
da ake baki, a wurin aiki, in yi wata shida ina aiki a wurin, wai ban iya aiki
ba, da yake kwanan nan ya dawo daga ƙaro karatu, tun da aka ɗaukemu ya
tafi".
Maimakon Nabila ta tausaya mata, sai ta hau dariya, "Ai
kawai ki fara soyyaya da MD ko ta bala'i, shi ne zaki rama".
Sai da ta ga Sumayya ta yi fushi sannan ta ce "Sorry my
sumy, maganar gaskiya babu daɗi, kuma kishi take da ke kuma tana ƙoƙarin kare
abun da take so, shikenan"
Idon sumayya ya tara hawaye ta ce "Sai kuma ta din ga
daƙile ni a harkar aikina? Ta yi mini adalci kenan?"
Nan ta ba wa Nabila labarin abun da ya faru, daga fitowarta
daga gida, zuwa yanzu.
Nabila ta ce "Na shiga uku, sumayya me ƙasarmu ke son
zama ne? A zahiri an nunawa mutane ana neman mai laifi, a baɗini kuma hukuma na
ɓoye shi? Duk yadda ake fama da ƴan daba da masu ƙwace a garin nan, tirƙashi
ana maganin ƙaba kai yana daɗa kumbura, ke ba ki san sunan wanda ya yi laifin
ba?".
Sumayya ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, bai faɗa ba,
korata ma suka yi".
"Mu ƙarasa titi mu tari napep mu je asibitin, mu
tattauna da shi mutumin, ni kin san ba na tsoron a mutu ko a yi rai. Sannan zan
je na samu Yaya Nasir na yi masa maganar wannan ai abun kunya ne"
Sumayya ta girgiza kai ta ce "A'a, na tsorata da
kashedin da aka yi mana, a bar zancen kawai, ban san suwaye mutanen ba".
Nabila ta ce "Wallahi sai mun je, akwai wata shashasha
da ta isa ta hana ki cigaba a rayuwa, idan ma ba a saka radiyo ba, sai mu
kwatsa a media ina da mabiya sosai a social media, sai ayi duk wadda za
ayi.!!!"
Ayshercool
08081012142
⚔️*ƘARFE A WUTA ⚔️
*AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Page 4
"No Nabila, abun da ki ke yi is too risky, mutanen nan
da gaske suke, they mean what they said, kar ki jefamu a matsala"
Nabila ta ce"Karatunki ya tashi a banza kenan sumayya?
Idonki har da hawaye saboda takaici. Wasu lokutan kin fiye sokwanci sumayya, da
ni ce da tuni na ci buhun ubanta".
Sumayya ta ce "Ni ce sokuwa ko? na gode amma ni ba zan
iya kasadar da ki ke yi ba, na rasa aikina, but wait mu je na rakaki in da aka
aike ki mana"
Nabila ta ce "Wa? Taɓ tuni na kira MD na bashi uzuri,
dama barrister Habib ne ya aike ni, yadda wannan matar ta wurin aikinku take,
lawashi ko lotion take, haka yake yi mini, ba ya ƙaunata"
"A'a, naki ya sha banban da nawa Nabila, shi taimakonki
yake yi ai"
Nabila ta kwaɓe fuska ta ce "Ke, idan fa kin ga ina
zuƙewa a aikin nan, wanda za a kare ba shi da gaskiya ne, MD zan saka ya canza
mini team daga na su Barrister Habib, na Barrister Bashir nake so, wata
zazzafar shari'a za su kara, shari'ar manya ce, a kan kuɗi, zuwa zan yi na sha
kallo, kuma an ce akwai yiwuwar na haɗu da masoyiyyata kwanan nan"
Sunayya ta ce "Wa kenan?"
"Anty Naja'atu Bunkure mana, kin san am die hard fan of
that woman, Barrister Naja'atu duniya ce, ga gayu malam, harshenta akwai
turanci, kamar wadda aka haifa royal palace ɗin Elizabeth"
Sumayya ta yi tsaki ta ce "Aikin banza ƴar wahala, ita
ta zama abun da ta zama a harkar aiki, har tana burgeki, ke kuma kina zaune
kina shashanci, wallahi ƙarshe ki koma ƴar ɗaukar jakarta"
Nabila ta ce "Kan uba, degree holder in yi dakon jaka,
Kin ci mutuncina fa,
Sumayya ta girgiza kai, haryanzu Nabila shirirta da yarinta
na damunta.
Ko da Nabila ta je gida, tun a tsakar falo take tambayar
magajiya, ina DSP.
"Bai dawo daga aiki ba, na ji ɗazu yana cewa ko za su
je ringin"
Nabila ta ce "Aikuwa ya yi ya dawo, sun bayar da maza,
in mun zauna ya yi ta cewa police ya fi lawyer, yau zai sha kunya idan ya ji me
suka yi. Yau zazzafan debate ne tsakanina da shi, har lemo zan yi mana aji daɗin
yin musu"
Anty ta ce "Ka ji mashirirciya, musun da za ku yi za ki
haɗawa lemo?".
"Eh mana, ɗan sanda sharri, lawyer kuma musu" tayi
maganar tana dariya.
Wani mugun kallo mama ta yi mata, yaran gidan nan har take
suke yi wa Nasir da discipline master, saboda yadda suke jin tsoron sa, amma
tsakaninsa da Nabila sam ba haka bane ba, suna good time sosai da Nasir, kuma
duk gidan bayan Abba ba ta da abokin hira ko shawara sai shi.
Nabila ta share mugun kallon da maman ke yi mata, ta tafi ɗaki.
Misalin ƙarfe huɗu na yamma, Sumayya ta ga kiran lawisa,
kawai ta basar ta cigaba da kallon tv, ta kira ya kai sau huɗu sannan ta ɗaga.
"Ki na ji ina kiran waya ki ka ƙi ɗagawa?"
"A silent take, bacci nayi ne".
"Ki tura mini recodings ɗin nan, su murtala ba su sami
wani samo rahotanni masu muhimmanci ba, kuma na ga su Mikiya radiyo duk sun
wallafa labarin yaron nan, ki turo mini mu ga wanda za a iya tacewa a
saka" Sumayya ta taɓe baki ta ce "To"
Ta kashe wayar, ta ce "Allah ya ƙara, da mu muka fara
sanar da labarin, kuma mu ka saka a internet, ai da ya fi, tun da ni ce ƴar
jarida ta farko da ta fara zuwa wurin, amma ki ka ƙi"
Ta lalubo lambar Nabila ta kirata, ta gaya mata abun da ya
faru. Nabila ta ce "Amma baki da wayo sumy, ke yanzu sai ki tura mata,
saboda ba ki da zuciya?"
"To yaya zan yi mata?"
"To amma kin san ko kin tura mata, sunanta za ta faɗa a
mai rahoton ko wanda ya karanta ba ke ba ko?"
Sumayya ta ɗan yi shiru ta ce "Kuma fa haka ne"
"To tun wuri ki ce mata kin goge kawai, gobe ba za ta
ƙara yi miki wulaƙanci ba".
Sunayya ta ce "Haka za ayi, na gode sosai" cikin
hanzari ta kira Lawisa, ta sanar mata da cewa ba ta ga recordings ɗin ba.
Aikuwa ta hau ta da bala'i, Sumayya ta danna recording tana
dariya ƙasa-ƙasa da niyyar ta turawa Nabila.
Bayan sun gama wayar, ta turawa Nabila, suka din ga dariya,
Nabila na ƙara bata ƙwarin gwiwar, kar ta sake ta ɗauki raini ko wulaƙanci daga
wurin lawisa.
Ta kuma cigaba da lallaɓa sumayya, a kan lallai ta koma
asibiti, ta sake tattaunawa da mutumin nan, ko iya sunan mai laifin ta samo.
Barrister Habib ne ya shiga office ɗin MD, ya zauna suka
gaisa, cikin takaici Habib ya fara magana, "Barrister, ni fa na gaji da
iskanci yarinyar nan, idan a team ɗi na za ta zauna, ta zauna, kuma dole ta yi
biyayya ga abun da na sakata, idan wurin Bashir za ta koma, ta koma na gaji da
iskanci da rashin mutuncin da take aikatawa, ba ta san aiki ba ko kaɗan"
MD ya ce "Calm down Habib, na sani wallahi, na san ku
na haƙuri da ita, wallahi nima nauyin mahaifinta nake ji ne, abun da yayi mini
a rayuwa idan na kore ta ban yi wa kaina adalci ba, shi ma yana yawan bani
haƙuri a kanta, marainiya ce kuma ba ta da cikakkiyar lafiya."
"Mu ma duk marayun ne ai, waye yake iskancin da take
yi? Ta zo lokacin da ta ga dama ta tafi lokacin da ta so, she's not serious at
all"
"Na sani, kuma nima ina gani, ka rabu da ita, duk wani
abu da za ku yi ku daina sakata a ciki, ƙyaleta da bashir ɗin, shi ne daidai da
ita, ku yi haƙuri dan Allah" MD ya din ga lallaɓa Habib, dan ba zai so
rasa gogaggen lawyer kamar Habib a law firm ɗin sa ba, a kan Nabila da ba aikin
ne a gabanta ba.
Yau weekends ne, gaba ɗaya iyalan major na babbn falo, kowa
ya ja nasa wuri yana karyawa, Nabila ce kawai babu a wurin.
Tun yana jurewa ya kasa, yayi gyaran murya ya ce "Ina
arfa ne?"
Anty ta ce "Bacci take yi"
Ya kalli walida ya ce "Tasota, ta fito ta karya, sai an
cinye an bar ta, ta cikawa mutane kunne da kuka"
Kusan mintuna goma da taso ta, sannan ta fito, kayan bacci
ne a jikinta, dogon wando da rigarsa har gwiwa, kanta babu ɗan kwali.
Nasir ya tsura mata ido, ko ƙiftawa ba ya yi.
Abba ya ce "Ina kallabinki? Ki ka fito da wannan gashin
ba kyan gani, kamar totuwar masara?"
Ta saka hular hannunta ta ce "Haba Abba, dan daga bacci
na tashi ne fa"
"Tafi can ƙazama, kullum kai babu kitso, ba za a rasa
kwarkwata a wannan gashin ba" dariya aka hau yi mata.
Ko a jikinta, ta zauna kusa da Abba, ta kalli Nasir ta ce
"DSP, yaushe ka dawo ba labari, ya hanya?"
Ya jinjina kai ya ce "Alhamdilillah"
Major da kansa, ya taya Nabila haɗa shayi, ga soyayyen
dankali, ga bredin ta, amma tana buɗe bredin ta ce ba za ta ci ba, kwantai ne.
Major ya miƙa mata nasa ya ce "Duba zaki iya cin
wannan? Dankali kawai ba zai riƙe miki ciki ba" ta duba buredin Abban ta
ce "Eh wannan sabo ne, Abba ka ƙara mini ƙwan, ni ba na son dankalin
ma"
Ya ce "To shikenan, ɗauki nawa da ma ni yanzu ƙwai bai
dace da ni ba, a shekaruna"
Idan da sabo, sun saba da ganin irin wannan fifikon da major
yake nunawa, duk da mutum ne mai ƙaunar yaransa sosai da sosai, amma son da
yake yi wa Nabila na musamman ne, amma fa hakan ba ya hana idan suka yi laifi,
ya hukunta su kamar ba ƴaƴan cikin sa ba.
Anty ta ce "Arfa ba zaki bari Major yayi ƙiba ba, kalli
yadda ki ke tara mazaunai, saboda ci"
Yayi murmushi ya ce "Tafi kowa girma a gidan nan"
Nabila ta ce "Abba, Allah ya ƙara arziki, ka yi ta
sayowa mu na ci"
"Amin arfan Abba"
Nasir ma ya juye mata nasa ƙwan, ta tattare tana dariya, dan
ta na son ƙwai sosai.
Mama kuwa kamar za ta yi bindiga, saboda baƙin ciki.
Bayan an kammala cin abinci, su walida ne suka kwashe
kwanukan da aka ci, Nabila kuma ta hau labartawa Nasir, abun da ya faru da
sumayya da ta je Asibiti.
Fafur Nasir ya ce ƙarya take yi.
Ta haɗe rai ta ce "Yaya, wai meyasa a duniya jami'an
tsaro ba kwa yadda kun yi laifi, ko wani ne daga cikinku yayi, sai kun ƙaryata,
kun kare mutum"
"Wa ya gaya miki hukuma tana laifi?"
"Ba mutane ne hukunar ba? Ai mutane na laifi, kuma
hukuma ma suna yi, wallahi da gaske nake, ka bincika ka ji kuma, koma na kira
maka sumayyan"
Ya ce "A'a ai ƙarya ki ke yi, ni zaki zauna kawai dan
ki ƙure"
Duk yadda ta so, ta fahimtar da shi, amma ya ƙi fafur.
Abba dai kallonsu kawai yake yi yana dariya, ganin ba zai
yarda ba, ya sanya ta ƙyale shi, ta koma wurin Abba.
"Abbana" tayi maganar tana ɗan murmushi.
Abba ya ce "Kuɗi zaki tambaya kenan?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a Abba, abu zan tambaye
ka"
"Ina jin ki"
"Abba dama, wata amarya ce, suka kira ni a waya, zan je
gida na yi musu make up, ita da ƙannenta na biki, za su biyani, VIP ne har
gida"
Haɗe rai yayi sosai sannan ya ce "Me na gaya miki a kan
wannan sheɗancin? Kin san na hana ki sabgar banzar nan, ban da kalen sheɗanu
jikinku, me wannan shashancin zai amafana miki, na fuskanci kin fi fifita
wannan kwalliyar a kan aikinki, to babu in da za ki je".
"Dan Allah Abba, wallahi zan samu kuɗi fiye da
salaryna, dan Allah"
"Ba in da zaki, tun da babu abun da ki ka rasa a gidan
ubanki, ba matar da zaki bi gida ki na shafawa hoda, idan ta matsu tayi da
kanta mana, banda shashanci ace mace ta zauna sai an bita gida shafa mata hoda
da gazar"
"Abba!"
"Shut up" yayi mata tsawa, hakan ya tilasata mata
yin shiru.
Walida kuwa faɗan Abban dariya ya bata, wai idan sun matsu
su yi da kansu, ba wadda za aje gida shafawa hoda.
Nabila ta din ga jin ko a ɓoye sai ta je, tana son sana'arta
ta kwalliya, Abba kuma ba ya so, wai shashanci ne da fatan aljanu, ita kanta
idan tayi a fuskarta wasu lokutan, ya din ga faɗa kenan.
Akwai ranar da za ta je biki, ta yi kwalliya ta saka
eyelashes, ya kirata dan ya ga meya samu idonta, gashin idonta yayi tsawo haka,
tun da ta ce masa sawa tayi, ba ta ankara ba, ya saka hannu, ya fige shi sai da
ya haɗa da gashin idonta, ya ce ya kuma ganinta da shi sai ya zaneta.
Har a gaban saurayi, ya taɓa korata gida, wai ta je ta wanke
fuskarta, ba za ta cuci ɗan mutane ba, duk ta damalmala fuska da hauka, ta zama
kamar wata bebin roba.
Ta rasa meyasa Abba yake adawa da sana'ar nan tata.
Nabila tun a weekend, take cigaba da zuzutawa Sumayya trial ɗin
da za su je, kotu ranar laraba, farincikin ta ya kasa ɓoyuwa, wanda hakan ya
samo asali ne, da yadda ta ga Barrister Habib ya ƙyale ta, ta koma team ɗin
Bashir, kuma ta samu labarin barrister Naja'atu ma tana da shari'a ranar a
kotun, dan haka za ta haɗu da ita.
Nabila uniform ɗin ta, tamkar su yi magana, saboda ɗaukar
guga, ita kanta a bar kallo ce a cikin kayan, ba fara ce tas ba, amma haskenta
mai kyau ne da ɗaukar hankali, domin kuwa jikinta kamar ƙwai, dan tana kashewa
Jikinta kuɗi ba kaɗan ba, ba ta da wata damuwa, ba abun da take yi da kuɗi, ban
da sayen kayan gyaran jiki, ta samu kuɗi a aikinta, major ya bata, Nasir ma ya
bata, ga wanda take tatsar samari, ga ƴan sana'ointa, dan haka kuɗi sam ba
matsalarta bane ba.
Barrister Naja'atu Bunkure matashiyar lawyer, mai dakawa
maza gumba a hannu, karo da ita sai lawyern da yake jin kansa ya isa, dan abu
ne mawuyaci case ya shiga hannunta ba ta yi wining ba. Ana yawan sanar da
ayyukan alkhairin ta, a gidajen rediyo na taimako da tsayawa marasa galihu a
kan shario'i daban-daban.
Bakin Nabila ya ƙi rufuwa, ganin yau ga ta ga Barrister Naja
bunkure, wata ƴar gayu da ita, yadda ta gabatarwa da kotu kanta kawai, ya isa
ka tabattar da ta san me take yi, ga yaren nasara a harshenta wato turanci.
Gaba ɗaya hankalin Nabila ba ya kan shari'ar, yana kan
bunkure, da yadda take magana.
Murna kamar nabila ta taka rawa, yau ga ta ga mentor ɗin ta.
Sumayya ta samu damar editing news yau da kanta, kasancewar
MD yana ta mitar, ta daina ware kanta, ta din ga shiga ana aiki da ita a haka
za ta goge.
Kiran Nabila ta gani, dan haka ta ɗaga ta ce "Kiran me
ki ke yi mini ina aiki?"
Sama-sama ta din ga jiyo numfashin Nabila, muryarta
ƙasa-ƙasa ta ce "Kin tashi daga aiki ne?"
"A'a menene meyafaru?"
A galabaice ta ce "Na dawo chamber ne, na ɗauki kayana,
ina hanyar komawa gida, ji nake kamar ciwona ne zai tashi, ina titi dan Allah
Sumy ki zo"
"Subhanallah, gani nan zuwa amma babu wani a wurin da
zai kai ki gida?"
"Ni ba na son damun kowa, dan Allah besty ki zo, kar na
mutu a titi"
Ganin ta gama abun da take yi, ya sanya a gurguje ta ɗauki
jakarta, ta fita, ba ta tsaya ko ina ba, sai hanyar wurin aikin su Nabila, tana
ta rarraba ido a titi tana kiran wayarta.
A kan wani tudu ta hango Nabila, idanunta sun yi jawur, da
alama tayi kuka sosai da sosai.
Ta ce "Mai napep, bari na ɗauketa ka kaimu gadon ƙaya
dan Allah, ba ta da lafiya"
Ya ce "To shikenan" ta sauka ta rungumo Nabila, ta
taimaka mata, ta shiga napep ɗin, sai dai babu baki, sai numfashi take
sama-sama.
"Arfa, meyafaru an ɓata miki rai ne?" Ta girgiza
kai alamar a'a.
"To menene? Haka kurum ciwon ya tashi" buɗe baki
ta yi, da nufin yi wa sumayya masifar ta ƙyaleta, amma ta ji numfashin ta, zai
gudu ya bar huhunta, hakan ya sakata yin shiru.
Can kuma a hankali ta ce "Sumayya mu je gidanku, wurin
umma"
Sumayya ta jinjina mata kai, haka aka yi.
umman sumayya na ganinsu hankalinta ya tashi, Nabila ta samu
wuri ta kwanta.
Umma ta ce "Sumayya, me aka yi mata ne?"
"Wallahi umma ban sani ba, kawai kirana ta yi a waya,
ciwonta ya tashi"
Cikin kuka Nabila ta ce "Umma dan Allah ki yi mini
addu'a, ki ƙyale sumayya"
Umma ta ce "To shikenan" ta din ga tofa mata
addu'a, har aka samu ta yi bacci.
Bayan awa ɗaya da rabi, ta farka, har ta samu ta ci abinci
ta yi salla, umma ta din ga tambayarta, ko wani abun aka yi mata, amma ta ce
a'a.
Ganin ta ware, ya sanya umman basu wuri, Sumayya ta sake
kallonta ta ce "Ke, wallahi wani abu aka yi miki, yanayinki ya nuna mini,
kin ga idonki kuwa, ki gaya mini menene?"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Sumy, ashe haka ake ji, idan
aka wulaƙanta mutum mussman a gaban jama'a, a dizaga ka"
"Menene? Waye ya wulaƙanta ki?"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kin san Naja'atu
Bunkure?"
"Ba dole na santa ba, a wurinki na santa ai"
"Ashe matar nan tsinanniya ce"
Da sauri sumayya ta ce "A'uzubillahi, me yayi zafi,
mentor ɗin taki?"
Nabila ta ce "Zilwajahiani ce, abun da muke ji a kanta
daban, yadda take daban. Yau muka haɗu a kotu, kin san ina cikin team ɗin
barrister Bashir, tare muka je court yau.
Bayan an fito, jiki na tsuma na bita, ƴan jarida sun
baibayeta, na yi mata magana kin ga wulaƙantaccen kallon da tayi mini? Ba shi
ne ya dame ni ba, duk da uniform ne a jikina, na cire girman kai na gabatar
mata da kaina, a matsayin lawyer mai koyi da ita, amma still ban isheta kallon
kirki ba. Abunka da zuciya da abun da take so, na matsa tare da miƙa mata
wayata, a kan ta bani lambarta, sai ce mini ta yi ba za ta bayar ba, kar na
isheta da kira. Na ce mata bakomai, a matsayina na mai koyi da ita, kuma mai
ƙaunarta, dan Allah ko mintuna uku ta bani, na daɗe ina burin haɗuwa da ita.
Ina son ta bani shawara a matsayina na lawyer mai tasowa, kuma ta bani tips da
zan bi, na zama kamarta a rayuwa, dan ina son ta da irin ayyukan da take yi. Ta
ƙare mini kallon baki isa ba, sannan ta ce 'Ki zama kamar ni kuma? Taka
matsayin da na taka? Never! Don't even give a try, ba zaki taɓa zama ba, and
leave my way please, ina da abun yi"
Haka fa ta ce mini, a gaban mutane da masu yi mini dariya,
da masu yi mini Allah ya ƙara wai neman suna da gidin zama ne ya janyo mini,
wasu kuma su ka bani haƙuri wai haka halinta yake. Sumayya yau na tozarta, an
wulaƙanta ni, duk yadda nake ganin ina da class, soyayya ta rufe mini ido,
saboda ina ƙaunar matar nan fisabilillahi, wallahi da ƙyar na ƙarasa chamber,
nan da nan na fara jiri, numfashina ya fara sama, kin ga dariyar da aka yi
mini, wallahi na muzanta fiye da tunaninki"
Sumayya ta ce "Nabila jikina yayi sanyi, ban taɓa zaton
matar nan za ta aikata haka ba, wai meyasa mu mata, galibin mu ƴan baƙin ciki
ne? Wato ba zaki zama kamarta ba, sai ka ce wayo da dabararta ne suka ba ta
matsayin da take kai".
"Wallahi sumayya, ko zan rasa raina, ko da kasada, sai
na tabattar da na yi suna nima, sai dai idan Allah ya ƙaddara na mutu. Amma ina
roƙon Allah, in sha Allah tana raye, sai na ɗaukaka fiye da tunaninta, kuma
bibiyarta zan din ga yi, da bibiyar duk wani abu da ya shafe ta, sai na rama
abun da ta yi mini. I will do a background check on her"
"Ke fa baki iya ɗaukar abubuwa da sauƙi ba, ki ƙyaleta
mana kanta ta yi wa, ni na ce me?, abun da nima ake yi mini, ni kusan kullum
ake yi mini, ke yau ne kawai, kuma arfa matsayi
na duniya ba na kiyama ba"
Nabila ta girgiza kai ta ce "Wannan ke ki ka ga zaki
iya, kuma ƙaramar alhaki ce ta wurin aikinku, wannan kuwa dizgin da ta yi mini,
in sha Allah rabbi, sai na rama shi, dole na ajiye shirme, na mayar da hankali
a kan aikina, ko dan fansar nan, kut wallahi matar nan ta gama cuta ta, kuma ba
zan huce ba har sai na rama wallahi. Rakani titi in tafi gida" ta ƙarasa
maganar tana ƙoƙarin tashi tsaye.
Sumayya ta danƙota ta ce "Nabila ki din ga sanyawa
zuciyarki salama mana, kin fiye zafin rai, ki bi komai a hankali, kalli yadda
ki ka kusa kashe kanki a banza. Idan Allah ya yi nufin ɗaukakaki fiye da ita,
ita ɗin banza ta hana, dan Allah ki manta da ita, ki cigaba da rayuwarki".
Ta kalli sumayya cikin takaici ta ce "Lallai ma
sumayya, dan ba ki ga abun da ta yi mini ba, a gaban mutane har da masu yi mini
dariya. Ni gaba ɗaya ma ji na yi ban yarda da ita ba, abun da ake faɗa a kanta
daban, abun da na gani yau a kanta daban, akwai wani abu a ƙasa, and i will run
a background check on her, for the first place ma, wacece ita? Idan ta kama har
bunkuren zan je mahaifarta, meyasa abun da ake faɗa a kanta daban, ita kuma
halinta daban".
Sumayya ta ce "Na shiga uku, Nabila" kafin ta yi
magana, Nabila ta yi waje, ta tarar da umman sumayya na salla, ta ce Umma na
tafi, ta fice daga gidan.
Sosai abun da ya faru ya tsayewa Nabila,da ta tuno abun sai
wani irin takaici yakamata.
Yau ba kowa ya san ma ta koma gida ba, dan yau babu surutu
da hayaniya.
Abu kamar wasa, har dare Nabila ta kasa walwala, ko fitowa
daga ɗaki taƙi yi, gani take kowa yana kallonta zai gane an dizgata yau, duk
iyayin na ta da jan ajin.
Nabila irin mutanen nan ce masu saka abu a ran su, dan haka
ko ta yi niyyar manta abun da ya faru, sai ta kasa.
Ta ɗaukko wayarta, ta kunna data, ta tarar da messages ɗin
sumayya, ta na ta yi mata faɗan ta yi haƙuri ta manta da abun da ya faru.
Nabila ta yi mata reply da "You are not serious, ki
saka ido ki yi kallo"
Social media ta hau, ta shiga searching ɗin sunan barrister
Naja'atu Bunkure, nan da nan sai ga hotunanta, da wasu daga cikin ayyukanta na
jin ƙai, sai dai ba ta samu wani cikakken bayani da take son samu a kanta ba.
Tsaki ta yi, bayan tuna yadda take mutuwar son matar nan a
baya, har hotonta take sakawa a dp ɗin ta, saboda yadda take ƙaunarta, amma
lokaci ɗaya a yanzu ji take yi, ba ta da wani maƙiyi idan ba ita ba.
Har sha biyu da rabi na dare, ba ta samu cikakken abun da
take son sani ba, sai ma zarge-zarge da suka din ga ɗarsuwa a ranta game da
matar.
Saukkowa ta yi daga kan gadonta, ta fice daga ɗakin, fita
tayi can babban falo, ta nufi kitchen ta samu abun da za ta ci, dan yunwa take
ji sosai.
Fridge ta buɗe, ta samu ruwa mai sanyin gaske, da coc ta
fito falo tana sha.
Hasken fitila ta hango a baranda, ba a kashe ƙwan wurin ba,
ga abba kullum sai yayi magana a kan rashin kashe kayan wuta, kafin a kwanta
bacci.
Wurin ta nufa, da niyyar ta kashe ƙwan, ta na zuwa ta leƙa,
ta hango nasir a kan kujera, yana ta danna system.
Ta window ta je ta zura hannu, tana taɓa masa kunne. Caraf!
Ya riƙe hannun ba tare da ya ɗago ba.
Tayi dariya ta ce "Shi ne ba ka tsorata ba"
"Me ki ke tunanin zai razana ɗan sanda?"
Ta ce "Ai dai ɗan sanda mutum ne, kuma na san ka ji
tsoro mazewa ka yi"
Yayi murmushi ya ce "Tsoro sai lauyoyi"
Ta buɗe ƙofa ta fita ta zagaya in da yake ta ja kujera ta
zauna sannan ta ce "Duk tsoron lauya bai kai ɗan sanda ba"
Ya ɗago ya kalleta, sanye cikin kayan bacci pink, masu bargo
kanta ko ɗan kwali babu, tayi parking ɗin gashinta"
Murmusawa yayi ya ce "Ke kin san babu tsoro ga wanda
yake riƙe makami, yayi yaƙi da ɓarna"
"Hmm, yi dai a hankali, dan harshe ya fi makami dafi,
kar lauyoyi su baka mamaki watarana"
"Ina aiki kin zo zaki dame ni, ina nawa aikin, ina
kallabinki?"
"Yana ɗaki" tayi maganar tana lashe murfin jarkar
lemon hannunta.
"Kalli abun da ki ke yi kamar ƴar ƙauye, sai an yi
magana ki fara ke barrister ce, ke degree holder " yayi maganar yana mayar
da hankali a kan system.
Ta numfasa ta ce "Wai aikin me ka ke yi ne?"
"Wani aiki ne mai wahala, wanda nasara a kansa, na iya
sawa na samu cigaba a aikina".
Nabila ta ce "Haba dai, to Allah ya taimaka"
"Amin" ya amsa ba tare da ya kalleta ba.
Shiri ya wanzu na wani ɗan lokaci, sannan ta ce
"DSP"
"Na'am barrister"
"Sannu da aiki" ya ɗago ya kalleta ya ce "Kin
isheni fa, za ki tashi ki bar wurin nan"
"Yi haƙuri, na daina magana"
Ya cigaba da aikinsa, ta na shan lemonta, tana jin yadda
iska ke kaɗata.
Duk abun nan, Abba ta ɗakinsa ya na hango su, sai dai ba ya
jin me suke cewa.
Can ta sake cewa "DSP"
A hasale ya ce "Ke! Meye ne? Tashi ki je ki kwanta dare
yayi"
"Ni na kasa bacci, raina ne a ɓace".
"Ai dama kullum cikin ɓacin rai ki ke, tun da ke a
rayuwarki ta duniya, baki da haƙuri tashi ki bani wuri"
Ta marairaice ta ce "To ka tsaya ka ji me aka yi mini
mana, dan Allah kafin na tafi, ka gaya mini me zan yi, wanda zai saka na yi
suna, kowa ya sanni" tayi maganar very serious.
Cikin gatse ya ce "Ki nemo in da Aminu Viper yake, ki
taimaka mini na kama shi, kin ga sai ki yi suna, ni na samu cigaba a aiki"
Ta fuskance shi sosai ta ce "Waye shi, a ina yake?
Kamar na taɓa jin sunansa"
Ya kalleta ya ce "Shi nake ta aiki a kansa, galibin
aikin ta'addancin da ƴan daba suke yi, a wasu shiyyoyin da saka hannunsa,
yaransa ne. An ce lallai na kamo shi, tun da yankin da ake ɓarnar ƙarƙashin
kulawata yake akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga prison"
"Dan Allah idan na nemo maka shi, zan yi suna, kowa ya
sanni?"
Kallon baki da hankali yayi mata, ya cigaba da abun da yake
yi.
"Ka ga riba biyu kenan, na yi suna, kuma ka samu cigaba
a wurin aiki, yes! Amma na ji ka ce akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga
prison how? Kun tabattar da hakan ko kuwa? Ka bani hints mana, laifin me ya yi
a ka kai shi prison ɗin?".
Takalminsa ya ɗauka ya miƙe tsaye ya ce "Tashi ki bar
wurin nan, tashi maza"
Da haka ya koreta, ta tafi ɗakinsu. Sai dai da ga koma
ɗakinta, ta dinga sintiri a cikin ɗakin, sosai ta ji maganar Yaya Nasir ta
shiga ranta, ina ma hakan ta tabatta.
"In taimaka masa ya kama ɗan ta'adda, in nemo haƙiƙanin
dalilin barinsa daga gidan yari, idan guduwa yayi me ma'aikatan suke yi, idan
sakinsa aka yi laifin me yayi, aka sake shi duk da hatsarinsa, na bankaɗo
ainihin identity ɗin Naja'atu Bunkure, na gyara career ta, wai ma menene
dalilin da ya sa ban zama ƴar sanda ba?, na zama wata lauya yau ka kare mai
gaskiya gobe mara gaskiya.
Ta yi wani irin shu'umin murmushi ta ce "Accepted DSP
Nasir, zan nemo maka Aminu Viper, na bibiyi laifin da ya aikata, da yadda aka
yi ya bar prison.
Ayshercool.
08081012143
*ƘARFE A WUTA*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
BRIGHT PENS SECOND BATCH.
5
Wurin shiru, ba ka jin motsin komai, hantsi yayi, yana zaune
a kan wani dutse, yana jin yadda ɗumin ranar ke ratsa shi, dan ba ta riga ta yi
zafi ba, hannunsa ɗaya ɗauke da taba sigari, yana ta zuƙa yana busawa, idonsa
yayi jawur.
"Viper" matashin ya kira sunansa, yana ta
sauke haki.
"Ina jinka" yayi maganar ba tare da waiwayawa, ya
kalli matashin ba.
"An kama ɗan mama da kayanmu fa jiya da daddare, a
chamber yamma da gari, yana tsaka da raba kayan ga mutane, kuma wadda aka kama
da yawa"
Ya saka yatsansa ya ɗan daki jikin sigarin, tokar jiki ta
zube, ya ja numfashi ya ce "Wace hukumar ce?"
"Masu ƙwaya ne"
Ya miƙe tsaye ya ce "Shikenan, kar ka damu, ku bar shi
a hannunsu"
Ya waro ido ya ce "A bar shi, Ka manta a halin da ake
ciki? Idan wani abu ya faru fa?"
Cikin takunsa na ƙaƙƙarfan namiji, ya ƙarasa gaban matashin,
ya riƙe kwalarsa a hankali sannan ya ce "Ba na butulci walid, ɗan mama ni
yake yi wa aiki, dole na fito da shi. Ni ba zan kamu ba, da zan kamu da basu
bari na fito ba. Kuma ko a yanzu suna sane suka bar guzuma, suke harbin
karsana. Ni na shirya a kama shi, sannan ina son ku je dabar Madaki, ko wurin
da yaransa suke, ku tayar da hayaniya, ku zubar da jini, kar ku raga musu ko kaɗan,
ko da kuwa hakan yana nufin jami'an tsaro su kama ku"
Yayi shiru yana kallon viper.
Ya shafi sumar walid, da tayi cibiri-cibiri ya ce "Ya
ka ke kallona kamar kana tantama a kaina?"
Ya risuna ya ce "Tuba nake mai gida, duk abun da ka ce
dole ayi shi, umarninka muke yi wa biyayya"
"Good. Idan aka kama ku, ko da mutum ɗaya ne daga
cikinku, ku ambaci sunana, ku ce ni ku ke yi wa aiki, ni ne na saka ku. Ina
sake jaddada maka, kar ku ragawa kowa a cikin su. Amma ku kiyaye ƙa'idar
aikina. Babu kisan kai, babu taɓa wanda babu ruwansa mata ko kuma ƙanan
yara"
Walid ya ce "An gama maigida"
" Ɓace " ya furta a hankali.
Yau Nabila ko karyawa ba ta tsaya yi ba, haka zalika ko
sumayya ba ta jira ba, ta tafi aiki.
Daga office ɗin ta, tana hangen harabar chamber, ta ga
isowar motar Barrister Bashir. Bayan mintuna talatin ta bishi office ɗin sa,
suka gaisa ya dube ta ya ce "Ƴar ƙwalisa ya jiki?"
Ta ce "Jiki kuma, ba ni da lafiya ne?"
Ya ce "Ranar da muka dawo daga court, kina ta tari har
ki ka tafi gida, ko kin manta?"
Ta ce "A'a na tuna, na ji sauƙi ai"
"Wai meyafaru ne a kotun, bayan na je na ga abokina, da
na dawo na tarar da ke gaba ɗaya ranki a ɓace, na tambayeki kin ce ba
komai"
Nabila ta ce "Da ma fa dan bana jin daɗi ne, ai ni ba
zan manta da ranar ba, na ga masoyiyata kuma mudubina"
Barrister ya ce "Wa kenan?"
"Barrister Naja'atu, ina son matar nan sosai "
Yayi murmushi ya ce "Bunkure ki ke nufi?, mace mai
hatsari kenan"
Ta waro ido ta ce "Hatsari kamar yaya?"
"No, kin san ba ta da wasa da aiki, duk shari'ar da ta
saka gaba, sai ta ga bayanta, ke kuma gashi ba haka ki ke ba, ba kya mayar da
hankali a kan aikin".
"Ai in gaya maka ganinta kawai da na yi, na ji wata
irin ƙwarin gwiwa, na ji sonake na nutsu na mayar da hankali sosai a kan
aikina. Sonake na bi footsteps ɗin ta, nima na yi nasara kamar ita. Amma me ka
sani a kanta da zaka iya gaya mini?"
Yayi murmushi ya ce "Nothing much, ki tambayi barrister
Habib, ya santa sosai " sai da ta ji wani dummm! Yadda suke faɗa da
barrister Habib, amma hausawa su ka ce ranar biyan buƙata, rai ba a bakin komai
yake ba, dan haka ta ce "To shikenan, na gode sosai ayi aiki lafiya".
Ta juya ta fita tana nanata "Dangerous woman, zamu gani ai".
Ba ta zame ko ina ba, sai ofishin barrister Habib, ta tarar
da shi da wasu client suna tattaunawa, ya ɗago ya kalleta ya ce
"Meye?" A ɗan hasale dan a ƙule yake da ita.
Ba tare da ta yi fushi ba, ta yi masa murmushi sannan ta ce
"Wurinka na zo, amma bari na jira ka gama".
"Idan na gama ina da abun yi" ya faɗa a taƙaice.
"Dan Allah yaya habib ko mintuna goma ne"
"Na gaya miki ina da abun yi, fita ki bani wuri"
tsayawa ta yi tana kallonsa, tare da tura baki, babu alamar ma za ta fita ɗin.
"Ba magana nake yi ba?"
A shagwaɓe ta ce "Dan Allah"
Ɗaya daga client ɗin ya ce "Barrister a taimaka mana,
kar ta yi kuka"
Ya ce "Ta daɗe ba ta yi ba, ba zaki fita ba?"
Nabila ta ce "Ya ka ke korata kamar wata kare ne? Na
san ina yin laifi, ka yi haƙuri na shiryu ai"
Tsaki yayi, ya cigaba da rubuce-rubuce.
Ta tura baki ta fice, a zuciyarta ta ce "Ai ko da me ka
ke yawo, sai na samu abun da nake son ji a wurinka"
Ta je ta samu MD, suka gaisa, sannan ta ce "MD, ka ga
Barrister Habib ko, na je na bashi haƙuri, amma ya kore ni a gaban
mutane".
Ya yi murmushi ya gyara gilashin fuskarsa ya ce "Anya
ba wani laifin ki ka yi masa ba?"
"Ba laifi na yi masa ba, haƙuri na je ba shi fa, amma
ya kore ni a gaban mutane"
MD yayi murmushi ya ce "Ai ke ɗin ce ba kya ji, ya so
ya koya miki aiki yadda yakamata, mussman yadda ki ke da faran-faran da mutane,
amma ki ka ƙi ba kya so, idan ya saka ki aiki ki ƙi yi, dole ku din ga faɗa
ai"
Nabila ta ce "Na daina fa, so nake na zama ƙwararriya a
kan aikina, ko dan farincikin Abbana, ku yi haƙuri"
Ya jinjina kai ya ce "Shikenan, Allah ya sa, ki je ki
bashi haƙuri"
Ya ce "Bayan ya kore ni, yauwwa sir dan Allah ka san
barrister Naja'atu Bunkure?"
Ya jinjina kai ya ce "Yes, she's famous a tsakanin
lauyoyi, har ma da jama'ar gari ma, ai sananniya ce sosai"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Wow ina yin matar nan
sosai da sosai, yadda take gudanar da aikinta, ya ƙara jan hankalina a kan
aiki, ai mun ganta kotu a lokacin da mu ka je kotu last, ni da barrister
Bashir, ƴar gayu da ita"
"Nabila, ke dai ki na son harkar gayu, amma ba gayun
ba, ki mayar da hankali sosai a kan aiki, ki yi ƙoƙari ki kamo ta, ko ma ki fi
ta".
"In sha Allah, na yi maka wannan alƙawarin but i need
your support"
Ya murmusa ya ce "Kin samu, ɗari bisa ɗari, ƴar gidan
major"
"Yauwwa to ka bawa barrister Habib haƙuri, zan koma
team ɗin sa dan Allah kar ya sake korata, mussaman a gaban mutane"
"To za a bashi in sha Allah"
Ta miƙe tsaye tare da faɗin "Godiya nake" ta fice
ta bar office ɗin cikin nishaɗi.
"Bunkure na ki zai zo mini da sauƙi, saura kuma Aminu
Viper"
***
Major ya ɗan tsurawa Uwargidan sa mama da ta tattare
kwanukan da ya kammala cin abinci.
Ta ɗago su ka haɗa ido, ta ce "Ya dai?"
"Nasir"
"Me yayi?"
"Ki ja masa kunne, hawainiyarsa ta kiyayi ramata, na daɗe
da gane in da ya dosa, amma tun da kin daƙile abun, to ya ƙara nesanta kansa da
ƴa ta, kar ya kuskura in ji ko in ga wani abu da zai sosa zuciyata, kuma kar ya
kuskura ya saka ta fara son shi, tun da ba ki amince ba, balle a jefa ta cikin
yanayi mara daɗi".
Cikin rashin fahimta ta ce "Amma major, wani abun ya yi
ne?"
"Bai yi komai ba,gugar zana dai nake yi, idan ma yana
shirin yin, to ya shiga hankalinsa" cikin mamaki take bin sa da kallo,
tabbas idan aka ji major yana magana da kurman baƙi, akwai abun da ya
gani, kuma ko me za ayi, ba zai fito yayi bayanin abun da yake nufi ɗin ba.
****
Kamar ɓarawo haka yake zagaye tilon matsakaicin gidan, wanda
can nesa da gidan, kamfanunnunka ne, sai gonaki.
Cikin ƙasaita yake tafiyar, yana yi yana duba ƙaramar
wayarsa mai madannai.
Kamar korarre, haka wani matashi ya ƙaraso in da yake tsaye.
Ya ɗaga kai ya kalle shi ya ce "Menene labari, yaya aka
yi ka fito?" Cak matashin ya tsaya, ya ce "Wai dama ba kai ne ka fito
da ni ba?"
"Me zan tambaya idan na san komai?" Yayi maganar a
ɗan hasale.
"Wallahi master....
Cikin wata irin razananiyar tsawa ya ce "Kar ka sake
kirana da wannan sunan"
Cikin tsuma ya ce "Tuba nake oga, suɓutar baki ce, ban
san waye ya fito da ni ba, kawai cewa aka yi na tafi"
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Kuma ka tabattar da ka
gaya musu sunana, cewar ni ne me kayan?"
"Wallahi na faɗa musu"
Ya jinjina kai ya ce "Shikenan"
Ya ɗaga rigarsa ya zaro wata sharɓeɓiyar wuƙa, ya danƙa masa
ya ce "Maza ka fasa cikin gari, unguwarmu, su walid sun tafi yaran Madaki
zaku farwa babu sani babu sabo, idan an yi ram da wani daga cikin ku, ku ambaci
sunana, ku ce ni ne jagoran aika-aikar, amma ku kiyaye ƙa'idar aikina"
Ɗan mama ya risuna ya ce "Umarninka ne abun biyayya a
gare ni, an gama za ayi yadda ka ce" ya soke wuƙar ya juya, ya tafi da
sauri yana haɗa hanya..
Cikin ƙaramin gidan ya shiga, ya nufi ɗakin kwanansa, ya
kunna fitilar wayarsa, ya kunna ƙwan solar, haske ya gauraye ɗakin.
Ya saka mukulli ya rufe ɗakin, sannan ya zauna yayi shiru
tsawon mintuna, daga bisani kuma ya ɗaukko wiwi ya naɗa ta, ya kunna ya fara
zuƙa.
Madadin ya ji ƙunci, da zafin da zuciyarsa ke yi masa, yana
raguwa, sai ma wani irin baƙin ciki da matsananciyar damuwa da suka kawo masa
ziyara.
Wani abu mai tsananin ɗaci yake ƙoƙarin haɗiyewa, amma abu
ya gagara.
Ya ɗaga wiwin yana kallonta cike da baƙin ciki da takaici,
yayi watsi da ita yana sauke numfashi.
Kamar mahaukaci ya zabura ya buɗe wata akwati, ya ɗaukko
kwalaben allura, ya farfasa ya haɗa, ya yi wa kansa, ya nemi wuri ya kwanta.
Bai fi mintuna goma ba, kansa ya fara barazanar tsagewa, ya
fara kakari yana rirriƙe kansa.
Duk yadda ya kai ga ƙara yawan doses ɗin abun da yake sha,
ba sa ɗaukarsa, su mantar da shi damuwarsa, sai dai su wahalar da shi, shi a
yanzu babban fatansa ya samu abun da zai yi amfani da shi, da zai goge masa
komai na ƙwaƙwalwarsa ya yi bacci mai nisan gaske.
***
Nabila ce tsaye a kitchen tana ta ciye-ciye, tana yi wa
magajiya surutu.
Baba magajiya ta ce "Dan Allah Arfa ki yi mini shiru na
ji radiyona, wai ni ya aka yi, ki ka tashi da sassafen nan ma"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Baba magajiya kin gane mai
muryar nan kuwa?"
Baba magajiya ta yi dariya ta ce "Sumayya ce mana"
"Ashe za ki gane ta"
"Ka ji ƴa, yau na sanku da ke da ita, da zan kasa gane
muryarta"
"Ai in gaya miki baba magajiya, wata mata ce ta takura
wa aminiyata, a wurin aiki, da iskanci kala-kala ga sumayya da son aiki, amma
matar nan tayi ta taɗiyeta, ni kuwa na ce ta daina saurara mata wallahi,shi ne
ma fa ake ba ta karanta rahotanni wasu lokutan, da experience ɗin ta da komai,
wata sokuwa ta cuceta, ta hana ta cigaba"
Baba magajiya ta ce "Ohh Arfa, ai mahaƙurci mawadaci,
yawan faɗa ba shi da amfani"
Nabila ta ce "A'a fa baba magajiya, ni ma ba faɗa ne da
ni ba, wulaƙanci ne ba na so, duk wanda ya wulaƙanta ni, sai mun yi fito na
fito da shi".
Baba magajiya ta ce "A dai din ga haƙuri, tun da.... ba
ta gama magana ba, Nabila ta yi wani irin tsalle ta ɗauki radiyon, tayi waje da
gudu.
Sashin mama ta faɗa, dan ta san tun da Nasir yana gari,
lallai zai shiga sashen ta ya karya kafin ya fita.
Aikuwa a sashen ta tarar da shi, yana karyawa, su na hira da
mama, da kuma sauda.
Ƙaro volume ɗin radiyon tayi, ta na yi masa nuni da ya
saurara.
Rahoto ne a kan rikicin faɗan daba, da ya gudana a cikin ɗaya
daga manyan unguwannin kano, wanda tun goma na dare ake rikicin, har ƙarfe sha
biyu ana rigimar, ƴan sandan sun yi nasarar cafke wasu daga cikin matasan, in
da ɗaya daga wanda aka kama, ya ce Aminu Viper ne ya aka su
Sai da suka kammala ji, Nabila cikin rawar jiki ta ce
"Yaya Nasir, ba wannan ne wanda ka ke nema ba?"
Ya jinjina mata kai ya ce "Shi ne"
"Ka yi sauri ka tashi, ka je division ɗin da aka tsare
ƴan daban, a baka su ka zurafafa bincike, gidan radiyon su sumayya ne, sai na
biya can na sake samo rahoto".
"Ke!" Mama ta daka mata tsawa, har sai da ta ɗan
razana.
"Tashi ki bani wuri, yaya ina magana da shi, ba sallama
ba gaisuwa babu neman izini, kawai ki zauna ki na surutun banza" Nabila ta
yi shiru ba ta ce komai ba.
Sauda ta ce "Dama mama yaushe za ta gaishe ki, tana abu
kamar mahaukaciya"
Ta kalle su, ta kalli Nasir da yake wurin, ta haɗiye wani
abu ta tashi, za ta fita.
Nasir ya riƙo hannun ta ya tashi ya tsaya, ya ce "Sorry
barrister, na gode sosai da wannan gudunmawa, zan je division ɗin, ki samo mini
bayani a wurin sumayyan".
Ya kalli mama ya ce "Haba mama, kin san tana gaishe ki,
tsananin zumuɗin ta kawo mini labari ne fa ya sa ta manta, thank you Arfa ki
shirya ki tafi aiki kar ki makara"
A ƙule mama ta ce "Wai kai har abada ba zaka yi hankali
ba, dan ubanka ya zauna yana cewa in ja maka kunne, a kan shishshigin da ka ke
yi mata, amma ina magana kana dizagani a gabanta" Nabila ta yi gaba ta
fice a fusace, dan idan ta cigaba da tsayuwa, za ta iya aikata abun da zai hana
kowa wuni cikin farin ciki.
Ya ce "Ni ɗin kuma mama?"
"Kai ɗin fa, ko ka shiga hankalinka, ko kuma duk abun
da ya biyo baya kai ka so".
Sam sai ya ji maganar kamar maman ce, ta shirya kayarta dan
ta saba, dan haka ya yi musu sallama ya fice.
A gurguje ta tsaya ta gaisa da Abba, ta fice cikin zumuɗi,
gidan radiyon su sumayya ta fara tsayawa.
Sumayya ta yi mamakin ganinta, ta ce "Hajiya lafiya ki
ka zo mana wurin aiki da sassafe? Talla ki ka kawo ko cigaya?"
"Ƙaniyarki na kawo" Nabila ta ba ta amsa.
Sumayya ta ce "Ai na san ke ungulu ce, ba kya jewar
banza, ya aka yi uwar makara"
Nabila ta ce "Yau da safe kan na fito, na ji baba
magajiya na jin program ɗin ku na labaran ƙarfe shida, bayan kin karanto
naki, na ji wani rahoto na faɗan ƴan daba, jiya a kano"
Sumayya ta ce "Eh meyafaru?"
"Kin je wurin ne?"
Sumayya ta zaro ido ta ce "In je in yi me?"
"Na ji an ce wai yaran Aminu Viper ne"
Sumayya ta ce "Eh to, ni ma haka na ji"
"Dan Allah ki tashi mu je asibiti, an ce an kama wasu,
wasu kuma da aka yi musu miyagun raunuka suna asibitin koyarwa na cikin
gari"
Sumayya ta ce "To wai ke duk menene haɗinki da
hakan?"
Kamar Nabila za ta yi kuka ta ce "Sumy ban gaya miki
ba? Yaya Nasir ne incharge ɗin bincike a kan mutumin nan, kusan kullum sai an
faɗi mugun aikinsa, ya tabattar mini da in dai na gano masa in da yake, ko na
taimakasa ya gano zan yi suna sosai"
Cikin matsanancin takaici Sumayya ta ce "Tashi ki tafi
ko na ɗura miki ashar, ƴar wahala, shi yaya Nasir ɗin ne ya gaya miki haka? Ƴar
sanda ce ke? Su ma ya suka ƙarke da su balle ke ki na mace, wallahi ba zan kai
kaina ga halaka ba"
"Sumy ki gane, this can all help our career ki zo mu je
mana"
"Wallahi ba zan shiga shirgin ƴan daba su kashe ni ba,
idan kin yi sunan uban me zai ƙara miki, za a binneki da shaharar ne idan kin
mutu?"
Cikin ƙoƙarin son fahimtar da sumayya ta ce "Ba za a
binne ni da shahara ba, amma atleast zan samu chances da zan iya fuskantar Naja
bunkure"
Wata uwar ashar sumayya ta yi wa Nabila, ta tashi ta ce
"Mahaukaciya, ai sai ki yi, ke da bunkuren ƴan wahala"
Nabila ta tashi a fusace, ta ɗauki jakarta ba tare da ta
sake cewa sumayya komai ba, ta tashi.
Sumayya ta girgiza kai ta ce "Arfa Allah ya taro ki ya
shirye ki, ya yaye miki baƙin taurin kai"
"Tun da kin ce ba zaki je ba, kar ki sake yi mini
magana, kuma na gode"
"Eh ba zani ba, haka kurum a kashe ni a banza, mutanen
da ba tsoron Allah ne da su ba, mutanen da suke shan ƙwaya tana gaya musu
gaibu, su ɓantarani biyu a banza ba da ni ba"
Nabila ta yi mata shiru ta fice.
Nabila ba ta yi tunanin komai ba, ta garzaya asibitin
koyarwa, na cikin gari.
Ba ta wani sha wahala ba, saboda tana zuwa, ta tarar jami'an
tsaro sun kewaye sashen emergency, ba wanda yake shiga ko ya fita.
Zagaye harabar wurin ta fara yi,tana neman hanyar shiga, da
son tabattar da abun da yake faruwa a wurin, ta samu wata cleaner, ko meyafaru
a in da ƴan sandan suke.
Nan ta sanar mata da cewa, yaran da aka illata a wurin faɗan
daba a daren jiya, aka kawo an hana kowa shiga ko fita.
Nabila ta yi mata godiya, ta yi mata alheri, ta nufi wurin
da aka hana shigar da fita..
Ta ƙarasa ta samu ɗaya daga cikin jami'an tsaro suka gaisa,
sannan ta nemi shiga, suka ce ba za ta shiga ba.
ID card ta nuna musu, amma ɗaya daga cikin su ya ce
"Madam nan ba prison bane, kuma ba police station ba ne ba, nan Asibiti
ne, ki bari idan aka kai su can, sai ki je ki yi aikin ki".
Ta kwantar da murya ta ce "Dan Allah yallaɓai, ku bar
ni na shiga, Ma'aikaciya ce nima"
"Get out from here" yayi mata tsawa.
Aikuwa ta hasala ta ce "A beg, don't shout at me,
aikinka ka ke yi, nima nawa nake son yi, a kan me za ka yi mini tsawa?"
Hankalin mutane ya fara dawowa wurin.
Sake hayayyaƙowa Nabila yayi, amma cikin dakiya da taurin
kai, take mayar masa da martani.
Da ƙyar aka rarrashi police ɗin, dan cewa yayi sai sun tafi
da ita station, wataƙila ma ƴar ƙunar baƙin wake ce, ko ta na da alaƙa da masu
laifin.
Nabila ta ce "Ni za ka yi wa sharri, ki in ƙunar baƙin
waken zan kai, zan tsaya saurarku ne, da yanzu wani zancen ake ba wannan
ba".
Ana ta ƙoƙarin sasanta magana, amma Nabila ta ƙi yin shiru.
Ta ciro wayarta, ta kira Nasir sai huci take yi.
Yana ɗagawa ta ce "Yaya, ya ake ciki ne? Akwai wani
labari ne?"
Ya ce "No, wallahi arfa kin ganni, na zagaya station
uku a yankin, duk ba a kai su ba, amma wata majiya ta tabattar mini da sakinsu
aka yi, just recently"
"Sakin su kuma? Saboda me?"
"Ban sani ba, a kan abun da nake ƙoƙarin yin bincike
kenan"
"Ka hanzarta ka taho asibitin cikin gari, akwai waɗanda
aka kwantar, police sun hana shiga sun hana fita, an hana kowa shiga, ko da
kuwa kusa da ɗakin. Har da ƴan jarida ma an hana su"
Cikin sauri ya ce "Ok shikenan, gani nan in sha Allah,
hankalina bai kai kan in zo asibiti ba ma na duba ko akwai abun da zai taimaka
mini, amma gani nan stay safe"
Ta amsa da "Ok"
Ta ajiye Wayar a jakarta, ta cigaba da kaiwa tana komowa,
ƴan sandan suka saka mata ido, dan kar ta yi wani mummunan yinƙuri, dan ba su
san manufarta na dagewa a kan son shiga wurin ba.
Babu tsammanni aka fito da matasan, wasu ɗauke da raunuka,
wanda ba za su iya tafiya ba, an turo su a kan gado, an nufi hanyar barin
emergency da su.
Nabila ta nufe su cikin sauri, amma ƴan sanda suka tare ta.
Ta kalli ɗaya ta ce "Yallaɓai ina za a kai su? Na ga
wasu a mugun yanayi, ya za a bar asibiti da su?"
Babu wanda ya kula Nabila, aka saka matasan a cikin
ambulance, har da iyayen wasu daga cikin matasan jami'an tsaron suka hana su
bin su, suka rufe ambulance ɗin, su kuma su ka hau ta su motar ta ƴan sanda,
suka bar harabar asibitin.
Ƴan jaridar da suka yi ƙoƙarin bin su ma, aka dakatar da su,
aka hana su ƙarasawa ma in da motar take har suka tafi.
Tsayawa ta yi kamar wata shashasha, tana mamakin yadda
abubuwa suke tafiya, kamar a film.
Motar DSP Nasir ce ta shigo cikin harabar asibitin, yayi
parking ya fito, yana ƙoƙarin kiran Nabila a waya,ya tambayi tana ina.
Da sauri ta ƙarasa in da yake, tana kallonsa, amma ta kasa
magana.
Ya ce "Yaya dai? A wane ɓangaren suke, kin samu ganin
na su kuwa?"
Nan ta kwashe duk abun da ya faru, ta gaya masa.
Cikin asibitin ya shiga, tana biye da shi, ya tambayi office
ɗin incharge na A&E ɗin, ya gabatar masa da kansa, tare da yi masa
tambayoyi, a kan dalilin da ya sa, aka sallami mutane da raunuka a jikinsu.
Amma ya tabbattar masa da cewa, babu wanda yayi musu wani cikakken bayani,
kawai ƴan sanda sun kawo musu yaran jina-jina tun a daren jiya, sun ba su
kulawar da ta dace, daga bisani ƴan sandan suka ce asibiti za su canza musu,
aka tafi da su.
Nabila ta yi shiru, sannan ta ce "Akwai wata a ƙasa
yaya Nasir, ko waye wannan Aminun, ya na da wanda su ke sponsiring ɗin sa. Shi
an kasa kama shi, amma ya na saka yaran mutane ta'addanci, you need to put more
effort, and i will hundred percent support you, everyone is equal before the
law, dole a nemo shi a hukunta shi"
Ayshercool
08081012143
*ƘARFE A WUTA*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g.
6
Nasir ya ce "Sannu da ƙoƙari arfanmu, amma ki daina
saka kanki a risk kin ji ko? Zan cigaba da ƙoƙarina in sha Allah sai na yi
sanadin kawo ƙarshen ta'addanci da harkar daba a garin nan, domin kuwa yana ci
mini tuwo a ƙwarya nima, but for now mu je na kai ki wurin aikinki"
Nabila ta ce "DSP, dan Allah idan ka gano wani abu na
rashin gaskiya, ko waye yake da hannu a ciki, ka tona masa asiri. Dan ina ga
sumy zan yi wa magana, su faɗi abun da ya faru a gidan rediyo, an saki waɗanda
aka kama, kuma wanda aka ji wa rauni ma, an hana kowa zuwa wurinsu, daga bisani
kuma jami'an tsaro sun kwashe su daga asibiti, babu wanda ya san in da aka kai
su, wannan wane irin abu ne?" tayi maganar cikin haƙiƙancewa.
Yayi murmushi ya ce "Kar ki soma, ki na wasa da hukuma
arfa, yanzu sai ki kwana a ciki ke, yanzu dai mu je mota" haka ya tasa ta
a gaba zuwa mota, suna tafe tana mita.
"Wallahi yaya na fara sarewa da lamarin ƙasar nan, anya
kuwa gyaran ake so ayi da gaske, ta yaya za ace an gagara kama mutum ɗaya? Ana
yekuwar ana nemansa, amma kuma ana kare laifukan da yake aikatawa, ni na kasa
gane kan wannan lamarin.
Ni fa muddin na gano wani abu na rashin gaskiya, sai na yi
magana"
"No Arfa, ba huruminki bane ba, ba kuma aikinki ba ne
ba, kar ki kuskura ki saka kanki a hatsari, ƴa mace ce ke lamarin ƙasar nan ya
wuce tunaninki, ba abu ne mai sauƙi kamar yadda ki ke hangensa ba"
Ta yi ajiyar zuciya, sannan ta ce "Yaya garin nan yana
kan gaba a garuruwan da ake ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, duk al'ummar da
matasanta suka lalace da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi ba ta da gobe mai kyau,
matasanmu su ne tushen al'umma mai kyau"
Nasir ya ce "Na fuskanci abun da ki ke nufi, but is
still not your field"
Tayi shiru ta mayar da hankalinta kan titi, tana ta tufka da
warwara a zuciyarta.
Ko da ya kai ta wurin aiki, ta sauka suka yi sallama, ta
shiga tana shiga office ɗin ta, sumayya ta fara kira.
Sumayya ta ɗaga ta ce "Kin gama fushin ne?"
"Ke ware ba wannan ba, matsoraciya da ba ki je ba ni na
je, na samo labari, ina ga bayyana labarin ka iya janyo hankalin manya a cikin
lamarin"
Sumayy ta gyara zama ta ce "Labarin me?" Nabila ta
gaya mata komai, yadda yaran da aka kama suka yi ɓatan dabo, da yadda aka fice
da na asibiti ba tare da sanin ina aka kai su ba.
Sumayya ta ce "Nabila lallai wannan magana ce babba,
bari zan yi magana da MD na ji mai zai ce, gaskiya yakamata a zurfafa bincike a
kan lamarin nan".
Cikin zaƙuwa ta ce "Dan Allah sumayya ki ƙoƙarta, ayi a
sanar, a ji mai hukuma za ta ce a kan haka, ko kin san shi kansa Aminu Viper
ana zargin ko dai guduwa yayi daga gidan yari, ko kuma sakinsa aka yi ba bisa
ƙa'ida ba, shiyasa ake tsananta nemansa yanzu"
"Ke ya aka yi ki ka sani?"
"Yaya ne ya gaya mini, akwai lauje cikin naɗi a lamuran
mutumin, mutum kamar wani sheɗani".
Sumayya ta yi shiru sannan ta ce "Bari, yadda mu ka yi
da su zan gaya miki, amma maganar nan ta ɗauki hankalina sosai"
"To shikenan, ina saurarenki, yadda ake ciki, ki sanar
mini" suka yi sallama.
Haka kurum zuciyar Nabila ta cigaba da azalzalar ta a kan
lallai tana son sanin wanene wannan Aminun, akwai yiwuwar ta samu gagarumar
nasara idan aka ce da saka hannunta wurin kama shi, shahararta ita zai ba ta
damar yin gaba da gaba da Naja'atu Bunkure.
Sai kuma ta tambayi kanta, for the first place, laifin me ya
yi aka kai shi prison, har ake tunanin ya fita ba bisa ƙa'ida ba?.
"Akwai ayar tambaya a kan abubuwa da dama" ta yi
maganar a fili.
***
Ƙurawa wayar gabansa ido yayi, yadda take ta vibration kamar
ta tashi, a wannan karon ma private number ce, lambar da ko ta halin ƙaƙa yake
fatan ganin ko waye mai ita ya bayyana a gare shi.
Ɗan mama da ke kusa da shi ne, ya ɗaga wayar ya sanyata a
hansfree, ya tura masa gaban sa.
Daga cikin wayar aka ce "Manya gatan wasa, ko ka
tsorata ne ya sanya ka gagara ɗaukar wayata?"
Yayi shiru bai ce komai ba.
"Idan za ka kwana dubu kana ɓarna, zan kwana dubu ina
goge ta, ina ɓatar da sahunka. Ka na ta cigaba da aikata ɓarna, saboda kana son
lallai sai ka san waye ni ko?"
"Wanene kai?" Yayi maganar a ɗan hasale.
Mutumin yayi murmushi ya ce "Mutum, mai zuciya cike da
muradai kamar ka. Ƴan kwanakin nan ka fi mayar da hankali a kan sanin wanene
ni, fiye da abun da yake damun zuciyarka. Ka bi a hankali kar garin kallon ruwa
kwaɗo ya yi maka ƙafa, kar ka saki reshe ka kama ganye, ya kai wannan maciji
mai hatsarin gaske"
Al-amin ya numfasa ya ce "Ni ba karen farauta bane ba,
da za ka din ga wasa da ni, tamkar ɗan kwiwiyon da ka raina, ka yi a hankali da
ni, ƙarfe nake cikin wuta, na fi ƙarfin ɗauka da hannu"
Ya sake murmusawa ya ce "Ka huta mutumina, ka samu abun
da zai ɗebe maka kewa, ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, ba za su taɓa rabaka da
damuwa ba, matuƙar ba ka yi abun da zuciyarka ke gaya maka ba, haryanzu ka na
da sauran ƙuruciyarka, zaka iya amfanar da al'ummarka"
Kafin Aminu yayi magana, mutumin ya katse wayar.
"Amma Yallaɓai, kana ganin wannan abun da muke yi shi
ne dai-dai? Akwai abubuwa da yawa da yakamata ace mun mayar da hankali a kai,
ba bawa ɗan daba kariya ba"
Ya ajiye jaridar hannunsa ya ce "Kalle ni da kyau, ba
na abun da babu manufa a kansa, dan haka kawai ka saka ido"
Waya ce ta fara ringing, ya ɗaga sannan ya miƙo masa.
Ya karɓi wayar tare da yin sallama.
"Wa'alaikum Salam, barka dai ya ƙoƙari?"
"Alhamdilillah sir, an yi clearing matsalar jiya, duk
da an kusa samun akasi, yaron ba ya ji ko kaɗan, idan aka cigaba da tafiya a
haka, kar asirinmu ya tonu fa, dan hakan tamkar yi wa doka karan tsaye ne, mu
na saɓa ƙa'idar aiki"
Yayi murmushi ya ce "Kar ka damu, doka ce ta fara yi wa
yaron karan tsaye, shiyasa nake amfani da dokar, wurin bi da komai"
"Haka ne sir, amma fa police suna neman shi ne ruwa a
jallo, mu kuma muna kare shi, muna taka doka da yawa"
"ASC, ko sun kama Al'amin, ba zasu bari doka ta yi aiki
a kansa yadda yakamata ba, za su bar shi da masu son zuciya ne, su yi abun da
suka ga dama da shi, ba wai hukumar ce kawai take nemansa ba, akwai lauje cikin
naɗi ne a neman da ake yi masa"
ASC ya numfasa ya ce "Shikenan, amma laifukansa sun yi
yawa, duk wani ta'addanci da za'ayi a garin nan sai ka ji yaransa ne, slide
mistake za'a iya kama shi, duk da wani abun kuma idan muka bincika, sai mu
tarar ba shi ɗin ba ne ba"
"Haka ne, amma idan an kama shi ma, sunana na ko naka,
babu wanda zai fito, haryanzu bai san ko ni waye ba, kuma ba zan bari ya sani
ba, kuma yana aikata wasu laifuka ne dan ya tilasta na ƙyale shi, ko kuma na
bayyana kai na a gare shi, amma ka rabu da shi, komai cikin tsari nake yin sa,
ka bar police su cigaba da neman sa, hukumarka kuma ta cigaba da aikinta, kamar
yadda na ce maka"
Ya amsa da "Shikenan sir, am always loyal to you, na
gode"
"Yauwwa ASC, duk halin da ake ciki dai, ina buƙatar ka
sanar da ni"
"No problem, sai an jima" bayan sun yi sallama,
yayi wata irin dariya, da shikaɗai ya san ma'anarta ya ce "Wannan shi ne
jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya" yayi maganar yana kallon yaronsa da yake
tsaye yana kallon sa.
Ya ce "Lallai, amma zan so in ji wani irin shiri ne
haka ka ke yi sir"
"Za ka gani a aikace, kai dai ka cigaba da biyayya ga
abun da duk na umarce ka, nima zan yi amfani da ƙarfin iko da kujerata, na yi
abun da ya dace".
"Ok sir, in sha Allah".
***
Misalin ƙarfe takwas na dare, wasu daga cikin manya na
ƙungiyar ƙato da gora na unguwar suka tattaru suka zauna meeting a cikin ɗan
madaidaicin office ɗin su. Duba da abun da ya faru, na faɗan daba da aka yi da
yaran Aminu da na Madaki a waccan unguwa, sanin ya na shigowa unguwar lokaci
zuwa lokaci, sannan kuma akwai yaransa a unguwar, ya sanya su zaman yin
meeting, dan ƙara ƙarfafa tsaro a cikin unguwar su, kar su gama da can su dawo
nan.
Suna tsaka da tattaunawar, wasu zaratan matasa suka yi
sallama, suka amsa suna bin su da kallo.
Suka shiga cikin office ɗin, suka kewaye su, duk suka tsaya
suna kallon su.
A hankali ya sauke face mask ɗin fuskarsa, a take suka
shaida shi.
Kafin su yi magana ya ce "Awa ɗaya rak nake buƙata, zan
gama abun da ya kawo ni na fita, muddin na kuma shigowa unguwar nan, ku ka sako
ni a gaba, kamar kare za ku kama ni, wallahi sai na yi muku abun da na yi wa
malam lawan".
Shugaban ƴan sintirin ya ce "Dan meyasa zaka din ga
shigo mana unguwa? Kai da hukuma take nema ruwa a jallo, ka san kai tauraruwa
mai wutsiya ne, duk in da ka je sai ka yi fitina, tun da yaranka suka yi ɓarna
jiya, na san cewa nan ma zaka shigo. Duk ka lalata mana yara ka tafi ka barmu
da masifa, kuma yanzu ka dawo kana cigaba da bibiyarmu"
Cikin tsawa Walid ya ce "Kai, ka iya bakinka, wallahi
ko na ɓare maka shi har ƙeyarka".
Cikin tamkakiyar fuskarsa Viper ya ciro zungureriyar wuƙar
da take ƙugunsa, ya karta ta a ƙasa tayi wata irin ƙara, sannan ya ɗora ta a
gefen wuyan mutumin ya ce "Ƴaƴanku za su cigaba da yi mini biyayya, sai na
mayar da unguwar nan mafi munin sansanin ta'adancci da zubar jini, komai ya
faru ai ku kuka so, yanzu dan Allah kai ba ka ji kunyar faɗar abun da ka faɗa
ba? Duk in da zan je zuciyata na tsakiyar unguwar nan, kuma zan cigaba da shiga
da fita yadda nake so, har sai na yi maganin azababbiyar ƙishirwar da ta addabi
ruhina. Duk abun da na aikata muku na ɓarna, ku kuka so, mutanen banza masu
butulci, kun taki sa'a da nake dakon alƙawari mai nauyi a kaina, ban da haka
tun a fitowa ta, ɗaya bayan ɗaya zan yi muku kisan gilla. Idan na sake shigowa
unguwar nan, kai da wannan mutanen, ku ka yi yinƙurin yi mini wani abu, duk
wanda na kama, zai zama mutum na farko da zan yi wa yankan rago!" Gaba ɗaya
suka zuba masa ido, suka kasa ko motsin kirki, saboda yadda suka zagaye su da
miyagun makamai.
"Ku karɓe wayoyinsu, ku rufe mini su, ku saurari order
da zan bayar. Duk wanda yayi muku gardama ku karya mini ƙafarsa, ko ku tsarge
masa cinya".
"Angama boss"
Yana fita daga office ɗin, suka mayar suka rufe, suka ƙwace
musu wayoyi, sannan suka tsaya a kansu da wasu irin zabga-zabgan wuƙaƙe, kamar
a abba tuwa.
Babu wanda ya iya wani ƙwaƙwƙwaran motsi, dan a yadda
matasan suke muzurai, kuma shaye-shaye ya huda su, duk umarnin da ya ba su za
su bi.
Sannu a hankali yake tafiya, har ya kawo cikin layin, ya
tsaya a ƙofar wani gida, ya shafe tsawon lokaci kawai ya zubawa gidan ido, yana
zancen zuci, daga bisani ya ƙarasa ya ƙwanƙwasa na kusa da shi, ya ja mask ɗin
sa, ya rufe fuskar shi.
Yaro ne ya fito ya ce "Waye?", ya cewa yaron
"Ka je ka cewa babanka an zo duba shi"
Mintuna kaɗan yaron ya dawo, ya ce ya shiga.
Bai yi sallama ba, haka ya kunna kai cikin gidan, har
tsakiyar falon maigidan, ba tare da an yi masa iznin hakan ba.
Daga maigidan har matar gidan, da ƴan matan yaran, tsuma
suka hau yi, ganin wanda ya shigo har cikin gidansu.
Ya zaro wuƙarsa ya ajiye a gaban malam lawan, sannan ya ɗaga
wani mukulli ya ce "Na rufe gidan nan da kwaɗo ta ciki, kuma duk wanda ya
yi wani ƙwaƙwƙwaran motsi, zan zaunar da shi kamar yadda na zaunar da kai"
yayi maganar yana kallon malam lawan.
Ya durƙusa kama ƙafar malam lawan, da aka naɗe da bandeji,
ya dudduba sannan ya ce "Ɗori yayi kyau, sai dai na yi mamakin yadda aka
dawo da kai gida, maimakon ka yi jinya a asibiti"
ya saita tsinin wuƙarsa a cinyar malam lawan ya ce
"Waye ya ɗauko ka daga asibiti?"
Cikin tashin hankali matarsa ta fara kuka ta ce "Dan
girman Allah Aminu kar ka yi masa wan....
"Wallahi ki ka sake magana, sai na karya ɗaya ƙafar, ka
gaya mini kafin na huda cinyarka" yayi maganar cikin razananiyar muryarsa.
Cikin matsanancin tashin hankali ya ce "Wallahi wasu
mutane ne, ban san su ba, su ne suka sauya mini asibiti, lokaci zuwa lokaci,
suke zuwa da likitansu ya duba ƙafata, kuma sun gargaɗeni a kan muddin wani ya
ji kaine ka yi mini haka, sai sun kashe ni"
"Waye ya kai ka asibiti ranar da abun ya faru?"
Cikin kyarma da rawar murya malam lawan ya ce "Wallahi
kana barin wurin, ina wannan kakarin, wani ya zo yayi mini kashedin muddin na
ce kai ne zai kashe ni, ya watsa mini wani abu, ban sake sanin in da kaina yake
ba, sai da safe maƙwabta suka tsince ni, na ce masu masu ƙwacen waya ne suka yi
mini"
Aminu ya ware masa jajayen idanunsa sosai ya ce "Idan
na samu labari akasin abun da ka gaya mini, kar ka manta take na, maciji
nake mai mugun dafi, sai na maka karayar da ba zaka sake taka ƙafarka ba a
doron duniya. Zan cigaba da zagayowa zan kuma cigaba da sanya maka ido. Kar ka
manta ka yi mini ganganci daban-daban, na kawar da kai, na riƙe biyu a raina
idan ka yi na uku kasheka zan yi har lahira".
Malam lawan ya jinjina kai, yana jin yadda mararsa ta cika
fam da fitsarin tsoro.
Viper ya a miƙe ya juya ya bi hanyar fita.
Sai da suka tabattar da tafiyarsa, sannan matar malam lawan
ta ce "Na shiga uku, baban su Amir dan Allah meya aike ka sake shiga
sabgar mutumin nan? Daga ƴan sandan har ƴan ƙato da goran kar wanda ya ƙara
tambayarka abu a kansa ka ce ka sani, kalli bala'in da ka jefa mu a ciki?"
"Ke dalla rufe mini baki, tun da yanzu na tsira da
raina shikenan, ina ga sayar da gidan nan zan yi na bar unguwar, idan ba haka
ba wataran kasheni zai yi "
"Ai koma menene Allah ya ƙara wallahi, abun da ka yi wa
bawan Allah nan ka yi butulci da yawa"
"Au so ki ke na rufawa mutumin banza asiri Haule? Ni ki
ke gaya wa haka?"
"Oho ai gaskiya ce" haka suka cigaba da faɗa, tana
mita da ɗora masa alhakin janyowa kansa ko ma menene.
Aminu kuwa, ta waya ya ce wa su ɗan mama, su baro ƴan
vigilante ɗin, su bi shi gida.
A gidan suka tarar da shi, ya dubi Walid ya ce "Ka
yawaita survey a cikin unguwar nan, mutumin nan ya tabattar mini da cewa, wanda
suka canza masa asibiti, suna zuwa da likta har gida yana duba shi".
"To shikenan Oga, in sha Allah za ayi yadda ka ce"
"Kuma na san mutanen nan ne, da mutumin yake kirana a
waya, ya zama dole na san waye, da kuma manufarsa a kaina, da yake bibiyata har
haka".
Walid ya ce "An gama maigida"
Nabila kuwa tun da ta shiga aiki tana office ɗin ta, suna
communicating da Yaya Nasir.
Wayar sumayya ce ta shigo ƙaramar wayarta, dan haka ta ajiye
ta hannunta ta ɗaga da sauri ta ce "Sunayya yaya ake ciki?"
"Kamar dai yadda na yi tsammani" ta bata amsa.
"Me ki ka yi tsammanin? Yi mini gwari-gwari"
"Ba irin labarin da suke buƙata ba kenan, hakan ka iya
kawo musu naƙasu ga cigaba da kuma tasirin gidan radiyon su, kuma wai ba ni da
cikakkiyar shaidar abun da na faɗa"
"Haba Sumayya, ni ina da shaida fa, ga kuma yaya Nasir
ma, kuma ya zaki tsaya a wurin wannan shashashar matar da ba ta son cigabanki?
Ki yi wa Manager magana mana direct, nima ina da lambarsa, sai na yi masa
magana".
Sumayya ta ce "Nabila kenan, duk kanwar ja ce, shi ne
ya jaddada mini hakan da kansa".
"Allah wadaran naka ya lalace, Yanzu sumayya shikenan
zuba ido zamu yi? Babu wani abun yi?"
Sumayya ta ce"Idan na matsa zan iya rasa aikina, abun
da ya nuna mini kenan, wai ba za su iya jayayya da hukuma ba, kuma na kawar da
kaina a kan abun da ba zan iya jurewa ba, da ina da wata hanyar samun kuɗin, da
ajiye aikin nan zan yi Arfa"
"Shikenan, zamu yi magana anjima, see you later"
ta ajiye wayar ta zauna ta yi shiru.
Wani irin tsaki ta ja, tana mamakin yadda galibin private
organizations suke buɗe wurare, for their personal interest kawai, kodayeke na
gwamnatin ma menene, duk ɗaya.
Ganin ɓacin ran ba zai amfanata komai ba, tana da abubuwan
da yakamata ta yi, ya sanya ta fita ta tafi office ɗin Barrister Habib.
Yana ta aiki a system, ya ɗago ya amasa mata sallamarta, ya
cigaba da aikinsa.
"Barka da aiki barrister".
"Yauwwa" ya amsa a taƙaice.
"Barrister wai haryanzu fushin ka ke yi, na shiryu fa
na daina duk wani abu da nake yi, sonake na zama cikakkiyar lawyer abar koyi ga
wasu, kamar gwanata Barrister Naja'atu Bunkure" da ɗan sauri ya ɗago ido
ya kalleta ya girgiza kai ya ce "No wonder, shiyasa ba zaki cigaba
ba"
"Subhanallah, meyasa?" Tayi maganar tana ware ido.
Maimakon yayi magana, sai yayi mata shiru.
Wani irin kallo tayi masa, a zuciyarta ta ce 'Sai fa ka yi
magana barrister'
A zahiri kuwa ta ce "Ni dai haka kurum nake sonta,
ayyukan ta na jin ƙai suna burgeni, ina son zama kamar ita. Amma tun da haka ne
ma, na canza kamar kai nake son zama, daga yau kai ne mudubina" tayi
maganar tana murmushi.
"Ke da ba zaki iya zalunci ba, mu ne azzalumai ai"
Nabila ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, waye
ya faɗi haka? Wallahi ba haka bane ba, ni ban ce ba"
"Idan har kina son zama shahararriya, dole ki yi iya
yinki, a kan duk abun da ya zo hannunki, ko da kuwa babu tabbacin zaki yi
nasara, idan ba zaki iya ba kuma, you can leave"
"No, zan iya, ai na shiryu yanzu"
Ya buɗe drower gabansa, ya ɗaukko wani file ya ajiye mata
sannan ya ce "Wannan client ɗi na ce, a nan ƙofar na'isa gidanta yake, zan
turo miki cikakken adress ɗin ta, ki je ku yi magana, sannan ki yi tunani a kan
case ɗin nata" Cikin girmamawa ta ce "Na gode sosai, zan yi in sha
Allah "
Tana fita daga office ɗin nasa, ta gyatsine baki, ta ce
"Kamar ni za a aika, gidan wata ƙatuwa, ba ma ta zo office ta same mu ba,
hamshaƙiya saboda ga ƴar Nabila ƴar wahala. Amma bakomai da na zama abun da
nake so, na fi ƙarfin kowane irin wulaƙanci" ta koma nata ofishin tana
cigaba da ƙunƙuni.
Da ta koma gida ma, ba ta bi ta kan aiken da barrister yayi
mata ba, ta kwanta ta sha baccinta, bayan ta tashi ta shirya ta yi wanka, ta
tafi gidansu sumayya.
Sun jima suna tattaunawa da sumayya, a kan harkar aiki, har
sumayya ta din ga ja mata kunne, a kan kasadar da take yi, tare da nuna mata
illar hakan a matsayin ta na ƴa mace, ta kunnen hagu maganganun sumayya suka
din ga shiga kunnenta suna fita, dan ba ta ji sun shigeta ba.
Ta bawa Sumayya labarin aiken da barrister Habib ya yi mata.
Sumayya ta ce "Kuma zaki ɗin?"
"To ya zan yi?"
Sumayya ta yi dariya ta ce "Ai na zata taurin kan yana
nan?"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Na ajiye taurin kai, zan
kama aikina yadda yakamata, ai sai burina ya cika sai na binciko wacece Bunkure
kuma in sha Allah, sai sunana ya shafe nata a tarihin duniyar ma'abota
shari'a".
"Allah wadaran naka ya lalace, Nabila, wai ke wani irin
taurin kai ne da ke ne? Ke abu ba ya wucewa a wurinki ne? Ki bar ta kawai, idan
Allah ya so, tana raye zata ga nasarar da zaki yi a rayuwa"
"Ina kwance nasarar za ta zo ta same ni kenan? Ke
ƙyaleni, ina ga sai Allah ya kaimu friday da yamma, zan je waccan unguwar gidan
matar, na ga bai turo mini contact ɗin matar ba tukuna, zaki rakani?"
Sumayya ta ce "A'a gaskiya, wannan unguwar, ana ta
fama, kamar ba kya jin radiyo, yadda suke fama da faɗace-faɗacen daba. Ki
gayawa barrister ya ce kawai matar ta je office ɗin ku, ko kuma ki bari
komai ya lafa, dan kullum cikin faɗan daba suke"
Nabila ta ce "So ki ke in kasa samun information ɗin da
nake so daga bakinsa kenan? Ai lallaɓa shi zan tayi, sai na san wacece matar
nan. Kodayake ma na saka Yaya Nasir ya rakani" sai kuma ta yi shiru, ta
sake maimaita zancen Sumayya a zuciyarta.
*Wannan unguwar ana ta fama da faɗan daba*
Ta sake kallon sumayya ta ce "A unguwar ne aka ce yaran
Aminu Viper sun yi sare-sare?"
Sumayya ta yi shiru tana kallon idon Nabila.
Nabila ta yi murmushi ta ce "Kar fa ki kawo komai a
ranki, ba wani abun zan aikata ba, bari na tafi kan Abba ya dawo ya nemi ina
nake" ta ɗau jakarta ta fita, tana jin kamar matsalarta ta zo ƙarshe.
*Masu nema daga farko, ku yi joining link channel ɗina na
saman page, idan kun shiga zaku samu daga farko*
Arewabooks ayshercool7724
Watpad
ayshercool7724
Ayshercool
08081012143
*ƘARFE A WUTA*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
BRIGHT PENS SECOND BATCH
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
7
Katafaren falo ne, wanda girmansa ya ishi wani talakan gina
gidan da zai rayu a ciki, talabijin ɗin da ke falon kawai ta fi rabon bango.
Kujera set biyu ce a falon, kuma tsakanin kowane set da wani
akwai tazara.
Tinkis-tinkis haka ya fito cikin wata irin dakakkiyar shadda
maroon, sai ƙyalli take yi, ba sai an faɗa ba ka san akwai tazara mai nisan
gaske tsakanin sa da talauci.
Ba wata ƙiba ce da shi ba, amma cikinsa yayi kurtsitsi a
riga, har wani nishi yake yi.
Ya nemi wuri ya zauna a ɗaya daga kujerun falon, ya kalli
matasan da suke zaune a ƙasa a kan carfet. Dukkansu babu mai suturar kirki a
cikinsu, kansu duk askin banza, yanayin shigarsu da fuskarsu kawai za ta
tabattar riƙaƙƙun masu laifi ne.
"Allah ya taimaki maigida" cewar ɗaya daga cikin
su.
"Ya aka yi madaki?"
"Akwai ƙura ne, ƙurar kuma na neman zama gagarumar
guguwa"
"Ina jin ka"
"Aminu Viper, haryanzu jami'an tsaro ba su kama shi ba,
ya sa an kaiwa yarana mummunan hari, an yi musu miyagun raunuka, jami'an tsaro
sun kama yarana sun saki nasa, wanda aka kai asibiti ma, an kwashe su daga
asibiti babu wanda ya san in da aka kai su"
Mutumin yayi tsaki ya ce "Ina mamakin yadda mutum ɗaya
ya gagari kamun hukuma, ni anya ba raina mini hankali ma suke yi ba a kansa?
Yanzu menene abun yi?"
"Ka saka a sakar mini yarana, dan sai da su ayyukanka
suke yiwuwa, kuma dole mu yi shiri sosai, idan da hali mu mu nemi in da yake mu
kashe shi kowa ya huta"
Mutumin yayi shiru yana kallonsa sannan ya ce "Aikuwa
da na yi maka tukucin da baka taɓa tunani ba, zan saka a saki yaran nan anjima
kaɗan, sai dai duk yadda zaka yi ka yi, a samo yaron nan, dama mugu shi ya san
makwantar mugu ai"
Madaki ya sauke numfashi ya ce "Zan shirya gagarumar ɗaukar
fansa kan mai uwa da wabi a unguwar su, jinin yarana da suka zubar ba zai tafi
a banza ba, dan shammatar su ka yi, suka mamaye su ba na nan"
"Wannan ku ta shafa, ni babban burina shi ne Aminu,
muddin yaron nan yana numfashi, kamar sarƙa ce a wuyana, dole a kawar da
shi".
Madaki ya ce "Ba kai kaɗai ba, ko kuma in ce da ni da
kai kusan abu ɗaya ne a wurinsa, nima ka san akwai tawa ni da shi, tsohuwar
gaba ce ta tsawon shekaru, wanda a kanta unguwanninmu suka kasa zaman lafiya
har yau, ga kuma wannan al'amari da ya faru. Muddin ban kashe Aminu ba, ni zai
kasheni"
Ya jinjina kai ya ce "Ai Viper na fuskanci ƙarfe ne a
wuta, ya fi ƙarfin ɗauka da hannu, sai dai da ɗan uwansa ƙarfe, kai kaɗai zaka
iya maganinsa"
"Ka bani lokaci kawai, zan kuma ƙoƙartawa, matsalar ko
yaransa ba kowa ne ya san in da yake ba, amma na san dole Walid ya san in da
yake, amma shi ma Walid ba lafiya ba ne taɓa shi, ka dai bani lokaci"
"Babu isasshen lokaci, ka yi huɓɓasa kawai"
Madaki ya jinjina kai.
Mutumin ya ɗebo kuɗi ya bashi, ya sallame su, suka juya suka
fita da shi da yaransa.
Nasir ne tsaye a office ɗin sa, ya kalli matashin da yake
zaune, da aƙalla zai yi sa'ansa ya ce "Mu'azzam lamarin ƙasarmu sai
Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ka san da ƙyar na gano station ɗin da yaran
nan suke, ba ma ta yankin da abun ya faru ba ce?"
Mu'azzam ya yi murmushi ya ce "Haka ka ce mini"
"Gaba ɗaya yaran under age ne, kuma duk cikinsu babu
yaran Aminu, dan tuni an sake su, sai wani wai madaki, na ce dai a ajiye mini
su, da yiwuwar mu kama madakin, zai iya sanin in da Aminun yake,tun da abokin
faɗansa ne, amma da na yi magana da DPO ɗin division ɗin yankin, ya ce shi ma
madakin ba ya kamuwa, kuma ya addabi yankin yana da yara sosai da sosai. Abun
takaicin ma ba unguwar su ɗaya da Aminun ba, amma suke cigaba da tayarwa da
mutane tarzoma"
Mu'azzam ya ce "Harkar nan tamu sai fa Innalillahi wa
Innalillahi raji'un, muna tufka manyanmu na warwarewa"
Nasir ya ce "Bari kawai, zan yi iya ƙoƙarin da zan yi,
ni zan kama Madakin, Arfa har asibitin da aka kai waɗanda aka yi wa rauni ta
je, muka yi waya kafin na je wai an kwashe su, an bar asibitin da su, na fara
zargin anya ba jami'an mu ne aka samu bara gurbin da suke mara masa baya
ba"
Mu'azzam ya ce "Ba abun mamaki bane ba, amma meya kawo
Arfa cikin wannan lamari, ta bar aikin lawyern ne?"
Yayi murmushi ya ce "Rigima mana, yarinyar nan ta zarce
tunaninka, ba ta wasa da duk abun da ya shafe ni ko cigaba na"
"Hmm Nasir kenan, wai yaushe zaka gayyacemu sabgar nan
ne? Shekarun ka fa suna ja"
Nasir ya rausayar da kai ya ce "Mama ce ta hana, ta
nuna ba ta so, ban taɓa gaya mata ba, saboda tun kafin na furta maman ta gargaɗe
ni a kan haka, kuma haryanzu ni ban ji ina son kowace yarinya ba, ita ɗin dai
nake so. Ban san adadin samarinta da na kora ba saboda kishi. Yadda take son
abun da nake so da son cigabana, na san da zan furta ina sonta, ba zata ƙi ba,
amma na rasa yadda zan yi da mama".
"A'a Nasir, dan Allah kar ka zalunci yarinya, haka zaku
zauna shekaru na tafiya, kai baka aureta ba, kuma ba ka bari wani ya aura ba?
Wannan ai mugunta ce, ka yi magana da Abba mana".
Nasir ya girgiza kai ya ce "Manta kawai, abun ya wuce
yadda ka ke tunani".
***
Arfa na kitchen tana taya baba magajiya aiki, suna hira tana
tambayar baba magajiya kwatancen cikin unguwar ƙofar na'isa, dan zuwa aiken
barrister Habib, dan ita ba zuwa ta taɓa yi ba.
Baba magajiya na girki, ita kuma tana wanke-wanke a sink.
Siyama da take ƴa ta uku ga mama ce ta shigo kitchen ɗin, ta
jefawa Nabila kwanukan hannunta maimakon ta ajiye.
Nabila ta yi shiru, ta cigaba aikinta suna hira, duk da abun
ya ɓata mata rai.
Amfani ta kuma yi da kofi, ta wurgowa Nabila cikin sink,
cikin zafin nama da masifa, Nabila ta ɗauki kofin ta jefa mata a fuska ta ce
"Ai ba baiwar ubanki ba ce ni, da zaki din ga jifana da kwanuka"
"Nabila ni ki ka daka?"
"An dake ki ɗin?"
Baba magajiya ce ke ƙoƙarin basu haƙuri, amma siyama ta
shaƙe Nabila, Nabila ta rarumo wani kwano ta buga mata, dambe ya kacame.
Baba uwani ta yi ƙoƙarin raba su, amma abu ya gagara.
Ta fito falo da gudu, tana neman taimako.
Dambe tun daga kitchen har falo, duk abun da Nabila ta
rarumo sai ta kwaɗa mata, kamar wasu kuraye.
"Mahaukaciyar ina ce ke? Ke kullum haka zaki ƙare ki
zagi wannan ki ci mutuncin ƴaƴan gida kina ƴar karere"
Cikin baƙin ciki Nabila take kallon mama, tana iya ƙoƙarinta
wurin danne abubuwan da mama take yi mata, duk faɗanta da tashin hankalin ita
da yaran gidan suke yi, amma sai mama ta shiga ta zaƙe ta shigarwa yaranta.
Anty ta ce "gaskiya maman Sauda wannan ba girmanki bane
ba, maimakon ki yi musu nasiha, sai ki din ga aibata Arfa, ai ba a haka"
Siyama ta din ga zagin Nabila, zagi na cin mutunci, tsawar
da Abba ya yi musu ne, ya sanya duk suka ɗago cikin tsuma.
Ya nuna nabila ya ce "Arfa, ban isa na saka doka ki bi
ba ko? Siyama ba gaba take da ke ba? Nake jiyo muryarki tun daga waje kina
zaginta?"
Arfa ta buɗe baki zata yi magana, amma ya daka mata tsawa ya
ce ta yi masa shiru.
Siyama kuma ta fashe da kuka tana gaya masa har dukanta arfa
tayi.
Aikuwa ta in da ya shiga ba ta nan yake fita ba, ya hana
kowa magana ya yi wa arfa kaca-kaca saboda sanin ba ta ji, ga rashin haƙuri da
taurin kai.
Da sauri ta tafi ɗakinsu tana wani irin kuka, ta je ta faɗa
kan gadonta, jikinta har rawa yake yi saboda baƙin ciki takaici ta din ga kuka.
Cikin kuka ta ce "Ya Allah ka bani miji kowane iri ne,
in dai zai zama alkhairi a gare ni, na tafi na bar gidan nan, na gaji Allah ka
amsa mini dan girmanka, kowane iri ne zan iya zama da shi".
Can falo kuma, jikin Abba ne yayi sanyi, ganin arfa na kuka
ya san akwai wani abu a ƙasa, dan idan tayi laifi, wataran ko kasheta zai yi ba
zata yi kuka ba, duk da tana da saurin kukan.
Ya kalli Anty ya ce "Zainab je ki duba yarinyar nan,
kar ciwonta ya tashi"
Anty ta jinjina kai, ta bi bayan arfa.
Mama kuwa a sashinta take yi wa Siyama mitar meyasa ba ta yi
wa Nabila dukan da za ta kasa tashi ba.
"Mama kin san yarinyar nan har aljanu take yi, haka
kurum su tashi ni ta kashe ni, komai ta rarumo buga mini take yi, ba ki ji kafaɗuna
ba"
Mama ta yi ƙwafa ta ce "Na rasa yadda zan yi maganin
yarinyar nan, wallahi bana sonta ba na ƙaunarta, gaba ɗaya ba kwa gaban
mahaifinku sai ita, in sha Allah sai ta zame masa masifar da ba zai iya shawo
kanta ba, sai ta kwaso abun kunyar da za ta kunya ta shi a idon duniya".
Nabila kuwa ƙin saurar anty ta yi, ta sha uban kuka, Anty ta
sanarwa Major kukan da take yi, ya basar kamar bai damu ba, amma ƙasan
zuciyarsa sam babu daɗi.
Tsakar dare suke waya da sumayya, take gaya mata abun da ya
faru.
Sumayya ta ce "Arfa, ke rashin haƙuri ne yake janyo
miki wasu abubuwan, da kin yi haƙuri ba ki tanka mata ba, dama neman magana ta
zo yi".
"Sumayya kin san ba zan iya ba, ni ina wulaƙanta mutane
ne?"
Sumayya ta ce "A'a idan na ce kina da wulaƙanci Nabila
na yi miki sharri, sai dai masifa da rashin haƙuri, ga jarababben taurin kai ba
a gaya miki ki ji ko kaɗan"
Nabila ta ce "Sai dai ayi haƙuri da ni a yadda nake, ni
ba zan yadda da wulaƙanci ba"
"Aikuwa zaki yi ta shan wahala dan ubanki"
Nabila ba ta damu da zagin da sumayya ta yi mata ba, domin
idan da sabo ta saba, dan wasu lokutan sumayya playing role take yi kamar na
uwa a rayuwarta, ta kan ji maganarta idan ta ga dama.
"Sumayya dan Allah ki yi mini addu'a, Allah ya bani
miji kowane iri ne, in dai zai zame mini alkhairi a shekarar nan na bar gidan
nan na huta"
Sumayya ta ce "Ba ki da hankali, kowane iri fa ki ka
ce"
"Eh, wallahi idan ba haka ba, zan gudu na bar garin
nan, na bar musu gidan, sumayya baki san me suke yi mini ba na gaji" ta
ƙarasa maganar cikin shagwaɓa tana kuka.
Sumayya ta san komai, dan haka cikin rarrashi, ta kwantar da
murya, ta din ga yi wa Nabila nasiha, da rarrashin ta, har ta sassauta kukan da
take yi.
Da haka suka yi sallama, ta kwanta bacci.
Sai dai ta kasa baccin, saboda yadda zuciyarta take zafi, ta
rasa me ta tsarewa maman su Sauda a rayuwa, da ita da yaranta suka tsaneta
haka, Nasir ne kawai suke ɗasawa da shi, da ƙyar bacci ya kwashe ta.
Da safe ta shirya cikin wata abaya baƙa, tayi kyau ko
karyawa ba ta tsaya yi ba, ta fito falo fuskarta babu walwala.
Kallo ɗaya zaka yi mata, ka san ba ta samu isasshen bacci
ba.
Da kamar ta yi fuska tayi tafiyarta, amma ta haura benan
Abba ta je ta gaishe shi, sai dai fuskarta babu annuri, babu raha da ta saba yi
idan ta je gaishe shi.
Ya ƙura mata ido ya ce "Kin karya kuwa?" Ta ce
"Idan na tsaya karyawa zan makara, zan karya a wurin aiki"
"Dan zaki makara sai ki fita ba ki karya ba, yaushe ki
ka fara tsoron makara? Menene ma ya hana ki tashi da wuri?"
Tayi shiru tana wasa da yatsun hannunta, idonta yana cika da
hawaye.
Ya saka hannu a aljihunsa, ya ciro kuɗi masu yawa, ya miƙa
mata ya ce "Ga wannan na san wata yayi nisa, babu lallai ki na da kuɗi a
hannunki, ki sai wani abun idan kin je ki karya, saura ki sai abun da zai ɓata
miki ciki, ko ya cutar da lafiyar ki"
Kamar ta ce ya bar su, amma ta saka hannu biyu ta karɓa, ta
ce ta gode, yanayin yadda take tafiya kawai, zai tabattar mata da tana cikin
damuwa ko rashin lafiya.
Gaba ɗaya jikin Abba ya yi sanyi, a tsakiyar zuciyarsa yake
jin zafi, idan ya ga Nabila a cikin damuwa, shiyasa wasu lokutan baya iya jure
yi mata hukunci yake kawar da kai a kanta.
Duk iya ƙoƙarin da Nasir yake yi, a kan yaƙi da harkar daba,
abu ya ci tura, dan yaran da aka kama ya koma ya tarar da wai an yi umarni daga
sama a sake su, abun ya ɓata masa rai sosai da sosai.
*****
A farfajiyar wata bishiya suke zazzaune, suna ta
shaye-shayen kayan maye, duk sun cika wurin da ƙaurin hayaƙi.
Madaki ya karta wuƙa a ƙasa, ya kalli tarin matasan da sun
fi ashirin a gabansa ya ce "Babu rangwame ko sassauci, babu mace babu
namiji, ko babba yaro ko tsoho, duk wanda aka samu idan aka shiga operation ɗin
nan a farmasa, ayi ɓarna ayi ta'adi a ɗauki fansar abun da Aminu yayi mana,
jini ya din ga gudana ko ta ina, duk shagon wanda aka samu a fasa ku kwashi
ganima, na yarje muku.
Haka zalika duk wanda ya gano in da Viper yake, muddin ya
kawo mini shi, a mace ko a raye, akwai tukuici mai tsoka"
Suka fara shewa cike da maye, ɗaya daga cikin su ya ce
"Aminu fa ƙarfe ne a wuta, duk wannan shewar kama shi ba abu ne mai sauƙi
ba, da mai sauƙi ne na san da ka riga mu kama shi"
Madaki ya ce "Rufe mini baki, ko na yi gunduwa-gunduwa
da namanka, dole ne a kama shi, kai gobe duk wanda aka gani daga tsallaken
unguwar su, ya shigo unguwar nan ma a sara mini shi kawai, a ɗauki fansa mafi
muni na abun da ya yi mana, zan ga da ni da shi, waye zai sarara waye gaba da
wani"
Cikin haɗa baki suka dinga faɗin "An gama oga, gobe
akwai ƙaramin yaƙi"
misalin ƙarfe sha ɗaya da rabi na safe, a sannu take tafiya
a cikin unguwar, tana duba kwatancen da barrister Habib ya tura mata.
Kasa ganewa tayi, ta tsaya a wurin wani mai kanti, ta sayi
ruwa ta sha, kuma tambaye shi.
Tana tsaye tana duba wayarta a cikin shagon provision ɗin,
wani matashi ya shigo, suka gaisa da mai kantin ya ce "Bani ƙulli biyu da
ruwa uku"
Mai kantin ya ce "Amma ka san ina binka sauran kuɗi
ko?"
"Zan biyaka, wannan yawa ne, ka bani na ware mana, caji
zan yi kaina gaba ɗaya babu network,aljihuna kuma yayi gobara"
"Ba zan bayar ba" mai shagon yayi maganar yana
miƙawa Nabila ruwan roba.
Nabila ta din ga satar kallon matashin, yadda bakinsa ya
karkace saboda shaye-shaye take kallo, laɓɓansa duk sun zazzago.
Tayi gyaran murya ta ce "Ɗan uwa ka bashi mana, tun da
ya haɗaka da Allah, in sha Allah zai kawo maka, tun da ya yi alƙawari"
"Rabu da shi, ba ya biyan bashi"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Nawa ne kuɗin nasa?"
Mai kantin ya ce "Dubu biyu nake bin sa"
Ta yi murmushi, tare da ciro kuɗi a jakarta ta ce "Dubu
biyu ai babu yawa, Ga dubu uku, na biya masa kuɗin da ka ke bin sa, ka bashi
wani bashin, ni kuma ka ɗauki kuɗin sayayyata"
Matashin ya kalleta ya ce "Sai kin yi babbar yaya,
Allah ya ƙara arziki"
Ta amsa da "Amin ɗan uwa na gode sosai".
Wani abu ta ga an bashi a nannaɗe a leda, da ruwa ya sake yi
mata godiya, ya fice.
Yana fita ta ce "Malam dan Allah menene wannan ya
saya?"
Mutumin yayi murmushi ya ce "Ƙanwata wiwi ce" waro
ido ta yi ta ce "Wiwi kuma, ka ke sayarwa? Amma na ga kai kamar ba ka sha
ko?"
"Ki yi ƙasa da muryarki mana, ya zamu yi sana'a ce, ni
ba abun da nake sha. ga canjinki"
Cikin mamaki ta ce "Meyasa ka ke sayar da abun da ba ka
sha?"
"Kar ki tsananta bincike malama" yayi maganar yana
haɗe rai. Ta jinjina kai ta ce "To Allah ya taimaka"
Fitowa ta yi daga shagon, ta hangi matashin yayi nisa, ta
rufa masa baya ta bishi da sauri.
"Bawan Allah ɗan tsaya dan Allah" ta ƙarasa tana
haki.
Ya tsaya yana kallonta ya ce "Ya dai?"
"Abu zan tambaye ka, amma kafin nan ka san abun da ka
saya ɗin nan, yana da illa ga lafiyarka?"
Tsayawa yayi yana kallon ta, tayi saurin cewa "Dan
Allah taimako nake nema, wani gida nake nema, amma na kasa gane layin, ko zaka
taimaka mini?"
"Ina ne?"
Ta gaya masa ya ce "Na san gidan, amma ba hanyar ki ka
biyo ba nan"
"Dan Allah kwatanta mini"
"Mu je na kai ki bakin layin"
Ta ce "Yauwa ɗan uwa, dan Allah mu yi wata magana mana,
ka san wani mutum Aminu Viper?" Wani irin burki ya ci yana kallonta.
"Yi haƙuri idan na ɓata maka rai, ɗan uwana ne shi, tun
da Allah ya sa ya bar gidan yari, bamu sake ganinsa ba, kuma na ji an ce
yaransa sun tayar da tarzoma a unguwar nan a satin nan, dan har asibitin da aka
kai waɗanda aka yi wa rauni na je, na zaci zan ganshi, amma ban tarar da shi
ba"
Ya ware mata jajayen idanunsa ya ce "Ki ka ce ɗan
uwanki ne?"
Cikin ƙarfin hali ta ce "Eh, ina da alaƙa da shi"
Ya ce "Na san shi, na kuma san in da yake"
Da sauri ta ce "Dan Allah ka taimaka mini a ina zan
ganshi?"
Ya ƙare mata kallo ya ce, idan kin tashi, ki tambayi ina ne
layin iraƙi a unguwar nan, idan ki ka je akwai wata babbar bishiya zaki ga wasu
a zazzaune a wurin, ki tambaye su, za su nuna miki shi.
Cikin tsananin farin ciki, ta din ga yi masa addu'a. Amma fa
sai dai ta kasa tantance irin kallon da yake yi mata, hakan bai dame ta ba.
Har ƙofar gidan matar ya rakata, ta kuma yi masa godiya, ta
ciro kuɗi ta bashi, sannan ta shiga gidan matar.
Matar ta karɓi Nabila hannu bibbiyu, bayan da Nabilan ta yi
mata bayanin barrister Habib ne ya turo ta.
Ta bawa Nabila duk wani information da take buƙata, tana
gama abun da take yi ta tashi ta ce tafiya za ta yi.
Babu yadda matar ba ta yi da ita ba, a kan ta zauna ta ci
abinci ta yi salla, amma taƙi, ta tashi ta tafi.
Babu tunanin komai, tana fita, ta tambayi wasu yara, ina ne
layin iraƙi?.
Duk sai da suka kalleta, ganin tana mace tana tambayar
wannan layin da ƴan daba suka mayar mallakinsu, abunka da yara, babu tunanin
komai suka sakata a hanya, ta yi musu godiya ta nufi kwatancen.
Tana ta addu'a Allah ya sanya ta dace, duk tana da burin
cikar nata muardin, amma za ta yi farinciki sosai idan aka ce Nasir ne yayi
nasarar kama Aminu, koba komai likkafarsa za ta sake ɗagawa, ta nufi layin ba
tare da ta san idan ta ganshin me za ta ce masa ba.
Layin shiru babu kowa, babu gina-ginan kirki, sai kangwaye,
sai da ta je tsakiyar layin, ta hango wata ƙatuwar bishiya, da mutane.
Kamar ba mace ba, babu razani ko fargaba ta tunkari
bishiyar.
Gaba ɗaya suka zuba mata ido, har ta ƙaraso.
Wiwi kawai suke busawa, ta ɗan tsaya nesa kaɗan da su,
saboda hayaƙi.
"Ina wuninku"
Suka amsa mata da lafiya ƙalau, suna mamakin ganin mace a
wannan chamber.
"Dan Allah tambaya nake yi, wani nake nema, aka yi mini
kwatancen nan aka ce zan sameshi".
Ɗaya daga cikin su ya ce "Waye shi?"
Ta ce "Amm, sunansa Al'amin, amma ana ce masa Aminu
Viper, tun da ya fito daga prison ba mu sake ganinsa ba"
Ɗaya ne ya miƙe tsaye ya ce "Ke, ba ki da hankali, a
dabar madaki ki ke naman wannan ɗan iskan? Kai kan taba, sako su mass su
rakata, tun kan oga ya zo ya saka ayi gunduwa-gunduwa da namanta"
Sai yanzu ta fuskanci shigo-shigo babu zurfi wanda ya yi
mata kwatancen ya yi mata.
Cikin sauri ɗaya ya ce "Meyasa za'a bari ta tafi? Bayan
ka san yau zamu fasa ɗaukar fansa, ta kanta ya kamata mu fara" yayi
maganar yana ƙoƙarin zare makami.
Sai dai tuni suka sako wa Nabila wasu irin murguza-murguzan
karnuka, masu kama da zakuna.
Cikin ihu ta kwasa da gudun tsiya, tana kururwar neman
agaji, saboda yadda take ganin kamar karnukan za su cinyeta ɗanya, sai dai
gudun da suke yi ya wuce hankali, ga takalminta mai tsini ne sosai, dan haka
suka kusa cimma ta.
Babu tsammani ta faɗi, saboda yadda numfashinta ya fara
sama-sama.
Ayshercool.
08081012143
*ƘARFE A
WUTA*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
P8
Ta saka hannu, ta kare kanta, tana jiran su hauta da cizo.
Wani irin fito ya yi wa karnukan, suka juya suka koma da
gudu in da yake.
Matashin nan ne na ɗazu, da ta biyawa bashi, ya kalleta ya
ce "Kin san meyasa na taimake ki?"
Bai jira amsar da za ta bashi ba ya ce "Ba na tunanin
Aminu yana da wata ƴar uwa mace, dan haka ƙarya ki ke yi, akwai wata manufa a
ranki da yasa ki ke nemansa. Sannan ya taɓa yi mini alfarma a lokacin da ya
samu damar da zai kashe ni, kuma kin kyautata mini, alhalin baki sanni ba.
Ɗan daba ba mahaukaci bane ba, shaye-shaye ne yake ruɗa mana
tunani.
Wannan shi ne kaɗan daga abun da ka iya samunki, idan ki ka
cigaba da neman sa, ko bibiyarsa, wannan dabar babu abun da suke buri da fata,
sama da su riga ƴan sanda kama aminu, mace ce ke ki kiyaye kanki, tashi maza ki
tafi gasu can tahowa, idan suka cimmiki babu lallai na iya hana su illata
ki"
Da ƙyar ta tashi, ta yi gaba da sauri, tana cigaba da haki,
adaidaita sahu ta hau, ta yi masa kwatancen in da zai kai ta.
Kasancewar mai rabon shan duka, baya jin bari, suna tafe
tana sauke numfashi, tana tunanin son sanin su kuma waɗan nan me yayi musu suke
son su riga ƴan sanda kama shi, suna ƴan uwansa ƴan daba.
"Ko wani ya kashe musu?" Ta tambayi kanta.
"Yayi kisan kai, kuma a sake shi?
Aikuwa sai na ga ƙwal uwar daka" ta furta a hankali.
Ta so ta gaya wa Nasir, abun da ya faru yau, amma ta san
tsaf zai ce zai zaneta, saboda kasadar da ta yi, dan haka ta bar wa ranta cewa
sai ta samu wata gagarumar nasara, sannan za ta sanar da shi.
Ko sumayya ma ba ta gaya wa ba, tayi shiru da bakinta, sai
dai faɗuwar da tayi, duk ta goge gwiwa.
Haka kurum tausayi, da tunanin makomar rayuwar matasan da ta
gani, a harkar daba da shaye-shayen nan, ya dami zuciyarta ta rasa abun da yake
yi mata daɗi, tana matuƙar son sanin me suke ji a cikin kayan shaye-shaye?
Tabbas da ita wata ce, sai ta taimakawa rayuwar su, ko a mutum goma, idan biyu
suka shiryu ai an rage.
Kamar wadda ta sha kayan maye, haka yau tayi bacci da wuri,
gudun da tayi jikinta duk ciwo yake yi mata, ga numfashi sai wahala yake ba ta.
A wani ɗaki ta ganta, mai duhu sai haske kaɗan a ciki, ga
karnuka duk a cikin ɗakin, sai haushi suke yi mata, an ɗaure su da sarƙa.
Ihu take yi tana neman agaji, amma babu wanda ya san tana
yi.
Can sai ga wani mutum ya shigo, dogo sosai, mai cikar
halitta, ba ta ganin fuskarsa saboda duhu, ya shigo ɗakin bai ce mata uffan ba,
ya danƙo hannunta ya biyo tsakanin karnukan ya fito da ita daga ɗakin, ya ciro
wuƙa zai caka mata a ciki.
Wani uban ihu ta saki, tana kiran sunan Allah, da na Abba da
Nasir.
Tana buɗe ido, ta ga Abba a kanta, da Nasir, da su walida
har da Anty da baba magajiya, ana ta tofa mata addu'a.
Kallonsu take yi ɗaya bayan ɗaya, ta ce "Abba ya na
ganku a nan? Meyafaru?"
Nasir ya ce "Sannu"
Abba ya ce "Arfa ba kya addu'a ko?"
Ta girgiza kai ta ce "Ina yi Abba"
"A'a ba kya yi, da kina addu'a babu yadda za ayi, ki
kwanta kina yi mana ihu da safiyar nan, shiyasa nake hanaki wannan shegen
fentin da bulbula turare a jikinki, dole sheɗanu su yi ayari, su yi ta
binki"
Nasir ya ce "Dan Abba ka yi haƙuri, haryanzu a tsorace
take ma, a bari ta dawo hayyacinta gaba ɗaya, sannu Arfat, ki ɗauro alwala ki
zo ki ɗauki Alqur'ani ki karanta".
Abba ya miƙe ya ce "Aishikenan, zan yi waya da
Barrister, su baki day off, ki samu ki huta"
Nabila ta yi shiru tana rarraba ido, ta san lafiyarta ƙalau,
tsabar tsorata ne da tayi.
Tayi shiru ba ta faɗi abun da ya faru ba, suka din ga yi
mata sannu.
***
YALOKO ƘARAMAR HUKUMAR UNGOGGO
Matashiyar yarinya ce, wadda dudu shekarunta ba su fi goma
sha huɗu ba, take ta iza wuta a cikin murhu, gefe ga garin tuwo a cikin ƙwarya.
Yaro ne ya yi sallama, ta ɗaga kai ta amsa masa.
Ya kalleta ya ce "Ramma ki zo ana sallama"
Ta ɗan waro manyan idanunta ta ce "In ji wa? Ko Habu
ne?"
"A'a, wani ne da mota"
Ta miƙe tsaye ta ce "To mota kuma, ina zuwa?"
Daga tsakar gidan ta ɗan ɗaga murya ta ce "Mama, wai
ana nemana a waje, bari na duba waye, ruwan ya kusa tafasa"
Daga cikin ɗaki matar ta amsa mata da "To ramma,
hanzarta ki dawo, ina son zan fita ne"
Ramma ta amsa da "to" ta ɗauki hijjabinta ta saka
ta fice waje.
Mintuna goma sha biyu ta dawo, jiki a sanyaye.
Mamanta ta kalleta ta ce "Menene?"
"Mama daga Kano ne, wai Anty mai jidda ce gidan da nake
aiki, ta yi waya wai azo a ɗauke ni a mayar da ni, a satin nan za su dawo"
Matar tayi sak ta ce "Da wuri haka, ba cewa aka yi sai
bayan wata guda zaki koma ba?"
Ramma ta ja ta tsaya ta ce "Jikina duk yayi sanyi, wai
yanzu-yanzu zamu tafi"
"To shikenan ai babu wani abu, ki yi haƙuri kin ji
ramma, ni kaina ba a son raina ki ke barin gabana ba, da Allah ya sa mun tara
kuɗin kayan gado, shikenan sai ki dawo ki yi auren ki. Maza mu je na tayaki haɗa
kayan"
Cikin abun da bai fi mintuna arba'in ba, suka haɗa kayan,
suka yi sallama ramma ta bi direba zuwa gidan aikinta da yake Kano.
Yana zaune ya zuba musu ido, suna haɗa masa tea, Walid ya
zuba ƙwayoyi a cikin kofin, sannan ya zuba shayin.
"Ƙara wannan ba zasu ɗauke ni ba"
Walid ya ce "Amma boss, kai fa ka ke hanamu sha a baya,
tayi yawa wallahi".
"Ka ƙara mini na ce" yayi maganar a hasale.
Ya ƙara masa ƙwayoyin yana kallonsa, saboda ƙwayar da suke
yi wa laƙabi da raina kama, a baya sam baya shan irinta, saboda yadda take
bugarwa, wasu lokutan rabi suke ɓallawa su sha, amma ya ce a saka masa kusan
biyar yanzu.
Ya ɗauki kofin ya kai bakinsa zai fara sha, Walid ya ce
"Yau fa madaki za su je ɗaukar fansa cikin unguwa, daga majiya mai ƙarfi
na ji zancen, daga jiya zuwa yau ya ce idan ɗan arearmu ya shiga ta su, a aika
shi kawai"
Ya cigaba da girgiza kofin ba tare da ya yi magana ba, ya
sake yinƙunrin kai kofin bakinsa, walid ya sake cewa "Wata ta je nemanka a
arear, aka kaita dabar madaki, Allah ne ya yi da kwananta a gaba, da kasheta za
su yi"
Duk da cikinsa yayi wata ƙara, jin an ce mace ta na nemansa.
Wace mai tsautsayin ce wannan? Me take nema a wurina?, amma ya maze ya ɗago
jajayen idanunsa ya kalli walid ya ce "Ni kuma?"
Walid ya ce "Ba zan yi maka ƙarya ba, da gaske
nake"
Wani dogon tsaki ya ja, ya dungurar da kofin shayin, ya
tashi ya ce "Ku ɗebo yaran nan na cikin unguwa, da na can wajen gari, ku
sake dira a dabar madaki, ina son ɓarnar da za ku yi ta fi waccan, kar ku basu
damar cutar da kowa. Ko kun gaya wa jami'an tsaro ƙudurinsu, babu abun da za su
yi musu, ku far musu kawai, ka shirya komai, a bawa yaran na shan sigari"
bai jira amsar walid ba ya fice.
Walid ya yi ajiyar zuciya, ɗan mama ya kalle shi ya ce
"Da gaske ka ke wata ta je nemansa, ko kuma ka faɗa ne, dan ka hana shi
shan ƙwayar nan?"
Walid ya ce "Duka, kai da ya sha abun nan, zai iya
mutuwa fa"
Ɗan mama ya ce "Ai rigimar da yake yi kwanan nan, ta
ƙara yawa, sai an ƙara saka masa ido sosai, kashe kansa yake son yi wallahi,
wasu lokutan bana son muke watsewa mu bar shi shikaɗai a gidan nan".
Walid ya girgiza kai ya ce "Ba zai kashe kansa
ba".
"Ya aka yi ka san hakan?"
"Yana da abun da yake son cimma, kawai kayan ne gaba ɗaya
ba sa ɗaukarsa gaba ɗaya yanzu, ka san yana cikin matsananciyar damuwa, duk
kayan cajin nan kansa ba ya ɗauka kamar aljani, amma ina bincikawa, an yi mini
alƙawarin wata zazzafar ƙwaya, daga kudu suke kawota.
Yanzu dai wannan aikin da ya ce , maza-maza ka kira kwangila
a waya, ya haɗa mana yara, a basu kayan caji, zamu fasa ƙofa, ai Madaki shi da ɗaukar
wata fansa a kanmu, sai dai a lahira idan ana yi. Sai mun ga abun da ya turewa
buzu naɗi.
Ɗan mama ya miƙe ya ce "Ok, bari na hanzarta na fara haɗo
su ta arear wajen garin nan".
Walid ya ce "Nima fitar zan yi, wurin liti zani, zan
shiga karɓar balance". Suka fice gaba ɗaya.
Bayan tafiyar su Aminu ya koma cikin ɗakin, ya fara duba in
da walid yake ajiye ƙwayoyi, amma ya dudduba bai gansu ba, ya zazzage ko ina,
amma babu.
Wani irin takaici ya tokare masa ƙirji, ya ja dogon tsaki,
ya ɗaga gefen katifarsa, allurar sa saura kwalba biyu kawai, kuma ya san ba ɗaukarsa
za ta yi ba.
Haka ya zuƙe ta ya yi wa kansa, sai dai kamar kullum, yau ma
ƙirjinsa ne ya fara da zafi, kansa yana juya masa.
Wuƙar da take gefensa yake ta kallo, zuciyarsa na raya masa
abubuwa daban-daban.
Tun da Ramma ta suka isa cikin kano, gidan da take aikatau,
kayanta kawai ta sauke a ɗakinta, ta hau aikace-aikace.
Duk da akwai wata mai aikin, wadda ta girmewa ramma, sosai
da sosai, amma matar gidan ita ta yarjewa ta shiga sashenta, har uwar ɗaka da
na maigidan ta gyara mata, a cewarta ramma ta fi nutsuwa, kuma ba ta taɓa ƴar
aikin da ba ta yi mata sata ba, sai ita.
Matar gidan da ƴaƴanta gaba ɗaya sun tafi dubai hutu,
shiyasa ta sallame ta, ta ce ta je gida ta huta, za su yi wata biyu kafin su
dawo, kuma kwatsam yanzu sati biyu wai dawowa za su yi.
Tana falon matar gidan, tana ta uban aiki, ɗan kwanakin da
aka yi ba a taɓa wurin ba, duk ya yi ƙura.
Ƙofar falon aka shigo, ta tashi da sauri, tana kallon mai
shigowar, dan ba ta yi tsammanin ganin kowa a sashen ba, dai-dai wannan
lokacin.
***
Nabila kuwa kusan kwanaki uku curr, ta kasa nutsuwa da
kwanciyar hankali, da ta kwanta bacci, sai mafarkin karnuka, tayi ta ihu.
Haka Anty da baba magajiya za su danneta, su yi ta shafa
mata man gelo da miski, ta ja bakinta, ta yi shiru, ba ta gaya musu abun da ta
aikata ba.
Yau kuwa gajiya ta yi da zaman gidan, dan baka cikin hijjabi
ta shirya, ta ɗauki ƴar ƙaramar wayarta, ta fito falo.
Umma ta kalleta ta ce "Ke da baki da lafiya, ina zaki
je kuma?"
Nabila ta ce "Wurin aiki, akwai buƙatar in je zan kai
wani bayani ne mai muhimmanci"
"Amma kin gaya masa, kar ya dawo ya tarar kin fita, ya
yi ta faɗa"
"Umma ba daɗewa zan yi ba"
Saudat ta ce "Mhmm, a ma faɗi gaskiya, ko yawon banza
za aje".
Nabila har za ta yi shiru, ta ga idan tayi shiru, za ta
cutu, dan haka ta ce "Idan fitsari banza ne, kaza ma tayi, idan yawon ma
zan tafi, mai lasisi ne akwai riba, ke ki yi mana"
Umma ta kalli Sauda ta ce "Sauda dan Allah ki din ga
jan girmanki, Nabila fa ba sa'arki ba ce ba".
"Na saka da ke ne?"
Umma ta girgiza kai ta ce "A'a baki saka da ni ba,
Allah ya taimaka".
Sumayya tana ta aiki a news room, Nabila ta yi sallama ta
shiga.
Sumayya ta kalleta ta ce "Ina aikin?"
"Ban je ba, ya aikin?"
"Lafiya ƙalau, meyasa ba ki je ba?"
Nabila ta ce "Ke ba wannan ba, yanzu na ga managern ku
a waje muka gaisa"
Sumayya ta ce "Good, ya aka yi?"
"Rahotonki na last week, a kan case ɗin yarinyar nan da
aka yi wa fyaɗe, na ji shiru baku sake cewa komai ba"
Sumayya ta ce "Eh ya aka yi?"
Nabila ta ce "ina da intrest a kai ne, ina son shiga
lamarin, na ji shiru haryanzu babu wani update, na an ɗauki mataki"
Sumayya ta ce "Dalla ware, kamar wata lawyer kirki, you
are not even serious about the job"
Nabila ta ce "Ke ban son wulaƙanci fa, am serious, na
ji an ce wanda yayi laifin mai lasisi ne a garin nan, ina son sanin waye
shi?"
Sumayya ta ce "Nima ban sani ba"
"Kamar yaya ba ki sani ba, am serious fa, da gaske nake
sumayya ina son shiga case ɗin, free of charge na taimaka wa yarinyar, na ji
tausayin su sosai da sosai, yadda uwar take kuka. Kuma daga ji ƴan karkara ne,
masu ƙaramin ƙarfi".
Sumayya ta galla mata harara ta ce "Sannu ambulance
uwar taimako, manyan lawyoyi sun riga sun shiga case ɗin tuni, sai ki ja
gefe"
"Suwaye manyan lawyoyin? Kuma wai waye dan Allah, waye
yayi fyaɗen?"
"Ke! Nifa a rubuce aka bani, karantawa kawai na yi,
hatta recording ɗin da aka saka, na muryar uwar da ƴar, tararwa na yi an yi,
ban ma gansu ba, ban ga suwaye ba, balle na samu wani bayani. Case ma fa
lamarin ya kusa zama a gidan nan, saboda saka muryar matar da aka yi, murtala
ne dama ya yi recording ɗin ya saka, sai da aka kusa korarsu"
Nabila ta ce "To fa, ina murtalan yake?"
Sumayya ta ce "Ba zan nuna ba, kin ganki Nabila"
"Ba wani abu zan yi ba, sonake kawai ya haɗani da matar
da yarinyar".
"Babu fa abun da zaki iya yi a kai, shi ma bai san waye
wanda yayi fyaɗen ba, yarinyar aiki take a gidan, baƙo ne daga zuwa yayi mata.
Dan Allah ki haƙura da case ɗin nan"
A ɗan fusace ta ce "Saboda me?"
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Na ji an ce mutuniyar ki
da jama'arta sun shiga cikin case ɗin, shiyasa na ce ki haƙura"
Nabila ta ce "Wa kenan?"
"Naja bunkure mana, antynki mudubinki, a bar
ƙaunarki" Sumayya ta yi maganar tana dariya.
A take annurin fuskar Nabila ya ɗauke, haka kurum jikinta ya
bata babu gaskiya a lamarin nan.
"Uban mudubin nawa, in dai wannan mudubin ne, Allah ya
fasa shi na huta, wallahi sumayya tun daga abun da matar nan ta yi mini, kawai
nake ji a jikina fuska biyu ce da ita, wadda take kallon jama'a da ita, da kuma
wadda take ɓoyewa"
"To ko ma dai yaya ne, sun shiga case ɗin, kin san kuma
ba zasu tsaya su saurareki ba, mussaman da ta iya yi miki kallon ke ba komai ba
ce ba"
Nabila ta ce "Haka ne, amma rai dai an cire wa fara
kai, lokaci ne, yana nan zuwa da zan bawa duniya mamaki, sai na saka ƙafa na bi
ta kanta ko da halin ƙaƙa"
"To ki bi a hankali, kar ke duniyar ta baki
mamaki"
Nabila ta yi shiru tana tunani.
Sumayya ta ce "Ya dai?"
Tayi guntun tsaki ta ce "Sumy zaman gidanmu babu daɗi,
kamar in gudu wallahi".
"Wai Nabila ba zaki daina wannan iƙirarin ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba zaki gane ba, faɗa muka yi da
Siyama, har da Abba ayi mini faɗa, sauƙinta ɗaya ta ci duka da tukunya na din
ga dukanta"
"Haba Nabila, wannan ai yawa ne, degree holder da
dambe?"
"To yaya ki ke so in yi? In zuba mata ido ta yi mini
duka? Ga uwarsu ta addabi rayuwata, ba ta san yadda ta tsane ni, nima haka na
tsaneta ba, kawaici kawai nake yi mata ba.
Duk uban ƴan matan gidan nan har da zaurawa, babu wanda duka
sanyawa ido sai ni, da na motsa ayi ta janyo mini jafa'in karuwanci" ta
ƙarasa maganar hawaye na cika mata ido.
Sumayya ta ce "No dear, dan Allah ki ƙara jurewa,
lokaci ne da kin yi aure zai wuce"
"Yaushe zan yi auren? Dan Allah ni mummuna ce Sumy? Duk
saurayin da ya zo, sai za a fara maganar aure, sai ya gudu kamar wata jaɓa"
"Nabila kina da matsala, Babu wata halittar Ubangiji
mummuna. Ga ki fara, ga gayu da ilimin addini da na zamani, kina da kwarjinin
da ki ke bawa maza tsoro ne, ai ke kalar manya ce tawan, ba duk kai ba"
Cikin takaici Nabila ta ce "Ba wasu manya, manyan da
suka din ga yaudarata Allah ya isa da ba su aure ni ba suka ɓata mini lokaci,
ni yanzu kowaye ma zan aura na bar musu gidan, ko ba na son shi. Idan ba haka
ba wallahi wataran sai na gudu"
Sumayya ga tausayin Nabila ga dariya, tabbas Nabila akwai
farijinin samari, masu kashe mata kuɗi ma kuwa, sai dai Nabila ta fiye zaɓe-zaɓe,
kuma ba ta fiye ba wa masu sonta da gaskiya muhimmanci ba.
"Ki gudu ki je gidan uban wa? Gaki ga Abba nan maza ki
gudu kar ki fasa"
Sai kuma ta koma rarrashinta, har bayan azahar suna tare,
sai da sumayya ta tashi suka fito tare.
A reception suka tarar da wani mutum, ana ta yi masa
fadanci, yana hura hanci cikin manyan kaya na alfarma, reception ɗin ko ina
security.
Sumayya ta risuna ta gaishe shi ya amsa, amma Nabila ko
kallonsa ba ta yi ba, ta sunkuyar da kai, kamar alla-alla take yi, ta yi ta bar
reception ɗin.
Ɗan rikicewa yayi, ya ƙura mata ido, amma ta basar ba ta
gaishe shi ba, sai so yake yi ta ɗago su haɗa ido, dan ya tabattar da abun da
yake tunani, amma taƙi ta mayar da kanta gefe.
Mamaki ya shiga yi, yana tunanin ko dai gizo idonsa yake yi
masa? Sai dai ya rasa abun yi kafin ya yi wani yinƙuri, sun bar reception ɗin.
Ɗaya daga cikin ma'aikatan ya kalla ya ce "Wannan mai
hijjabin ma'aikaciyar ku ce ita ma?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a sir, she's just a guest
here"
Ya ce "She looks familiar to me, anyway shikenan
dai" yayi gaba.
Cike da takaici Sumayya ta ce "Kina kallon babban mutum
ki ka basar ba ki gaishe shi ba, sai kallonki yake yi, ki ka sani ko shi ne
mijin a dace a daidaita ko ƙyasawa yayi? Da irin wannan halin naki, ki ke korar
samarinki na kirki wallahi".
"Kin fi kowa sanin bani da baƙin hali, wasu lokutan ma
cewa ki ke yi na fiye zaƙewa"
"Haka ne, amma baki kyauta ba, ko dan kallon da yake yi
miki, ai kya kula shi".
Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Ban taɓa jin na tsani
wata halitta a kallon farko da na yi mata a rayuwata ba, sai wannan mutumin.
Gaba ɗaya ya canza mini mood lokaci guda"
Sumayya ta waro ido ta ce "Meyasa kun taɓa haɗuwa ne?
Me yayi miki?"
"No, ina ganin shi a poster dai, ba ɗan majalisa bane?
Ban taɓa jin komai idan na ganshi a poster ba, sai yau da na ganshi ido da ido,
bana fatan Allah ya sa na sake sanya shi a idona. Kin san me? ji nake kamar ya
taɓa cutar da ni, cuta mai muni"
"Arfa, kina hayyacinki kuwa? Tayaya mutumin da ki ka
fara gani yau kawai, ki ce kin tsane shi, ya cutar da ke how?"
"Ban san tayaya ba, amma haka nake ji a raina, kuma da
gaske nake jin hakan"
"Ki daina irin wannan wasan, kar ki saka a din ga yi
miki mummunar fassara"
"Forget, ba zaki gane ba" tayi maganar a daidai
lokacin da suka ƙaraso titi.
Tun ba ayi sallar magariba ba, walid ya riga ya gama tatara
gayyar matasa zauna gari banza, wanda suka yi bankwana da fatan samun
ingantacciyar rayuwa, suka kama makamai da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi.
Kasancewar ba a cikakken hankalinsu suke ba, haka suka
raraka kowa da kowa gida.
Yaran madaki, na ta shirin shiga ɗaya unguwar sare-saren ɗaukar
fansa. Labari ya iske su cewar, yaran Aminu sun rigasu yin dirar mikiya.
Ba su yi zaton gayya guda, yaran aminun suka ɗaukko ba, dan
haka suka fita domin su far musu.
Kamar ba jikin ɗan Adam ba, haka suka din ga sara da sukar
junansu, mutanen unguwa duk suka shiga gida suka rufe.
Aka yi rashin sa'a madaki baya nan, ɗaya daga cikin yaransa,
ya kira shi ya sanar da shi halin da ake ciki.
Nasir yana zaune ya idar da sallar magariba yana lazumi, so
yake ya tambayi ina arfa, ya ga ya jikinta, amma mama na babban falo, ya san da
ya yi hakan, za ta yi masa faɗa, tare da sake gargaɗinsa a kan Nabila.
Wayarsa ce ta fara ringing, ya shafa addu'ar, ya ɗaga tare
da yin sallama.
Da sauri ya tashi tsaye, yana faɗin gashi nan zuwa.
Da sauri ya ɗauki mukullin motarsa, ya fito daga sashin
mama, zuwa falo.
Mama ta kalleshi ta ce "Ya dai? Ya na ganka a
birkice?"
Dai-dai lokacin Nabila ta fito daga ɓangaren ɗakinsu,
hannunta riƙe da kofi, hakan ya sanya ya kasa ba ta amsa.
Zuciyar sa ta tsananta bugawa da sauri, doguwar rigar
material ce a jikinta, kanta babu ɗankwali, tayi parking ɗin gashinta.
Wani irin kyau ta ƙara yi masa.
"DSP yaushe ka dawo?" Tayi maganar tana kallonsa.
"Da magaribar nan, yanzu nake shirin nemanki, in ga ya
jikin naki? Wayarki ba ta shiga"
Anty ta ce "Jiki yayi kyau, har fita tayi"
"Fita kuma, ki ka je ina? Kuma da iznin wa?"
"Dan ubanka ina yi maka magana ka shareni, maganarta ta
fi tawa muhimmanci ne ko yaya?"
A ɗan rikice ya ce "A'a mama, yi haƙuri kiran gaggawa
aka yi mini, faɗan daba ya ƙara ɓarkewa, ƴan daba sun rufe unguwar babu shiga
babu fita, yaran Aminu Viper ne da wani madaki, wai ƴan sandan da aka tura, sun
kasa kwantar da rigimar, kin san am incharge of his case, shi ne zan je na ga
abun yi"
"To ka kula da kyau, ni wannan aikin ya isheni,
shikenan kai ba hutu, ni hankali a tashe".
Ya jinjina kai ya nufi ƙofar fita.
Jin an ambaci Aminu, ya sanya jikin Nabila ya hau tsuma, ya
bishi da gudu ta riƙo rigarsa ta ce "DSP, amma ba kai kaɗai zaka je ba
ko?"
"Eh, na yi waya za a ƙaro mini ƴan sanda"
"Ko mu je tare?"
Ya zaro ido ya ce "Ki yi me?"
Sai kuma ta rasa me za ta ce "Kawai dai ko zan iya
taimakawa"
Murmushi ya yi ya ce "Ba fa kotu ba ce madam"
"Zaki sake shi ya tafi ko kuwa? Wane irin iskanci ne
haka, Meye haka ne Nasir?"
Nabila ta saki rigarsa ta ɗan ɗaga murya ta ce "Take
care, ka tsaya daga nesa nesa dan Allah, kar wani abu ya same ka, kar mu yi
asarar ɗan ƙasa na gari"
Dariya ya yi, ya fita da sauri.
Mama ta hayyayaƙo mata "Wallahi ki kiyayeni da rashin
tarbiyyar ki a kan ɗa na, na gaya miki" mama ta yi maganar tana nuna
Nabila da yatsa.
Nabila a ranta ta ce 'Ni yanzu ba ke ce a gabana ba, akwai
abubuwan da suka fiki muhimmanci a wurina"
Tayi gaba tana kiran lambar sumayya, ta sanar mata da halin
da ake ciki, na rikicin faɗan daba.
Sai dai kamar kullum, faɗa suka yi, sumayya ta gargaɗeta a
kan ta fita sabgar harkar faɗan daban nan.
Nabila tayi zuciya ta kashe wayarta, tare da jin da ita ƴar
jarida ce, sai ta shiga unguwar nan, ta samo rahoto, tana matuƙar jin haushin
yadda sumayya take ɗari-ɗari da gudanar da aikinta, sai dai ko ba dan sumayya
ba, ya zama dole ta taimakawa Nasir, kuma ta taimaki tata career, dan
idan ba ta rama abun da Najar bunkure tayi mata ba, ba zata huce ba dan haka za
ta cigaba da bibiya.
Ayshercool
08081012143
*ƘARFE A WUTA*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
https://whatsapp.com/channel/0029Va5fqs7E50UpMpXolU1T
Masu neman book ɗin ƘARFE A WUTA daga farko, su bi wannan
link ɗin, su yi following channel ɗin, za su samu previous pages👇👇👇.
https://whatsapp.com/channel/0029Va5fqs7E50UpMpXolU1T
9
Har ƙarfe goma na dare, Nabila tana kiran wayar Nasir, domin
jin ko yana lafiya, amma shiru wayarsa ba ta shiga, abu kamar wasa hankalinta
ya fara tashi, zuciyarta ta din ga raya mata wani abun ya same shi.
Da sauri ta tashi ta fita farfajiyar gidan, tana cigaba da
kiran wayarsa.
"Ke Arfa, me ki ke yi a wurin nan da daddare
haka?" Ta ji muryar Abba babu tsammani.
Cikin damuwa ta ce "Abba Yaya bai dawo ba, kiransa aka
yi kwantar da tarzomar faɗan daba, kuma haryanzu bai dawo ba".
Abba ya ce "Yana nan lafiya in sha Allah, da ki ka dawo
nan kina sintiri,ai ba bin sa zaki yi ki nemo shi ba, harkar aiki ne yana nan
lafiya in sha Allah"
Abba yana rufe bakinsa, sai ga ƙarar motar Nasir, yana ta
horn ba ƙaƙƙaitawa, gaba ɗaya suka nufi gate a tare.
Suka tsaye har ya shigo yayi parking ɗin motar.
Ya fito yana kallon su da mamaki ya ce "Abba lafiya na
ganku a nan tsaye?"
Major ya ce "Arfa ce ta fito tana jiran dawowarka, ya
ya aka yi wayarka ba ta shiga gaba ɗaya?"
"Tana cikin mota ne abba, ina ga network ne amma a
kunne take"
Cikin zaƙuwa ta ce "Yaya, komai lafiya dai ko?"
Ya ce "Alhamdilillah, an sha artabu dai, yaran sun
ninka yawan da muke tunani, mun kama wasu, wasu sun gudu, amma mun kama su da
yawa".
Mama ce ta fito ita ma, tare da su sauda, suna yi masa sannu
da zuwa yana amsawa.
Arfa ta ce "Amma dai ba su yi maka rauni ba ko?"
Yayi murmushi ya ce "Da sun yi mini rauni, ai da baki ganni a haka
ba"
Nabila ta ce "To Alhamdilillah, bari na je na kwanta na
yi bacci a nutse, tun da kana lafiya"
Ya ce "Ki bar wayarki a kunne, za mu yi magana"
Ta jinjina masa kai ta bar su a wurin ta tafi, mama kuwa
kamar ta bi Nabila ta naɗa mata duka, ta kalli yadda Nasir yake wani sassanyan
murmushi kamar shashasha, shi ma ji ta yi kamar ta kwaɗe shi da mari, duk
ƙoƙarin da take yi a kansa na nesanta shi da Nabila, abu ya ci tura.
Ta daure ta ce "Shiga ciki ka ci abinci, ka je ka nemi
wuri ka kwanta".
"No na tsaya na ci abinci a hanya ma, sai da safe,
gajiye nake kwanciya zan yi"
Major ya ce "To Allah ya tashemu lafiya" suka
watse.
A galabaice suka koma mafakarsu, domin kuwa sun sha artabu
da jami'an tsaro, duk da an kama wasu, wasu kuma sun tsira da ƙyar. Sai dai sun
yi wa su madaki mummunar ɓarna, dan ma Aminu ya yi musu kashedin babu ruwansu
da cewa za su kashe madaki, saboda ya san hatsabibancinsa.
Yana zaune suka faɗo ɗakin, suna ta mayar da numfashi, jikin
rigar ɗan mama face-face da jini.
Walid ya ce "Boss, an yi aika-aika amma kwaɓarmu ta so
yin ruwa, dan an kama da yawa daga cikin yaran nan da muka gayyato, amma fa
yaran madaki sun yi ɓarna, dan sun taɓa wanda ba su ji ba, ba su gani ba, duk
da mun yi yinƙurin daƙile hakan".
Maimakon Al'amin ya yi magana, kawai ya tashi tsaye ya shaƙo
wuyan walid, ya haɗa shi da bango, ya ware masa idanunsa ya ce "Ina
ƙwayoyin da ka kwashe a nan wurin?"
Cikin takaici walid ya ce "In fita yi maka aiki, in
dawo da ƙyar amma ka shaƙe ni?" Yayi maganar muryarsa na fita da ƙyar
saboda shaƙar da ya yi masa.
"Suna ina na ce?"
"Na kwashe su na fita da su, dan ba zan bari ka kashe
kanka ba, allurar da ka ke yi wa kanka ma, ba abun da take yi maka sai ƙara
maka zafin zuciya"
Fusata yayi da maganar Walid, ya ƙara shaƙe shi, Ɗan mama ya
tashi da sauri yana yi wa Al'amin magiyar ya rabu da Walid.
Walid ya ce "Idan ka kashe ni ma, ba zaka huce ba, ai
na yi maka alƙawarin kawo maka sabuwar ƙwaya, amma wannan kashe kanka zaka yi,
idan ka cigaba da sha, dan ba ta karɓe ka ba." A fusace ya hankaɗe Walid
ƙasa, ya koma ya zauna ya dafe goshinsa.
Wayarsa ce ta yi haske, ya ja wayar yana dubawa.
"Aminu ka daina wannan gangancin da ka ke yi, idan ka
sake shiga hannun mutanen nan, kar ka yi zaton za su hukuntaka da adalci,
dai-dai da abun da doka ta tanada, ka nutsu ka daina wannan mugun wasan, ka
mayar da hankalinka a kan burinka" iya ƙarfin sa ya saka wurin yin jifa da
wayar, ta dagargaje a tsakiyar ɗakin, ya tashi zai fita.
Duk da mugun ciwon da jikin walid yake yi masa, saboda
artabun da suka yi, amma haka ya tashi ya sha gaban Al'amin ya ce "Ina
zaka je ne?"
Hankaɗe Walid yake ƙoƙarin yi, amma walid ya sanya ƙarfin
sa, ya tura shi baya.
"Ka rabu da ni walid, ya zan yi ne? So suke sai na
haukace, waye wannan? Me yake nema da rayuwata? Wace manufarsa ce da su a
kaina? Me kuma suke buƙata yanzu?"
"Easy master"
Cikin ƙaraji ya ce "Na ce kar ka sake kirana da wannan
sunan"
"Sorry boss, na san komai ai, ka kwantar da
hankalinka"
"How? Duk abun da suka yi mini bai ishe su ba, wai yaya
zan yi ne? Kalli idona walid, ba na bacci fa, zuciyata kullum zafi take yi, ba
na iya saka komai a bakina na ji ɗanɗanonsa, ya zan yi ne?"
Walid ya ce na sani, ya amsa yana yi wa ɗan mama inkiya da
idonsa.
Viper ya a sake cewa "Ka san kwana nawa na shafe ba na
bacci? Ba kwanaki ban ba fa kawai, shekaru ne, ba na baccin da ya kai awanni
biyar, ka san me nake ji kuwa?"
Walid ya ce "Ban sani ba, amma na san da yawa daga
abubuwan da ka lissafa"
Jikinsa na tsuma ya ce "Wallahi zuciyata ci take yi da
wuta, ka sani, wallahi idan na riƙe makami sai na yi kisan kai" yayi
maganar yana rintse idanunsa, a lokacin da ruwan allurar da walid yake yi masa,
ya fara ratsa jijiyoyin jikinsa.
A nan take jikinsa ya saki, ya zubawa walid ido.
Walid ya ce "Ko ba zaka yi baccin ba, ka rufe idanunka
master, za ka samu releif" shiru yayi, domin ba zai iya motsa kowacce gaɓa
daga jikinsa ba.
Ɗan mama ya ce "Walid, anya ba zamu yi wani abu a kan
lamarin nan ba kuwa? Ba za a kai shi ya ga likita ba? Kar ya haukace tuburan
fa"
Walid ya ɗora yatsansa a kan laɓɓansa alamar ɗan mama ya yi
shiru.
A hankali al'amin yake buɗe idonsa yana lumshewa, sai dai ya
kasa ƙwaƙwƙwaran motsi.
***
YALOKO ƘARAMAR HUKUMAR TOFA.
Cikin tsananin ƙyanƙyami take ƙarewa ɗan ƙaramin ginin ƙasar
kallo, rabin katangar gidan ta zube, sai ciko aka yi da kara da buhu, aka
rurrufeta.
Abunka da mutumin ƙauye, cikin mutunci da girmamawa, matar
gidan ta karɓeta, tana yi mata sannu da zuwa.
Ta yi mata iso, har cikin ɗakinta, ta ba ta abun zama.
Kamar ta zauna a kan kashi, haka ta ɗan ɗosana ta zauna,
tana kame jikinta ta kalli matar ta ce "Baki gane ni ba ko?"
Matar ta ce "Eh ban waye ki ba"
"Ni ce barrister da na karɓi case ɗin ƴar ki, na zo mu
tattauna ne, in yi magana da ita"
Nan da nan hawaye ya cika idon matar ta ce "Tana banɗaki,
bari ta fito"
rufe bakinta ke da wuya, yarinyar tayi sallama a ɗakinta,
muryarta ƙasa-ƙasa.
Mahaifiyarta ta amsa, barrister kuwa zuba mata ido ta yi,
yadda yarinyar take ɗingishi, take tafiya da ƙyar, har ta zo ta zauna.
Ta kalli uwar ta ce "Kun kaita Asibiti ne?"
Ta ce "A'a, tun dai a can an kaita, maigadin
gidan ne ya kaita, har aka yi mata ɗinki a goshinta, gashi nan in da aka ya ji
mata rauni. Dan Allah baiwar Allah ki taimake mu, kamar yadda Allah ya taimake
ki, a karɓar wa yarinyar nan hakkinta. Saura ƴan kwanaki aurenta, ya lalata
mata rayuwa, idan zancen nan ya fasu a garin nan yaya zan yi?"
Ta kalli yarinyar sannan ta kalli uwar ta ce "Baiwar
Allah kuma hadda halinku, na son abun duniya duk yadda hukumomi ke jan kunne a
kan kai yara aikatau meyasa ba kwa ji? Meyasa zaki kaita aikatau, maimakon
makaranta?, a ƙa'ida fa kema sai an hukunta ki"
Cikin rauni da damuwa ta ce "Baiwar Allah da ina da
yadda zan yi yaushe zan kaita aikatau? An yi garkuwa da mahaifinta an ce mu kai
kuɗin fansa, mun tattara dabbobi da gonaki mun sayar, mun bayar a kai a sako
shi, sun rike ƙanin mahaifinta da ya kai kuɗin, sun haɗa su su duka sun kashe,
gona ɗaya ta rage mana, ita ma wani mutum duk ya tarkata ya ƙwace, wai zai gina
kamfani, an ce za a bamu diyya, gonar miliyan uku an bani dubu bakwai, abun da
zan girka na basu su ci, ita da ƴan uwanta, bani da shi, nima ba cikakkiyar
lafiya ce da ni ba, kuma ita ce babba, makaranta tana zuwa ajinta uku a
sakandare, kuɗin da ake biya na makarantar ba ni da su, ya zan yi?" Tayi
maganar kuka yana ƙwace mata.
"Shikenan ya isa haka?, Amma kuma irin haka kin yi
gaggawa zuwa gidan radiyo ki faɗa, ai wurin jami'an tsaro yakamata ki je".
Maman ramma ta ce "Na je, dan da aka kira ni na je can
birnin asibiti, da ƙyar aka karɓe ta wai ba ɗan sanda, daga can na je wurin ƴan
sanda naga suna nema su cuce ni, wai ƙarya muke yi, babu yadda za ayi a ɗauki
ƴa ta aiki a wannan gidan har ayi mata fyaɗe. Ba ki ga sintirin da na yi ba, na
rasa abun yi shiyasa na kai wurin masu radiyo ko Allah zai saka a taimake
mu"
Ta jinjina kai ta kalli yarinyar ta ce "Ramma
ko?" Ta jinjina kai alamar eh.
"Gaya mini yaya aka yi abun ya faru?" Ta ɗaga kai
ta kalli mahaifiyarta, sai ta fashe da kuka ta kasa magana.
"Hajiya ɗan bamu wuri mu yi magana" babu musu, ta
tashi ta fita ta bar ɗakin.
"Kin ga ki yi shiru ki kwantar da hankalinki, ki yi
mini bayanin yadda abun ya faru, in ga ta ina zamu ɓullowa lamarin"
Shiru ta yi tana tuna yadda lamarin ya kasance.
"Ke!" Ya kirata cikin tsawa, bayan sun haɗa ido da
ya shigo, ƙara razana ta yi, dan ba ta yi zaton wani zai shigo yanzu ba, a
dai-dai wannan lokacin, da ta duƙufa tana ta aiki a falon gidan.
cikin tsuma ta kalleshi ta ce "Na'am".
"Ina masu gidan?" Yayi maganar yana ƙare mata
kallo, matashiyar yarinya ce, da ba ta wuce shekara goma sha huɗu ba, irin
farkon tashen balagar nan, ƙirjinta ya fara tasawa, wannan ne karo na biyu da
yake ganinta a gidan. Tun a ranar farko yake jin wani abu na fuzgar shi a
kanta.
Cikin rawar murya ta ce "Ai ba su dawo ba tukuna,
gyaran gidan dai muke yi".
"Ke kaɗaice a gidan kenan?"
Cikin rashin wayo ta ce "Eh, amma zulai ta je sayo
katin waya, zata dawo, tare muke aiki da ita, wai a satin nan za su dawo".
Yayi wata irin ajiyar zuciya ya ce "Ɗaukko mini ruwa a
kitchen zan sha" ta jinjina kai, ta ajiye duster hannunta, ta tafi da
sauri har da gudu.
Sai dai tana shiga kitchen ɗin, ya bi bayanta, ya mayar da
ƙofa ya rufe.
Turus ta tsaya tana kallonsa, jikinta yana rawa, taga ya
fara tunkaro ta.
Ta ja da baya ta miƙa masa ruwan, amma ya haɗa da hannunta
ya riƙe.
"Dan Allah ka sakeni, in ƙarasa aikina"
Babu tausayi ko imani, ya ce "Nawa aikin zaki fara yi
tukuna, kafin nata"
Ganin akwai alamun ƙarfi a tare da ita, ba zata tsaya ba, ya
sanya ya gaura mata wani lafiyayyen mari. A take hancinta ya fara zubar da
jini.
Ta ƙwala ihu, ya sake buga kanta da cabinet na kitchen,
goshinta ya fashe, nan ma jini ya hau zuba, ga goshi ga hanci, dan haka ta kasa
magana, jikinta ya saki.
Haka ya keta mata haddi, ta hanya mai muni da rashin tausayi
ya tashi ya fice ya barta.
Idonta biyu, amma ta kasa taɓuka komai, ko ɗaga hannunta ta
kasa yi.
Zulai ce ta dawo ta tarar da ita cikin mummunan yanayi, a
rikice ta fita ta kira ɗaya daga cikin masu gadin gidan, suka ɗauke ta suka
kaita Asibiti.
Aka ƙi karɓar su, sai da aka kira matar gidan aka sanar
mata, suka yi magana da likitoci ta waya.
Sai dai duk abun nan, ramma ba ta san ko sunansa ba, balle
ta san ɗan waye shi.
Kafin matar gidan ta dawo, ta aiko a bawa ramma kuɗi, a bata
haƙuri su koma ƙauye, ko warkewa ba ta yi ba aka sallame su, shi ne mamanta ta ɗauke
ta suka tafi gidan radiyo.
Ramma ta bawa barrister labarin komai, tana kuka mai taɓa
zuciya, goshinta ga ɗinkin da aka yi mata a asibiti, ga na ƙasanta da yake
addabarta da raɗaɗi.
Tayi ajiyar zuciya ta ce wa mahaifiyar ramma ta shigo.
Bayan ta shigo ta zauna, ta kalle su ta ce "Baiwar
Allah, dan cuta na san an cutar da ku, amma za ki sake jefa kanki a halaka,
gara ku yarda ayi masalaha.
Babu wata kotu, ko wani alƙali, da zai tsaya miki ya ƙwato
muku hakkinku, saboda yaron nan ɗan gata ne gaba da baya, ubansa suke da ƙasar.
Dan haka ki yi haƙuri, a baku wani abun, ki samu ku sai
abinci, a kuma kaita asibiti, idan ta warware ta koma makaranta.
A take ramma ta fashe da kuka, mahaifiyarta ta ce "Haba
baiwar Allah, shikenan bawa dan talaka ne, ba zai samu adalci ba, kuɗi zasu
ƙare, mutuncin ƴa ta fa? ni gaskiya so nake a karɓa mata hakkinta".
Barrister tayi shiru tana zancen zuci "Ko yaushe
mutumin ƙauye ya wani san ƴancinsa? Da matar nan take zaƙewa?'
"Naira miliyan uku za a baku, kuɗi hannu, ki yi tunani
zan sake dawowa. Idan kuma kun ƙi, zan cire hannuna, duk matakin da uban yaron
ya ɗauka a kanku babu ruwana, ina sake gargaɗinki, babu ke babu magana da wani ɗan
jarida ko makamancin haka, idan kunne ya ji jiki ya tsira" ta ciro kuɗi a
jakarta, ta ajiye musu, ta tashi ta fice.
***
Kamar zai tashi sama, saboda tsananin tashin takaici da
haushi, ya ce "Madaki, wace irin shiririta ce wannan ku ka yi, ta yaya
zaku bari, jami'an tsaro su sake kamaku?"
Cikin muryarsa da ta riga ta fashe irin ta mashaya ya ce
"Kai ka san ba laifinmu ba ne ba, wani banzan bakware aka kawo mana, kai
zaka tsawatar, ka saka a sake su, dan idan babu su babu aikin nan"
"Shikenan, na ji, ka saurare ni da kyau, zuwa hankali
ya riga ya kwanta, mutane sun manta da abun da ya faru watan baya, ina son a
cigaba da yi mini aikina, amma a wannan karon yankin yamma da gari zaku je,
yaron kar ya wuce ɗan shekaru goma zuwa sha biyar, jininsa nake buƙata, a zuba
a babban dam ɗin da yake rarraba ruwa a yankina, tun daga mazaɓata, sai ku kawo
mini ƴan marainan yaron, da hanjinsa. Sa'ar aikin ranar laraba ce bayan
al'muru. Idan kujerata ta cigaba da tabattuwa kuma zaku mora"
Madaki ya ce "Wannan ba zai yi wahala ba, ka huta
kawai, kujerar nan ko an so ko an ƙi, mai hawanta sai bayan ka mutu
honorable"
"Eh, amma ba yanzu zan mutun ba ai, sai an kwana biyu
tukuna, zan aiko maka kuɗi, ayi abun da yakamata larabar tsakiyar wata za ayi,
yaranka kuma za a sake su"
"Sai da kai honorable, ka ci dubu sai ceto"
"Yauwa yayi".
Nabila kuwa sannu aka din ga yi mata a wurin aiki, ana
tambayarta yaya jiki, ta din ga amsa musu da yauwwa.
Ofishin barrister Habib ta je, ta gaya masa yadda suka yi da
matar, da duk abun da ta yi documenting.
Ya karɓa ya duba sannan ya kalleta ya ce "Yayi, amma me
ki ke gani a kan case ɗin? Do you have interest on it?"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Wani case na jiyo, na
wata yarinya da aka yi wa fyaɗe,amma ana ta ɓoye abun, amma na ji an ce su
barrister Naja'atu sun shiga case ɗin, hankalina ya fi karkata a can".
"Wai ke menene haɗinki da wannan naja'atun ne? Ki
kiyayi kanki da lamarin matar nan,tun da sun shiga case ɗin, ki ƙyale su, case ɗin
wannan hajiyar ki tsaya ki mayar da hankali a kai ki yi"
Ta marairaice ta ce "Amma barrister menene aibun hakan,
tun da class mate ɗin ka ce, ka haɗa ni da ita dan Allah, ina son irin
aikace-aikacenta na jin ƙai"
Ya cire medical glass ɗin sa ya kalleta ya ce "Wai ke
meyasa ki ke da taurin kai ne? Ke ma ki kafa naki harkar jin ƙan marasa gatan
mana, dole sai kin zama ita, ke kin san wacece Naja'atu kuwa? Zahirinta ki ka
sani, baki san baɗininta ba, go and work on this case now".
Tsatstsare fuskar Barrister ta yi da kallo, a ranta ta ce
"An zo gaɓar da nake so, hasashena ya tabbata, zan cigaba da matsa ka, har
sai ka amayar da abun da ka ke ɓoye mini"
A fusace ya ce "Ba zaki tashi ba, ki ka tsare ni da
ido?"
Miƙewa tayi tana zumɓura baki, ta ɗauki file ɗin ta fice.
***
Kaiwa yake ta yi yana komowa, a katafaren office ɗin sa,
hannunsa riƙe da waya a kunnesa, yana jiran a ɗauka.
Har fitar da ran za a ɗauka, aka ɗaga. Cikin harshen turanci
ya ce "Haba sir, kai fa nake jira kayan nan su iso, almost 2weeks, ayi ta
ga kaya nan amma shiru, ni na riga na gama clearing road, a yankinmu na arewa,
ka hanzarta na fara jin ƙishin-ƙishin canjin controllers na coustom, bana son a
kawo waɗanda za mu yi ta fama"
Daga cikin wayar mutumin ya ce"Sai fa ka yi haƙuri,
kayan ne ba a gama loda su ba, kuma nima dole sai na gama da controllers ɗinmu
na nan, kuma ka daina ɗaga hankalinka, babu wani wanda ya isa a ƙasar nan, ya
sha abun da ba mu muka dama ba, ranar laraba kaya za su shigo, amma sample ce
allurar, ba a shigo da ita da yawa ba, sai an ga yanayin aikinta tukuna, har da
tablet ma"
"To na ji, amma ka tabattar ranar larabar za su
iso?"
"Ko tantama babu"
"To shikenan, godiya nake"ya katse wayar, cikin
shauƙin irin ribar da zai mayar idan kayan suka tsira.
Zaune take a ƙasaitaccen ɗakin baccinta, jikinta sanye da
riga da wando na nylon, masu sauƙin zafi.
Ta zauna ta nutsu, ta zubawa kayan kan table ɗin gabanta
ido, tana ta saƙe-saƙe a kan ta sha ko kuma kar ta sha.
Kwalabe ne na magunguna, da ƙwayoyi haɗi da allurai.
Wata matashiyar mace ce tayi sallama, ta amsa mata, ta
ƙaraso hannunta riƙe da cup ta na shan wani abu.
"Sweetheart, ya dai na ga kin saka kayan nan a gaba
kina kallo?"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Tunani nake yi da zuciyata,
in sha ko kar in sha"
"So you are going to quit abusing drugs?"
Ta girgiza kai ta ce "Is not that easy dear, jikina is
resisting it, ba sa ɗauka ta sai na sha su in a very high doses, ba na son su
huda ni, a fara ganewa. Mun yi magana da honorable a kan sabuwar allurar da
suka yi order daga Mexico yana ta yi mini yawo da hankali"
"Haba barrister, ke fa ta hannun daman honorable ce, ba
zai yi miki yawo da hankali ba. An samu wani zazzafan malami fa"
Ta ɗago idanunta ta kalleta ta ce "Wow, are you
serious?"
"Yes of course, aikinsa tested and trusted ne, amma
kafin muje a kan buƙatarki, anya ba zaki duba a manyan mutanen nan, mu kai wani
ba, ki yi aure yadda zai zama backup kar abubuwa su zo su taɓarɓare fa, ko ki
samu wani kamar tsohon mijinki, ki aura"
Ta taɓe baki ta ce "Ba zan iya aure ba, na riga na saba
da rayuwar ƴanci, ba zan yi aure in zauna ƙarƙashin wani yana juya ni yadda
yake so ba. Ai tun da na yi joining organization ɗin nan kin san in da na
dosa".
Ta ce "Na sani dear, amma duk da haka, religion da
tradition yana da tasiri sosai da sosai a arewacin najeriya, ba na son wani ya
gano wani lagonki, ayi amfani da shi wurin yaƙarki"
Ta girgiza kai ta ce "Muddin ba zan samu wanda zan
gindayawa sharuɗa ya bi ba, zan iya zamana a haka, i have so many ways to
satisfy my feelings, when i need it, ba dai duk su ake yi wa a auren ba? Kin
san komai ai ke.
Ki saka mana time, mu je wurin mutumin, ba na son sunana ya ɓace,
har sai na cika burina, na kammala aikin da na karɓo a wurin shugabannina, sai
na tabattar da samun daidaituwar jinsi a tsakanin mutanenmu na arewa"
Badi'a ta yi dariya ta ce "Ki huta baby, ki ɗan yi
caji, sai ki kwanta, ko in fita da ke ne?"
"No, ba na son na yi bacci da yawa, zan sake komawa
wurin matar nan, a kan case ɗin ɗan gidan honorable, naga alamar za ta yi
taurin kai, idan taƙi yadda kawai mu bi hanyar da muka saba bi"
"Hmm, talaka akwai ƙi faɗi, kuɗin ne ba zata karɓa ba
kenan? Sa yi biyu babu kuwa"
"Manta da su, idan ki yi waya da journalist ɗin nan,
manta sunasa nake yi, ki tura masa kuɗi, a cigaba da ɓoye wanda ya yi laifin, a
sanarwa da duniya na shiga case ɗin, a sassaka a social media ma, a dai yi
ƙoƙarin ɗauke hankalin mutane daga kai" ta ƙarasa maganar tana tuttula
ruwan maganin da ke cikin wata ƙatuwar kwalba tana lumshe ido.
Yau Abba kamar ya san Nabila so take ta lallaɓa ta fita, ya
zauna a gida bai fita ko ina ba.
Tayi iya tunanin ƙaryar da zata sharara masa, ta fita amma
ta kasa tunawa, dan idan ya tsitiyeta zai gane ƙarya take yi, gashi weekends ne
babu aiki.
Cikin ikon Allah, aka samu tarzomar su madaki da Viper ta ɗan
lafa, saboda an jibge jami'an tsaro a unguwannin.
Nabila har alla-alla take yi, ranar Monday tayi ta fita
aiki, daga nan ta tafi nata wuri.
Ranar Litinin tun sassafe wasu daga cikin iyaye mata, suka
fara sintirin karɓar belin ƴaƴan su da aka kama, a ofishin su DSP Nasir.
Nasir yana zuwa ya tarar da su, an ce musu su jira sai ya
zo.
Tsakanin iyaye da ƴaƴa sai Allah, amma wannan rashin juriyar
yana ɗaya daga abun da yake taka rawa, wurin sake sangarta yaran.
Bayan sun gaisa da su, ya ce "Da farko ina mai baku
haƙuri, domin kuwa ba za mu bayar da belin yaran nan ba, sai mun kai su gaban
alƙali tukuna. Yaran nan ku kanku sun fi ƙarfin ku, ba kwa iya tsawatar musu,
suna barazana ga zaman lafiyar al'umma, dan haka ku yi haƙuri a wannan karon
babu sabo babu ɗaga ƙafa, sai dai na yi muku alƙawarin duk wanda muka kama ba
shi da laifi, zamu sake shi, masu laifi kwai zamu kai gaban hukuma".
Bai tsaya jin mai zasu ce ba, ya wuce office ɗin sa.
Koke-koke wasu daga cikinsu suka fara, yayin da wasu suka
din ga janyo masa jafa'i kala-kala, wai an zalunce su, an rufe musu ƴaƴa.
A cikin office ɗin sa ya karya, kasancewar ya makara, bayan
ya kammala, ya je in da ake tsare da yaran, tare da taimakon wasu daga cikin
jami'an tsaro, ya fara tuhumar su, da ƙoƙarin zurfafa bincike akan su gaya masa
in da viper yake.
Wanda aka ritsa ɗin ana tuhuma ya ce "Wallahi Yallaɓai,
da ne dai kafin ya je prison, na san in da yake, har gidansu na sani, muna yi
masa aiki sosai da sosai, amma tun da ya fito bamu sake ganinsa ba, su Walid da
tarago ne suka san in da yake, tarago kuma madaki ya kashe shi, walid kuma
wallahi shima ba a ganinsa, muna yi masa aiki amma bamu san in da yake
ba".
Nasir ya ce "Ta yaya ku ke karɓar order daga
wurinsa?"
"Randomly, suke zaɓar mutum ɗaya su kai masa takarda,
ko aje a ajiye takardar a in da muke taruwa shikenan"
Nasir zai sake magana, wayarsa ta fara ruri, ya zura hannu a
aljihunsa ya ɗaukkota, ya ɗaga ya saka a kunne, tare da yin sallama.
"Kana ina ne?"
"Na shiga wurin aiki sir"
"Yaran nan da ka kama, ka sake su, kowa ya tafi, kuma
ka janye jami'an tsaron da ka jibge a unguwar" cikin tsananin mamaki ya
tashi tsaye ya ce "Sir, yarane da suke ɓarna fa, har kisan kai aka yi a
ranar, yaya zamu....
"This is an order from higher up Nasir, ka saki yaran
nan, nima umarni aka bani daga sama, Aminu Viper muka ce ka kamo mana, ba yaran
unguwa ba"
Ya taune lips ɗin sa na ƙasa cikin ɗacin rai ya ce
"Amma sir, muna kan binciken wanda suka yi kisan kan ne".
"Ka sake su nace, is an order"
Nasir ya ce "Ok sir, as you wish"ya kashe wayarsa,
jikinsa yana wata irin tsuma, ya tuna yadda a garin kamo yaran, sai da suka
kusa kashe shi, a artabun da suka yi, ga kisan kai, ga miyagun makamai da suka
kama yaran da su, amma an bashi order ya sake su, anya kuwa ana son kawo gyara
da matsalar tsaro a ƙasar nan!?
Ƙarfe a wuta paid book ne, few pages zan bayar free, masu
buƙata za su iya contacting ɗi na, su fara subscribing, miƙaƙƙiyar tafiya ce,
mai cike da sarƙaƙiya da ban al'ajabi.
Ayshercool
08081012143
*ƘARFE A WUTA*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Ku yi following channel ɗin nan, domin samun littatafan
autar manya.
https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h
Masu son ƙarfe a wuta daga farko, ku bi link ɗin nan ku yi
joining channel ɗin
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
10
Gaba ɗaya zuciyarsa ta cunkushe, ya rasa me ma Yakamata
yayi.
Ya daɗe a zaune kafin ya tashi ya fita reception ɗin.
Sai dai yana zuwa ya tarar da wani mutum a tsaye, baƙi ƙirin
da shi, ya ɗaura ɗan kwali a kansa, ga wasu wulaƙantattun kaya a jikinsa kamar
mahaukaci, idanuwansa jawur kamar an rina masa.
Nasir ya ce "Lafiya kuwa? Wannan fa?"
Ya dube shi ya ce "Kai ne Nasir ko?" Yayi maganar
yana shagiɗe kafaɗa irin na cikakkun mashaya.
Nasir ya ce "Ya aka yi?".
"Na san ka samu saƙon ka sakar mini yarana, na zo na
tafi da su ne"
Wani irin ƙululun takaici ya tokare zuciyar Nasir, yayi
ajiyar zuciya ya ce "Kai ne wa?".
Yayi wani irin ihu, ya jinjina kai ya ce "Madaki nake,
gumbar dutse, na san ko bamu yi gaba da gaba da kai ba, ka san labarina, ina
son wannan ya zama gargaɗina da kai na farko na ƙarshe, babu kai babu shiga
harkata da yarana, idan ba haka ba" Nasir ya tsare shi da ido, ban da
lalacewa ace ɗan ta'adda ne zai shigo har office yana yi wa jami'in tsaro
kashedi, saboda wasu masu faɗa a ji sun tsaya masa.
Yayi murmushi mai ciwo ya ce sergent Iliya, ka fito da yaran
nan gaba ɗayansu"
Ya amsa masa da "Ok sir"
Nasir ya zagaya, ya kama gefen rigar madaki, suka fita waje,
ya kalle shi ya ce "Wanene Aminu? Ina zan same shi?"
Madaki ya ce "Wane Aminun?"
"Viper, na san ka san shi, tun da an ce abokin
rigimarka ne"
Madaki ya buɗe wawaken bakinsa, da wiwi duk ta dafar da
haƙoran, laɓaɓansa sun zama manya, sun yi baƙi saboda taba, ya kwashe da dariya
ya ce "Tabbas! Na san shi, ɗan zaki ne, da na yi sake ya girma yake neman
gagarar kundila, dan da na kashe shi tun a wancan shekarun da haka ba ta faru
ba. Nima neman sa nake yi ruwa a jallo, ko a raye ko a mace, dan haka idan ka
same shi, ka sadani da shi.
Sai dai ka bi a hankali wurin neman sa, jami'anku su suka
masa sunan Viper, kumurci ne mai hatsari da idan ya sareka zai kashe ka"
A dai-dai lokacin matasan suka fito harabar station ɗin suna
ihu, suna sarawa madaki, wasu daga cikinsu kuma da ba yaran madaki bane ba suka
fice.
Nasir ba ya tunanin tun da ya fara aiki, ya taɓa cin karo da
abun da ya ɓata masa rai kamar wannan, sai ya ji gaba ɗaya aikin ya fita daga
kansa.
Haka ya ja tawagar matasan suka bar harabar station ɗin suna
iface-iface.
Duk yadda Nabila ta so ta samu damar guduwa, daga wurin aiki
yau, ta kasa samun dama, dan haka ba ta tashi ba sai ƙarfe uku, a lokacin ba ta
da wani kuzarin kirki, babu abun da take buƙata wanda ya wuce ta tafi gida.
Ba ta fi mintuna ashirin da shiga gida ba, Nasir ya dawo.
Bayan sallar la'asar ya kirata a waya, ya ce ta fito yana
son ganinta.
Ba ta ɗauki lokaci ba, ta fita harabar gidan, wajen parking
space akwai fararen kujeru.
A can ta tarar da shi, sai dai yanayinsa ya tabbatar mata
akwai damuwa "DSP, yana ga kamar ranka a ɓace ne?" Tayi maganar tana
zama.
"Damuwa kam akwaita, gagaruma kuwa arfa"
Ta girgiza kai ta ce "Subhanallah, meyafaru
yayana?"
Nasir ya ce "An saki yaran nan fa, da muka kama
shekaranjiya"
Ta waro ido ta ce "Saboda me?"
Ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce "Saboda yaran ƴan siyasa ne,
ina zuwa office aka kira ni daga sama, wai suma umarni aka yi musu, kar in sake
kama yaran, aikin neman Aminu aka saka ni ba wannan ba, na daɗe ba ayi mini
abun da ya ɓata mini rai irin wannan ba, kamar ni wai ni ɗan daba ya kalleni a
cikin kakina, yake yi mini kashedi a office could you imagine. Sai an yi magana
ace ba ma taɓuka komai, an janye jami'an tsaron da aka ajiye a unguwar ma"
Nabila ta daki tebur tana huci, zuciyarta har wani tafasa
take yi ta ce. "Shikenan, da wanda suka kashe, da kwanciyar hankalin
mutanen unguwar, duk ba matsalar su ba ce ba? Personal interest ɗin su ne kawai
a gabansu?"
"Gashi kuwa kina gani, yanzu idan na matsa zasu iya
raba ni da state ɗin nan ma gaba ɗaya, ni kuma bana son barin garin nan saboda,
i don't want to miss you dear"
Kamar za ta yi kuka ta ce "Wallahi Yaya gaba ɗaya aiki
ya fita daga kaina, anya ba haƙura zan yi na kama kasuwanci ba, kai babu daɗi,
sumayya ma haka, nima dan jan wuya ce, idan aka addaba mini ajiye aikin zan yi,
gaba ɗaya ayyukanmu na taimako ne, amma ɓata gari sun yi kane-kane a ciki.
Yanzu menene abun yi?"
Nasir ya ce "Abun yi kawai na mayar da hankali, na yi
musu abun da suka ce, shi kansa wanda suke son a kama ɗin, ina zargin wani abu
ne akansa, ko tsakaninsa da wani ya sanya suke son in kama shi, ban da baka ya
za ayi ace ɗan daba ya gagara kamuwa, alhalin yana cikin garin nan"
Ta ce "To ka ce ba zaka yi ba mana, idan sun matsu su
manyan su kama shi mana"
Yayi dariya cikin takaici ya ce "Ba zai yiwu ba
arfa"
Ta kwantar da murya ta ce "Ka kwantar da hankalinka
yaya, komai lokaci ne, sai dai duk ranar da Allah ya sa muka kai wani matsayi,
mu yi iya yinmu, wurin ganin ana tsage gaskiya duk ɗacinta, lokaci ne ka yi
haƙuri"
Yayi murmushi ya ce "Idan ban yi haƙuri ba, ya zan yi,
dolena ai, na san lokaci ne
Ta ce "Yauwwa, in sha Allah, da ni da kai da sumy, zamu
yi nasara a rayuwar aiki, and zan yi duk iya yi na, na ga ka kama aminu"
Nasir yayi murmushi ya ce "How? Na yi amfani da
techniques ɗina, na kama masu laifi, amma na kasa samunsa, akwai alamun shi ma
yana da masu tsaya masa"
"Mu ma Allah ya tsaya mana, zamu yi yaƙi da duk wani
mai kawo cikas ga aiki da adalci"
Dariya ta bawa Nasir ya ce "Ka ga ƴan ƙasa nagari"
suka yi dariya gaba ɗaya.
***
Sanye yake da gajeren wando, da riga armless baƙa, joint ne
mai kyau sosai da sosai, yanayin matasan da suke shiga suna fita, zai tabattar
da na masu hannu da shuni ne.
Ya ɗora ƙafarsa a kan kujera, yana ta shan shisha, kusa da
shi wasu matasan ne, suma suna ta nasu shaye-shayen.
Sai matashi ɗaya da yake kujerar da take facing ɗin sa, yana
shan sigari, ya kalli Abdul ya ce "Kai Abdul, wai wannan lumshe idon da ka
ke yi, lafiya kuwa?"
Ya sauke ƙafafuwan sa, ya tashi ya gyara zamansa ya yi wani
murmushi ya ce "Ba lafiya ba" yayi maganar yana murmushi.
"Ba lafiya ba kuma ka ke dariya?"
Ya girgiza kai cike da shauƙi ya ce "Na rasa ya zan yi
ne, tun ranar da na samu wata cika, under 18, na sarara na kasa mantawa da ita,
duk matan da nake harkata da su, na kasa samun abun da nake so, kamar yadda na
samu a wurinta. Ashe duk wahalar banza nake yi da nake biyewa manyan yaran
nan"
Saif ya ce "To ka koma mata mana"
Abdul ya ce "I rape her" yayi maganar yana sake
sakin hayaƙi a iska.
"Rape kuma? How?"
Abdul ya ce "I don't know, i was drunk, bai gama sakina
ba kuma, na je gidan aunt maijidda, na tarar da yarinyar ashe ba ta gari ita da
mijinta, duk yadda nake da ƙyanƙyami, nake son manyan mata, amma na kwaɗaitu da
yarinyar nan, tun a ranar farko da na fara ganinta.
I don't know why, but i still need her, na kasa samun yadda
nake so, ita ɗin dai nake son sake kasancewa da ita.
Warin da jikinta yake yi, make me more crazy on her, she was
the first under 18 virgin i mate, i don't think...
Saif ya katse shi ta hanyar cewa "Anya kana hayyacinka
kuwa? Ko ka sha wani abun ne bai sake ka ba, ka ke yi mana surutun banza, ka yi
raping ɗin under 18 old girl, kana vewa warin jikinta make you more crazy are
you well?"
Abdul ya gyara zamansa ya ce "Saif da gaske nake, i
rape her, dad is even working on it, mamanta wai har sun shiga media sun kai
ƙara. I don't care what so ever, i still need her, at any cost".
"Abdul, ka ce dad ɗinka yana ƙoƙarin a rufe case ɗin,
amma kana wannan zancen, ka san idan magana ta shiga media sai a hankali, da
kai da dad ɗin abokan hamayya za su saka ku gaba".
"Abu nawa na yi babu wanda ya fashe? I don't care, you
will help me in nemo yarinyar nan, na ji dad ya ce naja ta shiga case ɗin, kuma
ba wata ba ce ba, she's just maid da gani ka san yar talakawa ce"
Cikin tsoro, Saif ya waro ido ya ce "Wannan barrister?
Aikuwa ka kaɗe Abdul, an ya zaka sha wannan karon?"
Abdul ya kwashe da dariya, har sai da ya janyo hankalin wasu
kansu ya ce "You don't get sense, malam zaka taimake ni na sake nemo
yarinyar nan, itakaɗai ce maganin ƙishirwata" yayi maganar yana cigaba da
ƙyaƙyata dariya.
***
Abun da Nasir ya gaya wa Nabila, ya ƙara azalzalar ta, akan
son samun Viper, ta tabbatar da kama Viper zai iya zama silar cigabansa da ɗaukakar
da take nema.
Sai dai ta kawar da tunanin daga zuciyarta, a lokacin da ta
nutsa, tana kallon hotunan Barrister Naja'atu a social media. Ayyukanta na jin
ƙai, da makamantansu.
Babu wani information da zai gaya mata haƙiƙanin wacece
Naja'atu Bunkure, amma ta barwa zuciyarta lallai akwai wani abu a ƙasa a kan
ta, kuma zata tono shi.
Ranar talata da safe tana shirin fita aiki, sumayya ta
kirata ta ce su haɗu, a in da suke saba haɗuwa, su tafi tare.
Tun da Nabila ta ji haka, ta san akwai wani abu a ƙasa, dan
haka ta amsa mata da to.
***
Walid ne yake ta yi wa Al'amin lissafi, da bayanin ayyukan
da ya saka ayi masa, amma sam hankalinsa baya kan abun da walid ɗin yake faɗa.
"Viper" walid ya kira shi.
Maimakon ya amsa sai ya ce "Haryanzu babu wani labari a
kan masu zuwa gidan malam lawan?"
Walid ya numfasa ya ce "Babu"
Ya ce "Yaran nan gaba ɗaya aka sake su, tare da yaran
madaki ko?"
"Eh, ɗazu duk suka fita, an sake su duka".
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Zuciyata tana bani, kamar so
ake a ɗauke hankalina daga abun da na ƙuduri aniyar yi, ni kuma wallahi muddin
ina numfashi a doron duniya, sai dai ayi mutuwar kasko"
"Amma tayaya haka zai yiwu, alhalin ka kasa sakin
jikinka ka ɗauki ƙaddara, ba ka cin abinci, baka walwala, daga kwanciya, sai
shaye-shaye, sai bayar da umarni, yakamata ka sakawa zuciyarka salama"
"Walid!" Ya ambaci sunansa da ƙarfi.
Ya amsa masa da "Viper"
"Tashi ka fita"
Cikin mamaki ya kalli Viper ya ce "In fita kuma? Ni ɗin
walid ne fa?"
"Eh ka tashi ka fita ka bani wuri"
"Saboda ina bibiyarka, ina yi maka biyayya ka ke neman
ka wulaƙanta ni? Ban da darajar ni ɗan halak ne da ba na manta alkhairi, kai ka
san da tuni na daɗe da barinka"
Aminu ya ce "Idan kai ɗan halak ne, a wannan karon ina
son ka bar ni"
Ya sake kallon viper ya ce "Ni ka ke kora?"
"Eh bana buƙatar sake ganinka"
Walid ya jinjina kai ya ce "Ok, na fahimta" ya
tashi tsam, bai sake cewa komai ba ya fita.
Aminu ya nemi wuri ya kifa kansa, ya dafe saitin ƙirjinsa.
"Ni zaku mayar tamkar ƙwallon ƙafa, ku din ga bugani a
tsakanin ƙafafuwan ku? Kun yi kuskure" ya furta cikin sanyin jiki.
***
Tun da suka haɗu, sumayya na tsuma ta fara bawa Nabila
labari.
"Arfa kin san menene?"
"Faɗi kar ta kashe ki"
"Wannan satin, Honorable Ma'aruf indabo, zai yi program
a gidan rediyon mu, kuma ni manager ya ce zan yi hirar da shi"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Wow congrats baby"
Sumayya ta ce "Nabila, ba abun congratulations bane,
indabo fa, wanda kwanaki aka ci mini mutunci a kansa, da na je mazaɓarsa ban
tarar da ayyukan da aka ce yayi ba, shi ki ka gani a reception fa, da baki
gaishe shi ɗin nan ba".
Nabila ta ɗan waro ido ta ce "Aikuwa sai ki rama,
ki zaƙulo masa tambayoyi na tsitsiyewa, tambayar yaya uwarka ta haifeka, ke har
waccan maganar ma ki ɗaukko, ki tutsuye ɗan bantan uba, ƴan siyasar nan wasu
babu Allah a ran su"
Ta ce "I wish ina da wannan damar, sai dai program ɗin
ba live bane ba, kuma wai rubuto mini tambayoyin da zan yi masa za ayi mini,
kamar dai karantawa zan din ga yi yana bani amsa"
"Ban gane ba, interview zaku yi, ko kuma tattaunawa a
kan cigaban da ya kaiwa mazaɓarsa?".
Sumayya ta ce "Bari kawai nabila, dama murtala ne yake
program ɗin, kuma baya nan aka ce na yi, ina ta murna amma gwiwata tayi sanyi,
kuɗi ya biya sosai za ayi program ɗin, amma a ɓoye campaign kawai zai yi, kin
san zaɓe ya fara ƙaratowa"
Nabila ta ce "Taɓ abun tsiya, toshi da ƙosan rogo,
wannan kawai tambaya da amsa zaku yi, haka yaya Nasir yazo yana gaya mini wai
ƴan daban da ya kama, an kira shi daga sama wai ya sake su, abun babu daɗin ji,
naga alamar sai mun zama jan wuya mun zage a kan ayyukanmu, yanzu dai ki
ƙarasa, zamu yi waya zan shiga wata unguwa, muna da client zan duba wata shaida
ne"
Sumayya ta ce "To shikenan, mu yi waya ko kuma ni sai
in zo gida"
"Ok bye" ta tsayar da mai adaidaita sahun ya tsaya
ta sauka.
Wata adaidaita sahun ta tsayar ta hau, ta tafi unguwar ƙofar
na'isa.
Shagon nan da ta taɓa tsayawa ta sai lemo, nan ta tafi.
Cikin mutuntawa, mai shagon ya karɓeta suka gaisa, da yake
ya gane ta ya ce "Hajjaju kin dawo unguwar ta mu kenan?"
Ta ce "Eh malam, da wata alfarma na zo nema ne"
Ya tattara hankalinsa a kanta ya ce "Ok, ina jin
ki"
Ta ce "Last da na zo, wannan mutumin da na tarar a nan,
na ce masa ya taimaka mini ina son na haɗu da aminu Viper, amma ya kwatanta
mini wani wuri, wai lungun iraƙi, suka kusa kasheni"
Mai shagon ya zare ido ya ce "Viper kuma? Ke menene haɗinki
da shi?"
"Ɗan uwana ne, tun da ya fito daga prison, ban sake
ganinsa ba"
Ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Allah ya rufa miki
asiri da ba su kashe ki ba, kin san yadda suke nemansa ruwa a jallo kuwa? Idan
suka riga jami'an tsaro kama shi, kashe shi za su yi.
Kuma a iya sanina, babu wata mace da Viper yake da alaƙa da
ita, dan haka ki rufawa kanki asiri, ko sunansa kar ki fiye ambata a cikin
unguwar nan"
Nabila ta waiwaya bayanta, babu kowa a wurin, ta ɗebo kuɗi
ta ajiye masa ta ce "Waye shi, ko a taƙaice ne ka gaya mini wanene shi, a
ina zan same shi"
"Ki ka ce ɗan uwanki ne?"
"Ka manta kawai, ni dai ka taimaka mini"
Yayi ajiyar zuciya sannan ya ce "Hajiya, na tabatta
kina da alaƙa da hukuma, gaskiya ina jin tsoro, ina da iyaye da ƙanne, da nake
taimakawa, ko basu saka an kashe ni ba, sai an yi mini illa, muddin na gaya
miki wani abu, daga baya su gano ni na faɗa"
Nabila ta ce "Manta da batun hukuma, ba ni da alaƙa da
ita, kuma babu yadda za ayi na bar wata ƙofa da zata nuna ka gaya mini wani
abu, taimakona zaka yi, idan kuɗin sun yi kaɗan zan ƙara maka wallahi".
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Aminu sun taɓa zama a
unguwar nan, bayan ya zama ɗan daba na iraƙi ake ce masa ko kuma mai dogon
zamani, ƴan sanda ne suka saka masa Viper, saboda rashin tsoronsa, da azabar
kwarjinin da yake da shi, gagararre ne sosai, kuma dealer ne na miyagun
ƙwayoyi. Kuma matasan yaran nan marasa ji, suna jin maganarsa fiye da ta
iyayensu, ba zan iya gaya miki sama da haka ba, amma zan kwatanta miki, in da
zaki samu wani yaronsa, amma dan girman Allah, kar ki bari sunana ya fito, ki
taimaka"
Nabila ta ce "Na yi maka alƙawarin babu wanda zai
ji".
Ya ce "Idan magariba ta yi, ki je tal'udu, hannunki na
hagu, akwai wanda yake zuwa a kan babur ya zauna yana sayar da katin waya, ya
saka facemask.
Ba katin yake sayarwa ba, balance yake karɓa na yaran da
suke rarrabawa tabar wiwi, ƙananan dealolin su, da suke yi sayar musu da katan
maye, yaron Viper ne makusantansa ne sosai, amma dan Allah ki riƙe
alƙawari".
Nabila tayi ajiyar zuciya ta ce "Zan riƙe in sha Allah,
na gode sosai". Ta sake ƙara masa kuɗi.
Fita daga shagon, tana jin kamar ta riski fiye da rabin
matsalarta, idan Allah ya sa ta yi wa DSP hanyar kama aminu, atleast ta taimaka
masa.
Babu tsoro ko tunanin komai, ta ƙallafawa ranta ko ta halin
ƙaƙa za ta yi nasara.
Honorable Ma'aruf indabo, yana kashingiɗe a katafaren falon
sa, hannunsa riƙe da waya ya kara ta a kunnensa, yana jiran a ɗaga.
Muryar madaki ce ya amsa da "Sai mai gida"
Indabo ya numfasa ya ce "An sakar maka yaran?"
"An sake su mai gida"
"Yayi kyau, ka fara ƙoƙarin yi mini aikina, zan shiga
Abuja wannan satin, ka tabattar aikin nan ya kammala kan na dawo"
"Baka da matsala oga"
"Yauwwa, ya batun Aminu?"
Madaki ya ce "Wallahi duk wata kafa da za a bi wurin
samunsu, ya tsosheta, jiya wani ɗan sanda yake tambayata wai idan na san in da
yake"
Da sauri indabo ya tashi zaune ya ce "Waye shi? Meyasa
yake tambayarka?"
"Wallahi ban sani ba, amma dai shi ne ya kama mini
yara, Nasir mai tama na gani a jikin kakinsa"
Indabo ya jinjina kai ya ce "Shikenan zan bincika"
Wata mata ce ta buɗe ƙofar ɗakin, ta shigo, hannunta riƙe da
ƙaramin plate ɗauke da tuffa, ta ƙaraso kusa da shi ta zauna.
"Ya dai na ganka kamar a tsorace?"
Indabo ya ce "Madaki ne ya ce mini wai wani ɗan sanda
yana tambayarsa Aminu jiya, dole na saka a bincika waye".
Cikin takaici ta kalleshi ta ce "Au da kanka ka ke waya
da ɗan daba, abun da ya faru tsakaninka da Aminu bai zame maka izina da darasi
ba, kana ganin yadda ya zame mana barazana, ɗan tahaliki ɗaya ya hanaka
sukuni".
Ya ce "Na san abun da nake yi bilikisu, komai a lissafe
nake yin sa, ai na yi kuskure na farko, ba zan yi na biyu ba. Aminu kuma ina da
tabbacin akwai wani abu a ƙasa, kuma zan kawar da shi, kafin ya buɗe
bakinsa".
Ta ajiye trayn hannunta ta ce "Yanzu ya ake ciki da
maganar Abdul, haryanzu Naja'atu ba ta ce komai ba?"
"Nima ita nake saurare, na fiki damuwa ma da wannan
lamarin, amma dole ki ja masa kunne, na fara gajiya da rashin mutuncin sa, ba
zai ɓata mini siyasata a banza ba, ina ta fafatuka a kai, ya je ya yi abun da
ƴan adawa zasu samu abun faɗa a kai ba".
Ɓata fuska ta yi ta ce "Kai ma ɗanka ne ai, ka ɗauki
matakin da ya dace da shi" ta ƙarasa maganar ta tashi ta bar masa ɗakin.
Yayi guntun tsaki, ya ɗauki wayarsa yana kiran wata lamba.
"Honorable, Allah ya taimake ka"
"P.A ya turo muku list ɗin tambayoyin da zaku yi mini
ko?"
"Eh ya turo, mun kuma bawa mai gabatarwar da ka buƙata
ta dudduba"
Ya jinjina kai ya ce "Ina fatan yarinyar da na ce maka
ce?"
"Eh ita ce Yallaɓai"
Ya ce "Yayi khau, ku turota gidana, ta zo ta yi
recording ɗin a nan, ba zan samu zuwa nan ayi program ɗin ba"
Cikin damuwa manager ya ce "Ina fatan ba wani laifin ta
sake yi ba ranka ya daɗe?"
Indabo ya ce "Da zan hukuntata, tun laifin da ta yi
mini na farko, da tuni na hukunta ta, wani abu mai muhimmancin gaske na gani a
tare da ita, da nake son tabattarwa"
"Subhanallah, dan Allah yallaɓai ka yi haƙuri, idan
laifi ta yi, ina nema mata afuwa ".
"Jamilu, ka turo yarinyar nan gidana, tayi recoding ɗin
program, kar ka sake yi mini musu". Ya kashe wayar ya ajiye.
Yanayin yadda zuciyarta ke tsananta bugawa ne, ya sanya ta
din ga karanto duk addu'ar da ta zo bakinta.
Sai dai ba ta ji za ta iya janye aikata abun da tayi niyya
ba.
Nesa kaɗan da in ya kwatanta mata ta je ta tsaya, sai dai
tun kafin duhun magariba ya gama rufawa, mutumin da aka kwatanta mata ya zo ya
kafa teburinsa na sayar da katin waya, ya nemi wuri ya zauna.
Ta ɗan jima a tsaye, tana kallon sa, sannu a hankali ta fara
tunkarar in da yake zaunen, tana addu'a a zuciyarta har ta ƙarasa in da yake.
Kafin ta yi magana, wani matashi ya rigata ƙarasawa, suka
gaisa ya miƙa kuɗi, aka bashi wata baƙar leda.
Ta tattaro jarumtarta ta yi sallama ta ce "Sannu
malam" ya ɗaga kai ya kalleta, sai dai kamar ya razana da ganinta.
Ta sake cewa "Sannu malam"
"Yauwwa" ya amsa da kakkausar muryar sa, yana
cigaba da ƙare mata kallo.
"Dan Allah kaya nake so" ya ƙare mata kallo daga
sama har ƙasa, ya ce "Wane irin kaya?"
"Irin wanda ka ke sayarwa, amma ni direct nake son na
din ga karɓa"
"Jami'ar tsaro ce ke?" Yayi maganar yana cigaba da
kallonta
Nabila ta ce "Jami'an tsaron ai sun san da zamanka a
nan, ina so ka haɗa ni da Aminu viper ne"
Waro ido yayi ya kalleta ya ce "Ke! Yayi maganar yana
zazzaro mata ido"
Tayi ƙasa da murya ta ce "Kar ka ɗaga murya, ka taimaka
mini, ɗan uwana ne, tun da ya fito daga prison ban sake ganinsa ba"
"Ƙarya ki ke yi wallahi! Ban da ke mace ce, da namiji
ce ke, wallahi sai na ciro hanjinki waje na zubar a titi, bar wurin nan, kafin
na karya ki"
Nabila ta marairaice ta ce "Ba ka da tabbacin ƙary.....
"Ki bar nan, kafin na tsarga ki biyu da makami" ta
ja da baya a hankali, tana kallon sa.
"Ki bar nan na ce" ta juya da ɗan sauri, cikin
tsoron yadda ya hayayyaƙo mata.
Wayarsa ya ɗaukko ya kira Walid yana huci, cikin sa'a ya ɗaga.
Walid ya ce "Maza ya ne?"
"Wata yarinya ta zo neman boss, wai ƴar uwassa ce, anya
ba a fara bibiyar sa ba? Idan ba haka ba, yaya aka yi ta san na sanshi".
Cikin mamaki walid ya ce "Kar dai yarinyar da gagare ya
ce mini ta je dabar madaki neman sa?"
"Ban sani ba, amma zan so ka ganta, ka ga wani abun
mamaki, mai ɗaure kai, dan na kusa guduwa wallahi"
Walid ya ce "Kamar yaya?"
"Ka ga, ina hangota haryanzu, zan bita na yi mata
magana, zan ce ta dawo gobe da safe, zaka ga abun da na gani"
Walid ya ce "Kai liti, ka tabatta ba matsala?"
"Babu, kawai sonake ka ganta"
"Shikenan, idan ka tashi yau, ka shiga area wurin dila,
ya baka balance, idan na zo zan karɓa"
"Sai da kai, an gama"
Nabila na shirin hawa ɗan sahu, ta ji an yi fito a bayanta,
ta waiwaya ta ga liti a tsaye.
"Zo mana" yayi maganar yana kallonta.
Kawai zuciyarta ta raya mata, ko wuƙa zai soka mata.
"Ki zo mana" yayi maganar cikin tsawa.
Cikin rauni ta ce "Dan Allah ba wuƙa zaka soka mini
ba?"
Ya ce "Ke da kashe ki zan yi, kin isa na bari ki bar
wurin nan, shawara na canza, ban san alaƙar ki da shi ba, dan haka zan haɗa
ku"
Da sauri ta ɗan ƙarasa gabansa ta ce "Dan Allah, amma
na ji daɗi na gode sosai da sosai".
"Mu haɗu a nan, gobe ƙarfe biyar na yamma, zan haɗaki
da wanda ya san in da yake, amma wallahi ki ka yi wani abu na rashin gaskiya,
kin san sauran"
Nabila ta ce "Babu wani abu na rashin gaskiya da zan
yi, na gode yayana Allah ya saka da alkhairi"
Ya ce "Ke ki nemawa kanki tsari, da na zama yayanki,
ware ki bar nan"
Hamadala ta yi, tare da jin kamar wata gagarumar nasara tana
tunkarota.
Ƙwas-ƙwas takalminta yake bayar da sauti a kan tiles ɗin
wurin, sai sauri-sauri take yi ta ƙarasa ofishin manager.
Da sallama ta shiga, ya ɗago ya amsa mata, ta ɗan risuna ta
ce "Afuwan sir, na tsaya ƙarasa editing ɗin news ne, shiyasa ban zo
kiranka da wuri ba".
"Bakomai sumayya, sannu da ƙoƙari, ina yabawa ƙoƙarin
ki da himmarki".
Tayi murmushi ta ce "Na gode sir"
"Ina sisternki, young barrister ne? Nabila ko, kwana
biyu ba ta kawo mana ziyara ba"
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Ayyuka ne suka yi mata
yawa, amma ko ɗazu muna tare"
Ya ce "To Allah ya taimaka, yauwwa dama batun program ɗin
nan ne, honorable ya ce ba zai samu zuwa ba, sai dai aje can gidansa ayi
recording program ɗin, dan haka driver zai kai ki, a can badawa gidansa yake,
za a kai ki ranar Friday, sunday zai yi tafiya ki yi recording program ɗin"
Cikin mamaki da sanyin jiki, ta ce "Gidansa kuma sir?
Amma ai yau murtala za su dawo, tun da su maza ne sai su je....
Ya ɗaga mata hannu ya ce "Look sumayya, ya zama dole ki
je, murtala ba zai dawo yau ba, honorable ba wani abun zai yi miki ba, gidan da
yake zaune da iyalansa ne, recording ɗin program kawai zaku yi. Idan kuma ba
zaki yi ba, you know the consequences"
Wata irin nannauyar ajiyar zuciya ta yi, ta ce "Allah
ya kaimu" ta juya a hankali ta fice.
₦500 ne, via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank
Special wanda ba sa son group 1k.
Wanda za su jira document, idan an kammala 1k ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
wannan layin
Sai a tura mini shaidar biya ta
08081012143 ko 07063065680
Ayshercool
08081012143
*ƘARFE A WUTA*
AREWABOOKS: ayshercool7724
Watpad: ayshercool7724
What's app: 08081012143
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
11
Bayanta manager ya bi da kallo, ta bashi tausayi sosai da
sosai, sai dai yana addu'a Allah ya sa kar honorable ya cutar da ita.
Kamar ɓarawo, haka walid ya diro a tsakar gidan, maimakon ya
biyo ta ƙofa, ɗan mama yana zaune yana shan sigari a ɗan tsakar gidan.
Bai kula shi ba, ya wuce ɗakin da viper yake, sai dai ya
duba baya ciki.
Walid ya dawo, ya kalli ɗan mama ya ce "Ina
Viper?"
Ɗan mama yayi dariya ya ce "Har ka gama fushin, ka
dawo?"
Walid ya ce "Kai ka san ba zan iya ba, ƙular da ni yayi
ne, ina yi masa uzuri ne kawai na san kansa ya taɓu, yana ina?"
"Baya nan" ɗan mama ya bashi amsa kai tsaye.
"Kamar yaya? Ina yaje?"
Ɗan mama ya zuƙi sigarinsa sannan ya ce "Ni na isa na
hana shi fita ne? Ko kuma na ce sai ya gaya mini in da za shi? Da dai kai ne
zai iya ɗaga maka ƙafa"
A fusace walid ya ce "Dan me zaka bari ya fita?"
"Au so ka ke na hana shi, ya karya ni, ko ya illata ni,
kaɗaici ne ya dame shi, gidan babu kayan caji, sai na hayaƙi, shi ne ya fice.
Yauwwa dama ina son gaya maka, ka daina kwashe kayan cajin nan gaba ɗaya, idan
wani yayi rawa an bashi kuɗi, kai idan ka yi, na jaki zaka ci a hannunsa
wallahi"
Cikin takaici Walid ya ce "Wai so ka ke sai ya kashe
kansa ne? Kana kallon allurar nan ba ta ɗaukar sa, farar ƙwaya ma fa ba ta yi
masa komai, sai rikita masa ƙwaƙwalwa, idan ya haukace fa?" Walid gani
yayi ɗan mama yayi tsuru-tsuru, yana rarraba ido, dan haka ya waiwaya bayansa,
Al'amin ya gani a tsaye a bayansa.
Bai kula su ba, ya zo ya raɓa walid ya wuce.
"Master"ya kira shi.
Al'amin ya waiwayo, fuskarsa babu annuri, idanunsa sun yi
ja, jijiyoyin kansa suka miƙe ya ce "Me na ce maka a kan kirana da
haka?"
Walid ya ƙarasa kusa da shi, dai-dai kunnensa, ya yi masa raɗa.
Viper ya kalli Walid ya ce "Kasheni ka ke so ka yi
sannan hankalinka ya kwanta ko Walid?"
Walid ya ɗage kafaɗa ya ce "Duk yadda ka gani"
Viper ya hankaɗe shi gefe, ya wuce ɗakinsa, ya rufe ƙofa.
Walid ya bishi ya leƙa ta taga ya ce "Me zaka yi ka
rufe ƙofa?"
Leda ya ciro daga aljihunsa, ya haɗa allura a sirinji, zai
yi wa kansa.
Walid ya ce "Al'amin, ba zaka daina yi wa kanka allurar
nan ba ko? Ba za ta yi maka ba, ka haƙura mana"
Al'amin ya tashi, ya je ya ja tagar ya rufe, ya bar walid a
waje yana surutu.
Sumayya kuwa tun da ta koma gida, mama ta lura da yanayinta,
sai dai ta yi zaton ko gajiyar aiki ce, amma har dare ba ta walwala.
Dan haka ta magantu, ta ce "Ƴar mama, wai ko babu
lafiya ne?"
Sumayya ta ce "A'a lafiyata ƙalau?".
"To faɗa ku ka yi da mutuniyar ne?"
"A'a bamu yi faɗa ba mama"
Ba ta gaza ba ta sake cewa "To ko wurin aikin ne suka
yi miki wani abun?"
Sumayya ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Hajiya mama, bamu yi
faɗa da ƴar ki ba, lafiyata kuma ƙalau, kawai kin san yanayin aikin namu ne,
kayi ta ganin abubuwa na ban tausayi daban-daban".
Mama ta ce "Ai baku ba sumayya, mu ma masu saurare,
kusan kullum cikin zullumin kunna radiyon muke, sai dai ku ƴan jarida ku ne
idonmu, ta bakinku kawai muke jin wasu labaran da jin halin da duniya ke ciki.
Allah dai ya saka muku da alkhairi ya tsare mana ku baki ɗaya, daga ke har
Nabilan aikin tainakon al'umma ku ke yi, Ubangiji Allah ya tsare ku ya kawo
mazajen aure na gari"
Sumayya kamar ta gaya wa mama, abun da aka umarceta a wurin
aiki, amma ta san hankalinta tashi zai yi, zata iya hanata aikin ma, kuma Allah
ne gatansu aikin nan ne gatansu, dan haka ta ja bakinta tayi shiru.
***
Sannu a hankali barrister Naja'atu take bin titin ƙauyen,
sai tsaki take yi saboda yadda garin yake babu kyakkyawar hanyar shiga. Sai
uwar ƙura da kwazazzabai a hanyar.
A hankali ta cigaba da tuƙin har ta ƙarasa in da take son
zuwa.
Sai da ta shiga tsakiyar tsakar gidan, sannan ta yi sallama.
Daga cikin ɗaki a ka amsa sallamar.
Daga baya matar ta fito daga ɗakin, ta ce "Waye?"
Ganin barrister Naja'atu ya sanya ta ɗan saki fuska, ta bata damar shiga ɗakin.
Shame-shame taga rammaa a kwance a kan katifa, ta nemi wuri
ta zauna a gefe.
Ta kalli in da ramma take, sannan ta mayar da idonta kan
maman ta ce "Na dawo ne na ji me kuka tsayar, kuma na ga haryanzu ba ta da
lafiya, anya ramma ba shagwaɓa a wannan lamarin? ya ci ace kin ware ai, da
auren ma aka yi miki ai da kina gidan miji, ko shi ma hakan zaki yi ta yi
masa".
Fashewa da kuka ramma tayi, cikin tsananin baƙin ciki da
takaici.
"Meye kuma na kuka? Wannan abun da ki ke yi, sai mutane
sun san halin da ki ke ciki?"
Cikin sanyin jiki da damuwa, maman ramma ta ce "Tun da
abun nan ya faru, take rashin lafiya, jiya mun je asibitin sha ka tafi, na
garin nan, an ce ciki ne da ita" tayi maganar tana fashewa kuka mai taɓa
zuciya.
Sak Naja'atu tayi, tana kallon su.
Ta numfasa ta ce "Wai wannan kukan na menene ku ke yi
haka, kukan zai yi muku magani ne? Ai wannan ba abun ɗaga hankali bane ba"
Cikin tsananin mamaki, maman rahama take kallon barrister
Naja'atu.
"Baiwar Allah, ce miki na yi fa, an ce mini ciki ne da
ita, wanda ya dubatan ɗan garin nan ne, na san dole maganar nan ta fita, auren
yarinyar nan ba zai yiwu ba, amma kina nuna bakomai bane ba, dan girman Allah a
karɓowa yarinyar nan hakkinta".
Naja'atu ta ce "Baiwar Allah, ko fa an kai yaron nan
kotu yayi prison, abun da zai faru ya riga faru, ba kuma zai goge ba, ɓacin
suna kuma ya riga ya ɓaci.
Matsalar mutanen mu na Arewa, kuna giramama al'ada da addini
a kan ƴancinku. Da in da aka cigaba ne, zata iya haife abun da ke cikinta, idan
tana so, and rise him as a single mother, har ta iya neman ya din ga biyanta
wani abu a kotu, shikenan. But for now, za a iya zubar da cikin ta cigaba da
harkokinta sai me? Is an adolescent crises kowa ma zai iya faruwa da shi".
Cikin mamaki maman ramma ta ce "Baiwar Allah kuma ke
musulma ce?"
"Ƙwarai kuwa, muslma ce ni gaba da baya, mafita nake
baku da shawara. Zan je na yi booking a saka rana a can cikin gari, private
hospital, a cire cikin lafiya ƙalau za a cire shi, yanzu an cigaba nesa ba kusa
ba, ku karɓi kuɗin ku ku rage zafi".
Rma ta fashe da kuka ta ce "Ni mama tsoro nake ji, an
ce mutuwa ake yi, dan Allah ni dai a kai shi wurin alƙali, an ce kina taimako
dan Allah ki taimaka mini, ji nake kamar na mutu na huta, ba a taɓa cikin shege
a garin nan ba sai a kaina, dan Allah ki taimaki rayuwata, wallahi wanda zan
aura ya ji labari ba zai aure ni ba, babu kuma wanda zai ce zai aure ni, cewa
za ayi na zama ƴar iska" ta ƙarasa maganar kamar ta shiɗe.
Barrister Naja'atu ta ce "And so what dan an fasa
aurenki? Zaki iya zama duk abun da ki ke so a rayuwa ko da aure ko babu, waye
ya ce muku aure shi ne limit na rayuwar ƴa mace ne? dan Allah ku fuskanci
rayuwarku, ku daina bari ana cutar ku da addini da al'ada".
Cikin baƙin ciki maman ramma ta ce "Kin ga ya isa
baiwar Allah, idan bawa bai riƙe addini ba haka zai ta rayuwa kamar dabba a
gari, babu ƙa'ida babu hukunci? Wannan ai salon bawa yaro damar ya je yayi zina
ne, ko ni da nake jahila a cikin ƙauyen nan, sam maganarki ba ta da tushe balle
makama a wurina, dan haka ki tashi ki tafi kawai, bana buƙatar taimakon naki,
cuta ce an cuce mu Allah ya isa kawai"
Naja'atu tayi wani irin murmushi ta ce "Ƙarshen abun fa
kenan, ki yi Allah ya isa, na biyo miki da masalaha amma kin ƙi, shikenan idan
kin ƙi ji ai ba kya ƙi gani ba, duk abun da ya biyo baya wannan shi ne abun da
ki ka zaɓa. Sai dai ina sake yi miki gargaɗi da babbar murya, kar ki kuskura ki
sake shiga kafafen watsa labarai ki yi magana, idan kuma ki ka sake, ba
ruwana"
Ta tashi ta sake ajiye musu kuɗi, da complementary card ɗin
ta, ta ce "Akwai lambar wayata a jiki, na san zai iya yi muku amfani, idan
ku ka ga babu sarki sai Allah, domin kuwa barin cikin nan, dai-dai yake da zama
da ajalinta, dan kome zai ɗauka, uban wanda ya aikata laifin, ba zai bari
ba"
Gaba ɗaya bin ta suka yi da kallo, har ta tashi ta fita,
ramma ta fashe da wani irin kuka, tare da jin ƙarshen rayuwarta ya zo.
Mahaifiyarta ta kalleta ta ce "Ki yi haƙuri ramma, ina
tare da ke in sha Allah, na san ko menene ya faru, ni ce sila, da ban tura ki
aikatau ba, da haka ba ta faru ba, amma babu yadda zan yi ne, ki yafe mini dan
Allah" tayi maganar tana kuka ita ma.
Sumayya na ta aiki a kan computer, sai dai hankalinta baya
kan aikin sam, kawai dai tana yi ne, amma ƙasan zuciyarta tsoro da fargabar
dalilin da ya sanya, aka ce ta je gidan honorable Indabo ta yi hira da shi take
ji, idan a kan laifin da ta yi wancan karon ne, ai ta bayar da haƙuri, kuma
lokacin tana farkon zuwa ne.
Sallamar murtala ce, ta dawo da ita hayyacinta, tayi
murmushin yaƙe ta ce "Uncle murtala, saukar yaushe?"
Ya nemi wuri ya zauna ya ce "Agogo sarkin aiki,
yakamata a ƙara miki matsayi a gidan nan fa"
Ta waro ido ta ce "Ni a wa?"
"Ke a ma'aikaciya jajirtacciya mana, wai ya aka yi
mutuniyar take ɗaga miki ƙafa yanzu, lawisa?"
Sumayya ta ce "Hmm, Arfa ce ta ce na daina jin
tsoronta, nima na nuna mata bani da kirki idan ta takura mini, shi ne fa ta
sarara mini".
"Ai matar nan ƴar bala'i ce lamba ɗaya"
Sumayya ta sake tattara nutsuwar sa a kan sa ta ce
"Yauwwa ncle murtala, akwai matar da ka yi recording, ta zo an yi raping
ƴar ta, an ce Barrister Naja'atu ta shiga case ɗin, ina aka tsaya ne?"
Da sauri ya ce "Rufa mini asiri, ni da aka kusa korata
a kan case ɗin, kuma lawyoyi da masu kare hakkin ɗan adam, sun yi casa a kan
case ɗin, sai dai tun da ta shiga cikin lamarin, kowa ya ja da baya"
Sumayya ta ce "Ikon Allah, to ai haryanzu ban ji a ina
aka tsaya ba, wai ɗan waye ne yayi?"
"Taɓ ba zaki ji mutuwar sarki a bakina ba, nima ba ta
faɗa mini ba matar, wai dai yaron ɗan masu kuɗi ne, wai ɗa ne ga wani ɗan
majalisa, ba ta san sunansa ba, a gidan ƙanwar ɗan majalisar yarinyar take
aiki, sun je gidan ta bi ba'asi, an hana su shiga, masu gadin da suka kai
yarinyar asibiti ma duk an canza su"
Cikin tausayawa Sumayya take girgiza kai ta ce
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, shikenan akwai Allah, amma kana ganin
ita Bunkuren za ta yi wani abun kirki a kai? Meyasa ba za a bibiyeta ba, a ji a
ina aka tsaya a case ɗin ba, atleast a gurfanar da shi a kotu mana"
Ya miƙe tsaye ya ce "Lallai ƙanwata baki san ƙasar nan
ba, ai dokar ƙasar nan a kan talaka kawai take aiki, ko ɗan kansila ne, ba za
su hukunta shi ba, ita kanta barrister nan akwai ayar tambaya a kan ta, duk da
a zahiri ta Allah ce, amma yadda ake tsoronta komai tayi, babu wani mai
challenging ɗin ta, akwai wata a ƙasa".
"Gaskiya dai, Allah ya sa mu dace "
Ya amsa mata da Amin.
Nasir yana ta yi wa Nabila bayanin, irin cigaban da yake
samu a neman viper, amma hankalinta ba ya kansa, jin sa kawai take yi, kawai ji
take kamar ta gaya masa halin da ake ciki, amma ta fasa, dan ta san faɗa zai yi
mata.
Hankalinta bai dawo jikinta ba, sai da ta ji ya ce zai je
Abuja.
Ta kalle shi ta ce "Abuja kuma? Me zaka yi?"
"Harkar aiki mana, a ƙalla sati zuwa wasu kwanaki"
Ta kwaɓe fuska ta ce "Har sati?"
"Eh mana, ko in tafi da ke ne?"
Tayi murmushi ta ce "Wace ni, Allah ya bada sa'a"
Kafin ya amsa, wayarsa ce ta fara ringing, ya ɗaga ya saka a
kunnensa, "To" kawai ya ce, ya ajiye wayar ya miƙe ya ce "Bari
na shiga sashen mama, tana nemana"
Nabila ta ce "To"
Agogon hannunta take kallo, yau ko Abba zai jajjagata idan
ya dawo bata nan sai ta fita, dan tuni ta ɓoye takalminta da hijjabinta a
harabar gidan, za ta lallaɓa ta fice, yadda take ji a ranta, ko zata rasa
rayuwarta, ba ta da wani burin da ya wuce ta ga an kama Aminu Viper, domin kuwa
shi ne ƙashin bayan matsalar aikin daba da dillancin miyagun ƙwayoyi, gefe guda
kuma ga dakon burin da take yi.
"Nasiru sau nawa nake gargaɗinka a kan yarinyar nan?
Ban isa in gaya maka magana ka ji ba ko?"
Cikin son kare kai ya ce "Wallahi mama ba abun da ki ke
tunani bane ba, magana muke yi kawai a kan harkar aiki"
"Ni ka yi maganar harkar aikin da ni mana. Wai ma yaya
muka yi da kai, ina alƙawarin mu?"
"Mama dan Allah ki ƙara mini lokaci, sonake na kammala
aikin nan na nutsu, kin san komai lokaci ne"
A hasale ta ce "Zan kwaɗe ka da kai da lokacin,
shekarunka nawa yanzu a duniya, me ka ke nema da Allah bai baka ba? Wato in
saki jiki ka ce wannan shegiyar yarinyar zaka aura ko? To wallahi baka isa ba,
idan ba ka kiyayeni ba, sai dai ka dawo ka tarar na aura maka duk wadda nake
so"
Yayi shiru ya sunkuyar da kai, shi bai ga aibun Arfa ba,
kuma a zuciyarsa ji yake kamar zai samu chance ɗin da zata zama mallakinsa,
rashin gaya mata abun da yake ji game da ita kawai, ba ƙaramin azabtuwa yake yi
ba.
Sanye take da face mask, tana rarraba idonta, ta ga ta ina
zata ganshi.
Liti ya kalli Walid ya ce "Ka ganta ko?"
"Eh, amma bana ganinta sosai, ta rufe fuskarta da
facemask".
Liti ya ce "Bari na yi wa gali magana"
Nabila na tsaye tana rarraba ido, wani matashi ya zo gabanta
ya tsaya, ta ɗaga kai tana kallonsa.
"Ki sauke takunkumin fuskarki".
Cikin tsiwa ta ce "Ban gane ba, ina ruwanka da
ni?"
Wayar hannunsa ya ɗaga mata, da take a kan kira, muryar liti
ta ji.
"Ki sauke takunkumin fuskarki, ko kuma na fasa haɗaku"
Waiwayawa take yi, ta ga ta ina za ta ga liti, ta kalli
matashin ta ce "Da kai zai haɗani?" Ya girgiza mata kai.
Ta din ga waige-waige ko zata ga daga ina liti yake ganinta,
har ya san ta saka facemask. Kafin ta waiwayo, gali ya bar wurin.
Ta sauke facemask ɗin, tana rarraba ido.
Zabura Walid ya yi ya ce "Kai, a ina ka samo wannan
yarinyar?"
"Jiya ta zo ta same ni, wai ita ƴar uwar viper ce, in
taimaka in haɗa su, na shiga area jiya na ɗan yi wuru-wuru, an tabattar mini
ita aka kwatantawa dabar madaki, ta je nemansa, suka sakar mata karnuka, ban
san waye ya kwatanta mata ni ba".
Walid ya ce "Tabbas! Yakamata a haɗa su"
Liti ya ce "Idan kuma haɗin baki ne, ko wata
maƙarƙashiya ce aka shirya masa fa?"
Walid ya ce "Zan kula da komai, amma yakamata su haɗu,
ka ce ta dawo jibi da safe"
"Kana ganin babu matsala?"
"Babu matsala"
Nabila ta fara gajiya da tsayuwa, matashin ɗazu ya sake
dawowa, ya miƙa mata wayar.
Ta karɓa ta yi sallama.
"Ki dawo jibi, ƙarfe sha ɗaya za'a haɗaki da shi".
Kamar Nabila ta yi zagi, dan haushi, amma ta danne ta ce
"To shikenan, Allah ya kaimu" haka ta bar wurin jikinta a sanyaye,
har ta fara tunanin ko dai raina mata hankali kawai zai yi.
Haka ta koma gida, ba tare da ta ji za ta sare ba.
Sumayya daga aiki gidansu Nabila ta je, dan su tattauna a
kan umarnin da ta samu a wurin aiki.
A ɗaki ta tarar da Nabila, tana bacci, dan daga wurin su
liti da ta dawo, kwanciya ta yi.
Tashinta tayi, Nabila ta tashi tana tsaki, saboda yadda ta
tsani a tashe ta tana bacci.
"Ke baccin uban me ki ke yi, bayan azahar, har kin dawo
daga aikin ne?"
Nabila ta yi miƙa ta ce "Ni ban je aikin ba ma"
"Allah ya shirya ki, tashi ki wanko fuskar ki, mu yi
magana akwai case Arfa".
Nabila ta sake mayar da kanta kan fulo ta ce "Faɗi in
ji"
"Dalla ki tashi ki saurare ni"
"Wai ba kunne ne yake ji ba?"
Sumayya ta ce "Kin gane mutumin da muka gani a
reception, ki ka ce kin tsane shi? Ɗan majalisa ne"
"Yanzu takanas ki ka zo gaya mini ɗan majalissa ne? Ai
na sanix
Sumayya ta ce "Dalla ki tsaya ki saurare ni, Honorable
Ma'aruf indabo ne ai"
Nabila ta tashi zaune ta ce "And so?"
"Shi ne wai ni zan yi hira da shi, a madadin murtala,
amma ya yi waya, wai sai dai na je gidansa na yi recoding ɗin program ɗin, shi
ba zai samu zuwa ba"
Nabila ta waro ido ta ce "Saboda me?"
"Wai ba shi da lokaci, Nabila tsoro nake ji, ko zaki
raka ni? Jibi in Allah ya kaimu ne zan je,ba na son rasa aikina, kuma ina
tsoron ya cutar da ni"
Nabila ta ce "Kash, gashi kuma nima zan je wani aikin
ne, da na raka ki aminiya. amma menene a ciki, ke zuwa gidan ɗan majalisa ba
cigabanki bane?"
A raunane Sumayya ta ce "Tsoro nake ji Arfa"
"Sumayya, wani abun fa dole sai mun cire tsoro,
tsoronki yayi yawa, ki yi addu'a, duk abun da ya same ki, gidan radiyon will be
responsible, babu wani abu in sha Allah, ai mun riƙe addu'a"
Yanayin fuskar sumayyan ya tabattar mata da gaske tsoron
take ji.
Sai dai ita ba ta ga abun tsron kamar yadda sumayya ta ɗaga
hankalinta ba.
Nan ta din ga jan ta da hira, har ta saki jikinta suka
cigaba da hira, suka ci abinci tare.
Sai daf da magariba ta raka Sumayya ta tafi gida.
Duk da ƙirjin Arfa na tsananta bugawa, amma ba ta ji zata
iya fasa abun da ta ƙudurta ba, domin kuwa sai ta ga ƙwal uwar daka, jibin nan
za ta shirya ta sake komawa wurin liti.
Paid book ne ₦500 via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank
Sai shaidar biya ta 08081012143
Special 1k, wanda za su jira complete document shi ma 1k ne.
Ayshercool
08081012143
*ƘARFE A WUTA*
Arewabooks : ayshercool7724
Watpad: ayshercool7724
What's app :08081012143
What's app channel
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Paid book ne ₦500 via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda ba ss som group akwai special 1k.
12
Yau ma ba ta sake zani ba, a yanayin da Walid ya iske Viper,
ya sha duk abun da yake tunanin zai sha, ya bugu yayi bacci, amma jikinsa ya
mutu murus, ya kasa baccin.
Idanunsa sun yi jawur, tamkar ana iza wuta, jijiyoyin kansa
sun kumbura, sai buɗe idonsa yake yi yana lumshewa.
Walid ya kalli ɗan mama ya ce "Ɗan mama kai ka ke kawo
masa kayan nan ko?"
"Wallahi bani bane ba, da kansa ya fita ya samo abun
sa, ban kawo masa komai ba".
Ya mayar da idonsa kan Viper ya ce "Ka na ji na?"
Ya ɗaga kai ya kalli Walid alamar eh.
"Wai ba zaka daina fita ba, sai wani abu ya faru
tukuna, ka sake sakamu a matsala?"
Viper ya kalli walid, amma yayi masa shiru.
Shikenan, ina son zamu fita da kai, zan nuna maka wani abu
mai ban mamaki"
Viper ya ce "Walid" ya kira sunansa da dakakkiyar
muryarsa.
Ya amsa da boss "Boss"
"Meyasa ba ka da zuciya ne?" Yayi maganar cikin
maye.
"Na ce bana son sake ganinka"
Walid ya ce "Saboda duk sheɗancina, ɗan halak ne ni. Ya
zaka bi ni mu je?"
"Ba zani ba"
"Yakamata ka fara sanin dalilin da ya sa yarinyar nan
ta matsa a kan lallai sai ta haɗu da kai, ina.....
Cikin hargowa ya ce "Wai wace irin yarinya ce? Meye haɗina
da ita? Wacece ita me take nema a wurina?" yadda ya firgice sai da Walid
ya matsa baya da sauri.
Ya cigaba da cewa "Kowacece, a kawar da ita, bani da
alaƙa ta kusa ko ta nesa da kowace mace, kar ka kuskura kar kuma ka fara, idan
ba haka ba duk abun da ya biyo baya kai ne sila"
Walid ya ce "Na ji na fahimta, easy ka yi haƙuri".
Ya ja tsaki, ya yinƙura dan ya tashi da niyyar ya fita, amma
jiri ya ɗebe shi yayi baya, cikin zafin nama walid ya riƙe shi, ɗan mama ya
taimaka masa, suka kwantar da shi.
Ɗan mama ya ce "Da gaske ka ke wai sai ka haɗa shi da
yarinyar? Kuma akwai alaƙar tsakaninsa da ita?".
Walida ya ce "Shi nake son tabattarwa".
"To ya ce baya so, amma kai ba ka tunanin ko ƙarya take
yi?"
Walid ya ce "Ƙaryar ma take yi, amma yakamata su haɗu"
Ɗan mama ya sake cewa "Sai ka haɗa sun kenan, idan ya
illata ta fa?"
Walid ya ɗora yatsansa a kan leɓensa alamar yayi shiru, dan
ya san Viper idonsa biyu kuma yana jin sa.
***
A office ɗin su Nasir kuwa, hira ta yi hira, ake gaya wa
Nasir, wani ɗan majalisa ne, yayi belin yaran madaki da aka kama, ya saka aka
sake su.
Cikin takaici ya ce "Allah wadaran naka ya lalace, muna
tufka suna warwarewa, mun zama tamkar bayinsu, kullum cikin ganin gazawarmu
ake, alhalin muna iya ƙoƙarinmu"
Suka cigaba da tattaunawa, a kan yadda manyansu kan yi musu
karan tsaye, a kan harkar aiki, da hana ruwa gudu.
Ramma ce take ta murƙususun ciwon ciki, hankalin mahaifiyar
ta a tashe, take ta ba ta jiƙe-jiƙen magunguna, da ta zuƙa kaɗan sai amai, ba
ta iya cin abinci ga wani irin zazzafan zazzaɓi da yake damunta.
Kullum ta na ɗaki, ko tsakar gida idan ba dole ba, bata
fita, saboda yadda labarin cikin nan ya watsu ya cika garin su, dama ta san isa
sai ya bayar da labari, tun da ɗan cikin garinsu ne, ku ma shi ne ya tabattar
da akwai cikin.
Cikin matsananciyar damuwa ta dubi ramma ta ce "Sannu
ramma, na baiwa sani kuɗi ya sayo miki maganin zazzaɓi, kin ga haryanzu babu
shi shiru bai dawo ba".
Cikin kuka ta ce "Mama mutuwa zan yi".
"Ki yi haƙuri ramma, ba zaki mutu ba, kina karya mini
gwiwa, ki daure. Amma anya ba zamu yadda a cire cikin nan ba? saboda rufin
asirinmu, kuma kema ki huta"
Cikin sauri ta girgiza kai ta ce "Mama tsoro nake
ji"
Rasa abun yi ya sanya maman ramma, sakata a gaba suka cigaba
da kuka tare, a zuciyarta ta din ga ja wa Abdul duk wani nau'i na masifa da
jafa'i.
Yau sumayya za ta je program gidan honorable Indabo,
maimakon ta kasance cikin farin ciki, a dalilin zata shiga gidan babban mutum
kamar sa, amma ta gaza nutsuwa da yin farinciki a kan hakan, sai wata irin
fargaba da faɗuwar gaba da take fama da ita.
Sai da ta fara shiga wurin aiki, ta gabatar da ayyukanta na
ranar, sannan ta fara harhaɗa kayan aikin da za ta yi amfani da su.
Gaba ɗaya jikinta babu ƙwari, sai tsananin tsoro da fargaba.
Murtala ne yake ta kwantar mata da hankali, tare da nuna
mata, hakan ma wani cigaba ne, ta sani ko daga program ɗin su daidaita da
honorable ɗin.
Jin sa kawai take yi, tare da murmushin yaƙe.
Har bakin motar gidan radiyon da za a kai ta a ciki, yana
ƙarfafa mata gwiwa, "Sumayya, abun da zan gaya miki shi ne, ki san iyakar
ki a kan program ɗin nan, iya tambayoyin da aka rubuta miki, ki yi masa su zaki
yi masa, kar ki ƙetare su ki jawo wa kanki matsala, ƴan siyasar nan ba kowa ne
mai imani a cikin su ba"
"In sha Allah uncle murtala zan kiyaye, na gode
sosai"
Ta shiga motar ta zauna, direban ya ja suka tafi.
Nabila kuwa tana office tare da barrister Habib, dan yanzu
ya saukko ya fara yaba mata, tana ƙoƙari, ya fuskanci kawai shiririta ce take
damunta a kan aikin, da rashin mayar da hankali.
Tana yi tana kallon agogo, kar ta saɓa lokacin da a ka bata.
"Barrister" ta kira shi, ya ɗago yana sauraren ta.
"Ban sani ba ko kana jin radiyo"
Ya ce "Ina ji mana, meyafaru?"
"Cases da dama, idan suka faru mussaman na masu ƙaramin
ƙarfi, sai in ga barrister bunkure ta tsayawa mutane, wai ita ba dan kuɗi take
aikin ba, dan barrister ce da ba kowa yake iya ɗauka ba, amma tana tsayawa
marasa ƙarfi, ko kuɗi ne suka yi mata yawa?"
Barrister Habib ya girgiza kai ya ce "Ke dai kawai ayi
sha'ani"
"Ka san wani abu kuwa? Akwai wani case da wata mata, ta
je gidan radiyon su sumayya, ta kai koken an yi wa ƴar ta fyaɗe, an dawo mata
da ita daga gidan aiki, ta je gidan da yarinyar take aiki, an hana su shiga, ta
kai wurin ƴan sanda, amma ana ta yi mata yawo da hankali, wai yaron ɗan manya
ne. To na ji an ce ta shiga case ɗin, amma haryanzu babu wani update, ka san da
na so na jarraba sa'a ta, nima na shiga case ɗin ayi da ni, na tausayawa matar
da yarinyar, amma na san ana babbakar giwa, wa zai ji ƙaurin zomo, na san ba za
ta saurare ni ba ma".
Barrister Habib ya tattara hankalinsa a kan Nabila ya ce
"Nabila"
"Na'am"
"Just be yourself, ke dai ki kalli mutum a riga kawai,
Naja'atu kura ce da fatar akuya, ba wata abar burgewa ba ce, da zaka yi koyi da
ita ba. Yarinyar ƴan siyasa ce, babu wani taimakawa masu ƙaramin ƙarfi, ta fake
da wannan ne, dan sunanta ya ƙara fitowa, kuma ya rinjayi ɓarnar da take
aikatawa, ai mun yi karatu da ita tare, ƙwalluwar shegiya ce, ke abun bai baki
mamaki ba, ace kowace shari'a idan ta tsaya maka, zaka yi nasara, ace komai kai
ka ke nasara akwai ayar tambaya ai, dan haka ki yi ta kanki kawai.
Duk da mu ma ɗin wasu lokutan, muna take gaskiya, amma
yanayin aiki ne ya zo da haka, kuma nata ya ƙazanta".
Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Biri yayi kama da
mutum"
Nabila a zuciyarta ta ce "Idan haka ne, ba gaba da gaba
yakamata na yi da ke ba, tona miki asiri zan yi"
Habib ya ce "Ya dai?"
"Nothing sir, jikina ne yayi sanyi kawai na gode sosai
da bayaninka"
Ba tare da neman iznin kowa ba, ta ɗauki jakarta ta fita.
A in da ta tsaya shekaranjiya, nan ta je ta sake tsayawa,
tana fatan Allah ya sa ba jirgata za su yi ba.
Ta shafe a ƙalla awa guda a wurin, har ta sare zata tafi,
matashin da ya kai mata waya, liti yayi mata magana da ita, ta gani a gabanta.
Bai ce mata uffan ba, ya miƙa mata wata takarda.
Sunan wata unguwa ne a jiki,da dai-dai wurin da zata je ta
tsaya, saboda tsabar wauta da rashin hankali, ta yi masa godiya ta tari abun
hawa ta nuna masa takardar.
Mai baburin ya gaya mata kuɗinsa, babu neman ragi, ta afka
ciki ta ce su tafi.
Lissafin da take ma a zuciyarta, na mamakin yadda Naja'atu
tayi mata kallon ƙasƙanci ne, ta wulaƙanta ta alhalin ma ba wata mutuniyar
arziki ba ce.
Babban abun da ta fuskanta, ƙasar nan ba zaka taɓa samun
wasu damarmaki ba, har sai ka taka wani babban matsayi na musamman, ka shahara
sai dai hanyoyin bi a shahara ɗin ne, ko da kasada ko ka kauce hanya.
Ta yi wa kanta alƙawarin, dole za ta bibiyi case ɗin
yarinyar nan, ba naja'atu ba, ko a hannun ƙaramar hukumar bunkuren case ɗin
yake, sai ta bibiya, ai da ƙananan kasada ake babba, ga kuma babban target ɗin
ta, Viper, ta san idan aka kama shi, dole a sara mata, ta shiga cikin mata da
suka kafa tarihi.
Da wannan gurguntaccen tunani na Nabila, mai cike da wauta
da rashin lissafi, suka cigaba da tafiya can ta ce "Malam, wai haryanzu ba
a zo ba?"
"Ba ki taɓa zuwa unguwar ba ne?"
Ta ce "Eh, sai yau zan fara"
Ya ce "saura kaɗan in sha Allah"
Sai dai gabanta ya fara faɗuwa, tun bayan da ta ga sun bar
cikin mutane, sun fita wajen gari. Dai-dai wani gidan gona ya ajiyeta, wurin
duk shuke-shuke, da alama akwai mutane a daf da wurin, amma sai an yi tafiya
kan a tarar da in da suke. Shi kansa titin wurin, babu ababen hawa da suke
kaiwa suna komowa a wurin.
Sai rukunin manya manyan kamfanunnuka a wurin, na shinkafa
da na taki, wurin shiru sai ƙarar injinan da masana'antun ke amfani da su.
Sai da ta sallami mai a daidaita sahun, sannan ta fara
tunanin, to ina ma za ta nufa?
Tsayawa ta yi, tana waige-waige, kawai ta hango wani mutum
ya tunkarota, nan ta fara ja da baya, tana tunanin ko zurawa za ta yi da gudu.
"Mu je" ya ce mata a kausashe.
Ta turje ta ce "Ina?"
"Ba ke ce baƙuwar Viper ba, mu je"
A raunane cike da tsoro ta ce "A'a, ka kirawo shi mu yi
magana a nan, ni dama kaya nake son saya a wurinsa"
Cikin mamaki ya kalleta ya ce "Wani irin kaya?"
"Wanda yake sayarwa" tayi maganar a tsorace tana
kallon Walid.
Ya gyaɗa kai ya ce "Baki san waye shi ba amma? Kin yi
kasada nafi muni, wuce muje kafin na saraki biyu a wurin nan"
Cikin rawar jiki ta ce "Dan Allah ka yi mini rai, ni ka
kirawo shi nan kawai".
"Wallahi zan saɓa ki a ka, wuce mu je"
Salati Nabila ta din ga yi, dan tun da ta yo dakon kasadar
nan, sai yanzu ta ga zunzurutun wautar da ta aikata.
Ya sakata a gaba, suka nausa bayan kamfanunukan.
A can gidan honorable kuwa, yana da office a cikin gidan sa,
in da yake ganawa da mutane na mussaman.
Hankalin sumayya ya ɗan kwanta, bayan da ta ga mutane na
shiga suna fita a gidan, da alama ba shikaɗai ne a gidan ba, kuma gidansa ne da
yake zaune da iyalinsa.
A harabar gidan aka dakatar da wanda suka rako sumayya, aka
ce itakaɗai za ta shiga.
Wani security yayi mata jagora, zuwa wani sashe na gidan, ya
kaita wani falo, ya ce ta jira a nan, ta samu wuri ta zauna, a kan kujera, tana
zaune a falon office ɗin, tana ɗan kalle-kalle, tana jira kamar yadda aka
umarceta.
Cikin office ɗin kuma, Barrister Naja'atu ce suke magana da
honorable.
"Ni fa na yi iya ƙoƙarina, amma da alama mutanen nan,
su na da taurin kai, juyin duniya sun ƙi saduda, sai iƙrarin a karɓar musu
hakkinsu suke yi, ina ga kawai a ɗauki matakin da ya dace a kan ta".
Indabo ya ce "Lallai dama haryanzu akwai masu ƙi faɗi a
talakawa?"
"Akwai su fa, ku kuna gefe, mune muke shiga cikinsu da
rufe bakunanansu a kan ɓarnar da ku ke aikatawa, sai dai kan mage ya fara
wayewa, babban abun damuwar sun gaya mini an tabattar musu tana da ciki"
Yayi saurin ɗaga kai ya kalleta "Ciki kuma? Sau nawa
yayi mata fyaɗen ne?"
Ta ɗage kafaɗa ta ce "Wannan kuma shi za ka tambaya, ba
zan iya cigaba da ɓata lokacina a kan wannan kucakan mutanen ba, ina da abubuwa
masu muhimmanci kawai ayi abun da ya dace".
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Abdul, ban san lokacin da zai
yi hankali ba, ina tsoron lokacin zaɓe, a samu wani ya fito da miyagun
halayensa, in the next couple of years, sonake ya samu ref, ko deputy governor
a tsayar da shi takara, saboda yarjejeniyar da muka yi, da jam'iyya kenan kafin
na yarda na zauna a cikinta, amma al'amarin sa kullum ƙara lalacewa yake
yi"
Barrister Naja'atu ta ce "To, gara dai ka san abun
yi"
"Anyway, shikenan, ki tura mini address ɗin su ita
yarinyar, za ayi abun da aka saba" ta miƙe tsaye ta ce "No
problem"
Ta buɗe ƙofar office ɗin ta fito, kallo ɗaya sumayya ta yi
mata, ta gane ta, saboda yadda Nabila take ɗora hotonta a status ɗin ta a baya.
Cikin son tabattar da abun da Nabila ta gaya mata, a kanta,
ya sanya ta tashi da sauri tana murmushi ta ce "Barrister Naja'atu
Bunkure, baya goya marayu, dama zan ganki ido da ido?" Sumayya ta yi
maganar tana murmushi.
Kamar ta ga kashi, ta yatsuna fuska ta ce "Sannu".
Sumayya ta maze ta ce "Na tsinci dami a kala yau, ni
ƴar jarida ce, a cikin ayyukan da ki ke gudanarwa, zan so yi miki tambaya ɗaya
zuwa biyu, na san masu sauraronmu, za su ji daɗin hakan, kasancewar ki abar so
da koyi ga al'ummar mu, mussaman mata. Dan akwai sister na, die hard fan ɗin ki
ce, ita ma lawyer ce.
Cikin fusata Naja'atu ta ce "Ke saurara mana, daga
ganina sai tsare ni ki hau zuba dan kina ƴar jarida, who permits you to do
that?"
Sumayya ta dake ta ce "No, barrister, ba as ƴar jarida
ba kawai, as a woman and one of your fans, ko ƙorafi ne da ni, ta yaya zan same
ki ki tsaya mini, atleast ko mintuna uku ki bani mana, dan Allah. Na san ƴan
jarida wasu lokutan mu na da zaƙewa amma a duba roƙona" kamar ta zagi
Sumayya, ta tsani baƙin naci irin na ƴan jarida, amma sanin halin su na yanzu
sai su samu abun ɗorarwa ta ɓata mata career ya sanya ta danne ta ce "Ina
jin ki"
Fitowar honorable, ta sanya ta yin shiru, ya kalli sumayya
ya ce "Mu je in da zaki ɗauki program ɗin"
Tana ji tana gani, Naja'atu ta tafi.
Can wani surƙuƙi ya ja ta, da sai da ta fara jin tsoro, sai
dai duk in da suka ratsa, akwai ma'aikata.
Sumayya ta sha mamakin, irin dukiyar da aka yi ɓarna, wurin
gida wannan gida da kamar ba za a mutu a bar shi ba.
Daga ita sai shi a ƙaton falon, mai ɗauke da ɓangarori
daban-daban.
Yayi mata iznin zama, yana ƙureta da idonsa, ta fito da
kayan aikinta, ta fara saitawa, tana ta addu'a a zuciyarta, dan kaɗaicewar nan
ta su kawai, hankalinta a tashe yake.
Nabila kuwa, Walid sakata yayi a gaba, har suka zo ƙofar
wani gida, a can bayan kamfanunukan nan, babu kowa a wurin, ba gida gaba babu a
baya, sai ma wani uban dutse idan ka yi tafiya can gaban gidan, ba ta taɓa
zaton akwai irin wannan wurin a kano ba.
Ya kalleta ya ce ta shiga.
Jikinta yana rawa ta ce ba zata shiga ba, sai dai ya kira wo
mata shi nan waje, wanda har a lokacin idan ta ganshin, ba ta san me za ta ce
masa ba, tsabar fitina ce da son ta ɗaukaka ko ta halin ƙaƙa ya sanya take
wautar.
Wani makami ya zare mata, mai kama da kibiya ya buga mata
tsawa ya ce "Ki shiga na ce" sai a lokacin ta tabattar da ta tafka
babban kuskure, haɗi da wauta mara amfani, idan suka illata ni fa?" Ta
tambayi kanta cikin tashin hankali, haka ta shiga, yana bin ta da wuƙa.
Ɗan mama yana ɗan matsakaicin tsakar gidan, yana wankin
kayansu, jin kukan mace ya sanya shi ɗaga ido, cikin tsananin mamaki.
Sai dai yayi wata irin zabura ya ja da baya, yana bin su da
kallo.
Yana cikin ɗaki a tsaye ƙyam, kamar an gina shi, ya bawa
ƙofar baya, yana kallon bango. Ya sha ya bugu, amma bai samu yadda yake so ba,
tunanin da yake son dainawa ya kasa, dan haka yana tsaye, yana ta nazarin
abubuwa daban-daban a cikin ransa.
Ɗan mama biyo su yayi, yana bin Nabila da kallo.
Turus Nabila ta yi, duk da ba ta ga fuskarsa ba, amma
yanayin suffar jikinsa, sai da ta ji tamkar ta zunduma ihu, kallo ɗaya zaka yi
masa ka san madakin maza ne, ingarman namiji ne, da Allah ya yi shi da tsawo da
kuma kakkauran jiki.
Idonta ya sauka a kan miyagun makaman da suke ɗakin, kamar
za aje yaƙin duniya, gefen katifar da take ɗakin kuma, sirinjai ne, da kwalaban
allura a wurin, sai kuma satchets na magunguna da kwalabe da kwalayen sigari.
Ban da warin sigari, da wani irin ƙauri da ba ta gama tantance ko na menene ba,
babu abun da yake tashi.
Tirƙashi! Ai ko lokacin da aka rufta ta, aka turata dabar
madaki, ba ta ga abun da ya razanata ba, kamar yanzu ba, dan tarin ƴan dabar da
ta tarar na su wasa ne, ba su firgita ta ba, tun da ta samu ƙwarin gwiwar yi
musu magana.
"Boss, ga ta na kawo maka ita, sai ka ji dalilin da ya
sa take nemanka"
Babban abun da ya ƙular da Viper, bai wuce watsi da
umarninsa, da Walid yayi ba, tun da fari ya gargaɗe shi, a kan kawo masa wata
mace, dan ba shi da alaƙa da su, amma ya yi burus da maganar sa.
Kasancewar ya sha sai dai buguwar ta gagara yadda yake so,
ya sanya ƙwayoyin suka taimaka wurin tunzura shi, ya waiwayo a fusace domin ya
sauke wa Walid rashin mutunci.
Sai dai gabansa yayi wata irin mummunar faɗuwa, adadin bugun
zuciyar sa ya ƙaru da sauri da sauri, wani irin gumi ya fara tsatstsafowa ta
kafafen gashin sa, jijiyoyin jikinsa suka kukkumbura.
Shi dai ya san a farke yake, ba iya bacci yake mai nauyin da
zai ɗauke shi, har ya sa shi mafarki yake, balle ya ce mafarki ne, kuma ya san
a hayyacinsa yake, domin kuwa bai yi buguwar da hankalinsa zai gushe ba.
Sai dai a zahiri, sam yanayin sa bai nuna irin halin da ya
shiga ba, dan babu abun da ya canza a tattare da shi, ya zuba mata manya-manyan
jajayen idanunsa.
Tirƙashi! Jin ka ya fi ganinka! Nabila za ta iya cewa, tun
da Allah ya sa ta buɗi ido a duniya, ba ta taɓa ganin mutum mai kwarjini da
razanarwa kamarsa ba, kodayake ai ya wuce ta kira shi kwarjini, sai dai mai ban
tsoro.
Yadda ake faɗarsa a baki kawai, ta ɗauka wani ƙaramin alhaki
ne kawai, sai dai yanzu ta tabattar da ya wuce duk yadda ta yi tsammanin
ganinsa sa.
Ashe waɗanda take gani ƙaryar daba suke yi, ga ɗan daba na
gaske yau ta gani,kamar ta fashe da kuka a cikin zuciyarta ta ce "Na shiga
uku, wani tsautsayin ne ya kawo ni? Daga ni sai su idan suka kashe ni fa? Na
san ko gawata ba za a gani ba, balle ayi mini salla, kamar yadda addini ya
tanada"
So take ta ɗaga ido ta kalle shi, amma abu ya gagara, saboda
daga kallo ɗayan da ta yi masa, ba ta fatan sake yi masa na biyu, duk da
zuciyarta na azalzalar ta, ta sake yin hakan, ba zata iya tantance abun da take
gani a cikin idanuwanta ba, da kuma ma'anar irin kallon da yake yi mata ba.
Ƙoƙarin sake satar kallonsa tayi, amma suka yi ido huɗu,
tayi saurin sunkuyar da kanta ƙasa, saboda mummunar faɗuwar gaban da ta ziyarci
zuciyarta, tabbas cikakken mashayi ne duba da yadda launin idanunsa suke, sai
dai Allah ya yi shi da siffar girma da cikar zati, ya isa a kira shi da
cikakken namiji.
"Shi kuwa wannan meya haɗa shi da aikin daba, a irin
ƙira da Allah ya yi masa, da aikin office ya dace, ko na tsaro, ya ɓata
wayonsa, da ya ƙare a shaye-shaye da daba.
Duk da ta sunkuyar da kanta, a tsakiyar ƙirjinta take jin
kallon da yake yi mata.
Walid ya zagaya saitin kunnensa ya ce "Ka ga abun da
nake gaya maka?"
Jinjina masa kai kawai yayi, taku ɗaya yayi, ba tare da
Nabila ta ankara ba ya danƙi wuyanta.
Ba wani riƙon kirki yayi mata ba, amma idanuwanta suka yo
waje, jikinta ya hau kyarma, tamkar ana kaɗa mata gangi.
Ta saka hannunta ta riƙe nasa, numfashinta na fita da sauri
da sauri, cike da tsoro take ta gwagwarmayar ƙwatar numfashinta, saboda yadda
take jin yana barazanar barin ƙirjinta.
Ba ta ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da ta ji tsini a
cikinta, ga wani irin azababben zafi da ya ratsa fatar cikinta.
Ba ta san bata tsorata ba, sai da ya buɗe baki yayi magana.
"Wacece ke? Me ki ke nema a wurina?!!"
Numfashinsa ya sauka a fuskarta, warin sigari ya daki
hancinta, jikinta ya hau tsuma.
A rikice Walid ya ce "Boss zaka kashe ta fa, ka kalli
abun da ka ke yi"
Bai saurari walid ba, ya sake buga mata tsawa, tare da ƙara
nutsa wuƙar da ya saita a cikinta.
"Viper, jini ya fara zuba daga cikinta, ka dawo
hayyacinka mana" yayi maganar yana ƙoƙarin kai hannu ya ƙwace wuƙar
hannunsa.
Idan ka taɓa ni, kai zan cakawa!" Yayi maganar yana
kallon idon Nabila da suka yo waje, ga jikinta ya saki, sai numfashi da take yi
da kyar.
Buɗe baki tayi, da niyyar ta yi magana, amma jikinta ya
saki, ta daina ganin komai sai duhu.
"Viper kar ka kashe yarinyar nan" Amma kan walid
ya yi wani yinƙuri, Viper ya watsar da ita a wurin, ta faɗi sumammiya.
Ayshercool
08081012143
🔞
*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ
BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*
*Ina masu buƙatar sayen nagartattun kayan magungunan mata,
wanda babu cuta ko algus a ciki, ku yi joining link ɗin nan, domin samun
nagartattun magungunan mata*
https://chat.whatsapp.com/BLqFsnlyNf0B483RhoWq8v
Tsoro Nabila ta fara ba wa Sumayya, "Are you serious?
Nabila da ya kashe ki fa, ko kuma idan ya biyo ki fa? Meyasa ba kya tausayawa
rayuwarki ne?"
"Wallahi nima na yi tunanin hakan, amma ranar biyan
buƙata rai ba a bakin komai yake ba, ai bai san in da nake ba, yadda zan ba wa
DSP wayar nake tunani, ba tare da ya yi mini faɗa a kan dalilin da ya sa na yi
ba, ko tuhumata"
Ta ciro ƙaramar waya mai madannai, ta miƙawa sumayya,
sumayya ta karɓa tana salallami, da sarawa sheɗancin Nabila.
Nabila ta ce "Wayar babu caji, sai na je gida zan
sakata a caji" tayi maganar tana karɓar wayar, ta sakata a aljihun ƙaramin
wandonta na ciki.
Ta sauka daga kan gadon, ta ce "Bari na shiga banɗaki
na fito, na baki labari" ta sauka ta shiga banɗakin da yake cikin ɗakin.
Sumayya tayi ƙuri da ido tana kallon ƙofar da Nabila ta
shiga, tana tunanin yadda abubuwa masu karo da juna suka sakata a tsakiya.
Wayarta ce ta fara ringing a cikin jakarta, ta ɗaukko taga
baƙuwar lamba, ta ɗaga tayi sallama.
Muryar namiji ce ya ce "Ya ku ka yi da ita?"
Sumayya ta ce "Ita wa?"
"Wurin wa ki ka je?" Aka tambayeta.
Ta basar ta ce "Wa ke magana?"
"Ya zama dole fa ki yi aikin da aka saka ki, ko kina so
ko ba kya so, a in da taken nan idan aka so za a iya kasheta, ko a saceta ayi
abun da ake so ta yi, yin abun da aka saka ki ne kawai zai tseratar da rayuwar
ta. Ta haɗu da shi ko kuwa?"
ta sunkuyar da kai ta ce "Wai dan Allah a tunaninka,
tayaya mutumin da ƴan sanda ba su kama ba, ita ta haɗu da shi? Ƙarya kawai take
yi dan ta raina mini hankali, Nabila tana da yawan wasa wasu lokutan, amma
ƙarya take yi"
Nabila ce ta fito daga banɗaki, ta ce "Da wani garan
ake waya? Ko kin yi sabon kamu ne?"
Sumayya ta katse wayar ta ce "Ba wani sabon kamu"
"Sumy, ciwon nan na cikina ne yake yi mini zafi
fa"
Sumayya ta ce "Ai Allah ya ƙara, ni dama shegen duka ya
yi miki, ya kakarya ki "
"Ta Allah ba taki ba muguwa, wallahi sumayya da dukana
yayi, zai iya kashe ni, kin ga ƙirarsa kuwa, kin ga tsawonsa?. Kin ga a yadda
ya din ga kallona, na kasa gane wane irin kallo yake yi mini"
Ta kashingiɗe kanta tana gwadawa Sumayya irin kallon da yake
yi mata.
"Wallahi sumayya ban taɓa ganin ido mai ban tsoron nasa
ba, kin ji muryarsa, daga cikin ƙirjinsa yake fitar da ita, abun tsoro, ya ci
sunansa viper".
Wayar sumayya ta fara vibrating, ta tashi tsaye ta ce
"Ina zuwa"
Ta fita waje ta ɗaga wayar ta ce "Ya aka yi kuma?"
"Idan har ba ta haɗu da shi ba, meye dalilinta na gaya
miki ta haɗu da shi?"
Kamar sumayya za ta yi kuka ta ce "Yayanta ɗan sanda
ne, na gaya muku, a bakinsa da kafafen watsa labarai kawai take jin
sunansa" katse wayar aka yi, ba tare da an sake ce mata komai ba.
Ta koma ɗakin da Nabila take, sai dai abun mamaki taga
Nabilan kamar matacciya.
Da sauri ta ƙarasa ta taɓa ta, ta ga bacci kawai take yi,
daga fitarta zuwa yanzu bai ci ace har ta yi wannan baccin ba.
Message aka turo mata "Idan ki ka bamu bayanin da yake
saɓanin gaskiya, abun zai wuce haka, ya zama dole ki bi duk wani umarni da zamu
baki, muna bibiyarku daga ke har ita"
Sumayya ta ajiye wayar, ta dafe kanta tana salati.
Tsaye yake ƙyam a kan ƙololuwar dutsen, yana kallon yadda
rana ta doshi faɗuwa, gari ya fara duhu sosai, a hankali ya ɗago hannunsa, ya
kalli inhaler da take hannunsa, seretide inhaler ya din ga jujjuyata, yana
sauke ajiyar zuciya.
"Boss" ya ji muryar Walid a bayansa.
Ya zagaya gabansa ya ce "Ka saukko haka dan Allah,
magana nake son mu yi"
"Bana buƙata kowace iri ce"
"Na san na yi maka laifi, amma ka yi haƙuri, zan nemota
duk in da take, kuma zan dawo maka da wayarka ina mai baka haƙuri"
Ko motsawa bai yi ba, balle walid ya saka ran zai yi magana,
daga bisani ya goya hannayensa a bayansa, ya cigaba da kallon rana.
"Amma me ka ke tunani game da yarinyar nan? Anya babu
wani abu a ƙasa da yakamata mu sani?"
A hankali ya juyo, ya dafa kafaɗar Walid, ya matsa da ƙarfi
ya ce "Hakan bai dame ni ba, koma wacece, Ma'aruf , madaki, da kuma wannan
yarinyar da ka kawo, sai na tabattar da na kashe su gaba ɗaya, ko ta halin
ƙaƙa".
"A'a master, mace ce, wataƙila sakata aka yi, dan Allah
ka yi haƙuri, zan yi maka bincike a kanta "
"Idan ka kuma gaya mini wannan sunan, zan hankaɗaka
daga kan dutsen nan"
Walid ya yi murmushi ya ce "Baka girmama sunan ne
viper, idan har ka damu har haka, yakamata ka bawa kanka da lafiyarka kulawa,
ta haka ne zaka yi abun da ka ke so, yanzu ka taimaka ka sakar mini kafaɗata,
wallahi kamar na karye"
Ƙurawa walid ido yayi, Walid ya sunkuyar da kansa, ya san ya
tunzuro zuciyar Viper, sakar masa kafaɗarsa ya wuce shi, ya fara sauka daga kan
dutsen.
Har bayan azahar Nabila ba ta farka ba, su kansu ma'aikatan
asibitin, sun yi mamakin irin baccin da Nabila take yi.
Hankalin sumayya kuwa yayi mummunan tashi, ganin Nabila ba
ta farka ba.
Bayan la'asar sai ga Abba, tare da Salim, wanda ƙani ne ga
Nasir.
A ɗakin da Nabila take suka tarar da Sumayya.
Sumayya ta gaishe su, Abba ya amsa ya ce "Sumayya ke ce
a wurinta?"
Ta jinjina kai ta ce "Eh Abba"
"Ai ni ce mini tayi, ba wani abun damuwa bane, ana gama
yi mata abun da za ayi mata, za ta koma gida, sai da na koma na tarar ba ta
dawo ba"
Sumayya ta ce "Eh, ai ta samu bacci ma".
Idonsa ya sauka a kan gefen rigarta, da take a huje ga jini,
cikin mamaki ya ce "Ya nake ganin jini a jikinta?"
Da sauri Sumayya ta ce "amm, dama wai faɗuwa suka a
adaidaita sahu, shi ne ta ji rauni"
"Amma ni bata gaya mini haka ba ai" yayi maganar
cikin matsananciyar damuwa.
Wata irin miƙa Nabila ta yi, tare da yin salati, duk suka yi
kanta suna yi mata sannu.
Suka din ga jera mata sannu, suna yi mata ya jiki.
Sumayya ta kirawo likkta, ya zo ya ƙara duba Nabila, yayi
rubuce-rubuce a file ɗin ta, ya sallame ta.
Abba ya din ga yi mata faɗan meyasa ba ta gaya masa ta faɗi
a adaidaita sahu ba, ta nunawa likitoci ciwon da ta ji.
Sumayya ta kalleta, suka haɗa ido, sai ta fahimta, dan haka
ta ce "Ai ba wani ciwo bane Abba, mu tafi gida na gaji".
"Kin tabattar babu wani abu da yake yi miki ciwo?"
Ta jinjina kai alamar eh, suka fito zuwa motar Abba, suka
tafi tare da sumayya, su ajiyeta a gida.
Sumayya ta kalli Nabila ta ce "Wai ya aka yi ɗazu daga
fita ta, ki ka fara bacci, kusan awa huɗu ki na bacci?"
Nabila ta ɗan yi shiru tana tunani, ta ce "Wani likita
ne ya shigo yayi mini allura"
"Ba Nurse ba, likita da kansa?"
Nabila ta jinjina kai alamar eh, Sumayya ta yi shiru ba ta
ce komai ba, a zuciyarta, take jinjina tsagwaron rashin imanin honorable
Indabo, kenan idan ba ta yi abun da suke so ba, za su kashe Nabila kenan.
Gabanta ya faɗi, ta kalli Nabila da ta kashingiɗa, tana ta
lumshe ido, alamar baccin bai isheta ba.
Tunani take da wa zata tattauna wannan maganar ne? ko wurin
hukuma ta kai, ba ta da shaida ta zahiri, kuma ta san babu wani mataki da za a
iya ɗauka a kai.
***
Yana kwance a kan gadonsa yana kaɗa ƙafa, hannunsa ɗaya yana
riƙe da waya, ɗaya kuma kan shisha, yana ta fesar da hayaƙi.
"Hello" sautin muryar mace ya fito daga cikin
wayar.
Ya ce "Hello, how far?"
Ta amsa da "Ya aka yi?"
"Mun yi magana da tsoho, ashe kin gano in da yarinyar
nan take?"
"Eh, na gano, sai dai sun ce ba za su karɓi kuɗi ba,
hakkinsu suke nema, dan haka sai ka san yadda zaka yi"
Yayi murmushi ya ce "Ki san yadda za ki yi dai, ai kin
san dolenki ki ɓoye laifin nan ma, kamar yadda ki ka saba".
Cikin takaici ta ce "Ka ce dole?"
"Ƙwarai dole, idan asirinmu ya tonu ai kema naki ya
tonu, yanzu wane matakin ki ka ɗauka?".
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Yadda na lura, takamaimai, ba
su san waye kai ba, daga ita bar babarta, dan haka zan je gidan ita Antyn taka,
a bamu adress ɗin maigadin da suka kaita Asibiti lokacin da abun ya faru, duk
da Yallaɓai ya gaya mini, an sallame shi daga aiki, amma dole za mu yi framing ɗin
sa da laifin, in case wani zai tayar da maganar, sai mu ce mai laifin ya shiga
hannu, abun da nake ƙoƙarin yi kenan"
Ya kwashe da wata irin dariya ya ce "Daɗi na da ke
akwai brain, anyway ina ne gidan su yarinyar, she needs to learn a lesson, da
ita da babarta da ɗan jaridar da ya saka zancen".
Da sauri ta ce "Kar ka kuskura, ba zaka ɓata mini aiki
ba, na gaya maka ba su san kai waye ba, idan kuma ka yi wani yinƙuri, da ya
samar da wata ɓaraka babu ruwana a ciki na gaya maka"
Abdul ya ce "Na ji, ina son ganin yarinyar ne
kawai"
"Abdul, ina da abubuwan yi da yawa a gabana"
"Naja'atu, kar ki katse mini waya, ki bani adress ɗin
yarinyar".
Kashe wayar ta yi, tare da jan tsaki, ta cigaba da
rubuce-rubucenta.
Nabila sai wajen sha ɗaya saura na dare, sannan ta ɗan dawo
dai-dai, sai a lokacin ta samu ta yi wanka, a cikin ɗakinta ta tsaya tana
kallon cikinta, da ciwonta, da haryanzu yake yi mata zafi.
A haka ta lallaɓa, tayi shafe-shafen skin routine ɗin ta, ta
fita kitchen ta haɗo tea, ta dafa indomie, ta koma ɗakinta, ta saka wayar Viper
a caji.
Ta ɗauki wayarta ta tarar da tarin missed calls ɗin Nasir,
ta kira shi ta saka wayar a hansfree, tare da kashingiɗa.
Ya ɗaga tare da yin sallama, ta amsa masa a hankali.
"Arfa ko ki neme ni, ki ji ya na sauka ko?"
A shagwaɓe ta ce "Am sorry, i got a little accident ne,
a asibiti na wuni"
A ɗan rikice ya ce "Subhanallah, garin yaya
meyafaru?"
"Don't mind, akwai labari ne"
"Wane irin labari? Amma dai kina lafiya ko?"
Tayi murmushi ta ce "Gashi muna magana da kai, lafiya
ƙalau nake, ka ce Viper daga prison aka sake shi ko? Laifin me yayi aka kama
shi?"
Nasir ya ce "Ohhh my God, meyasa ki ka damu da lamarin
nan ne har haka Arfa?"
"Ni ka amsa mini Please"
Ya ce "Yeah, amma ya shiga prsion, ba sau ɗaya ba, ba
sau biyu ba, shigarsa na ƙarshe ne, ya ɗan daɗe, kuma da alama laifin da ya yi
babba ne, sai dai ba wannan ne a gabana ba, kama shi nake son yi.
Akwai jami'anmu suna yawo a farin kaya, suna neman bayanai a
kansa"
"Ka daina wahalar da kanka, na samo maka abubuwan da za
su sauƙaƙa maka komai"
Ƙasa-ƙasa yayi da murya ya ce "What do you mean? Ba na
son wasa fa".
Ɗan shiru ta yi, ta tabattar idan ta gaya masa gaskiya a
yanzu, ba gwaninta za ta yi masa ba, dan muddin ta gaya masa ta san in da yake,
zai ce ta je wurin ƴan daba, zaneta zai yi, kuma sai ya gaya wa Abba ta shiga
uku.
Dan haka ta ce "Da gaske nake, na je wurin wata client ɗin
mu, a unguwar da yake, na samo labari, yana da yaransa da suke ƙananan dilallan
tabar wiwi, amma ba su san in da yake ba, wai akwai wani guda ɗaya a tal'udu,
yana sayar da katin waya bayan magariba, amma ƙwayoyi yake sayarwa, ya san in
da yake".
Ya ce "Look arfa, ba na son wasa, daga zuwa unguwar
wurin client, har ki ka samu wannan rahotannin?"
"Haba DSP, kar ka manta ni ma fa ma'aikaciya ce,
wallahi ba ƙarya nake yi ba, daga majiya mai ƙarfi na ji labarin, na je wurin
kuma na ga mutumin yana zaman sayar da katin wayar, idan baka yarda ba, idan ka
dawo da kanka ka bincika"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "No, ba sai na dawo ba, zan
aika a bincika mini, ina fatan baki gaya wa kowa ba?"
"No, babu wanda na gayawa"
Nasir ya ce "Good, amma kar ki kuskura ki yi wani abu,
da zaki saka kanki a cikin hatsari kin ji ko?"
Nabila ta ce "To, idan ka dawo zan baka wani abu mai
muhimmancin da zai taimaka maka, amma sai idan zaka yi mini alƙawarin ba zaka
dake ni ba, ko ka yi mini faɗa" tayi maganar tana kallon wayar Viper.
"Menene abun?"
"Sai ka dawo tukuna zan gaya maka, take care"
"Shikenan, Allah ya kaimu na dawo ɗin, ki kwanta ki
huta"
"Ok bye-bye" ta kashe wayar ta ajiye, ta ɗauki ta
Viper, da ta yi caji, ta kunna ta.
Ta kai wayar hancinta ta sinsuna, ga warin sigari tana yi,
ga ƙamshin turare.
Ta fara shige-shige a wayar.
Cikin call log ɗin sa ta duba, ga lambobi nan, sai dai duk
kiransa ake yi ba ya kira, sai jerin private number da ake kiransa da ita.
Ta duba cikin messages ɗin sa, babu komai a ciki, sai dai a
cikin drafts ɗin sa, yayi saving ɗin wasu kwanakin wata.
Tayi shiru tana tunanin yadda ta ɗaukko wayar ta sa, lokacin
da take tattare kayan jakarta, da ta buɗe idonta ta gansu a tarwatse, ta ga
wayar a gefe, ta haɗa da ita tana sane.
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Wani laifi ka yi aka kama ka,
sannan aka sake ka, ba bisa ƙa'ida ba? Shi yafi cancanta ma in mayar da hankali
in binciko, yadda ana kama ka, zan yi raising case ɗin nima, a hukunta waɗanda
suka sake ka" tayi maganar tana sake mayar da wayar ta sa caji.
"Ko ban ce na san in da ka ke ba, wayarka zata bawa
jami'an tsaron damar nuna in da ka ke".
Ta mayar da kwanukan kitchen, ta dawo ɗakin ta rufe ƙofarta
ta kashe fitila za ta kwanta, sai dai tana kashe fitilar, sai ta ga kamar Viper
ne a tsaye a gabanta, saura ƙiris ta kurma ihu, ta kunna fitilar tana zazzare
ido, tana cigaba da ƙarewa ɗakin kallo, zuciyarta na saƙa mata ko ya biyo ta.
Da ƙyar ta nufi gadonta ta kwanta, gabanta na faɗuwa, ba
tare da ta kashe fitilar ba.
Zumbur ta kuma tashi zaune, ta ɗauki wayar ta sa, ta sakata
a cikin wardrobe ɗin ta, ta rufe ta ta dawo ta kwanta tana rarraba ido.
Sai dai fa fafur ta kasa bacci, tsoro ya baibayeta, mussaman
idan ta tuna ya ce idan suka sake haɗuwa sai ya kashe ta, sai yanzu ma ta fara
tunanin da yaya zata miƙa wayar nan ga DSP Nasir, dan dolen dole sai ya tuhume
ta, to idan ya tuhume ta wace amsar za ta bashi? Yaya aka yi wayar ɗan daba ta
zo wurinta?.
Sai kuma ta koma tunanin, yaya iyayensa suke ji, sun haifi ɗa
ya zame wa mutane masifa a gari?.
Tsananin zurfin da tayi a cikin tunani, ya sanya, wani ɓarawon
bacci, ya yi awon gaba da ita, sai dai baccin bai je ko ina ba, ta din ga jin
numfashi a fuskarta.
A hankali ta buɗe idanunta, jin saukar numfashi a fuskarta,
sai dai me, tayi tozali da fuskar Viper, ya kafeta da manyan idanunsa da suka
yi jawur, dogon karan hancinsa yana taɓa nata, ko ƙiftawa ba ya yi.
A firgice ta yi ihu, ta faɗo daga kan gadon, jikinta na wata
irin kyarma, tana jejjera numfashi, sai dai ta buge wurin ciwonta, dan har ya
fara zubar da jini.
Sai da ta ɗago ta sake kallon gadon, sannan ta ga ashe filo
ne yake taɓa mata hanci, sai ta ga kamar Viper.
Ta rintse idanunta tana addu'a, tare da dafe gefen cikinta
da yake ta yi mata zafi.
Ɓangaren sumayya ma hakan take, dan kasa bacci tayi, dan ita
kwanciyar ma gagararta ta yi, tayi dana sanin sha'awar fara aikin jarida, wace
irin masifa ce haka tana zaman zamanta, ana neman mayar da ita ƴar ta'adda,
saboda an fi ƙarfin ta.
Alwala ta yi, ta tayar da salla, ta din ga addu'a, tana
fatan Ubangiji Allah ya tsare su daga sharrin honorable Indabo, mussaman Nabila
da ba ta san wainar da ake toyawa ba, gashi a yau kawai an yi wasa da
rayuwarta, ba tare da ta san hakan ba, nan gaba ba ta san me za su yi mata ba,
kuma ta san muddin ta gaya wa Nabila, akwai ƙura dan za ta iya aikata abun da
zai sanadin su rasa rayuwarsu gaba ɗaya.
Sai dai tana ta tunanin wace hanya Nabila ta bi ta ga Viper,
tun da ta ce sun haɗu to lallai sun haɗu ɗin, hatsabibancin Nabila da taurin
kanta, har tsoro yake ba ta. Tun da ta ƙududi aniyar yin sunan nan, idan ba
wuƙa ta gani a maƙogwaronta ba, babu lallai ta haƙura.
Honorable Ma'aruf ne a tsaye yana ta zazzagawa Abdul masifa
kamar zai ari baki, shi kuma sai cika yake yana batsewa yana harare-harare.
"Na fara gajiya da rashin mutuncinka Abdul, na gaji,
gashi a banza ka nemo magana a wurin ƴar matsiyata, sun ƙi yadda a haɗa kai da
su, a binne taiyar da ka shuka, dole sai na ɗau mataki a kai. In the next
couple of years, kai zaka tsaya takarar deputy governor a garin nan, kamar
yadda muka yi yarjejeniya da party, kafin na shiga, amma sai shashanci ka ke
yi, so ka ke yi sai lokacin ya yi ƴan adawa, su ɓata mana shiri, na gaji da
zubar da jini, saboda rashin hankalinka da wautarka, na ce ka yi aure ka ƙi, daga
shaye-shaye sai neman mata, idan ma zaka yi yakamata ka san abun da ka ke
ciki"
Abdul ya numfasa ya ce "Ka yi haƙuri, ni yakamata na
goge wannan ɓarnar da kaina, ka karɓar mini address ɗin yarinyar, zan san abun
yi"
"A baka ka je ka kuma yi wa mutane wani shirmen
ko?"
Ya girgiza kai ya ce "No, na yi maka alƙawarin ba wani
shirmen zan yi ba, zan goge komai ne kawai"
"Ɓace ka bani wuri" yayi maganar yana hakin
baloƙoƙon da ya yi.
Nabila fa abu ya zame mata ga ƙoshi, ga kuma kwanan yunwa,
wayar Viper ta zame mata larura, ta rasa yadda za ta yi.
Da safe Abba ya ce ta zauna a gida ta huta, saboda jikinta,
amma ta ce masa ita ta ji sauƙi, fita za ta yi, da kansa ya ɗauke ta a mota, ya
tafi kaita wurin aikin, suna tafe yana yi mata nasihohin da ya saba yi mata,
amma da za a yankata, ba zata iya faɗar me yake cewa ba.
A gate suka haɗu da Director, yana ganin major kamar zai
dungura, saboda risunawa cikin girmamawa, ya gaida major.
Ya amsa masa cikin girmamawa yana tambayarsa aiki.
Director ya amsa da "Aiki Alhamdilillah, yau kuma da
kanka ka kawo ta?"
Major ya ce "To ya na iya, ƴar gudaliyata babu lafiya,
kuma ta dage sai ta fito aiki. Ina fatan dai yanzu tana mayar da ka?"
Director yayi murmushi ya ce "Alhamdilillah, ta rage
shiririta, tana aiki sosai ranar Alhamis ma za ta fita trial ita ce incharge of
case ɗin"
Major ya ce "Masha Allah, idan ki ka yi wining, akwai
special gift" Tayi murmushi kawai ta sauka daga motar, dan ba wani ganewa
take yi ba.
A wurin aikin ma, jin ta ta din ga yi tamkar wadda ta
shekara tana amai da gudawa, gaba ɗaya gaɓoɓinta a sage suke, da ta motsa, sai
ta ga kamar za ta ga Viper a gabanta.
Layin Nasir ta kira, tayi sa'a ya ɗaga ya ce "Ya aka yi
kuma?"
"Ka aika a bincika maka maganar mutumin nan ne?"
"Ki kwantar da hankalinki mana, ina sane zan
aika".
"Ai kar ka zo ka ce ƙarya nake yi ne"
"Haba dai ni na isa ma"
"Yaya"
Ya amsa da "Na'am barrister Nabila maitama".
"Wane laifi Viper yayi na ƙarshe ne, aka rufe
shi?"
"Ban gani ba a cikin record ɗin sa, waɗanda na gani
dai, kawai rigima ce da mutane, da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi da kuma
dillancin su".
"Wace kotu da wace kotu aka taɓa kai shi?".
"Arfa ban sani ba wallahi, wai menene akwai matsala
ne?"
Ta kashingiɗa ta ce "No, babu wani abu sai anjima"
Ta kashe wayar ta ajiye, ta tashi ta tafi office ɗin
Barrister Habib.
Bayan ta yi sallama, ya amsa mata, yana ƙura mata ido, har
ta ƙarasa ta zauna.
Kai tsaye ya ce "Menene matsalar?"
Ta ce "Na yi kama da mai matsala ne?"
"Eh mana, yau ba kwalliya, ba ƙwalisa ba biscuit, ba
sweet a hannu, duk yau dai sai a hankali"
Tayi murmushi ta ce "Barrister ka bani dariya, saka
mini ido ka ke yi kenan, ka san jiya a asibiti na wuni, shiyasa ban zo ba
jiya"
"Eyya, ai na zata mulkin ne ya motsa, ki ka ƙi zuwa,
tun da ke ba tuhumarki ake yi ba, ba kya laifi"
Sake sunkuyar da kai ta yi tana murmushi.
Shi ma murmushin ya yi ya ce "Ina jin ki, meyafaru, dan
ba kya zuwa office ɗin nan sai da dalili"
Ta gyara zamanta ta ce "Barrister, na san ka san wani ɗan
daba da ake nema ko? Aminu Viper"
Yayi mata ƙuri da ido yana kallonta.
"Dama wani labari na ji, wai wani laifi ya yi aka kai
shi prison, kuma kawai sai aka sake shi ba bisa ƙa'ida ba, gashi sai ɓarna yake
yi a gari" sai kuma ta yi shiru.
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ina jin ki"
"To shi ne, sonake na san wani laifin ya yi, ban sani
ba dan Allah ko zaka bincika mini, a wace kotun aka yi masa shari'a"
"Meyasa ki ke son sani?"
"Eh, sonake idan an kama shi, na bibiyi shari'ar da za
ayi masa, kuma na binciki meyasa aka sake shi da"
Wata ƴar dariya ya yi ya ce "Nabila kwanan nan na ga
you are so much serious, amma kin san hakan kamar tarar aradu da ka ne ko? Amma
let's see how far you can go, zan bincika miki in sha Allah, nan da 3days zan
neme ki"
"Na gode sosai babban yaya, Allah ya ƙare ka, na gode
sosai da sosai"
Yayi murmushi tare da jinjina mata da hannunsa ya ce
"Ki huta little barrister "
***
Can gidan su rahama kuwa, ta samu bacci, mamanta na tsakar
gida tana ta shara, kasancewar ta mace mai son tsafta, jin motsi a bayanta, ya
sanya ta waiwaya domin ta ga abun da yake faruwa.
Matasa ne su uku, zabga-zabga cikin shigar banza a tsakiyar
tsakar gidan.
A tsorace ta ce "Lafiya kuwa? Meyafaru?"
Ya ƙarewa gidan kallo ya ce "Dama a nan ku ke rayuwa,
ƙasƙantattun matsiyata, amma har ki ke fatan ganin an kai ni kotu an karɓowa
ƴar ki hakkinta? Har wani hakki ne da ita? Talaka yana da wani hakki ne ko
ƴanci?"
Cikin rawar baki ta ce "Waye kai malam?"
"Na yi miki kama da malam? Ni na yi wa ƴar ki fyaɗe, da
ki ka tafi nema mata hakkinta?".
Sakin tsintsiyar ta yi, tana kallonsa, a ƙalla zai kai
shekaru talatin da takwas, kallon idonsa ta yi babu mutunci ko imani a cikin
su.
"Yanzu kai ka iya samun ƙwarin gwiwar zuwa gabana, ka
gaya mini ka yi wa ƴa ta fyaɗe? Bayan ka turo mini waccan bayahudiyar ta
yaudaremu, ba ta yi nasara ba, shi ne ka zo gabana ka gaya mini ka keta wa ƴa
ta haddi?"
Ya fara takowa gabanta ya ce "Yes, na zo na ƙara kashe
ƙishirwa ta ne, sannan in yaba wa baiwar Allah da Allah ya yi wa ƴar ki, kin
iya haihuwa"
Yayi maganar yana wata irin dariya, a fuskar maman rahama,
da tuni idonta ya fara zubar da hawaye.
Ya saka hannu ya riƙe ɗan kwalin kanta, haɗe da gashin
kanta, ya tsuke fuska ya ce "Kin san ko ni waye, da ki ka saka na tako
ƙafata wannan ƙazamin kucakin ƙauyen"
Ihu ta saki, saboda zafi.
Salim ya ce "Kai Abdul wannan yawa ne fa, ba wurinta mu
ka zo ba fa"
"Bar ni Salim, duk da hausawa sun ce abun cikin ƙwai,
ya fi ƙwai daɗi, what if na wajen ƙwan ya fi?" Yayi maganar yana riƙe
rigarta.
Salim ya ce "No, kar ka yi haka, akuyanci kenan ai, dan
Allah ka bari"
Abdul zai yi magana, suka yi ido huɗu da rahama, a tsaye a
ƙofar ɗakin su, tana kallonsa.
Ayshercool
08081012143
🔞
*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ
BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*
*Ina masu buƙatar sayen nagartattun kayan magungunan mata,
wanda babu cuta ko algus a ciki, ku yi joining link ɗin nan, domin samun
nagartattun magungunan mata*
https://chat.whatsapp.com/BLqFsnlyNf0B483RhoWq8v
Tsoro Nabila ta fara ba wa Sumayya, "Are you serious?
Nabila da ya kashe ki fa, ko kuma idan ya biyo ki fa? Meyasa ba kya tausayawa
rayuwarki ne?"
"Wallahi nima na yi tunanin hakan, amma ranar biyan
buƙata rai ba a bakin komai yake ba, ai bai san in da nake ba, yadda zan ba wa
DSP wayar nake tunani, ba tare da ya yi mini faɗa a kan dalilin da ya sa na yi
ba, ko tuhumata"
Ta ciro ƙaramar waya mai madannai, ta miƙawa sumayya,
sumayya ta karɓa tana salallami, da sarawa sheɗancin Nabila.
Nabila ta ce "Wayar babu caji, sai na je gida zan
sakata a caji" tayi maganar tana karɓar wayar, ta sakata a aljihun ƙaramin
wandonta na ciki.
Ta sauka daga kan gadon, ta ce "Bari na shiga banɗaki
na fito, na baki labari" ta sauka ta shiga banɗakin da yake cikin ɗakin.
Sumayya tayi ƙuri da ido tana kallon ƙofar da Nabila ta
shiga, tana tunanin yadda abubuwa masu karo da juna suka sakata a tsakiya.
Wayarta ce ta fara ringing a cikin jakarta, ta ɗaukko taga
baƙuwar lamba, ta ɗaga tayi sallama.
Muryar namiji ce ya ce "Ya ku ka yi da ita?"
Sumayya ta ce "Ita wa?"
"Wurin wa ki ka je?" Aka tambayeta.
Ta basar ta ce "Wa ke magana?"
"Ya zama dole fa ki yi aikin da aka saka ki, ko kina so
ko ba kya so, a in da taken nan idan aka so za a iya kasheta, ko a saceta ayi
abun da ake so ta yi, yin abun da aka saka ki ne kawai zai tseratar da rayuwar
ta. Ta haɗu da shi ko kuwa?"
ta sunkuyar da kai ta ce "Wai dan Allah a tunaninka,
tayaya mutumin da ƴan sanda ba su kama ba, ita ta haɗu da shi? Ƙarya kawai take
yi dan ta raina mini hankali, Nabila tana da yawan wasa wasu lokutan, amma
ƙarya take yi"
Nabila ce ta fito daga banɗaki, ta ce "Da wani garan
ake waya? Ko kin yi sabon kamu ne?"
Sumayya ta katse wayar ta ce "Ba wani sabon kamu"
"Sumy, ciwon nan na cikina ne yake yi mini zafi
fa"
Sumayya ta ce "Ai Allah ya ƙara, ni dama shegen duka ya
yi miki, ya kakarya ki "
"Ta Allah ba taki ba muguwa, wallahi sumayya da dukana
yayi, zai iya kashe ni, kin ga ƙirarsa kuwa, kin ga tsawonsa?. Kin ga a yadda
ya din ga kallona, na kasa gane wane irin kallo yake yi mini"
Ta kashingiɗe kanta tana gwadawa Sumayya irin kallon da yake
yi mata.
"Wallahi sumayya ban taɓa ganin ido mai ban tsoron nasa
ba, kin ji muryarsa, daga cikin ƙirjinsa yake fitar da ita, abun tsoro, ya ci
sunansa viper".
Wayar sumayya ta fara vibrating, ta tashi tsaye ta ce
"Ina zuwa"
Ta fita waje ta ɗaga wayar ta ce "Ya aka yi kuma?"
"Idan har ba ta haɗu da shi ba, meye dalilinta na gaya
miki ta haɗu da shi?"
Kamar sumayya za ta yi kuka ta ce "Yayanta ɗan sanda
ne, na gaya muku, a bakinsa da kafafen watsa labarai kawai take jin
sunansa" katse wayar aka yi, ba tare da an sake ce mata komai ba.
Ta koma ɗakin da Nabila take, sai dai abun mamaki taga
Nabilan kamar matacciya.
Da sauri ta ƙarasa ta taɓa ta, ta ga bacci kawai take yi,
daga fitarta zuwa yanzu bai ci ace har ta yi wannan baccin ba.
Message aka turo mata "Idan ki ka bamu bayanin da yake
saɓanin gaskiya, abun zai wuce haka, ya zama dole ki bi duk wani umarni da zamu
baki, muna bibiyarku daga ke har ita"
Sumayya ta ajiye wayar, ta dafe kanta tana salati.
Tsaye yake ƙyam a kan ƙololuwar dutsen, yana kallon yadda
rana ta doshi faɗuwa, gari ya fara duhu sosai, a hankali ya ɗago hannunsa, ya
kalli inhaler da take hannunsa, seretide inhaler ya din ga jujjuyata, yana
sauke ajiyar zuciya.
"Boss" ya ji muryar Walid a bayansa.
Ya zagaya gabansa ya ce "Ka saukko haka dan Allah,
magana nake son mu yi"
"Bana buƙata kowace iri ce"
"Na san na yi maka laifi, amma ka yi haƙuri, zan nemota
duk in da take, kuma zan dawo maka da wayarka ina mai baka haƙuri"
Ko motsawa bai yi ba, balle walid ya saka ran zai yi magana,
daga bisani ya goya hannayensa a bayansa, ya cigaba da kallon rana.
"Amma me ka ke tunani game da yarinyar nan? Anya babu
wani abu a ƙasa da yakamata mu sani?"
A hankali ya juyo, ya dafa kafaɗar Walid, ya matsa da ƙarfi
ya ce "Hakan bai dame ni ba, koma wacece, Ma'aruf , madaki, da kuma wannan
yarinyar da ka kawo, sai na tabattar da na kashe su gaba ɗaya, ko ta halin
ƙaƙa".
"A'a master, mace ce, wataƙila sakata aka yi, dan Allah
ka yi haƙuri, zan yi maka bincike a kanta "
"Idan ka kuma gaya mini wannan sunan, zan hankaɗaka
daga kan dutsen nan"
Walid ya yi murmushi ya ce "Baka girmama sunan ne
viper, idan har ka damu har haka, yakamata ka bawa kanka da lafiyarka kulawa,
ta haka ne zaka yi abun da ka ke so, yanzu ka taimaka ka sakar mini kafaɗata,
wallahi kamar na karye"
Ƙurawa walid ido yayi, Walid ya sunkuyar da kansa, ya san ya
tunzuro zuciyar Viper, sakar masa kafaɗarsa ya wuce shi, ya fara sauka daga kan
dutsen.
Har bayan azahar Nabila ba ta farka ba, su kansu ma'aikatan
asibitin, sun yi mamakin irin baccin da Nabila take yi.
Hankalin sumayya kuwa yayi mummunan tashi, ganin Nabila ba
ta farka ba.
Bayan la'asar sai ga Abba, tare da Salim, wanda ƙani ne ga
Nasir.
A ɗakin da Nabila take suka tarar da Sumayya.
Sumayya ta gaishe su, Abba ya amsa ya ce "Sumayya ke ce
a wurinta?"
Ta jinjina kai ta ce "Eh Abba"
"Ai ni ce mini tayi, ba wani abun damuwa bane, ana gama
yi mata abun da za ayi mata, za ta koma gida, sai da na koma na tarar ba ta
dawo ba"
Sumayya ta ce "Eh, ai ta samu bacci ma".
Idonsa ya sauka a kan gefen rigarta, da take a huje ga jini,
cikin mamaki ya ce "Ya nake ganin jini a jikinta?"
Da sauri Sumayya ta ce "amm, dama wai faɗuwa suka a
adaidaita sahu, shi ne ta ji rauni"
"Amma ni bata gaya mini haka ba ai" yayi maganar
cikin matsananciyar damuwa.
Wata irin miƙa Nabila ta yi, tare da yin salati, duk suka yi
kanta suna yi mata sannu.
Suka din ga jera mata sannu, suna yi mata ya jiki.
Sumayya ta kirawo likkta, ya zo ya ƙara duba Nabila, yayi
rubuce-rubuce a file ɗin ta, ya sallame ta.
Abba ya din ga yi mata faɗan meyasa ba ta gaya masa ta faɗi
a adaidaita sahu ba, ta nunawa likitoci ciwon da ta ji.
Sumayya ta kalleta, suka haɗa ido, sai ta fahimta, dan haka
ta ce "Ai ba wani ciwo bane Abba, mu tafi gida na gaji".
"Kin tabattar babu wani abu da yake yi miki ciwo?"
Ta jinjina kai alamar eh, suka fito zuwa motar Abba, suka
tafi tare da sumayya, su ajiyeta a gida.
Sumayya ta kalli Nabila ta ce "Wai ya aka yi ɗazu daga
fita ta, ki ka fara bacci, kusan awa huɗu ki na bacci?"
Nabila ta ɗan yi shiru tana tunani, ta ce "Wani likita
ne ya shigo yayi mini allura"
"Ba Nurse ba, likita da kansa?"
Nabila ta jinjina kai alamar eh, Sumayya ta yi shiru ba ta
ce komai ba, a zuciyarta, take jinjina tsagwaron rashin imanin honorable
Indabo, kenan idan ba ta yi abun da suke so ba, za su kashe Nabila kenan.
Gabanta ya faɗi, ta kalli Nabila da ta kashingiɗa, tana ta
lumshe ido, alamar baccin bai isheta ba.
Tunani take da wa zata tattauna wannan maganar ne? ko wurin
hukuma ta kai, ba ta da shaida ta zahiri, kuma ta san babu wani mataki da za a
iya ɗauka a kai.
***
Yana kwance a kan gadonsa yana kaɗa ƙafa, hannunsa ɗaya yana
riƙe da waya, ɗaya kuma kan shisha, yana ta fesar da hayaƙi.
"Hello" sautin muryar mace ya fito daga cikin
wayar.
Ya ce "Hello, how far?"
Ta amsa da "Ya aka yi?"
"Mun yi magana da tsoho, ashe kin gano in da yarinyar
nan take?"
"Eh, na gano, sai dai sun ce ba za su karɓi kuɗi ba,
hakkinsu suke nema, dan haka sai ka san yadda zaka yi"
Yayi murmushi ya ce "Ki san yadda za ki yi dai, ai kin
san dolenki ki ɓoye laifin nan ma, kamar yadda ki ka saba".
Cikin takaici ta ce "Ka ce dole?"
"Ƙwarai dole, idan asirinmu ya tonu ai kema naki ya
tonu, yanzu wane matakin ki ka ɗauka?".
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Yadda na lura, takamaimai, ba
su san waye kai ba, daga ita bar babarta, dan haka zan je gidan ita Antyn taka,
a bamu adress ɗin maigadin da suka kaita Asibiti lokacin da abun ya faru, duk
da Yallaɓai ya gaya mini, an sallame shi daga aiki, amma dole za mu yi framing ɗin
sa da laifin, in case wani zai tayar da maganar, sai mu ce mai laifin ya shiga
hannu, abun da nake ƙoƙarin yi kenan"
Ya kwashe da wata irin dariya ya ce "Daɗi na da ke
akwai brain, anyway ina ne gidan su yarinyar, she needs to learn a lesson, da
ita da babarta da ɗan jaridar da ya saka zancen".
Da sauri ta ce "Kar ka kuskura, ba zaka ɓata mini aiki
ba, na gaya maka ba su san kai waye ba, idan kuma ka yi wani yinƙuri, da ya
samar da wata ɓaraka babu ruwana a ciki na gaya maka"
Abdul ya ce "Na ji, ina son ganin yarinyar ne
kawai"
"Abdul, ina da abubuwan yi da yawa a gabana"
"Naja'atu, kar ki katse mini waya, ki bani adress ɗin
yarinyar".
Kashe wayar ta yi, tare da jan tsaki, ta cigaba da
rubuce-rubucenta.
Nabila sai wajen sha ɗaya saura na dare, sannan ta ɗan dawo
dai-dai, sai a lokacin ta samu ta yi wanka, a cikin ɗakinta ta tsaya tana
kallon cikinta, da ciwonta, da haryanzu yake yi mata zafi.
A haka ta lallaɓa, tayi shafe-shafen skin routine ɗin ta, ta
fita kitchen ta haɗo tea, ta dafa indomie, ta koma ɗakinta, ta saka wayar Viper
a caji.
Ta ɗauki wayarta ta tarar da tarin missed calls ɗin Nasir,
ta kira shi ta saka wayar a hansfree, tare da kashingiɗa.
Ya ɗaga tare da yin sallama, ta amsa masa a hankali.
"Arfa ko ki neme ni, ki ji ya na sauka ko?"
A shagwaɓe ta ce "Am sorry, i got a little accident ne,
a asibiti na wuni"
A ɗan rikice ya ce "Subhanallah, garin yaya
meyafaru?"
"Don't mind, akwai labari ne"
"Wane irin labari? Amma dai kina lafiya ko?"
Tayi murmushi ta ce "Gashi muna magana da kai, lafiya
ƙalau nake, ka ce Viper daga prison aka sake shi ko? Laifin me yayi aka kama
shi?"
Nasir ya ce "Ohhh my God, meyasa ki ka damu da lamarin
nan ne har haka Arfa?"
"Ni ka amsa mini Please"
Ya ce "Yeah, amma ya shiga prsion, ba sau ɗaya ba, ba
sau biyu ba, shigarsa na ƙarshe ne, ya ɗan daɗe, kuma da alama laifin da ya yi
babba ne, sai dai ba wannan ne a gabana ba, kama shi nake son yi.
Akwai jami'anmu suna yawo a farin kaya, suna neman bayanai a
kansa"
"Ka daina wahalar da kanka, na samo maka abubuwan da za
su sauƙaƙa maka komai"
Ƙasa-ƙasa yayi da murya ya ce "What do you mean? Ba na
son wasa fa".
Ɗan shiru ta yi, ta tabattar idan ta gaya masa gaskiya a
yanzu, ba gwaninta za ta yi masa ba, dan muddin ta gaya masa ta san in da yake,
zai ce ta je wurin ƴan daba, zaneta zai yi, kuma sai ya gaya wa Abba ta shiga
uku.
Dan haka ta ce "Da gaske nake, na je wurin wata client ɗin
mu, a unguwar da yake, na samo labari, yana da yaransa da suke ƙananan dilallan
tabar wiwi, amma ba su san in da yake ba, wai akwai wani guda ɗaya a tal'udu,
yana sayar da katin waya bayan magariba, amma ƙwayoyi yake sayarwa, ya san in
da yake".
Ya ce "Look arfa, ba na son wasa, daga zuwa unguwar
wurin client, har ki ka samu wannan rahotannin?"
"Haba DSP, kar ka manta ni ma fa ma'aikaciya ce,
wallahi ba ƙarya nake yi ba, daga majiya mai ƙarfi na ji labarin, na je wurin
kuma na ga mutumin yana zaman sayar da katin wayar, idan baka yarda ba, idan ka
dawo da kanka ka bincika"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "No, ba sai na dawo ba, zan
aika a bincika mini, ina fatan baki gaya wa kowa ba?"
"No, babu wanda na gayawa"
Nasir ya ce "Good, amma kar ki kuskura ki yi wani abu,
da zaki saka kanki a cikin hatsari kin ji ko?"
Nabila ta ce "To, idan ka dawo zan baka wani abu mai
muhimmancin da zai taimaka maka, amma sai idan zaka yi mini alƙawarin ba zaka
dake ni ba, ko ka yi mini faɗa" tayi maganar tana kallon wayar Viper.
"Menene abun?"
"Sai ka dawo tukuna zan gaya maka, take care"
"Shikenan, Allah ya kaimu na dawo ɗin, ki kwanta ki
huta"
"Ok bye-bye" ta kashe wayar ta ajiye, ta ɗauki ta
Viper, da ta yi caji, ta kunna ta.
Ta kai wayar hancinta ta sinsuna, ga warin sigari tana yi,
ga ƙamshin turare.
Ta fara shige-shige a wayar.
Cikin call log ɗin sa ta duba, ga lambobi nan, sai dai duk
kiransa ake yi ba ya kira, sai jerin private number da ake kiransa da ita.
Ta duba cikin messages ɗin sa, babu komai a ciki, sai dai a
cikin drafts ɗin sa, yayi saving ɗin wasu kwanakin wata.
Tayi shiru tana tunanin yadda ta ɗaukko wayar ta sa, lokacin
da take tattare kayan jakarta, da ta buɗe idonta ta gansu a tarwatse, ta ga
wayar a gefe, ta haɗa da ita tana sane.
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Wani laifi ka yi aka kama ka,
sannan aka sake ka, ba bisa ƙa'ida ba? Shi yafi cancanta ma in mayar da hankali
in binciko, yadda ana kama ka, zan yi raising case ɗin nima, a hukunta waɗanda
suka sake ka" tayi maganar tana sake mayar da wayar ta sa caji.
"Ko ban ce na san in da ka ke ba, wayarka zata bawa
jami'an tsaron damar nuna in da ka ke".
Ta mayar da kwanukan kitchen, ta dawo ɗakin ta rufe ƙofarta
ta kashe fitila za ta kwanta, sai dai tana kashe fitilar, sai ta ga kamar Viper
ne a tsaye a gabanta, saura ƙiris ta kurma ihu, ta kunna fitilar tana zazzare
ido, tana cigaba da ƙarewa ɗakin kallo, zuciyarta na saƙa mata ko ya biyo ta.
Da ƙyar ta nufi gadonta ta kwanta, gabanta na faɗuwa, ba
tare da ta kashe fitilar ba.
Zumbur ta kuma tashi zaune, ta ɗauki wayar ta sa, ta sakata
a cikin wardrobe ɗin ta, ta rufe ta ta dawo ta kwanta tana rarraba ido.
Sai dai fa fafur ta kasa bacci, tsoro ya baibayeta, mussaman
idan ta tuna ya ce idan suka sake haɗuwa sai ya kashe ta, sai yanzu ma ta fara
tunanin da yaya zata miƙa wayar nan ga DSP Nasir, dan dolen dole sai ya tuhume
ta, to idan ya tuhume ta wace amsar za ta bashi? Yaya aka yi wayar ɗan daba ta
zo wurinta?.
Sai kuma ta koma tunanin, yaya iyayensa suke ji, sun haifi ɗa
ya zame wa mutane masifa a gari?.
Tsananin zurfin da tayi a cikin tunani, ya sanya, wani ɓarawon
bacci, ya yi awon gaba da ita, sai dai baccin bai je ko ina ba, ta din ga jin
numfashi a fuskarta.
A hankali ta buɗe idanunta, jin saukar numfashi a fuskarta,
sai dai me, tayi tozali da fuskar Viper, ya kafeta da manyan idanunsa da suka
yi jawur, dogon karan hancinsa yana taɓa nata, ko ƙiftawa ba ya yi.
A firgice ta yi ihu, ta faɗo daga kan gadon, jikinta na wata
irin kyarma, tana jejjera numfashi, sai dai ta buge wurin ciwonta, dan har ya
fara zubar da jini.
Sai da ta ɗago ta sake kallon gadon, sannan ta ga ashe filo
ne yake taɓa mata hanci, sai ta ga kamar Viper.
Ta rintse idanunta tana addu'a, tare da dafe gefen cikinta
da yake ta yi mata zafi.
Ɓangaren sumayya ma hakan take, dan kasa bacci tayi, dan ita
kwanciyar ma gagararta ta yi, tayi dana sanin sha'awar fara aikin jarida, wace
irin masifa ce haka tana zaman zamanta, ana neman mayar da ita ƴar ta'adda,
saboda an fi ƙarfin ta.
Alwala ta yi, ta tayar da salla, ta din ga addu'a, tana
fatan Ubangiji Allah ya tsare su daga sharrin honorable Indabo, mussaman Nabila
da ba ta san wainar da ake toyawa ba, gashi a yau kawai an yi wasa da
rayuwarta, ba tare da ta san hakan ba, nan gaba ba ta san me za su yi mata ba,
kuma ta san muddin ta gaya wa Nabila, akwai ƙura dan za ta iya aikata abun da
zai sanadin su rasa rayuwarsu gaba ɗaya.
Sai dai tana ta tunanin wace hanya Nabila ta bi ta ga Viper,
tun da ta ce sun haɗu to lallai sun haɗu ɗin, hatsabibancin Nabila da taurin
kanta, har tsoro yake ba ta. Tun da ta ƙududi aniyar yin sunan nan, idan ba
wuƙa ta gani a maƙogwaronta ba, babu lallai ta haƙura.
Honorable Ma'aruf ne a tsaye yana ta zazzagawa Abdul masifa
kamar zai ari baki, shi kuma sai cika yake yana batsewa yana harare-harare.
"Na fara gajiya da rashin mutuncinka Abdul, na gaji,
gashi a banza ka nemo magana a wurin ƴar matsiyata, sun ƙi yadda a haɗa kai da
su, a binne taiyar da ka shuka, dole sai na ɗau mataki a kai. In the next
couple of years, kai zaka tsaya takarar deputy governor a garin nan, kamar
yadda muka yi yarjejeniya da party, kafin na shiga, amma sai shashanci ka ke
yi, so ka ke yi sai lokacin ya yi ƴan adawa, su ɓata mana shiri, na gaji da
zubar da jini, saboda rashin hankalinka da wautarka, na ce ka yi aure ka ƙi, daga
shaye-shaye sai neman mata, idan ma zaka yi yakamata ka san abun da ka ke
ciki"
Abdul ya numfasa ya ce "Ka yi haƙuri, ni yakamata na
goge wannan ɓarnar da kaina, ka karɓar mini address ɗin yarinyar, zan san abun
yi"
"A baka ka je ka kuma yi wa mutane wani shirmen
ko?"
Ya girgiza kai ya ce "No, na yi maka alƙawarin ba wani
shirmen zan yi ba, zan goge komai ne kawai"
"Ɓace ka bani wuri" yayi maganar yana hakin
baloƙoƙon da ya yi.
Nabila fa abu ya zame mata ga ƙoshi, ga kuma kwanan yunwa,
wayar Viper ta zame mata larura, ta rasa yadda za ta yi.
Da safe Abba ya ce ta zauna a gida ta huta, saboda jikinta,
amma ta ce masa ita ta ji sauƙi, fita za ta yi, da kansa ya ɗauke ta a mota, ya
tafi kaita wurin aikin, suna tafe yana yi mata nasihohin da ya saba yi mata,
amma da za a yankata, ba zata iya faɗar me yake cewa ba.
A gate suka haɗu da Director, yana ganin major kamar zai
dungura, saboda risunawa cikin girmamawa, ya gaida major.
Ya amsa masa cikin girmamawa yana tambayarsa aiki.
Director ya amsa da "Aiki Alhamdilillah, yau kuma da
kanka ka kawo ta?"
Major ya ce "To ya na iya, ƴar gudaliyata babu lafiya,
kuma ta dage sai ta fito aiki. Ina fatan dai yanzu tana mayar da ka?"
Director yayi murmushi ya ce "Alhamdilillah, ta rage
shiririta, tana aiki sosai ranar Alhamis ma za ta fita trial ita ce incharge of
case ɗin"
Major ya ce "Masha Allah, idan ki ka yi wining, akwai
special gift" Tayi murmushi kawai ta sauka daga motar, dan ba wani ganewa
take yi ba.
A wurin aikin ma, jin ta ta din ga yi tamkar wadda ta
shekara tana amai da gudawa, gaba ɗaya gaɓoɓinta a sage suke, da ta motsa, sai
ta ga kamar za ta ga Viper a gabanta.
Layin Nasir ta kira, tayi sa'a ya ɗaga ya ce "Ya aka yi
kuma?"
"Ka aika a bincika maka maganar mutumin nan ne?"
"Ki kwantar da hankalinki mana, ina sane zan
aika".
"Ai kar ka zo ka ce ƙarya nake yi ne"
"Haba dai ni na isa ma"
"Yaya"
Ya amsa da "Na'am barrister Nabila maitama".
"Wane laifi Viper yayi na ƙarshe ne, aka rufe
shi?"
"Ban gani ba a cikin record ɗin sa, waɗanda na gani
dai, kawai rigima ce da mutane, da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi da kuma
dillancin su".
"Wace kotu da wace kotu aka taɓa kai shi?".
"Arfa ban sani ba wallahi, wai menene akwai matsala
ne?"
Ta kashingiɗa ta ce "No, babu wani abu sai anjima"
Ta kashe wayar ta ajiye, ta tashi ta tafi office ɗin
Barrister Habib.
Bayan ta yi sallama, ya amsa mata, yana ƙura mata ido, har
ta ƙarasa ta zauna.
Kai tsaye ya ce "Menene matsalar?"
Ta ce "Na yi kama da mai matsala ne?"
"Eh mana, yau ba kwalliya, ba ƙwalisa ba biscuit, ba
sweet a hannu, duk yau dai sai a hankali"
Tayi murmushi ta ce "Barrister ka bani dariya, saka
mini ido ka ke yi kenan, ka san jiya a asibiti na wuni, shiyasa ban zo ba
jiya"
"Eyya, ai na zata mulkin ne ya motsa, ki ka ƙi zuwa,
tun da ke ba tuhumarki ake yi ba, ba kya laifi"
Sake sunkuyar da kai ta yi tana murmushi.
Shi ma murmushin ya yi ya ce "Ina jin ki, meyafaru, dan
ba kya zuwa office ɗin nan sai da dalili"
Ta gyara zamanta ta ce "Barrister, na san ka san wani ɗan
daba da ake nema ko? Aminu Viper"
Yayi mata ƙuri da ido yana kallonta.
"Dama wani labari na ji, wai wani laifi ya yi aka kai
shi prison, kuma kawai sai aka sake shi ba bisa ƙa'ida ba, gashi sai ɓarna yake
yi a gari" sai kuma ta yi shiru.
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ina jin ki"
"To shi ne, sonake na san wani laifin ya yi, ban sani
ba dan Allah ko zaka bincika mini, a wace kotun aka yi masa shari'a"
"Meyasa ki ke son sani?"
"Eh, sonake idan an kama shi, na bibiyi shari'ar da za
ayi masa, kuma na binciki meyasa aka sake shi da"
Wata ƴar dariya ya yi ya ce "Nabila kwanan nan na ga
you are so much serious, amma kin san hakan kamar tarar aradu da ka ne ko? Amma
let's see how far you can go, zan bincika miki in sha Allah, nan da 3days zan
neme ki"
"Na gode sosai babban yaya, Allah ya ƙare ka, na gode
sosai da sosai"
Yayi murmushi tare da jinjina mata da hannunsa ya ce
"Ki huta little barrister "
***
Can gidan su rahama kuwa, ta samu bacci, mamanta na tsakar
gida tana ta shara, kasancewar ta mace mai son tsafta, jin motsi a bayanta, ya
sanya ta waiwaya domin ta ga abun da yake faruwa.
Matasa ne su uku, zabga-zabga cikin shigar banza a tsakiyar
tsakar gidan.
A tsorace ta ce "Lafiya kuwa? Meyafaru?"
Ya ƙarewa gidan kallo ya ce "Dama a nan ku ke rayuwa,
ƙasƙantattun matsiyata, amma har ki ke fatan ganin an kai ni kotu an karɓowa
ƴar ki hakkinta? Har wani hakki ne da ita? Talaka yana da wani hakki ne ko
ƴanci?"
Cikin rawar baki ta ce "Waye kai malam?"
"Na yi miki kama da malam? Ni na yi wa ƴar ki fyaɗe, da
ki ka tafi nema mata hakkinta?".
Sakin tsintsiyar ta yi, tana kallonsa, a ƙalla zai kai
shekaru talatin da takwas, kallon idonsa ta yi babu mutunci ko imani a cikin
su.
"Yanzu kai ka iya samun ƙwarin gwiwar zuwa gabana, ka
gaya mini ka yi wa ƴa ta fyaɗe? Bayan ka turo mini waccan bayahudiyar ta
yaudaremu, ba ta yi nasara ba, shi ne ka zo gabana ka gaya mini ka keta wa ƴa
ta haddi?"
Ya fara takowa gabanta ya ce "Yes, na zo na ƙara kashe
ƙishirwa ta ne, sannan in yaba wa baiwar Allah da Allah ya yi wa ƴar ki, kin
iya haihuwa"
Yayi maganar yana wata irin dariya, a fuskar maman rahama,
da tuni idonta ya fara zubar da hawaye.
Ya saka hannu ya riƙe ɗan kwalin kanta, haɗe da gashin
kanta, ya tsuke fuska ya ce "Kin san ko ni waye, da ki ka saka na tako
ƙafata wannan ƙazamin kucakin ƙauyen"
Ihu ta saki, saboda zafi.
Salim ya ce "Kai Abdul wannan yawa ne fa, ba wurinta mu
ka zo ba fa"
"Bar ni Salim, duk da hausawa sun ce abun cikin ƙwai,
ya fi ƙwai daɗi, what if na wajen ƙwan ya fi?" Yayi maganar yana riƙe
rigarta.
Salim ya ce "No, kar ka yi haka, akuyanci kenan ai, dan
Allah ka bari"
Abdul zai yi magana, suka yi ido huɗu da rahama, a tsaye a
ƙofar ɗakin su, tana kallonsa.
Ayshercool
08081012143
🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA
ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*
*Ina masu buƙatar sayen nagartattun kayan magungunan mata,
wanda babu cuta ko algus a ciki, ku yi joining link ɗin nan, domin samun
nagartattun magungunan mata*
https://chat.whatsapp.com/BLqFsnlyNf0B483RhoWq8v
15
A take ya hankaɗe uwar a gefe, ya yi wa ramma wani irin
miskilin murmushi, ya nufe ta yana wata irin tafiya, irin ta riƙaƙƙun ƴan iska
ya ce
"Hi baby girl, long time almost 2months kenan fa
ko?"
Hawaye ne ya fara bin fuskar ramma, jikinta ya hau rawa.
Ya sanya hannu ya dafa jikin bango, yana ƙare mata kallo ya
shafi sumarsa ya ce "To ya ki ke, kin warke?"
Shiru ta yi ta sunkuyar da kai, tana tuna waccan ranar, da
irin yadda ya keta mata haddi cike da zalunci.
Ya ce "Ohh, wai waccan ranar ce haryanzu ba ki manta ba
ki ke kuka? Ya wuce ai wancan, kin bar ni da tsananin kewarki, duk ruwan da na
sha komai sanyin sa, ya daina kashe mini ƙishirwa".
Ya kai hannu ya ɗago fuskarta, ya shafi hawayen da suke ta
ambaliya a kan fuskarta.
Yinƙurawa mamanta ta yi da sauri, tana kururuwa ta ce
"Kar ka taɓa mini ƴa, mugu azzalumi, wai babu wanda zai kawo mini ɗauki
ne?"
Ya kalli su Salim ya ce "Ku saka mini matar nan a
silent"
Haka suka rirriƙeta, suka ɗaure mata baki, suka shaƙa mata
wani abu, a take jikinta yayi laƙwas.
Ya sake kallon ramma ya ce "An ce akwai unborn ɗi na a
cikin ki ko? da gaske za ki haife shi kuma?"
Cikin kuka ta ce "Ban yafe maka ba, ka lalata mini
rayuwa, ban sanka ban taɓa ganinka ba, ka biyo ni gida kana wulaƙanta mini uwa,
dan bamu da kuɗi, Allah ya saka mini" tayi maganar tana fashewa da kuka
iya ƙarfin ta.
Salim ya sunkuyar da kai ya yi shiru, haka nan ya ji abun
yayi masa wani iri a zuciyarsa, sauran matan da suke lalata da su, suke kai kan
su, wannan kuma yarinya ce ƙarama.
Dariya ya yi ya ce "Dan kin ce baki yafe ba, ba zai
hana ni shiga aljanna ba, kun ƙuduri aniyar neman hakkinku, duk da an yi muku
tayin kuɗi kun ƙi, zan nuna muku ƙarfi da izzar kuɗi a ƙasar nan".
Ya danƙi hannun ramma, da jikinta ya ɗauki zafi sosai.
Tana ihu tana kiran mama, ya ja ta suka fice daga gidan,
suka sakata a mota suka tafi da ita.
*****
Ɗan mama ne ya shiga ɗakin Viper, ya tarar da shi yana ta
sintiri a ɗakin.
"Ka daɗe ka yi ƙarko uban gidana"
Viper ya tsaya cak, yana jiran ya ji me zai ce.
"Na yi aikin da ka saka ni, ya tafi yadda yakamata
"
Ya kaɗa kai tare da yi masa alamar ya ƙaraso.
"Ina labarin malam lawan?"
"Kamar dai yadda ka ce, an kula da komai, sai dai babu
wanda ya sake zuwa, gashi yanzu yana yawo a cikin unguwa".
"Madaki fa?"
"Shi ma kamar dai yadda ka sani, Honorable indabo yake
yi wa aiki yanzu".
"Ina buƙatar isassun kayan aiki, a kwanakin nan zan
dirar masa, mu ɓalla ƙarfe, sai dai mu yi mutuwar kasko, ayi wadda za
ayi".
"Ba yanzu ba" suka ji muryar Walid.
Suka mayar da hankalinsu kan sa.
Walid ya ce "Viper da sauran lokaci, kai ka san madaki
ba haka kurum yake daba ba, da zai kasu cikin sauƙi, da tuni mun kawar maka da
shi, ka ɗan saurara tukuna"
A hasale ya ce "Ba zan saurara ɗin ba tukuna"
"Viper!"
Ciki ƙaraji ya ce "Walid ka ƙyale ni"
Walid ya girgiza kai ya ce "Da zan iya, da tuni na yi,
mutumin nan ya fi ƙarfinmu ko ta ina, idan ka yi amfani da zuciya wallahi ba
zamu yi nasara ba, ka bari mu bi komai a hankali mu lissafa, yadda ko mutuwar
kasko ce mu yi"
Cikin ƙaraji ya ce "Ba zan jira ba, na gaji, na gaya
maka na gaji. Na so bin komai a hankali, meyasa ka kawo mini yarinyar saboda
me? ka san ka ƙara tunzara zuciyata yaya ka ke so na yi, so ka ke sai na
haukace tukuna? Kalli yadda na koma walid, kalle ni, abun da nake ta ƙoƙarin
dannewa ka fama mini, dan me zaka kawo mini wannan yarinyar sannan ka ce na
nutsu how? Ta ɗauki wayata ta tafi, ka na da tabbacin hannun wa wayata za ta
shiga? Idan aka tashi kama ni, kana da tabbacin su waye za su kama ni, idan na ƙare
a haka ban aikata abun da nake ƙuduri ba fa? Ko dai ka nemo duk in da yarinyar
nan take na kasheta, ko kuma a yau ba sai gobe ba, sai na yi gaba da gaba da
madaki ko na kashe shi ko ya kashe ni, amma kafin nan sai na fara gaba da gaba
da wancan dabban" tuni gumi ya tsatsttsafo masa, jijiyoyin kansa suka
mimmiƙe, kafofin gashinsa ya bubbuɗe.
Walid ya taka gabansa a hankali, cike da shirin ko ta kwana,
dan ya san ƙarshenta sai ya ba shi gwale-gwale, ko ya mangare shi.
Ya shammace shi, ya soka masa sirinji a damtsensa,
kasancewar jikinsa babu riga, ya fara yi masa allura, sannan ya fara yi masa
magana.
Walid ya ce "Na san na yi laifi, amma ka bari na gyara
laifina da kaina, na san abun da ka ke ji ɗan uwa, ba kai kaɗai ka ke ji ba
Al'amin"
Viper ya zubawa walid ido, ya rasa me zai yi, yana tsaye ya
kashe masa jiki, ba zai iya komai ba, kasa tsayuwar yayi, ya tafi zai faɗi
walid ya riƙe shi ya kwantar, ɗan mama kuwa dama tuni ya arce, dan yana tsoron
a shaƙe shi.
Barrister Naja'atu ce zaune a katafaren ofishin ta, tamkar
na matar gwamna, yana ɗauke da duk wani kayan alatu da ake buƙata.
Sannu a hankali take shafa screen ɗin wayarta, daga bisani
ta saka wayar a kunnenta.
"Honorable, ka isa Abujan ne?".
Ya amsa da "Eh ma sauka"
"Ok, yaya maganar yarinyar nan da Abdul ya yi
raping?"
"Yes, he handle the case himself, yayi maganin
abun".
Ta ce "Ok, ina fatan ka ja masa kunne, kar ya je ya
aikata wani shirmen da ba zamu iya gyarawa ba".
Ya ce "No, kar ki damu, zai yi abun da ya dace".
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, dama ina tsoron ya
yi wani shirmen ne, amma tun da ka ce haka, shikenan"
Ta katse wayar, ta mayar da hankalinta kan sakatariyarta da
ta shigo.
Cikin gyatsine ta ce "Ke kuma ya aka yi?"
"Kin yi baƙi ne ma"
"Suwaye?"
"Eh to, da alama dai ƙorafi suka kawo, ke suke.....
"Ke bani da lokaci, ayyuka sun yi mini yawa, su ganki
ko wani daban, hutawa nake buƙata, wannan jaraba a uzzurawa rayuwarka, london
zan wuce ma ni this week na je na huta. Ki fita ki je ki sallame su" ta
juya jiki a sanyaye ta bar office ɗin.
Salim ya kalli Abdul da ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, yana
shan giya a cikin wine cup ya ce "To wai yanzu ya zaka yi da yarinyar nan
da ka kawo ka ajiye, Ga abun da aka tsara, kai kuma ga abun da ka yi?"
Ya ɗan girgiza giyar a cikin kofin sannan ya ce "Gani
na yi za ta ci bulus idan ta tafi a haka, sai na gama moreta zan aikata
kawai"
"Amma ba ka ganin, hakan zai iya kawo matsala, yanzu ko
a nan gaba?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba wata matsala, na ɗan lokaci
ne, zan gama abun da zan yi da ita, zaka iya tafiya ma kawai"
Ya jinjina kai ya ce "To shikenan"
Sannu a hankali ta buɗe idonta, ta din ga gani dishi-dishi,
ta kasa tantance a ina take, dan ba ta taɓa ganin wurin ba.
Ji ta yi an rufe ƙofa, ta ɗaga kai ta kalli mai shigowar,
take gabanta yayi mummunar faɗuwa, duk da idonta bai gama washewa ba, amma
sarai ta gane shi.
"Kin tashi kenan? abun da aka shaƙa miki bai taka kara
ya karya ba, amma ki ka yi wannan dogon zangon" yayi maganar lokacin da ya
tsuguna a gabanta yana kallon idonta.
Ƙirjinta ya din ga bugawa da sauri da sauri.
Ganin ba ta ce komai ba, ya sanya ya tashi ya fita, babu
jimawa ya dawo da plate a hannunsa, ɗauke da indomie da kifi a ciki, sai ruwan
roba, hannunsa ɗaya kuma ledar magunguna ce.
Ya tura mata plate ɗin gabanta, sannan ya fara haɗa alluran.
Tayi shiru ta zuba masa ido, har sai da ya ce "Ki ci
mana, allura zan yi miki"
Cikin kuka ta ce "Dan Allah kar ka kashe ni"
Abdul ya yi wani murmushi ya ce "Saboda me?"
"Ni dai kar ka kashe ni, dan Allah ka mayar da ni wurin
babata"
Ya kalleta ya ce "Kashe ki fa sai na yi, ba dai ke
taurin kai ba ke da babar taki, zan nuna muku cewa talaka ba komai bane illa
bawa kuma takalmi ga masu kuɗi da dukiya, ba yanzu zan kashe ki ba, sai kin
gama yi mini amfani tukuna.
Yanzu ki ci abincin nan, zan yi miki allurai na zazzaɓin da
yake jikinki".
"Ni ba zan ci ba" ta yi maganar za ta tashi tsaye,
amma ya daka mata tsawa ya ce "Wallahi idan ba ki ci ba, a yanzu zan kashe
ki, ko gawarki babarki ba zata gani ba".
Babu shiri ta fara cin abincin, sai dai a loma ta uku, ta
hau amai, ta amayar da duk abun da ta ci.
Cikin tsananin takaici ya ce "Ke mahaukaciyar ina ce
zaki yi mini amai a nan? Nan yayi miki kama da wurin juye ƙazanta?.
Tayi shiru ta sunkuyar da kai.
"Tashi mu je in nuna miki in da duster da mopper suke
ki gyara"
Cikin tsoro ta tashi, tana jiri tana bin bango, haka ya saka
ta gyara wurin da ta yi aman.
Bayan ta gyara, ta shiga banɗakin tayi alwala, ta fito ta
tayar da salla, ba tare da ta san ina ne gabas ba, da kuma adadin sallolin da
ake bin ta ba, dan ba ta san adadin lokacin da ta shafe, ba a hayyacinta ba.
Ya dawo ya tarar da ita a zaune, a takure wuri guda, bai
kulata ba, ya ƙarasa ya sanya hannun sa a goshinta, ya ji shi da zafi rai. ɗaga
ta ya ja ta ya dungurar da ita a kan gadon.
Ya kama hannunta, ya saka sirinji, ya fara ɗaukar jininta.
Bayan ya gama ɗaukar jininta, ya yi mata wasu allaurai duk a
jijiyar hannunta.
Ta zubawa saurautar Allah ido, dan kasa magana ta yi, tun
yana allurar ta fara jiran jin alamar ciwonta ya ƙaru, dan ta sallama kashetan
zai yi kamar yadda ya faɗa, amma bayan ya gama yi mata ya tashi ya fice, ya
kulleta a ɗakin, ba tare da ta ji yanayinta ya sauya ba.
***
Abun duniya fa ya ishi Nabila, wayar Viper ta zame mata
wahala, dan kuwa kashe ta tayi gabaki ɗaya, sai dai duk in da ta zauna,
musamman da daddare, idan ta shiga cikin duhu, Viper ne yake yi mata gizo, har
abun ya fara tasiri a yanayin mu'amalarta.
Tana toilet tana wanka, wayarta ta din ga ringing babu
ƙaƙƙautawa, ta kammala wankan ta fito, ta ɗauki wayar tana dubawa.
Lambar Nasir ta fara kira, ta nemi wuri ta zauna a gefen
gado, tana jiran ya ɗaga.
"Ina ki ka shiga ne? Ko kina wurin aiki ne?"
Ta ce "A'a, yanzun nan na dawo gida"
"Baki da lafiya ne?"
"No, gajiyar aiki ce kawai"
"To, aikin ki yayi kyau arfa, na yi waya da mu'azzam,
gayen nan da ki ka faɗa mun kama shi, tare da tabar wiwi da ƙwayoyi"
Sassanyar ajiyar zuciya ta yi ta ce "Alhamdilillah ala
kulli halin, Allah shi ne abun godiya, what next?"
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Na saka lallai su fara
tuhumarsa, ya faɗi in da Viper yake".
Zuciyarta ta din ga raya mata ko ta sanar masa kai tsaye,
abubuwan da suke gudana, ta bashi wayar hankalinta ya kwanta, amma zuciyarta ta
gargaɗe ta a kan aikata hakan.
***
In da ya bar ta a kan gadon, nan ya je ya sake tarar da ita,
ta tashi ta zauna ta dunƙule jikinta a wuri ɗaya tana bacci, sai ajiyar zuciya
take yi.
Wani irin murmushi ya yi, yayi miƙa lokaci guda, ya fara
rage kayan jikinsa.
Motsinsa ya sanya ta farka, fes ta buɗe idanunta, sai dai
hankalinta ya yi mummunan tashi, ta ja da baya, ba ta ƙaunar ganinsa ko kaɗan.
Ya hawo kan gadon ya nufota, ta din ga ihu tana kiran sunan
Allah, ta na yi masa magiyar ya ƙyaleta, ya mayar da ita gida.
Amma kamar ya kamo ƴar kaza, haka ya danƙota zai yi mata
rashin mutunci, sai dai yana haɗa ta da jikinsa, ya ji kamar ana hura wuta a
Jikinta, saboda zafin zazzaɓi, gashi sai wani irin ƙarni take yi, da warin man
kaɗanya da take shafawa ya haɗe da ƙarnin koren sabulun da take wanka da wanki
da shi.
Ba wannan ya fi damunsa ba, rashin saukar zazzaɓin jikinta
ne bai so ba, dan ko a yanzu a galabaice take.
A ɓangaren ramma ma, warin giyar da yake yi, da ƙamshin
turaren sa ya sanya ta fara yinƙurin amai, ba shiri ya cikata, ta sauka da
gudu, ta tafi banɗakin da yake cikin ɗakin, ta din ga kwara aman, sai dai ruwa
kawai take amayarwa, bayan shi babu komai a cikinta.
Ta gama aman tana ta sauke numfashi, ta lallaɓa ta fito,
tana bin bango, sai dai ta tsaya cak tana kallon sa yadda ya zuba mata ido.
Cikin kuka ta haɗa hannayenta ta ce "Dan girman Allah
ka yi haƙuri, ka mayar da ni in da ka ɗauko ni, hankalin mamana na san yana can
a tashe, dan Allah ka yi mini rai ka yi haƙuri" ta ƙarasa maganar tana
zubewa a kan gwiwoyinta tana bashi haƙuri".
Strip ɗin gwajin ciki ya ɗago da yake hannunsa, wanda ya
gwada da jininta da ya ɗiba ɗazu ya ce "Ke ce mace ta farko da ta fara ɗaukar
cikina, kin kafa tarihi, tun da ki ka ce ba za a zubar ba, nima na ji ya shiga
raina, ina son abuna, zaki haife shi kafin na kashe ki, kuma ba zan kashe ki ba
sai bayan kin haihu" ta yi shiru tana cigaba da zubar da hawaye, wai ita
ce ɗauke da ɗan shege a cikinta, a wani keɓantaccen wuri tare da ɗan iska,
saboda kawai ba su da kuɗi, sai yau ta ƙara tabattar da illar talauci.
Ya miƙe tsam daga kan gadon ya fice ya bar ta a ɗakin, ba
tare da sanin makama ko abun yi ba.
Sumayya ce a office ɗin manager, fuskarta ɗauke da
matsananciyar damuwa.
Ya kalleta ya ce "Sumayya yaya aka yi ne? Ko yayi miki
wani abun ranar da ku ka yi program ɗin?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"To menene? Na ga kin yi editing ma kin tura mini,
komai yayi normal, na ce a saka idan lokaci yayi kin yi ƙoƙari sosai, ina ga
program ɗin hannunki zai dawo gaba ɗaya"
Ta sauke numfashi ta ce "Sir"
Ya amsa da "Yes ma"
Sai kuma ta yi shiru.
"Ki gaya mini mana idan da wani abu" ta girgiza
kai ta tashi ta fita.
Addu'a ya din ga yi a zuciyarsa, tare da fatan Allah ya sa
ba wani abun indabo yayi mata ba, dan ya san halinsa sarai.
Nabila tana office ɗin ta, tana aiki, barrister Habib ya buɗe
ya shiga da sallama.
Miƙewa tayi tsaye ta ce "Sannu da zuwa, da ka kirawo ni
ai"
Ya ƙarasa gaban teburinta ya ce "Babu damuwa, aikin da
ki ka ba ni ne na yi"
Tayi murmushi ta ce "Taimakon da na nema dai aka yi
mini"
Shi ma murmushin ya yi ya ce "Zan tura miki court ɗin
da aka fara yi masa shari'a, da sunan wurin wanda za ki je ya binciko miki file
ɗin, akwai dai wani abu a ɓoye".
Cikin sauri ta ce "Ok, ai daga nan ma kana tura mini
sai na tafi"
Ya ce "Wait, ki tafi yanzu ba ki da aiki ne?"
"Ai na kusa kammalawa saura kaɗan ne"
Ya ce "shikenan, zan tura miki ta what's app, amma ki
bi a hankali, fa kar ki je ki yi abun da ba shikenan ba"
"In sha Allah, na gode sosai"
Yana fita ta fara lissafi a ranta, tun kan viper ya je
hannu, za ta bibiyi cases ɗin sa na baya, domin a shirye take da ta ƙalubalanci
hukumar shari'a ciki har da alƙall da kuma hukumar gidan yari, kan sakin Viper
ba tare da ƙa'ida ba, ta san ko ba ta yi nasara ba, za ta yi suna sosai.
Tattara jakarta ta yi, ta fita bayan da saƙon barrister
Habib ya shiga wayarta.
Ba ta wani sha wahala ba zuwa kotun da ya bata adress ɗin,
tun da dama sananniyar magistrate court ce a kano.
Ofishin rijistra ta je, suka gaisa da mutanen wurin, sannan
ta tambayi office ɗin mutumin da barrister Habib ya gaya mata.
Aka yi mata iso, sannan ta gabatarwa da mutumin kanta, da
wanda ya turo ta.
Ya karɓeta da mutuntawa sannan ya ce "Baiwar Allah,
gaskiya ta in da ki ka biyo, babu yadda za ayi na kasa yi miki alfarma, amma
riƙe file ɗin nan, tamkar saka hannu ne ki ɗaukko ƙarfen da yake cikin wuta ne,
dan Allah kar ki je ki yi wani abu da bai kamata ba, tun kan ki zo aka yi waya,
aka ce a baki idan kin zo"
Nabila ta ce "In sha Allah, babu wani abu da zan yi,
ina ɗan yi wani bincike ne kawai".
Ya ja ta suka tafi wani wuri a cikin kotun, suka shiga can
wani office, da ba zaka ce akwai mutane a wurin ba, sai da suka shiga can ciki,
suka iske wani mutum yana ta aiki a computer.
Suka gaisa, wanda ya rakota ya ce "Oga, ga baƙuwa mun
yi, Barrister Habib ne ya aikota, shi kuma daga top oga, ya ce a kawo ta file ɗin
Al'amin viper zaka ɗaukko mata"
Shiru mutumin yayi yana kallon ta sannan ya ce "Ya
sunanki?"
"Nabila yusuf maitama"
"Me za ki yi da file ɗin?"
Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Wani bincike nake yi
ne"
Ya mayar da hankalin sa kan mutumin da ya rakota ya ce
"Ka gaya mata illar da ke cikin hakan?"
"Na gaya mata, ko ma dai menene na gaya maka wanda ya
ce a ba ta ai"
Yayi ajiyar zuciya yana cigaba da yi wa Nabila kallon
tuhuma, ya tashi ya shiga wani wuri.
Ta kalli mutumin da ya rakota ta ce "Yallaɓai, meyasa
file ɗin yake da hatsari har haka?"
Yayi murmushi ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Yana da
alaƙa da rashin gaskiya"
Mutumin ya fito ɗauke da file ɗin, duk ya yi ƙura, hannu na
rawa ta karɓa ta ja kujera ta zauna, ta fara dubawa.
Sannu a hankali ta din ga bin bayanan ciki, da binciken
rahoton ƴan sanda a kai, sai dai komai ba straight forward aka yi shi ba, gaba ɗaya
kanta ya kulle, ba ta fuskanci wani abun kirki a ciki ba.
"Amma sir, ina ƙarshen shari'ar, ai wannan ba a yanke
hukunci ba, ranar ƙarshe da aka ɗaga shari'ar an ce sati uku za a sake zama,
yanzu kusan shekara biyar, ba a sake rubuta komai ba"
Mutumin ya ce "Eh yadda ki ka gani a haka yake"
Cike da mamaki ta ce "Dan Allah wane alƙalin ne ya yi
masa shari'ar?"
"Yana abuja" suka bata amsa a taƙaice.
"Wannan documentation ɗin, sam ba a yi shi ma yadda za
a fahimta ba, amma dan Allah....
Wanda ya ɗauko mata File ɗin ya ce "Mu fa babu abun da
za mu iya sake gaya miki, ba wanda yake da damar zuwa wurin nan sai staff ɗinmu,
dan haka ki tashi ki tafi".
Ta miƙe tsaye ta ce "Na gode sosai"
Ta fito daga office ɗin tana mamaki, ta ja ta tsaya tana
kallon office ɗin, a abun da ta fuskanta wuri ne da ake ɓoye files na musamman.
"Yayi kisan kai!" Ta faɗa a fili.
"Ba abun mamaki bane ba, da gani zai aikata abun da ya
fi kisan kai, amma menene dalilin ajiye shi shekara biyar, ba ayi masa shari'a
ba, an ɓoye file ɗin sa a wuri na musamman, ya shekara biyar a prison, kuma
kwatsam an sake shi, babu document na wanke shi aka yi daga laifin ko kuwa, duk
da an rubuta ya amsa laifin, amma wane hukuncin aka yanke masa? Wayyo Allah
kaina zai fashe" ta yi maganar tana dafe kanta, da ya yi mata nauyi.
***
A tsaye yake a kanta yana ƙare mata kallo, yanayin yadda
take a kwance ya tabbatar masa da salla ta yi.
Ruwan robar hannunsa ya fara zuba mata a Jikinta, hakan ya
razanata ta tashi a gigice.
Ya watsa mata sabulu da soso a jiki ya ce "Ki tashi ki
je ki yi wanka, ba na son ƙazanta, kar ki haifar mini ɗa mai dauɗa"
Ta yinƙura ta tashi da kyar, tana jiri, ga yunwa ga zazzaɓi
ga kwana da ta yi amai, ta din ga bin bango, har ta isa banɗaki.
Ta daɗe a banɗakin tana kuka, sannan ta yi wankan ta fito,
ta tarar da shi a kan gado a zaune yana danna waya.
Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Dalla cire wannan kayan,
ƙazamar banza da wofi, har amai ki ka yi a jikin kayan amma ki ka mayar da su
jikinki" kallonsa take yi, to tsirara yake son ta zauna?
Ya buɗe wardrobe ɗin da ke ɗakin, duk kayansa ne a ciki, ya
jefa mata wata shirt, ya ce ta ɗauka ta saka.
Banza ta yi masa, ta kawar da kanta gefe, wanda hakan ya
hasala shi, yana zuwa gabanta ya kwasheta da mari, abunka da jiki babu ƙwari,
take ta faɗi ƙasa, ta riƙe fuskarta.
"Ke kin isa ina magana ki yi mini banza, ƴar wahala
mara amfani, ɗauki ki saka kan na tattakaki"
Ramma ba ta ƙaunar duk da abun da zai taɓa lafiyar jikinta,
haka ta zura rigar nan, ta zo mata har gwiwa, sai rufe jikinta take yi.
Ya danƙota, ya fita falo da ita.
A falon ya haɗa mata baƙin shayi, sai soyayyen dankali da
ketchup ya ce ta ci.
Gaba ɗaya a tsorace take, saboda kar ya kuma dukanta, haka
ta din ga tsakura tana ci tana hawaye.
Ta gama ci, ya ɗaukko alluran zazzaɓi da yake yi mata yayi
mata.
Ta lura yana da mai aiki a gidan namiji, har girki da gyaran
gidan shi ne yake yi masa su.
Ya kashingiɗa yana kallon tv, ita kuma tana gefensa a ɗarare,
sai mutsu-mustu take yi tana share hawaye.
Sahidar yatsunsa ya gani kwance a fuskarta, har ya ɗaga ya
basar ya cigaba da kallonsa yana kaɗa ƙafa.
***
"Allah ya taimaki maigida"
"Menene labari?"
"Na samu kiran waya ɗazu, wata yarinya ta je an kaita
har ofishin secret files, an ɗaukko mata file ɗin viper ta duba"
"Wacece ita?"
"Yarinyar da ka ce ayi amfani da ita a kama Viper"
Da sauri ya ce "What? Ya aka yi ta san da file ɗin ta
je? Waye ya ce a bata?"
"Wallahi ban sani ba, amma an tabattar mini da ga sama
su ma aka ba su umarnin ba ta"
"Sama ina, waye ya bayar da umarnin?"
"Ban sani ba wallahi, kuma da gaske lawyer ce, idan
kuwa haka ne, za ta iya yiwuwa da gaske ta haɗu da Viper, ƴar jaridar nan raina
mana hankali ta yi"
Indabo ya numfasa ya ce "Kar ku yi gaggawa, kar ta san
mu na bibiyarta, ka bi ta hannun ƙawarta, ku samo me take son samu a kansa,
idan ta ƙi, ku kamata ku azabtar da ita".
Ya amsa da "Ok sir".
Daga kotun, gida arfa ta tafi, tun daga shigarta, Sauda ta
fara tsokanarta da faɗa, amma ba ta ita take ba, ɗakinta tafi ta cigaba da
tunani da lissafi.
Kamar wadda aka zungura, ta ɗaukko wayarta ta kira Nasir.
Murya ƙasa-ƙasa ya ce "Arfa ya dai? Mun shiga meeting
ne"
Kamar za ta yi kuka ta ce "Yaushe za ka dawo?"
"Zamu yi waya an jima, ki yi haƙuri"
"Kar ka kashe mana dan Allah, ni ina cikin damuwa
magana nake son mu yi, wani abu zan baka"
Ya ce "Wani abu me?"
"Abu ne mai muhimmanci a kan viper, amma sai ka yi mini
alƙawarin ba zaka yi mini faɗa ba ko ka gayawa abba ba"
Tattara nutsuwarsa ya yi ya ce "I hope, ba wata kasadar
ki ka je ki ka aikata ba"
Ta girgiza kai ta ce "Ba wata kasada da na yi, ni dai
ka yi ka dawo, kan na mutu"
A rikice ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
menene ki gaya mini"
"Ka kwantar da hankalinka, kawai dai ka yi ka dawo,
abun yana da muhimmanci, na san yadda zaka same shi kai tsaye"
"Kin ga ba zan iya jira ba, gaya mini menene sai na
aika su Mu'azzam, dama wanda aka kama ɗin nan ya ƙi magana"
"Sai ka dawo gaskiya" ta kashe wayar gaba ki ɗaya,
dan kar ya biyo ta, ta sake dafe kanta.
Sumayya na news room, tana jiran lokaci ya cika, ta gabatar
aka turo ƙofar aka shigo. Sak tayi tana kallon mai shigowar.
Mutumin da honorable ya saka ya karɓi wayarta ne, ranar da
ta je gidansa.
Ya ja kujera yana kallonta, ya ce "Ya dai, kin yi
mamakin ganina ne? Mintuna goma sha biyar suka rage miki, kan ki fara karanta
labaran, zaki yi mini aiki".
Ta zuba masa ido, amma ba ta ce uffan ba.
"Meyasa ki ke yi mana ƙarya a aikinmu? Da gaske ƙawarki
ta haɗu da Viper?"
Cikin ɓacin rai Sumayya ta ce "Na gaji da amsa wannan
tambayar, idan ba ku yadda da ni ba, ku nemeta ta amsa muku mana"
Ya shafi sajensa ya ce "Zamu gani ai, yau ta je court ɗin
da aka yi wa Viper shari'a, ta karɓi secret file ɗin sa ta duba, zaki kira ta,
ki ji dalilin zuwan ta, da kuma abun da za ta yi da file ɗin"
Sumayya ta girgiza kai ta ce "Nabila ba wani abu da za
ta amfana muku, kawai na san ƴar rigima ce, so take ta yi suna ta ɗaukaka ta
taimakawa yayanta shikenan"
Yayi dariya ya ce "Za mu gani, daga yanzu zuwa azahar ɗin
gobe, idan baki kawo rahoton dalilin bin diddigin shari'ar Viper da take yi ba,
abun da ba kya zato zai faru" ya miƙe tsaye ya ce "lokaci ya cika, ki
gabatar da aikinki"
Sumayya ta dafe kai cikin matsananciyar damuwa, tana tunanin
wannan wace irin rayuwa ce.
Murtala ne ya shigo yana faɗin "Afuwan sisyna, mamager
ya kira ni ne, na saita komai ki fara".
"Ba ka ga mutumin da ya fita yanzu ba?"
Ya kalli ƙofar ya ce "Ban ga kowa ba"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan mu fara".
***
Ƙaramar wayarta ce isheta da vibration a ƙasan pillow, ta ɗaga
ta ce "Bacci fa nake ki ke ta kiran wayata".
"Haka dai, daga bacci sai kwalliya da cin abinci, ke
har kin koma gida kin kwanta, ni tun 9 gani har 5 ban tashi ba"
Nabila ta ce "Ke ba na samun bacci a ƴan kwankin nan
wallahi"
"Meyasa?"
"Wallahi a tsorace nake, ba na iya bacci, gani nake
kowane lokaci viper zai kashe ni, cewa yayi fa sai ya kashe ni, sonake Yaya ya
dawo na danƙa masa wayar nan, na huta, wai da wayar wa ki ka kira ni ne?"
Sumayya ta ce "Wayata ce ta ɗauke, ina ki ka je ne
yau?"
"Wurin aiki mana, amma da labari sosai, mu haɗu gobe in
Allah ya kaimu"
"Yakamata mu haɗu kam, dan na ga mutuniyarki bunkure, a
gidan honorable Indabo"
Daga kan gadon da Nabila take ta miƙe tsaye ta ce "Amma
ba ki gaya mini ba sai yau?"
"Na san halinki ne, uzzura mini zaki yi, ke bari na
tafi gida ma yi magana"
Ta kashe wayar, ta kaiwa murtala wayarsa, dan ta fuskanci
mutanen honorable na bibiyar kiran wayar da take yi.
Wuni guda ramma ba ta sake saka Abdul a idonta ba, sai dai
kukunsa idan ya kammala girki, ya ƙwanƙwasa mata ƙofa ya ajiye mata abinci.
Tayi kuka har ta gaji, ta koma addu'a, tare da fatan Allah
ya kuɓutar da ita daga sharrin zaluncin Abdul.
Tana zaune a ƙasan carfet, har wurin sha biyu na dare, ya
shigo yana kokawa da ƙofar ɗakin, saboda a buge yake.
Ta tashi tsaye cikin tsoro, sai dai ba tare da ta yi masa
laifin komai ba, ya hau ta duka, ya din ga ball da ita yana taka ta da ƙafarsa,
tun tana kururwa har ta kasa sai ajiyar zuciya, ko ƙwaƙwƙwaran motsi ba ta iya
yi.
Tamkar dabba haka ya afka mata, ba tare da la'akari da
ƙarancin shekarunta ba, kodayeke ina tunani ga wanda hankalinsa ya gushe?.
Bai farka ba sai kusan tara na safe, yayi miƙa ya tashi yana
kallon ɗakin, da sauri ya kalli gadon bai ganta ba, ya kalli jikinsa, ya tashi
yana mayar da kayansa, kawai ya ga jini a gefensa, har zuwa banɗaki, cikin
hanzari ya nufi banɗakin, ƙofar tana buɗe dan haka ya shiga, ya tarar da ita a
zaune ta jingina da jikin bath jini yana ta zuba daga jikinta, ga jikinta duk a
kumbure saboda duka, idonta a rufe.
Ya ƙarasa ya durƙusa ya ɗaga hannunta ya saki, ya ga ya koma
babu alamar numfashi a tare da ita, rigarsa dake jikinta, tayi sharkaf da jini.
Dafe kansa yayi yana tuna abun da ya faru jiya, kamar
mafarki.
🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA
ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*
16
Shi gashi ko sunanta ma bai sani ba, ya sake ɗaga hannunta,
amma hannun ya sake dawowa ƙasa.
Ya kai hannunsa hancinta, ya ji tana numfashi kaɗan-kaɗan.
Ya haɗa ruwa a bath ɗin mai ɗumi, ya cire rigar jikinta ya
ajiye a gefe.
Ya ƙarewa jikinta kallo, ko ina shatin duka ne da ya yi
mata, take wani abu mai kama da tausayinta ya ɗarsu a ransa, ya ɗaga ta, ya
sakata a cikin bath ɗin, ga abun da ta yi ɓari nan daga cikinta a ƙarƙashin ta.
Duk da ƙyanƙyaminsa, da yadda ƙarnin jinin yake hawar masa
ka, haka ya din ga tarar ruwa, yana kwarawa a banɗakin, ita kuma ya din ga
canza ruwan da take ciki, saboda yadda yake ɓaci da jini.
Rigarta kuwa, wuri guda ya ware ta, dan kuwa yarwa zai yi,
bai san yadda zai yi da ita ba.
Ya fita da sauri, ya kira mai aikinsa solomon, ya rubuta
masa abubuwan da yake buƙata ya ce ya sayo masa.
Har solomon ya je ya dawo, yana ta ƙoƙarin ganin ya tsayar
da jinin da take zubarwa.
Ya ɗauke ta zuwa kan gado ya kwantar da ita kamar gawa, ya
sake ɗiban jininta, ya yi bawa solomon ya ce ya kai kowane lap ne, idan ya kai
ya kira shi a waya.
Ya saka mata drip hannu biyu, ya sake su, yana yi yana duba
vitals ɗin ta.
Ƙofar ɗakin ake ta bubbugawa, ya tashi ya buɗe, ya ga saif a
tsaye.
Saif ya kalleshi ya ce "Ya na ganka kamar mara gaskiya?
Lafiya kuwa?"
Ya girgiza kai ya ce "Ina fa lafiya, yarinyar nan ce
tayi miscarriage"
Saif ya ce "Shi ne me to? Dama ba haka kake so ba, na
ga ma fa kasheta za ka yi ka bar ta"
Abdul ya ce "Haka ne, jiya daka sauke ni bayan ka tafi,
ka san a buge nake, na dake ta sosai"
"Lallai Abdul, yau ka fara yi wa mata haka to?"
Ya girgiza kai ya ce "No, kawai su sauran su ne suke
kawo mini kansu, shiyasa ban taɓa jin komai ba a kan abun da nake aikatawa, sai
ta ji sauƙi sosai, zan kasheta na huta"
Saif ya ce "Well mu je in ga jikin nata"
Abdul ya tsaya a gaban ƙofar ya ce "No, ba zaka shiga
ba"
Cikin mamaki ya kalli Abdul ya ce "Lafiyarka
kuwa?"
"Ras nake, ba zaka shiga bane kawai"
"Ka kashetan kenan?"
"Idan na kasheta, zan kasa gaya maka ne, ko tsoronka
nake ji?"
Suna haka solomon ya kira shi, ya haɗa su da masu lap, ya
gaya musu gwaje-gwajen da yake so a yi wa jinin ramma da ya bayar aka kai.
Ya koma ɗakin da take, ya rufe ya saka mumulli, ta ciki, ya
sake nufar gadon, ya hau yana tattaɓata ya ga ko ta na da rai.
Ambaton Allah ya ji tana yi, tare da kiran sunan mama
ƙasa-ƙasa, sai dai bai ma san sunanta ba balle ya kira sunan.
A hankali ta buɗe idonta a kansa, ta yinƙura za ta tashi,
amma ta kasa, duk jikinta ciwo yake yi, mararta ma wani irin ciwo take yi mata.
Ya riƙe hannunta, yana tsareta da idanunsa ya ce
"Sannu"
Hawaye ya shiga ziraro mata ta gefen idonta ta ce "Me
na yi maka jiya ka dake ni?"
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "A buge nake ne ba abun da
ki ka yi mini"
Cikin ƙarfin hali ta ce "Allah ya saka mini, na barka
da Allah"
Ya amsa da "Tom"
Ta sake yinƙurawa za ta tashi, amma ya riƙeta ya ce
"Ina zaki?"
"Salla zan yi"
Abdul ya ce "Ki na zubar da jinin zaki yi salla?"
Ta ɗan gyara kwanciyar ta, cike da takaicin yanayin da
take ciki, da kuma kallon da yake yi mata, cikin marairaicewa ta ce "Dan
Allah ka rufe mini jikina, ka daina kallona".
Da idanunsa ya tsatstsareta, yana yi mata wani irin kallo,
da ya ƙara ɓata mata rai, ta ɗaga hannunta da kyar, za ta ja zanin gado da ya
rufe mata ƙafa, ta rufe jikinta da ko arzikin vest babu, amma ya riƙe hannunta,
ya mayar ya ajiye wuri guda.
Ya ce "Idan ruwan nan ya goce, mutuwa zaki yi, dan kin
zubar da jini sosai, kuma bana fatan ki mutu yanzu, sai kin samu ciki, kin
haifa mini ɗa, saboda zuciyata ta so abun da yake cikinki, ya zube".
A hankali ta cigaba da sheshsheƙar kuka, tare da fatan ta
mutu ta huta da wannan bayahudiyar rayuwar da ta faɗa, duk a silar talauci da
rashin galihu, ta san Allah kaɗai ya san halin da mahaifiyar ta take ciki, na
tashin hankalin rashin sanin in da take.
Idonsa ya sauka a kan taruwar jinin da ya kwanta a gefen
wuyanta, ya ƙara tabattar da ba ƙaramin duka ya yi mata ba.
A karo na farko da ya ji waji abu mai kama da tausayin wani
ya shiga ransa, she look very innocent and calm.
***
Tun da Nabila ta shiga office ɗin Barrister Habib, take
murmushi, shi ma murmushin ya yi mata ya ce "Ya ake ciki ke ƴar
ƙwalisa"
Ta zauna tare da faɗin "Godiya nake barrister, jiya ai
na je, an bani duk abun da na buƙata, na gode sosai da sosai Allah ya saka da
alkhairi"
Barrister Habib ya amsa da "Amin ya rabb, ina fatan
babu wani abun?"
Ta ce "Akwai, abubuwan da na gani sun ɗaure mini kai,
ashe kisan kai yayi"
"Ba abun mamaki bane ba, dan mutum irin wannan ya yi
kisan kai ai".
Ta ce "Haka ne, amma shekara biyar ya yi ba a yi masa
shari'a, kuma aka sake shi, ba tare da wani cikakken dalili ba, gaba ɗaya ma
akwai abubuwan da babu a cikin file ɗin nasa ma"
Ya ce "Nabila cases irin wannan ai da yawa, sai fatan
Allah ya kyauta"
Ta amsa da "Amin, yanzu saura alƙalin da ya yi masa
shari'a, na ga an rubuta justice zakariyya, amma babu surname ɗin sa"
Barrister Habib ya yi murmushi ya ce "Shi kuma me zaki
yi masa?"
"Kawai so nake na sani"
"Ai an yi masa transfer ma daga kano, bama ya ƙasar ya
je ƙaro karatu"
Nabila ta ce "Kuma duk hakan yana da alaƙa da case ɗin
viper?"
"A'a ba na ce ba, na dai san shi ne before, bani da
tabbacin yanzu"
Ta ce "Na fahimta, na gode sosai da sosai, bari na je
zan ga Sumayya, yanzu zan dawo, na yi mata alƙawarin haɗuwa da ita yau"
Ya ce "Ok, Allah ya tsare"
Ta tashi ta fita, dan kuwa yau ba ta da aiki sosai.
Sosai take son ganin sumayya, domin ta ba ta labarin halin
da ake ciki, a kan binciken da take yi a kan viper.
Ta kira sumayya ta ce mata za ta shiga gidan radiyonsu, su
haɗu a can.
Tana fitowa daga gate ɗin, ta tarar da wani mai napep a
tsaye, ta ce "Malam tafiya zaka yi?"
Ya ce mata "Eh"
"Yauwwa, mu je" ta kama adaidaita sahun ta shiga,
tana ƙoƙarin ɗaga kiran da yake shigowa wayarta.
Sai dai ba ta kai ga hakan ba, wasu matasa suka shigo napep ɗin,
suka zauna a gefe da gefenta, suka rufe mata baki da ido, mai adaidaita sahun
ya ɗauke kan babbar hanya ya yi wani wurin.
Kusan awanni biyar, ramma ta ɗan samu ƙwarin jikinta, har ta
samu ta yi wanka, sai dai ta kasa cin komai, ya sake ba ta wasu kayan a cikin
nasa, duk da sun yi mata yawa, ta karɓa ta saka, ya ja hannunta zuwa falo.
Solomon ya kawo abinci, da fruit, Abdul ya kalleta ya ce
"Me zaki ci a nan?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"Wallahi ko ki ci abinci, ko na sake yi miki tsinannnen
duka a wurin nan, bana son shashanci bar ganin ina lallaɓa ki"
Cikin tsoro ta din ga cakalar abincin, tana ci tana kuka.
"Ke, meye sunanki ne ma?"
Jiki a sanyaye ta ce "Ramma"
Ya yatsine fuska ya ce "Meye wani ramma, ba rahama
ba?"
"Eh rahama"ta amsa tana sunkuyar da kai.
"Meye yake yi miki ciwo yanzu?"
Ta ja majinar da take shirin zubo mata, ta goge hawayenta ta
ce "Duka jikina"
"Dukan da na yi miki ne, gama mu koma ɗaki, sai na yi
miki tausa"
Manyan idanunta ta kafa masa, tana kallonsa.
"Ki daina kallona da wannan ƙwala-ƙwalan idanun naki,
idan ba haka ba, na fita sai kin ganni".
Ta din ga wasa da doyar, ta kasa ci, ta kuma rasa abun yi.
Shiru-shiru sumayya ta din ga kiran wayar Nabila, ga wayar
na shiga, amma ta ƙi ɗagawa har ranta ya fara ɓaci, gefe guda kuma ga mutanen
honorable na ta kiranta su ji, yaya suka yi me Nabila ta yi da file ɗin viper
da ta je nema.
Nabila ta na ji aka sauko da ita daga cikin adaidaita sahun,
bayan shafe lokaci ana tafiya.
Babu bakin magana, an rufe mata baki, an ɗaure mata ido, sai
addu'a kawai take yi a zuciyarta.
Kwance mata idanu suka yi, ta yi tozali da Walid a gabanta
yana yi mata wani irin mugun kallo, sai da hantar cikinta ta kaɗa.
Wurin da suke kamar jeji, babu gida gaba babu a baya, sai
shi da ƴan daban da suka kawota, ashe mai napep ɗin nan ma duk set up ne.
Jikinta ya hau tsuma, sai dai ta kasa magana, amma duk da
haka godewa Allah take yi, da ba wurin Viper suka kaita ba.
"Yanzu abun da ki ka yi kin kyauta kenan?" Walid
ya yi maganar yana tsareta da idanunsa.
Ta sunkuyar da kai, ya daka mata tsawa ya ce "Tambayar
ki nake yi, da ki ka saka a ka kama liti shi laifin me yayi miki, ina har in da
Vipern yake kin sani, kuma kin je, meya hana ki tura kai tsaye a kama shi?
Yanzu gashi ina ta fama da shi, ya ce lallai zai miƙa kansa
ga hukuma, saboda a saki liti, ba zai sake bari wani ya wahala saboda laifinsa
ba"
Cikin dakiya Nabila ta ce "Dama haka ne ya dace da shi
ai, mutumin da yayi kisan kai aka sake shi, kuma yake zubar da jinin mutane ai
hakan yakamata yayi, ta haka ne zai wanke nauyin laifukan da ya aikata"
Walid ya ce "Haka ki ka ce? Da ya yi kisan kai wa ya
kashe?"
Ɗaya daga cikin su ya ce "Me gida, ka bari mu cire mata
ta yatsu ko za ta dawo hayyacinta, ji fa maganganun da take faɗa a kan
master".
Ya ɗaga musu hannu, ya dube ta ya ce "Shikenan, kin yi
gaskiya yayi kisan kai, zan bar Al'amin ya miƙa kansa ga hukuma, amma ki sani
duk hukuncin da aka yi masa, ke zaki ɗauki nauyin alhakinsa, idan ma amfani ake
da ke dan cimma wata manufa a kansa, wanda suke amfanin da ke sun bar ki a
duhu, amma kafin nan yakamata ki san waye Al'amin, meyafaru da shi, daga nan
kuma duk abun da ki ka yanke ya rage naki!!!.
GUNDARIN LABARIN.
Tsaki yake tayi a jejjere, yana kaiwa yana komowa a
matsakaicin falon, yana sauke numfashi.
Matar da ke zaune a kan kujera ta kalleshi ta ce "Wai
yanzu dan Allah wannan sintirin ne zai baka mafita?"
Kamar mai jiran ƙiris ya ce "To yaya zan yi? Magana fa
ake ta makomar siyasata, idan muka faɗi zaɓen nan akwai matsala, kuma malamin
nan ya tabattar mini da na cika kowane sharaɗi, sai zubar da jini ranar zaɓe,
kuma alamu sun nuna gwamnati da gaske take, za a tsaurara tsaro sosai da sosai
a wurin zaɓen nan, kuma idan ba a cika wannan sharaɗin ba, komai fa ya
rushe"
Matar ta numfasa ta ce "Duk ina yaranka marasa jin nan
ne, da suke yi maka aiki?"
"Bilki duk suna hannu, kuma babu wani cikakken jan wuya
da zai iya tarar aradu da kan nan, idan aka kama mutum da tayar da tarzoma a
wurin, shekara sha biyar ne a gidan yari".
"To sai me, kai zaka yi, ka biya su su yi aiki
kawai".
"To ai ki gane, duk sun tsorata da hukuncin ne"
Bilki tayi murmushi ta ce "Ka fito da mai dogon zamani
mana, kai ka san zai iya, Al'amin ba"
Ya kalleta sannan ya nemi wuri ya zauna ya ce "Kuma fa
kin kawo shawara, sai dai yaron ne hukuma ne sai da rarrash, ban taɓa ganin ɗan
iska mai mulkin tsiya ba sai shi, tsaf zai ƙi yi, saboda kusan watanni shida
yana tsare ban fito da shi ba"
Ta ce "Amma ai yana jin maganar ka, zai yi ba ni da
wata tantama"
Ya jinjina kai ya ce "Hakan za ayi, zan saka a fito da
shi"
***
Sanye take da dogon hijjabi launin maroon, har ƙafarta
hijjabin ya ɗauki guga, ƙafarta sanye da safa baƙa, sai sauri take yi tana
ratsa lunguna har ta iso ƙofar gate ɗin makarantar islamiyyar. Sai dai duk
wannan saurin da take yi, an riga an fara tarar makara, wanda idan da abun da
ta tsana, shi ne a taɓa lafiyar jikinta.
Kusan mintuna goma ya ƙara, bai shiga ajin ba domin yi musu
ƙari, yana jira ya ga ta ina za ta ɓullo, yana ofishin malamai, yake hango
yadda malam hamza ya zage ƙarfin sa, yana shimfiɗa mata murtukekiyar dorina a
jikinta, sai kuka take tana bashi haƙuri.
Sam bai ga fa'idar duka a cikin ladabtar da ɗalibai ba,
mussaman mata, macen ma mai rauni kamar wannan baiwar Allah.
Litattafan sa ya kwasa, ya tafi ajin nasu, malam Jamil
kenan, ba ya duka ba ya zagi da cin mutuncin ɗalibi, amma ɗalibai na ganin
girmansa da mutuntashi.
Ana tsaka da tilawa ta shigo ajin, ta nemi wuri ta rakuɓe a
gefe, ɗaya bayan ɗaya ɗaliban suke tasowa, suna zuwa gabansa da littafi, suna
bayar da haddar Alqur'ani mai girma, idan ya kammala ji, ya rubuta maka making
haddarka, sauran ɗalibai kuma na cigaba da tilawa, sai dai fiye da rabin
hankalinsa yana kanta.
A haka har aka zo kanta, ta tashi jiki babu ƙwari, ta je
gabansa ta zauna, ta miƙa masa littafinta, ya karɓa yana dubawa, ba bu in da
take da maki ƙasa da casa'in da biyar.
Tayi bisimillah, ta fara karanto wurin haddarta, sai dai ba
aje ko ina ba, muryarta ta fara rawa, kuka ya ƙwace mata, bai ce mata uffan ba,
ya cigaba da kallon ɗaliban, tamkar haddarta yake ji.
Sai da tayi sosai, sannan ta cigaba da karatun, tana yi tana
share hawaye.
"Ba kya son duka meyasa ki ka makara?" Maimakon ta
bashi amsa, sai ta sake fashewa da kuka.
"Kin ci abinci ne?"
Ta ɗaga masa kai alamar eh.
"Wani abun suka yi miki a gidan" ta girgiza kai
alamar a'a.
"To ni wannan haddar taki, ban ji ta sosai ba, dan haka
sai kin sake wata, je ki zauna, kuma ki daina wannan kukan" ta jinjina
masa kai, ta share hawayenta.
Sai dai zamanta ke da wuya, sai ga malam hamza ya shigo da
dogon littafi, yana muzurai.
Yayi wa malam Jamil magana sannan ya ce "Duk wanda ya
ji sunansa, ya tashi ya je gida, kar ya sake zuwa sai ya biya kuɗin term, tun
da ba da yawun bakinmu zamu biya malamai ba, tun da iyayenku ba sanin darajar
malaman addini suka yi ba, da dai na boko ne.
Sunan farko sunanta ya fara kira, ya ce "Ke waliyiyya,
duk term sai an kore ki, sai an yi ta artabu kan ki biya kuɗin term, duk wannan
uban shirgegen gidan naku, dubu uku a wata uku sai an yi ta fama, tafi gida
idan kin karɓo kuɗin kya dawo".
Ba wannan ne karon farko da aka koreta saboda kuɗin
makaranta ba, sai dai a duk lokacin da aka koretan, ta kan ji ta muzanta ainun.
Haka nan ta ɗauki jakarta ta tafi gida, tana zuwa gidan ta
tarar da wata babbar mace ta shirya za ta fita unguwa, ita da wata budurwa.
"Me kuma ki ka dawo yi, an tashi ne?"
"A'a mama, wai kuɗin makaranta aka turo ni na karɓa"
Matar ta kwaɓe baki ta ce "Uban naki bayanan ai, tun da
kin dawo dama unguwa zan je, maza ki ɗora girkin dare, bana son yin daren
girkin nan" ta amsa da to.
Budurwar ta ce "Yauwwa Jauhar, akwai kayana a kan gado,
dama jibi zan koma school, tun safe nake jiran mai wanki, ya zo ashe ya tafi
gida, kya wanke mini, har bedsheets ɗi na, bargona kuma na jiƙa shi, yana baya,
idan ya so kan mu dawo idan sun bushe, ko gugar kya rage mini ki goge su".
Ta sake amsawa da "To, sai kun dawo"
Ta ƙarasa ɗakin da take kwana, ta hau cire uniform, ranta
babu daɗi, duk ƴan gidan suna makarantun islamiyyar su, ita kuwa an korota daga
ta su, kullum sai an kai ruwa rana kan a biya mata kuɗin makaranta, alhalin
sauran har na term uku ana biya musu.
Ta canza kayanta zuwa na gida, ta shiga kitchen ta kunna
gas, ta tarar ya ƙare, ba ta jira komai ba ta ɗebi itace, ta fita garejin
gidan, ta tayar da wuta ta ɗora girki.
Ba ta fi shekara goma sha shida ba, amma yadda take sarrafa
jikinta tana aiki, kamar wata babba.
Tana girki tana wanki, a haka ƴan islamiyya suka dawo, kowa
ya watsar da jakarsa, da uniform ɗin sa, masu ball suka tafi, masu wasa suka
fita, duk suka sake ɓata gidan, ta bi ta sake tattarewa, ta haɗo kan kayan da
suka watsar su ma ta zuba ruwa za ta wanke.
***
Fuskarsa murtuk, kamar bai taɓa dariya ba, haka ya tunkari
ƙofar gidan, yana wata irin tafiya, mai kama da ta ƙasaita, maimakon ya saka
hannu ya buɗe ƙofar gidan, wani irin duka ya yi mata da ƙafarsa, ya shiga ba
tare da ko sallama ba.
"Wane mara hankalin ne yake dukar mana ƙofa haka, sai
ya karya..... Shiru ta yi ta haɗiye sauran maganar, ganin wanda yake tsaye
ƙerere a gabanta.
"Yaushe ka fito? Ko in ce waye ya fito da kai?" Ko
kallonta bai yi ba, ya cigaba da takun ƙasaita, ya je ya tura ƙofar wani ɗaki,
ya shiga sai dai babu kowa a ciki, dan haka ya fito ya nufi kitchen.
"Al'amin kar ka shigar mini kitchen, ban dafa komai da
kai ba, na ga lokacin fitowarka daga prison ma bai yi ba, wannan jaraba da
masifa Allah ya yi mini maganinka" ba ta gama maganar ba, ya fito daga
kitchen ɗin, da kulolin abinci.
Shan gabansa tayi ta ce "Kar ka taɓa mini abinci,
abincin ƴaƴana ne da na mijina, bana son tashin hankali Aminu, ka je ka ajiye
mini"
Take ya juya idanunsa yayi mata wani irin kallo, a take ta
ja da baya ta koma gefe, tana bin fulasan hannunsa da kallo.
Wani irin fito ya yi, wani daga waje ya amsa masa da fiton,
ya fita da fulasan abincin ba tare da ya amsa ko ɗaya daga maganganun da matar
ke ta yi masa ba.
Jauhar kuwa, kafin magariba ta kammala girkin nan, ta
kawwame a flask, sai gyara gidan take yaran suna ɓatawa, da masu hankalik
cikinsu da marasa hankalin duk babu mai taimakawa a gyara. Ta ɗauki abincin
maigidan ta kai masa ɗakinsa.
Tana idar da sallar magariba, ta shirya ta ɗauki jakarta,
dan tafiya makarantar dare.
Tana fita maigidan yana dawowa, yayi parking ya sauke
glashin motar ya ce "Waliyiyya an fito?"
Murmushi ta yi, sai da fararen haƙoranta suka bayyana ta
ce "Baba kai ma waliyiyyar zaka ce mini?"
"Eh mana, ba haka malamanku suke ce miki ba, za a tafi
makarantar ne?"
Ji tayi kamar tayi masa maganar kuɗin term ɗin ta na
islamiyya, amma ta kasa, mussaman da tuna gargaɗin mama da tayi mata.
Ta ce "Eh baba, sannu da zuwa, na kai maka abincinka ɗaki
ma, kana zuwa sai dai ka ci"
Yayi murmushi ya ce "To Allah ya yi albarka, a kula
sosai ayi karatu da kyau"
Ta ce "In sha Allah" ta wuce makaranta shi kuma ya
gyara parking.
Gudun kar ta makara a makarantar dare, ya sanya ta fita ba
ta ci abinci ba, duk da yunwar da take ji, ta ce idan ta dawo sai ta ci.
Sai dai bayan dawowartata, ta tarar da an cinye komai.
Cikin girmamawa ta ce "Mama an cinye abinci ne?"
Mama ta kalleta ta ce "Au ba ki ci ba dama?".
"Eh, na rana ma ban samu ba, na rufe nawa saboda kar na
makara na tafi makarantar dare".
"Eh to ai yayi kyau, al huda huda ina da littafi, to an
cinye ki zuba ki ci kan ki tafi ba zaki iya ba, duk salon ace zaluntarki ake yi
ba a baki abinci, kin wa kanki ai, ni ki hanzarta ki yi wa yara gugar uniform,
tun da ga wuta, kar a ɗauke"
Ran jauhar ya sosu rashin samun abincin nan, dan har ga
Allah tana jin yunwa sosai da sosai, sai dai babu yadda ta iya, dole ta shiga
ta kwaso tulin guga ta hau yi.
Tana gugar nan zabga-zabgan ƴan matan gidan suna kawo mata
karon nasu, har wurin sha biyu na dare tana abu ɗaya, ga cikinta sai ƙara yake
yi tana hamma, ga bacci da gajiya, ga kuma yunwa.
Bayan ta kammala guga, ta bi manyan ɗakunansu ta ba su, ta
kai na sauran yaran ɗakin iyayensu, sannan ta koma ɗakinta, ta yi alwala tayi
sallar isha'i, ta yi shafa'i da wuturi, ta nemi ta kwanta. Ba ta yi mintuna
goma sha biyu da kwanciyar ba, ta jiyo ana ƙwala mata kira a tsakar gida.
Haka ta sake yinƙurawa, ta fito matashin saurayi ne, tsaye
hannunsa riƙe da leda ya kalleta ya ce "Kin fara bacci ne?"
Ta ce "A'a yaya, idona biyu"
"To ga indomie nan, faka-faka dafa mini dahuwar nan
taki, mai muslmin daɗi, akwai gasashshiyar hanta a ciki da ƙwai, na san akwai
attaruhu da alabasa a gidan, tayi yaji fa sosai"
Ta karɓa ta ce "amma yaya da daddare nan ka ci yaji ka
kwanta, ulcer fa"
Zare mata ido yayi ya ce "Sai kin saka an yi mini faɗa
ko, maza dafota ƙwan nan fa ya soyu shi ma"
Tayi murmushi ta koma ta sake gangamin haɗa wutar da ƙanan
itace, dan kuwa, ta riga ta kashe murhun, kuma ba ayi refilling ba.
Kasancewar a gareji take girkin, sauro yayi mata rubdugu da
cizo, sai da wutar ta kama sosai, hayaƙi ya kore su.
Sai da ta gama tana juye masa, sai gashi ya shigo, hannunsa
da leda ɗauke da lemon roba mai sanyin gaske.
"Yauwwa waliyiyya, Allah dai ya tuttula miki albarka,
ya baki miji nagari" ta sunkuyar da kai cikin jin kunya.
Ya samu wuri ya zauna, ya ce "Samo plate ki ɗiba, sai
ki jiye mini sauran"
"A'a ni fa a ƙoshe nake, ka bari na lashe tukunya, ka
san ina son romon indomie"
Yayi murmushi ya ce "Ke ce romon ai"
Ya zuba mata a tukunyar, ya datsar mata ƙwan, jikinta har
tsuma yake yi, tana hannu baka hannu ƙwarya, ba tare da ta san tana hakan ba.
Yadda ya lura tana ta suɗar kwanon, ya san babu lallai ta ci
abinci yau, dan haka ya sake tura mata ta gabansa ya ce "Ungo na
ƙoshi"
Ta ɗan yi saroro ta ce "Yaya Saifu ba daɗi ne?"
"Ina fa, ke kin san duk duniya, babu wanda ya kai ki
iya dahuwar indomie, ƙoshi nayi kawai, ki hanzarta ki gama ki je ki kwanta,
dare yayi"
Ta karɓa ta yi masa godiya.
Sai dai tana gama ci, wani matashin da zai girmewa saifu ya
fito, ya zube mata kayansa na ƙwallon ƙafa, har da takalmi, sai tsamin rana da
warin hammata suke yi, ya ce ta wanke masa kafin ta kwanta. Kamar saifu yayi
magana, amma yayi shiru ya fasa.
Ƙarshe ba ta kwanta ba, sai ɗaya da rabi na dare, shi ma ko
da ta tuna, kwanaki kaɗan suka rage mata jinin al'ada ya zo mata, gashi ba ta
da audugar tare jini, ga kuma kuɗin makarantar islamiyyarta, babu shiri ta fasa
kwanciyar, ta ɗaukko kwanon da take zuba dutsen da take shiri da shi, ana
biyanta, tana tara ƴan kuɗi, duk da shirin ba wata riba ce da shi ba, amma yana
taimaka mata sosai.
Tamkar mai shirin hawan aljanu, haka ta haƙiƙance, tana zuba
masa bala'i, "Wallahi ba zai yiwu ba, dole ka zaɓa ko ni ko ɗan ka, idan
har zai cigaba da shigowa gidan nan, to wallahi ni zan bar shi, dan ba zai
illatani da yarana a banza ba, ko ya lalata mini ƴaƴa ba.
Sanin kanka ɓaras ya karya mini ɗa, Allah ne yayi da sauran
rabon Musa ya taka ƙafarsa a duniya, ga ni da yara mata, ya din ga shiga yana
fita, ba ma wannan ba, yadda ya yi ƙaurin sunan nan a duniya, tsaf zai hana
mini ƴaƴa auruwa, to wa ma zai zo ƙofar gidan nan zance, yana tsoron a
raba shi da rayuwarsa, ba zai yiwu ba gaskiya".
Ya numfasa ya ce "Rahila, da wani idon ki ke so duniya
ta kalle ni? Idan na kore shi na hana shi zuwa gidan nan, yana da in da ya fi
nan ne?"
"Idan ba shi da shi ka nema masa, ni fa ba zan cigaba
da rayuwa da tantirin ɗan daba a cikin gida ba, ya sabauta mini rayuwata da
ƴaƴana ba, Allah ya mayar da shi kurku ya dauwwama a can kowa ya huta, ina
dalili za a hana ni rawar gaban hantsi, mutum ba tarbiyya duk na sangarta shi,
an mutu an bar mutane da masifa da bala'i a bayan ƙasa, me ake da ɗa irin wanda
zahra'au ta mutu ta bari, Aminu ai cikon asara ne a cikin al'umma, wallahi ta
yi asarar haihuwa".
Yana tsaye a bakin ƙofar shiga falon, yadda ta ɗaga murya,
ya sanya ya ji komai, zuciyarsa ta din ga wani irin hanƙoro, wani abu mai
masifar ɗaci ya din ga taso masa.
Ya saka hannu ya danƙe handle ɗin ƙofar iya ƙarfin sa,
saboda muddin ya shiga cikin falon, yadda yake jin sa a saman nan, ya cake da
wiwi, babu abun da zai hana shi ɗaga matar nan, ya buga da ƙasa.
Ya kasa gaba ya kasa baya, shi bai shiga ba, kuma bai bar
wurin ba, kunnuwansa suka cigbaa da karɓar miyagun maganganun da take faɗa a
kansa.
Ƙarar da handle ɗin ya bayar ne, ya sanya su juyowa su kalli
bakin ƙofar, ɓaras ya karya handle ɗin nan, duk ƙwarin sa, ya fara yi mata wani
irin kallo, da ta kasa gane ma'anarsa.
Ayshercool
08081012143
🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA
ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*
Da sauri ta ɓuya a bayan maigidan, hantar cikinta na wani
irin kaɗawa.
Ya nuna kansa da yatsansa ya ce "Haihuwata ce asara ko?
Ni?"
Cikin tsawa ya ce "Kai aminu, ya isheka haka, kar ka
kuskura ka aikata wani rashin mutunci, ko ka ce zaka yi mata wani abu, koma
menene ba kai ka janyo ba, ka nustu ka zama mutumin kirki mana, kalli yadda ka
yi shuhura a shashanci da harkar sara suka, ni kaina ban so fitowarka ba
wallahi, yanzu zaka zo ka cigaba da ɗaga mini hankali, ka hana ni zaman lafiya
da iyalina, dan haka ka bar mini gida, kar ka sake shigo mini gida, ba na
buƙatar ka".
A hankali ya saki handle ɗin ƙofar da ya karya, ya kalli
mahaifinsa ya ce "In daina zuwar maka gida, Abbu ina zani? Wurin wa zan
je?"
"Ka je duk in da ya yi maka, ko wurin ƴan iskan da suka
ka ke jin maganar su sama da tawa, amma kar na sake ganinka a gidana"
Yayi murmushi mai ciwo, ya ce "Shikenan, zan tafi zuwa
lokacin da huce zan dawo"
"Ba na buƙatar dawowarka, tun da ban isa da kai ba, ka
je ka ƙarata"
Tuni idanunsa suka rine, zuwa launin ja jawur "Ba a
canza tuwo suna, ba ni da wanda ya kai ka ko ya fika, ba ni da gidan da yafi
nan, dan haka ba zan daina zuwa gidan nan ba, amma idan ka matsa zan tafi, idan
kuma na tafi na bar shi kenan har abada, wani aiki aka fito da ni na yi, da
yiwuwar idan na gama aikin, na koma gidan yari, komawar da ba zan sake fitowa
ba, sai ku huta da ganina" ya ƙarasa maganar kafofin gashinsa na mimmiƙewa
saboda ɓacin rai.
Rahila ta ce "Allah ya raka taki gona"
Juyawa ya yi ya fice, har da sassarfa, dan yanzu abun da
zuciyar sa ke raya masa, ba iya ya bugata da ƙasa bane, ya raba maƙogwaronta da
wuƙar ƙugunsa haka yake ji.
Tafiya kawai yake yi, yana tunani barkatai a cikin
zuciyarsa, har ya ƙarasa in da yake son zuwa.
Suna ganinsa suka mimmiƙe tsaye, sun risunar da kawunansu,
tamkar dai yadda ake yi wa shugabbani, a wurin shugabancinsu, ba tare da ya ce
komai ba ya zauna, yayi shiru.
Liti ne yayi gyaran murya ya ce "Allah ya taimaki mai
dogon zamani, menene damuwarka ne?"
Al'amin yayi shiru, dan shi bai san me zai ce ba ma.
Ba yadda ba su yi da shi ba, amma yaƙi magana.
Liti ya miƙo masa wani satchet ɗin magani, ya ce "Ga
wannan ka sha rabi, yanzu za ka ji ka ɓata, ka manta komai, wasu ƴaƴan
matsalarka duk za su sauka, daga hau ka saukko za ka ji komai ya goge"
Ya saka hannu ya karɓa, yana jujjuya satchet ɗin.
"Ka saka ɗaya a ƙasan harshenka, shikenan".
Ya ɓalli ɗayan ya saka a ƙasan harshen sa, ya jingina da
bango, zuciyarsa na cigaba da tafasa.
Sai dai bai fi mintuna sha biyar ba, idanunsa suka fara
lumshewa.
Yayi gyaran murya ya ce "Liti"
Liti ya ce "Boss".
"Chairman ya fito da ni saboda na yi masa aiki, ya ce
na je yana son ganina, zai gaya mini aikin da zan yi masa, sai dai kafin na yi
masa aikin zan yi nawa, ko da kuwa zan koma gidan yari ban yi nasa ba"
"Allah ya taimaki maza, wane aikin ne, a shirye muke mu
yi maka ko menene"
Ya jinjina kai ya ce "Madaki zan kashe! Sai na kashe
madaki!!"
Liti yayi turus ya ce "Maza, duk lokacin da muka yi
yinƙurin ɗaukar fansar nan, wahala muke sha madaki fa har tsafi yake yi
wallahi, ya gagaremu"
Ya ɗora yatsansa a kan laɓɓansa ya ce "Shhhh, ni bai
gagare ni ba, zan kashe shi na koma gidan yari"
Liti ya ƙura masa ido sannan ya ce "Maza ko ƙwayar ta
fara yi maka aiki ne?"
Ya buɗe idanunsa da suka yi ja, ya kalli liti, sannan ya
mayar ya lumshe su a hankali, bacci yayi awon gaba da shi.
***
Rana ta take sosai, ƴan makaranta na ta ɓullowa da ga
lungunaa da titunan unguwannin.
Sosai jauhar take sauri, ta je gidan da take yi musu shirin
dutse, ta kai wanda ta yi, ta karɓo wani su bata ƴan kuɗaɗenta.
Babban layi ne sosai, ababen hawa na kaiwa suna komowa, ta
tabattar babu abun hawa, wata danƙareriyar mota, ta shawo kwana a guje, ba tare
da ko yin horn ba.
Gaba ɗaya ta ruɗe, ta kasa gaba ta kasa baya, kawai ta tsaya
ta ɗora hannunta a kan ta, tana maimaita lahaula wala ƙuwwata illa billah.
Da ƙyar ya iya cin burki, ya fito a fusace mutumin, babban
mutum ne sosai, ya kusa sa'an Baba ma, ya hau ta da faɗa "Ba kya gani ne,
wannan wani irin rashin hankali ne?"
Ta kalleshi da fararen idanunta ta ce "Dan Allah ka yi
haƙuri, wallahi na duba ban ga mota ba, ka yi haƙuri dan Allah"
Mutanen wurin da suka saddaƙar sai ya buge Jauhar, suka taso
suna salallami, sai dai aka rasa me nuna masa shi ne yayi kuskure, saboda uwar
shaddar da ta bi lafiyar jikinsa ta kwanta.
Sai kuma jikinsa yayi sanyi, ganin yadda take ta bashi
haƙuri, duk da shi ne mara gaskiya, pressure da yake ciki da tension ne ya
sanya shi hucewa a kanta.
Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "Ki yi haƙuri, ai ba
ki ji ciwo ba ko?"
Ta ce "Babu abun da ya same ni" daga haka ta
tsallaka ta shiga layin da take son shiga.
Kusan dozen biyar tayi na shirin, aka bata naira ɗari da
hamsin, ta kuma karɓo wani tana lissafin saura ɗari biyu da hamsin, ta samu kuɗin
pad, wanda magana ake ta saura ƴan kwanaki jinin ya zo.
***
Al'amin ne zaune a kan kujera, yana wasa da zoben azurfar
hannunsa, Indabo yana ta bayani, amma sam hankalinsa ba a kansa yake ba, dan
bai san me ma yake faɗa ba.
"Aminu magana nake fa"
Ya ɗaga idonsa ya kalle shi ya ce "Ina jinka"
"Yaƙin neman zaɓe da zan je, ina son a zubar da jini
ne, a tayar da tarzoma ayi hatsaniya sosai da sosai, sai kuma ranar zaɓe"
Ba tare da ya kalle shi ba ya ce "Shiyasa ka fito da
ni, saboda zan yi maka aiki shi ne ka fito da ni ko?"
"Eh saboda haka ne, kai ne ba ka ji, ka fiye rigima, na
yi na yi ka fita sabgar madakin nan, ka haƙura, amma kamar annabi da kafiri,
kullum cikin harin juna ku ke, kai ne faɗa a nan kai ne a can, wai fa har sayen
rigima ka ke yi"
Ya katse shi da cewa "Nawa zaka biyani?"
"Zan baka dubu hamsin kai da yaranka".
"Ɗaurin shekara biyar a gidan yari, shi zan yi a dubu
hamsin ni da yarana, ka duba babbar kasada ce"
Indabo ya yi murmushi ya ce "Baka da matsala in dai kuɗi
ne"
Ya tashi tsaye ya ce "Kamar yadda ka yi a wannan karon,
ka neme ni kai tsaye, haka nake son ya cigaba da kasancewa, ba na buƙatar sanya
wani P.A ɗinka ya neme ni, ya sanar mini da saƙonka"
"Na fahimta, ka san mu ƴan siyasa dole sai muna yi,
muna ɓad da sahu, baka da matsala".
Al'amin ya jinjina kai, ya sa kai ya bar falon, cikin takun
ƙasaita.
*****
Saifu ne ya shigo gida, wajen ƙarfe uku da rabi, ya tarar da
Jauhar tana wanki a tsakar gida, gidan babu kowa, yaran duk sun tafi makaranta.
Ta ɗago ta ce "Yaya sannu da zuwa"
Ya amsa da Yauwwa "Ina makarantar islamiyyar?"
Shiru ta yi ta sunkuyar da kai, ba ta amsa masa ba.
"Da ne nake fa"
"Amm..dama ban biya kuɗin makaranta bane, sun ce kar na
sake zuwa sai na biya"
"Kuna kin gaya wa Baba?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
Cikin takaici ya ce "To saboda me?" Ta yi shiru ba
ta ce komai ba.
Saifu ya ce "Ke dai sokuwa ce wasu lokutan, dubu uku ne
ko? Tashi ki saka uniform ki tafi" yayi maganar yana ciro kuɗi daga
aljihunsa, ya miƙa mata dubu uku.
Fuskarta ta faɗaɗa da murmushi, ta saka gwiwoyinta a ƙasa,
ta saka hannu biyu ta karɓa ta ce "Na gode sosai da sosai yaya, Allah ya
ƙara arziki".
Ya ce "Amin, bar wankin, tashi maza"
Ta ce "To kar maman su Hafsa ta dawo ban gama ba,
labulayenta ne"
"Ajiye, su hafsa idan sun dawo su wanke mata, maza ki
tafi".
Cikin murna ta tashi, ta tattare kayan wankin, ta shirya
cikin uniform ɗin ta, ta tafi islamiyya.
Duk da yau ma sai da aka zane ta, sannan ta shiga ta kai kuɗin
makarantar tana ta kuka, dan ba ta ƙaunar duka sam.
Sai dai duk da kukan da tayi, hakan bai hanata farincikin
ganin ta koma makaranta ba.
Sai dai bayan ta koma gida, Anty ta rufeta da bala'in ta
tafi ta bar mata bedsheets ɗin da ta saka ta wanke mata.
Jakarta kawai ta ajiye, ta hau wankin da aka sakata, bayan
ta sha uban zagin tsamar nama, ita duk hakan bai dameta ba, ta kammala wankin
sauran bedsheet ɗin, ta wanke kwanuka ta mayar da abincin dare.
Duk ƴan matan gidan suna zaune, itakaɗai take aikinta a
tsakar gidan, idan baƙo ya zo sai ya yi zaton mai aiki ce.
***
Yau tun a makarantar boko, Jauhar ta ji period ya zo mata,
gashi kuɗin pad ɗin nata saura ɗari da hamsin ba su gama cika ba, sai kame
jikinta take yi, saboda tsoron kar jini ya ɓata ta.
Da ƙyar ta isa gida, tana ta lissafin yadda za ta yi, gashi
idan ta yi amfani da tsumma, lalata mata fata yake yi, ƙuraje duk su feso mata,
ta rasa in da zata saka ranta.
Haka ta wuni tana fama, ga uban ciwon mara, kamar tayi
hauka, dan ma ta samu paracetamol a wurin Yaya saifu ta sha, ga uban aiki dan
babu mai ɗaga mata ƙafa, haka nan ta saka tsumman, take amfani da shi, idan ba
haka ba ta san haka za ta yi ta staining.
Da magariba, tana zaune a tsakar gida, ta cinye ɗan abun da
ta samu ta ci, wanda sam ba ta ƙoshi ba, duk da ita ta girka, sai lashe hannu
take yi, Baba yayi sallama.
Aka din ga jera masa sannu da zuwa, yana amsawa.
Ya kalli Jauhar ya ce "Waliyiyya ya na ga kina suɗe
hannu, ba ki ƙoshi bane?" Tayi murmushi ta girgiza masa kai ta ce
"Alhamdilillah, na ƙoshi baba".
Ya ce "To madalla, Allah shi ne abun godiya, akwai wani
mutum da ya zo wurina yayi mini maganarki, ban sani ba, ko ke ki ka turo
shi" Gaban juahar ya faɗi, ta kalli in da mama ke zaune a kan tabarma, ita
ma tana cin nata abincin. Sau ɗaya saurayi ya taɓa biyota gida, mama ta ce idan
wani ya kuma zuwa wurinta, ko ta bawa wani damar ya zo wurinta, sai ta kusa
halakata, yayyenta ba su auru ba, ba za ta fara kawo musu maza ba, duk da dama
shekarun nata ba yawa ne da su ba, haryanzu a SS2 take shekara goma sha shida,
sai dai hasken fatarta ke ɗaukar idon samari ƴan bana bakwai, su biyota wai
suna so, saboda kashedin mama ta koma saka niƙab.
But Anty, babar su hafsa ta fito daga ɗakin ta, tana jiran
ta ji ƙarashen maganar.
Mama ta ce "Ba magana ake yi miki ba?"
Jauhar ta girgiza kai ta ce "A'a Abba, wallahi ban san
kowa ba, ban turo kowa wurinka ba"
"Ƙarya ki ke yi, zaki aikata, ba abun mamaki bane ba
kina halin kule-kule a waje, dan a zahiri kina da fuskar tsoron Allah, amma a
baɗini ba kya ji" Anty ta ara ta yafa ta ƙarar da zancen.
Baba ya ce "No, shi ma ya gaya mini, bai yi mata magana
ba, ya zo ya fara samuna ne, na dai tambayeta ne kawai dan na tabattar, zan
bashi dama ya fara zuwa wurinta, dan naga da gaske yake yi."
Dumm ƙirjin Jauhar ya buga, ta fara zance yanzu, makarantar
kuma fa, ga burinta na son yin karatu, duk da aure ba ya hana karatu, to amma
idan wanda zata aura ɗin ba zai bari ba fa?.
Da sauri mama ta tashi ta bishi ɗaki, tana yi masa magana
"Yanzu aurar da jauhar ɗin zaka yi, ga yayenta duk a jibge, su kusan biyar
babu wadda ka aurar?"
Ya tsaya ya kalleta ya ce "To laɗifa, tara su zamu yi
tayi ba zamu aurar ba? Tun da ita Allah ya fara kawowa sai mu fara da ita, ita
ma ta huta"
A take ta haɗe rai ta ce "Ban gane ita ma ta huta ba,
na fuskanci duk lokacin da magana irin wannan ta tashi, sai ka nuna kamar bana
ƙoƙari a kan riƙonta, kamar zaluntar ta nake ko?"
Kamar yaronta ya ce "A'a bance ba"
"To wallahi ba za ayi wa jauhar aure ba, ga su Sajida
ba, wannan ai cin mutunci ne".
Yayi mata shiru, bai sake cewa komai ba, ya ƙuduri aniyar,
aurar da jauhar ko ba ta so.
***
A tsakar gida ta tsaya tana ta kwaɗa sallama, daga cikin
falon aka amsa mata, wata matashiyar mata ta fito.
Suna ganin juna suka rungume juna, suna murna.
"Zakiyya Bala, yau ke ce a gari?"
"Wallahi kuwa Rahila".
"Ya aka yi ki ka gane gidan nan? Kin san lambarki na
rasa".
Zakiyya ta ce "Ke wayata aka sace mini, tun da na canza
layi na rasa lambarki nima, ai da Abba na haɗu a bakin titi, ya ce mini ai kun
jima da dawowa unguwar nan, bamu da wani nisa bamu sani ba".
Rahila ta ce "Allah sarki, shigo daga ciki, shegiyar
ƙawata, na yi missing ɗinki fa" suka shiga suna dariya.
Ta kawo mata ruwa da lemo ta ajiye, Zakiyya ta kalli gidan
ta ce "Ikon Allah, nan ku ka dawo kenan?"
"Wallahi kuwa, ai yanzu ba abun, tun da aka damfare shi
ɗin nan, lamuran sai godiyar Allah, amma a hakan ma ai bamu tagayyara ba"
Zakiyya ta ce "Gasakiya ne, Allah ya ƙara rufa asiri,
ina su kursum?"
"Duk suna makaranta, kin san tana level 3 ita yanzu,
ina su hafsa, haryanzu babu labarin aure ko?"
"Haba Rahila, yaushe za ayi auren su Hafsa ba ki ji
labari ba, wallahi babu shiru, abu kamar saka hannu, har na fara zargin
uwargidana, sai na ga ita ma ga nata nan biyu, Sajida da surayya, suma babu ana
ta shige-shige shiru, dan ma ni da ita kar ta san kar ce, an daɗe ana gogawa
taga babu riba, na sha gabanta shi ne ta sarara mini".
Rahila ta ce "Subhanallah, kin ga nima ana ta fama, duk
wanda ya zo kamar walƙiyya sai ya tafi, ni kuma ba zan bawa talaka aure ba
wallahi"
"Ba ke kaɗai ba Rahila, kin ga yaran nan, har mai suka
shafa, sun yi ɗas sun zama farare, kwalliyar nan, supplements ɗin nan, na gyara
dai, amma ba tsayayye duk sai shirmanmu"
"Ki daina damuwa fa, lokaci ne"
"Wallahi haka ne, ba ki san wani abun takaici ba, wai
sai yarinyar nan, ƙanwar bayansu, jauhar ƴar bafulatanar nan da ya taɓa aura
kwanaki, aka rabu tsiya-tsiya ƴar da ta mutu ta bari, wai ita wani ya ce yana
so da aure, yarinyar nan sai da Laɗifa ta shiga ta fita, ko suturar kirki ba ta
sakawa, wai amma a haka wani ya gani yake so, kin san ita ya bawa riƙonta"
Rahila ta kwashe da dariya ta ce "Ai wasu lokutan maza
ƴan wahala ne, ga in da ya dace su je, amma wani wurin suke kai kan su. Ni
kaina ga nawa ɗan riƙon ya sani a gaba, ɗan gidan zahra'u tsinannen yaron da
asiri baya cin sa, babu irin kurciyar dan ban saka ayi masa ba, amma abu ya
gagara".
Zakiyya ta gyara zama ta ce "Ke haba? Al'amin ko"
"Shi, ai ya zame mini bala'i Zakiyya, ya zama riƙaƙƙen ɗan
daba da shaye-shaye, za ki ji matasa suna mai dogon zamani shi ne fa"
Zakiyya ta dafe kai ta ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un, ke ina jin labarinsa har a radio, dama shi ne, amma lokacin kina
amarya kamar a nutse yake"
"Ke rabu da ni oho masa, ni sonake ya bar gidan nan,
kar ya hana mini ƴaƴa auruwa, ko ya illata wani, dan Abba da ki ke gani ɓaras
ya karya mini ɗa kamar kara.
Kina kallon halin da muke ciki, yanzu babu bushasha kamar
da, ɗan abun da ta bari ya gada, ubansa ya fito da shi, ya ƙara jari, yaƙi wai
ba zai taɓa masa kaya ba, kin ga da zai bar gida a neme shi a rasa ai ma samu
mu ci, babu irin korar da ban saka ya yi masa ba, amma yaƙi tafiya".
Haka suka cigaba da hirarraki, wadda galibi a kan rayuwar
makaranta da suka yi, sai na iyalinsu hirrar take.
Kusan sati biyu, da maganar da baba yayi, a kan wanda ya zo
wurinsa a kan jauhar, yayi shiru da maganar kamar ta wuce, ya dawo da yamma,
kasancewar juma'a ce, jauhar ta duƙufa tana ta shirin dutse. Kuɗinta da suka
taru ba ta samu ta sai pad ba, sai ta sayo riɗi, ta ce zata soya ta juya kuɗin,
idan suka taru ta saya da wuri.
A tsakar gida baba ya tsaya, ya ƙwala mata kira, ta amsa ta
fito ta tsuguna.
Ya kalleta ya ce "Ki shirya, ki je ga baƙonki can a
waje ya zo ku gaisa".
Ji tayi kamar ta fyalla da gudu, ta tsaya da saurayi, ya ce
mata me, ko ta ce masa me?
Amma ta amsa masa, ta tashi ta shiga ɗakinta, jikinta duk
yayi sanyi.
Sajida ta shiga falo in da su surayya ke kallon Bollywood.
"Kai kuna nan kuna kallo, baba fa da gaske yake auren
jauhar zai yi muna zaune"
Surayya ta ce "Kamar yaya?"
"Kamar yadda na gaya muku, wallahi wai wani ne wai yake
son ta"
Hafsa ta ce "Da yardar Allah ba za ta yi aure ta barmu
ba".
Jauhar kuwa turus ta yi, tana kallon ƙatuwar motar da ke
ƙofar gate ɗin gidan an yi parking ɗin ta.
Zura kai ta yi tana lelleƙawa ta ga waye baƙon.
Ya buɗe ƙofar motar ya fito, yana murmushi.
Turus ta yi tana kallonsa, ya yi murmushi ya ƙaraso ya
jingina da jikin motar, ya ce "Mayar da idon mana, kin yi mamakin ganina
ko?"
Da sauri ta durƙusa ta ce "Ina wuni?"
"Lafiya ƙalau Faɗimatul Jauhar"
Ya ɗan gyara tsayuwarsa ya ce "Na san dole zaki yi
mamakin ganina, zuwa na yi na sake bayar da haƙuri, a kan incident ɗin da ya
faru, na tsorata ki da na yi, na kusa buge ki da mota"
Jauhar ta ce "Ai bakomai ya wuce, na ma manta"
"Ai ni ban manta ba, dan sai da na koma wurin da muka
haɗu, na tambayi ina ne gidanku, na samu baba muka yi magana, hankalina ba zai
kwanta ba, har sai na aure ki, na kai ki gidana, na rarrasheki da kyau"
Jauhar ta sunkuyar da kanta, tana jin abun wani banbarakwai.
Ita gaba ɗaya ma ji take yi ya takurata.
"Jauhar"
"Na'am" ta amsa tana kallonsa da idanunta da suke
farare tas, sai dai ba manya ne can ba.
"Me ki ka ce? Ni aurenki nake son na yi, kuma nan kusa
wallahi ba da nisa ba, na yaba da tarbiyarki fiye da yadda ki ke tunani".
Kamar za ta yi kuka ta ce "Ai ban gama makaranta ba, ni
yarinya ce kai kuma babba ne"
Dariya yayi ya ce "Wow, ashe shagwaɓaɓɓiya ce har haka?
To dan ni babba ne ba za a aure ni ba? Kar ki ce haka, zaɓin Allah ake nema kin
ji sweetheart, ki yi ta addu'a Allah ya tabattar mana da alkhairi. Ina da mata ɗaya
da yara biyar kacal, yaro ne ni haryanzu" yayi mata maganar yana kashe
mata ido ɗaya.
Ita kam gabanta ne ma ya faɗi, yara biyar ne kacal, ita duk
wata harka da za ace kishiya, tsoronta take ji.
"Kar in cika ki da surutu, bani lambar wayarki, a
hankali zamu saba, kin shiga raina sosai, zan yi iya ƙoƙarina na baki kulawa
dai-dai iyawa ta, kuma karatunki, in sha Allah sai kin ce kin gaji dan
kanki" yayi maganar yana miƙa mata wayar ta saka masa lambarta.
"Bani da waya ai"
Ya ce "Ohh, ashe fa ƴar baby ce, ba ta isa riƙe waya
ba, zan kawo waya in sha Allah"
"A'a dan Allah kar ka kawo mini, ba ma za a bari na
riƙe ba"
"To ikon Allah, to ta ina zan din ga jin muryarki? Amma
shikenan bai kamata na karya dokar gidanku ba, zan san abun yi na nemi iznin
baba na kawo wayar. Amma baki tambayi sunana ba"
Ita dai tayi shiru, tana mamakin yadda babban mutum kamar
wannan, yake ta kashe mata murya.
"Sunana Alhaji Mu'azzam. Ina dillancin kayan sawa,
mussaman na mata, ina shigo da kaya daga ƙasashe daban-daban, kuma ni ɗan
siyasa ne, yanzu haka ina da muƙmi a gwamanati, amma ba dai wannan ba, ni
amincewarki nake nema, kar ki yi saurin rejecting ɗina ki yi mana addu'a kin ji
zahrana"
Jauhar dai ta yi gum, ita wannan tsayuwar ma kawai, kunya
take bata kamar ta falfala da gudu.
Haka ya gama surutansa, ba komai take fahimta ba, lissafi
kawai take a zuciyarta, saura dozen nawa ta gama shirin dutse, ta kai ta karɓo
kuɗin, ta cika ta soya riɗi.
Kuɗin da ya miƙo mata, ya sanya ta ja da baya, tana girgiza
kai. Ya kaɗa ya raya, amma fafur ta ƙi karɓa, sai haƙura yayi.
Haka yayi mata sallama ya tafi, da sauri ta shiga gida, dan
kuwa Alhaji mu'azzam duk ya cinye mata lokaci, ba ta ƙarasa shirinta ba, mugun
kallon da ta tarar da ƴan matan gidan na yi mata a tsakar gida, ya sanya ta
shan jinin jikinta, dan kuwa tuni yaran gidan suka kawo musu tsegumin irin
motar da aka zo wurin Jauhar da ita.
Sai jikinta yayi sanyi, ta hau tunanin laifin me tayi? Jiki
a sanyaye ta ɗaukko aikinta ta cigaba.
Sai dai suka din ga zaginta babu dalili, hafsa ta saka ƙafa
tayi fatali da ɗan plate ɗin jauhar da take zuba dusten.
Hankali a tashe ta ɗaukko tsintsiya tana tattarewa, ba tare
da ta damu da son sanin dalilin da ya sa hafsan tayi mata haka ba, domin kuwa
idan da sabo ta saba.
Yaya saifu da ya fito daga banɗaki ne, ya ɗurawa Hafsa
ashar, saboda ya ga abun da ta yi hafsa.
Babarta ce ta fito tana yi masa masifa, tana kare hafsa, da
mayar masa da zagin da yake yi mata.
Aikuwa mama ma ta fito ta haushi da bala'in menene ruwansa
da shiga abun da babu ruwansa, nan faɗa ya harƙe, sum-sum jauhar ta ja jikinta
ta koma ɗaki.
Da daddare bayan sallar isha'i, baba ya kira jauhar ɗakinsa,
ya tambaye ta yaya suka yi da baƙonta, amma ta kasa magana, sai duƙunƙuna
hannunta da ta din ga yi a hijjabi.
"Jauhar"
Kanta a sunkuye ta ce "Na'am baba".
"Ba zan yi miki dole ba, ban bawa mutumin nan damar
zuwa wurinki ba, sai da na yi bincike a kansa, na san makarantar ki ke tunani,
ina mai tabbatar miki ya tabattar mini zai bari ki cigaba. Bana jin daɗin irin
rayuwar da ki ke yi a cikin gidan nan, babu yadda zan yi ne. Amma idan ba kya
son sa, ba zan yi miki dole ba, ki bi komai a sannu, ki yi istikhara da addu'a,
na san ke mai yawan addu'a ce, da miƙa lamuranta ga Allah, ki ƙara dagewa sosai
da sosai, ki nemi zaɓin Allah"
"To Baba in sha Allah"
"Yauwwa yarinyar kirki, Allah ya yi miki albarka, ya sa
naga jikokina ƴan farare masu kyau kamar jauhar ɗina" rufe fuska tayi ta
ƙunshe fuskarta tana murmushi.
Tun da ya shigo layin, wasu daga matasan layin ke darewa,
suna ɓuya, ko a jikinsa, tafiyarsa yake yi cikin hanzari da ƙasaita, sumar sa
ta cika masa kai, ya aske wani wurin ya bar wani, irin cikakken mara jin nan.
Kai tsaye ya buɗe ƙofar gidan, ya kunna kai cikin gidan.
Babu sallama ba komai, ya kutsa cikin falon in da suke zaune
suna karyawa.
Abbu ya ɗaga kai ya kalle shi, ya ce "Uban me ka zo yi
mini gida? Me na gaya maka a kan zuwar mini gida?".
Ya sunkuyar da kai ya ce "Ganinka na zo na yi na
gaisheka"
"Ba na buƙatar gaisuwarka Al'amin, ai tun da ka zaɓi
watsewa a duniya, ka yi fatali da tarbiyarka nima na sallamaka, ka koma wurin
abokanka ƴan wiwi da suka fi ni a wurinka. Kalli tsinannen askin da yake kanka,
ka zo mini banda warin wiwi babu abun da ka ke yi, sanna ka ce ka zo gaishe ni?
Ai ni na barwa duniya kai ka tashi ka bar mini gida"
Yayi shiru yaƙi tashi, kuma ya ƙi magana, sai murza zoben
azurfar hannunsa da ƙarfi da yake yi, zuciyarsa na zafi.
Rahila ta ce "Dan Allah ka fita Aminu, wannan warin da
ka ke yi, zan iya amai wallahi, kuma ni idan ina ganinka tsoro nake ji wallahi,
tun da kullum a buge ka ke kar ka illatani ko yarana a banza" tamkar tana
magana da dutse, haka yiyin gingirin gim, bai motsa ba.
"Ba magana ake yi maka ba?" Yayi masa maganar
cikin tsawa.
Al'amin ya ɗaga idanunsa, da suka yi ja fiye da lokacin da
ya shigo, ya ƙara matsawa kusa da mahaifiyar, ya zuba masa ido sannan ya ce
"Na san ina wari, na san kullum a buge nake, a kowane lokaci zan iya ɗaukar
makami na hallaka duk wanda ya yi gaba da gaba da ni, ko wanda bai ji ba bai
gani ba. Wasu lokutan ma banbancina da mara hankali kaɗan ne, na san ba na jin
magana ko kaɗan, bana tsoro ko shakkae aikata duk wani abu da zuciyata ta raya
mini, amma idan ban zo wurinka ba wurin wa zan je? Da haka nake? haryanzu ban
san laifina a wurinka ba Abbu, zan yi ƙoƙarin daina zuwa gidan nan kamar yadda
ka buƙata, ko aka ce maka ana buƙata, amma idan na daina na daina kenan har
abada wallahi! Ka huta lafiya" yayi maganar yana shafar saman hannun
mahaifinsa.
Yana miƙewa zai wuce, yayi ball da flask ɗin ruwan zafin da
yake tsakiyar wurin, da kwanukan. Gaba sai da suka razana.
Ta ce "Ka gani ko?"
Shiru mahaifin Al'amin yayi, ya tashi da sauri ya bi
bayansa, sai dai yana fitowa daga falon, ya ga an jefo Abba, babban ɗan Rahil,
ƙaton saurayi amma kamar an watso shara.
Ko ba a gaya masa waye ba, ya san aikin Al'amin ne, Abba
kuwa bajewa yayi, ko shurawa ba ya yi, rahila ta fito tana kururwa.
Abbu ya leƙa waje da sauri, a can ƙarshen layi, ya hango
Al'amin, ya zare wuƙa yana ta zuba sauri.
Ya rufa masa baya, yana ƙwala masa kira, amma ya ƙara sauri
har da gudu, ya bar layin.
Ayshercool
08081012143
*KARFE A WUTA*
*18*
🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA
ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*
Ganin Aminu ya ɓace masa, ya sanya ya koma gida da sauri,
rahila sai kururwa take yi, tana jijjiga Abba.
Ƙannensa mata su azima, suka kewaye shi suka hau kuka.
Abbu ya ɗebo ruwa, ya din ga zubawa Abba, har Allah ya sa ya
buɗe ido.
Cikin kuka take cewa "Ka gani ko? Ba zaka taɓa yadda da
ta'addancin ɗanka ba, har sai ranar da ya kashe mini ƴaƴa, me yayi masa zai yi
masa wannan ɗibar karan mahaukaciyar ya watsar? Wallahi na gaji, ina ga tafiya
zan yi na bar maka gidan nan kai da ɗanka, na rasa uban me yaron nan yayi masa,
ko dan ba kai ka haifi abba ba, ya tsane shi daga shi har nazifi ni ban sani
ba. Ni ba abun na kai shi ƙara wurin hukuma ba, ba sa yi masa komai sai dai a
sako shi, ni na gaji".
Abbu ya ce "Dan Allah ki daina wannan maganganun, bari
na samo mota, mu kai shi asibiti"
Abba kuwa ko magana ya kasa, Nazifi ne ya taimaka aka fita
da Abba zuwa mota.
Al'amin kuwa da ya tabattar da ya tserewa Abbu, ya samu wani
lungu, ya jefar da wuƙar hannunsa, ya samu wuri ya zauna, yana ƙoƙarin haɗiye
wani abu mai tsananin ɗaci da zafi a maƙogwaronsa, ji yake kamar numfashin sa
zai ɗauke, babu abun da zuciyar sa ke raya masa, banda ya kashe matar Abbu wato
rahila ya huta.
***
Gidan babu kowa, duk yaran sun tafi makaranta, mama tayi
sallama a falon zakiyya.
Ta amsa tare da fitowa daga bedroom ɗin, tayi miƙa ta ce
"Lafiya kuwa?"
"Au bacci ma ki ke yi? Lallai kam, to magana na zo mu
yi"
Zakiyya ta ce "Ok, bisimillah zauna mana"
Ta nemi wuri ta zauna, ita ma ta zauna.
Mama ta kalleta ta ce "Kin san waye yake son Jauhar
kuwa?"
"A'a sai kin faɗa".
"Ɗan familyn mai atamfa ne"
Waro ido Zakiyya ta yi, har tana neman faɗowa daga kan
kujera, ta ce "Wani mai atamfar?"
"Waɗanda dai ki ka sani,ba ma wannan ba shi zai tsaya
takarar majalissar tarayya a yankinsu, jiya na tutsuye shi, yake gaya mini, ga
kasuwancin atamfofi da lesuna da yake sayarwa, daga ƙasashe daban-daban yake
order kaya, na din ga bugun cikinsa yana gaya mini, wai zata yi karatu idan
tana so, idan business take so zai ba ta jari, idan ma zaman gida take so, ayi
din ga yi mata komai, duk zai iya kuma nan kusa yake son ayi auren".
"Bantan uba, namu ƴaƴan suna zaune za ayi hakan, muna
me?"
Mama ta ce "Hmm, ni fa na daɗe ina hana faruwar wasu
abubuwan, rannan daga aikenta gidan Hajiyar lamin, wai ɗan wan maigidan ya
ganta, ya ce ayi masa hanyar aurenta, uban yaron fa sanata ne a Adamawa, hauka
nake? Na toshe na hana, na din ga aika su surayya, da walida amma ko kare a
familyn babu wanda ya sinsuna su.
Lokacin da suka yi sauka ma, babu kunya wai chairman yana
son ta, tun ba ta kai haka ba ma, na ce ba za a lalata mata tunani ba, karatu
take yarinya ce, na rasa wannan masifar".
"Mun shiga uku, meyasa kowa sai ita? Kuma duk masu kuɗi,
namu yaran fa?".
Mama ta ce "Wannan shegiyar farar fatar suke yi wa
ai"
"Wace farar fatar? Su ma duk ba suna shafa mai ba,
manyan zaratan ƴan mata, sun sha mai da kwalliya amma ace su duk shiru sai
ita?"
"Shiyasa tun jiya ban yi bacci ba wallahi, na saƙa
wannan na kwance wancan, dole fa a rusa wannan maganar ma"
Zakiyya ta ce "To yanzu menene shawara? Wallahi na rasa
abun cewa, ko malamai zamu shiga ne?".
"Babu lallai yayi tasiri, na fuskanci ƙashin masu
arziki ne da ita, amma mu cigaba da shawara kafin faruwar abun".
Zakiyya ta ce "In sha Allah "
Mama ta miƙe ta ce "Sai na ji ki".
***
Cikin ikon Allah Abba ya warware, babu abun da ya same shi,
sai dai ya bugu, ya yi ta fama da jiri, sai da ya kwana uku a asibiti, aka
sallame shi.
Rahila ta cigaba da ɗagawa Abbu hankali a kan Al'amin, a kan
lallai ya kai shi wurin hukuma, a san yadda za ayi da shi, kafin ya yi mata
kisan gilla ita da yaranta.
Gaba ɗaya maganganun Al'amin sun yi tasiri a zuciyarsa, amma
kuma wani ɓangaren, Rahila tana da gaskiya, al'amin barazana ne a gare su,
saboda yadda sunan mai dogon zamani, yayi ƙaurin suna a bakin mutanen unguwa,
ba iya unguwar ba, har gidajen radiyo, duk wani faɗan daba da zai tashi a arear
rukunin unguwannin to sai an ambaci mai dogon zamani wato Al'amin.
Ƴan sanda har sun gaji da kama shi, idan an kama shi ma, ƴan
siyasa sai sun saka an sako shi, daɗinta ɗaya ba ruwansa da taɓa kowa ko kayan
kowa, sai ƴan daba da jami'an tsaro da su yake faɗansa.
Bayan Jauhar ta dawo daga makaranta, mama da Anty suka
sakata a gaba, suna sake yi mata tambayoyi a kan Alhaji mu'azzam, Jauhar ta
rasa me za ta ce musu, dan ita ba komai ta sani a kansa ba, dan tun da ya zo
sau ɗaya, bai sake zuwa ba, dan haka ta din ga ce musu ba ta sani ba.
Aikuwa suka din ga zaginta, tare da kiranta munafuka.
Suka gama zaginta, ta cigaba da sabgoginta.
Yaya tijjani ya shigo, wanda shi ne babba a gidan, ya shiga
wurin mama, jauhar ba ta san hawa ba, ba ta san sauka ba, ya kamata ya zane a
yammacin nan, wai an ce masa kule-kulen maza take yi.
Ihun jauhar ne ya sanya yaya saifu shigowa, ya tarar TJ yana
mata bala'i, wai tana kula maza.
"Haba yaya TJ, idan ba ta kula maza ba, kai za ta kula?
Ko za a jiƙata a ruwa a sha ne? Da iznin baba fa ya zo wurinta idan ma a kan
wannan mutumin nan"
Mama ta ce "Rufe mini baki, kai da ba ka san me duniyar
take ciki ba, yadda maza ke lalata yaran mutane yanzu, idan aka sake lalata ta
kawai zai yi ya gudu, kuma fuska ya gani shiyasa ya biyota har gida, da ba ta
bashi fuska ba ba zai zo ba. Idan da gaske yake auren zai yi, duk ga mata nan
da suka fita komai sai ita.
Saifu kawai ya girgiza kai ya fice, ransa ba ya yi masa daɗi,
da irin riƙon da ake yi wa ƙanwarsa a gidan nan, shikenan maraici sai ha zama
makamin cutar da bawa?.
Har jauhar ta gama girkin dare, kuka take yi, dan ta daku
sosai da sosai, fatarta duk tayi ja.
Baba da ya dawo, bai san me aka yi ba, na dukan Jauhar.
Ɗan autansu ne wato amir, ya shigo ya ce "Jauhar ana
kiranki a waje, in ji wannan mai motar, kin ga har ya bani kuɗi dubu
biyu".
Anty ta ce "Ba zata je ba, je ka ce ba ta nan, ki mayar
da kai ki gama sauran aikace-aikacen ki, idan kuma baki da abun yi, ki zo ina
da shi ki yi mini".
Baba ya fito da kansa ya ce "Amir, je ka ka ce tana
zuwa, Waliyiyya, ajiye duk abun da ki ke yi, ki je ki sallami baƙonki".
"Amma Alhaji.....
"Amma me? A kan me zaku hana yarinya zance, maganar
aurensu fa za a fara kwanan nan, da yaya za su fahimci juna?".
Jauhar kamar ta ce wa Baba ba zata je ba, dan tana tsoron a
sake saka yaya TJ ya dake ta.
Amma ta kasa magana, ta zura hijjabinta, ta fita.
Tun kan ta fita ta fara jiyo ƙamshin turaren sa, kamar
wancan karon ta durƙusa tana gaishe shi.
Sai dai bai amsa ba, ya ce "Na yi missing ɗinki Jauhar,
sai dai na baki lokaci ne, dan kar na dame ki. Yaya ake ciki kin yi mana
addu'ar? Kin fara so na?"
Maimakon ta bashi amsa, sai ƙifta ido take yi, tana waiwaye
kar TJ ya zo ya ce zai sake dukanta, tun da ta tsaya da wani ne ba sa so.
Ya ɗora da cewa "Dama baba ne ya ce na ɗan baki lokaci,
to kuma ga tafiya ta kamani babu cikkaken shiri, na ce a kawo mini kuɗin aure,
kafin na tafi, amma na ga bari na ji ta bakinki, kar na yi miki shigar
sauri"
Tayi shiru kamar ba da ita yake ba.
"Baby yangar nan tana yawa fa, dan Allah ki yi mini
magana na ji nutsuwa mana" yayi maganar yana dawowa kusa da ita ya tsaya.
"Jauhar ki yi magana mana"
"Allah ya zaɓa mana abun da ya fi alkhairi" ta faɗa
a hankali.
Ya ce "Kin amince zaki aureni?"
Ta ɗaga masa kai alamar eh.
"Wow, anya ba zan ce a ɗaura mu tafi chinan tare
ba?"
Ta ce "A'a, dan Allah a bari na gama makaranta, mun
kusa yin WAEC".
Alhaji mu'azzam ya ce "Na so ace zan iya yi miki hakan,
amma ba zan iya jurewa ba, kar wani ya rigani, ko da na tafi ina can, iyayena
zasu zo ayi maganar, da na dawo sai maganar bikinmu, i will be with my little
baby amarya very soon in sha Allah"
Tayi murmushi cikin jin kunya, tana murmushi.
"Jibi in Allah ya kaimu fa zan tafi, babu tsammani
tafiyar ta zo, me zaki gaya mini kafin na tafi, da zan din ga tunawa da ke, kin
ƙi yarda na baki waya, balle mu din ga waya ina jin daɗi. Yanzu me zaki ce
mini?".
Ta ce "Duk lokacin da ka tuna ni, ka yi mini
addu'a"
"In sha Allah amaryar mu'azzam, zan din ga yi mana, daɗin
auren mace mai addini kenan"
Ya din yi mata hira, har ta ɗan sake tana yi masa murmushi.
Ita dai ba ta sani ba tana son sa ko ba ta son sa, duk da ya
girme mata, ya iya magana, ya sauke shekarunsa dai-dai da nata, ga ƙamshin
turaren sa daɗi yake yi mata, dan a hakan yadda take fama, idan ta samu ƴan kuɗi,
baka rabata da turare.
Daga kan Surayya zuwa walida da hafsa, babu wadda ba ta fito
ba, da niyyar za su fita yin wani uzurin, kuma babu wadda ba ta gaishe shi ba,
sai dai gaba ɗaya hankalinsa da nutsuwarsa yana kan ƴar bainun gabansa wato
Jauhar.
Da zai tafi, sai da ya haɗe rai sosai, sannan ta yarda ta
karɓi kuɗin da ya bata.
Sai da ya tabattar ta shiga gida, sannan ya tafi.
Ɗaki ta je ta bawa baba duk abunda ya bata, kuɗi masu yawa,
mama ta din ga masifa, kamar ta ari baki, da sunan kula da tarbiyyar Jauhar.
***
Al'amin yana kashingiɗe yana busa wiwi, yana kaɗa ƙafarsa ɗaya,
yana jin sa a sama, dai-dai da kowa, sai dai busa hayaƙin yana bashi nishaɗi,
yana jin daɗin hakan.
Wuƙar gefensa ya ɗauka ya zauna sosai, ya karta ta a ƙasa,
ya gyaɗa kai sannan ya ɗago ya ce "zan shiga ƙofa, zan tayar da
tarzoma, zan je ɗaukar fansa"
"Wurin madakin dai?" Walid yayi maganar yana
kallon sa.
"Koma wurin waye, ka manta abun da suka yi mana kafin
na je prison?"
Walid ya girgiza kai ya ce "Ban manta ba"
"Zamu ɗauki fansa, madaki kuma ban ce kowa ya taya ni
ba, faɗana ne nikaɗai wannan".
"Shikenan yaushe zamu shiga?"
"Shammatar su zamu yi, zan yi muku magana"
Ya koma ya kashingiɗa, ya cigaba da zuƙar wiwi.
*****
Tun da Allah ya sa Alhaji mu'azzam ya tafi, Jauhar ta manta
da babinsa, sai dai in mutanen gidan sun ɗaukko hirarsa, ita da yake zuwa
wurinta ma ba ta zancensa kamar yadda suke yi.
Babbar murnarta ita yanzu, ganin yadda kantunta yake ƙarewa
da wuri, duk da ana yi mata mugunta a gidan, yaya saifu ya ƙara mata jari, ya
bata dubu ɗaya.
Ɗan kuɗin da take juyawa, da na riɗin, da na shirin dutsen,
bai fi dubu biyu da ɗari biyar ba, amma murna take yi da hakan, jin kuɗin take
da yawa, dan ƴar hamsin ɗarin da take bi na riba, ba ƙaramin daɗi yake yi mata
ba, dan nan da nan ta tara kuɗin pad, har ta fara tarin kuɗin makarantar
islamiyyarta, kan lokaci yayi ta zo tana nema.
Yau an tashi daga islamiyya, ta sayar da riɗinta tsaf, dama
da ɗaurin shirin dustenta, ta fito daga aji, tana lissafin tayi maza ta kai
musu, ta karɓo wani.
Ko da ta fito wajen gate ɗin makarantar, matasa suka gani
suna guje-guje, wai faɗan daba ake yi, mai dogon zamani ya shigo ɗaukar fansa.
Jauhar ko a jikinta tayi gaba, tun da daga in da ake gudun
bayansu ne, dan haka tayi gaba abun ta, ta nufi hanyar gidan da take karɓar
shirin.
In da take bin shiru babu mutane ma, tana shiga layin gidan
shirin, ta ɗaukko robar riɗinta, ta ciro kuɗin cinikinta, ta hau ƙirgawa
murmushi ta saki, tana jin daɗi, ta fara tunanin tambayar kuɗin aya gwangwani
biyu, ita ma ta din ga soyawa da gishir tana sayarwa.
Hankalinta ne yayi mummunan tashi, bayan da tayi baƙin ganin
da ba ta farga da shi ba sai yanzu.
Hannunsa riƙe da wani mutum, da ba ta da tabbacin yana da
rai ko babu, da wuƙa a gefen cikin mutumin, hannunsa duk jini, kuma shi ma da
yake riƙe da mutumin da take kyautata zaton kashe shi ya yi ƙafarsa sai zubar
da jinin take yi.
Tun da ta shigo layin ta fara lissafa kuɗi, ya ɗaga kai ya
ganta, amma ita sam ba ta ganshi ba, hankalinta yana kan lissafin kuɗin da yake
hannunta, sai da ta je tsakiyar layin, ta kusa zuwa daf da shi sannan ta farga.
Zuciyarta ce ta fara wani iri razanannen bugu, gashi ta kasa
ko da motsa ƙafarta, balle ta cirata ta gudu, ba ta taɓa ganin mummunan tashin
hankali ba tun da take a rayuwarta ba sai yanzu, ita ko film ne ta ga ana
kashe-kashe, ko harbe-harbe bata kalla, kodayeke ita kallo ma bai dameta ba,
amma sai yau gata ga gawa da jini.
Ba tare da ta yi tsammani ba, wani irin ƙarfi ya zo mata, ta
taƙarƙare iya ƙarfinta, ta kurma wani irin uban ihu, ta yinƙura da niyyar ta
gudu, sai dai tsananin bugun da zuciyar ta take yi, ya sanya numfashinta kasa
daidaituwa a ƙirjinta, kuma ta gaza ɗaukar nauyin jikinta, dan haka ta faɗi a
wurin a sume, robar da cinikin, da jakar islamiyyar duk suka watse a wurin,
gefen kwata.
Duk da wannan uban ihun da tayi, babu wanda yayi ƙoƙarin buɗe
ƙofarsa ya ga mai yake faruwa.
Duk da dama, gidaje biyu ne kacal a layin, sauran duk bayan
wasu gidajen ne a cikin layin.
Tsaki ya ja, ya mayar da idonsa kan liti, da yake numfashi
sama-sama.
Ya kalli ƙafarsa da take ta zubar da jini shi ma, saboda
saran da aka yi masa.
Ya kwantar da liti, ya tashi ya tafi kan jauhar, ya kai
hannun sa kan hancinta, ya ji tana numfashi.
Ya kamo hannunta, ya riƙe tsintsiyar hannunta, ya ji
zuciyarta na wani irin bugu, da saurin gaske.
Kamar ya ɗauki tabarma, haka ya ɗauketa daga kan hanya, ya
kwantar da ita a tsallaken kwatar, ya tattaro kayanta ya haɗe mata wuri guda,
sai dai uniform ɗin ta, duk sun ɓaci da jinin da yake zubarwa.
Wald ne ya ƙaraso layin da sauri, shi ma hannunsa riƙe da
wata sharɓeɓiyar wuƙa tana zubar da jini, ya ƙarasa in da Al'amin yake harya
fara ganin jiri, saboda jinin da ya zubar.
"Subhanallah, waye yayi gangancin yankarka?"
"Ƙyaleni, ka kira su baffan?"
"Eh, suna bakin titi da ɗan sahun"
Ya miƙe ya saɓa liti da yake zubar da jini a kafaɗarsa.
Walid ya ce "Kawo shi, na ga kamar jiri ka ke yi mu
ƙarasa".
Ya ce "A'a bar ni da shi, zan yi wa honorable waya, ya
aika mana ƴan sanda asibiti, waccan yarinyar, ka buga ɗaya daga gidajen layin
nan, su fito su kaita Asibiti, ta tsorata ne, idan kuma ba haka ba za ta yi
musu mushe a wurin, saboda zuciyarta na bugawa da sauri sosai"
Walid ya ce "Wai wa yake ta wata yarinya, kai kaɗai
zaku tafi asibitin, kalleku fa jina-jina"
"Mai rai ce fa, idan ba su buɗe ba, ka haura gidan
kawai, ka saka su buɗe, yanzu idan muka tafi da ita zai zama wani abun
daban" daga haka yayi gaba, ya nufi barin layin.
Walid ya yamutsa fuska, ya samu ɗaya daga gidajen, ya din ga
wani irin bugu, kamar yaƙi.
***
Cikin tsananin hanzari ta yinƙura, za ta diro daga kan gadon
da take, tana faɗin"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dan Allah ku
taimake ni, zai kashe ni"
Cikin azama baba ya riƙe ta, ƙoƙarin ture shi take yi, ta
saukko daga kan gadon. Baba ya ce "Jauhar, buɗe idonki, ki kalleni ni ne
ki nutsu" sannu a hankali ta buɗe idonta, ta kalli baba, ta juya ta kalli
su mama da Yaya saifu da suke wurin, sai malam jamilu da malam hamza.
Jikinta ya hau wata irin tsuma, ta dinga fizge-fizge tana
ƙoƙarin fizge robar ruwan hammunta.
"Ke ki nutsu mana, meye haka ne ana yi miki
magana" mama tayi maganar tana haɗe rai.
Ta girgiza kai ta ce "Mama tsoro nake ji, wani ya kashe
fa, dan Allah ku ɓoye ni zai kashe ni nima, ganinsa nake yi a idona, dan Allah
baba ku tafi da ni tsoro nake ji" tayi maganar tana ƙoƙarin tashi tsaye.
Baba ya ce "Wai shi wa?"
Cikin kuka ta ce "Ban san shi ba, kawai gani nayi dai
ya kashe wani yana kallona, nima na san zai biyoni ya kashe ni".
Baba ya ce "To ai babu wani wanda aka gani an kashe, ke
kaɗai aka gani a layin a sume".
Anty ta ce "Uban me ma ya kai ki can, in da ba hanyar
gida ba?".
"Shiri na je karɓowa"
"To ubanwa ya aike ki?"
Baba ya ce "Dan Allah duk a daina wannan maganar, yanzu
a bari ta samu nutsuwa".
Ƙoƙarin kwantar da ita Baba yake yi, ta kalli jikin uniform ɗin
ta, ta ga jini, ihu ta sake yi, tana faɗin "Meya same ni, baba kalli jini
a jikina, na gaya maka nima kasheni zai yi, kalli jini fa wataƙila ma na mutu
ne".
A take wani abu ya ɗarsu a zuciyar mama, tayi wani shu'umin
murmushi, yaya saifu kuwa likitoci ya kira, aka sake yi wa jauhar allurar
bacci, dan gaba ɗaya nema take ta zare.
Malaman islamiyyar suka yi wa su baba sallama, malam Jamil
dama a kusa da layin da take zuwa karɓar shirin yake, yana yawan ganinta,
wataran shi yake korata makaranta ko gida, tun da ya fuskanci halin da take
ciki, yake ƙyaleta, dan watarn har gidansu take shiga, ƙannensa ƙawenta ne.
Shi ya din ga bawa baba baki, da bashi tabbacin jauhar ba
yawo take tafiya ba, kamar yadda mama ke ta iƙrari.
Baba ya ce "Ni ma na san jauhar ba ta yawo, wannan abun
da ya faru ma tsautsayi ne, Ubangiji Allah ya kiyaye gaba" suka yi sallama
su malam jamil suka tafi.
Kusan awanni biyu, jauhar ta sake farfaɗowa, sai dai wannan
karon da sauƙi, ba cikin razani ta farka ba kamar da farko.
Likita ya zo yana sake dubata, Mama ta ce "Likita kun
dubata da kyau kuwa, wannan jinin na jikinta ba fyaɗe ƴan daban suka yi mata
ba?"
Dummm! Ƙirjin Jauhar ya buga, ba ita ba hatta baba sai da
gabansa ya faɗi, suka kalli mama a tare.
Likitan ya girgiza kai ya ce "No, bana tunanin hakan,
razani ne kawai".
"To amma meya kawo jini jikinta?".
Likitan ya yi shiru yana kallon jauhar.
Baba ya ce "Likita ka yi magana mana"
Jikin jauhar ya cigaba da rawa, tana nanata fyaɗe a
zuciyarta, amma kuma da gaskiyar mama, meyakawo jini jikinta?.
Likitan ya ce "Zaki iya tuna abun da ya faru?".
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Na shiga layin kawai na
ga ya kashe wani, da wuƙa a cikin sa, shi ma ƙafarsa tana zubar da jini"
"Kin san shi ne? Kin taɓa ganinsa?" Ta girgiza kai
alamar a'a
Ya ce "Zaki iya tafiya?"
Ta jinjina masa kai alamar eh.
Ya cire mata ruwan sannan ya ce "Saukko ki biyo
ni" ta yinƙura ta sauka daga kan gadon, ta bi bayan likitan, zuwa wani ɗakin
daban, ya kira wata nurse ya ce ta duba masa jauhar, amma jauhar fafur ta ce ba
zata buɗe jikinta ba, sai ma ta hau kuka.
Nurse ɗin ta din ga lallaɓata tana yi mata tambayoyi, ta
saka ta ciro mata phant ɗin ta, ta duba ta ce wa likitan ba abun da aka yi wa
jauhar ɗin mai kama da fyaɗe.
Wataƙila da ta suma ya taɓa ta, tun da ta ce shi ma da rauni
a jikinsa, amma ba dai fyaɗe ba.
Likita ya koma ya yi wa baba bayani, baba ya din ga hamdala,
mama ta ce likitan ƙarya kawai yake yi, babu yadda za ayi, ta samu jini a
jikinta, idan ba fyaɗe aka yi mata ba.
Likitan ya ce "Amma dai ba ƴar ki ba ce hajiya, da taki
ce ba zaki yi mata wannan mummunan fatan ba, bani da wata riba da zan ci, idan
na yi muku ƙarya, kuma babu yadda za ayi ayi mata fyaɗe ku kawota a haka, ba
wani rauni ko alamu na fin ƙarfi, dan babu ɗan iskan da zai yi wa yarinya fyaɗe
ya tsaya mayar mata da kayanta a tsakiyar layi, kamar yadda muka karɓi
report"
Baba ya ce "Doctor, a bar zancen ma gaba ɗaya, ni dai
na gode sosai da sosai, na gode Allah da babu abun da ya sameta, za a iya
sallamar mu yanzu?".
Ya ce "Eh, yanzu zan sallame ta". Aka rubuta musu
sallama suka tafi gida.
Maƙwabta suka din ga shigowa yin jaje, saboda labari ya cika
tsukin, faɗan daba ya rutsa da jauhar, an tsintota can a sume.
Sai dai duk wanda ya zo, sai su mama sun bashi labarin,
cewar cikin jini aka tsintota kuma jikinta babu rauni, ana kyautata zaton ko
sun yi mata fyaɗe.
Jauhar hankalinta ya kasa kwanciya, ta din ga tunani
daban-daban, ko da ƙarancin shekarunta, a science class take ss2, kuma tana
zuwa islamiyya ta san duk wadda aka yi wa fyaɗe sai ta ji wani sauyi a tare da
ita, amma ita ba ta ji komai ba, babu wani abu da take ji na sauyi a tare da
ita.
Tun tana damun kanta, har ta watsar, sai dai ƙasan zuciyarta
tana jin zafin abun da su mama suke faɗa, dan idan ta fita har tambayarta ake
yi, wai da gaske an yi mata fyaɗe?.
Har fita ta so ta fara gagararta. Sati biyu da faruwar
lamarin, Baba ya zo ya sanar musu da cewa, iyayen Alhaji mu'azzam za su kawo kuɗin
auren jauhar.
Hankalinsu yayi mummunan tashi, daga su har ƴaƴan su. Suka
ƙara tsananta tsangwama da kyarar jauhar.
Duk da tana da matuƙar juriya, da kawar da kai, har abun ya
fara effecting ɗin ta.
Bai sanar da su lokaci ba, sai ranar da za a kawo ya sanar
da su, hankalinsu ya ƙara tashi, sai dai ba su tsinke da lamarin ba, sai da aka
kawo kuɗi masu yawan gaske.
Anty ta kira Rahila, cikin matsananciyar damuwa da tashin
hankali take gaya mata, tare da tambayarta ko akwai wani zazzafan malamin ta haɗa
su, a samu a watsa lamarin.
Rahila ta ce "Wallahi ni kaina a cikin matsala nake
Zakiyya, yaron nan ya zame mini bala'i fiye da koyaushe, idan ya ga dama fa
cikin gidan yake zuwa ya kwana a tsakar gida, gaya miki ne ban ba, sai da muka
kwanta a asibi, ya ɗaga Abba ya buga da ƙasa saboda babansa ya hana shi zuwa
gidan, gashi kamar ya fara jin tausayinsa, wallahi kamar na bawa tsinanne guba
ya ci ya mutu"
"Innalillahi, rahila menene abun yi? Ni fa sonake
maganar ta watse, a dawo mutumin ya auri hafsa".
Rahila ta ce "Aikuwa kin yi dabara, ina da wani malami,
wurinsa nake son komawa, ina jin daɗin aikinsa sosai da sosai, duk da su ma
malamn yanzu duk sun zama ɓarayi, su ci maka kuɗi babu biyan buƙata, amma nasa
babu laifi".
"Wallahi kuwa, saka mana rana, ko da tsiya da masifa,
lamarin ya dawo kan hafsa".
"Idan a shirye ki ke, kawai ki zo mu je, ba a bori da
sanyin jiki"
Suka yi sallama a kan haka, ɓangaren mama ma, tuni ta zari
mayafi ta tafi nata wurin malamin, a kan lallai al'amarin nan kar ya yiwu.
Haka ita ma anty ta shirya, ta tafi gidan rahila.
Ita kuwa jauhar, addu'a take ta yi, Allah ya sa mutanen
unguwar su manta da sharrin su mama da suka yi mata, na cewar fyaɗe aka yi
mata.
Maganar kawo kuɗin auren duk bai wani dameta ba, ita gaba ɗaya
ba ta jin dadin rayuwar ma gaba ɗaya, gashi har a lokacin tana yawan tsorata,
idan ta tuna abun da ta gani, haka take ganin abun a mafarki, sai dai tayi ta
addu'a tana fatan Allah ya yi mata tsari da wannan mutumin mara imani.
Malamin ya gama surƙullensa, ya kalli su zakiyya ya ce
"Za a iya watsa lamarin amma fa kafin dawowarsa, muddin ya dawo, babu
yadda za ayi".
Zakiyya ta ce "Malam tayaya kenan?"
"Ko dai a aura mata wani, ko kuma a kasheta"
Tayi jimmm ta ce "Kisa kuma malam, a'a gaskiya ban da
kisa, muguntar tawa ba ta kai nan ba, ni fa burina kawai ya auri ƴa ta".
"Ta yaya zai aureta, alhalin yana ganinta?"
Rahila ta ce "Sai a juya masa tunani mana malam".
"Za a iya juya masa tunani, amma ba zai juyu yadda ake
so ba, abun zai sake shi da wuri, dan su ma masu kuɗin ba da ka suke zaune ba,
kuma maganin ba zai yi aiki a kansa ba, dole sai ya dawo ƙasar nan, zan haɗa
laƙanin, ya manta da wannan ya auri wadda ku ke so, amma muddin ya dawo yayi
tozali da wadda yake son ɗin, ƙasa ta nuna mini ba zai yiwu ba"
Zakiyya ta ce "Tirƙashi! Ana wata ga wata, ga ƙoshi ga
kwanan yunwa"
Rahila ta ce "Malam mun gode, idan mun yanke shawara
zaka ji mu, tashi mu je ki ji ina da shawara"
Suka sallami malamin, suka tashi suka fito, ta kalli rahila
cikin damuwa ta ce "Wace irin shawara ce da ke?"
"Shawara ce mai kyau, amma ina ga mafita ce, tun da
damuwar mu kusan ɗaya ce, me zai hana a haɗa ta aure da wannan fitinannen yaron
na gidana, kin ga kun huta na huta, su je su ƙarata, ya bar ni da mijina da
ƴaƴana".
Zakiyya ta buɗe baki ta ce "Ta yaya? Babanta kuwa zai
yarda?"
"Ke dalla can, shiga zaki yi ki fita, idan ba haka ba
wallahi daular da ki ke kallo ta gagareki, kin ga mun jefi tsuntsu biyu da
dutse ɗaya".
"Wallahi maganarki gaskiya ce rahila, zan yi magana da
matar gidan, ta fi ni iya sarrafa shi yadda take so a kan yarinyar, zan je mata
da zancen, ayi a ƙarƙare kan wancan ɗin ya dawo".
"Yauwwa, amma fa kar ki gaya mata wurin malami ki ka
je"
Zakiyya ta ce "Hauka nake zan gaya mata haka? Ke dai ki
saurare ni kawai"
"To shikenan, sai na jiki, yadda ku ka yi ki sanar da
ni da wuri, nima zan wa babansa magana" suka yi sallama zakiyya ta tafi da
ƙarfin gwiwar ta.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cike da ƙwarin gwiwa, zakiyya ta tafi gida, tare da hasaso
daular da za su shiga, idan hafsa ta auri Alhaji mu'azzam.
Al'amin kuwa yana zaune ya miƙe ƙafarsa, da ta sha bandeji,
hannun sa ɗaya riƙe da kofin shayi yana sha a hankali.
Walid ya miƙa masa buredi ya ce "Wai yaya aka yi har
yaran nan suka samu suka sareka ne? Ni fa haryanzu mamaki nake yi"
Al'amin ya ce "Liti suka rufarwa da sara, shi na je karɓowa,
saboda sun ga suna da yawa, shi ne nima suka yi tunanin za su yi mini taron
dangi" yayi wani irin murmushi yana kallon walid.
"Murmushin me ka ke yi kuma?"
Ya ajiye kofin ya ce"swizalan ɗina ta sha jini sosai,
wannan yankanma, ban lura yaron ya taho ba ne, yadda nake ji na anya ba wasan
dambe zan fara ba walid. Idan na kwana biyu ban motsa ba, idan na tashi
motsawar ba na iya riƙe kaina fa".
Walid shi ma yayi murmushi ya ce "Ai ƙarfi ya yi maka
yawa aminu, ka shiga dambe abun ba zai yi mana kyau ba, daga karate zuwa dambe,
amma da sauƙi jikin ai ko?"
Ya kalli ƙafar ya ce "Alhamdilillah, da sauƙi sosai,
jibi za ayi aikin honorable, zai je campaign fa"
Walid ya ɗan tsuke fuska ya ce "Akwai hatsari fa a
aikin nan".
"Ai ban ce wani ya tayani ba, nikaɗai zan yi
abuna"
Walid ya girgiza kai ya ce "Sorry, ba zaka yi kai kaɗai
ba, amma da rauni a jikinka, ba ka warke ba".
"Ba ruwanka da ciwona, zan yi abuna a haka" walid
ya girgiza kai, dan ya san ko me zai ce, bai isa ya hana Al'amin abun da yayi
niyya ba.
***
Kamar zakiyya za ta tashi sama dan sauri ta ƙarasa gida,
saboda rahila na bata shawarar nan, ta ji shawarar ta kama zuciyarta, kuma taga
hakan ne kawai mafita, ayi ayi jauhar ta bar gidan kafin Allhaji mu'azzam ya
dawo, wataƙila ita ke tsokanewa samarin kirkin ido, ba sa ganin nasu ƴaƴan sai
ita.
Ko da ta koma gida a can ta tarar da mama, ita har ta dawo
tuni.
Ta ja ta ɗakinta, ta ce "Na samo mafita fa, amma ban
sani ba ko zata yi miki?"
Cikin zaƙuwa mama "Wace mafitar ce, ina jinki"
"Me zai hana mu san duk mai yiwuwa, a aurar da jauhar,
kafin Alhaji mu'azzam ya dawo, tun da dama sai ya dawo, za a tsayar da lokacin
bikin".
Mama ta ce "To wa za a aurawa kafin ya dawo ɗin?".
Anty ta ce "Ba zai gagara ba, sai dai shawo kan Alhaji
ne aiki"
"Wane irin aiki kuma? Babu wani aiki, ni a wurina ba
aiki bane ba, wa ki ke gani yakamata ta aura".
Zakiyya ta muskuta ta ce "Kin san dai muka bari ta auri
wani mai danshi, daga ni har ke babu wanda za ta saurara, tun da bamu muka
haifeta ba".
Mama ta ce "Na sani"
"To, kin san yaron nan da yayi suna a ƙofa, mai dogon
zamani?"
"Eh ina jin sunansa sosai"
"To mariƙiyarsa, ƙawata ce tare muka yi boarding ai
rahila shehu, kwana biyu bamu haɗu ba, kwatsam na je ƙofar na'isa na ga ɗan ta,
ya rakani har gidan, to ita ma haka take fama da shi, ta rasa sukuni, kullum
cikin tashin hankali take, neman maraba take da shi, uban ya kore shi, amma
yaƙi barin gidan, kin ga idan aka aura mata shi, mun huta, a fake da fyaɗe aka
yi mata, kuma dai ga tambarin da ki ka yi uwarta na maita, kawai dai ki lallaɓa
maganar, kin san yadda zaki yi dai sabgar nan ta yiwu, wallahi muddin ba ta bar
gidan nan ba, bana tunanin za a din ga kula namu, kuma wallahi ta auri mai kuɗi,
kashinmu ya bushe, ai kin san riƙon da muka yi mata".
Mama tayi ajiyar zuciya ta ce "Maganarki duka gaskiya
ne, kar ki damu, wannan shawarar ta yi, kuma na aminta da ita, yadda muka
kwashi baƙincikin uwatta, ita ma ba zata ji daɗi ba. Duk da wasu lokutan tana
bani tausayi tana da biyayya, amma idan ba haka ba, namu ba zasu auru ga irin
wanda muke so ba, ki gayawa ƙawartaki azo a nema masa aurenta, zan ji da
komai"
Anty ta washe baki ta ce "Alhamdilillah, magana ta
ƙare".
Jauhar kuwa, ba ta san me ake ƙulla mata ba, ita
lissafinta yadda za ta mayar da jarinta, dan tun da ta farka a asibiti, da ta
dawo gida sai jakarta babu kuɗin cinikinta, dan ma mai shirin dutse ta yafe
mata.
Duk yadda take jin nauyin yin roƙo, haka ta cire kunya, ta
tambayi yaya saifu ya taimaka mata da jari, ta cigaba da sana'arta, kuma cikin
ikon Allah ya bata, saboda ta hannun daman sa ce sosai da sosai, aiki duk
yawansa duk wahalarsa babu ƙyuya take yi masa, gyaran ɗaki, wanki guga idan
baya nan tayi girki, ta zuba ta kai masa ɗakinsa, idan ya gama ci ya bar
kwanukan a ɗakin, ta kwaso ta gyara masa, dan haka baya jin ƙyashin kyautata
mata sam.
***
Abbu yana daga kwance ya kammala azkar, ya juya zai yi
bacci, rahila ta shigo ɗakin, ta nemi wuri ta zauna a kan gadon ta ce "Tun
da idonka biyu tashi mu yi magana"
Ya juyo ya ce "Ina jinki"
"Magana ce mai muhimmanci, a kan Aminu".
"Aminu dai Aminu dai, me kuma ya faru wannan
karon?"
"Menene ma bai faru ba, tun da an mutu an bar mini
jaraba da masifa, kullum hankalina a tashe, nan aka zo ana bayar da labari, sun
je ya tayar da tarzoma, har an yanke shi a ƙafa, rashin mutuncin sa kullum ƙara
gaba yake yi"
"To, na ji, maganar kenan ki sake maimaita mini abun da
yake aikatawa? Wannan ai wani abu ne da na riga na sani".
"Ba shi ne ba, magana ce a kan mafita game da abun da
yake yi"
Ya tashi zaune ya ce "Wace irin mafita?"
Rahila ya gyara zama ta ce "Akwai wata ƴar ƙawata,
yarinyar rashin ji take yi, tana neman fanɗarewa, gashi ba ta da wani tsayayye,
na ce tun da shi gashi, kuma akwai wannan kangon gidan da ya gada, a gyara masa
ka nema masa aurenta, ta je su ƙarata ko zai yi hankali idan ya ajiye
iyali".
Abbu ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Too, ikon Allah,
banda abunki wane mai hankalin ne zai bawa Al'amin auren ƴar sa, yadda suanansa
ya yi shuhura, a kan rashin ji".
"To ai yarinyar na ce maka fitina take yi ita ma"
"Kuma sai ayi gyaran ɓarna da ɓarna? Sai a aura masa
wadda ba ta ji?"
Rahila ta ce "To shi ɗin menene? Shi na kirkin ne?ko
Jin yake yi? Sai su rufawa juna asiri, amma aka ƙyale shi a haka, nan da
shekara ashirin, kana ganin zai yi nutsuwar da zai kula wata mace da sunan zai
aura, tsabagin wauta da kayen maye ne kawai a cikin kansa"
Abbu ya numfasa ya ce "Maganarki haka take, amma kamar
yayi ƙanƙanta ma da auren shekara ashirin da bakwai, ga ba sana'a yake ba sai ɗaukar
magana, da yaya zai riƙe auren? ga faɗa da faɗin rai".
"Idan ya san ya ajiye mace, dole ya nemo ya ba ta ai,
tun da morarta zai din ga yi, ko kuma kana tunanin zafin rai da faɗin ransa zai
hana shi, mu'amala da ita ne namiji ne fa".
Abbu yayi murmushi, har sai da haƙoransa suka fito, ya ce
"Na san ɗa na kamar yunwar cikina, ban san meyasa mata ku ke tunanin maza,
bamu da wani tunani idan ba wannan ba, Aishikenan".
Ta kwanta ta ce "Aikuwa idan haka ne, da sai an dangana
da nema masa magani, idan baya wannan tunanin"
Ya kwanta a kusa da ita ya ce "Zuwa da safe in Allah ya
kaimu, sai ki yi mini kwatancen gidan su yarinyar, na samu mahaifinta".
Ta ce "Yauwwa Abbu ko kai fa"
****
Jauhar ta dawo daga makarantar dare, ta tarar da Baba da
baƙo a waje, ta durƙusa ta gaishe su, sannan ta shiga cikin gida.
Baba ya nuna wa Abbu ita, ya gaya masa ita ce jauhar ɗin da
suke maganarta, Abbu sam bai ga alamar rashin ji, a tare da jauhar ba sai ma
nutsuwa da kamala, hatta muryarta mai sanyi ce, yayi mamakin da rahila ta ce
masa wai ba ta ji, fanɗararriya ce, sai dai bai yi magana ba, suka cigaba da
magana da Baba a kan nemawa Al'amin auren jauhar, ya sanar da baban jauhar
Al'amin ɗin ba ya ji, sai dai bai gaya masa irin rashin jin ba, ya zata Baba ya
san komai, saboda yadda rahila tayi masa bayani.
Baba ya ce "Babu damuwa, Allah ya tabbatar musu da
alkhairi, na san iyayen nata ba za su zaɓa mata abun da zai cutar da ita
ba".
Suka taɓa hira, ya tambayi Baba ko akwai wani shiri da za su
yi? Baba ya ce idan sun shirya kawai su kawo abun da suke da shi, ayi komai a
wuce wurin.
Suka gama magana, Abbu ya tafi gida yana farinciki, tare da
fatan Allah ya sa ƙarshen matsalar Al'amin ce ta zo, Shi ma Baba ya shiga gida,
can ƙasan zuciyarsa yana ta kokwanto da wasi-wasi, amma ya kasa ayyana hakan a
zahiri.Sam bai iya tambayar menene rashin jin da Aminu yake yi ba,
bai tambayi menene sana'arsa ba da sauran su, kawai shi dai ya tsinci kansa da
amincewa, bayan da mama tayi ta jaddada masa idan har Alhaji mu'azzam ya dawo,
ya ji ƴan daba sun yi mata fyaɗe za ta wulaƙanta, ba zai aureta ba, shi gaba ɗaya
ma ya manta da batun ya karɓi kuɗin auren Jauhar.
Abbu na komawa, Rahila ta tare shi, tana tambayarsa yadda
suka yi, ya ce "Ya amince zai ba shi ita, amma ni da ya nuna mini
yarinyar, ba ta yi kalar marasa ji ba".
"Ban da abunka Abbu, dama a goshi ake gane marasa jin?
Kai dai kawai ayi sha'ani".
"Amma anya ban yi ganganci ba kuwa, ban sanar da shi ba
na je na nema masa aure, idan ya bujire fa".
"Au sai ma ya yarda? Ashe na kabari zai dawo duniya
idan shi ne zai yadda, ka yi iya yinka a matsayin ka na uba, kar ma ka sanar
masa, sai ka kai kuɗin, kuma ku saka lokaci kaɗan, kar ya tafka wata tsiyar, ba
akwai gidan da ya gada na wurin babarsa a chiranci ba, aje a ɗan gyara masa, ya
zauna".
Abbu ya jinjina kai ya ce "Shikenan Allah ya yi mana
jagora".
Kwana huɗu, Abbu ya kira baba, ya ce za su zo, su kawo
dukiyar aure.
Ko da Baba ya sanar da wanda za su karɓi kuɗin Jauhar ɗin
tare, sun yi mamaki, suka din ga tambayar sa, meyafaru da waccan saka ranar, ya
ce musu matsala aka samu.
Dubu ɗari uku da hamsin, aka kai kuɗin komai da komai, har
da lefe da sadaki da kuɗin aure, wai bayan sati biyu za a ɗaura aure.
Mama ta fito tsakar gida ta din ga rangaɗa guɗa, suna Allah
ya sa za su gani, gaba ɗaya sai jauhar ta zama confused, wane irin abu ne haka?
Alhaji mu'azzam ne ya dawo? Ko kuma yaya aka yi, aka kuma karɓar wani kuɗin. ta
ji ana zancen wani Al'amin shi kuma daga ina? Ta tambayi kanta.
Sai dai tsananin kunya, da kawaicin jauhar, bai sanya ta yi
magana ko ta tambaya ba.
Su surayya suka din ga yi mata dariya, wai ta ga samu ta ga
rashi, from grace to grass.
Duk wani shirin auren, Mama ce take yi, ita ke karɓar kuɗin
a hannun Baba wani abun ta saya mata mai kyau, wani akasin haka, masu kyan ma
tana saya ne, saboda kar a yi mata gori, ta riƙe yarinya shekara goma sha shida
za a shiga sha bakwai, amma ba ta yi mata abun kirki ba.
Aminu kuwa tun kan a kai kuɗin, yayi ɓatan dabo, dan
rigimarsa ba ta ciwo shi ya zo gidan ba, dan haka tilas Abbu ya fara bin dabar
da yake zama, da duk in da ya san zai ganshi, amma babu shi babu labarin sa,
haka ya din ga bayar da cigiyarsa, kamar wani kuɗi, kowa ya tambaya sai ya ce
masa bai ganshi ba.
Rahila ta ce masa ya cigaba da shirin sa, duk in da ya tafi
ma zai dawo.
A gidan su jauhar kuwa, hankalinta ne ya tashi, da ta ji
Anty na yi mata iƙirarin wai nan da sati biyu za a ɗaura mata aure, da angonta
Al'amin.
Saifu ya kasa jurewa, ya samu Baba ya tambaye shi, wai meke
faruwa da auren jauhar ne?.
Baba ya ce "Eh, nan da sati biyu za ayi"
"Amma na ga kamar sau biyu aka kawo kuɗin, wancan an ce
Alhaji mu'azzam, yanzu kuma an ce Al'amin wanne ne gaskiyar lamarin ne?"
Baba ya ce "Maman ka da Antynku, ne suka yanke shawarar
a aura mata wani, wancan za a iya samun matsala, ta ɓangaren zakiyya ma aka
kawo wannan ɗin" cike da takaici yake kallon Baba ya ce "wace irin
matsala kuma Baba? Meyasa wanda aka kawo ɗin ba za a haɗa shi da wata ba, sai
jauhar? A ina yake, kuma menene sana'rsa? Yazo ya ganta ta ganshi, yayi
mata?"
Baba ya sunkuyar da kai tare da girgizawa ya ce "No,
amma na san ba za su zaɓi abun da zai cutar da ita ba, kuma jauhar yarinya ce
mai biyayya"
Takaici ya ishi Saifu, ya tsani yadda matan gidan suke
shirya wa Baba abun da suke yayi, kuma yayi babu musu mussaman a kan jauhar.
Kawai ya tashi ya fita tsakar gida, ya tarar da ita, tana ta
uban wanke-wanke, gefe ta jiƙa kayan wankin uniform ɗin ƙanan yaran gidan.
Ya ja kujera ya zauna a kusa da ita ya ce "Waliyiyya,
wai saura sati biyu aurenki?"
Tayi yaƙe ta ce "Haka na ji, amma dai Baba bai gaya
mini ba".
"Wanda zaki aura ɗin kin taɓa ganinsa ne? Ki na son
sa?".
Ta sunkuyar da kai tana murmushi ta ce "Ko ban ganshi
ba, tun da an ce su mama ne suka zaɓa mini shi, kuma Baba ya amince na san ba
zai cutar da ni ba"
"Baki taɓa ganinsa ba kenan?" Sai ta kasa amsa
masa, ta cigaba da durza tukunyar hannunta cikin ƙarfin hali.
Can kuma ta ce "Dan Allah yaya, ka roƙi baba, ya ce
masa dan Allah ina son ƙarasa makarantata, ko WAEC na yi"
Saifu ya girgiza kai ya ce "Ki kwantar da hankalinki,
na san juriya kawai ki ke yi, amma in sha Allah, ba zaki ji kunya ba
jauhar".
Mama ce ta fito ta ce "Kai saifu, uban me ka ke gaya
mata, hure mata kunne zaka yi?"
Ya tashi tsaye ya ce "Ko na hure mata kunne, ba zai
huru ba, kawai ina tausayin sauran ƴan matan ne, saboda komai nisan jifa ƙasa
zai dawo"
Ta ce "Saifu ni ka ke gaya wa haka? Me ka ke
nufi?"
"Mama kin san fa me nake nufi sarai, Allah ya haramta
zalunci a kan kansa, babu wanda zai yi ya tsira wallahi" ya ƙarasa maganar
yana ficewa.
Cike da takaici da son hucewa, mama ta rarumi takalmi, ta
jefi jauhar da shi a fuska, aikuwa ya tsokane mata ido.
Ta zauna ta din ga mutsutsuka idon, sai da idon yayi taruwar
jini.
Ƴan unguwar su jauhar sai ganin invitation suka yi na bikin
jauhar, suka din ga zuwa gulma da jin ba'asi, wane irin aure ne haka faka-faka
ko lefe ba a nuna musu ba, da yake ba su san ma zancen kawo kuɗin auren farko
ba.
Mama da zakiyya, suka din ga cewa saboda ayi a rufa mata
asiri, ake son ayi gaggawa a aurar da ita, sadakarta aka bayar babu ko kayan
lefe.
Saboda cin fuska a gabanta, suke faɗar hakan. A gabansu sai
ta jure, tayi kamar ba ta ji ba, idan ta ɓuya kuma sai tayi ta kuka.
Al'amin kuwa, honorable Indabo ne ya saka aka kai shi
asibiti ta ƙarfin tsiya, saboda ciwon ƙafarsa an sake fama masa lokacin da ya
tayar da rigima a wurin campaign, a haka yake lanjarata, ya tafi nasa wuri,
saboda soyake Aminun ya warware sosai, kafin lokacin zaɓe kuma, yadda zai yi
masa aikinsa yadda yakamata.
Yana shiga arearsu, aka sanar da shi cewa, babansa yana ta
yawon nemansa, mamaki ya kama shi, dan idan zai kwana nawa bai ganshi ba, babu
ruwansa da in da yake, dan haka cikin gaggawa ya nufi gidan, domin jin dalilin
neman nasa.
Sai dai da ya je ya tarar da Abbun yana shirin fita.
"Kai baka iya sallama bane Al'amin, sai dai mutum ya ga
ka bayyana kamar wani shaiɗani?"
"To meye marbarsa da shaiɗanin?" Tayi maganar
ƙasa-ƙasa.
Sarai ya ji ta, amma ya yi shiru, ya samu wuri ya zauna ya
miƙe ƙafarsa ya ce "An ce kana nema na"
"Ba an ce bane, nemanka nake yi, ka dawo daga gantalin
kenan? Kodaye ba yau ka fara ba, ka buɗe kunnenka da kyau ka saurare ni"
Yayi shiru bai ce komai ba.
"Daga nan ba kasuwa zani ba, Abba ne zai je ya buɗe
shago, gidanka na chiranci, na gado zan je, za ayi masa wasu ƴan gyare-gyare,
ba ni da kuɗi sosai a hannuna, za a yi masa abun da ya sauwwaƙa, kai ka ƙarasa
gyarawa daga baya".
Ya yi shiru yana wasa da zobensa, kamar yadda ya zame masa ɗabi'a,
idan ba ya son yin magana.
Abbu ya cigaba da cewa "Kuɗin aure na kai maka, next
week za a ɗaura maka aure"
Lanƙwashe ƙafarsa ɗaya yayi, ya koma wasa da yastun ƙafarsa,
yana kallon wani wurin daban.
Rahila ta ce "Taɓɗijan, lallai gagare".
Abbu ya ce "Al'amin da kai nake fa"
Ya ɗago idonsa ya kalli Abbu ya ce "Wai ni ko wa?"
"A'a da ubanka nake ba kai ba, ni da waye a wurin
nan?"
Al'amin ya ce "Ni fa yau ban sha komai ba, garau nake
balle ace a buge nake ban ji dai-dai ba, wannan kawai zance ne, ni da ake cewa
gagarrare haihuwar asara, wa zai bani wani aure? Ni bana buƙata, idan kuma ba
haka ba, duk abun da ya biyo baya ba ruwana idan na kashe yarinya, ko na yi
mata illa, kar a zo ana yi mini ƙanan maganganu, ba na so bana buƙata".
Ya yinƙura zai fice, Abbu ya riƙe shi ya ce "Umarni
nake baka, ba shawararka ko ra'ayinka nake nema ba, dole ne wannan, aurenka
wani satin, na kai kuɗin aure da komai, dole ka nutsu ka shiga hankalinka, idan
ka illata musu ƴa ko kasheta kuma, zan sallamawa duniya kai, wannan shi ne
hukuncin da na yanke"
A fusace ya ce "Meyasa zaka yanke wa rayuwata hukunci,
ba tare da amincewata ba bayan ka daɗe da sallamawa duniya rayuwar tawa? Ka yi
hakan ne saboda farincikin matarka ko? Ta daina ganina na gusa na bar mata
gidan nan ita da iyalinta. Da zan iya wallahi garin zan bar muku na ɓacewa
ganinku ku samu cikakken kwanciyar hankali kamar yadda ku ke buƙata, amma ba
zan iya ba.
Ka sani ina ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, da gaske zan iya
kashe ƴar mutane, ko na illata ta, sai dai ba na fatan na fi haka lalacewa,
idan ka yi mini baki, zan ƙara lalacewa ne zan bi umarninka, amma duk abun da
na yi mata da ni da kai zamu ɗauki nauyin zunubin. Saboda ni babu mata a tsarin
rayuwata, miyagun halittu da babu Allah a ransu, bana fatan raɓar su, saboda
yadda tasirin kaidinsu ya kassara rayuwata, kassarawar da ba za ta gyaru ba,
mace ɗaya da nake wa kallon rayuwata, uwata kenan na rasata a yanzu babu wata
mace mai sauran kima da mutunci a idona, nayi alƙawarin nesanta kaina da mata,
nesantawa mai nisa ta har abada, amma ka karya mini alwashi, ta hanyar janyo
mace rayuwata, ina sake nanata maka, duk abun da ya biyo baya, tare zamu ɗauki
nauyin zunubin".
Ya saka hannu, ya cire hannun Abbu da ya riƙe masa riga, ya
saka kai ya fice.
Har ya bar gidan, babu wanda ya sake magana, daga ita har
Abbu.
Gaba ɗaya aka hana jauhar fita daga gida, ana ta shirin
biki, ita kuma tana rama kamar ana tsotseta, duk ta fiƙe sai farar fata da
idanuwa.
Maƙwabciyar su ta din ga cewa "Gaskiya mama ban so a
aurar da jauhar yanzu ba, na so a bari maƙerin budurci ya gama ƙere mana ita,
wannan kyawun da gidan wani hamshaƙin ya dace"
Anty ta ce "Wannan ma hamshaƙin ne".
A gida mama ta saka su surayya sa walida, suka dinga kwaɓe-kwaɓe
suna murzawa jauhar da sunan gyaran jiki.
Malam jamilu ya shiga matsananciyar damuwa, da samun labarin
auren jauhar, dan har ga Allah yana matuƙar sonta, tsoron kar ta daina ganin
mutuncinsa, ya sanya ya ɓoye mata.
Gidan jauhar da aka je jere, yana da girma, sai dai tsakar
gidan tsurar ƙasa ce, cikin ɗakuna babu floor, sai dai an yi plasta a ɗakunan,
falo ɗaya da ɗakuna uku a ciki, kowanne da banɗaki, sai kitchen a tsakar gida
da tsakar gida mai girma.
An yi wearing ɗin wutar lantarki, a gidan.
Sai buhunhuna, aka shimfiɗa a ƙasa, sannan cikin ɗakunan aka
saka leda, falo kuma aka shimfiɗa carfet, saboda duk turɓaya ne.
Tagogin duk babu na kirki, sai kame-kame da faci.
Sai kujerunta, ƴan gida masu kyau, ɗaki ɗaya an saka
furnitures, ɗaya kuma sai aka saka ƙatuwar katifa da wardrobe mai biyu, abun
saka takalma. Duk da haka gidan ya yi kyau.
Amarya ta din ga fargaba da tunanin, waye mijin nan, da
haryanzu za ace, bai taɓa ganinta ba, kuma ba ta taɓa ganinsa ba? Kuma ya
amince da zai aureta.
Dogon gashinta baƙi, aka gyara mata shi, aka yi mata lalle
ja da baƙi.
Haka kurum take tuna Alhaji mu'azzam, a haɗuwarsu biyu,
yadda yake nuna yana sonta, ba ta son ya zai ji ba, idan aka ce masa an yi mata
aure.
Kodayeke ita ba ta san dalilin fasawa da shi ba.
Su liti suka lura da shirun Al'amin ya ƙara yawa, duk da ba
mai yawan magana ba ne dama, sai ya zauna yayi shiru yana zancen zuci.
Walid ya ce "Baaba, wai dan Allah kwanan nan meyake
faruwa ne? Kamar ka na cikin damuwa" tabbas ba dan Walid ya tambaye shi
yanzu ba, ba zai gaya masa ba.
Ya karkace ya ɗaukko invitation a aljihunsa, ya miƙa wa
walid.
Wani irin ihu walid yayi, haɗi da kururwa, yayi katantanwa a
ƙasa ya kuza uwar ashariya.
Sannan ya ce "Allah dai ya biya maza, dama zaka afkawa
sabgar nan, ka yi mana shiru haka? Ba ka gaya mana ba, balle mu shirya saura
kwana uku fa".
Sauran matasan da ke wurin suka miƙe suna tambayar Walid ko
lafiya?.
Ya miƙa musu invitation ɗin, take suka hau shewa suma, suna
dara.
Kawai ya dafe kansa, yayi shiru.
Walid ya ce "Wai tsaya, auren dole za ayi maka ne? Na
ga baka murna, kuma shi ne ba ka taɓa kai mu ehhh, mun gaisa da antyn namu ba,
iya wuya mun samu mai dafa mana abinci"
"Walid, Abbu ne ya shirya komai, ni ko ganinta ban taɓa
yi ba, kuma ba na fatan na ganta, kuma ba kowa ne ya shirya wannan abun ba, sai
wannan shaiɗaniyar matar ƴar haramun, ya ce umarni yake bani ba shawara ba, ni
kuma na yanke guduwa zan yi, ba abun da zai haɗani rayuwa da wata mace, ba za a
mayar da ni nusari ba, kalli yadda mace ta yi silar rushewar farincikin
rayuwata gaba ɗaya"
Walid ya zauna kusa da shi ya ce "A'a maza, duk
lalacewar naka naka ne, kai ka san albarkar dattijan ke riƙe da mu, ka daina
kallon abun da yake yi maka na rashin jin daɗi, idan yayi maka baki ƙara
watsewa zaka yi.
Duk da lokaci ya ƙure, dole ayi celebration, zamu gayyaci
gayu a sha shayi a babbaka hayaƙi, abun farin ciki ya same mu" ya ƙarasa
maganar suna shewa, ban da Al'amin da zuciyarsa kamar ta yi bindiga.
Hatta kayan da Al'amin zai saka na aure, sai da Abbu ya saya
wa Al'amin, dan ko ganinsa bai sake yi ba, sai dai ya fita yawon neman
sa.
Ƙarfe goma na dare, su Walid suka shirya party, aka dafa
shayi aka raba lemuka, da kayan shaye-shaye.
Gogan yana gefe, yana zancen zuci, har ga Allah so yake ya
gudu, amma ya san ya gudu alaƙarsa da Abbu za ta ƙara tsami. Kuma ya san ko ya
gudu sai ya dawo, ba zai iya barin Abbun ba.
Tunani yake kowace mai tsautsayin da ba a so, ce haka, aka
zaɓi a aura masa oho.
Ana tsaka da walimar hayaƙin, faɗan daba ya kaure, Al'amin
kuma ya koma gefe ya ƙi magana, ƴan sanda suka yi wa wurin dirar mikiya, saboda
rahoton da ƴan unguwar suka kai wa jami'an tsaro, ai kuwa suka kame su har da
shi suka tafi da su ana gobe ɗaurin auren da bai san wacece matar ba.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Hanyar da ta bi ya bi da kallo, yana tunanin a ina ya taɓa
ganin fuskarta.
A ransa ya ce "Mahaukaciya ce kenan, Shiyasa aka aura
mini ita, haukana ya fi naki" ya fito daga falon ya saka takalmansa ya
fice.
Jauhar kuwa durƙushewa tayi, ta ɗora hannunta a ka ta ce
"Na shiga uku" a take ta fashe da kuka ta ce "Allah ka sanya
mafarki ne ba gaske ba, Allah ka sa ba wannan ne mijin nawa ba? A gabana ya
kashe wani, Allah Ubangiji ka rufa mini asiri ka dube ni, ya Allah ka dubi maraicina
da ƙangin da na baro, ka sassauta mini a nan, ya Allah ka sa ba shi ne mijina
ba". Ta cigaba da addu'ar tana kuka, ta kasa fitowa sai ma ƙara sakata da
ta yi a ɗakin tana kuka.
A take komai ya dawo mata fes, yadda ta ganshi, ya yi kisan
kai, hannunsa riƙe da mutum da wuƙa a gefen cikinsa.
"Na shiga uku, ko biyoni yayi ya kasheni, me na yi masa
wallahi ban gayawa kowa yayi kisa ba" tayi maganar ƙasa-ƙasa tana kuka.
Ko da wasa ba ta yi yinƙurin, sake buɗe ƙofar nan, a banɗakik
nan tayi alwalar magariba da ta isha'i, ta kasa addu'a komai, sai fatan Allah
ya sa ba wannan ne mijinta ba.
Ba ta sake fitowa ba, har garin Allah ya waye.
Zaman ɗakin ya isheta, fitowa kuma ta gagareta, sai da ta
leƙa ta ga babu kowa a falon, bakinta ɗauke da addu'a ta fito.
Ba kowa, ta leƙa tsakar gida, ya rufe mata ƙofar, babu
taklmansa kuma a wurin.
Ta dawo falon, ya cinye taliya da man da da ta zuba masa
tas, ya ajiye komai a wurin, hatta wadda ta ɗan zube a ƙasa bai kwashe ba, jug ɗin
ma daban kofin jug ɗin daban.
Ta kwashe komai ta fitar tsakar gida, ga sauran kwanukan da
ta fara wankewa ta bar su a wurin, komai yana nan.
Sai zuciyarta ta fara raya mata, ai ba shi ne mijin nata ba,
ya shigo ne kawai ya tsorata ta, sai ta cigaba da addu'a Allah ya ƙara nesanta
ta da shi.
Ta yi 'yan gyare-gyaren ta na gida, yaran da suke shigo
mata, yau ba kowa duk sun tafi makaranta, ga tsakar gidan wasu irin manyan
ƙadangaru suna bin bango, dan haka fitowa tsakar gidanma wahala yake bata,
saboda tsoro.
Ta datse gidan, yadda babu wanda zai shigo sai ya bubbuga.
A jere ta sake jera kwana biyu ba ta sake saka shi a idonta
ba, akwai ranar da bai kwana a gidan ba. Bai sake dawowa da rana ba, sai cikin
daren nan, idan ya tarar da abinci ya zauna ya cinye abun sa, kafin ta tashi ya
fice.
Abun ya fara damunta, ga tsoron gidan take ji, sosai da
sosai.
Wajen la'asar ta ji ana buga ƙofa, ta din ga tambayar waye,
amma ta ji shiru.
Har zata haƙura da buɗe ƙofar, ta zata ba kowa, aka kuma
buga gate ɗin maimakon ƙofar da ƙarfin gaske.
A tsorace ta buɗe, aikuwa ya hankaɗo ƙofar, ta kuma kurma
ihu, ta kwasa da gudu, ta shiga kitchen ta rufe ƙofa.
Sororo ya tsaya yana tunanin, ihun me take yi dan ta ganshi?
Ya basar ya shiga ya yi abun da zai yi ya fice.
Sai a yanzu ta fara gazgata lallai wannan ne mai gidan, shi
ne mijin da aka aura mata.
Cikin kuka ta ce "Allah komai ka yi dai-dai ne, Allah
ka sanya shi ne mafi alkhairin da nake ta fata". Ta sanya wa zuciyarta za
ta yi ƙoƙarin, danne tsoronsa da take ji, amma abun da ba ta gane na shi ne, ba
iya abun da ya faru waccan ranar ne kawai yake ba ta tsoro ba, tsananin
kwarjinin sa ne ke ƙara rikita ta.
Suna dabarsu, Al'amin yana ta shan sigari, Walid ya ce
"Maza, gaskiya abun da ka ke yi baya dacewa, an kai maka mata, amma kullum
kana nan kana cakewa, akwai matsala ne?".
Al'amin ya rausayar da kai ya ce "Yarinyar Mahaukaciya
ce ashe"
Cikin rashin fahimta ya ce "Mahaukaciya kamar
yaya?".
"Kamar yadda na gaya maka, ihu take yi itakaɗai"
Walid ya ce "Ko dai tsorata ta ka ke yi? Ki tsaya kun
yi magana kun gaisa?"
Aminu ya ce "Da wa?"
"Da amaryar mana" ya ja tsaki, yana mayar da
sigari bakinsa.
"Wallahi Aminu da ni aka yi wa auren gatan da aka yi
maka da na more, haba baka kyautawa gaskiya "
Yayi masa shiru, yaƙi ko kallonsa, dan ko zancen auren ba ya
son ji, haka kurum ji yake yi kamar an yi masa dabaibayi.
Saifu kuwa yanzu ban da gaisuwa, babu abin da yake haɗa shi
da da mama da Baba, dama Babar su hafsa Zakkyya ba shiri suke yi ba, ko kallo
ba ta ishe shi ba.
Sai dai sun fara zancen a kawo 'yar aiki, dan duk yawan 'yan
matan gidan nan, ba sa iya aikin gidan, girki sai dai a jagwalgwala, wani ya
ciwu wani ba zai ciwu ba, gidan nan kuwa wasu lokutan kamar fadar mahaukaciya,
dama jauhar ce ana ɓatawa tana gyarawa, yara na cire kaya suna zubarwa tana
kwashewa, amma yanzu bata nan babu mai gyarawa.
Baba kuwa ƙasan zuciyarsa yana nadamar auren da ya yi wa
jauhar, amma ba zai iya nuna hakan ba, ya duƙufa yana yi mata addu'ar samun
kwanciyar hankali a gidan aurenta.
Cikin dare da ya dawo, ya ji gidan a rufe, bai tsaya jiran
komai ba, ya kama katanga ya dira kamar ɓarawo.
Gaba ɗaya jauhar a zatonta, itakaɗai ta kwana a gidan,
saboda ba ta ji bugun ƙofa ba, ta fito tana ta share-sharenta, ta ɗora ruwan
zafin dafa makaroni, saboda su yaya saifu ya sayo mata, taliya makaroni, mai
maggi sugar da sauransu.
Ta fara bin ɗakunan tana gyarawa. Sai dai ta din ga jin
warin taba, ta rasa daga ina take jin warin.
Kawai ta nufi ɗakin da yake ciki, ba tare da ta san yana
ciki ba, ta afka, a zatonta ita kaɗaice a gidan.
Yana kashingiɗe yana zaune yana kaɗa ƙafa yana shan tabarsa,
ya zazzage kayansa a kan katifar ɗakin, ghana must go ɗin, ya cillar da ita a
tsakar ɗakin. Har da takalma a kan katifar, soson wanka da brush duk suna kan
katifar.
Ba wannan ba kawai, har da ledoji da kwalayen taba, ga tokar
maganin sauro ko ina.
Kamar mahaukaciya haka ta juya, ta ɗiba da gudu, sai dai a
wannan karon, rufa mata baya ya yi, ya cimmata, tana ƙoƙarin rufe ƙofar ɗakin
da ta shiga, ya hankaɗa ƙofar ta faɗi jikinta na wata irin tsuma.
Ya zuba mata ido, wanda ya haddasa mata tsuma da karkarwa
cikin razani da matsanancin tsoro.
Bai ce mata komai ba, sai cigaba da kallonta da yake yi.
"Dan Allah ka yi haƙuri, wallahi ban gayawa kowa ka
kashe shi ba, dan Allah ka yi haƙuri, ni matar aure ce, ka daina shigo mini
gida" tayi maganar wani irin gumi na tsatstsafowa daga fuskarta.
Ya sunkuyo saitinta, warin sigarin da ya sha, tana dukan
hancinta, sai a lokacin ya gane ta, ya gene a in da ya taɓa ganinta.
"Kin ganni na kashe shi?"
Ta jinjina kai alamar eh.
"Mahaukaciya ce ke? Ki na da taɓun hankali ne?" Ta
girgiza masa kai alamar a'a, tana ja da baya.
"Idan ki ka kuma ganina, ki ka gudu kina ihu" ya
zaro wuƙa a ƙugunsa, ya nuna mata. Sannan ya ce "Sai na yi miki abun da ki
ka ga na yi wa wancan mutumin, wato in kashe ki"
Ta girgiza kai ta ce "In sha Allah ba zan sake ba"
ya miƙe, ya mayar da wuƙarsa ya fita ya bar ta.
Wani irin numfashi ta din ga saukewa, cike da tsoro, ta ƙara
gazgata cewar, shi ɗin ne dai mijinta ba wani ba.
Ta jima a wurin tana kuka, sannan ta tashi a hankali, ta
sake komawa ɗakin da ta gano shi.
Ɗakin yana nan, kamar mahaukaciya ta buɗe dealer, ya watsar
da komai, sai warin sigari ɗakin yake yi.
Ta ɗaɗɗaga labulaye, ta zo ta durƙusa ta fara ware kayansa,
wankakku da masu datti, ta kwashe takalmansa, ta jera masa a bayan ƙofa,
wankakkun kayansa, ta shirya su a cikin wardrobe, marasa wankin ta fita da su,
ta share ɗakin tsaf, ta ɗauki brush ɗin sa da toothpaste, ta kai masa banɗakin
cikin ɗakin, da bokiti da buta.
Kayanta akwai turarukan wuta, da aka bata na gudunmuwa, sai
dai ba ta da gawayi, dan haka ta kunna na tsinke, ta sassaka a ko ina, saboda
korar warin sigarin nan. A cikin kayan sa ta ga wata Mp, ta ɗauki mp ta kunna
ta ji tana yi, ta kunna radion jiki, ta ji tana yi, ta fita tsakar gida da ita,
tana ta aikace-aikace, da zummar kan ya dawo ta kashe ta ajiye masa, ta ɗan ɗebe
mata kewa, ta manta ko sallama baya yi kafin ya bayyana.
Gidan su jauhar, akwai maƙwabciyar su Anty lubabatu, tana
tausayinta sosai, suna mutunci da juahar, dan idan ta haihu, jauhar ta yi ta
zuwa gidanta, dan ta ɗauki yaranta, ita ce ta haɗata da 'yan gidan su, take karɓar
shirin dutse tana yi.
Tun washegarin kai jauhar, ta shiga gidan ta ce wa su mama,
a bata mutum ɗaya ya rakata gidan jauhar, amma suka ce ba wanda ma ya san
gidan.
Jauhar kuwa, ta gama aikinta tayi wanka, gidan babu komai na
abinci, sai taliyar nan da macaroni da yaya saifu ya saya mata, gashi sun
isheta, sai dai babban abun da yake yi mata daɗi, tana da damar ta dafa ta ci
yadda take so, saɓanin idan a gida ta girka, sai ta gama wahalar a sanmata.
Tunani take yi, idan ta dafa taliya yau ma ko zai ci, tana
tunanin ko shi ma sun fara isar shi. "Karfa ya ce ko ban iya girki bane,
shiyasa kullum nake dafa taliya. To ai gidan bakomai sai su"
Ta ɗan yi shiru, tana tunanin yau bari ta aika a sayo mata
kayan miya, tayi da miya, so take ma ta nuna masa kuɗin da kakarshi ta ba ta,
amma tsoronsa take ji.
Tana ta tunani, ta ji ana buga ƙofa, cikin murna ta tashi,
ta san baƙi tayi sa ɗebe mata kewa.
Anty lubabtu ta gani, maƙwabciyar su, da ƙanwarta wadda take
karɓar shirin dutse a gidanta, cikin murna tayi musu maraba.
Allah ya sa tana da ruwan pure water, ta basu.
Ta ce "Anty lubabatu shi ne sai yau zaku zo ko? An
barni nikaɗai, ba wanda yake leƙo ni".
"Ki yi haƙuri jauhar, tun washegarin kawo ki, nake
sintirin neman mai rako ni a gidanku, wallahi fafur 'yan gidanku da 'yan tsukin
nan aka rasa masu zuwa su rako mu, wai tsoro suke ji, 'yan gidanku ma wai ba za
su rakomu ba, mijinki ɗan daba ne, ni kuwa na ce ko menene zamu zo, sai
kwatance suka yi mana".
Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Shikenan bakomai, yaya
saifu ma ya zo, daga ni sai yaran maƙwabta, ni kaɗai nake wuni".
Samira ta ce 'Allah sarki, mma dai jauhar ba wata matsala
dai ko?"
Tayi murmushi ta ce "Babu anty samira, ya shiri kin zo
mini da shi?"
"Taɓ kina amarya, kawai sai na kawo miki shiri?"
Jauhar ta ce "Eh mana, zai din ga ɗebe mini kewa ai,
dan Allah idan an samu mai zuwa, ki bayar da yawa a kawo mini, na din ga
yi"
Anty lubabtu ta ce "Jauhar iyayen neman kuɗi".
Samira ta ce "Bar ta ta nema, rayuwar nan ba a zama
haka"
Miya lubabatu ta soyawa jauhar, mai yawa ta sha naman kaji,
da shinkafa da 'yan kayan buƙatu.
Jauhar ta ji daɗin hakan sosai da sosai, ta din ga murna,
suka wuni tare har la'asar, sannan suka tafi.
Suna tafiya ta aiki almajiri, ya sayo mata salak da kayan haɗin
sa, ta zauna ta shirya salak ɗin nan, ta juye miyar a tukunya, ta ƙara soyata
tayi mata gyare-gyare ta ƙara mata su maggi da kayan ƙamshi ta kammala komai.
Ta ɗebarwa yaran da suke shigo mata abincin ta basu, ta ɗebe
wani ta rufe, dan abincin da yawa, ta sake turara shinkafar ta zuba a wani
flask mai kyau kamar a lokacin ta dafa ta.
Tana aikinta, tana jin radiyo a mp.
Ta bawa yara kuɗi, suka sayo mata ruwa da lemo mai sanyi.
Ta gama aikin, ta share kitchen ɗin, ta kwaso sharar abun da
ta ɓata, ta fito kawai ta ga Al'amin a tsakar gida, aikuwa ta razana ta saki
abun kwashe sharar tana ihu, ta zubar da sharar a wurin, har zata gudu sai kuma
ta tuna kashedin da yayi mata, ta tsaya jikinta yana rawa ta ce "Yi
haƙuri, tsorata nayi, ban san ka shigo ba" tayi maganar tana kare jikinta,
saboda babu hijjabi a jikinta, bai jira ta gama maganar ba ma, ya shige falo.
Ta daɗe a tsakar gida, ta kasa shiga falon ma, ta lallaɓa ta
shiga zuciyarta na bugawa da sauri-sauri, gaba ɗaya falon ya gauraye da warin
wiwin da yake yi.
Ba ya falo, ta shiga ɗaki ta sako hijjabi ta fito, sai dai
ta kasa zuwa ɗakin da yake.
Wanka yayi ya fito, ya tarar ta ajiye masa sabulun wanka, a
cikin wanda ta zo da shi, banɗakin ta kai mas bokiti da ruwa, ga buta ita ma
cike da ruwa.
Ya gama wankan, ya ɗora soson a kan sabulun yayi fitowarsa,
da zai canza kaya kuwa, duddubawa ya din ga yi, da ya gan su a cikin wardrobe,
sai da ya watso su gaba ɗaya ƙasa, sannan ya zaɓi wanda zai saka, ya bar su a
wurin ba tare da ya gyara ba.
'yar siririyar muryata ya ji a bakin ƙofar ɗakinsa, tana ta
sallama.
A fusace ya ce "Meye ne?".
Ta razana ta ɗan shigo daga bakin ƙofa ta tsuguna, ta ce
"Dama tun washegarin kawo ni, wasu sun zo, da kakarka hajiya da wasu, suna
nemanka na ce baka nan, suka bani kaya da kuɗi dubu goma, amma na sai maggi da
ashana da omo, a ciki baka zama a gida, ban nuna maka ba, shi ne na kawo
maka"
Ɗan shiru ya yi, jin ta ce hajiya ta zo, ya ji babu daɗi da
bai haɗu da hajiyar ba, dan rabon da yaje ya ganta har ya manta.
"Ga kuɗin" muryarta ta dawo da shi daga tunanin da
yake yi.
"Bar nan wurin kafin na yi ball da ke, ba ruwanki da
shiga sabgata na gaya miki, tashi ki ware" ta tashi ta ce "Kuɗin
fa" banza ya yi mata, ya tsaya yana kallon fuskarsa a mudubin ɗakin.
Ganin ba zai kulata ba, ya sanya ta ajiye masa kuɗin, ta
tashi za ta tafi, cikin tsawa ya ce "Ke!" A razane ta waiwayo.
"Kwashe kuɗin nan ki bar nan" jiki na rawa, ta ɗauka
ta ce "To bar mini ka yi" mugun kallon da ya yi mata ya sanya, ta
juya da sauri ta bar ɗakin.
Ta je kitchen, ta shiryo masa kwanukan abinci a kan tray,
amma ta tsaya tana wasi-wasi, kar ta kai masa ya kuma korarta, ta shiga falon
tana taradaddi.
Ta na shigowa yana fitowa daga ɗakin, take hannunta ya hau
rawa, ta ji tana neman ta saki farantin da kwanukan, ta ƙarasa tsakiyar falon,
ta ajiye ta ce "Fita zaka yi, ga abinci" ta juya ta koma kitchen ta ɗaukko
ruwan roba da lemo, da ta saya masa ta ɗora a kan wani plate ɗin ta kawo. Tana
zuwa taga ya zauna ya kame zai ci abincin, kasancewar yana girmama cikinsa,
Al'amin yana son abinci, dan haka ba kowane tayi yake wucewa ba.
Maimakon ya ɗebi abincin, ya zuba a plate, kawai ya buɗe
flask ɗin, ya juye salad ɗin a ciki, ya ɗaga flask ɗin miyar ya girgije a kai,
ko kallon cokalin bai yi ba, ya zura hannu ya kama kai loma.
Duk da wani irin mugun tsoronsa take ji, amma haka cikin
tsoron, ta tsiyaya masa lemo a kofi ɗaya, ɗaya kuma ta zuba masa ruwa.
Satar kallonta ya yi, yadda take komai a nutse, sai dai
hannunta rawa yake yi, saboda tsoro, mamaki yake yadda take wani zuba masa ruwa
kamar ya sakata.
Ya din ga tunanin ita kuwa wani zunubi ta aikatawa 'yan
gidansu, suka zaɓa su aurar da ita ga shi? Gaba ɗaya yanayinta kalar 'ya'yan
hutu ce, irin wanda ba sa son wahalar nan.
Sai dai yadda yake auna loma, yana basarwa ba zaka ce, ita
yake satar kallo ba.
Ta koma can gefen kujera ta zauna ta yi tsuru, gabanta na
cigaba da faɗuwa da zarar ta kalleshi, sai dai duk da haka, a ranta ta ji tana
son yi masa magana a kan kakarsa, da sauran tambayoyi, duk da miskila ce, amma
idan ta samu wuri akwai hira. Sai dai ko kusa ko alama, ba ta ga wannan fuskar
ba.
Kan ta ankara ta gama zancen zucin, ya kawar da abincin
cikin kula 'yar tsakiya, shanye ruwansa da lemo tsaf, ta zuba masa ido, duk da
ba abun mamaki bane ba, ta saba ganin maza da shegen cin tsiya, dan tsaf Yaya
Saifu zai iya cinye cikin babban flask, dan akwai ranar da suka din ga musu da
surayya, ya ce zai iya cinye shinkafa rabin kwano a zama ɗaya, dama taliya leda
guda yake cinyewa.
Dan haka ba ta yi mamakin yadda ya cinye abincin ba, ya dubi
carfet ɗin ta, milk mai haske, ya goge hannunsa a kai ya tashi tsam ya bar mata
wurin da kwanukanta a wurin.
A hankali ta ce "Na shiga uku, miya a kan carfet ɗina"
da sauri ta kwashe kwanukan, ta ɗebo ruwa da omo, ta goge wurin da ya goge mata
hannu a carfet, ta koma ɗakinsa, ta sake kwashe kayan da ya zubar.
Ya watso su duka gaba ɗaya, ya cire na jikinsa duk ya watsar
ya ƙara gaba.
Ta sake gyara masa, ta kwaso wanda ya cire, da wanda ta
kwashe na wanki ɗazu, ta fito ta jiƙa su zata wanke.
Ta koma ta sake sharo falon, sai dai ta ga leda a in da Ya
tashi, ta ɗauki ledar, ta taɓa ta buɗe, tana tunanin ko ita ta ajiye wani abun,
amma ta ga wani abu kamar ganye a ciki, ta sinsuna ta kasa gane ko menene, kuma
a iya tunanin ta, ba ta ajiye ba. Ta samu wani wurin ta ajiye, ta cigaba da
aikinta.
Sallama aka din ga rangaɗawa a ƙofar gida, ta wanke hannunta
ta ce "Waye"
Ya amsa da "Ni ne" ta saka mayafi, ta fita ta
leƙa.
Wani jibgegen ƙato ta gani, jiki duk a murɗe, duk bai kai
girman Al'amin ba ba.
A ɗan tsorace ta ce "Sannu"
Ya ce "Yauwwa, matar gidan tana ciki ne?"
Ta ce "Eh meyafaru?"
"Ɗan je ki ce mata ana sallama da Boss"
Ta yatsuna fuska ta ce "Waye hakan?"
"Mai dogon zamani nake nufi, ba shi ne maigidan
ba?"
Jauhar ta ce "Ba wani mai irin sunan nan a gidan nan,
ba sunansa kenan ba"
Ya ce "Kee, ni fa nake rako shi har gidan nan, ki ce
mini ba sunansa kenan ba?"
Ta tsuke fuska ta ce "To shikenan idan ba ka yadda
ba"ta mayar da ƙofa ta rufe.
Walid ya koma gefe ya kira Al'amin ya ɗaga ya ce "Ya
mai laya".
Walid ya ce "Na kiyayi mai zamani, maza na zo gidanka
wata 'yar cika, ta leƙo ta raina mini hankali, na kusa kwarfeta, na ƙyaleta ne
kar na kwafsa"
"Wacece ya aka yi?"
"Kai na zo nema, ina ta jiranka, yaran nan za su karɓi
kaya su rarraba, ba ka zo ba, na biyo ka gida, wata jar yarinya nunar rana mai
kama da 'yan china ta ce mini wai ba mai irin sunanka a gidan, na ce mata mai
zamani wai ba gidan ba ne"
Al'amin ya ce "Ita ce matar gidan fa"
"Kai haba maza, wannan ɗin?"
"Yarinyar da ta suma, na ce ka saka a kaita
Asibiti"
Walid ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, maza
ka sha kwana wallahi, dama ita ce, kaga rabo, wata 'yar caras beauty ka ji
muryarta".
"Kai dalla malam, ka buga mata ƙofa, ka ce ta duba in
da na tashi, na bar leda ta baka, ka tsaya shirme".
Walid ya ce "To meye na yi mini masifa kuma, na ga dai
auren dole aka yi maka" katse wayar walid ya yi, yayi ashar ya ce
"Ina da wannan, ai kan a ganni a ƙofar gida, sai an sha wuya, kai Aminu
kamar ba biladam ba" yayi maganar yana bubbuga ƙofar gidan.
Kamar ba zata buɗe ba, ta sake buɗewa cikin mamaki ta ce
"Malam lafiya?"
"Ya ce ki duba in da ya tashi, ya manta leda ki
bani"
"Shi wa?"
Cikin mamakin yadda take neman raina masa hankali ya ce
"Maigidan"
"Dan Allah ka yi haƙuri, bai bar mini wannan sallahun
ba"
Ya ce "Saboda bai bar miki sallahu ba, ba zaki bayar
ba?"
Ta marairaice ta ce "Idan na baka ya dawo, ya ce mini
ba shi ya aikoka ba, kaga bani da abun da zan ce masa".
Ya ce "Gaskiya ne, shikenan" ya juya ya tafi, ta
mayar da ƙofar ta rufe.
Duk da kayan suna da nauyi, haka ta zage ƙarfinta a kan
kayan nan, ta wanke su.
Sai a lokacin ta kalli window, ta ga mpn da ta ɗaukko masa
ta ce "Na shiga uku, da ya ganta fa me zan ce masa?" Ta ɗauka ta
mayar masa ɗakinsa
Al'amin kuwa duk in da ya juya, sai dai ya yi gyatsa saboda
yadda ya ƙoshi.
Walid ya je ya samu Al'amin, ya din ga yi masa mitar
yadda jauhar fafur ta hana shi saƙon nan. Yayi ya gama, bai ce masa komai ba,
sai sakace da yake yi, yana cigaba da jin ƙamshin miyar da ya ci a hannunsa.
"Yanzu mai zamani shikenan yau b za a sayar da kaya ba?
Saboda ka yi aure 'yar yarinya ta hana aiki yau?"
Al'amin ya kalle shi ya ce "Ƙila"
Yayi tsaki ya ce "Yauwwa, na haɗa maka da mp ɗina a
kayanka, ka kawo mini kayata kafin ita ma ta ce taka ce ba zata bayar ba"
Al'amin ya tuna ya ganta a kan window, kuma ya ga yadda ta
gyara masa ɗakin, ya tabattar ɗauka tayi ta kunna.
A ransa ya ce 'Ashe ba tsoron ki ke da gaske ba'
"Malam magana nake yi maka, a kawo mini mp ɗina. Yunwa
ma nake ji, ko zamu je cin garau-garau ne?".
Aminu ya miƙe ƙafa ya ce "Sai ka dawo"
Walid ya fice yana tunanin asarar da za su yi, na rashin
sayar da kayan nan yau, ya san ko zasu dambace da Al'amin, ba zai koma gidan
nan ya ɗaukko kayan ba.
Ƙarfe tara na dare ya shiga cikin unguwar, tare da su liti,
da Walid, sai dai ba su shiga cikin gidan ba, suka zauna a barandar kusa da
gidan, suka din ga hira suna shaye-shaye.
Jauhar kuwa kamar a cikin falonta suke shaye-shayen, saboda
yadda duk gidan ya gauraye da wari.
Yau da gari yayi haske ta fito, a falo ta tarar da shi, a
kwance a kan doguwar kujera.
Ta durƙusa ta ce "Yaya ina kwana" waiwayowa yayi
ya kalleta ya kawar da kansa, sai dai ba ta tashi ba.
Har ta fitar da ran zai amsa ya ce "Lafiya"
Ta miƙo masa leda ta ce "Ga abun da ka manta jiya, wani
ya zo ya ce ka aiko shi, ni dai ban bashi ba. Na ga kamar ganyen shayi ne, ko
na ɗiba na dafa mana tea?" Afujajan ya kalleta, tashi ya yi zaune ya ce
"Da me zaki dafa tea ɗin?" Ta nuna masa ledar tana sunkuyar da kai ta
ce "Naga kamar ganyen shayi ne, sai na dafa mana ko jallof ɗin taliya
ce?"
"Wiwin zaki dafa a matsayin shayi, saboda mahaukaciya
ce ke?"
Da sauri ta kalleshi ta saki ledar da sauri, sai dai ba ta
ji daɗin mahaukaciya da ya kira ta da ita ba.
"Dan Allah ka yi haƙuri, ban sani bane".
"Jiya mai laya ya zo, ya ce miki yana neman mai dogon
zamani, kin ce ke baki san shi ba, to ni ne mai dogon zamani, idan kuma jami'an
tsaro ne suka ce miki Viper ni suke nema, idan ki ka cigaba da yi musu rashin
kunya kuma, za su sassaraki ne a banza su bawa karnuka namanki"
Shagwaɓe fuska ta yi zata yi kuka ta ce "Innalillahi wa
Innalillahi raji'un, dan Allah ka bashi haƙuri, ba zan sake ba, dama ban san me
zai yi maka bane, shiyasa na ce masa ba kai bane ba shiyasa"
Ya saka hannu ya ɗauki ledarsa ya tashi zai fita ta ce
"To karin kumallon fa" ko waiwayowa bai yi ba, ya fita.
Bayan fitarsa, ta je ta kwaso kayansa da ta wanke, ta ninke
su tsaf, ta shiga ɗakinsa, tana shirya masa kayan, ta fito masa da guda ɗaya da
zai saka, ta ɗaukko bedsheet tana canzawa katifarsa, kawai ta yi karo da wata
irin zabgegiyar wuƙa.
Gabanta ya faɗi wuƙar kawai abun tsoro ce.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, jikinta na rawa ta
hau kuka, ta kai hannu za ta ɗauka"
"Idan ta ji miki rauni, ke ki ka sani".
A razane ta ɗago jikinta na tsuma.
"Fita ki bar mini ɗaki, bincike ki ke yi mini ko?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a wallahi, bedsheet zan canza
maka na ganta, ba bincike nake yi maka ba"
"Fita to"
Ta ce "To, ga kaya na fito maka da su, wanda zaka
saka".
Ya sake tsuke fuska ya ce "Ki fita na ce"
Ta zo fita, ta kasa saboda yana tsaye a wurin.
Yayi tsaki ya bata hanya, ta fita har da tuntuɓe, a tsakiyar
falon ta ga ledar buredi, da sugar da madara da Lipton.
Ta lallaɓa ta fita ta kunna gas, ta ɗora shayi.
Buga gate ɗin gidan ake yi da ƙarfi, ba shiri ta tafi ta buɗe.
Wani matashin magidanci ta gani, a tsaye ya kima uwar hula,
ya rufe kunnuwa.
Ta gaishe shi cikin ladabi, ya ce "Ina matar
gidan?" Mamaki take yi, meyasa mutane suke neman matar gidan idan suka
ganta.
"Lafiya?"
"Eh, megidan muke nema? Sunana malam lawan, ni ne mai
wannan gidan na kusa da ke"
Jauhar ta yi murmushi ta ce "Allah sarki, baban su
halimatu? Ai suna shigo mini".
"Eh, mai unguwa yana neman mijinki, ƙararsa muka
kai"
Ta ce "Subhanallah, laifin me yayi muku?"
"Au jira zamu yi sai ya yi kan mu ɗauki mataki, an ce
mana mutumin banza ne, kuma da ya zo bai yi mana sallama ba, bamu san da wani
irin mutum zamu zauna ba, jiya an hanamu sukunk da warin wiwi, ya tara mana
'yan iska a layi. An gaya mana gawurtaccen ɗan daba ne da ya addabi in da yake,
aka yi masa aure mu aka kawo mana bala'i. Gara aje a zauna da mai unguwa da
'yan sanda, ko ya tashi, ko ayi yarjejeniyar zaman lafiya da shi".
Jauhar ta ce "Haba malam, bai yi muku komai ba kuma sai
a kai shi wurin 'yan sanda, ina laifin mai unguwar ma, in sha Allah ba zai sake
sha muku komai a layi ba, kuma ba zai cutar da kowa ba ma. In sha Allah wataran
sai labari zai daina".
"Ke rufe mini baki kan na kwaɗe ki, nasiha zaki yi
mini, ba zamu zauna da mutumin banza da wofi ba wallahi, ya lalata mana yara
haka kurum ba"
Motsi ta ji a bayanta, tana waiwayawa ta ganshi a tsaye,
ashe duk ya ji abun da malam lawan ke faɗa.
Da sauri ta leƙa ta ce "Ka tafi kar ka bari ya
ganka"ta waiwayo ta rufe gate ɗin tana kallonsa.
"Ya tafi kar ya bari na ganshi ko? To ke bari na yi
miki abun da zan yi masa".
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Kafin ta yi wani yinƙuri, ya janyeta daga jikin gate ɗin,
sai dai kasancewar ba ƙwari ne da ita ba a kansa, sai da ta kai ƙasa.
Ya buɗe ƙofar ya lelleƙa, bai ga kowa ba, tuni malam lawan
ya ɓace.
Ya dawo ya kalleta, ta sunkuyar da kai, sai murza yatsan
ƙafarta take yi, da yake yi mata zafi, saboda faɗuwar da ta yi.
Ƙwafa ya yi ya wuceta, ta lallaɓa ta tashi, ta shiga kitchen
ta ɗora tea, ta ɗebi miyar nan da su Anty lubabatu suka kai mata, ta ƙara
gyarata ta zuba ta kai masa falo.
Ya wani maze yana basarwa, nan kuwa jira yake yi, tayi ta
kawo masa ya ci.
Sai dai yadda yake cin abinci ya goge mata a jikin kujera,
ko carfet yana damunta, sai dai idan ya gama ya tashi ta goge.
Dan haka ta sayo toilet paper, take haɗo masa da ita, amma
ko kallonta ba ya yi, idan Allah ya taimaketa ne, wani lokacin sai ya goge a
jikin kayansa kamar wani ƙaramin yaro.
Da daddare kuwa kullum, sai ya cika gidan da warin sigari,
wasu lokutan ba zai dawo ba, sai sha biyu na dare, ya shige ɗakinsa yayi ta
shaye-shaye, da safe kuma idan ta ajiye abinci zai ci, idan ba ta ajiye ba ba
zai tambaya ba, kuma ba zai sayo ya kawo ba.
Idan za ta gyara masa ɗaki sau goma a rana kuwa, muddin ya
shiga sai ya watsar da komai ya ɓata, yayi shaye-shayensa ya bar mata toka da
sauran karan sigari duk a ɗakin.
Wasu lokutan sai su shafe kwana biyu ba su haɗu ba, gashi
zai kwana a gidan, amma ba zai shigo ba sai ta yi bacci, duk da wataran ba ta
baccin sai ta ji shigowarsa, asubar fari kuma sai ya fice, ranar da ya ga dama
kuma, sai ya bari gari yayi haske, ko za ta bashi abinci, dan sai yanzu ya
fuskanci abincin waje wasu lokutan ga ƙaurin hayaƙi gashi ba sa jin sinadaran ɗanɗano,
nata kuwa har cikin kansa yake jin su.
Yau ma dawowa ya yi rana tsage-tsage, walid ya sayo musu
abinci, yana fara ci ya ji babu daɗi, ya ajiye ya ce gida zai tafi.
Walid ya ce "Da ranar nan tsaka zaka fi gida?"
"Eh" ya amsa a taƙaice.
"Lallai, na fuskanci lamari yana ta daidaita to Allah
ya sa mu ji alkhairi ya kawo zuriya ɗayyiba"
Ya haɗe rai ya ce "Mai laya"
Walid ya ce "Sorry maza, na kiyayi mai zamani" ya
fice ya tafi gida.
Jauhar tana ta lissafin kuɗin hannunta, sun kusa ƙarewa,
girkin ma duk da dabaru take yin sa, ga gogan babu ruwansa sai dai ta dafa ya
lashe.
Da 'yan dabaru take yin ɗan wake yau, ta aiki almajiri ya
sayo mata kabeji da cucumber, tana jiran dawowarsa, Al'amin ya dawo, a duk
lokacin da za ta ganshi sai ta razana, gashi ba sallama yake yi ba, ya hangota
da tukunya a kan gas, ya yi ajiyar zuciya ya san zai ci abinci.
Ya shiga ɗakinsa, ya tarar ta sake wanke masa kaya, ta gyara
ɗakin tsaf.
Tsaki yayi ya ce "Ita dai wannan an yi 'yar
wahala"
Ya daidaici lokacin da ta gama girki, ya dawo falo ya zauna,
aikuwa sai ga ta abinci bakinta ɗauke da sallama.
Bai amsa na sai Alla-alla ta kawo ta ajiye, saboda yadda
ƙamshin manjan, ya cika masa hanci.
Ta ajiye masa ya haɗa abun sa ya fara ci.
Ta zauna a gefensa, cikin fargaba ta ce "Yaya"
shiru ya yi mata, yana haɗiye ɗan wakensa da hurhuɗu biyar-biyar.
Ta sake cewa "Yaya magana nake dan Allah abu zan
tambayeka".
"Malama sunana Aminu, kar ki sake ce mini wani
Yaya" a ranta ta ce 'Ai na san a rina'
A zahiri kuma ta ce "Ai ba zan iya faɗar sunanka ba, ya
za ayi na faɗi sunan mijina kamar mara ɗa'a" sai ya ji abun wani
banbarakwai wai mijinta.
"To me zan din ga ce maka?" Ba ta jira amsar sa
ba, dan ta san ba zai amsa ba, ita kuma zaman kuramen nan da suke yi ba son sa
take yi ba, ace kana zaune a ƙarƙashin mutum, amma ba zai kulaka ba.
"Na ji abokanka suna ce maka boss, ni kuma sai na ce
maka master, idan na ce master zaka amsa, ko nima boss zan ce? Tun da ba ka son
yaya?" Ta tambaye shi tana murmushi ba tare da ta kalli in da yake ba,
saboda kwarjinin da yake yi mata, yanzu haka ma ƙarfin hali kawai take da take
yi masa magana.
Kallonta yayi, tana murmushi dimple ɗin ta na side ɗaya ya
lotsa, ya gane dakiya kawai take yi, amma a tsorace take yi masa magana.
Duk da bai bata amsa ba, amma matsern da ta ce zata din ga
kiransa da shi, ya so yayi murmushi, amma yaƙi ya sha kunu, yana suɗe kwanon ɗan
wakensa.
Cikin hikima ta ce "Da da sauran garin ɗan waken nan,
da na dafa maka wani, ko na ƙaro maka?"
"A'a" ya ajiye kwanon, cikin sauri ta miƙa masa
wani tsumma mai kyau, ta ce "Gashi ka goge hannunka, manjan yana da kamu,
sai mu je waje na zuba maka omo ka wanke sosai" ya karɓa ya goge, ya koma
ya kashingiɗa yana duba wayarsa mai madannai.
"Na ce, dan Allah sonake na shiga maƙwabta na yi musu
sallama na tare, wai haka ake yi, ka ga mu bamu cewa kowa mun tare ba"
"Sauka lafiya" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba.
"Yauwwa na gode sosai master, bari ayi la'asar, sai na
je. Yauwwa mutumin ɗazu ya ce wai mai unguwa na nemank..... Ba ta ƙarasa ba ya
tashi, dan surutunta ya fara isar sa.
Bayansa ta bi da kallo, 'Da sannu wataran zaka tanka mini
ne, ni ba zan iya rayuwar zaman kurame ba' tayi maganar a hankali.
Huɗu da rabi, bayan ta yi la'asar, ta leƙa ɗakinsa ta ce
masa za ta fita, ta tarar yana salla.
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, tare da hamdala a zuciyarta,
ba ta taɓa tsammanin yana kai goshinsa ƙasa ba.
Ta zauna a bakin ƙofar tana kallonsa, duk da shaf shaf yake
yi, kuma azahar da la'asar ya haɗa a lokacin, amma ta ji dadin ganin yana
salla.
"Master bari na je, idan ka idar ka sani a addu'a,
Allah ya sa ka daina jin haushina, ban san me nayi maka ba" dama ta san ba
amsawa zai yi ba ta fita.
Matasan 'yan mata ne su biyu a gaban rahila suna cin abinci,
da alama daga makaranta suka dawo, domin kuwa bayansu jibga jibgan akwatuna ne,
na 'yan makaranta.
"Umma, nifa haryanzu na kasa daina mamaki, wai yaya ne
yayi aure? Wai dan Allah ya aka yi aka samu aka bashi 'ya a yadda yake? Kuma ba
a bari mun dawo ba aka yi bikin?"
Rahila ta ce "Ke dallacan, waye ya ce miki abun na
shiri ne shahida? Neman mafita nake ba shiri faka-faka na saka aka samo wata
yarinya ya je can ya ƙarata, ya ƙara sako mini yaro a gaba, irin kallon da yake
yi mini, tsaf zai halakka ni, cikin ikon Allah tun da aka yi auren, ban sake
ganinsa a gidan nan ba, ya samu mace yayi luf"
Shahida ta ce 'Ni wallahi mai tsautsayin da aka aurawa nake
jin tausyai, yaya za ta yi da shi dan Allah dan Annabi?"
Amira ta ce "Ke ina ruwanki ne shahida, ina ruwanki da
ko ma wa ce ta aure shi, ba dai an samu ya tafi na, case close".
Shahida ta yi murmushi ta ce "Ina ne gidan nasa
ne?"
"Yana can gidansa na ɗorayi, ba kuma cewa na yi ki je
ba, kar abun da ya kai ki gidansa, balle ya lallaɓa ya dawo mana nan ya je can
su ƙarke".
"Ahh haba umma, sai mu yanke alaƙa da shi duka kenan?
Yayi aure muna school kuma mun dawo ba zamu ganshi ba?"
Amira ta ce "Wallahi a garin shishshigin nan da ki ke
masa, zai kassara rayuwar ki, ki yi ta shige masa yana yarfaki"
"Wallahi ki ka je gidansa ma sai na ci ubanki shahida,
na gaya miki, ke baki san sai ku kasa auruwa ba saboda mugun halinsa da
mummunan tabon da yake da shi ba a unguwar nan?"
Shahida ta ajiye cokalin hannunta ta ce "Umma, shi fa
jini ya fi ruwa kauri, the only male brother i have, sai ki ce sai na yanke
alaƙa da shi?"
"Au jayayya zaki yi da ni? Shi Abban uban meye idan ba
yayanki ba?"
Ta tashi ta ce "Ai ba babanmu ɗaya ba, Yaya Al'amin
kuma babanmu ɗaya, kowane ina son sa"
Rahila ta ce "La ila ha illalahu Shahida "
Amira ta ce "Dan Allah umma bar shashasha, za ta gane
kurenta ne"
Rahila ta cigaba da salallami, a kan yadda ke adawa da ita
wasu lokutan a kan Al'amin.
***
Juahar gidan malam lawan ta fara shiga, wato gidansu
halimatu da walida, yaran da suke zuwa tayata hira, suka gaggaisa da maman,
sannan su halimatun, suka rakata sauran gidajen maƙwabta, tayi musu sallama.
Har wurin masu kayan miya, da masu shaguna suka nunnuna mata da wurin makarɗe.
A bayan gidan suka je har gidan wata tela, da har da
yaranta, su na shigarwa jauhar, suka gaisa jauhar ta tarar da yaran suna stone
work a jikin ɗinki, har ta karɓa tana taya su, saboda a rayuwarta tana son
sana'oin hannu suna matuƙar burgeta.
Take cewa matar, idan an samu stone work ta din ga aika mata
da shi tana yi mata.
Matar ta ce 'To nawa zan din ga baki, dan kuwa ina samun
aikin su sosai da sosai"
Cikin tsananin murna, da jin cewa ta samu abun yi, ta cewa
matar, ko nawa ne ta bata, tana son za ta din ga yi, nan hira ta ɓarke, take
gaya wa matar, ta iya shirin dutse, har adon da ake yi da shi a jikin ɗinki,
duk zata iya, suka yi yarjejeniyar matar zata din ga bata ta yi mata.
Ganin hadari ya fara haɗowa, ya sanya ta yi mata sallama, ta
koma gida, sai dai tana komawa, ya zura takalmansa zai fice, ta ce masa kar ya
fita, hadari ne a garin, amma ba ta gama rufe baki ba, ta ji ya buɗe ƙofa ya
fice.
Ta kawar da abun da zata kawar, ta rurrufe ko ina, ta laluba
ta ɗauki mp a in da ta ajiye, ta tarar ya ɗauke kayarsa, ta ce "Da sauƙi,
tun da ba ka yi mini faɗa ba".
Ruwan sama aka yi, kamar da bakin ƙwarya, ga wata irin iska
da ta jefa jauhar, cikin razani da tashin hankali, yadda kwanon yake ƙara ji
take tamkar zai kwashe ne, saboda ƙarfin iskar da ruwan.
Ta takure wuri guda, tana ta addu'a, kasancewar lokacin da
ake ruwan sama, lokaci ne na karɓar addu'a, mafi yawan addu'arta a kan Al'amin
ne, da take masa fatan shiriya.
Ko da ruwan ya tsagaita, ta fito falonta, ruwa ya shigo
sosai, ya jiƙe ɗakin, ta buɗe ƙofar falon, rashin kyakykyawan magudanan ruwa,
ya sanya kwatocin layin yin ambaliya, duk suka shigo mata gida, gashi ba ga da
rariyar kirki, sai ta banɗkuna, dan haka babu wurin da ruwan zai fita, tsakar
gidan ya shafe da ruwan kwatami, falonta ma duk ruwan ya shigo, gashi idan aka
yi ruwan, tsigar jikinta tayi ta tashi.
Haka ta samo kwano, ta din ga ɗibar ruwan tana zubarwa, ta
naɗe carfet ɗin ta, ta jingine, sai zallar buhun da aka shimfiɗa a ƙasa, ta din
ga kwarfe ruwa a falon nan.
Ta je ta yi sallar magariba, Allah ya sa ruwa bai shigar
mata bedrooms ba.
Ana sallar isha'i sai gashi ya dawo, ya tarar da ita,
fitilarta babu batirin kirki, duk tayi duhu, sai kwashe ruwa take a falo.
A ransa ya ce "Iyayenki ne suka ja miki" tayi masa
sannu da zuwa, ta cigaba da aikinta, har zai wuce ya dawo ya karɓi kwanon, ya
haɗe mata kujerunta wuri guda, ya kunna fitilar ƙaramar wayarsa, ya ƙarasa
kwashe ruwan.
Shi kansa ya san gidan nan kango ne, yana buƙatar gyara
sosai, bai ci ace har an saka mutum a ciki ba, amma da iyayensa da na ta, ya
rasa wannene uban garajen da ya saka aka yi haka.
Ya ɗaɗɗaga labulayen, saboda ɗakin ya sha iska, daga nan ya
tafi makwancinsa, ta tafi nata.
Da safe ruwan duk ya tsane, amma sai ƙanƙame jikinta take
yi, ƙarnin ruwa da ya kwanta ya din ga damunta.
Haka nan ta daure, ta gyara gidan, ta zuba miya ta yi jallof
ɗin macaroni, kasancewar falon a jiƙe yake, da danshi, da sauran Lipton ɗin
jiya, ta dafa shayi har da su citta ta yi sallama a ƙofar ɗakinsa, bai amsa ba
dama labulen a ɗage yake ta shiga.
Ta ajiye masa ta ce "Ina kwana?" Ba ta jira ya
amsa ba, ta haɗa masa tea, ta tashi ta fita.
Aka jima ta dawo, ta shiga banɗakinsa ta wanke, ta ɗauki
bokiti ta dawo, ta haɗo ruwan zafi na wanka, ta kai masa banɗakin ta ce
"Master ga ruwan wanka nan na kai maka, mai ɗumi ne" idan ta ce
mastern nan, sai ya ɗaga kai ya kalleta.
Ta ce "Yauwwa, master zan kafa ƙusa a toilet ɗin ka,
idan ka gama wanka, ka dinga saƙale soson, idan ba haka ba sabulun narkewa yake
yi, sai ka ga ya ƙare da wuri"
Ta zagaye shi, ta fara tattare kayan duk da ya watsar a ɗakin
kamar ƙaramin yaro.
Ya gama cin abincin sa, ya fara shan tean, yana jin yadda
ƙamshin da yajin citta yake ratsa shi yana yi masa daɗi.
Yana zaune ta gyare ɗakin, ta kukkuna masa turaren wuta, sai
dai kafin ta ƙarasa, ya kunna sigari a ɗakin.
Sai da ranta ya sosu, akwai sauran warin ta jiya da daddare
ma da ya sha, ta gama aikin ɗakin, ta kunna turaren wuta, ya kuma kunna wata
sigarin.
Ta maze ta ce masa "Ruwan wankanka, kar ya huce fa, na
ga garin da sanyi haryanzu, idan ka yi wanka da na sanyi, zaka yi mura"
A hasale ya ce "Ke, fita ki bar mini ɗaki, kin gama
tsegumin ai, kin sakani a gaba kin ga abun da nake yi, to fita ki bar min ɗaki,
ba zan wankan ba"
Ba ta sake cewa komai ba, ta juya ta fice, ta cigaba da
ayyukan ta, tana tsaka da wanke-wanke, ya fito da sauri, hannunsa riƙe da waya
yana cewa "Kar ku raga musu, gani nan zuwa" ta miƙe tana kallonsa,
amma ta kasa yi masa magana.
A haka yana ƙaurin sigarinsa da komai, ga kayan da su ya
wuni jiya, ya wayi gari da su, amma bai canza wasu ba, ya fice cikin
matsanancin sauri.
Ta koma ta cigaba da aikinta, tana addu'a Allah ya sa ba
wani rashin jin zai je yayi ba.
Baba yana gida, aka aiko ana sallama da shi.
Yana fita ya tarar da 'yan uwan Alhaji mu'azzam da suka kawo
kuɗi.
Suka gaggaisa, ƙanin mahaifin Alhaji mu'azzam ya ce
"Gamu mun dawo, ɗanka ne ya dawo da mu, ya ce a bayar da haƙuri, kar a ji
mu shiru, ayyka sun yi masa yawa, ba zai samu dawowa nan kusa ba, shi ne ya ce
mu zo ayi magana, a ƙarasa shirye-shirye kawai, ayi auren a tura masa ita
can".
Gaban Baba ya faɗi jikinsa a sanyaye ya ce "Alhaji dama
ko da baku zo ba, zan neme ku ni na zo, an sami matsala ne, zan dawo muku da kuɗin
aurenku".
Suka yi turus gaba ɗaya suka ce "Wace irin matsala ce
haka?"
"Yarinyar nan, yau ta kusa sati biyu, ina mai baku
haƙuri, a bashi haƙuri dan Allah. Zan kawo muku kuɗin aurenku"
"Amma wani abun yayi ne, ko wani laifin shi mu'azzam ɗin
yayi?".
Baba ya ce "Ko ɗaya, ka san matar mutum kabarinsa,
mu'azzam bai yi mini komai ba, dan Allah a bashi haƙuri"
Suka ce "To shikenan, Allah ya tabattar mana da
alkhairi".
Suka amsa da "Amin"
Baba ya ce "Ku bani account number, na mayar muku da kuɗin
auren"
Ɗaya daga cikin su ya ce "A'a, a bar wannan maganar sai
ya dawo tukuna, Allah ya basu zaman lafiya"
Ya amsa da "Amin".
Bayan la'asar yara duk suna islamiyya, babu 'yan aike, ta ce
bari ta fita ta sayo maganin sauro, idan ya dawo sai ta gaya masa.
A ƙofar gida suka haɗu da maman su halimatu a waje da wata
maƙwabciyar su, suka gaisa ta ce "Maman halimatu, ba ku shigo mini mun
gaisa ba haryanzu".
"Wallahi Amarya, ba ƙi muka yi ba, kin sa yanayin mijin
naki sai a hankali, abun da tsoro, kar wani abu ya faru".
Ranta bai yi mata daɗi ba ta ce "Haba dai, ina ruwansa
da ku? Kawai dai a shigo a gaisa, shikenan a gaida su halimatu" tayi gaba
zuciyarta babu daɗi, a duk lokacin da ta ji an aibata shi, sai ranta ya sosu.
Har dare ba ta sake ganin Al'amin ba, gashi ita ba waya ba,
wasa-wasa har dare yayi babu Al'amin babu dalilinsa har garin Allah ya waye,
bai kwana a gida ba.
Sai abin ya fara damunta, gashi ba ta san a ina za ta ganshi
ba.
Abu kamar wasa, aka sake shafe wuni, aka shiga kwana na
biyu, babu shi babu labarinsa, nan fa hankalinta yayi mummunan tashi, gashi ba
ta san wa za ta nufa ta gayawa ba.
Maman halimatu ce tayi sallama, Jauhar ta saka hijjabi ta
fito tana murmushin yaƙe ta ce "Maman halimatu, sannu da zuwa shigo"
"A'a ba shigowa zan yi ba, abbansu yana nan bai fita
ba, bai san ma na shigo ba na ce kin kuwa san an kama mijinki?" Gaban
Jauhar ya faɗi ta ce "Yaushe? A ina? Waye ya gaya miki?"
"A bakin Abban su halimatu na ji, cune suka yi masa aka
kama shi, amma dan Allah kar ki gaya masa wanda suka saka aka kama shi ɗin dan
Allah, na gaya miki ne na san baki sani ba".
Tuni idon Jauhar ya cika da hawaye ta ce "Eyya, meysa
abban su halimatu yayi haka? Wallahi babu abun da zai yi wa wani, ba ruwan shi
da kowa idan ba taɓa shi aka yi ba, ina aka kai shi? Dan Allah ki gaya mini,
ina gidan ban san ina zan nufa ba ma".
Tayi ƙasa da murya ta ce "Yana anti daba can aka kai
shi".
"Menene anti daba kuma? Ina ne?".
"Can in da ake kai 'yan daba, ki shirya ki je ki duba
shi".
Ta ce "To na gode" bayan tafiyar maman halimatu,
take ta ji haushin malam lawan ya kamata.
Tayi tunanin ko gidansu za ta je, ta faɗa, amma sai ta ga
idan tayi hakan, kamar ta tozarta kanta ne, dan haka ta fasa ta ɗora girki, ta
gama ta shirya, ta zuba a flask, ta bi kwatancen da maman halimatu tayi mata.
Su kansu yanayin jami'an tsaron wurin, tsoro suka bata, ba
ta taɓa zuwa police station ba, ta gaishe su cikin girmamawa sannan ta ce
"Dan Allah wani nake nema"
"Wa kenan?" Wani ya tambayeta.
"Al'amin sunansa"
Ɗan sandan ya ce "Anya, babu wani mai irin wannan sunan
da muka kama".
Ta ce "Dan Allah nan aka ce mini an kawo shi, dan Allah
officer ka duba mini"
Na kusa da shi ya ce "Ko viper take nufi?"
Ta ce "Eh shi, mai dogon zamani"
"Ya aka yi me zaki yi masa?"
"Wurinsa na zo, maƙwabciyata ta ce mini cune aka yi
masa aka kama shi, wallahi bai yi komai ba".
"Ke ya aka yi ki ka san bai yi komai ɗin ba? Wacece ɗin
sa ke, ni tun da muke kama shi ma, ban taɓa ganin wani ya zo wurinsa ba, idan
ba ire-iren sa ba ko yaran ubangidansa ba"
Ta ce "Mijina ne"
Saroro suka yi suna kallon jauhar, kyakywar yarinya ƙarama
da ita.
"Ke kuma auren soyayya ku ka yi? Jama'a kun ga matar
Viper, yaushe ne kuwa zuwansa na ƙarshe aka fito da shi aka ce aure yayi"
waiwayowa suka yi suna kallonta, ta sunkuyar da kai tana fatan Allah ya sa su
bar ta ta ganshi.
Ɗaya daga cikin su ya ce "Ku fito da shi, ta ganshi,
amma dai Viper yayi asara, daga aurensa ya saka 'yar mutane fara sintiri saboda
shi".
Saroro yayi da ya hangota cikin hijjabi, 'yan sandan suna yi
mata tambayoyi.
Tana ganinsa tayi ajiyar zuciya, ya ƙaraso gaban kantar ya
kalleta ya ce "Me ya fito da ke?"
"Kwana biyu baka nan, ban san in da ka ke ba, sai yau
ban san kama ka aka yi ba"
Ya sake kallonta ya ce "To ware ki koma"
Jauhar ta ce "To in koma, kai fa ba sakinka za su yi mu
koma ba?"
Al'amin ya ce "Ki tafi na ce, kuma kar ki sake zuwa
wurin nan kina mace, ware" haushi ne ya kamata, yadda yake korarta, shi ba
ayi masa abun arziki sai hantara.
Ta ɗora leda ɗuake da flask ɗin Abinci ta ce "Gashi
abinci ne na kawo maka" sai da ya ɗan yi shiru yana kallonta.
Tun da ya fara rashin jin sa, babu mai tunawa da shi, ya
kawo masa ziyara ko abinci, idan ba su walid ba, sai kuma ita yanzu.
"Ahh yau zamu ci girkin amarya, amma hajiya sai kin
fara ci kafin ya ci"
Bai saurari ɗan sandan ba, ya ɗauki abincinsa ya koma gefe.
Ya buɗe, ta yi sauri ta zagaya, ta huda ruwa pure water, ta
ce masa "Ka fara wanke hannunka"
Kamar ya shareta, sai kuma ta zuba masa ya wanke, ya saka
hannu ya fara cin abincin.
"Akwai sauro ne wurin? Na ga kamar ya cijeka, jikinka
duk cizon sauro?"
"Mmm" ya amsa yana cigaba da cin abincin.
"To yaushe zasu sake ka, kar ka yi rashin lafiya,
saboda cizon sauro" shi dai yayi shiru yana cin abun sa.
Ya gama ci ta bashi ruwa, ya karɓa ya zuƙe, ta ƙara masa
wani ya shanye.
Ta ce "Officer, to zaku sake shi? Bai yi komai ba"
"Ke, da wiwi muka kama shi da ƙwayoyi, sai kuma ki ce
bai yi komai ba? NDLEA zamu kai shi".
Jauhar ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dan
Allah ku yi haƙuri, ba zai ƙara ba in sha Allah, Master ka basu haƙuri su
ƙyaleka mu tafi" miƙewa yayi tsaye, ya nufi hanyar komawa cikin ceil.
"Officer to, idan na sayo maganin sauro da ashana, zaku
bar shi ya kunna?"
Gaba ɗaya sai ta basu tausayi, ya ce "Sayo"
Ta juya ta fita da sauri, shi kuma ya tsaya ya waiwayo ya bi
bayanta da kallo.
"Viper, wai dan Allah ka bamu labari, wurin wani bokan
ka kai 'yar mutane da iyayenta, suka aura maka 'yar su?"
Shi dai ya ƙarasa ya koma cikin ceil, yayi zamansa, ba a
jima ba, sai gata da maganin sauro, da ashana.
Suka karɓa a nan kan kanta, suka ce ta tafi.
"Dan Allah ku bari na sake ganinsa"
"Ke wuce ki bar nan, da ki ka samu ma aka bari ki
ganshi?"
Ba ta karaya ba ta sske cewa "To ana bashi abinci? Ko
ina kawo masa na dare ma"
"Au uban wa ki ka ajiye da zai bashi abinci a nan? Ware
ki tafi"
Jiki a sanyaye ta ce "To, zan tafi ga wannan dan Allah
officer ko buredi ku bashi" ta ajiye musu ɗari biyar sannan ta ce
"Dan Allah kuma ku yi haƙuri, kar ku kai shi NDLEA, dan girman Allah in
sha Allah zai daina, ba zai ƙara ba ma dan Allah"
"Ki je ki kawo dubu hamsin, sai mu sakar miki shi"
Tayi shiru, har ga Allah ba ta da ita, ba ta da dalilinta
amma ta ce "To zan kawo, amma dan Allah kar ku kai shi, zan kawo muku in
sha Allah"
Ta fito daga wurin, tana tunanin ina zata nufa ta samo dubu
hamsin a sake shi.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Tun da ta hau adaidaita sahu, tunani take yi, yaya za ta yi
ta samu dubu hamsin ta kai, a sako shi. Ta san muddin aka kai shi NDLEA case ɗin
tsayi zai yi, ba zata musa an ganshi da kayan maye ba, tun da yana sha.
Ta koma gida tayi salla, amma abun duniya ya isheta, ta kasa
ko cin abinci, tausayinsa duk ya cika mata zuciya, jikinsa yayi ruɗu-ruɗu da
cizon sauro, gashi almu sun nuna ba abinci ake ba shi ba.
Baba kuwa abun duniya ya dame shi, yadda ya ji kunya a idon
iyayen Alhaji mu'azzam, ace sun kawo kuɗi sun gama magana, amma ya aurar da ita
ga wani, ko gaya musu bai yi ba, ya rasa me yake yi masa daɗi, har sai da
zakiyya ta fahimta ta ce "Baban su Saifu, wai lafiya kuwa? Tun da ka yi
baƙi jiya, gaba ɗaya ka rasa nutsuwar ka"
Ya sauke numfashi ya ce "'yan uwan Alhaji mu'azzam ne,
suka zo suna bayar da haƙuri a kan jin su shiru da aka yi. Wai za ayi mata visa
ayi auren a tura ta can"
Waro ido tayi ta ce "Sai kuma ka ce musu me?".
"Na aurar da ita" yayi maganar a sanyaye yana sake
jinjina wautar da ya yi.
"Ba a haka fa, sai ka ce musu Allah ne ya ƙaddara a
hakan, amma akwai yayyenta, ko hafsa ba sai a maye gurbinta da ita ba, hafsa ba
ta fi jauhar komai ba ma? Ai bai kamata a bari ya tafi haka ya tsallake gidan
nan ba".
"Zakiyya, kun saka na yi abun da yake damuna, na cuci
'ya ta ba gaira babu dalili, na aurar da ita ga mutumin da ba na kirki ba, na
rasa yadda aka yi, lamarin nan ya faru, kunyar haɗuwa da jauhar ma nake yi, na
kasa komawa gidanta, zuciyata zafi take yi mini"
Zakiyya ta ce "Jauhar fa an gama babinta, sai a
fuskanci 'yan uwanta, bai kamata a bari mutumin nan ya tafi haka ba"
"Zakiyya, dan Allah ki bari na samu nutsuwa, ni ban san
ma meyake damuna ba, dan Allah ki bari na ji da abun da yake damuna"
Ta kwantar da murya ta ce "Babu wani abu fa da yake
damunka, kai ne ka ke neman ɗorawa kanka matsala, amma komai mai sauƙi ne, idan
ya dawo ba sai a lallaɓa shi a bashi Hafsa ba ya aura".
Baba ya ce "Na ji, amma dai yanzu ki ƙyaleni" ya ɗauki
hularsa ya saka ya fita.
A tsakar gida ya tarar da su surayya, aiki duk ya kacame
musu, aiki ba aiki, wanda da jauhar na nan, ita kaɗai take yi suna mimmiƙe
kamar kifi a fridge.
Suna ta yi masa a dawo lafiya, ya dawo da baya ya tsaya, ya
kalle su ya ce "Surayya, kun je gidan ƙanwarku kuwa kun ganota?" Duk
suka yi shiru, suka kasa amsa masa.
"Yakamata ku je ku ga in da aka kaita, ita ma ta ji daɗ".
Mama ta fito daga kitchen ta ce "A'a fa, ka san dai
yadda mijinta yake, ba zuwa gidanta ne ba za ayi ba, kar mutum ya je ya illata
shi". Yayi shiru bai ce komai ba.
Jauhar kuwa kasa nutsuwa tayi, har sallar nafila tayi
mussaman tana fatan Allah ya sa kar a kai Al'amin NDLEA.
Duk yadda ta kai ga tunani, ta rasa mafita, bacci ya
gagareta, a gidanma ya ta ƙare da sauro, ina ga shi da yake can, ta yi ta fatan
Allah ya sa su saya masa buredin nan su bashi, sai kuma ta tuna ba ta bayar da
kuɗin da za a saya masa ruwa ba, gaba ɗaya ta shiga damuwa, haka har garin
Allah ya waye.
Ta ji ƙarar babur ɗin malam lawan alamar ya fita, tana ta
tunanin ko shiga za ta yi gidan, ta yi wa maman halimatu magana, ko akwai
taimakon da za ta iya yi mata.
Tana cikin tunanin, maman halimatu ta shigo, suka gaisa
jauhar ta ce "Yanzu nake tunanin zuwa gidan wurinki".
Maman halimatu ta ce "Yaya kin same shi ɗin?"
"Eh yana can, sun ce na kai dubu hamsin a bayar da
belinsa, amma wallahi bani da ita"
"To yanzu ya za ayi?"
Jauhar ta ce "Wallahi ban sani ba, shi nake ta
tunani"
"To ki kira gidanku mana ki faɗa" ta girgiza kai
ta ce "A'a, daga yin auren sai na fara kai musu complain, a'a gara na rufa
masa asiri na samu ya fito"
"Aikuwa Jauhar sai ki yi tunanin in da zaki samo kuɗi".
Tayi saurin cewa "Dan Allah ko akwai wanda zaki haɗa ni
da shi, ya sai carfet ɗina?"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Eh akwai wata dillaliya,
kusa da titi gidanta yake"
Cikin ɗoki jauhar ta ce "Mu je ki rakani maman
halima".
"Shikenan, amma Jauhar kina me ki ka auri mutumin nan,
gashi daga aurenku kin fara wahala, da kyanki da ƙuruciyarki, kin auri wanda
zai wahalar da ke".
Jauhar ta yi murmushi ta ce "Maman halimatu ku daina
aibata shi dan Allah, ku din ga yi mana addu'a"
"To Allah ya kyauta"
Jauhar ta saka hijjabi, suka tafi gidan dillaliya, sai dai
bata nan, aka kirata a waya, ta ce sai yamma zata dawo, zata biya gidan maman
halimatu, su je gidan Jauhar ɗin.
Wunin ranar jauhar kamar ta yi hauka, saboda dillaliya ba ta
zo ba, sai tunanin halin da yake ciki take yi.
Sai wajen ƙarfe biyar sannan ta zo, ta ga carfet ta ce zata
saya dubu goma.
Maman halimatu ta ce "Haba sahura, wane irin dubu goma,
bai fi sati biyu ba ca carfet ɗin sabonsa dubu kusan sittin ne fa".
"To ku ɗauka ku mayar kasuwar mana, tun da an shimfiɗa
ai ya zama taoho".
Jauhar ta ce "Bakomai na yadda" ba ta da burin da
ya wuce ta ga Al'amin ya fito.
Sahura ta ce 'Saboda kin ban tausayi, na saya dubu sha biyu,
bari na baki kuɗin.
Maman halimatu ta ce "Wallahi sahura shiyasa da yawanku
ba kwa arziki dillali, duk cuwa-cuwar ta ku, a tsiyace ku ke mutuwa"
Sahura ta ce "Oho miki dai"
Ganin ta fito da kuɗi da yawa, ya sanya jauhar shiga kitchen
ɗin ta, ta ɗauko blender da set na tukwanenta masu kyau, ta cewa dillaliya su
ma ta saya.
Maman halimatu ta ce "Jauhar, idan 'yan gidanku suka
gane kin sayar da kayanki fa?"
Sahura ta ce "Wallahi uwar su halimatu ke 'yar baƙin
ciki ce, ke kika saya mata?".
Jauhar kamar ta yi kuka ta ce "To ya zan yi maman
halimatu, bana son zamansa a wurin nan, sauro ma kawai ya ishe shi"
Sahura ta ce "Allah sarki yarinya, Allah ya mayar da
alkhairi, idan an tashi sayar da wasu ma ki kira ni"
Da ƙyar ta bawa Jauhar dubu ashirin da huɗu gaba ɗaya. Wanda
a ƙalla sun kai kayan dubu ɗari da wani abu.
Ƙoƙarin nemo wani abun take, maman halimatu ta hanata, ta ce
ta bari gobe ta je station ɗin, ta basu haƙuri ta ce musu abun da take da shi
kenan.
Jauhar ta ce "Ki na ganin za su karɓa kuwa?"
"Za su karɓa mana, ai kin yi ƙoƙari" kamar ta
janyo wayewar gari, ta din ga addu'a Allah ya sa su karɓa su sake shi.
Da wuri ta gama komai, wurin ƙarfe goma da rabi ta fita, shi
ma maman halimatu ce ta hanata fita da wuri, ta ce mata ba da wuri suke zuwa
ba.
Suna ganin Jauhar suka ce "Madam ya aka yi ne? Kin sake
dawowa ganinsa ne?"
Ta ciro kuɗin ta ce "Gashi dan Allah yallaɓai ku sake
shi, sukaɗai na samo dan Allah ku yi haƙuri"
Ya zuba mata ido ya ce "Shekarar ki nawa ne?"
Ta ce "Na kusa shiga sha bakwai, dan Allah ku yi
haƙuri"
"To ai ba zamu iya baki belinsa ba, kin ga mace ce ke,
kuma yarinya, Allah ya sa ya daina abun da yake ko dan saboda ke, karɓi kuɗinki,
ba zamu sake shi a kan wannan ɗan kuɗin ba, kotu ma zamu kai shi"
Kawai ta saka kuka, "Dan Allah ku yi haƙuri, ba zai
ƙara ba dan Allah kar ku saka a kai shi prison"
Ɗaya daga 'yan sandan ya ce mata "Yi haƙuri ki daina
kuka, da wasa yake yi miki, an zo belinsa ma, ke ki ke tayar da hankalinki, ko
mun kama shi zamu sake shi"
Kasa daina kukan tayi, hannunta riƙe da kuɗin, wani ɗan
sanda ne ya fito, da alama babba ne, bayansa kuma walid ne da Al'amin da wani
mutum.
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, ta zubawa fuskarsa ido, da
take a ɗaure babu walwala.
Walid ya ce "Kai Viper, wannan ce yarinyar da na tarar
a gidanka, tayi mini rashin mutunci"
"Wannan fa me aka yi mata take kuka?"
"Sir, matar Viper ce" ya kalleta ya ce
"Hajiya me aka yi miki ki ke kuka?".
"Ce mini suka yi na kawo dubu hamsin za a sake shi, na
kawo kuma suka ce mini wai kotu za su kai shi" ta ƙarasa maganar tana sake
fashewa da kuka cike da yarinta.
Ya kalli 'yan sandan ya ce "Waye ya ce ta kawo dubu
hamsin"
"Sorry sir, dan ta daina zuwa aka gaya mata haka"
Nan ya hau yi musu faɗa, suka din ga bayar da haƙuri,
Al'amin kamar bai santa ba, yayi gaba. Da sauri ta bi bayansa, tana ta yi masa
magana yayi shiru.
Walid ya ce "Haba mai dogon zamani, ka tsaya ka
saurareta mana"
A fusace ya waiwayo ya hau ta da masifa "Ban ce miki
kar ki sake zuwa wurin nan ba? Kin san suwaye ake kawowa wurin nan? Mutuncinki
ne a ganki a nan?" Sai da ta ja da baya a tsorace ta rufe fuskarta, saboda
razana da masifar da yake yi mata.
"Wai Aminu meyasa ka ke yin haka? Da uban waye ya damu
da kai, yake ta taka? Macen kenan haka zuciyarsu take, ko dan matar gidanku ba
ta da kirki kowa ma haka yake?" Tsaki ya yi yayi gaba.
Walid ya ce "Yi haƙuri mu je, rabu da shi ya ƙarata,
kar ki sake tayar da hankalinki saboda shi" suka tari a daidaita sahu suka
tafi gida.
Da suka je gida, ta shiga gidan ta bar shi da Walid.
"Aminu, dan girman Allah ka rage jaraba, kalli yadda
duk ta rikice saboda kai, kar ka yi wasa da damar da ka samu, ka saka ta
tsaneka dan Allah"
Ya tsaya ya ƙarewa ƙofar gidan malam lawan kallo, yayi ƙwafa
ya shiga gidan, ba tare da ya tanka Walid ba.
Jiki na rawa ba tare da ta yi fushi ba, ta kawo masa tea da
buredi.
Ya gama baccinsa ya tashi, ya yi wanka, ya gama ya ga ta
kafa masa ƙusar rataye soso a banɗakin, har zai rataye yayi tsaki ya yar da
soson a kan sabulun ya fito.
Ya canza kayansa ya fito falo, Satar kallonsa take yi, kamar
ya ƙara kyau, kwana biyun da ya yi a tsare ba ya shan komai, kamar ya yi kyau
sosai. Sai murna take yi ya dawo gida.
"Ke!" Ta ɗago ta kalleshi.
"Meye sunanki ne?"
"Jauhar"
Ya kalleta ya ce "Me? Angela?"
Murmushi ta yi ta ce "Angela kamar wata mage,
sunana Jauhar"
Guntun tsaki ya yi ya ce "A saka muku normal suna, sai
dai a saka ƙaƙale-ƙaƙale da iyayi, ni ba zan iya ba"
"To ka kirani da fatimata fatima zahra" wani irin
zirrrr ya ji a jikinsa, fatima zahra, sunan mace mai girma da daraja a idonsa,
Ummansa abar ƙaunarsa, duk da ba ta duniyar, amma idan ya ji sunan har wata
tsuma yake yi.
Ya maze ya ƙarewa falon kallo, ya fita tsakar har zai wuce
ya kalli kitchen ɗin ta sannna ya ce "Zo nan"
Ta fito ta ce "Gani"
"Wa ki ka sayar wa carfet ɗinki da kwanukanki?"
Gabanta ya yi wata irin mummunar faɗuwa, yaya aka yi ya gane
ko ya sani? Sai ka ce aljani?
Ya ƙare mata kallo ya ce "Ina jinki, ya aka yi ki ka
samu wannan kuɗin da ki ka kai? Ina kuma abubuwam da na tambayeki? Ki ka yi
mini ƙarya kuma jikinki ya gaya miki"
Kamar munafuka, haka ta zayyane masa komai.
Bai ce mata komai ba, ya fita.
Sahura na tsakar gida, tana hira ita da wasu coustomominta,
kawai ta ga wasu irin zaratan matasa su uku, a tsakiyar tsakar gida da manyan
gorori kamar za su farauta.
Ta tashi ta ce "Lafiya malam? Me ku ka zo yi mini a
gida. Wannan ai.... Haɗiye maganar tayi, da ya sako ƙafarsa cikin isa tsakar
gidan.
Yana shigowa idonsa ya sauka a kan carfet ɗin, a shimfiɗe a
falonta.
Ya ce "Liti, ku naɗo mini carfet ɗin nan"
Ta waro ido ta ce "Malam lafiya?" Walid ya zaro
wuƙa ya ce "Ki ka kuma magana, sai kin ɗaware daga sararin nan yanzun
nan" daga ita har sauran matan, suka hau tsuma.
Kamar abun banza, suka din ga yi mata cilli da kujeru, suka
naɗo carfet.
Viper ya ce "Dubu sha biyu ki ka saya ko?" Ta
jinjina masa kai.
Ya ce "Ɗaukko mini sauran kayan da ki ka karɓa a
wurinta" jiki na tsuma ta shiga ta kwaso su.
Ta ajiye masa a tsakar gidan, ya ce "Ɓarauniyar zaune,
daga yanzu ki san abun da zaki din ga saya, ban da a nutse na zo miki, sai na
saka an zana miki awarwaro a hannu, yadda gobe ba zaki sake zalunci ba. Liti ba
ta kuɗinta".
Liti ya zaro kuɗi zai bata, Al'amin ya ce "Wait, ta
riga ta shimfiɗa a ɗakinta, ka cire dubu uku a kai, sannan ka sake cire dubu
biyu zan cika ku wanke mini carfet ɗin ku kai mini gida.
Haka kuwa aka yi, suka cilla mata kuɗi, suka kwashe kaya
suka tafi.
Jauhar ta na yi wa wasu stone work, dan kuwa matar ta fara
kawo mata kayan tana yi, hakan yana ɗebe mata kewa.
Ba ta yi aune ba, ta ganshi a tsakiyar falo, hannunsa da
kaya, ya dungurar mata da su a tsakiyar wurin ya ce "Daga yau, ko cokali
ki ka kuma sayarwa, saboda ni sai na ɓata miki rai, fiye da yadda ki ke
tunani"
Baki buɗe ta ce "Master, karɓowa ka yi, kuɗinta suna
wurina fa, Allah zai kaman..."
"Na ba ta kuɗinta, ko tsintsiya ki ka sake sayarwa, zan
gane kuma ranki sai ya ɓaci".
A hankali ta ce "Na shiga uku".
***
Matasa ne a ƙalla su biyar, dukkanin su, babu wanda ya gaza
ko ya wuce shekaru ashirin da biyu, suna sanye da tufafi masu nuna datti,
gashin kansu da yanayin fuskarsu kuwa, babu tambaya sun bayyanar da tsantsar
rashin ji a tattare da su, sai bushe-bushe suke yi, suna shewa.
Wani matashin ne ya diro ta saman katanga, gaba ɗaya suka
nutsu, suna yi masa sannu da zuwa.
"Kai gayu akwai matsala wallahi" gaba ɗaya suka
tattara masa hankalinsu suna sauraren sa.
Ya ce "Kaii, wai ashe mai zamani ne ya tare a unguwar
nan kusan sati biyu bamu sani ba?"
Ɗaya daga cikin su ya miƙe ya ce "Ƙarya ne wallahi, me
yake yi mana a unguwa".
"Nustu, ni ma ban sani ba sai ɗazu, mai unguwa na ji
yana maganar, sai za su je police station, ko a sasanta ayi zaman lafiya da
shi, ko ya bar unguwar nan".
Ɗayan ya yada sigarin hannunsa ya tashi ya ce "Guduma
gaskiya kar dagus ɗin ka ya janyo mana matsala, ya san waye mai dogon zamani
kuwa?".
"Guys mafita ɗaya ce wallahi, kun san ba a sarki biyu a
zamani ɗaya ko?"
"Me ka ke nufi?"
Guduma ya ce "Dole ɗaya ya bi ɗaya"
"To waye zai bi wani?"
"Kwanciyar hankalinmu da nustuwarmu, shi ne mu yi
mubayi'a, samunsa ma a unguwar nan wani security ne, zai sa a din ga jin
tsoranmu"
Wani matashi ya ce "Ƙarya ne wallahi, babu wanda ya isa
ya zo unguwarmu mu yi masa mubayi'a ba a isa ba".
"Kai Kwano, bari na yi maka wani lissafi, duk sarkin da
ya zo garinka ba da ziyara ba, ya shafe awanni arba'in da takwas, a irin
harƙallarmu, to ɗayan biyu, ko dai ɗaya ya bi ɗaya, ko kuma a yaƙi juna, a kama
sarki ɗaya da mutanensa a matsayin ganimar yaƙi, mu rayu a matsayin bayinsa,
harƙalar da Mai zamani yake yi, ta ci uban tamu, ba sa'anmu bane ba, mu yi abun
da ya dace, idan kuma mu ka bari rigima ta ɓalle, wallahi a unguwar tamu, zamu
rayu kamar bayi ne amma ku yi tunani".
Can Al'amin kuwa yana zaune a station, ga mai unguwar da
yake da sauran mutanen unguwa.
Yana zaune yana kallonsu, suna ta ɓaɓatun gaskiya ya tashi
ya bar musu unguwa, saboda bad record ɗin da suka samu, a kansa daga in da ya
baro, kuma nan ma ya zo yana yi musu shaye-shaye kar ya ɓata musu yaran unguwa.
Suka yi suka gama, yayi shiru kamar mai zancen zuci, suka yi
suka gama, D.P.O ya ce "Malam Aminu, ka ji abun da mutanen unguwar da ka
tare suka ce, me za ka ce?" Sai da ya ja wasu seconds, sannan ya ɗaga kai,
ya kalle su da jajayen idanunsa masu matuƙar kwarjini, duk suka yi shiru, suna
sauraren sa, ya ce "Haryanzu ban ji an ce ga abun da na yi ba ai. Ba zan
ce komai yanzu ba, gobe in Allah ya kaimu, mu haɗu a nan ƙarfe huɗu na yamma,
zan faɗi abun da na yanke".
D.P.O ya ce "Ina fatan ba wata ɓarnar zaka yi ba?"
"Ba na sara sai an zo ramina" daga haka bai kuma
cewa komai ba, ya tashi ya fice, ba tare da ya jira iznin hakan ba.
D.P.O ya ce "Abun da nake so da ku shi ne, ku bi yaron
nan a sannu a samu maslaha, kar ku yi wani abu da zai tunzura shi, ya fara yi
muku fitina a unguwa, ku bari mu bi a hankali mu sasanta, ɗan ƙasa ne yana da
damar zama a in da yake so, ku bi a hankali ayi musu sulhu".
Shi kuwa yana fita, ya kira wayar liti, bugu biyu ya ɗaga.
"Liti, nan da mintuna arba'in zuwa awa ɗaya, ina son ka tattara mini, duk
wasu yara marasa ji a arear unguwar nan da nake da kewayenta, duk wanda ya yi
gardama, ayi masa ɗaurin igiya da swizaland gaba da baya, a layin gidana nake
son su taru".
Liti ya amsa da "An gama shugaba"
Sahura kuwa, sai da ta je har gidan maman halimatu ta ƙare
mata cin mutunci, a kan yadda Al'amin ya je har gida, ya ƙare mata tanadi, a
kan ta sai kayan matarsa, maman halimatu ta din ga ba ta haƙuri, ta ce su shiga
gidansa su yi magana da jauhar ɗin, amma ta ce ai ba mahaukaciya ba ce ita, da
zata shigar masa gida ya ritsata ya kashe.
Jauhar tana ta aikin stone, ta ji ana wata irin busa a
unguwar, kamar da ƙaho ake yin busar, irin bushe-bushen da aka din ga yi, ranar
ɗaurin aurenta, dan haka gabanta ya faɗi ta shiga cikin tsoro.
Sannu a hankali, hayaniya ta fara cika layin nasu, da
surutan matasa, ɗaki ta gudu ta rufe ƙofar falo, dan tunani ta fara yi, ko
yaran madaki ne, gashi ba waya ce da ita ba, balle ta kira Al'amin
Kafin ya ƙarasa layin gidan, liti ya kira shi a waya, ya
sanar masa sun fara taruwa matasan, dan haka bai bi ta cikin ba ya bi ta baya.
Jifff! Ta ji dirar abu a tsakar gida, ta katanga ya diro
gidan, ya fara ƙoƙarin buɗe ƙofar falon, amma a rufe ya jijjiga ya jijjiga amma
ya ji a rufe. Ya shiga bugun ƙofar kamar yaƙi, ƙulewa tayi a ɗaki, ta hau
addu'a, tare da tunanin ta ta ta ƙare, yaran madaki sun zo neman Al'amin, ko
sun zo sassarata.
"Ke malama ki zo ki buɗe mini ƙofa" sai da ta ji
muryarsa, sannan ta fito ta buɗe, ta kalle shi, ta leƙa tsakar gida ta ce
"Ai ban san kai ba ne, biyoka aka yi ne?" Wani irin kallo ya yi mata,
ya ce "Matsa ki bani wuri" ta matsa ta bi bayansa tana surutu
"Master ka daina dirowa ta katanga dan Allah, gaba ɗaya na tsorata
wallahi, na zata madaki ne, suka zo nemanka na ji sai busa ake yi ga warin
kayan shaye-shaye...... Haɗiye maganar tayi, da ya waiwayo yana yi mata kallon
warning.
Ta ce "Yi haƙuri, ka ga abokanka sun dawo da carfet ɗin,
wai wanke shi suka yi, amma dai yakamata na je na bawa dillaliyar nan haƙuri,
ai ka ga an shiga hakkinta, har gida ta zo tayi wa maman halimatu masifar abun
da ka yi" ɗakinsa ya shiga, ya kulle ƙofar ya saka sakata ya bar ta a
bakin ƙofa.
Sai abun ya bata dariya, kafin awa ɗaya matasan nan sun kusa
cika layin nan, sai hayaniya suke yi.
Malam lawan kuwa, a waya matarsa ta kira shi, ta ce kar ya
kuskura ya dawo yanzu, 'yan daba sun cika layin nan.
Jauhar na ɗakinta, tana aikinta, ta ji yana buɗe gate, a
razane ta fito saboda yanayin bushe-bushen da ake yi, ya tabattar mata da akwai
matsala.
Yana fita wurin yayi tsit, kamar ba su ne suke hayaniya ba
da.
"Sai da kai sarki, ƙaramin dodo magajin babban, ko ma
in ce ka ɗara shi. Mu na yi maka maraba da zuwa wannan unguwar, mun fito ƙwanmu
da kwarkwata domin yi maka mubayi'a". Cewar guduma yana geɓare baki,
yanayin yadda yake maganar kawai a buge yake.
Viper ya goya hannunsa a bayansa, ya ce "Manyanku sun
kai ƙarata a kan yarjejeniyar zaman lafiya, sai dai ni da ku zan yi wannan
yarjejeniya.
Abu goma a cire bakwai a tara da ɗaya zan gaya muku, a bi
iyaye, ayi caji kaɗan saboda lafiyar jiki da ƙwaƙwalwa, a kiyayi taɓa kayan
wani. Babu zubar jini a tsakanin ku, ko duk wani wanda yake unguwar nan, abu na
ƙarshe mafi muhimmanci da fari salin alin na so zama a unguwar nan, wataƙila na
ɗan lokaci na baku wuri, amma tun da abun ya zo da haka, sarki biyu ba zai yi
sarauta a zamani ɗaya ba. Ko dai mutum ya yi mubayi'a ko ya bar unguwar nan.
Kar kuma a kuskura a matsi ramina idan ba haka ba, zan yi ɓarna. Mu haɗu da
shugabannin dabar Unguwar nan da kewayenta gobe a station ɗin unguwar nan,
domin yarjejeniyar zaman lafiya. Kuna iya samfewa"
Su ka din ga yi masa kirari, yana jin kansa yana sake
fashewa.
Bayan sun watse, maman halimatu ta shigo, tana ba ta labarin
abun da sahura ta zo ta yi mata.
Jauhar ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri maman halimatu,
dan Allah ki bata haƙuri, ba yadda zan yi, na so mayar mata ma da kayan, ya ce
idan na sake sayar da wani abu, zai ɓata mini rai. Wallahi yana ankare da
komai, ko cokali na sayar zai gane, ni har tsoro yake bani, bari na baki dubu
goma a kuɗin, ki kai mata ta ƙara ki bata haƙuri dan Allah"
Maman halimatu ta ce "To shikenan, Allah ya
kyauta" ta bata dubu goma ta kaiwa dillaliya, ita kuma ta bata kyautar
dubu biyu, sauran kuɗin kuma ta ɗan yi musu cefane dan kuwa shi babu ruwansa.
Washegari tun ƙarfe biyu, su mai unguwa suka koma police
station, suna jaddada dole a kori Al'amin, dan jiya kafin su je gida ya rigasu
zuwa, ya tara musu dandazon 'yan daba a unguwa.
Al'amin bai je ba, sai ƙarfe huɗu tare da rakiyar su walid,
da kuma matasan yara 'yan shaye-shaye da sun kai ashirin da wani abu.
D.P.O ya ce "Lafiya, waɗanan fa?"
Al'amin ya kalli mai unguwa, ya nuna masa guduma ya ce
"Ka san wannan? Ko ba ka bani amsa ba ɗanka ne, meyasa ba ka kore shi daga
unguwarka ba? Ko dan shi ɗanka ne?. A wannan ba wannan matasan wakilai ne
da suke jagorantar wasu yaran a ƙarƙashin su, wanda duk a cikin unguwarka suke,
kana nufin a sati biyu da zuwana duk ni na lalata su? Har na tare a unguwar
nan, ba su san waye ni ba, sai jiya da na saka a tara mini su.
Dama can kuna da lallatun yara, harƙallata nake, ba na
lalata ɗan kowa, duk ɗan wanda ya lalace, dama lalataccen ne. Ina sake
maimaitawa ba na harbi sai an matsi ramina ko in da nake.
Ga mafita zan bayar, wadda ba zan ƙara ko rage wani abu daga
abun da zan faɗa ba.
Mafita biyar ce ba uku, ko dai a haɗa a kore ni, da ni da
yaran nan, ko kuma ku yi wa gidana kuɗi ninki uku, yadda zai isheni na sai
wanda ya fishi, na bar muku unguwa, idan ba haka ba....... Ba na ƙarasa magana
sai dai na aikata.
Duk sai suka yi ɗif D.P.O ya ce "Mai unguwa mai ku ka
yanke?"
Shiru suka yi ba su ce komai ba, D.P.O ya ce "Tashi ka
ja zugarka ka tafi, babu wani abu in sha Allah".
Ya miƙe ya ce "Galibi yaran nan secondary school drop
out ne, wasunsu idan son zuciya ne ya kai su wannan halin, wasun su laifinku
ne, ko dai ku nutsu ku gyara rayuwar matasan yaran nan, ko kuma su cigaba da
lalacewa kuna rusa al'ummarku da hannunku" yana gama maganar suka fice da
shi da su.
D.P.O. ya ce "Yaron nan fa ya san abun da yake yi, jiya
kuna barin wurin nan, daga can unguwar su, Aka kira ni aka ce a gargaɗe ku,
babu ruwanku da shi, yaron 'yan siyasa ne, dan Allah ku lallaɓa ku zauna lafiya
da shi.
Bayan sun bar station ɗin, wani irin ɓacin rai ya din ga
cizon zuciyarsa, a duk lokacin da aka samu matasa ire-iren sa, al'umma ba su da
wani burin da ya wuce, yin watsi da shi, da nesanta kansu da ire-iren su, bayan
su ne ƙashin bayar lalacewar ta su.
Yau abun na sa ya fi na kullum, domin kuwa a buge ya dawowa
jauhar, wajen ƙarfe sha ɗaya na dare, ya wuce ɗakinsa, ba ta kula shi ba ta
koma gefe ta zuba masa ido.
Washegari da safe shiru bai fito ba, ta leƙa ɗakinsa, ta
tarar da shi a kwance yana bacci, gefensa ga kwalin ashana da na taba, ga
kwalabe.
Shiru ta yi ta sunkuyar da kanta ƙasa, a hankali ta fara
magana "Sun san da haka suka aura mini kai, Allah na roƙi ka bani mafita
ka zaɓa mini shi, Allah ka kawo mini mafita, Allah ka shirya mini shi, Allah
shiriya taka ce, Ni da shi duk bayinka ne, Allah bai gagari ikonka ba, Allah ka
shirya min mijina. Allah ka sa ya daina abun da yake yi, Allah kar ka sa ya
mutu yana saɓa maka" ta yi maganar tana kuka.
A hankali ya yi juyi, satchets ɗin ƙwayoyi, suka zubo daga
aljihun gaban rigarsa, ta saka hannu ta kwashe su, da kwalaben, ta hau caje ɗakinsa,
duk wani nau'i na abun da ba ta yarda da shi ba, sai da kwashe daga ɗakin.
A hankali ya motsa, ya buɗe idonsa, ita kuma ta fice daga ɗakin.
Da ƙyar ya iya tashi, dama bayan sallar asuba, ya sake yin
shaye-shayen.
A yunwace, ba tare da ko wanke baki yayi ba, ya hau cin
abinci, saboda kayan shaye-shayen sun rarake masa ciki, ji yaya ko tsayuwa ba
zai iya yi a kan ƙafafuwansa ba, sai da ya gama ci ya dawo dai-dai.
Ya shiga banɗaki, ya wanke bakinsa ya fito falo, ko ɗaga
jauhar ba ta yi ba, balle ta kalleshi.
Ya je gabanta ya miƙa mata hannu.
Ta ɗago ta kalleshi. "Bani abun da ki ka caje mini ɗaki
ki ka ɗauka" gabanta ne ya faɗi, mutumin da yake bacci ya aka yi ya san ta
ɗauka?.
"Bani mana"
"Na zuba a shara an zubar!"
(Yau juma'a mu yawaita salati, ga shugaba Sallallahu alaihi
Wasallam)
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Duk da cikin matsanancin tsoro da tashin hankali ta bashi
amsar, amma ta tattaro jarumtarta ta dake, ta ƙi kallonsa.
"Ai ɗago kai zaki yi ki kalle ni, ki bani amsar da ki
ka faɗa yanzu"
Ta yi shiru, tana jiran yayi mata duk abun da zai yi mata.
Ya ce "Dama ba ni na kawo ki gidan nan ba, kuma ba ni
na ce a kawo ki ba, idan kin gaji ki tafi dama kin isheni, kuma idan ki ka kuma
zuwa kaina ki ka tsaya ki na kuka, sai na ɓarar da ke".
Gabanta ya faɗi, a buge ta tarar da shi yana bacci, ya aka
yi ya san duk abun da ya faru, sai dai kalmarsa ta ƙarshe da ya ce a kawota ba,
ta yi mata ciwo.
Ta zata zai yi mata tijara, da ta ce ta zubar, sai kuma ta
ga ya tashi ya nufi hanyar fita, kawai ta fara kukan da ba ta san na menene ba
ma.
Waiwayowa ya yi yana kallon ikon Allah, da ta samu bai
casata ba, da ta ɗebe masa kaya,ta ce ta watsar kuma ya san ƙarya take yi ba ta
zubar ba, shi ne saboda samun wuri har da ɓare baki tana kuka.
Sosai yarintarta ta fito, yadda ta tura baki tana kuka,
tamkar irin 'ya'yan madarar nan shagwaɓaɓɓu.
Kawai ya girgiza kai ya fice, kafin ta fusata shi.
Rahila da Zakiyya kuwa sai shewa suke yi, tare da farincikin
yadda shawarar da suka yanke ta yi amfani.
Zakiyya ta ce "Ni fa na zata yadda yake ɗin nan, ana
kaita ya korota tun da ba son auren yake yi ba, amma dama na san ko zai daketa
ya cinye abu ne mai wahala ta faɗa ko tayi yaji, juriya ce da ita kamar dutse
shegiya".
Rahila ta ce "Shi ɗin me? A duniya akwai namijin da zai
ce ba ya son mace ne, ke ban da abun makirci wannan yarinyar son kowa ƙin wanda
ya rasa, wa zai ce ba ya so, dan ma ƙarama ce, gashi ai sati biyu kenan sun yi
luf daga shi har ita".
"Wallahi na zata ba zai saurareta ba, ƙila ma ya
korota, a yadda ki ke bani labarin yadda ya zama, da kuma rashin jin da yake
yi".
"Ba fa mahaukaci ba ne, idan ta iya zama da yaron nan,
ba lallai ki ji kansu, ai duk wannan bala'in da nake yi da tashin hankali a
kansa, wasu lokutan shi da 'yar uwassa yana yi mata abu, ke har magana shahida
take gaya mini a kansa"
Cikin mamaki zakiyya ta ce "Kai haba dai?"
"Wallafa Allah, ba suna school aka yi auren ba, sai da
na kusa dukan yarinyar nan, ƙiri-ƙiri wasu lokutan take nuna in daina takurawa ɗan
uwanta, aikuwa ubanta nake ci".
"Gaskiya kar ki zauna a kanta, ita ana neman mafita
tana shirme? Ni kam yanzu menene abun yi ne? Ƴan uwan Alhajin nan fa sun zo,
wai ayi aure ayi visa ta bi shi china"
Rahila ta ce "Aikuwa sai dai a lahira idan ana
zuwa".
"Aikuwa, wai yanzu ya fasa dawowa nan da watan ɗayan
ba, ina nan dai ina ta lallaɓa uban, a kan ya haɗa shi da hafsa".
"Ai ba iya lallaɓa shi ba, malamai zamu cigaba da yi,
in sha Allah sai abub nan ya tabatta, ita waccan ai an gama da babinta".
Zakiyya ta ce "Haka ne kam, to Ubangiji Allah ya
amince, ni dai ko nawa ne zan kashe, idan ta aure shi na san zan mayar da kuɗina".
"Kar ki damu ai ba zama, za ayi duk mai yiwuwa, hafsa
zata auri mutumin nan".
***
"Ku yanzu a ganinku ya dace mu na ji mu na gani, baƙo
ya zo unguwarmu ya saka mu yi masa mubayi'a? Baƙo ne fa, mu kuma a nan aka
haife mu muka girma, muka kafa sabgar nan, kuma ace sai dai mu bi shi, ba dai
ya bi mu ba?"
"Wallahi nima dai haka na gani, abun yayi mini ciwo,
guduma ya fi kowa bani haushi shege, ai wallahi sai dai a rabu biyu, ayi ta
zubar da jini, har sai ya yarda ya bi mu, ba wani shege da zai shigo arearmu ya
buɗe mana ido, mu zagaya mu ji ta bakin sauran, mu ji su waye suka bi, kuma
suwaye za su yi tawaye".
Ɗaya matashin, ya hurar da hayaƙin wiwi ya ce "Mu
tabattar da suwaye a tare da mu tukuna, zamu yi masa sara na warning, idan ma
ta kama, mu kawar da shi da ga sararin nan, ba wani ɗa da zamu yi wa biyayya,
tun da muka yi wa iyayenmu ma tawaye".
Suka cigaba da tattaunawa a kan yadda za su ɓullowa lamarin,
su yi maganin Al'amin.
*****
Kamar masu kasa gyaɗa, haka suka kewaye farantin wiwi, suna
naɗawa a takarda.
Suka mayar da wata ƙwaya garri, suka haɗata a cikin wiwin,
ita ma suka ɗaura ta daban.
Matasa ne suka din ga shigowa da ɗai ɗai, suna karɓa, suna
zube balance, suna karɓar kaya.
Liti ya shigo cikin ɗakin da Al'amin yake, da robar abinci,
ya zauna ya ce "Taso ga abinci"
Ya tashi zaune ya kalli miyar kan abincin, sai ya ji
ƙyanƙyamin abincin, miyar sam ba ta ji mai ba, ga ta ba ta soyu ba, ba irin
wadda waccan taɓararriyar yarinyar take bashi ba.
Guntun tsaki ya ja, Walid ya ce "Lafiya?".
"Na ƙoshi"
"Meyasa?"
Ya girgiza kai ya ce "Bakomai".
"Ka ce mini kawai, abincin amarya zaka je ka ci, wai mu
ko sau ɗaya ba zaka kawo mana abincin na ta mu ci ba? Sai dai ka yi ta ci kai
kaɗai?".
Kai tsaye ya ce "Ba zan kawo ba"
"To ka ƙarata, ku ci ku kaɗai, dama ni naga kamar
haushina ma take ji, ban san me nayi mata ba".
Ya tashi yana fatan Allah ya sa ya je ya tarar ta yi abinci.
Sai kuma ya tuna kukan da tayi kan ya fito, ƙila ma ba ta yi girkin ba.
Sai dai kafin ya ƙarasa gidan, aka tsuge da ruwan sama, dan
haka ruwa yayi masa duka, yayi ta sauri ya ƙarasa gida, ya san ƙarshenta ruwa
yau ma ya shigar mata falo.
Sai dai yau aka yi sa'a, ruwan bai shiga da yawa ba, sai dai
tsakar gidan ya cika da ruwa.
Tana ɗakinta tana salla, ya fara cire kayan da suka jiƙe, ta
shigo da sallama, sai dai cikin matsanancin hanzari, tayi wani irin burki, ta
juya.
Shi mamakin ta yake yi, sam ba ta da zuciya ba ta fushi.
Ba tare da ta waiwayo ba ta ce "Ina da ruwan zafi a
flask, na kawo maka ka yi wanka, sai ka ci abinci kar ka yi mura saboda ruwan
da ya dake ka?".
"Kawo" sumi-sumi kamar mara gaskiya.
Ihunta ya jiyo a tsakar gida, bai san ya aka yi ba, sai
ganinsa yayi a tsakar gida, cikin hanzari yana zaton wani abun ne ya sameta,
tayi jifa da flask ɗin a gefe, Allah ya sa na silver ne tana ihu, ta maƙale a
jikin bango.
"Ke menene? Meyafaru?"
"Kwaɗo ne, zai riƙe mini ƙafa"
Ji yayi kamar ya ƙarasa, ya kwaɗeta, wai kwaɗo take yi wa
wannan ihun.
"Zaki rufe mini baki ki zo ki wuce, ko sai na zo na
tumurmusa ki?"
Jauhar ta ce "Tsoro nake ji wallahi" tayi maganar
tana ɗagowa, idanunta har sun yi ja.
Sai dai mayar da kanta ƙasa tayi, da sauri, tana tsuma
saboda babu riga a jikinsa, wani irin gashi ne a jikinsa, tun daga ƙirjinsa har
saman cibiyarsa.
"Ke ba na son gulma, miƙo mini flsk ɗin, idan ya so ki
dauwwama a wurin"
Cikin shagwaɓa ta ce "Wallahi da kwaɗo a cikin ruwan
nan, tsoronsa nake ji" tayi maganar idanunta na bayyanar da tsantsar tsoro
da tashin hankali.
Cikin ruwan ya biyo, ya zo ya ɗauki flask ɗin, zai bar
kitchen ɗin ya bar ta, ta saka hannu ta riƙe masa wando, tana ihu.
Sai yanzu ya leƙa ya ga kwaɗon ne da gaske, amma girmansa ba
wani ƙato bane take wannan ihun, shi bai taɓa jin wai ana tsoron kwaɗo ba, sai
yau.
A ransa ya ce 'Laifin iyayeki ne da suka zaɓa miki wannan
rayuwar'
Kwaɗo ya tsalla yayi waje, ita kuma jikinta sai rawa yake
yi, cike da tsoro.
"To ai sai ki cikani, tun da ya tafi ko?"
Cikin tsananin jin kunya, ta sake shi, ta koma gefe.
"A nan wurin zaki dauwwama kenan?"
Ta ce "A'a idan ruwan ya bushe, na wuce, ka duba ɗakina
akwai man zafi a kan mudubi, idan ka yi wankan ka ɗan shafa kar ka yi mura,
abincinka yana ɗakinka" kallonta yake yi, yana son gane nature ta ce a
haka, ko kuma iya shege ne, amma yadda take ƙifta ido a tsorace ya tabattar
masa da gaske take.
Ba ta yi tsammani ba, ya saka hannu ɗaya ya ɗago ƙugunta,
hannunsa ɗaya kuma da flask taku kaɗan yayi, ya direta a tsakiyar falo.
Kallonsa take yi da mamaki, shi kuma ya nufi ɗakinsa.
Har ɗan tsalle ta yi, dan ta tabattar ta na da nauyi ne, ko
ba ta da shi, da ya ɗauke ta kamar wata 'yar teddy.
Ta fi mintuna sha biyar tana cigaba da mamakin yadda ya ɗagata
kamar a bar banza.
Tuwon shinkafa ta yi da miyar taushe, kamar ya cire kunne
dan daɗi, ga katifarsa ta saka sabon bedsheet, ɗakin yana ta ƙamshi, amma hakan
bai hana shi goge mata hannu a jiki ba, ya gama ya miƙe yana bacci, kayan na sa
ma sai ƙamshi suke yi.
Leƙawa ta yi ɗakin nasa, ya mimmiƙe a kan katifa, bai saka
rigar ba yana bacci ta lallaɓa ta shiga da sanɗa zata kwashe kwanukan.
Yanayin garin da sanyi saboda ruwan da aka yi, amma ya
takure yana bacci.
Ta fitar da kwanukan, ta ɗaukko bargo daga ɗakinta, ta zo
zata rufe shi, ɗan ƙura masa ido ta yi. Al'amin ba shi da wata makusa, da yake
baccin nan ma he looks very innocent and calm.
Kasa rufe shi ta yi, ta tafi tunanin ya aka yi ya fara
shaye-shaye, ya aka yi su mama suka samo shi ma, suka aura mata? A ina yake ina
ne gidansu? Duk take tambayar kanta.
Tashi ya yi zaune kamar aljani ya ce "Meye ne kin zo
kin sakani a gaba kina kallona"
Zabura ta yi ta ce "Yi haƙuri, na zata bacci ka ke yi,
ba kallonka nake yi ba, na ga kamar kana jin sanyi ne, bargo na kawo maka"
tayi maganar tana tsuma.
Ya miƙa mata hannu, ta bashi bargon, ya ware shi ya lulluɓa,
ta fita tana mamakin al'amin idan yayi wani abun mamaki yake bata, har da
ajiyar zuciya ta ji yana yi alamun baccinsa yayi nisa, amma kawai ta ganshi a
zaune.
***
"Allah ya taimaki maigida"
"An gaisheka, ya ake ciki?"
"Komai normal, ba wani abu"
"Yaya za ayi? An kama Ja'afar da kaya, hukumar nan sun
ƙi sakinsa, ba zan matsa ba, amma ina buƙatar a musanya shi da wani"
"Oga ba zan iya sakinsa kai tsaye ba, amma dole za'a
samu wani a kama shi da kayan, sai a saki jafar a kama shi, ka san wannan karon
shugaban namu, yana da sanya ido sosai"
"Shikenan, ayi abun da yakamata kawai"
"Ok sir".
Cikin ikon Allah, matar nan tela, tana biyan jauhar, duk da
ba wani kuɗin kirki take bata ba, amma tana jin daɗi sosai da sosai, ta sayi
katin tara kuɗi, ɗan abun da tayi cefane, sauran sai ta saka a kati, kuma Allah
ya saka mata albarka a ciki.
Yaran maƙwabta idan sun shigo, tayi musu tsifa da kitso,
babu ko sisin iyayensu.
Ta duƙufa tana aikinta, ba ta ji motsinsa ba, sai jefo mata
bargo yayi a ka.
A razane ta tashi, bargon kuma ya cukuikuyeta.
Ya ce "Zaki taka kwaɗo" Ihu ta saka ta samu ta
cire bargon da ƙyar, tana dube-dube, yana tsaye yana kallonta, kamar ba shi
yayi maganar ba.
Ta ce "Ina kwaɗon?" Ya yi shiru bai ce komai ba.
Ta kalli yadda stone ɗin ya zube kamar ta yi kuka ta ce
"Kalli yadda ka saka na zubar da kayan sana'ata." Ta durƙusa za ta
kwashe, sai kuma ta yi sauri ta hau kan kujera, ta maƙale ƙafafuwanta ta ce
"Ina kwaɗon ya shiga ne?"
Haryanzu shi dai bai daina mamakin yadda kwaɗo ya zama abun
tsoro ba.
Hanyar fita ya nufa, ta gane tsokanarta yake yi, nan ta ƙara
jinjinawa ƙi faɗinsa, har ya iya ya tsokaneta, amma ya sha kunu ba fara'a.
"Master" ta kira shi. Ya tsaya bai waiwayo ba.
"Dan Allah idan Allah ya yassare, ka taho da omo, zan
yi mana wanki".
Yanzu ma bai yi magana ba ya fita, ta naɗe bargonta, ta
cigaba da aikinta.
Zakiyya kuwa, kamar zata zare, Rahila na ta janta wuraren
malamai kala-kala, yadda za su samu, Hafsa ta auri Alhaji mu'azzam da zarar ya
dawo.
Har sha ɗaya na dare, jauhar na aikin jera stone ɗin ta a
kan gadonta, dan tun tana jin tsoron zaman gidan, har ta saba, sai da ta ji
bacci yana kama idonta sosai, sannan ta tashi ta ajiye kayan, tayi wanka ta
fito tana shirin kwanciya.
Ji ta yi ana buɗe ƙofa, dan haka ba ta damu ba, ta san mai
gidan ne, sai dai bayan wasu mintuna ta ji kamar yayi jifa da wani abu a falo,
yana ta haki mai kama da kakari, gabanta ya faɗi ta fito da sauri, ta tarar da
shi ya riƙe hannunsa yana ta nishi, hannunsa an yanke shi, da ƙafarsa ta hagu,
kasancewar da wuta, ya sanya ta ga yadda yake zubar da jini, a gigice ta ƙaraso
cikin matsanancin tashin hankali ta ce "Master faɗa ku ka yi da wani? Ya
aka yi ka ji ciwo haka?" Yayi shiru yana fesar da iska daga bakinsa.
Da gudu ta shiga ɗakinta, ta ɗaukko zani ta danne masa na
hannunsa da ya fi zubar da jini, ta rikice ta rasa me za ta yi, kawai ta nufi
hanyar fita.
Ya ce "Ina zaki?"
Cikin tashin hankali ta ce "Maƙota zan je, a samo abun
hawa a kai ka asibiti kar jininka ya ƙare".
"A haka kuma zaki fita?"
Sai a lokacin ta ga, ko hijjabi babu a jikinta, ta koma ɗaki,
ta ɗaukko hijjabinta sai kuka take yi, tana dawowa falon ya ce "Kar ki
fita"
"Meyasa? Jini fa ka ke zubarwa"
Ya ce "Ki ƙyale ni, zai daina zuba ne"
Cikin kuka ta ce "Ni dai dan Allah ƙyale ni, sai wani
abun ya same ka, idan jininka ya ƙare fa mutuwa zaka yi" ba ta ma jira me
zai ce ba, ta kasa da gudu, tayi waje. Ta din ga buga gidan maman halimatu,
malam lawan ya buɗe, ya tsaya yana tambayarta menene?".
"Dan Allah baban su halimatu, ka taimaka mini, na ga
kana da babur, mijina ne aka sare shi dan Allah a kai shi asibiti, sai zubar da
jini yake yi"
Ya waro ido ya ce "A daren nan, haka kurum garin
taimakonku, wani abun ya same ni, shi ma idan ya samu wani haka zai yi masa,
sai da safe" ya rufe ƙofarsa.
Haka ta din ga buga gidajen layin nan, na ƙarshe ne mai
gidan ya biyota, sai dai ba shi da abun hawa, suka zo ya tsaya a ƙofar gidan,
ta shiga ciki.
Yana zaune, ya kashingiɗa ya lumshe idonsa, yana jin yadda
raɗaɗi yake ratsa wurin saran.
"Master, taso mu je"
Bai buɗe idonsa ba ya ce "Ina?".
"Wai meyasa ka ke haka, asibiti mana" tayi maganar
hawaye na ta ambaliya a fuskarta.
Ya miƙe yayi waje, ya tarar da maƙwabcin na su a tsaye, suka
gaisa Al'amin ya ce "Malam ka rabu da ita dan Allah, ka je ka kwanta, ba
wani abu in sha Allah"
Ya ce "A'a ga jini kana ta zubarwa, ni bani da abun
hawa, na kira wani ƙanina, a nan titi chemist ɗin sa yake, ko taimakon gaggawa
sai a baka"
Tayi farat ta ce "Yauwwa mun gode Allah ya saka da
alkhairi"
Haka suka tafi, ya kira ƙanin nasa, ya buɗe chemist ɗin
babban wuri ne sosai.
Ya fara yi masa ɗinki, saboda raunin na hannunsa yayi zurfi
sosai da sosai.
Sai dai shi da ake ɗinkewa kamar ƙwarya ko a jikinsa, ita
kuwa sai uban kuka take yi, tana yi masa sannu.
Kawai bin ta yake yi da ido, har mamaki yake yi, yadda take
nuna matuƙar damuwarta a kansa.
Mai Chemist ɗin ya ce "Dan Allah ki daina kukan nan, ba
wani abu, ba ki ga shi jarumi bane?"
"To jininsa ba zai ƙare ba, ya zubar da jini sosai tun
a gida"
Ya ce "Ba zai ƙare ba in sha Allah, idan ma ya ƙare sai
mu saka masa naki".
"Ki daina yi mini surutu a ka kin cika mini kunne"
yayi maganar a ƙule. Haushi ne ya cika masa rai, kamar ya kife mai chemist ɗin
da mari.
Ta ce "To na daina sannu" tayi maganar cikin
kulawa.
A ka gama ɗinki, ya ce zai ɗan saka masa ruwa, saboda ya
taimaka masa ya zubar da jini sosai, amma fafur ya ce ba ya so.
Ya haɗa masa magunguna, ya ce ya din ga zuwa ana wanke
ciwon, jauhar ta ce "Sai dai ka bani kayan dressing ɗin, ba zai din ga
zuwa ba".
Mai chemist ɗin yayi dariya, ya haɗa ya bata, ta ce
"Nawa ne kuɗin maganin? Da abun da aka yi masa?".
Maƙwabcin ya ce "A'a kar ki damu, Allah ya bashi
lafiya, ni zan biya".
Jauhar sai da ta risuna, ta din ga yi masa godiya, sannan ta
ce "Tashi mu tafi" ya miƙe tsam ta bi bayansa.
Suka baro maƙwabcin na su a can, suka nufi gida.
"Sannu, ka na jin jiri ne? Idan kana jin jiri mu tsaya
ka huta, ko ka dafa ni" kallonta ya yi ya ga me zai dafa. Ya dai yi shiru
bai yi magana ba.
Suka isa gida, ya shiga ɗaki ya zauna, ta fito ta hau aikin
wurin da ya ɓata da jini, dan a buɗe su ka bar gidan ma.
Ya zauna ya ci abincin da ya tarar a ɗakinsa, ta ga ledar
omo ce da sabulu da ta ce ya sayo, su yayi wurgi da su.
Ta dawo ɗakinsa, ta tarar ya jingina ya lumshe ido,
"Sannu master, yana yi maka zafi ne? Ga magungunan nan ka sha kan ka yi
baccin".
Ya girgiza mata kai alamar ta ƙyale shi, gumi ya fara
tsatstsafo masa, saboda allurar ta sake shi, zafi ya fara ratsa shi.
Saboda kar ta takura masa da surutu, ya kwanta ya hau baccin
ƙarya.
Ta fita ta ɗaukko mafici ta dawo, ta zauna a gefensa, ta hau
yi masa firfita.
Sai dai lokacin kusan ƙarfe biyu ne na dare, ta din ga zabga
hamma, yana kallonta, har bacci ya ci ƙarfinta, ta saki maficin.
Ya buɗe idonsa fes a kanta, har mamaki take bashi, yadda
take nuna matuƙar damuwarta a kansa, kuma komai zai yi mata ba ta jin haushi.
Hakazalika bai daina mamakin yadda aka yi, iyayenta suka
yarda suka aura masa ita ba.
Ya ciro wayarsa a aljihunsa, ya kira walid, uku sauran nan,
ya ɗaga.
"Walid"
"Maza, ya aka yi ne?".
"Ka san akuyancin da yaran nan suka yi mini?"
Walid ya ce "Wane yaran, suwaye?".
"Na baro chamber, na shigo cikin unguwa, kawai na ji
sara a hannuna, sun kai su bakwai, suka hau ni da sara, kasheni suka so
yi"
Walid ya zabga ashar ya ce "Suwaye?".
"Bari na yi wa ɗaya shaida, haryanzu ba su san waye ni
ba, na karya biyu, sauran sun gudu, sun yi mini rauni a hannuna da
ƙafata".
"Yanzu kana ina?"
"Ina gida, ni wallahi yarinyar nan ta fara takura mini,
komai kuka, duk ta tashi hankalinta, iyayenta ba su yi mata adalci ba, ni fa ba
zata hana ni rayuwata yadda nake so ba".
Walid ya ƙyalƙyale da dariya ya ce "Mai dogon zamani,
da uban waye ya damu da ka ji koma menene mana, tana da tausayi ne kawai da
alama, ka dai daina yi mata muzurai da zare ido kawai"
Yayi tsaki ya ce "Ka saka liti ya nemo mini suwaye
yaran nan"
"Shikenan, zamu faso gobe in ga jikin naka, sai da
safe". Ya ajiye wayar ya kalli fuskarta, tana ta bacci a zaune.
Hannunsa ɗaya ya saka, ya janyota ta kwanta a kan katifar,
shi kuma ya jingina da bango ya cigaba da bacci.
Kasancewar ba salla za ta yi ba period take yi ya sanya,
tana ji ana kiran sallar asuba, ta cigaba da baccinta, sam ta manta a ina take.
Ƙaurin da ya isheta ne, ya sanya ta fara tari, tayi juyi ta
buɗe ido, da fuskarsa ta fara tozali, yana busa sigari. Ta tashi tana kallon ɗakin,
sai yanzu ta tuna ta shigo tana yi masa fifita.
Ta hau soshe-soshen cizon sauro.
Ƙura masa ido ta yi, ya kawar da kansa gefe.
A raunane ta ce "Master"
Idonsa ya ɗago ya kalleta.
"Dan Allah ka daina, ba na so zuciyata ba ta yi mini daɗi,
kuma zaka cutar da kanka, kalli yadda ka je aka yi maka rauni, ka zubar da
jini, haba master manya ba sa haka" tsuke bakinsa yayi yana sakin hayaƙin,
a ƙoƙarin sa na hana maganganun ta yin tasiri a zuciyarsa.
Ta girgiza kai ta ce "Shikenan, ya jikin?".
Yayi mata banza, ya cigaba da busa sigari.
"Dan Allah ko ba zaka daina ba, ka rage mana, lafiyar
ka fa".
"Ke, ki koma in da ki ka fito mana, ko na ɗaure ki na
ce ki zauna ne? Tashi ki bar mini ɗaki".
Ta gyaɗa kai ta ce "Abun har da gori, Allah ya baka
haƙuri" ta miƙe idonta fal hawaye.
Tana kitchen tana aikin karin kumallo, aka buga ƙofa, ta
saka hijjabi ta buɗe ƙofar, ta ga walid d wasu matsa su biyu, suka gaisa suka
ce mata, wurin mak dogon zamani suk zo.
Ta haɗe rai ta ce "Sunan shi Al'amin, bari na yi masa
magana".
Tana shiga ta tarar da shi a falo ya fito.
Ta ce "Ka zauna sai su shigo su ganka, amma ka ga da
rauni a jikinka" tayi maganar tana sunkuyar da kai, tana jiran ya gaya
mata baƙar magana.
Idonta ya ɗan yi ja, saboda kukan da ta yi.
Ya nemi wuri ya zauna, ba tayi tunanin zai yadda da hakan
ba.
Ta je ta leƙa ta ce musu su shigo.
A falo suka tarar da shi, gida sai ƙamshi yake yi, gashi dai
ba wani haɗaɗen gida ba, amma ta gyare gidan tsaf.
Suka zauna a falo, Walid ya ce "Maza wallahi ka more,
mu ma Allah ya tsamo mu, dan Allah ji wani ƙamshi kamar a gidan masu kuɗi".
"Duba ni ka zo yi, ko munafunci ka zo yi?"
Walid ya ce "Duka, amma dai ya jikin? Kut ka sha ɗinki
kamar ƙwarya, za su ci ubansu yaran nan, kan yamma an gano su in sha
Allah".
Suna ta zuba, tana jiyo shi yana saka baki sama-sama, da ita
ce dai ba zai yi hira ba, amma yana magana.
Tayi sallama suka amsa, ta zo ta ajiye musu kofuna, da
cokula da flask ɗin shayi, ta koma ta kawo jallof ɗin taliya a faranti, sai
ƙamshi take yi.
Liti ya ce "Allahu Akbar, sannu amarya, wannan hidima
haka? Ai da mun sani tuntuni mun zo" Al'amin kallonta yake yi, da
jinjinawa ƙarfin halinta, har ta ƙar sanwa, ta yi girki da su.
Suka kewaye, suka din ga cin taliyar nan, liti ya ce
"Kalarta kalar girkinta, abincinta mai daɗi, ita kuma 'yar beauty, wallahi
maza ka more, ga gida mai ƙamshi"
Ji yayi ya kasa haɗiye abincin, maimakon ya ji daɗin yabon
suka yi mata, sai ya tsuke fuska ya tsame hannunsa daga kwanon abincin.
Har suka gama santin, bai sake cewa komai ba, Walid kuma
yana ankare da shi, dan haka da gayya, ya cigaba da kunna shi, suka gama abun
da za su yi, suka fita tsakar gida suka din ga yi mata godiya.
Walid ya ce "Wai ba zaka fito ka raka mu ba?"
Tayi farat ta ce "A'a ba shi da lafiya ai"
Walid ya ce "Au, to Allah ya baku haƙuri, Allah ya ƙara
afuwa ya bar ƙauna".
Bayan fitarsu ta kwashe kwanukan, ta wanke, tana ta aikinta,
yana kan doguwar kujera a kwance, sai dai ba ta kula shi ba.
Kusan kwanaki uku, jikin master yayi kyau, ba shi da ƙan
jiki, ba zai sha magani ba sai ya ga dama, dressing kuwa cewa yayi ba ya so.
A kwanakin nan jauhar na jin ciwon kai, da ciwon jiki, sai
dai ba ta wani damu ba.
Duk yadda ta so hana master fita, da 'yan dabaru sai da ya
saka ƙafa ya fice, ya tafi nasa garari.
Cin abinci ne yake dawo shi, ko sau ɗaya bai tambayi yadda
take samun yin cefane ba, sai da ya zo ya ci.
Tun da ya dawo gidan ya ji shiru bai ji motsinta ba, kuma
bai ga abinci ba, sama da awa guda, saɓanin da, da ya shigo za ta fito.
Kasa kwanciya hankalinsa yayi, ya nufi ɗakinta.
A kwance take a kan gadonta, amma bai tabattar da idonta
biyu ko bacci take yi ba.
Ya ƙarasa gaban gadon, sai dai ya manta sunanta, Fatima
zahra kuma yayi masa nauyin da ba zai iya faɗa a bakinsa ba.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Dukan gefen katifar da take kai yayi, amma ba ta motsa ba,
ya zura kai ya leƙa fuskarta, ya ga bacci take yi. Duk da bai saba zuwa ya
tarar da ita tana bacci ba.
Ficewa ya yi, ya bar ɗakin, shi babban takaicin sa, rashin
samun abun da zai ci.
Jauhar kuwa, tun dare ta kwana ta na fama da matsanancin
ciwon mara, ga ulcer ta tayar mata, sai gudawa take fama da tashin zuciya, ta
samu ya lafa mata, ta kwanta ta hau bacci ga gidan yau babu abun da za ta dafa,
ɗan kuɗin hannunta sam ba su da yawa.
Ƙarshe dai buredi ya fita ya samo, ya dawo ya zauna a falo
yana ci.
Wayarsa ce ta fara ringing, ya duba ya ga kiran indabo ne,
kallon wayar ya cigaba da yi, yana cin buredinsa, sai da ta kusa katsewa ya ɗaga
ya saka a kunnensa, yayi shiru.
"Aminu"
"Mmm"
"Na dawo, kai nake jira, haryanzu ba ka zo ba"
"Zan zo"
"Yaushe kenan? Haba kai kuwa dan Allah, ba ka san kiran
me nake yi maka ba fa"
Al'amin ya ce "Na ce zan zo ai"
"To shikenan, Allah ya kawo ka"
Ya ajiye wayar, gaba ɗaya haushin buredin da yake ci ma yake
ji, sam ba ya yi masa daɗi, har aka yi kiran la'asar, ba ta fito ba.
Ya tashi yayi salla, ya fito falo ya sake zama, sai ga ta ta
fito tana ɗan yamutsa fuska. Fuskar duk ta ɗan ɗaga tayi jawur.
Ta zo ta nemi wuri ta kwanta, ba tare da ta ce masa komai
ba.
"Wai yau ba abinci ne?" Yayi maganar yana wani
basarwa.
Maimakon ta ce masa babu abun da za ta dafa ne, sai ta ce
masa "Ba na jin daɗi ne"
Ya taɓe baki, ya tashi ya saka takalmansa ya fice daga
gidan, fitarsa ba kaɗan, ta ji horn da tsayuwar mota a ƙofar gidan, mintuna kaɗan
ta ji ana bugun gate, ta saka hijjabi ta je ta buɗe.
Baba ta gani a tsaye, cikin matsananciyar murna ta ce
"Baba" yayi murmushi ta ba shi hanya ya shigo.
Suka isa har falonta, ya samu wuri ya zauna ta ce "Baba
meyasa baka kuma zuwa ba?" Tayi maganar hawaye na cika mata ido.
Wani irin matsanancin tausayinta ya kama shi, har ya ji
kamar shi ma ya yi kukan, amma ya danne ya ce "To ba gani na zo ba,
Waliyiyya 'yar baba"
"Baba babu wanda ya zo mini, sai yaya saifu da Anty
lubabatu, kowa yaƙi zuwa in da nake, wai ba za su zo ba, mijina ɗan daba ne,
kuma ba abun da zai yi musu, ba ruwan shi da su.
Baba ya ce "Waliyiyya, ki daina saka irin wannan
abubuwan a ranki, kar su dameki, ki yi haƙuri ke mai haƙuri ce, amma ki ƙara.
Ya gidan ya mijin naki?"
Cikin jin kunya ta ce "Yana nan lafiya, yanzun nan ya
fita"
"Jauhar, ina fatan dai babu wata matsala dai ko?"
Ta girgiza kai ta ce "Babu".
Turus yayi ganin takalma a ƙofar falo, amma ya ƙarasa ya
shiga, ba tare da ya yi sallama ba.
Kallo ɗaya ya yi wa mutumin, ya ga yana yanayi da jauhar ya
ƙarasa cikin falon, hannunsa riƙe da baƙar leda.
Durƙusawa yayi har ƙasa ya ce wa Baba "Ina wuni"
hakan ba ƙaramin daɗi ya yi wa jauhar ba, dan tun da ta ji motsin shigowar sa,
take fatan Allah ya sa kar ya yi wa baba wani abun na rashin ɗa'a.
Baba ya ƙare masa kallo, kai ba ka ve mara ji bane ba, dan a
cikin nutsuwarsa yake, ya ce "Lafiya ƙalau malam Aminu, yau dai Allah ya
yi mun haɗu, ya gidan ya iyalin naka"
Ya amsa da "Lafiya ƙalau".
"To masha Allah, Ubangiji Allah ya yi muku albarka, ayi
ta haƙuri, ka san ita rayuwar aure, zama da mace sai haƙuri, dole za ku saɓawa
juna, ayi ta haƙuri. Ba yabon kai ba, na san Waliyiyya yarinyar kirki ce, amma
duk da haka na san dole wataran a saɓa Allah ya yi muku albarka"
Ya amsa da Amin, ya tashi ya bar wurin ya tafi ɗakinsa.
Ta ce "Baba bari na dafa maka abinci" ta faɗi
hakan, dan kar baba ya fahimta wani abu.
Baba ya ce "A'a, zuwa na yi dama na ganki, ni da ba a
san da zuwana ba"
Jauhar ta ce "Dan Allah baba ka tsaya"
Ya ce "Gidanku ba zan tsaya ba, kira mini mijinki, zamu
yi magana"
Ta tashi ta shiga ɗakinsa, ta ce "Master, baba yana son
ganinka".
Ya jinjina mata kai, ya tashi ya fito, ya samu wuri a ƙasa
ya zauna.
Baba ya ce "Malam Aminu dan Allah alfarma zan nema, ka
san jauhar ba ta kammala sakandare ba, an fara registration ɗin WAEC ne, shi ne
na ce ina neman alfarma, zan biya mata tayi registration ta yi jarrabawa dan
Allah".
Aminu ya ce "Babu damuwa, Allah ya bada sa'a".
"Amin Aminullahi, Allah ya saka da alkhairi" Baba
ya miƙe ya ce zai tafi.
Cikin rauni ta ce "Baba daga zuwanka sai tafiya
kuma?".
"To Waliyiyya ba dai na ganki ba".
Kamar mara gaskiya, haka ta biyo bayan baba, a tsakar gida
ya tsaya ya kalleta ya ce "Jauhar menene?" Ta girgiza masa kai alamar
bakomai.
Ya juya zai buɗe gate, ta riƙe rigarsa ta fashe da kuka.
Ya ce "Subhanallah, gaya mini menene? Wani abun yake yi
miki?" Girgiza masa kai ta sake yi.
Ta cukuikuye rigarsa, ta cigaba da sheshsheƙar kuka, shafa
kanta ya dinga yi sai dai ya kasa hanata cigaba da kukan.
Sai ma hannu da ya sa, yana goge hawayen da suke ƙoƙarin
zubo masa, ya san ba zata faɗa masa koma menene ba, amma yanayinta ya nuna masa
tana da damuwa.
Dan kanta ta cika masa riga, ta goge hawayenta ta ce
"Ka gaida gida baba, ka ce ina gaida su mama da Anty da kowa da kowa"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Za su ji in sha Allah, gashi
ke ba waya ba, ranar talata ki je ki samu malam Hadi, a office ɗin su, zaki yi
thumb print, yayi miki registration"
Ta ce "To baba, na gode sosai, Allah ya saka da
alkhairi" ya fita ta rufe gate ɗin, ta jingina da jikin gate ɗin, hawaye
na cigaba da zuba daga idonta.
Duk yadda suka yi, Al'amin yana kallonsu ta window, ta goge
hawayenta kafin ta dawo ɗakin, ya bar falon. Haka ta koma bedroom ɗin ta, ta
kwanta tana ta tunani daban-daban a cikin zuciyarta.
****
'yan uwan Alhaji mu'azzam kuwa, ba su gaya masa cewar an
aurar da jauhar ba, suka ce masa babanta ya ce yayi haƙuri idan ya dawo ayi
auren, abun ya bashi mamaki, ga wata irin kewar yarinyar da yake yi, yana jin
son ta sosai da sosai a ransa, ya din ga addu'a da fatan Allah ya sa ba wani
abun ne zai faru ba, saboda jinkirin da ake samu ba.
Kusan kwanaki biyu kenan, jauhar bayan ta gama ciwon mara,
ta koma zazzaɓi, gashi babu abincin kirki, kuɗin da take tarawa a kati, ba ta
son ta je ta ce a bata, a fuskanci akwai matsala, hakan kamar tonon asiri ne ga
mijinta, 'yan unguwa su samu abun faɗa.
Haka zata fita ya sayo gari, da gyaɗa ko suga babu ta sha,
shi kuwa garujen ko a jikinsa, sai dai yana ankare da yanayin jikinta.
Al'amin na zaune a katafaren falon honorable Indabo, yana
jiransa.
Babu jimawa ya iso falon, yana ganinsa yayi murmushi ya ce
"Ango ka sha ƙamshi, da alama amarya ce ta ɓoye mana kai har haka"
Shiru yayi, ya saka babban yatsansa yana sosa girarsa.
Indabo ya zauna ya ce "Tun shekaranjiya na shigo, nake
nemanka amma ka ƙi zuwa. Da farko dai ina yi maka murnar angwancewa da ka yi,
ina Abuja aka sanar da ni an kama ka, ana gobe ɗaurin aure, na tura P.A . Allah
ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya"
"Amin" ya amsa a ciki kamar an yi masa dole.
"To yaya shirye-shirye? Ina fatan kana ƙara shirya mini
yaranka, babban zaɓe yana gabatowa, idan aka yi nasara aka samu kujerar nan,
Aminu zaku warwasa daga kai har yaranka, har da na kusa da ku ma, dan Allah kar
ka bani kunya, duk da ba ka saba bani ɗin ba".
"To" ya amsa yana kallon wani wurin daban.
"Ka san meyasa na kira ka?"
"A'a"
"Akwai wani matashi, yana nan a social media, ba shi da
wani aiki da ya wuce adawa da ni, da aibata mana jam'iyya,kuma hankalin matasa
ya fara komawa kansa, na rasa yadda zan yi da yaron nan, duk wasu hanyoyi da
zan bi a siyasance, na yi amma ya ƙi ganewa".
"Me ka ke so ayi?".
Ya jefowa Al'amin hoton matashin, an rubuta adress ɗin sa a
jiki.
Kallo ɗaya ya yi wa hoton, ba tare da ya ɗauka ba, ya ce
"Me ka ke so ayi masa?"
"Ire-iren sa suna da yawa, amma sonake ayi musu misali
a kansa. Ina son yayi ido biyu da Switzerland ɗin ka, ka yi masa shaida alamar
kun haɗu".
Wani irin murmushi ya yi, ya fito da dogon harshen sa, ya
lashi laɓaɓɓansa na ƙasa da suka yi duhu ya ce "Switzerland. Kamar ka ce
idan aka samu kujerar nan, zamu warwasa da yarana da na kusa da ni, alƙawari ne
ko zance?"
"Wace irin magana ka ke haka ne, ba zance bane ba, da
gaske nake yi mana".
Al'amin ya ce "In ɗauke shi a matsayin alƙawari
dai"
Indabo ya yi turus, ya kasa bashi amsa.
"Ba zan tura mota, ta tashi a bule ni da hayaƙi ba, ba
senator ba wallahi ko shugaban ƙasa ka zama, ba za a bule ni da hayaƙi ba, dan
haka maganar nan a matsayin alƙawari na ɗauketa"
"Kai fa matsalarka kenan Aminu".
"Menene sallamar aikina?"
"Masu kauri ne, ga wannan ka fara rage ta" yayi
maganar yana ajiye masa envelopes.
"Ka san dai in da ka tura ni ko? Wallahi idan ka bani
abun da bai yi mini ba, ba zan yi ba"
Indabo yayi murmushi ya ce "Ai somin taɓi na baka,
akwai ciko"
Ya miƙe tsaye ya ɗauki envelope ɗin sa ya fice.
Sai da ya je can dabar su, ya sallame su, sannan ya nufi
gida.
Da ya je gidan a buɗe ya tarar da ƙofar gidan, kai tsaye ya
shiga ya tarar duk ta cika igiya da kayansa, ta wanke masa su.
Mamakin jauhar yake, rashin sanin ciwon kai ne, ko me yake
damunta, ta ce ba ta da lafiya, amma ta zage ta yi masa wanki, hatta ɗakinsa da
ya bari kaca-kaca ta gyara masa.
Ya samu wuri ya zauna a kan kujera, ya kunna sigari yana
sha.
Sallamarta ya ji a tsakar gida, bai amsa ba ya cigaba da
shan sigarinsa.
A hankali take takawa, ga yunwa ga ciwo, ta shigo hannunta
riƙe da 'yar leda.
Ta zauna a kan carfet jiki a sanyaye ta ce "Ka yi
haƙuri, baka nan ne ban tambayeka ba na fita, magani na je chemist ɗin bakin
titi na sayo"
Sai da yayi wani munafukin tari, saboda tun ranar da mai
chemist ɗin nan yayi masa ɗinki, ya din ga jan ta da hira, ya ji ya tsane shi,
amma ya fuske yayi mata shiru.
"Kar ka ga ban yi girki ba tun jiya, kuɗin hannuna ne
suka ƙare, amma ga gurasa na taho mana da ita daga titi" ƙara yawan
hayaƙin da yake fitarwa daga bakinsa yayi, ba tare da ya ko kalleta ba.
Jin ba shi da niyyar kulata, ya sanya ta yinƙura za ta
tashi, sai dai ta yi wani irin razanannen ihu, kallonta yayi da sauri, ya ga
ihun me take yi, dan ya san ba zai wuce wani abun haushin ne ba, dan kamar
gyare haka take da ihu.
Ashe ƙadangare ne a ƙarƙashin kujerar da ta zauna a gabanta,
tun shigowarsa ya ganshi, amma bai damu ba, ƙadangaren na ta neman hanyar fita,
jikinsa yayi baƙi sosai, kamar an ciro shi daga kwata, yayi ba kyan gani.
Tuni ta suma a wurin, dan kuwa hannunta ta ɗora a kansa ba
ta sani ba.
Maimakon ya tashi, sai ya zuba mata ido, cikin takaici, abu
kaɗan sai ta suma, ko ta hau ihu.
Kamar ba zai tashi ba, sai kuma ya miƙe.
Ya saka hannu ya ɗauketa ya kwantar da ita a kan kujera, sai
dai jikinta ya yi zafi sosai, sai yanzu yake tunanin zazzaɓi take yi kenan?.
Ya duba ledar magungunan da ta sayo, maganin ɗaya mai hoton
sauro, ɗaya kuma pcm ne.
Ya kama gefen hannunta, ya ji bugun zuciyar ta yana bugawa
da sauri, ya saki hannun nata yana kallonta, ita a rayuwata komai ma tsoro yake
ba ta kenan.
A hankali ta fara motsawa, ta yinƙura za ta tashi, ya ce
"Koma ki kwanta" ta ɗaga idonta a hankali ta kalleshi.
"Tsoro nake ji" ta faɗa muryarta na rawa cikin
tsoro.
Ya sake kama hannunta, yana jin bugun zuciyar ta, ya saki ya
ce "Tashi" ta yinƙura ta tashi a hankali, kanta na sara mata ga jiri
saboda yunwar da take ji.
Tana daga kan kujerar a kwance, ya ɗage ɗaya kujerar da
ƙadangaren yake ƙarƙashin ta, kawai ya saka hannu ya danƙi ƙadangaren ya jefa
shi waje.
"Na shiga uku master, ƙadangaren ka ke kamawa da
hannunka"
Tsaki yayi, ya wuce ɗakinsa, jikinta ya din ga rawa, tsigar
jikinta ta din ga tashi. Ya dawo ya dire mata leda, ya ce "Ki ci ki sha
magani" ya jefa mata wani kwali sannan ya fita.
Kwalin ne ya fara ɗaukar hankalinta, ta ɗauka da sauri tana
dubawa, sabuwar mp ce kar 'yar ƙarama mai kyau.
Ba ta san lokacin da ta yi murmushi ba, ta hau kukkunata
tana dubawa, sai da ta gama, ta ajiye ta buɗe ledar.
Irin meatpie ɗin nan ne oasis manya kusan biyar, da ƙatuwar
robar fura da nono.
Kasancewar a yunwace take kuwa ta hau ci, ta ji babu daɗi
kwana biyu tana ciwo, amma bai iya yi mata sannu ba, dama magani ba ta saka ran
ya saya mata ba, mutumin da bai ba ta abinci ba wane magani zai bata, ashe yana
sane, sannu ce ko ya jiki ba zai iya ce mata ba.
Sai dai da tuna yadda ya ɗauki ƙadangare da hannunsa, sai
tsigar jikinta ta tashi.
Ana yin sallar isha'i ya dawo, mp ɗin ta har da fitila.
Ta tashi tana yi masa sannu da zuwa, ya wani maze ya bata
wata ledar, sannan ya zauna ya ce "Ki nemi wata ma'aikaciyar idan akwai a
nan kusa, tayi miki, idan ki ka je wurin wancan ɗan iskan na bakin hanya kuma
ni da ke ne"
Ta saka hannu biyu ta karɓa, allurar zazzaɓi ce mai tsada ya
sayo ya kawo mata, amma bai iya cewa ya jiki ba.
"To godiya nake master, Allah ya ƙara arziki ya sa a fi
haka, na ga saƙo ma na gode sosai da sosai Allah ya sa afi haka".
"Amin".
Ta ce "Ga naka na ajiye maka"
Ya ce "Idan zan ci ba sai kin ce na ci ba, ki daina
kuma wannan mugun tsoron, komai ya baki tsoro, idan ba haka ba ki kashe kanki a
banza"
Jauhar ta rausayar da kai ta ce "Nima ban san ina jin
tsoron ba ne. Amma kai ba ka jin tsoron sa ka riƙe shi da hannu?"
"Ban sani ba? Rannan kwaɗo yau ƙadangare, meye abun
tsoro a jikinsu, har da suma saboda ƙadangare" tayi shiru ta sunkuyar da
kai.
Sai da ya gama sannan ta ce "Ka yi haƙuri to, ban san
ya ake yi nake jin tsoron ba".
"Idan ma kina sane ki cigaba da yi mini ihu a gida
kamar gyare".
Sai da ta yi murmushi ta ce "Zan koyi jarumta, zan
daina jin tsoro in sha Allah. Yauwwa master yaushe zamu je ka kai ni na gaida
su mama? Ba su taɓa ganina ba, ban taɓa ganinsu ba, su hajiya kawai na taɓa
gani, yakamata ka kaini na gaishe su. Sai ayi girki mu je mu gaishe su, na ga
haka ake yi".
Shiru yayi, yana tuna Ummansa, tana yawan cewa Allah ya raya
mini babana na ga aurenka, in ga mai sa'ar da zata auri ɗan autan mazana
Jauhar ta ce "Ka yi haƙuri idan na ɓata maka rai ne
maganar da na yi"
Ya tashi tsam ya ce "Yauwwa, Ina sake jaddada miki,
idan ba zaki iya zama ba, ko kin gaji zaki iya komawa gida, babu takura, na ga
shekaranjiya kina ta koke-koke, idan da takura you are free to go" daga
haka ya nufi ɗakinsa.
Gabanta ya faɗi ta fara tunanin, me ta ce da zai ɓata masa
rai har haka?.
Haka nan ta ji ba ta fatan abun da zai sake mayar da ita
gida yanzu, da sunan zawarci ko ace ta kasa zama, saboda ta san dama mugunta ce
ta saka aka aura mata shi.
A ranta ta ce 'Zan jure, in sha Allah zan bawa mara ɗa
kunya, in sha Allah, Allah ba zai kunyata ni ba, ba zan tagayyara ba"
Lokaci-lokaci yake leƙowa falo, sai ya hangota tana aikin
stone ɗin ta, tana jin radio a mp. Yana so yayi mata maganar ta je ayi mata
allura, amma ya fasa.
Bacci ta fara, ji ta tafi ta je ta kwanta, har ta fara bacci
aka kawo wuta, hasken lantarki ya hasketa, ba shiri ta tashi, sai a yanzu ta
tuna ba ta kashe ƙwayayen ba, ta fita falo dan ta kashe, taga Al'amin ya fito
daga ɗakinsa, yana soke wuƙa a ƙugunsa.
Ta tsura masa ido tana kallonsa, bai san tana falon ba, yana
ɗaga ido, suka yi ido huɗu, ɗaure fuska yayi ya zo zai fice.
Ta ce "Master ina zaka je a daren nan, kuma?"
Ai ko sake kallonta bai yi ba, ya nufi ƙofar fita.
"Dan Allah kar ka je in da za a illataka, zuciyata ba
ta yi mini daɗi in ga kana zubar da jini".
Bai tsaya ba, sai da ya dangana da tsakar gida, ya kama
katanga ya dira, ita kuma ta zauna a wurin ta fashe da kuka mai taɓa zuciya.
Ko da ya fita titi, liti ya zo a kan babur ya ɗauke shi,
suka tafi.
Unguwar shiru, kowa ya shige gida, suka maƙale a wani wuri
su na shaye-shaye.
Can sai ga wanda suke hari, ya kwararo layin a kan babur,
Al'amin ne ya fita da sauri, ya daki tayar gaban babur ɗin, aikuwa ya faɗi ƙasa
da shi da babur ɗin.
Suka rirriƙe shi, Al'amin ya zagaya dai-dai kunnensa ya ce
"Tijjani Faruk ko? Gargaɗi aka ce ayi maka, a kan rubuce-rubucen da ka ke
yi a dandalin sa da zumunta, da waɗanda ka ke suka, da Switzerland na so na yi
maka warning ɗin, amma a yadda ka ke ɗin nan, zaka iya ɗayewa idan nayi maka da
ita, ko iraƙi na saka maka a jiki ba zaka shura ba.
Liti, duba bayana, ka ciro Russia ka yi masa rijiya a cinya,
ka yi masa eleven da iraƙi a gadon bayansa".
Tijjani yana ihu, yana kururuwa, yana komai, liti ya caka
masa wuƙa a cinyarsa, ya yage masa riga, ya yanke shi sau biyu a baya, ya
watsar da shi a wurin yana kururuwa.
Can gida mama tana ta sintiri, har sha biyu saura, ba ta ji
an ce Tijjani ya shigo gida ya ɗauki abinci ba, ta din ga kiran lambar wayarsa
amma a kashe.
Tana ta mita, aka kira baba a waya, aka sanar musu, an
tsinto tijjani a hanyar dawowa gida, an yanke shi da makami, an tafi kai shi
asibitin cikin gari, sashen bayar da agajin gaggawa.
Ɗora hannu ta yi a ka, tana ihu tana ta shiga uku an kashe
mata ɗa.
Baba ya ce 'Ba cewa aka yi ya mutu ba, an yanke shi aka ce,
ƙila masu ƙwacen waya ne ki bari mu je mu gani mana"
Ya fita ya kira maƙwabcinsa, ya ce ya raka shi asibiti,
domin su ga a halin da Tijjani yake ciki.
Ala'amin bayan ya koma gida, a falo ya tarar da jauhar,
sauro yayi dandazo a kanta yana cizo, sai ajiyar zuciya take yi ta ci uban
kuka.
Tsayawa yayi yana kallonta, tare da jinjinawa taurin kanta.
Kamar ya tsallaketa ya wuce, ya durƙusa ya kwasheta kamar
tsuma ya nufi ɗakinta da ita, yana zuwa ya kwantar da ita a kan gadon, ta buɗe
idonta tare da ƙura masa ido.
Tsaki yayi ya fita, ta mayar da kanta ta kwantar a kan
pillow.
Al'amin sawun keke ne, Allah kaɗai ya san in da ya dosa, ɗazu
ya gama cewa idan ba zata iya zama ba, ta tafi gida, amma yanzu ya tsinto ta a
falo ya kawota ɗaki.
Da safe ta dafa tea, ta kawo masa da sauran meatpie ɗin da
ya so jiya, yau bai yi rejecting ba ya karɓa ya fara ci.
"Master"
"Mmmm"
"Na iya irin wannan meatpie ɗin fa, idan ka na so ka
sayo mini kayan, na iya sosai mai daɗi".
Ya ce "To".
Da tana jin kunyar cin abu a gabansa, amma zuwa yanzu ta
saba, ta gama cin nata, ta je ta kwaso kayansa da suka bushe, tana ninkewa ta
saka zare da allura, tana ɗinke masa waɗanda suka yage.
Yana kallonta tana yi, shi kuma ya karkace zai kunna sigari.
"Master, shan sigari yana cutar da lafiya fa, ka din ga
ragewa dan Allah, kar ka yi rashin lafiya".
"Kin je an yi miki allurar?"
"Zan sha magani, ba na son allura ne tsoro nake
ji"
Tashi ya yi zaune ya ce "Ƙadangare, kwaɗo yanzu kuma
allura, sannu 'yar madara. Sai ki biyani kuɗin allurar da na saya" yayi
maganar yana barsawa yana gyara gefen rigarsa.
Tayi dariya, jin yau ya kulata, har ya ɗan yi doguwar magana
da ita.
"To nawa ne, sai na tara da kaɗan-kaɗan na biya
ka" yayi shiru yana cigaba da sakin hayaƙi.
Ta sake gyara zamanta ta ce "Master Mp nan fa tayi kyau
sosai, Allah ya ƙara maka buɗi"
Ya jinjina mata kai.
Tijjani kuwa ba ma ya hayyacinsa, saboda ya zubar da jini
sosai da sosai saran da su Viper suka yi masa, da ƙyar aka samu ya farfaɗo.
Cinyarsa sun yi masa rami da ɗan buda, likitoci sai ƙoƙarin
ceto ransa yake yi.
"Sai oga"
"Yaya na ji shiru fa, haryanzu kuna tsare da
yarona".
"Na sani, trape ɗin muke setting, idan muka yi gaggawa
aikinmu zai kwaɓe"
"Ok ina saurarenku".
Jauhar sai murna take yi, zata je registration makarantar
su, dama tun da aka kawota ba ta je unguwar ba.
Da safe tana ta shiri, ya fito zai fita ya ajiye mata dubu ɗaya
ya ce "Ki hau mota"
"Na gode sosai da sosai, Allah ya sa a fi haka, ya ƙara
buɗi, ya tsare mini kai" ba shiri ya kalleta, ya ga ba shi take kallo ba,
sai jujjuya dubun take yi tana murmushi.
"Da ina da wata ba zan kasheta ba, ina son sabon kuɗi
sosai" tayi maganar tana ƙara faɗaɗa murmushin ta.
"Sai ki ɗinka ta ki saka tun da riga ce"
"Kuma zata yi mini kyau fa, adawo lafiya, Allah ya
tsareka"
Ya amsa da "Amin"
Jauhar ta ƙarasa shirinta, ta tafi makaranta, kamar yadda
Baba ya ce mata ta je tayi registration, a nan ta haɗu da 'yan makarantar su,
ta din ga murna sun haɗu da 'yan makarantar su, da malaman makarantar ma.
Ta din ga yi wa ƙawayenta mitar ba su je gidanta ba.
"Jauhar wa zai zo gidanki kina auren ɗan daba? Ba ma za
a bar mu mu zo ba"
Jauhar ta yi murmushi ta ce "Ku daina fakewa da haka,
ni da muke tare, ya aka yi bai yi mini komai ba?"
"A'a ai ke matarsa ce, mu kuwa fa"
Duk da ba ta gaya masa ba, haka kawai ta ji tana son ta je
gida.
Ganin ko ta fita ba hanata yake yi ba, ya sanya ta nufi
hanyar gida.
Gaba ɗaya sun yi mamakin ganinta, Anty ta ce "Yaya, ya
na ganki yanzu meyafaru?"
Jauhar ta yi murmushi ta ce "Lafiya lau anty,
registration na zo na ce bari na biyo, tun da kun ƙi zuwa".
Kallon jauhar suke yi, su ga ko akwai wani abu na tashin
hankali a tare da ita, ko alamar duka ko makamancin haka, amma ba su gani ba,
sai ma wata nutsuwa ta mussaman da suka gani a tare da ita.
Mama ta ce 'm"Jauhar kin kyauta, wato miji daɗi, ki ka
kasa zuwa ki duba ɗan uwanki, ya kusa mutuwa"
Cikin tashin hankali jauhar ta ce "Subhanallah, mama
ban sani ba ba shi da lafiya ne?"
"Ina fa, ya dawo daga aiki, aka samu wasu suka sassare
shi".
Abun ya ɗagawa jauhar hankali, ta ce musu ba ta sani ba.
Al'amin yana can wurin su Walid, kansa yana yi masa ciwo, ga
yana jin yanayin jikinsa kamar zazzaɓi yana son kama shi.
Yana jin wayarsa na ta vibrating yayi banza.
"Viper wayarka fa ta cika mini kunne, dan Allah ka ɗaga"
"Ƙyale ni, kamar zazzaɓi ne zai kama ni"
"To ka kashe wayar mana".
"Ba zan kashe ba"
"Ka duba mana ko beb ɗin ka ce take nemanka, yarinyar
nan ta na kula mana da kai yasin".
Viper yayi tsaki, ya sake gyara kwanciyar sa.
Walid ya miƙa hannu, ya ɗauki wayar ya ɗaga ya ce "Ya
aka yi?"
"Ka gaya wa uban gidanka, na ga cikarsa ta shigo mana
arear, duk da kashedin da na yi kar ta sake zuwa, tun da ya kwasheta. Yayi
ganganci mafi girma da muni, tun tun da ya bari ta shigo, ya zo ya ɗauki
gawarta a dabata!.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Walid ya kalli Al'amin, ya lumshe idanunsa, wasu irin
jijiyoyi suka fito raɗa-raɗa a goshinsa.
Yayi shiru ya ƙi ko motsawa.
"Mai zamani, ba ka ji me ya ce ba ne, matarka fa yake
maganar ka je ka ɗauki gawarta"
"Na aiketa ne?"
"Ban gane ka aiketa ba? Kai kut....." Ya ɗura masa
ashar.
"Idan da gaske ya kasheta fa?"
Al'amin ya tashi zaune, ya ɗauki wayarsa, ya danna ya kira
wata lamba.
"Yeah maza"
Ya ce "Ina aikin da na saku?"
"Ai ta gama ta tafi ma"
Ya ce "Ba tafiya a ta yi ba, gidansu ta tafi, ba ka
kira ni ka gaya mini ba. Wancan garan ya ce in je in ɗauki gawarta a dabarsa,
wallahi ya kashe 'yar mutane sai na kasheka kai ma"
"Haba maza, cewa ka yi mu saka ido, ta shiga ta gama
abun da take yi ta tafi, kuma min bi ta ba ta sani ba, ta gama ta tafi ba ka ce
mu bi ta mu ga ina zata tafi ba"
"Wallahi liti ka bari muka haɗu sai na saka maka ƙarfe,
ka ji na rantse. Ya ajjye wayar ya yinƙura, Walid ya ce "Ina zaka je, ka
ce ba ka jin daɗi, ka zauna bari ni na je"
"In zauna sai ya kasheta, sannan zan je?" Yayi
maganar a zafafe.
Walid ya bi shi da kallo, yana son gano haƙiƙanin in da ya
dosa, amma bai gane ba, Al'amin ya sake birkicewa ya ce "Ya kasheta
ko ya bar ta da rai, ba shi ne a gabana ba, tun da ba ni na gayyato ta rayuwata
ba, abu mafi muni shi ne ace madaki ya kuma yi mini illa, idan haka ta kasance,
kan mai uwa da wabi, zan ɗauki matakin da ya dace".
Ya fita da sauri, Walid ya bi bayansa, bai ma san ina ne
gidan na su ba, sai da walid ya yi masa jagora, yaran madaki suna ganin Al'amin
ya shigo musu unguwa da rana tsaka, amma aka rasa mai tunkararsa, dan ba su
fiye galaba a kansa ba, sai sun yi masa taron dangi.
Suna tafe a hanya, liti ya kira Walid ya ce masa "Ka ce
ya kwantar da hankalinsa, na yi waya tana lafiya tana cikin gidan su, zamu fito
da ita lafiya in sha Allah"
Walid yana gaya wa Viper, ya ce "Ka ce masa bana
so" ya yi maganar yana ƙara sauri.
Jauhar kuwa na can, har ta ɗora musu girki, sai zungurarta
suke yi, su ji a wani hali take ciki a gidanta, da irin zaman da take yi da
Al'amin, amma ta dinga waskewa, taƙi gaya musu komai.
Hafsa har da tambayarta, wai wuri ɗaya suke kwana?.
Jauhar ta kwashe da dariya ta ce "To zai kwana a waje
ne yana da mata?".
Surayya ta ce "Iyee zama da maɗaukin kanwa, wato har
bakinki ma ya buɗe haka?"
Jauhar ta yi dariya ta ce "Kai Anty surayya tambayata
fa tayi, bari na ƙarasa na je gida ma na yi girki, kar ya dawo".
A tunaninsu za su ga jauhar cikin mawuyacin hali, amma sam
ba su ga alamar hakan ba.
Ta shiga suka gaisa da anty lubabatu,ta din ga murna yadda
ta ga jauhar, babu alamar wahala a tare da ita, ta aika 'ya'yan anty lubabatu
su je gidan kakannin su, su karɓo mata shirin dutse a wurin ƙanwar anty
lubabatu. Da yake duk a unguwar ne.
Anty lubabtu har da harhaɗawa jauhar 'yan kayan gyaran aure
na mata, ita dai ba ta ce komai ba, ta karɓa ta ce ta gode.
Da ta fito daga gidan, ta lura da wasu matasa da ba ta san
suwaye ba, a layin amma ba ta damu ba ta shige gida.
Walida ta tare ta ta ce "Me Anty lubabatun ta
baki?" Suka karɓi ledar hannunta, suka ga kayan mata da turarukan wuta da
humra masu kyau da ƙamshi.
Suka din ga yi mata dariya cikin izgilanci surayya ta
ce "Wai nan ba ki yadda ba ke matar aure ko jauhar? Dan Allah ya ki
ke yi ke kuwa da shi, ga 'yan shaye-shaye da ƙazanta, kuma har kiss ku ke
yi?"
Jauhar ta yi wani irin murmushi ta ce "Yaya surayya
kenan"
"Gaya mana man"
"To ni me zan ce? Annabi ya hana faɗa, sirrinmu ne
ai"
Surayya ta ce "Lallai, yau na ga illar ƙani ya rigaka
aure, ni ki ke gaya wa baƙar magana jauhar?
"A'a ki yi haƙuri, ba baƙar magana ba ce"
Ta karɓe kayanta, ta saka a jakarta, ta cigaba da aikinta.
Ta zauna tana yanka salak, sai mita take yi ba ta haɗu da
yaya saifu ba, kuma baba ma baya nan"
Tijjani ya fito yana ɗan tattakawa, ta din ga yi masa sannu.
Tun da ya shigo layin yake ganin yaran madaki tsilla-tsilla,
alla-alla yake yi ya ƙarasa ya tabattar da abun da madaki ya faɗa gaske ne ko
akasin haka, idan gaske ne bai san iya adadin haukan da zai yi masa ba.
Walid ya ce "Ga gidan nan" dai-dai lokacin ɗan
gidan anty lubabatu ya zo zai shiga gidan su jauhar, hannunsa riƙe da ledar
viva, an zubo mata dutsen shiri da kayan yi kala-kala, babar anty lubabatu ta
ce a bata kyauta a matsayin jari, shi ne gudunmawarta na biki.
"Kai shiga nan gidan ka ce.... Sai kuma ya yi shiru dan
ya manta sunanta, sai Fatima yake iya tunawa.
Walid ya ce "Ka faɗa masa sunan"
Tsaki yayi ya ce "Na manta sunan, sunan wani iri ne dai
haka kamar Angela"
Walid ya ce "Amma kuwa ka yi asara"
Al'amin ya ce "Ka ce 'yar madara ta zo in ji
Master"
Walid na son yin magana, ya maze ya ce "Na san ƙarya fa
madaki dama yake yi bai kasheta ba".
Yaron ya shiga ya fara ba ta saƙon hajiya kakarsa, na bata
kyautar dutse, ta karɓa tana murna da godiya, sannan ya ce "Wani a waje ya
ce wai 'yar madara ta zo" take gaban Jauhar ya faɗi.
Walida ta ce "Wace wata 'yar madara, babu ita a gidan
nan, in ji wa ya ce maka?"
Yaron ya ce "Wai in ji Master "
Jauhar ta ce "Na shiga uku, master ne, ban gaya masa
zan zo nan ba, waye ya gaya masa?".
Ta ce "Bari na ɗaukko jakata"
Anty ta fito ta ce "wannan aikin kuma wa zai ƙarasa
shi? Ai sai yayi haƙuri ta gama, kai je ka ka ce masa aiki take yi, ya dawo an
jima"
Buɗe baki jauhar ta yi ta ce "A'a anty kar ya gaya masa
haka, kaga haidar ka ce masa...
Anty ta katse ta ta ce "Fita ka je ka gaya masa haka,
waye shi ba gidan sirikansa ba ne ba".
Gaban Jauhar ya tsananta faɗuwa, ba ta san me hakan ka iya
haifarwa ba.
Mama ma fitowa ta yi ta ce "Ba zaki zauna ki cigaba da
aikin ba"
Viper kuwa wani marurun takaici ne ya ƙule masa a wuya, jin
irin saƙon da aka aiko masa da shi, kamar shi za a aikowa da wannan banzar
maganar. kawai ya sai kai zai shiga gidan, walid ya riƙe shi ya ce "Mai
zamani gidan sirikanka ne fa, dan Allah kar yi wani abu mara daɗi, ka zubar
mata da mutunci"
"Tun da suka zaɓi su aura mini ita, sai na tabattar
musu da maganata ce gaba da ta su a yanzu" kawai ya saka kai cikin gidan.
Cak ta tsaya, jikinta yana tsuma, ganinsa ya shigo yana
wannan takun nasa, ya ƙureta da ido, tun kafin ya ƙaraso.
Tsit suka yi suna kallon ikon Allah, ya ƙaraso, ta wutsiyar
ido ya kalli yaya tijjani da ke zaune a kan farar kujera, ya sauke idonsa a kan
mama, su surayya sannan Anty Zakiyya ta ƙarshe.
Yana ganinta ya ƙara tabattar da Rahila ce ta saka aka yi
masa aure, bai ga alamar akwai mahaifiyar jauhar a cikin su ba.
Ya kalli Jauhar ya ce "Ni na aiko ki zo ki ka ce mini
ba zaki zo ba?"
Ta ce "Dan Allah Master ka yi haƙuri"
"Shut up!" Yayi maganar cikin ƙaraji, tare da ball
da bokitin da aka kawo markaɗe, da kwanon salak ɗin duk suka tarwatse a wurin,
ta zabura ta ƙanƙame jikinta. Ai ba ita ba, har sauran matan gidan da 'yan
matan.
Tijjani kuwa ɗimaucewa yayi, dan kuwa ba zai manta muryar
nan ba, duk da yana tantama amma kamar muryar wanda suka yi ma aika-aika.
"Dama mun yi da ke zaki zo nan? Kin zata ƙarya suke yi
da suka ce za su saraki idan suka kuma ganinki a unguwar nan?" Ɗago ido ta
yi cikin tsoro tana kallonsa.
Ganin yadda duk ta rikice ya sanya ya saki muryarsa ya ce
"Zo ki wuce mu tafi"
Ta ce "Bari na ɗakko hijjabina"
Mayar da idonsa yayi kan Anty Zakiyya, ko ƙiftawa ba ya yi,
babu shiri ta juya da sauri ta shige ɗaki.
Jauhar ta fito, da jakarta da ledojinta, ya danƙi hannunta,
suka yi waje.
Suna fita Surayya ta ce "Bala'i dama wannan ne mai
dogon zamanin? Jaraba jauhara na cikin bala'i".
Hafsa ta ce "Ni kuma abun da na gani daban, kut wallahi
na ɗauka zan ga wani gardin mummuna, ji mutum hanci har baka, kai amma yayi
kalar tsoro da yawa, haka yake yi mata wannan tijara"
Mama ta ce "Dalla ku yi mana shiru, kalli asarar da ya
yi mana, abincin ranarmu ya mayar da mu baya" mama tayi maganar a ƙule.
"To mama aikin gama ai ya riga ya gama, ni wallahi na
zata dukanta zai yi ma. Anty har an gudu ɗaki, bayan ita ta bayar da saƙon da
aka gaya masa"
Daga ɗaki ta ce "Haka kurum in tsaya ya kasheni a
banza, kin ga wani huci da yake yi kamar kumurci, gashi sai kallona yake yi, ya
ƙara girma fiye da yadda na san shi".
Jauhar kuwa suna fita, walid ya rufa musu baya, Viper ya din
ga jan ta, gashi saurinsa ya ninka nata, kamar ta hantsila, Alla-Alla yake yi
su ƙarasa titi ya saka ta a abun hawa, sai dai suka yi karo da madaki da
yaransa.
Wata irin muguwar dariya madaki yayi, wadda ta ƙara fito da
ainihin muninsa, baƙi ne wuluk kuma gabjeje, yana da jajayen idanuwa, wanda
yake rambaɗa musu farin kwalli, ga wani ƙaton sara a fuskarsa a kaikaice da ya
raba fuskar in to two equal parts.
Sai ta ga Al'amin ɗin ta nutsatstse ne mai kyan gani, a kan
madaki, ta san gidansu ta san sunansa a unguwar su, amma ba ta sanshi a fuska
ba.
Jikinta ya hau tsuma, Al'amin ya sakata a bayansa, ya tsaya
yana fuskantar madaki, Walid ya tsaya a gefensa.
"Tun da aka gaya mini matarka ta shigo unguwar nan, na
ce bari in auna adadin son da ka ke yi mata. Ka san bikin ma bana nan aka yi,
labari na samu ban haɗu da kai na yi maka Allah ya sanya alkhairi ba. Ƙarfin
halinka ya kai, tun da ka iya ratso cikin unguwarmu ka auri 'ya. Shiyasa na so
ka zama ɗaya daga yarana tun a wancan lokacin amma ka ƙi.
Ya leƙa ya kalli fuskar jauhar ya ce "Ashe 'yar gidan
Alhaji faruku ce, rabona da ita tun tana 'yar mitsitsiya, ashe haka ta girma ta
ƙara kyau, ka bani kunya ma, wannan ai ba ta wani gama nuna ba, wannan ai ka yi
mata girma, kodayeke ba a nan take ba an danne bodari ta ka, bakinta mai kyau ɗan
ƙarami zai yi daɗin sha, anya wannan ba....
Wani wawan mari Al'amin ya ɗauke madaki da shi yana huci,
Walid ya riƙe shi ya ce "Viper ka san me ka yi kuwa?"
Al'amin ya hankaɗe shi, ya kalli madaki cikin ido ya ce
"Ka daɗe da kashe Al'amin ɗin da ka raina, ka mayar abun nishaɗinka, Kar
ka sake ka shiga shingena, duk wala-walar da zaka yi, kar ka ƙetare
iyaka".
Yaran madaki suka yinƙuro, Madaki ya ɗaga musu hannu, ya
ciro wata muguwar wuƙa a jikinsa, ya ce "Bari in nu na wa duniya kai rago
ne, a gaban matar taka, da ka yi dan ka burgeta"
Wani irin ihu jauhar ta ƙwala, ta rirriƙe Al'amin tana kuka
ta ce "Dan Allah kar ka caka masa, zaka kashe shi idan ka caka masa, dan
Allah ka yi haƙuri kar ka kashe shi".
Viper ya ce "Kafin ɗayanmu ya bar duniya, za a ga waye
ragon, ƙazamin kare kawai"
Ya sake danƙar hannun jauhar, ya keta ta tsakanin yaran
madaki yayi gaba, walid kuma ya tsaya a kan hanyar yana kallonsu, dan kar wani
ya bi bayansu ya illata su.
Madaki ya bi bayansu da kallo, ya din ga kallon wuƙar
hannunsa yana murmushi, lallai yayi sake ɗan zaki ya girma, ya fara zama
barazana a gare shi.
Babban abun da ya ƙular da Al'amin, bai wuce yadda jauhar
take ta rusa masa uban kuka ba a cikin a daidaita sahu, bayan koma menene ita
ya janyo, kamar ya cillata kan titi ya huce, yana zaman zamansa an ƙaƙaba masa
ita, yanzu dole duk in da zai yi sai yana tunanin kar a cutar da ita.
Bai kulata ba har suka je gida,ga wani irin ciwo da kansa
yake yi, ga zazzaɓi tun a hanya ya rufe shi.
Suna zuwa gida, ya wuce ɗakinsa ya bar ta.
Bin bayansa ta yi, cikin marairaicewa ta ce "Dan Allah
Master ka yi haƙuri, ban san haka za ta faru ba, nayi niyyar gaya maka dama
idan na dawo, dan Allah ka yi haƙuri"
Banza yayi mata, ya rufe idanunsa, saboda yadda sanyi yake
ratsa shi, ga wani abu mai ɗaci da ya tsaya masa, ya ƙi wucewa, saboda yadda
abubuwan da suka wakana a rayuwar sa, suke dawo masa cikin kansa a yanzu. Idan
ya tuna abun da madaki ya faɗa a kanta, sai ya ji kamar ya kurma ihu, ya gama
cutarsa, ko shi jai tsaya ya ƙare mata kallo, ya ga bakin nata ba sai shi.
A marairaice ta ce "Master, Yaya Al'amin dan Allah ka
yi mini magana, ka yi haƙuri ka yafe mini dan Allah, na san koma menene ni ce
sila".
"Get out from sight, ki tashi ki fita kafin ni na
sassaraki a wurin nan" a tsorace ta tashi ta fita, tana waiwayen sa.
Tana fita ya riƙe kansa, saboda yadda ya yi masa nauyi.
Anty Zakiyya kuwa, Rahila ta kira a waya, bayan sun gaisa ta
ce 'Ƙawata yau na ga tsiya da wasali"
"Bani na sha meyafaru?"
"Yau ɗanki ya zo gidan nan ai"
"Wa kenan"
"Sirikinmu mana, wai ashe yaran madaki ɗan dabar nan na
unguwarmu sun ce idan ta sake zuwa unguwar nan, sai sun sassarata, ta zo gidan
nan bai sani ba, a sukwane ya taho, yau mun ga bala'i, kin ga tijarar da ya yi
ya ja hannunta suka tafi?"
Rahila ta ce "Zai aikata fiye da haka ma, in dai Aminu
ne ɗan banzan bawa kenan ake gaya miki"
"Taɓ amma anya ba son yarinyar nan yake yi ba? Kin ga a
yadda ya zo kuwa?".
"To ke ina ruwanki, dama dai ba burinki ita wannan ta
bar miki gida ba, shi ya sani ba mace ba ce ba? Luf zai yi ai, ni fa tun da aka
yi auren ba mu sa shi a idonmu ba, na ce can ya ƙarata"
Suka kwashe da dariya, Zakiyya ta ce "Taɓ amma ƙato ne,
sai ka ce ɗan dambe, kuma wallahi ba wani abun gyara da muka yi mata, yau ne ma
da ta zo maƙwabciyarmu ta bata, amma haka nan muka kaita"
"Oho musu, in dai buƙata ta biya, ba shikenan ba, su
ƙarata"
Suka kwashe da dariya gaba ɗaya.
Jauhar ta kasa zaune ta kasa tsaye, master ya ɗau fushi da
ita, gashi ya ƙi fitowa, kuma ya korota daga ɗakinsa.
Da canjin hannunta, ta haɗa ta sayo fulawa, ta kwaɓa
alkubus, da wata irin miya ya 'yan dabaru, sai dai har ta yi ta gama bai fito
ba.
Sai ta kasa ci, ta sake lallaɓawa ta leƙa ɗakinsa, ta ga
yana banɗaki, ta cigaba da tsayuwa ya fito, ta tsaya tana sallama a bakin ƙofa.
"Idan ki ka bari na zo na sameki a wurin nan, sai na ɓata
miki rai"
Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri master, na
tuba ba zan sake ba"
Kwanciya ya sake yi, ya juyawa ƙofar baya.
"To in kawo maka abinci?"
Kamar ya ce eh, amma yayi mata shiru.
Abun da ya ɗaure mata kai, bai wuce har dare kwanciya yake
yi ba, yaƙi fitowa, cikin tsananin fargaba ta shiga da kwanukan abinci ta ajiye
masa.
Ƙamshin miyar da ya cika masa hanci, ya sanya ya buɗe
idonsa.
Gwiwoyinta ta saka a ƙasa ta ce "Dan Allah ka yi
haƙuri, ni ko wani hukuncin ka yi mini dan Allah ka daina yin fushi da ni, bana
son na ga na yi laifi dan Allah" hawayenta ne yake ɗiga a kan katifarsa,
ya gyara kwanciyar sa ya juya mata baya.
Ya tsani kuka, ba ta san ƙara ƙular da shi take yi ba.
Tashi ta yi ta sake zagayawa kamar mayya, tana yi masa
magiya.
Ya buɗe jajayen idanunsa yana kallonta, sai dai yaƙi magana.
Yarrrr haka ta ji tsigar jikinta tana tashi, ba ta san
kallon ma yake yi mata ba.
"Ka yi magana Please, ka ce ka haƙura" tayi
maganar tana jan majina.
Ƙafarsa ya ɗora ɗaya kan ɗaya yana kaɗawa, saboda ciwon da
kansa yake yi, amma a zahiri abun da yake yin, kamar yana yi ne da gayya da
nuna mata iko da izza irin ta ɗa namiji.
"Kin cika mini kunne" yayi maganar a hankali, duk
da buɗɗaɗiyar murya ce da shi irin ta jaruman maza.
"To ka ce ka haƙura mana" tayi maganar cikin
shagwaɓar da ba ta san ta yi ba.
"Kai mini ruwa zan yi wanka" cikin sauri ta ce
"To"
Tunani yake yi daban-daban a ransa, ya ma rasa wanne zai yi,
yana shiga wankan, ta sake gyara shimfiɗar katifarsa, ya yi wanka ya fito yanzu
ma jikinsa babu riga, yana ƙoƙarin mayar da kayan da ya cire, da sauri ta ce
"Ai kana da wankakkun kaya, na wanke maka ka saka wannan" ta yi
maganar tana miƙo masa kayan da ta ciro masa.
"Ɓace zan canza kaya" ta fita da sauri,mintuna
goma da ta dawo, tuni ya kusa rabin abincinsa.
Garin ta miƙa hannu ta ɗauki jug ta zuba masa ruwa, hannunta
ya taɓa ƙafarsa ta ji zafi sosai, ta kalleshi ta sake kai hannunta ƙafarsa.
"Master zazzaɓi ka ke yi?"
Lomarsa ya cigaba da yi, cikin tsoro ta sake kai bayan
hannunta ta taɓa hannunsa.
"Na shiga uku ba ka da lafiya ai, duk ni na janyo
ko?"
Ya karɓi jug ɗin hannunta, ya cire murfin, ya kafa kai ya
sha fiye da rabin ruwan, sai ka ce tsohon raƙumi.
Ya gama ya jingina da jikin bango ya sake lumshe ido.
"Master, akwai allurar nan da ka sayo mini ba ayi mini
ba, mu je in raka ka ayi maka to"
Gyatsa ya saki, maimakon ya yi hamdala, sai ita ta ce
"Alhamdilillahilazi aɗa'amana haza, Ubangiji Allah ya ciyar da mu kullum,
ya bawa wanda bai samu ba"
"Amin" ya faɗa ƙasa-ƙasa zai kwanta, a sukwane ta
ce "Dan Allah kar ka kwanta, mu je a duba ka, kar ka sha wahala, sauro ne
yayi yawa a unguwar nan shiyasa muke ta zazzaɓi, dan Allah ka zo mu je a duba
ka"
"Kai wallahi kina addaba mini, kin dame ni"
Jauhar ta kwantar da murya cikin sigar rarrashi ta ce
"To na sani, amma ka yi haƙuri, na daina, dan Allah mu je a dubaka ka ji
Mijin 'yar madara, ba ka ji yadda jikinka yayi zafi ba?"
Ya kalli yadda ta dafe kafaɗarsa, tayi saurin sakinsa, ya ce
"Sai an yi sallar magariba"
"To mu koma falo, sai na saka maka maganin sauro a ɗakin,
idan ka cigaba da kwanciyar jikinka mutuwa zai yi"
Da ƙyar ta lallaɓo shi, suka dawo falo, ta kunna maganin
sauro.
Ana idar da sallar magariba, ta ɗaukko allurar, ta ce su
tafi, ya ce ya fasa zuwa, shi ba zai iya tafiya ba.
Da ƙyar sai ka ce ɗan goye, ta lallaɓa shi suka fita.
Ta rufe ƙofar gidan, ta riƙe hannunsa ta ce "To mu je,
kar ka ji jiri idan ka gaji ka yi mini magana sai mu tsaya ka huta".
Kallonta kawai yake yi, ɗan hannun nata ɗan mitsitsi a cikin
nasa.
Suna tafe tana ƙara ba shi haƙuri, a kan laifin da ta yi.
Nasiru mai chemist na ganinsu ya ce "A'a jauhar, kin
warware shi ne shi ma ya kwanta" tayi murmushi ta ce "Allura na kawo
shi, ayi masa mai sanyi dan Allah"
Da jauhar ta san yadda yake ji a zuciyarsa idan ya ga tana
tankawa mai chemist da ba ta yi ba, sai dai bai san dalilin hakan ba, kawai ba
ya son ya ga wani yana kulata.
Aka gama yi masa suka fito za su tafi, ta tsaya tambayar mai
ɗanyen dankali nawa kwano.
Al'amin ya zaro kuɗin ya bayar, suna tafe tana godiyar
dankali.
Da safe ta soya musu dankali da tea, ya gama karyawa, ya
kalleta ya ce "Wannan matar da na gani a gidanku wacece?"
Ta ce "Wacce?"
"Mai baƙaƙen kayan nan"
"Anty zakiyya ce, matar Baba ce" ya jinjina kai
bai sake cewa komai ba.
"Ka santa ne?" Yayi shiru bai amsa ba, daga haka
ta ja bakinta tayi shiru.
Babu yadda ba ta yi ba, a kan ya je a ƙarasa allurar nan,
amma ya ƙi. Da ya ji ƙwarin jikinsa ma, fita ya cigaba da yi.
Jauhar na zaune a falonta, tana tunanin ƙirƙirar sabbin
styles na abun hannu da jigida, ta fara sayarwa.
Aka bubbuga mata gate, ta tashi ta je ta buɗe, ta ga wani
mutum da ba ta san shi ba, fuskarsa sanye da facemask ya ce "Mai zamani
yana nan?"
Ta girgiza kai ta ce "Ya fita"
"Ga wannan ki ajiye masa". Ya bata leda mai baƙi
da fari.
Ta karɓa ta ce "In ji wa zan ce?".
"Idan ya zo zai gane, ki ajiye masa a ɗakinsa, zan kira
shi"
Ta ce "To shikenan"
Ta rufe ƙofa, kamar ta buɗe, sai ta fasa ta kai masa cikin
drower sa, ta ajiye masa ta cigaba da sabgoginta.
Kayan da anty lubabatu ta bata ta ɗauka tana duddubawa, ta ɗan
ɗanɗana abun, tayi shiru tana tunani, ita sam abun da ake faɗa a auren, ba ta
ga alamar sa ba, dan shi ba ta tata ma yake yi ba, ya ƙule a ɗakinsa yayi
shaye-shayensa ya ci abinci ya fita yawonsa shi ne kawai a gabansa.
Ta ɗan taɓe baki, ta ɗauki turaren wutar, ta tirara na
gidan, ta turara na jikinta, ta ɗora girki.
Da daddare da wuri ya dawo gida, gidan sai ƙamshi yake yi na
musamman, giftawar farko da tayi, sai da ya ɗaga kai ya kalleta, ƙamshin har
cikin ƙwaƙwalwarsa ya ji shi.
Yau faten dankalin ta yi, dan shi ne kawai da su, sai
dai yayi masa daɗi bai taɓa sanin ana faten dankalin hausa ba, sai yau da ta
bashi, har mamakin yadda take sarrafa abinci yake yi.
Ya gama cin abincin ta ce "Master yanzu allurar nan dai
ba za a ƙarasa ba ko?"
"Eh" ya faɗa kai tsaye.
"Ai shikenan, thank God tun da ka warke ai. Ka yi mini
addu'a mun kusa fara WAEC, Allah ya sa result ɗina yayi kyau".
"Sai ki yi karatu"
"Ina yi ai" ya kalleta ya ce "A hakan, kina
shirme dai" ta gane da kayan beat ɗin ta da stone yake, tayi murmushi jin
yadda yau yake yi mata doguwar magana.
"Ina karatu sosai da sosai fa".
"Akwai kwaɗo a ƙarƙashin kujerar nan da ki ke" da
sauri ta kalli kujerar, sai kuma ta yi dariya ta ce "Ai na daina jin
tsoron" wai nan tsokanarta yake yi, amma fuskar nan a haɗe.
Har wajen ƙarfe goma suna tare, yana ta danna wayarsa, mai
madannai, ita kuma tana jin radio tana aikinta, ba hira suke yi ba, amma
kasancewar su a hakan ma, daɗi take yi mata.
Ya yi miƙa ya tashi zai tafi ɗaki ta ce "Tafiya babu
sallama"
Ba tare da ya yi Magana ba, ya ɗaga mata hannu, murmushi ta
yi ta ce "Asuba ta gari mijin Angela" ɗan rausayar da kai ya yi kamar
zai yi murmushi ya shiga ɗakinsa.
Ya kwanta yana shaƙar ƙamshin da bedsheet ɗin sa yake yi,
bai taɓa tunanin zai yi aure ba, dan babu wannan lissafin a gabansa, ba dan
albarkacin auren ba, da a cikin tsummokara zai kwana a can gidan da suke tare
da su Walid.
Tsakar dare jauhar ta ji motsi, kamar ana watsi da kaya.
"Malam kar ka shiga wannan ɗakin ba komai a ciki, mata
ta ce a ciki, kuma babu in da shari'a ta baka damar shiga in da matata
take"
Jin muryar Al'amin, ya sanya ta saukko daga kan gadon da
sauri, wata irin dalleliyar fitila aka saka ana haske gidan.
"Shut up, kar ka sake magana, kar na sake jin
bakinka"
Cikin ƙaraji ya ce "Sai na yi magana, wallahi ka shiga ɗakin
nan, zan illataka".
Da gudu ta fito dan ta ga meyake faruwa, ma'aikata ta gani,
har da jami'an tsaro, sun saka wa Al'amin ankwa sun durƙusar da shi a kan
gwiwoyinsa.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Yallaɓai me yayi
muku? Laifin me ya yi?"
"Ki koma ɗaki Ki nemi hijjabi ki saka" yayi
maganar cike da takaici.
"Oya ku yi searching ko ina a gidan nan, kar ki motsa
daga in da ki ke"
Wani jami'in ne ya fito daga ɗakin Al'amin, da wannan ledar
da aka kawo aka ce a ajiye masa, ya ce 'Ga abun da muka samu sir"
Shugaban operation ɗin ya karɓa, ya zazzage sai ga ƙwayoyi,
da allurai da wiwi da sauran tarkace sai kuma wata 'yar leda mai ɗauke da wani
farin gari.
Ya ce "Good, mu tafi da shi mun samu abar"
"Yallaɓai, wallahi wani ne ya kawo su ɗazu, ba shi ya
kawo su ba, dan Allah kar ku tafi da shi.
Ko kallonta ba su yi ba, suka tasa ƙeyar Al'amin.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Biyo bayansu tayi, tana wani irin kuka mai ban tausayi, tana
yi musu magiyar su sake shi, ba shi da laifi, amma babu wanda ya saurareta a
cikinsu.
Maƙwabta na jiyo kukanta, amma babu wanda ya iya ko leƙowa
ya ga abun da yake faruwa.
Shi kuwa Al'amin ko a jikinsa, kukan da take yi ne kawai ba
ya so.
Suka saka shi a mota, ta ce "To Yallaɓai ina za ku kai
shi dan Allah"
"NDLEA, daga nan zamu miƙawa 'yan sanda shi, su kai shi
gaban kotu".
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu dai sai kun
kai shi NDLEA ɗin kenan? Wancan karon baku kai shi ba sai yanzu, dan Allah ku
duba lamarin nan"
Suka saka Al'amin a mota, suka tafi da shi, a falonta ta
zauna, ta fashe da kuka, ta daɗe a wurin tana kuka, ganin hakan ba mafita bane,
ya sanya ta tashi ta ɗauro alwala ta koma ɗakinta, tayi ta sallar da ba ta da
tabbacin tana karanta ayoyin daidai saboda tashin hankali, ta ɗaga hannu tayi
addu'a, amma ta kasa kawai ta mayar da kanta sujuda ta fashe da kuka.
Har asuba ta yi idonta biyu, ta yi sallar asuba ta idar, ta
zauna tana karanta duk abun da ya zo bakinta, wani abu mai nauyi ya tokare mata
ƙirji, ta ji tamkar numfashinta zai ɗauke gaba ɗaya.
Bayan sallar asuba magidantan layin suka tsaya suna
salallamin, jiya da daddare ma'aikatan sun shigo layin, amma babu wanda ya
fito.
Malam lawan ya ce "Har kwa tambayi lafiya? Ai tun da ɗan
daba ya tare muku a unguwa, sai abun da Allah ya yi, wurinsa suka zo, wataƙila
ma wata ta'asar ya je ya tafka, suka zo suka yi masa ɗaukar amarya tsakar
dare".
Suka yi ta salallami da fatan Allah ya kyauta.
Har rana ta yi haske, jauhar tana zaune a wuri ɗaya, idanun
ta sun yi ja, duk sun kumbura fuskarta tayi ja ta kumbura saboda kuka.
Maman halimatu da wata mata mai kallon gidan na jauhar suka
shigo, sai da suka yi ta sallama, da ƙyar ta iya amsawa sam ba ta ji sallamar
ta su ba ma, ta fito falo ta ce su shigo.
Maman halimatu ta ce "Jauhar, lafiya kuwa? Wai meyafaru
ne jiya mun ji hayaniya, babu damar mu fito.
Take wasu hawayen suka ziraro mata ta goge su ta ce
"Jami'an tsaro ne suka zo suka tafi da shi"
"Subhanallah, laifin me yayi?"
Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba"
"To ki yi haƙuri, ki samu ki ci abinci, sai ki
nutsu a san abun yi, Allah ya kyauta ya kiyaye gaba"
Ta amsa musu da to ta gode.
Kai ka ce takaba take yi, duk ta fita hayyacinta, ba ta san
wurin wa za ta nufa da maganar nan ba, kuma ba ta san ina hukumar hana sha da
fataucin miyagun ƙwayoyin take ba ma, balle ta je, ba kuma ta san ta tambaya a
gano wani abun, gashi ko gidan su Al'amin ɗin ma ba ta sani ba, balle ta je ta
gaya musu, ko da wani abu da za ayi a kai.
Ta dudduba ta tattara ɗan kuɗin da take da shi, ta fita, ta
samu mai napep ta tambaye shi idan ya san ina ne hukumar hana sha da fataucin
miyagun ƙwayoyi.
Ya ce mata ya sani, ya ɗauke ta ya tafi da ita.
Ta din ga yawo a cikin hukumar, aka ce mata ba ya wurin, ba
a kai shi ba, sai da ƙyar aka ce mata yana nan, amma ba zata ganshi ba, babu
irin magiyar da ba ta yi ba, amma suka hanata ganinsa, ƙarshe sai gida ta koma
a matuƙar galabaice.
Ta rama salollin da suke kanta, ta din ga addu'a da fatan
Ubangiji Allah ya fitar da shi lafiya, da ta san abun da zai faru kenan, da ba
ta karɓi abun da ba ta san ko menene ba ta ajiye masa.
Ɗaya maƙwabciyar ta ta wasila, wadda mijinta ya taɓa raka su
wurin mai chemist ta shigo gidan.
Ta ce "Jauhar yaya ake ciki, kin same shi kuwa, kin je
wurin 'yan sandan?"
Ta ce "Eh na je, ba su bari na ganshi ba"
"Kuma ba su gaya miki abun da yayi suka kama shi
ba?" Ta jinjina mata kai alamar eh, wasu hawaye masu ciwo suna zubo mata.
"Ki yi haƙuri ki kwantar da hankalinki jauhar, in sha
Allah komai zai wuce kamar ba ayi ba, kuma in sha Allah zai fito"
Ta ce "To Allah ya sa".
Yau ma haka ta kwana salloli, da kai wa Allah kukanta, da
fatan Allah ya saka mijinta yana lafiya ya kuɓutar da shi.
Da safe ta sai ƙosai da buredi, ta dafa tea, ta kuma wanke
ƙafa ta koma wurin nan, amma suka sake ce mata ba za ta ganshi ba, tayi magiyar
har ta gaji, ta basu abincin ta ce su bashi.
Ta koma harabar wurin, ta nemi wuri ta zauna, ta rasa abun
da yake yi mata daɗi, rabonta da abinci tun a jiya, gaba ɗaya tunanin halin da
Al'amin yake ciki, da wanda zai shiga a nan gaba ya dame ta, ta gaji da zama ta
tashi ta nufi gida.
Ɗakinsa da suka shiga duk suka watsar da kaya ta shiga, dan
damuwa ba ta bari ta shiga ta gyara ba.
Duk sun watsar da komai na ɗakin, ta tattare masa kayan,
tana cikin gyarawa ta gano wayarsa, ta ɗauka tana duddubawa sai ta ga tarin
kiran walid da liti, cikin hanzari ta kira lambar walid.
"Ya ne maza? Tun shekaranjiya ban sake jin ɗuriyarka
ba, na zo gidanka ba kowa ka kuma ƙi ɗaga waya".
"Assalamu alaikum" tayi masa sallama.
Ya ce "Ahh madam ke ce ashe? Ya ake ciki yana
ina?"
Muryarta na rawa ta ce "Shekaranjiya da daddare jami'an
tsaro sun zo sun tafi da shi"
"Kamar yaya? Me yayi?".
"Abu aka kawo aka ce na ajiye masa, su kuma suka zo da
daddare suka ga kayan a leda, suka tafi da shi na je sun hanani ganinsa"
tayi maganar cikin kuka.
Walid ya ce "Ya isa haka yi shiru, bari na zo gidan
gani nan"
Sai ta ɗan ji sanyi a ranta, tamkar yana zuwa zai fito mata
da Al'amin ɗin.
Kusan awa ɗaya da rabi, ta ji ana knocking gate.
Da sauri ta tashi ta je ta buɗe, liti ta gani da Walid, har
ƙasa ta durƙusa ta gaishe su.
Walid ya amsa ya ce "Ya aka yi, meyafaru?"
"Yadda dai na gaya maka, wani ne ya kawo wata leda ya
ce a ajiye masa, na manta ban nuna masa ba, kawai suka zo cikin dare suka tafi
da shi, naje na je hukumar sun hana ni ganinsa"
Liti ya ce "Ki yi haƙuri, ki daina kukan haka, kuma kin
tabattar bai yi wani laifin ba?"
"Ni dai a iya sanina bana tunanin yayi wani abun, duk
da ba tare muke yawo da shi ba, amma dai sun ce a kan kayan da suka gani a
gidan nan ne"
Walid ya ce "Ki kwantar da hankalinki, in dai Viper ne,
mutum ne mai sa'a koma menene zai fito, amma ki kwantar da hankalinki, yanzu
idan muka je babu lallai su sauraremu, amma in sha Allah gobe in Allah ya kaimu
da wuri zamu je mu ga yadda za ayi".
Ta ce "To shikenan na gode sosai, bari na kawo muku
ruwa"
"Kar ki damu a ƙoshe muke, ki kwantar da hankalinki
idan da wani abu ki kira lambata"
Ta ce "To na gode"
Ta rufe ƙofa suka tafi, liti ya ce "Ikon Allah"
"Menene?"
"Kawai rayuwar Mai zamani nake kalla, yadda yake
gararambarsa da kamar babu mai so, idan muka faɗa cakwakiyarmu, iya mu muke
warware kayarmu, babu wanda ya damu da mu, shi kalli Allah ya kawo masa mai
kula da shi".
"Haka ne, amma tausayi ta bani wallahi, yarinya ce
sosai. Yana ta buyagi da rashin mutunci an yi masa aure, amma sai da ya mari
madaki saboda ya tankata".
Liti ya kwashe da dariya ya ce "Kai mace fa aka ce
maka, na raba ka"
Walid ya kwashe da dariya ya ce "A ƙi faɗinsa, da
madaki ya ce ya kashe ta, mazewa yayi ba zai motsa ba, wai ba shi ya aiketa ba,
amma ka ga wasu jijiyoyi da suka tashi a goshinsa, ga wani gumi da yake a iya
karan hancinsa, bai san yana wasu abubuwan ba" suka sake kwashewa da
dariya.
Liti ya saka su guduma ɗan gidan mai unguwa, su din ga kaiwa
sun komowa, suna ɗan zagaywa a layin gidan viper, idan suka ga wani abu da ba
su yadda da shi ba, su sanar masa.
Suka cigaba da kaiwa suna komowa a hukumar hana sha da
fataucin miyagun ƙwayoyi, amma su ma ba su samu ganin Viper ba, suka ce sai dai
idan sun kai shi wurin jami'an tsaro su je can su ganshi.
Hankalin Jauhar ya ƙara mummunan tashi, ta rasa in da za ta
saka ranta ta ji daɗi.
Ta sake amfani da wayarta, ta kira walid a waya, da yake sun
ce kar ta sake zuwa hukumar, ta bari za su din ga zuwa su.
Ta duba wayar kaf, babu sunan wani mutumin kirki a ciki,
balle tayi tunanin akwai lambar wani ɗan gidansu, ta kira duk sai sunayen
su Liti da ire-iren su.
Sai kuma ta fara tunanin ko ba shi da kowa ne? Amma da ba
shi da kowa ai ba zata ga kakarsa ba, kuma an nuna mata Rahila ranar da aka yi
bikinsu Anty Zakiyya ta ce mata wai babarsa ce, amma tana tantama tun da aka yi
auren, bai taɓa kai ta gidansu ba, kuma babu wani wanda ya zo daga gidan.
Walid suka Kuma dawowa suna rarrashin ta, a kan suna ta
ƙoƙarin ganin ya fito, ta gaza haƙuri ta ce "Dan Allah to ina ne gidansu,
yakamata ace sun sani"
Walid ya ce "Taɓ ke 'yan gidan na su da suna ta tashi,
da baki gansu ba, ki manta da maganar su kawai ki cigaba da addu'a".
Ta ce "Amma kamar yakamata a gaya musu halin da yake
ciki, ko ba za su yi komai a kai ba".
Walid zai yi magana, liti ya ce "Bari na kwatanta miki
gidan na su" yayi mata kwatance sannan suka yi mata sallama suka tafi.
Liti ya ce "A irin wannan yanayin da take ciki, idan ba
ka kwatanta ba sai ta tsaneka ai, idan ta je ta ganewa idonta shikenan"
"Haka ne, amma ka san wannan matsiyaciyar matar gidan
na su ba mutunci gareta ba, kar ta ƙara mata zafi". Suka cigaba da
tattaunawa.
Kusan kwanaki bakwai da kama Al'amin, idan ka ga jauhar sai
ka ce tayi jinyar shekaru, duk ta ƙare ta fita hayyacinta.
'yan sana'oin ma ba ta iyawa, saboda tunani da damuwa.
Liti ya zo da safe, tana falo tana karatun Alkur'ani, ta ga
kiran waya a wayar Viper, ta tashi ta fita ya ce "Sako hijjabinki mu je,
sun bawa 'yan sanda shi, idan Allah ya taimake mu, wataƙila mu ganshi"
cikin tsananin zumuɗi, ta yafo mayafinta, ta rufe gidan suka tafi.
Sai dai da suka je ɗin ma, tsugono ba ta ƙare ba, dan sun fi
ƙarfin awa biyu, walid da liti suna safa da marwa, da faɗi tashin su ga
Al'amin, Jauhar addu'a kawai take yi, tun da ta ga haka ta san lamarin ba
ƙarami ba ne.
Da ƙyar aka ce za su ganshi, aka tafi da wasu wani wuri,
suka jira a reception ɗin sashen.
Babu tsammani ta ɗaga kai ta ga yana tahowa, yana ɗingisa
ƙafa, cikin hanzari ta miƙe tsaye ta zuba masa ido, kansa a ƙasa jami'an tsaro
sun taso shi a gaba, su liti ma miƙewa suka yi tsaye, da ya kusantota sai ta ga
jikinsa duk alamar duka, gefen fuskarsa a kumbure, haka wuyansa, shirt ɗin
jikinsa tayi datti, duk busasshshen jini, take jikinta ya hau tsuma cikin
tashin hankali.
Ya zo ya nemi wuri ya zauna kamar basarake, gabansa ta
ƙarasa cikin tashin hankali muryarta na rawa ta ce "Master, dukanka suke
yi haka?"
"Maza wai meyafaru ne? Me ka yi haka aka kawo ka
nan?" Walid ya tambaye shi cikin damuwa.
Jauhar ta ce 'Yallaɓai, dan Allah ku sake shi, dan Allah ku
yi haƙuri ba zai ƙara ba, wallahi kayan da ku ka gani a gidan lafina ne, bai
san da su ba, dan Allah ku yi haƙuri ku sake shi"
Ɗaya daga cikin 'yan sandan ya kalleta ya ce "Yarinya
yayanki ba ya ji, ba zamu sake shi ba, wanda aka kama da cocaine ki ke cewa a
saki ba shi da laifi? For more than 7days ya amsa laifinsa yaƙi, ga kaya an
kama shi da shi, yayi magana yaƙi kamar dutse"
Gaba ɗaya sak suka yi suna kallon ɗan sandan.
"Wace irin cocaine kuma? Ka ga malam ba ma son rainin
wayo, haba kai tare fa muke sabgar nan da shi, a gidan uwar wa zamu ga cocaine ɗin?"
Walid ya yi maganar a matuƙar fusace.
Cikin tsawa wani ya ce "Kai ka san a ina ka ke?"
"Na sani mana, ai ba lahira ba ce, balle ace mutum ta
sa ta ƙare, ƙarshen abun dai ku kashe mutum, kai da muna harka da cocaine zaku
ganmu a haka ne?"
Jauhar ta yadda sai hali ya zo ɗaya ake abota, daga Al'amin
har abokansa ba su da tsoro.
Fashewa ta yi da kuka ta ce "Wallahi Yallaɓai zan iya
rantsewa ba ya ta'amalli da cocaine, bai san ma in da zai same ta ba".
"Yayi bayani da bakinsa mana"
Cikin hanzari ta koma wurinsa, ta ce "Dan Allah Master
ka yi musu magana ko zasu ƙyale ka mu tafi, ka gaya musu ba taka ba ce ba,
laifina ne"
Yadda ginin wurin ba ya motsi, balle yayi magana haka
Al'amin yayi kirim a wurin.
"Dalla malam ka yi musu bayani, ka gaya musu ba ka
ta'amalli da ita kar su yi ta tila maka na jaki a banza su nakasa ka"
Walid yayi maganar cikin ƙunar rai, dan ya san ƙage kawai aka yi wa Al'amin.
Liti ya ce "Kai ma ka san ba zai yi ba, wasu lokutan
zuciya in dai irin ta shi ce ba ta yi ba"
Jauhar ta riƙe hannunsa za ta yi magana, sai dai jikinsa
kamar wuta Saboda zafi, sai yanzu ta tuna bai gama warkewa ba aka kama shi,
durƙushewa tayi a gabansa ta cigaba da kuka.
"Lokacinku yayi, zaku iya tafiya"
Liti ya ce "Ko ba ku ce ba zamu tafi, kowa yayi na gari
dai kansa ya yi wa"
Al'amin ya miƙe tsaye, ya saka hannu ɗaya ya ɗagata daga
durƙushen da take, ya juya zai koma, ta saka ƙarfinta ta rirriƙe shi tana kuka.
"Ke wai meye haka, da ki ka samu aka bari ki ka
ganshi" ɗan sandan ya daka mata tsawa.
"Wallahi sai dai ku rufe mu tare, ni ba zan tafi ba,
wai ya ake so na yi ne? Ya zan yi ko ina babu daɗi, ni komai nawa ba sa'a. Na
gaya muku ba shi da laifi, amma dukansa ku ke yi, tayaya hankalina zai kwanta
idan na tafi? Ba laifinsa ba ne wallahi, laifina ne na karɓi abu daga hannun
wanda ban sani ba dan Allah ku ƙyale shi"
Matsanancin tausayin da jauhar ta bawa liti, ya sanya ya
fice ya bar wurin, kuka take iya ƙarfinta, Al'amin har mamaki yake yi,
tsakaninsa da ita ba wata shaƙuwa ko kulawa ta musamman amma idan abu ya same
shi, gaba ɗaya sai ta rikice.
Walid tsayawa yayi ya ga viper zai rarrasheta ko kuma
ƙasaitar zai tsaya ya cigaba, da kuwa ko 'yan sandan za su rufe shi, sai ya
zage shi.
Ɗaya daga jami'an tsaron yayo kan jauhar, da nufin ya ɓanɓareta
ta ƙarfin tsiya, su mayar da Viper, cikin hanzari ya ja baya da ita a jikinsa,
ya ɗaga masa hannu yana ƙara tsuke fuska.
Ya saka hannu, ya ɓanɓareta daga jikinsa, ya riƙe
hannayenta, gaba ɗaya kammnin fuskarta sun canza saboda idanunta sun kumbura
sosai ta koma pink saboda kuka.
Ya sunkuyo dai-dai fuskarta ya ce "Kin kusa fara exam,
ki yi karatu sosai, kar ki zauna zaman shiriritar nan, ki yi ƙoƙari ki yi
karatu ki zama lawyer ko likita, ko dan saboda fitinannen mijinki, ki gaida
mini da kwaɗinki da ƙadangaru idan kin koma gida" tana jin yadda jikinsa
yake fitar da hucin zafi da warin datti, kwana bakwan nan babu alamar wanka ko
wadataccen abinci a tare da shi.
Ya kama kafaɗarta, ya saita ta hanyar fita ya ce "Kar
ki sake zuwa wurin nan saboda ni" ya kalli walid ya nuna masa Jauhar, ya
yi masa wata inkiya, ya juya suka mayar da shi.
Suka fito tana kuka, liti ya girgiza kai ya ce "Wallahi
Mutanen nan 'yan wuta ne"
Walid ya ce "Kai wannan hurumin Ubangiji ne, amma ko
dan hakkin yarinyar nan Allah sai ya kama su, a gidan uwasu zai ga cocaine ɗin,
wallahi ƙila su suka zo da abar su suka saka masa"
"Zasu aikata ai ba tsoron Allah suke yi ba" sun yi
gaba suna ta surutu suna zage-zage da tsine-tsine.
Suka nemi jauhar suka rasa, suka waiwaya, tana bakin ƙofar
in da suka baro, ta zauna dirshan tana matsar hawaye.
Liti ya ce "Taɓ lallai sabga da mata sai haƙuri, wannan
ko mutuwa yayi abun da za ta yi kenan"
Walid ya ce "Sai an yi mata uzuri, ba ta saba ganin
wannan tashin hankalin ba, ina zuwa".
Ya koma da baya wurinta, ya zauna ya din ga rarrashinta,
tare da ba ta tabbacin Aminu zai fita.
Cikin kuka ta ce "Ba ma fa shi da lafiya, zazzaɓi ne a
jikinsa"
"Ki yi haƙuri, Allah zai bashi lafiya"
Ta sake cewa "To yanzu daga nan me za su yi masa?"
"Wallahi ba mu sani ba, amma zamu cigaba da bibiya in
sha Allah, sai mun ga abun da ya ture wa buzu naɗi" da ƙyar ta taso, suka
kaita har gida, Walid ya ba ta kuɗi, ta ce ba zata karɓa ba, sai da ya ce mata
Al'amin ne ya ce ya bata sannan ta karɓa.
Har ta shiga falo, aka buga mata ƙofa, ta dawo ta buɗe, ta
ga Malam lawan baban su halimatu a tsaye.
Ta durƙusa ta gaishe shi, ya ce "Wato duk na san ke da
mijinki, kuna jin haushina, amma ni duk in da gaskiya take sai na faɗa. Ke
yanzu ki ji da halin da mijinki yake ciki, amma kin zo kina tara mana maza a
layi, kusan kullum sai sun zo, shi fa aure abu ne mai daraja da
muhimmanci".
Jiki a sanyaye ta ce "Tara maza kuma?"
"Eh mana, wannan da ku ke fita tare da su ku dawo,
muharraminki ne?"
Kalmar ta yi mata nauyi sosai, amma ta dake ta ce
"Aboknsa ne, su ne suke taimaka mini a kan case ɗin sa"
"To ke me yayi miko zafi? Ki koma gidanku mana, idan ya
fito kya dawo, ko ma ki haƙura da auren, da kyanki da ƙuruciyarki nan da nan
wani zai aureki, shi kuma ya cigaba da shashancinsa".
Ta ce "To na gode sosai"
"Ai gara dai ki san abun yi, ni Allah ya sa ma ba
iyayenki ki ka bujirewa a kansa ba, Allah yake jarabatarki ba" gaba ɗaya
sai ta ji kimarsa ta zube a idonta.
Jauhar ta kama Alƙur'ani da da carbi, tayi ta Addu'a tana
gaya wa Allah.
Aka sake shafe kwana biyar, su liti suna yi mata yawo da
hankali, suka kuma hanata komawa wurinsa, sai su ce mata sun je yana lafiya
yana gaisheta.
Haka kurum ta ji a ranta ƙarya suke yi mata, ba tare da sun
sani ba, ta sake ɗaukar ƙafa ta tafi wurin 'yan sanda, har da abincinta ta tafi
da shi, sai dai suka tabbatar mata sun kai shi kotu, har alƙali ya aike da shi
gidan gyaran hali, zuwa lokacin da za a cigaba da shari'a.
Cikin tashin hankali ta tambaye su, zuwa yaushe zai fito.
Suka ce mata ta tafi kotun ta tambaya, suka din ga yi mata
wasa da hankali, har da wanda suka biyota da maganar lalata.
A ƙofar gida, ta tarar da su walid, sai jan ƙafa take da
ƙyar, ta ƙarasa.
Walid ya ce "Madam ina ki ka tafi ne, mun zo ba kya
nan?"
Ta kalleshi cike da karaya ta ce "Dama an kai shi
prison ba ku gaya mini ba?"
Liti ya ce "Komawa ki ka yi kenan, ke ana ta ɓoye miki,
dan kar ki tayar da hankalinki, shi muka zo gaya miki, sai da muka tsara yadda
zamu gaya miki, yadda ba zaki damu ba, amma kin tashi kin tafi kin jiyo wa
kanki damuwa"
Ta ce "To ya zan yi, na kasa jurewa".
Walid ya ce "Yanzu dai tun da kin riga kin je kin ji da
kanki, shikenan amma ki yi haƙuri zamu nemo wata hanyar mijinki zai fito in sha
Allah"
Jinjina musu kai kawai tayi, ta shiga gida. tuna da liti
yayi mata kwatancen gidan su Al'amin, kamar korarriya, ta sake ɗaukar hanya, ta
tafi unguwar su Al'amin tare da fatan Allah ya sa idan ta je gidan su Allah ya
sa a dace a samu hanyar fitar da shi.
Sai da ta haɗa da tambaya, sai dai gidan na su ba ɓoyayye
bane ba, mussaman ma sunansa da ya riga ya shahara sosai.
Sau biyu tana sallama aka amsa, mata wata matashiyar
budurwa, da zata girme mata ta leƙo ta amsa.
Ta ce "Ya aka yi?"
Jauhar ta yi murmushi ta ce "Baƙuwa ce"
Amira ta ce "Baƙuwa daga ina?"
Rahila ta ce "Amira ki bari ta shigo mana"
Ta bawa jauhar hanya, ta ƙarasa ta shiga falon da sallama.
Rahila na ganinta ta washe baki, cike da duniyanci ta ce
"Amrya ba kya laifi, ko kin kashe ɗan masu gida" jauhar ta zube har
ƙasa ta gaisheta.
"Lafiya ƙalau, zauna a kan kujera mana jauhar" ta
sunkuyar da kai tare da girgizawa ta ce "Nan ma ya isa"
"Amira matar Aminu ce fa, kawo mata ruwa dan
Allah" kallon banza ta yi wa jauhar, ta gyara zamanta ta cigaba da danna
waya.
Rahila ta ce "Ke fa 'yar wulaƙanci ce amira".
Jauhar ta ce "Ai a ƙoshe ma nake"
"Allah sarki, ya mijin naki, tun da aka yi auren ba ki
zo mana ba" tayi shiru tare da sunkuyar da kai tana murmushi.
"Bari yanzu babansu zai shigo, sai ku gaisa".
Amira ta saci kallon jauhar, kyakywar bafulatanar yarinya,
daga muryarta kawai zaka san ba ta da hayaniya, ita aka aurawa Al'amin.
Abbu ne yayi sallama suka amsa masa gaba ɗaya, ko da ya
shigo sau ɗaya jauhar ta kalle shi ta mayar da kanta ƙasa, babu in da Al'amin
ya bar kamanin mahaifinsa.
"Abbu ga 'yar ka fa, sirikarka matar Aminu"
Ya ce "Subhanallah" ya zauna yana faɗin
"Yarinyar kirki, tuba nake yi yakamata ace na zo gidan naku, tafiya ta
kama ni ne, ina ga yau kwanana huɗu da dawowa, kuma ina maganarku sosai
wallahi, dan Allah ki yi haƙuri"
"A'a babu komai, ai mu ne masu laifi, tuntuni yakamata
ace mun zo, ban san gidan nan ba ne shiyasa shi kuma bai kawo ni ba"
Rahila ta ce "Hmm, dama ya za ayi ya kawo ki, ai ko za
a shekara sai idan rashin mutuncin sa ne ya kawo shi" yanayin maganganun
da rahila tayi, ya tabattar mata da ba ita ce mahaifiyar Al'amin ba.
Abbu ya ce "Ina fatan dai ba wata matsala, ba yayi miki
wani abu na rashin kyautatawa?"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ba ya yi mini sai dai.."
sai kuma ta yi shiru.
Rahila ta yi farat ta ce "Sai dai me, ki faɗa ba wani
abu, ai mu duk iyayenku ne".
"Ƴan sanda ne suka zo mana cikin dare, suka kama shi
suka tafi da shi, naje na kuma zuwa anƙi sakinsa, wai suna zarginsa da
ta'amalli da hodar iblis".
Rahila ta ce "Taɓ! Ki ce shi likkafa ce ta cigaba a
harkar shaye-shayen har ya kai wannan matakin?"
Jauhar ta ce "A'a ba ya amfani da ita, wani ne ya kawo
ya ce a ajiye masa, ban san kowaye ba, su kuma suka zo amma wallahi ba shi da
laifi, shi ne na ce bari na zo, dan Allah baba ko da hanyar da za a bi a sako
shi, ba ma shi da lafiya wallahi, da na je dukansa suke yi, jikinsa duk shaidar
duka" ta ƙarasa maganar tana kuka, duk yadda ta so riƙe hawayen amma abu
ya gagara.
Rahila ta ce "Au dama shi ne dalilin zuwan naki? Sai da
matsala ta afku ki ka nemi gidan ubansa, in dai wannan ne ya saba, kina zaune
'yan iskan da suke bashi goyon bayan yin rashin mutunci za su saka a sake
shi".
Abbu ya ce "Ya isa haka rahila" ya kalli Jauhar ya
ce "Ki daina kuka yarinyar kirki, case da ya haɗa da irin wannan case ne
babba ba ƙarami ba, Al'amin ba ya jin magana ko kaɗan".
"Wallahi baba ba shi ya kawo su ba, ban taɓa ganinsa da
ita ba".
"Idan ma yana ta'amalli da ita, ba gaya miki zai yi ba
ai"
Abbu ya ce "Ki kwantar da hankalinki, idan da wata
matsala ki koma gidanku, zuwa lokacin da komai zai daidaita, zan je na ga abun
yi"
"Abbu ka san cocaine kuwa? Wallahi ka je suka fuskanci
belinsa ka ke son yi, za su iya haɗawa da kai, ka dai koma gefe ka taya su da
addu'a, duk masifar da ya janyo ta ƙare masa a kansa idan yana da rabo ya fito,
idan babu ya ƙarata a can".
Kalaman rahila suka yi wa jauhar zafi da nauyi, ba shiri ta
tashi ta ce "To bari na tafi sai anjima".
Rahila ta ce "Ki je gida ki yi ta addu'a, idan babu
dama ki koma gida, amma shigar mahaifinsa wannan case ɗin ba mafita bane ba,
kina zaune za a sako shi".
Abbu ya ce "Ki yi haƙuri kin ji, zai fito in sha Allah,
zan san abun yi"
"Ka daina saka mata rai da zaka yi wani abu fa, haka
kurum wani abu ya sameka gani ga 'ya'ya ka barmu"
Bayan tafiyar jauhar, Abbu ya ce "Rahila, anya ban yi
wauta ba da na biye miki aka aura wa yarinyar mutane Al'amin ba, kalli yadda
take cikin tashin hankali da damuwa fa".
"Wannan yarinyar fa da ka ke gani, ba a bar tausayi ba
ce ba, ko ka manta kangarewa iyayenta ta yi suka nemi maraba da ita?"
"Duk da haka rahila, ni fa tantama nake yi a kan
maganar nan, gaskiya ina ga zan jagoranci raba auren nan, Al'amin ba zai yi
hankali ba"
"Abbu ina ruwanka, dan Allah ka bar maganar yaran
nan"
Jauhar kuwa bayan ta fita, ba tare da tunanin komai ba, ta
nufi unguwar su, ta je ta samu baba, ko da wani abu da zai iya taimaka mata, ba
tare da tuna haɗarin da hakan ka iya haifarwa ba, kodayeke wanda yake cikin
ruwa ko takobi ka miƙa masa kamawa zai yi.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan
kitchen wnd suke available ba order ba??
Kina bukatar
adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??
Kiyi joining wnn
group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya
available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Sosai take sauri, tare da fatan Allah ya sa baba yana nan.
Sai dai tayi iya ƙoƙarinta wurin daidaita nutsuwarta, kafin
ta ƙarasa gidan.
Yamma ta fara yi, yaran gidan sun dawo, sun yi kaca-kaca da
shi, duk sun zubar da kayan makarantar su ko ina, ga uban wanke-wanke da aka
rasa mai zaman kawar da shi daga wurin.
'yan ƙananan yaran gidan ne suka fara murnar ga jauhar, ɗakin
mama ta shiga suka gaisa, ta kalleta ta ce "Lafiya na ganki yanzu? Wani
abun ne?"
Jauhar ta ce "Lafiya ƙalau wurin baba na zo".
"In ce ko dai lafiya, kuma ya san kin zo? Ki tashi ki
tafi kar ki saka makakken mijinki ya zo yayi mana tijara da tashin
hankali"
Anty ce ta leƙo falon ta ce "Jauhar ashe abun da ya
faru kenan?"
Jauhar ta kalleta ta ce "Anty dama kina nan ina
wuni?"
"Lafiya ƙalau, ashe kuma kama mijinki aka yi da hodar
iblis, abu bai yi daɗi ba".
Dammm! Ƙirjin jauhar ya buga, yaya aka yi anty ta san wannan
zancen, mama ta ce "Kamar yaya?"
"Yanzu muka yi waya da rahila, ta ce bata daɗe da barin
gidan ba, ta je musu wai an kama shi".
Wani abu ɗaci ya tsaye wa jauhar, kamar ta fashe da kuka, ta
ce "Ba ya ta'amalli da hodar iblis, rigima ce kawai ta haɗa su da wasu,
shi ne dai na je na sanar musu, kar ya zamana ba su sani ba"
"Dan ubanki ni zaki yi wa ƙarya dan ki kare mijinki, ai
rahila ba zata yi miki ƙarya ba"
Walida ta ce "Taɓ, Allah ya kiyashemu taɓewa, hodar
iblis abun ba arziki ai na zata a sara suka kawai ya tsaya ashe babban kai
ne"
Duk yadda ta so ta riƙe hawayenta ta kasa, ta fashe da kuka,
suka din ga aibata Al'amin, gashi ba ta tarar da baba a gida ba, babu alamar za
su tausaya mata, ko su rarrasheta, kawai ta tashi ta ɗauki jakarta tana kuka,
ta fice.
Hafsa ta ce "Allah sarki jauhara da tuni ana china ko
gidan Alhaji mu'azzam ana shan A.C" suka din ga dariya.
Ta kwashi ƙafa ta nufi gida, tare da ƙudirce wa ranta da
yardar Allah, babu abin da zai saka ta sake zuwa gidan nan da matsalarta,
ƙarshen ƙiyayya da tsana dai ana nuna mata a gidan nan.
Kamar daga sama ta ji an buga mata tsawa "Ke bamu hana
ki shigowa unguwar nan ba?"
Sai a lokacin ta tuna abun da ya faru, cikin tsoro ta kalli
mai yi mata tsawar, sai dai ta kasa magana, ta bishi da ido.
"Ba magana nake yi ba"
"Nawa ubanka ya bayar aka shimfiɗa unguwar da za a
hanata shigowa mahaifarta?" Ta ji wata muryar daban.
Ta kalli matashin yaron, guduma kenan ɗan gidan mai unguwa,
da su Walid suka bawa ragamar kula da gidan Al'amin da shige da ficen jauhar,
har ta je gidan su Al'amin ta taho nasu gidan yana biye da ita.
Saroro ta yi tana kallonsa, dan ba ta san shi ba.
"Waye kai? Meya kawo ka unguwar nan?"
Guduma ya nuna masa Jauhar, ya ce "Wannan, wallahi kana
taɓa ta zamu ɓalla ƙarfe a wurin nan, mu rabu salin alin" ɗayan ya ja da
baya ya basu hanya, guduma ya ce wa jauhar "Mu je"
Ita dai ba ta iya yi masa magana ba, ta cigaba da tafiya ita
yanzu gaba ɗaya hankalinta da lissafinta yana kan halin da take ciki a yanzu.
Misalin ƙarfe uku da rabi na dare, jirginsu ya sauka malam
Aminu Kano international airport, direba ya zo ɗaukarsa.
Duk da a gajiye yake, saboda doguwar tafiyar da ya yi,
hankalinsa da lissafin sa yana kan, ya ƙarasa gida garin Allah ya waye, ya je
ya ji ba'asin dalilin fasa aurensa da yarinyar da ya ƙallafa rai a kanta,
kullum cikin tunanin ta yake, kuma tun da aka ce, an fasa bashi ita, ya ji ya
ƙara ƙaunarta, ta shiga ransa fiye da yadda yake tunani.
***
Kwanaki kaɗan ya rage jauhar ta fara jarrabawa, amma ba ta
iya karanta komai, ga uniform ɗin ta, ga litattafanta sai dai ba ta da nutsuwar
da za ta yi karatu, duk ta ƙare tayi rama ga rashin abinci dama damuwar da take
ciki ba ta barinta ta ci abincin.
Walid sai da yayi mata faɗa a kan zuwanta gidansu ba tare da
saninsu ba, tare da jaddada mata mugunta da gaba mai tsanani da take tsakaninsa
da Al'amin.
Tana kwance a falo, maman halimatu ta shigo gidan, ta tarar
da ita a kwance cikin damuwa ta ce "Jauhar, rayuwa za ta yiwu a haka kuwa?
Yanzu da mutuwa yayi ba dole ki yi haƙuri ba, kin addabi kanki, kamar ko abinci
ma fa ba kya ci" kamar ta soso mata wurin da yake yi mata ƙaiƙayi, ta hau
rera kuka, ta zauna ta rungume ta ta din ga rarrashinta.
Ta ce "Sako hijjabinki mu je gidana, kya ɗan sake ki
sha iska, zaman kaɗaicin nan ba abun da zai amfana miki sai ɓacin rai"
Haka ta bi maman halimatu, dan ba ta da wani zaɓi face
hakan, ta zuba mata abinci ta bata, sai dai ta cakala ta bar shi ta ce ta
ƙoshi.
Halimatu ta zauna kusa da ita ta ce "Anty jauhar dan
Allah ki daina kuka, zaki yi rashin lafiya " tayi maganar tana goge mata
hawaye. Akwai shaƙuwa sosai a tsakanin jauhar da yaran layin, wasu ma ko iyayen
su ba ta sani ba, amma su tana hulɗa da su, ta yi wa matan kitso, ta koya musu
karatu idan tana da abinci ta ba su, ko 'yar alewa ko abun kusa da baka,
shiyasa suna son taruwa a gidan idan master baya nan, sai dai rashin walwala da
ba ta yi yanzu ya sanya duk suka watse suka daina zuwa.
Baban su halimatu ya dawo, dama juahar na tsakar gida, ta
gaishe shi ya amsa sama-sama, ya shige falo, ya fara ƙwalawa salamatu kira.
"Baban halimatu sannu da zuwa "
"Me matar mutumin nan take yi mini a gida? Haka kurum
da tsinannen kwashe-kwashenki, ki janyo mana masifa muna zaman lafiya"
Cikin takaici ta ce "Haba dan Allah, menene a ciki,
tana zaune ita kaɗai cikin damuwa shiyasa na ce ta shigo, amma ka san haka
kurum ba mai shige-shige ba ce ba".
"Ke ki ka sakata a damuwar da zaki cirota, ambulance
uwar taimako "
Jauhar na jin su sama-sama, ta tashi ta ɗauki mukullin
gidanta, ta fice ta koma gida.
Jauhar ta kama addu'a iya yin ta, su liti fafur sun ƙi gaya
mata kotun da ake yi wa Al'amin shari'a, kuma suka ƙi gaya mata prison ɗin da
yake.
Baba yana karyawa da safe, ya ga kiran waya da baƙuwar
lamba, ya ɗaga ya ɗan yi gyaran murya yayi sallma.
"Wa'alaikum Salam, barka da safiya baba".
"Yauwwa barka dai, da wa nake magana?"
"Alhaji mu'azzam ne baba, ina ƙofar gida na zo, na ce
Allah ya sa ba ka fita ba".
Jikin baba yayi sanyi, ya ce "Ahh ina nan ban fita ba
tukuna, ashe ka dawo"
"Eh baba na dawo"
"To gani nan"
Ya miƙe zai fita, mama ta ce "Ina zaka kuma kai da
waye?"
"Baƙo" ya bata amsa a taƙaice.
Ya fita tsakar gida, hafsa ta shirya za ta tafi makaranta ya
ce "Ke haryanzu baki tafi makarantar ba me ki ke yi?"
"Ba ni da lectures ne da wuri, shiyasa yanzu zan
tafi"
"To Allah ya tsare" ta amsa da amin.
Baba ya fito suka gaisa, ya ce "Malam mu'azzam ka dawo
ashe?"
Cikin girmamawa ya ce "Eh baba, na sameku lafiya?"
"Alhamdilillah"
"Masha Allah, baba tun ina china na samu wani labari,
hankalina duk bai kwanta ba, na yi iya ƙoƙarina wurin dawowa, baba ko wani
laifin na yi ka hana ni auren jauhar?"
Baba ya girgiza kai ya ce "Wallahi ko ɗaya, kawai dai
ka san matar wani ba ta auren mijin wata, Allah bai ƙaddara aurenku ba, ina mai
baka haƙuri, na yi maka laifi ban kyauta ba, da kuɗin aurenka a hannuna na
aurar da ita, amma ka yi haƙuri dan Allah"
A razane ya kalli Baba ya ce "Aure aka yi mata?"
Baba ya jinjina masa kai a sanyaye ya ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un"
Hafsa kuwa har ta sako kai za ta fita, ta hango Alhaji
mu'azzam, ta koma cikin gidan da gudu, ta samu mahaifiyarta a ɗaki ta ce
"Anty, saurayin nan na jauhar ne ya zo, Alhaji mu'azzam gashi can da baba
a waje"
A sukwane ta tashi ta ce "Haba dai?"
"Wallahi da gaske nake"
"To maza ɗauko kayayyakin nan ki yi amfani da su ki
fita kafin ya tafi"
Can kuwa Baba sai haƙuri yake bashi, yana yi masa nasiha,
dan shi bai san ma an yi mata aure ba sai yanzu, gaba ɗaya ya shiga damuwa,
aƙalla zai bawa jauhar shekara ashirin da wani abu, ya girmeta nesa ba kusa ba,
sai dai ta shiga ransa sosai da sosai, duk da ya sha yinƙurin ƙara aure a baya,
amma matarsa tana hanawa, bai taɓa shiga damuwa na rashin wata ba sai jauhar,
kamar ya zubar da hawaye haka yake ji.
Jiki a sanyaye ya ce "Shikenan baba babu damuwa, na
gode sosai da sosai, Ubangiji Allah ya basu zaman lafiya da zuriya ɗayyiba".
Baba ya amsa da "Amin"
Suka yi sallama, ya shiga motarsa amma ya kasa tuƙin, ya
kifa kansa a sitiring motar, yayi shiru ya ji gaba ɗaya duniyar tayi masa wani
iri, babu irin zargin da bai kawo a ransa ba, na dalilin hana shi auren jauhar.
"Malam ya dai" da sauri ya ɗago kansa ya ce
"Jauhar"
"Ba ita ba ce, yayarta ce, tun ɗazu na ganka a nan baka
tafi ba, lafiya?"
"Yauwwa Alhamdilillah, dan Allah in tambayeki
mana?"
"Ok, Allah ya sa na sani" tayi maganar tana sake
gyara tsayuwarta cikin iyayi.
"Ko kin san dalilin da ya saka aka fasa bani aurenta,
tun da kin ce ke yayarta ce"
"Eh to, rashin ji ta fara yi, baba ya yanke shawarar
aurar da ita kawai, tun da baka nan"
Alhaji mu'azzam ya ce "Wani irin rashin ji?"
"A tunaninka wane rashin ji mace za ta yi, a aurar da
ita babu shiri?"
Cikin matsanancin mamaki ya ce "Jauhar ɗin?"
Hafsa ta ce "Ita fa, ko dan kana ganinta a haka? Dama
ba sonka take yi ba, akwai wani saurayinta ɗan daba, da ta ƙallafa rai a kansa,
ta fara rashin ji, kawai baba ya aurar da ita, ai ka ga ba zai gaya maka haka
ba" yayi shiru yana kallon hafsa, kawai ya ji maganganun nata ba su shige
shi ba, ya gyaɗa kai ya ce "Shikenan, Allah ya basu zaman lafiya"
Ta ce "Amin, dan Allah ko zaka sauke ni a hanya, school
zan tafi ko a titi ne sai na sauka na samu abun hawa?"
Ya ce "Bakomai bisimillah"
Jauhar ta idar da sallar la'asar, ta ga kiran walid a wayar
Viper, ta tashi ta ɗaga da sauri, suka gaisa, ya ce "Wani tunani na yi,
akwai uban gidansa da muke yi wa aiki, ɗan majalisa ne, sai dai Viper ne kawai
yake iya samunsa kai tsaye, na ce ko wurin P.A ɗin sa zamu je, ki gaya masa dan
ni ba shiri muke yi da shi, na taɓa marinsa idan mu ka je da ke wataƙila su
saurareki".
Cikin ɗoki ta ce "To shikenan, Allah ya sa dai su fito
da shi ɗin" ya amsa mata da amin.
Hafsa kuwa cike da salo da kisisina, da tasirin sihiri, sai
da ta karɓi lambar Alhaji mu'azzam, har bakin department ɗin su ya kaita, sai
dai idan zai yi mata magana sai ya kirata da jauhar, sai dai hakan bai dameta
ba, lambarsa kawai da ya bata, ya sanya ta din ga jin kamar ta ma riga ta aure
shi an gama.
Tun safe jauhar ta shirya, ya din ga kiran wayar Walid da ta
liti, amma ba ta shiga, tun tana saka ran za su zo, har ta fara sarewa, sai
azahar walid ya zo, kamar ta yi masa kuka ta ce "Tun safe nake kiran
wayarku, ina jiranka amma shiru ba ta shiga"
Walid ya ce "Ai wayar nan ta sa ma kawo ta zaki
yi"
Cikin mamaki ta ce "Saboda me?"
"Akwai dalili, yanzu idan kin shirya ki zo mu je can
wurin P.A ɗin ki gaya masa, da mun je shiga zaki yi, mun gama magana da wani
yaronsa" ta ce "To"
Suna tafe tana yi masa magiyar, dan Allah ya kaita ta ga
master, amma ya ce "Shi fa ya ce kar a kuskura a kai ki, yanzu idan muka
kai ki tijara zai yi mana".
Cikin damuwa ta ce "Haushina yake ji, ba ya son ganina
ko?"
Ya ce "Gaskiya ba na ce ba, ya ce dai kar a kuskura a
kai ki, kuma ranar Litinin zaku fara jarrabawa, ki je ki fara"
Mamaki ne ya kama ta, ya aka yi ya san lokacin da za su fara
jarrabawa?
Tayi ajiyar zuciya ta ce "To yaya jikin sa ya
warware?"
Walid ya ce "Eh ya warke"
"Ina nan ina ɗan haɗa 'yan kayayyakin abinci, sai in
baka ka kai masa"
"Kar dai ki takurawa kanki"
Jauhar ta ce "Ban takura kaina ba, amma dan Allah idan
ka je ka ƙara bashi haƙuri, wallahi laifina ne ban gaya masa an kawo abun ba,
kuma mantawa na yi"
Ya ce "Manta kawai, dama Allah ya riga ya ƙaddara
faruwar hakan".
Suna zuwa ofishin, ba su wani sha wahala ba, aka shiga da
Jauhar, ta gaishe shi ya amsa mata, ya ɗan ƙare mata kallo ya ce "Kamar na
taɓa ganinki"
Jauhar ta ce "Eh, akwai ranar da na je wurin mijina, na
tarar ka je kai da yaya walid an fito da shi a police station".
"Oh matar mai zamani ce, Viper?"
Ta jinjina masa kai ta ce "Eh nice"
Ya ce "Allah sarki, ya gida ya fama da rigimammen
mijinki"
Tayi murmushi tana wasa da yatsun hannunta.
"Yaya aka yi?"
Jauhar ta sauke numfashi ta ce "Dama, mijin nawa aka
kama, har an kai shi prison an ƙi sakinsa, shi ne na ce bari na zo wurinka dan
Allah ko zaka yi wa honorable magana, ko za a fito da shi"
Ya girgiza kai ya ce "Al'amin ba zai canza hali ba, me
kuma yayi a wannan karon?"
"Ba laifinsa bane, abu aka kawo aka ce na ajiye masa,
ban san ko menene ba, kuma na manta ban gaya masa ba, jami'an tsaro suka zo
suka yi bincike cikin dare, suka kama shi, wai sun ga hodar iblis a cikin
kayan"
Cikin mamaki ya ce "Hodar iblis kuma? A ina ya
sameta?"
"Ai ba shi ne ya kawo ba, ba ya ta'amalli da ita"
"Taɓɗijan, a wannan karon case ɗin babba ne, bari na
kira honorable duk da ba ya gari".
Ya kira honorable Indabo, ya sakata a hansfree tana jin duk
abun da suke faɗa, suka gaisa. P.A ya ce "Honorable, mutumin ka fa ya
janyo babbar jagwal ga matarsa nan a gabana ta zo a taimaka mata a fito da
shi"
"Wa kenan?"
"Ma dogon zamani mana"
Indabo ya ce "Kuma dai? Me kuma yayi?"
"To wai hodar iblis ce, aka kama shi da ita?"
"What! Coacine? Yaron nan yana da hankali kuwa, a ina
ya samu coacine kuma?"
"To ina zan sani, matarsa dai ta ce ba laifinsa bane
ba"
"Please count me out of this please, haka kurum na je
fito da shi, 'yan adawa su sami na yi mini yarfe, ace nima safararta nake yi?
Dama dai wani rashin jin yayi ba wannan ba, ni fa dama Saboda aikina na cin zaɓe
siyasa dole sai da irinsu, shiyasa nake fito da shi, amma ban da haka meye haɗina
da shi, zan nemi wani ya cigaba da yi mini ayyukana ni babu ruwana"
P.A ya ce "A'a honorable, wani kaya fa sai amale,
wallahi ba kowane matashi ne yake da ƙwarin da yake da shi ba, kar ka yar da
shi wani ya ɗaka"
"Ka san dai yanzu bana gari ko, dan Allah ka bar ni, ni
yanzu lissafin siyasata na saka a gaba, idan ina buƙatar sa a gaba, na fito da
shi" ya kashe wayarsa.
P.A ya kalli Jauhar da jikinta yayi sanyi, mamaki ya cika
mata kai da zuciya, wato yana amfani da jini da lafiyar Al'amin ne kawai dan
cimma nasa burin, abun ya bata mamaki sosai da sosai.
"Madam, kin ji abinda honorable ya ce, amma ki yi
haƙuri zuwa ya dawo, mu gani zan cigaba da lallaɓa shi, kar ki damu da abubuwan
da ya faɗa, kansa ne ya ɗauki zafi, amma shi da Aminu ba ta ɓaci, in dai wannan
harkar ce, ba shi da sama shi".
Ba ta ce masa uffan ba, ta tashi ta fita, yanayin yadda ta
fito ne, ya tabbatar masa da akwia matsala.
Ya ce "Yaya? Wani abun yayi miki ko maganar banza yayi
miki, na shiga na ci ubansa"
Ta girgiza masa kai alamar a a.
"To meyafaru?"
"Honorable ɗin ya ce babu ruwansa, ba zai shiga maganar
ba saboda kar sunansa ya ɓaci" tayi maganar hawaye yana gangarowa daga
idanunta.
Walid ya yi shiru, tare da jinjina kai ya ce "Shikenan,
bakomai mu tafi"
Haka suka tafi duk jiki a sanyaye, ta ce "Yanzu
shikenan babu abun da za ayi? Haka zai cigaba da zama?"
"A'a zai fito, haryanzu ba a gama shari'ar ba ma, dole
za a nemi wata hanyar".
Jauhar ta ce "To shikenan, dan Allah ranar juma'a ka zo
ka karɓi kayan da na tara, sai ka kai masa".
Walid ya ce "Shikenan, in sha Allah, amma kar ki je ki
saka damuwa a ranki, idan da wata matsala, ki kira ni a wayarki"
Ta girgiza kai ta ce "Bani da waya"
"To ki ara a ta maƙwabta, barinki da wayarsa akwai
matsala, haka ya karɓe wayar Viper ya tafi da ita.
Ta cigaba da faɗi tashi, wasila ta din ga aiko mata da
abinci, sai dai sam jauhar ba ta son hakan.
Aka fara exams, sai dai ba ta iya mayar da hankali wurin yin
wani abun kirki, wataran kuɗin motar ma gagararta yake yi.
Sai dai tana iya ƙoƙarin ta wurin aro jarumta, da ɓoye
damuwarta, idan ta shiga cikin 'yan uwanta ɗalibai.
Sannu a hankali ta fito daga harabar makarantar, ta tarar da
yaya saifu.
Murmushi ta yi ta ce "Yaya saifu, kai ne?"
Ya ce "Eh, hau babur ɗin na kai ki gida" cikin
murna ta ƙarasa ta rirriƙe shi ta hau, ta ce "Na zo gida sau biyu ban same
ka ba".
"Yau ai gani, mu je gidan naki".
Ya ja babur ɗin, ta ce "Allah ya sa ba laifi na yi maka
ba, na ganka kamar ranka a ɓace".
Yayi mata shiru, suka ƙarasa gidanta, ta buɗe musu suka
shiga.
Ta kawo masa ruwa a jug, dan na rijiya yanzu take sha, ko kuɗin
sayen ruwa ba ta da shi.
"Waliyiyya"
"Na'am yaya saifu"
"Meyafaru da mijinki?" Tayi shiru ta ƙi magana.
"Ki yi mini bayani ina jinki"
Kawai ta fashe da kuka, yayi mata shiru tayi mai isarta, ya
koma kusa da ita ya zuba mata ido ya ce "Jauhar, wani irin zama ki ke yi a
gidan nan, na san akwai ƙalubale da ki ke fuskanta a gidanmu, amma atleast ai
ko ni kya gayawa, sai ji na yi ana zancen an kama shi da cocaine, a tsakar gida
ko baba ba ma bai sani ba, da yaya ki ke rayuwa ke kaɗai? Da yaya ki ke samun
abun da za ki ci?"
"Yaya saifu, ni cin abinci ko akasin haka bai dame ni
ba, fatana da burina ya fito, ba shi da laifi, ko a yaya yake na yadda shi
Allah ya zaɓa mini, ba ya dukana ba ya zagina. Ban san dalilin da ya sanya su
mama suka zaɓi na aure shi ba, na karɓi ƙaddarata, na je gidan ai, amma yanayin
karɓar da na samu na san ba zan yi nasara ba, kuma ban ma samu baba a gida
ba".
"Jauhar, a raba auren nan, ni ban ga alamar za a samu ɗa
mai ido ba a auren nan ba, rannan fa cewa aka yi sai da ya zo ya tafi da ke,
'yan daba za su saraki, wace irin rayuwa ce haka? Ko khul'i ayi a raba auren
nan"
Tayi shiru ta sunkuyar da kanta.
"Yaya ki ka yi shiru? Ko kina son shi ne?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To kin amince a raba auren?" Nan ma ta girgiza
kai.
"Ki yi mini magana jauhar, idan kin amince in yi wa
baba magana, a raba auren nan"
"Dan Allah kar a raba, ni dai a fito mini da shi dan
Allah"
Saifu ya ce "Wai son shi ki ke yi ne?"
Cikin kuka ta ce "Idan aka raba auren za ace mini
bazawara"
"To a kanki aka fara? Ba sai ki koma makarantar ki ki
yi a tsanake ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Dan Allah ni dai yaya saifu kar a
kashe mini aure, duk abun da yake yi zai daina a hankali, sharri ake yi masa ba
ya ta'amalli da hodar iblis" saifu yayi shiru yana kallon ta, ya fara
tunanin any ba son shi take yi ba, ya ma kasa gane me take nufi.
"Shikenan, ƙyale baban ma, yanzu da an yi magana da
shi, sai ya gaya wa matansa, wace kotun ake yi masa shari'a? Akwai wani baban
abokina, sai na yi wa abokin nawa magana a san abun yi"
Cikin murna ta ce "Na gode sosai yaya, ban san wace
kotun ba ce ba, wai ya hana a kai ni, amma akwai lambar abokinsa, da tare muke
up and down, ka ga daga nan ma sai mu je na ganshi".
"No, tun da ya ce kar ki je, ba sai kin je ba, duk abun
da ake ciki, zan din ga sanar miki, amma ki kwantar da hankalinki dan
waliyiyya, tun da kin na ce, ke uwar soyayya Allah ya bar ƙauna, amma wallahi
na tsani mijin nan naki"
Ta ce "Dan Allah ka daina faɗa, ba zan ji daɗi ba, a
din ga yi mana addu'a, ba na jin daɗi idan aka aibata shi"
Ya ce "Iyee lallai waliyiyya baki ya buɗe, ki na so dai
ki gaya mini ki na son mijinki maybe ma fiye da ni, to wallahi ki fi so na a
kansa"
Ta ɓoye fuskarta tana dariya ta ce "Wallahi yaya
tausayi yake bani kawai, idan aka raba auren nan, akwai damuwa, kuma ina saka
ran komai zai zama tarihi in sha Allah"
Ya ce "Tafi can, kya ma faɗi gaskiya, kuma ko ba yau
ba, kar ki sake wani ma ya san na shiga maganar nan, ai mu na da alfarma
shige-shige yayi mana rana" jauhar tayi murmushi, ya bata kuɗi ya tafi.
Kusan sati ba ta ƙara jin ɗuriyar saifu ba, ga babu su walid
balle ta ji wani abu daga gare su, sai da ta ari wayar wasila, ta kira walid ta
ce ya zo ya karɓi kayan da zai kai wa master.
Ta saya masa maggi, mai, da sauran ɗan abun da ba a rasa ba,
da prisoner zai buƙata.
Ya karɓa tare da ƙara bata haƙuri, da ba ta tabbacin, yana
nan suna ƙoƙarin fitar da Mijinta.
Saifu ya sake komawa makaranta ya sameta, cikin murna ta hau
tambayar sa, ya ake ciki?.
"Ke mijinki abun da aka yi masa shiri ne kawai, na
bibiyi abun ni da abokina, zaki sha mamaki idan na gaya miki an yi wani mugun
sara a kan gaɓa, amma ba zan gaya miki ba, in je zaƙin soyayya ya ja ki ki gaya
masa ba idan ya fito, ki haddasa husuma, baban abokin nawa yayi magana, sun ce
ayi haƙuri ya ƙarasa wata ɗaya, kotu za ta wanke shi ya fito, ashirin da biyu
ga watan gobe za a sake shi"
"Wayyo Allah, yaya saifu kusan watanni uku fa kenan zai
yi a prison?"
"Au baki gode ba kenan?"
Jiki a sanyaye ta ce "A'a na gode sosai yayana,
Ubangiji Allah ya saka maka da gidan aljanna, to zaka kai ni na ganshi?"
Ya ce "Amin ya rabb, yana prison na ciki gari, kuma ban
ce ki je ba, kar ki kuskura ki je, kin ji na gaya miki"
"Amma yaya meyasa?"
Saifu ya ce "Saboda haka na ce miki, kuma ke ma kin ce
ya ce kar ki je, kar kuma gaya wa wani gashi zai fito shi ma bai sani ba".
Jauhar ta ce "To shikenan, na gode Allah ya saka maka
da mafificin alkhairi"
"Amin ki koma gida, ki cigaba da exams ɗinki, idan da
wani abu, ki neme ni a waya, kar ma ki sake zuwa gidan nan da wani batu a kan
aurenki, tun da ki na son abun ki ki yi zamanki"
Tayi murmushi ta ce "Ban san menene son ba dai yaya,
ban san me ake ji ba, da farko dai na san ina jin tsoronsa sosai, amma yanzu
kuma tausayin sa nake ji"
Yayi murmushi ya ce "Ga kuɗin mota, ki sauka lafiya,
yau ba zan je gidanki ba"
Ta karɓa cikin murna tayi masa godiya, ta tafi gida.
Ta ji sanyi a ranta jin cewar zai fito, sai dai tana cikin
damuwa na rashin sanin halin da yake ciki, ya ji sauƙi ko kuwa, yana samun
abinci ko kuwa?"
Da ta samu kuɗi, take yin sayayya, ta ari waya ta kira
walid, ya zo ya karɓa ya kai masa.
Sana'a tuƙuru jauhar kamar tayi ƙwace, dama ga azumi yana
gabatowa, ana samun ɗinkuna, dan haka tana samun aikin stone da beads, sai dai
ba ta iya sakin jiki ta kashe kuɗin, saboda akwai abun da take son yi.
Ita ce mayafai, har da su kantu da aya, haka take saya
ta soya ta ɗaura a leda yara na saya.
Har guga take karɓar kayan maman halimatu, ta ta da ta yara
tayi mata, ta biyata.
Sana'oi kamar zata yi ƙwace, duk da ana yi mata mugunta a
kan wasu abubuwan, mussman gidan mai ɗinki, da take yi mata aikin stone ta fara
yi mata mugunta.
Ta ƙara tsananta addu'a, da roƙon Allah, a kan Allah ya kuɓutar
mata da mijinta, ya shirya mata shi.
Rana ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, saura
kwanaki biyu Al'amin ya fito, jauhar ta yi ta gyaran gida, ta ƙara gyara masa ɗakinsa.
Ranar da zai fito ɗin, ta yi girki, sai dai kuɗin hannunta
ba su da yawa, duk mutane sun riƙe mata kuɗi, dan muɗin hannunta ba za su ishe
su kuɗin mota ba ita da shi.
Ta dafa ruwa ta zuba a flask, ta shirya tun ƙarfe tara, ta
tafi prison ɗin, gashi damuna ta ja baya, an fara wani irin sanyi mai ratsa
jiki.
Ta nemi shiga cikin prsion ɗin, aka ce mata a waje za ta
jira, idan yau za a sake shi, za ta ganshi ya fito.
Tana nan zaune, wasu suna ta fitowa, 'yan uwansu suna ta
murna, sai dai shiru-shiru ba ta ganshi ba.
Nan hankalinta ya tashi, ta sake nufar wurin masu gadin ta
ce "Wai haryanzu ban ganshi ba, kuma yau aka ce mini za a sake shi"
"Waye ya ce miki za a sake shi?" Wani gandiroba ya
tambayeta.
"Yayana ne"
"Yayan naki alƙali ne? Ko shi ya kawo shi nan ɗin,
wanda zamu saki kenan yau sun gama fitowa"
"Innalillahi na shiga uku" ta faɗa a raunane.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan
kitchen wnd suke available ba order ba??
Kina bukatar
adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??
Kiyi joining wnn
group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya
available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Sosai take sauri, tare da fatan Allah ya sa baba yana nan.
Sai dai tayi iya ƙoƙarinta wurin daidaita nutsuwarta, kafin
ta ƙarasa gidan.
Yamma ta fara yi, yaran gidan sun dawo, sun yi kaca-kaca da
shi, duk sun zubar da kayan makarantar su ko ina, ga uban wanke-wanke da aka
rasa mai zaman kawar da shi daga wurin.
'yan ƙananan yaran gidan ne suka fara murnar ga jauhar, ɗakin
mama ta shiga suka gaisa, ta kalleta ta ce "Lafiya na ganki yanzu? Wani
abun ne?"
Jauhar ta ce "Lafiya ƙalau wurin baba na zo".
"In ce ko dai lafiya, kuma ya san kin zo? Ki tashi ki
tafi kar ki saka makakken mijinki ya zo yayi mana tijara da tashin
hankali"
Anty ce ta leƙo falon ta ce "Jauhar ashe abun da ya
faru kenan?"
Jauhar ta kalleta ta ce "Anty dama kina nan ina
wuni?"
"Lafiya ƙalau, ashe kuma kama mijinki aka yi da hodar
iblis, abu bai yi daɗi ba".
Dammm! Ƙirjin jauhar ya buga, yaya aka yi anty ta san wannan
zancen, mama ta ce "Kamar yaya?"
"Yanzu muka yi waya da rahila, ta ce bata daɗe da barin
gidan ba, ta je musu wai an kama shi".
Wani abu ɗaci ya tsaye wa jauhar, kamar ta fashe da kuka, ta
ce "Ba ya ta'amalli da hodar iblis, rigima ce kawai ta haɗa su da wasu,
shi ne dai na je na sanar musu, kar ya zamana ba su sani ba"
"Dan ubanki ni zaki yi wa ƙarya dan ki kare mijinki, ai
rahila ba zata yi miki ƙarya ba"
Walida ta ce "Taɓ, Allah ya kiyashemu taɓewa, hodar
iblis abun ba arziki ai na zata a sara suka kawai ya tsaya ashe babban kai
ne"
Duk yadda ta so ta riƙe hawayenta ta kasa, ta fashe da kuka,
suka din ga aibata Al'amin, gashi ba ta tarar da baba a gida ba, babu alamar za
su tausaya mata, ko su rarrasheta, kawai ta tashi ta ɗauki jakarta tana kuka,
ta fice.
Hafsa ta ce "Allah sarki jauhara da tuni ana china ko
gidan Alhaji mu'azzam ana shan A.C" suka din ga dariya.
Ta kwashi ƙafa ta nufi gida, tare da ƙudirce wa ranta da
yardar Allah, babu abin da zai saka ta sake zuwa gidan nan da matsalarta,
ƙarshen ƙiyayya da tsana dai ana nuna mata a gidan nan.
Kamar daga sama ta ji an buga mata tsawa "Ke bamu hana
ki shigowa unguwar nan ba?"
Sai a lokacin ta tuna abun da ya faru, cikin tsoro ta kalli
mai yi mata tsawar, sai dai ta kasa magana, ta bishi da ido.
"Ba magana nake yi ba"
"Nawa ubanka ya bayar aka shimfiɗa unguwar da za a
hanata shigowa mahaifarta?" Ta ji wata muryar daban.
Ta kalli matashin yaron, guduma kenan ɗan gidan mai unguwa,
da su Walid suka bawa ragamar kula da gidan Al'amin da shige da ficen jauhar,
har ta je gidan su Al'amin ta taho nasu gidan yana biye da ita.
Saroro ta yi tana kallonsa, dan ba ta san shi ba.
"Waye kai? Meya kawo ka unguwar nan?"
Guduma ya nuna masa Jauhar, ya ce "Wannan, wallahi kana
taɓa ta zamu ɓalla ƙarfe a wurin nan, mu rabu salin alin" ɗayan ya ja da
baya ya basu hanya, guduma ya ce wa jauhar "Mu je"
Ita dai ba ta iya yi masa magana ba, ta cigaba da tafiya ita
yanzu gaba ɗaya hankalinta da lissafinta yana kan halin da take ciki a yanzu.
Misalin ƙarfe uku da rabi na dare, jirginsu ya sauka malam
Aminu Kano international airport, direba ya zo ɗaukarsa.
Duk da a gajiye yake, saboda doguwar tafiyar da ya yi,
hankalinsa da lissafin sa yana kan, ya ƙarasa gida garin Allah ya waye, ya je
ya ji ba'asin dalilin fasa aurensa da yarinyar da ya ƙallafa rai a kanta,
kullum cikin tunanin ta yake, kuma tun da aka ce, an fasa bashi ita, ya ji ya
ƙara ƙaunarta, ta shiga ransa fiye da yadda yake tunani.
***
Kwanaki kaɗan ya rage jauhar ta fara jarrabawa, amma ba ta
iya karanta komai, ga uniform ɗin ta, ga litattafanta sai dai ba ta da nutsuwar
da za ta yi karatu, duk ta ƙare tayi rama ga rashin abinci dama damuwar da take
ciki ba ta barinta ta ci abincin.
Walid sai da yayi mata faɗa a kan zuwanta gidansu ba tare da
saninsu ba, tare da jaddada mata mugunta da gaba mai tsanani da take tsakaninsa
da Al'amin.
Tana kwance a falo, maman halimatu ta shigo gidan, ta tarar
da ita a kwance cikin damuwa ta ce "Jauhar, rayuwa za ta yiwu a haka kuwa?
Yanzu da mutuwa yayi ba dole ki yi haƙuri ba, kin addabi kanki, kamar ko abinci
ma fa ba kya ci" kamar ta soso mata wurin da yake yi mata ƙaiƙayi, ta hau
rera kuka, ta zauna ta rungume ta ta din ga rarrashinta.
Ta ce "Sako hijjabinki mu je gidana, kya ɗan sake ki
sha iska, zaman kaɗaicin nan ba abun da zai amfana miki sai ɓacin rai"
Haka ta bi maman halimatu, dan ba ta da wani zaɓi face
hakan, ta zuba mata abinci ta bata, sai dai ta cakala ta bar shi ta ce ta
ƙoshi.
Halimatu ta zauna kusa da ita ta ce "Anty jauhar dan
Allah ki daina kuka, zaki yi rashin lafiya " tayi maganar tana goge mata
hawaye. Akwai shaƙuwa sosai a tsakanin jauhar da yaran layin, wasu ma ko iyayen
su ba ta sani ba, amma su tana hulɗa da su, ta yi wa matan kitso, ta koya musu
karatu idan tana da abinci ta ba su, ko 'yar alewa ko abun kusa da baka,
shiyasa suna son taruwa a gidan idan master baya nan, sai dai rashin walwala da
ba ta yi yanzu ya sanya duk suka watse suka daina zuwa.
Baban su halimatu ya dawo, dama juahar na tsakar gida, ta
gaishe shi ya amsa sama-sama, ya shige falo, ya fara ƙwalawa salamatu kira.
"Baban halimatu sannu da zuwa "
"Me matar mutumin nan take yi mini a gida? Haka kurum
da tsinannen kwashe-kwashenki, ki janyo mana masifa muna zaman lafiya"
Cikin takaici ta ce "Haba dan Allah, menene a ciki,
tana zaune ita kaɗai cikin damuwa shiyasa na ce ta shigo, amma ka san haka
kurum ba mai shige-shige ba ce ba".
"Ke ki ka sakata a damuwar da zaki cirota, ambulance
uwar taimako "
Jauhar na jin su sama-sama, ta tashi ta ɗauki mukullin
gidanta, ta fice ta koma gida.
Jauhar ta kama addu'a iya yin ta, su liti fafur sun ƙi gaya
mata kotun da ake yi wa Al'amin shari'a, kuma suka ƙi gaya mata prison ɗin da
yake.
Baba yana karyawa da safe, ya ga kiran waya da baƙuwar
lamba, ya ɗaga ya ɗan yi gyaran murya yayi sallma.
"Wa'alaikum Salam, barka da safiya baba".
"Yauwwa barka dai, da wa nake magana?"
"Alhaji mu'azzam ne baba, ina ƙofar gida na zo, na ce
Allah ya sa ba ka fita ba".
Jikin baba yayi sanyi, ya ce "Ahh ina nan ban fita ba
tukuna, ashe ka dawo"
"Eh baba na dawo"
"To gani nan"
Ya miƙe zai fita, mama ta ce "Ina zaka kuma kai da
waye?"
"Baƙo" ya bata amsa a taƙaice.
Ya fita tsakar gida, hafsa ta shirya za ta tafi makaranta ya
ce "Ke haryanzu baki tafi makarantar ba me ki ke yi?"
"Ba ni da lectures ne da wuri, shiyasa yanzu zan
tafi"
"To Allah ya tsare" ta amsa da amin.
Baba ya fito suka gaisa, ya ce "Malam mu'azzam ka dawo
ashe?"
Cikin girmamawa ya ce "Eh baba, na sameku lafiya?"
"Alhamdilillah"
"Masha Allah, baba tun ina china na samu wani labari,
hankalina duk bai kwanta ba, na yi iya ƙoƙarina wurin dawowa, baba ko wani
laifin na yi ka hana ni auren jauhar?"
Baba ya girgiza kai ya ce "Wallahi ko ɗaya, kawai dai
ka san matar wani ba ta auren mijin wata, Allah bai ƙaddara aurenku ba, ina mai
baka haƙuri, na yi maka laifi ban kyauta ba, da kuɗin aurenka a hannuna na
aurar da ita, amma ka yi haƙuri dan Allah"
A razane ya kalli Baba ya ce "Aure aka yi mata?"
Baba ya jinjina masa kai a sanyaye ya ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un"
Hafsa kuwa har ta sako kai za ta fita, ta hango Alhaji
mu'azzam, ta koma cikin gidan da gudu, ta samu mahaifiyarta a ɗaki ta ce
"Anty, saurayin nan na jauhar ne ya zo, Alhaji mu'azzam gashi can da baba
a waje"
A sukwane ta tashi ta ce "Haba dai?"
"Wallahi da gaske nake"
"To maza ɗauko kayayyakin nan ki yi amfani da su ki
fita kafin ya tafi"
Can kuwa Baba sai haƙuri yake bashi, yana yi masa nasiha,
dan shi bai san ma an yi mata aure ba sai yanzu, gaba ɗaya ya shiga damuwa,
aƙalla zai bawa jauhar shekara ashirin da wani abu, ya girmeta nesa ba kusa ba,
sai dai ta shiga ransa sosai da sosai, duk da ya sha yinƙurin ƙara aure a baya,
amma matarsa tana hanawa, bai taɓa shiga damuwa na rashin wata ba sai jauhar,
kamar ya zubar da hawaye haka yake ji.
Jiki a sanyaye ya ce "Shikenan baba babu damuwa, na
gode sosai da sosai, Ubangiji Allah ya basu zaman lafiya da zuriya ɗayyiba".
Baba ya amsa da "Amin"
Suka yi sallama, ya shiga motarsa amma ya kasa tuƙin, ya
kifa kansa a sitiring motar, yayi shiru ya ji gaba ɗaya duniyar tayi masa wani
iri, babu irin zargin da bai kawo a ransa ba, na dalilin hana shi auren jauhar.
"Malam ya dai" da sauri ya ɗago kansa ya ce
"Jauhar"
"Ba ita ba ce, yayarta ce, tun ɗazu na ganka a nan baka
tafi ba, lafiya?"
"Yauwwa Alhamdilillah, dan Allah in tambayeki
mana?"
"Ok, Allah ya sa na sani" tayi maganar tana sake
gyara tsayuwarta cikin iyayi.
"Ko kin san dalilin da ya saka aka fasa bani aurenta,
tun da kin ce ke yayarta ce"
"Eh to, rashin ji ta fara yi, baba ya yanke shawarar
aurar da ita kawai, tun da baka nan"
Alhaji mu'azzam ya ce "Wani irin rashin ji?"
"A tunaninka wane rashin ji mace za ta yi, a aurar da
ita babu shiri?"
Cikin matsanancin mamaki ya ce "Jauhar ɗin?"
Hafsa ta ce "Ita fa, ko dan kana ganinta a haka? Dama
ba sonka take yi ba, akwai wani saurayinta ɗan daba, da ta ƙallafa rai a kansa,
ta fara rashin ji, kawai baba ya aurar da ita, ai ka ga ba zai gaya maka haka
ba" yayi shiru yana kallon hafsa, kawai ya ji maganganun nata ba su shige
shi ba, ya gyaɗa kai ya ce "Shikenan, Allah ya basu zaman lafiya"
Ta ce "Amin, dan Allah ko zaka sauke ni a hanya, school
zan tafi ko a titi ne sai na sauka na samu abun hawa?"
Ya ce "Bakomai bisimillah"
Jauhar ta idar da sallar la'asar, ta ga kiran walid a wayar
Viper, ta tashi ta ɗaga da sauri, suka gaisa, ya ce "Wani tunani na yi,
akwai uban gidansa da muke yi wa aiki, ɗan majalisa ne, sai dai Viper ne kawai
yake iya samunsa kai tsaye, na ce ko wurin P.A ɗin sa zamu je, ki gaya masa dan
ni ba shiri muke yi da shi, na taɓa marinsa idan mu ka je da ke wataƙila su
saurareki".
Cikin ɗoki ta ce "To shikenan, Allah ya sa dai su fito
da shi ɗin" ya amsa mata da amin.
Hafsa kuwa cike da salo da kisisina, da tasirin sihiri, sai
da ta karɓi lambar Alhaji mu'azzam, har bakin department ɗin su ya kaita, sai
dai idan zai yi mata magana sai ya kirata da jauhar, sai dai hakan bai dameta
ba, lambarsa kawai da ya bata, ya sanya ta din ga jin kamar ta ma riga ta aure
shi an gama.
Tun safe jauhar ta shirya, ya din ga kiran wayar Walid da ta
liti, amma ba ta shiga, tun tana saka ran za su zo, har ta fara sarewa, sai
azahar walid ya zo, kamar ta yi masa kuka ta ce "Tun safe nake kiran
wayarku, ina jiranka amma shiru ba ta shiga"
Walid ya ce "Ai wayar nan ta sa ma kawo ta zaki
yi"
Cikin mamaki ta ce "Saboda me?"
"Akwai dalili, yanzu idan kin shirya ki zo mu je can
wurin P.A ɗin ki gaya masa, da mun je shiga zaki yi, mun gama magana da wani
yaronsa" ta ce "To"
Suna tafe tana yi masa magiyar, dan Allah ya kaita ta ga
master, amma ya ce "Shi fa ya ce kar a kuskura a kai ki, yanzu idan muka
kai ki tijara zai yi mana".
Cikin damuwa ta ce "Haushina yake ji, ba ya son ganina
ko?"
Ya ce "Gaskiya ba na ce ba, ya ce dai kar a kuskura a
kai ki, kuma ranar Litinin zaku fara jarrabawa, ki je ki fara"
Mamaki ne ya kama ta, ya aka yi ya san lokacin da za su fara
jarrabawa?
Tayi ajiyar zuciya ta ce "To yaya jikin sa ya
warware?"
Walid ya ce "Eh ya warke"
"Ina nan ina ɗan haɗa 'yan kayayyakin abinci, sai in
baka ka kai masa"
"Kar dai ki takurawa kanki"
Jauhar ta ce "Ban takura kaina ba, amma dan Allah idan
ka je ka ƙara bashi haƙuri, wallahi laifina ne ban gaya masa an kawo abun ba,
kuma mantawa na yi"
Ya ce "Manta kawai, dama Allah ya riga ya ƙaddara
faruwar hakan".
Suna zuwa ofishin, ba su wani sha wahala ba, aka shiga da
Jauhar, ta gaishe shi ya amsa mata, ya ɗan ƙare mata kallo ya ce "Kamar na
taɓa ganinki"
Jauhar ta ce "Eh, akwai ranar da na je wurin mijina, na
tarar ka je kai da yaya walid an fito da shi a police station".
"Oh matar mai zamani ce, Viper?"
Ta jinjina masa kai ta ce "Eh nice"
Ya ce "Allah sarki, ya gida ya fama da rigimammen
mijinki"
Tayi murmushi tana wasa da yatsun hannunta.
"Yaya aka yi?"
Jauhar ta sauke numfashi ta ce "Dama, mijin nawa aka
kama, har an kai shi prison an ƙi sakinsa, shi ne na ce bari na zo wurinka dan
Allah ko zaka yi wa honorable magana, ko za a fito da shi"
Ya girgiza kai ya ce "Al'amin ba zai canza hali ba, me
kuma yayi a wannan karon?"
"Ba laifinsa bane, abu aka kawo aka ce na ajiye masa,
ban san ko menene ba, kuma na manta ban gaya masa ba, jami'an tsaro suka zo
suka yi bincike cikin dare, suka kama shi, wai sun ga hodar iblis a cikin
kayan"
Cikin mamaki ya ce "Hodar iblis kuma? A ina ya
sameta?"
"Ai ba shi ne ya kawo ba, ba ya ta'amalli da ita"
"Taɓɗijan, a wannan karon case ɗin babba ne, bari na
kira honorable duk da ba ya gari".
Ya kira honorable Indabo, ya sakata a hansfree tana jin duk
abun da suke faɗa, suka gaisa. P.A ya ce "Honorable, mutumin ka fa ya
janyo babbar jagwal ga matarsa nan a gabana ta zo a taimaka mata a fito da
shi"
"Wa kenan?"
"Ma dogon zamani mana"
Indabo ya ce "Kuma dai? Me kuma yayi?"
"To wai hodar iblis ce, aka kama shi da ita?"
"What! Coacine? Yaron nan yana da hankali kuwa, a ina
ya samu coacine kuma?"
"To ina zan sani, matarsa dai ta ce ba laifinsa bane
ba"
"Please count me out of this please, haka kurum na je
fito da shi, 'yan adawa su sami na yi mini yarfe, ace nima safararta nake yi?
Dama dai wani rashin jin yayi ba wannan ba, ni fa dama Saboda aikina na cin zaɓe
siyasa dole sai da irinsu, shiyasa nake fito da shi, amma ban da haka meye haɗina
da shi, zan nemi wani ya cigaba da yi mini ayyukana ni babu ruwana"
P.A ya ce "A'a honorable, wani kaya fa sai amale,
wallahi ba kowane matashi ne yake da ƙwarin da yake da shi ba, kar ka yar da
shi wani ya ɗaka"
"Ka san dai yanzu bana gari ko, dan Allah ka bar ni, ni
yanzu lissafin siyasata na saka a gaba, idan ina buƙatar sa a gaba, na fito da
shi" ya kashe wayarsa.
P.A ya kalli Jauhar da jikinta yayi sanyi, mamaki ya cika
mata kai da zuciya, wato yana amfani da jini da lafiyar Al'amin ne kawai dan
cimma nasa burin, abun ya bata mamaki sosai da sosai.
"Madam, kin ji abinda honorable ya ce, amma ki yi
haƙuri zuwa ya dawo, mu gani zan cigaba da lallaɓa shi, kar ki damu da abubuwan
da ya faɗa, kansa ne ya ɗauki zafi, amma shi da Aminu ba ta ɓaci, in dai wannan
harkar ce, ba shi da sama shi".
Ba ta ce masa uffan ba, ta tashi ta fita, yanayin yadda ta
fito ne, ya tabbatar masa da akwia matsala.
Ya ce "Yaya? Wani abun yayi miki ko maganar banza yayi
miki, na shiga na ci ubansa"
Ta girgiza masa kai alamar a a.
"To meyafaru?"
"Honorable ɗin ya ce babu ruwansa, ba zai shiga maganar
ba saboda kar sunansa ya ɓaci" tayi maganar hawaye yana gangarowa daga
idanunta.
Walid ya yi shiru, tare da jinjina kai ya ce "Shikenan,
bakomai mu tafi"
Haka suka tafi duk jiki a sanyaye, ta ce "Yanzu
shikenan babu abun da za ayi? Haka zai cigaba da zama?"
"A'a zai fito, haryanzu ba a gama shari'ar ba ma, dole
za a nemi wata hanyar".
Jauhar ta ce "To shikenan, dan Allah ranar juma'a ka zo
ka karɓi kayan da na tara, sai ka kai masa".
Walid ya ce "Shikenan, in sha Allah, amma kar ki je ki
saka damuwa a ranki, idan da wata matsala, ki kira ni a wayarki"
Ta girgiza kai ta ce "Bani da waya"
"To ki ara a ta maƙwabta, barinki da wayarsa akwai
matsala, haka ya karɓe wayar Viper ya tafi da ita.
Ta cigaba da faɗi tashi, wasila ta din ga aiko mata da
abinci, sai dai sam jauhar ba ta son hakan.
Aka fara exams, sai dai ba ta iya mayar da hankali wurin yin
wani abun kirki, wataran kuɗin motar ma gagararta yake yi.
Sai dai tana iya ƙoƙarin ta wurin aro jarumta, da ɓoye
damuwarta, idan ta shiga cikin 'yan uwanta ɗalibai.
Sannu a hankali ta fito daga harabar makarantar, ta tarar da
yaya saifu.
Murmushi ta yi ta ce "Yaya saifu, kai ne?"
Ya ce "Eh, hau babur ɗin na kai ki gida" cikin
murna ta ƙarasa ta rirriƙe shi ta hau, ta ce "Na zo gida sau biyu ban same
ka ba".
"Yau ai gani, mu je gidan naki".
Ya ja babur ɗin, ta ce "Allah ya sa ba laifi na yi maka
ba, na ganka kamar ranka a ɓace".
Yayi mata shiru, suka ƙarasa gidanta, ta buɗe musu suka
shiga.
Ta kawo masa ruwa a jug, dan na rijiya yanzu take sha, ko kuɗin
sayen ruwa ba ta da shi.
"Waliyiyya"
"Na'am yaya saifu"
"Meyafaru da mijinki?" Tayi shiru ta ƙi magana.
"Ki yi mini bayani ina jinki"
Kawai ta fashe da kuka, yayi mata shiru tayi mai isarta, ya
koma kusa da ita ya zuba mata ido ya ce "Jauhar, wani irin zama ki ke yi a
gidan nan, na san akwai ƙalubale da ki ke fuskanta a gidanmu, amma atleast ai
ko ni kya gayawa, sai ji na yi ana zancen an kama shi da cocaine, a tsakar gida
ko baba ba ma bai sani ba, da yaya ki ke rayuwa ke kaɗai? Da yaya ki ke samun
abun da za ki ci?"
"Yaya saifu, ni cin abinci ko akasin haka bai dame ni
ba, fatana da burina ya fito, ba shi da laifi, ko a yaya yake na yadda shi
Allah ya zaɓa mini, ba ya dukana ba ya zagina. Ban san dalilin da ya sanya su
mama suka zaɓi na aure shi ba, na karɓi ƙaddarata, na je gidan ai, amma yanayin
karɓar da na samu na san ba zan yi nasara ba, kuma ban ma samu baba a gida
ba".
"Jauhar, a raba auren nan, ni ban ga alamar za a samu ɗa
mai ido ba a auren nan ba, rannan fa cewa aka yi sai da ya zo ya tafi da ke,
'yan daba za su saraki, wace irin rayuwa ce haka? Ko khul'i ayi a raba auren
nan"
Tayi shiru ta sunkuyar da kanta.
"Yaya ki ka yi shiru? Ko kina son shi ne?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To kin amince a raba auren?" Nan ma ta girgiza
kai.
"Ki yi mini magana jauhar, idan kin amince in yi wa
baba magana, a raba auren nan"
"Dan Allah kar a raba, ni dai a fito mini da shi dan
Allah"
Saifu ya ce "Wai son shi ki ke yi ne?"
Cikin kuka ta ce "Idan aka raba auren za ace mini
bazawara"
"To a kanki aka fara? Ba sai ki koma makarantar ki ki
yi a tsanake ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Dan Allah ni dai yaya saifu kar a
kashe mini aure, duk abun da yake yi zai daina a hankali, sharri ake yi masa ba
ya ta'amalli da hodar iblis" saifu yayi shiru yana kallon ta, ya fara
tunanin any ba son shi take yi ba, ya ma kasa gane me take nufi.
"Shikenan, ƙyale baban ma, yanzu da an yi magana da
shi, sai ya gaya wa matansa, wace kotun ake yi masa shari'a? Akwai wani baban
abokina, sai na yi wa abokin nawa magana a san abun yi"
Cikin murna ta ce "Na gode sosai yaya, ban san wace
kotun ba ce ba, wai ya hana a kai ni, amma akwai lambar abokinsa, da tare muke
up and down, ka ga daga nan ma sai mu je na ganshi".
"No, tun da ya ce kar ki je, ba sai kin je ba, duk abun
da ake ciki, zan din ga sanar miki, amma ki kwantar da hankalinki dan
waliyiyya, tun da kin na ce, ke uwar soyayya Allah ya bar ƙauna, amma wallahi
na tsani mijin nan naki"
Ta ce "Dan Allah ka daina faɗa, ba zan ji daɗi ba, a
din ga yi mana addu'a, ba na jin daɗi idan aka aibata shi"
Ya ce "Iyee lallai waliyiyya baki ya buɗe, ki na so dai
ki gaya mini ki na son mijinki maybe ma fiye da ni, to wallahi ki fi so na a
kansa"
Ta ɓoye fuskarta tana dariya ta ce "Wallahi yaya
tausayi yake bani kawai, idan aka raba auren nan, akwai damuwa, kuma ina saka
ran komai zai zama tarihi in sha Allah"
Ya ce "Tafi can, kya ma faɗi gaskiya, kuma ko ba yau
ba, kar ki sake wani ma ya san na shiga maganar nan, ai mu na da alfarma
shige-shige yayi mana rana" jauhar tayi murmushi, ya bata kuɗi ya tafi.
Kusan sati ba ta ƙara jin ɗuriyar saifu ba, ga babu su walid
balle ta ji wani abu daga gare su, sai da ta ari wayar wasila, ta kira walid ta
ce ya zo ya karɓi kayan da zai kai wa master.
Ta saya masa maggi, mai, da sauran ɗan abun da ba a rasa ba,
da prisoner zai buƙata.
Ya karɓa tare da ƙara bata haƙuri, da ba ta tabbacin, yana
nan suna ƙoƙarin fitar da Mijinta.
Saifu ya sake komawa makaranta ya sameta, cikin murna ta hau
tambayar sa, ya ake ciki?.
"Ke mijinki abun da aka yi masa shiri ne kawai, na
bibiyi abun ni da abokina, zaki sha mamaki idan na gaya miki an yi wani mugun
sara a kan gaɓa, amma ba zan gaya miki ba, in je zaƙin soyayya ya ja ki ki gaya
masa ba idan ya fito, ki haddasa husuma, baban abokin nawa yayi magana, sun ce
ayi haƙuri ya ƙarasa wata ɗaya, kotu za ta wanke shi ya fito, ashirin da biyu
ga watan gobe za a sake shi"
"Wayyo Allah, yaya saifu kusan watanni uku fa kenan zai
yi a prison?"
"Au baki gode ba kenan?"
Jiki a sanyaye ta ce "A'a na gode sosai yayana,
Ubangiji Allah ya saka maka da gidan aljanna, to zaka kai ni na ganshi?"
Ya ce "Amin ya rabb, yana prison na ciki gari, kuma ban
ce ki je ba, kar ki kuskura ki je, kin ji na gaya miki"
"Amma yaya meyasa?"
Saifu ya ce "Saboda haka na ce miki, kuma ke ma kin ce
ya ce kar ki je, kar kuma gaya wa wani gashi zai fito shi ma bai sani ba".
Jauhar ta ce "To shikenan, na gode Allah ya saka maka
da mafificin alkhairi"
"Amin ki koma gida, ki cigaba da exams ɗinki, idan da
wani abu, ki neme ni a waya, kar ma ki sake zuwa gidan nan da wani batu a kan
aurenki, tun da ki na son abun ki ki yi zamanki"
Tayi murmushi ta ce "Ban san menene son ba dai yaya,
ban san me ake ji ba, da farko dai na san ina jin tsoronsa sosai, amma yanzu
kuma tausayin sa nake ji"
Yayi murmushi ya ce "Ga kuɗin mota, ki sauka lafiya,
yau ba zan je gidanki ba"
Ta karɓa cikin murna tayi masa godiya, ta tafi gida.
Ta ji sanyi a ranta jin cewar zai fito, sai dai tana cikin
damuwa na rashin sanin halin da yake ciki, ya ji sauƙi ko kuwa, yana samun
abinci ko kuwa?"
Da ta samu kuɗi, take yin sayayya, ta ari waya ta kira
walid, ya zo ya karɓa ya kai masa.
Sana'a tuƙuru jauhar kamar tayi ƙwace, dama ga azumi yana
gabatowa, ana samun ɗinkuna, dan haka tana samun aikin stone da beads, sai dai
ba ta iya sakin jiki ta kashe kuɗin, saboda akwai abun da take son yi.
Ita ce mayafai, har da su kantu da aya, haka take saya
ta soya ta ɗaura a leda yara na saya.
Har guga take karɓar kayan maman halimatu, ta ta da ta yara
tayi mata, ta biyata.
Sana'oi kamar zata yi ƙwace, duk da ana yi mata mugunta a
kan wasu abubuwan, mussman gidan mai ɗinki, da take yi mata aikin stone ta fara
yi mata mugunta.
Ta ƙara tsananta addu'a, da roƙon Allah, a kan Allah ya kuɓutar
mata da mijinta, ya shirya mata shi.
Rana ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, saura
kwanaki biyu Al'amin ya fito, jauhar ta yi ta gyaran gida, ta ƙara gyara masa ɗakinsa.
Ranar da zai fito ɗin, ta yi girki, sai dai kuɗin hannunta
ba su da yawa, duk mutane sun riƙe mata kuɗi, dan muɗin hannunta ba za su ishe
su kuɗin mota ba ita da shi.
Ta dafa ruwa ta zuba a flask, ta shirya tun ƙarfe tara, ta
tafi prison ɗin, gashi damuna ta ja baya, an fara wani irin sanyi mai ratsa
jiki.
Ta nemi shiga cikin prsion ɗin, aka ce mata a waje za ta
jira, idan yau za a sake shi, za ta ganshi ya fito.
Tana nan zaune, wasu suna ta fitowa, 'yan uwansu suna ta
murna, sai dai shiru-shiru ba ta ganshi ba.
Nan hankalinta ya tashi, ta sake nufar wurin masu gadin ta
ce "Wai haryanzu ban ganshi ba, kuma yau aka ce mini za a sake shi"
"Waye ya ce miki za a sake shi?" Wani gandiroba ya
tambayeta.
"Yayana ne"
"Yayan naki alƙali ne? Ko shi ya kawo shi nan ɗin,
wanda zamu saki kenan yau sun gama fitowa"
"Innalillahi na shiga uku" ta faɗa a raunane.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan
kitchen wnd suke available ba order ba??
Kina bukatar
adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??
Kiyi joining wnn
group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya
available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Da kallo suka bi jauhar, ganin yadda take yi musu kuka wiwi,
wani gandiroba ya ce "Koma tsallake, idan ki ka gama kukan, sai ki
tafi".
Ta juya ta kama hanyar tafiya, tana ji a ranta kamar duk
duniya, babu wanda ya kaita rashin sa'a.
Sannu a hankali yake tunkaro gate ɗin fitowar, zuciyarsa
cike da mamakin yadda aka sake shi, dan bai san ma zai fita ba, sai yau ɗin.
Tsayawa yayi bayan ya fito daga cikin gate ɗin, ya lumshe
idanunsa sakamakon hasken ranar da ya ji ya yi wa idanuwansa yawa, sannu a
hankali ya cigaba da buɗe su, har ya ji hasken yayi dai dai da abun da idon
nasa yake buƙata.
Kamar an kira sunanta ta waiwayo, ta hangoshi a tsaye, shi
ma ita yake kallo da mamaki, ba ƙaramin kashedi ya yi wa su liti ba, a kan kar
su kuma ɗaukarta su kaita in da yake.
Da sauri ta nufo shi, ta kasa tsayar da hawayenta ta na wata
irin ajiyar zuciya ta ce "Har na ji daɗi, da suka ce mini, ba za su sake
ka yau ba"
Yayi shiru yana kallon ta.
Ƙare masa kallo take yi, an yi masa aski an aske masa
sajensa da gemunsa, sai ɗan kaɗan da ya fara fitowa, idanunsa sun washe yayi
haske, saboda babu kayan shaye-shaye a nan, sai dai ya rame sosai.
Kallonta kawai yake yi, kamar wata baƙuwar halitta, sai dai
bai yi mata magana ba.
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Mu tafi?" Ya jinjina
mata kai yayi gaba.
Ta ɗaga ƙafarta kenan takalminta ya tsinke, ta durƙusa ta
cire takalmin ta ce "Takalmina ya tsinke" ya kalli ƙafarta sannan ya
dubeta, ƙafarta busu-busu, duk yadda ya santa da gayu, ko ba ta gaya masa ba,
ya san tafiyar ƙafa ta yi.
Ta tsayar musu da abun hawa suka hau, sai dai har suka je in
da za su sauka, duk surutun da take yi, ko sau ɗaya bai tanka mata ba.
A titi suka sauka, saboda kuɗin motar ba zai isa a shiga da
su har ƙofar layin ba, har ta yi gaba, ya janyota ya cire mata takalmansa ba
tare da ya ce komai ba.
Ta ce "A'a ka saka kar ka taka wani abun".
Kallon da yayi mata, ya sanya ta yin shiru, ta saka takalman
kamar zata tashi sama a kansu suka shiga layinsu, kamar ta taka rawa, master ya
fito.
A falo ya zauna, ya kashingiɗa ya lumshe idanunsa, ta shiga
banɗakinsa, ta haɗa masa ruwa mai zafi, ta ce "Master ga ruwan wanka na
kai maka" bai yi mata musu ba, ya tashi ya tafi, kafin ya fito ta jera
abinci a falo, ya yi wankan ya fito falo, ya tarar da abinci, yanayin yadda
yake cin abincin ya tabattar mata da yana jin yunwa sosai duk da dama can acici
ne.
Yana so yayi mata magana, amma ya rasa me zai ce mata ma, ya
gama ci ya tafi ɗakinsa ya kwanta, dan surutunta ya fara takura shi, duk da
yayi kewar abubuwa da yawa a tare da ita, sai dai yadda yake jin zuciyarsa a
cunkushe babu daɗi, ya sanya shi jin surutunta ya gundure shi.
Allah ya taimaketa, ya wuni a ɗaki, bai fita ko ina ba, tun
da ya dawo.
Hafsa kuwa ta samu abun yi, dan tun da Allah ya sa ta
mallaki lambar wayar Alhaji mu'azzam, take kiransa a waya, da sunan rarrashin
sa a kan rashin jauhar, tare da ƙoƙarin sake ɓata jauhar ɗin a wurinsa.
Mahaifiyarta ta sake miƙewa wurin shige-shige a kan Allah ya
tabattar da lamarin aure tsakanin hafsa da Alhaji mu'azzam.
Cikin ikon Allah, idan ta kira shi, yana amsawa ba ya yi
mata wulaƙanci ko makamancin haka, hakan ya sa ta cigaba da ƙoƙarin cusa kanta
cikin hikima da kissa.
Sannan suka yi ƙoƙarin rufe wa mama duk wani abu da yake
faruwa, ba ta san halin da ake ciki ba.
Kasancewar Al'amin ya fito ya dawo gida, ya sanya jauhar yin
isashshen baccin da rabonta da shi, tun kan a rufe shi, dan bayan sallar asuba
da ta kwanta, ba ta farka ba sai goma saura.
Ta fito tsakar gida da sauri, ta fara aikace-aikace, ta dafa
tea ta soya dankalin hausa.
Ta dafawa Al'amin ruwa a heater, ta je ƙofar ɗakin ta tsaya
tana sallama.
Ƙasa-ƙasa ya amsa, ban da yana da buɗaɗɗiyar murya ma ba za
ta ji ba, ta shiga tana sake yin wata ta ce "Ina kwana master"
"Lafiya ƙalau"
"Ban san ka tashi ba, yau na makara da na fara kawo
maka ruwan wankan ai, bari na haɗa maka" ta haɗa masa, yanzu ma bai yi
musun yin wankan ba, ya tashi ya shiga banɗakin.
Ɗakin fes yake, amma ta din da karkaɗe karkaɗe, da
goge-goge, ta kunna turaren wuta, ta fito masa da kaya ta saka musu turare.
Ya gama ya fito, jikinsa yana ɗigar da ruwan wanka, ya ɗauki
dogon wando ya saka, ya zube mata wanda ya cire a kan katifa ya fito.
Kallo ɗaya tayi masa ta kawar da kanta gefe ta ce "Ba
ka saka rigar ba, na fito maka da ita ma".
"Ba na buƙata, wandon ya isheni".
Jauhar ta ce "To ai kar ayi sallama, a ganka a
haka".
"Ki koma ɗaki idan ba zaki iya kallona a haka ba"
yayi maganar yana zama.
Ya kalleta ita ma yau ba hijjabi a jikinta, doguwar rigar
material ta saka, mamaki yake yi, yadda ta yi duhu, ga wani uban ƙashin wuya da
ya fito mata, tayi rama sosai da sosai, ashe jiya dan ya ganta a cikin hijjabi
ne ya sanya bai gane ba, sai ya ji ransa babu daɗi.
Ta haɗa masa abincin ta miƙa masa, ya ɗauka zai kai baki ta
ce "Bisimillah" a zuciyarsa ya maimaita sannan ya fara ci.
"Askin nan da aka yi maka, ka yi kyau, sai dai ban so
aka aske gemun ba gaba ɗaya"
Idan ba gizo idanunta suka so yi mata ba, da murmushi zai yi
ya shanye abun sa.
Ta tanƙwashe ƙafarta ta sake cewa "Sannu master, a
prison ɗin ma duka ake yi, na ga bayanka duk shaidar duka. Wallahi ba zan taɓa
yafewa wanda suka yi maka sharri ba, ban taɓa shiga tashin hankalin da na shiga
ba, na san baka ta'mali da wannan abar, sauran ma zaka daina wataran in sha
Allah" tayi maganar hawaye na cika mata ido.
"Kun kusa gama exams ko?"
Jin yayi magana ya sanya ta saurin ce wa "Eh, cikin
azumi zamu gama in sha Allah"
"Allah ya taimaka"
"Amin na gode, baka tambayeni kwaɗinka da ƙadangaru
ba?"
Ya rausayar da kai ya ce "Ai naki ne ba nawa ba"
hakan yayi da kammala cin abincin.
Ta ce "Alhamdilillahilazi aɗa'amana haza, warazaƙatana
min gairi haulin minni wala ƙuwwa, Ubangiji Allah ya ciyar da mu na
anjima" tayi maganar tana tattare kwanukan.
Kafin ta dawo ya ɗauki pillown kujera ya kwanta.
Ta je gabansa, ta durƙusa ta kai hannunta goshinsa ta ce
"Wai haryanzu kana zazzaɓin ne?"
Ya girgiza kai alamar a'a.
"Master duk ka yi wani iri kamar an canza mini
kai" duk lokacin da ta danganta shi da ita, sai ya ji wani abu a ransa da
bai san Menene ba.
Yana daga kwance ya din ga miƙa, yana ɗan banƙare kafaɗunsa
zuwa bayansa.
"Ciwo bayanka yake yi ne?"
Ya gyaɗa mata kai alamar eh.
"Bari na ɗaukko man zafi na shafa maka zaka ji daɗi,
naga wani raunin bai gama warkewa ba". Ya jinjina mata kai, sai dai bai buɗe
idonsa ba.
Ta je ta ɗauko man, ta dawo ta zauna a bayansa, tana shafa
masa a hankali.
Ta ce "Juyo" ya gyara kwanciyar sa a hankali,
jikinsa wasu wuraren duk shaidar yankan wuƙa, bayan tabon duka.
Haka kurum zuciyarta ke raya mata, kai hannu kan gashin da
yake kwance a ƙirjinsa, da sauri ta rintse idanunta ta kawar da wannan tunanin
ta kira sunansa.
"Master"
"Mmm?" Ya amsa idonsa a rufe.
Ta ce "Ka na jina?"
"Mmm"
A ɗan shagwaɓe ta ce "To ka kalle ni, magana zamu yi
fa"
Ya buɗe idanunsa a kanta, take ta sunkuyar da kanta, saboda
wani irin nauyi da kwarjinin da idanun nasa suka yi mata, a tunaninta ta daina
jin tsoron sa, ashe haryanzu da sauran rina a kaba, yayi mata shiru yana
kallonta yana jiran tayi maganar, sai dai ta kasa.
Gaba ɗaya sai ta diririce, ta kasa maganar sai cigaba da
shafa masa man zafi a wuri ɗaya a kafaɗarsa.
Hannunsa ya saka ya cire nata, ya karɓi man zafin ya ajiye,
ya ce "Ya aka yi?"
"Dama sonake na ce dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini,
na yi sanadiyar shigarka wahala, duk laifina ne da ban gaya maka an kawo maka
saƙo ba, ka yi haƙuri mantawa na yi ka yafe mini dan Allah"
"Idan naƙi fa" yayi maganar very serious.
Cikin damuwa ta ce "Please dan Allah ka yi haƙuri"
"Zan duba, ki je ki yi karatunki saboda exams" ta
jinjina kai ta tashi, tsakar gida ta fita ta hau wanke-wanke, ta ɗaukko kayansa
da ya cire, da wanda ya dawo da su daga prison, ta jiƙa su dan ta wanke.
Wasila maƙwabciyarta ce tayi sallama, kasancewar ƙofar ba a
rufe take ba, jauhar ta ce "Anty wasila sannu da zuwa ga kujera"
"Yauwwa jauhara, ashe mai house ya dawo, jiya na ji
halimatu ta ce ta ganku, na zata sharrinta ne ma, na zo ɗazu tun takwas da
rabi, na yi ta bugu baki buɗe ba na ce bari na tafi, su jauhar ana can jikin
miji an liƙe ba a tashi ba"
Jauhar kawai ta yi murmushi tana fatan Allah ya sa bai jiyo
ba, tun da yana falo a kwance.
Ta ce "Jiyan ya fito, ban samu na shigo na gaya muku ba
ke da maman halimatu".
"Allah sarki jauhar, kin sha wahala shikenan kuka ya
ƙare, ki daina anty wasila ba ki san me nake ji ba, zuciyata kamar ciwo take,
Allah dai ya bar wannan ƙauna, zuciyar ya daina ciwo ko?"
Dariya kawai jauhar take yi ta ce "Ta daina"
"To ai da kamata yayi, da ki ka san zai fito, ki yi
magana ayi gyare-gyare a gyara masa turaka, ki zo na baki kayan maman nihal
Anty maryam, na sanmiki kayanta ki gwada ki ji, ai ba kya yi shiru ki zauna
haka ba" (Ga mai buƙatar jarraba kayan maman neehal sai ya tuntuɓeta ta
wannan lambar 0706 677 4630).
Wasila ta din ga sakin layi, sai da jauhar ta ce "Anty
wasila yana nan fa, yana falo yana jinki"
Tayi ƙasa da muryarta ta ce "Na shiga uku, kuma ki ka
bar ni nake ta zuba, amma baki kyauta mini ba".
Ta durƙusa ta kwashi takalmanta cikin sanɗa, ta fice, jauhar
ta din ga dariya, ta rufe ƙofarta, sai dai ita ma shiga falon ya gagareta,
saboda kunyar abun da wasila ta din ga faɗa, dan ta san halinsa, sai ta
sakankance, bacci yake yi, ta ga idonsa biyu.
Ta jima tana raɓe-raɓe kafin ta shiga ɗakin, baccinsa yake
yi, sosai take jin tausayinsa, yanayin yadda yake miƙa ma, kawai ya tabbatar
mata da zaman gidan kaso bai yi masa daɗi ba.
Tana ta dirzar kayansa, ta ji an yi wani irin fito a waje,
sannan aka buga mata gate, ta saka hijjabi ta buɗe ta ga su walid.
Ta ce "Yaya walid, ina wuni"
"Madam dama mutumin nan ya fito baki sanar mana ba? Sai
yaran da muka saka gadinki ne suka faɗa mana".
"Dan Allah ku yi haƙuri, na san zai neme ku, bacci yake
yi ne".
Liti ya ce "Ko dai ki ka ɓoye shi ki ka hana shi
fitowa"
Ta ce "A'a na isa? Ban hana shi fitowa ba, ina dai
roƙon Allah ku bar mini shi, na san dole dai zai zo in da ku ke".
Walid ya sake wani irin fito, tana waiwayawa ta ga har ya
zira riga ya fito.
Saroro ta yi ta tsaya tana kallon sa, ya ƙaraso, zai raɓata
ya wuce.
Jiki a sanyaye ta ce "Fita zaka yi? Ban gama ganinka ba
fa"
Kallonta ya yi, ya raɓa zai wuce ta ce "Dan Allah
Master kar ka sha komai, ko ka je in da ake aikata laifi, dan Allah"
maganar da tayi, har hawaye ya cika mata ido.
Bai kulata ba ya fita, gaba ɗaya sai ta ji garin yayi mata
babu daɗi, duk da tana cikin shauƙi, da farincikin dawowarsa.
Tana jin shewar su walid, da suka ganshi, ta ja jikinta, ta
koma ɗaki, aikin ma ta kasa cigaba, kawai ta saka kuka, kasancewar shi ne kaɗai
abun da take yi, ta rage damuwarta, sai kuma tsananta ambaton Allah.
Tun wannan fitar da yayi, tun tana saka ran dawowarsa, har
ta cire rai, dan har magariba ba ta kuma saka shi a idonta ba.
Tayi ta addu'a a ranta, Allah ya sa yana lafiya.
Har bayan goma na dare, ta kasa kwanciya, sai sha ɗaya da
wani abu, ta ji yana rufe ƙofa, ta fito falo da sauri, ya shigo yana haska
fitilar wayarsa, gaba ɗaya falon ya gauraye da warin wiwin da yake yi, jikinta
yayi sanyi ta kasa yi masa magana, yadda yake tafiya ya tabattar mata da a buge
yake, ya wuce ta ya tafi ɗakinsa.
Ta nemi wuri ta zauna a wurin, ta haɗa kai da gwiwa, ta din
ga kuka ƙasa-ƙasa, ta tashi ta nufi ƙofar ɗakinsa ta leƙa, ɗakin duhu, sai dai
tana hango hasken wutar jikin sigarinsa, ta juya ta koma ɗakinta, ta ji tana
neman sarewa, kamar Allah ba zai karɓi addu'arta a kan sa ba, da sauri ta din
ga istigfari, ta nemi wuri ta kwanta.
Da safe da ta tashi, ba ta ko nufi ƙofar ɗakinsa ba, sai da
ya fito ya tarar da ita a falo, tana shirin dutse.
Cikin girmamawa ta ce "Ina kwana"
"Lafiya ƙalau" ya zauna a kan doguwar kujera, ta
ce "Afuwan kar ka ga ban kawo komai ba, wallahi ba kuɗi a hannuna ban
girka komai ba"
Bai yi magana ba, sai kamar bayan mintuna goma, ya ɗauki
wayarsa ya ɗan danna ya saka a kunnensa.
"Kawo mini bredi da lipton, kayan tea dai na dubu biyu,
kawo mini gida ka karɓi kuɗin". Ya ajiye wayar.
Jin wayar da ya yi ya sanya ta tashi ta ɗora tea, kasancewar
da wuta ta ɗora a heater.
Tana cikin kwashe tea ɗin, ya fito ya je ya karɓo kayan
shayin, ya ajiye mata a ƙofar kitchen.
Ta ce "To, Allah ya saka da alkhairi"
Ta ɗauka ta dudduba, da yabi ta ita, iya buredi da sugan ya
isa, sauran kuɗin ko taliya sa saya, ta ɗauka ta soya ƙwan, ta kawo kayan
karin.
Shikaɗai ta haɗawa ta koma gefe, ta cigaba da shirinta.
"Wannan shirirtar ta fi ki karya kumallo?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba na jin yunwa ne, zan karya
amma".
Gaba ɗaya ba ta walwala, duk surutun nan ma da take yi
masa, yau bakinta shiru, ta kunna mp ɗin ta, ta ajiye a gefe, tana saurar
radio, ana ta zancen za a tafi yajin aiki, saboda tsadar rayuwa da rashin
ingantacciyar rayuwa ga ma'aikata.
"Amm Angela ki ke ko?"
Tayi murmushi ta ce "Ko 'yar madara ba" tayi
maganar cikin ƙoƙarin ɓoye damuwar da take ciki.
"Koma dai wanne ne, magana ce da ni"
Ta ce "To" ta ajiye kayan abun da take yi, ta
fuskance shi, amma ba ta yadda sun haɗa ido ba.
"Kalleni, idan ina magana na fi son ki kalleni, ki
daina sunkuyar da kai"
Kallo ɗaya tayi masa ta sake sunkuyar da kai ta ce "Ba
zan iya ba ne, wani abu nake gani a cikin idon naka da yake bani tsoro"
"Kin kusa daina gani, wata shawara na yanke a kan
zamanmu, ni wannan yawan koke-koken da ki ke yi, da wahalar da ki ke sha ba na
so, jin sa nake yi kamar wani nauyi a kaina, kuma ni gaskiya ba zan iya daina
wasu abubuwan ba, ina saka ki a damuwa da matsala sosai, ga rayuwar ki a cikin
hatsari, duk saboda ni.
Kina takura rayuwata sosai da sosai, nima kuma ma san ina
takura ki dan haka na yanke shawarar kawai na sauwwaƙe miki, ki koma gida Allah
ya baki wani mijin ki yi aure, ni ba na buƙatar mace a cikin rayuwata".
Tun da ya fara maganar, ta ji kamar an jona mata shocking,
zuciyarta ta din ga bugawa da wani irin sauri, ta rasa me ma za ta ce.
Sai da ya kammala tsaf, sannan cikin ƙarfin hali ta kalleshi
ta kawar da mai ta ce "Wannan ne tukuicina kenan? Baka buƙatar mace a
rayuwarka, nima ƙaddara ce ta kawo ni in da ka ke, na zata idan na jure na
cigaba da yi wa baba biyayya, na yi biyayyar aure, komai zai wuce, zan ci riba,
amma yanzu na fuskanci ni ce mara sa'ar, ko ina ba a buƙata ta, yanzu
tozarta maraicina shi ne ka ga ya dace da ni, har ya sanya ka ce ba zaka yafe
mini ba jiya? shikenan ka bani a rubuce na kai wa baban, na gode master, amma
duniya da ba a yafiya da mu zo i yanzu ba, na san nayi maka kuskure amma na
baka haƙuri, amma ka sani idan ka sake ni, ka tozarta maraici" ji tayi
numfashinta ya yi wa ƙirjinta nauyi, kawai ta tashi jikinta na rawa.
Tsananin fargaba da tashin hankalin maganar da ya gaya mata,
ya sanya period ya zo mata ba shiri, har jikinta ya ɓaci, dama sauran kwana ɗaya
ya zo.
Har tayi maganar ta gama, ba ta kalleshi ba ko sau ɗaya.
A ransa ya din ga maimaita ;idan ka sake ni, ka tozarta
maraicina. Ita a tunaninta abun da ya faru ne ya sanya ya ce zai rabu da ita?
Marainiya ce kenan? Ya tambayi kansa a lokaci ɗaya ya bawa kansa amsa da no
wonder.
Sai kuma jikinsa yayi sanyi, shi wannan wahalar da take sha,
ya ɗauka za ta yi murna da abun da ya ce, kawai ya basar ya kwanta.
Sosai ta din ga kuka, a ɗakinta, tana tunanin wane irin
baƙin jini ne da ita haka? Duk yadda take haƙuri tana lallaɓa auren nan, amma
ya yi mata wannan sakayyar, take ta fara tunanin wane irin zama zata koma ta yi
a wannan gidan na su, da suke nuna mata ƙiyayyarsu a fili?
Da ƙyar ta shiga banɗaki ta gyara jikinta, ta fito zauna a
ƙasa ta cigaba da kuka.
Bayan ya gama abun da yake yi, ya fice ya bar gidan.
Kanta ne ya fara ciwo, ga numfashinta da yake ta barazanar ɗaukewa,
ga wani irin azababben ciwon mara da yazo mata da zazzaɓi duk a sanadin tashin
hankalin maganganun Al'amin.
Yaya saifu kuwa tun da ya dinga bibiya, aka tabattar masa da
an saki Al'amin, hankalinsa ya kwanta, ya so ya je gidan nata ya tabattar amma
har ga Allah ba ya ƙaunar shi, duk da sau ɗaya ya taɓa ganinsa, ranar ɗaurin
auren a masallaci, kawai a jikinsa yake jin azabatar da jauhar yake yi, dan ba
zata faɗa bane kawai.
Al'amin kuwa, su walid suna ta hirar irin tashin hankalin da
matarsa ta shiga, da aka kai shi prison, da irin aiken da ta din ga yi masa da
kayan amfani yana prison.
Gaba daya sai ya tafi lissafin yanzu idan ya saketa, to
abinci fa? Amma shi duk da haka gani yake hakan ne mafita, wannan tashin
hankalin da take shiga idan ya shiga cakwakiya, sai ya ga kamar yana shiga
hakkinta da yawa, kuma a idonta yake ganin damuwa idan ta ganshi a halin maye.
Da daddare da ya dawo, yadda ya fita ya bar kayan karin
kumallo, haka ya dawo ya tarar da su, ba ta taɓa ba, sai yayi tunanin ko wani
abun ta ci, dan haka ya ƙarasa hallake buredin da ƙwan, ya shige ɗakinsa ya
cigaba da busa hayaƙi cikin nishaɗi.
Washegari ya din ga zaman jira, ya ga ta fito ta yi abun
karyawa, amma shiru, gashi bayan sallar asuba ya yi shaye-shaye dan haka yunwa
yake ji sosai.
Ganin har sha ɗaya ba ta fito ba, ya sanya ya fice, sai dai
kuma yajin aiki ake yi, da ƙafarsa ya tafi unguwar su, wurin su Walid.
Yau ko tsintsiya jauhar bata ɗauka ba, tana ta fama da
kanta, da la'asar ya dawo, ya sake tarar da gidan yadda ya bar shi.
Gaba ɗaya sai gidan yayi masa wani iri, ya kwashe kwanukan
da ya karya da su jiya, ya fara tunanin ko fushi tayi, shi ne ya sanya taƙi yin
shara a gidan.
Yana tsaye yana kallon falon, ya ɗaga kai ya ga ta fito daga
ɗakinta, kamar fuskarta ta kumbura.
Ya tsaya yana kallonta, ya ga tana ɗaga ƙafa da kyar a
hankali.
Kawai ta yanke jiki ta faɗi a wurin, a sukwane ya yo kanta,
ya ɗagata.
ta motsa da ƙyar, hannu ya saka ya juyota jikinsa sosai,
wani irin hucin zafi jikinta yake fitarwa, ta ɗaga idonta da ƙyar ta kalle shi,
idanunta sun yi ja sosai da sosai ta mayar da su ta lumshe.
Hankali tashe ya ce "Menene?"
"Kaina ne zai fashe" tayi maganar hawaye na bin
gefen fuskarta, kafin yayi magana, jikinta ya hau karkarwa, haƙoranta na karo
da juna, idonta na neman juyewa saboda zafin zazzaɓi da matsanancin ciwon kai.
Ɗagota yayi sosai ya ce "Ki na ji na?" Ta ɗaga
masa kai da ƙyar.
"Zan je in samo abun hawa, mu je asibiti"
"Yajin aiki ake yi, ka manta?" tayi maganar a
galabaice.
Sai yanzu ya tuna, dan da ƙafa ya je yawonsa ya dawo,
ƙungiyar ƙwadago na jagorantar yajin aiki da kuma zanga-zanga domin janyo
hankalin gwamnati a kan wasu haƙƙoƙin 'yan ƙasa.
"Na sani, yanzu zan dawo"
Ba tare da ya san in da zai nufa ba, ya kwantar da ita kawai
ya fita, a ransa yake jin idan ya bar yarinyar nan da ciwo, bai yi wa kansa
adalci ba.
A titin unguwar, ya ga wani ɗan adaidaita sahu, ya tsayar da
shi ya ce "Malam mara lafiya zaka ɗaukar mini"
Mai baburin ya ce "A'a yi haƙuri ba aiki na fito ba, ba
ka san ana yajin aiki ba ne maigida?"
"Ana yajin aikin amma ka fito da babur?"
"Eh na yi wani uzuri ne, gida zan koma".
A ɗan hasale ya ce "Mara lafiya zaka ɗaukar mini"
Shi ma a hasale mai baburin ya ce "Na ce ba zani ba,
ana dole ne? Ka nemi wani mana"
A fusace ya daki tayar gaban adaidaita sahun, mai napep ya
waro ido ya ce "Malam meye haka?"
Kawai ya shiga bayan adaidaita sahun, ya zare wuƙa ya ce
"Bi cikin layin nan, ko na zaro hanjinka yanzun nan da russia" tsit
mai ɗan sahun yayi, ya bi layin tare da yin sarandar ƙwace masa baburin ma zai
yi.
A ƙofar gidan ya saka shi yayi parking, ya sauka ya ƙwace
mukullin babur ɗin, ya shiga cikin gidan da shi.
Ya ɗauko hijjabinta ya saka mata.
"Master"
Ya kalleta ba tare da ya amsa ba, ta ce "Yi haƙuri, na
saka wahala"
"Ki yi mini shiru"
Ta ce "To" ya ɗaukkota kamar matacciya, ya shiga
da ita napep ɗin.
Ya ciro mukullin ya miƙa wa mai baburin ya karɓa yana
cunkusa fuska ya ce "Megida amma ka san yajin aiki ake yi, ina zan kai ku?
asibitin gwamnati babu aiki".
Al'amin ya ce "Ko ma wane asibitin ne mu je"
Kamar wata 'yar kyanwa, haka ta kwanta luf a jikinsa, da
suka hau kwalta, sai sanyin da take ji ya ƙaru, dan haka ta ƙara shigewa
jikinsa, jikinta na ta rawa.
Wani Asibitin kuɗi ya kai su a gadon ƙaya, Al'amin ya cilla
masa dubu ɗaya, ya rungumi jauhar ya shiga da ita.
Ba a taɓa ta ba, sai da ya biya kuɗin file da komai, sannan
aka fara yi mata abun da yakamata.
suka shiga wurin likita, aka tambayi sunanta, ya manta
surname ɗin ta da ya gani a invitation ɗin su, dan haka ya ce a saka mata Zahra
Al'amin, shekaru ya ce bai sani ba, sai kintata akayi, aka tura su yin
gwaje-gwaje.
Bayan sun dawo,ikitan da ya duba ta, yayi ta mita malaria
tayi mata mummunan kamu, ga ulcer kuma ga jininta ya hau.
Al'amin ya ce "Malam ba lissafi ko masifa zaka yi mini
ba, ayi mata abun da yakamata kawai" yanayin yadda yayi maganar, ya sanya
likitan gane waye shi.
Sai dai Al'amin yayi mamakin jin an ce jininta ya hau.
Likitan ya ce "Tana da aure ne?".
"Eh"
Likitan ya ce "Ayi gwajin ciki, kar mu yi treatment da
ka".
Al'amin ya ce "Babu ciki"
Likitan yayi saroro yana kallonsa.
"Malam ni ne mijinta, babu wani ciki, ka yi sauri a
fara yi mata abun da yakamata, tana ta murƙususun ciwo. Ko ba ka yadda ba?
Al'ada take yi, ko kuna ganin cikin kwana ɗaya ne ko biyu?"
Likitan ya ce "Ikon Allah"
Jauhar duk da tana fama da kanta, wata irin kunya ta rufeta,
ya aka yi ya san tana period ma.
Tana ta yinƙurin amai, sai dai babu komai a cikinta, aka ce
ya samo mata wani abun ta ci, kafin a fara treatment.
Ya fita ya sayo uwar gurasa mai nama, da ruwa ya kawo mata.
Ya zo ya tarar, an saka mata ruwa, da allurai.
Ya kalli fuskarta, bacci take yi sosai, tana iya ƙoƙarin ta
a kan sauro, kar ya cije ta, ba ita ba har shi, da magariba ta yi za ta hau
rufe ko ina tana kunna maganin sauro.
Abun da bai sani ba, tsananin damuwar da ta shiga bayan kama
shi, da maganganun da ya gaya mata jiya ne suka haifar mata da ciwon.
Sai dai babbar damuwarsa, hawan jinin da aka ambata.
Sai wajejen magariba, ta ɗan samu afuwa.
Wajen isha'i aka sallame su, suka yi mata wasu allauran, aka
ce masa maza ya kaita gida, alluran suna kashe jiki.
Duk kuɗin jikinsa sai da suka ƙare, suna fitowa harabar
asibitin, jikinta ya saki ta tafi zata faɗi, ya riƙeta da ƙyar suka fita, sai
dai gaba ɗaya titin babu ababen hawa.
Ganin sai tangaɗi take yi, kuma bashi da wata dabara ya
sanya, ya ɗaure ledar magungunan ta, ya ɗaga ta ya saɓa a bayansa, ya ɗauki
takalmanta ya riƙe a hannunsa, ya zagaya ya bi lunguna.
A din ga yi ana sauke hakki, idan baki saya ba 0009450228
Aisha Adam jaiz bank
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan
kitchen wnd suke available ba order ba??
Kina bukatar
adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??
Kiyi joining wnn
group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya
available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
A ƙalla ya kai awa ɗaya da mintuna talatin, yana tafiya da
ƙafa, bayansa ɗauke da jauhar, wani wurin idan da mutane, ayi ta kallonsa, tun
da sauran sahun mutane, har ya zama saura ɗai-ɗai.
A haka ya isa gida, ya buɗe gidan, ya shiga da ita ɗakinta
ya kwantar da ita, zazzaɓin jikinta ya sauka, sai dai gaba ɗaya jikin nata ya
saki.
Ya kunna fitilar wayarsa yana haskata.
Surutai take yi, wanda tun suna hanya take yi, sai dai ba ya
gane me take faɗa sai yanzu.
"Allah ka shirya mini mijina, Allah ka sa ya daina abun
da yake yi. Ya Allah, Allah ka sa ya shiryu.
Allah na san ba zaka kunyata ni ba, Allahumma inni as'alukal
jannata wa na uzubika mina narr. Rabbana hablana min azwajina, wa zuriyyatuna
ƙurattu a'ayunun waja'alna lil muttaƙina imama. Rabbigfir ummi wa abi,
warahamhuma, kama rabba ya ni sagira" ta ƙarasa tana shafar fuskarta, da
tafukan hannayenta, hakan ya tabattar masa da addu'aoin ta ne na salla, take
maimaitawa.
Ya lulluɓeta, ya tashi ya sake fita, sai dai abubuwa
daban-daban suna ta cigaba da kai komo a zuciyarsa, ya ji ƙwarai yana son sanin
wacece yake zaune da ita a matsayin mata, shi dai ya san ba shi da nagartar da
uban kirki zai bashi auren 'ya, idan ba da wata a ƙasa ba.
Cikin gari ya sake ninkawa ya tafi, bai zarce ko ina ba sai
gidansu, ya tarar har sun rufe ƙofa.
Bugawa ya fara yi iya ƙarfinsa, Abba ya zo ya buɗe, yana
ganin Al'amin ya ruga da gudu ya koma, saboda yana bala'in tsoronsa.
Ba tare da ya kula kowa ba, ya shiga kitchen, ya dudduba
babu komai sun cinye abincin.
Rahila ta fito, ta ce "Kai Aminu lafiya ka zo mana a
wannan daren? Yaushe aka sako ka?"
"Shahida" ya ƙwala mata kira, kasancewar ya
hangota a falo.
Cikin hanzari, ta fito ta ce "Gani yaya"
Yayi mata alama ta shiga kitchen, ta shiga ya bi bayanta, ya
ce "Dafa mini shayi cikin flask ɗin nan" yayi maganar yana nuna mata
flask ɗin shayinsu, family size.
"Wai Aminu me ka ke yi haka, dan me zaka sakata girki a
wannan tsohon daren?"
Bai kulata ba, ya kwaso ƙwai ya zube mata ya ce "Ki
soya mini wannan ma".
Rahila ta koma bedroom ta taso Abbu ta ce "Ta so, ga ɗanka
can ya zo a wannan tsohon daren, kar ya yi mana ɓarna".
Abbu ya taso ya fito, dan ya fara bacci ma.
Ya fito yana faɗin "Kai Al'amin lafiya, ka zo mana a
daren nan? Ina matar taka ina gidan naka?".
Shahida ta ce "Abbu ka koma ka kwanta, ba wani abu,
girki kawai ya ce na yi masa".
"Kuma a daren nan, ina matar ta sa?".
Abbu yana ta ɓaɓatu, Amma Al'amin bai kula shi ba, sai ma ɗaukko
ledar viva, ya buɗe fridge ya kwashe lemon ɓawo ya zuba a ciki, kankana da
sauran abubuwan da ya gani a ciki har da su madarar ruwa.
"Ka yi masa magana, wannan kayan da yake ɗiba ina zai
kai su?".
Al'amin ya kalli rahila ya ce "Da kuka aura mini 'yar
mutane, ai kun san bani da abun yi, in bari yunwa ta kasheta ko na fara satar
kayan mutane ne na kula da ita? Ba ta da lafiya dan haka dole na fito na nemi
abun da zan kai mata ta ci".
"Da can kai da me ka ke riƙe kanka, ba sai ka nema ba,
kuma saboda lalacewa da abun kunya, daga gidanku ne za a ciyar maka da mata?
Al'amin ya waiwayo a fusace, ya nunata da yatsa ya ce
"Ki kiyayi lokacin da haƙurina zai ƙare a kanki"
Shahida ta ce "Yaya gashi na gama, ka ga akwai su maggi
ma a nan, tayi maganar tana buɗe drower tana ɗaukkowa. Ta buɗe wata ta ɗebo su
taliya da macaroni ta ce "Ka haɗa da su"ya girgiza kai ya ce
"Ban da wannan, wannan sun isa"
Ta sake cewa "Yaushe zan zo gidanka, ina son kan na
koma school na zo muku ziyara, tun da ba ma nan aka yi bikinka, samu zo mu
dubata"
A taƙaice ya ce "Sai kin zo".
Ta ce "Wannan ɗin sun isa, ko kuna buƙatar wani
abun?"
Ya ce "A'a, sun isa. zo ki rufe muku gidan" ya
ƙarasa maganar yana kwasar kayan, ya nufi hanyar ficewa.
"Al'amin" Abbu ya kira sunansa, ya tsya cak bai
waiwayo ba.
"A tunanin auren nan da aka yi maka nutsuwa zaka yi, ka
daina wasu abubuwan da ka ke aikatawa, amma abu ya ci tura, ka sanya 'yar
mutane a tasku da tashin hankali, meya kai ka ta'amalli da hodar iblis?.
Lokaci yayi da yakamata ka daina wasu abubuwan, ko dan kare
mutuncinka da na iyalinka. Ko dan ka ga ka sameta a ɓagas ka ke nema ka wahalar
da rayuwarta"
"Kaga Abbu dan Allah ka daina jan maganar nan, ya tafi
kawai su je can su ƙarata, dama ai ba ji take ba ita ma, daidai da ita ne"
Wani abu mai nauyi ya haɗiye, ya saka kai ya fice, ba tare
da ya sake cewa uffan ba.
Bayan ya tafi, Shaida ta ce "Mama dan Allah ki daina
tayar da hankalinki a kan yaya, idan yana wannan abubuwan ki zuba masa ido, tun
da ba kullum yake zuwa ya yi ba. Abu ɗaya kawai yake buƙata yayi iko da kayan
mahaifinsa a matsayin sa na ɗa, kamar yadda muke yi, kin san fa ke da shi, ba
kwa jituwa ki din ga kawar da kai a wasu abubuwan da yake yi, yana ɗaga miki
ƙafa fa kar yayi miki wata illar".
Abbu ajiyar zuciya ya yi, maganganun shahida gaskiya ne,
amma shi babban takaicin sa, Al'amin ba ɗan da za a haɗu a rufawa kai asiri
bane ba, miyagun halayensa ya sanya ba ya son ya zo ko in da yake. Gaba ɗaya
auren da aka yi masa bai sanya ya nutsu ba, kodayeke da sauƙi tun da ya san ya
fito ya nemi abun da zai bawa 'yar mutane.
Ya koma ɗakinsa, Rahila ta bi bayansa, Amira ta ce "Ohh
yau ni nake ganin tsiya, yanzu fa sai a ce ciki ne da ita ko?"
Shahida ta ce "Ba abun mamaki bane"
"Taɓ, a wannan muzuran da tashin hankalin nass har ta ɗau
ciki, iko sai Allah"
Al'amin ya sake ninkawa, ya koma gida ya shiga ɗakinta, ya
tarar tana ta baccinta, kamar ya tashe ta, sai ya fasa, ya koma ɗakinsa ya
kwanta.
Bai farka ba, sai wajen tara na safe, a gaggauce ya yi
sallar asuba, ya fito falo, ba ta nan ya shiga ɗakinta, tana kwance ta takure
wuri ɗaya.
"Kin tashi?" Ta jinjina masa kai almar eh.
"To taso ki karya ki sha magani"
Ta ce "To, bari na yi wanka nayi brush"
A hankali ta lallaɓa jikinta, ta shiga ta yi wanka, ta canza
kaya ta fito falon.
Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Ina kwana?"
"Lafiya ƙalau, bari na kawo miki abinci"
Kitchen ya je ya ɗaukko kofi, da shayin da ya zo da shi a
flsk, da uban ƙwan da ya saka shahida ta soya masa.
Ya ajiye mata a kausashe ya ce "Gashi nan ki karya, ki
sha magungunan da suka baki. Saura ki ƙi ci wani ciwon ya kuma kama ki"
Ta na fara ci ta ji ta ƙoshi, amai ma take ji.
"Wai ba kya so ne ki ke jagwalgwalawa?"
Ta ce "Na ƙoshi ne"
"A ɗan abun da ki ka ci ne har kin ƙoshi" ya taɓe
baki, ya miƙa mata magungunan ta karɓa ta sha.
Ya bata wayarsa ya ce "Saka mini lambarki, idan da wani
abuk sai ki kira ni fita zan yi"
Kallonsa tayi da mamakin yana sane ko wulaƙanci ne, ya sanya
yake tambayarta lambar waya.
"Bani da waya" ta amsa kanta a ƙasa.
Ya mayar da wayarsa aljihunsa ya ce "Shikenan, maganar
da nayi miki, ki yi tunani a kai, a ɓangarena ni ina ganin hakan shi ne mafita
kawai, amma ki yi tunani abun da ki ka yanke, ki sanar da ni".
Dummm ƙirjinta ya buga, kenan haryanzu yana kan bakansa? Ba
ta ce masa uffan ba, ya fice.
Rasa abun yi tayi, duk da ba ta da tsarki, tayi alwala ta
zauna ta kalli gabas, tayi ta addu'a a kan lamarin rayuwarta.
Can wurin su Walid ya tafi, in da suke zama su yi
shaye-shaye, su naɗa wiwi.
Walid ya kalli Al'amin ya ce "Maza lafiya kuwa?
Yanayinka ya nuna kamar akwai damuwa".
Banza ya yi wa walid, dan haka shi ma ya share shi, ya
cigaba da aikin gabansa.
Sai kuma can ya ce "Mai laya"
"Na kiyayi mai zamani, ya aka yi?"
"Dama yara matasa suna hawan jini ne, ba sai tsofaffi
ba?"
Ya ce "Eh to, na ji an ce akwai wanda ake haifar su da
shi ma, amma hawan jini a matasa, maybe damuwa ce ko gado".
Ya jinjina kai.
Liti ya ce "Maza ko kai hawan jinin ke damu? Kana da
'yar madara, ai ba zaka yi hawan jini ba"
Tsuke fuska ya yi, jin liti ya kira jauhar da 'yar madara.
Gidansu Al'amin, Abbu ya shirya zai fita ya kalli rahila ya
ce "Yakamta idan an janye yajin aikin nan, ku je ku duba matar yaron
nan"
Rahila ta ce "Taɓ haka kurum, su dai yaran su je ni in
je ya illata ni a banza? Su dai su je"
Abbu ya ciro kuɗi a aljihunsa ya ce "Amira, ga kuɗi nan
ku hau mota, ga dubu biyar ku saya mata fruit ku kai mata, na ji an ce zuwa
jibi in Allah ya kaimu, za a janye yajin aikin, sai ku je ku duba jikin nata,
kafin na samu na je nima"
Ta amsa da to Abbu. Sai dai bayan fitarsa Amira ta ce
"Na samu na saka data, dan ba za ta ci 5k ɗin nan ba".
Shahida ta ce "Wallahi kuwa da sai na gaya masa, ai ba
haka ake yi ba" haka suka cigaba da faɗan su na sakonni.
Jikinta ya ɗan yi sauƙi, sai dai ba ta daina ciwon kai ba,
ga damuwar abun da Al'amin ya sake nanata mata, kenan yana nan a kan bakansa na
rabuwa da ita.
Kusan kwanaki biyu, ba ta bari su zauna wuri ɗaya, saboda
kar ya sake tayar mata da maganar.
Ya gama karyawa, yana kallonta tana ta shirin dutsenta,
karyawar ma ba ta yi ba, kamar yayi magana kawai ya shareta, ya tashi ya fita.
Su halimatu suka shigo, suka tayata aikace-aikace, sannan
suka koma gidansu.
Tana falo tana karatunta tana shirin dutse, aka yi sallama a
tsakar gida.
Ta amsa tare da bayar da izinin a shigo, 'yan mata ne da
zasu girme mata su biyu, suka shigo falon.
Jauhar ta faɗaɗa fara'arta tayi musu maraba.
Suka gaisa da ɗayar, ɗayar kuwa sai hura hanci take yi.
Shahida ta ce "Kin gane mu kuwa?"
Jauhar ta ce "Na gane wannan ranar da na je gidan, mun
haɗu da ita ai, ƙannensa ne ko?"
Shahida tayi murmushi ta ce "Kin canka"
"Sannunku da zuwa, baku taɓa zuwar mana ko sau ɗaya
ba"
Shahida ta ce "Ai da yake ba ma zama a gari saboda
school, shekaranjiya ya je gida ya ce baki da lafiya, Abbu ya ce lallai mu zo
duba ki kafin ya zo shi ma. Ya jikin?"
"Jiki Alhamdilillah na warware"
"To Allah ya ƙara afuwa, ko mu ce Allah ya raba lafiya,
ya kawo mana baby lafiya" Shahida tayi maganar tana murmushi.
Buɗe baki Jauhar tayi ta tashi da sauri ta ce "Bari na
kawo muku ruwa"
Ta kawo musu ruwa, lokacin ta hura gawayi, ta ɗora girki.
"Wancan ba tea flask ɗin mu bane?" Amira tayi
maganar tana nuna flask ɗin.
Jauhar ta ce "Ina ga naku ne, shi ne ya zo da shi, ina
ta so nayi masa maganar na waye, yanayin jikina ya hana, amma tun da Allah ya
kawo ku shikenan".
Suka cigaba da hira da shahida, yayin da Amira ke ta
harare-harare itakaɗai.
Shahida ta ce "Yaya muka ji da abun da ya faru da yaya
na rufe shi da aka yi, Ubangiji Allah ya tsare gaba"
Jauhar ta ce "Amin ya Allah, sharri ne ma aka yi masa,
amma duk da haka a tayamu da addu'a dan Allah, duk zai daina wataran sai
labari. Ina mama?"
"Haka ne, ana nan ana yi, mama tana nan ƙalau, tana
gaishe ki"
Shahida ta sake cewa "Nikam wai dan Allah ya aka yi
kuka haɗu da yaya ku ka yi aure, har ya taka ya je gida, sha biyu fa ta wuce,
ya ce na yi masa girki matarsa ce ba lafiya na ce wace 'yar baiwa ce haka? Kin
san a rayuwarsa ta duniya mata ba sa gabansa mu kanmu yadda ki ka san dodo haka
yake a wurinmu".
Jauhar za ta yi magana, Amira ta ce "Kin jiki da wata
magana shahida, a ina kuwa za su haɗu?, Tallarta fa aka kawo masa ba ta ji, ta
fanɗare a gida an rasa yadda za ayi da ita, aka haɗa su, aka jogana masa, da
yake shi ma ba sanin ciwon kansa yayi ba, ko ke baki san zancen ba? Kin zauna
kina ta zuba ni ina da wurin zuwa" ta ƙarasa maganar tana tashi tsaye ta ɗauki
jakarta tayi waje.
Gaba ɗaya jauhar ta yi sak, jikinta yayi shock, yayi wani
irin sanyi da mamakin maganganun Amira.
Cikin dirircewa shahida ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri,
wallahi ƙarya take yi, ina zuwa" ta lallaɓa ta ɗauki takalmanta cikin
tsananin jin kunya ta bi bayan Amira.
Biri yayi kama da mutum, duba da yadda aka yi auren cikin
gaggawa ko wata guda ba a rufa ba, ashe abun da aka gaya musu kenan a kanta?
A take ta ji ciwon kanta ya tsananta, ta fara tunanin wace
irin muguwar ƙiyayya ce tsakaninta da 'yan gidansu har haka.
Gidan su jauhar, Hafsa ta shigo daga zance, ta zauna a
tsakar gida, Yaya saifu ya shigo, ya kalleta ya ce "Daga ina ki ke?"
"Zance" ta bashi amsa kai tsaye.
"Wurin wa?" Tayi shiru tana kallonsa.
Ya ce "Wallahi kun yi asara, yanzu dama Saboda hafsa ta
auri mutumin nan, da yake son jauhar shiyasa ku ka aurar da ita ga mutumin
banza, wallahi ba ku kyautawa kanku ba, kuma da ikon Allah sai Allah ya saka
mata".
Mama ta ce "Saifu maganar me ka ke yi ne ban fahimta
ba?" Ji yayi kamar ya gayawa mama baƙar magana, sa'arta ɗaya mahaifiyarsa
ce, babu yadda zai yi da ita, kawai ya fice.
Mama ta ce "Zakiyya, da gaske mutumin nan ne yake zuwa
wurin Hafsa?"
Ta haɗa rai ta ce "Ni ma ban san zancen ba sai
yanzu"
Mama ta ce "To meye abun ɓoyewa ban da abunki, ai abun
farinciki ne a gare mu baki ɗaya. Dama ai jauhar ɗin ce ba ma son ya aura,
wallahi nayi murna haƙanmu t cimma ruwa".
Sai kuma ta ɗan saki ranta ta ce "Wallahi ina ta son na
gaya miki, abubuwa ne sun sha mini kai, kuma ba gama daidaitawa suka yi
ba"
"Ai bakomai, Allah ya tabattar mana da alkhairi"
suka gama maganar ta shiga ɗakinta, ta jinjina kai ta ce "Hmm zakiyya
kenan, baki da wayo da ni ki ke zancen, duk wanda ya rigaka kwana dole ya
rigaka tashi, zaki gane kuskurenki".
Yau tun la'asar ya dawo, kwana biyu ba ya yin dare, saboda
rashin lafiyarta sai dai fa ba zai ce mata sannu ba.
Ya kasa gane kan yanayinta, ta zuba masa abinci, ta koma
gefe ta yi shiru.
Ya gama ya tashi ya tafi ɗaki, zai ɗan kwanta ya huta, kasa
jurewa ta yi ta tashi ta bi bayansa.
Ta ssme shi, yana ta watso kayan wardrobe ɗin sa da ta gyara
da ƙyar.
"Master"
"Yeah" ya amsa ba tare da ya kalleta ba.
"Ƙanneka sun zo ɗazu baka nan"
"Ok" kawai ya ce, amma ƙasan zuciyarsa mamaki yake
yi, tun da ƙannensa ta ce, da ƙanwa ta ce ya san shahida ce kawai.
"Dan Allah abu nake son tambayarka, na san kai ba
ma'abocin ƙarya bane ba, na san ba zaka fara a wannan karon ba" bai amsa
ba, dama ba tayi tsammanin hakan ba, ta ce "Da gaske tallata aka kawo
maka, wai ba na ji na fanɗarewa iyayena shi ne aka aura maka ni?"
Ya ɗaga rigar hannunsa yana kallo kamar ba zai yi magana ba
sai kuma ya ce "Eh, haka na ji"
Cikin rauni ta ce "Kuma ka yarda?"
"Kusan haka, dan na san ba yadda za ayi a aureni haka
kurum babu dalili, a abun da bai wuce sati biyu ba"
Yayi maganar yana ajiye rigar, ya ɗauki wata, sautin da tayi
na ƙwacewar kuka ne, ya sanya shi ɗagowa a tsorace yana kallonta.
Cikin kuka ta ce "Wallahi ni ba lalatacciya ba ce, ban
fanɗarewa iyayena ba, dama kallon da ka ke yi mini kenan, kallon da 'yan uwanka
da sauran mutane suke yi mini kenan" da ƙyar maganarta take fita, saboda
numfashinta da ya fara sama.
Ya ƙaraso gabanta ya ce "Wai ke ba kya gajiya da kuka
ne? Komai kuka?"
Hannunta take fifitawa kusa da hancinta, alamar numfashi
yana bata wahala, da sauri ya ɗauketa ya fita da ita tsakar gida, ta lumshe
idonta hawaye na bin gefen fuskarta, sai dai ƙirjinta sai ɗagawa yake yi yana
sauka, alamar numfashin da ƙyar take yi.
"Ko mu koma asibiti? dama sati ɗaya suka bamu mu
koma"
Ta girgiza masa kai.
"Ba zaki daina kukan ba?" Maimakon ta daina, sai
ma wata sheshsheƙa da ta zo mata, ga numfashinta yayi nauyi.
Ya ciro wayarsa a aljihun wandonsa, ya kira liti.
"Maza ya ne?"
Viper ya ce "Kana ina?".
"Na shiga area raba kaya".
"Samo adaidaita sahu, ka zo gidana zan mayar da 'yar
madara asibiti"
"An gama mazaje"
Zai ajiye wayar, ta fara vibrating, ya ɗaga bai yi magana
ba.
"Honorable ya dawo, akwai taron gaggawa da zai yi, yana
son ganinka"
"Na ji"
"Dan Allah kar ka ɓata lokaci sosai, ka san zaɓe yana
ƙara gabatowa"
Ras jauhar ta gane muryar waye, muryar P.A ce, a take ta
jinjina rashin kunya irin na ɗan siyasa.
"Dan Allah kar ka je, idan ka tafi mutuwa zan yi"
"Allah ya jiƙanki"
A sanyaye ta ce "Amin, amma dan Allah ko na mutu kar ka
je ba na son ka din ga zuwa wurin 'yan siyasa"
"Ki yi mini shiru, idan ba haka ba zan tashi na bar
ki"
"Yi haƙuri" ta faɗa tana haki.
A hankali take iya takawa, saboda numfashinta, ya sakata a
napep ɗin da liti ya zo da ita, sannan ya shiga, liti ya zauna a gefe suka tafi
Asibiti.
File ɗin ta aka kai wa likita, shi da ita suka shiga, liti
kuma yana can waje.
Likita ya ce "Ka ƙi yadda ayi mata gwajin ciki, gashi
tana ta fama da an duba dai"
Ya ce "To duba"
Jauhar ta ce "Ni bani da komai".
"Shikenan, ki na da athma ne dama, wannan hakin da ki
ke yi?" Ta jinjina masa kai ta ce "A'a allergy ne, shi ma kuma tun
ina yarinya ne"
Al'amin ya kalleta, likitan ya sake cewa "Akwai magani
da ki ke sha ne? Ai kusan duk abu ɗaya ne, allergy ɗin da athma"
Ta girgiza kai ta ce "A'a ai na daɗe ba na shan magani,
addu'a nayi ta yi, ya daina tashi, tun ina ƙarama sosai ban kum jin
alamun sa ba"
Likitan yayi murmushi ya ce "Masha Allah, ka ga 'yar
baiwa, to a din ga sakamu a addu'ar mu ma, amma dai yanzu zan rubuta miki
magani, sai ki kiyayi hayaƙi, ko kin shaƙi wani abun ne?"
Ta ce "A'a kuka na yi kawai na ji na kasa numfashi
sosai"
Likitan ya jinjina kai, ya ce "Bari na duba bp naki na
gani".
Shi dai gogan bai ce komai ba, likitan ya duba bp ɗin ta
sannan ya ce "Zahra kina shan magungunan da na baki kuwa?"
"Ta jinjina kai alamar eh".
"A iyayenki akwai mai hawan jini?"
Ta ce "A'a"
Ya kalli Al'amin ya kalli jauhar ya ce "Akwai abun da
yake damunki ko?" Tayi yaƙe ta girgiza kai.
"Zahra, ita rayuwar duniya haƙuri ake yi. Malam ka
zauna da matarka ku tattauna idan a cikin aurenku matsalar take, a magance ta,
idan ba haka ba, hawan jinin nan zai iya taɓa mata zuciya, idan wani abu ka ke
yi mata da ba ta jin daɗin sa, ku tattauna dan Allah ku fahimci juna, amma tayi
ƙanƙanta da wannan ciwon"
"Zahra" likita ya kuma kiran sunanta, kamar yadda
ya gani a jikin file.
"Idan kun je gida, ki zauna da mijinki, idan damuwa ce
da ke, ki gaya masa, ki cire koma menene a ranki, mijinki da kuma al'umma baki ɗaya
muna buƙatar ki a raye" kawai ta sunkuyar da kai sai kuka.
Al'amin ya ce "Rubuta mana magungunan kawai mu
tafi"
Ya rubuta maganin, ya bawa Al'amin yana kallon jauhar cikin
tausayawa.
Al'amin ya kalleta ya ce "Mu tafi? Ko yau ma goyakin
zan yi?"
A hankali ta tashi tsaye, ya ce "Kin daina hakin?"
Ta ce "Ya ragu"
Ya saka hannunsa ya riƙe nata, suna tafe a hankali har suka
fito wajen asibitin in da pharmacy yake, ya saya mata maganin suka hau napep ɗin
da ya kawo su zuwa gida.
Shi dai bai iya rarrashi ba, bai ma san ta ina zai fara ba,
amma gaba ɗaya yanayin da jauhar take ciki, bai yi masa daɗi ba, ya san fiye da
rabin damuwar ta shi ne sila, ya ce su rabu kuma ta cigaba da kuka.
Tana kwance a kan kujera, tayi lamo, shi kuma yana zaune a
ƙasa, yana kaɗa ƙafa.
"Master"
"Mmm"
"Kana ta ɗawainiyar asibiti da ni, na gode sosai Allah
ya saka da alkhairi, ya ƙara arziki"
"Amin"
Ta sake cewa "Master"
Ya ɗago yana kallonta. "Dan Allah da gaske kallon mara
ji wadda ta fanɗarewa iyayenta ka ke yi mini?"
"Haka aka ce mini ai"
Ta ce "Aishikenan, shiyasa ka ke so ka sake ni?".
Ya ce "A'a kina takura mini ne kawai, kin isheni yanzu
ina zaman zamana ba zan fita ba, sai dai na zauna kula da ke"
Ta ce "To ka yi haƙuri, dan Allah kar ka fita yanzu, ji
nake kamar kana fita zan mutu" idan tayi zancen mutuwar nan, gabansa faɗuwa
yake yi, amma ya maze ya ce "To zan hanaki mutuwa ne?".
"A'a, amma dan Allah ka daina yi mini kallon mutuniyar
banza, dan Allah ka gaya wa 'yan gidanku, aje ayi bincike ma a kaina, wallahi
ba mutuniyar banza ce ni ba" ɗago ido yayi yana kallonta, kenan zuwansu ne
suka gaya mata wannan maganar, yayi shiru ya cigaba da latsa wayarsa.
"Master"
" 'yar madara" ya amsa bai kalleta ba.
Likita ya ce "Ka daina yi mini abun da na so, ka
tambaye ni abun da nake so ka daina yi mini"
Ya ce "Tom" ɗan murmushi ta yi, yau tayi sa'a ana
amsa mata ma.
"Yaushe zaka sake nin?"
Ya yinƙura ya tashi ya ce "Na fasa yanzu, sai an kwana
biyu, idan aka yi yanzu ina ga warewa zaki yi".
Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, ya shiga ɗakinsa.
Cikin ikon Allah, washegari ta tashi jikinta da sauƙi, sai
dai damuwar cewar ita fanɗararriya ce, ta kasa barinta.
A tsakar gida ya taso, ya tarar da ita, tana aiki.
"Ina kwana"
"Kin warke ne?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a, bayan ba ka zauna mun yi
maganar da likita ya ce ba"
"Akwai abinci ne?"
Ta ce "Eh shinkafa na dafa amma akwai sauran buredi in
dafa tea"
Ya ce "Zubo mini, ke ki sha tea ɗin"
Ta zubo abincin ta kawo masa, ya kalleta fuskarta duk ta faɗa.
"Amma yau ba zaka fita ba ko? Ka zauna ka kula da
ni"
Murmushi ya yi da gefen bakinsa, ta sake cewa "Idan ka
gama cin abincin zan gaya maka abubuwan da nake son ka daina yi mini, ko sannu
baka yi mini bama".
Tayi ta zuba, amma yayi gum.
Wayarsa da take ringing ya ɗaga ya ce "Ina sane zan zo
yanzu"
Ta haɗe rai ta ce "Amma ba fita zaka yi ba ko?"
Ya ce "Fita zan yi"
"Ni dan Allah ka zauna ka kula da ni" shagwaɓa da
rikici kawai take yi masa tsakanin jiya da yau, kamar yau an cire mata tsoron
sa.
Ta tashi ta ɗauki kwanukanta, ta tafi kitchen cike da
takaici. Ko ba zai kulata ba, tana son ganinsa a gida.
Sosai ta ji ranta ya yi mugun ɓaci fitar da zai yi, ɗan
tattalin da aka yi mata jiya zuwa yau yayi mata daɗi, duk da ana yi ana haɗe
mata rai.
Tana cikin ƙunƙuni, ya fito da sauri hannunsa da wayarsa a
kunnensa, hannunsa ɗaya da makamin da yake kira da iraƙi.
Ya ce "Gani nan, ka duba bayan nan, russiata da
sweazland suna nan, ka ɗaukar mini su, kar ku bari su motsa, gani nan
zuwa" hannunsa ɗaya yana soke makaminsa iraƙi a cikin ƙugunsa.
Ya ce "Fitar gaggawa ta kama ni, idan nayi dare ban
dawo ba, ki rufe ƙofa, duk wanda ya buga kar ki buɗe, idan na dawo na
hauro"
Banza tayi masa, ta cigaba da yanka albasarta.
"Ke ba magana nake yi miki ba?" Shiru ta sake yi
masa.
Ƙoƙarin leƙawa yake yi, ya ga ko lafiya.
Kawai ya ga ta jefo masa murfin tukunya, a zatonsa ko ba ta
san me tayi ba, kawai ya ga ta sake jefo masa rariya.
Saroro ya tsaya cikin mamaki, ta cigaba da zaro kwanuka tana
jefa masa tana kuka, bai ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da suka haɗa ido ta
jefo masa ludayin hannunta a ƙirji.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Tunani ya fara yi, ko tana da aljanu ne.
Ganin idan ya ƙyaleta, fashe-fashe za ta yi, ya sanya shi
takawa ya riƙo hannunta, amma sai ƙoƙarin fizgewa take yi.
Kasancewar ba ta yi masa wahalar ɗauka, ya sanya ya danƙota
kamar kazar cikin akurki, aikuwa ta cigaba da fizge-fizge da ƙoƙarin ƙwacewa,
falo ya shiga da ita, ya tattara hannayenta ya riƙe, hakan ya sanya ta kasa
cigaba da ƙoƙarin ƙwacewar.
"Meye haka ki ke yi? Kanki ɗaya kuwa?"
Kallonta yake yi, har ta fara kuka, shi bai ma san me yayi
mata ta aikata hakan ba.
"Me nayi miki ki ke jifana?"
Cikin takaici ta kalleshi ta ce "Meye ma baka yi mini
ba, ni bani da wani amfani a wurinka, bani da ikon roƙon alfarmarka, komai ma
yi mini ka ke yi, ko yayi mini daɗi ko akasin haka, ba ka tausaya mini dama ka
tsane ni, so kake yi na mutu ka huta".
"To yanzu kuma me nayi miki?"
"Wuƙa fa ka ɗauka zaka fita, idan aka yi maka wani abun
ko ka yi wani laifin nikaɗai nake fama, sai su yaya walid da suke taimaka mini,
amma kai gaba ɗaya baka tausayina, ba ka tausayin maraicina saboda da ma ba so
na ka ke yi ba. Kodayeke ba laifinka bane, tun da sama ta ka aka aura maka ni,
bayan an gama ɓata ni a wurinka. Ko hira ba ka yi da ni, in tayi maka magana
kayi mini shiru, idan aka ga na mutu kai ne, sai ma na rubuta na bar wasiyya,
idan na mutu kai ka ƙarasa ni da takaici"
Yayi shiru ta din ga yi, tana faɗa tana kuka, sai da ta gama
tsaf, sannan ya miƙe ya ce "Ki kula da abun da na gaya miki, kar ki fita
kar ki bar gida a buɗe, idan na yi dare ki kwanta zan hauro".
Ta ɗaga idanunta da suka yi ja ta ce "Sai ka fita
ko?"
"Ai na ce idan ba zaki iya ba, ki koma gidanku ko ban
gaya miki ba?" Tayi shiru ranta na yi mata wani irin zafi, ya fita ya
kwashe kwanukan da ta watso waje ya fice.
Unguwar su ya nufa, faɗa ya haɗa ɗan unguwarsu, da ɗan
unguwar su madaki, yaron ya kwaso 'yan daba yaran madaki, sun shiga unguwar su
Al'amin su na ta faɗace-faɗace.
Yana zuwa chamber su, ya ɗaukko wuƙaƙensa, ya fita, sai dai
da ya je, yaran suka din ga darewa, saboda wanda suka taɓa karo da shi, sun san
irin ƙarfin da Allah ya yi masa.
Wani yaron madaki ne, da yake ji da tashen balaga da rashin
mutunci, ya sha gaban Al'amin yayi yana zage-zage yana ƙoƙarin saran Al'amin.
Ya jefar da wuƙarsa, ya nufi yaron, wanda suka san Al'amin
suka din ga ce masa ya gudu, kar ya bari ya kama shi, amma kasancewar ya yi wa
wiwinsa haɗin kauri da wata ƙwaya da suke yi wa laƙabi da 'yar fara, ya sanya
yake jin kansa a sama, ko barikin sojoji zai iya shiga yayi rashin mutunci.
Duk iya ƙoƙarin sa ya kasa saran Al'amin, saboda yadda yake
da zafin nama, wurin kare saran, wanda idan ba professional athlete ne ba, babu
lallai ya iya.
Ya shammaci yaron, ya soka masa iraƙi a cinyarsa, a take ya
kurma wani uban ihu, liti ne ya karyo kwanar, riƙe da nasa makamin yana ɗigar
da jini, "Mai zamani yi haƙuri, kar ka karya yaron nan" sai dai bai
rufe bakinsa ba, ya ga Al'amin ya fito da dogon harshensa, ya lashi laɓɓansa na
ƙasa da su, idan har yayi haka sai aiwatar da muguntar da yayi niyya, kan liti
yayi wani yinƙuri ya karya ƙafar yaron ya watsar da shi yana kururuwa.
"Mai zamani, yanzu zaka sake janyo mana faɗa, madaki
zai ce sai ya ɗauki fansa, da baka karya shi ba"
Ya ɗago jajayen idanunsa a slow, yayi wa liti wani irin
kallo ya ce "Ya zo ya ɗauki fansar a kaina, idan ya isa" ya wulwula
iraƙinsa, ya cafe ya yi gaba.
Kai tsaye gidan su ya tafi, da wannan wuƙar tana ɗigar da
jinin da ya soki yaron nan.
Yana shiga ya wuce falo, sai ganinsa suka yi a tsaye a kansu
da makami tsirarsa.
Salati suka fara yi da kururuwa, ya kalle su ɗaya bayan ɗaya,
"Me ya kai ku gidana?" Yayi maganar yana kallon shahida.
Cikin tashin hankali ta ce "Abbu ne ya ce Mu je mu duba
matarka".
"Shi ya ce ku je ku gaya mata cewar kangarewa ce ta
sanya aka yi aurena da ita? Ku je ku ci zarafinta?"
Cikin tashin hankali shahida ta ce "Ba ni na faɗa ba
Amira ce wallahi".
Rahila kuwa hankalinta ya dugunzuma, ta ce "Ka yi wa
Allah da ma'aikinsa ka yi haƙuri, dan Allah kar ka yi musu wani abu"
Ai kamar ta tunzura shi, ya saka wuƙa a wuyan Amira,
"Ya zama na farko ya zama na ƙarshe, ayi duk cin kashin da za ayi a kaina,
ban da 'yar mutane da ki ka haɗa kai ku ka cutar, idan aka kuma zan yi ɓarna,
wallahi sai na saka wa mutum ƙarfe"
Shahida ce ta iya cewa "In sha Allah ba za a sake
ba" yayi ƙwafa ya fita.
"Amira kin ga abun da ki ka ja mana ko? Da ya illatamu,
da kin cuce mu"
Amira kam kasa magana tayi, sai dafe ƙirji tana hakin tsoro.
Al'amin wuni yayi ranar, yana partrol da yaransa a unguwar,
saboda kar yaran madaki su zo su afkawa wanda bai ji ba bai gani ba.
Cikin ikon Allah, har dare yaran madakin ba su sake shiga
unguwar su Al'amin ba, duk da sun yi artabu sosai da wasu, dan sai da aka yi
masa rauni a cikinsa, ya kama hanyar tafiya gida.
Jauhar na falo tana karatun exam, duk da sun kusa kammala
jarrabawa.
Ta katangar ya diro kamar ɓarawo,s an samu cigaba, yanzu
idan ya ga dama ya kan yi salama.
Sallamarsa kawai ta amsa, ba ta sake kula shi ba, ya wuce ɗakinsa,
mintuna goma amma ba ta biyo shi ba, ya fito ya ce "A kawo mini ruwan zafi
zan yi wanka"
Ta tashi ba ta ce komai ba, ta ɗaukki flask, aurensa da ita
ta saba masa da wanka da ruwan ɗumi, saɓanin da da har a kuddudufi wankansa
yake yi ya ƙara gaba.
Yanzu kuwa kusan kullum, da an kawo wuta, take dafa ruwan a
heater, ta saka a flask.
Ta zo ta haɗa masa ruwan, sai dai ta ga kamar yana ɓoye wani
abu.
Kawai ta leƙa ta ga me yake ɓoyewa, yanka ne a gefen
cikinsa, ya saka rigarsa yana ƙara goge jinin kasancewar ba mai zurfi bane ba.
"Ka gani ko? Sai da ka je aka yanko ka ko? Abun da nake
ta gudu, sai da ka zubar da jini ko, ba za kai daina zuwa wurin da za a cutar
da kai ba ko master? Kodayake ma ni abun yake damu, kai ko a jikinka".
"Na ce ya dame ki ne? Ba jikina bane?" Idan ba
gizo idonsa yayi masa ba, hararsa ta yi ta fice.
Shi mamaki ma take bashi, tun da ta yi rashin lafiyar nan,
take rigima kuma kamar ta rage tsoron sa.
Ya shiga ya yi wanka, ya fito ya tarar da ita da ɗan ƙaramin
kwanon abinci, sai kuma kayan dressing, tun na lokacin da aka yi masa wancan
raunin.
Bai kulata ba, ya ja kwanon abincinsa ya cinye, awara ce da
miya, ya sha ruwa.
Ita ma ba ta kula shin ba, ta saka auduga da spirit tana
goge, kan ciwon, tana gogewa tsigar jikinta na tashi, kamar jikinta take
gogewa, shi kuwa kamar dutse latsa wayarsa ma yake yi.
Haushi ya isheta, ta kalleshi ta ce "Wai ba zafi
ne?"
"Eh babu, idan ma dirzawa ki ke da ƙarfi, dan na ji
zafi, ba na ji" ta tashi ta fice fuuu, tana yi masa fatan shiriya a ranta.
Kusan awa ɗaya da rabi, ya shigo mata ɗaki, ta yi sauri ta
tashi zaune, saboda ta san tsiyar da ta aikata masa.
Ya kunna fitila ya hau yi mata bincike a ɗaki.
"Me ka ke nema?"
Ya tashi ya nufo ta, ya miƙa mata hannu ya ce "Bani
kayana da ki ka sace mini yanzu"
"Ni ba na sata"
Ya ce "To baki nayi ki ka ɗauka? Ko kema kin fara sha
ne ban sani ba? Kodayeke biri yayi kama da mutum, da ki ka iya kallona ki ka
din ga jifana nan gaba ina ga swizaland zaki saka mini ina ga"
"Ni ba na shan komai, kuma ban ɗau komai ba".
"Ba ki ɗauka ba ya aka yi ki ka san a kan me nake
magana?" Tayi shiru ba ta ce komai ba.
Hankaɗata yayi, ya janyo ledar kayan shaye-shayen sa a cikin
bargonta.
"Na gaya miki idan kin gaji ba zaki iya zama ba, ban ɗaure
ki ba, ki ƙara gaba"
A ƙule ta ce "Ka ɗaure ni mana, zan tafi ba ka sallame
ni bane, ka rubuta ka gani idan ban tafi ba. Tun da baka da tausayi idan ba
mutuwa na yi ba hankalinka ba zai kwanta ba" tayi maganar tana sheshsheƙar
kuka.
Ya kalleta, gaba ɗaya ko faɗan ba ta iya ba, voice ɗin ta
sam ba na masu faɗa bane, shagwaɓa kawai take yi.
Ya ce "Kin yanke hukunci kenan? Ai da kin gaya mini da
duk ba a zo nan ba, zan rubuta na baki, dama na gaji".
"Kuma wallahi idan ka yi shaye-shaye kai da Allah"
Bai kulata ba, ya jefo mata kwalin sabuwar waya gal, ya ce
"Gashi nan, akwai layi a ciki na yi rijista, idan kuma na yi wani laifin
na gudu ke za a kama".
"Bana so" ta faɗa tana kwanciya, duk da ƙasan
zuciyarta tayi mamakin wayar.
Ya saka hannu ya ɗauka ya ce "To kin huta" ya fice
ya bar ɗakin.
Ta kwanta ta yi shiru, sai ta fara tunanin ya aka yi ya ɗaga
mata ƙafa ya ƙyaleta, sai kuma ta ga rashin kyautuwar abubuwan da ta yi masa.
Bayan sallar asuba bacci ta koma, ƙarfe takwas da rabi ta
farka, tana ƙoƙarin saukkowa daga kan gadon, tayi tozali da farar takarda da
biro. Gabanta ya faɗi ta ce "Na shiga uku sakin nawa ya yi?" Ba ta taɓa
takardar ba, ta saukko a sukwane ta tafi ɗakinsa sai dai baya nan ya fice.
Gaba daya jikinta yayi sanyi, sai yanzu ta ƙara jinjina
girman wauta da aikata.
Yau rahila har gidan su jauhar ta je, suka ƙule a ɗaka ita
da Anty Zakiyya suna ta surutu da shewa.
"Zakiyya ina ga 'yar ku fa an gamu laulayi take
yi"
"Kai haba dan Allah"
"Wallahi da gaske, ke 'ya mace shu'uma komai
ƙanƙantarta, kin san yaron nan har gida ya zo da wuƙa ya gama ta'addancin sa
tana zubar da jini, zai yi mini hauka a gida wai su Amira sun je masa gida sun
yi matarsa ko me oho musu, na ga tashin hankali na ce iyee yanzu har ta samu
wannan matsayin. Wallahi mamaki nake yadda ta iya zama da yaron nan"
Zakiyya ta ce "Ba ki ganta ba kamar sokuwa, kafin ki ga
ta yi fushi, ko tayi zuciya da abu za a jima, ko kuma kawai tsabar ƙarfin hali
ne da ƙi faɗi ba"
Rahila ta ce "Sai ta yiwu, ya ake ciki da maganar
hafsa?"
"Mu na nan ana ta murginawa, ana shirin kawo kuɗin
aure, na ce lallai ta ce masa a haɗo da kayan lefe, ana sallacewa ayi auren,
duk da wannan matar ta nuna bakomai na san tsohuwar muguwa ce, wataƙila wani
abun zata kitsa, dan haka kan tayi wani yinƙuri ayi a wuce wurin".
"Yauwwa kar ki kuskura ki sakankance ko ki yadda da
ita, ni ban zaci lamarin ma zai zo da sauƙi haka ba, ku cigaba da tatsarsa kuna
tarin kayan aure"
Zakiyya ta ce "Ke kin ga hidima, ai ni dai Allah ya
kashe ya bani, da yanzu sai dai mu ga ana yi wa waccan yarinyar jauhar"
Rahila ta kwashe da dariya ta ce "Ga mijinta can suna
fama, amma wallahi ya fara son yarinyar nan, kai amma ba ƙaramin haƙuri take yi
ba bala'i Allah ya kyauta" suka cigaba da hirarrakinsu, da shirin biki.
Misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare, suka fito daga taron
meeting, daga ofishin jam'iyya, sakamakon gabatowar manyan zaɓuka da za a
gudanar a cikin Nigeria.
Yau bai san iya adadin meetings ɗin da ya yi attending ba,
suka jero da shi da mataimakin firaministan jam'iyya na jiha, ya ɗan yi miƙa ya
ce "Kai, yau na gaji over"
"Kai honorable, da an yi babban zaɓe an wuce wurin,
haka ne, ka san ban yi sati da shigowa daga Abuja ba, can ma wasu tarurrukan
ne, abun duk babu sauƙi, ina ta ƙoƙari in sha Allah sai na kawowa excellency
yankina, ina nan a satin nan zan yi empowerment na matasa, kuɗina duk sun tafi
a campaign ɗin nan"
"Kar ka damu honorable, hannun jari ka saya, da an wuce
wurin sama zaka din ga kwashe ribarka, ka mayar da uwar da ribar ka ɓace ba
zasu sake ganinka ba, sai bayan shekara huɗu" suka kwashe da dariya.
Suka yi sallama, kowa ya nufi motarsa, ko da ya je gida,
matarsa tuni tayi bacci, yayi wanka ya nemi wuri ya kwanta, dama ba yunwa yake
ji ba, sai dai bacci ya gagare shi, ya din ga juyi a kan gadon, ga gajiya ga
baccin yana ji, amma ya kasa ya ɓuge da lissafe-lissafe abubuwan da yake son yi
idan ya dace ya samu ya ci zaɓen nan.
Ji yayi kamar kansa zai fashe, saboda stress kawai ya tashi
ya ɗauki mukulli, ko direba bai nema ba ya hau motarsa ya fice.
Yamma da gari yayi, ya hau kan titin gwarzo road kasancewar
dare ne, titin babu ababen hawa, ya sauke glas ɗin motar kaɗan, yana tafe a
hankali yana shaƙa wani abu a hancinsa. Sai d yayi nesa da cikin gari sosai,
sannan ya yi parking a gefen hanya, ya rufe glasan motar, ya cigaba da shaƙa
abun nan, kusan mintuna talatin, sannan ya juyo kan motar ya nufi dawowa yana
tafe iskar kan titin nan na ratsowa cikin motar, sannu a hankali har ya koma
gida.
Jauhar kuwa tun da tayi tozali da takardar nan ta kasa
nutsuwa, ta kasa zaune ta kasa tsaye, kuma taƙi buɗe takardar, da ta leƙa ta
hangota ma, sai ta yi sauri ta fito daga ɗakin, ta din ga lissafa irin halin da
za ta shiga idan ta koma gida, da irin dariyar da za su yi mata.
Kuma yaƙi dawowa, har dare ba ta ganshi ba, hakan ya ƙara
sanyata cikin tashin hankali, ba irin tunanin da ba ta yi ba, har ta fara
tunanin ko da ya saketa, barin gidan yayi gaba ɗaya, sai dai kayansa suna nan,
dan ita ta gyara ɗakin ya watso da komai ya bar mata a wurin.
Sai sha biyu saura ya dawo, idonta biyu ya dawo ba ta yi
bacci ba, sai da ta tabattar ya shiga ɗakinsa, sannan ta ɗauki takardar ta
bishi ɗakinsa.
Yana kwance a kan katifarsa, ya cika ɗakin da warin taba.
Yanayinsa ya nuna a buge yake, saboda fitilar ɗakinsa a
kunne take, ya haye katifa ya mimmiƙe idanunsa sun yi ƙanana da ƙyar yake ɗaga
su, kallo ɗaya ya yi mata ya mayar da idonsa ya lumshe.
"Master sai da ka rubuta takardar nan hankalinka ya
kwanta ko?"
Bai buɗe idonsa ba ya ce "Ke ki ka ce na rubuta"
"Kuma sai ka rubuta ɗin ko? Saboda ina fargabar kar ka
sake ni, bakomai maraici ne ya janyo mini, Allah ya gani na yi iya yi na, na yi
biyayyar aure, amma kullum kallona ka ke yi wadda ta takura rayuwarka, ga
takardarka nan, ban ma buɗe ba balle na san meye a ciki, kuma wallahi ban saku
ba" ta dire masa takardar a jikinsa, ya ziro harshensa tare da naɗe shi ya
mayar, ya gyara kwanciyar sa, har ta gama surutanta, bai kuma motsawa ba.
Kasa bacci tayi, ta ɗaura alwala ta tayar da salla, ta din
ga addu'a Allah ya sa ya fasa sakinta, saboda ita a ganinta gara ƙalubalen
gidan Al'amin a kan na gidansu.
Duk rintsi ba zai daketa ko ya ci mutuncin ta ba, ko yi mata
sharri ba, sai dai miskilancinsa da gaya mata baƙar magana wasu lokutan da har
daɗi take ji ya kulata, ciyar da su kuma da take yi mafi yawan lokuta baya
damunta, sai ma yi wa Allah godiya da take yi da ko yaya ba ya hanata abun da
zata sarrafa su ci, ko yaya ta kasa abun sayarwa za a saya dan ma ana yi mata
mugunta.
Bayan sallar asuba tayi shiru tana tunani, ta ga sam ba ta
kyauta ba, wasu abubuwan da ta yi masa, tun daga jifansa da kwanuka, har zuwa
tsiwar da ta yi masa, ita tayi mamaki ma da ya ƙyaleta.
Yau ba ta iya komawa bacci ba, ta fito aikace-aikacen ta,
tana yi tana leƙawa ko ta gani ko ya tashi.
Tana falo ta jiyo motsinsa, ta tashi ta shiga ɗakin da
sallama.
Ya amsa mata, ba tare da ya kalleta ba.
Jiki a sanyaye ta durƙusa ta ce "Master ina
kwana?"
"Lafiya ƙalau"
"Ka tashi lafiya, ya ciwonka?" Sai a wannan karon
ya kalleta sai dai bai ce komai ba.
"Master dan Allah dan Annabi ka yi haƙuri ka yafe mini,
abubuwan da na yi maka kwanan nan ban kyauta ba, dan Allah ka yi haƙuri ba zan
sake ba, wallahi ni ba mara kunya ba ce, kawai na rasa ya zan yi da wasu
abubuwan ne, damuwa tayi mini yawa, dan Allah ka yi haƙuri idan ka sakenin ma,
ka yi haƙuri ka mayar da ni" tayi maganar cikin rauni.
Ya lumshe idanunsa ya ce "Bani wuri zan kunna
hayaƙi"
Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri master, ka
yafe wa 'yar madara ɓacin rai ne ba zan sake ba, na san ban kyauta ba, dan
Allah ka yi haƙuri"
"Sai fa kin tafi, kin isheni ne kawai takura mini ki ke
yi"
"Dan Allah ka yi haƙuri, na daina takura maka, har
cincin na yi maka jiya, in kawo maka?"
"Eh ki kawo mini, sai fa kintafi"
"Da ka san abun da hakan ka iya haifar wa rayuwata, da
baka sake ni ba, dan ka ga ina ta roƙonka shikenan, duk ranar da ka bari na bar
rayuwarka na bar ta har abada lokacin da zaka so ka ganni da kuɗi ba zaka ganni
ba".
"Eh na ji, kafin ki fara ɗaukar makami, gara mu rabu,
ungo takardarki tafi da ita" yayi maganar yana danƙa mata takardar da ya
warware. Ta rintse idanunta, tuni ta fara kuka, ta buɗe idanunta ta sauke a kan
kyakkyawan rubutunsa, dan ganin saki nawa ya yi mata.
*Ba zan dawo da wuri ba, na bar kuɗi a kan katifata ki sai
wani abun ki ci*
Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, ta ce "Shi ne ka yi
ta wahalar da ni? Dama ba sakina ka yi ba, ka sakani kuka?"
Hamma yayi, yayi shiru ta ce "A'uzibillah" duk
gurbin da ya yi wani abu, yakamata ya yi addu'a bai yi ba, sai tayi masa.
Ta ce "Aishikenan amma dan Allah ka yi haƙuri abubuwan
da na yi maka ka yafe mini"
"To, ki bani wuri zan sha abu"
Ta ce "To bani wayar da ka bani jiya" gefen
katifarsa ya nuna mata, ta tashi ta ɗaukkota a kwali.
Ta kalleshi ta ce "Yanzu dan Allah wannan ta wa ce
master? To kai ina taka?" Ya nuna mata keypad ɗin sa.
"Wallahi ko a mafarki ban taɓa tunanin riƙe waya ba,
yaya saifu ya taɓa bani keypad mama ta ƙwace, Allah ya saka maka da alkhairi ya
saka ka a aljanna, Allah ya nuna mini ranar da zaka daina shan komai, ka zama
limami saboda salihancinka, Na gode master na gode sosai da sosai" tayi
maganar tana tattaɓa wayar.
"To excuse me, ina son yin caji"
"To yi mana"
Ya ce "Ki fita ki bani wuri dai, kar ki sume mini yau
bani da kuɗin zuwa asibiti"
Maƙale kafaɗa tayi, ta ce "Master, wai yaushe zaka kai
ni na gaida mama ne? Da wurin hajiya ma?".
"Wace maman?"
"Mamanka mana, bamu taɓa zuwa ba, na san wadda na gani
a gidanku ba ita ce mamanka ba"
"In ji wa?"
Jauhar ta ce "Babu uwar da zata zauna hankalinta a
kwance, alhali an yi wa ɗanta sharri an tsare shi".
"Mama ta mutu" ji tayi kamar ya soka mata mashi,
ta kalleshi ta ce "Kai ma ka san pain ɗin master? Ka girma da ita ka
santa?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
Jiki a sanyaye ta ce "Ni ban ma santa ba, ina yawan
takura ƙwaƙwalwata, dan na tunota, da rayuwar da muka yi tare, amma bana iyawa,
baba ne yake da hotonta, nayi-nayi ya bani, ya hanani, idan na shiga ɗakinsa
zan gyara masa, sai na ɗauki hoton in yi ta kallo ina jin daɗi, duk da ina jin
kewarta, ina son in san yaya take ya halinta yake, yadda su mama suke faɗa ne
ko akasin haka? Kawai saboda Baba ya saka hoton a cikin wallet ɗin sa, ya ce
zai kai a wanko wani ya saka a yi enlarging ɗin sa ya bani, mama ta ɗauki hoton
ta yayyaga, ta watsar wallahi ji na yi kamar ta yaga zuciyata, bana riƙo idan
an yi mini laifi mantawa nake yi, ana yawan cewa bani da zuciya amma haryanzu a
raina, na kasa jin cewa na yafe wa mama abun da ta yi mini.
Da farko da na taso, na zata mama ce ta haife ni, daga baya
na gane ba ita haife ni ba, sai na fara tunanin ko kawai faɗowa na yi ko tsinto
ni aka yi, kowa yana da uwa ban da ni, wataƙila a haka aka haifeni, daga baya
na yi tunanin ko kawai 'yar aiki ce ni, na zata 'yan aiki duk ba su da iyaye.
Daga baya na gane baba ne babana, uwa ce bani da ita, sannu a hankali kuma na gane
ina da uwa amma bata duniyar.
Sai dai ba na jin daɗin irin yadda su mama ke aibata mamana,
duk da ba ta raye ban san ta ba, har suna cewa mayya ce ta taɓa kama su ma,
amma baba yana faɗar cewa mamana mutuniyar kirki ce, irin halina ɗaya da ita,
haka yaya saifu ma yana faɗa.
Mama ce mariƙiyata, na so in tashi kamar ita ce wadda ta
haife ni, amma ƙiriƙiri sai ta nuna mini banbanci ba ita ta haife ni ba. Ta
saka aka cire ni daga makarantar kuɗi, aka mayar da ni ta gwamnati wai ba na
gane karatu ni daƙiƙiya ce, kuma ni babu mai kula da ni, ko koya mini
assignment komai ni nake yi wa kaina gashi baba ba ya iya magana a kan abun da
ake yi mini.
Ita kuma anty Zakiyya cin zali na zahiri, na daku a wurinta,
duk ba wannan ba ni ya riga ya wuce, kawai haryanzu ina jin zafin yaga mini
hoton uwata da mama tayi, da ƙazafin nan da suka yi mini, na fanɗarewa, na san
zan yafe musu wataran amma ba yanzu ba.
Ina son in ga mutum yana hira da mamansa, ko suna wasa irin
na ɗa da uwa, abun yana burgeni, ko mutum ya din ga gaya wa mamansa damuwarsa
da daɗi master, wataƙila kai ka samu wannan damar ni kuwa ban samu ba, maybe da
mamanka ta yi tsawon rai wannan rayuwar za ta zo maka da sauƙi". Tana gaya
masa raɗaɗin abun da take ji a zuciyarta yana raguwa, duk da kuka take yi.
Ya ce "You are missing her?" Yayi maganar yana
kallonta.
Ta jinjina masa kai ta ce "So badly"
"Ki yi mata addu'a" ta jinjina masa kai tana goge
hawayenta, a take shi kuma ya tuna irin tasa rayuwar, duk da lokuta da dama
idan ka haɗu da wanda ku ke da irin matsala ɗaya ku ka yi sharing ana samun
releif, amma yanzu shi ba ya son doguwar magana idan ya fara ma gajiya zai yi,
duk da kwanan nan jauhar na isarsa da saka shi magana, kuma muddin ya gaya mata
shi nasa labarin, zata shiga damuwa dan haka ya ƙyaleta.
Duk da kuka take yi, ta fara ɗaukarsa a hoto tana murmushi
ta ce "Kai zan fara yi wa hoto da wayar nan, haryanzu mamaki nake yi, wai
master ne ya saya mini waya, Allah dai ya sanya mini kai a cikin aljanna ya
jiƙan mama, ya ja da ran wanda suka rage mana, Allah ya goyi bayanka ya yi maka
jagora a cikin lamuranka. Kai master na rasa wace addu'ar ma zan yi maka, na
rasa wace irin godiya zan yi maka ma"
Har cikin ransa ya ji daɗin Addu'ar da take yi masa.
Ya kuma amsa da Amin.
"To mun gama ki tafi"
"To me na yi maka ka ke korata?"
Ya ce "Sigari zan sha"
Ta ɓata fuska ta ce "Da sassafen nan ba ka ci komai ba,
sai ka fara da hayaƙi, haba mai babban suna, idan a baya babu wanda ya damu da
lafiyarka, ni ina son ka yi lafiya, ka rayu saboda ka ajiye 'yar madara, yau
dai ɗaya ayi haƙuri dan Allah a ɗaga ƙafa kar a sha da sassafen nan" kamar
shashasha haka yake bin ta da kallo, ta karɓe lighter da sigarin hannunsa, har
da ta gefe ta cikin kwali ta tattaresu.
"Bari na dafa mana shayi, cincin na yi jiya, amma na
kasa ci saboda damuwa, ka yi brush sai ka fito ka karya, kuma zan din ga leƙowa
saura na ga mutum ya sha wani abu"
Sunkuyar da kai ya yi, yana murmushi da gefen bakinsa.
Jauhar ta samu na yi, lambar baba ta kira, yana ɗagawa ko
gaisawa ba su yi ba ta ce "Baba na yi waya"
Baba ya ce "Masha Allah Alhamdilillah, ina tayaki murna
waliyya"
"Ka hau what's app mu yi video call"
Baba ya ce "To shikenan waliyya" Al'amin ya
kalleta ya maimaita waliyya a ransa, lallai ta ci sunan da mahaifinta ya kirata
da shi.
"Master, nan ne wurin video call ɗin ko?" Ya
jinjina mata kai alamar eh.
Tana kira baba ya ɗaga fuskarsa ta Bayyana a screen ɗin
wayar.
"Baba wayata touch screen ce mai kyau".
Baba yayi dariya ya ce "Masha Allah, Allah ya sanya
alkhairi."
"Amin, ina su yaya saifu su mama da Anty?"
"Duk suna nan lafiya, baba dan Allah kowa da kowa a
turo mini lambarsa, duk zan yi musu magana ta what's app, zan din ga kiran su
kuma a waya"
"To shikenan, a ina ki ka samu waya ne?"
"Master ne ya saya mini" sai kuma ta ce "Au
amm maigidan ne ya sai mini"
Wani irin sanyi ya ratsa zuciyar baba, ya ce "Allah ya
saka masa da alkhairi, ya yi muku albarka baki ɗaya"
"Amin baba" ta kaste wayar.
"Master " ya ɗago ya kalleta.
"Na gode sosai" ya ɗan tsuke fuska ya ce "Kin
faɗa kin sake, ya isa haka"
"Bar ni na yi yabon gwani ya zama dole".
Tana cikin maganar hankalinta ya kai kan labarin da ake yi a
radio, wata mata ce take kuka, take roƙon gwamna, sarki da kuma jami'an tsaro
su kama Aminu mai dogon zamani bisa karya mata ɗa da yayi, ya soke shi da wuƙa,
an kai shi asibiti rai a hannun Allah gashi ba ta da ƙarfi, tana neman a bi wa ɗanta
hakkinsa.
Cikin tsananin tashin hankali, jauhar ta kalli Al'amin,
tamkar bai ji me aka faɗa a radiyon ba, sai tauna cin-cin yake yi ƙururus ƙurus
ko a jikinsa an mari dutse.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Tunani ya fara yi, ko tana da aljanu ne.
Ganin idan ya ƙyaleta, fashe-fashe za ta yi, ya sanya shi
takawa ya riƙo hannunta, amma sai ƙoƙarin fizgewa take yi.
Kasancewar ba ta yi masa wahalar ɗauka, ya sanya ya danƙota
kamar kazar cikin akurki, aikuwa ta cigaba da fizge-fizge da ƙoƙarin ƙwacewa,
falo ya shiga da ita, ya tattara hannayenta ya riƙe, hakan ya sanya ta kasa
cigaba da ƙoƙarin ƙwacewar.
"Meye haka ki ke yi? Kanki ɗaya kuwa?"
Kallonta yake yi, har ta fara kuka, shi bai ma san me yayi
mata ta aikata hakan ba.
"Me nayi miki ki ke jifana?"
Cikin takaici ta kalleshi ta ce "Meye ma baka yi mini
ba, ni bani da wani amfani a wurinka, bani da ikon roƙon alfarmarka, komai ma
yi mini ka ke yi, ko yayi mini daɗi ko akasin haka, ba ka tausaya mini dama ka
tsane ni, so kake yi na mutu ka huta".
"To yanzu kuma me nayi miki?"
"Wuƙa fa ka ɗauka zaka fita, idan aka yi maka wani abun
ko ka yi wani laifin nikaɗai nake fama, sai su yaya walid da suke taimaka mini,
amma kai gaba ɗaya baka tausayina, ba ka tausayin maraicina saboda da ma ba so
na ka ke yi ba. Kodayeke ba laifinka bane, tun da sama ta ka aka aura maka ni,
bayan an gama ɓata ni a wurinka. Ko hira ba ka yi da ni, in tayi maka magana
kayi mini shiru, idan aka ga na mutu kai ne, sai ma na rubuta na bar wasiyya,
idan na mutu kai ka ƙarasa ni da takaici"
Yayi shiru ta din ga yi, tana faɗa tana kuka, sai da ta gama
tsaf, sannan ya miƙe ya ce "Ki kula da abun da na gaya miki, kar ki fita
kar ki bar gida a buɗe, idan na yi dare ki kwanta zan hauro".
Ta ɗaga idanunta da suka yi ja ta ce "Sai ka fita
ko?"
"Ai na ce idan ba zaki iya ba, ki koma gidanku ko ban
gaya miki ba?" Tayi shiru ranta na yi mata wani irin zafi, ya fita ya
kwashe kwanukan da ta watso waje ya fice.
Unguwar su ya nufa, faɗa ya haɗa ɗan unguwarsu, da ɗan
unguwar su madaki, yaron ya kwaso 'yan daba yaran madaki, sun shiga unguwar su
Al'amin su na ta faɗace-faɗace.
Yana zuwa chamber su, ya ɗaukko wuƙaƙensa, ya fita, sai dai
da ya je, yaran suka din ga darewa, saboda wanda suka taɓa karo da shi, sun san
irin ƙarfin da Allah ya yi masa.
Wani yaron madaki ne, da yake ji da tashen balaga da rashin
mutunci, ya sha gaban Al'amin yayi yana zage-zage yana ƙoƙarin saran Al'amin.
Ya jefar da wuƙarsa, ya nufi yaron, wanda suka san Al'amin
suka din ga ce masa ya gudu, kar ya bari ya kama shi, amma kasancewar ya yi wa
wiwinsa haɗin kauri da wata ƙwaya da suke yi wa laƙabi da 'yar fara, ya sanya
yake jin kansa a sama, ko barikin sojoji zai iya shiga yayi rashin mutunci.
Duk iya ƙoƙarin sa ya kasa saran Al'amin, saboda yadda yake
da zafin nama, wurin kare saran, wanda idan ba professional athlete ne ba, babu
lallai ya iya.
Ya shammaci yaron, ya soka masa iraƙi a cinyarsa, a take ya
kurma wani uban ihu, liti ne ya karyo kwanar, riƙe da nasa makamin yana ɗigar
da jini, "Mai zamani yi haƙuri, kar ka karya yaron nan" sai dai bai
rufe bakinsa ba, ya ga Al'amin ya fito da dogon harshensa, ya lashi laɓɓansa na
ƙasa da su, idan har yayi haka sai aiwatar da muguntar da yayi niyya, kan liti
yayi wani yinƙuri ya karya ƙafar yaron ya watsar da shi yana kururuwa.
"Mai zamani, yanzu zaka sake janyo mana faɗa, madaki
zai ce sai ya ɗauki fansa, da baka karya shi ba"
Ya ɗago jajayen idanunsa a slow, yayi wa liti wani irin
kallo ya ce "Ya zo ya ɗauki fansar a kaina, idan ya isa" ya wulwula
iraƙinsa, ya cafe ya yi gaba.
Kai tsaye gidan su ya tafi, da wannan wuƙar tana ɗigar da
jinin da ya soki yaron nan.
Yana shiga ya wuce falo, sai ganinsa suka yi a tsaye a kansu
da makami tsirarsa.
Salati suka fara yi da kururuwa, ya kalle su ɗaya bayan ɗaya,
"Me ya kai ku gidana?" Yayi maganar yana kallon shahida.
Cikin tashin hankali ta ce "Abbu ne ya ce Mu je mu duba
matarka".
"Shi ya ce ku je ku gaya mata cewar kangarewa ce ta
sanya aka yi aurena da ita? Ku je ku ci zarafinta?"
Cikin tashin hankali shahida ta ce "Ba ni na faɗa ba
Amira ce wallahi".
Rahila kuwa hankalinta ya dugunzuma, ta ce "Ka yi wa
Allah da ma'aikinsa ka yi haƙuri, dan Allah kar ka yi musu wani abu"
Ai kamar ta tunzura shi, ya saka wuƙa a wuyan Amira,
"Ya zama na farko ya zama na ƙarshe, ayi duk cin kashin da za ayi a kaina,
ban da 'yar mutane da ki ka haɗa kai ku ka cutar, idan aka kuma zan yi ɓarna,
wallahi sai na saka wa mutum ƙarfe"
Shahida ce ta iya cewa "In sha Allah ba za a sake
ba" yayi ƙwafa ya fita.
"Amira kin ga abun da ki ka ja mana ko? Da ya illatamu,
da kin cuce mu"
Amira kam kasa magana tayi, sai dafe ƙirji tana hakin tsoro.
Al'amin wuni yayi ranar, yana partrol da yaransa a unguwar,
saboda kar yaran madaki su zo su afkawa wanda bai ji ba bai gani ba.
Cikin ikon Allah, har dare yaran madakin ba su sake shiga
unguwar su Al'amin ba, duk da sun yi artabu sosai da wasu, dan sai da aka yi
masa rauni a cikinsa, ya kama hanyar tafiya gida.
Jauhar na falo tana karatun exam, duk da sun kusa kammala
jarrabawa.
Ta katangar ya diro kamar ɓarawo,s an samu cigaba, yanzu
idan ya ga dama ya kan yi salama.
Sallamarsa kawai ta amsa, ba ta sake kula shi ba, ya wuce ɗakinsa,
mintuna goma amma ba ta biyo shi ba, ya fito ya ce "A kawo mini ruwan zafi
zan yi wanka"
Ta tashi ba ta ce komai ba, ta ɗaukki flask, aurensa da ita
ta saba masa da wanka da ruwan ɗumi, saɓanin da da har a kuddudufi wankansa
yake yi ya ƙara gaba.
Yanzu kuwa kusan kullum, da an kawo wuta, take dafa ruwan a
heater, ta saka a flask.
Ta zo ta haɗa masa ruwan, sai dai ta ga kamar yana ɓoye wani
abu.
Kawai ta leƙa ta ga me yake ɓoyewa, yanka ne a gefen
cikinsa, ya saka rigarsa yana ƙara goge jinin kasancewar ba mai zurfi bane ba.
"Ka gani ko? Sai da ka je aka yanko ka ko? Abun da nake
ta gudu, sai da ka zubar da jini ko, ba za kai daina zuwa wurin da za a cutar
da kai ba ko master? Kodayake ma ni abun yake damu, kai ko a jikinka".
"Na ce ya dame ki ne? Ba jikina bane?" Idan ba
gizo idonsa yayi masa ba, hararsa ta yi ta fice.
Shi mamaki ma take bashi, tun da ta yi rashin lafiyar nan,
take rigima kuma kamar ta rage tsoron sa.
Ya shiga ya yi wanka, ya fito ya tarar da ita da ɗan ƙaramin
kwanon abinci, sai kuma kayan dressing, tun na lokacin da aka yi masa wancan
raunin.
Bai kulata ba, ya ja kwanon abincinsa ya cinye, awara ce da
miya, ya sha ruwa.
Ita ma ba ta kula shin ba, ta saka auduga da spirit tana
goge, kan ciwon, tana gogewa tsigar jikinta na tashi, kamar jikinta take
gogewa, shi kuwa kamar dutse latsa wayarsa ma yake yi.
Haushi ya isheta, ta kalleshi ta ce "Wai ba zafi
ne?"
"Eh babu, idan ma dirzawa ki ke da ƙarfi, dan na ji
zafi, ba na ji" ta tashi ta fice fuuu, tana yi masa fatan shiriya a ranta.
Kusan awa ɗaya da rabi, ya shigo mata ɗaki, ta yi sauri ta
tashi zaune, saboda ta san tsiyar da ta aikata masa.
Ya kunna fitila ya hau yi mata bincike a ɗaki.
"Me ka ke nema?"
Ya tashi ya nufo ta, ya miƙa mata hannu ya ce "Bani
kayana da ki ka sace mini yanzu"
"Ni ba na sata"
Ya ce "To baki nayi ki ka ɗauka? Ko kema kin fara sha
ne ban sani ba? Kodayeke biri yayi kama da mutum, da ki ka iya kallona ki ka
din ga jifana nan gaba ina ga swizaland zaki saka mini ina ga"
"Ni ba na shan komai, kuma ban ɗau komai ba".
"Ba ki ɗauka ba ya aka yi ki ka san a kan me nake
magana?" Tayi shiru ba ta ce komai ba.
Hankaɗata yayi, ya janyo ledar kayan shaye-shayen sa a cikin
bargonta.
"Na gaya miki idan kin gaji ba zaki iya zama ba, ban ɗaure
ki ba, ki ƙara gaba"
A ƙule ta ce "Ka ɗaure ni mana, zan tafi ba ka sallame
ni bane, ka rubuta ka gani idan ban tafi ba. Tun da baka da tausayi idan ba
mutuwa na yi ba hankalinka ba zai kwanta ba" tayi maganar tana sheshsheƙar
kuka.
Ya kalleta, gaba ɗaya ko faɗan ba ta iya ba, voice ɗin ta
sam ba na masu faɗa bane, shagwaɓa kawai take yi.
Ya ce "Kin yanke hukunci kenan? Ai da kin gaya mini da
duk ba a zo nan ba, zan rubuta na baki, dama na gaji".
"Kuma wallahi idan ka yi shaye-shaye kai da Allah"
Bai kulata ba, ya jefo mata kwalin sabuwar waya gal, ya ce
"Gashi nan, akwai layi a ciki na yi rijista, idan kuma na yi wani laifin
na gudu ke za a kama".
"Bana so" ta faɗa tana kwanciya, duk da ƙasan
zuciyarta tayi mamakin wayar.
Ya saka hannu ya ɗauka ya ce "To kin huta" ya fice
ya bar ɗakin.
Ta kwanta ta yi shiru, sai ta fara tunanin ya aka yi ya ɗaga
mata ƙafa ya ƙyaleta, sai kuma ta ga rashin kyautuwar abubuwan da ta yi masa.
Bayan sallar asuba bacci ta koma, ƙarfe takwas da rabi ta
farka, tana ƙoƙarin saukkowa daga kan gadon, tayi tozali da farar takarda da
biro. Gabanta ya faɗi ta ce "Na shiga uku sakin nawa ya yi?" Ba ta taɓa
takardar ba, ta saukko a sukwane ta tafi ɗakinsa sai dai baya nan ya fice.
Gaba daya jikinta yayi sanyi, sai yanzu ta ƙara jinjina
girman wauta da aikata.
Yau rahila har gidan su jauhar ta je, suka ƙule a ɗaka ita
da Anty Zakiyya suna ta surutu da shewa.
"Zakiyya ina ga 'yar ku fa an gamu laulayi take
yi"
"Kai haba dan Allah"
"Wallahi da gaske, ke 'ya mace shu'uma komai
ƙanƙantarta, kin san yaron nan har gida ya zo da wuƙa ya gama ta'addancin sa
tana zubar da jini, zai yi mini hauka a gida wai su Amira sun je masa gida sun
yi matarsa ko me oho musu, na ga tashin hankali na ce iyee yanzu har ta samu
wannan matsayin. Wallahi mamaki nake yadda ta iya zama da yaron nan"
Zakiyya ta ce "Ba ki ganta ba kamar sokuwa, kafin ki ga
ta yi fushi, ko tayi zuciya da abu za a jima, ko kuma kawai tsabar ƙarfin hali
ne da ƙi faɗi ba"
Rahila ta ce "Sai ta yiwu, ya ake ciki da maganar
hafsa?"
"Mu na nan ana ta murginawa, ana shirin kawo kuɗin
aure, na ce lallai ta ce masa a haɗo da kayan lefe, ana sallacewa ayi auren,
duk da wannan matar ta nuna bakomai na san tsohuwar muguwa ce, wataƙila wani
abun zata kitsa, dan haka kan tayi wani yinƙuri ayi a wuce wurin".
"Yauwwa kar ki kuskura ki sakankance ko ki yadda da
ita, ni ban zaci lamarin ma zai zo da sauƙi haka ba, ku cigaba da tatsarsa kuna
tarin kayan aure"
Zakiyya ta ce "Ke kin ga hidima, ai ni dai Allah ya
kashe ya bani, da yanzu sai dai mu ga ana yi wa waccan yarinyar jauhar"
Rahila ta kwashe da dariya ta ce "Ga mijinta can suna
fama, amma wallahi ya fara son yarinyar nan, kai amma ba ƙaramin haƙuri take yi
ba bala'i Allah ya kyauta" suka cigaba da hirarrakinsu, da shirin biki.
Misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare, suka fito daga taron
meeting, daga ofishin jam'iyya, sakamakon gabatowar manyan zaɓuka da za a
gudanar a cikin Nigeria.
Yau bai san iya adadin meetings ɗin da ya yi attending ba,
suka jero da shi da mataimakin firaministan jam'iyya na jiha, ya ɗan yi miƙa ya
ce "Kai, yau na gaji over"
"Kai honorable, da an yi babban zaɓe an wuce wurin,
haka ne, ka san ban yi sati da shigowa daga Abuja ba, can ma wasu tarurrukan
ne, abun duk babu sauƙi, ina ta ƙoƙari in sha Allah sai na kawowa excellency
yankina, ina nan a satin nan zan yi empowerment na matasa, kuɗina duk sun tafi
a campaign ɗin nan"
"Kar ka damu honorable, hannun jari ka saya, da an wuce
wurin sama zaka din ga kwashe ribarka, ka mayar da uwar da ribar ka ɓace ba
zasu sake ganinka ba, sai bayan shekara huɗu" suka kwashe da dariya.
Suka yi sallama, kowa ya nufi motarsa, ko da ya je gida,
matarsa tuni tayi bacci, yayi wanka ya nemi wuri ya kwanta, dama ba yunwa yake
ji ba, sai dai bacci ya gagare shi, ya din ga juyi a kan gadon, ga gajiya ga
baccin yana ji, amma ya kasa ya ɓuge da lissafe-lissafe abubuwan da yake son yi
idan ya dace ya samu ya ci zaɓen nan.
Ji yayi kamar kansa zai fashe, saboda stress kawai ya tashi
ya ɗauki mukulli, ko direba bai nema ba ya hau motarsa ya fice.
Yamma da gari yayi, ya hau kan titin gwarzo road kasancewar
dare ne, titin babu ababen hawa, ya sauke glas ɗin motar kaɗan, yana tafe a
hankali yana shaƙa wani abu a hancinsa. Sai d yayi nesa da cikin gari sosai,
sannan ya yi parking a gefen hanya, ya rufe glasan motar, ya cigaba da shaƙa
abun nan, kusan mintuna talatin, sannan ya juyo kan motar ya nufi dawowa yana
tafe iskar kan titin nan na ratsowa cikin motar, sannu a hankali har ya koma
gida.
Jauhar kuwa tun da tayi tozali da takardar nan ta kasa
nutsuwa, ta kasa zaune ta kasa tsaye, kuma taƙi buɗe takardar, da ta leƙa ta
hangota ma, sai ta yi sauri ta fito daga ɗakin, ta din ga lissafa irin halin da
za ta shiga idan ta koma gida, da irin dariyar da za su yi mata.
Kuma yaƙi dawowa, har dare ba ta ganshi ba, hakan ya ƙara
sanyata cikin tashin hankali, ba irin tunanin da ba ta yi ba, har ta fara
tunanin ko da ya saketa, barin gidan yayi gaba ɗaya, sai dai kayansa suna nan,
dan ita ta gyara ɗakin ya watso da komai ya bar mata a wurin.
Sai sha biyu saura ya dawo, idonta biyu ya dawo ba ta yi
bacci ba, sai da ta tabattar ya shiga ɗakinsa, sannan ta ɗauki takardar ta
bishi ɗakinsa.
Yana kwance a kan katifarsa, ya cika ɗakin da warin taba.
Yanayinsa ya nuna a buge yake, saboda fitilar ɗakinsa a
kunne take, ya haye katifa ya mimmiƙe idanunsa sun yi ƙanana da ƙyar yake ɗaga
su, kallo ɗaya ya yi mata ya mayar da idonsa ya lumshe.
"Master sai da ka rubuta takardar nan hankalinka ya
kwanta ko?"
Bai buɗe idonsa ba ya ce "Ke ki ka ce na rubuta"
"Kuma sai ka rubuta ɗin ko? Saboda ina fargabar kar ka
sake ni, bakomai maraici ne ya janyo mini, Allah ya gani na yi iya yi na, na yi
biyayyar aure, amma kullum kallona ka ke yi wadda ta takura rayuwarka, ga
takardarka nan, ban ma buɗe ba balle na san meye a ciki, kuma wallahi ban saku
ba" ta dire masa takardar a jikinsa, ya ziro harshensa tare da naɗe shi ya
mayar, ya gyara kwanciyar sa, har ta gama surutanta, bai kuma motsawa ba.
Kasa bacci tayi, ta ɗaura alwala ta tayar da salla, ta din
ga addu'a Allah ya sa ya fasa sakinta, saboda ita a ganinta gara ƙalubalen
gidan Al'amin a kan na gidansu.
Duk rintsi ba zai daketa ko ya ci mutuncin ta ba, ko yi mata
sharri ba, sai dai miskilancinsa da gaya mata baƙar magana wasu lokutan da har
daɗi take ji ya kulata, ciyar da su kuma da take yi mafi yawan lokuta baya
damunta, sai ma yi wa Allah godiya da take yi da ko yaya ba ya hanata abun da
zata sarrafa su ci, ko yaya ta kasa abun sayarwa za a saya dan ma ana yi mata
mugunta.
Bayan sallar asuba tayi shiru tana tunani, ta ga sam ba ta
kyauta ba, wasu abubuwan da ta yi masa, tun daga jifansa da kwanuka, har zuwa
tsiwar da ta yi masa, ita tayi mamaki ma da ya ƙyaleta.
Yau ba ta iya komawa bacci ba, ta fito aikace-aikacen ta,
tana yi tana leƙawa ko ta gani ko ya tashi.
Tana falo ta jiyo motsinsa, ta tashi ta shiga ɗakin da
sallama.
Ya amsa mata, ba tare da ya kalleta ba.
Jiki a sanyaye ta durƙusa ta ce "Master ina
kwana?"
"Lafiya ƙalau"
"Ka tashi lafiya, ya ciwonka?" Sai a wannan karon
ya kalleta sai dai bai ce komai ba.
"Master dan Allah dan Annabi ka yi haƙuri ka yafe mini,
abubuwan da na yi maka kwanan nan ban kyauta ba, dan Allah ka yi haƙuri ba zan
sake ba, wallahi ni ba mara kunya ba ce, kawai na rasa ya zan yi da wasu
abubuwan ne, damuwa tayi mini yawa, dan Allah ka yi haƙuri idan ka sakenin ma,
ka yi haƙuri ka mayar da ni" tayi maganar cikin rauni.
Ya lumshe idanunsa ya ce "Bani wuri zan kunna
hayaƙi"
Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri master, ka
yafe wa 'yar madara ɓacin rai ne ba zan sake ba, na san ban kyauta ba, dan
Allah ka yi haƙuri"
"Sai fa kin tafi, kin isheni ne kawai takura mini ki ke
yi"
"Dan Allah ka yi haƙuri, na daina takura maka, har
cincin na yi maka jiya, in kawo maka?"
"Eh ki kawo mini, sai fa kintafi"
"Da ka san abun da hakan ka iya haifar wa rayuwata, da
baka sake ni ba, dan ka ga ina ta roƙonka shikenan, duk ranar da ka bari na bar
rayuwarka na bar ta har abada lokacin da zaka so ka ganni da kuɗi ba zaka ganni
ba".
"Eh na ji, kafin ki fara ɗaukar makami, gara mu rabu,
ungo takardarki tafi da ita" yayi maganar yana danƙa mata takardar da ya
warware. Ta rintse idanunta, tuni ta fara kuka, ta buɗe idanunta ta sauke a kan
kyakkyawan rubutunsa, dan ganin saki nawa ya yi mata.
*Ba zan dawo da wuri ba, na bar kuɗi a kan katifata ki sai
wani abun ki ci*
Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, ta ce "Shi ne ka yi
ta wahalar da ni? Dama ba sakina ka yi ba, ka sakani kuka?"
Hamma yayi, yayi shiru ta ce "A'uzibillah" duk
gurbin da ya yi wani abu, yakamata ya yi addu'a bai yi ba, sai tayi masa.
Ta ce "Aishikenan amma dan Allah ka yi haƙuri abubuwan
da na yi maka ka yafe mini"
"To, ki bani wuri zan sha abu"
Ta ce "To bani wayar da ka bani jiya" gefen
katifarsa ya nuna mata, ta tashi ta ɗaukkota a kwali.
Ta kalleshi ta ce "Yanzu dan Allah wannan ta wa ce
master? To kai ina taka?" Ya nuna mata keypad ɗin sa.
"Wallahi ko a mafarki ban taɓa tunanin riƙe waya ba,
yaya saifu ya taɓa bani keypad mama ta ƙwace, Allah ya saka maka da alkhairi ya
saka ka a aljanna, Allah ya nuna mini ranar da zaka daina shan komai, ka zama
limami saboda salihancinka, Na gode master na gode sosai da sosai" tayi
maganar tana tattaɓa wayar.
"To excuse me, ina son yin caji"
"To yi mana"
Ya ce "Ki fita ki bani wuri dai, kar ki sume mini yau
bani da kuɗin zuwa asibiti"
Maƙale kafaɗa tayi, ta ce "Master, wai yaushe zaka kai
ni na gaida mama ne? Da wurin hajiya ma?".
"Wace maman?"
"Mamanka mana, bamu taɓa zuwa ba, na san wadda na gani
a gidanku ba ita ce mamanka ba"
"In ji wa?"
Jauhar ta ce "Babu uwar da zata zauna hankalinta a
kwance, alhali an yi wa ɗanta sharri an tsare shi".
"Mama ta mutu" ji tayi kamar ya soka mata mashi,
ta kalleshi ta ce "Kai ma ka san pain ɗin master? Ka girma da ita ka
santa?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
Jiki a sanyaye ta ce "Ni ban ma santa ba, ina yawan
takura ƙwaƙwalwata, dan na tunota, da rayuwar da muka yi tare, amma bana iyawa,
baba ne yake da hotonta, nayi-nayi ya bani, ya hanani, idan na shiga ɗakinsa
zan gyara masa, sai na ɗauki hoton in yi ta kallo ina jin daɗi, duk da ina jin
kewarta, ina son in san yaya take ya halinta yake, yadda su mama suke faɗa ne
ko akasin haka? Kawai saboda Baba ya saka hoton a cikin wallet ɗin sa, ya ce
zai kai a wanko wani ya saka a yi enlarging ɗin sa ya bani, mama ta ɗauki hoton
ta yayyaga, ta watsar wallahi ji na yi kamar ta yaga zuciyata, bana riƙo idan
an yi mini laifi mantawa nake yi, ana yawan cewa bani da zuciya amma haryanzu a
raina, na kasa jin cewa na yafe wa mama abun da ta yi mini.
Da farko da na taso, na zata mama ce ta haife ni, daga baya
na gane ba ita haife ni ba, sai na fara tunanin ko kawai faɗowa na yi ko tsinto
ni aka yi, kowa yana da uwa ban da ni, wataƙila a haka aka haifeni, daga baya
na yi tunanin ko kawai 'yar aiki ce ni, na zata 'yan aiki duk ba su da iyaye.
Daga baya na gane baba ne babana, uwa ce bani da ita, sannu a hankali kuma na gane
ina da uwa amma bata duniyar.
Sai dai ba na jin daɗin irin yadda su mama ke aibata mamana,
duk da ba ta raye ban san ta ba, har suna cewa mayya ce ta taɓa kama su ma,
amma baba yana faɗar cewa mamana mutuniyar kirki ce, irin halina ɗaya da ita,
haka yaya saifu ma yana faɗa.
Mama ce mariƙiyata, na so in tashi kamar ita ce wadda ta
haife ni, amma ƙiriƙiri sai ta nuna mini banbanci ba ita ta haife ni ba. Ta
saka aka cire ni daga makarantar kuɗi, aka mayar da ni ta gwamnati wai ba na
gane karatu ni daƙiƙiya ce, kuma ni babu mai kula da ni, ko koya mini
assignment komai ni nake yi wa kaina gashi baba ba ya iya magana a kan abun da
ake yi mini.
Ita kuma anty Zakiyya cin zali na zahiri, na daku a wurinta,
duk ba wannan ba ni ya riga ya wuce, kawai haryanzu ina jin zafin yaga mini
hoton uwata da mama tayi, da ƙazafin nan da suka yi mini, na fanɗarewa, na san
zan yafe musu wataran amma ba yanzu ba.
Ina son in ga mutum yana hira da mamansa, ko suna wasa irin
na ɗa da uwa, abun yana burgeni, ko mutum ya din ga gaya wa mamansa damuwarsa
da daɗi master, wataƙila kai ka samu wannan damar ni kuwa ban samu ba, maybe da
mamanka ta yi tsawon rai wannan rayuwar za ta zo maka da sauƙi". Tana gaya
masa raɗaɗin abun da take ji a zuciyarta yana raguwa, duk da kuka take yi.
Ya ce "You are missing her?" Yayi maganar yana
kallonta.
Ta jinjina masa kai ta ce "So badly"
"Ki yi mata addu'a" ta jinjina masa kai tana goge
hawayenta, a take shi kuma ya tuna irin tasa rayuwar, duk da lokuta da dama
idan ka haɗu da wanda ku ke da irin matsala ɗaya ku ka yi sharing ana samun
releif, amma yanzu shi ba ya son doguwar magana idan ya fara ma gajiya zai yi,
duk da kwanan nan jauhar na isarsa da saka shi magana, kuma muddin ya gaya mata
shi nasa labarin, zata shiga damuwa dan haka ya ƙyaleta.
Duk da kuka take yi, ta fara ɗaukarsa a hoto tana murmushi
ta ce "Kai zan fara yi wa hoto da wayar nan, haryanzu mamaki nake yi, wai
master ne ya saya mini waya, Allah dai ya sanya mini kai a cikin aljanna ya
jiƙan mama, ya ja da ran wanda suka rage mana, Allah ya goyi bayanka ya yi maka
jagora a cikin lamuranka. Kai master na rasa wace addu'ar ma zan yi maka, na
rasa wace irin godiya zan yi maka ma"
Har cikin ransa ya ji daɗin Addu'ar da take yi masa.
Ya kuma amsa da Amin.
"To mun gama ki tafi"
"To me na yi maka ka ke korata?"
Ya ce "Sigari zan sha"
Ta ɓata fuska ta ce "Da sassafen nan ba ka ci komai ba,
sai ka fara da hayaƙi, haba mai babban suna, idan a baya babu wanda ya damu da
lafiyarka, ni ina son ka yi lafiya, ka rayu saboda ka ajiye 'yar madara, yau
dai ɗaya ayi haƙuri dan Allah a ɗaga ƙafa kar a sha da sassafen nan" kamar
shashasha haka yake bin ta da kallo, ta karɓe lighter da sigarin hannunsa, har
da ta gefe ta cikin kwali ta tattaresu.
"Bari na dafa mana shayi, cincin na yi jiya, amma na
kasa ci saboda damuwa, ka yi brush sai ka fito ka karya, kuma zan din ga leƙowa
saura na ga mutum ya sha wani abu"
Sunkuyar da kai ya yi, yana murmushi da gefen bakinsa.
Jauhar ta samu na yi, lambar baba ta kira, yana ɗagawa ko
gaisawa ba su yi ba ta ce "Baba na yi waya"
Baba ya ce "Masha Allah Alhamdilillah, ina tayaki murna
waliyya"
"Ka hau what's app mu yi video call"
Baba ya ce "To shikenan waliyya" Al'amin ya
kalleta ya maimaita waliyya a ransa, lallai ta ci sunan da mahaifinta ya kirata
da shi.
"Master, nan ne wurin video call ɗin ko?" Ya
jinjina mata kai alamar eh.
Tana kira baba ya ɗaga fuskarsa ta Bayyana a screen ɗin
wayar.
"Baba wayata touch screen ce mai kyau".
Baba yayi dariya ya ce "Masha Allah, Allah ya sanya
alkhairi."
"Amin, ina su yaya saifu su mama da Anty?"
"Duk suna nan lafiya, baba dan Allah kowa da kowa a
turo mini lambarsa, duk zan yi musu magana ta what's app, zan din ga kiran su
kuma a waya"
"To shikenan, a ina ki ka samu waya ne?"
"Master ne ya saya mini" sai kuma ta ce "Au
amm maigidan ne ya sai mini"
Wani irin sanyi ya ratsa zuciyar baba, ya ce "Allah ya
saka masa da alkhairi, ya yi muku albarka baki ɗaya"
"Amin baba" ta kaste wayar.
"Master " ya ɗago ya kalleta.
"Na gode sosai" ya ɗan tsuke fuska ya ce "Kin
faɗa kin sake, ya isa haka"
"Bar ni na yi yabon gwani ya zama dole".
Tana cikin maganar hankalinta ya kai kan labarin da ake yi a
radio, wata mata ce take kuka, take roƙon gwamna, sarki da kuma jami'an tsaro
su kama Aminu mai dogon zamani bisa karya mata ɗa da yayi, ya soke shi da wuƙa,
an kai shi asibiti rai a hannun Allah gashi ba ta da ƙarfi, tana neman a bi wa ɗanta
hakkinsa.
Cikin tsananin tashin hankali, jauhar ta kalli Al'amin,
tamkar bai ji me aka faɗa a radiyon ba, sai tauna cin-cin yake yi ƙururus ƙurus
ko a jikinsa an mari dutse.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Jiki a sanyaye jauhar ta ce "Master, dama rigima ka je
ka yi, ka ji wai a nemoka"
Bai tanka mata ba, ya ɗauki kofin shayinsa, ya kai bakinsa.
"Dan Allah ka yi magana, menene abun yi yanzu? Ko zuwa
zamu yi mu ba ta haƙuri" kallon Allah ya kiyaye ya yi mata.
Ta gyara zamanta ta ce "Ka san wani abu? Uwa uwa ce,
kuma duk lalacewar ɗanta tana son shi, ba zata taɓa mantawa da kai ba, illata
mata ɗa da ka yi, babu faɗuwa a ciki idan mun je mun bata haƙuri, idan dan ɗan
wani abu mu bata. Ba yanzu ake ji ba gaba ake ji master, duk rintsi duk wuya
kar ka bari wani ya ƙullaceka, sai ka manta ka cutar da mutum, amma nauyin
hakkinsa yayi ta ɗawainiya da kai".
Ya shanye shayinsa tsaf, kamar a mafarki ta ji ya ce
"Alhamdilillah"
Ta ce "Masha Allah, Allah ya ƙara mana wadatar zuci da
rufin asiri, mu koma waccan maganar master, dan Allah ka yarda mu je mu bata
haƙuri"
Ƙwanƙwasa gate ɗin gidan aka fara yi, Al'amin ya tashi ya je
ya buɗe.
Ɗaya daga cikin yaran unguwar ne marasa ji, ya risuna ya ce
"Allah ya ja zamaninka"
"Ya aka yi?"
"Wallahi guduma ne suka yi faɗa da dattijonsa jiya, ya
kore shi daga gidan ya ce ya bar masa gida, ya sallamawa duniya shi, shi ne yau
ya je ya sha wani abu, gashi can ya kulle mai unguwa a gida, da makami ya ce
sai ya sara shi, an kirawo jami'an tsaro an kasa buɗe gidan"
"Mu je in gani"
Suna zuwa suka tarar da mutane cirko-cirko a ƙofar gidan, ga
'yan sanda su huɗu, ana ta fama a buɗe ƙofar gidan an kasa, sai kururwar mai
unguwa ta cikin gidan, yana a taimake shi, a raba shi da ɗan sa kan ya kashe
shi"
Al'amin ya zagaya, ya dira cikin gidan, ya tarar da guduma a
tsaye a ƙofar ɗakin mai unguwa, riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙa, sai ƙyalli take
yana dukan ƙofar ɗakin, yana maye yana sai ya kashe mai unguwa babansa.
Sauran matan gidan da yara, duk sun rufe ɗakuna suna neman ɗauki.
Al'amin ya tunkare shi, yana zuwa ya riƙe shi, ya karɓi
makamin hannunsa ya kwaɗa masa mari, hakan ya sa ya ƙara gigicewa, ya danƙo
rigarsa ya buɗe ƙofar ya fito da shi sai tangaɗi yake yi.
'yan sandan suka yo kansu, za su kama guduma, Amma Al'amin
ya ce "Zamu zo da shi station anjima idan ya dawo hayyacinsa.
Mai unguwa da ya tsira da ƙyar ya ce "Ofusa kar ku bari
ya tafi da shi, dama shi yake goya musu bayan iskanci a unguwar nan, da ɗa na
bai kai haka lalacewa ba, a haɗa a Kama har da shi".
Al'amin bai kalleshi ba ya ce "Ko ya gudu ni a kama ni,
ba zai gudu ba, idan ya dawo hayyacinsa zan kawo shi da kaina, mu haɗu a
station zuwa ƙarfe biyar na yamma ina son a zauna da babansa"
"Shikenan, mu na jiranka"
Mai unguwa ya ce "Ofusa ya zaka yi mini haka, yaron da
ya nemi rayuwata"
"Mai unguwa ka jira ya dawo hayyacinsa mu gani, Allah
ya kaimu ƙarfe biyar ɗin.
Jauhar na wanke-wanke, Al'amin ya turo ƙofa, hannunsa riƙe
da guduma, ta tashi tana bin sa da kallo.
"Sako hijjabinki, ki kawo mini tabarma"
Ta jinjina masa kai, ta sako hijjabi, ta kawo masa tabarma,
ya kwantar da guduma, ta ƙare masa kallo ta ce "Wannan ai shi ne ya hana
wani ya sare ni, lokacin da na je gida da aka tsare ka"
Al'amin ya ce "Kawo mini ruwa a bokiti da kofi"
Ta kawo masa ruwa, ya ɗiba ya dinga sheƙawa guduma a ka, ya
din ga zabura kamar zai zare, ya ɗaukko gawayi a kurfotin Jauhar, ya daddaka ya
kaɗa a kofi, ya matse guduma ya dinga ɗura masa a bakinsa, ya sha wani ya zubo
da wani, ya gama ya hankaɗa shi ya kwanta.
"Master wai meya same shi ne? Ba shi da lafiya
ne?"
"Ƙwayar da ta fi ƙarfin kansa ya sha, ya kusa halaka
mahaifinsa"
Waro ido ta yi ta ce "Mahaifinsa kuma? Subhanallah
lamari ya ɓaci"
Bayan mintuna arba'in, guduma ya wartsake, ya din ga kallon
gidan, sai da yayi ido huɗu da Al'amin, sai ya ƙara nutsuwa.
"Ka farfaɗo?" Guduma ya sunkuyar da kai.
"Ka san me aikata ko?" Yayi shiru bai ce komai ba.
Al'amin ya yi ajiyar zuciya ya ce "Me ka sha?"
"Wiwi ce"
"Da me?"
"Itakaɗai"
A fusace ya ce "Zan saka maka ƙarfe wallahi, uban me ka
sha ka ke yinƙurin kashe mahaifinka?"
"Wiwi ce kawai ban sha komai..... Ba rufe baki ba,
Al'amin ya riƙe maƙogwaronsa ya ce "Zaka faɗa ko sai ni na kashe ka?"
A rikice jauhar ta ce "Dan Allah Master ka ƙyale shi,
kar ka kashe shi"
Cikin kakari guduma ya ce "Baƙin capsule ne"
"Waye ya baka, kuma way yake dillancin sa a unguwar
nan".
"Botorami ne"
"Botorami, yaran da suka sareni, na ƙyale shi, shi ne
ya fara sayar muku da wannan muguwar ƙwayar? To wallahi sai ya bar unguwar nan.
Uban me babanka yayi maka ka nemi kashe shi? Bayan sharrin ƙwaya har da
iskanci, uban meyasa ba ka yi yinƙurin kashe kowa ba sai shi?".
Cikin damuwa guduma ya ce "Korata yayi, ya ce kar na
sake zuwar masa gida"
"Ba dole ya kore ka ba, tun da abun naka babu hankali a
ciki, in anjima zamu je police station, ka bashi haƙuri, idan kuma ka bari yayi
maka baki, ka shirya lalacewa da taɓewa fiye da wadda ka ke ciki yanzu" ya
jinjinawa Al'amin kai.
Al'amin ya ce "Ka zauna a nan kar ka fita ko ina"
Jauhar mamaki ta din ga yi, dama Al'amin ya san abun da ya
dace, amma shi yake wanda bai dace ba.
Jauhar ta gama abincin rana, ta zuba ta bawa guduma, ya karɓa
ya ce "Ya gode"
Al'amin ya zaunar da shi yana yi masa tambayoyi, sai dai
bayanin da ya yi wa Al'amin, a kan irin rayuwar da ya tashi a kai, gaba ɗaya
jikin jauhar yayi sanyi, wato wasu lokutan mutane na yin gaggawar yankewa wasu
hukunci, ba tare da sanin ainihin abun da ke ɓoye ba.
"Da la'asar suka tafi police station, tun da suka je
mai unguwa yake bala'i, har da cewa 'yan sanda su kama guduma su yi masa duk
abun da za su yi masa shi yafi ƙarfinsa.
"Uwarsa ce ta lalata shi, sannan ta dawo mini da shi,
baya sana'r komai sai shaye-shaye na tsiya da ya ɗorawa ransa, yau kuma
rayuwata yake nema, to wallahi ba a haifi ɗan da zai kashe ni ba, waccan
shashashar uwar ta sa ita ce silar komai, bayan ya lalace ta nannaɗo ta kawo
mini shi"
Al'amin ya ce "Ina mamakin yadda aka bawa mutum irinka
jagorancin al'umma alhalin ba ka iya jagorantar gidanka ba.
Kai da ka haife shi, baka iya bashi tarbiyya ba hukuma ce za
ta tarbiyantar maka da shi? Ka san ba zaka iya kula da shi ba meyasa ka haife
shi? Da ka saki majaifiyarsa ka maye masa gurbinta? Sakinta ka yi ka bar mata
shi, ba ka san cin sa da shan sa ba, balle iliminsa da lafiyarsa, baka nuna
masa sana'a ba, baka bashi jari ba, ita ba cikakken ƙarfi ba itakaɗai tayaya
zata iya yi maka rainon ɗa?
Ka san jikinka yana buƙatar ka auri mata barkatai, ka yi
jima'i ayi ta haifa maka 'ya'ya amma ba ka tunanin inganta rayuwarsu, ko
buƙatar ka kawai ita ce buƙata?"
"Kaga Al'amin ya isa hak.... Al'amin ya ɗaga masa hannu
ya dakatar da shi, ya cigaba da magana.
"Babu in da za shi, tun da ka haife shi, dole ka kula
da shi, ka yi masa role ɗin uwa tun da ka saki uwarsa a lokacin da ya fi
buƙatar ku rayu tare, idan ba haka ba ko ba shi ba, a cikin wannan tulin
'ya'yan zaka samu mai halaka ka.
Ya mayar da idonsa kan Guduma ya ce "Kai kuma ya muka
yi da kai?"
Guduma ya durƙusa ya ce "Baba dan Allah dan Annabi ka
yafe mini, ka yi haƙuri ba zan sake ba in sha Allah, dan Allah ka janye korar
da ka yi mini daga gidanka, nayi kuskure ka yi haƙuri "
Sai dai mai unguwa yayi tsit, dan kuwa Al'amin ya gama
kwaikwaye shi a gaban mutane, yayi mamakin maganganun da suka fito daga bakin
Al'amin ɗin.
"Officer, zan kawo yaron da yake sayar da wannan
capsule ɗin, a riƙe shi a matsa shi, ya faɗi ina yake samota" ya sake
kallon guduma ya ce "Ka shelanta, cikin unguwar nan, duk wanda na kama da
sayar da irin wannan nau'in kayan, sai na lahira ya fi shi jin daɗi"
Ya jinjinawa Al'amin kai.
"Yanzu dai ina nema masa afuwa, yayi nadama in sha
Allah ba zai sake ba".
"Idan ya sake fa, ni fa gaskiya rayuwata tana cikin
hatsari"
"Ayi rubutu, duk abun da ya yi zan ɗauki laifin"
Ba mai unguwa ba, har Guduma Nura sai da ya kalli Al'amin.
Aka yi sulhu da rubuce-rubuce, suka fito, guduma ya risuna
yana yi wa Al'amin godiya.
"Manta, mu je ka rakani asibiti, kan waccan uwar mitar
ta sakani a gaba"
Guduma ya ce "Antynmu ayi mata godiya, abinci yayi daɗi
na gode master" bai ce komai ba, suka tafi asibiti.
Ko da suka je emergency, Al'amin har gaban gadon yaron da ya
karya ya je, ya tarar da shi a kwance, ana saka masa ruwa.
Yana ganin Al'amin ya rikice, ya yinƙura zai ɗago, Viper ya
mayar da shi, ya kalle shi ya ce "Na ji babarka na kururuwa na nakasta ka,
a ɗaukar mata mataki, kai ba ka gaya mata babu mai iya ɗaukar mata mataki ba?
Yanzu ka dawo hayyacinka ka tuna abun da ka yi ko? Ba ka sanni ba ko? Saboda ka
sha ta gaya maka ƙarya, ni ka tunkara zaka sara ko? Wai ba kai ne ɗan mama ba,
da aka rufe kwanaki madaki ya saka ka kashe wani yaro a dabarku ba? Ya shiga ya
fita an sake ka, yanzu kuma da ka nakasa ya kasa taimakon ka ko?".
Ya sunkuyar da kai ya yi shiru.
"Za a zo a biya kuɗin maganinka, nan gaba ka sake zuwa
ka tari gaban tirela, ta kanka zan bi"
Ya kalli guduma ya ce "Tashi mu ware"
Ya tashi suka tafi.
Bayan fitar su Al'amin, jauhar ta kaiwa telar da take yi wa
aiki kaya, ta rage mata wani abu a cikin kuɗin, amma ba ta bata duka ba.
Ta tarar da yaran matan layin, suna ta bajekolin magungunan
mata, ana ta shewa.
"Jauhara ba za ki sayi abun arziki ba, ga kaya nan sai
wanda ki ke so, kuɗi kuɗi iya kuɗinki iya shagalinki"
Kawai tayi murmushi ta basar da su.
Wasila ta ce "Wai sai an yi magana sai ki wani din ga
mazewa kamar baki san komai ba? Ke an daina irin wannan abun kamar a zamanin
da, idan baki zanzare kin fitsare ƙafafuwanki ba,bar ganin mijinki a haka ba
ruwansa da kowa, wallahi sai ki ga ya fara 'yan leƙe-leƙe, ki zo ki ɗauki gyara
hajiyata, ita mace sai d gyara, wannan kyan fuskar ta ki ba shi kawai yake so
ba"
Jauhar ta ce "Hmm Anty wasila kenan"
"Ba wani anty wasila, malama ki rage maƙo dan Allah,
kin iya neman kuɗi sai aukin saka turaren wuta a gida, da goge goge, amma ba
zaki sai kayan gyara ba, ina ta tallata miki kayan maman neehal ɗin nan, baki
ga kyan su ba, amma sai ki yi burus".
Suwaiba tela ta ce "Wai wasila ki ƙyaleta mana, ki ka
sani ko tana abun ta, idan tana yi gaya miki zata yi?"
"Ba wani, ni fa jauhar ƙanwata ce, ƙanwa na ɗauketa,
kunyarta tayi yawa Allah ya sa ba haka ki ke yi masa ba, babu yadda za ayi ki
je ki ganta da shirt da wando, sai uban hijjabi da dogwayen riguna kamar zata
yi ɗawafi. Ki tsuke ki ci zamaninki tun da ƙuruciyarki, ni ga wani tsumi nan na
baki, na maman neehal ne, tested and trusted, ki gwada zaki bani labari.
(0706 677 4630 ga lambar da zaku samu maman neehal, domin
samun kayanta)
Kamar sokuwa haka Jauhar ta karɓa, kasancewar ta san ba wani
amfani da zai yi mata.
A gurguje ta kammala abun da za ta yi a gidan, ta fito
saboda irin manyan karatun da ta ji suna yi, da suka fi ƙarfin kanta.
Ta koma gida, ta din ga kallon robar abun da anty wasila ta
bata, na wurin Anty lubabatu ma suna nan, ko kallonsu ma ba ta yi.
Aka fara kiraye-kirayen sallar magariba, tana salla,
ƙarar wani babur ya cika mata kunne, bayan ta idar tana cikin lazumi, ta ji ana
kokowar shigowa da abu, ta tashi ta fito tsakar gida, ta tarar da Al'amin yana
shigowa da wani tsohon babur jincheng, hannunsa riƙe da salansar babur ɗin.
"Master, wannan kuma fa?"
"Jaki ne" ya bata amsa.
"Wai sai ka yi ta gaya mini baƙar magana, wai ko shi ne
ya cika layin nan da ƙara?"
"Eh"
"To meyasa ka cire masa salansa? Ka ji ƙarar kuwa ba daɗi,
kamar ya shekara ba a kunna ba".
Ya jingine salansar, duk ya ɓata jikinsa da baƙin mai, ya ce
"Na fi son sa a haka"
"To wai a ina ka samo babur?"
"Sata na fara" yayi maganar zai shigar mata falo.
Ta ce "Allah ya baka haƙuri, amma tsaya na kai maka
ruwa banɗakin tsakar gida ka yi wanka, idan ba haka ba zaka ɓata carfet ɗin da
baƙin mai"..
"Naɗe abun ki na wuce, ba zan yi wanka a tsakar gida
ba"
Ta shagwaɓe ta ce "Ba fa a tsakar gida ba, toilet ɗin
tsakar gida".
"Ƙoƙarin shiga falon yake, tayi sauri ta ɗaukko tsumma,
ta durƙusa ta ce "Bari na goge maka, kar ka ɓata mini carfet" ta
gogge masa, sannan ya shiga.
Warin sigarin da yake yi ya sanya ta bin sa da ruwan zafi,
ta matsa masa toothpaste a kan brush, ta ajiye masa.
Allah ya taimake ta, babu musu yayi wanka yayi brush, ya
fito yana goge jikinsa, ya buɗe wardrobe ta shigo da sauri ta ce "Saura ka
watso mini kaya ƙasa, na sake gyarawa, nuna mini wanne zaka saka na ɗaukko
maka?"
Ya nuna mata, ta ciro masa su, kafin ya karɓa ta miƙo masa
kwalbar turare ta ce "Ka shafa turaren, sai ka saka"
Haɗin da take amfani da shi ne, ta daka alumun, da farin
muski na gari, da kanumfari, da lalle, ta dafa su suka tsumu ta ta ce, ta zuba
madarar turare a ciki.
Ya karɓa ya shafa, ya miƙa mata, ta karɓa ta ce "Ai
naka ne, na bar maka"
Ya karɓa zai ajiye, ta ce "Baka ce ka gode ba" sai
ya miƙo mata abun ta, da ya ce ya gode gara ya dawo mata da abun ta.
Tayi dariya ta ce "Hukuma sai da rarrashi, na janye ba
sai an yi godiyar ba"
Ya ajiye, ya fara ƙoƙarin saka kayan, ta fita ta bashi wuri,
shi kansa ya ji daɗin jikinsa sosai da sosai, ga ƙamshin yayi masa daɗi sosai
da sosai.
Ya fita ya kame a falo, ƙamshin turare sai ɗibarsa yake yi.
Akwai English wears a cikin kayanta, sai dai ba ta taɓa
gwada sakawa ba, dan kunya ma take ji, domin kuwa sai kwanan nan ta daina yawo
da hijjabi a cikin gidan.
Da ƙyar ta iya fitowa da doguwar rigar atamfa, da ta ɗan
kamata cif jikinta, ta zo ta zauna a falon, ta ce "Master ya ku ka yi a
police station kuwa?"
"Labari zan baki ko yaya?"
Ta ce "Eh mana"
"Kunna radiyonki, ki ji labarai idan shi ki ke son
ji".
Cikin shagwaɓa ta ce "Ni naka nake so"
Ya ce "To ni ban san me zan ce ba"
Ta ce "Ai shikenan"
"Yauwwa, na ce ba ka ga azumi saura 'yan kwanaki,
yakamata ace ko sugar da lemo mu saya mu je mu gaida su Abba"
"Sai kin dawo" ya faɗa yana shan kunu.
"Master meyasa?"
"Kawai".
"Na san akwai dalili, amma koma menene ka yi haƙuri, ba
a fushi da iyaye, kai fa ka gama yi wa wani nasiha ɗazu, meyasa ba zaka yi
amfani da ita a kanka ba?"
Juya mata baya ya yi, irin idan kin gama kya yi shiru.
Zuciyarta cike da fargaba, ta taka ta je kusa da shi ta
zauna ta ce "Masu sunanka manyan mutane ne, dattawa, ba sa haka, dan Allah
kar ka saka mu shiga fushin Allah, iyaye ba abun watsarwa bane ba, ranar da
babu su da kuɗi ba zamu gansu ba, mun rasa iyaye mata, mazan sai mu nemi
albarkar su"
Ya ɗaga hannunsa ya ɗora a kan kunnensa, ta kalli dogwayen
yatsunsa, faratansa sun yi tsayi.
"Gobe in Allah ya kaimu friday ce, a yanke farce, sumar
nan ma tayi yawa yakamata a rage ta, ayi maka gyaran fuska kafi kyau idan aka
aka rageta"
Juyowa yayi gaba ɗaya, ya ƙureta da idonsa.
Sai jikinta yayi sanyi, tsigar jikinta ta tashi yarrr.
"Kin fa dame ni" yayi maganar a hankali, amma
muryar da yayi amfani da ita, har cikin zuciyarta.
"To me nayi maka na takura?" Shiru yayi bai yi
mata magana ba, ya cigaba da ƙare mata kallo.
Ja tayi da baya, ta ce "Dama wainar fulawa zan yi mana
mu sha da tea, bari na ɗora"
Ta fita tsakar gida, ta hura kurfoti, ya biyo ta gaban
kaskon ya zauna, sai dai kallon da yake yi mata duk ta takura.
"Master, kamar fa akwai ɓera a gidan nan, dan Allah ka
sayo maganin ɓera"
"Shi m tsoron nasa ki ke ji kenan?"
Tayi murmushi ta ce "Eh, amma ba sosai ba"
"Ya haɗa nasa shayin, tana soyawa yana cinyewa"
"Master ban gane ba, idan ka cinye ni fa?"
"Sai ki soya wata"
"Ko kuma ka soya mini ba, ƙullin fa bashi da yawa, ka
ƙoshi gaskiya" ta janye plate ɗin.
Ta gama ta haɗa nata tea ɗin, ta fara ci.
Ya zuba mata ido, cin abincin ma yanga take yi masa.
Yana zaune yana kallonta, ta gama ta haɗa wanke-wanke ta yi.
Ta gaka komai, zata shiga ɗaki ta ce "Na gama taso mu
tafi, kar sauro ya saka maka zazzaɓi".
"Dama na ce miki ke nake jira ne?"
Jauhar ta ce "Eh dole ka ce haka, tun da na cika maka
cikinka, aishikenan sai da safe, dan Allah kar ka sha komai ka ji master".
Yayi mata shiru, ta ce "Master, magana nake fa, na san
kana ji na, dan Allah kar ka sha komai ka ji Mai zamani"
Ɗagowa yayi ya kalleta, tayi masa murmushi, tasowa ya yi, ya
biyo bayanta. Tsayawa tayi ta ga me zai yi mata.
Yana zuwa ya riƙe kunnenta ya ce "Me ki ka ce?"
"Master na ce"
"In kuma jin kin faɗi wannan sunan" sai dai duk
wannan abun fuskarsa ba fara'a.
Cikin shagwaɓa ta ce "Kunnena zai cire fa" ya tura
ƙeyarta, har ƙofar ɗakinta, ta ce "Kar in sake ganinki sai gobe in Allah
ya kaimu".
"To na ji, amma dai kar ka sha komai dan Allah"
wucewa yayi ɗakinsa, ta ƙarasa gaban gadonta tana murmushi.
Ta yi wanka, ta shirya ta shafa turarukan ta, ta nemi wuri
ta kwanta. Sai murmushi take yi, tana jin daɗin cigaban da ake samu a kan zaman
su.
Ta kalli pillown da take rungume da shi, ta shafi pillown a
hankali, tana tuna hirarrakin da aka yi ɗazu da su Anty wasila.
Tabbas abun da take ji game da aure ya sha banban da abun da
ta tarar, to ko ba haka abun yake ba? Sai kuma ta tuna har a littatafan addini
ta karanta.
Hakan yana nufin Al'amin ba shi da lafiya ne? Ko kuma ita ɗin
ce ba ta gabansa, sai dai ya ci, yayi shaye-shayensa ya je yawonsa, ko kallon
kirki ba ta ishe shi ba.
Tunani take yi ko dai tana da wani naƙasu ne, da ya sanya ba
ta gabansa, ko da wasa
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955Jiki a sanyaye jauhar ta ce "Master, dama
rigima ka je ka yi, ka ji wai a nemoka"
Bai tanka mata ba, ya ɗauki kofin shayinsa, ya kai bakinsa.
"Dan Allah ka yi magana, menene abun yi yanzu? Ko zuwa
zamu yi mu ba ta haƙuri" kallon Allah ya kiyaye ya yi mata.
Ta gyara zamanta ta ce "Ka san wani abu? Uwa uwa ce,
kuma duk lalacewar ɗanta tana son shi, ba zata taɓa mantawa da kai ba, illata
mata ɗa da ka yi, babu faɗuwa a ciki idan mun je mun bata haƙuri, idan dan ɗan
wani abu mu bata. Ba yanzu ake ji ba gaba ake ji master, duk rintsi duk wuya
kar ka bari wani ya ƙullaceka, sai ka manta ka cutar da mutum, amma nauyin
hakkinsa yayi ta ɗawainiya da kai".
Ya shanye shayinsa tsaf, kamar a mafarki ta ji ya ce
"Alhamdilillah"
Ta ce "Masha Allah, Allah ya ƙara mana wadatar zuci da
rufin asiri, mu koma waccan maganar master, dan Allah ka yarda mu je mu bata
haƙuri"
Ƙwanƙwasa gate ɗin gidan aka fara yi, Al'amin ya tashi ya je
ya buɗe.
Ɗaya daga cikin yaran unguwar ne marasa ji, ya risuna ya ce
"Allah ya ja zamaninka"
"Ya aka yi?"
"Wallahi guduma ne suka yi faɗa da dattijonsa jiya, ya
kore shi daga gidan ya ce ya bar masa gida, ya sallamawa duniya shi, shi ne yau
ya je ya sha wani abu, gashi can ya kulle mai unguwa a gida, da makami ya ce
sai ya sara shi, an kirawo jami'an tsaro an kasa buɗe gidan"
Ya ce "Mu je in gani"
Suna zuwa gidan mai unguwa suka tarar da mutane cirko-cirko
a ƙofar gidan, ga 'yan sanda su huɗu, ana ta fama a buɗe ƙofar gidan an kasa,
sai kururwar mai unguwa ta cikin gidan, yana a taimake shi, a raba shi da ɗan
sa kan ya kashe shi"
Al'amin ya zagaya, ya kama katanga ya dira cikin gidan, ya
tarar da guduma a tsaye a ƙofar ɗakin mai unguwa, riƙe da wata sharɓeɓiyar
wuƙa, sai ƙyalli take yana dukan ƙofar ɗakin, yana maye yana sai ya kashe mai
unguwa babansa.
Sauran matan gidan da yara, duk sun rufe ɗakuna suna neman ɗauki.
Al'amin ya tunkare shi, yana zuwa ya riƙe shi, ya karɓi
makamin hannunsa ya kwaɗa masa mari, hakan ya sa ya ƙara gigicewa, ya danƙo
rigarsa ya buɗe ƙofar ya fito da shi sai tangaɗi yake yi.
'yan sandan suka yo kansu, za su kama guduma, Amma Al'amin
ya ce "Zamu zo da shi station anjima idan ya dawo hayyacinsa.
Mai unguwa da ya tsira da ƙyar ya ce "Ofusa kar ku bari
ya tafi da shi, dama shi yake goya musu bayan iskanci a unguwar nan, da ɗa na
bai kai haka lalacewa ba, a haɗa a Kama har da shi".
Al'amin bai kalleshi ba ya ce "Ko ya gudu ni a kama ni,
ba zai gudu ba, idan ya dawo hayyacinsa zan kawo shi da kaina, mu haɗu a
station zuwa ƙarfe biyar na yamma ina son a zauna da babansa"
"Shikenan, mu na jiranka"
Mai unguwa ya ce "Ofusa ya zaka yi mini haka, yaron da
ya nemi rayuwata"
"Mai unguwa ka jira ya dawo hayyacinsa mu gani, Allah
ya kaimu ƙarfe biyar ɗin.
Jauhar na wanke-wanke, Al'amin ya turo ƙofa, hannunsa riƙe
da guduma, ta tashi tana bin sa da kallo.
"Sako hijjabinki, ki kawo mini tabarma"
Ta jinjina masa kai, ta sako hijjabi, ta kawo masa tabarma,
ya kwantar da guduma, ta ƙare masa kallo ta ce "Wannan ai shi ne ya hana
wani ya sare ni, lokacin da na je gida da aka tsare ka"
Al'amin ya ce "Kawo mini ruwa a bokiti da kofi"
Ta kawo masa ruwa, ya ɗiba ya dinga sheƙawa guduma a ka, ya
din ga zabura kamar zai zare, ya ɗaukko gawayi a kurfotin Jauhar, ya daddaka ya
kaɗa a kofi, ya matse guduma ya dinga ɗura masa a bakinsa, ya sha wani ya zubo
da wani, ya gama ya hankaɗa shi ya kwanta.
"Master wai meya same shi ne? Ba shi da lafiya
ne?"
"Ƙwayar da ta fi ƙarfin kansa ya sha, ya kusa halaka
mahaifinsa"
Waro ido ta yi ta ce "Mahaifinsa kuma? Subhanallah
lamari ya ɓaci"
Bayan mintuna arba'in, guduma ya wartsake, ya din ga kallon
gidan, sai da yayi ido huɗu da Al'amin, sai ya ƙara nutsuwa.
"Ka farfaɗo?" Guduma ya sunkuyar da kai.
"Ka san me aikata ko?" Yayi shiru bai ce komai ba.
Al'amin ya yi ajiyar zuciya ya ce "Me ka sha?"
"Sigari ce"
"Da me?"
"Itakaɗai"
A fusace ya ce "Zan saka maka ƙarfe wallahi, uban me ka
sha ka ke yinƙurin kashe mahaifinka?"
"Wiwi ce kawai ban sha komai..... Ba rufe baki ba,
Al'amin ya riƙe maƙogwaronsa ya ce "Zaka faɗa ko sai ni na kashe ka?"
A rikice jauhar ta ce "Dan Allah Master ka ƙyale shi,
kar ka kashe shi"
Cikin kakari guduma ya ce "Baƙin capsule ne"
"Waye ya baka, kuma waye yake dillancin sa a unguwar
nan".
"Botorami ne"
"Botorami, yaran da suka sareni, na ƙyale shi, shi ne
ya fara sayar muku da wannan muguwar ƙwayar? To wallahi sai ya bar unguwar nan.
Uban me babanka yayi maka ka nemi kashe shi? Bayan sharrin ƙwaya har da
iskanci, uban meyasa ba ka yi yinƙurin kashe kowa ba sai shi?".
Cikin damuwa guduma ya ce "Kora ta yayi, ya ce kar na
sake zuwar masa gida"
"Ba dole ya kore ka ba, tun da abun naka babu hankali a
ciki, in anjima zamu je police station, ka bashi haƙuri, idan kuma ka bari yayi
maka baki, ka shirya lalacewa da taɓewa fiye da wadda ka ke ciki yanzu" ya
jinjinawa Al'amin kai.
Al'amin ya ce "Ka zauna a nan kar ka fita ko ina"
Jauhar mamaki ta din ga yi, dama Al'amin ya san abun da ya
dace, amma shi yake wanda bai dace ba.
Jauhar ta gama abincin rana, ta zuba ta bawa guduma, ya karɓa
ya ce "Ya gode"
Al'amin ya zaunar da shi yana yi masa tambayoyi, sai dai
bayanin da ya yi wa Al'amin, a kan irin rayuwar da ya tashi a kai, gaba ɗaya
jikin jauhar yayi sanyi, wato wasu lokutan mutane na yin gaggawar yankewa wasu
hukunci, ba tare da sanin ainihin abun da ke ɓoye ba.
"Da la'asar suka tafi police station, tun da suka je
mai unguwa yake bala'i, har da cewa 'yan sanda su kama guduma su yi masa duk
abun da za su yi masa shi yafi ƙarfinsa.
"Uwarsa ce ta lalata shi, sannan ta dawo mini da shi,
baya sana'r komai sai shaye-shaye na tsiya da ya ɗorawa ransa, yau kuma
rayuwata yake nema, to wallahi ba a haifi ɗan da zai kashe ni ba, waccan
shashashar uwar ta sa ita ce silar komai, bayan ya lalace ta nannaɗo ta kawo
mini shi"
Al'amin ya ce "Ina mamakin yadda aka bawa mutum irinka
jagorancin al'umma alhalin ba ka iya jagorantar gidanka ba.
Kai da ka haife shi, baka iya bashi tarbiyya ba hukuma ce za
ta tarbiyantar maka da shi? Ka san ba zaka iya kula da shi ba meyasa ka haife
shi? Da ka saki majaifiyarsa ka maye masa gurbinta? Sakinta ka yi ka bar mata
shi, ba ka san cin sa da shan sa ba, balle iliminsa da lafiyarsa, baka nuna
masa sana'a ba, baka bashi jari ba, ita ba cikakken ƙarfi ba itakaɗai tayaya
zata iya yi maka rainon ɗa?
Ka san jikinka yana buƙatar ka auri mata barkatai, ka yi
jima'i ayi ta haifa maka 'ya'ya amma ba ka tunanin inganta rayuwarsu, ko
buƙatar ka kawai ita ce buƙata?"
"Kaga Al'amin ya isa hak.... Al'amin ya ɗaga masa hannu
ya dakatar da shi, ya cigaba da magana.
"Babu in da za shi, tun da ka haife shi, dole ka kula
da shi, ka yi masa role ɗin uwa tun da ka saki uwarsa a lokacin da ya fi
buƙatar ku rayu tare, idan ba haka ba ko ba shi ba, a cikin wannan tulin
'ya'yan zaka samu mai halaka ka.
Ya mayar da idonsa kan Guduma ya ce "Kai kuma ya muka
yi da kai?"
Guduma ya durƙusa ya ce "Baba dan Allah dan Annabi ka
yafe mini, ka yi haƙuri ba zan sake ba in sha Allah, dan Allah ka janye korar
da ka yi mini daga gidanka, nayi kuskure ka yi haƙuri "
Sai dai mai unguwa yayi tsit, dan kuwa Al'amin ya gama
kwaikwaye shi a gaban mutane, yayi mamakin maganganun da suka fito daga bakin
Al'amin ɗin.
"Officer, zan kawo yaron da yake sayar da wannan
capsule ɗin, a riƙe shi a matsa shi, ya faɗi ina yake samota" ya sake
kallon guduma ya ce "Ka shelanta, cikin unguwar nan, duk wanda na kama da
sayar da irin wannan nau'in kayan, sai na lahira ya fi shi jin daɗi"
Ya jinjinawa Al'amin kai.
"Yanzu dai ina nema masa afuwa, yayi nadama in sha
Allah ba zai sake ba".
"Idan ya sake fa, ni fa gaskiya rayuwata tana cikin
hatsari"
"Ayi rubutu, duk abun da ya yi zan ɗauki laifin"
Ba mai unguwa ba, har Guduma Nura sai da ya kalli Al'amin.
Aka yi sulhu da rubuce-rubuce, suka fito, guduma ya risuna
yana yi wa Al'amin godiya.
"Manta, mu je ka rakani asibiti, kan waccan uwar mitar
ta sakani a gaba"
Guduma ya ce "Antynmu ayi mata godiya, abinci yayi daɗi
na gode master" bai ce komai ba, suka tafi asibiti.
Ko da suka je emergency, Al'amin har gaban gadon yaron da ya
karya ya je, ya tarar da shi a kwance, ana saka masa ruwa.
Yana ganin Al'amin ya rikice, ya yinƙura zai ɗago, Viper ya
mayar da shi, ya kalle shi ya ce "Na ji babarka na kururuwa na nakasta ka,
a ɗaukar mata mataki, kai ba ka gaya mata babu mai iya ɗaukar mata mataki ba?
Yanzu ka dawo hayyacinka ka tuna abun da ka yi ko? Ba ka sanni ba ko? Saboda ka
sha ta gaya maka ƙarya, ni ka tunkara zaka sara ko? Wai ba kai ne ɗan mama ba,
da aka rufe kwanaki madaki ya saka ka kashe wani yaro a dabarku ba? Ya shiga ya
fita an sake ka, yanzu kuma da ka nakasa ya kasa taimakon ka ko?".
Ya sunkuyar da kai ya yi shiru.
"Za a zo a biya kuɗin maganinka, nan gaba ka sake zuwa
ka tari gaban tirela, ta kanka zan bi"
Ya kalli guduma ya ce "Tashi mu ware"
Ya tashi suka tafi, kamar wa da ƙani, suka bar mai unguwa da
kunya.
Bayan fitar su Al'amin, jauhar ta kaiwa telar da take yi wa
aiki kaya, ta rage mata wani abu a cikin kuɗin, amma ba ta bata duka ba.
Ta tarar da yaran matan layin, suna ta bajekolin magungunan
mata, ana ta shewa.
"Jauhara ba za ki sayi abun arziki ba, ga kaya nan sai
wanda ki ke so, kuɗi kuɗi iya kuɗinki iya shagalinki"
Kawai tayi murmushi ta basar da su.
Wasila ta ce "Wai sai an yi magana sai ki wani din ga
mazewa kamar baki san komai ba? Ke an daina irin wannan abun kamar a zamanin
da, idan baki zanzare kin fitsare ƙafafuwanki ba,bar ganin mijinki a haka ba
ruwansa da kowa, wallahi sai ki ga ya fara 'yan leƙe-leƙe, ki zo ki ɗauki gyara
hajiyata, ita mace sai d gyara, wannan kyan fuskar ta ki ba shi kawai yake so
ba"
Jauhar ta ce "Hmm Anty wasila kenan"
"Ba wani anty wasila, malama ki rage maƙo dan Allah,
kin iya neman kuɗi sai aukin saka turaren wuta a gida, da goge goge, amma ba
zaki sai kayan gyara ba, ina ta tallata miki kayan maman neehal ɗin nan, baki
ga kyan su ba, amma sai ki yi burus".
Suwaiba tela ta ce "Wai wasila ki ƙyaleta mana, ki ka
sani ko tana abun ta, idan tana yi gaya miki zata yi?"
"Ba wani, ni fa jauhar ƙanwata ce, ƙanwa na ɗauketa,
kunyarta tayi yawa Allah ya sa ba haka ki ke yi masa ba, babu yadda za ayi ki
je ki ganta da shirt da wando, sai uban hijjabi da dogwayen riguna kamar zata
yi ɗawafi. Ki tsuke ki ci zamaninki tun da ƙuruciyarki, ni ga wani tsumi nan na
baki, na maman neehal ne, tested and trusted, ki gwada zaki bani labari.
(0706 677 4630 ga lambar da zaku samu maman neehal, domin
samun kayanta)
Kamar sokuwa haka Jauhar ta karɓa, kasancewar ta san ba wani
amfani da zai yi mata.
A gurguje ta kammala abun da za ta yi a gidan, ta fito
saboda irin manyan karatun da ta ji suna yi, da suka fi ƙarfin kanta.
Ta koma gida, ta din ga kallon robar abun da anty wasila ta
bata, na wurin Anty lubabatu ma suna nan, ko kallonsu ma ba ta yi.
Aka fara kiraye-kirayen sallar magariba, tana salla,
ƙarar wani babur ya cika mata kunne, bayan ta idar tana cikin lazumi, ta ji ana
kokowar shigowa da abu, ta tashi ta fito tsakar gida, ta tarar da Al'amin yana
shigowa da wani tsohon babur jincheng, hannunsa riƙe da salansar babur ɗin.
"Master, wannan kuma fa?"
"Jaki ne" ya bata amsa.
"Wai sai ka yi ta gaya mini baƙar magana, wai ko shi ne
ya cika layin nan da ƙara?"
"Eh"
"To meyasa ka cire masa salansa? Ka ji ƙarar kuwa ba daɗi,
kamar ya shekara ba a kunna ba".
Ya jingine salansar, duk ya ɓata jikinsa da baƙin mai, ya ce
"Na fi son sa a haka"
"To wai a ina ka samo babur?"
"Sata na fara" yayi maganar zai shigar mata falo.
Ta ce "Allah ya baka haƙuri, amma tsaya na kai maka
ruwa banɗakin tsakar gida ka yi wanka, idan ba haka ba zaka ɓata carfet ɗin da
baƙin mai"..
"Naɗe abun ki na wuce, ba zan yi wanka a tsakar gida
ba"
Ta shagwaɓe ta ce "Ba fa a tsakar gida ba, toilet ɗin
tsakar gida".
"Ƙoƙarin shiga falon yake, tayi sauri ta ɗaukko tsumma,
ta durƙusa ta ce "Bari na goge maka, kar ka ɓata mini carfet" ta
gogge masa, sannan ya shiga.
Warin sigarin da yake yi ya sanya ta bin sa da ruwan zafi,
ta matsa masa toothpaste a kan brush, ta ajiye masa.
Allah ya taimake ta, babu musu yayi wanka yayi brush, ya
fito yana goge jikinsa, ya buɗe wardrobe ta shigo da sauri ta ce "Saura ka
watso mini kaya ƙasa, na sake gyarawa, nuna mini wanne zaka saka na ɗaukko
maka?"
Ya nuna mata, ta ciro masa su, kafin ya karɓa ta miƙo masa
kwalbar turare ta ce "Ka shafa turaren, sai ka saka"
Haɗin da take amfani da shi ne, ta daka alumun, da farin
muski na gari, da kanumfari, ta dafa su suka tsumu ta ta ce, ta zuba
madarar turare a ciki.
Ya karɓa ya shafa, ya miƙa mata, ta karɓa ta ce "Ai
naka ne, na bar maka"
Ya karɓa zai ajiye, ta ce "Baka ce ka gode ba" sai
ya miƙo mata abun ta, da ya ce ya gode gara ya dawo mata da abun ta.
Tayi dariya ta ce "Hukuma sai da rarrashi, na janye ba
sai an yi godiyar ba"
Ya ajiye, ya fara ƙoƙarin saka kayan, ta fita ta bashi wuri,
shi kansa ya ji daɗin jikinsa sosai da sosai, ga ƙamshin yayi masa daɗi sosai
da sosai.
Ya fita ya kame a falo, ƙamshin turare sai ɗibarsa yake yi.
Akwai English wears a cikin kayanta, sai dai ba ta taɓa
gwada sakawa ba, dan kunya ma take ji, domin kuwa sai kwanan nan ta daina yawo
da hijjabi a cikin gidan.
Da ƙyar ta iya fitowa da doguwar rigar atamfa, da ta ɗan
kamata cif jikinta, ta zo ta zauna a falon, ta ce "Master ya ku ka yi a
police station kuwa?"
"Labari zan baki ko yaya?"
Ta ce "Eh mana"
"Kunna radiyonki, ki ji labarai idan shi ki ke son
ji".
Cikin shagwaɓa ta ce "Ni naka nake so"
Ya ce "To ni ban san me zan ce ba"
Ta ce "Ai shikenan"
"Yauwwa, na ce ba ka ga azumi saura 'yan kwanaki,
yakamata ace ko sugar da lemo mu saya mu je mu gaida su Abba"
"Sai kin dawo" ya faɗa yana shan kunu.
"Master meyasa?"
"Kawai".
"Na san akwai dalili, amma koma menene ka yi haƙuri, ba
a fushi da iyaye, kai fa ka gama yi wa wani nasiha ɗazu, meyasa ba zaka yi
amfani da ita a kanka ba?"
Juya mata baya ya yi, irin idan kin gama kya yi shiru.
Zuciyarta cike da fargaba, ta taka ta je kusa da shi ta
zauna ta ce "Masu sunanka manyan mutane ne, dattawa, ba sa haka, dan Allah
kar ka saka mu shiga fushin Allah, iyaye ba abun watsarwa bane ba, ranar da
babu su da kuɗi ba zamu gansu ba, mun rasa iyaye mata, mazan sai mu nemi
albarkar su"
Ya ɗaga hannunsa ya ɗora a kan kunnensa, ta kalli dogwayen
yatsunsa, faratansa sun yi tsayi.
"Gobe in Allah ya kaimu friday ce, a yanke farce, sumar
nan ma tayi yawa yakamata a rage ta, ayi maka gyaran fuska kafi kyau idan aka
aka rageta"
Juyowa yayi gaba ɗaya, ya ƙureta da idonsa.
Sai jikinta yayi sanyi, tsigar jikinta ta tashi yarrr.
"Kin fa dame ni" yayi maganar a hankali, amma
muryar da yayi amfani da ita, har cikin zuciyarta.
"To me nayi maka na takura?" Shiru yayi bai yi
mata magana ba, ya cigaba da ƙare mata kallo.
"Baka saka mini lambarka a wayata ba"
Ya miƙa mata hannu, ta bashi wayarta, ya saka mata lambarsa,
ta ce "Yauwwa na gode, zan din ga yi maka flashing, kamar sau arba'in a
rana"
"Iya arba'in?"
"Eh, ko yayi kaɗan?" Ya girgiza mata kai alamar
a'a.
"To ɗan yi mini downloading ɗin game"
Ya ce "Sai kin gama jarrabawa tukuna"
"Ai mun kusa in Sha Allah" ya lumshe idonsa ya ce
"Allah ya bada sa'a"
"Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum master, 'yar madara na
godiya"
Ta sake cewa "Dama wainar fulawa zan yi mana mu
sha da tea, bari na ɗora"
Ta fita tsakar gida, ta hura kurfoti, ya biyo ta gaban
kaskon ya zauna, sai dai kallon da yake yi mata duk ta takura.
"Master, kamar fa akwai ɓera a gidan nan, dan Allah ka
sayo maganin ɓera"
Ya ce "Shi ma tsoron nasa ki ke ji kenan?"
Tayi murmushi ta ce "Eh, amma ba sosai ba"
"Ya haɗa nasa shayin, tana soya waina yana
cinyewa"
"Master ban gane ba, idan ka cinye ni fa?"
"Sai ki soya wata"
"Ko kuma ka soya mini ba, ƙullin fa bashi da yawa, ka
ƙoshi gaskiya" ta janye plate ɗin.
Ta gama ta haɗa nata tea ɗin, ta fara ci.
Ya zuba mata ido, cin abincin ma yanga take yi masa.
Yana zaune yana kallonta, ta gama ta haɗa wanke-wanke ta yi.
Ta gama komai, zata shiga ɗaki ta ce "Na gama taso mu
tafi, kar sauro ya saka maka zazzaɓi".
"Dama na ce miki ke nake jira ne?"
Jauhar ta ce "Eh dole ka ce haka, tun da na cika maka
cikinka, aishikenan sai da safe, dan Allah kar ka sha komai ka ji master".
Yayi mata shiru, ta ce "Master, magana nake fa, na san
kana ji na, dan Allah kar ka sha komai ka ji Mai zamani"
Ɗagowa yayi ya kalleta, tayi masa murmushi, tasowa ya yi, ya
biyo bayanta. Tsayawa tayi ta ga me zai yi mata.
Yana zuwa ya riƙe kunnenta ya ce "Me ki ka ce?"
"Master na ce"
"In kuma jin kin faɗi wannan sunan, zamu gauraya da ni
da ke" sai dai duk wannan abun fuskarsa ba fara'a.
Cikin shagwaɓa ta ce "Kunnena zai cire fa" ya tura
ƙeyarta, har ƙofar ɗakinta, ta ce "Kar in sake ganinki sai gobe in Allah
ya kaimu".
"To na ji, amma dai kar ka sha komai dan Allah"
wucewa yayi ɗakinsa, ta ƙarasa gaban gadonta tana murmushi.
Ta yi wanka, ta shirya ta shafa turarukan ta, ta nemi wuri
ta kwanta. Sai murmushi take yi, tana jin daɗin cigaban da ake samu a kan zaman
su.
Ta kalli pillown da take rungume da shi, ta shafi pillown a
hankali, tana tuna hirarrakin da aka yi ɗazu da su Anty wasila.
Tabbas abun da take ji game da aure ya sha banban da abun da
ta tarar, to ko ba haka abun yake ba? Sai kuma ta tuna har a littatafan addini
ta karanta.
Hakan yana nufin Al'amin ba shi da lafiya ne? Ko kuma ita ɗin
ce ba ta gabansa, sai dai ya ci, yayi shaye-shayensa ya je yawonsa, ko kallon
kirki ba ta ishe shi ba.
Tunani take yi ko dai tana da wani naƙasu ne, da ya sanya ba
ta gabansa, ko da wasa bai taɓa ko makamancin yi mata wani abu ba.
Ta yi juyi ta kalli gadon, yanzu idan Al'amin ba shi da
lafiya ne, ko bashi da ra'ayin hakan, haka za su cigaba da rayuwa kenan, ita ba
kowa ne da ita balle su tattauna, ko da wasa kuma ta san ba zata tunkare shi da
wannan maganar ba, ko ta kai masa kanta, wannan ma ba mai yiwuwa bane ba.
Wataƙila wani babin ne na ƙaddarata. Ta faɗa a zuciyarta, a
lokacin da bacci yake ƙoƙarin awon gaba da shi.
Misalin ƙarfe uku da rabi na dare, wani matashin saurayi ne,
yana ta kai komo a tsakanin wasu gidaje can wajen gari, da alama wani abu yake
jira.
Wani mutum ne ya zo a keke, ya tsaya ya kalle shi ya ce
"Nan ce sabuwar mahaɗarmu?"
Mutumin ya amsa da "Eh, kuma ka yi taka tsantsan, kar a
gane, kar kuma ka yadda da kowa"
"To shikenan, yanzu zan je na rarrabawa gayu kayan, ga
wannan balance ɗin jiya ne" yayi maganar yana miƙa masa kuɗi, mutumin ya
karɓa, shi kuma ya tafi.
Sai dai ya nufi in da yake son tafiya, ya ji an danƙi
jijiyar wuyans, a take ya sulale sumamme.
Suka ɗauke shi suka tafi da shi, Walid ya kira Al'amin ya ce
"Maganarka haka take mai dogon zamani, mun kama yaron nan, ka san yaron
madaki ne ya rarraba musu ita, idan ban yi kuskure ba madaki yana cikin manyan
dilolin capsule ɗin nan.
"Ku shigo da shi cikin unguwa, ku ɗaure shi, ɗauri na
gasken gaske ku bar shi, zan yi magana da 'yan sanda"
"To shikenan, amma ka din ga yi kana ankarewa da
hankakin nan ka san ba mutunci suka cika ba"
"Ina ankare, sai da safe"
Har ƙarfe tara na safiya, Al'amin ya je yayi sabgoginsa ya
dawo, jauhar bacci take yi.
Ya tsaya a ƙofar ɗakinta, yana ƙwanƙwasawa, a hankali ta yi
juyi, ya ɗaga labulen ya ce "Ba a san gari ya waye ba ne? Yunwa nake
ji"
"Afuwan gani nan" tayi maganar cikin muryar bacci.
Da kayan jikinta ta fito falo, gashinta duk a hargitse ta ce
"Yi haƙuri, baccin nawa ne yayi nauyi".
Ta tarar ya sayo gasara, ya sayo awara ɗanya.
Mamaki ta din ga yi, a ina ya san ana sayarwa, amma tafi
yadda aikawa yayi a sayo masa.
Ta shiga ɗakinsa gyarawa, ta buɗe wardrobe ɗin sa, kayan da
ya cire jiya ta tattara zata wanke, ya kwasa ya mayar da su cikin wardrobe ɗin,
kayan dai da ba ta so, sai da watso su, ya ɗauki abun da zai ɗauka duk ya
cukurkuɗa su ya mayar cikin wardrobe ɗin.
Yana ganin ta tsaya tana kallon wardrobe ɗin, yayi waje dan
ya san mita za ta yi.
Ta kuwa biyo shi falon "Master, yanzu duk gugar da nayi
ka wargazata, ka haɗa mini wankakkun kaya da marasa wanki, har da jiƙaƙu duk ka
gwamutsa mini su a ciki" tayi maganar kamar tayi kuka.
"Ke fa ki ka ce, na daina zubar miki da kaya ko ina a
cikin ɗakin"
"Kuma master kaya kala ɗaya da zaka saka, sai ka
hargitse ilahirin wardrobe ɗin? Zan samo maka bagco, ka din ga zuba marasa kyau
a ciki, dan Allah ka daina hargitsawa" yayi mata shiru, ta gama mitarta ta
gama, tana komawa gyarawa ya dafe kai, ta gama mitar kuma ta gyara.
Sai da ya tabattar ta fita daga falon, tana aiki a kitchen
ya ɗaga wayarsa yayi kira.
"Kuna aikin da na saka ku?"
"Eh muna yi"
"Kar ku kuskura ku bari wani ya kwance shi, idan ba
jami'an tsaro ne suka zo ba"
Ya gama karyawa, yana son ya tashi ya fice, ta tistiye shi
da zancen yanke farce, haka ya koma ya zauna, ta saka reza ta yanke masa farce
tsaf, tana yi tana yi masa surutu.
Baya son ta gane ya yi wata tsiyar a waje, kar ta zauna ta
yi ta masa kuka.
Ta yi masa gugar kayan da zai saka, wai ya tafi masallacin
juma'a, shi rabonsa da zuwa sallar juma'a har ya manta, yayi wanka ta bashi
goggagun kaya, ta shafa masa turare ta ce "Ka dawo da wuri dan Allah, ina
gama abinci ka ci da zafinsa, ka yi mana addu'a idan ka je"
Ya gurgura babur ɗin sa da ya cire wa salansa, ya fice ya
cika layin da ƙara.
Daji ne sosai babu gida a gaba, babu a baya, daga shi sai
direbansa suke tafiya sai P.A, har suka ƙaraso wurin wani dutse, suka sauka da
shi da P.A, suka tattaka har gaban bukkar.
Cikin bukkar tamkar fadar mahaukaci, duk an yi mata ado
ƙahunhuna da ƙwarangwal ɗin dabbobi, har da wasu sassa na ƙashin ɗan Adam.
Gefe ga wani mutum na tsurut, kamar an fato shi, jikinsa ko
riga babu, daga shi sai wani ɗan warki ɗaure a ƙugunsa.
Suka nemi wuri suka zauna, ya kalli indabo ya ce "Aikin
farko yayi, wa'adin da muka ɗiba maka yau ya cika, aljanu sun sha jini a ƙasar
da suka buƙata.
Saura mahaɗin aiki na biyu, za a samo matashiyar yarinya,
matar aure shekara sha biyar zuwa sha takwas, zaka kasance da ita, tsawon
kwanaki uku, a ketowar alfijir ɗin kowace rana, zaka fara aikin a larabar
tsakiyar wata, shi ne sa'ar aikin! An ɗeba maka wa'adin kwanaki Arba'in ba
biyar"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Jinjina kai indabo yayi, ya ce "Za ayi ba zai gagara
ba, zamu dawo idan an kammala aikin, kuma wa'adin da aka ɗibar mana ya
cika".
"Shikenan, nasara tana tare da kai, ba yaƙini muke da
shi ba, tabbaci nake bakaz duk da akwai ƙalubale a gaba, sai da ba za su gagara
ayi maganin ƙalubalen ba, amma a gaba kaɗan ɗin akwai dutse, da zaka yi karo da
shi, na buga na duba, duk babu hanyar maganin dutsen nan, sai dai ayi ragas, ko
ka kar dutsen ko ya kar ka"
P.A ya ce "Kuma babu yadda za ayi da dutsen? Ko wata
mafitar?"
"A yanzu dai babu,
Suka tashi suka fito, suna tafe a hanya Indabo ya ce
"P.A"
"Na'am honorable"
"Bokan nan kullum cikin faɗin ayyuka masu hatsarin
gaske yake, ina tsoron tonuwar asirina, kar mu je in sake janyo wa kaina jagwal
kana kallon yadda yarinyar nan Naja'atu ta zame mini alaƙaƙai"
"Mu bi komai a sannu sir, zamu yi nasara kuma samo
yarinya ba zai gagara ba, ko cikin ƙauyukan nan aka bincika za a samu, ko kuma
Naja'atu ta samo a irin mutanen da ke hulɗa da su" yayi ajiyar zuciya ya
ce "Ba zan so ce a samo ta ɓangaren ta ba, amma kai na ɗora maka ragamar
samowar"
"Za a bincika in sha Allah sir"
"Yayi, ina jiranka, ka ga idan lokaci ya ƙure, aikin da
muka yi ya koma baya"
"Haka ne, da yardar Allah ka ci kujerar nan ka gama, mu
je injiniyoyin suna can gida suna jiranka, aje ayi lissafi"
"Ok to, Aminu haryanzu ya ƙi zuwa ko?"
"Wallahi yaƙi, Allah da wani wanda zai iya yi mana irin
kasadar da yake ɗauka, da mun canza shi, ɗan rainin hankali ne, ko fushi yake
saboda wannan karon ba ka fito da shi ba?"
"Da fushi yake yi, ba zai ɗauki wayata ba, kuma ina son
aiki da shi, ba ya jin kasada komai zafinta kuma ba shi da mgana ko kisan kai
zaka yi a gaban sa, sai ya ga dama zai ɗaga kai, balle ka ji zancen a waje.
Sannan babban abun shi ne, bokan nan ya ce nasarata tana tattare da wanda yake
zubar mini da jini, na riƙe shi sosai, shiyas nake shanye iskancin sa".
P. A ya ce "haka ne ya na da amana, ba shi da magana
sam, amma shi ya san da hakan ne?".
"Haba dai, hauka nake yi na bari ya sani, ba abun da ya
sani, kawai aiki yake yi mini"
Misalin ƙarfe huɗu da rabi na yamma, manyan injiniyoyi ne
zaune a falon indabo, suna ta lissafin ginin plazarsa.
Ga wanda zai tattauna da su a kan harkar yaƙin neman zaɓensa,
suma su na jiransa.
Al'amin yana cikin falon, ana ta lissafi, shikuwa yana
hakimce yana kallon tv.
Sai da aka gama lissafi, za ayi total ɗin kuɗi, Al'amin ya
kalli shugaban engeneers ɗin ya ce "Kayi plusing da kuɗin siminti buhu
shida, da tiles carton biyar"
Ya ce "Na menene?"
"Ina ruwanka, ka saka kawai".
Injiniya ya kalli Indabo, Indabo ya ce "Kuɗi ka ke
buƙata ne na baka?"
"Gyaran gidana zan yi nima"
Indabo ya ce "Engeneer a rubuta, a bashi"
Al'amin ya sake cewa "Akwai yarana mutum biyar, da nake
son a saka mini su a cikin aikin ginin nan, su yi su ma a sallame su"
P.A ya ce "An gama mai dogon zamani"
"Zamu zo tare da su, ni ne cikon na shida, da ni za ayi
aikin a biyani"
P.A ya sake cewa "Ba ka da matsala"
Aka gama aka sallami injiniyoyi, 'yan jami'iyya suka shigo,
duk yana zaune, aka gama meeting.
Duk sai da suka gama, sannan Indabo ya mayar da hankalinsa
da Al'amin ya ce "Mai zamani" ya ɗaga ido ya kalli indabo.
"Akwai tafiya da zan yi ƙaddamar da takarata, a
yammacin garin nan, ina buƙatar tawagar ka kai da mutanen ka, saboda ban san ya
zata kaya a wurin ba, 'yan sandan nan gaibu ne wasu lokutan".
"Yaushe ne?"
"Nan da kwana goma"
"Cikin azumi kenan?"
Indabo ya ce "Eh"
"Allah ya kaimu, baka da matsala"
P.A ya ce "Allah ya ƙara maka nisan zango mahadi mai
dogon zamani. Ina matarka kuwa?"
Da sauri ya kalli P.A ya ce "Kamar ya ina matata, meye
haɗinka da ita?"
"A'a babu komai, lokacin da kana tsare ne, ta zo ita da
Walid, ko da yadda za ayi ka fito, lokacin honorable baya nan"
Viper ya yi shiru bai sake cewa komai ba.
Wata ƙatuwar mage ce ta shigo, da matasan 'ya'yanta, fara
tas kana ganinta ka san 'yar waje ce.
Al'amin ya tashi ya nufi in da take, ya saka hannu ya ɗauki
guda ɗaya ya ce wa P.A "Wannan mace ne ko namiji?"
"Namiji ne"
"Zan tafi da shi"
P.A ya ve "Ka san kuɗin abun nan kuwa? Ya kai dubu ɗari
shida fa, wannan ƙaramin".
"Da gold aka yi shi ne?" Yayi maganar yana nuna ɗan
muzurun da yake ta ihu saboda ya ji matsa.
Indabo ya ce "A'a ɗan Germany ne"
"Tun da ba daga aljanna ya zo ba shikenan, kai kawo
leda na saka shi" yayi maganar yana kallon mai goge-goge.
"P.A ya ce wace irin leda kamar zaka ɗauki masara,
kwando dai za a baka.
Yayi ƙerere, aka kawo masa kwando, ya saka muzurun ƙato da
shi fari, jikinsa cunkushe da gashi mai kyau.
Ya kalli Indabo ya ce "Zan tafi"
Indabo ya yi murmushi ya ce "Ga abun kuɗi nan ka ɗauka
a hannunka, ai ba sai an sallameka ba"
"Za a sallame ni ko in tafi?"
"P.A sallame shi"
P.A ya buɗe jaka, ya ɗebo kuɗi ya miƙawa Viper.
Al'amin yayi masa wani mugun kallo, indabo ya ce "Ƙara
masa"
"Ya ƙara ɗebowa, ya ƙara masa"
Ya karɓa ya ce "Na karya wani yaro, yana emergency,
babar yaron tayi maganar a kamani, a bi wa ɗanta hakkinsa, yana can a emergency
asibitin tsakiyar gari, a kashe wutar, ko ta ƙone yiwuwar aikinka, hankakin nan
suka yi ram da ni, ba zan yi aikinka ba" daga haka ya fice daga falon.
P.A ya ce "Kai, honorable Mai zamani yana hawa kanmu da
yawa wallahi, wai sai abun da yake so za a din ga yi yayi ta yi wa mutane
tunƙaho?"
Indabo yayi murmushi ya ce "Rabu da shi lokaci ne, bari
a ci zaɓen, ai ka ga mutumin can ya ce akwai nasarar mu a tattare da shi, yanzu
abun da za ayi, ka koma ka yi waya, ka saka a haɗa wata tawagar ta 'yan daba,
da zasu far mana a wurin taron, yadda za a samu a zubar da jinin shi ma a can.
Sannan ka tara mana 'yan media, idan hakan ta faru a ce abokan adawa ne suka yo
hayar 'yan daba suka far mana".
"An gama honorable, yanzu kuwa zan je na tara su na
sanar musu tun yanzu"
"Yauwwa, idan ka gama da su, a hanzarta ko aike ka yi
wurin wanda ya karya ɗin, a rufe bakin babarsa"
"Ok sir"
***
Al'amin ya koma gida, ya tarar da Jauhar da maƙwabta, tana
yi musu kitso.
Yana shigowa hannunsa riƙe da ledoji, ta tashi tana
murmushi, suka gaishe shi, babu wanda ya amsa sai sannu zuwan da tayi masa ya
amsa.
Ta miƙe hannu za ta karɓi kwandon, ya ce "Banda
wannan" ya shiga falo da shi.
Ta dudduba kayan, kayan abinci ne wata irin ajiyar zuciya ta
sauke, tare da yi wa Allah godiya.
Allah ya sa ta gama kitson, ta sallame su suka tafi, ta
shiga falon hannunta riƙe da cup ta risuna ta miƙa masa. Ya karɓa ya ga zoɓo
mai sanyi, sai ƙamshi yake yi. Ya kafa kai ya zuƙe ya miƙa mata kofin ta ce
"Ba ka ce ba"
Ya ce "Alhamdilillah" tayi murmushi ta ce
"Sannu da zuwa" ya jinjina kai ta ajiye kofin, ya jefo mata muzurun
nan a jiki, ta saki ihu tana tsalle, ta ce "Meye wannan?"
"Shi ma wannan ɗin tsoronsa ki ke ji?"
"Kamar kare fa?"
"Mage ne, saboda ƙadangarun da suke damunki, ko shi ma
tsoronsa ki ke ji?"
Ta ce "Laaa, to ai bai yi kama da mage ba, masha Allah
so cute" ta durƙusa ta ɗauke shi.
"Master ina ka samo shi dan Allah, kamar ba ɗan nan
ƙasar ba. Kai amma na ji daɗi sosai, wani sunan zamu saka masa"
Ya ce "Muzuru"
Ta kwaɓe fuska ta ce "Muzuru kuma? Sunan gayu za a saka
masa, wane irin muzuru?".
"Ba sunansa kenan ba?"
"A'a, na saka masa suna mai zamani"
"Ki ka kuma ko?" Yayi maganar yana kallonta.
Tayi murmushi tana shafa kyakkyawan jikin muzurun.
Ya ve "Da gaske kin je wurin P.A ɗin Honorable lokacin
da aka rufe ni?"
Ta kalleshi ta sunkuyar da kai. "Ki bani amsa"
Ta jinjina masa kai alamar eh.
"Ko wani irin hali zan shiga, kar ki sake zuwa wurin
wani, mussman gidanmu da wurin 'yan siyasar da nake mu'amala da su, dan su fito
da ni"
Ta ce "In sha Allah, ba zan sake ba, amma dan Allah ka
daina zuwa wurin da zaka cutu, kaga idan aka rufe ka, nikaɗai nake damuwa ba
wanda yake taimaka mini, ni kuma ba zan iya jurewa ba ganinka a tsare"
tayi maganar jikinta a sanyaye.
Ya saka hannu a aljihunsa ya ciro kuɗi, ya ce
"Ungo"
Ta saka hannu ta karɓa ta ce "Na menene master?"
"Ana zubar da kuɗi ne?"
"Wai bani ka yi? Duka nawa ne?"
"Mmm ki sha madara"
Ta washe baki ta ce "Allah ya saka da alkhairi, Allah
ya yi maka jagora, ya ƙara jan dogon zamanin nan"
Ya ce "Za ki ga zamani, idan na kamaki"
Tayi murmushi ta ce "Wannan kuɗin ya fi ƙarfin shan
madara ai"
Ta din ga kwarara masa addu'a, tare da nuna tsantsar
farincikinta a kan abun da ya yi matan.
A daren ya kira guduma a waya, ya sanar masa da batun aikin
ginin da za ayi, ya kira Walid da su liti, da wasu daga cikin yaransa, sai dai
sai da suka sha wiwi, suka yi bushe-bushen su, domin samun ƙarfi wurin gabatar
da aikin.
Sai dai tun da Allah ya sa Al'amin ya kawo ɗan muzurun nan,
jauhar ta samu nayi, ta tattara nutuswarta da hankalinta a kansa.
Duk ranar da babu aiki, sai guduma ya zo gidan Viper, ya
tambayi jauhar ko ta na da aike ta kawo ya kai mata, tun ranar da ya ga zata
kai markaɗe, ya karɓa ya kai mata, Anty sama Anty ƙasa, kasancewar ta mai
kyauta, ya sanya take farinjini a wurin mutane, dan idan yayi mata aike, idan
tana da Abinci ta na bashi, ba da abincin nan ba ƙaramin kankaro mata kima yake
yi a.
Sai guduma ya mayar da Al'amin kamar yayansa, bashi kaɗai
ba, har 'yan sauran yaran da suke rashin jin, jama'ar guduma, idan suka ga
Al'amin, tsakaninsu da shi girmamawa, idan da kuɗi a jikinsa, haka zai bi su
mai ɗari biyar mai dubu, hakan ya sa suke yi masa biyaya sosai da sosai.
Hatta layin gidansa, idan kwata ta cika, ko ciyayi suka
fito, haka za su zo da kayan aikin su, su gyara tsaf.
Sannu a hankali, Al'amin ya fara janye matasan, shi dai ba
zai hana su shaye-shaye ba, sai dai akwai abubuwan da ya yi musu iyaka da sha.
Da sharuɗan da ya gindaya musu, a kan in dai za su zauna da
shi, sai sun kiyaye su.
Jauhar tana makaranta jarrabawa, biyu suka yi ranar, ta dawo
ta tarar an yi plasta a gidan gaba ɗaya, da shi da su Walid da guduma, sun yi
kaca-kaca da gidan.
Tana tsaka da mamakin ya dawo, ya tarar da ita ta ce
"Master, aiki ku ka sha haka? Baka gaya mini ba, balle na kwashe kayan
kuma ayi wa masu aikin girkin?".
"Da su mai laya muka yi, ba wani abu".
"Master wai a ina ka samu kuɗi haka? Amma ka yi haƙuri
idan tambayar da na yi tayi tsauri".
"Bana sata" amsar da ya bata kenan ya fita.
Zata iya shaidar hakan, amma yakamata ace ta san in da ya
samu kuɗi, tana tsoron ya ɗaukko musu rigima, sai dai gidan yayi kyau sosai.
Da daddare ya dawo, sai dai sai wani share ta yake yi, dan
ya ji haushin tambayar da tayi masa.
"Master, dan Allah ka yi haƙuri, na san tambayar da
nayi maka tayi tsauri, amma ka yi haƙuri dan Allah, Allah Ya ƙara maka arziki
da wadata, ya tsare mini kai a duk in da ka ke" yayi mata shiru yaƙi
amsawa.
"Tuba nake, tare da dukkanin girmamawa kaina bisa
wuyana, nake roƙon ayi mini afuwa, ayi haƙuri a yafe wa ƴar madara ranka ya daɗe,
Allah ya ƙarawa zamaninka tsayi, ya kare ka ko a gida ko dawa ayi haƙuri ina
ƙara bada haƙuri namijin mazaje"
Ba ƙaramin fasa masa kai kalamanta suka yi ba, duk da ba yau
aka fara yi masa kirari ba, amma sai ya ji nata ya zama na musamman, har cikin
kansa ya ji kirarin.
Amma kamar wani basaraken zaki, haka yayi shiru ya cigaba da
kaɗa ƙafa.
"To in dafa ruwan wanka na kai toilet ɗin tsakar gida?
Na san an gaji da yawa yau.
Ya kalleta ya ce "Ba na so"
Ta sakar masa wani ƙasaitaccen murmushi ta ce "Ai na ce
ayi haƙuri, manya ba sa fushi fa" ta yi maganar cikin shagwaɓa.
A taƙaice ya ce "Kai mini"
Bayan yayi wanka, suka zauna a falo, suka ci abincin dare,
dama tun a hanya ta sayo wa magenta kifi, ta nutsu tana bashi, tana yi wa
master hira.
Kasancewar ɗakunan an yi sabuwar plasta, ya sanya suka kwana
a falo, sai da ya tabattar ta yi bacci, sannan ya fice tsakar gida yayi
shaye-shayensa.
Gaba ɗaya washegari jauhar a gidan mai ɗinki ta wuni, ta
tayata aikin ɗinki, saboda gidanta su Al'amin suna aiki, hatta ƙofar gidan sai
da aka yi wa plasta, gyara ko yaya yake kyau ne da shi, sai ga gida yayi kyau
sosai da sosai.
***
Yau ɗaya ga azumi, ranar jauhar tana da exams, Al'amin ya ce
ta zo ta hau babur ɗin sa ya kaita, babu abun da ta tsana irin yadda yake yawo
da babur ɗin babu salansa, ga babur ɗin kamar na 'yan gwangwani,saman babur ɗin nan duk a
ragargaje, kana kallon wayoyin da aka yi wearing ɗin nan da su.
Amma dan kar ta watsa masa ƙasa a ido, haka ya karkato babur
ɗin, ta rirriƙe shi ta hau, suka tafi.
Ko da ta dawo a gida ta tarar da shi, duk idonsa yayi ja,
wanda idan ba da ƙwaƙwƙwaran dalili ba, ba za ka ganshi a gidan ba.
Ta kalleshi ta ce "Master na dawo"
Ya ɗaga mata hannu kawai.
Ta shiga ta canza uniform, ta dawo yana kwance yayi
wujiga-wujiga.
Ta fito ta shiga kitchen, dan ta ɗora musu abun buɗa baki da
wuri.
"Master wai duk azumin ne, ko magana ta gagara"
yayi mata shiru. Kawai ta hau dariya "Wallahi master ranar da babu abinci
ban san yaya zaka yi ba, wato ba ka ko azumin nafila, yau ɗaya duk ka fita
hayyacinka har haka?" Hararta yayi, yayi mata banza.
Ta din ga yi masa dariya, ƙarshe ya koma tsakar gida ya
shimfiɗa tabarma, yayi shame-shame kamar gawar sababi.
Ko da aka sha ruwa, ba yadda ba ta yi da shi ya tafi
masallaci ba, ya ƙi ya shanye lemo jug guda, da uban ruwa kamar amale, kuma ya
fara da cin shinkafa, maimakon ya fara da abu mai ɗumi yaƙi.
Ta ce "Ohh ni matar master, ya Allah kar ka hanamu abun
da zamu ci a kowane hali, ranar da babu abinci akwai matsala master magana ma
ta gagara yau azumi ɗaya kamar zaka rasu?" Yayi mata shiru yaƙi kulata.
A ɗan tarin da take yi, da kuɗin da ya bata daf da azumi,
tayi musu sayyayar kayan tea saboda tanadin azumi.
Sai da aka yi azumi biyar, sannan Al'amin yake iya fita idan
yana azumi, ya je ya ɗan yi neman kuɗinsa, gefe ga black market ɗin su ta sayar
da kayan maye.
Yau ya dawo da la'asar ya sheme a falo, sai sauke numfashi
yake yi.
Ta kalleshi tana dariya, ya kalleta ya ce "Ki ka sake
ki ka yi magana ni da ke ne".
Jauhar ta ce "A'a ni ban ce komai ba" tayi maganar
tana cigaba da dariya.
Tana ta aikinta an kusa shan ruwa ya ce "Anya kina
azumin nan kuwa?"
Ta ce "Ina yi mana"
"Gani nayi yau sha bakwai ga wata, ba kya azumi"
Ta kalleshi ta ce "To meye da sha bakwai ga
watan?"
Al'amin ya ce "Period ki ke yi, dan banaba kya
azumi" zaro ido tayi cikin mamaki, yaya aka yi ya san tana period, cikin
jin kunya, ta ce "Ni ba abun da nake yi, ba wanann date ɗin bane"
Kawai ya gyaɗa kai, ya ce "Ai da ki ka gama cin ƙosan a
kitchen ki ka cika cikinki, ba ki goge bakinki ba, kuma lemon da ki ka sha ma
cup ɗaya kin sha naki, tun da ba azumi ki ke yi ba, sai iya yi mini
dariya" ai kamar ƙasa ta tsage ta nutse, ba ta sanin ya ake yi, yake sanin
ta aikata wasu abubuwan ta hau goge baki ta ce "Sa ido ba kyau, azumi ka
ke yi kar ka zobe ladanka, ko a kwashe ladan naka a bani"
Yayi murmushi bai ce komai ba.
A wurin shan ruwa faɗa suka yi ta yi, wai ba zata cika kofi
da kunu ba, ba tayi azumi ba, kamar sako da sakuwa.
"Wai master, dan ban yi azumi ba ai ni na girka, sai ka
barbaɗawa duniya ban yi azumi ba? Haba master"
Ya ce "Eh ai ba yi ki ka yi ba, dan haka nawa sai ya fi naki yawa, ƙara mini"
Ta tura baki ta ce "Aikuwa da gobe in Allah ya kaimu
sai dai ka karɓo kunun sadaka, da ƙosai ka ci, ba zan yi girki ba, tun da ni ba
na azumi, ko ka girka abunka".
Ya ce "Eh dan dai girki, ba wuya zan iya, ƙosan nan ma
rago shi nan, gandiya ƙatuwa da ke ba kya azumi"
"Bani da lafiya ne" haka suka yi shan ruwan, ya
din ga jin kamar bai taɓa shan ruwa da nustuwa irin wannan ba.
Ita kanta tsokanar da yake yi mata daɗi take ji, bayan
sallar isha'i ya zauna a falo, ya ɗauka zata yi masa surutun da ta saba, sai
dai hankalinta ba ya kansa, yana kan magenta da take cewa boti, tana bashi
abinci tana shafa shi, haushi ya ishe shi, shi gashi ba iya hirar yayi ba,
balle shi ya fara, kawai ya tashi ya tafi ɗakinsa. Bayansa ta bi da kallo kawai
ta yi murmushi ta ce "Master kenan, hukuma sai da rarrashi".
Bakwai ga watan azumi ya kama ranar da za su bi Indabo
campaign, tun dare ya haɗa yaransa da wurin da za su haɗu su tafi.
Da sassafe bayan Jauhar ta tashe shi yayi sahur, ta idar da
sallar asuba ta kwanta bacci, ya silale ya fice.
Wunin ranar ba ta ganshi ba, ba ta damu ba sai da ta ga an
kusa shan ruwa, ta din ga kiran wayarsa, amma ba ta shiga, sai hankalinta ya
fara tashi, dan ta san duk in da ya je da an kusa shan ruwa yake tahowa gida.
Al'amin kuwa bayan sun dawo daga campaign, an yi sare-sare
sun yi shaye-shaye, an yi wa indabo aikinsa yadda yakamata, Al'amin ya sallammi
yaransa, shi kuma Indabo ya ce ya bishi gida, da shi da wasu 'yan jami'iyya su
sha ruwa a gidansa, ya sanya an shirya abun shan ruwa.
Al'amin ya ce sai dai su tafi tare da walid.
Ƙaton falo ne na musamman, mai ɗauke da haɗaɗɗem dining,
kayan abinci aka kawo, na ƙasaita aka din ga jerewa a kan dining ɗin nan, cikin
fulasai na alfarma.
Walid ya ce "Mu na cin albarkacinka mai zamani, wannan
sabga haka?"
Al'amin ya bari, aka gama jere abinci, ana ta rawar jiki a
fara ci ayi buɗe baki, ya tashi, ya bubbuɗe fulasan.
Wani irin farfesu aka yi na kajin gidan gona, ƙosassu, ga
flask ɗin dankali dana ƙwai abincin ma har da na almubazzaranci.
Al'amin ya ja flask ɗin kaji, ya janyo na dankali, ya haɗe
kan kayan shayi madarar gwangwani da milo, ya kalli Walid ya ce "Dafe mini
wannan mu ɓace".
Indabo ya ce "Ina zaka tafi kuma, za a ci abinci?"
"Gida" ya bashi amsa.
"To kuma na ga kana harhaɗe kan kwanukan abincin, ya
zaka yi da su ga mutane za su ci?"
Kai tsaye ya ce " 'yar madara zan kaiwa"
"A'a ya mage zata yi da wannan uban abinci haka?"
Walid ya ce "Ba mage ba ce, madam za a kaiwa"
Indabo ya ce "Haba mai zamani, sai ka ce a ɗibar mata,
amma yaya za ayi mutane na zaune abincin mutum sha biyu duk ka kwashe
rabi?".
"Ba zai yiwu da ni da na saka rayuwata a hatsari, da
wanda ku ka tsaya a cikin rumfa hankali kwance, ka yi mana sallama iri ɗaya ba,
ai kana da kuɗi a dafa musu wani. Ka san son zuciya ba halina bane, a baya ban
yi ba ba zan fara yanzu ba. Ba zan ci wannan abincin ita ba ta ci ba, kuma ai
ga wasu nau'in abincin nan ku ci. Walid ɗaukko kwandon kayan marmarin nan
ma"
Indabo ya ce "To fulasan fa? Ka tsaya sai a juye maka a
leda, na madam ne wannan"
"Madam ba ta fi madam ba, sadaki bai fi sadaki ba. Ina
fatan ka fahimci lissafin? kuma kuna da
kuɗin sayen wasu, ko ba yanzu ba idan kun ci zaɓe zaku samu, dan haka har
fulasan mun cinye" Indabo yana ji yana gani, Al'amin ya yarfa shi a gaban
jama'a, suka kwashe abinci suka tafi.
Jauhar ban da ruwa babu abun da ta sha, har bayan sallar
isha'i sai yawo take yi a cikin unguwar tana nemansa, hankalinta a tashe. Ta
gaji ta dawo gida da nufin ta kira Walid.
Kawai ta dawo ta tarar da shi.
"Master ina ka tafi, hankalina ya tashi tun safe
rabonka da gida, ba ka gaya mini ina zaka je ba, gaba ɗaya tun da aka sha ruwa
na kasa cin komai, ban san ina ka ke ba".
"To kukan zaki yi?"
"Baka gaya mini ina zaka je ba, hankalina gaba ɗaya ya
ƙi kwanciya haba master dan Allah"
"Ohh murya kamar tsuntsuwa, yenyenyen, ki din ga buɗe
baki ki yi magana sosai" kawai tayi shiru cike da takaici, idonta kawai ya
kalla, ya san hankalinta a tashe yake.
Ƙeyata ya tura, zuwa ɗakinsa kawai ta tarar da jeren
kwanuka, haɗaɗɗun fulasai, da uban kayan marmari.
Tayi saroro tana kallon kayan.
"Zo ki zuba mana mu ci, ba kayan wani bane, mun je
campaign ne muka dawo aka shirya shan ruwa, na ce a gida zan ci na taho da
shi".
A ɗan tsorace ta ce "Master duk wannan kuma?"
"Eh kwaso kwanuka"
Iya kajin sai da suka tsorata ta, dan sun kusa goma, fulasai
ne na alfarmar gaske.
Ta ce "Ai ba zamu iya cinyewa ba".
"Gasu nan dai, ki yi abun da ya dace".
Duk son Jauhar da nama, sai da ya isheta, ta bawa maƙwabta,
ta zuba wani ya kira guduma a waya, ya ce masa ya zo ya karɓa.
Hatta magenta, sai da ya ƙoshi da ciye-ciye.
Haka kurum ya din ga jin annashuwa a ransa, ganin ta ci ta
ƙoshi, har abun ya gundureta.
Bayan jera masa godiya da ta gama yi, kamar yadda ta saba,
tare da addu'oi, ta ce "Master Alfarma zan nema a wurinka dan Allah"
"Ina jinki"
Ta saka hannu ta karɓi wayarsa ta ce "Dan Allah kar ka
ce mini a'a, ko ba zaka yi ba".
"To kar ki tambayi abun da ba zan iya ba".
"Zaka iya mai babban suna, kaga naman nan yayi mana
yawa, duk da an babbayar dan Allah sonake na ƙara gyara shi, ayi miya gobe in
Allah ya kaimu, mu je yi wa su baba sannu da shan ruwa"
A take ya tsuke fuska, ya ƙi magana.
"Dan Allah Master, na neman albarka mu je mu gaishe
su"
"Wai ke wace iri ce ne? Tun da muka yi aure, bayan su
hajiya, kin ga wani ya zo gidan nan daga ɓangarena? Ko Abbun kin ga ya zo? Dama
maraba suke nema da ni, har gara mahaifinki ma ya zo"
Jauhar ta ce "Kar ka ce haka, dama ba su yakamata su zo
ba, mu yakamata mu je, ai su iyaye ba a fushi da su, kai fa ka yi wa wani faɗa
a kan haka, bai kamata kai ace ka aikata haka ba, dan Allah ka yarda mu
je" An kai ruwa rana sosai tsakaninta da shi, kafin ya amince.
Washegari suka shirya, bayan azahar suka fara zuwa gidan su
Al'amin.
Suka fara zuwa gidan su Al'amin, suka yi sa'a Abbu yana nan,
sai dai rahila tayi mamakin ganin Al'amin, yayi wani shar da shi, sai ƙamshin
turare yake yi kayansa sun sha guga.
Ashe Abbu zuwansa gidan su biyu, ba ya samun kowa, a gidan,
gashi Al'amin ya wanke ƙafarsa ya daina zuwa gidan.
Abbu baki ya kasa rufuwa, mamaki yake ganin Al'amin, a nutse
da shi ya sako 'yar matarsa a gaba gwanin sha'awa, sai dai sai cika yake yi
yana batsewa yana wani basarwa.
Dan tun da suka gaisa da Abbu, bai sake cewa komai ba,
jauhar ce take bashi amsa idan yayi magana.
Rahila ma sai zuba take ta ce "Ikon Allah, anya ba a
canzo wani Aminun ba, kun yi kyau abunku kun ƙara ƙiba, an ce kin yi rashin
lafiya kwanaki, To na san dai ba zai wuce laulayi ba, Allah ya raba
lafiya"
Al'amin ya ce "Amin, tashi mu tafi rana tana yi"
kawai ta girgiza kai jin Al'amin ya amsa, idan ma haka ne ai kamata yayi, yayi
shiru kawai.
Rahila ta sake cewa "To sai ayi ta kula da ita, ka san
masu ciki sai ana lallaɓa su, ban da hantara da abun da zai ɓata mata rai, kuma
ba zama zaka yi ba, ciki tun yana ƙarami ake fara sayayyar kayan jariri".
Jauhar ta ajiye food flask, da leda ta ce "Mama ga
wannan, kwa yi buɗa baki, a saka mu a addu'a"
Abbu ya ce "Masha Allah, addu'a kullum cikin yin ta
ake, Allah ya yi albarka"
Rahila ta ce "Iyee har da su suga da kayan
marmari?" Ta buɗe fulas ta ce "Abbu kaza ce fa a ciki, ikon Allah
sana'a ka samu ne haka? Ko kuma haryanzu miyagun ƙwayoyi ka ke sayarwa, gara
mutum ya san halaccin abun da zai ci".
Al'amin ya kalli jauhar, irin kallon kin ga abun da nake
gudu ko?.
Ya ce "Ubana na zo gani, kuma banda 'yar madara ta
matsa, da sai dai na je ƙofar masallaci, idan ya fito na ganshi kamar yadda na
saba, dan haka ba sai kin san sahihanci da halaccin cin sa ba, tun da bani da
alaƙa da ke" ya tashi ya danƙi hannun jauhar a gaban su.
Abbu ya ce "Aminullahi tsaya mana"ya tsaya cak
yana huci, jauhar sai ƙoƙarin zame hannunta take yi daga nasa, saboda kunya.
Abbu ya ce "Allah ya saka da alkhairi, ya yi albarka.
'ya ta Allah ya saka miki da alkhairi, yayi muku albarka gaba ɗaya"
Ta ce "Amin Abbu, a sha ruwa lafiya "
A zatonta, zai ta yi mata masifa, sai dai ta ji bai ce mata
komai ba, ya wuce da ita unguwar su, ya kaita har ƙofar gida.
"Ki yi sauri ki fito mu tafi, mu koma gida"
Ta ce "To*
Ta sauka daga babur ɗin ta shiga gidan, suka gaggaisa, sai
dai baba baya nan, ta ce "Dama ɗan abun sannu da shan ruwa na kawo masa,
sauri nake yi na bar shi a waje, kar ya gaji da jirana"
Anty Zakiyya ta ce "Lallai jauhar, shi mijin naki ya fi
ƙarfin ya shigo ya gaida mu kenan?"
"A'a ba haka bane Anty, kin san ba ya jituwa da 'yan
unguwar nan, bana son wani abu ya faru ne"
Mama ta ce "Haryanzu bai shiryun ba kenan? Sai labari
muka ji wai ya fito ai, Jauhar wannan naman kajin, shi ya saya ko ke?"
Ta ce "Shi ne"
Suryaya ta ce "To a dai yi a hankali, Allah ya sa ba na
sata bane ba".
Jauhar ta ce "Allah ya tsare shi, Al'amin ba ya
sata".
Anty Zakiyya ta ce "Wato Jauhar ba zaki yi mana Allah
ya sanya alkhairi ba ko, ko kishi ki ke yi?"
Cikin rashin fahimta jauhar ta ce "Anty na me?"
"Alhaji mu'azzam ya dawo, tun da kin yi aure yanzu
hafsa zai aura, ya bayar da miliyan biyu tayi lefe, dubu ɗari biyar kuma kuɗin
aure!"
Ayshercool
08081012143.
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Abunka da zuciya, dumm haka ƙirjin Jauhar ya buga, da ƙarfin
gaske, take wani abu da ba ta san menene ba ya taso mata.
A ranta ta ce "Saboda haka dama ku ka aura mini
Al'amin, dan rusa aurena da Alhaji mu'zzam?"
'kul jauhar, Al'amin zaɓin Allah ne a gare ki, babu wanda
yake da ikon canzawa wani ƙaddararsa, dama haka Allah ya tsara miki'
Cikin sauri ta ce "Ahh haba, amma ba a gaya mini ba, ga
shi muna waya, ina yi muku magana ta what's app, Anty ke ma ina da lambarki,
amma ba a gaya mini, ko dan kar in haɗa lefen na zo na ɗauki kayan kwalliya ne
ya sa ba a gaya mini ba?"
Anty Zakiyya ta ce "A'a kar a gaya miki ki ji wani abu
a ranki ne, dama Allah bai ƙaddara mijinki bane"
Jauhar ta ce "Haka ne, mijin wata baya auren matar
wani, idan an gama haɗawa ni dai zan zo a bani kayan kwalliya".
Surayya ta ce "Au, ashe fa ba ayi miki lefe ba ke
ko?"
Jauhar ta girgiza kai ta ce "A'a kin manta an yi mini
sayayyar kaya?"
"Duk da haka wannan ai ba lefe bane ba"
Wayar jauhar ta fara ringing, ta cirota daga jakarta ta ce
"Master"
"Fito mu tafi"
"To gani nan"
"Bari na tashi yana jirana, idan an saka lokaci sai a
gaya mini"
Hafsa ta ce "An saka bayan salla da sati uku ne"
"To Allah ya sa zamu gani, a gaishe mini da baba, sai
kuma Allah ya kaimu salla, Anty walida ku kuma na gaji da roƙonku ku zo gidana,
ko sau ɗaya babu wanda ya taɓa yi mini kara ya zo".
Hafsa ta ce "Ke fa babu wanda zaki gani a gidanki, muna
yayyenki zamu din ga zuwa gidanki, ko so ki ke mu zo mijinki yayi mana
illa?"
"Haba dai, ba fa mahaukaci ba ne, da zai yi muku illa,
da ban kawo yanzu tare da shi ba, sai anjimanku"
Zuba mata ido yayi, har ta ƙaraso, sai dai ya lura da
jikinta a sanyaye yake, bai ce mata uffan ba, ya kunna babur ɗin, ya karkata
mata ta riƙe shi ta hau suka tafi.
Sai yanzu ta ƙara gane dalilin yin amfani da yi mata sharri,
wurin aura mata Al'amin, ba wai tana baƙin ciki da auren hafsa bane ba, ta san
haka Allah ya ƙaddara kawai mamakin tsananin ƙin da suke yi mata take yi, ta
san ko da kuɗi ba za su yadda su aurawa 'ya'yan su mutum irin Al'amin ba,
saboda kar ta huta shiyasa suka yi mata wannan muguntar.
Kallon bayan Al'amin take yi, a ranta ta ce "Kai Allah
ya zaɓa mini, kuma in sha Allah sai na yi kyakywar rayuwar aure da kai master'.
Da haka suka ƙaraso gida, sai dai yana ankare da yadda
walwalarta ta gushe, take komai jiki a sanyaye babu kuzari.
Ɗan muzurunta na ta kewayata, yana yi mata ɗan kuka, amma ta
kasa kula shi, wanda da tana cikin walwala da tuni ta ɗauke shi tana yi masa
rawa, da ma shi ba shiri yake yi da muzurun ba, dan dana sanin kawo mata shi ma
yake yi, saboda yadda take tsananin ba wa muzurun kulawa, kamar ya jefar da shi
haka yake ji wasu lokutan.
Ya zuba mata ido, tana ta yi wa wani mayafi ado da beads, na
kayan sallar mutane da take ta yi, sai dai a saɓule take aikin.
Muzurun ma ya gaji, ya koma gefe ya kwanta, saboda ta kasa
kula shi.
Har aka sha ruwa, ko surutun yau ba ta iya yi, abincin ma
cakalarsa kawai take yi, ta kasa ci ta ajiye ta tashi tayar da sallar taraweeh.
Ta cigaba da aikin beads.
"Ssss, Ji mana" ta ɗaga kai ta kalleshi.
"Zo mana"ta ce "To" ta yinƙura ta tashi,
ta ƙaraso gaban sa, tana ƙoƙarin zama a ƙasa, ya nuna mata kusa da shi, ta
zauna tare da sunkuyar da kanta.
"Kin ga muna zamanzamanmu, ki ka kwashe mu, muka je
wurin mutanen nan, gashi kin je an yi miki wani abun kin kasa sukuni, shiyasa
tun farko na ce kar mu je, ki ka dage, kin dawo kin kasa nutsuwa, me aka yi
miki?"
Ta girgiza masa kai ta ce "Bakomai"
Ya ce "Bana tambaya sau biyu"
"Ka yi haƙuri dan Allah, babu komai, zuwa da safe zan
wartsake in sha Allah".
"Ba ki da juriya, kin fiye rauni, da wuri ake ganin
gazawar ki, ki ƙara ƙoƙarin zama jaruma, ko dai ayi miki ki shanye ko shirya
ramuwar gayya sama da abun da aka yi miki. Ki ajiye wannan abun da ki ke yi, ki
tafi ki je ki kwanta"
Ta jinjina masa kai ta ce "To master, na gode
sosai" ta tashi jiki a sanyaye ta tafi ta kwanta.
Sai dai bacci ya gagari idonta, ta din ga tunanin, meke
damunta kishi ne ko hassada. Sai dai ta tabattar wa da kanta ba kishi bane ba,
saboda ta riga ta zama matar wani, ko ba komai a yadda yake ɗin nan, ta fara
appreciating yanayin zaman na su yanz saɓanin da, dan haka tana matar wani ba
zata yi kishi a kan wani ba.
Hakazalika ba hassada ba ce ba, ba ta ji ta damu dan hafsa
zata shiga cikin daular da, da ita ce zata shiga, ta san wannan nufin Allah ne,
kawai tana jinjina yadda suka shiga suka fita, suka aura mata Al'amin dan kawai
kar ta auri Alhaji mu'azzam.
Wannan gillin ɗabi'a ce ga zuciya, da duk yadda ɗan adam ya
kai ga dannewa sai yayi tasiri, ta din ga istigfari da roƙon Allah ya sanyaya
mata ranta, ta manta ta fuskanci Rayuwarta.
Yanayin yadda Al'amin ya fara nuna damuwarsa a kanta, ya ke
sanya wa ta ji tabbaci da ƙwarin gwiwar cewa wataran za ta ji daɗinsa, tun da
dai babu duka ko zagi a tsakanin su, shaye-shayen sa da nema rigimarsa ne
babbar matsalarta, gashi yanzu cefane ma yana yi ko ba kullum ba.
A cikin kwanakin da ta dage da addu'a, sai ta fara jin
sassauci ta fara mantawa, ta cigaba da mayar da hankali a kan sana'arta, da yi
musu Addu'a babu dare babu rana.
Al'amin ya fara rage yin shaye-shaye a gabanta, sai ta yi
bacci, sai ya fita tsakar gida, ko ƙofar gida yayi, duk da wasu lokutan idan ta
shiga ta tarar da shi yana yi, mazewa yake yi ya haɗe rai ya cigaba da shan
abun sa, amma sosai yake rage abun da zai yi, wanda zai sanya ta shiga damuwa.
Ya mayar da ita asibiti, likita ya tabattar da jininta ya
sauka, kuma ya dakatar da ita daga shan magani, na wani ɗan lokaci.
Saura sati guda salla, gidan jauhar mutane ne kawai ke shiga
suna fita, masu mayafai, masu ɗinkuna da zata yi wa stone work, masu kitso da
lalle, a haka kuma tana kasa kayanta, na shirin dutse, sarƙa abun hannu,
jigida, ga kayan lemo, masu zuwa kitso suna yi mata ciniki. Ta zama very busy,
idan yamma ta gabato, ga aikin abinci, sai dai garin Allah yana wayewa, ya fice
ya bar gidan, saboda mutane.
Sai dai ana shan ruwa take sallamar kowa, ta ce sai gobe, za
ta kula da mijinta.
Yana falo a zaune, ya gama shan ruwa ya kasa tashi, wata
mata tayi sallama, tayi ta yi wa jauhar magiya, wai tana son ta turo yaran, ta
wanke musu kai, tayi musu kitso, kowace yarinya ɗari da hamsin, su huɗu.
Jauhar ta ce "Haba Maman Nana, ki bani ɗari bibbiyu
mana, ga wanke musu kai, ga kitso?"
"Taimakawa zaki yi jauhar, idan ki na son gobe mu kawo
miki coustomers, kin san yadda garin yake, ubansu bai bani ko sisi ba, ni nake
wahalata dan yaran su fito fes, ko hankici bai yi mana ba"
Jauhar ta ce "To shikenan, bari na sallami master, gobe
in Allah ya kaimu akwai mutane sosai, turo su yanzu a wanke musu kan, in dafa
ruwa a heater tun da da wuta, gobe in Allah ya kaimu da sassafe sai ayi
kitson"
"Ke, na hana kitson, kwashi yaranki ki tafi wani wurin
ayi miki" ta ji muryarsa a ƙofar falo.
Jauhar ta ce "Master meyasa?".
"Na hana kitson, duk wannan wahalar da ki ke wuni kina
yi a ɗari da hamsin? Dama wuni ki ke wahalar banza, saboda aikin yi yayi miki
ƙaranci? Get out malama kwashe yaranki ki fita, iyayen son banza".
Kamar jauhar ta yi kuka ta ce "Master dan Allah...
"Shhh" yayi maganar yana ɗora yatsansa a kan laɓɓansa.
Matar ta fita ta kalleshi kamar za ta yi kuka ya ce "Na
ga aiki ne yayi miki ƙaranci, mu je ina da aikin da zan baki ni, ki zauna ki
wuni kina wahala, a ɗari da hamsin, ina zaki kai kuɗi ne wai? Duk kin rame
saboda kin saka azabar son kuɗi a ranki" Yayi maganar yana kallon ta, tana
tsaye tana tura baki.
Ya fizgota gabansa ya ce ya kai hannunsa wuyanta ya ce
"Wannan ƙashin na wuya da ki na shi? Duk kin yi wuri-wuri ga azumi ga
wahala" da sauri ta ɗan kama jikinta, saboda unexpected ya saka hannunsa a
wuyanta.
Maimakon ya sauke hannunsa, sai ya miƙar da hannunsa zuwa
kan maƙogwaronta, ya fito da dogon harshen sa har wurin haɓarsa, ya lanƙwasa
shi, sannan ya mayar cikin bakinsa ya ce "Na ga kina motsa baki, me zaki
ce?"
Jauhar ta ce "Ai shikenan ka korar mini coustomer, kuma
ka shaƙeni zaka kasheni ka huta. Kuma sai ka biyani kuɗin wanda ka korar mini, ɗari
shida"
"Bana son ganin wannan ƙashin, kwana uku kawai na baki
ya koma" yayi maganar yana sake shafa wuyanta. Riƙe hannunsa tayi, tana
kallon idonsa, da abun da yake yi matan ko a jikinsa.
Ɗan muzurunta ne, ya yo tsalle yana yakushin ƙafar Al'amin,
saboda riƙe wuyan jauhar da ya yi, yana kuka.
Al'amin ya kalli muzurun, yayi cilli da shi, ya ce "Na
kusa mayar da abun nan in da na ɗauko shi, ya fiye zaƙewa, zo ki yi mini
aikina"
Ta biyo shi tana mitar ya korar mata coustomer's , ya nuna
mata kujera 3seater ya ce ta zauna.
Ta nemi wuri ta zauna, ya kwanta ya miƙe ƙafafuwan sa a kan
cinyarta ya kaɗa mata yatsunsa, alamar tayi masa tausa.
Ta ji haushin yi mata asarar ɗari shidan da yayi, shi kuwa
ko a jikinsa, sai dai ƙasan zuciyarta mamaki take yi, ashe yana kallonta har
haka da ya gane ta rame.
Iya ƙarfinta ta saka tana jan yatsun ƙafarsa, tana son yayi
magana, amma ko a jikinsa.
Tun tana yi da marmari, har ta fara gajiya, dama gashi wuni
tayi aiki, tun tsakiyar azumi rabonta da baccin kirki.
A take ta fara gyangyaɗi, bacci mai ɗan nauyi ya yi gaba da
ita, kamar a mafarki ta ji abu yana taɓa cikinta, ta buɗe idonta ta ga menene,
babban yatsansa ya saka yana taɓa cikinta.
Da sauri ta ɗame cikinta, ta kalle shi, ya rufe idonsa kamar
mai bacci. Ta riƙe ƙafarsa, ta sake kallonsa, amma ya saka ɗayar ya cigaba.
Ta saka duka hannunta biyu, ta rirriƙe ƙafafunsa, tana
ajiyar zuciya kamar mara gaskiya.
A hankali ya buɗe idonsa, yana kallonta, ta sake ɗaga kai ta
kalleshi, suka haɗa ido, tayi saurin kawar da kanta.
"Dambe zamu yi ne ki ka rirriƙe mini ƙafa? Tausa fa na
ce ki yi mini".
Kamar ta yi kuka ta ce "Na gaji bacci nake ji"
"Eh da aikin banzanki ne, ba zaki gaji ba ai, kin ga
yanzu kya samu lada sama da ɗari shidan da ki ke yi mini ƙunƙuni a kanta"
A shagwaɓe ta ce "Ni ba ƙunƙuni nake yi ba fa, ka yi
haƙuri to" ya janye ƙafafuwan sa daga kan cinyarta, ta tashi da sauri,
muzurunta ya bi bayanta, ta saka hannu ta ɗauke shi ta nufi ɗaki.
Baba ya ji daɗin abun da ya tarar jauhar ta kai masa, ya din
ga murna da sanya mata albarka, tare da yi mata addu'a iri-iri.
Ganin hankalin Jauhar yana kan 'yan kuɗaɗen da take samu, na
sana'ointa, ya sanya ya ƙyaleta, baya son yawan takura mata.
A goman ƙarshen nan, haka ta din ga damunsa, a kan yawaita
ibada, dan azumin kawai yake yi, ba sauran ibadu. Da ƙyar take saka shi yayi
salla cikin dare ko raka'a biyu ce.
Dama idan aka sha ruwa, ya ƙoshi sai ya je dabar su, sun yi
shaye-shaye tukuna ya dawo gida.
Ana jibi salla, ta saka shi a gaba da naci, da magiya, su je
ayi masa aski saboda gabatowar bikin salla ƙarama.
Ya ce na za shi ba, ƙarshe ita ta zauna, ta wanke masa kan,
ta rage masa sumar da almakashi, tayi masa gyaran fuska da shaver, tamkar ɗa da
uwa.
Ana gobe salla, ta yi masa list dai-dai na talaka, ta ce ya
sayo, za ta yi abincin salla, dan abubuwa da dama idan ba ta ce masa yayi ba,
ba zai yi ba, idan kuwa ta ce ya sayo zai sayo, idan ba shi da hali kuma zai
gaya mata ba yanzu ba.
Da sassafe ƙarfe bakwai, ta shigo ɗakinsa da mp ɗin ta, an
sako kabarbari da ake yi yayin tafiya idi, tana maimaitawa.
*Allahu Akbar, Allahu Akbar la'ilahaillala*
*Allahu Akbar, Allahu Akbar walillahil hamd*
*Allahu Akbar kabiran*
*Walhamdilillahi kathiran*
*Wa subhanallah bukratan wa asila*
"Master, kar mu makara sallar idi fa, ka tashi" ya
motsa a hankali yana yamutsa fuska.
Ta miƙa masa hannu ta ce "Barka da salla? Ina fatan ka
yi sallar idi lafiya"
Yayi miƙa tare da hamma, ta ce "A'uzibillah,
Alhamdilillahilazi ahyana, ba'ada ma amanatana wa ilaihil nushur. Ga ruwa mai
zafi can, ka zo ka karya mu shirya"
"Sai na karya tukuna"
"To taso ka yi brush, ko sai na ɗauke ka ne, sai ƙara
maƙalewa ka ke yi a katifa"
Kukan ɗan muzurun nan ne ya sanya Al'amin shi tashi zaune ba
shiri, ya biyo jauhar yana yi mata ɗan kuka.
Ta kalli muzurun ta ce "Sweetheart, mu je na baka
abinci" Al'amin ya tashi ya bar ta da muzurunta, saboda zaƙewar muzurun ta
fara yawa a kan matarsa.
Ya fito daga wanka, ta shigo ɗakin da wata leda, ta saka
dogon hijjabi light blue, sai zuba ƙamshi take.
"Master yi sauri zamu makara"
Ya shafa mai, ta buɗe ledar ta fito da ɗinkakkiyar shadda
light blue, da hula, ga agogo sai takalmi soso na ta da nasa, iri ɗaya na ta na
mata na sa kuma na maza.
Turus yayi yana kallonta, cikin tsananin mamaki.
"Ungo saka, bari na je na rufe ɗakina kan ka gama"
Kamar soko ya kasa karɓar kayan.
"Ko ba ka so ne?" Tayi maganar a sanyaye.
"A ina ki ka samo wannan kayan?"
Ta ce "Dama ana samo kaya ne? Neman kuɗin da ka ke cewa
na saka a gaba ne, ka san wata nayi ina yi mana tarin nan? Hmm saka kayanka ina
zuwa bari na ɗaukko wayata da darduma" ta ajiye masa ta fice.
Kallon kayan ya din ga yi yana jujjuya su, har da aiki a
jikin kayan, shi bai yi mata kayan salla ba tayi masa?.
Ya saka wandon, ya tsaya yayi shiru yana kallon rigar, har
ta dawo ɗakin.
"Master saka mana" ta karɓi rigar tana ɓalle
botiran jiki, ya karɓa yana sakawa ta ce "Alhamdilillahilazi kasani haza
saub, waraƙatani min gairi haulin minni wala ƙuwwa"
Ta saka masa hula, ta saka masa lence ɗin hannun rigar, ta ɗaura
masa agogo, tare da saka masa farin glass na maza.
Tayi wani irin murmushi ta ce "Tubli wa yuklifllahu
ta'ala. Wallahi kana da kyau master, ka ga yadda ka yi kyau kuwa? Subhanallah
saka takalmin mu ke falo na yi maka hotuna" gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi,
ashe matan ma sunan suka tara? Wace irin mace ce jauhar.
"Master ka yi dariya mana, sai hoton ya fi kyau"
Ta gama yi masa hotunan, ta riƙo hannunsa, ita ma ta saka
nata gilashin fari, suka fita sallar idi.
Musulunci mai daɗi, al'ummar musulmi na ta ɓarkowa ta kowane
angle zuwa masallacin idi.
Shi rabonsa da zuwa sallar idi ma, har ya manta lokacin,
amma yau albarkacin auren mace ta gari, ta saka shi a gaba har zuwa masallaci.
Aka idar da sallar idi, suka haɗu a wani gate ɗin daban,
bisa koyi ga sunna, jauhar ta bawa wata wayarta, ta ce dan Allah tayi mata
hoton first eid with habinbi.
Ta ɗauka zai ce baya so, bisa ga mamakinta, sai ta ga ya
saka hannu, ya dafo kafaɗarta jikinsa, yana kallonta, ta saka hannu ta zagaya a
ƙugunsa kasancewar da kaɗan ta wuce ƙugunsa, ta kalleshi ita ma tana murmushi.
Hotunan sun yi kyau sosai, banda wanda ya yi wa Al'amin kyakkyawan sani, ba zai
gane shi ba, sai ya zama very decent and calm.
Har suka dawo gida, hannunta na cikin nasa, cike da shauƙi
da nishaɗi.
Ya karɓi mukulli ya buɗe musu gida suka shiga, jauhar baba
ta fara kira, ta yi masa barka da salla, ya ce mata idan mijinta na da account,
ta tura masa ya saka mata barka da salla.
Ta kira yaya saifu ma, haka ta din ga bin family tana yi
musu barka da salla.
Ta kalli Al'amin ta miƙa masa wayarta ta ce "Saka mini
lambar baba, mu yi masa barka da salla"
"Bani da ita" ya bata amsa.
Ta marairaice ta ce "Dan Allah master"
Ya ce "Sai kuma ki yi"
Haka ta haƙura ta tashi ta ƙyale shi, ta tafi ɗakinta, ya
din ga kallon kayan jikinsa, yana sake jinjina ƙoƙari da ƙarfin hali irin na
jauhar, wai shi ta yi wa kayan salla.
A status ɗin ta, ta yi posting "Alhamdilillah first eid
with my amazing Habibi, Allah ya ƙara wa zamaninka tsayi, ya maimaita
mana"
Surayya ce ta fara ganin status ɗin, ta din dariya tana nuna
wa 'yan gidan, suka din ga cewa pretending ne, na lallai sai ta nuna wa mutane
tana cikin kwanciyar hankali, sai dai suna tsaka da gulmar, ta sake saka
hotonsu riƙe da dadduma a filin idi, wanda hakan ba ƙaramin girgiza su yayi ba
da ba su mamaki.
Master ya kai mintuna goma sha biyar yana zaune, ta fito
sanye da leshinta da ta saka ranar ɗaurin aure, ta shafa powder da jambaki, ta
saka kwalli, ta kwantar da gashin gaban kanta, da gel, ta yi ɗauri mai kyan
gaske, gashi ta kaiwa Suwaiba tela ta gyara mata ɗinkin, dai-dai jikinta.
Har ya tashi zai shiga ɗakinsa, ya waiwayo ya ganta ta fito,
mp ce a hannunta, tana bin waƙar da aka saka, a cikin nishaɗin barka da salla.
Cikin waƙar m sharif *Farin gani kai ne tauraro, ko a cikin
samari, mai ji da ni ba ka yin ƙwauro ka sa na wuce gori, na ɗau takarda na
riƙe biro, kai na saka a fari, kai zan ba dawakai, kowanne da silkai,
matsayinka ya kai ba zan yi ma kishiya ba.......
Da haka ta ƙaraso gabansa tana rawa, tana yi masa fari da
ido.
Tsayawa yayi yana kallonta yana murmushi, sai dai bai tsinke
da lamarin na ta ba, sai da ta ƙaraso gabansa ta riƙe hannunsa wai sai ya yi
rawa.
Karo na farko da ya buɗe haƙoransa talatin da shida yayi
dariya.
"Ba dariya zaka yi ba, ka yi mini liƙi ko ka yi mini
rawa" ya buɗe baki ya ce "You are not serious"
"Am serious mana, rawa ko liƙi, biyani ɗari shida ta ma
da ka korar mini coustomer's" ya saka hannu a aljihunsa ya ciro dubu biyu
da ɗari uku ya ce "Suke nan nake da su, uwar son kuɗi"
"Ungo dubu ɗaya, sauran bari na bayar da ayata a markaɗo
mini, na haɗa da snacks da tuwon salla na raba. Ba ka ce ma na yi kyau ba, ka
taɓa ganin mace da tayi kwalliya tayi kyau kamar yadda na yi yau?"
Yayi murmushi ya ce "Ni da ba kallon mata nake yi ba,
ya za ayi na sani, ni dai ba ki yi mini kyau ba, kamar babyn roba haka ki ka
zama" yayi maganar yana matsa kumatunta.
"Daga Angela zuwa 'yar madara, yanzu kuma babyn
roba?"
"Eh, irin na wasan nan ba"
Jauhar ta ce "Kyau nayi maka ne"
Ta fice tsakat gida, tabbas tayi kyau kam, tayi fresh farar
fatarta ta karɓi baƙin leshin sosai da sosai, kwalliyar ta yi mata kyau.
Tana tsakar gida, wasila ta shigo ta kawo mata tuwon salla,
suka gaisa tare da yi wa juna barka da salla.
Wasila ta ce "Jauhar iyayen soyayya, mu matan layin
nan, tare muka haɗa kai muka tafi idi, a hanya muka hango ku, an maƙalƙale
hannun master ana yashe baki, kai jauhar a ji tsoron Allah"
Jauhar ta ce "Anty wasila kina saka mini ido wallahi,
ki sa ka in ta jin kunya"
"Ke ba wata kunya, riƙe abunki wallahi, abunku gwanin
sha'awa, kafin lokacin ya wuce, ba kowane namiji ne yake jure ayi ta soyayya
ba".
Al'amin ne ya fito, Wasila tayi tsit dan ba ta san yana nan
ba, ta gaishe shi ya amsa ciki-ciki.
"Master ina zaka? Kunun aya ka san baya daɗewa"
"Nura ne a waje ya kirani, ba nisa zan yi ba"
Ta ce "Ok to"
Daga jikin gate guduma ya ce "Antynmu barka da
salla".
Jauhar ta ce "Yauwwa malam nura, ina fatan ka je
idi?"
"Eh na je, na biyo mu gaisa sannan ki bani tuwon
salla".
Jauhar ta ce "Aikuwa ka samu, amma sai ka kai mini
markaɗen aya, ka sayo ƙanƙara sai na haɗa maka da tuwon"
Ya ce "Ba case matar babban yaya"
Al'amin bai sani ba, har gidansu jauhar ta aika da abincin
salla, guduma ne ya kai ya kai na gidan su ita ma.
Ta zuba wa Al'amin, ya tafi da shi, tun da ya shiga wurin na
su, Liti da sauran yaran suke bin sa da kallo.
Liti ya ce "Maza, wannan shuɗiyar audugar ruwan sararin
samaniya fa, waye ya sayeka cikinta?"
"Ban sani ba"
Walid ya ce "Abun a tambaya ne, ni fa tun da na sanka
sau ɗaya na ga ka saka manyan kaya, ranar da aka zarga maka uku, ina nufin
igiyar sunnar ma'aiki da bint laban ɗin ka, wato madam 'yar madara"
Ya tsuke fuska ya ce "Mai laya"
Walid ya ɗaga masa hannu ya ce "Tuba nake, na kiyaya
wannan ma'adanar abincin fa?"
Al'amin ya ajiye musu kwanuka, suka dirarwa abincin nan da
ci babu ji babu gani.
Baba kuwa yaya saifu ya aiko, aka kawo mata fulasanta, da kuɗi
dubu goma, kasancewar ba ta tura account number da ya ce ba a matsayin barka da
sallar ta.
Da daddare da ya dawo, yana shigowa ta ji warin sigari, dan
da alama ma a cake yake, bai kulata ba, ya tafi ɗakinsa ya baje a kan katifa,
ta bi bayansa har cikin ɗakin, cikin matsananciyar damuwa ta ce "Haba
master, shi ne ka je ka sha da yawa, kalli a yadda ka dawo fa, gaba ɗaya ka ɓata
mini ɗan farincikin da na tsinci kaina a ciki yau" yayi shiru yana sauke
numfashi.
Ta ƙaras ta ce "Tashi a cire kayan to, sai ka saka
wasu"
"Get out"
"Ai zan tafi amma......
"I said get out" yayi maganar cikin tsawa.
Ta tashi a razane, ta bar masa ɗakin, cikin azumi dai Allah
ya taimaketa ya ɗan nutsu, saboda baki a rufe yake, ba ya shaye-shaye sosai,
yau da ga sallacewa ya koma ruwa.
Saboda tsabar takaici, ko baccin kirki ba ta yi ba.
Da safe kamar ba shi ba, ya tashi ya fito abun sa, ya sayo
abun karyawa, sai share shi take yi, amma ya nuna ko a jikinsa. Kasancewarta
mai matukar raunin zuciya, sai kuma ta sake.
Suna karyawa, Hafsa ta kira ta a waya, jauhar ta ɗaga tayi
mata sallama ta ce "Amarya ba kya laifi"
"Mhmm, dama anko ne mama ta ce sai an nuna miki, shi
'yan gida za su yi da bikina, zan turo miki ta what's app lace ne dubu goma sha
biyar sai atamfar kamu dubu tara, na san ba lallai ma ki yi"
Jauhar ta yi murmushi ta ce "Anty hafsa kenan, aikam
dai kun san mijina talaka ne, zan sako dai abun da Allah ya hore mini na zo, in
sha Allah"
"Dama na sani ai, mama ce ta takura a turo miki kar
abun ya zama surutu, a ga kin fita daban. Allah ya sauwwaƙe tisya"
"Ba tsiya ba ce anty hafsa, idan ruwanka bai isa alwala
bane sai ka yi taimama Allah ya kaimu bikin lafiya" ba shi aka gaya wa ba,
amma sai ya ji maganganun hafsan tamkar direct da shi take, wani irin haushi da
takaici ya kama shi. Sai dai ya basar ya cigaba da karyawa abun sa.
Ya kammala ci, ta tashi ta yi aikace-aikacenta, yau ma wata
kwaliyyar ta yi da abun da Allah ya yassare mata.
Ya ce "Babyn roba"
Ba ta kalle shi ba ta ce "Saura ta rodi"
"Zaki gama kumbure-kumburen naki ki sace"
Ta share shi, tana shafa muzurunta d take cewa boti.
"Ina magana ki ka share ni, kina wasa da wannan abun da
nake dana sanin kawo shi?"
"To me zan ce maka? Kawai ka je ka sha abun da ka sha,
daga yi maka magana ka hantare ni" tayi maganar idonta na cika da hawaye,
saboda takaici.
Maimakon ya damu, sai yayi murmushi ya saka hannu ya matsa
kumatunta a hankali ya ce "Abun wasa na, you are like a toy to me, wani
abu mai ɗan bani nishaɗi wasu lokutan"
Galala take bin sa da kallo, ita ce ma abun wasan.
"Kin daɗe kina yi mini abubuwa, abun da ki ka yi mini
jiya ya tsaya mini a rai, ki ka ɗinka sutura sukutum ki ka bani, Allah ya
suturtaki ranar da bayi za su tsaya a gabansa babu sutura. Na gode Allah ya
baki miji nagari"
Da sauri ta sake kallonsa, sakamon abun da ya faɗa na Allah
ya ba ta miji nagari.
"I still mean it, haryanzu ina kan bakana na rabuwa da
ke a duk lokacin da ya dace, kina takura mini da yawa"
A fusace ta saka hannu, ta buge hannunsa da ya riƙe
kumatunta, ta waiwaya tana kallon gefenta.
Ya ce "Idan ki ka kuskura ki ka jefe ni, yau ni da ke
ne" tashi ta yi tana kuka, ta nufi ɗakinta.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan
kitchen wnd suke available ba order ba??
Kina bukatar
adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??
Kiyi joining wnn
group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya
available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Ba ta ƙara kula shi ba wunin ranar, dama kuma ficewa yayi ya
bar gidan, ta rasa sai zuwa yaushe Al'amin zai yadda ya karɓeta su yi rayuwa,
kullum ba shi da magana, sai maganar da zata tayar mata da hankali na zai rabu
da ita, gaba Al'amin yayi hannun riga da duk tausayi.
Abun da zuciyarsa ta raya masa kawai yake yi, ko ya yi maka
daɗi, ko akasin haka ba damuwarsa bane ba.
'yan yaran da suka din ga shigo mata yawon salla, su ne suka
din ga ɗebe mata kewa da rage mata damuwa.
Sai bayan sallar magariba sannan ta sake ganinsa, tun da ta
yi masa sannu da zuwa, ta ajiye masa abinci, ta koma gefe ta na danna wayarta.
Sai da ya ci ya ƙoshi, ya samu wuri a kusa da ita ya zauna,
ya ce "Abun wasan, ya dai?"
Ta ɗaga kai ta kalleshi ta sunkuyar, ta hau wasa da yastun
ƙafarta.
Hannunsa ya saka shi ma a yatsun ƙafarta yana tayata wasan
da take yi da su.
"Master"
"Mmm"
"Meyasa ka ke son lallai sai ka sake ni ne? Saboda ka
ga bani da makoma ko? Ban taɓa burgeka, duk ƙoƙarin da nake yi, ba ka
appreciating kullum cikin tsorata ni ka ke, kana gaya mini abun da zai ɗaga
mini hankali, me nayi maka ne?"
"Baki dace da ni ba, da salihin mutum nagari ki ka
dace. Da zan iya samun mutum mai amana da zai riƙe ki, zan iya rabuwa da ke ya
aura, you have an innocent soul, that
doesn't deserve someone like me, shiyasa nake yawan gaya miki haka. Ko jiya a
fusace nake, na yi miki tsawa sai da ki ka yi kuka, ina ɗaukar hakkinki"
"To ni na ce maka bana son zama da kai ne? Ina yi maka
addu'a, wataran zaka daina ai ko?" Tayi maganar tana kallonsa.
Yayi shiru bai yi magana ba, "Dan Allah ka yi magana,
zamu iya rayuwa tare, irin damuwar ɗaya, matsalar iyalan da muka tashi a
tsakanin su, ba sai mu zama familyn junanmu ba, mu rayu cikin aminci da
walwala. Amma master meyasa ka ke shaye-shaye bayan ka san yana da illa ga
lafiyarka? Yana saka aikata abubuwan da bai kamata ba, kayi faɗa da mutane a
zubar maka da jini, ko ka zubarwa wani, har kisan kai fa yake saka".
"Wa na kashe?"
Ta ce "Ranar da na fara ganinka, a unguwarmu, gawar
wani na ganka da ita ka soka masa wuƙa"
Yayi murmushi, ya haɗiyi wani abu mai ɗacin gaske.
"Ban taɓa kisan kai ba, ranar ce haɗuwarmu ta farko ko?
Ban kashe kowa ba"
Cikin damuwa ta ce "Amma wuƙa fa na gani a gefen
cikinsa, kuma meyasa ka ke shaye-shaye?"
"Bana son silly question, rabu da ni" ta gyaɗa kai
kawai ta ƙyale shi.
Ranar hawan salla kuwa,
Jauhar ba ta san me ake yi ba, Al'amin ya haɗa yaransa, da miyagun
makamai, da sunan tsaro kar wasu daga wani wurin su zo su fake da kallon hawan
salla, su kawo musu farmaki su cutar da wani.
Sai dai sun yi ba ta kashi da wasu marasa jin sosai da
sosai, ciki kuwa har da yaran madaki.
Sai da 'yan sanda suka yi kame sosai da sosai, daga wurin
hawan Al'amin bai koma gida ba, ya wuce cikin gari, saboda kar jauhar ta ganshi
da makami, da jini.
A cikin garin ma, sai da suka yi wata fitinar, aka yi
sare-sare da faɗace-faɗace.
Sai bayan kwana biyu, jauhar take jin labarin abun da ya
faru a wurin hawa, ganin Al'amin lafiya ƙalau ya sanya ta kwantar da
hankalinta, tare da bawa kanta yaƙinin cewar babu shi a rigimar.
Kwana na huɗu, tana kitchen tana girki, tana shirin kaɗa
miyar cin tuwo, maman halimatu ta shigo gidan a gigice.
Jauhar ta ce "Maman halimatu lafiya kuwa?"
"Ke kina nan baki san abun da yake faruwa ba?"
Cikin rashin fahimta ta ce "A ina?"
"Wani ɗan daba ne wai madaki, daga can unguwar ku ya zo
unguwar nan wai neman mijinki, wai ya illata masa yara, sai tarwatsa mutane
suke yi, suna sara kan mai uwa da wabi a guje na ƙaraso"
Cikin tashin hankali ta ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un" take kanta ya sara, jikinta ya hau rawa, ta ɗauki wayarta ta kira
lambar sa, sai dai tayi ta ringing baya ɗagawa.
Hijjabinta ta ɗauka, maman halimatu ta ce "Ina zaki?
Saran mutane fa suke yi, duk wanda suka samu duka ko sara".
Ai ba ta ko tsaya bata amsa ba, ta fita cikin matsanancin
sauri da tashin hankali.
Ba ta san in da za ta nufa ba, addu'a kawai take yi da roƙon
Allah, Allah ya tsare mata mijinta.
Mutane na guje-guje ita kuwa kutsawa take tana duba ina zata
ganshi tana kuka.
A wani layi ta hango shi, ya riƙe wani matashi, idon Al'amin
kawai ta kalla ta san a buge yake, babu alamar mutunci a idonsa, idanun sun yi
jawur sai gumi yake yi, yanayin sa ya tabattar mata da ha tafka ɓarna, kafin ta
ƙarasa, ya fito da harshen sa waje, kamar yadda yake yi, idan ya ƙudirci aniyar
yin wani abu, ya ɗaga sweazland ɗin sa, babu tsammani ya ganta a gabansa, ta
riƙe rigarsa tana girgiza masa kai cikin tsananin tashin hankali.
"Idan ka kashe shi, rufe mini kai za ayi, ba lallai na
sake ganinka, ka yi haƙuri kar ka yi kisan kai dan Allah"
Jikinsa tsuma kawai yake yi, ya aiwatar da abun da zuciyar
sa take raya masa, saboda yadda haɗin da yayi amfani da shi, yake fizgar kansa
yake jin sa tamkar jinjirin doki, zuciyarsa kuma kamar an kunna wuta.
Ta rirriƙe hannun da ya riƙe wuƙar da shi, da hannu ɗaya ya
yi jifa da matashin gefe, shi kuma ya saki wuƙar, sai tangaɗi yake yi, ya kasa
tsayuwa, sai gumi da yake tsatsafo masa ya furta "Madaki" kawai ya
yanke jiki ya faɗi, sai a lokacin ta ga uban saran da yake gadon bayansa, ashe
duk abun nan an sare shi a baya, rigarsa ta rine da jini.
Wani irin gigitaccen kuka ta saki, ta ce "Na shiga uku,
dan Allah ku taimaka mini a kai shi asibiti" tayi maganar tana girgiza
shi. Ya kalleta da idanunsa, suka yi jawur, jikinsa ya fara rawa ga gumi ya
jiƙa masa fuska.
Ragowar mutanen da suke wurin, suka dare suka bar ta da shi,
a wurin.
"Master dan Allah kar ka rufe idonka, yanzu zamu tafi
asibiti, Allah ka kawo mini ɗauki, Allah ka duba lamarin nan".
Guduma ne ya shigo cikin layin da gudu, ya jefar da makamin
hannunsa ya ƙaraso, wata irin ajiyar zuciya ta saki, yana zuwa ya jijjiga
Al'amin ya ce "Master" sai dai idanunsa sun lumshe, saboda jinin da
ya zubar.
Yayi ƙoƙarin ɗaga Al'amin, ya saɓa shi a kafaɗarsa, amma abu
ya gagara, ba ƙiba ce da shi ba, sai dai akwai nauyi.
Ya kalli Jauhar da ta rikice, take ta kuka ya ce "Anty
ki kwantar da hankalinki, in sha Allah yanzu zamu kai shi asibiti".
Ya din ga wani irin fito, kan ka ce kwabo, wasu matasa suka
din ga ɓullowa da ɗaya ɗaya, su ma suna fiton wasu suna fitowa.
Suna zuwa suka yi tara-tara suka sunkuci Al'amin, guduma ya
saɓa shi da ƙyar, da ƙarfin tsiya suka ƙwaci 'yar ƙurƙura a titi, suka ce mai
ita ya bi si Asibiti su karɓa.
Sai dai da suka je, ma'aikatan lafiya, suka ce ba za su karɓe
shi su duba shi ba, sai da jami'an tsaro.
Cikin kuka ta ce "Dan girman Allah kar ku yi mini haka,
ku ceto ransa kar ya rasa ransa, dan Allah ku fara duba shi, kan a kawo 'yan
sandan" ma'aikatan suka ƙeƙashe ƙasa suka ce, sai fa jami'an tsaro sun
zo".
Ta din ga rusa kuka a cikin emergency, guduma sai bata
haƙuri yake yi.
Ta kasa jurewa, ta tashi ta bi wani likita, ta riƙe rigarsa
tana kuka ya ce "Dan girman Allah ka ceto rayuwar mijina, kar a rasa ransa
dan Allah"
Ya ce "Ba laifina bane ba, dole mu san meyafaru kafin
mu taɓa shi".
Kan kace kwabo, sashen emergency ya cika da 'yan daba,
saboda an kawo al'amin.
Babu tsammani ta ga shigowar liti tare da Walid, da wasu
tawagar marsa jin suna take musu baya.
Suka ƙaraso, in da jauhar ke zaune, da Al'amin a gabanta.
Walid ya ce "Madam, ya aka yi haka ta same shi?"
Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, kawai ce mini aka yi
ana faɗa, na je na tarar da shi, da zai cakawa wani wuƙa amma ya fasa, kawai
dai ya ce madaki ya faɗi ashe an sare shi, kuma sun ƙi duba shi wai sai ƴan
sanda sun zo, dan Allah ka saka baki yaya Walid.
Ya kalli liti ya ce "Zan ɓallo ruwa, a toshe magudanan
daga waje" liti ya jinjina kai, ya ja guduma suka fita.
Wasu daga cikin matasan suka shigo, suka koro wasu daga
majinyata waje, suka ritsa likitoci da makamai, sai sun duba Al'amin.
Aka ce su kai shi kan gado, Walid ne ya ɗauke shi, suka kai
shi kan gado, saran da aka yi masa ba ƙarami bane, yayi zurfi, hakan ya ƙara
razana Jauhar.
Liti ya ce "Wannan yankan madaki ne yayi masa shi,
wannan shegiyar wuƙar da aka ce ta tsafi ce, da ita yayi masa saran".
Jauhar ta ce "Na shiga uku, ba zai tashi ba
kenan?"
Walid ya ce "Zai tashi ki kwantar da hankalinki"
Aka yi wa Al'amin ɗinki, kamar ƙwarya aks ɗinke bayansa, sai
dai walid ba su bari an yi a gaban jauhar ba, aka ɗibi jininsa, dan dubawa idan
sai an ƙara masa jini, sai dai baya buƙatar ƙarin jini, sai dai an saka masa
ruwa saboda jirin da yake yi ya hana shi tashi.
Sai dai ana tsaka da duba shin, jami'an tsaro suka iso,
Walid ya ce kar matasan nan su bar su su shigo, sai an gama yi masa komai.
Aka din ga artabu da 'yan sanda da dandazon, yaran da suka
yi wa harbar emergency ƙawanya, da kyar 'yan sandan suka shiga.
Da ƙyar aka tarwtsa tarin matasan nan, tana zaune ta ƙurawa
fuskarsa ido, ƴan sanda suka ɗauki statement ɗin abun da ya faru.
Jauhar sai addu'a take yi, tana fatan Allah ya sa ya farfaɗo.
Ta riƙe hannunsa, tana shafawa a hankali ta ce "Allah
ya shirya mini kai, ya baka lafiya master, inuwarka ce kawai nake tsaye a ciki
nake saka ran samun farin ciki, dan Allah ka daina zuwa ana cutar mini da
kai"
Idonsa a rufe, ya ɗaga hannunsa a hankali, ya shafi fuskarta
sannan ya buɗe idon a hankali ya kalleta sai dai bai yi magana ba.
"Sannu master, an yi maka ɗinki a bayanka, akwai abun
da yake yi maka ciwo ne?" Ya girgiza kai almar a'a.
Ta shafi sumar kansa ta ce "Allah ya baka lafiya"
Juyi yayi a hankali, ya kwanta a kan cinyarta, muryarsa
ƙasa-ƙasa ya ce "Idan kina kuka ciwon ƙara zafi yake yi" ta goge
hawayenta ta ce "To na daina, amma idan aka ji maka ciwo, zuciyata ce take
kuka ba na so master".
A hankali yake matsa hannunta, yana jin wata nutsuwa ta
mussaman, da sassaucin zafin da zuciyar sa take yi masa.
Zuwa magariba, ya miƙe ya ce sai sun tafi gida, Jami'an
tsaro suka ce za su tafi da shi, sakamakon tayar da tarzoma a unguwa.
Walid ya ce "Saboda hauka ake yi, master ku ware gida,
ni ku tafi da ni mu muka je muka tayar da tarzomar"
Ana fito da Al'amin, guduma ma ya taso, da sauri, Al'amin
daga shi sai dogon wando, suka tari napep suka tafi gida.
A wurin maman halimatu jauhar ta karɓi mukulli, ta buɗe musu
gidan suka shiga.
Ta saka yayi wanka, yayi alwala ya rama sallolin da ake bin
sa, ta kawo masa abinci ya ci.
"Master" ya kalleta "Dan Allah ka fita daga
shirgin madakin nan, ba shi da imani, kar ya hallaka ka dan Allah"
"Sai dai ɗaya yayi ajalin ɗaya ko ni ko shi, shari'ata
da shi, Allah ne kawai zai rabata"
Cikin rauni ta ce "Ina haɗaka da girman zatin
Allah"
"Shhhh, ki daina haɗa ni da Allah, kin san nauyin abun
da aya aikata mini?"
"Ban sani ba, amma ina da yaƙinin koma me zaka yi masa,
ba zaka huce ba, ka yi haƙuri ka bar wa Allah mana, idan wani abun ya same ka
ya zan yi ne? Yanzu kalli halin da ka sakamu a ciki, na san yanzu haka a cikin
pain ka ke, ciwon a jikinka yake, amma a zuciyata nake jin raɗaɗin, haba
master, haba dan Allah" tayi maganar wasu zafafan hawaye na gangarowa daga
cikin idanunta.
Ya miƙa hannunsa ɗaya da ba a side ɗin ciwon yake ba, ya
janyota jikinsa, ba ta musa ba ko yi masa gardama, ta kwanta sosai ta cigaba da
kukan, tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa sosai, kasancewar babu riga a jikin
sa.
"Ba zan ɓoye miki ba, ban taɓa tunanin zan yi wata
alaƙa da wata 'ya mace ba, saboda ina yi musu kallon azzalumai, ke ki ka fara
canza tunanina".
Al'amin Ibrahim shi ne cikakken sunan Al'amin, mahaifinsa
haifaffen garin kano ne, gidansu gidan yawa ne, baban Al'amin shikaɗai ne a
wurin mahafiyarsa, sai tarin 'yan uba da galibinsu mata ne.
Yayi karatu daga primary zuwa sakandare har yayi diploma,
sai dai aikin yi ya gagara samuwa, akwai abokinsa sammani da suka yi karatu
tare, tare suke yawon neman aiki, ya ja shi garin su tofa, aka samo musu gona,
suka fara noma.
A can ya haɗu da Zahra'u, ya ce yayi mata, da fari
tsokanarta yake yi, saboda kwalliyar da take yi ta 'yan ƙauye ce take bashi
dariya, daga baya soyayya ta ƙullu a tsakaninsu.
Abu kamar wasa, har ta kai ga aure, duk da bashi da wata
ƙwaƙƙwarar sana'a, sai kame-kame.
Sun sha gwagwarmayar rayuwa tare, sun yi faɗi tashi, sun yi
fama da yanayin rayuwa, kafin Allah ya buɗa masa ya fara samu.
Lokacin da suke cikin wahala babu mai taimakonsa, daga shi
sai ita suke wahalar su, ta samu ciki a lokacin ta haifi ɗan ta na fari, aka
saka masa Abubakar Assidiƙ, sai lokacin da Allah ya fara buɗa masa, 'yan uwansa
suka saka musu ido, da surutun yana zaƙewa da yawa a kanta.
Komai ya samu ita, ya tashi daga tsakiyar cikin garin kano,
ya koma gwauron dutse yayi mata gida mai kyau.
'yan uwansa suka fara tsangwamar ta, da cewa ta shanye musu ɗan
uwa, Ibrahim ya mayar da ita makaranta ya samo mata admission a FCE, ta ke
karantar English islamic. Kasancewar ta mace kyauta, da fara'a da sakin fuska
ga mutane, ya sanya take da masoya sosai. Sai dai duk da kyautarta, da son
mutane dangin mijinta ba sa ƙaunarta.
A can gwauron dutsen, ta haɗu da wata mata rahila,
maƙwabciyarta ce, tana yawan zuwa ta kawo mata complain a kan mijinta ba ya
kula da ita da yaranta, hakan ya sanya tausayin rahila ɗarsuwa a zuciyar
Zahra'au, kusan kullum cikin yi wa rahila aike take, na abun da zata kula da
yaranta, kuɗi, sutura, abinci kayan masarufi, saboda Ibrahim yana sakar mata
sosai baya yi mata iyaka da komai.
Tana NCE 2, Sadik ya shekara biyar, ta samu ciki, tayi ta
fama ga laulayi ga karatu, rahila take barwa Abubakar ta tafi makaranta,
ƙarshen wata, take biyanta da kuɗi mai kauri saboda ita ma ta samu.
Ta haifi ɗanta na biyu, aka saka masa Muhammad Al'amin,
saboda haihuwar maza da take yi, dangin miji, suka ƙara yi mata caaa wai tana
ta haifar maza, dan ta kwashe komai na gado idan ya mutu.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Ya saki Sadik a ƙasa bayan ya caka masa almakashin, cikin
tsananin tashin hankali, Al'amin ya yi kukan kura ya danƙi ɗan daban, amma wani
daga cikin yaransa, ya lallaɓa ya sake maka masa gora a baya, ya gantsare yana
wani irin ihu, suka yi gaba suka bar su.
Ya din ga dukan gate ɗin gidan, yana ƙwalawa Abbu kira, ya
koma kan Sadik, ya rungumo shi, yana jijjiga shi.
Sai da garin yayi shiru, sai kururuwar Al'amin yana kiran
Yaya.
Maƙwabcinsu ya fito, na kusa da shi ma ya fito, aka din ga
buga gidan su Al'amin, har aka tafi nemo mota, sannan Abbu ya buɗe. Sai dai ya
shiga tashin hankali, ganin Sadik a kwance kamar mara rai.
Cikin tashin hankali Abbu ya tafi kici-kicin fito da mota,
Al'amin ya zuciya ya ɗauki Sadik a kafaɗarsa, kawai yayi gaba.
Da ƙyar aka riƙe shi, aka saka Sadik a mota.
Al'amin sai zubar da hawaye yake yi, ya na kiran "Yaya
ka buɗe idonka ka kalleni, ka tsaya yanzu zamu je asibiti"
"A galabaice, Sadik ya motsa ya riƙa hannun Al'amin,
sai kuma hannunsa ya saki. ko da suka je Asibiti, aka tabattar musu da Sadik ya
koma ga Allah.
Al'amin ya durƙusa a kan gawar, ya din ga rusa kuka, kukan
da ko lokacin da umminsu ta mutu bai yi shi ba, maƙwabta na ta rarrashin
Al'amin.
Cikin kuka Abbu ya ce "Al'amin komai ya samu ɗa na kai
ne sila, ka sa nayi rashin ɗa mai biyayya"
"A'a Alhaji Ibrahim, kar ka sake ka ɗorawa Al'amin
laifi, kai ne babban mai laifi, kana sane sarai unguwar nan babu kwanciyar
hankali, ka bar su a waje, da ka buɗe musu sun shiga gida, koman dare ai da
haka ba ta faru ba".
A daren aka yi wa Sadik sutura, Al'amin gani yake yi kamar a
mafarki, awannin da suka gabata suna tare amma a yanzu wai babu Sadik. Kodayeke
Abbu yana da gaskiya shi ne sila, da bai ce zai bar gidan yayi tafiyarsa ba, da
haka baya faru ba, dan kuwa Sadik ba ya yawon dare.
Har jami'an tsaro sai da suka zo suka ɗauki bayanan abun da
suka faru, sai dai Al'amin ya kasa magana.
Sadik ya tara ɗimbin mutane, yara da manya matasa da dattawa
wurin sallatar gawarsa, kasancewar sa mutumin kirki.
Al'amin ya ji ina ma shi aka kashe, Sadik ya rayu, yayan
nasa guda ɗaya tal da yake saukewa duk wata damuwarsa ya ɗauka babu ƙosawa ko
gazawa, an kashe masa shi.
Alhaji sammani, ya yi wa Ibrahim tatas, a kan yadda ya koma
soko a kan gidansa, tare da ci wa Rahila mutunci tsaf, a kan abubuwan da take
aikatawa.
Ƙarshe ta shiga ta fita, ta raba abotar da aka yi shekaru
ana ginata, suka rabu dutse a hannun riga, suka yi uwar watsi.
Depression ya nemi ya kama Al'amin, babu wand yake ta tasa,
gashi yanayin halayarsa idan ba wanda ya sanshi ya saba zama da shi ba, ba kowa
zai iya masa ba, saboda miskili ne, ga nuƙufurci, ba zai taɓa cewa wani ga
damuwarsa ba, shi ba abokai ba, haka ya din ga ragaita a layi, raɗaɗin mutuwar
Sadik taƙi barinsa.
Ya tafi wurin 'yan sanda ya tambayi, ko sun kama wanda ya
kashe yayansa, suka ce masa bincike suke yi a kai, dan har a lokacin ba su
tabattar da wanda yayi kisan kan ba, kuma a ranar ba Sadik kawai aka kashe ba.
Al'amin ya koma gida, yayi ta addu'a Allah ya sa a kama
wanda ya kashe masa Sadik, duk da dare ne, amma a ko ina ya ga wanda ya kashe
shi zai gane, dan kuwa ƙofar gidan su akwai security light.
Duk bayan kwana biyu sai Al'amin yaje, tun suna sauararsa
har suka fara korarsa.
Ga matsi ya ƙaru daga gidansu, babu in da zai samu abinci,
ya yanke shawarar fara zuwa kasuwa ya duba ko dako ya fara, sai da ya je ya
tarar ashe dakon ma sai ka san wani, sai an san da kai, duk sana'ar da yayi
tunanin farawa sai ya ga dole sai da jari, gashi Rahila ta cigaba da ziga Abbu,
ya ƙara tsanar Al'amin wai shi ne silar mutuwar Sadik.
Al'amin ya fara gajiya da yunwa da take neman tagayyara shi,
ya fara zuwa gida ya ɗauki duk abincin wanda ya tarar ya cinye, idan ya tafka
wannan tsiyar, sai ya gudu ya kwana a kangwaye, gashi ya koma HND tun Sadik na
raye, dama shi ne yake ta fafutukar tara school fees ɗin sa kan ya rasu, yanzu
kuma ga yunwa da rashin kuɗin transfort dan haka ya daina zuwa makaranta gaba ɗaya.
Gashi ko a maƙwabta aka rasa wanda zai yi wa Abbu nasiha, ko
su din ga taimakonsa, saboda ana ganin babansa yana da rufin asiri.
Yana can garin yawonsa, kawai ya hango wanda ya kashe Sadik,
a tsallaken titi, da tawagar matasa 'yan daba, da gudun gaske Al'amin ya
tsallaka titin, sai dai kan ya ƙarasa sun ɓace masa, cikin tashin hankali ya
ƙarasa wurin wani mai ice ya ce "Malam dan Allah wanda ya wuce ɗin nan ina
yayi?"
Ya kalli Al'amin ya ce "Meye haɗinka da shi?"
"Yayana ya kashe da almakashi, bai yi masa komai ba,
'yan sands suna ta nemansa"
"Taɓ, ka raba kanka da wannan. Madaki kenan gawurtaccen
ɗan daba ne, hukuncin kisa ma aka yanke masa a gidan yari, amma muka ga an sake
shi, duk ya gallabe mu, ya hanamu sukuni mu ma, sai dai ka bar wa Allah
kawai" Ai Al'amin bai tsya jin ƙarshen zancen ba, ya shiga cikin unguwar
ya din ga yawo, amma bai ga madaki ba.
Washegari da sassafe, ya koma wurin 'yan sanda ya gaya musu
ya ga wanda ya kashe yayansa, su tafi tare da shi a nemo shi, an gaya masa
sunansa madaki.
Wani ɗan sanda ya kada baki ya ce "Ka san mutum nawa
madaki ya kashe aka ƙyale shi?" al'amin ya ce "Ni ina ruwana da mutum
nawa ya kashe, ku kama shi a kai shi kotu ni dai".
"Ko an kai shi ma, za a sake shi, ka je ka yi haƙuri
haryanzu bamu tabattar da shi ya kashe shi ba".
Kasancewar Al'amin yana kan tashen balaga, ya sanya ya tsaya
yana yi musu rashin kunya, aka saka wani sageant, ya zane shi aka kore shi.
Hakan yayi matuƙar tunzura zuciyar Al'amin, ya din ga jin jinin ɗan uwansa ba
zai tafi a banza ba.
Ya din ga sintiri a unguwar da madaki yake, kasancewar ba su
da nisa sosai, ya samu duk bayanin da yake son samu a kan madaki, da in da yake
zama da shi da yaransa.
Ya je gida ya shiga kitchen ya samo, wuƙa sabuwa gal, ya je
ya ɓoye, ya saka a ransa shi ma sai ya kashe madaki, ko da kuwa za a kama shi a
kashe.
Sai dai aka yi rashin sa'a, Madaki bai fiye zama a unguwar
ba, sai idan zai shigo yayi rashin mutunci, Al'amin ya din ga fakonsa, har ya
yi wataran sa'a ya tarar yana nan.
Gadan-gadan ya ratsa tarin matasan da suke ɗauke da makamai
suna shaye-shaye, ya nufi madaki da wuƙa.
Matasan suka mimmiƙe, amma madaki ya ɗaga musu hannu, a
kallo ɗaya madaki ya gane Al'amin.
Kafin ya ƙarasa gaban madaki, sani ya sanya ƙafa ya taɗiye
Al'amin dan haka ya faɗi a gaban madaki, suka kwashe da wata irin dariya.
Al'amin ya yinƙura zai tashi, madaki ya saka aka take masa
kafaɗun Al'amin da ƙafa, yana ƙoƙarin tashi, amma cikin ƙarfin Al'amin ya
tashi, madaki ya tako gaban Al'amin ya shaƙe wuyansa.
Take Al'amin ya ji kamar an shaƙe shi da wata muguwar sarƙa
mai nauyin gaske, a take ya ji numfashin sa na neman ƙwace masa. Al'amin ya
saki wuƙar ya koma kokowar raba hannun madaki da wuyansa, madaki ya tsare shi
da jajayen idanunsa da ya rambaɗa musu farin kwallin tsafi, yana ƙyaƙyata wata
uwar dariya, daga bisani kuma ya tsuke rai tamau, ya ƙara tsananta shaƙe
Al'amin, sai da ya ga ya daina motsi, sannan ya watsar da shi a wurin, ya kalli
wani ya ce "Ku kai shi arear su ku watsar"
"Ba za a saita ma hanya daga duniyar ba ya ci bulus
kenan?"
Madaki ya girgiza kai ya ce "Yana cikin tsananin ɗacin
rashin ɗan uwansa, idan aka yage shi daga sararin nan, hutawa zai yi, sai ya
gane kuskuren da ya aikata na yinƙurin da yayi"
Suka ɗauki Al'amin suka kai shi unguwar su, suka jefar da
shi a sume a gaban wani mai kayan miya, suka ce wa mutanen wurin "Gashi
nan, ajiyarmu ne, zamu din ga bibiyar sa ku kira tsohonsa ya ɗauke shi idan yan
buƙatarsa".
'yan unguwa suka ɗauke shu, suka kai shi gida, Abbu yana
nan, aka kwantar da shi a tsakar gida, ana shafa masa ruwa, mai kayan miya ya
gaya wa Abbu abun da yaran madaki suka ce, aka shawarce shi a kan ya kai
maganar wurin jami'an tsaro, amma Abbu ya ce babu ruwansa, tsuntsun da ya ja
ruwa shi ruwa kan doka, shi bai aike shi wurin 'yan daba ba.
Tun daga nan madaki ya mayar da Al'amin kamar karen
farautarsa, ya saka rayuwarsa a gaba, wataran har cikin unguwar su yake aikawa,
a nemo masa Al'amin, a kai masa shi har dabarsa, su casa shi da zalunci
kala-kala, wai sa ya saduda ya nemi afuwar abun da ya yi wa madaki, dan ba a taɓa
samun wanda ya yi abun da Al'amin yayi ba, ya rasto har dabarsa ya nemi ya
kashe shi, yana ƙanin ƙanin bayansa.
Al'amin ya kalli madaki ya ce "Ka yi kaɗan na nemi
afuwarka, baƙin kare kuma in sha Allah sai na zubar maka da jini, kamar yadda
ka zubar da jinin ɗan uwana da bai yi maka komai ba"
Ya durƙusa ya soka wa Al'amin wata kibiya a cinyarsa, cinyar
sa na zubar da jini, amma saboda azabar taurin kai, ya datse haƙoransa ya ƙi
ihu.
"Na fuskanci zaka yi mini amfani, na saka ka cikin
yarana daga yau, zaka din ga yi mini aiki"
Al'amin ya girgiza kai ya ce "Ni fa kallon kare nake yi
maka, da na bika gara na yi mutuwar wulaƙanci"
Ya ce "Shikenan zamu gani, dafin ciwon da nayi maka na
fili da na zuciya ya isheka ka saduda".
Al'amin ƙafa taƙi takuwa, sai da kyar, ya din ga tagayyara a
gari, yaran madaki suka matsawa unguwar su Al'amin, duk da suma suna da
ƙasurguman 'yan daba, amma ba sa shiga harkar faɗan matasan 'yan daba.
Al'amin ya ƙi ya karaya ya saduda, ga ƙafa yana ɗingisawa,
ga yawon neman in da zai ci abinci, kullum rahiila cikin gaya wa Abbu take,
Al'amin abubuwan da yake da yadda 'yan daba suke kawo masa farmaki, sun
tabbatar da cewar shaye-shaye ya fara yi, dan haka lallai ya kori Al'amin daga
gidan, ya daina zuwa kan ya kuma janyo musu wata masifar, ta ce a kama masa
shago a cikin unguwa ya bar kwana a cikin gidan, duk da dama ba kullum yake
kwana a gidan ba.
Wata ranar juma'a da yamma, Al'amin yana tafe yana ɗingisa
ƙafarsa, yaran madaki suka shigo, da wasu irin mahaukatan karnuka, kuma kai
tsaye suka sakarwa Al'amin su, gashi ba zai iya gudu ba, saboda ƙafarsa, suka
dirar masa da cizo, ya din ga danƙar karnukan nan yana jifa da su, manyan
karnuka ne sun kai biyar, wannan ya yage shi ta nan, wancan ya kai masa cizo ta
nan, sai da suka ga yana neman fara halaka karnukan, ko su yi mutuwar kasko da
su, sannan suka nufi Al'amin suka fito da makamai. Dan madaki cewa yayi, su kai
masa wani sashe na jikin Al'amin sun cire masa.
Karnuka sun yi masa kaca-kaca da kayansa, da fatarsa da cizo
da yakushi, jikinsa duk jini, amma ya yinƙura ya tashi, ganin sun tsaya a kansa
da makamai.
Ɗaya ya shammace shi, ya sara masa wuƙa a cinya ta baya, ya
hankaɗa shi ya faɗi, yana faɗuwa suka ga ɗaya daga cikinsu ma ya faɗi ƙasa jini
na zuba daga jikinsa.
Gaba ɗaya suka ɗaga kai suna kallon wanda ya yi aikin.
Wani gabjejen mutum ne, baƙi mai jiki sosai, da jajayen ido,
a yaran madaki wani ya yinƙuro, amma ya caka masa wuƙa a ciki shi ma, ya faɗi.
Ya durƙusa ya ɗago Al'amin, jikinasa jina-jina, ya kalli
wanda suke tare ya ce "Samo abun hawa, a kai yaron nan asibiti" ya
kalli sauran yaran madaki ya ce "Ku je ku gaya wa madaki, ya zo dabata ni
dodo babban sarki, ina nemansa. Na ji labarin irin ɓarnar da yake shigowa
unguwar nan yana yi, kasancewar bana shiga shirgin shirmen ƙananan matasa, ya
sanya ban damu ba. Sai dai na wuce a mota, a wancan lokacin na ganku kuna dukan
yaron nan, wannan karon ma na ganku kun saka karnuka na cizon sa, kamar ba ɗan
adam ba awanni ashirin da huɗu na bashi, ya zo yayi mini bayani, idan ya bari
na taka na je in da yake sai dai uwarsa ta haifi wani. Ku ɗauke mini wannan
mushen, ku ɓace daga gabana" jiki na tsuma, suka ɗauki wanda aka cakawa
wuƙar suka tafi da shi.
A asibiti ɗan wando kawai aka bar Al'amin da shi, jikinsa
sai tsatstsafar da jini yake yi, saboda cizon karnuka da yakushi, ga raunin da
yake ƙafarsa, sai da aka yi dressing raunukan jikinsa, sannan aka yi masa
rigakafin cizon mahaukacin kare, dan ba a san wane irin karnuka ne suka ciji
Al'amin ba, aka saka masa ruwa, sannan aka kawo masa lafiyayyen abinci daga
restaurant.
Dodo babban sarki, bai sake bi ta kan Al'amin ba, sai bayan
magariba, ya je Asibiti da shi da yaransa, aƙalla dodo ya kai shekaru arba'in
da biyar, ya girmi madaki sosai, madaki kuma ya girmi Al'amin.
Ya tarar da Al'amin a zaune, hannunsa ana saka masa ruwa, ya
ƙarasa gaban gadon Al'amin ya ce "Sannu ka ji" Al'amin ya jinjina
masa kai.
"Yaron nan ba shi da imani ko kaɗan, tayaya zai saka a
sakarwa yaro karnuka su je shi, zai ci ubansa da ni yake zancen, zan gani zuwa
dare idan bai zo ba, sai na kashe shi wallahi" ya sake kallon Al'amin ya
ce "Kai ba kai ne kuka tare a unguwar nan shekarun baya ba? Kuna zuwa islamiyyar
dogon bene, kai da ɗan uwanka ba?"
"Ni ne"
"Ina ɗan uwan naka? Meya haɗaka da madaki kuma, na ga
kai ba irin su bane" Al'amin ya yi shiru, sannan ya ce "Kashe mini
Sadik yayi, ba abun da yayi masa, ni kuma na ga ba zan haƙura ba sai na kashe
shi nima"
Dodo ya ce "A'a dama yayanka ne aka ce mini an kashe a
layin dawaki? Madaki yana fama da gigin daba, tun da ya samu masu tsaya masa,
ya je prison ya haɗu da wanda suka fi shi rashin mutunci yake abun da ya ga
dama. Zan ci ubansa kuwa yanzu me ka ke son ayi masa gaya mini"
Al'amin ya ce "Kawai sonake shi ma ya mutu, in soka
masa almakashi kamar yadda ya yi wa Yaya" yayi maganar cikin damuwa.
Dodo ya dafa kafaɗarsa ya ce "Kwantar da hankalinka,
yanzu dai fatanmu ka samu lafiya, za aje a sanar da babanka, ya zo asibiti ya
duba ka, a samu mai jinyarka"
Ya girgiza kai ya ce 'A'a kar a gaya masa, zan koma gida
kawai"
"Na ji ba za a gaya masa ba, amma sai ka zauna an kula
da kai tukuna".
Madaki hankalinsa ya tashi, jin an kashe masa yaronsa na
hannun damansa, a hannun wanda ba zai iya ɗaukar fansa ba, dan gaba da gabanta.
Yana tsuma, suka tafi in da Dodo yake zama, aka ce sai dai
su bishi asibiti, baya nan.
Asibitin gwamanti ne, Amma amenity dodo ya biya aka kwantar
da Al'amin.
Madaki cikin girmamawa ya ce "Na amsa kira ranka ya daɗe".
"Ka san wannan ai?" Dodo yayi maganar yana nuna
masa Al'amin.
"Na san shi"
"Daga rana mai kamar irin ta yau, idan kai ko wani daga
cikin yaranka, ya sake taɓa shi, ko tsoratar da shi, wallahi sai na ƙarar da
tarihin mutum a bayan duniya. Bana shiga harkar ƙananan dabarku, amma aka kuma
ratso unguwar nan, aka taɓa shi, wallahi sai na yi abun da ba a zata ba. Ka
durƙusa ka bashi haƙuri a kan cin zarafin da ka saka aka yi masa, ka sanya
karnuka suka yi masa illa, yana ɗan adam ba dabba ba, sauran abun da ka yi masa
kuma kai da shi ne".
Madaki ya kalli Dodo ya ce "Ni zan bashi haƙurin?"
Wani wawan mari, dodo ya ɗauke madaki da shi, da sai da ya
kife ƙasa, "Ka shiga hankalinka, ka san da wa ka ke magana kuwa? Har ka
mutu ba zaka yi iskancin da nayi ba, shekarata goma a ƙiri-ƙirin lagos, ba wani
ɗan iskan da ban gani ba, ko ban sani ba, ka bashi haƙuri, ko na ciyar da
macizaina namanka"
Madaki ya kalli Al'amin, shi ma ya kalleshi, ya kalli dodo
sannan ya ce "Ka yi haƙuri, bisa abun da na saka aka yi maka da
karnuka".
Al'amin ya ce "Ko ka bani haƙuri ko baka bani ba, gaba
da ni da kai sai ranar da na rama zubar da jinin ɗan uwana da ka yi" sai
da duk suka kalli Al'amin, Al'amin ba dai taurin zuciya ba.
Madaki ya fice a muzance, a gaban yaransa aka saka ya bawa
Al'amin haƙuri, an wulaƙanta shi ƙarshen wulaƙanci, dan haka ya ƙullaci abun a
ransa.
Al'amin har ya kwana huɗu a asibiti, Abbu bai neme shi ba,
kullum abincinsa mai rai da lafiya yake samu ya ci, ga dodo shi ma kullum sai
ya zo duba shi, ya yi ta yi wa Al'amin hira, har yaransa suka fara mamakinsa,
dan Al'amin ba wani sakin jiki yake da shi sosai ba.
"Al'amin da gaske kana son ka rama abun da madaki yayi
maka?"
Al'amin ya ce "Eh"
"Tunani mai kyau, amma ka sani shi ƙarfe dole sai da ɗan
uwansa ƙarfe, yanzu an sallameka, mu je mu kai ka gida, sai ka din ga zuwa
dressing, na biya kuɗin dressing ɗinka, duk abun da ka ke buƙata zan baka
adress ɗina, a nan cikin unguwar, ka je ka same ni"
Al'amin ya jinjina kai ya ce "Na gode sosai" ya
dafa kafaɗarsa ya ce "Kar ka damu Aminullahi"
Da ya koma gida, babu wanda ya tambayi ina yaje, tsawon
kwanakin nan, ga jikinsa duk raunuka, amma babu wanda ya tambayi ya yake,
sai ƙanwarsa shahida da suke uba ɗaya.
Tun da dodo yayi wa madaki iyaka da Al'amin, ya samu
sassauci, ya cigaba da sabgoginsa, bai kuma sake bi ta kan dodo ba.
Da ƙyar ya samu aiki a wurin wani mai shayi, yake yi masa
wanke-wanke da abun da ba a rasa ba, idan ba ya nan, da shi da ƙanin mai shayin
ne suke riƙe wurin, hakan ya sanya ya fara rage damuwa da halin da yake ciki.
Sai dai ƙanin mai shayin ya nemi da su haɗa kai da Al'amin,
su ɗan din ga ɗaukar wani abu, Al'amin ya ce ba zai yi ba, ba a jima ba, yaron
ya yi wa Al'amin sharri wai yana ɗebar masa kuɗi, kuɗi kusan dubu talatin, mai
shayi ya kai Al'amin wurin 'yan sanda aka daka aka yi rarrashin ya ce shi bai ɗauka
ba, ba kuma zai amsa yayi ba. Aka yi ta kai ruwa rana, da ƙyar case ya mutu,
bayan ya shafe kwanaki a hannun 'yan sanda.
Yamma liƙis, ya je ya samu ƙanin Habu mai shayi, har rumfar
mai shayi, ya karya shi a hannun dama, aka kuma cafke shi zuwa wurin hukuma,
aka nemi Abbu, amma ya ce ba ruwansa, tun da kangarewa ya ɗauka.
Ɗaya daga cikin matasan da suke yi wa dodo aiki, wato Walid,
shi ya gaya masa halin da ake ciki. Da kansa yaje station ya karɓo Al'amin.
Ya saka shi a gaba, yana yi masa tambayoyi, a kan dalilin da
ya sa, ya aikata abun da yayi. Ya kwashe komai ya gaya masa.
Dodo ya ce "To daga yau, kar ka sake zuwa ka nemi wata
sana'a, duk abun da ba ka da shi, ka zo na baka. Na fuskanci tsohonka baya
yinka, ni kuma ehhh kawai ka kwanata mini a rai, tausayi kake bani, kana rayuwa
da kai da wanda aka bugoku cikin samfurin jini ɗaya, an ɗaye maka shi, ta
ƙarfin tsiya. Amma ba komai, zaka rama ne"
Tun daga lokacin Al'amin ya zama yaron dodo, wurinsa yake
zuwa ya karɓi kuɗin abinci, ya biya masa kuɗin registration, ya mayar da shi
makaranta ya cigaba da HND, dama shekarunsa ba su kai shiga University ba,
shiyasa ya fara zuwa poly.
Dodo harkar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi yake yi, babban
distributor ne, har garuruwa yake rarrabawa kaya.
Bai damu da harkar daba ba, sai wannan sana'ar, Abbu bai taɓa
tuhumar ya aka yi Al'amin ya koma makaranta ba, wace sana'ar ya fara duk bai
tuhume shi ba.
Dodo yana da manyan yara da matasa, ciki har da sa'an
Al'amin mai suna Walid. Sai dai Walid ya tsani Al'amin ganin yana neman ƙwace
masa fada a wurin dodo babban sarki.
Ko aike babu wanda ya isa ya aiki Al'amin, dodo ne kawai
yake sa shi ko ya hana shi, haka zai zauna a cikin su, su yi ta shaye-shaye
suna ƙuƙƙula kayan maye, amma ba ruwansa da su, ko sigari bai taɓa gwada sha
ba.
Idan yayi dare a yawonsa, sai ya tafi gidan dodo, yayi
kwanansa, dodo har safarar makamai yake yi, babban criminal sosai da sosai.
Komai Aminullahi, komai Aminullahi, lokaci lokaci, ya kan
tuntuɓi Al'amin, ko zai iya yafe wa madaki, amma ya ce har abada, har sai ya
rama abun da yayi masa ya kan yi murmushi ya ce "Aminullahi kenan, in dai
zaka zauna a haka, ba ka shirya ɗaukar fansa ba, ƙarfe dole sai da ɗan uwansa
ƙarfe, roba ba ta tasiri a kan ƙarfe" baya gane mai dodo yake nufi, dan
haka sai dai ya bi shi da to
Al'amin ya ce masa dan Allah ya samo masa sana'a, ko wace
iri ce zai din ga yi. Dodo ya ce masa zai duba.
Duk abun da Al'amin zai yi, dodo bai yadda yaransa su yi
masa wani abu na horo ko cutarwa ba, hatta kaya idan Al'amin ya cire, sai ya ce
Walid ya wanke masa, wanda kan zuwan Al'amin shi ne na gaban goshi.
Sannu a hankali, ya fara aiken Al'amin kai kayan shaye-shaye
wasu wuraren, cikin dare idan motar kaya ta isao, haka zai ɗauke shi, su tafi
su karɓo kaya.
Wataran ya aike shi, hukumar hana sha da fataucin, suka kama
shi, aka din ga tuhumar Al'amin, ya ƙi faɗan wanda ya aike shi da kayan, sai da
aka kwana biyu ana nemansa, hankalin dodo ya tashi, aka bincika aka gano masa
shi a hannun hukuma.
Ya je ya karɓo Al'amin, sannan ya ce "A bashi kayan da
aka ƙwace ayi musu kuɗi zai saya, idan suna da wasu ma a haɗa masa ya saya.
Kuma hakan aka yi.
Ya yi ta yi wa Al'amin faɗa, a kan dan me, ya zauna a
hannunsu, bai saka an neme shi, ya fito da shi ba?.
Ta kai ta kawo, Dodo yana tafiya da Al'amin wurin 'yan
siyasa, dan a nan ne suka haɗu da Indabo, a lokacin baya shan komai.
Duk da wannan abubuwan da suke wakana, Al'amin yana zuwa
gida, ya ga Abbu, ko da kuwa zai yi masa faɗa ya kore shi, yana zuwa ya ganshi.
Yaran dodo sun sha attempting koya masa shaye-shaye, amma ya
ƙi, tun Walid yana jin haushin Al'amin, har ya haƙura, manyan yaran dodo suka
saka masa mai zamani, ya kori gwamantin Walid dan haka idan yana son zaman
lafiya ya kiyayi mai zamani"
Dodo ya din ga dariya, ya ce "Kuma zamanin Aminullahi
dogo ne a wurin dodo ba, bana tunanin akwai wanda zai ture gwamantin sa a
wurina, dan mai dogon zamani dan haka mai laya" yayi maganar yana kallon
Walid.
Aka haɗa baki aka ce "Ka kiyayi mai zamani" suka
yi abun da sigar raha.
Al'amin ya je gida, domin ganin Abbu, amma ya tarar baya
nan, Rahila kuma tayi baƙi, ya shiga kitchen ya ga an yi uban abinci, ya kwaso
fulasan yayi gareji da su, ya zauna ya hau ci, duk da ya san na baƙin ne.
Yana cikin ci, sai ga wata 'yar yarinya ba ta fi shekaru
biyu ba, ta zo in da yake tana kallonsa, ta tsuguna ta saka hannu a kwanon,
tana tsintar abincin tana ci.
Ya kalleta, sai ya tuna jaririyar ummi da ta rasu, yanzu ga
shi duk su ukun babu su.
Sai ya din ga bata abincin a baki, amma hakan bai hanata
saka hannu a kwanon miya ba, haushi ya kama shi, kamar ya kwaɗe ta, ya kama
rigarta yana goge mata hannun, kawai ya ji salatin Rahila.
Ya ɗaga kai ya kalleta ta ce "Innalillahi wa
Innalillahi raji'un, na shiga uku jama'a ku taimake ni, zai lalata 'yar mutane,
Allah ya sa ba yi mata komai ba"
Sai yayi saroro yana kallonta, ya rasa gane mai take nufi,
wanda ta yi hakan ne, dan huce takaicin tozarcin da yayi mata, na cinye abincin
baƙi.
Shahida ta ce "Mama wanke wanke nake yi, ina hango su
ba abun da yayi mata, abinci kawai yake bata"
"Ƙarya ne rufe mini baki dan ubanki, ke kin taɓa
ganinsa yana ɗaukar yara ne, balle ba da abinci a baki, ni na ga abun da na
gani" dama 'yar ta maƙwabta ce, uwatta ta kawota ta fita.
Ta tara wa Al'amin jama'a, wai ya saka wa yarinyar hannu a
wando, da idonta abun da ta gani kenan.
Duk dakiya da dauriyar Al'amin, jikinsa ya hau rawa, ya kasa
ko motsi daga wurin, mutane suka taru a garejin gidan, Abbu dama sallar la'asar
ya fita, a masallacin yana lazumi aka je aka kirawo shi.
Cikin tashin hankali ya danƙo Al'amin, ya kwaɗa masa mari ya
ce "Me ka yi wa 'yar mutane? Al'amin lalacewar taka har ta kai ga haka? Ni
zaka zubarwa mutunci a idon duniya"
Shahida tana kuka za ta yi magana, Rahila ta hanata, wata
mata ta cire pampers ɗin yarinyar ta duba ta, ta ce "Wannan yarinyar fa
babu abun da aka yi mata, lafiyarta ƙalau da ya taɓata ma, ba za a ganta a haka
ba"
Al'amin ya ƙwace rigarsa daga hannun Abbu, ya fice, yana jin
zuciyarsa zata tarwatse, bai zarce ko ina ba, sai gidan dodo, suna ganin sa
suka din ga tambayar sa, menene saboda yadda idonsa ya yi jawur, amma ya yi
shiru ya ƙi kula kowa.
Walid ya kira dodo a waya, ya sanar masa ga mai zamani ya
zo, cikin ɓacin rai da tashin hankali.
Ba a ɗauki lokaci ba, sai gashi, ya ce "Waye ya taɓa
zuciyar magajin dodo, wa ya taɓa mini Aminullahi?"
"Al'amin ya ƙi magana sai huci da ajiyar zuciya, ga
wani gumi da yake yi"
Dodo ya ce "Walid"
"Allah ya taimaki babban sarki"
"Narka jan tablet, ka bani" Walid ya narka ya
bashi, ya miƙa wa Al'amin.
Ba tunanin komai, ya karɓa ya shanye ya ajiye kofin, wani
zuuuuu ya fara ji a kansa, ya fara ganin hazo-hazo, a hankali ya fara ganinsu
bibbiyu, daga haka bai sake sanin abun da ya faru ba, sai sha biyun dare ya
farka.
Yayi sallolinsa, ya ci abinci, dodo ya ce "Magajin
dodo, ba zan takuraka na ji menene ba, amma ya ka ke ji yanzu damuwar ta tafi
gaba ɗaya?"
Al'amin ya girgiza kai alamar a'a.
"Duk wannan dogon zangon da ka yi? Bari na baka wani haɗin"
Ya naɗa masa wiwi, ya kunna ya bashi, sai dai zuƙa ɗaya
Al'amin ya hau tari, kamar zai shiɗe ya ce "Ƙara gwadawa, ba zaka yi
ba" ya din ga zuƙa a hankali, tun yana tarin har ya daina.
Ayshercool
08081012143
A din ga yi, ana sauke hakki ₦500
0009450228
Aisha Adam jaiz bank
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Tun daga lokacin, Al'amin ya fara shaye-shaye. Shiga layinsu
ya gagare shi, saboda tsananin kunyar abun da Rahila ta yi masa na sharri.
Sai da ya shafe wata guda bai sake takawa gidan su ba, sai
dai kewar Abbu ta din ga damunsa, da asuba ya tafi masallacin da Abbu yake
salla, ya yi sallar asuba a waje, ya jira ya fito, Abbu yana tafe ya ji kamar
ana bin sa a baya, ya tsaya ya waiwaya, duk da gari bai gama yin haske ba, da
sauran duhu, amma hakan bai hana abbu gane Al'amin ba.
Ya tsaya, jiki a sanyaye ya ƙaraso, Al'amin ya risuna ya ce
"Ina kwana"
"Kai daga ina? Ina ka tafi tsawon kwanakin nan? Duk
yawonka ba ka wuce kwanaki kaɗan, amma ban sake saka ka a idona ba" kallon
Abbu yayi, yana tunanin da ma yana jin wani abu idan bai saka shi a idonsa ba?.
"Ina nan"
Abbu ya ce "Kana can kana shashanci, gaishe ni ma ba
zaka iya zuwa ka yi ba ko?"
Ya ce "Korata ka ke idan na zo"
"Ba dole in kore ka ba? Tun da kai a rayuwarka ba ka
gaya wa kanka gaskiya, kuma duk in da ka zauna sai an yi faɗa da kai. Ka yi
salla ne?" Al'amin ya jinjina kai.
"To wuce mu tafi" yayi maganar yana nuna masa
hanya, sai Al'amin yayi ajiyar zuciya, tare da tuna masa baya, da yake ɗora shi
a wuyansa idan suka dawo daga masallaci, har tsere suke yi da Abbu, duk yadda
Abbu yake ji da shi, yanzu ya zama tarihi.
Yana tuna abun da ya faru ƙarshe, sharrin da Rahila ta yi
masa, sai ransa ya ɓaci, ya ƙi shiga layin ya tsaya.
Abbu ya waiwayo ya ce "Ya ka tsaya kuma?"
"Tafiya zan yi"
"Zuwa gidan uban wa?"
Al'amin ya ce "Da wani idon zan kalli sauran mutanen
layin, bayan ga sharrin da aka yi mini, idan na ga matar nan, zan iya kasheta,
sai anjima kawai na tafi, dama ganinka nake son na yi, tun da kana lafiya Allah
ya ƙara lafiya" ya juya ya tafi, Abbu ya tsaya yana kallon Al'amin har ya ɓace
wa ganinsa.
Ko da ya koma gidan da suke, walid ya fuskanci Al'amin yana
cikin damuwa, yayi masa tayin sigari, ya girgiza masa kai, can ya ce
"Walid"
Ya amsa da "Na'am"
"Dan Allah ya aka yi ka fara Shaye-shaye?"
Walid ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Wan babana ne ya
cinye mini gado, nake ta wahala ina fama da rayuwa, matsin rayuwa ya isheni,
kuma shi ba tallafa mini yake yi ba, kawai na fara dafar kan kayan mutane, kuma
da nasa na fara, aka kama ni aka kulle, rodi ma na sata lokacin, aka ɗaure ni
watanni shida, da aka kai ni prison ban saba ba, nake ta kuka saboda wahala, a
can na haɗu da mai gida, sarki dodo, ya din ga kula da ni, bayan ya fita ya
dawo ya biya mini tarar aka yanke mini, sake ni, kawai ya cigaba da kula da
ni"
"Ina mamanka?"
Walid ya ce "Taɓ tana can tana fama da rayuwarta, kinko
ya kanannaɗe rayuwarta, wannan tsohon auran wan baban namu, ya tattare gadonmu
ya cinye, Sakandire kawai nayi, ita ma ba ganewa nake yi ba da kyar na kai.
Tana fama da kula da ƙannena, ga bata da cikakkiyar lafiya, ni kuma bana iya
tallafa mata, har gara yanzu mai gida ya kan bani kuɗi ya ce na je na gaishe
ta"
Al'amin ya jinjina kai ya ce "Ka cigaba da kula da ita,
dan duk ranar da ka rasata, za ka yi kuka, kuma kar ka bari ta san irin rayuwar
da ka ke yi"
"Na nawa kuma, ai wancan tsohon munafukin tuni ya gaya
mata, tana yi mini nasiha sosai da addu'a, ba ta taɓa fushi da ni ba"
Daga haka Al'amin yayi shiru, yana cigaba da tunani.
Da sannu Al'amin ya zama gawurtaccen mashayi, duk in da dodo
za shi, da Al'amin. Ta kai ta kawo har kudancin Najeriya yake tafiya da
Al'amin, ba fatauci ba, har wuraren sarrafa miyagun ƙwayoyi Al'amin ya sani,
har manyan mutane a ƙasar nan da suke ta'amalli da su da kasuwancin su ya sani.
Ya haɗa Al'amin da wani inyamuri, ya ƙara gogar da shi a kan
harkar na'ura mai ƙwaƙwalwa, yadda ake amfani da ita a aikata laifuka
daban-daban, suka sake danganawa da wani bature, ya ƙara koyar da Al'amin
sarrafa computer wurin yin laifuka.
Ya zamana kasuwancin miyagun ƙwayoyi, na ƙasashen da suke
maƙwabtaka da Nigeria, Al'amin ke tafiyar da kasuwancin su ta online.
Bai tsaya a nan ba, har cikin manyan 'yan fashi, dodo yake
shiga da Al'amin.
Dodo ba ya fashi da makami, amma zama a gidajen gyaran hali
daban-daban ya sanya ya san masu laifuka kala-kala da yadda ake aikata su, bai
fiye harkar daba ba, yafi gane wa safarar ƙwayoyi da makamai.
Idan aka cewa Al'amin magajin dodo, sai dodo ya ce
"Wannan dodon, da sauran imani a ransa, ɗan ƙaramin dodo ne, ba zai iya
zama kamar ni ba, sonake ya horu, yadda zai iya tunkarar kowane ƙalubale, ciki
har da babban burinsa na son ganin bayan madaki, dan kuwa madakin ma ya ƙwafe
shi a rai, na cewar sai ya ga bayansa, tun da na saka ya sanya gwiwar sa a ƙasa
wurin bashi haƙuri".
Duk wani sirri na dodo, babu wanda Al'amin bai sani ba,
kallon abu dodo yayi Al'amin ya san me yake nufi.
Kai tsaye ya kan tura Al'amin wurin indabo, a lokacin yana
fafutukar neman kujerar ɗan majalisa, sai dai wasu lokutan baya son dodo ya
aika masa Al'amin, dan idan yayi masa abun da bai yi masa ba, tafiyar sa yake
ya ƙyale shi, ba ya jure cin zarafi ko wulaƙanci, komai ƙanƙantarsa, ya yaɓawa
indabo baƙar magana ya ƙara gaba, duk ba abu ne mai wahala a wurin Al'amin ba,
Indabo ya kai wa dodo ƙarar Al'amin.
Amma ya ce "Ina nema masa afuwa, ka riƙe Al'amin yaro
ne mai amana, kuma duk cikin yarana babu wanda zai iya yi maka aikin da ka ke
so bayan shi, yaro ne mai amana sosai da sosai, kuma ba shi da surutu,
hakazalika yayi hannun riga da tsoro.
Dodo ne ya nuna masa makamai kala-kala samfurin wuƙaƙe, da
in da in ka sakawa mutum zaka kashe shi, da wanda za ka yi masa illa.
Dodo yana yawan faɗar, Son da yake yi wa Al'amin daga Allah
ne, bai taɓa son abu sosai da yake jin sa a ransa kamar shi ba. Ya san son da
yake yi masa, ba zai kai na ɗa da uba ba, dan haka ya din ga mamakin yadda aka
yi, mahaifin Al'amin ya wofantar da shi, duk da soyayya irin ta ɗa da uba.
Ba yadda bai yi da Al'amin ya ɗora karatu ba ya ƙi.
Ya ce "Aminullahi, harakar daba da shaye-shaye ba abune
da nake yi maka fatan ka ɗore a kai ba, yakamata ka koma makaranta.
Al'amin ya ce "Ni ma ba na fatan na ɗore, ina ɗaukar
fansar abun da madaki yayi mini zan bar daba".
Ya dafa kafaɗarsa ya ce "Ina maka fatan hakan, sai dai
haryanzu ba ka kai ƙarfin da zaka tunkari yaron nan ba, dan kuwa shi har da
tsafi yake yi, kai kuma na san komai za a yi maka, ba zaka yi tsafi ba, amma ba
a shiga dawa dan ƙarya, ko na kare kai, zan nema maka".
Duk da an ɗauki lokaci, yaran madaki ba su shiga unguwar su
Al'amin ba, sai rana tsaka, suka shigo unguwar neman faɗa, a karon farko
Al'amin ya ɗauki makami, jikinsa na wata irin tsuma, zuciyarsa na tafasa, wanda
hakan ya faru ne a sakamakon abubuwan da yake ta'amalli da su.
Dan shaye-shaye nasa, kala-kala ne, kowanne akwai lokacin
amfaninsa. Idan wani aiki yake son yi, ba ya son gajiya da wuri, sai ya banki
wiwi sai ya daɗe yana abun da yake so, ba tare da ya gaji ba. Idan kuwa rashin
mutunci yake son yi, haka zai yi mata haɗe-haɗe na mussaman, haka ma idan so
yake ya bugu. Bai fiye ta'amalli da ƙwaya sosai ba, ya fi ƙarfi ga wiwin.
Ya je ya samu yaran, kan mai uwa da wabi, yayi musu ɓarna,
sannan ya taka har dabar madakin, ya yi masa warning, "Ka gargaɗai
karnukanka, a kan shigar mini area su nemi faɗa, idan ba haka ba, kan babban
karen zan zo, na yi masa takunkumi, yadda haushi ma sai ya gagare shi"
Madaki tun da dodo ya sanya ya bawa Al'amin haƙuri, ba su
sake arangama ba, kusan shekara biyu, sai a wannan lokacin, sai da gabansa ya
faɗi, saboda yadda kamannin Al'amin suka juye, ƙarara alamun shaye-shaye suka
bayyana a tare da shi, yadda ya sake zuwar masa kai tsaye ba tsoro ko fargaba,
ya sanya shi gane kuskuren da ya yi na barin Al'amin a raye.
Tun da Al'amin yake tare da dodo, bai taɓa rashin kuɗi ba,
kuɗi yake kamawa manya da ƙanana, kuma bai taɓa ci wa dodo amana ba.
Har a cikin ma'aikata, ana samun ɓata gari waɗanda suke
sayar wa dodo kayan maye, idan sun kama, duk wani salo na yadda ake sayar da
kayan, ba tare da an gane ba, Al'amin ya goge, haka idan kana ta'amalli da su,
kallo ɗaya zai yi maka ya gane.
Yan kwamutin unguwa, suka kai ƙarar Al'amin wurin hukuma, a
kan yana tayar musu da tarzoma, ba tare da la'akari da yaran da suke rashin jin
tun kafin ya fara ba.
Dodo ya je ya samu shugaban 'yan vigilant, ya ce masa
"Wallahi duk wanda ya sake ɗaukar ƙafa, ya kai ƙarar Aminullahi sai ya ci
ubansa, lokacin da aka kashe ɗan uwansa ku nawa ku ka tashi ku ka je wurin
jami'an tsaro domin ganin an ƙwatarwa yaron hakkinsa, saboda ba yaranku aka
kashe ba. Lokacin da yake ragaita ba shi da sana'a, mutum nawa ne suka mayar da
shi makaranta? Ko suka bashi sana'a, dan mahaifinsa ya wofantar da shi, kuna
'yan unguwa ba ku ga dacewar ku nusar da shi kuskuren sa ba? Ai duk society da
suka yi watsi da yaran su irin su Aminullahi muna nan muna jiran su, mu zamu
karɓe su, mu mayar da su abun da ya dace. Gargaɗi nake yi, ni dai an san ba zan
kamu ba, to haka Al'amin ma, ko bayan raina, ina da masu fito mini da shi idan
ya shiga cakwakiya. Ku shirya Al'amin bai fara yi muku rashin ji ba
tukuna"
Ƴan unguwa suka rasa abun yi, yaransu da suke ƙanan rashin
ji, suka fara bin Al'amin, yana ba su kayan wiwi suna sayarwa, yana ba su kuɗi,
dama gashi da kyauta kuma ba shi da baƙin ciki.
Duk yaran dodo, suna shakkar Al'amin, ko dan saboda masifar
dodo idan aka taɓa shi, dama Al'amin ya fi yin faɗa da Walid, dodo ya kan ce
masa Mai laya, ka kiyayi mai zamanin nan, idan ka ƙure shi, ba zan saka baki
ba, idan ya tashi yi maka ɓarna ba. Su yi faɗa su yi daɗi.
Tafiyar gaggawa ta kama dodo, zuwa kudancin Najeriya, sai
dai ya ce wa Al'amin ya zauna, ya kula masa da harƙallarsa ta kano, ba zai tafi
da shi ba.
Abun da Al'amin bai taɓa yi ba, sai a wannan karon ya ce
"Meyasa ba zaka tafi da ni ba?"
"Aminullahi, tafiya ce mai hatsari, ka kula mana da
harƙallarmu, sannan kar ka manta rules ɗin, a tafiyarmu babu BODMAS, idan ka ji
wuta, ka wargaza komai ka ɓace"
Al'amin ya jinjina kai ya ce "Allah ya taimaki sarki
babban dodo"
"Na gode, Allah ya ja zamaninka, zuwa in da ba ka zata
ba, a cigaba da riƙe amana Aminullahi" haka nan Al'amin ya ji baya son
dodo ya tafi.
Kwana uku da tafiyar Dodo, suna zazzaune, suna shan sigari,
aka jefo wata jaka ta katanga.
Walid ya ɗaukko jakar, wasu daga cikin yaran wurin, suka
fita da gudun tsiya, suna neman wanda ya jefo jakar, ba su ga wanda ya jefo ba.
Al'amin ya ja jakar ya buɗe, kawai yayi tozali da kayan dodo
a ciki, face-face da jini, har da takalminsa.
Cikin ƙaraji Al'amin ya ce "Nooooo" ya tashi
jikinsa yana tsuma ya girgiza kai ya ce "Impossible, ba zai yiwu ba, sarki
yana raye, raina mana hankali kawai ake yi"
Walid ya riƙe Al'amin ya ce "Al'amin ka nutsu mana,
musulmai ne mu, idan ba a kashe sarki ba, babu yadda za ayi a ciro kayans
jina-jina a kawo mana".
Al'amin ya fara neman ya fita hayyacinsa, Walid suka danne
shi, suka shaƙa masa wani abu, jikinsa ya saki ya hau bacci.
Al'amin ya razana, ya shiga tashin hankali, ya ɗimauce sosai
da sosai, da mutuwar dodo, ba zai manta gudunmuwar da ya bashi ba, duk da ba ta
arziki ba ce ba, Al'amin kamar zai zare.
Duk wata hanya da zai bi ya gano wanda ya kashe dodo, ya
rasa, damuwa ta ƙara yi masa yawa.
Ya ɗaukko makaman da ya saka aka ƙera masa, sweazland,
Russia da kuma iraƙi, ya zuba musu ido, bai taɓa zaton ya shaƙu da shi haka ba.
Mussman madaki ya zo ya sami Al'amin, yana ƙyaƙyata masa
dariya, wai garkuwar da fake a bayanta, an samu wani gwanin saitin ya rusata,
yanzu zai koma Al'amin ɗin sa matsoraci na ainihi.
Sai dai cikin sa'a, Al'amin yana tare da sweazland, dan haka
madaki ya fara yi wa rauni da ita ya ce "Dan an fasa garkuwata, ba ya
nufin zaka cim mini, *Ƙarfen cikin wuta nake* na fi ƙarfin ɗauka da
hannu, ko da mariƙin roba, daga yau ka rubuta ka ajiye, ɗaya ya riski ajalinsa
ne kawai zai kawo ƙarshen gabata da kai".
Madaki ya kalli cinyarsa da ke jini ya ce "Meyasa ba ka
kawo ƙarshen gabar yanzu ba, ka kashe ni?"
"Saboda na fika sanin waye kai, akwai lokacin da ya
dace da hakan".
Yaran dodo, sun so Al'amin ya gaji harƙallar dodo, ba ita ba
har manyan hada-hadarsa da manyan mutane. Amma Al'amin yaƙi, ya ce baya buƙatar
duk wani abu da zai din ga tuna masa da dodo, kuma zai yi abun da zai Allah zai
gafarta masa, ba ɗorar da laifukansa a bayan ƙasa ba.
Da yawa sun so su ya basu sirrikan dodo, su cigaba da
sana'arsa, amma Al'amin ya ƙi, ƙarshe ma suka bar wannan gidan gaba ɗaya, ya je
ya kafa masa sansanin.
Walid suna zuwa da Al'amin duba mahaifiyarsa, da ciwon
Cancer ya kama, aka kwantar da ita a asibiti, kullum cikin neman jini ake, duk
wani kuɗi na Al'amin, sai da ya ƙare a wurin kula da mahaifiyar Walid.
Liti dama shi isaknci ne da abokai, suka saka ya lalace, dan
har waje babansa ya kai shi yin karatu, bai koyo komai ba sai shashanci ya
dawo.
Kasancewar jinin Al'amin da na babar Walid iri ɗaya ne, ya
bayar da jininsa sosai an saka mata, kullum cikin Kwantar wa da Walid hankali
yake, tare da bashi tabbacin zata warke.
Har zariya suke kaita Asibiti gashi, amma cikin ikon Allah
ta koma ga Allah, abun nan da Al'amin ya yi wa walid, ya sanya ya sanya duk
abun da zai yi masa baya fushi da shi, ko yayi sai ya huce.
Suka koma ƙaramar harƙallar sayar da wiwi, idan kuma aikin
ƙarfi ya samu su yi.
Al'amin ya numfasa sannan ya ce "Ban kuma taɓa kashe
kowa ba, duk rashin ji na, wanda ki ka ganni da shi, liti ne, yaran madaki suka
soka masa wuƙa, kar ki sake cewa na yi kisan kai".
Jauhar wani irin kuka take man ban tausayi, rayuwar Al'amin
akwai tarin ƙalubale, sai ta ga ita tata rayuwar nafila ce.
"Ki yi haƙuri, da yawan furta miki zan sake ki da nake
yi, baki cancanci mutum mai tarin laifuka irina ba, wallahi ba zan iya yafewa
madaki ba, da shi da wanda suka kashe dodo. Ban yi miki alƙawarin daina abun da
nake nan kusa ba, binciken da na ƙara yi akan ki, na fuskanci kusan ƙalubale ɗaya
muka fuskanta, dan na san duk wani abun alkhairi wannan shegiyar matar ba zata
bari ya raɓe ni ba, dan haka na yi zaton ta shirya mini wata maƙarƙashiyar ne,
dan haka ta aura mini ke, ashe wai wani mai kuɗi zaki aura, suka hana ita da
wannan banzar matar ta gidanku, ban manta lokacin da take zuwa gidanmu ba ita
ma. Haryanzu a shirye nake, mu rabu ki auri mutumin kirki, baki dace da ni da
rayuwata ba, rayuwata ta riga ta gurɓace, kullum kina cikin tashin hankali bai
kamata ba, duk a sanadina. Dama kin ga ke kalar matan masu kuɗi ce, in da zaki
huta a kula da ke sosai. Ni kuma na gurgura na ƙarasa rayuwata"
Jikinta na rawa, ta toshe masa baki, ta kalleshi, hawaye
wani na bin wani a fuskarta, amma ta kasa magana ta cigaba da sheshsheƙar kuka
iya ƙarfin ta.
Ya sauke hannunta daga bakinsa ya ce "Lafiya kuwa?
Wannan kukan fa?"
"Zan zauna da kai a haka, na san wataran zaka daina, a
lokacin da raɗaɗin kaɗaici da damuwar da ka ke ciki suka barka, a lokacin da ka
fahimci wani zaluncin idan an yi maka wata shari'ar sai a lahira, ba zaka iya ɗaukar
wa kanka mtaki ba. Zan zauna da kai har zuwa lokacin da komai zai zama tarihi.
Ni ba zama da mai kuɗi ne damuwata ba, kwanciyar hankali nake so, in da za a ga
mutuncina a kula da ni, dama miji nagari nake fata ba mai kuɗi ba".
Ya lumshe idonsa ya buɗe ya ce "To ni na garin
ne?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
Murmushi ya yi ya ce "Tashi ki je ki kwanta, ɗaya da
rabi yanzu. Ba zan manta ƙoƙarin ki a kaina ba, kina cikin mutane ma su
muhimmanci da ba zan manta da su ba" da ta kalleshi, sai ta cigaba da
zubar da hawaye, wani irin tausayin sa na ratsa zuciyar ta.
Ya gyara pillow zai kwanta, ya kalli yadda take ta kuka, ya
ce "Har mamki ki ke bani, yadda ki ke taƙarƙarewa ki yi ta kuka, ni fa da
wayona, zan iya ƙirga sau nawa na yi kuka". Yayi maganar yana kwanciya
amma ta cigaba da zama a wurin.
"Idan ki ka bari na rufe ki a ɗakin nan, akwai
ƙura" ta kalle shi ya ce "Ban taɓa ɗaga sweazland na fito da harshe,
ba ta sha jini ba, sai a wannan karon da ki ka hana ni, ko ki tafi ko in sha
naki jinin in huce".
Wato shi gaba ɗaya labarin da ya bata ma, ko a jikinsa.
Sai da ta gama koke-kokenta, sannan ta tashi ta fita daga ɗakin.
Ba ta kwanta da wuri ba, ta daɗe tana salloli, da karatun
Alqur'ani, a kan Allah ya shirya Al'amin, ya sanya tarayyar ta da shi, ta zama
sanadin shiriyarsa.
Sai da tayi sallar asuba, sannan ta kwanta, dan haka wani
irin nannauyan bacci ya ɗauke ta.
Sama-sama ta ji muryar Al'amin, yana faɗa da boti, ya zo
tashinta yana jin yunwa, ya ga boti ya lafe a jikinta, shi ma yana tashi.
Ya danƙo shi ya jefa ƙasa ya ce "Ware ka bar nan wurin
dan ubanka"
Boti ya tsaya, yana kallon Al'amin yana kuka.
Al'amin ya mayar da idonsa kanta, bacci take sosai, shi kuma
yunwa ta ishe shi, dan yayi shaye-shaye.
Dukan katifar gadon yake yi a hankali, ta motsa kaɗan ta
cigaba da bacci.
Yaye bargon yayi gaba ɗaya, daga ita sai vest da gajeren
wando, a razane ta tashi zaune tana kare jikinta.
Ya riƙe bargon ya ce "Ki na ji na ki ka yi mini shiru?
Ina son na karya na sha magani, kin ɗauki wancan abun kin kwanta kina bacci da
shi".
Cikin muryar bacci, mai haɗe da tsoro, ta ce "Na ji,
amma ka bani bargon zan fito yanzu".
Ya ce "In tafi ki cigaba da baccin, tashi mu je"
To ka je ka jira ni, zan saka kaya.
Taɓe baki ya yi ya ce "Da kin kwantar da hankalinki, ba
na jin komai, ba abun da zan yi miki" ya miƙe yana ajiye mata bargon ta,
ya danƙo kan boti ya yi waje da shi.
A jejjere ta din ga ajiyar zuciya, tana maimaita maganarsa
shi ba ya jin komai.
Da ta fito kasa haɗa ido tayi da shi, ya kwanta ruf da ciki
saboda raunin bayansa, yana jiran abinci.
Bayan ya karya, ta ce "To wanka fa?"
"Ba yanzu ba, gasa mini ciwon nan kai"
Ta haɗo ruwan ɗumi, ta gasa masa, ciwon, tana yi yana raki,
saboda yadda ya ga tana damuwa sosai, wai da zafi.
Wayarsa ta fara ringing, ta hana shi ɗagawa, har ta katse,
ta sake fara ringing, ta ɗaga ta ce "Assalamu alaikum, ba shi da lafiya
bacci yake"
"Ya jikin nasa?"
Ta ce "Da sauƙi"
"Masha Allah, ke ce matar ta sa? Al'amin ya karɓe wayar
ya kasheta gaba ɗaya ya kalleta ya ce "Meyasa ki ka tsaya kina magana da
wani?"
"Na zata su yaya walid ne, yi haƙuri, amma yakamata ka
kira shi ka ji, ko an sako shi"
Al'amin ya haɗe ce "Wai ke kowa ma damuwa ki ke da shi
ne?"
"To ai gani nayi saboda mu ya shiga matsala, aka kama
shi"
"To ba ruwanki, da ni kawai zaki din ga damuwa" ta
kwashe da dariya ta ce "To shugaba, in sha Allah. Juya in shafa maka man
zafin a wurin" ya juya tana shafa masa a hankali, dan kar ya ji zafi.
Wayarta ce ta fara ringing, ta ɗauka ta duba
Ta ga lambar mama ce, ta ɗaga suka gaisa, ta ce
"Yauwwa, dama kiranki na yi, ana ta shirin bikin hafsa, tun saura sati ɗaya
biki yakamata ki dawo gida, akwai aikace-aikace da za ayi, saboda bikin.
Ta ce "To shikenan mama, Allah ya kaimu lafiya"
"Amin" ta kaste wayar.
"Ba in da zaki" ya faɗa dai-dai lokacin da ta
ajiye wayar.
"Master meyasa, bikin Yaya hafsa ne fa"
"Ko bikin wacece, ba zaki ba? Idan akwai mai neman
dalili, sai a tuntuɓe ni".
Jauhar ta ce "Master za su ga kamar wulaƙanci ne, ko
baƙin ciki, ko ba zan yi satin ba, dan Allah ka bari na je bikin"
Ya girgiza kai ya ce "No, bayan bikin kya je
gidanta".
Jauhar ta marairaice za ta yi masa magiya ya buga mata tsawa
ya ce "Ina magana kina mayar mini, ba zaki je ba na ce" a razane ta
ja da baya, ta sunkuyar da kai ta yi shiru, ya tashi ya bar mata falon.
Yana ƙwafe da wayar da suka yi, aka ce ba zata iya sayen
anko ba, yanzu kuma an ce ta zo ayi aiki, saboda baiwar su ce ita, ita kuma
gaba ɗaya hakan bai dameta ba, wasu lokutan kamar ba ta da zuciya sam.
Tun da Indabo ya ajiye wayar, yake jujjuyata yana jin yadda
muryar jauhar, ke kai komo a cikin kwanyarsa, kana jin muryar ka san ta yarinya
ce, haka kurum ya ji ya kwaɗaitu da son ganinta.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available
ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya
kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah
xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da
rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955 da
Indabo ya cigaba da jujjuya wayar yana kallonta.
Sosai jauhar ta ji babu daɗi, hanata zuwa bikin da Al'amin
yayi, ba ta san dalilin sa na yin hakan ba, kuma bai gaya mata ba, ba ta san me
za ta ce wa su mama ba, su yarda da ita.
Kuma yayi fuska, ya hau hura hanci yana wani basar da ita,
dan ma kar ta ce zata yi fushi da maganar hanata zuwa bikin da yayi, shiyasa
yayi sauri ya rigata fara fushin.
Haka ta wuni, idan ta tuna abun sai ta ji ba daɗi, da duk in
da za ta je, ba ruwansa, amma yau bikin 'yar uwatta, ya ce ba zata je ba,
Al'amin kenan.
Sai dai tayi iya ƙoƙarinta, ta danne fushinta, ba ta canza
masa ba, amma yanayinta kallo ɗaya yayi mata ya gane, a cikin damuwa take, kuma
ya san hakan yana da nasaba da hanata zuwa biki da yayi.
Can gidansu amarya hafsa, ana ta rawar kai, an sha gyaran
jiki, magungunan mata kuwa ba a magana, fatar nan ta ƙara ɗashewa, tayi fara
ƙal kamar aljana.
Sai hura hanci ake yi, za a auri mai kuɗi, mama kuma sai yi
musu lumbu-lumbu, kamar tana tare da su a komai.
Suka din ga karɓar kuɗi a wurin Alhaji mu'azzam kamar ba
gobe. Shi kuma duk abun da suka nema, haka zai ba su.
Zakiyya ta saka hafsa ta tambaye shi, wai a ina za su je
honeymoon. Murmushi ya yi da ta tambaye shi ya ce "Hafsa yawon ƙasashen
duniya har sai kin gaji, dai ƙasar da ki ke so zamu je" hakan ya ƙara fasa
mata kai, ta din ga jin cewa ta gama dacewa.
Al'amin ciwonsa ya fara warkewa, kasancewar ba shi da ƙan
jiki, ga kulawa da Jauhar take yi da shi sosai da shan magani.
Ta ɗaura aniyar, fara ɗora Al'amin a turbar tafiya masallaci
kuma, ya din ga salla a cikin jama'a, kamar yadda Annabi Sallallahu alaihi
Wasallam, ya kwaɗaitar da al'ummarsa, mussaman da ciwonsa ya kame, dan ya fara
saka riga ya fita ma.
Sai dai fa aikin ba na wasa bane ba, dan wasu lokutan idan
ta tashe shi sallar, har a idar tana fama da shi bai tashi ba, mussman idan a
cake yake, idan ta yi alwala kuwa ta zo tashinsa, ƙarshe sai ta ta alwalar ta
karye, shi kuma bai yi ba.
Sai dai ta tsananta addu'a da gaya wa Allah. "Ya Allah
ga bawanka Al'amin, kai ka halicce shi, ka shirya wanda suka aikata laifuka
fiye da nasa, Ubangiji Allah ka shirya mini shi. Allah ka sa ya shiryu a
sanadin zamana da shi, Allah kar ka saka na ƙosa ko na gaji, Allah ka dubi
niyyata ta son zama da shi da yin biyayyar aure kamar yadda ka umarta, Allah
dan kunfayanunka ka shiryi wannan bawa naka"
Duk in da jauhar ta ji Addu'ar biyan buƙata, irin su salatul
haja, salla raka'a biyu, fatiha da sura, idan ta idar ta mayar da goshinta
ƙasa, ta karanta la'ila ha illa ant subhanaka inni kunt mina zalimin. Ƙafa
arba'in da ɗaya, ba ta ɗagowa sai ta gaya wa Allah buƙatunta.
Salatul tasbih, da sauran tasbihai haka take yi, tana yi wa
Allah magiya da yin tawassuli da su, ta roƙi Allah ya shirya mata mijinta, ya
haɗa kan su su zauna lafiya.
Yau ta samu yayi sallar asuba ƙarfe shida saura da ƙyar, ta
dawo dan ta saka shi yayi azkar, ta tarar har ya kunna sigari daga idar da
sallar.
Bai yi tsammanin za ta dawo ɗakin ba, kawai ya ji sallamarta
ta shigo. Kamar yadda tayi tsammani, bai daina sha ba, kuma ya tsuke fuska.
Ta ƙarasa gabansa ta zauna, ta zuba masa ido.
"Kin san an hanaki shaƙar hayaƙi ko? Kin san ba
cikakkiyar lafiya ce da ke ba"
"Kai ma bai dace da kai ba, ina gaya maka ina son
lafiyarka, su kan su masu kamfanin abar sun yi gargaɗi a kan haka, dan Allah ka
ajiye magana zamu yi".
Bai ajiye ba, yayi mata shiru yana cigaba da fesar da
hayaƙin wani wurin daban.
Tashi tayi ta zagaya, in da yake fesar da hayaƙin tana
kallonsa.
"Meye haka ne wai?"
"Dan Allah ka ajiye mu yi magana"
"Ina jinki ai" wani abu mai ɗaci ta haɗiye, kawai
ta tashi ta bar masa ɗakin.
Ta koma ɗakinta ta tsaya, kuka ya ƙwace mata, sai ta fara
saito abubuwa, sai Al'amin ya sake burkice mata, tun da suka yi aure take yi
masa addu'a, amma abun nasa sai a hankali.
"Kul jauhar, kar ki yi saɓo, ko ki yi wa Allah butulci,
Allah sami'ul alim ne, idan ka roƙa baka ga tasirin abun ba, lokacin ne bai yi
ba, tun da shi ya ce mu roƙa zai amsa, kuma Allah ba ya sabon aiki' wata
zuciyar ta gargaɗe ta.
Istigfari ta cigaba da yi, ta nemi wuri ta zauna a tsakiyar
gadonta, tana cigaba da tasbihi.
Sai da gari yayi haske sosai, ta fita tana aiki, ya fito
cikin takun ƙasaita, ya nemi wuri ya kame a kan kujera.
Sai da ta kai zuciyarta, sanna ta iya ce masa "Ina
kwana?"
"Lafiya ƙalau" a ranta ta ce 'Ka yi laifi, kuma ka
maze kana hura mini hanci, da ni ka ke zancen'.
Ta ajiye masa karin kumallonsa, ta koma ɗakinsa, ta na
gyarawa, yanzu ya rage watso mata kaya daga wardrobe, sai dai ya tara mata
kayan wanki, a kan katifarsa.
Tsayawa yayi a bakin ƙofa, yana kallonta.
Yayi gyaran murya ya ce "Kin ce zamu yi magana, ta
menene?"
Ta kalleshi ta ce "Ka manta kawai" ta ƙarasa
maganar tana kwaso kayan wankin za ta fita.
Har ta gota shi, ya janyo ta kamar wata 'yar tsana, ya tsuke
fuska ya ce "Gaya mini menene?"
Ta sunkuyar da kanta, hawaye ya fara zubowa daga idonta,
wani na bin wani.
"Menene kuma yanzu?"
Cikin rauni ta ce "Kai ne"
"Na yi me?"
"Kusan kullum sai ka sakani kuka mussaman kwanan nan,
na ce dan Allah ka daina shan komai ka ƙi dainawa, haba master wane irin uba ka
ke son ka zama idan Allah ya bamu zuriya? Ina son in ga ka daina shan komai ka
daina abun da ka ke yi. Amma ƙir-ƙiri ɗazu ka ƙi daina sha".
Ya ce "Ke, wai an gaya miki daina shaye-shaye kamar
daina cin tuwo ne? Ina ƙoƙartawa fa, duk kin addaba mini, ina ji ina gani,
asuba ina shan kara biyar zuwa sama, amma ɗazu uku kawai na sha amma ba kya
gani, kuma yaushe na ganki, balle a tara wata zuriya? Shiyasa ma ban bari sun
ƙaraso ba tukuna sai na gama abun da nake yi. yayi maganar yana basarwa.
Wata irin kunya ta kama ta, jin abun da ya mayar da maganar.
"Ki daina damuwa, ina ƙoƙari sosai, ba zan iya dainawa
ba, sai na cika burina, mutum ɗaya kawai zan kashe, shikenan"
Jauhar ta kalleshi ta ce "Kisa kuma? Ana ga ƙura kana
ga yaƙi, idan an yi nan sai ka yi can"
Dogon harshensa ya zaro mata, yayi wani irin murmushi, sai
ta ga kamar ya canza gaba ɗaya, ya dafo kafaɗarta kamar ƙawarsa ya ce "Bar
wankin, zan yi ki haɗo da naki ma, idan na gama zan yi gyaran kwatar layin nan,
duk an bari ta cushe da shara, me zaki dafa mana da rana?"
"Master ba ka da aiki sai zancen abinci ne?"
"To idan ban yi zancen abinci ba zancenki zan yi babyn
roba"
"Saura ta katako, rana zata yi mini, ko wankin ka saɓa
sai na yi mana ɗauraya"
Al'amin ya ce "A'a ki yi aikin ki zan wanke" yayi
maganar yana yi mata wani irin kallo tare da murmushi.
Ita ma murmushin ta yi masa ta ce "Harshenka dogo ne,
meyasa ka ke fito da harshe ne?"
Ya ce "Rantsuwa ce, kowane specie ɗinmu, akwai irin ta
su".
Jauhar ta yi dariya ta ce "Wai specie kamar a
biology?"
"To in ce kowane ɗan daba?"
Ta yi saurin girgiza kai ta ce "A'a ba na son wannan
kalmar, babu daɗin ji"
Ba tare da ta gane ba, yayi mata wayo, ta daina fushin da
take yi, dan babban burinta ya kula ta, ya sakar mata fuska.
Aka shiga satin bikin Hafsa, Anty Zakiyya ta kira Jauhar ta
ce "Jauhar wai yaushe zaki zo ne? Ayyuka sun kacame, ko dai baƙin ciki ki
ke yi da lamarin nan ne?"
Jauhar ta ce "Haba Anty, ba haka bane wallahi. Kin ga
maigidan ne ba ya jin daɗi, idan na taho babu mai kula da shi".
"Kamar yaya? Au mijinki ya fi 'yar uwakki, kamar wani
mijin kirki, da waye yake kula da shi idan ba shi da lafiyar?"
"A'a Anty, ai miji duk in da yake miji ne, yana buƙatar
kulawa ne, ba dan....
"Dalla yi mini shiru, har wani tinƙaho ki ke yi da
wannan abun? Makakken ɗan wiwi.
Ba tare da Anty ta sani ba, tuni ya karɓi wayar daga hannun
jauhar, ya saka a kunnensa tana ta masifa "To ki zauna sai yadda yayi da
ke, ai mutumin kirki mai kuɗi shi yake saka doka a bi, ba irin mijinki ba da
har ki ke gaya mini wai ai miji miji ne ba".
"Makakken ɗan wiwi yana godiya, kuma kun san da
makakken ne, ku ka aura mata ni. Ni na hanata zuwa matata ba baiwa ba ce, ta zo
ta yi muku bauta, ba zata zo ba, idan kun ga dama ku bar bikin kar ku yi"
Jauhar tana girgiza masa kai, amma sai da ya gama maganar ya jefar da wayar.
"Master, iyayena fa, ba a haka yakamata a gaya musu ba,
da ka bi a hankali, na san yadda zan gaya musu".
Al'amin ya ce "Kin san bani da tarbiyya, ban iya magana
da manya ba"
"A'a ba haka nake nufi ba"
"Idan ma dai hakan ki ke nufi, idan kuma ban isa ba, ki
shirya ki tafi "
Jauhar ta ce "A'a ka ma isa, ai na fasa zuwan, amma ai
ka yi mini alƙawarin zaka kai ni gidanta bayan bikin ko?" Tausayinta ne ya
kama shi, ba dan haka ba da gidan hafsan ma ba zai bari ta je ba, amma ya tuna ɗan
uwa duk in da yake daɗi ne da shi, kuma bai kamata ya hanata zuwa wurin 'yar
uwatta ba, amma kamar ko a jikinsa ya ce "Zan yi shawara"
Anty Zakiyya kuwa, sai da kayan cikinta suka yanutsa, saboda
tashin hankali da ta ji muryar Al'amin a waya.
Sai dai jauhar ta sha zagi a gidan, ana cewa baƙin ciki ne
da hassada ya sanya ba zata zo ba.
Yaya saifu ya ce 'm"Jauhara ba ta da irin wannan
zuciyar, hankalinta na kan mijinta, wannan aure dai, in dai dan cin amana aka
yi shi, ba in da zai je zai watse".
A fusace Anty ta ce wa mama "Ki ja wa ɗanki kunne, kar
ya sake aibata mini auren 'ya"
An kai kwanaki huɗu ana events kala-kala na auren Hafsa,
jauhar sai kallo da ta din ga yi, tana murmushi tare da jin babu daɗi rashin
halartar auren yayarta, ga 'yan uwa da abokan arziki duk an taru.
Ita ma ta ɗora hotunan, tana yi wa hafsan fatan alkhairi.
Aka gama biki, aka kai hafsa gidanta, wanda suke haɗe da
uwar gidansa, kowacce part ɗin ta daban.
Aka yi sayen baki aka watse, ya tara su yayi musu nasiha,
bayan Uwargidan ta fita, Alhaji mu'azzam ya ce "Bari na je na ɗan ƙara
rarrashinta, na san tana cikin damuwa" haushi ya kama hafsa, dan a zatonta
yana zumuɗinta, ba zai saurari uwar gidan ba.
Sai dai har ɗaya na dare bai dawo ba, ta kira wayarsa a
kashe, tun tana saka ran ya dawo, har ta gaji, bacci yayi awon gaba da ita.
Da safe ma, ga yunwa ga gajiya, amma ba ta ganshi ba, sai
sha ɗaya na safe.
Ya ce "Jauhar am sorry please" ta kalle shi cikin
takaici ta ce "Jauhar kuma?"
"Afuwan Hafsat, wallahi madam ce nayi ta faman
rarrashinta, taƙi yin shiru kin san kishi babu daɗi, shiyasa na zauna da safen
nan ma da ƙyar na fito, duk a cikin damuwa ta ke, yanzu haka kanta ciwo yake
saboda kuka, ina ga da kaina zan fita nema mata magani"
Tamkar hafsa ta zabga masa mari haka ta kalleshi ta ce
"Ni bana buƙatar kulawarka kenan sai ita?"
Ya ce "No ba haka bane ba? Ai ke sabuwa ce, sai ta fiki
shiga damuwa, bari na je na sayo mata maganin na kai mata, na yi ordern abinci,
idan ban dawo da wuri ba ki karya kawai.
Abu kamar wasa, har wurin kwanaki uku, bai saurari hafsa ba,
wai uwargidansa ba ta da lafiya, har ma ya ɗauki fushi da ita, wai ba ta je ta
yi mata sannu ba, ta ɗauki waya tana kuka ta sanar da Anty, Hankalin Anty ya
tashi, ta ce ta je ta dubata ɗin, za su sake shiri su ma.
Baya nan hafsa ta shiga duba ta, ta ce "Na ji an
ce baki da lafiya, na zo duba ki"
Ta ce "Ko ɗaya, lafiyata ras, kawai ina ƙoƙarin nuna
miki ƙarfin ikon da nake da shi a cikin gidana da irin gangancin da ki ka
aikata na shigo mini gida"
Hafsa ta ce "Shigowar ai ita ce mai wuyar, tun da an ce
hanawa ki ke yi, ni kuma na yi nasara na shigo, mu zuba da ni dake".
"Lallai yaro bai san wuta ba sai ya taka, ga fili ga
mai doki".
Har hafsa ta kwana bakwai a gidan nan, ba su haɗa shimfiɗa
da Alhaji mu'zzam ba, duk ɗokin amarcin da take yi, komai ya fita daga kanta,
ta rasa abun da yake yi mata daɗi, ƙiri-ƙiri yake nuna mata shi ta matarsa yake
yi ba ita ba, saɓanin abun da ya nuna mata a waje.
Jauhar kuwa ta cigaba da yi wa master magiyar, ya taimaka ya
bari ta je gidan hafsa tun da an yi bikin, kuma ta na son ta je gida ta gaida
baba, ta bashi gudunmawar biki.
"Ni fa nayi miki alƙawarin zuwa gidan yayrki, amma
amarya ce, ya zaki je musu gida sati ɗaya da biki?"
Cikin rashin fahimta ta ce "To ba a zuwa?"
"Eh, idan sun shirya samun zuriya su, ai ba za so ki
dame su ba, idan lokaci yayi zan kai ki".
Anty da Rahila suka cigaba da yawon bin bokaye, ƙauye-ƙauye,
dan su sake kama Alhaji mu'azzam, kuma ya saurari hafsa.
Komai na buƙata gashi nan a zube, amma miji ya gagareta sai
dai ta ganshi daga nesa.
Tayi iya ƙoƙarinta, duk wanda ya zo, ba ta bari ya fuskanci
tana cikin damuwa, ta baka abinci ka ci ka sha, idan zaka tafi ta baka na mota
mai yawa, tayi ta hura hanci, saboda tana cikin gida na alfarma ga motoci a
parking lot.
Jauhar ta gaji da yi wa Al'amin magiya, ta ƙyale shi, dan
kansa ya ce ta shirya, shi zai kaita gidan hafsan, su gaisa ya dawo da ita.
Ta din ga murna tana yi masa godiya, amma ta ce "Dan
Allah master a sakawa baburin nan salansar sa, idan muka fita fa saboda ƙarar
da yake yi, sai kowa ya waiwayo ya kallemu".
Ya ce "Ni fa na fi son abuna a haka"
Ta kwantar da murya ta ce "Na sani, amma a taimaka
mini, ko so kake kowa sai ya ɗaga kai ya kalli babyn robar taka?"
"Zan duba"
"Yauwwa master na"
Yayi murmushi ya ce "Naki, waye ya baki?"
Ta ce "Allah ne ya bani, kuma na karɓa hannu bibbiyu
ina yi masa godiya"
Ta kira hafsa a waya, hafsa ta ɗaga da ƙyar tana cika tana
batsewa, Jauhar ta ce "Anty hafsa ina wuni, ina ta kiranki ba kya ɗagawa"
"Bana kusa ne, shiyasa"
"Adress ɗin gidan zaki bani, gobe in Allah ya kaimu zan
zo in sha Allah"
Kamar hafsa ta ce mata ba ta so, b tare da la'akari da su ba
su taɓa taka gidan jauhar ba, amma sai ta ga ya dace jauhar ta zo ta ga daular
da take ciki, dan haka ta bata adress ɗin.
Bayan ta gama wayar, ta ce "Master ta bani adress ɗin,
babu wuya ma gane gidan nata. Zo mu yi kallo a wayata" ta yi maganar tana
zama a kusa da shi.
"Ni kallon nan gajiyar da ni yake yi"
Ta ce "Ahh haba dai, ko kaɗan nan, yana da kyau ka samu
abubuwan da za su din ga ɗebe maka kewa"
Al'amin ya ce "To zaɓi ɗaya, ko dai ki sauke wannan
abun, ko kuma a haƙura da kallon" yayi maganar yana nuna boti, da yayi ɗare-ɗare
a kan cinyar jauhar.
Jauhar ta kwashe da dariya ta ce "Boti master ya ce ka
tashi daga cinyar matarsa" kwanciya magen ya ƙara yi, yana lafewa.
"Ban taɓa ganin abun da ya raina ni ba, kamar ke da
magen nan ba"
Jauhar ta din ga dariya, ita yadda ba sa ga maciji da botin
ma dariya yake bata.
Ta zauna a kusa da shi, tayi connecting da mp, ta saka musu
film.
Ta kalleshi ta ce "Ka ji ko? Baby ake cewa mace, kai
baka yi mini irin wannan kalar soyayyar, sai zare mini ido da sakani kuka"
Yayi murmushi bai ce mata komai ba, sai dai ta ji ya saka
hannayensa ya riƙe nata. Mintuna goma da ta ɗaga kai ta ga yayi bacci. Ta zuba
masa ido yana bacci, a ranta ta cigaba da yi masa addu'a.
Ta kashe wayar ta ce "Master ka tashi ka je ka kwanta
tun da kallon ne ba ka so"
Yayi shiru bai motsa ba. "Master"
"Mmm" ya amsa ba tare da ya buɗe idonsa ba.
"Mu je na yi maka addu'a ka kwanta"
Ya ce "Ɗauke ni, na gaji"
Ta ce "Na ɗauke ka, ai kuwa da sai dai wata ba ni ba,
aikin me ka yi ka gaji har haka?"
"Ƙasa muka kwashe tifa biyar, ban sha komai ba kuma na
yi aikin, ni da su Walid"
Jikinta a sanyaye ta ce "Har tifa biyar master. Baka
gaya mini ba sannu, amma dai sun biya ku ko?"
Ya tashi zaune ya ce "Eh, har na kai wa mai solar kuɗin,
ya zo ya saka miki solar, ya kawo miki fankar solar zafi ya fara yawa kuma ba
wuta".
"Solar kuma master? Da mun sai kayan abinci, zafi
lokaci ne zai wuce, solar fa da tsada".
"An ce masu asma, ba sa son zafi" ya yi maganar
yana tashi tsaye, tashi ta yi ita ma, sai ta rasa me za ta ce masa, ya nufi ɗakinsa,
ta rasa ta ina yakamata ta fara ma. Akwai abubuwa masu muhimmanci da yakamata
ace yana yi da kuɗi, da solar da ya saya, kamata yayi ace ya sai musu kayan
abinci, ya ɗinka sutura da ko ɗan takalmi ne mai kyau na kwalliya. Duk in da ya
kwashi taklminsa soso haka yake ƙarawa gaba da su, kayansa ma ita ta ware masu
kyan ta kai ɗakinta, sai idan za shi wani wuri na musamman ko juma'a ta bashi
ya saka. Sai dai ta san bai kyautu, ta nuna ba ta ji daɗin abun da yayi ba,
domin ko ba komai, yayi ne dan ya kyautata mata.
Ya nemi wuri ya kwanta, ta zauna a kan katifar, ta ɗora
hannunta a kansa, tare da karanto masa addu'oin kwanciya bacci.
Abun da jauhar ba ta sani ba, bayan ciyar da shi da ta din
ga yi farkon auren su, Addu'ar da ya ji tana yi masa cikin magagin ciwo, tayi
matukar tasiri a zuciyarsa, Addu'a ce da idan ba uwa ba, ba kowa zai yi maka
ba. Addu'oin da take yi masa idan yayi mata wani abu na kyautatawa ma, ba
ƙaramin daɗi yake ji ba. Ga uwa uba kirarin da take yi masa wasu lokutan, da
suke fasa masa kai. Duk wani abu da zai yi baya manta tarin alkhairin ta.
"Allah ya saka maka da alkhairi, ya buɗa arzikin ka, ya
wadata mu da halal ya nesanta mu da haramun. Na gode sosai da sosai Allah ya
biya ka da gidan aljanna, ya jiƙan iyayenmu"
Idonsa a lumshe ya ce "Amin 'yar aljanna, addu'ar ta yi
daɗi" tayi murmushi ta tashi.
Washegari da wuri ta shirya, tana ta murna za ta je gidan
hafsa, ta wanke laifinta na rashin zuwa biki.
Shi kuma ya ce zai kaita, amma ya din ga yanƙwanata.
Ba su fita ba sai sha ɗaya saura, tiryan-tiryan, har gidan
hafsa.
Gida ne babba na gaske, Al'amin ya ce "Ba daɗewa zaki
yi ba, da wuri zan dawo mu tafi"
"To Allah ya dawo da kai lafiya, take care".
Ya ce "To, ki shiga, sai na tafi"
"Saboda kar in gudu?"
"Idan kin gudu ma zaki dawo" yayi maganar yana
tayar da babur ɗin sa.
Juahar ta shiga har falon Hafsat, ta din ga bata haƙuri na
rashin zuwanta bikin nan ta ce "Kin san halik maza wasu lokutan sai a
hankali, babu yadda ban yi ba, amma ya hana, ba shi da lafiya lokacin"
Hafsa sai ɗan fizgar kai take yi, wai ita dole ga matar mai kuɗi.
Har la'asar tana gidan hafsa, bayan ta gama shan ƙamshin, ta
saki jiki kuma suka hau hira, da yake ita ce sakuwar jauhar, daga ita sai
jauhar.
Ta din ga koɗa mata irin son da Alhaji mu'zzam yake yi mata,
dan ta tura mata haushi. Jauhar kuwa ko a jikinta, ta ce "Wallahi yaya
hafsa idan Allah ya baka miji mai sonka tsakani da Allah, duk wani ƙalubale mai
sauƙi ne"
Ta ce "Aikuwa shiyasa nake tausyinki, aure ba soyayya,
ga miji sai a hankali"
Jauhar ta ce "Aikuwa ke da ki ka yi na soyayyar ma, ba
ki fi ni samun kulawa ba, da farko a tsorace nake da shi, tun da muka saba
Alhamdilillah"
"Taɓ, haryanzu yana safarar cocaine ɗin?"
Duk da jauhar ta ji haushin maganar ta ce "Da safarar
cocaine yake, ai mun girmi zaman Kano sai Abuja"
Al'amin ya kira jauhar, ya ce ya zo ta fito su tafi.
Ta leƙa ta window falo ta hango shi, a cikin harabar gidan.
Ta ce "Ɗago kanka sama ka ga" ya ɗaga kai, ya
hangota.
"To ka tafi, ba yau zan dawo gida ba, sai gobe"
"Wallahi idan ba ki fito ba, zan shigo har ciki"
"Kaikaikai, gidan mutanen za ka shigo?"
"Sai na shigo ɗin tukuna kenan?"
Tayi dariya ta ce "A'a, rufa mini asiri, kar ka saka da
ni da kai a zanemu, gani nan"
Hafsa ta yi ƙuri da ido, tana kallon jauhar, tana leƙen
Al'amin kuma suna waya, tana ta dariya.
"Yaya hafsa, bari na tafi"
Hafsa ta tashi ta ce "Mu je na raka ki".
Suka fito harabar gidan tare, yanayin Al'amin a yanzu, akwai
nutsuwa a tare da shi, ba kamar lokacin da ya je gidan su ya ɗauki jauhar ba.
Hafsa ta ce masa "Ina wuni?"
"Lafiya ƙalau" ya amsa idonsa a kan jauhar.
"Ya ka ke hararata ne, ba gani na fito ba"
Ya ce "Zaki yi bayani" motar Alhaji mu'azzam ce ta
shigo gidan, yana hangen jauhar, ya ci wani irin wawan burki ya buɗe motar ya
fito.
Ya ƙaraso ya kalli Jauhar ya ce "Jauhar, dama kina
nan?"
Tayi murmushi ta ce masa "Eh, ina wuni?"
"Lafiya ƙalau jauhar, sai dawowa na yi aka ce mini kin
yi aure, na ce ko wani laifin na yi miki? Hafsa ta ce mini dama akwai wanda ki
ke so, shi ki ka aura, ni kuma baki gaya mini ba lokacin da nake neman
aurenki"
Kallo ɗaya jauhar ta yi wa Al'amin, ta ga ya murtuke fuska,
idonsa ya fara kaɗawa zuwa ja.
Ta ce "Eh, gashi nan a gabanka mijin nawa, Allah dama
ya ƙaddara yayata zaka aura. Yaya hafsa sai anjima".
Ya ce "Tsaya na baki na mota" ya saka hannu a
aljihunsa ya ɗebo kuɗin da bai san yawan su ba, ya miƙa mata ta girgiza kai ta
ce "A'a na gode"
Hafsa ta ce "Baby kawo ka ga" ta karɓi kuɗin ta
turawa jauhar a jakarta, ta ce ba a mayar da kyautar manya, ku gaida gida. Tuni
Al'amin ya juya ya fice, idan ya cigaba da tsayuwa, zai iya yi wa Alhaji
mu'azzam illa, da wuƙar da take cikin rigarsa a soke.
Tun da suka tafi hanya, bai ce mata uffan ba, hakan ya sanya
ta cikin matsanancin tashin hankali.
Da ya ajiyeta a gidan ma, tafiyar sa yayi, bai ko shiga
gidan ba.
Ta din ga addu'a Allah ya sanyaya masa zuciyarsa. Duk yadda
ya so ya sarrafa kansa ya kasa, sai da yayi shaye-shaye, domin rage raɗaɗin
abun da yake ji, dan zuciyarsa har wani tururi take yi.
Har sha biyun dare, idonta biyu tana zaune, tana jiran
dawowarsa, ya koma mata Al'amin ɗin sa, dan ko sallama bai yi ba ya shigo, ya
wuceta ya tafi ɗakinsa.
Cikin fargaba, tana addu'a, ta bi bayansa, warin wiwi duk ya
cik wurin.
"Sannu da zuwa, nan zan kawo maka abincin?"
"Fita ki bani wuri, kafin na kakkaryaki na zubar. Idan
ba kya son zama da ni, ba sai kin wulaƙanta ni, ta hanyar kai ni wurin tsohon
saurayinki ba, shiyasa nake ta baki zaɓi tuntuni a kan zama da ni, ba dan na
sarrafa zuciyata ba, sai na kashe mutumin nan har lahira yau, fita ki bani
wuri, bana ƙaunar ganinki ma".
Ta marairaice ta ce "Dan girman Allah ka yi haƙuri,
wallahi da na san zamu ganshi da ba mu je ba, ni saboda 'yar uwata na je".
"Saboda 'yar uwakki, ko kuma saboda ki ganshi?"
"Ya za ayi na je ganin wani, alhalin ina ɗauke da
igiyar aurenka a kaina"
"Ki daina wani kwantar da murya, na riga na gane abun
da ki ke nufi, da in da ki ka dosa, if you still loves him zan iya sakin ki, ki
iya koma wurinsa, tun kafin na illata ki, ba zan juri wannan cin fuskar ba, nan
gaba ban san me zaki aikata ba"
Cikin tsananin ɓacin rai ta ce "Idan ka sake ni, hakan
baya nufin rayuwata ta zo ƙarshe, jaririn da ya zo duniya ma Allah ya na iya
karɓar rayuwar mahaifiyar sa, kuma ya raya mata shi. Ka yi mini duk hukuncin da
ka ga shi ya dace ni" ta fice daga ɗakin, cikin tsananin ɓacin rai da
damuwa.
Ransa yayi matuƙar ɓaci, jin yadda ta gaya masa maganganu,
gashi dama a cake yake, ya nemi wata ƙwaya ya haɗiya ya kwanta, dan kar ayi ɓatacciya.
Da asuba ya farka, ya saba ta zo tayi ta fama ta tashe shi, amma yau taƙi zuwa.
Yayi sallar asuba, gari yayi haske ya fito, amma ba ta fito
ba, ya gaji da zama ya fita.
Da azahar ma, abincinsa ta ajiye masa ta yi zamanta a ɗaki,
idan yana falo tana ɗakinta, idan yana ɗaki sannan zata fito.
Ya shareta shi ma, yana jiran ta zo ta bashi haƙuri kamar
yadda ta saba, amma taƙi, sai ya ji gidan yayi masa duhu babu daɗi. Kusan
kwanaki uku, ba wanda yake shiga harkar wani.
Yau har ya cire kaya ya kwanta, ya tashi ya zauna yayi shiru
yana tariyo maganganun da ya gaggaya mata, sai ya ji sun ɗan yi nauyi da yawa.
Ya tashi ya tafi ɗakinta, kasancewar babu wuta, ya kunna
fitilar wayarsa, ya shiga.
Tana banɗaki tana wanka, ta jingina fitilarta a kan mudubi,
tana haska mata cikin toilet ɗin.
Ya ƙarasa gaban mudubin, ya ɗauki wayar ya kashe fitilar.
"Waye a nan?" Tayi maganar cikin tsoro, dan ba ta
san ma ya dawo ba.
"Waye?" Yayi shiru bai yi magana ba.
Da sauri ta gama kwara ruwan a jikinta, ta fito sai dai ɗakin
yayi duhu, ba ta ganin komai.
"Wai waye ne?" Tayi maganar tana laluba hanya.
Direction ɗin da yake ta nufo, cikin tsoro, kawai ta ji ya
zaunar da ita a kan cinyarsa. Cikin tsananin tsoro ta ware baki za ta yi ihu ya
tsohe mata baki ya ce "Shhhhh, Al'min ne"
Ayshercool
08081012143
🔞 LITTAFIN KUƊI NE ₦500 VIA 0009450228
AISHA ADAM JAIZ BANK
SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143
YOUR RECEIPT VALIDATE YOUR PAYMENT.
Cikin cunkusa baki ta ce "To kuma shi ne zaka tsorata
ni? Ko gama wankan ban yi ba na fito"
Ya ce "To mu je na ƙarasa miki"
Tsuke bakinta ta yi ta kasa magana, jin abun da yake yi, da
ba ta yi zato ba.
Kasancewar bayanta, yana jikin ƙirjinsa, yana jin bugun
zuciyarta yana fita da sauri-sauri.
"Meyasa ki ke shareni? Kwana uku kin yi mini laifi,
kuma kina gaba da ni ko?"
Ba ta yi mamakin ƙarfin hali, da ƙwarewa a iya rainin
hankali, irin na Al'amin ba, wato ma zaman jiran ta bashi haƙuri yake yi.
"Kin san zaki yi gaba da ni, meyasa ki ka bari muka
saba? Ba ni da saurin sabo, ki ka yaudare ni ki ka sa na fara sabawa da ke, shi
ne zaki wani din ga mazewa. A din ga manta abu a kwana ɗaya ya wuce kawai a
cigaba da life. Ni kaina ban san dalilin da ya sanya nake matuƙar jin baƙin
ciki idan na ga wani abu ya raɓe ki ba"
Da ƙarfi ta ce "Master" tayi maganar tana ƙoƙarin
miƙewa.
Hankali kwance ya ce "Yes" ba tare da daina abun
da yake yi ba.
Cikin rauni ta ce "Wai meye haka?"
"Aure" ya bata amsa kai tsaye.
Shiru yayi, jin yadda zuciyarta ke cigaba da bugawa da
sauri, tana nema ta fara haki, saboda tsoro.
A hankali ya ce "Common, relax mana"
"Babyn roba" tayi masa shiru, "Kodayeke yanzu
babyn ƙarfe ce, ki amsa mana" still ta yi masa shiru, yana jin yadda ta
saka ƙarfinta ta riƙe hannunsa.
Fito yake yi mata a kunne, hakan ya sanya ba shiri, ta saki
hannunsa, ta toshe kunnenta.
"Ki amsa mana, tambaya zan yi miki mai muhimmanci. Kin
san bana mantuwa, kamar na'aura mai ƙwaƙwalwa nake, in dai ka ajiye zaka zo ka ɗauka.
Idan ban manta ba kin ce kina so mu rayu tare. Ina ta tsoron taɓa abun da nake
ganin ban dace da shi ba. Ba na son cutar da rayuwarki, in yi silar gurɓacewarta
kamar yadda tawa ta gurɓata, duk da kin daɗe ki na nuna mini ina rintse ido,
Al'amin ba ya abu bisa zalunci"
"Na nuna maka me?"
"In faɗa kenan, ko shekaranjiya meya kawo zancen
zuriya? Ke 'yar yarinya kallonki kawai nake yi, amma kar ki damu da hakan ai
lafiya ce" wato da wani ne yake ba wa jauhar labarin maganganun nan daga
bakin Al'amin suke fitowa, sai ta ƙaryata, amma ƙiri-ƙiri, ya shige duhu yana
sakin maganganu yadda yake so, alhalin ya ce ba ya jin komai.
Tana cikin tunanin ta ji ya ce "Kin amince mu rayu
tare, a matsayin abu guda? Ba na son cutar da ke, ke ma kin shiga ƙalubale da
dama, bana son ki sake shiga matsalar rayuwa, rayuwarki ta tafi a haka kawai.
Idan kin amince, zan yi iya ƙoƙarina wurin zama da ke da zuciya ɗaya, amma sai
kin yi wa yanayin rayuwata uzuri, duk da a yanzu ma kin taka muhimmiyar rawa a
rayuwata. Be mine"
Haka kurum ta fara kuka, kukan da ba ta san na menene ba ma.
"Talk babyn roba".
"To ka ƙyale ni, gobe da asuba sai na gaya maka"
Cikin buɗɗiyar muryarsa, da take fitowa daga ƙirjinsa, ya ce
"Na ƙi wayon, yanzu zamu gama maganar"
"Master"
"Mmmm"
"To zaka daina saka ni kuka?"
Ya ce "In sha Allah"
Ta ce "Zaka daina shaye-shaye?"
"In sha Allah, ina iya ƙoƙarina, ba abu ne da zan daina
lokaci ɗaya ba. Mu bar wannan maganar, baki bani amsa ta ba, zaki cigaba da
zama da ni, a yadda nake, ina talaka marayan da ya rasa kulawa, sai bayan
shigowar ki rayuwata?"
Tana kuka ta ce "Dama ai kai ka ke cewa zaka sake ni,
ka ke sakani kuka, ina son in zauna da kai"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Duk wani abu da ki ka yi mini
na alkhairi, yana rubuce a ƙirjina, ba zai taɓa gogewa ba, ban taɓa mantawa da
ko guda ɗaya ba, babu wata mace da ta taɓa playing role ɗin uwa a rayuwata sai
babyn roba, bashi ne a kaina kulawar da ki ka yi mini".
"Ni saboda Allah nake kula da kai"
"Ni na isa in biya ki ne dama?"
Jauhar ido yayi tsilli-tsilli, bayan da Al'amin ya ƙaryata
tunaninta na ko ba shi da lafiya ne.
Ya tabattar su a matsayin miji da mata. babu tsammani aka
kawo wuta, haske ya gauraye ɗakin, Jauhar ta takure jikinta, sai rawa jikinta
yake yi, yayi murmushi ya ja bargo ya rufeta.
Ya zuba wa gashin kanta ido, ba baƙi ne wuluk ba, amma mai
laushi irin na fulani, ya hargitse, ta cusa kanta cikin bargo sai gashin a
waje.
Ya daɗe yana kallonta, kafin ya kai hannunsa yana shafa
gashin ya ce "Amm ya ma sunan angela ko?" Tayi masa shiru, ta sake
dunƙulewa wuri ɗaya.
Ya cire bargon daga fuskarta, amma ta rintse idanunta.
"Kalleni mana, abu zan gaya miki fa"
Ta cunkusa baki, tana ta jan majina a hancinta, fuskarta duk
ta yi ja saboda kuka.
Wani nishaɗi yake ji, ya cigaba da kallonta yana ta
murmushi, kamar wanda aka yi wa Albishir da kujerar makka.
Wayarsa da ta faɗa ƙasan gado ce, ta fara vibrating, ya juya
ya zura hannunsa ya ɗaukota, ya sake matsawa kusa da jauhar, ya ɗaga wayar.
"Maza" muryar liti tayi amsa kuwwa a wayar.
"Mmm"
"Kana ina ne?"
A taƙaice ya ce "Gida" yayi maganar yana cigaba da
shafa gashin jauhar.
"Wai me ka ke yi ne? Ko baka da lafiya ne?"
Al'amin ya ce "Meyafaru?"
"To ai ji nayi kana amsawa kamar ana yi maka dole"
"Ina jinka ya aka yi?"
Liti ya ce "Akwai matsala ne fa"
"Ta me?"
"Yaran madaki, duk sun cire pastocin indabo, ka san ɗazu
Walid da su guduma suka gama sasskawa, mu na dawowa muka tarar duk sun cire, ya
tambaya aka ce masa yaran madaki ne, gashi can ya tafi, nayi-nayi ya ƙyale su,
ya ɗau wuƙa ya tafi, shikaɗai kar su yi masa wani abun, ka san Walid da baƙin
taurin kai, kamar jinjirin jaka, dan yafi jaki taurin kai"
Al'amin ya ja guntun tsaki ya ce "Gani nan, bari na
tafi cikin garin, maza ka kira yaran nan, ka yi magana da su guduma ma, zan
kira yaran unguwar mu, maza su bishi kar su yi masa wani abun, gani nan"
ya yinƙura zai tashi, jauhar ta ja jikinta ta riƙe shi ta ce "Rigima zaka
je ka yi ko?"
Ya girgiza mata kai ya ce "Ba rigima zan yi ba, amma
idan har ba a kai masa ɗauki ba, za su iya kashe shi"
Cikin takaici ta ce "Kana ganin halin da ka sakani,
a haka zaka tafi ka bar ni, a wannan yanayin da nake ciki?"
Ya ɗagota ya ce "Ki yi haƙuri, bana son a sake asarar
rai saboda ni, wallahi suka ga Walid shikaɗai, za su iya kashe shi, am sorry
yanzu zan dawo, ki kwanta kar ki tashi kina buƙatar hutu" ya ƙarasa
maganar yana kwantar da ita ya bar ɗakin.
Ta lumshe idonta, hawaye suka cigaba da zuba, sai da ta yi
ta gaji, sannan ta saukko daga kan gadon da kyar, ta haɗa ruwa mai ɗumi sosai
ta tsarkake jikinta, ta nemi wuri ta kwanta.
Da asuba da ƙyar ta tashi, ko alwala ba ta yi ba, ta tafi ɗakinsa
ta duba, ko ya dawo cikin ƙoshin lafiya.
Ƙarar buta ta jiyo a banɗakinsa, alamar yana alwala, wani ɗan
sanyi ta ji a ranta, yau da kansa ya tashi sallar asuba, ko yaushe ya dawo ma
oho.
Ta koma ta yi salla, ta sake fitowa ta leƙa, ta ga yana
salla, ga kayan shaye-shaye a kan katifarsa, ganin yana salla, ta shiga kanta
tsaye, ta tattare kayan ta fice.
Bacci ya ƙara kwasheta, tana cikin baccin ta ji ta a takure,
ta yi miƙa ta buɗe idonta, ta saka a nasa.
"Kalli agogo ƙarfe sha ɗaya, yunwa duk ta yi mini illa,
na sayo ƙosai na kasa ci, ya ja mai, kuma farin maggi ya yi yawa a ciki sosai.
'ikon Allah, shi ko ɗan rarrashin nan ma ba zai yi bs,
zancensa kawai abinci.
A ƙule ta ce "In da ka tafi ba su baka abincin ba?
"Me ki ka ce?"
Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Na ce in da ka tafi ba
su baka abincin ba?".
Ya ce "Ba su bani ba, ke zaki tashi ki bani yanzu"
Kawai ta juya masa baya, dan daren jiya ta ƙulu yadda ya
tafi ya bar ta.
Ba ɗaga ƙafa, ba komai, ya ƙara huce baƙar maganar da ta
gaya masa, ya gama ya tada kai da jikinta, ya lumshe ido ya hau bacci.
Ta gama koke-kokenta, duk iya ƙoƙarin da tayi, ta ture shi
ta tashi, ta kasa sai ma ji da tayi tana haki, Al'amin ya gama raina mata
hankali ta ko ina.
A haka har baccin dole ya sake yin gaba da ita.
Ƙarshe har azahar ko wanke-wanke ba ta yi ba.
Ta yi wanka, ta canza kaya, ta fito ya basar da ita, kamar
babu abun da ya faru, ta tarar da shi da wayarta a hannunsa, yana game, ta
share shi ta wuce, sai da ta fita ya bi bayanta da kallo yana murmushi.
Ta tarar yayi wanke-wanke, ya share tsakar gidan tsaf, har
markaɗen kayan miya ya kai.
Ta dawo ta koma ɗakinta, ta ɗaukko bedsheet, zata fita ya ce
"Me zaki yi ne?"
"Wanki"
"Me ya same shi, zaki wanke? Ko karyawa ba ki yi ba? Ki
saka shi a baho, zan wanke, ki samu ki karya"
Sai cika take tana batsewa, mazewa kawai yake yi, don dariya
yake son yi, amma ya maze shi ma ya sha kunu.
Tun da ya kai markaɗen nan, ya dawo bai sake fita ba, wuni
guda yana gida, duk da babu wanda yake kula wani, amma zaman kula da ita yake
yi.
Har isha'i, kowa ya koma ɗakinsa, har ta kwanta, ta ji ya
shigo ɗakin, kan tayi magana ya ƙaraso kan gadon ya hau.
"Malam ya ne? Menene kuma?"
"Kamar yaya?" Yayi maganar yana janyo bargonta, ya
rufe ƙafarsa.
Kamar tayi ihu ta ce "Menene kuma?"
Ya ce "Da na kawo miki kajin mutum goma sha biyu, ki ka
cinye ki ka yi kyautar wasu, kin tambayi ta mecece?"
Cikin rashin fahimta ta ce "Ban gane ba, ka ce a gidan
oganka ka karɓo".
"To gaba sai ki dinga tambaya, kwaɗayayyiya, ki ka din
ga ci kina rabarwa, ni sai dai ki sammini, yanzu kuma tambayata lafiya? Ba
lafiya ba"
Cikin rauni ta ce "Master" ya ce "Yes"
"Dan Allah ka koma ɗakinka" ya kwanta ya ɗora
ƙafarsa ɗaya kan ɗaya ya ce "Zuriya fa ki ke so, ki ke wani basarwa"
Jauhar ta yi danasanin faɗar maganar nan.
Kawai ta zauna a zaune tana kallonsa, sai kaɗa ƙafa yake yi.
"Zo ki kwanta, na ga lokacin da baki da lafiya, har
wani ƙara lafewa ki ke yi, bisimillah" yayi maganar yana nuna mata
ƙirjinsa.
Pillow ta gyara ta kwanta a kai, ta ƙi kula shi, mutumin da
suka wuni ba sa magana, saboda tsabar son tayar da tarzoma, ya lallaɓo yana
tayar da wani tsohon zance.
Da asuba ta riga shi tashi, ta shiga ta yi wanka, tayi
alwala ta zo tana tashinsa, ƙarshe sai kusan shida da rabi suka yi sallar,
bayan ya saka ta canza wani wankan da alwala. A wurin da tayi salla, ta kwanta
a kan sallaya ta cigaba da bacci.
Iya ƙoƙarin sa yake yi kar ya sha komai, ya kasa jurewa,
kamar zai fita hayyacinsa, ya lallaɓa ya dawo ɗakinta, ya tarar tana kwance a
ƙasa tana bacci, boti ma yayi lakur a kan sallayar yana bacci.
Tankaɗe boti yayi can gaba, ya kwanta a kusa da ita, ya ƙura
wa fuskarta ido, ya kai bakinsa ya sumbaci goshinta.
A ranar aka saka wa jauhar fankar solar, da ƙwai, ta din ga
murna tana yi masa godiya.
Sai dai Al'amin ya uzzura mata, duk dare, sai ya ce mata wai
shan fanka ya zo, zafi yake ji, sai da ta gaji ta ce "Dan Allah master ka ɗauke
fankar nan taka ka mayar ɗakinka , ko na huta"
Ya ce "A'a ai dama ke na sayawa, dan haka gara na din
ga zuwa nan kawai ina shan isakar, idan na mayar da fankar can, bayan iska kuma
takura mini za ta yi din ga yi".
Ta ce "A taƙaice dai, ni ce fankar kenan?"
Ya ce "Eh mana, ke ga taki fankar, ni kuma ga
tawa" yayi maganar yana nuna ta.
***
Kwanaki suka cigaba da tafiya, sai dai tsakanin Alhaji
mu'azzam da Hafsa sai dai kallo, ranar da uwargidansa ta bari ya zo ɗakin
hafsa, kawai ta ga ya nemi wuri ya kwanta.
Duk da irin kunya da kawaici irin ta 'ya mace, sai da ta
cire kunya ta ce "Wai ni Alhaji, menene matsayina a wurinka ne? Na kasa
gane kan wannan al'amarin"
Ya kalli hafsa ya ce "Jauhar, yakam...
A fusace ta ce "Wace irin jauhar kuma? Wulaƙancin naka
da rashin mutunci har ya fi da, ga mari ga tsinka jaka? Tun ranar da jauhar
suka zo, ka rasa sukuni, ka ke kirana da sunanta ba na so"
Ya ce "Am sorry mistake ne, ki ƙara haƙuri ki bani
lokaci, na yi wa Safiyya Alƙawarin babu abun da zai shiga tsakanina da ke, har
sai lokacin da ta samu nutsuwa hankalinta ya kwanta, tana cikin damuwa sosai da
sosai, kin san tana da kishi ne sosai da sosai ".
Kamar ta ɗura masa ashar ta ce "Au har gaya mata ka ke
ba abun da ya shiga tsakanina da kai, har sai ta yadda? Ita take aurena kenan?
Bakomai na gode, ta ci lokacinta when it comes to my turn, zata gane shayi ruwa
ne" ya girgiza kai ya ce "Kin ga ba na son rigima, ba zaki zo ki
sameni, ina zaune lafiya da iyalina ki ɗaga mini hankali ba Please, ina
respecting farincikin matata sosai da sosai "
Hafsa ta ja tsaki, ta fice ta bar masa ɗakin.
Al'amin na zaune a falon Indabo, ana ta tattauna yadda
al'amura za su tafi kafin lokacin zaɓe, dan wata ɗaya kawai ya rage babban zaɓe,
wanda yake dai-dai da lokacin sallar layya.
Ya rage daga Al'amin sai P.A da Indabo yana ta sake
jaddadawa Al'amin, idan aka ci kujerar nan za su ji daɗi, dan tun yanzu an ce
masa idan ya samu senator ɗin nan, akwai vacancyn mutum uku za a bashi a NNPC.
Al'amin ya ce "A cikin yarana, ko Nura guduma ne, ina
son a samo masa aiki ko direban manyan motoci ne, yana can na saka ana koya
masa jan manyan motoci"
Indabo ya ce "Ba ka da matsala, kawai ku yi aikinku,
duk akwatin da ku ka ga zata bayar da matsala, ku tayar da tarzoma. Maganar da
nake yi maka, a yarjejeniyar da muka yi da uwar jami'iyya ta ƙasa, kan na dawo
cikinta, nan da wasu shekaru, za a tsayar da Abdul takarar mataimakin
gwamna"
Al'amin ya ce "Har masu shaye-shaye ake tsayarwa su yi
jagorancin al'umma kenan?"
"Shaye-shaye kuma, yaron da yake karatu a waje, in sha
Allah shi zai zama mutum mai ƙarancin shekaru da zai zama gwamna"
"Menene sadakin aikina?"
Indabo ya ce "Me ka ke so ayi?"
Hajiya Bilki ce matar indabo ta shigo da laces, da atamfofi
da lesuna sun kai talatin a hannunta, ta shigo ta zube a gaban Indabo.
Ya kalleta ya ce "Madam ya dai?"
Ta ce "Kala goma zan zaɓa ka saya"
"Ke dai kullum cikin ɗinka tsumma, ko gajiya ba kya
yi"
"Kana shirin zama distinguish, ba dole na ɗinka sutura
ina shiga ina fita, ina barazana ba".
Indabo ya ce "To ki ɗauka, ina ta jiran Kwamishinan
ayyuka ne, rage kuɗin wata kwangila, mu ƙara rage na campaign, ya haɗa kayansa
yana kan katanga, jami'iyyar da tayi nasara zai koma da an yi zaɓe.
Ala'amin ya tashi ya tafi gaban kayan, ya zaɓo zuƙa-zuƙan
lesuna, guda uku, da atamfa uku.
Indabo ya ce "Yaya saya zaka yi?"
"Kai dai zaka saya, daga cikin sadakin aikina".
Hajiya Bilki ta ce "Kai, lesunna hannunk fa dubu
tamanin guda biyu, ɗaya dubu hamsin da takwas, atamfofin nan dubu arba'in da
biyar, har nawa zai baka? Kuɗin da yawa ai"
Ya kalleta ya ce "Ke zaki biya? Kuɗin kwangilar mutane
za a sata a biya miki ai, wannan ma ya biya, ai ba kyauta zai bani ba, jinina
da rayuwata zan saka a hatsari dan samun nasararsa. Ya miƙe da kayan a
hannunsa, ya kalli Indabo ya ce "Sauran kuɗina za su zama ajalan a kanka,
komai daren daɗewa zan waiwaye su, yadda ku ke ƙwamusar kuɗin mutane ta
gajimare dole a din ga kasawa da mu, idan ana son a ga dai-dai, tun da damu ake
wahalar waccan 'yar yarinyar ta gidana, itama yakamata a din ga damawa da ita.
Kuma rabon tallafin karatu ma, a saka mini ita a ciki"
Indabo ya ce "Aminu kenan, shikenan jeka Allah ya
taimaka"
Ya haɗa hannayensa biyu ya ce "Sa'a dai" ya fice
daga falon.
Hajiya Bilki ta ce "Gaskiya honorable, yaron nan yana
wuce gona da iri, kamar tsoronsa ka ke ji"
Ya ce "Ba tsoronsa nake ji ba, aikin da yake yi mini
yana da yawa, kasada duk girmanta yana ɗauka. Akwai lokacin da tilas na yakice
shi ai".
Al'amin bai shiga da kayan gida ba, sai cefane da yayi na
abincin dare.
Ya tarar ta yi dambu tayi wa dambun miyar jajjage, da salad
da awara.
"Ke dai Allah ya yi miki iyayi, dambun da ake sakawa
mai, ki ke yi wa miya, har da wata munafukar awara".
Jauhar ta ce "Idan munafuka ce, bamu mu raba da ni da
boti, shikenan ba canji, kullum sai dai dambu da mai? Ai gara a din ga
upgrading"
"Sai dai ya mutu da yunwa kuwa, to ai awarar ce, 'yar
kaɗan"
"Wai master ba ka iya abun 'yan gayu ba? Babu naman da
zan saka a cikin miyar, sai na haɗa da awara, bai bada ma'ana ba? Ko sai an
cika kwanon da awarar passion ce a kai"
Ya taɓr baki ya ce "Eh to, gashi nan dai, zoɓon ma
kamar yayi tsami, amma kwantai ne na jiya ne ko?"
"Mmmm, na waccan shekarar ne" ta bashi amsa tana
cigaba da aikin gabanta, na shirya stone.
Tsoknarta yake yi, ya matsata tayi tsiwa, ita kuma taƙi.
"Yaushe WAEC ɗin ku za ta fito ne?"
Jiki a sanyaye ta ce "Ta kusa, har ba na son tunawa da
ita"
"Saboda ba ki yi abun arziki ba ko?"
"A'a lokacin kana tsare, bana iya karatun"
Ya ɗan rausayar da kai ya ce "Eyya, abun tausayi, Yallaɓai
dan Allah ku sake shi, ba shi da laifi, laifina ne, wallahi ba shi da lafiya
ma, master dan Allah ka gaya musu ba ka da laifi" yayi maganar cikin sigar
kwaikwayon yadda ta yi waccan ranar.
Murmushi ta yi ta ce "Kada Allah ya kawo abun da ba zai
wuce ba, a lokacin nan ji nake a duniya kamar nikaɗai aka tsana wallahi. Da aka
ce mini an kai ka prison, kawai na saddaƙar ciwon zuciya ya kama ni, kuma wai
ka ce kar a kaini na ganka, ai na ji haushi, a duniya ba zan manta da su yaya
walid ba, duk da suna taimakawa wurin ƙara ingizaka a shaye-shaye, amma sun
tsaya tare da ni a lokacin da kow yake ganin idan ya taimaka mini zai kwana a
ciki"
Ya ce "Allah sarki 'yar madara, ba na son in ga kina
kukan nan ne, ko kina yi wa 'yan sanda magana, suna wani yanƙwana mini ke,
raina ɓaci yake yi shiyasa na ce kar a sake kawo ki".
Ta ce "Gashi ya wuce, duk da lokacin gani nake kamar ba
zai wuce ɗin ba"
Ta tashi ta shiga ɗaki, ta dawo ta tarar da robar alawar
madarar da take sayarwa, a gefensa bakinsa kuma yana ta tauna, ta ɗaga robar ta
ce "Alawata ka ke sha ko?"
"Eh, ta guda uku na sha sittin, a rage mini naira goma
hamsin kenan"
Sororo take kallonsa, "To ai ba a jikina ake tatso
madarar ba, da zan sayar da ita ashirin ashirin, naira hamsin ce fa duk ɗaya
"
Ya waro ido ya ce "Ki ji tsoron Allah, har na sha ta ɗari
da hamsin, gaskiya saba'in zan bayar".
Abun da yake so ya gani ɗin ta fara, shagwaɓa tana cewa sai
ya biya ta.
"Gaskiya bani da kuɗi yanzu, zo ki shanye abarki"
ya fito mata da harshen sa.
Ta harare shi ta ce "Bana so, kuma idan na zo yi maka
wanki na tsinci kuɗi, sun zama nawa"
"Eh ai dama kin saba kwashe mini 'yan canjina, da kayan
cajina shiyasa ki ke yi mini wanki ba dan Allah ki ke yi ba" ya tashi
kamar zai tafi, amma ya riƙeta, yayi kissing ɗin ta, ya ce "To kin ga tare
muka shanye, yanzu talatin ma zan baki" ya saka hannu a aljihunsa ya ciro
dubu biyu ya ɗora mata a wuyanta ya ce "Gashi nan, uwar son kuɗi"
"Ai talatin ka ce zaka bani, saura dubu ɗaya, dubu uku
yakamata ka bani"
Ya ce "Biyoni ɗaki ki karɓa"
Ta ce "A'a na yafe maka sauran, amma kar ka sake"
Sosai wani bond mai ƙarfin gaske ya shiga tsakaninta da shi,
har mamakinsa take yi, duk da mai hali baya fasawa, idan miskilancinsa ya
motsa, ko kuma ya cake, ba ya sarrafuwa ta daɗi, amma haka take jurewa. Ga
babban abun da yake ci mata tuwo a ƙwarya yanzu, wasu lokutan idan ya dawo daga
shaye-shayen sa, da ƙaurinsa da komai yake zuwar mata, gashi ba abu ne mai
sauƙi ba, ta nuna masa hakan ba, dole sai ta cikin hikima da dabara.
Haka zata zauna, komai daren da zai yi sai ta jira
dawowarsa, ta saka shi yayi wanka, ya canza kaya.
Yau bayan ya bar ɗakinta, bayan ta idar da salla ta je ta
same shi, a zaune a kan katifa.
Ta ɗauki kwalin sigarin gabansa, ta ciro guda uku ta bashi
ta ce "Wannan ta isa, kar a sha sama da haka dan Allah"
"Bani in je ƙofar gida in sha"
Ta ce "A'a ai shan nake so ka rage sosai da sosai,
wannan ta isa"
Ya juya mata baya ya shanye, tana zaune tana jiransa, ta
bubbuɗe window, saboda hayaƙin ya fita.
Jira yake ta fita ya kuma kunna wata, amma ta cire masa
shirt ɗin jikinsa, ta ce ya kwanta, ya kwanta yana jiran ta fita, amma ta
kwanta a jikinsa, a hankali ta din ga karanto azkar ɗin safiya.
Babbar salla na ta ƙaratowa, jauhar hada-hadar neman kuɗi,
ta cigaba da kankama, Al'amin bai taɓa saka ido a kan abun da take samu ba, dan
yanzu iya ƙoƙarin sa yake yi, ya yi cefanensa, duk da kuɗin da take ɗan samu,
in dai ya ji kuɗi a jikinsa, a kaso ɗari tamanin, ita zai kashewa, bai fi ya
ƙarar da kaso ashirin ba, goma ya rabar goma ya yi shaye-shaye.
Idan ta fuskanci da kuɗi a hannunsa, ta din ga lallaɓa shi
kenan, ayi wani abu mai muhimmanci, idan ba haka ba, ba zai sai abubuwan da
suka fi buƙata ba.
Kuma babbar hanyar samun kuɗinsa, wurin Indabo, ya din ga
tatsarsa kamar mai, duk da yana samun hanyoyin samun kuɗi yanzu, tun da kakar
siyasa ce.
Ana jibi salla, ya ba wa jauhar kuɗi, wai tayi kitson salla
ita ma, ta je ayi mata zane a hannunta.
Ta dawo ta tarar da kaya a kan gadonta, ta zazzage taga kaya
na alfarma duk an ɗinka su, har da takalmi da turare.
Mamaki ya cikata, yana dawowa ta fito falo ta ce
"Master kayan waye a kan gadona?"
"Na kishiyarki ne"
"Wace kishiyata?"
"Ban sani ba, ko ina da wata matar ne bayan ke"
Gaba ɗaya ta rikice ta ce "Master wai nawa ne Gaba ɗaya?"
Ya ce "Naki ne babyn roba"
Har ƙasa jauhar ta durƙusa tana yi masa godiya, ta rasa ma
wace kalar godiya za ta yi masa, har da matse ƙwalla.
"Ni ba irin wannan godiyar nake so ba, a sheƙa mini
girki, a yi wa fankata caji, in sha iska sosai" sunkuyar da kai ta yi,
cikin matsananciyar jin kunya.
"Allah ya ƙarawa fankata gudu, tana ba da iska
sassanya, ƙarfin gudunta, bai sanya tana bada iska mai cutarwa ba"
"Amm bari na je na yi jajjage" ta juya ta nufi ɗaki.
"Dama a ɗaki a jajjagen" ko waiwayowa ba ta yi ba,
ta shige.
Ranar idin babbar salla ma, tare suka tafi sallar idi.
Ta sha kwalliya, tayi kyau sosai da sosai, a abun da bai fi
wata guda ba, ta yi ƙiba fatarta ta ƙara fresh.
Ta sha ɗaurin ɗan kwali, hannunta yayi kyau da zanen lalle
ja da baƙi. Su liti suka din ga kiransa a waya, suna jiransa, yaƙi fita, sai da
suka zo har gida sannan suka fita da shi, bayan sun kwashi wainar masa da
sinasir da miyar agushi.
Bayan la'asar sosai, ya dawo gida da nama kaya guda, har da
karfatar sa, ga kayan ciki da uban nama.
Kamar tayi kuka ta ce "Master, aiki daf da magariba ya
zan yi?"
"Ke da aiki ba ya yi miki wahala, ɗan wannan aikin zaki
yi raki?".
"To aikuwa sai ka tayani, kuma ba ka sayo itace
ba"
Ya kalleta ya ce "Ba a yi a gas, an hanaki shiga
hayaƙi".
"Gas ɗin dubu nawa za a zuba? Dole sai a itace"
Ya kalli naman, ya ce "Ki shiga ciki, bari na aika nura
ya sayo itacen, su walid suna waje, sai su shigo mu yayyanka"
Ƙarshe dai hayaƙin da ba ya so, sai da ta shiga, har sha
biyun dare suna aiki ita da shi.
Duk da haka aikin bai ƙare ba, sai washegari, ta ce masa
tana son zuwa gida, ya ce sai ta gama yi masa kwalliyar salla kan ta fita.
Ya samu dambun nama da cin-cin, ya din ga tumurmusa, jauhar
ta ce "Ni ban gane wannan lamarin ba, gaskiya rabawa za ayi. Kana ta ci
idan cikinka ya ɓaci babu ruwana".
"Ke ki ke da ruwa kuwa".
Sai huɗu ga salla, sannan ya bari ta je gida, ya kaita da
kansa.
Aka yi sa'a Hafsa ma ta je gidan, tun da ta jauhar ta je,
suke kallonta da kayan jikinta.
Sai da mama ta magantu ta ce "Jauhar wannan leshin
fa?"
"Mama kayan salla ne"
"Kin san kuɗin leshin nan kuwa?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a shi ne ya kawo mini"
Ta kalleta ta ce "Wai sana'ar me yake yi haka ne?"
Tayi murmushi ta ce "Yana sana'oin sa, kuma kin san
yana tare da 'yan siyasa".
Hafsa ta din ga kallon jauhar, yadda take komai nata cikin
walwala, kamar ba ta da wata damuwa, duk da tana auren ɗan daba.
Bayan jauhar ta ba su nama, dambun nma da cincin, aka din ga
gaya wa jauhar, ai mijin hafsa rago ya kawo.
Ta ce "Masha Allah, Allah ya saka da alkhairi" Duk
yadda Hafsa ta so mazewa, sai da yanayin ta ya nuna akwai damuwa.
Sai yamma Al'amin ya dawo, ya ce ta fito su tafi, babu yadda
ba ta yi da shi ba, amma ya ce ba zai shiga ba.
Gidansu ma da ya kaita, a waje ya tsaya, a gurguje jauhar ta
shiga ta gaisa da Rahila, ta bata naman sallar sai dai ita ma, kayan jauhar
kawai take kallo.
Ana gama bikin salla, aka shiga hada-hadar zaɓe.
Hankalin jauhar ya kasa kwanciya, saboda yawan shige da
ficen da yake yi yawa.
Yau ake zaɓen sanatoci, dan haka tun kan ta tashi daga bacci
ya fice.
Har yamma shiru bai dawo ba, kuma wayarsa ba ta shiga.
Gaba ɗaya jikinta a sanyaye yake, jikinta ya din ga
bata akwai matsala, har bayan magariba bai dawo ba.
Jin ana knocking ɗin gate, gabanta ya faɗi, ta saka hijjabi
ta fito, ta ga Nura guduma a tsaye ta ce "Yaya wannan karon me kuma
yayi?"
Ya ce "Ki sako hijjabinki mu tafi"
"Mu tafi ina?"
"Asibiti!"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un!"
Ayshercool
08081012143.
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Muryarta na rawa ta ce "Meyafaru? Wani abun ne ya same
shi, ko ya yi wa wani?"
Ya ce "Ni ma ban sani ba, oga walid ne ya ce "In
zo mu tafi tare "
Jikinta a sanyaye, ta kulle gidan, ta bi Nura guduma suka
tafi, suna tafe tana ta addu'a a ranta.
Wani private clinic suka je, emergency suka nufa, ana ta kai
komo da matasa, da aka ji wa raunuka daga wurare daban-daban na harkar zaɓe,
kasancewar an yi tarzoma sosai da sosai a wasu wuraren, kuma nan asibitin ne
mafi kusa.
Da ƙyar take iya ɗaga ƙafarta, wani irin yammmm haka jikinta
yake yi mata, saboda tsoro da tashin hankali.
A ƙofar wani ɗaki, ta tarar da Walid hankalinsa a tashe,
yana kaiwa yana komowa.
"Yaya walid, meyasame shi? Ko mutuwa yayi?"
Walid ya ce "Ki nutsu ba mutuwa yayi ba, yana ta kiran
sunanki ne kafin mu zo nan".
"To meya same shi, yana ina?"
Ganin likita ya fito daga ɗakin da yake facing ɗin su, ya
sanya ta saka kai ta shiga ita ma.
Gigicewa ta yi, ganin Wuƙa a kwiɓin Al'amin a tsaye tsororo,
jini baya zuba, amma tana jikinsa, ga gefen kansa, an naɗe shi da bandeji. An
saka masa oxygen, gefe ga oxymetre na reading vitals ɗin sa.
Cikin kuka ta ce" Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
meya same shi haka? Waye yayi masa haka, Master dan Allah ka tashi, kar ku ce
mini mutuwa yayi" tayi maganar tana rirriƙe hannunsa cikin tsananin tashin
hankali.
Kukan jauhar ya janyo hankalin likitoci, da m'aikatan jinya,
suka ce meyasa aka bari ta shiga?
Da ƙyar aka fito da jauhar ana rarrashinta, aka tabattar
mata da yana da rai, tiyata za a shiga da shi a cire masa wuƙar, sai a
duba kansa.
Cikin tashin hankali ta ce "Dan Allah likita zai
rayu?"
"In sha Allah, da kun biya kuɗin za a shiga da
shi"
Ta kalli Walid ta ce "Yaya Walid, nawa ne kuɗin?"
Walid ya ce "Kuɗin da yawa, P.A ɗin Indabo muke kira,
su biya kuɗin, hannunmu kuɗin ba za su kai ba ayi masa aikin"
"Ka gani ko? Sun ma ƙi ɗaga wayar, su suna can
hankalinsu a kwance, suna jiran sakamakon zaɓe, ni kuma an kassara shi, wannan
tashinsa ai sai Allah"
Liti ya ce "Ki yi haƙuri, in sha Allah zai tashi"
"Nawa ne kuɗin?"
"Da ɗan yawa, ki bari kawai"
Ta girgiza kai ta ce "Ni ku gaya mini dan Allah, a nema
tun da wuri, wuƙa ce fa a cikinsa" tayi maganar tana wata irin ajiyar
zuciya mai ban tsoro.
Suka din ga rarrashinta, amma taƙi saurarsu, Liti ya ce
"Bari na yi gaggawa na je na samu wannan banzan mutumin P.A, ko dai a san
yadda za ayi a biya, wallahi ko mu jiƙa musu aiki"
Jauhar kamar za ta yi hauka, ƙarfin Addu'a ne kawai ya saka
mata nutsuwa, ta din ga kaiwa tana komowa, gashi an ce ba zata sake shiga ta
ganshi ba.
Jauhar ba ta san yadda aka yi ba, liti da Nura guduma suka
dawo da kuɗi, suka biya.
Ake ce ana buƙatar jini, dan da yiwuwar ana cire wuƙar, jini
ya ɓalle.
Haka suka din ga zirga-zirga, jauhar itakaɗai a cikin su,
babu wani daga danginsa, babu daga nata.
Nura guduma ne ya bayar da jininsa, dan shi ne yayi dai-dai
da na Al'amin, aka shiga da shi tiyata.
Hawaye suka kasa barin idanunta, zuciyarta ta din ga wani
irin zafi, ba ta taɓa tsanar wani abu ba, tsana mai muni sai yau duk da ba ta
taɓa ganin indabo ba, tsananin haushinsa take ji, dan shi ne musababbin wannan
tashin hankalin.
Ta kai ta kawo, ta tsuguna tayi kuka, aka shafe sama da awa
guda, ba a fito da shi ba, tayi alwala ta shimfiɗa ɗan kwalinta, ta tayar da
salla, sai dai tana cikin sallar sai ta hau wasi-wasi, da tunanin me zai faru
ta kasa nutsuwa.
Babu tsammani likitocin suka fara fitowa, dan team ɗin
tiyatar sun kai su biyar, gaba ɗaya suka nufe su, suna tambayar yaya?.
Jagoran tiyatar ya ce "Alhamdilillah, an cire wuƙar,
kamar yadda muka yi tsammani ya zubar da jini sosai, amma an saka masa jini,
zamu kai shi ɗakin hutu, amma ba ma son a din ga shiga ana fita da sunan
dubiya, kafin a kai shi ɗakin hutun, za a yi masa hoton kai, duk da saran da
aka yi masa a ka bai yi zurfi ba, amma akwai buƙatar a duba".
"Alhamdilillah ala kulli halin, Doctor mun gode Allah
ya saka muku da alkhairi, ya jiƙan magabatanku, Allah ya sa ku gama da duniya
lafiya ku bar aiki lafiya, ka da Allah ya wulakanta rayuwarku bayan ajiye
aiki".
Cikin farinciki suka din ga amsar addu'a jauhar, da Amin,
tare da ba ta ƙwarin gwiwa a kan zai tashi ya warware gaba ɗaya.
Bayan an yo hoton, suka tabattar da babu internal injury,
jauhar ta zauna ta zuba masa ido, ga jini yana shiga jikinsa a hankali.
Walid ya ce "Ina ganin ki koma gida, ko ni sai na kwana
da shi a nan, kin ga idan ya tashi ba abun da zaki iya yi masa"
"A'a idan na koma ba zan iya zama bama, hankalina ba
zai kwanta ba, ni kawai ku bar ni".
"To ai dole sai da namiji, ko zaki iya ɗaga shi, idan
yana buƙatar hakan?"
Cikin ƙwarin gwiwa ta jinjina kai alamar eh.
Duk da alhini da suke ciki, sai da suka yi murmushi.
Walid ya ce "Bakomai, ki kwana da shi, sai na kwanta a
waje ni, idan ana buƙatar wani abun sai ki kira ni, yanzu bari na sayo wani
abun, ki ci".
"Bana jin yunwa"
Haka suka kwana da Al'amin, amma bai farfaɗo ba.
Ta din ga kallon wayarta, tana tunanin wa za ta kira, kamata
yayi ace tana da wanda za ta kira, a kawo mata abun da zata buƙata saboda zaman
asibiti, amma ta san ko za ayi mata sai an yanƙwanata ko gaya mata maganar da
zata ɓata mata rai.
Kwana suka yi likitoci na kaiwa da komowa a kansa, ƙarfe
shida ta kira Abbu a waya, ya dawo daga masallaci kenan, ya ga kiran jauhar. Ya
ɗaga a nitse suka gaisa.
Ta gaya masa abun da ya faru, dumm ƙirjinsa ya buga, duk da
ba wannan ne karon farko da Al'amin yake kai kansa in da ake cutar da shi ba.
Abbu ya ce "Shikenan, ki yi haƙuri ki daina kuka, in
sha Allah zan zo asibitin, daina kukan haka yarinyar kirki".
Rahila da bacci take yi, sama-sama take jin sa ta ce
"Lafiya, kai da waye?"
"Matar Al'amin ce, wai suna asibiti an caka masa wuƙa a
ciki jiya a wurin zaɓe"
"Kai amma ka tsorata ni, shi ne ka ke ta rafka wannan
salatin haka? Yau ya fara zuwa ayi masa illa a yawonsa? Dan Allah ka kwantar da
hankalinka"
Ya kalleta ya ce "Wuƙa a cikin sa fa aka ce mini, waya
sani ma ko mutuwa yayi, Rahila Al'amin fa ɗa na ne, ba shi nake ƙi ba miyagun ɗabi'unsa
ne ba na so"
"Lallai kam na ga Alama, Allah ya bar soyayya" ta
juya ta cigaba da bacci.
Ƙarfe shidan, Nura guduma ya zo Asibitin, Walid ya saka ya
raka jauhar gida, ta ɗebo kaya.
Suka tafi, jikinta duk a sanyaye.
"Dan Allah Nura kana ganin zai tashi?"
Ya ce "Eh mana, in sha Allah, shi fa master ɗan baiwa
ne, bar ganin abun da yake yi, yana da sa'a sosai da sosai in sha Allah zai
tashi "
"Amma ya aka yi aka yi masa haka?"
"Wallahi ban sani ba, wai dai husuma ce ta tashi a
wurin tattar sakamakon ƙananan hukumomi, amma ban san shi ya aka yi hakan ta
faru ba"
Jauhar ta ce "Allah ya sa ya tashi ya warke"
Ya amsa mata da "Amin"
Ko da taje gida, ta ɗebo kaya suka koma, Alluran da aka yi
masa sun fara sakinsa, ya na 'yan maganganu a hankali.
Ban da 'yar madara babu abun da yake kira, ta je ta zauna a
kusa da shi, ta riƙe hannunsa, ta kifa kai tana kuka mai ban tausayi.
"Gaskiya ƙanwa idan baki daina kukan nan ba sai kin
tafi gida, duk muna jin abun da ki ke ji, daurewa muke yi, ba gashi yana magana
ba ya kusa dawowa duka"
Ta girgiza kai "Yaya walid ba ka san me nake ji
bane"
"Mun sani, amma ki yi haƙuri"
Abbu ne yayi sallama, wanda jauhar ba ta taɓa tsammani ba,
ta dai gaya masa ne kawai, kar ace ba ta faɗa ba.
Da sauri ta tashi ta durƙusa ƙasa tana gaishe shi ya ce
"Jauhar sannu ya mai jikin?"
"Jiki da sauƙi Alhamdilillah"
Su Walid ma duk suka gaishe shi.
Ya ƙarasa gaban gadon, ya ƙura masa ido, ya ce "Ya aka
yi abun ya faru"
Tayi sauri ta ce "Zai dawo gida ne wasu suka yi masa
haka da daddare"
Kallon da su liti suka yi mata, ya sanya Abbu gane ƙarya
take yi.
"Yanzu ya ake ciki to?"
Walid ya ce "An yi aiki an cire wuƙar"
Ya jinjina kai ya ce "Alhamdilillah, Allah ya tashi
kafaɗunsa"
Suka amsa da "Amin"
'yar madara da yake ta maimaitawa ya sanya Abbu cewa
"Wace 'yar madara kuma?".
Gaba ɗaya suka kalli Jauhar, ta sunkuyar da kai cikin jin
kunya.
Abbu ya yi murmushi ya ce "Ikon Allah"
Nurse ta shigo, ta ba su takarda a sayo magani.
Abbu ya bayar da kuɗi aka sayo, ya din ga yi wa jauhar
nasiha a kan ta nutsu ta kwantar da hankalinta, dan har a lokacin tana kuka.
Sai dai wata nustuwa ta saukar masa, ganin Al'amin yayu
ƙalau da shi.
Har azahar suna tare da Abbu, daga bisani, ya ajiyewa jauhar
kuɗi, ya ce "Duk yadda ake ciki su kira shi.
Liti ne ya fita waje, ya kira P.A da wayar Al'amin, aikuwa
ya ɗaga.
Wata muguwar ashar ya narka wa P.A sannan ya ce "Saboda
kai ɗan haramun ne, nake kiran wayarka tun jiya, ka ƙi ɗagawa. Saboda baku da
mutunci daga kai har ubangidan naka, saboda kare ƙuri'arku, da ƙoƙarin hana
ƙona sakateriya, yara sun fi sha biyar suka rufar masa da sara, ban da Mu ma
akwai yaranmu a wurin da sai sun kashe shi, ka san ba maganin tauri yake sha ba,
bakomai ba. Ka tsaya ka saurareni ma jiyan ka ƙi, da ƙyar aka samo kuɗin yi
masa aiki, to wallahi ku saurari abun da zamu yi mu ma, wallahi hukumar zaɓen
zamu cinnawa wuta, uban kowa ma ya rasa. Zaka gane ba ka da wayo daga kai har
shi"
"Ka ga tsaya, duk na san a cikin yaransa ne, ku yi
haƙuri kun san yanayin halin da muke ciki ba a nutse muke....
"Halin da ku ke ciki ya fi rayuwarsa kenan? Ku
sauraremu nan da wani lokaci" ya kashe wayar.
Ya koma ɗakin da Al'amin yake, ya tarar da ya farfaɗo, har
an ɗaga shi zaune ma, jauhar ta haɗa tea tana bashi, sai dai idanunta sun gaza
daina zubar da hawaye.
Al'amin ya zuba mata ido ya ce "Abbu ya zo nan?"
Ta ɗaga masa kai alamar eh.
"Dan ke ya zo ko bani ba? Ke ki ka yi masa magiyar ya
zo?"
"A'a"
Walid ya ce "Liti mu ba su wuri, abun na baru ne"
"Master"
Ya kalleta, idanunsa sun yi ja, alamar yana jin jiki.
"Ba na ce ka daina yi wa kanka illa ba, ko dan saboda
ni? Sai zuciyata ta fashe hankalinka zai kwanta ko? In sha Allah kujerar nan ko
ya sameta sai ta zame masa masifa. Ban taɓa yi wa wani muguwar addu'a ba amma
na yi masa. Nayi nayi ka rabu da mutumin nan, ba mutumin arziki bane ba, amma
ka ƙi aishikenan gashi nan yanzu ka janyo mana wahala".
Ya lumshe idanunsa, dan ba ya son ya ga tana zubar da
hawaye.
Jauhar ba irin addu'a da ba ta ja wa indabo ba, dan shi ne
kanwa uwar gamin ƙara ta'azzara rashin jin Al'amin.
A washegari hukumar zaɓe, ta sanar da soke zaɓen ƙaramar
hukuma uku, ciki har da ta su Al'amin wadda kuma take ta indabo, sakamakon
tashe-tashen hankali da aka samu, da kuma ƙona wasu daga takardun da aka kaɗa
ƙuri'a.
Tuni P.A ya sanar da Indabo saƙon su Walid, kuma kansile
ƙanan hukumomin, babbar barazana ce ga nasarar indabon.
Babu shiri, washegari da daddare suka shirya suka tafi wurin
malamin su, da shi da P.A, malamin ya tabbatar musu da cewa, an samu tangarɗa a
aikin da aka yi ne, yarinyar da yayi amfani da ita, ta haura shekarun da ake
buƙatar, kuma a yanzu ba abun da zai iya yi musu, sai dai a bi wasu sabbin
dabarun, a samu a haye.
Suna tafe a hanya P.A ya ce "Honorable, wallahi
yakamata ka duba mai zamani, da ƙyar idan ba yaransa ne, suka tayar da tarzoma
ba, ka san dole zamu sake buƙatar su, mussaman yanzu da zaɓen ya zama
inconclusive".
Indabo ya ce "Matsalar yaron nan na ta ƙarewa
wallahi"
"To ya zamu yi, haƙuri zamu yi tun da muna
amfanarsa". Indabo ya amince da hakan, P.A ya kira liti ya tambaye shi in
da suke kwance
Al'amin so yake Jauhar ta zauna a kusa da shi, ya ji ɗuminta
su yi hira, amma alamu suka tabattar masa da fushi take yi, dan da tayi masa
abun da za ta yi masa sai ta koma gefe, ta ɗauki wayarta tana karanta
Alqur'ani.
Ga kawo-kawo ɗin da ake yi, kuɗin hannunta duk sun ƙare, dan
ma su liti suna tsaye suna tallafawa, kuma idan Abbu ya zo ya kan ba ta kuɗi,
duk da zuwan nasa biyu ne kawai.
Wajen ƙarfe ɗaya na dare ne, Ranar Walid da liti duk suna
nan, duk da da facemask, a fuskar Indabo sai da suka gane shi, suka tashi suka
ni bayansu.
Jauhar ta ɗaga kai ta kallesu, Al'amin ya buɗe idonsa da
yake a rufe a da.
Jami'an tsaron suka bashi kujera ya zauna, yana kallon
Al'amin da satar kallon jauhar.
Ta tashi ta ce "Lafiya?"
P.A ya ce "Baki gane ni bane, wanda ku ka zo wurina
lokacin yana prison, honorable ne wannan, ya zo da kansa ba saƙo duba shi"
ta haɗe rai sosai, kamar ya make shi ta huta haka take ji.
Ya sauke facemask ya ce "Sannu kin ji, ya mai
jikin?"
Shiru tayi tana cigaba da haɗe rai.
Ya kalli Al'amin ya ce "Wannan ce 'yar madarar
kenan?" Al'amin ya ƙura masa ido, bai yi magana ba.
Ya kalli Walid ya ce "Ba ya iya magana ne?"
"Yana yi"
"Dama cewa na yi bari na zo na ga yanayin jikin naka,
Allah ya ƙara sauƙi. Ban sani ba ko ka samu labarin an soke mana wasu ƙuri'un
abun bai yi daɗi ba, muna nan dai muna ta addu'a "
Ya karkace ya ciro kuɗi kaya guda, ya miƙawa jauhar ya ce
"Ga wannan a sai magani"
Ta girgiza kai cikin takaici ta ce "Ba ma so, ka riƙe
kuɗinka ni babban burina da fatana, ka fita daga rayuwar mijina, nima ina burin
na ga ya shiryu ya zama mutumin kirki, kai ne ka ke saka shi aikata duk wani
abu na rashin kyautawa. Idan ya shiga matsala kuma ka zame ka bar shi. Yanzu an
riga an cuce ni, an tsugunar da shi. 'ya'yanka su suka fi cancanta su yi maka
irin aikin da yake yi maka, tun da sun fi morarka, idan abun na Allah ne ka karɓi
takardunsa ka sama masa abun yi mana, amma babban burnku yaran wasu su sha su
bugu su sayar da rayuwarsu a banza gare ku".
Ɗaya daga cikin jami'an tsaron ya daka mata tsawa, ta ce
"Wallahi ko zaku kashe ni sai na faɗi gaskiya, nima 'ya ce, kuma na
cancanci zama da nagartaccen miji, na san akwai iyaye da yawa da suke da burin
ganin yaransu a hanya madaidaiciya amma duk hana hakan, ni dai dan Allah ka
rabu da mijina, ka ƙyalemu"
Maimakon ya ji haushi, sai yayi murmushin ya ce "P.A
wato duk isa da kwarjinin namiji ya je gaban mace, sai abun da Allah ya yi,
kalli Mai zamani a gaban matarsa. Aishikenan yarinya haryanzu baki san rayuwa
ba, wannan yanayin mafita kawai ake nema, ki daina yi wa manya rashin kunya.
Kuma mijinki zaki gaya wa ya daina abun da yake yi ba ni ba. Tun da a haka na
ganshi, ki karɓi kuɗin nan".
"Ba ma so, ba zamu karɓa ba" tayi maganar tana
kuka.
Ya miƙawa P.A kuɗin, ya karɓa ya miƙawa Viper, shi kuma ya
karɓa.
Indabo yayi murmushi ya fice da tawagarsa.
"Master ni ka dizga ka kunyata a gaban mutane, gara ka
cigaba da karɓar kuɗinsu kana shaye-shaye ana yi maka lahani, ni ko? Kai am
tired na gaji, ba zan iya ba na sare. Na ɗauka abun mai sauƙi ne, amma ya wuce
yadda nake tunani, you are not willing to change. Kana samun sauƙi gida zan
koma, na gaji da auren"
Liti ya ce "Subhanallah, dan Allah kar ki yi mana haka
anty ƴar madara, muna murna Allah ya saya mana shi, kuma ki tafi ki barmu, ba
fa shikaɗai ba har mu zamanki tare da shi muna amfana"
"Eh, kuma har da ku ai, kullum ku kuke ƙara haɗuwa da
shi, ku ke ƙara abun da bai kamata ba, Allah ya sa na mutu na huta".
Duk wannan abun, yayi burus yaƙi magana.
"In sha Allah, ba zaki mutu ba, ana mugun tare ai"
"Ba wani tare, ku daina shaye-shaye mana, kuma kullum a
kansa tsautsayi yake faɗawa, ni na gaji, yana warkewa tafiya zan yi na haƙura
da zaman da shi" tayi maganar tana kuka, har ta fara tari mai haɗe da
haki.
"Mai laya"
"Allah ya ƙara maka lafiya"
"Ayi walƙiya, sai da safe"
Walid ya ce "Iya wuya, yadda ka ke so haka za ayi"
suka tashi suka fice, ya juya ya saukko daga kan gadon.
Kamar ba ciwo ne a cikin sa ba, ya tunkaro in da take ya
zauna, ya ƙura mata ido tayi shiru ta sunkuyar da kai, tana haki sama-sama.
"Ki ka ce tafiya zaki yi?"
"Eh" ta bashi amsa kai tsaye.
"Yaushe?"
"Kana warkewa gida zan koma, tun da ba ka so na, kullum
cikin sakani ka ke a tashin hankali, na ce maka ba na son ka din ga zuwa in da
za a ji maka ciwo, amma ka ƙi, ka dizgani a gaban wannan mutumin. Wallahi ba
zan taɓa yafe masa ba, duk shi yake ƙara ɓata ka".
"Yanzu abun da ki ka yi dai-dai ne? Ubangidana ne fa,
ki ka tsaya kina yi masa rashin kunya".
A ƙule ta ce "Shi dai-dai ɗin yayi mini, ba dan Allah
ya yi da sauran kwananka a gaba ba, da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, ni
na rasa in da zan saka raina, abun da nake ta tunanin zan iya ashe ya fi
ƙarfina, shikenan".
Gyara zamansa yayi, ya janyota jikinsa, yana kissing ɗin ta
a hankali.
She's not in mood, ta so ta ƙwace, sai dai kuma raunin
jikinsa ya hanata yin hakan, kar ta fama masa.
A hankali ya cire bakinsa daga nata yana kallon ta, amma ta
haɗe rai tayi kicin-kicin.
"Ki gaya wa likitocin nan su sallameni gobe, ko kuma na
yi tafiyata"
Da sauri ta kalleshi ta ce "A hakan ba ka warke
ba?"
"Eh na gaji da yadda ake zuwa ana magana da ke, haushi
nake ji, shi kansa indabo shirun da nayi masa, shi ne mafi alkhairi da mummunan
naushi zan yi masa"
"Dan Allah ni ka daina taɓa ni, asibiti ne fa, idan
wani ya shigo fa?"
"To je ki rufe ƙofa ki dawo, zafi nake ji, ina buƙatar
fankata, lamba uku kawai, ba sai an ƙure mata gudu ba"
"Ko mafici ba zaka samu ba, ni rabu da ni" tayi
maganar tana sake ture shi.
Ya ƙi tashi ya din ga takura mata, duk dan ta sake ta ɗan
samu nutsuwa daga fushin da take yi.
"P.A wane mahaukaciya ne ya aura wa yarinyar nan mai
zamani?"
"Allah masani honorable"
"Ikon Allah, kalarta kalar muryarta, ai rannan na kira
ta ɗaga, kai ka ga yarinya zuƙeƙiya kamar ita tayi kanta. Amma kamar ta dace da
aikin da malamin nan fa ya bayar, ya aka yi ba ka yi mini zancenta ba, gashi
wannan an samu matsala"
P.A ya ce "Honorable, kai ka san ba kowane kaya ne yake
taɓuwa ba, idan aka taɓa wannan za a iya samun matsala, kuma na manta da ita ne
gaba ɗaya wallahi"
Indabo ya ce "Wace irin matsala? Ai tsaf za ta taɓu, ba
tare da ya sani ba, idan ma ya sani na san yadda zan yi da shi. Lallai 'yar
madara tayi kalar madarar sosai. Wannan yarinyar ita ce rauninsa kenan?"
"Sosai kam, dan alamu sun nuna yana mugun sonta"
Indabo yayi wani irin murmushi yana shafa tumbinsa.
Maƙwabtan su Jauhar sun yi mata kara, na zuwa duba Al'amin,
suka kakkai mata abinci, daga gidan su Baba ya je Saifu sai mama, sun je sun
duba shi, duk da maman ta gaggaya mata baƙar magana a kansa.
Satinsa ɗaya da ƙyar, ya uzzura akan lallai, sai an sallame
shi, haka aka sallame su suka koma gida.
Cikin ikon Allah, Indabo yayi nasara, bayan faɗi tashi, da
shige-shige yayi nasarar samun kujerar ɗan majalisa.
Har gida Abbu ya sake zuwa duba Al'amin, sai dai kamar wurin
jauhar ya zo, da ita suka ɗan yi hira, ya tashi ya tafi.
Hafsa kuwa abun duniya ya hanata sukuni, da ƙyar ta samu
Alhaji mu'azzam ya fara saurararta, sai dai yadda yake bin matarsa sau da ƙafa,
yake ƙona mata rai, sai abun da ta tsara yake yi a gidan, idan ba ta ga dama
ba, sai ya shafe kwana goma bai taka wurin Hafsa ba, amma kuɗi akwai su, komai
take buƙata akwai shi, sai dai fa tsakaninta da miji sai an ga dama a bata aro,
wataran yana wurin nata ma, za ta kira shi, kuma haka zai tsallaketa ya tafi
wurin matarsa, ga yaransa marasa kirki, sun rainata rashin kunya kala-kala.
Da ta matsa ma da ƙorafi, ya ce idan ta gaji ta tafi, shi fa
duk lokacin da ya zo wurinta, baya gane komai, haƙuri kawai yake yi shi ma, ta
ƙyale shi.
Ta gaji tayi yaji, Anty ta din ga yi mata masifa, a kan dan
me zata dawo gida, sai asirinsu ya tonu, dole ta cigaba da zama har zuwa
lokacin da za a samu mafita.
Al'amin ya warke sarai, ya cigbaa da harkokin sa, sai dai
jauhar kusan kullum tana gargaɗinsa a kan indabo.
Gashi ta riƙe masa wuta a kan yin salla a kan lokaci, da yin
azkar, har zama tayi ta ciro masa addu'oi na musamman ta rubuta masa su.
Ita kanta ta san ikon Allah ne, da ƙarfin addu'a da take yi,
da kuma yadda take bin sa da kyautatawa da biyayya, ya sanya take iya sarrfaa
Al'amin, har yake jin nauyin aikata wasu abubuwan saboda ita.
Da asuba idan ya je salla ya dawo, da kanta take ajiye masa
sigari, kara biyu ko uku, ta ce masa ya sha banda shan ƙwaya kuma.
Ta jira ya gama sha, yana ƙaurin yana komai, ta naniƙe masa
a jikinsa, dan mantar da shi damuwa, kewar kayan shaye-shayen sa.
Da daddare suna kwance, ta ce "Master, ka san abun da
matar nan tela tayi mini?"
Ya ce "A'a"
"Wai na cewa matar nan dan Allah, ta koya mini ɗinki,
idan ta yarda zan tambaye ka, na din ga zuwa, ta ce mini za ta yi shawara, wai
daga baya ta ce mini mijinta ya ce a'a bai yadda na din ga zuwar masa gida ba,
ko kara ba ta yi mini ba, duk wahalar da nake yi mata, wani abun ta biyani wani
sai dai na yafe kuɗin, na ji haushi dama kuma ba ta zo tayi mini jajen abun da
ya same ka ba"
"Saboda ni me mijin ya ce bai yadda ki je gidansa
ba?"
"Wallahi ban sani ba, na dai ji babu daɗi gaskiya, amma
ban san dalilinta ba"
Al'amin ya ce "Manta da ita, Allah ya baki wani abun da
ya fishi, uwar son kuɗi"
"To wa ya ƙi kuɗi master" yayi murmushi yana shafa
bayanta.
Da asuba, mutane sun fito daga masallaci, faruku tela ya ga
Al'amin a ƙofar gidan sa.
Gabansa ya faɗi ya ce "Lafiya kuwa?"
Al'amin ya ce "Saƙonka na ji, 'yar madara ta ce a koya
mata ɗinki ka ce a'a, fine idan na kuma ganin 'ya'yanka sun tako mini gida, sai
na daddatsa su, na zuba a leda na kawo maka.
Na kuma yi suspending ɗin shagonka, na wata guda, wallahi ka
buɗe sai an sassara mini kai" yayi tafiyar sa ya bar faruku a wurin, cikin
tashin hankali.
Ƙarshe sai da aka haɗa da zuwa har gida, magidanta suka zo
ban haƙuri, jauhar tayi mamakin abun da yayi, ita kawai hira tayi masa abun
miji da mata, amma ya je yana yi wa mutumin barazana. Ta ce zata yi masa magana
ba wani abu, malam faruku ya cigaba da buɗe shagonsa.
Ya dawo da daddare, ta sha kwalliya, kamar yadda ta kan
caccanza tare da ƙirƙiro da sabbin abubuwa, domin sabunta abubuwa da yawa a
rayuwar auren na su, saboda rage barazanar gundurar juna.
Ya nemi wuri ya zauna a falo, yana ta sauke numfashi, ta
fito ta na murmushi ta haye kan cinyarsa, ta zuba masa ido ya lumshe idonsa
yana ta huci kamar kumurci.
"Nawan" tayi maganar tana shafa sajensa.
"Yau kuma me aka sha haka? aka ƙi kulani" yayi
shiru bai ce mata komai ba.
"Master"
"Mmm"
"Me ka sha yau?"
"Wiwi"
Jauhar ta ce "Da me?"
Ya girgiza mata kai alamar babu.
"Ba ka saba ƙarya ba" ta saka yatsanta a bakinsa,
ta ciro guntuwar ƙwayar da take ƙasan harshensa, laɓɓansa sun yi fari.
"Ƙwaya ko? Meyasa. Na ce fa idan an ɓata maka rai ne,
ko kana cikin damuwa ka yi ta ambaton Allah, kana azkar, meyasa za aje a sha
ƙwaya, ka ɓata mini shirina na yau gaba ɗaya"
Babu tsammani, ya miƙe da ita a jikinsa, ya tafi da ita ɗakinsa,
rabi a buge yake, rabi a cikin hayyacinsa, yayi ƙoƙarin kissing ɗin ta, ta ce
"Ba zaka sumbace ni, da sauran ƙwaya a bakinka ba master, me aka yi
maka?"
"Mhmmm bakomai, i need you"
Ta ce "A hakan, a buge fa ka ke"
"Ina hayyacina, kin yi mini kyau ne sosai" kasa
hana shi tayi, ya gama ya cigaba da yi mata surutai.
Ta rungume kansa a ƙirjinta tana shafawa ta ce "Na san
wataran zaka daina master, Allah ya shirya mini kai mijina"
"Madarata"
Ta ce "Idonka biyu"
"Mmm"
"Me zaka gaya mini?"
"In sha Allah zan daina, ki cigaba da yi mini
addu'a" yayi maganar cikin muryar maye sama-sama.
"Addu'a kullum ina yi maka master, Allah ya nuna mini
ka daina"
"Madarata"
"Master na"
Ya ja jikinsa, ya kai bakinsa saitin kunnenta, ta yi shiru,
tana jiran ya yi mata magana.
Kawai ya fara murmushi, yana yi mata numfashi a kunne.
"Zaki koma makaranta"
"Allah ya ja zamaninka, godiya nake"
Cikin mayen ya sake cewa "Ki daina yawan kuka ba na
so"
"To ka daina sakani"
"Allah ya bani kuɗi na kai ki makka"
"Amin Mijina, da alama ƙwayar nan nishaɗi take
sawa"
"Ke ce nishaɗin nawa" yayi maganar yana dariya.
Ita ma murmushin ta yi masa, ya kwanta a gefenta, bacci ya ɗauke
shi.
Da Asuba ya rigata tashi, ya tasheta shi kuma yayi wanka
yayi alwala ya fita.
Da wani irin tashin zuciya ta tashi, kamar za ta yi amai, ta
danganta hakan da awarar da ta yi wa cin ƙoshi jiya da daddare ulcer ta tayar
mata.
A ɗakinsa ta yi sallar ta idar, idonta ya sauka a kan robar
cocala da ke gefen katifarsa.
A take ta ji idan ba ta sha coke ɗin nan ba, akwai matsala.
Ta ɗaukko, ta buɗe ta kafa kai ta fara sha, sai da ta shanye
tas, sannan ta ajiye jarkar, still ta din ga jin kamar za ta yi amai. Ta
yinƙura ta tashi, ta tafi banɗaki, ta yanke jiki ta faɗi, jini ya fara
gangarowa daga hancinta.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Al'amin a masallaci, magidanta suka tare shi suna ƙara bashi
haƙuri, a kan abun da ya ce wa faruku tela.
Ya koma gida ya shiga ɗakinsa, yanayin kwanciyar da ya ga
jauhar ne ya sanya ya tsaya yana kallonta.
"Wace irin kwanciya ce ki ka yi haka, ko baki da lafiya
ne?"
Ya ga shiru ba ta motsa ba.
Ya ƙarasa gabanta, ya ɗagota, gabansa ya faɗi, ganin
hancinta na ta zubar da jini, bakinta ma jinin ne yake fita haɗe da wata kumfa.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ya furta
cikin tashin hankali yana jijjiga jauhar.
Amma shiru ba ta amsa ba, ya ɗaga hannunta ya ga ya saki, ya
kai hannunsa hancinta amma babu alamar numfashi a tare da ita.
"Jauhar, meya same ki haka? Meya sameki ne?"
Jijjigata yake iya ƙarfin sa, amma ba ta motsa ba, kawai
idonsa ya sauka a kan robar cocala. Ya kai hannu ya ɗauka ta shanye komai tas.
A wurin Nura guduma ya ƙwace, ganin yadda ya haɗa uban
ƙwayoyi a ciki zai sha, ya ƙwace ya ƙare masa zagi, ya ce idan yana wannan haɗin
kashe kansa zai yi. Ya taho da shi gida ya ajiye a bayan katifar, ya kai kwana
uku a ɗakin, shi ya ma manta da ita a ɗakin.
Da sauri ya ɗaukota ya fito da ita falo, ya kwantar da ita,
ya fita da gudu, ya rasa wani gidan ma zai dosa, saboda ba shiga harkar mutanen
layin yake ba, amma kasancewar a kiɗime yake, ya saka ya nufi gidan wasila, dan
maigidan ya sai mota.
Wani irin mahaukacin bugu ya din ga yi wa gate ɗin gidan, ba
shiri mijin wasila ya fito daga shi sai gajeren wando, ya buɗe yana rarraba
ido.
"Ɗaukko mota matata babu lafiya" ya ce
"To" dan a yanayin fuskar Al'amin ko ba'asi ya tsaya tambaya, bai san
me zai yi masa ba.
Jin bugun gate ɗin, ya sanya wasu daga maƙwabtan su fitowa,
su ji ko lafiya.
Mijin Wasila ya fito da mota, yanayin halin da ya fito da
jauhar, ya sa gaba ɗaya jikinsu yin sanyi, dan babu alamar rai a tare da ita.
Mijin wasila ya ce "Bari ya taso matarsa a tafi da ita,
asibitin"
Cikin ikon Allah suka yi wa Al'amin kara, mussaman da jauhar
tana girmama su da jan yaransu a jiki, maƙwabcin mijin wasila ma ya shiga motar
ya ce su tafi tare.
Asibitin da ya taɓa kaita aka buɗe mata file suka tafi.
Suna tafe yana girgizata yana ta tashi.
"Malam Al'amin ka yi haƙuri, ka daina jijjigata kar ka
ƙara gajiyar da ita"
Al'amin bai bi takansa ba, ya riƙe hannun jauhar, "Dan
Allah ko motsi ki yi Zahra, dan Allah ki tashi" su dai duk suka yi shiru,
yanayin tashin hankalin da yake ta tattare da Al'amin ya ƙara bayyanar da
tsantsar soyayyar da yake yi wa jauhar.
Suna zuwa Asibitin, Al'amin ya nufi emergency da ita, sai da
aka bishi aka tambaye shi file numbern ta.
Mijin wasila ne ya biya kuɗin ganin likita, dan ba ya cikin
nutsuwar da za a tambaye shi kuɗi.
Likita ya ce "Malam, meyasame ta?"
Al'amin ya rasa ta ina zai fara.
"Guba ta sha"
"Guba kamar yaya? Wannan ma ai kamata yayi sai an zo da
'yan sanda, ya aka yi ta sha guba?"
"Ka fara ceto mini ranta, duk wani bayani na yi maka
daga baya, ka ceto rayuwar ta tukuna".
Likitan ya ce "Ai sai ka fara gaya mini meyafaru?"
Ya juya kan jauhar, ya duba pulse ɗin ta, tana bugawa a hankali.
Aka samo bandage, aka toshe hancinta, saboda jinin da yake
fita, aka ɗagota ƙirjinta a sama a kan gadon.
Likitan ya ce "A cire mata hijjabin nan"
Al'amin ya riƙe hijjabin, ya yi shiru.
Nurse ɗin ta ce "Malam ranta za a ceto, ka yi
haƙuri"
Mijin wasila ya cewa maƙwabcinsa su fita.
Suka fita daga emergency, kayan bacci ne kawai a jikinta,
doguwar riga iya gwiwarta.
Halin da take ciki, bai hana shi jin matsanancin kishinta
ba, likita kuwa aikinsa kawai yake yi, zuƙe jinin da yake bakinta, da kumfar da
take fita.
Sannan suka fara yi mata CPR, a hankali take ajiyar zuciya,
zuciyarta na ƙoƙarin responding.
Wasila ta ce "Likita wani jinin na bin ƙafarta"
Wani likitan aka kuma kira, aka tafi da ita scanning room,
nan suka ga akwai ciki, sai dai shi ma ya fita.
Al'amin ya rasa in da zai saka ransa, Nurses suna aikinsu,
likitoci na nasu, aka ce Al'amin ya fita ya ce wallahi ba zai fita ba.
Haka aka din ga ɗaga jikinta, ana ƙoƙarin tsayar da jinin da
yake fita ta ƙasanta, allurai kuwa tsira mata kawai ake yi, ban da wanda ake
zuba mata a cannula.
Al'amin ya ji da ma shi tsautsayin nan ya faɗawa ba jauhar
ba, ko a iya haka ta galabaita.
Sakamakon gwajin jini, ya fito jininta ya yi ƙasa matuƙa ana
neman a ƙara mata wani.
Ya fita hankali a tashe, mijin wasila ya ce "Al'amin ya
ake ciki?"
Idonsa jawur ya ce "Jini za'a bayar, ku bani aron waya
dan Allah, na kira a kawo mini kuɗi, da kuma wanda za su bayar da jinin".
Ɗaya maƙwabcin na su hadi ya ce "Ai sun ce sai an yi
depositing dubu hamsin za su ganta, mun je reception mun biya, yanzu jinin a
fara dubawa a namu, ko za a dace".
Ya ce "To, amma a bani aron wayar dai, na yi
kira".
Walid ya fara kira ya ɗaga da ƙyar ya ce "Maza"
"Kana ina ka nemo kuɗi ka zo asibitin da nake kai Ƴar
madara cikin hanzari ba ta da lafiya"
Tuni Walid ya ware ya ce "Meya same ta?"
"Ka zo kawai".
"Gani nan"
Likitocin suka kira Al'amin, suka zauna da shi suna tambayar
sa meyafaru da ita.
"Ƙwaya na ajiye a cikin cocacola ta ɗauka ta sha ba ta
sani ba"
"Kwanakin baya fa, haka nayi ta counselling ɗin ka, a
kan ka daina yi mata abun da yake saka jininta ya hau. Yau kuma ka bari ta sha
ƙwaya wannan sakaci ne baka kyauta ba, idan ka yi silar rasa yarinyar nan,
Allah ba zai barka ba"
Al'amin jikinsa yayi sanyi matuƙa.
"Ko ka san cewa tana ɗauke da juna biyu? Yanzu dai ciki
ya zube babu shi, kuma a shawarce, idan Allah ya bata lafiya, yakamata tayi
tsarin iyali, mahaifarta ta sake hutawa, dan ƙwayoyin sun yi wa jininta ƙarfi
fiye da kima"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ba zata sake ɗaukar
ciki ba kenan?"
"A'a zata iya ɗauka, amma a shawarce, mahaifarta ta
huta, dan ya yi affecting ɗin mahaifar, akwai buƙatar ta huta kan ta sake wani
cikin "
Daga shi har jauhar babu wanda ya san da cikin, tsananin son
da take yi wa yara, ya sanya ta mayar da boti kamar ɗan da ta haifa, dan ma
kwanan nan ya hanata ɗaukko yaran mutane, tayi ta fama da su tana yi musu
hidima.
Ya tashi jiki babu ƙwari ya fita, su Walid suka ƙaraso
Asibitin, a kiɗime suka nufe shi "Mai zamani ina take? Meyafaru?"
Bai ɓoye musu komai ba, ya gaya musu.
Cikin tashin hankali Walid ya ce "Amma wallahi ɗan
kutm..... Ne kai, wane irin hauka ne zai sanya ka ajiye abu in da zata ɗauka ta
sha, kuma ba ka gaya mata menene ba? Ka san jikinta ba zai iya ɗaukar abun da
yake ciki ba wannan ai hauka ne"
"Mai laya" yayi wa Walid tsawa.
Sai dai walid ya kuma narka masa ashariya ya ce "Ba za
a kiyayeka ɗin ba, idan ka ji haushi ka saka mini ƙarfe, idan ta mutu kai ka yi
asara, wannan ai ganganci ne da wauta"
Wata irin zuciya ta yinƙuro Al'amin, ya nemi ya huce
takaicin sa a kan Walid, amma Walid ma ya hayyayaƙo masa, dan ba ƙaramin
mutunta su Juahar take yi ba, yarinyar was very simple and innocent.
Security ne suka shigo, suna ƙoƙarin korar su Al'amin, suna
nema su tayar da hayaniya a cikin Asibitin.
Liti ya kalli security ya ce "ko dai ka ƙyale su, ko
abun ya ƙare a kanka"
Walid a fusace shi ma yake yi wa Al'amin martani
"Saboda ka ga ba ta da baki, iyayenta ba tuhumarka za su yi ba, shi ne
zaka yi musu ganganci da rayuwar 'ya, wallahi daga nan gidan su zan je na faɗa,
idan ma kashe auren za su yi, su ɗauke 'yar su" Al'amin kawai yayi shiru,
dan da makami a jikinsa sai ya yi wa Walid illa.
"A ina za a duba jinin?" Yayi maganar yana kallon
Al'amin.
Yayi masa banza yaƙi magana.
"Wallahi sai dai ka fashe, gaskiya ce sai na gaya
maka" ya ce "Liti zo mu duba ina ne za a ɗauki jinin".
Mijin wasila da suka koma gefe suna kallon sarautar Allah,
suka gaya musu in da lab yake.
Ba a samu irin jinin Jauhar ba, sai dai sun bayar da jinin
su leda biyu, aka tafi da shi babban asibiti, za a canzo da kalar nata jinin.
Suka shiga dudduba in da Al'amin ya shiga, aka nuna musu ɗakin
da jauhar take.
Suka yi sallama suka shiga, an lulluɓe ta da green ɗin
bedsheet, idonta a rufe hannunta biyu duka an saka mata ruwa.
Al'amin na durƙushe a gaban gadon, ya riƙe hannunta idonsa
yayi ja, fuskar jauhar ta yi yellow sosai alamar ƙarancin jini.
Walid ya ƙarasa ya dafa kafaɗar Al'amin ya ce "Mai
zamani, ka yi sakaci da wauta, amma ka kwantar da hankalinka in sha Allah za ta
tashi, ka yi mata addu'a. Ba a samu irin jininta ba, amma mun bayar da jinin za
a canzo, likita ya ce a kira ka"
Ya miƙe a hankali, suka fito, Walid yana ta cigaba da
rarrashin sa, ya ciro kuɗi a aljihunsa ya ce "Wallahi ka ga dubu ɗari da
hamsin aka samu, shi ma jarin kaya ne, na ɗebo su kawai, kuɗaɗenmu na hannun
mutane, kana ganin za su isa kuwa?"
Al'amin ya haɗiye yawu ya ce "Ban sani ba, maƙwabcinmu
ya bayar da dubu ɗari, sai a cire a bashi, in gani idan sauran za su isa".
Walid ya dafa kafaɗarsa ya ce "Ka yi haƙuri za su isa
in sha Allah, yanzu me ake buƙata kuma?"
Ya ce "Jinin dai muke jira a saka mata"
"To shikenan, zan je na sake lalubawa ko za a samu kuɗi,
ka yi haƙuri ka nutsu. Amma dole a sanar da iyayenta"
Al'amin ya ce "Wallahi babu wanda ya isa ya rabani da
matata, ka ma daina wannan tunanin"
"Nima ban ce a rabaku ba, haushi ka bani ne, Allah ya
taimake ka, na kiyayi mai zamani" yayi maganar cikin sigar girmamawa ga
Al'amin.
Al'amin ya daki kafaɗarsa ya ce "Get out"
Yayi murmushi suka fita da liti.
Mamaki sai da ya kama mutanen da suka gansu suna faɗa ɗazu.
Al'amin ya bawa mijin wasila kuɗinsa, amma ya ce kyauta ya
biya ba sai an biya shi ba.
Babban burin Al'amin bai wuce ya ga ta farka ba, da ya tuna
abun da aka ce na game da mahaifarta sai ya ji ya tsani kansa, sai kokowa yake
da zuciyarsa yaƙi bari haushin Nura guduma yayi tasiri a zuciyarsa.
Wasila ta koma gida, ta dafo musu abinci ta dawo asibitin.
Har la'asar Al'amin ya rasa nutsuwa, aka kawo jini aka saka
mata.
A gigice Nura ya zo asibitin jin abun da ya faru, sai dai ko
kallonsa Al'amin ya ƙi yi.
Ya rasa in da zai saka kansa, mussaman da ya ga juahar a
kwance ana saka mata jini, duk da tsananin kishi irin na Al'amin, Nura yana
good time da jauhar, mussaman yake zuwa idan tana da aike, ya karɓa yayi mata,
har kasuwa yake zuwar mata, sayen kayan beads da stone work.
Ta dafa abinci ta bashi, duk da yaron mijinta ne, kuma tana
aikensa, hakan bai hanata girmama shi ba, da yi masa nasiha wasu lokutan.
Ganin shi ne sila, a ƙoƙarin hana shi illata lafiyar sa da
Al'amin yayi tsautsayi ya faɗa kanta, ya sanya ya koma gefe yana kuka, saboda
ya firgita da yanayin da ya ganta kamar gawa.
Al'amin cikin tsawa ya ce masa ya fita ya bashi wuri.
Nura ya fita wajen ɗakin ya tsaya cikin damuwa.
Al'amin ya je gida, ya bar jauhar da wasila, ya je ya yi
wanka, ya ɗaukko mata kayan da za a canza mata.
Sai bayan sallar magariba ya dawo, ya tarar da Baba tare da
mama Anty zakiyya da kuma saifu a ɗakin, wasi ta goge mata jikinta, da taimakon
Nurses ta saka mata kaya.
Tsayawa yayi yana kallonsu, yana tunanin ma a ina ya san su.
Sai daga baya, ya tuna Baba, ya durƙusa ya gaishe shi, ya
amsa masa tare da faɗin ya mai jiki.
Ya amsa da "Da sauƙi" yana tunanin me Walid ya je
ya gaya musu.
Baba ya ce "Meyafaru ne? Wani ya je ya ce mana abokinka
ne shi, wai ka turo shi an kwantar da jauhar a asibiti, hankalinmu duk ya
tashi"
Al'amin ya ce "Ɓari ta yi"
Anty ta ce "Amma shi ne aka je aka ɗaga mana hankali,
ni wallahi na zata wani abun ne ya same ta ma".
Mama ta ce "Duk da haka, tun da aka kai ga ƙarin jini
tana jin jiki, Allah ya sa ba wani abun ne ya faru ba tayi ɓarin"
Al'amin bai ce komai ba, ya ajiye kayan hannun sa, dai-dai
lokacin Jauhar tayi wani yinƙuri zata faɗo daga kan gadon tana kiran
"Master kana ina?"
Cikin hanzari ya ƙarasa gaban gadon, suna rige-rige da shi
da Saifu.
Yayi hanzarin riƙe ta ya ce "Zahra"
"Master"
"Na'am sannu"
"Meyasame ni ne? Kaina fa zai tarwatse ciwo
master"
Babu kunya ya rungumeta ya ce "Zai daina, ki daina ɗaga
muryarki"
Cikin kuka ta ce "Master bana gani, duhu nake gani bana
ganinka" tayi maganar tana tittirza ƙafarta a kan gadon.
Ya ce "Zaki ganni in sha Allah, ki daina magana"
Al'amin ko a jikinsa, ya ttatara hankalinsa a kanta, Baba ya
ce "Waliyiyya, sannu kin ji"
Ta ce "Baba"
"Na'am jauhar"
"Baba kai ne ka zo bana ganinku, duhu nake gani,
makancewa na yi?"
Saifu ya ce "Baki makance ba, bacci ki ke ji, ki yi
shiru"
"Yaya saifu, bana gani fa"
Saifu ya ce "Bacci ki ke ji ne"
Cikin fita hayyaci ta ƙanƙame Al'amin ta sake cewa
"Master"
"Na'am madarata"
"Kaina zai fashe, ka riƙe mini shi da ƙarfi, marata ma
ciwo take yi mini sosai" tayi maganar numfashinta yana fita sama-sama.
Yayi ƙasa da muryarsa yana yi mata raɗa ya ce "Kina
jina" ta ɗaga masa kai.
"Ki daina magana, ki yi shiru baki da lafiya"
"To meyasame ni?"
"Zazzaɓi ki ke yi"
Ta ce "To, ka je sallar asubar ne?"
"Na je mana, har na yi mana addu'a"
"To ka riƙe kaina da ƙarfi ka yi mini addu'a, jikina ma
kamar an jona mini shocking nake ji"
Nurse ɗin da ta shigo ta ce "Malam ya ka ɗagata ana
ƙara mata jini, so ake ta kwanta"
Mama ta ce "Faɗowa zata yi daga kan gadon, fizge-fizge
take yi"
Nurse ɗin ta ce "Kwantar da ita, sai ayi mata allurar
bacci"
Ta rirriƙe Al'amin ta ce "Kar ka ajiyeni, idan na
kwanta bana iya numfashi".
Al'amin ya ce "To shikenan, ba zan kwantar da ke
ba"
Anty Zakiyya ta ce "Wannan wane irin ɓari ne, zai saka
mutum yayi ta surutai kamar mahaukaci?".
Nurse ɗin ta kalleta ta ce "Jini ta zubar sosai da
sosai, dan haka jikinta yayi weak, alluran da muke yi mata kuma, sune suke
burkita ta, dan haka ba abun mamaki bane ba".
Al'amin yayi ajiyar zuciya, jin yadda Nurse ɗin ta rufe musu
ainihin abun da ya faru.
Ita kuwa tayi hakan ne, dan tausayin yadda tun da ya kawo
jauhar yake ɗawainiya, ko da ganganci a lamarin yayi nadama.
Sai wurin sha daya suka tashi za su tafi, dan bayan allaurai
ƙarancin jini ya saka ta fara haki, athma kuma ta tashi, sai da aka sakata a
kan oxygen.
Sai dai daga baya ta zama stable, baba ya din ga yi mata
addu'a kan su tafi ya ce tsakanin mama ko Anty Zakiyya wani ya kwana da ita
Al'amin ya je gida.
Al'amin ya ce "A'a baba, zan kwana da ita ba wani
abu" dama yanayin fuskarsu ya nuna ba su yi niyya ba.
Baba ya din ga yi masa addu'a, sannan suka tafi.
Har suka je gida, suna mamakin kulawa da tashin hankalin da
suka gani a tatatare da Al'amin.
Su Walid ma a reception suka kwana, da an ce a nemo abu, za
su fita su sayo, shi kuma yana tare da ita yadda ya ga rana haka ya ga dare.
Lokaci -lokaci tayi ta surutu, duk a dalilin mugun ƙarfin da
ƙwayoyin suka yi mata.
Daf da asuba ta sake farkawa, sai dai ba ta zaburar, wannan
karon tana gani, sai dai daga kwance ma jiri take yi.
"Master" ya ɗago daga kifa kan da yayi, ya ce
"Sannu zahra ya jikin?"
"Alhamdilillah, jiri nake ji".
"Ki yi haƙuri, kin ga jini ake ƙara miki. Zaki
daina ji in sha Allah, sannu" yayi maganar yana shafa kanta, yana yi wa
Allah godiya da ta farfaɗo.
Da sassafe Nura ya sake dawowa, har da guzirin bredi da
madara da suga, ya dawo sake duba Jauhar, amma al'amin ya kore shi.
Liti ne ya dawo da shi ya ce "Haba maza, Nuranka ne fa,
waye ba ya kuskure? Kar ka yi masa haka dan Allah, kuma sakacin naka ne ba na
sa ba, daka karɓa kamata yayi ka zubar ai, dan Allah ka yi haƙuri"
Nura har da kuka ya ce "Dan Allah yaya Aminu ka yi
haƙuri, dan Allah wallahi ban ji dadin abun da ya faru ba"
Daga kwance ta ce "Master, laifin me ya yi ka ke korar
ƙaninka, ayi haƙuri dan Allah, kalli ka saka yana kuka"
Al'amin ya ce "Ki daina magana kar hakin ya dawo"
"To ka ce masa ka haƙura, ka ga kuka yake yi"
A hankali ya furta"Ya wuce"
"Yauwwa mai zamani, Allah ya ja zamanin maza" tayi
maganar tana ɗaga hannunta da ƙyar ta taɓa fuskarsa.
Cikin jin daɗi yadda take ƙarfin hali, yayi murmushi ya ce
"Ban hana ba?"
Murmushi ta yi masa ba ta ce komai ba.
Da nurse ta shigo ta tarar da ita, tana magana, ga su liti a
gefe ta ce "Zahra gawa taƙi rami, sannu kin ji"
"Yauwwa Anty na gode "
Ta kalli Al'amin ta ce "Congratulations, na tayaka
muranr farfaɗowarta, dan wallahi mun sare bamu zaci zaki tashi ba"
Walid ya ce "Sannunku da ƙoƙari, Allah ya biya ku"
"Amin, bari mu gyara mata jikinta, a bata abinci "
su liti suka fita, ya taimakawa nurse ɗin, ta gyara jauhar, ta zaunar da ita,
duk da tana ta kuka da jiri da ciwon kai da na mara.
Ya haɗa mata shayi, da buredi, sai dai ta kasa ci, sai lallaɓata
yake yi.
Wasila tayi sallama, suka amsa.
Ta ce "Alhamdilillah anty jauhar jiki yayi kyau, ikon
Allah"
Nan suka ƙara gaisawa, ta ajiye abincin da ta zo da shi,
jauhar ta ce za ta sha kunun gyaɗar da ta kawo.
Ana haka su Baba suka zo, suka tarar da Al'amin yana ba ta
abinci an zaunar da ita.
Gab ɗaya zamansu a wurin, bai hana shi tattalin matarsa ba,
dan gani yake yafi kowa sa'a farfaɗowar da ta yi.
Babban abun da ya yi wa jauhar daɗi, bai wuce ganin 'yan
gidan su, sun zo dubata ba, ko ba komai sun nuna damuwar su da ita.
Duk saifu na ta zuga Baba ya bi diddigin yadda aka yi tayi ɓarin,
ko dukanta Al'amin yake yi, amma yanayin yadda suke mu'amala ita da Al'amin ya
sanya kowa yin wani tunanin daban, dan saɓanin abun da ake tunani ake gani.
Har Abbu sai da ya zo duba jauhar, su shahida ma duk sun zo,
Baba sai da ya yi ta yi wa wasila godiya da Addu'a, tana ta ƙoƙari da jauhar,
maƙwabtan su ma na ta zuwa dubata.
A kwana na uku, da daddare take tambayar Al'amin
"Master wai dan Allah meya same ni ne? Na san kawai na ga lemo a ɗakinka
na sha, daga nan ban san meyafaru ba, kuma na ji ana cewa nayi ɓari, ya aka yi
na yi ɓari ai bani da ciki, ko kuma ina da shi ban sani bane? To yaya aka yi ya
zube?"
"Ki yi haƙuri, likita zai yi miki bayani in sha
Allah"
"To kai ka yi mini mana, wai shikenan babyn yanzu babu
a cikina" tayi maganar tana shafa cikin ɗauke da damuwa.
"Ni likita ne?"
"A'a amma ka gaya mini, haryanzu ina da cikin?"
Al'amin ya ce "Wai abun da baki san da shi ba ma, zaki
bi ki damu, ki yi haƙuri za su yi miki bayani"
Ta ce "To shikenan, yi mini addu'a na yi baccin".
Ya ce "To"
Gari ya waye, su surayya ma suka zo dubata, saifu ya kawo
su, take tambayar ina yaya hafsa, aka ce mata ta tafi umara.
Jauhar ta ce "Dan Allah ku ce ta yi mini addu'a sosai
da ni da master"
Suryaya ta ce "Wai ke kowa na gaya wa miji sunan 'yan
gayu ke kina master"
Tayi murmushi ta ce "Baki ga mastern ne ba? Kuma ai mu
ba 'yan gayu bane"
Kasancewar Al'amin ba ya ɗakin ya sanya saifu cewa "Ke,
ki faɗa mini gaskiya, wani abun yayi miki ko?"
Ta ce "A'a me ka gani?"
"Wallahi ki ka rufa masa asiri sai kin daku, har likita
na saka baba ya tambaya, ko dukanki yayi ya ce babu alamar duka a jikinki da
aka kawo ki"
Jauhar ta ce "Master ba ya duka, bai taɓa dukana
ba".
"Na san halinki da shegiyar gwaninta ne, da kare mai
laifi ki gaya mini gaskiya"
"Wallahi babu abun da ya yi mini"
Dawowar Al'amin ya sanya su yin shiru, ya ƙarasa gaban
gadonta ya ce "Me zaki ci?"
"Bakomai, kawai a sallame ni"
Ya zauna a gefen gadon ya ce "Ba na son rigima, wace
irin sallama kuma?"
"Kai ka koya mini ai, kai fa har guduwa ka ke daga
asibiti"
Yayi murmushi ya ce "Zaki gudun kenan?"
Ita ma murmushin ta yi ta ce "Kashe kuɗin yayi yawa,
ina iya tashi ai"
Rarrashin ta ya din ga yi, dan shi kansa ya san zaman
asibiti da gundura.
Sai da ta kwana shida, an saka mata jini ya kai leda biyar,
sannn aka fara zancen sallamar ta ranar.
Daga likitan sai ita da Al'amin a ɗakin, yayi mata bayanin
abun da ya faru, tare da gaya mata akwai buƙatar ta huta kan ta sake ɗaukar
ciki.
Ya yi wa Al'amin faɗa a kan ya kiyaye sosai da sosai, wannan
karon sun rufa masa asiri idan ya ƙara faruwa.
Jauhar ta sunkuyar da kai, sai kuka.
Likitan ya ce "Menene? Meyafaru? Kuma?"
Al'amin ya ce "Bakomai, zamu yi magana da ita"
Likitan ya rubuta musu sallama ya fita.
Yana fita ya ce " 'yar madara menene kuma?" Shiru
ta yi masa ta cigaba da kuka.
Duk yadda ya rarrasheta, tayi haƙuri ta ƙi yin magana.
Baba ya zo da mota, ya ɗauke su ya kai su gida, ya yi ta yi
wa Al'amin godiyar ɗawainiyar da ya yi ta yi da jauhar a asibiti, yayi musu
sallama ya tafi.
Al'amin ya zauna kusa da jauhar ya ce "Dan Allah ki
gaya mini menene?"
"Komai ma, kawai ka janyo na rasa babyna, kuma wai ba
zan haihu yanzu ba, wataƙila ma ba zan sake haihuwa ba".
"Subhanallah kar ki yi mana wannan fatan, zaki kuma
haihuwa cewa suka yi kawai ki bayar da tazara saboda yanayin jikinki".
Cikin kuka ta ce "Ai da ka daina shan Wannan abubuwan,
duk da ba haka ba. Kawai ka ja na yi asara ga jinina ya ƙare, kuma wai ba zan
haihu yanzu ba"
Cikin tsananin nadama yake rarrashinta, sallamar mutane ya
sanya ya tashi, 'yan dubiya suka din ga zuwa duba jauhar.
Al'amin na ta hidima da ita, da sassafe yake tashi ya yi
aikace-aikace, girki ne kawai sai maƙwabta sun shigo suke yi mata.
Shahida ma ta yi ƙoƙari sosai, dan tana zuwa ta taya jauhar
aiki, a haka suka saba.
Guduma ya sake zuwa har gida ya duba jauhar, tare da gaya
mata abun da ya faru.
Jauhar tayi masa nasiha sosai a kan shaye-shaye.
Al'amin ya fara bata tausayi, har rama yayi sosai, mussaman
daina kula shi da tayi, sai yayi ta kame-kame.
Yau da ya dawo, normal ta karɓi abun ta.
Har ya tafi ya kwanta, ta bishi ɗakinsa.
Ta hau gadon ta kwanta ta ce "Master"
"Mmm"
"Ka yi haƙuri dan Allah, komai ya wuce na ji babu daɗi
ne kawai shiyasa kawai"
Ya ce "To"
"Kayi magana mana, ba to ba"
"Ina jin babu daɗi, missing babynki da ki ka yi, ki yi
haƙuri laifina ne"
"Ba fushi na yi dan cikina ya zube ba, fushi na yi
saboda bani ba har kai kana yi mini ganganci da rayuwarka, ka daina dan Allah
for our own good and safety"
Ya ce "To in sha Allah"
"Yaya za a sha fankar ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Likita ya ce ki huta tukuna kar
ki sake ɗaukar ciki".
"Sun yi mini allura ai, ko haryanzu ba ka jin
komai"
Ya ce "Da ɗin ma ina ji, mazewa nake yi, a madadin
hakan sai in sha in bugu in manta da ke"
"Master nawa nikaɗai, daga ni ba ƙari"
"A'a saura uku"
Ta ce "To ga fili ga mai doki nan ai"
Ya ce "Filin da dokin naki ne ai, ki yi yadda ki ke so
madarata"
***
Jauhar ba ta samu damar yin jamb ba, saboda rashin lafiya,
dan haka Al'amin ya samu indabo ya ce A alƙawarurrukan da ya yi masa, yana son
ya samawa jauhar admission, tare da samawa Nura guduma aiki ko na direba ne, a
manyan ma'aikatu.
Al'amin ya daina shigo da duk wani abu na shaye-shaye gidan,
ko zai yi a iya waje yake tsayawa yayi abun sa.
Jarin su duk ya ƙare a asibiti, dan haka ya yanke wata
shawara a ransa.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Jauhar ya fara samu da maganar, da daddare suna tare ya ce
"Na ce ba"
"Ka ce me ranka ya daɗe?"
"Wani abu na yanke ne, ina son na samu Abbu, ya bani
gadona na wurin ummi, in sayar da abun da zan sayar na karɓi kuɗi a wurin
indabo na haɗa na fara wata sana'ar ina son barin sayar da wiwi gaba ɗaya".
Tayi murmushi ta ce "Alhamdilillah, tunani mai kyau,
amma ba a yadda ka gaya mini haka zaka je ka gaya wa Abbun ba ko?"
"A yaya zan gaya masa?"
"Cikin kwantar da murya, zaka yi masa bayani, ka san
iyaye sai ana lallaɓa su, ka sani ma ko ya kai ka kasuwa?"
Ya ce "Ko ya kai ni ba na so, ya je ya cigaba da riƙe
'ya'yan matar can. Dama alhkina ne ya sa yanzu ba shi da kuɗi kamar da"
Jauhar ta ce "Haba master, Abbun ka ke gaya wa haka,
kai zaka ji daɗi ka haifi ɗa yayi maka haka?".
Cikin ko in kula Al'amin ya ce "Duk tsanani, ba zan yi
wa ɗa na abun da yayi mini ba"
"Master ka san shiga tsakaninka aka yi da Abbu, dan
Allah ka daina irin wannan maganar".
Yayi mata shiru, ta sake cewa "Master yaushe zaka kai
ni mu gaida su Hajiya?"
"Ba rana? Tun bayan kawo ki sun kuma zuwa?"
"Hmm master, Allah ya baka damarmaki, duk da ka rasa
ummi da yaya sadik, da kuma uban gidanka. Ko yaya dole nan gaba yaranka su so
ganin 'yan uwanka, dan da dangin uba ake ado. Ni fa duk wannan abun da ake yi,
bani da wayo sanin mahaifiyata ta rasu, ba 'yar gari bace, yar jalingo ce, ba a
taɓa kai ni garinsu ba, ba a taɓa nuna mini ko mutum ɗaya a danginta ba, kuma
ban taɓa ganin kowa ya zo daga garinsu ba. Da na fuskanci babu uwata a gidan,
na nemi ba'asin in da take, baka ga dukan da mama tayi mini ba, ban haƙura ba
na tambayi baba, amma ya ce idan na kuma yi masa zancen dangin mamana, sai ya
zane ni. Yadda yake nunawa da yadda su mama ke faɗa yana son mamana, amma nayi
mamakin yadda yaƙi yadda a kai ni garin su na ga ko 'yan uwanta, da naga ba ya
so kawai na daina maganar. Kai kuwa da ka rasa uwa akwai makwafinta, yakamata
mu je mu ga hajiya mu gaisheta, ni ba wanda zan kalla na ce daga wurin dangin
mahaifiyata yake".
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Kuma ba ki san a ina take a
jalingon ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, kawai iya abun da na
sani kenan"
"Shikenan, zamu je mu gaida hajiya, amma sai na tambayi
Abbu in da take a tofan ba zan iya tunawa ba"
"Yauwwa maigidan Allah dai ya iya maka, ya goyi bayanka
yayi maka jagora "
Ya shafa fuskarta ya ce "Amin madarata"
"Yauwwa milona"
Ya ce "Ga madara ga milo, sai Shan shayi" suka yi
dariya tare.
Washegari da safe bayan sun karya, ya bata magunguna ta sha,
tana ta lallaɓa jikinta, za ta yi aikace-aikacenta, ya hanata ya fito ya yi
mata share-share, har tsakar gida ya wanke mata.
Kayan da ta cire yake wankewa, aka buga ƙofa, ya je ya buɗe
hafsa ya gani a tsaye, hannunta riƙe da leda.
Ya bata hanya ta shigo, a tsorace ta kalli Al'amin fuskarsa
a haɗe ta ce "Ina kwana"
"Lafiya ƙalau".
"Dan Allah wurin jauhar na zo" da hannu ya nuna
mata falo.
Daga falon ta ce "Muryar wa nake ji kamar Yaya
hafsa"
Ta ce "Nice"
Ta tashi ta taro hafsa ta ce "Sannu da zuwa".
Hafsa ta ce "Yauwwa sannu ya jiki?"
"Jiki Alhamdilillah, ya aka yi ki ka gane gidan?"
"Yaya saifu ne ya gaya mini hanya, kuma direbana da
yayi tambaya aka nuna masa gidan ba wuyar ganewa".
Ta ce "Allah sarki yaya hafsa tun ina Asibiti nake
tambayar kina ina, aka ce mini kina umara, na ce baki gaya mini ba muna chat,
ai da na jero addu'a ayi mana ni da mai gida"
Tayi murmushi ta ce "yanzun ma an yi miki, wai jauhar ɓarin
da wahala ne, na ga kin rame haka kin yi fari?"
"Kai da wahala mana, jini na zubar sosai shiyasa na yi
haka, amma kwanaki ai ƙiba na yi sosai, ashe ciki ne ban sani ba"
"Allah sarki, Allah ya kawo mai amfani, sannu"
"Yauwwa ai na warware "
Al'amin ya shigo falon, jauhar ta ce "Master ba ka
ganeta ba ne? Yayata ce da muka je gidanta fa, ba ka ga muna kama ba?"
Kai tsaye ya ce "Na gani, kin fita kyau"
Jauhar ta ce "Kai fa ka fiye son kai ta ina?"
"Ta ko ina" yayi maganar yana shigewa ɗakinsa.
Hafsa tayi murmushi ta ce "Aikam kin fi mu kyau ai duk
gidan nan"
Jauhar ta ce "Rabu da shi, shi ma faɗa kawai yayi"
suka cigaba da hira, ya sake fitowa ya shirya tsaf zai fita.
"To yau me ki ke so? Kayan cikin ko ganyen wanne ki ke
so?"
Ta shagwaɓe fuska ta ce "Kai"
"Ni ki ke so?" Ta ɗaga masa gira tana murmushi.
"Aikuwa zaki kwana da yunwa, me ki ke so?"
"Komai ka samu na gode"
Ya ce "Abun da zai ƙara miki jini aka ce ai"
"Jininka zan sha" ta yi maganar tana dariya.
Yayi murmushi ya ce "You are not serious, ki yi addu'a
Allah ya sa na samu kuɗi, na sayo miki kaza".
Hafsa ta ce "Ai ga miya ma na yi miki, da kazar a
ciki"
Jauhar ta ce "Ashe zaku yi faɗa da master, tun da ki ka
riga shi kawo mini kaza"
Murmushi ya sake yi, wanda ya bawa hafsa mamaki, take bin su
da kallo, gwanin burgewa.
Har zai fita ta ce "Master"
Ba tare da ya juyo ba ya ce "Kar na yi shaye-shaye da
yawa, kar na yi faɗa da kowa, banda rigima da mutane" ta kwashe da dariya
ta ce "Au ka haddace ma kenan, addu'a zan yi maka ai, Allah ya iya maka,
ya goyi bayanka yayi maka jagora ya wadatamu da halal ya nesanta mu da
haram"
Ya waiwayo ya ce "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, 'yar
aljannata" ya juya ya tafi.
Yana fita Hafsa ta ce "Innalillahi, jauhar dan Allah ya
aka yi ki ka canza mutumin nan, dariya fa yake yi miki, kalli yadda yake yi
miki, dan Allah jauhara ya ki ka yi ki taimake ni" tayi maganar cikin
tsananin damuwa.
Jauhar ta ce "Ban fahimci in taimake ki ba yaya hafsa,
meyafaru? Wannan ai normal ne tsakanin ma'aurata, kodayeke shi ya koya mini
rashin kunya, da ko kallonsa bana iya yi a gaban mutane"
Idon hafsa ya cika da hawaye ta ce "Jauhar, wallahi tun
da na auri Alhaji mu'azzam hankalina bai kwanta ba, bai taɓa bani awa biyar
cikakkiya ba. Sai abun da matarsa take so yake yi, bai tare a ɗakina ba sai da
matarsa ta amince. Ga kuɗin yana da su, yana kashe mini ya sakar mini amm ba su
nake so ba, kulawarsa nake so da lokacin sa".
Juahar ta ce "Yaya hafsa ba fa abun da ki ke kalla a
film ne soyyaya ba a ƙasar hausa da wurin mijin bahaushiya, dole ki fara kallon
wane irin mutum ne shi, kin ga mijinki mutum ne mai hidindimu da yawa, ba zai
yiwu ace kullum yana da lokacinki ba yakamata ki din ga yi masa uzuri"
"Uzuri jauhar, yana da lokacin matarsa da yaransa, gaba
ɗaya auren ya fita daga kaina, na je na gaya wa anty, wai wallahi na ɗaga
maganar nan, sai ta yi mini Allah ya isa, wai zan saka ayi mata dariya, na zama
kamar hoto a wurinsa, ko ɗan abun ɗokin nan na amarci, duk fa ban san su ba. Ke
da ki ka auri wanda ake yi wa kallon sai a hankali, babu imani da tausyai a
zuciyarsa kalli abun da yake yi miki fa. Ni dai dan Allah idna wani malamin ne
da ke, ki haɗa ni da shi"
Cikin damuwa jauhar ta ce "Yaya hafsa ni wallahi ban
san in da ake ganinsu ba ma, canza mutum daga wani abu da baka so zuwa wani, ba
abu ne mai sauƙi ba. Kin san ni irin wahala da gwagwarmayar da na sha kafin mu
zo wannan matakin kuwa?
Da fari nima damun kaina na din ga yi, daga baya na kama
addu'a babu dare babu rana, na haɗa da biyyaya da kuma haƙuri.
Master mutum ne, kallon da mutane suke yi masa daban, wanda
nake yi masa daban, biyayya da addu'a ne suka canza mini shi. Alkhairin da yake
yi mini nake kalla kullum, nake yi wa laifukansa uzuri, har gara ke kina da uwa
a raye, ni daga ni sai Allah, da na san bani da wata mafita, na bi abun da
ƙaddara ta zaɓa mini, na rungumi abuna hannu bibbiyu. Kuma Allah ya shiga
lamarina Alhamdilillah, mijina talaka ne, amma ba kowace mace take da ikon da
nake da shi a gidan aurena ba. A zahiri shi nake bawa girman, shi ne jagoran
amma a baɗini ni ce sitiyarin rayuwarsa, ina fatan kasancewa da shi har
aljanna. Ke ma ki nutsu ki gano menene kurakuranki, sai ki gyara".
"Ba wani kuskure, ina kyautata zaton asri aka yi mini
wallahi "
"A'a yaya hafsa, ki daina faɗar haka, ki miƙa wa Allah
lamuranki, wallahi zaki ga canji "
Duk yadda jauhar ta so nusar da Hafsa muhimmancin haƙuri da
juriya, da dagewa a kan addu'a amma taƙi ganewa kuma taƙi yadda.
Zuwa azahar ta tafi, ta yi wa jauhar uban farfesun kaji, da
abinci, ta kuma ajiye mata kuɗi ta tafi.
Har a lokacin ba ta yadda har da hakkin jauhar a abun da
yake faruwa da ita ba.
Al'amin ne zaune a gaban Abbu, tun da ya gaishe shi, yayi
shiru.
Abbu ya ce "Ya jikin 'ya ta?"
"Da sauƙi"
Abbu ya ce "To Alhamdilillah yarinyar kirki, 'yar
aljanna Allah ya ƙara mata lafiya, matso ka haɗa shayi ga kayan breakfast
nan"
Sai da Al'amin ya kalli Abbu, ya girgiza kai ya ce "Na
ƙoshi"
"Too, yau kai ne ka ƙoshi da abinci kuma?"
Ya bashi amsa da "Eh na ci a gida"
Abbu ya yi murmushi ya ce "Na manta ne, ashe fa
magidanci ne, ya aka yi?".
"Sonake a sayar da gadona, zan ja jari, sana'oin da
nake yi, ba sa iya riƙe mu sosai, gashi ina so ta koma makaranta, babu isasshen
kuɗi a hannuna.
Sai kuma ina son ka bani full adress ɗin hajiya, zan kaita
ta gaisheta ta matsa a kan haka"
Abbu yayi shiru yana ƙarewa Al'amin kallo, duk ya ɗan yi
sanyi daga wani rashin mutuncin, babu uwar sumar da yake tarawa da faratan da
yake bari zaƙo-zaƙo, gashi yadi ne a jikin sa saɓanin da, da idan bai ga dama
ba da 3quater yake yawo da shirt damatsansa a waje, ya wani nutsu sosai.
Abunka da uba da ɗa, wani irin shauƙi ya ji yana kama shi, a
yadda ya ga tarin sauye-sauye a tattare da Al'amin.
"Kai amma 'yar nan tawa ta kyauta, amma wace sana'ar
zaka yi?"
Al'amin ya ce "Da wurin buga bulo nake so, ko wurin yin
buredi, amma ban gaya mata ba tukuna, ban sani ba ko tana da wata
shawarar"
Abbu ya numfasa ya ce "Kana ji na Al'amin, tsawon
shekarun nan, filayenka sun yi daraja sosai da sosai, idan ka bari suka ƙara
kwana biyu sai sun fi haka sosai. Ka je ka rubuto business plan ɗin ka kawo
mini, tare da list ɗin abun da za ayi mata na makarantar, sai na baka kuɗin,
idan Allah ya dafa maka, aka samu cigaba, sai a sayar da ko gona ce a garinsu a
ƙara, ka san kana da wasu kadarorin a tofa"
Al'amin ya ce "A'a ni ba na son ka yi mini abu, daga
baya azo a saka ka din ga yi mini gori, kawai dai a bani wanda na san nawa ne,
kuma ma ni na fi son registration nayi mata da kuɗina da kaina, sai na fi
alfahari da haka"
Abbu ya ce "Gaskiya ne, kamar ba a nan ka zauna kana ce
mini, ba ka son auren ba"
Al'amin yayi shiru yana basarwa.
"Ka rubuto business plan ka kawo mini, zan san abun yi,
ka je ku yi shawarar ina jiranka.
Gaba ɗaya haushi ya cika Al'amin, kawai ya ji ba shi ne ba
zai yi ba, ya ce "Ina ne gidan hajiya a tofa"
Abbu ya kwatanta masa, ya tashi ya fita.
A waje suka yi karo da Rahila, bai ko kalli in da take ba ya
fice.
Ta shiga gidan da sauri, ta samu Abbu "Yanzu na ga
Aminu ya fita, Allah ya sa ba wani abun ya aikata ba?"
Abbu yayi murmushi ya ce "Al'amin ai rigima ta ragu
yanzu, duk da wata rigimar ya zo yayi mini ya tafi. Wai gadonsa yake son a
bashi, saboda yayi sana'a ya kula da matarsa" gabanta ya faɗi, ɗan kuwa ba
ƙaramin harin filayen nan take yi ba, manyan filaye ne awon gwamanti ga gidaje
guda uku. Ko da Abbu ya samu karayar arziki bai taɓawa Al'amin su ba.
"Wace irin sana'a kuma, wallahi kar a sayar, ba shi da
shi a ina ya samu kuɗin sayen leshin dubu tamanin ya bata ta saka, kalli a
asibitin da ta kwanta fa na kuɗi, kalli uban kaji da naman da aka kawo gidan
nan da salla, duk ba shi da kuɗin yayi haka? Ni ban taɓa zaton zai iya zama
soko har haka ba a kan mace wallahi, yanzu saboda kula da itan ne za a sayar da
wannan wuraren?"
Abbu ya ce "Ba dai nasa bane ba, shi ya ga zai iya
ai"
Jauhar ta lallaɓa ta cigaba da sana'oin ta, yanzu tana iya
aikace-aikacen ta, ta gama aikin, ta idar da sallar magariba, ta ji bugunsa.
Ta buɗe ta kalle shi, ta ce "Malam lafiya ka ke yi wa
mutane wannan bugun haka?"
"Zance na zo"
"A me ka zo"
Ya ce "Ƙafata"
Ta ce "Ko keke ba ka da shi ma?" Ta fito ta zauna
a kusa da shi, a kan barandar gidan malam lawan ta ce "To me ka kawo mini
"
Ya ajiye baƙar leda ya ce "Gata nan gyaɗa ce marau,
suyar yau mai zafi"
"Ka rasa me zaka kawo mini sai gyaɗa, anya ka na so na
din ga fitowa zancen nan" ya saka hannu zai ɗauke ledar, ta riga shi ɗaukewa
ta ce "Allah ya shiryeka, Allah master da da kanka a ka bari ka samo matar
aure, za a sha wahala kan ka samu"
"In ji wa? Farinjini fa zan yi "
"A hakan kana muzurai da zare idon? Kan na saba da kai
fa na daɗe, tsoro ka ke bani da sosai "
Ya ce "To yanzu fa?"
"You are my best friend ever, sauƙin kai ne da kai fiye
da yadda ka ke tunani, miskilanci ne kawai matsalarka wuyatta na dafa abinci
mai daɗi shikenan an wuce wurin "
Suka kwashe da dariya tare, a kan barandar gidan, suka
cigaba da hira, suna cin gyaɗa, kasancewar a cikin duhu ne, babu wuta, yake ba
gaya mata yadda suka yi da Abbu.
"To yanzu wanne zaka yi a ciki, wace sana'ar zaka
yi?"
Ya ce "Rabu da shi, idan muka je ƙauye zan saka a nuna
mini gonakin, a sayar da wata na karɓo kuɗina"
"A'a kar ka yi haka master "
"Haka fa za a yi, wallahi ba zai taimaka mini ba muddin
shegiyar matar nan ta sani, ban da ina duba darajar amintar da suka yi da
marigayiyya, wallahi da sai na tsinke mata laka"
"A'uzibillah, wannan wace irin magana ce?"
"Mu bar wannan maganar, ɗaukko key ki rufo gidan mu
fita yawo " ta ce to.
Ta rufe gida, ya goya ta a babur, suka tafi ya din ga zaga
gari da ita, ya kaita gidan su, ya ce ta shiga ta gaisa da baba mintuna goma ta
fito, saboda ya lura shi ne kullum yake kiranta a waya, yana tambayarta ya
jiki.
Baba ya din ga murna, ganin ta warware, baba da kansa ya
rakota, suka gaisa da Al'amin, ya yi ta yi musu fatan alkhairi, da fatan samun
wani rabon mai amfani jauhar ta yi shiru, shi kuwa ya amsa da Amin.
Ba su da wurin zuwa, ya cigaba da zagaye da ita, suna tafe
suna shan iska, ya saya mata kayan ciye-ciye, su rake, awara, dafaffen ƙwai
kasancewar dama ba iya cin abinci take yi ba.
Har wurin sha daya sannan suka koma gida, ya ci abinci.
Ganin yana ta kaiwa da komowa tsakanin falo da tsakar gida,
bayan sun yi shirin kwanciya, ya sanya ta gane shaye-shaye yake son yi.
Ta kalleshi ta ce "Master ka je ka sha, amma kaɗan dan
Allah, ba da yawa ba, kar ka bugu" ya ce "To"
Ya fita tsakar gida yayi abun sa ya gama, tana jin sa ya
shiga ɗakinsa yana wanka, ya fito ya saka turare ya nufo ɗakinta, duk da yana ɗan
warin sama-sama amma ƙamshin turaren ya hana warin yin tasiri.
"Ba ki yi bacci ba?"
Ta ce "Ban yi ba jiranka nake, na san ko na yi sai ka
tashe ni"
"Allah sarki madarata" yayi maganar yana
rungumeta, ya kwanta da ita a jikinsa.
"Wace sana'ar ki ke ganin zan fara?"
"Ka yi tunanin ko kala uku ce, sai mu yi addu'a Allah
ya zaɓa mana mafi alkhairi "
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Babu laifi"
"Masterna, kai zaɓin Allah ne a gare ni, na gode Allah
da bai sanya ni cikin masu yi masa butulci ba".
Ya ce "Ni ɗin?"
Ta jinjina masa kai. Nan ta bashi labarin hafsa, ya ce
"Allah ya ƙara, alhakinki ne ai, daga har ke turin jeka ka mutu suka yi
mana mussaman ke, Allah ya ƙara"
"Master yayata ce fa"
"Koma wacece, ai Allah ba ya barin zalunci".
"Duk da haka master"
"Ni yanzu dan Allah da gaske kina jin daɗi rayuwar da
muke yi a haka?"
Ta ce "Gaya mini matar da aka taɓa goyawa a tarihi, aka
yi tafiyar da aka yi da ita a baya, saboda ba ta da lafiya? Gaya mini matar
talakan da ake ajiyewa masu kula da ita? abubuwa da dama da mata suka rasa a
gidan aure ni na samu".
"To ai wannan duk ba wani abu bane ba a kan wanda ki ka
din ga yi mini, dan Allah kina jin daɗin zamanmu a haka? Just recently kin kusa
rasa ranki saboda ni?"
Ta ce "Ba laifinka bane ba ai" ya yi murmushi
cikin jin nishaɗi, yake ƙoƙarin canza hirar zuwa wani abu daban".
"Master"
"Mmm"
"Ban taɓa jin ka ce kana so na ba, ko dai kara kawai ka
ke yi mini, saboda halaccin da kake iƙirarin na yi maka?"
"Nima baki taɓa gaya mini ba, kuma ina yi a aikace ai,
ba dan haka ba, babu wanda ya isa ya saka na zauna da ke ai".
Tana dariya ta ce "Sai abinci"
"Ki kiyayeni da abincin nan, kina takura mini fa"
Ta shafa bayansa cikin shagwaɓa ta ce "Ba ka ce
ba"
"Me?"
"Ka na so na"
"Yanzu dai jirani tukuna, na gama caji, koma menene ya
biyo baya".
"Ba zaka yi cajin ba, sai ka gaya mini"
"Yanzu na tashi na yi waje, zan je na yi wanda na saba,
na manta komai, yanzu zaɓi ɗaya"
"Ni zaka yi wa wayo ko?"
"A'a ba wayo zan yi miki ba, zaɓi na baki".
Da safe jauhar ta fito falo, ta tarar da Al'amin a kan
kujera, ta ce "Master da me ka yi wanka ne a banɗakina?"
"Sabulu"
"Wanne?"
"To ai abubuwan naki ne da yawa, kuma kina bacci kawai
na ɗauki na wata roba, na zuba a soso"
"Master feminine wash ne fa"
Ya kalleta ya ce "Me ke nan?"
"Abun kama ruwa ne, dan Allah yayi kama da abun
wanka?"
Al'amin ya ce "Kai, wallahi tsirfarki tayi yawa, kama
ruwan ma, sai an yi masa wani abu, to sai ki din ga rubutawa a jikin
robar"
Cikin shagwaɓa ta ce "Gaskiya sai ka saya mini wani,
dubu uku fa na saya".
"Iyee dubu uku, ke fa wasu lokutan kin iya damfara,
dubu uku, wannan abun ne dubu uku, car wash ne fa"
"Morning fresh ne, wai car wash kuma yasin sai ka biya
ni, ina jin daɗin amfani da abuna fa, kai da ba a gyarawa ka din ga lallaɓowa"
"A daina gyarawar, a bar mini abuna a haka, ko kuma ki karɓi car wash"
"Sai fa ka biyani, wuyatta na soya maka wainar fulawa
da zoɓo mai sanyi, sai ka zazzage mini komai na aljihunka"
"Ai dama kin saba cin zalina, ki kwashe mini kuɗi"
***
Tun sassafe jauhar ta shirya, kasancewar yau za su tafi
tofa, gidan Hajiya, duk da ya ce wuni kawai za su yi da yamma su dawo gida, ba
ta damu da hakan ba, tun da dai ya amince za su je ɗin.
Ta zata tafiyar mai nisa ce sosai ma, sai dai ba su daɗe ba
suka isa garin, kwatancen babu wahala, suka isa har gidan Hajiya.
Da ta amsa sallamar su ba ta gane su ba, sai daga baya ta
gane Al'amin.
Cikin hanzari ta tashi tana yi musu sannu da zuwa.
"Al'amin, dama zaka tako ka zo in da nake?"
"Tun da ke kin watsar da ni ko?"
Ta ce "Ba haka bane, ku shigo"
"Amarya, ki yi haƙuri ban sake zuwa ba, ina ta fama da
ciwon ƙafa, kuma ina tsoron wulaƙancin matar mahaifinka, ko lokacin bikinka, ba
ka ga abun da ta din ga yi mana ba, mahaifinka ma haushina yake ji, shiyasa na
janye jikina daga gare ku"
Jauhar ta ce "A'a hajiya ki yi haƙuri, ai laifin wani
ba ya shafar wani, mu dai zamu din ga zuwa muna neman albarka"
"Allah sarki, aure mai gyara mutum, yanzu a dalilin
auren ya sanya ka zo in da nake"
Al'amin ya ce "Eh, ba dan ta matsa ba ba zan zo ba
gaskiya, tun da kema ba ƙaunata ki ke yi ba".
Jauhar ta ce "Master ya haka kuma?"
"Ba ƙarya nayi ba,
ki ke zare mini ido"
Sai hajiya ta kama kuka, ta ce "Wallahi da gayya ba zan
yi haka ba, ina son 'ya ta ina son ku, amma an yi mini iyaka da ku, kusan
kullum sai na yi kukan abun da mahaifinku yayi mini a kanku".
Jauhar ta ce "Dan Allah hajiya ki yi haƙuri, ki yafe
musu, ke ce makwafin uwa a wurinsa dan Allah ki daina kallon abun da suka yi
miki".
Al'amin ko a jikinsa, dan ita kanta tsohuwar haushinta yake
ji, yadda laifin abbu ya shafe su a wurinta.
Daga baya kuma cikin hikima, jauhar ta din ga jan su da
hira, kasancewar ranar kasuwar garin take ci, har kasuwa suka je sayen ƙwan
zabi, Hajiya ta haɗa wa jauhar sha tara ta arziki ta ce ita da jauhar take
jikar, shi kuma ya je ya ƙarata.
Yayi mata zancen gonakin mahafiyarsa, ta ce masa
"Hayarsu ake bayarwa ana noma, duk shekara ana karɓar kuɗin, mahaifinka
bai bani damar zama da shi mu yi magana a kan hakkinka ba, amma kuɗinka suna
nan ana tara su, ƙanina ne yake ajiyewa, sai dai ya je Lagos yanzu"
"Idan ya dawo zan dawo nima"
"Allah ya kawo ka lafiya, kuɗi ne masu kauri sosai
kam".
Sai yamma sosai, sannan suka koma gida.
Ana ta kiran sallar magariba sannan suka shiga gida.
Da daddare har sun yi shirin kwanciya, Anty zakiyya ta kira
jauhar a waya, jauhar ta ɗaga ta ce "Anty lafiya kuwa?"
"Ban sani ba, wallahi jauhar ba kya tsoron Allah, kina
so ki gama da duniya lafiya kuwa?"
Cikin tashin hankali ta ce "Anty me na yi,
lafiya?"
"Ban sani ba, yadda mugun abun uwarki ya koma kanta,
kema da yardar Allah sai naki ya koma kanki".
"Anty haryanzu baki gaya mini me nayi ba?"
"Asirin da ki ka yi wa hafsa, gashi an dawo da ita
gida, tana ta fizge-fizge tana kiran sunanki, wallahi ki gaggauta karya abun da
ki ka yi mata, kafin mu gauraya da ni da ke, baƙar annoba kawai" ta kashe
wayar.
Cikin tashin hankali ta fita falo tana kuka, ta ce
"Master"
"Yes yaya"
Cikin kuka ta ce "Ka tashi ka kaini gida".
"Meyafaru a gidan?"
"Ka kaini gida kawai, ba zan iya bacci ba, wai an ce ni
na yi wa yaya hafsa asiri, wai sai ihu take yi, tana kiran sunana, wallahi ni
ban yi mata asiri ba".
Tashi yayi zaune ya ce "In ji uban wa?"
"Anty ce ta kira ni, dan Allah tashi mu je, wallahi ban
yi mata komai ba" tayi maganar tana wani irin kuka.
"Na ga alamar sai na taka wa 'yan gidan nan naku burki
a kan zaƙewar da suke yi, ba Zamu je yanzu ba, sai da safe, zan je ni su yi
mini bayani"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin kuka ta ce "Ni dai dan Allah ka tashi mu je, kar
ayi mini wani sharrin ina zaune ban sani ba, dan Allah ka tashi mu je"
"No ba in da zamu je, sai da safe idan Allah ya
kaimu"
Kuka ta din ga yi masa, har sai da ta ƙular da shi, ya daka
mata tsawa, ya korata ɗaki, daga kuka kuma numfashi ya nemi ya tafi gaba ɗaya,
sai da ya ɗaukkota ya fito da ita tsakar gida, ta kwanta ya din ga yi mata
fifita.
Kusan dai ba su yi baccin kirki ba.
Washegari da safe shikaɗai ya karya, hankalinta gaba ɗaya a
tashe yake, ta kasa cin abinci, sai wajen goma sannan ya ɗauketa suka tafi
gidan.
Ita ta fara shiga gidan da sallama, ba kowa a tsakar gidan,
duk sun tafi makaranta yaran gidan.
A ƙofar falon baba tayi sallama, ya amsa mata ta shiga ta
tarar da shi a zaune yana dudduba wasu takardu.
"Waliyiyya, lafiya na ganki a yanzu menene?"
Kawai ta je gabansa ta zauna tana kuka, hankali a tashe ya
dafa kanta ya ce "Menene? Wani abun ne ya haɗa ki da mijin naki? Wani abun
yayi miki?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
Mama ta shigo falon, tayi turus, ganin jauhar a gaban baba
tana kuka.
"Ikon Allah, sakinki yayi ne ko wani abun ne ya faru,
ki ke wannan uban kukan haka?"
"Yana waje ma"
"Yana waje meyafaru?" Gaba ɗaya ta kasa magana.
Ya kalli mama ya ce "Tashi tijjani ko saifu, su je su
ce masa ya shigo" mama na fita, ya kalleta ya ce "Gaya mini kafin ta
dawo"
Kasa magana ta yi, da ta buɗe baki za ta yi, sai haki.
Mama ta dawo ta zauna, mintuna kaɗan Al'amin ya shigo da
sallama, sanye da baƙar jallabiya.
Cikin girmamawa ya gaida baba, amma mama ko kallo ba ta ishe
shi ba.
"Malam Al'amin, meyafaru da iyalin naka ne? Ko wani
abun ne ya haɗa ku?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a, lafiya ƙalau nake zaune da
ita, dama na rakota mu zo mu ji ba'asin kiran wayar da aka yi mata ne jiya da
daddare, da har ya hanata bacci. Bana son ace na yi wani abu na rashin
kyautawa, amma zan iya cewa wannan zai iya zama zuwanta gidan nan na ƙarshe
kuma bana buƙatar kowa ya je in da take, in dai har za a cigaba da tafiya a
haka".
Baba ya ce "Duk me ya yi zafi haka? Baka faɗi meyafaru
ba"
"Baba kwanaki yayarta ta zo ta dubata, a gidan na fita
na bar su ma tare, na manta sunanta, amma wadda ta auri wanda za ta aura da,
kwatsam jiya da daddare an kirata a waya, wai waccan ɗin an dawo da ita gida
babu lafiya, tana ihu tana kiran sunanta wai ta yi mata asiri, kwana tayi tana
wannan koke-koken ba ta bari mun yi baccin kirki ba, wane irin asiri ana zaune
ƙalau?"
Cikin tsananin ɓacin rai ya ce "Zakiyyan ce ta kira ki,
ta ce kin yi wa hafsan asiri?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
Ya tashi ya fita tsakar gida, yana ƙwalawa zakiyya kira.
Mama tayi wani irin mugun murmushi, sannan ta maze ta cigaba
da sallalami.
Tana mutsutsuka ido ta fito ta ce "Lafiya ka ke yi mini
wanan kiran, ka san jiya ba mu yi baccin kirki ba, saboda jikin hafsa".
"Yanzu kin kyauta, abun da ki ka yi?"
"Na me fa?"
"Ɗaukar waya ki kira jauhar, wai ta yi wa hafsa asiri,
wannan wace irin magana ce?"
"Amma ai ba ƙarya nayi ba, tun da aka kawo ta sunanta
kawai take kira ai"
Ihun da hafsa take yi ne ya sanya, suka nufi ɗakin gaba ɗaya,
ciki har da jauhar.
Sai fizge-fizge take yi, tana kiran sunan jauhar.
Jauhar ta ce "Yaya gani nan, kin ganni menene"
tana jin muryar jauhar ta hau miƙa mata hannu.
Ta ƙarasa ta ce "Gani menene, me ya same ki?"
"Jauhar, ji nake kamar na fita da gudu, ai ke na gaya
miki abun da yake damuna, dan Allah ki gaya musu ko zasu yadda, Anty taƙi
fahimta ta, ni a kashe auren nan na huta, bana son kuɗin, bana son auren.
Wallahi jauhar an kai wata guda bana iya bacci saboda ɓacin rai kullum sai na
sha maganin tari rabin kwalba, nake iya bacci.
Bani da nustuwa, babu walwala da kwanciyar hankali yaya zan
yi ne? Ta mallake komai, ban ishe shi kallo ba, yanzu kuma ji nake kamar in
fita da gudu, kamar ana yagar naman jikina" tayi maganar tana wani irin
kuka mai tare da gunji.
"Yaya hafsa magnin tari ki ke sha dan ki yi bacci, ai
ni ba ki gaya mini ba, shaye-shaye fa ki ka fara kenan"
"Ni ki gaya musu a kashe auren nan, ba zan koma ba na
gaji" tayi maganar tana buge-buge. Babu kunya Al'amin ya tsallako, ya
janye jauhar gefe, saboda kar tayi mata illa.
Asirin da zakiyya take gudun tonuwarsa, ya tonu kowa ya
gani.
Baba ya girgiza kai ya ce "Kowa ya sai rariya, ya san
za ta zubar da ruwa, ki tsaya a nema mata magani, wannan abun da take yi babu
lalallai wani asiri ne, wataƙila shaye-shayen da take yi ne".
"Haba ya zaka ce haka? Wannan surutan da take yi ba fa
a hayyacinta take ba, balle a tabattar da abun da ta faɗa gaskiya ne"
Al'amin ya ce "Amma ki ka yadda ita take yi mata asiri,
count her of this please, kar a ƙar sakata a wannan maganar"
Baba ya ce "Al'amin kama hannun matarka ku tafi, in sha
Allah hakan ba zata sake faruwa ba"
Jauhar kuwa kuka ta din ga yi wiwi, har da roƙon Al'amin ya
bari ta zauna, amma ya ƙi ya ce sai dai su tafi gida.
Saifu kuwa ya ce "ba dai kuna murna kun cuci marainiya
kun aura mata ɗan wiwi ba, kun aurawa taku mai kuɗi, ai ga reshe nan ya juye da
mujiya".
Jauhar har sai da ta ji haushin Al'amin, na hanata zama a
wurin 'yar uwatta.
Aka rasa ainihin abun da yake damun hafsa, shaye-shaye ne?
Sihirin ne ko aljanu aka kasa gane kanta, wasu lokutan babu magana abinci ma
taƙi ci sai kuka, da daddare ta kasa bacci tayi ta koke-koke tana ihu kamar
mahaukaciya.
Iyaka Alhaji mu'azzam ya zo dubata, ya zube musu uban kuɗi
ya tafi.
Jauhar ta samu admission a legal, ta fara karanta shari'a
law, indabo ne ya bata scholarship, sauran hidimar makaranta kuwa shi yake yi
mata.
Har keken ɗinki, ya samo mata a irin wanda Indabo yake cewa
zai rabawa mata goma, amma ace an bawa mata ɗari, ya ce ba zai bashi ba, sai
idan ya yadda za a ɗauki hoton jauhar da keken a saka a social media.
Ya ce babu wanda ya isa ya ɗauki hoton matar sa, ya saka a
social media, a kan wani keken ɗinki kuma sai an bata.
Indabo ya ce wa Al'amin, ya saka yaron da ya ce a samowa
aiki a abuja, an samu gurbin direba a wata babbar ma'aikata top 10 na Nigeria,
tare da albashi mai tsoka ya ce ya kai takardunsa na sakandare da aka ce yayi.
Guduma bakinsa ya ƙi rufuwa, saboda tsantsar farinciki da
murna ta gaske, jin zai tafi Abuja aiki, alhalin idan da wanda ya kamata ya
tafi, shi oga kwata-kwatan ne.
Mahaifiyar Nura, sai da ta zo tun daga garin da take aure,
ta zo ta yi wa Al'amin godiya, tare da jauhar, dan Nura duk ya bata labarin
irin zaman da suke yi da su.
Jauhar ta mayar da hankali a kan karatu sosai, duk da a gefe
guda tana yi wa Al'amin magiyar shi ma ya koma makaranta. A kaso ɗari yanzu
babu kaso arba'in na shaye-shaye da neman rigima da Al'amin yake yi.
Ya shiga ya fita, aka bawa unguwar su sabuwar transformer
daga wurin indabo, lokacin da ta su ta lalace, a cewarsa 'yar madara ba ta son
zafi.
Har burji aka yi wa unguwar aka gyara musu kwatocin
layukansu, aka zuba musu burji a manyan hanyoyin su.
Abu kamar wasa, sai 'yan unguwar suka fara girmama Al'amin,
ganin cigaban da suke samu a dalilin sa, duk da wani abun Indabo ba a son ransa
yake yi wa Al'amin ba, dan dai kawai ba shi da yadda zai yi da shi ne.
Aka bashi kuɗin sa na garin tofa, na gonakin mahaifiyar sa,
kuɗi ne masu yawa, ya yi wa jauhar gyaran gida sosai da sosai, ya canza mata
wasu abubuwan, ya saka mata talabijin, dan ma tana hana shi yi mata wasu
abubuwan, saboda kar kuɗin su ƙare a banza.
Ya buɗe wurin sayar da shayi, a can unguwar su, liti zai din
ga kula da wurin, ko Abbu bai san ya buɗe wurin ba. Ta saka shi sun yi addu'a
sosai a kan buɗe wurin.
Al'amin ya cewa jauhar tafiyar ggagawa ta kama shi zuwa
Lagos, juyin duniya ya gaya mata me zai je yi, ya ce mata bakomai, zai je ya
duba ne, idan da wani abun da zai iya sayowa ya zo ya sayar a kano.
Kafin ya tafi, wasu irin mahaukatan karnuka ya ajiye a
layin, su uku masu faɗan tsiya, malam lawan ya tambayi dalilin ajiye wannan
karnuka da suke barazana ga rayuwar su.
"Tafiya zan yi, gadin mata ta za su yi mini"
"Amma banda abun ka, ai Allah ne zai kareta ba karnuka
ba"
"Meyasa ka gina gida ka saka matrka a ciki, duk da ka
san cewa Allah ne zai kare maka ita, ba ka bar ta a titi ba?" Yayi shiru.
"Kar ka sake shiga harkat da abun da nake yi na gaya
maka"
Ita kanta jauhar da fari ba ta ma san saboda ita aka ajiye
su ba, ita kanta tsoronsu take ji, gashi sun san lokacin da take dawowa daga
makaranta, a bakin titi take tarar da su, da sun ganta, sai biyu su shige gaba,
ɗaya kuma yana bin ta a baya.
Sai da yayi kwanaki takwas a lagos, sai dai kullum su yi
waya amma still bai gaya mata me ya je yi ba.
Wurin shayin su liti kuwa, jauhar ita ce yin meatpie,
cin-cin, dafaffen ƙwai ne, duk abun da ya samu yi take yi, a lokacin ana
processing tafiyar Nura guduma bai tafi ba tukuna, shi yake zuwa ya ɗauka ya
kai.
Ko ta tsiri yin awara bayan magariba ko wainar fulawa, ya ɗauka
ya kai can wurin shayin, kasancewar matasa na taruwa a wurin, sai dai ya kawo
mata kuɗinta an saye.
Ta ce "Nura ina yi maka murnar tafiyar nan, amma ta
wani fannin ni aka yi wa"
Ya ce "Wallahi ni kaina na fara kewar ku, na san a can
babu abinci mai daɗin naki"
Tayi dariya ta ce "Halinka ɗaya da yayan naka ai".
Ranar da Al'amin ya dawo kuwa, ta sha tsaraba, har maƙwabta
sai da suka samu.
Ga kyakykyawar tarba da ya samu daga wurin Uwargida sarautar
mata.
Hafsa kuwa haka nan aka sasanta, bayan ta ɗan samu sauƙi aka
mayar da ita gidan Alhaji mu'azzam, sai dai ba a wani samu sauyi ba, a kan
abubuwan da suke faruwa, a baya damuwa da take yi mata yawa ya sanya take shiga
tashin hankali, amma tun da ta samu maganin damuwarta ta hanyar shan magunguna
masu sanya bacci, sai ta yi overdose yadda za ta bugu sosai ta manta duk wani
abu da yake damunta.
Dawowar Al'amin ya zo da kuɗaɗe, kuma ya ƙi gaya mata yadda
aka yi ya same su. Ba ta zargin sa, dan ta san ba ya taɓa kayan wani, duk abun
da zai kai shi ga taɓa abun da ba nasa ba, ba ya ci.
Cikin ikon Allah, tun zuwan da suka yi tofa, hajiya take
zuwa kawo musu ziyara, da wasu daga dangin mahaifiyar Al'amin.
Ana ta shirin tafiyar guduma babban birnin tarayya, ya ce ya
fasa ba zai je ba, mahaifiyar sa ta zo har gida ta gaya wa Al'amin, dan bai
gaya wa Al'amin cewar ya fasa zuwan ba, mamansa ya je ya gaya wa.
Mai unguwa yana ta barbaɗa an yi wa nura hanya zai tafi
Abuja aiki.
Al'amin ya sa aka nemo masa Nura guduma, ya tambaye shi,
menene dalilin sa na fasa tafiya.
Ya girgiza kai ya ce "Bakomai"
"Ban gane babu komai ba, idan ka zauna a nan ɗin uwar
me zaka ci ko ka yi, iyayenka na murna ka samu wurin da zaka rufawa kanka asiri
ka ce ba zaka je ba, saboda me?"
"Babu komai".
A fusace Al'amin"Zan fasa maka kai, ka buɗe baki ka yi
mini bayani, meye dalilin da ya sanya lokaci ɗaya ka ce ka fasa tafiya? Duk
yaran da suke ƙarƙashina babu wanda na ɗauka na zaɓa sai Kai ka watsa mini ƙasa
a ido?"
Yayi shiru.
"Ba magana nake yi maka ba"
"Yaya bakomai"
Jauhar ta ce "Master, ka kira shi indabon a waya, ko
cire sunansa suka yi? Ko wani abun ne ya faru, tun da ai da murna yake yi zai
tafi".
Yana huci ya kira wayar indabo, yana ɗagawa ya ce "Yaya
aka yi Nura ya ce ya fasa tafiyar nan, ko akwai matsala ne?"
Indabo ya ce "Shi zaka tambaya, su kusan bakwai ne,
ranar juma'a za su tafi, a kai su wuraren da za su yi aiki, ni ban ma san ya
fasa ɗin ba, P.A ne yake kula da shirin tafiyar su".
Al'amin ya kashe wayarsa, ya ce "Ba ka da wani dalili
ko hujja, dan haka tafiya ranar juma'a " Nura yayi shiru.
"Ba magana nake yi maka ba?"
Ya ce "To in sha Allah "
Bayan tafiyar sa, Jauhar ta ce "Master da ka ƙara
matsawa ka bincika, babu yadda za ayi ace da farko yana ɗokin tafiyar nan,
lokaci ɗaya kuma ya ce ya fasa, anya babu lauje cikin naɗi?"
Ya girgiza kai ya ce "Iskanci ne kawai, maybe abokai
suke ziga shi, idan ya tafi can zai zama busy sosai, ba zai samu isasshen
lokacin yin rashin ji ba".
Ta ce "Eh to, zai iya yiwuwa Allah Ubangiji ya tsare
shi, ya sa sanadin shiriyar kenan. To kai ma master a samo maka mana"
Ya kalleta ya ce "Wa?"
"Kai mana"
"Kema kin san ba zan yi ba"
Ta ce "Amma ai na ga ba ka raina sana'a komai
ƙanƙantarta"
"Ba sana'ar na raina ba, ba zan ɗauki duk wani nau'i na
rashin mutunci bane, kema kin sani"
"Haka ne kam, shiyasa nake mamakin yadda ka ke yi wa
indabon nan, yake ƙyaleka, yadda suke wulaƙanta mutane wasu lokutan"
Yayi murmushi ya ce "Ni da shi wannan kar ta san kar ne
ai"
"To ayi amfani da takardunka mana, a samo maka
aikin"
Ya ce "Ni fa aikin ne ba na so, da zan yi da tun kan
maigida dodo ya ware, da na yi, kuma uwa uba yanzu na ajiyeki, yaushe zan iya
nesa da ke?"
Ta kwantar da murya ta ce "Master nema babu in da ba ya
kai mutum, ka taimaka mana"
"Ba in da zani, ina maƙale da ke, ga wurin shayi Allah
ya dafa mana, wurin bulo ma zamu buɗe, indabo nake jira, shi zai sai injin
bugawar"
"Ubangiji Allah ya taimaka ya dafa, idan Nura ya tafi,
kai zaka din ga kai mini kayan sayarwa ta wurin shayin"
Yayi dariya ya ce "Ai idan ma cewa ki ka yi na sayar
miki zan sayar madarata, balle kuma kaiwa kawai.
"Sannu mijin ta ce"
"Bakomai, normal ne" suka cigaba da hira cikin
nishaɗi.
Al'amin ya tattara Nura sai da ya tafi, Jauhar kuma haki ya
addaba mata, wasu lokutan tana makaranta, za a kira Al'amin ace masa an kai ta
Asibiti babu lafiya.
Sati ba ya zuwa ya shafe, asma ba ta tayar mata ba, kusan
kullum suna hanyar asibiti, har ta fara tsoron kar ya fara gajiya. Sai dai sam
ba ta ganin alamar gajiyawa, ko ƙosawa a tattare da shi.
Ga jiri ga haki, abinci ma gagararta ci yake yi, ga ciwon
mara da ya sakata a gaba, period ɗin ya ƙi zuwa sai kaɗan ta gani a phant.
S uka sake komawa Asibiti, aka tabattar da ƙarancin jini a
tare da ita.
Likitan ya ce "Zahra, kina cin abinci ki ƙoshi
kuwa?"
Ta ce "Sosai ma, master yana ƙoƙari a wannan ɓangaren"
Ya ce "To ai ba kowane irin abinci ne ya dace da ke ba,
kin manta rashin lafiyar da ki ka yi, da irin abincin da muka ce ki din ga
ci".
Juahar ta ce "Wallahi Alhamdilillah, dai-dai gwargwado
yana bani, duk abun da nake so, ko ba na so ma yana sayo mini"
Al'amin ya ce "Ka ga likita, da dai idan na sayo tana
ci, amma yan, kwanakin nan, zaɓe-zaɓen abinci take yi, ba komai take ci
ba".
Likita ya ce "Ayi gwajin ciki gaskiya"
Jauhar ta ce "Ai ka ce ayi mini allurar tsarin iyali,
an yi mini kuma "
Ya ce "Guda nawa?"
"Ɗaya aka yi mini, an ce in dawo ta biyun, amma na ji
an ce idan baka period ba ta sake ka ba, to period ɗin ma so yake ya zo, amma
yaƙi zuwa sai wahalar da ni yake"
Ya ce "A nan asibitin aka gaya miki?"
Ta ce "A'a"
Yayi rubutu ya ce su je ayi scanning.
Suka je suka yi, suka dawo, ya karɓa ya duba, ya ce
"Ikon Allah, to akwai ciki, kuma jinin da yake zuba alamu ne na akwai
tangarɗa da yiwuwar ya zube idan ba a ɗauki mataki ba"
Al'amin ya rasa me zai yi, murna ko kuwa.
"To amma likita kana ganin babu matsala, tun da kun ce
kar ta ɗauki ciki, a nan kusa bai fi watanni biyar ba yanzu"
"Eh, zamu bar ta a ƙarƙashin kulawar mu, in Allah ya
yarda babu matsala, yanzu haka ya fara alamun zai fita, tun da ta fara zubar da
jini, dan haka muna buƙatar ta samu bedrest, na sati guda daga ci sai bacci,
ban da aikin wahala".
Cikin damuwa ta ce "Ko a hankali ba zan yi ba"
"A'a ba zaki yi ba"
"Amma master ka san ba wanda zai zo ya zauna da ni yayi
mini fa"
Al'amin ya ce "Ni zaman me nake yi?"
Doctor Khalid ya ce "Allah dai ya bar wannan ƙauna,
sannan kai master kana ji na"
"A'a fa, wannan sunan ba kowa yake faɗa ba, kira ni da
Al'amin ɗina"
Yayi murmushi ya ce "Bedrest ɗin da muka ba ta har da
kai a ciki"
Ya ce "Kamar yaya kenan?".
Doctor ya ce "Ba zuwa turaka"
"Meye turaka?"
Cikin jin kunya jauhar ta ce "Idan mun je gida zan gaya
maka"
"A'a ai ba sai kun je gida ba, bayani zan yi masa yana
sane ai, babu kai ba ita zuwa mu ga abun da Allah zai yi, ba cikakken hutu ake
so ta samu"
Al'amin yayi shiru yana kaɗa ƙafa.
"Ina magana ka yi banza, idan ka na son babyn ya rayu
lafiya kenan, ba tare da an samu matsala ba, idan kuma ka ƙi ba ruwana"
"Ai ni sai abun da Allah ya yi ne ban gane ba, nan da
yaushe ka ke nufi ne?"
"Zuwa cikin yayi ƙwari mana"
"To" ya amsa a taƙaice.
Doctor ya ce "Ba ka yadda ba kenan?"
"Na yadda mana, sallame mu na mayar da ita gida, rana
tana yi"
Doctor Khalid yayi counseling ɗin su sosai, sannan suka tafi
gida, Allah ya taimaketa a cikin hutu suke a makaranta.
Sai dai ba a rufa sati da zuwan su Asibiti ba, laulayi ya
saka jauhar a gaba, komai ta ci sai ta yi amansa, duk ta rame, har abun ya fara
damun Al'amin, yake ganin kamar ɗaukar cikin da tayi da wuri ne, ya sanya take
shan wahala har haka.
Babu tsammani Abbu ya zo gidansu da daddare, sun yi mamaki
sosai da sosai.
Bayan sun karɓe shi ya ce "Al'amin ina can ina jiranka,
ka kai mini business plan, in ga abun da yakamata na taimaka maka, ashe ka
zagaye ka je wurin kakarka ka karɓi kuɗi har ka buɗe wurin sayar da
shayi".
"Eh, na san ko na rubuta, matarka ba zata bari ka bani
ba"
Jauhar ta ce "Abbu dan Allah ka yi haƙuri, bai kamata a
ƙi gaya maka ba, dan Allah ka yi haƙuri mun yi kuskure"
Al'amin ya ce "A'a ni ne ban gaya maka ba, ta ce a gaya
maka na ce a'a, saboda ba na son matar nan ta din ga saka mini baki, a abun da
ya shafe ni"
Abbu ya girgiza kai ya ce "Jauhar ba ki yi laifin komai
ba, ni yabo da godiya na zo takanas na yi miki, rayuwar Al'amin ta canza sosai
da sosai, fiye da yadda nake tsammani, da na san aure zai katange shi daga wasu
laifuffukan da tuni na yi masa an wuce wurin. Allah ya saka miki da alkhairi.
Duk da daga baya na samu labarin yadda aka yi, aka zo ga gaɓar aurenki da shi,
amma ki ka yi haƙuri ki ka zauna da shi a yadda yake, ki ka din ga gwagwarmaya,
a gaskiya ina ƙara yaba miki, Allah ya yi miki albarka ya sa ki gama da duniya
lafiya"
Jauhar ta ce "Babu komai Abbu, da na yi watsi da shi
nima, kamar yadda sauran al'umma suka yi, da ba a samu Wannan nasarar ba"
"Haka ne, kai kuma" yayi maganar yana kallon
Al'amin.
"Ka ji tsoron Allah, a zaman da ka ke yi da yarinyar
nan, kana ganin duk wata masifa da kake ɗaukkowa babu mai tsayuwa a kanka, sai
ita sai abokan shashancin ka, kai kanka ka san yanzu rayuwarka ta canza ba
kamar da ba. Duk rintsi duk wuya, ka rayu da yarinyar nan da mutuntawa da
girmamawa, idan ka sake ka cutar da ita, ko wani abu mara daɗi ya faru da ita a
dalilinka, to ni da kai sai dai kowa ya kama gabansa".
"A'a Abbu ba za ayi haka ba, yana iya ƙoƙarin sa, babu
wani abu da yake yi mini ma na rashin kyautawa, ni yanzu roƙo ɗaya nake da shi
Abbu, dan Allah ka janye maganar a dalilinsa a ka kashe ɗan uwansa, kuma ka
saka baki a kan yayi haƙuri da batun ɗaukar fansar da zai yi a kan madakin nan,
tun da ya fita sabgarsa ya zauna lafiya kwana biyu, hankalinmu a kwance"
Aikuwa Al'amin ya haɗe rai, Abbu ya ce "Ka ji abun da
matarka ta ce, ka yi mata wannan alfarmar da ta nema, kuma nima na nema"
"Tom" kawai ya faɗa a taƙaice.
Abbu ya din ga saka musu albarka ya tashi ya fita.
"Ban yi miki alƙawarin kawo ƙarshen gaba ta da madaki
ba, har sai ranar da na tabattar na daina jin ɗanɗanon baƙin cikin, abun da ya
yi mini"
Cikin kwantar da murya ta ce "To ka bi ta hanyar da ta
dace ta shari'a, ba ta makami da illata junanku ba dan Allah"
"Ta in da aka hau, ta nan ake sauka" ya bata amsa.
Ta fuskanci muddin tana son ganin ɓacin ransa, to tayi masa
maganar madaki.
Washegari hafsa ta kirta a waya, ta ce "Kwana biyu bana
ganinki a online, ko ba data ne matar master?"
Jauhar ta yi dariya ta ce "Wallahi akwai data, kawai
bana jin daɗi ne, wayar ma ba iya taɓa ta nake yi ba, ya jikinki kuwa?"
Ta ce 'Hmmm jiki gani nan dai, ko dai ciki ne kin ce ba kya
jin daɗi?"
Tayi murmushi ta ce "Ba wani ciki, jikin ne dai
kawai".
"Bari zan wuce ta unguwar taku, sai na tsaya mu gaisa,
me zan taho miki da shi?"
"Babu komai, ke dai Allah ya kawo ki lafiya".
Bai fi awa biyu ba, sai ga hafsa, sai dai yanayin da jauhar
ta ganta bai yi mata daɗi ba.
"Yaya, wannan shigar fa kamar ba matar aure ba?
Hafsa ta ce "Taɓ, matar aure ai na ajiye aure a gefe,
mafita nake nemawa kaina"
"Ban gane ba"
"Wanda yakamata na yi wa ya gani, bai damu da ni ba, ya
haɗa kan matarsa da yaransa sun tafi dubai, sun bar ni ga kuɗi ga gida,
nayi-nayi anty ta fahimce ni a raba auren nan, taƙi har tana nema tayi mini
baki, zan cigaba da ba ta kuɗi, nima kuma zan nemawa kaina mafita"
"A'a yaya, wallahi gara ki kai ƙara hisba a kashe
auren, da ki yi zina da aure, ko a sasanta ku ayi masa nasiha".
Ta girgiza kai ta ce "Mama tayi mini asiri, banda wanda
matarsa take yi mini. Gaba ɗaya ba na gabansa, duk sai na yi maganinsu, daga
nan har chadd ko zan tafi tsirara, su surayya ba zasu auru ba, kuma sai na
kashe auren nan, ba zan iya ba. Kar ki damu da sai kin yi mini nasiha, dan ba
zan ji ba wallahi. Kin ga bari na hanzarta zan je na karɓo kayan cajina a wurin
wanda nake karɓa. Ke ni ko da mastern naki zaki haɗa ni ne, ya din ga bani
kayan "
Jauhar ta girgiza kai cikin matsananciyar damuwa ta ce
"Ki dai canza tunani yaya hafsa, ni master na yi nasara a kansa, da addu'a
da haƙura, abun da yake yi ya kusa zama tarihi, ke ma da zaki yi haƙu......
"Kin ga tafiyata jauhar, ga farfesun kifi nan da doya,
ki samu ki ci, sai anjima".
Abun duniya ya ishi jauhar, dan sai da ta zubar da hawaye,
ta ɗauki waya ta kira Baba, suka gaisa ya tambayeta ya makaranta ya mijin naki,
ta ce "Lafiya ƙalau Baba, dama wani abu ne ya saka na kiraka".
"To waliyiyya, Allah ya sa lafiya"
"Baba dan Allah ka shiga lamarin auren yaya hafsa ka
saka baki, kar abun da ba a so ya afku, yanzu ta bar gidan nan ni dai ina jin
tsoro, dan Allah baba ka saka baki"
"Waliyiyya kina ji na?"
"Eh baba"
"Duk Wanda ya ce ;zai haɗiyi gatari, sai ka sakar masa
ƙota. Babu yadda ban yi ba, idan auren nan ba zai yiwu ba, a raba uwatta taƙi,
na zauna da shi mijin, ya ce shi ba ta da cikakkiyar lafiya, kuma ba ta da
kunya, uwatta ta tsaya a fuskanci menene matsalar, tun da ta saka son abun
duniya a gabanta, amma taƙi. Ta ce wai asiri babar tijjani tayi mata, suna nan
suka ta faɗace-faɗace, kuma na san duk hakkinki ne, ni na zubawa sarautar Allah
ido".
"A'a baba, dan Allah kar ka ce haka, kada laifinsu ya
shafeta, su matanka ne, ita kuma 'yar ka ce, hafsa fa ta cigaba da ta'amalli da
miyagun ƙwayoyi baba ka yi wani abu a kai".
Ya girgiza kai ya ce "Jauhar kenan, zan yi ki yi mata
addu'a Allah ya shiryeta"
Suka yi sallama ta ajiye wayar cikin matsananciyar damuwa.
Al'amin ya dawo gidan yana mitar kwana biyu lambar guduma ba
ta shiga sam, yana ta kiransa a kan idan an yi musu albashi, ya gaya turo da kuɗi
a yi wa iyayensa sayayya, ya basu na neman albarka.
Amma shiru lambar ba ta shiga, ya kira P.A ya tambaye shi ya
kasa samun sa. P.A ya ce masa suna nan ƙalau yana can yana aikinsa, yana zaton
ko wayar ce ta samu matsala. Haka kawai Al'amin ya ji bai amince ba.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Gaba ɗaya ya kasa samun nutsuwa sai da jauhar ta farga ta ce
"Master ya ne?"
"Na kasa samun Nura a waya"
Ta ce "Allah sarki, ɗan uwa nagari in sha Allah zaka
same shi, maybe ko babu caji ne a wayar"
Ya ce "No, kusan sati fa kenan, na kira P.A ya ce mini
suna nan lafiya, wataƙila wayarsa ce ta samu matsala, idan ma haka ne, ai ko
wayar wani ya ara ya kira ni, tun da kusan kullum sai na yi waya da shi, na ja
masa kunne"
Jauhar ta ce "Haka ne, amma ƙara masa kwana biyu mu
gani"
Jiki a sanyaye ya ce "To shikenan"
Al'amin ya hana jauhar duk wani aikin wahala, su halimatu ne
ke zuwa ta yi guiding ɗin su, su yi mata snacks ɗin da ake kai wa wurin shayi,
sai bead work da take yi tana daga zaune, shi ma faɗa yake yi yana mita.
Iya haƙuri da ɗaga ƙafa ta san yayi mata, dan yau sakata
yayi a gaba yana mita, ba dan yana son cikin nan ba, da tuni ya daɗe da bin
rariya shi ma.
"Master" ya ɗaga kai ya kalleta, ya haɗe rai.
"Wai laifin me na yi ne?"
"Ni gaskiya na gaji, sai yaushe cikin zai gama ƙwari
ne? Nima ai yakamata a duba lamarina"
Murmushi ta yi, yadda yayi kicin-kicin, kamar wani ƙaramin
yaro.
"Lamba nawa ake so?" Tayi maganar tana kashe masa
ido.
"Na gaji da lamba uku huɗu, lamba ɗaya nake so"
Jauhar ta ce "Baka damu da babyn nan ba ko?"
Ya girgiza kai ya ce "Wallahi na damu da shi, ina son
abuna, amma ba shikaɗai yake buƙatar ya rayu ba, kuma ba shikaɗai yake buƙatar
ki ba" yayi maganar a marairaice.
Ta ɗan yi shiru tana nazarinsa, da gaskiyar sa, kusan kullum
ba ta da lafiya, tana kallo wasu lokutan sai dai yayi zamansa a ɗakinsa, ya
busa hayaƙi, dan kar ya takura mata, ko ya karya dokar da aka saka saboda
cikin.
"Kin yi shiru fa"
Dariya ta yi ta ce "Subhanallah, master da shagwaɓa,
lamari ya ɓaci, to lallaɓani".
"Ai lallaɓakin nake yi"
"Inyee dama ka iya shagwaɓa baka taɓa yi mini ba, yanzu
da da safe zan ce ka yi mini mazewa zaka yi kana hararata. To daga yau mayar
maka da fankarka zan yi, dama ta fara tsufa".
Al'amin ya ce "Zan yi zuciya fa"
Ta ce "To yi mana idan zaka iya, huta roro waken gizo
yaƙi 'ya'ya" tayi maganar tana jan dogon hancinsa.
"A'a ba zan yi ba ma"
Tayi murmushi tare da rungume shi.
Har suka kwanta tana lafiya, sai cikin dare ya farka ya
ganta a zaune, ta takure wuri guda.
"Madarata, ya aka yi ne?"
Jauhar ta ce "Bakomai, zafi ne ya dame ni"
"Zafi kuma? Ga fanka na yi?. Ko numfashin ne?"
Ta ce "A'a, lafiya ƙalau nake numfashina"
Ya ce "To ya aka yi na ganki a zaune?"
Tausayinsa ya kamata, har istigfari take yi, ta gaji da ce
masa ba ta da lafiya ba yau ba gobe.
"Master ka kwanta dan Allah, na kasa baccin ne"
Cikin damuwa ya ce "Ka kwanta ka yi baccinka"
"A'a ban yadda ba, akwai matsala ne, gaya mini?"
"Marata ce take ciwo"
Cikin tashin hankali ya ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un, Allah ya sa ba zubewa zai yi ba, ya salam"
Ta jingina da jikinsa ta ce "Ciwon fa ba mai damu bane
ba, ƙullewa tayi, na ji kwanciyar babu daɗi, shiyasa na tashi zaune"
"Ko asibiti zamu je? Wallahi ina son cikin nan zahra,
na kwaɗaitu da son ganin abun da zaki haifa mini, tun da muka rasa na farko,
nake tunanin ko yaushe zamu kuma samu? Kuma mun samu wannan karon ma, zan yi
dalilinsa, mu je asibiti kawai".
Cikin sigar rarrashi ta ce "Master, dan Allah kar ka ɗaga
hankalinka, ba ciwo take yi mini ba, ƙullewa tayi ne sosai kuma na duba babu
abun da yake fita. Ɗawainiyar da ka ke yi da ni ka da Allah ya gajiyar da kai,
Ubangiji Allah ya nuna mini ka daina komai kan Allah ya kawo mana babynmu"
Yayi ajiyar zuciya ya ɗora hannunsa a mararta ya ce "Ba
zan taɓa gajiya da duk wani abu da ya jiɓance ki ba, ba alfahari nake yi miki
ba, ɗan halak ne ni, kar ki taɓa sakawa ranki zan gaji, da ƙarfin ikon Allah ba
zan gaji ba, in sha Allah, ni dai duk abun da ki ka ji na ciwo ki gaya mini dan
Allah, ina son kasancewa da ke da iya adadin abun da zaki haifa mini, mu yi
rayuwa mai tsayi da daɗi. In sha Allah zan yi iya ƙoƙarina na zama uban kirki
ga 'ya'yana, kuma miji abun alfahari gareki"
Haka kurum ta ji jikinta yayi sanyi, da maganganun sa, ji
take kamar akwai wani abu mai girma da zai faru da su, sai dai ba ta sani ba,
na daɗi ne ko akasin haka.
Ta sake lafewa a jikinsa, tana jin tsananin buƙatuwar son
cigaba da kasancewa da shi a cikin rayuwarta, ita wannan kulawar da yake yi
mata, tana shafe dukkan sauran abubuwan da yake aikatawa.
Zuwa da safe ta ji ƙwarin jikinta, har ta ce masa zata
makaranta, da ƙyar ya amince, saboda tana da test.
Har ta fito ya karɓi jakarta, ya ce shi zai kai ta, kar ta
hau ɗan sahu, ayi ta gargada da ita.
Ya duba jakar ya ce "Ina inhaler ki?"
Ta ce "Tana aljihun wandona"
"Meyasa ba zaki saka a jaka ba"
"Zai iya yiwuwa ciwon ya tayar mini, jakar tana nesa da
ni, amma a wandona da na laluba zan ji ta"
"Allah ya baki ingantacciyar lafiya, ya rabaki da ciwon
nan gaba ɗaya"
Ta ce "Amin bugun zuciyata"
Ya ce "Iyeeee?"
Ta jinjina kai ta ce "Eh mana"
"To bani da kuɗi dai, kayan abinci zan sayo mana, idan
kuma na ɗauka na baki shikenan"
Ta tsuke fuska ta ce "Kai ba ayi maka abun arziki, da
na yi maka kalamai, sai ka hau ce mini ba ka da kuɗi, me ka ke nufi"
Al'amin ya ce "Ai ke ɗin ce, wasu lokutan haka ki ke yi
mini, bana sanin lokacin da ki ke sakawa na zazzage miki aljihuna"
Jauhar ta tura baki ta ce "Wannan kalaman wataran da kuɗi
ba zaka ji su daga bakina ba"
Take jikinsa yayi shock ya ce "Ban da irin wannan
wasan" idonsa ya nuna ƙarara tsananin fargabar rasata.
Ta basar da zancen, ya kaita makaranta.
Abu kamar wasa, sama da kwanaki biyar, Al'amin bai ji ɗuriyar
Nura ba, bai kuma same shi a waya ba, dan haka ya wanke ƙafa ya tafi gidan
indabo, kasancewar ba shi da shamaki da gidan, babu mai tambayarsa wurin wa ya
zo, ina za shi, kai tsaye ya shige.
Ofishin indabo na gidan ya tafi, kasancewar imdabon yana
Abuja, cikin sa'a ya tarar da P.A.
"Mai zamani, ya aka yi ne?"
"Na kasa samun Nura a waya"
"To ai ina zaton wayarsa ta samu matsala ne kamar yadda
na gaya maka"
Ya girgiza kai ya ce "Ba zai yiwu ba, shirun yayi yawa.
Ba zai yiwu na baku amanar yaro, garin da ba uwar sa babu ubansa na kasa
samunsa a waya, kusan sati biyu, na zauna na yi shiru ba, ba zai yiwu ba, dole
ka san duk yadda zaka yi ka haɗa ni da shi"
"Amma mai zamani ina nan yana Abuja, a ina zan iya haɗaka
da shi?"
Cikin ɗaga murya ya ce "Ka kira indabon, duk yadda zai
yi ya haɗani da shi"
P.A ya tsaya yana kallon sa.
"Zaka yi abun da na ce, ko sai na saka maka
ƙarfe?"
Ya janyo waya ya kira Indabo, suka gama magana. Ya kalli
Al'amin ya ce "mun yi magana da honorable, ya ce in anjima zai aika a duba
shi, yanzu suna meeting da shugaban ƙasa".
Yayi ƙwafa ya juya zai fita, Abdul ya kawo kai shi ma ya
shigo. Sai dai Abdul ya tsaya yana jiran Al'amin ya bashi hanya, wannan ce haɗuwar
su ta biyu, kasancewar ba a ƙasar yake zaune ba, ya fi sanin ɗayan wato
Ja'afar.
Ala'amin bai tsaya jira ba, ya yi wa Abdul wata muguwar
bangaza da kafaɗarsa, sai da ya dangana da faɗuwa ƙasa.
A fusace ya miƙe zai bi bayansa, P.A da sauri ya tsare shi
ya ce "Kul, sai ya yi maka illa, ba mutunci ya cika ba wasu lokutan"
A fusace Abdul ya ce "Mahaukaci ne shi, baka ba ka ga
irin bangazar da ya yi mini bane?"
"Yi haƙuri, ai duk abun da ka ga honorable yana bi a
sannu, ka san ba ƙarami bane ba, yi haƙuri".
Ya kalli P.A ya ce "Babu ruwana za abun da yake bi a
sannu, wallahi muka sake haɗuwa sai na koya masa hankali" ya juya ya fasa
yin abun da zai yi.
Har la'asar Al'amin yana kallon wayarsa, yana jiran kiran
indabo, ya je wurin shayi, komai yana tafiya dai-dai, ya tafi gida.
Yayi jajjage ya feraye doya, ya dafa ruwa ya zuzzuba a
flask, duk ya rage wa jauhar aiki.
Wayarsa ta fara ringing, ya ɗaga ya kara a kunnensa.
Muryar Nura yaji ƙasa-ƙasa ya ce "Yaya"
"Kai Nura wani irin shirme ne zaka kashe waya, ko ta
wani ba zaka ara ba ka kirani, ina ta tunanin meyafaru da kai?"
Nura ya ce "Ka yi haƙuri dan Allah"
"Ya ake ciki? Na ji muryarka wani iri?"
Nura ya ja numfashi ya ce "Zazzaɓi ne yake damuna, sun
bani hutu ma, an kai ni asibiti an bani magunguna ma"
"Yasalam, kai daga zuwa garin mutane sai rashin lafiya,
ko aikin ne da wahala?"
Ya ce "A'a"
"To Allah ya sauwwaƙe, zan cigaba da kiranka, idan ka
ga babu hali, kawai ka dawo gida"
Nura ya ce "Godiya nake, Allah ya kiyaye ka ya ƙara
tsawon zamaninka"
"Ka huta, ka kula sosai duk yadda ake ciki, ka sanar
mini, ina fatan sun sallameka, dan na ga wata ya ƙare"
"Eh an bani kuɗi masu yawa ma, ka bani account number ɗinka,
na sako maka abun da na samu, amma a ciki a sayawa Antynmu turimin atamfa dan
Allah, da ita da babata a sai musu iri ɗaya"
Al'amin ya ce "A'a, ta gode sosai, amma ba haka za ayi
ba, ka ba wa maman abun da zaka bata, ka tallafawa babanka da wani abun ya sai
kayan abinci"
Nura ya ce "Shikenan, tun da ka ce haka, amma dan Allah
ka saya musu atamfa iri ɗaya da mamanmu, tana sonta sosai "
Al'amin ya ce "Zan duba na ga abun yi, ka kula da shan
magani ka ji ko?"
"In sha Allah"
"Good boy, sai anjima" ya kashe wayar, sai ya ji
wata irin sa'aida a zuciyarsa jin muryar nura, dan babu irin saƙe-saƙen da bai
yi a kansa ba.
Da jauhar ta dawo, aikin gida ƙarashe ne, duk yayi, sai
godiya take yi masa tana yi masa addu'a.
Jauhar tun da cikinta ya fara tasawa, da an buga gate, sai
ta saka hijjabi tana ɓoyewa, wai kunya take ji.
Yayi ta yi mata dariya, ya ce "Da ki ɓoye, da ki bar
shi, ƙarewa haifarsa zaki yi ƙarshen kunya, gara ma ki bar shi kowa ya
gani".
Cikin shagwaɓa ta ce "Ni dai ka bari na ɓoye
abuna"
Ya ce "Ai sai ki yi ta yi"
Al'amin ya sha mamaki kuɗin da guduma ya turo masa, dubu ɗari
da hamsin, wai a bawa babansa dubu ashirin kawai, sauran har da su oga liti da
oga walid ya ce duk rarraba musu.
Al'amin ya ce "Wai aikin direban ne aka baka wannan kuɗaɗen
har haka?".
"Eh Oga, ka san birnin tarayya ne nan, kuɗi ba wahala
suke yi musu ba, ka cigaba da yi mini addu'a, jikina ne babu daɗi"
Al'amin bai matsa da bincike ba, ya ƙyale shi.
Jauhar ta yi mamaki da ya kawo mata atamfa, sai Nura ne ya
turo da kuɗi a saya mata iri ɗaya da mamansa.
A lokacin ta ƙara yadda da ƙani ya ɗauki Nura, da wani ne
daban ya bata, cewa zai yi ba zata saka ba.
Al'amin da kansa tare da rakiyar su Walid, suka je suka
kaiwa mahaifiyar Nura, abun da ya aiko a bata, ta din ga murna tana yi wa
Al'amin godiya tare da yi masa addu'ar gamawa da duniya lafiya.
Mai unguwa kuwa raina dubu ashirin ɗin nan yayi, a ganinsa
tun da Nura ya tafi Abuja, dubunan ɗaruruwa zai aiko masa, ya fara zargin ko
Al'amin ne ya rage kuɗin.
Ɓangaren Abbu kuwa, Abba ɗan wurin rahila, ya haɗa kai da
abokai, suka fara yi wa Abbu sata, da ƙaramar sata suke yi masa, wani ya gani
ya kawar da kai, wani kuma ma bai san sun yi ba.
Sai dai a wannan karon, satar da suka yi masa ba ƙarama bace
ba, dan har ya kai ga reporting wurin Jami'an tsaro, da fari rahila ta ɗauka
abun mai sauƙi ne, dan ta na ta yi wa Abbu masifar a kan me zai tayi mata
terere da ɗa dan ya ɗauki kuɗi, ai shi mai rufa masa asiri ne yayi masa nasiha,
sai dai ta girgiza da ta ji ya saka 'yan sanda sun kama shi.
Tamkar za ta yi hauka, da ƙyar ya saka aka sake shi, ya ce
sai dai ya bar masa gida ya koma gidan ubansa, nan ma ta ce sai dai ya zaɓa ko
dai ya zauna da ita da yaranta ko kuma idan ya matsa su tafi gaba ɗaya, ya ce
ta kwashe yaranta su tafi.
Sai da ta ga ba ta da sauran mafita, sannan ta koma lallaɓa
shi, da ƙyar ya saukko.
Juahar tuni ta fara zuwa awo, dan yau shi ya rakata awon ma,
a wurin scanning aka nuna masa yadda zuciyar jaririn take bugawa.
Gaba ɗaya ya rikice, bakinsa ya ƙi rufuwa, ya zubawa screen ɗin
ido, yana ta washe baki yana murmushin.
Jauhar ta ce "Ni fa na gaji zan tashi"
Ya ce "Ɗan yi haƙuri, bari na ƙara ganinsa mana"
"Ka ga me? Me ake ganewa a nan, ni banda duhu ba na
ganin komai"
Al'amin ya kalleta ya ce "Sautin bugun zuciyar ta sa ne
nake ji har cikin raina"
Sai da mai scanning ɗin ya yi dariya, aikuwa ta tashi zaune
ta ce "Ni na gaji, haka kurum, na fuskantar tun yanzu kafi son ɗan tayin
nan, to ka matso ka saukko da ni"
Ya miƙe ya saukko da ita daga kan gadon, ya ce "Ki din
ga motsawa a hankali, kar ki takura shi".
Tayi murmushi ta ce "Idan ban tafi da gudu ba, ka ce ba
ni ba ce"
Ya ce "Yi haƙuri, ai dole na lallaɓaki" suka je
aka gama yi mata awo, suka tafi wani shago na kayan jarirai, suka fara sayayya,
kasancewar an ce musu tun a wata shida, kan ciki yayi bakwai ake haɗa kayan
haihuwa, saboda haihuwa za ta iya zuwar mata a wata bakwai, sannan ya tanadi kuɗi,
dan ba a san ya haihuwar zata zo ba, ko ta haihu da kanta, ko kuma ayi mata
tiyata.
Ta zo ta shirya kayan da suka sayo a wani ɓangare na
wardrobe ɗin ta, kallon kayan kawai nishaɗi yake sakata.
Washegari da safe, yana falo yana kallon wrestling, ta fito
daga ita sai wata rigarsa da ta saka shirt ce, tayi mata yawa nesa ba kusa ba,
iya cinyarta ta tsaya, sai kanta tayi kalba guda biyar, ta sake su ta fito tana
miƙa tare da hamma.
Ya buɗe mata hannayen sa, yana murmushi, ta ƙarasa ta zauna
a kan cinyarsa, ya rungumeta ya ce "Sannu"
"Yauwwa. Ina kwana?"
"Lafiya ƙalau, ya jiki ya babyna?" Yayi maganar
yana shafa bayanta.
Ta ce "Ni babyn ko wa?"
"Ƙatuwa da ke ke ce babyn, unborn dai"
Boti ya hawo saman kujera, ya hawo jikin Jauhar, Al'amin ya
kai hannu zai cillar da shi, ta riƙe shi tana dariya ta ce "Master dan
Allah ka bari magen nan ya huta, duk ya tsaneka saboda cin zalinsa da ka ke yi,
akwai buƙatar na yi muku sulhu"
"Babu sulhu tsakanina da wannan abun"
Ta ɗauki boti tana shafawa ta ce "Boti ku daina faɗa da
master dan Allah" muzurun ya kawar da kansa gefe, Al'amin ya ƙwace shi ya
ajiye shi a ƙasa, ya koma da baya yana kartar carfet ɗin yana yi masa kuka.
Jauhar ta din ga dariya, ta ce "Wallahi daga kai har
shi dariya ku ke bani"
Al'amin ya lumshe ido ya buɗe, yana shafa cikinta ya ce
"Duk kin zama ƙazama, kalli kin daina kitso, ga wata uwar riga kin saka,
wadda sai an saka irinki goma a ciki, ni ɗaga rigar na din ga kallon
jaririna"
"Master kenan, ba zaka gane ba, ni kaina ba na son zama
da kan nan a haka, amma da an fara yi mini kitso zafi yake yi mini, kayana kuma
duk sun yi mini kaɗan, amma idan na saka rigar nan taka, balance nake yi a
ciki"
Ya kashingiɗa a jikin kujera, yana cigaba da kallonta, yana
jin wani irin kusanci da shauƙin kasancewar sa da ita wuri ɗaya. Kullum yana
ƙara girmama lamarin Ubangiji yadda ya ƙaddara kasancewar su tare, wanda idan
ba ƙarfin ikon Allah ba, babu abun da zai haɗa shi da ita, har ya nemi aurenta.
To wa ma zai bashi auren yarinya irin jauhar a yadda yake.
"Master ka san menene?"
Ya girgiza mata kai.
"Na ji an ce akwai lokacin da ma'aurata kan gaji da
juna, ko miji ya ji matarsa ta gundure shi, dan Allah idan Allah ya raya mu ka
fara jin irin haka a kaina, dan Allah ka yi haƙuri kar ka canza mini, na saba
da kai sosai da sosai. Ina jin daɗin yadda na samu mai tausayina wanda ya mayar
da ni mutum, yake zama ya saurari damuwata. Dan Allah ko nan gaba ka samu wadda
ta fini, ko na fara gundurarka kar ka yi mini wulaƙanci ko ka manta da ni dan
Allah" tayi maganar very serious.
Ya ƙura mata ido, yana mamakin maganganunta.
"To ai ni ko yanzu kin gundureni, duk kin hana ni
rashin ji na, na saba da rayuwata ta ɓalla ƙarafa da hawa network duk kin
hanani, zaman haƙuri kawai nake yi da ke, kin isheni"
Wasa yake yi mata, kawai ya ga tana kuka.
A ɗan rikice ya ce "Haba Madarata, ke yanzu idan aka ce
miki zan yi miki abu makamancin haka zaki yadda? Ina sake maimaita miki ni ɗan
halak ne bana manta alkhairi. A lokacin da kowa ya yasar da ni, yake yi mini
kallon mara amfani a lokacin ki ka rungumeni a yadda nake, ki ka yi ya ɗawainiya
da ni, ba tare da kin gaza kin ƙosa ba, bana fatan Allah ya nuna mini ranar da
zance kin gundureni"
Ta share hawayenta ta ce "Ka san wani abu, kai diamond
ne da mutane ba su farga da shi ba, suke maka kallon mara amfani. Sai yanzu da
ƙyallinka da haskenka ya fito"
Ya kwantar da kanta a ƙirjinsa yana murmushi ya ce "Ke
dai ki ke kallon hakan, ga al'umma na zama mara amfani, saboda ɗan daba ne
ni"
"To ni dai kana da amfani a wurina"
Yayi murmushi ya ce "A ɓoye fa rigima kawai ki ke so ki
yi na rarrasheki, to na ji sannu yi haƙuri"
"Yauwwa mata da yawa ba ayi mus irin yadda ka ke yi
mini ɗin nan, zuciyar zinare ce da kai master, kana da tausayi sosai da
sosai" ta kara kunnenta a ƙirjinsa ta ce "Zuciyarka sai kiran sunana
take"
Al'amin ya ce "Ni dai yi magana a hankali, na ji babyna
yana motsi, kar kwanciyar da ki ka yi ce kika takura masa, tashi zaune"
Ta ɗaga kai ta kalleshi ta ce "Master, zaka dawo ka
tarar da ni, ina 'yar gala-gala da cikin nan, duk sai nuna banbanci ka ke
yi"
Shi ma kallon fararen idanunta yake yi yana dariya, ya ce
"To breakfast fa, me zamu ci?" Ta tashi zaune ta ce "zan dafa
maka wani abun, amma ni anty wasila nake jira, za ta kawo mini wainar
gero"
Ya tsuke fuska ya ce "Roƙo ko?" Ta ce "A'a
geron da ka kawo na ɗiba na bata tayi mini, idan ni na yi ba zan iya ci
ba"
Ya ce "Ok"
Har azahar yana gida, jauhar ta hana shi fita, sai azahar
yayi shiri ya fita, saboda sallar azahar, yanzu jauhar ta daina fama da shi a
kan yin salla a kan lokaci.
Sai ga anty lubabatu, ta zo maƙwabciyar su mai ba ta aikin
bead a gida.
"Oyoyo anty lubabatu, yau ke ce a gidan".
"Yau gani na lallaɓo, an ce mini kin kusa juyewa, na ce
bari na zo ga ya kike"
Jauhar ta ce "Ohh ni zahra'au in ji wa? Ba a gaya miki
daidai ba"
"Eh ba a gaya mini ba, ni na gani yanzu ai"
Da sauri jauhar ta kalli cikinta ta ce "Haba dai dan
Allah a na gani" Anty lubabatu ta kwashe da dariya ta ce "Lallai
yarinya, wannan uwar ƙibar da ki ka yi ma da haka ki ke? Kin zama uwar
mata"
Juahar ta yamutsa fuska ta ce "Na yi muni ko?"
"A'a babu wani muni, wallahi kin yi kyau, kallo ɗaya
mutum zai yi miki ya san a kwanciyar hankali ki ke. Jauhar gyaran gida aka yi
miki haka, lokacin da na zo gidan nan kina amarya tsurar bulo ne fa, ikon Allah
har da sola, wato a duniya idan Allah yana yinka ko wa ma yaƙi ka. Ga Alhaji
mu'azzam can Allah ya bar su da shi, matarsa na ta gana wa hafsa azaba, abu har
da 'yan sanda, ya ce idan ba zata zauna da matarsa lafiya ba tayi mata biyayya
ta tafi gida. Gidanku kuma ana ta tashin hankali, Anty zakiyya ta ce mama ke yi
mata asiri"
Cikin damuwa jauhar ta girgiza kai ta ce "Bari kawai
Anty lubabatu, lamarin gidan nan namu sai Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
kuma wasu lokutan har da laifin baba, kodayeke shi ma sun mayar da shi sai
yadda suka yi da shi, ai da ni aka ce ina yi wa hafsan asiri. Ko gidan ya
hanani zuwa, sai idan da daddare ya kaini na gaida baba na dawo gida"
"Allah ya taimake ki, ke da suka so su tozarta
rayuwarki Allah ya rufa miki asiri, ɗan daban da suka aura miki dan ki
wulaƙanta, hakan ba ta faru ba"
"Tababs babu abun da zan ce wa Allah sai godiya, Anty
lubabatu mijina a maza ɗari irnsa ɗaya ne tak. Daba da shaye-shaye su ne
ƙaddararsa amma, ya ci sunansa amintacce rauninsa mutane suke kallo, basa
kallon nagartarsa" sun daɗe suna hira sosai kafin ta tafi.
Kusan duk bayan kwana biyu zuwa uku, sai hajiya kakar
Al'amin ta kira Jauhar ta yi mata ya jiki, dan tun wani zuwa da tayi ta
fuskanci hakan.
Tun da ya fita da azahar har bayan magariba bai dawo ba, sai
da ta kira shi a waya, ya ce mata gashi nan.
Hnakali a tashe ya dawo mata, dan sai da gabanta ya faɗi ya
ce "Master lafiya?"
"Nura aka kawo daga Abuja, wai ba shi da lafiya, tun
lokacin nan da ya ce mini ba shi da lafiya, yake kwance"
Ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, meya same
shi haka?"
Ya ce "Ban sani ba, an dai kai shi asibiti, na je na
ganshi a galabaice, yayi magana ya faɗi meyake damunsa ya ƙi, na ga a galabaice
yake sosai, an saka masa ruwa da sauran abun da yakamata gobe in Allah ya kaimu
dai zan koma".
Jiki a sanyaye ta ce "Allah sarki Nura, sai da ka ce
idan ba zai iya ba ya dawo, wataƙila dan kar ka yi masa faɗa ne ya zauna bai
dawo ba. Allah ya bashi lafiya"
Ya amsa da Amin.
Ya ciro mata envelope ya ajiye mata.
Ta ce "Menene wannan?"
Ya ce "Duba ki gani mana"
Hotunasu ne shi da ita, wanda galibi a wayarta suka yi, ya
kai aka ciro su, sai kuma ƙatuwar viva, da aka yi frame ɗin hoton da suka yi na
sallar eid ɗaya an rubuta musu happy marriage life, ɗaya kuma an rubuta first
eid with habibi.
Tayi murmushi ta ce "Kamat yayi a rubuta Master weds
madara" duk da a cikin damuwa yake sai da yayi murmushi, ya ce da safe zai
kafe a falo.
Ta kalleshi tana murmushi, bai taɓa ce mata yana son ta ba,
sai dai actions ɗin sa, yana tabattar mata da hakan. Da fari kai ba ka ce ya
iya duk wani abu da yake da alaƙa da kulawa ba, saboda he's always serious, sai
dai a hankali ainihin halayensa suke fitowa.
Jikin Nura yayi tsananta, kullum Al'amin cikin sintiri yake,
jauhar ce mai lallaɓawa tayi musu girki, mahaifiyarsa ce take zaune da shi a
asibiti tana kula da shi, gashi an rasa gane abun da yake damunsa, Al'amin har
gona ya saka aka sayar masa a ƙauye, saboda kula da Nura, dan asibitin kuɗi ya
saka aka mayar da shi.
Da daddare babar Nura ta fita, Al'amin ya zo, cikin ƙarfin
hali ya ce wa Al'amin "Yau ina Antyna ba ta zo ba?"
Ya ce "Eh, ni na hanata zuwa, tayi nauyi. Nura yakamata
zuwa yanzu ka gaya mini menene yake damunka, ana ta kashe kuɗi an rasa gane
abun da yake damunkaa yayi maganar cikin damuwa"
Nura ya ce "Idan na gaya maka ba zaka yi fushi da ni
ba?"
"Ya za ayi na yi fushi da kai? Ka gaya mini in san ta
in da zan kamo bakin zaren".
Ya riƙe hannun Al'amin ya ce "Na san ba lallai na rayu,
amma ba ka da laifi ka taimaki rayuwata ne. Na gayawa mama na ce kar ta gaya
maka. Lokacin da na ce maka na fasa tafiyar nan, Honorable ne ya ce sai ya yi ɗabi'ar
mutanen annabi luɗ da ni, na ƙi yarda, ni kuma na kasa gaya maka, dan ya ce
idan na gaya maka, kashe mai unguwa zai yi, amma idan na amince shikenan, ba
wanda zai san an yi kuma zai bani aikin.
Na ɗauka daga haka shikenan, sai dai tun da ya tafi da mu, a
wani gida aka ajiye mu, abun da suke yi mana kenan, yana da masu kula da mu,
babu ta in da mutum zai gudu, kuma ba shikaɗai ne yake yi mana hakan ba, akwai
wasu manyan mutane a ƙasar nan, da duk zan gaya maka sunayensu.
Kuma kamar tsafi suke yi ta hanyar amfani da mu, bana iya
riƙe bayan gida, mama ce take gyara mini kafin mutane su zo dubiya, Indabo ya
lalata mini rayuwa amma ka rufa mini asiri dan Allah, kuma kar ka zargi kanka!
Ina da hujja mai ƙarfi da zan baka a kan haka!
Ayshercool.
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Gaba ɗaya fuskar Al'amin ta sauya takmar ta horo, ta koma
Al'amin ɗin sa na ainihi, tamkar bai taɓa sanin wani abu wai shi dariya ba.
Wani irin gumi ya shiga tsatstsafo masa, jijiyoyin goshinsa zuwa kansa suka
miƙe suka kukkumbura, idonsa yayi wani irin ja mai ban tsoro, bugun zuciyarsa
ya ƙaru da saurin gaske, jikinsa ya fara ɗaukar wani irin zafi saboda tashin
hankali da tsananin ɓacin rai.
Ba tare da tunanin halin da Nura yake ciki ba, yayi wa
hannun guduma wani irin mugun riƙo, da sai da ƙasusuwansa suka yi ƙara.
Nura ya ɗora ɗaya hannun a kan na Al'amin ya ce "Yaya,
kai ɗan uwa ne da Allah ya bani rana tsaka a titi, duk wannan abun ka yi ne dan
inganta rayuwata, ba ka taɓa yin wani abu da zaka cuceni ba, na san da ka san
abun da zai faru da ni kenan, ba zaka bari na je ba, dan Allah ka kwantar da
hankalinka, ni na san ba zan rayu ba, abun da suka yi mini ya fi na kowa muni
da tashin hankali, ban san yaya zan misalta maka ba, amma dan Allah kar ka yi
yinƙurin yin wani abu, idan ba haka ba za su yi maka illa. Na bar su da Allah
ka tayani Addu'a Allah ya yafe mini laifukana, idan na mutu dan Allah ka yi
mini wanka kar asiri na ya tonu, ba na son a zargeka da abun da mutane ba su
san menene ainihin abun da ya faru ba.
Wurin bayan gidana ya riga ya ɓaci, kowa ya gani zai gane
meyafaru dan Allah kar wani ya je kan gawata idan ba kai ko mama ba"
Al'amin ya riƙe hannun Nura gam, amma ya kasa magana sai
wani irin numfashi mai haɗe da huci, ya sunkuyar da kai yana sauke numfashi.
Yanayin yadda mahaifiyar Nura ta tarar da Al'amin, ya sanya
ta gane ya gaya masa.
Ta ƙarasa gaban gadon, jiki a sanyaye ta ce "Al'amin,
ka kwantar da hankalinka dan Allah, zan iya dafa Alqur'ani na rantse, ba zaka
kai mini nura in da za a cutar da shi ba, na san da ka san me zai faru kenan ba
zaka yadda ya je ba, a irin yadda yake bani labarin zamanka da shi. Iya ɗawainiyar
da ku ka din ga yi da mu kai da matarka ya ƙara tabattar mini da haka. Cuta ce
an riga an cuce mu, amma mun bar wa Allah, ni ba zan zargeka ba"
Ya saki hannun Nura a hankali, ya tashi ya juya ya fice.
Nura yayi ajiyar zuciya ya ce "Allah ya sa kar ya ce
zai ɗauki wani mataki, dan mutanen nan sun wuce duk yadda yake tunani, ni dai
ku cigaba da yi mini addu'a da fatan cikawa da imani"
Duk da juriya da mahaifiyar Nura take yi, sai da ta kasa ta
zubar da hawaye, cike da karaya, dan magana kawai Nura yake yi, amma komai sai
an yi masa, gashi buni-buni jininsa ya ƙone, sai an saka masa wani, dan bayan
bayan gidan, har da jini ne yake zuba daga wurin, jini sosai ba kaɗan ba, a
tunaninsa da na mahaifiyarsa ɓoye wa likitocin ainihin abun da ya faru shi ne
rufin asirin su, dan babu wanda zai fahimce su, cewa za a yi shi ya kai kansa,
saboda kwaɗayi da son abun duniya, dan Nura ya yi girman da ya fi ƙarfin ace
dole aka yi masa.
Ikon Allah ne kawai ya kai Al'amin gida, dan ko me za ayi
masa bai san ya aka yi ya isa gidan ba.
Jauhar har ta yi bacci, dan 'yan kwanakin nan bacci take yi
sosai da sosai, duk in da ta ji kwanciya ta yi mata daɗi sai bacci.
Ba ta farka ba, sai bayan sha biyun dare, shi ma dan taji ta
gaji da kwanciyar ne, a hankali ta tashi jikinta duk yayi tsami, ta kalli ƙofar
ɗakin Al'amin, ta tashi ta nufi ɗakin, ta ɗaga labule ta shiga.
Yanayin kwanciyar da ya yi, ya tabattar mata da yayi
shaye-shaye ya bugu, dan wata irin kwanciya yayi.
Jiki a sanyaye ta ƙarasa gaban katifarsa ta zauna a hankali
ta ce "Haba master yau kuma?" Dan bai fiye shan abun da zai gusar
masa da hankali gaba ɗaya har haka ba, yana yi amma ba sosai ba, ya fi ganewa
busa hayaƙi. Kuma kwanakin nan da Allah ya taimaketa tayi galaba a kansa, bai
fiye shan abun buguwa ba sai shan sigari, wiwin ma ya rage shan ta sosai, amma
ta zo ta tarar da shi a wannan yanayin.
Da ƙyar tana haki, haka ta gyara masa ƙafarsa da hannunsa,
ta shafi sumar kansa, sai wani irin gumi yake yi, naman fuskarsa yana ɗan yi
rawa lokaci zuwa lokaci ga ajiyar zuciya da yake ta yi a kai kai.
Ganin ba ya hayyacinsa, balle su yi magana, ya sanya ta
tashi ta tafi ɗakinta, cikin zullumi da tunanin me aka yi masa?.
Kiran sallar farko ya farka, sai dai zuciyarsa cike da
tsananin baƙin ciki da ɓacin rai, ya san ko ya je gida ba zai samu indabo ba
yana Abuja, kuma ba zai iya tafiya Abuja ba, cikin fargaba zai tafi kar yana
matsawa wani abun ya samu Nura.
Alwala yayi ya fice, a hanya yayi sallar asuba, ya ƙarasa
Asibitin, maman nura na ta kokowar yadda zata ɗaga shi, ta saka masa pampers,
yayi mata girma.
Al'amin ya bubbuga ƙofar, ta ce "Waye?"
Da ƙyar ya iya magana ya ce "Al'amin ne"
Nura ya ce "Mama buɗe masa"
Ta buɗe masa ya shigo, Nura ya gaida Al'amin, jinjina kai
kawai yayi, suka gaisa da maman Nura, da ƙyar yake iya magana, saboda tsananin ɓacin
rai da tashin hankali.
Ya taimaka mata, suka canzawa Nura pampers, jinin da Al'amin
ya gani a pampers ɗin ya ɗaga masa hankali, gaba ɗaya halittar duburar Nura ta
fito waje, babu ƙyanƙyami babu komai, ya taimaka mata suka gyara shi, suka saka
masa pampers uku, kamar yadda take saka masa, sai kuma ta kawo zannuwa ta
tuttura masa ta toshe ko ina, ta fesa masa turare, ta kunna turaren wuta, ta
shiga banɗaki ta wanke kayan da aka cire mas.
Al'amin ya rasa me ma zai cewa Nura, abun duniya ya ishe
shi, ya ji ya tsani kansa, komai baya yi masa daɗi.
A hankali ya kalli Nura ya ce "Zan gaya wa likitoci, su
duba idan da abun da za a iya yi, ayi maka babu dabara a ɓoyewa likitoci wannan
lamarin"
Da sauri Nura ya ce "Dan Allah kar ka yi mini haka, ka
rufa mini asiri, wallahi babu wanda zai yadda dole aka yi mini, na san ba zan
rayu ba, lokaci kawai nake jira, dan Allah yayana wannan ce alfarmar ƙarshe da
zan nema a wurinka, dan Allah kar ka gaya wa kowa"
Cikin matsananciyar damuwa Al'amin ya ce "Nura ka yafe
mini, wallahi ban san abun da zai faru ba kenan, na zata hakan zai taimaki
rayuwarka ne... Sai ya kasa ƙarasawa muryarsa ta fara rawa.
Guduma ya ce "Wallahi na sani, kai mutumin kirki ne
yayana, dan Allah idan na mutu ku din ga yi mini addu'a, na san sauran jama'ar
gari babu lallai su yi mini, saboda ban shuka alheri ba, amma na san kai zaka
yi mini kai da mama, da Antynmu. Dan Allah idan ta haihu, idan namiji ne, ka
saka masa Nuraddenni ka din ga tunawa da ni" yayi maganar yana murmushi.
Al'amin ya haɗiye wani abu mai tsananin ɗaci, ya kalli Nura,
amma ya kasa magana.
Nura ya sunkuyar da kai, yana share hawayen karaya.
Maman Nura ta fito ta gama wanke kayan Nura, muryar sa na
fita a hankali, ya kalli maman Nura ya ce "Me za a sayo muku ne? Da me
zaku karya ba ta tashi ba na taho"
Mama ta ce "Kar ka damu Al'amin, ƙanwata suna nan tafe,
da wuri za su zo, ai da ƙannensa ma su duba shi, baiwar Allah ai tana ƙoƙari
Allah dai ya raba ta da cikin nan lafiya, ta sauka lafiya ƙalau. Ai ta ce tuwon
dawa zan yi mata, da miyar ɗanyar kuka da man shanu idan ta haihu, in sha Allah
kuma ana ce mini ta sauka, zan dafo na taho kano, yajin daddawa ma ni zan yi
mata".
Nura ya ce "Mama ni dai ki tayani roƙo, na ce a saka
sunana idan an samu ɗan saurayi"
Suna yin hirar ne, dan Al'amin ya kwantar da hankalinsa, sai
dai fuskar nan tamau ya kasa yin fara'ar.
Ƙarfe takwas da mintuna, wata yarinya ta shigo ɗakin, 'yar
baƙa mai kyau, da siririn billenta, a gefen fuskarta.
Babu ko sallama ta faɗo ɗakin ta ce "Mama mun zo"
"Baki iya sallama ba ne?"
Ta ce "Assalamu alaikum, yaya wai da gaske ka je
Abuja?" Tayi maganar tana ƙarasawa gaban gadonsa.
Nura ya ce "Eh ramma, ya gida ya makaranta?"
Ramma ta ce "Lafiya ƙalau, yaya wai to ka ga shugaban
ƙasa?" Ya girgiza mata kai alamar a'a.
"To idan ka koma zaka ganshi? Ka ce masa dan Allah a
gina mana burtsatse, wurin ɗebo ruwa da nisa sosai"
Ya shafa kanta ya ce "To zan gaya masa, ina Sani?"
"Babanmu ya ce ba za a zo da shi ba, ya tafi makarantar
Allo, nima da ƙyar ya bar na biyo innar su jafarun muka taho".
Mama ta ce "Ke baki iya gaisuwa ba, balle ki yi wa
yayan naki yaya jiki ba?"
Ta kalli Al'amin ta durƙusa ƙasa ta ce "Ina wuni?"
Ya jinjina mata kai kawai, ta ce "Yaya sannu ya
jiki?"
"Jiki da sauƙi Alhamdilillah"
"To Allah ya baka lafiya"
Wata mace ce tayi sallama, tana faɗin "Ke kuwa ramma an
yi ƴar bantan uba, ina can ina bulayin in da aka kwantar da ku, kawai na nemeta
na rasa shashasha ba zaki yi hankali ba"
Ta zauna suka gaggaisa, Mama ta nuna mata Al'amin ta ce
"Atine ga uban gidan Nura, shi ya samo masa aikin nan, yake ta ɗawainiya
da mu"
Atine ta ce "Allah sarki, ni wallahi kama yake yi mini
da mai gyaɗa, yana kama da 'yar nan ta ta da ta rasu wadda tayi aure a birni,
zahra'u" da sauri Al'amin ya kalleta Mama ta ce "Wallahi kuwa, mun yi
waya da ita ma, ta ce zata zo duba Nura".
Taɓ yana da alaƙa da Nura ne, ko kuwa kawai dai hasashe ne,
ko abun su na mutanen ƙauye, da kowa ma ɗan uwan su ne? saboda tsabar
miskilanci bai yi musu magana ba, ya tashi ya tafi.
Ya je gidansa ma, ya kasa kawai ya tafi ya samu wani kango,
yayi zamansa, abun duniya ya ishe shi, bai ma san ta ina zai fara ba.
Bai koma gida ba sai can bayan la'asar sannan ya koma gida,
ba ta ce masa uffan ba, tayi masa sannu da zuwa, ita babbar godiyarta ga Allah,
dawowarsa lafiya, ba tare da wani abu ya faru da ita shi ba.
Sai dai ta haɗa abinci ta bashi, amma ta ga ya daɗe bai
motsa ba, daga baya ya ɗauki cokali ya din ga tura abincin da ƙyar, kamar mai
tura magani, ya gama ya nemi wuri ya kwanta bai ce mata uffan ba.
Duk da yanayin hakan bai yi mata daɗi ba sam, amma ta daure
ta ɗan bashi lokaci, amma taga a jere, kusan kwana uku, ba ya ce mata uffan,
kuma kullum sai ta yi bacci zai dawo, da asubar fari kuma yake ficewa. Idam ya
fitan nan, asibiti yake tafiya ya taimakawa babar Nura ta gyara masa jikinsa,
sai dai kullum jikin nasa babu sauƙi.
Ranar na haɗu, da ya fito zai fita ta tare shi ta ce
"Master, wai dan Allah laifin me na yi maka har haka ne? Meyake faruwa
yakamata ka sanar da ni"
Ya ce "Zan gaya miki idan na dawo" daga haka ya
fice ya bar ta.
Abun duniya ya ishi jauhar, ta kasa gane meyake faruwa haka
yake ɓoye mata.
Yana zuwa asibiti ya tarar da mahaifiyar Nura a gefen gadon
Nura, ta rufe shi, idanunta sun yi jawur.
Cikin matsanancin tashin hankali ya ƙarasa gaban gadon, ya
yaye zanin, ya tarar Nura ya cika.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ya furta
cikin matsanancin tashin hankali, ya zauna yayi shiru shiru, ya kasa zubar da
hawaye sai wani abu da yake yi masa zillo, tsakanin maƙogwaronsa da ƙirjinsa.
Ya saka gwiwoyinsa a ƙasa a gaban mahaifiyar Nura ya ce
"Ki yafe mini saboda girman Allah, ban taɓa tunanin abun da zai faru da
Nura kenan ba, da na san haka zata kasance wallahi ba zan tura shi ba"
Ta share hawayenta ta ce "Wallahi na sani, kuma ni ban
zargeka ba, Yanzu fatana Allah ya sa mutuwa hutu ce a gare shi, Allah ya yafe
masa kai ma ɗawainiyar da ka yi da mu, Allah ya baka lada".
Ya ɗauki waya ya sanar da su liti su samo mota, a asubar su
zo a tafi da gawar Nura Allah ya yi masa cikawa.
Sun girgiza sun kaɗu matuƙa da mutuwar Nura, da asubar aka
tafi da gawarsa gidan mai unguwa, ta ce ita za ta yi wa Nura wanka, Al'amin ya
tayata ya ce ban da su biyu, kar wanda ya je kan gawarsa.
Mai unguwa ya din ga bala'i, yana yayi asara kuwa, ya rasa
wanda zai gayyato kan gawarsa sai ɗan daba.
Maman Nura ta ce "Ɗa na bai yi asara ba wallahi, kai ka
yi asara, dan da ka kula da shi ka riƙe shi da mutunci da amana, ba zai faɗi
haka ba. Kuma ba in da aka ce ɗan daba ɗan wuta ne, ko an haramta masa zuwa kan
gawa".
Haka suka yi wa Nura sutura, aka sanar da rasuwar sa.
Duk da ana ganin Nura baya ji, amma ya tara mutane, saboda
daga baya duk wani aikin gayya na cigaban unguwa da shi ake yi.
Sai ƙarfe goma na safe, Al'amin ya dawo gida, yana zullumin
yadda zai gaya wa Jauhar mutuwar Nura, ga zuciyarsa da take wata irin tafasa
take raya masa kashe Indabo ya huta da baƙin cikin da ya jefa shi a ciki.
Cikin matsananciyar damuwa ta ce "Master wai meyake
faruwa dan Allah?"
"Allah ya yi wa Nura rasuwa"
Gaba ɗaya sai ta manta waye ma Nura, ta ce "Waye kuma
Nura?"
Ya ce "Guduma ɗan gidan mai unguwa" kamar
shashasha haka ta bishi da kallo, daga bisani wani irin jiri ya ɗebe ta, cikin
azama ya riƙe ta, jikinta ya hau wata irin tsuma, ta saka hannu iya ƙarfin ta,
ta toshe bakinta, dan hana kukan da yake ƙoƙarin taso mata fitowa amma ta kasa,
iya ƙarfinta ta din ga maimaita "Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Allah
ya sa ba Nuran da na sani ka ke faɗa ba"
Jiki a sanyaye ya zauna da ita a jikinsa ya ce "Ba kyau
yi wa mamaci kuka fa kin sani, ki yi masa addu'a"
Cikin kiɗimewa ta ce "To me zan ce?"
"Ki ce Allah ya jiƙan Nura yayi masa rahama"
Tari ta fara yi, ya ɗaga ta yana yi mata fifita, tare da yi
mata sannu.
Sai da ya tabbatar ta ɗan samu nutsuwa, sannan ya riƙe
hannunta, suka tafi gidan mai unguwa, idanunta sun kumbura sun yi jawur,
fuskarta ma tayi ja sosai da sosai.
Sai dai suna shiga ɗakin da mahaifiyar Nura take karɓar
gaisuwa, suka tarar da hajiya a ciki a zaune, a kusa da Maman Nura.
Hajiya ta ce "Al'amin, yanzu nake cewa zan kiraka na ga
kamar unguwarku ce nan"
Maman Nura ta ce "Ai wannan ne ubn gidan nasa da ya ɗauke
shi kamar ɗan uwa da nake gaya miki"
"To ai ɗan wurin Zahra'u ne, jikana ne"
"Iko sai Allah, Al'amin da kakarka da mahaifiyata uwar
su ɗaya uban su ɗaya, Allah bai saka mun san juna ba"
Ya zaunar da jauhar, ta zubawa mahaifiyar Nura ido, amma ta
kasa magana sai sheshsheƙar kuka, maman Nura ta rungumeta tana ƙoƙarin
rarrashinta, amma ta kasa sai suka cigaba da kukan tare gefe ga ramma da
ƙaninta sani, da suke uwa ɗaya da Nura, suma su na ta kuka, hakan ya ƙara karya
zuciyar Al'amin.
Har aka gama zaman makoki, Al'amin yana cikin damuwa da
tashin hankali, Hajiya da su ramma, a gidan Al'amin suke kwana, har zuwa kwana
bakwai, sai dai kafin a gama zaman makoki, mai unguwa ya fara yada maganganu
cewar Al'amin ne yayi silar mutuwar ɗan sa, Allah kaɗai ya san ina ya kai shi,
idan abun gaskiya ne, meyasa shi bai je ba ya tura shi.
Kafin a ƙare zaman makokin, sai da maman Nura suka yi
kaca-kaca da mai unguwa, ta ce Al'amin babu yadda za ayi ya kai shi in da za a
cuce shi, idan ma haka ne, ai ɗan uwansa ne ba ruwansa.
Aka share zaman makoki, amma Al'amin ya kasa cigaba da
walwala, tun jauhar na bin sa na tambayarsa ko lafiya? Ta yi rarrashin tayi ban
bakin, har ta gaji ta zubawa sarautar Allah ido.
Zuciyar sa na ta azalzalarsa ya bi Indabo can Abujan, ya
halaka shi kowa ma ya huta, amma ya daure ya jira ya dawo.
Sai da Nura yayi sati uku, sannan aka gaya wa Al'amin Indabo
ya dawo.
Gaba ɗaya baya cin abinci yadda yakamata, idan ya fita baya
iya zuwa wurin sayar da shayi, sai ya samu wurin da babu wanda zai takura masa
ya kwanta yayi ta tunani, ya din ga jin da ma bai san Nura ba a rayuwarsa gaba ɗaya
da duk haka bata faru da shi ba, ashe duk abun nan ma suna da alaƙa da juna.
Hatta jauhar yanzu ba ta iya samun kulawarsa yadda yakamata,
dan ko in da take ya daina zuwa, ba ya dawo wa ma sai ta yi bacci.
Gashi ta shiga wata na bakwai, haki ya sakata a gaba, ga
nauyin cikin ya fara damunta, da ƙyar take iya tafiya.
Indabo yana zaune a falonsa, yana ganin mutane, ya ga
Al'amin ya faɗo falon kamar daga sama.
Cikin sauri ya sallami waɗanda suke tare da shi, ya miƙe
tsaye ya ce "Mai zamani lafiya kuwa? Ya na ganka a haka?"
Kafaɗar Indabo ya daka ya hantsila kan kujera, "Me
zamani distinguish senator kamar ni ka yi wa haka, dan na sakar maka na ba dama
a kaina?"
"Zuwa na yi na gaya maka shukar da kayi tayi
huda".
"Kamar yaya?"
Al'amin ya kalle shi da jajayen idanunsa ya ce "Ba na
jin magana, amma wallahi ba na cin amana, kuma duk wanda ya ci tawa sai ya
biya. Nura guduma ya mutu, na karɓi saƙonka ka jira amsar da za ta biyo
baya".
Ras! Gaban indabo ya faɗi, dan ba haka suka tsara ba, ya aka
yi ya san Nura ya mutu?.
"Ban gane Nura ya mutu ba"
"Shut up! Ka sam komai, tsohon munafuki algungumi, na
san komai, ka lalata rayuwar yaron da nayi niyyar ingantawa. An dawo da shi rai
a hannun Allah, na san baka san ya aka yi aka dawo da shi gida ba, bayan ka
shirya yayi hatsari idan ya tashi dawowa yadda zaka ɓatar da abun da ka aikata.
Wallahi ka ci amanar Al'amin kuma sai ka biya.
Ba ka yi mamakin yadda nake yi maka biyayya ba na yi duk
abun da ka ke so?, ka zata kawai saboda kana bani kuɗi ne? Bari na tuna maka ni
yaron dodo ne, dodo babban sarki doodn da yake ɗauke da makamin tarwatsaka, ka
zata ya mutu da sirrin nan a cikin sa ne? Wallahi ma'aruf na sanka fiye da
yadda ka san kanka, a Nigeria ko wajen Nigeria wuraren da ka ke tafka
tsiyatakunka.
Wallahi na buɗe bakina a kanka, ka gama kaɗewa bar ganin
kana da rigar kariya, kuma ku ne ku ke juyar ƙasar, dodo ya mutu ya bar ni da
babban kundun da zan iya rusa ku.
Niyyata idan na zo na kashe ka, sai dai hakan ba zai saka na
huce ba, saboda yanzu ba irin da ba ne, na ajiye wanda suke buƙata ta. Akwai
dabarun da masu kimiyyar lissafi suke bi, wurin yin solving wato BODMAS.
Bracket Open, division, multiplication addition sannan subtraction. To ni
upside down nake yi indabo, sai na fara division nake multiplication na yamutsa
komai sannan na saka a bracket na rufe.
Ka rubuta ka ajiye daga yanzu, ni ne babbar barazanar
rayuwarka
Daga yanzu duk motsin da zaka yi, zaka yi shi a tsakanin
tarkunan da zan saka maka, ka daina shan ruwa cikin kwanciyar hankali, ni ne
magajin dodo kuma zaka biya cin amanar da ka yi mini" ya juya ya fita yana
huci.
Cikin tsananin tashin hankali, Indabo ya tashi, ya ɗauki
wayarsa ya daddana, ya kara a kunnensa.
Cikin tashin hankali ya ce "Ya aka yi Nura guduma ya
bar gidan nan, garin yaya? Waye ya dawo da shi kano ban sani ba wane munafukin
ne ya rusa mana plan?"
Jifa yayi da wayar, ya hau safa da marwa, cikin tashin
hankali "Kenan kallon biri yake yi mini duk tsawon lokacin da muka yi
tare? Amma Allah ya tsinkewa dodo albarka, ya ƙara tsine masa cin amanar da ya
yi mana kenan?" Ya kuma ɗaukko wata wayar ya kira P.A ya ce "Maza ka
ƙaraso gida ina nemanka".
Ya ajiye wayar ya cigaba da kaiwa yana komowa.
Afujajan P.A ya ƙaraso, ya ce "Yallaɓai ya ake ciki ne,
meyafaru na ganka cikin tashin hankali?"
"Dodo"
P.A ya ce "Me dodon yayi?"
"Dodo ya daɗe da kashe mu, kafin mu kawar da shi ashe
ya gaya wa mai zamani komai? An dawo da yaron nan Nura kano, ya san komai, na
yi waya wai an nemi obi an rasa, ya gudu yanzu ya san komai, na kaɗe idan yayi
magana ya gama rusa ni, Allah ya tsinewa dodo albarka"
"Ka kwantar da hankalinka, honorable wai waye wani mai
zamani, me aka yi aka yi shi ne? Mutum nawa ka kawar kan mu zo in da muke
yanzu? Ba zai tayar mana da tarzoma ba, bayan mun yi nasara kawar da shi kawai
zamu yi"
Indabo ya ce "Tayaya wannan yaron mai shegen taurin
rai, da ƙarfin tsiya, ashe tsawon lokacin nan kallona kawai yake yi"
P.A ya ce "Kwantar da hankalinka akwai abun yi, zan yi
maka bayani".
Cikin dare jauhar na zaune tana lazumi, tayi sallar dare, ta
ji shigowar Al'amin, ta ɗan jira wasu mintuna, sannan ta bi shi ɗakinsa.
Ƙwayoyi ta tarar da shi ya haɗa zai sha, cikin azama, ta
durƙusa ta kwashe ƙwayoyin, ta dube shi ta ce "Akwai abun da ka ke ɓoye
mini master, ba iya mutuwar Nura ce take damunka ba, akwai wani abu a ƙasa ka
gaya mini. Baka saba ta'amalli da ƙwayoyi haka ba".
Yayi shiru bai ce komai ba.
"Master ka yi mini magana dan Allah ka gaya mini "
tayi maganar cikin matuƙar rauni.
"Ki yi haƙuri ki je ki kwanta, dare yayi"
"Ka san kwana nawa nayi bana iya bacci, saboda damuwar
da ka ke ciki? Kallonka kawai nake yi kar na takura maka ina jiran ka yi mini
bayanin menene amma shiru, haba master ka gaya mini dan Allah"
Ya juyo ya riƙe hannun jauhar, yana murzawa cikin
matsananciyar damuwa, ya sunkuyar da kai ya ce "Duk da abun a ɓoye ne,
amma bai kamata na ɓoye miki ba, bai kamata na bar abun a raina nikaɗai
ba".
Sai a lokacin ya gaya wa jauhar abun da ya faru.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un" tayi ta
maimaitawa cikin matsanancin tashin hankali.
"Master, ka ga irinta ko? Yana ɗaya daga abun da ya sa
nake ta fatan ka nesanta kanka da mutumin nan, ya cucemu amma kansa ya yi wa.
Baka yi da niyya ba, Allah ya jiƙan Nura ya saka masa"
Al'amin ya kifa kansa a kan cinyar jauhar, sai a lokacin ya
ji wasu irin hawaye suka zubo masa.
"Sadik ya mutu a sanadina, Nura yayi wulaƙantacciyar
mutuwa a dalilina, na zama annoba kenan? Mahaifiyar Nura har ta mutu ba zata
manta, ni na kai yaron ta, in da ka yi dalilin gurɓata masa rayuwa ba"
Jauhar ta girgiza kai ta ce "Dan Allah ka daina faɗar
haka master, kowa abun da Allah ya rubuta masa yake riska ba kaine sila
ba" tana kuka tana rarrashin sa.
Tun da Allah Nura ya mutu, Al'amin ya ƙara nutsuwa, babu
abun da yake yi masa daɗi. Ita kanta jauhar ta kasa daina jin ɗacin rashin
Nura, dan tun da Al'amin ya ce masa an samo masa aiki a Abuja yake murna, yake
bata labarin shi wata yarinya ya gani yake so, kullum sai ya je ƙofar
makarantar islamiyyar su idan an taso su ya ganta, yanzu yana fara aiki, idan
ya ginawa mama gida a cikin kano, ta dawo sai ya nemi auren yarinyar, amma kar
ta gaya wa master.
Take yi masa dariya ta ce masa ai mamansa aure take yi sai
dai ya haɗo da mijinta, ya ce ya fasa zai yi aure ya ɗaukko ramma ta dawo cikin
gari, ta baro ƙauye.
Ta ce "Ban da abunku Nura haryanzu fa da sauran
ƙuruciyarka, ɗawainiyar aure da yawa fa".
Ya ce "Ni dai kawai ki yi mini addu'a, da na dawo, zan
fara zuwa wurin yarinyar nan zance"
Da haka tayi ta tuna ire-iren hirarsu, da barkwancinsa, ta
kasa mantawa da shi.
Al'amin har tofa ya sake zuwa, ya yi wa mahaifiyar Nura
gaisuwa, ya kai mata abun alkhairi, ya biya ya gaida Hajiya ya dawo gida.
Jauhar cikinta yayi girma sosai, kamar kana fita ka dawo
zaka tarar ta haihu, ƙafafuwan ta duk suka kukkumbura, saboda girman cikin, aka
ce yana shiga wata tara ayi inducing ɗin ta ta haihu ta huta, dan bayan nauyin
cikin kullum cikin haki take, a haka kuma take lallaɓawa ta je makaranta.
Wurin shayin Al'amin kuwa, wasu irin kuɗi ne suke shiga suna
fita, dan tun safe ake aikin ɗorawa da saukewa, ya zama chamber matasa sosai da
sosai, duk da suna sayar da kayan shaye-shayen su a wurin, ba sa cutar Al'amin
shi kuma ba ya yi musu mugunta.
Da safe su yi shayi, da rana indomie shayi, taliya haka suke
wuni saye da sayarwar abinci.
Juahar sun gama haɗa kayan haihuwa, dan washegari ne ya kama
ranar da za su je ayi mata inducing, tana ta jin tsoro yana kwantar mata da
hankali.
Ta ce "Master"
Ya ce "Mmm"
"Ka ji sai motsi yake yi, kamar ya san gobe in Allah ya
kaimu za a fara inducing ɗin nan"
Ya ce "Ya ƙagu ya ga daddynsa, Nuradeenin daddy, in sha
Allah sunan Nura zan saka, kamar yadda na yi masa alƙawari".
Ta ce "Allah ya jiƙan Yaya Nura ya sa ya huta"
Ya ce "Amin".
Cikin shagwaɓa ta ce "Amma a gabanka zan haihu master,
tsoro nake ji, an ce haihuwa akwai wahala fa"
"Ba wata wahala in sha Allah, ina kusa da ke, ina yi
miki addu'a zaki haihu, Ni zai fara gani kafin ya ganki " yayi maganar
yana sumbatar cikin nata.
"Ni dai na fuskanci ba a so na, ta babynka kawai ka ke
yi" tayi maganar cikin shagwaɓa.
"Ni na isa? Dukkanku ina sonku madarata"
"Ba wani, ni baka taɓa cewa kana so na ba".
Yayi murmushi ya ce "Amma kina gani a aikace ai".
"Baka taɓa faɗa ba"
Yayi dariya ya ce "Ai ke da ruwan zinari aka rubuta
sunanki a zuciyata. Ina sonki madarata, ina ƙaunarki ƙauna mai tsanani ya fi
ubban shadidan"
Ta ce "Wayyo Allah daɗi. Wallahi har cikin tsakiyar
zuciyata na ji kalaman nan, ba ka taɓa gaya mini ba, ka cigaba da gaya mini, da
daɗi"
Ya ƙara rungumeta ya ce "I love you madarata"
"I love you too babyna, kuma baban babyna, masterna
abun ƙaunata"
Har mamakin irin kalaman soyayyar da suka din ga musaya take
yi, da ba ta taɓa tsammanin jin su daga bakin mastern ba.
Cikin matsanancin shauƙin so da ƙauna, suka kasance cikin
farin ciki. Suka yi wanka, ya rungumota daga toilet tana takawa a hankali da
ƙaton cikinta a gaba.
Ya taimaka mata, ta saka rigar bacci, sannan suka kwanta, ta
kwanta a jikinsa, tayi balance da ta motsa sai yayi mata sannu.
Wani irin nannauyan bacci ne yayi awon gaba da ita.
Ji tayi kamar ana kokowa a falo, ta laluba ba ta ga Al'amin
ba, ga wani irin ƙaurin taba ya cika ko ina.
Hasken fitila ta hango an kunna ƙwan falo, ta saukko ta fito
falon tayi arba da wasu matasa hannunsu riƙe da miyagun makamai, madaki ta fara
ganewa gabanta ya faɗi.
Sun rirriƙe Al'amin, suna shaƙa masa wani abu, jikinsa ya
saki yana ta layi.
Madaki ya bushe da dariya ya ce "Ka ce baka ji, dama ka
ce da ni da kai sai wani ya kawo ƙarshen wani, to ni zan kawo naka ƙarshen yau
ina dodon da kake taƙama da shi? Duk da zuwan ba nawa bane ba, na uban gidanka
ne Indabo, amma ya jaddada mini in tabattar ka tafi da wani mugun miki a
zuciyarka".
Cikin tashin hankali jauhar ta janyo jikinta ta nufi in da
Al'amin yake tana kiran sunan sa "Al'amin me ka yi musu ne? Dan Allah ku
yi haƙuri mana".
Al'amin ko harshensa ya kasa motsawa, balle wata gaɓa ta
jikinsa.
Madaki ya riƙo gashin jauhar, ya kalleta ya ce "Yanzu
kin zama ragowa, ni kuma ba zan ɗana abun da yake ragowar maƙiyina ba, gashi
kin zama cuus" ta riƙe ƙasan gashinta da Madaki ya riƙe.
Cike da mugunta, ya saka ƙafa ya kawashe na jauhar ta gaba
ya saketa, ta faɗi a kan cikinta, ta ƙwala wata irin razananiyar ƙara ta ce
"Ya Allah, Ya Allah, Ya Allah" ta faɗa sau uku, take jini ya fara
malala daga jikinta, harshen ta kawai take motsawa a hankali tana kiran sunan
Allah, ta din ga ɗaga hannunta tana son kiran sunan Al'amin. Ya ƙura mata ido
yana kallon ta, cikin buguwa da mutuwar jiki, tun tana ƙoƙarin magana a hankali
har ta daina motsi.
Madaki ya samu wani ƙarfe ya bugawa Al'amin a ka, shi ma
suka sake shi a wurin.
Ayshercool
08081012143.
🔞₦500 ne via
0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Wayar Walid ce ta fara ringing, yayi shiru ya cirota daga
aljihunsa ya kara a kunnensa ya ce "Ya aka yi?"
"Oga walid ka yi sauri ka dawo dan Allah, ya fara
dawowa hayyacinsa, kar ya dawo gaba ɗaya ka san ba zan iya da shi ba".
Walid ya ce "Gani nan, ka yi iya ƙoƙarinka, kar ka
kuskura ya fita, idan ya fita akwai ƙura ka sani, gani nan zuwa" ya katse
wayar ya sakata aljihunsa, ya kalli matasan ya ce "Ku mayar da ita
kawai" ya juya zai tafi.
Cikin azama Nabila da idanunta suka yi ja saboda kuka ta ce
"Dan girman Allah ka yi haƙuri, kar ka tafi, ka ƙarasa mini labarin nan,
yaya aka yi Viper ya tafi prsion? Shi aka ɗorawa kisan matarsa? Ta mutu ne ma
ko kuwa yaya aka yi, ya kuma aka yi ya fito yanzu? Ni abubuwa da yawa ban gama
fahimtar su ba, sun cukurkuɗe mini sun shige mini duhu, dan Allah kar ka tafi
baka ƙarasa mini ba"
Walid ya ce "Ba zan ƙarasa ba ɗin, ba dai ke mara
mutunci ba, na ɗauka haɗuwarki da shi, zai zama alkhairi amma ki ka yi mana
halinku na mata, laifina ne da na kawo masa ke, Al'amin ya daɗe da cire mata a
rayuwarsa, sai zuwan jauhar cikin rayuwarsa daga kawo ki a tashin farko kin
mayar mana da hannun agogo baya, Viper ba zai taɓa zama ya bar liti a tsare ba,
saboda shi ɗan halak ne"
Cikin matsananciyar damuwa ta ce "Na ji, na yi kuskure
amma dan Allah ka yi haƙuri ka ƙarasa mini"
"Ba zan ƙarasa ba, ki je shi ya ƙarasa miki"
Cikin hanzari ta sake tarar Walid ta ce "Dan Allah ka
sake yi mini jagora, ka kai ni wurinsa na nemi afuwarsa, na yi kuskure kaina ne
ya riga ya gama kullewa na faɗawa lamuran a gaggauce cikin duhun kai, amma a
shirye nake na gayara kuskuren da nayi"
Walid ya ƙare mata kallo ya ce "Kin riga kin aikata
abun da ba zai gyaru ba, kuma kar ki sake yin gangancin zuwa in da yake, idan
ba haka ba, ko bai kashe ki ba ni zan kashe ki. Ku ɓatar da ita daga
gabana".
Suka saka Nabila a gaba, suka tasa ƙeyarta zuwa cikin napep ɗin
da suka kawota, tana ta kallon walid tana yi masa magiya, amma suka ja babur ɗin
suka tafi da ita.
Suka mayar da ita hanyar law firm ɗin su, suka bata wayarta
suka tafi, wani abun hawan ta tare, ta nufi gida, zuciyarta sai bugawa dake da
sauri da sauri, cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali, ga matsanancin
tausayin Al'amin da ya mamaye zuciyarta, lallai an yi wa rayuwarsa yankan ƙauna
mafi munin da har ya mutu ba zai manta da shi ba.
A falo magajiya take ce mata sumayya ta zo har gida tana
nemanta, duk an kira layukanta ba sa shiga, ko akwai matsala ne, gashi yau ta
daɗe sosai ba ta dawo ba.
Ai har baba magajiya ta gama maganarta, ba ta fuskanci komai
ba, ta tafi ɗakinta ta rufe ƙofa, wayarta na ta ringing ta duba, missed calls ɗin
sumayya sun fi ashirin, ga na Nasir, ban da barrister Habib, ta kashe wayar, ta
cillata kan gado, ta shiga banɗaki tayi alwala ta fito ta yi sallar azahar da
la'asar.
A kan daddumar ma haɗa kai da gwiwa ta yi, ta din ga kuka,
za ta iya cewa tun da ta buɗe ido a duniya, ba ta ji labari mai ban tausayi da
tsayawa a zuciya ba kamar na Al'amin.
"Why Nabila kin yi garaje, why would you judge the
book, according to cover? Why?" Ta tambayi kanta cikin tsananin takaicin
abun da ta aikata.
Ta kifa kanta a kan gadonta, wani abu tsananin ɗaci yana yi
mata zafi a tsakanin ƙirjinta. Gaba ɗaya ta ji ta tsani kanta, wani mugun
haushin kanta ya isheta.
"Ko yaya yake ji a zuciyarsa yanzu? Dole ya zama
bugagge gaba ɗaya, amma idan aka bar shi ya cigaba a haka, to tabbas zai
haukace, amma yanzu yaya za ayi na samu ƙarashen labarin nan? Ta haihun ko
mutuwa tayi, kuma wa ya kashe aka kai shi prison? Wait, to yaya ma aka yi aka
sake shi daga prison ɗin, yana yawonsa idan ya ga dama har ya je yayi ɓarna,
kuma still a haka wai nansa ake yi. Wai wannan wane irin lamari ne mai
sarƙaƙiya haka? Kar na je na haukace a banza mana" tayi maganar kamar za
ta haukace ɗin.
Ta cigaba da sintiri, tana ƙirga yatsunta, tana lissafi.
"Kai dole na samo ƙarashen labarin nan, ko da kuwa me
zai yi mini, ko dai wanda ya fara ya ƙarasa mini, ko kuma shi Vipern ya ƙarasa
mini, no matter how and what it takes sai na ji ƙarshen labarin nan, kuma sai
na yi wani abu a kai. Haba dan Allah What a pitful life of his? Kai, to ita
meye nata ma da za ayi mata haka? Me ta yi she don't deserve this at all"
tayi maganar tana fashewa da kuka iya ƙarfinta.
Bugun ƙofar ɗakinta ake yi, amma ko gezau, da ta gaji da jin
bugun ma, sai ta tashi ta tafi banɗaki, ta rufe ƙofa ta kunna fanfo, ta cigaba
da kuka da tunani.
Ƙarfe takwas na dare Abba ya dawo gida, Nabila ya fara
tambaya tana ina, Mama ta yamutsa baki ta ce "Ta dawo"
Ya jinjina kai, ya tafi sashensa, har ya fara cin abincin
dare, ya ajiye cokalin ya kalli mama ya ce "Kirawo mini ita, ina ga ba ta
san na dawo ba"
Haushi ya ƙule mama, ta tashi ta fita, ta je ɗakin Nabila,
ta tarar da ƙofarta a rufe, ta din ga jijjiga ƙofar tana bugawa, amma ba ta buɗe
ba.
Magajiya ta ce "Hajiya tun da ta dawo fa ta rufe kanta
a ɗaki, taƙi buɗe wa, ba yadda ban yi ba taƙi buɗewa"
Mama ta yi tsaki, ta koma ta ce wa Abba, "To ka ji tun
da ta dawo, ta rufe ƙofa taƙi buɗewa"
"Kuma lafiyarta ƙalau?"
"Ƙalau take, tsagwaron iskanci ne"
Ya girgiza kai ya ce "No, ko an ɓata mata rai ne, a
wurin aiki ko a gida, ƙyaleta na ganta da safe na ji menene, ko kuma rigimar ce
ta motsa" yayi maganar yana murmushi. Wani malolon takaici, ya ƙule mama,
yadda yake lallaɓa Nabila, yana bin ta kamar wata uwarsa.
***
Abdul kuwa ganin ramma taƙi mayar da hankali ta ci abinci,
hakan ba ƙaramin ƙular da shi yayi ba.
Ita kuwa jikinta ne babu daɗi, ga kewar gidansu, tana
tunanin mama, ga baƙin cikin abun da yake aikata mata, gashi ya sakata a gaba
duk sai ta kasa cin abincin.
Tana cikin zancen zuci, ta ji hannunsa a kan fusarta, ta
tsorata ta ja da baya, ya tsuke fuska ya ce "Meye haka ne?" Ya buɗe
idonta, ya ga she's still pale.
"Solomon" ya ƙwalawa kukunsa kira.
Solomon ya fito tare da cewa "Yes sir"
"Kana da kayan miya ko?"
Solomon ya jinjina kai alamar eh.
"Kawo mini tumaturi manya guda uku, da wuƙa ka haɗo
mini da Apple ja guda biyu"
Ya ce "Ok sir" ya cigaba da kallon ramma, da ta
ajiye cokalin, ta hau jan rigarsa da take jikinta, tana rufe ƙafafuwanta.
Mintuna kaɗan solomon ya dawo, da plate biyu, ɗaya ɗauke da
tumatir, ɗaya kuma Apple sai ƙaramar wuƙa guda ɗaya.
Ya karɓa, ya matsa kusa da ita, ya ɗora ƙafarsa ɗaya a kan
cinyoyinta, ta ɗago cikin rauni idanunta sun tara hawayen takaici, ya yanka
tumatirin ya miƙo mata. Ta tsaya tana kallonsa tana kallon tumaturin.
Miƙa mata yayi bakinta, ta kawar da kanta ta ce "Ni ba
zan iya cin tumatur a haka ba"
"Zaki karɓa ko sai na burma miki wuƙar nan a
ciki?" Yayi mata maganar cikin tsawa. A tsorace ta buɗe baki, ya din ga
bata tumaturin nan, tana taunawa da kyar.
A zatonta zai bata tuffar, ta washe bakinta da ta ci
tumatur, amma ya hau yanka tuffar yana ci, yana yi mata tauna a fuska, yana
kallonta ga ƙafarsa a kan cinyoyinta da tayi musu nauyi.
Ya gama cin Apple ɗin sa, ya taɓa wuyanta ya ji babu zazzaɓi,
ya ce "Haryanzu kina zubar da jinin ne sosai?" Tayi masa banza kamar
ba da ita yake ba, ya harzuƙa ya ɗaga hannu zai kwaɗa mata mari, ya ga ba ta
motsa ba, sai hawaye da yake bin kuncinta.
Ya janye ƙafarsa daga kan cinyarta, ya ce "Ki cigaba da
ina yi miki magana kina kallona, ki yi mini banza kashe ki zan yi a banza"
tayi shiru ba ta tanka masa ba.
Jin ana knocking ɗin ƙofar falon, ya sanya ya tashi tsaye,
ya ce "Tashi ki tafi ɗaki, za a shigo". Ga mamakinsa ko gezau ba ta
yi ba, ta cigaba da zama tana zubar da hawaye.
Zuba mata ido yayi, cike da tsananin mamakin shegen taurin
kai a wurin kucakar 'yar ƙauyen yarinyar.
Tashi tsaye yayi, ya fizgi hannunta, amma ta faɗi a wurin,
saboda dama jikin babu ƙwari, ga jiri tana ta fama.
Ya durƙusa ya ɗauke ta, ya nufi bedroom ɗin da ita, a bakin
ƙofa ya dungurar da ita ta ciki, ya ja ƙofar ya rufe, ya koma ya buɗe ƙofar
falon.
Wata matashiyar budurwa ce a tsaye, sanye cikin doguwar
rigar material, sai hula a kanta, hannunta riƙe da Jakarta.
"Ko wata ce a ciki ne? Ina ta bugu amma baka buɗe
ba?" Bai yi magana ba, ya bata hanya, ta shigo ta ajiye jakarta ta nemi
wuri za ta zauna ta ce "Abdul, staining ɗin jini nake gani a kan kujerar
nan"
Cikin ko in kula ya ce "And so?"
"Mace ka kawo gidan nan?"
"Eh, akwai magana ne?"
Cikin takaici ta ce "Abdul don't try me, ka sanni ka
san halina, ba zai yiwu nayi dumping guys ɗina just because of you ba, and ka
din ga rough play da ni ba"
Yayi murmushi ya ce "Nina, ki na da matsala, saif ne ya
yanke hannu da wuƙa, yana cin Apple, yayi bleeding sosai, amma ba abun da ki ke
tunani bane ba" tayi ajiyar zuciya ta ce "Yauwwa ko kai fa, har
hankalina ya tashi, i so much miss you" tayi maganar tana rungume shi.
Gaba ɗaya sai ya ji banbarakwai, kamar ranar ya fara
rungumeta, haka ya lallaɓata suka tafi ɗaya ɗakin sheƙe ayarsu, sai dai
hankalinsa na kan ramma, kuma gaba ɗaya ya ji bai samu abun da ya samu a
tattare da 'yar ƙaramar baƙauyyiyar yarinyar ba.
Duk yadda ya so mazewa, sai sa Nina ta fuskanci hankalinsa a
ba a kanta yake ba da tayi magana sai ya ce mata ba shi da lafiya ne.
***
Har washegari, Nabila ba ta ci abinci ba, ta dai buɗe ƙofar
cikin dare da zafi ya isheta, ta fara numfashi da ƙyar.
Ta ɗaukko wayar Viper, ta din ga kallo, kamar shi ne a
gabanta, ta rintse idanunta tana tuno kamanninsa, a zahiri suffarsa ta ban
tsoro ce, amma a baɗini abun tausayi ne.
Ƙarfe takwas na safe, yaran gidan na ta zuwa gaida Abba, sai
da sauda ta shigo ta gaishe shi, ya ce "Sauda duba mini Arfa ko ta buɗe
ƙofar, ki ce mata ina bata haƙuri idan laifi nayi mata, da ya sanya tun jiya ba
ta neme ni ba, yau kuma ba ta zo ta gaishe ni ba" Sauda ta tashi, ranta a ɓace
ta tsani yadda Abba yake sakata a shirgin Nabila ta girmeta gashi ba shiri suke
yi ba, amma ayi ta zubar mata da girmanta.
Ta je ta tura ƙofar ɗakin taga ta buɗe, taga Nabila a kwance
a kan gado, ta kwanta a kan hannunta, ta murɗe jikinta.
"Ke! Malama ki taso Abba yana kiranki" sai dai
shiru Nabilan ba ta motsa ba.
Walida ce ta shigo ɗakin tana faɗin ta ga dama ta buɗe ɗakin
kenan, sai dai tana ganin irin kwanciyar da Nabila tayi ta ja ta tsaya.
A fusace sauda ta tafi ta ɗala mata duka Walida ta ce
"Yaya sauda kina ganin irin kwanciyar da tayi, da ƙyar idan ba iskokai za
ta yi ba" da sauri Sauda ta ja da baya ta ce "Taɓ wallahi ba zata
dake ni a banza ba" Nabila ta saka hannayenta, ta toshe kunnuwanta dan ta
daina jin maganar su.
Sauda ta koma ta gaya wa Abba, cewar Nabila iskokai ta
tayar.
Abba ya taso yana yi wa sauda faɗa, a kan cewa ya hana cewa
Nabila tana da da iskokai, takura ce kawai ba ta so da ɓacin rai.
Ya ƙarasa ɗakin yana kiran sunan Nabila.
Ya ɗagota daga kwanciyar da ta yi, jikinta yayi wani irin
mahaukacin zafi, har wani huci take yi.
Idanunta sun kumbura sun yi suntum, ga wani irin ja da suka
yi, ga wasu irin siraran jijiyoyi da suka kwanta a saman goshinta.
Sai da Abba ya razana da yanayin da ya ganta, "Arfa,
meyasame ki haka? Meyake yi miki ciwo"
Ta buɗe baki za ta yi magana, amma bakin ya din ga karkarwa
ta kasa furta komai, hawaye ya din ga bin gefen idonta.
Ya kalli walida ya ce "Bani bedsheet a rufe mata
jikinta" ta duba ta ɗaukko masa, ya rufe wa arfa jikinta, ya din ga tofa
mata addu'a.
Wani abu mai nauyi, ya tokare mata ƙirji, ya hana
numfashinta fita yadda yakamata, a ƙalla Abba ya kai awanni biyu, yana yi mata
addu'a yana tofa mata, sai bin sa take yi da ido, amma ta kasa magana, sai can
wani irin nananuyan bacci ya ɗauke ta, dan ba ta yi bacci ba jiya gaba ɗaya.
***
Walid ne yake ta kokowa da Al'amin, a kan lallai sai ya fita
ya kai kansa wurin 'yan sanda, a sakar masa liti, shi a kama shi, amma kafin
nan sai ya fara kashe Nabila.
"Ita wannan da tayi maka abun da bai taka kara ya karya
ba zaka kashe, ko kuma zaka fuskanci indabo da madaki ne ka bar maganar wannan
ƙaramar alhakin?".
Viper ya ɗaga rinanun idanunsa jawur da su ya ce "Zuwa
yaushe? Zuwa yaushe mutane za su daina cutuwa a dalilina? Ba zan sake gangancin
da na yi a baya ba, dole a saki liti, in dai kai kaina zai saka a sake
shi"
"Is a minus case, dole zai fita, amma bama buƙatar a
sake kama ka, ka gane mana, dole mu shirya ɗaukar fansar ka"
Viper ya sake kallon Walid ya ce "Sai na kashe yarinyar
nan fa"
"Indabo yakamata ka kashe da Madaki, wani tunanin
yakamata ka yi a kan wannan yarinyar ba wannan ba"
"Tarko aka yi mini da ita, ko ba ka gani?"
Walid ya girgiza kai ya ce "Haryanzu bamu da tababcin
hakan, amma ba ka da wani sharhi ko tunani a kanta?"
"Babu, idan na sake ganinta kuma sai dai wata ba ita
ba" ya bashi amsa kai tsaye.
"Shikenan, yanzu dai zan fita in ga me za ayi a sako
mana liti".
Viper yayi shiru bai ce masa komai ba, sai da ya yinƙura zai
tashi, Al'amin ya riƙe shi. Walid ya juyo ya kalleshi ya ce "Ina alƙawarin
da ka yi mini?"
Walid ya ce "Ina sane, haryanzu kayan ba su sauka bane
ba, ka san yanzu hanyar akwai tsaro sosai ba irin na da bane ba"
"Bani wanda ka kwashe ka fita"
Cikin damuwa walid ya ce "Wai dan mai zamani so ka ke
yi sai ka haukace ne gaba ɗaya hankalinka zai kwanta, wannan uban ƙwayoyin da
ka ke jibgaw kanka ba abun da suke yi maka, jikinka duk ya riga ya bujire, ka
yi haƙuri mu bi a sannu"
"Mai laya.....
Walid ya ce "Mai zamani"
"Ka yi mini abun da nake so, ai na riga na daɗe da gama
haukacewa, ka bani idan na cigaba da zubawa na san za su yi mini"
Walid ya girgiza kai ya ce "Da za su yi maka, da tuni
sun yi, ka yi haƙuri ka bani lokaci"
Al'amin ya waro masa idanunsa ya ce "Ka fara kaini
bango, baku san fa me nake ji ba, bana bacci, ƙwaƙwalwata so take ta tarwatse,
sonake komai ya shafe daga cikin kaina, ko da hakan yana nufin zan
haukace"
"Fansar ta ka fa"
"Zan ɗauka"
Walid ya yinƙura zai fice ya bar Al'amin, amma ya sake riƙe
shi, Walid yana ƙoƙarin ƙwacewa, hakan ya ƙara tunzura Al'amin, ya fara ƙoƙarin
shaƙe Walid.
Babu yadda Walid ya iya, duk da yadda Al'amin yake zuba wa
kansa kayan maye, amma yafi ƙarfin sa, ya dunƙule hannu, ya daki jijiyar wuyan
Al'amin, ya silale ya faɗi ƙasa.
Yayi sauri ya durƙusa a kansa, ya ga Al'amin yana ta ƙifta
idanunsa, bai kai ga suman ba, jikinsa ya saki gaba ɗaya.
Walid ya dafe kai yayi shiru, abubuwa na neman su ƙwace
musu, gashi alamu sun fara nuna ƙwaƙwalwar Al'amin na nema ta fara taɓuwa.
Ya dafa kafaɗar Al'amin ya ce "Ka ƙara bamu lokaci ɗan
uwa, zamu kawo ƙarshen komai, da yardar Allah" ya tashi ya fice.
***
Abba da magajiya sai anty, su ne suka yi ta ɗawainiya da
Nabila, har ta ɗan samun nutsuwa, take ta uban bacci, tana tsaka da baccin
sumayya ta zo, dan jiya hankali a tashe ta kwana, ta jirata har ta gaji, taje
can wurin aikinta an ba ta je ba, ta zo gida an ce ba ta zo ba, ga lambobinta
ba sa shiga, ta din ga fargabar Allah ya sa ba su indabo ne suka yi mata wani
abun ba, gashi suka din ga kiranta suna tambayarta ta gaya musu me suka
tattauna da Nabila.
Yanayin da ta ga Nabila, ya tsoratata, gaba ɗaya kamar ba
ita ba, duk ta yi wani iri.
Cikin ikon Allah ta farka daga nannauyan baccin da ya
kwasheta, da sumayya ta fara tozali, cikin kulawa sumayya ta ce
"Sannu" ta jinjina mata kai kawai.
Duk shegen surutu irin na Nabila, sai bakin ya mutu, ta kasa
cewa kowa uffan.
Sai da suka kaɗaice, sannan sumayya ta ce "Nabila ki yi
magana mana, meyafaru da ke? Kiran me ki ka yi mini kina so mu haɗu? Kuma na
neme ki na rasa jiya, yau kuma na ganki a haka ko wani abun ne ya faru?"
Nabila ta ƙura mata ido, yanzu ita ta ina za ta fara yi wa
Sumayya bayani ma, wataƙila idan ta bata labarin abun da ya faru ma ƙaryata ta
zata yi, ta ce mata ba ta da hankali, ta san babu lallai ta bata goyon baya, a
kan abun da take niyyar yi. Ba wannan ba shi kansa Nasir idan ya dawo, ta ina
za ta bi ta warware mugun ƙullin da tayi, muddin ta yarda aka kama Viper a
sanadinta, ta zama azzaluma duk da ba ta ji ƙarashen labarin ba, amma yin hakan
shiga hakkinsa ne.
Sumayya duk yadda ta kaɗa ta raya, fafur Nabila taƙi cewa
komai, hasali ma zancen zuci ta din ga yi taƙi kulata.
Abba ya din ga yi wa Nabila faɗan yawo ba ɗankwali, jin kaɗe-kaɗe
da kuma yawan kwalliya.
Walida ta shigo da waya a hannunta, ta miƙawa Nabila ta ce
"Gashi Yaya ne zai yi magana da ke"
Nabila ta girgiza mata kai, ba zata karɓa ba.
"Me zan ce masa to?"
Sumayya ta karɓi wayar suka gaisa da Nasir ta ce "Yaya
mutuniyar jikin ba daɗi, taƙi magana ma gaba ɗaya, ka yi haƙuri ko zuwa anjima
mu gani idan zata yi"
Ya ce "Shikenan, hanklina ne a tashe, ban ji ɗuriyarta
ba ai, na sake kira anjima". Suka yi sallama ta kashe wayar.
***
Kwanaki kusan uku ramma na fama da jikinta, kafin ta ɗan ji
ƙwari, a kwanaki ukun nan, Abdul bai kulata ba, zai dai ba ta abinci ya bata
magani, sai a kwana na uku da ya ga yi ƙwari, har tana salla.
Tun da rana ta fara ganin take-takensa dan haka hanklinta ya
ƙi kwanciya, da daddare ta kasa bacci sam, aikuwa kamar yadda ta yi tsammani,
sai gashi ya shigo ɗakin, yana miƙa yan kallonta. Cikin hanzari ta tashi tsaye.
Ya mayar da ƙofar ya rufe ya ce "Ina zaki ne?"
Ta hau ja da baya, ya nufota gadan-gadan kawai ta ciro wuƙar
yanka fruit, ta ce "Wallahi ka taɓani sai na caka maka, sai na kasheka
azzalumi mara imani kawai"
Ya ce "Ohh wow, in ajiyeki ina ciyar da ke, ki ɗauki
wuƙa ki ce zaki kashe ni, ni da ki ka samu ban kashe ki ba? Dole na canza taku.
Ya danƙota sai ga wuƙar a hannunta, amma ta kasa yi masa
komai da ita, ba ta wuƙar yake yi ba, ya fara ƙoƙarin yi mata abun da ya saba,
taƙi sakin wuƙar, garin kokowar ƙwatar kanta ya yanke shi da wuƙar hannunsa.
Sakin wuƙar ta yi ta ce "Na shiga uku" ya tsaya yana kallonta,
hannunsa na zubar da jini.
Tayi sauri ta saka hannunta, ta danne wurin da yake ta zubar
da jinin, ta ga hakan ba zai yi ba, ta kama rigar jikinta tana dannewa tana
cewa "Ka yi haƙuri" ya ƙura mata ido, gaba ɗaya sai ta rikice.
"Ni zaki kashe ko?"
"A'a ba kasheka zan yi ba, sonake kawai ka ji tsoro ka
ƙyaleni, ka yi haƙuri" ya fizge hannunsa ya fice, ta samu wuri ta zauna
hankalinta rabi a tashe, rabi kuma tana gode wa Allah da ya saka ya ƙyaleta.
Nabila ta warware, sai dai gaba ɗaya walwalarta ta ragu
sosai da sosai, ba ta iya bacci, tunaninta da lissafinta kawai yaya zata ɓullowa
lamarin.
Ta sake ɗaukko wayarsa tana jujjuyawa, ta tuna abun da Walid
ya ce mata "Sai dai ki je shi ya ƙarasa miki"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Dole zan je, zan neme shi,
sai na ji ƙarshen labarin, for now dole na tsayar da aikin DSP, na kamo bakin
zaren nan, dan gudun kar a haihu a ragaya.
Ranar monday ta kunna wayarta, ta shirya ta ce wurin aiki
zata tafi, ana ta zancen Nasir zai dawo, sai dai ko a jikinta, dan ba ta shi
take yi ba, ta shirya ta fice.
Da ƙafarta take ta tafiya, dan kar ta hau abun hawa tayi
saurin zuwa wurin aiki, ba ta gama tunanin da take son yi ba, wataƙila ko za ta
samu mafita a haka.
Kamar an ce ta waiwaya, ta ga wata baƙar mota, na ta bin ta
sannu a hankali, tun da ta fito titi kuma ta ga motar, ta basar ta cigaba da
tafiya, bayan wasu mintuna ta ƙara waiwayawa ta ga motar still tana bin ta.
Tsayawa tayi ta juya ta nufi motar, sai aka tsaya aka yi
parking aka daina bin ta, glasses ɗin motar tint ne, dan haka ba ta ganin na
ciki. Ta ƙarasa ta hau ƙwanƙwasa glass ɗin, amma ba a sauke ba.
Ta gaji ta tari abun hawa, ta tafi.
Ta shiga reception kenan, ta tarar da wasu matasan
mata su biyu, a cikin tashin hankali.
Ba ta damu ba ta wuce su, ta tafi office ɗin ta, ta ajiye
kayanta ta sake fita harabar wurin, ta gansu a tsaye suna kuka.
Har ta gota su ta dawo, ta kallesu ta ce "Lafiya
kuwa?"
Ɗayar ta ce mata "sannu"
Nabila ta ce "Yauwwa meyafaru ne?"
"Dama babanmu aka yi wa sharri, an kai shi wurin 'yan
sanda ma, wai kotu za a kai shi, an ce mu ɗaukar masa lawya mai zaman kansa,
mun ji ba zamu iya ba, abun da tsada sosai"
Nabila ta ce "Sharrin me?"
"Gadi yake yi a wani gida, sai ɗan wan matar gidan ya
yi wa mai aikinta fyaɗe ya gudu, su suka fara kaita asibiti, da shi mai wankin
gidan, shi ne daga baya aka kama su, wai su ne suka yi mata"
Nabila ta yi shiru tana nazarin maganar ta kalli ɗayar ta ce
"Yayata kin tabatta, ba na shiga case ɗin mutumin da ba shi da gaskiya,
kar na yi bincike na tarar da saɓanin abun da ku ka gaya mini"
"Wallahi ba ƙarya muka yi miki ba"
Ta ce "Well, yanzu ina da tarin ayyuka a office ɗina,
personally zan taimaka muku, ku zo gobe in Allah ya kaimu ƙarfe tara na safe,
zamu je wurin mahaifin naku, na ga abun da zan iya yi a kai"
Godiya suka din ga yi mata, tamkar za su durƙusa mata,
yanayinsu kawai ya nuna suna fama da matsin rayuwa.
Ta so haɗuwa da barrister Habib, amma bai shigo ba, ya tafi
gudanar da wasu shari'oi dan haka ta zauna ta gudanar da nata ayyukan.
Sha biyu na cika, ta ɗauki jakarta ta fita, kiran Nasir ya
shigo wayarta, kamar ta share, sai ta ɗaga tayi sallama.
"Barrister, kina office ne na biyo?"
"Ka dawo kenan?"
Ya ce "Eh ina cikin kano"
Nabila ta ce "No, zan yi wata shri'a ne, ka je gida ka
huta na kusa dawowa nima" ba ta jira mai zai ce ba, ta saka wayar a Flight
mode, ta tari abun hawa, ta nufi unguwar da Viper yake.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Suna tafe a hanya, Nabila na ta saƙe-saƙe daban daban a
cikin ranta, har suka iso dai-dai in da ta sauka wancan zuwan, ta sallami mai
napep ɗin, ya din ga kallonta yana tunanin ita kuwa me za ta yi a irin wannan
wurin haka ranar tsaka.
"Malam lafiya, ka tafi mana" ya ce "To,
tafiyar zan yi" ya ja baburinsa ya tafi.
Sannu a hankali ta bi waccan hanyar da Walid ya bi da ita
wancan karon, amma ta kasa gane hanyar da suka bi, balle ta gano gidan.
Ta din ga nausawa cikin wurin, tana bulayi, amma ko rabin
gano hanyar ba ta yi ba, gashi ta fara gajiya ga rana tana yi.
Sosai take bulayi, tana sake nausawa wani wurin, amma sai ta
ga ta ɓulla wani wurin daban.
"Ke baiwar Allah" ta ji muryar wani a bayanta, ta
waiwayo tana kallon mutumin, sanye da uniform ka security.
"Me ki ke yi a nan wurin rana tsaka haka?"
Ta ce "Dan Allah malam wani gida nake nema"
Ya kalleta ya ce "Gida a nan kuma?"
Ta ce "Eh"
"Gida fa ki ka ce?"
"Eh wani ƙaramin gida ne, rannan na zo ma amma hanya ta
ɓace mini" ya girgiza kai ya ce a'a babu wani gida a nan haka, duk
kamfanunnunka ne, sai gonaki, can kuma idan ki ka bu dutse ne, daji zaki shiga
dan haka babu wani gida a nan"
Nabila ta ce 'Malam akwai gida a nan haka, na je gidan
fa"
Cikin tsawa ya ce "Ke babu wani gida a nan, ki bar
wurin nan tun ban sakar miki karnuka ba, ko na kama ki na haɗaki da jami'an
tsaro"
Ta ƙare masa kallo ta ce "Ni zaka saka a kama, na yi
maka kama da ɓarauniya ne?"
Ya ce "To wa ya sani, yanzu ai ɓarayi ne kawai ɓata
gari ba, kuma ba a goshi ake ganin ɓata garin ba, ta cigaba da ƙarewa wurin
kallo, ba ta ga hanyar gidan ba" ta ja guntun tsaki ta juya ta fara
tafiya, sai mamaki take yi, tabbas gidan a nan haka yake, amma ya aka yi haka
ta faru?
Haka ta koma ba tare da ta gane wurin ba.
Tun daga haraba yake murmushi, kamar bakinsa zai yage, cikin
ƙarfin hali ta ƙaƙalo murmushin ita ma, ta ƙarasa ta ce "Welcome home
DSP" ya miƙa mata hannu, ta miƙa masa na ta suka gaisa ya ce "I
really miss you barrister"
"Me too, ya aiki?"
"Aiki Alhamdilillah, daga shekranjiya zuwa yau duk ina
cikin damuwa, an ce ba ki da lafiya, ba kya ɗaga wayata"
Ta ce "Ka san ni ɗin ce a lallaɓa, auren zamani, yau da
lafiya gobe babu, bari na je na yi wanka na ci abinci"
Ya ce "Take your time, ki huta sosai zuwa yamma, zan je
office ne, zan ga mutumin da aka kama, aka ce ya san in da Viper yake, kan na
dawo ki bani abun da ki ka ce" dammm! Ƙirjinta ya buga, amma ta maze ta ce
"Ok bye bye, sai ka dawo" ya ɗaga mata hannu ta shiga cikin gidan.
Sai yanzu ta tuna tayi alƙawarin gaya masa wani abu idan ya
dawo, wanda dama wayar Viper take son ba shi, wanda a yanzu ko me za'ayi mata
ba zata miƙa wayar nan ba, sai ta ji ƙarshen labarin nan.
Tana wanka tana zancen zuci, idan ta ce za ta yi wa Nasir
bayani, ba ta da wata cikakkiyar hujja, da za ta sanya ya fuskanci in da ta
dosa, kuma sai ta tonawa kanta asiri na cewa ta haɗu da Viper.
***
Ɓangaren ramma kuwa, tun da ta yanki Abdul da wuƙa, ba ta
sake ganinsa ba, har gari ya waye, duk abun duniya ya ishe ta, wai ita ta yi wa
mutum illa da wuƙa har ya zubar da jini.
'sai me, ke kin manta abubuwan da ya aikata miki?' wata
zuciyar ta tambayeta.
'Duk da haka, da kuma na caka masa in da zai mutu fa?"
Ta tambayi kanta.
Ta buɗe falon, ta fito da rigarsa sai towel da ta ɗaura, ta
rufe jikinta da ɗan kwalin kayanta, ta fito falon ba kowa.
Solomon ya fito zai shirya abinci a kan dining, ta ce masa
"Ina kwana?"
Cikin gurɓatacciyar hausarsa ya amsa mata, ta ce "Yana
ina?" Yayi mata saroro ba ya jin hausa.
"Kai ba ka jin hausa ne? No hausa?" Ya jinjina
mata kai tare da yin murmushi.
Hausa da turanci take haɗawa, tana tambayar sa ina wannan
mutumin, mai gidan nan?"
Turancin nata ya bashi dariya, da turanci ya ce mata bai
kwana a gida ba.
"Ina ya tafi?"
Ya ce "Ba a tambayarsa in da ya tafi" tayi ajiyar
zuciya ta kalli, kwanukan abincin ta ce "Duk kai ka ke dafa wannan? A ina
ka iya girki?"
Ya ce "Catering school na yi, tun ina ƙarami kuma, ina
taimakawa mamana wurin yin girki, tana sayar da abinci"
Ramma ta ce "Ka san koko?"
Ya yi shiru yana kallonta, kwatanta masa ta shiga yi, yayi
dariya ya ce "Pap" ta ce "Eh, shi ka din ga yi mini turancin
ƙanana yadda zan gane"
Yayi dariya ya ce "Ai normal turanci ne, kawai dai
pidging ne" a dai-dai lokacin Abdul ya shigo falon, ya tarar da ramma a
tsaye, tana magana da solomon tana murmushi.
Wani abu ne ya tokare masa wuya, suka ɗago suna kallonsa,
tana ganinsa ta haɗa fuska, ta din ga satar kallon hannunsa, da ya naɗe da
bandeji.
"Solomon, yaushe na zama sa'anka da zan ajiye yarinya
ka din ga hira da ita? Kai ka ajiyeta? So kuna shirya yadda za ta gudu
kenan?" Da sauri solomon ya girgiza kai ya ce "Ba zan taɓa cin
amanarka ba sir, abu ta tambayeni nake ba ta amsa"
"Babu ruwanka da ita, idan tambayar ce ta tambaye
ni"
Ya jinjina kai. "Bar wurin nan" da sauri ya bar
wurin.
Ya ƙarasa dining ɗin, zai zauna ramma ta tashi. "Zauna
ina zaki je? Haɗa mini abinci in karya"
Cikin tsananin takaici take bin sa da ido. "Zaki haɗa
mini, ko sai na turmusheki na yi breakfast ɗin da ke, 'yar dabar ƙauye kawai,
ki na 'ya mace kina ɗaukar wuƙa".
"Ni ba 'yar daba ba ce ba, kare kaina nayi yinƙurin yi
daga mugu irinka mara imani"
Ya ɗora ƙafarsa a kan dining ya ce "Na ji, haɗa mini,
ko kuma wallahi na yi abun da na ce"
Tuni hawaye ya cika mata ido, ta haɗa masa tea, da doyar ta
tura masa gabansa, ta tashi zata tafi ya riƙota, ya ɗaga mata hannunsa na dama,
wanda a nan ta yanke shi, ya ce "Da wani hannun zan ci?" Ta tsaya
tana kallonsa.
"Oya feed me, tun da kin riga kin yi wa hannun illa,
idan ba haka ba kin san condition ɗin" babu kalar tsinuwa da zagin da ba
ta yi masa a zuciyarta ba.
Cike da ƙwarewa a fannin iya rashin mutunci da bariki, haka
yake haɗawa da hannun ta idan ta bashi a bakin, yana wani ƙare mata kallo. Sai
ƙanƙame jikinta take yi, gaba ɗaya wani iri take jin ta.
Ya cinye doyar ya ce ta ƙara masa, a ranta ta ce "Shege
jaki"
Lomar ƙarshe, ya riƙe hannunta, da yatsunta a bakinsa,
kokowar ƙwacewa take yi, amma ya riƙe su a bakinsa yana yi mata kallon 'yan
iska a cewarta. Ba ta san lokacin da ta dunƙule ɗaya hannun nata ta ɗirka masa
duka a kafaɗarsa ba, ɗan dukan da babu in da ya je, ya saki yatsun yana
murmushi, da ƙoƙarin tauna sauran doyar, wani irin mugun kallo take yi masa,
tare da goge yatsunta a jikin rigar jikinta, ba ta fargaba ya sake tashi, ya haɗe
bakinsa da nata, yana ɗura mata ragowar abincin bakinsa, cikin tsananin
jarumta, take naushinsa ta ko ina, amma ya saka hannu, ya danna maƙogwaronta,
babu shiri ta haɗiye, ya cikata ya nufi 3seater ya kwanta.
Iya ƙarfinta ta zage ta din ga zaginsa, har da kalar wanda
ba ta taɓa tunanin ta iya ba, ya lumshe idanunsa ya yi mata banza ya ce
"Na san maganinki"
Nasir ya ƙarewa liti kallo, sannan ya kalli sageant ɗin da
suke tare ya ce "Kana nufin bai yi magana ba gaba ɗaya?"
"Eh sir, ya ƙi yi"
Ya mayar da idonsa kan liti ya ce "Ka sauƙaƙawa kanka,
ka sauƙaƙa mana aiki, ka gaya mana abun da muke tambayarka a kai. Ina Aminu
Viper?"
"Ban san in da yake ba"
"Ƙarya ka ke yi, rahoto ya zo mana a kan ba shi da wasu
makusanta bayan iyayensa sai ku, babu iyayensa a lissafi tun da dama sun riga
sun sallama shi, ka fi kowa sanin in da Aminu viper yake"
Liti ya ce "Tun da ka samu wannan rahoton, kai ka san
amanar da ke tsakaninmu ba wadda zan yadda ta rushe ba ce a kan ƙaramar
bazarana ba ce. Kalleni da kyau, na yi gwagwarmaya na ga rayuwa, prison ceil,
na shiga kala-kala. Kuma ban taɓa zuwa gaban ɗan sanda na yi magana biyu
mabanbanta ba, idan zan yi zan yi kawai. Eh ko a'a. Ko kasheni zaku yi a yanzu,
ban san in da yake ba"
Nasir ya kaɗa kai ya ce "Kar ka cika baki, wataƙila
wannan karon, ka zo in da zaka yi magana biyu, ina Aminu Viper yake"
Liti ya ziraro harshen sa, kamar yadda Al'amin ya ke yi ya
ce "Allah ya ja da ran mahadi mai dogon zamani. Ambaton sunansa kawai,
girma muke bashi na musamman. Abun da ba ka gane ba shi ne, shi fa mai gida ya
ci dubu sai ceto wallahi. Idan ba haka ba tayaya za a saki mutumin da yake
tsare, kuma a dawo ana nemansa? Gangan ma kenan"ya yi maganar yana dariya.
Nasir ya ce "Babu laifi, zaka yi magana dan dole"
"Magana biyu, abun da liti bai taɓa yi ba kenan, ko
wace irin azaba kuwa zaka gana mini, ai ƙarshen ƙwarewar taku kenan, ku yi ta
ganawa mutum azaba, ya amsa laifi nasa da ba nasa ba. Idan har manyanka ba su
saka na yi magana biyu ba, ba ka da wata izaya da zaka yi mini na yi magana
biyu, idan kuwa na yi magana biyu ashe ba yaron Viper bane ni".
Wata inkiya Nasir yayi, kamar yadda liti ya faɗa kuwa, aka
saka wasu kurata, suka din ga jibgarsa da kulki, kamar sun samu tumu, suka yi
iya yin su suka yi masa lilis, sannan suka kai shi wani ɗaki mai duhu suka
kulle shu.
Gaba ɗaya Nabila tana ɗakinta, tana ta lissafin yadda za ta ɓullowa
al'amuran nan da suka sakota a gaba.
Ta idar da sallar isha'i, ta zauna a kan daddumar, sai tufka
da warwara take yi, gashi ta rasa da wa zata tattauna maganar ta ji daɗi.
"Tunanin me ake yi haka ne?" Ta ji muryar Nasir.
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Yaya sannu da zuwa"
Ya zauna a gefen gadonta tare da cewa "Yauwwa arfa, kin
ga ban dawo da wuri ba ko? Na je na ga mutumin da ki ka yi mini bayani, na saka
aka kama, ta tabbata yaron Aminu Viper ne, amma riƙaƙƙen mara mutunci ne, ya ƙi
magana, duk wani nau'i na tuhuma an yi masa amma ya ƙeƙashe ƙasa yaƙi
magana".
Nabila ta ce "Ikon Allah, bai faɗi in za yaken ba
kenan?"
Ya girgiza kai ya ce "Bai faɗa ba. Amma muna nan muna
trying, alamu sun nuna ya sani, ɓoyewa yake yi. Yauwwa yanzu gaya mini me ki ke
son ki gaya mini lokacin bana nan"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Nothing much, dama dai duk a
kan case ɗin nan ne, na ce me zai hana ka bibiyi case ɗin daga tushe, misali
daga gidansu, iyayensa mutanen kewayen da ya zauna da su".
"Me hakan zai amfana?" Yayi maganar yana kallonta.
Ta ce "Kawai ji nake kamar akwai lauje a cikin naɗi, a
kan sha'anin Aminu Viper, kamar abun da aka baka a kansa is not complete,
something is missing, yakamata a fara samo full details na abun da ya
faru".
Ya girgiza mata kai ya ce "Duk bani da isashshen
lokacin yin haka, na yi ƙoƙarin yin hakan, aka ce ba shi aka sakani ba, kuma
duk maganar nan da ki ke yi is a very long way, gara shortcut, idan ya zo hannu
muka gama da shi, kotu zamu tura shi, a can ne aikinki yake idan ma tssya masa
zaki yi" tayi murmushi ta ce "Hakan fa zai iya sawa na yi suna
ko?"
Yayi dariya ya ce "Ke dai kin damu da maganar yin sunan
nan, gaba ɗaya kin canza, ko dai haryanzu jikin ne? Gaba ɗaya kin rage ɗokin
case ɗin Vipern ma, ko akwai wani abu ne ki gaya mini " ta girgiza kai ta
ce "Babu komai"
Ya ce "Are you sure?" Ta jinjina masa kai, ya
tashi tsaye ya ce "Ban yarda iya abun da ki ke son gaya mini ba kenan,
akwai abun da ki ke son gaya mini ki ka fasa, amma da sannu zan gano menene da
kaina"
Shiru kawai ta yi tana murmushi ya fita, yana ƙoƙarin fita
daga falon, ya ci karo da mama, sai da ya ɗan tsorata ya ce "Mama"
"Me ka ke yi a ɗakinta da daddaren nan?" Tayi
maganar rai a ɓace.
Ya ce "Subhanallah, dan Allah mama kar ki kawo komai a
ranki, muna magana ne a kan aiki... "Rufe mini baki, aikin banza da na
wofi, sai ubanka ya farga ya fara yi maka terere a cikin gidan nan ko, kana
zuwa ɗakinta da daddare, ka dai san ita ba zai tagayyarata ya nuna laifinta ba
sai kai. Duk lokacin da na yi ƙoƙarin fahimtar da kai, irin wannan abun ba ka
gani, daga dawowar ka, zaka fara sakani magana saboda wannan sheɗaniyar
yarinyar ko Nasir? Ka cigaba ban ce ka fasa ba" ta nufi ɗakinta ta bar shi
a tsaye a wurin saroro yana kallonta.
***
Ramma tana kwance ta sha kuka har ta gaji, tunanin halin da
mamanta take ciki kawai take yi, ta san tana can hankalinta a tashe, tana faɗi
tashin neman in da take.
Ta gaji da kwanciyar, ta ɗauki ruwan da yake ajiye, a kan
side bed, ta sha fiye da rabi, saboda maƙogwaronta duk ya bushe, saboda kukan
da ta sha.
Ta kwanta tana jiran bacci ya kwasheta, amma bacci ya
gagara, sakamakon wani irin yanayi da ya din ga bijiro mata, har wani irin gumi
take yi, ta tashi cikin matsananciyar damuwa, amma ta rasa takaimaimai
meyakamata ta yi. Ta nemi wuri ta kwanta, ta takure, tana ta mamakin wannan
wane irin abu ne haka.
Abdul ne ya shigo yana fito, tayi shiru ba ta motsa ba, ya
nemi wuri ya kwanta a bayanta.
Ba ta yi masa tashin hankali ba, ko ƙoƙarin yin gardama ba,
babban abun da ya ɓata mata rai, ya sanya ta ji tamkar ta kashe kanta, bai wuce
yadda ta iya biyewa Abdul ba, ta tabatta mazinaciya!. Kuka take yi iya
ƙarfinta, har da sheshsheƙa ko a jikinsa, kaɗa ƙafa kawai yake yi, daga baya ya
tashi zaune yana kallonta, yayi dariya ya ce "Ba dai ke taurin kai ba, ai
na san maganinki, you are very healthy and unique, zaki yi mana baƙin ciki. Ba
kya buƙatar komai kan ki yi functioning lafiyayyiya ce ke, amma tsinanane
taurin kai irin na ɗan ƙauye ba zai bari ki yi abun da ya dace ba". Ya ɗago
wata ƙwaya ya ce "You force me to use it on you. Idan ki ka bari muka
cigaba a haka ke zaki sha wahala, dan zata iya cutar da ke, aikin gama ya riga
ya gama ba wani sauran amfani da zaki yi, ni ban ga abun ƙi ko damuwa ba. Na
aika a gaya wa babarki ta daina nemanki na ajiye mata ke a in da ya dace".
Cikin kuka ramma ta ce "Ba zan taɓa yafe maka ba, Allah
ya isa, mazinaci mugu".
Ya ce "Mazinata dai har ke"
"In sha Allah ba zaka gama da duniya lafiya ba"
Ko a jikinsa ya ce "Idan Allah ya nufa na gama da ita
lafiyan, sai ki hana ai" ta cigaba da kuka, shi kuma ya juya ya hau bacci.
Ta bi shi da kallo, ba ta tunanin ko wankan janaba yana yi,
sai da tayi mai isarta, ta tashi ta yi wanka, ta saka wata jallabiya, ta leƙa
fuskarsa, ta ga bacci yake yi sosai.
Ta lallaɓa ta fita daga ɗakin, ta fara laluben ƙofar fita,
sai dai ta nemi hanya ta rasa.
Ko ina a rufe ta girgiza manyan ƙofofin, amma ko motsi ba sa
yi, ta zauna a falo, ta cigaba da kuka, ta din ga jin haushin karnuka, tsoro
yakamata, ta tashi ta koma bedroom ɗin, ta tarar da shi a zaune yana danna
wayarsa.
Ta nemi wuri ta kwanta a ƙasa.
"Idan ki ka kuma yinƙurin guduwa, sai na bar garin nan
da ke, ba garin nan ba kawai, zan iya barin ƙasar nan da ke, babu wanda zai
sake jin ɗuriyarki, gara ki shiga hankalinki".
"Ai ba zan tabattar da kai tabattacen azzalumi bane,
sai ka rabani da duniyar" ya kalleta, kamar ba daga bakinta maganar ta
fito ba.
Duk a yawon barikinsa, babu karuwar da ta isa ta ci masa
mutunci ko ta zage shi, amma a garin kwashe-kwashensa, ya kwaso 'yar
mitsitsiyar yarinya tana cin zarafin sa, yayi mata shiru, yana jin ta tana yi
masa Allah ya isa ƙasa-ƙasa har da Allah ya tsine masa, amma ya shareta, tun da
yau ya samu abun da yake so.
Nabila tana office ɗin ta a zaune, tana ɗan danna system,
sai dai hankalinta ba a kan system ɗin yake ba.
Aka danna ƙarrarawar office ɗin, ta bada umarnin a shigo,
matasan matan nan ne, wani masinja ya rako, ya ce "Hajiya Nabila, ga baƙi
kin yi"
Ta ce "To na gode sosai. Bisimillah ku zauna" suka
zauna tare da gaida Nabila.
A kallo ɗaya zaka ga Nabila ta yi kalar mata masu izza da
jin kai, amma kuma kana zama da ita zaka ga saɓanin hakan.
Suka gaisa ta ce "Jiya ina sauri zan fita, mun fara
magana bamu ƙarasa ba, duk da yau ɗin ma ina son fita ne"
Ɗayar ta ce "Ai mun gode ma saurarmu da ki ka yi.
Lauyan gwamantin sai yawo yake yi mana da hankali, aka ce mu ɗaukar wa baban
lauya mai zaman kansa kawai, mun zata abun mai sauƙi ne, ashe yafi
ƙarfinmu".
Nabila ta yi musu tambayoyi, ciki har da in da aka ajiye
mahaifinsu, ta yi musu alƙawarin za ta je da kanta, ta tattauna da shi, za ta
bibiyi komai, kafin a shiga zaman kotu.
Suka yi ta yi mata godiya, ta ce "Kar ku damu, ku bani
lamabar wayar da zan iya samunku"
Suka bata, ɗayar ta ce "To ƙanwata nawa ke zamu
baki?"
Nabila ta ce "Karku damu, ku yi mini addu'a kawai,
akwai abun da na saka a gaba, Allah ya sa na yi nasara baki ɗaya, da case ɗin
ku da ɗaya abun da na saka a gaba" da suka fara yi mata addu'a, sai da ta
fara jin nauyinsu, dan tamkar ta yi musu bushara da mahaifinsu ya fito, suka
hau yi mata hira da labarin yadda sunan mahaifin na su ya ɓaci, a cikin unguwa.
Tayi ta basu ƙwarin gwiwa, da tabbacin da yardar Allah za su yi nasara.
Bayan tafiyarsu, kawai ta yi wani tunani, ta ɗauki jakarta
ba ta zame ko ina ba, sai wurin aikin sumayya, ba ta tarar da ita ba sai
Lawisa, sai zuba iko take tana hura hanci.
Nabila ta yi murmushi ta ce "Anty lawisa, Sumy ta shigo
kuwa?" Ta ɗaga kai da ƙyar ta kalli Nabila ta ce "Eh"
"Tana ina?"
"Recording take yi".
Ta ce "Ok, bari na jirata a nan" tayi maganar tana
ƙoƙarin zama.
"No please, ba na son takura, ko zaki jirata a
reception?"
Nabila ta ce "Ba zan iya zaman reception ba, kujerun ba
su da daɗin zama a nan zan zauna" tayi maganar tana zama a kan kujerar
office ɗin.
Baki buɗe lawisa take kallon Nabila, ta maze ko a jikinta,
ta na danna wayarta.
Ta kalli lawisa ta ce "A kan kujera kawai na zauna, ba
hira na ce mu yi ba, 10-20 minutes, ai is not that much da zaki ce ba kya son
takura" ta cigaba da danna wayarta.
Bayan mintuna goma sha biyar, Nabila ta ji yo muryar
sumayya, ta ɗauki jakarta ta fice, ba tare da ta sake kula lawisa ba.
Sumayya na ganinta ta harareta, Nabila tayi murmushi ta ce
"Haba masoyiyya daina hararata mana"
"Matsa ko na make ki, ni ki ka yi wa wulaƙanci ki ka
daina ɗaga wayata"
"Ba haka bane ba, ayyuka ne suka yi mini yawa, daga nan
ma wani wuri zan je na ce bari na biyo mu yi magana"
Suka shiga wani office da babu kowa suka zauna, Sumayya ta
ce "Wai ni me zaki gaya mini last week ne? Ki ka shanya ni da yake ba
mutunci ne ya ishe ki ba, wayarki ma gaba ɗaya ta daina shiga, har gida na je
ina nemanki"
Nabila ta kaɗa kai ta ce "Aiki ne ya zo mini
unexpected, mun je court ne, ina da shari'a kuma zan ga wasu clients ɗina. Dama
a tsakanin lokacin nayi tunanin zan iya squeezing time ɗina, mu haɗu, kuma bai
yiwu ba".
Sumayya ta ƙare mata kallo tayi murmushi ta ce "Ko dai
kin sake komawa wurin Aminu Viper ba?"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Kina zargin na koma
ne?"
"Na san hali zaki aikata ai, ina gargaɗinki a kan
kasada da rayuwarki Arfa"
Tayi murmushi ta ce "Ina ma zan iya jin maganarki"
Sumayya ta ce "Baki yadda ba kenan?"
Nabila ta ce "Mu bar maganar nan, ni wani taimako nake
son ki yi mini "
Sumayya ta ce "Ina jinki"
"Ke ce uwar neman labari, bincike nake son yi a kan
honorable ma'aruf Indabo"
Sumayya ta kalleta ta ce "Kamar yaya?"
"Kamar yadda na gaya miki, taimaka mini nake son ki yi,
ki binciko mini duk wani labari da yakamata a kansa"
"Me ku ke so ku mayar da ni ne daga ke har shi?"
Nabila ta ce "Shi wa?"
Sai kuma sumayya ta farga da katoɓarar da ta kusa tafkawa.
"Indabon yayi miki wani abu ne?"
Sumayya ta ce "No kar ki damu, haushi ki ka bani ne,
kin ce Naja'atu Bunkure, kin ce Aminu Viper yanzu kuma kin ce Indabo, Nabila me
ki ke son ki zama ne?"
Nabila ta tashi tsaye ta ce "Zan je wani wuri yanzu,
Ina jiranki dan Allah sumayya, da tarihinsa da tarihin siyasarsa komai da komai
da yakamata ina son sani a kansa"
Sumayya ta ce "Wai me zaki yi da shi to?"
"Amfani mai muhimmancin gaske, sai anjima, ki gaida
umma zan zo har gida na gaisheta, kwana biyu ba mu gaisa ba. Ina jiranki dan
Allah" ta ɗauki jakarta ta yi waje.
Kamar ta tafi gida, sai ta fasa ta ɗaukar mai napep, ta tafi
police station ɗin da aka ce mata dattijon nan yana tsare, da ta je ta tarar an
canza masa wuri, an mayar da shi sashen kula da manyan laifuffuka.
ID card ɗin ta kawai ta nuna, aka bata damar ganinsa, aka
fito da shi, dattijo ne amma ba tsoho cancan ba.
Suka gaisa ta ce "Baba ni ce, wadda 'ya'yanka suka same
ni, a kan maganarka, yaya meyafaru?".
Nan ya ba ta labarin duk abun da ya faru, ta ce "To
baba yaya sunan shi ɗan yayar matar?"
Yayi shiru ya ce "Wallahi ban sani ba, yana dai zuwa
gidan da yake ban daɗe da fara aiki a wurin ba"
Ta ce "Yanzu ina ne gidan da ka ke aikin, sannan ina
yarinyar take, dole zan ganta "
Ya share hawayensa ya ce "Wallahi ban sani ba"
Nabila ta tambayi 'yan sandan suka ce sai dai ta koma can in da aka fara
binciken case ɗin"
Ta ɗauki bayanan da zata ɗauka, ta yi musu sallama ta tafi.
***
Kasancewar Abdul da wuri ya fita, solomon ma baya nan, Ramma
ta din ga yawo tana neman hanyar fita tana kuka, amma ta rasa, tayi-tayi ta
samu hanya ta rasa, ƙarshe ta koma falo ta zauna tana kallon Tv.
Wata magazine da tarin takardu ta gani, ta ɗauka tana kallo,
signing ɗin sa mai kyau, Abdul yassar ma'aruf Indabo.
Shiru ta yi tana tunanin, kamar ta san sunan nan.
Ƙofar falon ya saka key ya buɗe ya shigo, yayi sallama ta
amsa a hankali, sai dai yayi kissing ɗin kumatunta sannan ya zauna, ta tsuke
fuska tana matsawa.
Ya kuma matsawa kusa da ita ya ce "Kin ci abinci
kuwa?" Ta yi masa shiru.
Ya ɗago mata jakar hannunsa ya ce "Yakamata ki san
menene a jakar nan" taƙi kula shi.
Ya buɗe jakar, ya zazzage mata, kayanta ne a ciki, da kuma
wasu sababbin kayan ya sayo mata.
"Babarki tana gaishe ki"
Ta kalleshi idonta fal hawaye ta ce "Me ka ke
nufi?"
"Na ce ta sallama mini ke, ba sai ta cigaba da nemanki
ba"
Ta sake kallonsa ta ce "Waye indabo?"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Queen collection, dealers of all kind of textiles, bedsheet,
Adashi stock fish and others.
Follow this link to join my what's app group
https://chat.whatsapp.com/Hp4ZLNtrNXvJQkAV8UWZcv
Ya kalleta ya ce "Meye alaƙarki da sunan? Kin san shi
ne?" Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To a ina ki ka ga sunan?" Ta ɗago masa takardar
ta ga signing ɗin sa, da full name ɗin sa.
Ya ce "Well babana ne, ba abun mamaki bane dan kin san
shi, ɗan siyasa ne"
Cikin rauni ta ce "Me ka ce wa mamana da ka je?"
"Ba na gaya miki ba, na ce kar ta sake nemanki, kin
zama mallakina"
"Saboda ba ka da tausayi da imani ko? Wallahi idan
baƙinciki ya kashe mahaifiyata ba zan yafe maka ba"
"Ikon Allah, me zai sa baƙin ciki ya kasheta, na kai
mata kayan buƙata a matsayin ina tare da 'yar ta. Ku ne haryanzu ku ke wannan
kidahumancin, kun ƙi ku waye, turawa duk in da mace ta kai 18yrs tana da ikon
zuwa in da take so tayi rayuwa, amma ku da an yi magana sai ku ce aure aure, in
anjima kuma ku yi ta surutun wahala ku ke sha a auren"
Ramma ta ce "Saboda yahudanci ko? Mu ai ba turawa bane,
musulmai ne baƙar fata, hausawa masu riƙo da addini da al'ada. Ni ban shekara
sha takwas ɗin ba, idan ma na yi ai sai da yadda ta da amincewa ta. Kawai
saboda bamu da kuɗi ka yi mini fyaɗe ka je har gidanmu gaban uwata ka ɗaukko
ni, ka rabani da ita, kuma ka koma ka karɓo kayana ka ce mata ta daina nemana
kai ba aurena ka yi ba, kai ba wani abu ka yi da zaka taimaki rayuwata ba, ka ɗauki
hakkinmu ba ka yi mana adalci ba"
Ya ce "Ke kin isheni, sai ka ce ke kaɗai ce 'ya? Ni fa
ban taɓa ɗaukar wata mace na ajiye ina lallaɓata ba sai ke, kuma ma ku da ake
haihuwar ku barkatai babu tsari, har wani damuwa za a shiga dan an ɗauki ɗaya?
Kashe ki fa na yi niyyar yi na ƙyale ki".
"Mu ba ai haife mu barkatai ba, mu uku ne, yayanmu ya
rasu, ƙanina ba shi da cikakkiyar lafiya, ni kuma ka ɗauke mata ni, ban da
dalilin maraici babu abun da zai saka ka ganni a birni aikatau, har ka keta
mini haddi, bayan ka turo mana wata azzaluma, da fari ta ce zata taimaka mini,
ta koma gaya mana yahudanci, ka ɗauke ni a gaban uwata, ka zo ka mayar da ni
karuwa ka yi wa kanka adalci dan Allah kuma nima ka yi mini?"
"Naja'atu Bunkure ba ƙarya ta gaya miki ba, tun a
lokacin da ba ku nuna taurin kai ba, da ba a zo nan ba, ku ku ka janyo koma
menene ai"
Ramma ta haɗa hannayenta biyu, ta rufe fuskarta tana kuka ta
ce "Ka cuce ni, ka lalata mini rayuwa, dama kasheni ka yi na huta, ka
wulaƙanta rayuwata a matsayina na 'ya mace musulma da addinina ya suturta. Da
ƙanwarka ce ni ko 'yar ka, ba zaka zuba mini ido ka ce na je na yi tarayya da
wani ba aure ba, kayi amfani da kuɗi, ka wulaƙanta ni dan ni 'yar talaka ce ba
ka kyautawa rayuwata ba" ga ta yarinya ƙarama, sai iya tsara magana.
Abun da bai taɓa ji ba sai a wannan karon, kukan ramma a
cikin zuciyarsa, maganganun ta suka tsaya a zuciyarsa, amma a zahiri ya nuna ko
a jikinsa, ya tashi ya bar ta a falon ya tafi ɗaki.
***
Ɗan mama yana ta kaiwa yana komowa, tsakanin ɗakin Viper da
tsakar gida, yana jiran Walid ya fita, amma ya ƙi fita ya zauna ba shi da
niyyar fita.
Viper kuma sai bin ɗan mama yake yi da ido.
Walid ya ce "Kai ɗan mama, kamar ba ka da gaskiya"
Ɗan mama ya ce "Haba Oga walid me ka gani?"
"Ba sai na gani ba, alamun hakan na gani, wallahi na ga
abun da bai yi mini ba, sai ranka yayi mugun ɓaci"
Ɗan mama ya ce "Kar ka damu Oga walid, babu wani abu da
zaka gani wanda zai ɓata maka rai"
Walid ya jinjina kai, ya cigaba da shan sigari.
Al'amin ya yinƙura ya tashi, Walid ma ya tashi ya ce
"Ina zaka?"
Al'amin ƙura masa idanunsa da suka yi wani irin mugun jaa.
"Ba wai tuhumarka nake yi ba, ko wani abu ba, kawai dai
ba na son ka yi wani abu da zai wargaza mana shiri ne"
"Iska zan je sha, ko yau ma yinƙurin kashenin zaka
yi?"
Walid ya girgiza kai ya ce "Last time ɗin ma, ni ba
niyyar kasheka na yi ba, ƙoƙarin hanaka abun da ka yi niyya na yi, a dawo
lafiya" Al'amin ya nufi ƙofar fita, ɗan mama ya ce "Oga Viper, bari
na zo mu je na taka maka" Walid ya riƙe rigarsa, ya tsare shi da ido.
Ya sosa kai ya ce "Dama raka shi zan yi"
Al'amin bai waiwayo ba, kawai ya fita, Walid ya fara saka
hannu a aljihun ɗan mama yana caje shi, Ɗan mama ya riƙe hannunsa ya ce
"Dan Allah ka yi haƙuri zan yi maka bayani".
"Sakar mini hannu, ko na kwaɗa maka mari"
Ɗan mama ya sakar masa hannu ya ce "Amma dai da ka
tsaya na yi naka bayani"
Walid ya ciro baƙar leda a aljihunsa, ya buɗe, ampoules ɗin
allura ne da sirinji, sai baƙin capsule.
Walid ya kalleshi, ɗan mama ya ce "Wallahi cewa yayi
sai na nemo masa su, idan ba haka ba, ba ya iya bacci, kansa zai fashe ni kuma
sai ya bani tausayi, daga ƙarshe kuma ya ce wallahi idan ban samo masa ba sai
ya kashe ni"
"Sai ya kashe ka, kai ka taɓa ganin ya kashe
wanin?" Ɗan mama ya girgiza kai.
"Wallahi idan ka kuma sayo wannan hard drugs ɗin ka
kawo masa, sai na saka maka ƙarfe ka ji na rantse" ɗan mama ya ce
"To, amma dan Allah shi ma ka gaya masa, ka san idan na ce masa a'a ba zai
yi mini da daɗi ba".
Walid ya ce "Idan ya ce ka kawo masan, ka ce masa to,
ka gaya mini" ya jinjina masa kai.
Viper yana zaune a kan dutsen, ya zubawa wuri ɗaya ido,
kansa kamar ya tarwatse haka yake ji, ga ƙirjinsa kamar an ɗora masa dutse, da
ƙyar yake iya numfashi, ga jikinsa sam babu ƙwari, banda kashe masa jiki babu
abun da ƙwayoyin nan suke yi, soyake yayi bacci mai sunan bacci, ko ya manta
komai da yake cikin ƙwaƙwalwarsa amma abu ya gagara.
"Madaki! Indabo!" Ya faɗa a hankali yana sunkuyar
da kai, ya ɗaga kai kamar a mafarki ya hangota, ta sauka daga adaidaita sahu,
sai waige-waige take yi, yana saman dutsen sosai, dan haka yana hangota. Ta
tsaya tana kallon hanya, in da yake take facing, amma ita ba ta ganinsa.
Dogon hijjabi ne a jikinta yau, a hankali take tafiya tana
cigaba da waige-waige, mamaki ne ya kama shi, me kuma ya dawo da ita wurin nan
yau? Zuciya ce ta tinziro shi, ya ji kamar ya sauka ya je ya naɗa mata shegen
duka. Mata halin su ɗaya, cin amana 'yar madarar sa ce kawai ta fita daban sai
umminsa, ta sace masa waya ta gudu, ta saka an kama liti, saboda tsagwaron
rashin kunya ta sake dawowa, ko uban me ta dawo yi oho?.
Hakan ya ƙara tabattar masa he's not safe, za ta iya kawo
jami'an tsaro su kama shi, sai dai kash, shi ba ya fargabar a kama shi, a kama
shi ko a ƙyale shi, shi ba wannan ne a gaban shi ba yanzu.
A yau ma ba ta iya gane hanya ba, bulayi take ta yi, tana
nema, amma ta kasa ganewa.
Babu tsammani suka yi kiciɓis da ɗan mama, ya kalleta ta
kalle shi, ya ce "Ke! Me ki ke yi a nan wurin?"
Ta ce "Yauwwa, kai ne wanda na gani a gidan Viper ranar
ko?"
"Ke, ki ka kuma kama sunansa, sai na ƙara wa ƙofar
bakinki faɗi wallahi, kar ki sake ambatar sunansa ko ki kama sunansa".
Nabila ta ce "Tom, ba zan sake ba, dan Allah taimakona
nake son ka yi, ganinsa nake son yi dan Allah"
Ɗan mama ya ce "Ka ga wata mayyar kuma, baki ji
kashedin da yayi miki ba kenan? Kin ɗauka da wasa yake yi da ya ce "Ya
sake ganinki zai kashe ki, kin san waye Viper kuwa?"
"Ba zai kashe ni ba, muhimmiyar magana nake son mu yi
da shi, na san na yi muku laifi, ku yi haƙuri dan Allah, ka taimaka mini ka haɗani
da shi dan Allah"
Ɗan mama yayi mata wani irin mugun kallo ya ce "Ya aka
yi ki ka san ba zai kashe ki ba?"
"Viper ba ya kashe mutane, mussaman mata da ƙanan yara,
dan Allah ka haɗa ni da shi na kasa gane gidan".
"Ke bar nan wurin, na haɗaku ki saka a kama shi ko, to
ta Allah ba taki ba, wuce ki bar wurin nan"
Ta sake marairaicewa za ta yi magana.
Ya zaro wuƙa ya ce "Idan shi ba ya kisa ni ina yi, ware
ko na zaro hanjinki yanzun nan" wuƙar sai ƙyalli take yi, ya fara
tunkarota, yana wulwula wuƙar, ba shiri ta juya, gwiwa a sanyaye ta bar wurin.
Har ta miƙe ta ɓacewa ganin Al'amin yana hangota, ya miƙe ya
kwanta a kan dutsen, ya lumshe idanunsa rana tana dukansa, yana jin yadda zafin
ranar ke ratsa shi, yana ƙara masa ciwon kai, amma ba shi da niyyar tashi.
***
"P.A"
"Na'am honorable"
"Ka tabattar binciken da ka yi a kan yarinyar nan
daidai ne, babu kuskure a cikin sa?".
P.A ya jinjina kai ya ce "Babu fa, ka san ba na yadda a
samu kuskure a irin wannan lamarin, mussaman a irin wannan ƙadamin, ba a samu
kuskure ba, yadda na gaya maka hakan ne"
Ya jinjina kai ya ce "Shikenan, ina ita ƙawar ta ta,
ana cigaba da bibiyarta?"
"Eh, a wurinta muka samu wasu abubuwan ma"
Indabo ya ce "Haryanzu ina mamakin yadda aka yi ta ce
ayi mata bincike a kaina ne, shiyasa nake ta tantama anya ka yi binciken a
kanta dai-dai?"
P.A ya ce "Haba honorable, ya ma za ayi wannan ƙaramar
alhakin ta yi wani bincike a kanka, wataƙila hakan yana da alaƙa da harkar
siyasa ne kawai, ko kuma sakata aka yi".
"Ba ita ce a gabana ba, Viper mai zamani, shi ne babbar
barazanata, shi ne damuwata, ku cigaba da aikinku kawai, duk abun da ake ciki,
ka din ga sanar da ni "
P.A ya ce "In sha Allah, ai yaronsa ɗaya yana hannu,
sai dai na bincika an ce Haryanzu bai yi magana ya faɗi in da yake ba"
Indabo ya ce "Ƙyale 'yan sandan nan, sonake na riga su
samunsa, idan na riga su kawai kashe shi za ayi salin alin, duk madaki ne yayi
mini shirme wallahi, amma yanzun ma komai zai daidaita"
"Kar ka damu honorable, ai kai maganin kowane shege ne
a ƙasar nan, ba ma ɗan daba ba, zamu yi maganinsa, amma da alama kamar kana da
maguatan ɓoye, da suke tallafa masa"
"Na sani, amma yanzu duk ba wannan ba, a cigaba da abun
da yakamata"
P.A ya ce "To shikenan, na barka lafiya "
Bayan fitarsa Indabo ya shiga cikin gidansa, ya tarar da
Abdul a falo, tare da mahaifiyarsa.
Ya kalli indabo ya ce "Welcome"
"Thank you" ya zauna ya kalli Abdul ya ce
"Dama nemanka nake yi".
Abdul ya ce "To gani"
"Ya maganarmu ta rannan?"
"Daddy maganganun namu ai da yawa, wacce daga
ciki?".
"A'a, ka san wanda suka fi muhimmanci ai, mun daddale
da jam'iyya, kai za a tsayar mataimakin gwamna, tun yanzu yakamata ka fara
harkar campaign, da buga pastoci. Amma ka san dole ka daina duk wani shashanci
da kake aikatawa. Sannan maganar da nake yi, maganar aure, shekara talatin da
biyar, uban me ka ke jira? Muddin lokaci ya cigaba da gabatowa, abokan adawa
suka san baka da aure, sai ku samu matsala a harkar takarar nan, amma da na yi
maganar auren sai ka din ga gocewa"
Ya ɗan tsuke fuska ya ce "Wai constitution ne ya ce
dole sai mutum yayi aure zai yi shugabanci meye amfanin auren mutum a cikin
siyasa to?"
Indabo ya ce "Ban sani ba, idan ba zaka yi ba, ni ina
da wadda zan haɗaka aure da ita, ga 'ya'yan abokai da yan uwa nan sai dai
ka ji an yi".
Hajiya Bilki da tun ɗazu ba ta yi magana ba sai yanzu ta ce
"Haba distinguish, ka bi shi a hankali mana, zai yi, ba sai an yi masa
dole ba".
"Ba zan bishi a hankalin ba, na gaji da wannan shirmen
nasa, rayuwarku nake ƙoƙarin ingantawa, wataƙila idan ya zama mataimakin
gwamna, shi ya fi ni samun dama, ya kuɓutar da ɗan uwansa".
Hajiya Bilki ta ce "Distinguish, kai da ka fishi daɗewa
a harkar, ba ka samu yin hakan ba sai shi, ni na karaya da lamarin jafar"
"No, kar ki yi mamaki ya fi ni samun authority, da
damar fitar da shi, da dai a nan Nigeria ne, da tuni an daɗe da wuce
wurin"
Ta ce "Haka ne, Abdul dole ka yi haƙuri ayi maganar
auren nan, tun yanzu za a fara share fagen samun damar yin nasarar ka, dan idan
ku ka gama tenure ku, kai zaka yi gwaman nan gaba"
Cikin sangarta ya ce "Mummy ba ƙi na yi ba, auren ne ba
na so"
"Aikuwa haka zaka yi haƙuri" suka cigaba da
tattaunawa a kan yadda tsare-tsaren za su kasance.
***
DSP Nasir na tsaka da aiki, aka sanar da shi yayi baƙuwa, ya
ce ace ta shiga, tana shiga ya ga Nabila.
Yayi murmushi ya ce "Ke ce baƙuwar dama?".
"Eh mana, ko na koma ba ka san ganina?"
"A'a ni na isa na na ce haka. Zauna bari na kawo miki
lemo, daga wurin aiki ko daga ina?"
Nabila ta kashingiɗa ta ce "Na je wani trial ne"
Ya ɗaukko mata ruwa a fridge ya ce "Sannu"
Ta ce "Yauwwa" ta karɓi ruwan ta sha, ya ce
"Amma kin bawa kanki wahala da yawa, wace court ɗin ki ka je, har ki ka
iya biyowa nan?"
Ta ajiye robar ruwan ta ce "Wani wuri na je, na ga wani
client, DSP"
"Na'am barrister Nabila maitama "
Tayi murmushi ta ce "Wai ina mutumin nan?"
Ya ce "Wanne?"
"Wanda ku ka kama, haryanzu bai faɗi in da Vipern yake
ba?"
"Ina fa zai faɗa, yana ta wahalar da mu".
"Dan Allah ka nuna mini shi"
"Ki yi masa me?"
"Babu komai, ganinsa kawai zan yi"
Nasir ya ce "To bari na gama aikina, sai mu je ki
ganshi"
Nabila ta zauna ta jira Nasir ya gama abun da yake yi, ta ɗauki
jarkar ruwanta suka fito, yana ta nuna wa abokan aikinsa ita, yana gaya musu
ita yana gaya musu ƙanwarsa ce, lawyer ce. Suka gaggaisa da abokan aikinsa,
sannan suka ƙarasa in da liti yake.
Laɓensa duk ya bushe, saboda yunwa da ƙishirwa, yana ganin
Nabila ya ganeta ya ƙura mata ido, ta kawar da kanta ta ce "DSP tun da ya
ce bai san in da yake ba, haka zaku cigaba da ajiye shi?"
"Eh har sai ya yi magana tukuna"
Ta girgiza kai ta ce "Amma a doka, ai kotu za a kaishi
ko a sake shi, ina ga fa tun da ya ce bai sani ba, bai sani ɗin ba"
Nasir ya ce "Ya sani ba zai yi magana ba ne" ta
miƙa wa liti ruwan hannunta, ta ce "Ga ruwa" banza yayi mata, Nasir
ya juya ya fita yana amsa waya daga wurin ogansa.
Tayi ƙasa da murya ta ce "Na san na yi muku laifi, amma
dan Allah ka yi haƙuri, zan san yadda zan yi ka bar wurin nan".
Ta ciro wani ruwan a jakarta ta bashi, ta ce "Dan Allah
ka yi haƙuri, na fahimci kuskuren da na yi, ban kyauta ba amma zan gyara
komai"
Nasir ya dawo ya ce "Mu tafi?"
"Eh, amma gaskiya, yakamata a san abun yi, kar a taka
doka da yawa"
Ya ce "To masu doka, mu je gida"
"Da gaske fa nake, ko mu shigar da hukumarku
ƙara".
Ya mayar da abun wasa, suka tafi gida.
***
Ƙarfe huɗu na yamma, Nabila ta shirya ta fita, ta tafi gidan
matar da aka ce an yi laifin fyaɗen nan a gidanta.
Ganin Nabila cikin shiga mai kyau, ya sanya masu gadin ba su
tsaya tuhumar wacece ba, suka bata damar shiga gidan.
Sai da haushi ya fara kamata, saboda jiran da aka bar ta
tana yi, daga baya matar gidan ta fito, suka gaisa da Nabila.
Nabila ta ce "Na san baki sanni ba, sunana barrister
Nabila Yusuf maitama, lawyer ce ni mai zaman kaina. Akwai mai gadin gidan nan
malam isyaku, da ake accusing da laifin fyaɗe, ni ce lawyer sa. Na zo ne dan
Allah in ji details ɗin abun da ya faru".
Matar ta tsuke fuska ta ce "Ke, ni ki ka zo ki yi wa
wannan tambayar? Wurin 'yan sandan na je na fara karɓar report, an ce na dawo
station ɗin da aka fara case ɗin, amma na ga dacewar fara zuwa gidan nan, tun
da an ce yarinyar 'yar aikinki ce, kuma ainihin wanda ya yi laifin kina da
alaƙa da shi, ku ka yi framing ɗin sa aka ce shi ne. Yanzu duk ba wannan ba a
matsayinki na uwa kuma 'ya mace nake so mu fara magana. Ina yarinyar take? Ina
ne gidan iyayenta? Ban damu da sanin koma waye yayi laifin ba, fatana kawai a
wanke mai gadi, tun da kun san wanda yayi laifin "
Matar ta miƙe ta ce "Ki koma wurin jami'an tsaro, su
zaki yi wa wannan tambayar, kuma ba ki da wata hujja, da take tabattar da ba
shi yayi ba, idan kin gama kina iya tafiya"
Nabila ta miƙe tsaye ta yi murmushi ta ce "Na gode
sosai antyna da bani lokacinki" ta juya ta fice.
Station ta sake nufa, wanda a nan aka fara case ɗin, aka
nemo statement ɗin da aka rubuta, da sunan Asibitin da aka kai ramma, na cikin
gari, tana tsaka da dubawa, wanda yake evening duty, shugaba a wurin, ya fito
afujajan, ya ƙwace file ɗin wai ba a ba su damar su bata file ɗin tayi bincike
ba.
Cikin mamaki da takaici Nabila ta ce "Waye zai bayar da
damar, bayan wadda ƙasa ta bayar, lawyer ce fa ni, dan me za a hana ni damar
dubawa, doka ta bani damar neman hujjojin da zan gabatarwa kotu, na wanda zan
kare, yaya za ayi a hana ni"
Fafur suka hanata, suka ce ta tafi, ta kira Nasir a waya,
amma wayarsa ta ƙi shiga, ranta yayi mummunan ɓaci.
A gajiye ta koma gida, ana ta kiraye-kirayen sallar
magariba, ta yi wanka tayi salla, ta ɗaukko wayarta ta kira sumayya.
"Ke ya ki ke aikin?"
"Sumy raina a ɓace yake, kin san menene?" Sumayya
ta yi sauri ta katse wayarta, ta saka a Flight mode, ta ɗauki wayar ummanta, ta
kira Nabila ta ce "Sorry wayar ce caji ya ƙare"
Nan ta labartawa Sumayya abun da yake faruwa.
Sumayya ta ce "In dai ƙasar nan ce, ai kaɗan ki ka gani
d.....
Cikin sauri Nabila ta katseta ta ce "Sumayya few months
back, ina wannan case ɗin da yaya murtala ya saka, har aka kusa korarsa? The
case are similar".
Sumayya ta ce "How?"
"In so many ways, dan Allah ki sake binciko mini
labarin, ko ma ki haɗani da yaya murtalan, ke zan ma zo na same shi, the same
yadda matar ta ce an yi wa yarinyar fyaɗe, ɗan yayan matar gidan, shi ma
dattijon nan haka ya ce mini, ɗan yar matar gidan ne yayi abun ba shi ba ne ba,
shi asibiti kawai suka kaita, da shi da ɗaya mai aikin da wani mai yi musu
hidima a gidan, definitely duk case ɗin ne but i want to confirm"
Sumayya ta numfasa ta ce "Ban ƙi ta taki ba, amma ki bi
a hankali, kin ga a kan case ɗin, sai da Murtala ya kusa rasa aikinsa, ke daga
ji kin san case ɗin babba ne"
"Sumayya tsoron da muke ji, da ja da baya shi ke saka
wasu ma suke Fuskantar irin matsalolin, idan na gama bincike na, i will raise
the case, hatta 'yan sandan nan da abun da suka yi mini, duk sai na yaɗa, just
support me sumy, Allah zai taimekemu, ke 'yar jarida ce, zaki iya kema".
Sumayya ta ce "Haka ne, amma kar ki kira ni a wayata,
zan ki ra ki da wani layin, sai mu haɗu da yaya murtalan" ta yi wa sumayya
godiya, tana sake bawa kanta ƙwarin gwiwar lallai za ta tsaya wa wannan
dattijon kuma za ta yi nasara.
***
Abdul ne yake kallon ramma, yadda duk take a takure, tana
kallon tv, amma hankalinta ba a kan tv yake ba.
"Rahama"
"Na'am" ta amsa tana kallonsa.
"Meyake damunki ne?" Tayi shiru ta sunkuyar da
kai.
Ya kwanta a kan cinyarta, ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana
danna remote.
Ya tashi ya ce canzo hijjabinki ki zo, ta yinƙura jikinta na
rawa, ta sako hijjabi, ta fito.
Ta tarar da shi a tsaye da mukulli a hannunsa yana waya.
Ta ƙaraso jikinta yana tsuma, tunaninta ko gida zai mayar da
ita, ya riƙe hannunta, ya buɗe ƙofar falon suka fito.
Da kansa ya sakata a mota, ya rufe sannan ya zagaya ya kunna
motar ya fita da ita.
Sai kallon gari take yi, duk da dare ne ko ina da hasken
fitila, tun da ya kawota a sume, ba ta sake fita ba, kuma ba ta san a ina take
ba.
"Gida zaka mayar da ni?"
Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Ai na ce ki daina
wannan tunanin ma"
Cinema ya kaita, wai kallon film, bayan tv suka baro a gida,
ta din ga waige-waigen yadda za ta yi ta gudu, amma a in da suke zaune, yana
rungume da ita, ga wurin duk ƙabilu ne, abun da ta fuskanta, ba iya cinema ne
wurin ba, dan daga can wani wuri, kaɗe-kaɗe na tashi.
"Naga ki na ta waige-waige, ba mahaukaci bane ni, da
zan kawo ki inda zaki iya guduwa, ko ki yi wa wani magana ba, kowa sabgar
gabansa kawai yake yi a wurin nan, gara ma ki nutsu"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ko bangon duniya zaka kai ni,
idan Allah ya yi niyyar fitar da ni ba ka da dabara".
Yayi murmushi kawai, sai da ya gama abun da yake yi, ya ɗauke
ta, suka tafi ya kulleta a mota, ya sayo mata abinci, ya mayar da ita in da
suke.
***
Nabila kuwa tana ta bin kwatancen da dattijon nan yayi mata,
na gidan zulai ɗaya mai aikin da suke aiki tare da ramma, amma ta kasa gane
kwatancen, ganin ta gaji, kuma ta hanyar ake bi, a je in da Viper yake, ya
sanya ta tare abun hawa, ta sake tafiya.
A wannan karon da ta sauka, google map ɗin ta buɗe, tana
duba abubuwan da suke wurin, ba tare da gazawa ba, ta cigaba da yawon bulayin
neman gidan, cikin sa'a bayan shafe mintuna talatin tana bulayi, ta hango
gidan.
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, sannan ta nufi gidan.
Ƙofar gidan a rufe, ta saka hannu ta tura ƙofar, tayi
sallama.
Ƙofar ta buɗe, sai dai ba ta ji motsi ko alamar mutum a
gidan ba.
Duk da gabanta faɗuwa yake yi, amma haka ta ke ta addu'a ta
shiga. Tsakar gidan ko ina shirgi, can bokiti, ga tukunya can kaya sauran
sigari tsakar gidan kaca-kaca.
Ta ƙarasa ta leƙa ɗakin, ta hango Viper durƙushe a kan
gwiwarsa, yana ƙoƙarin yi wa kansa allura, sai dai hannunsa sai rawa yake yi,
gashi ya huda jijiyar, jini ya fara zuba.
Da sauri ta ƙarasa, ta durƙusa, ta gyara masa sirinjin, ta
cigaba da zuba masa ruwan allurar.
Rintse idanunsa yayi, jin yadda allurar take ratsa jikinsa.
Babu tsammani, ta zare sirinjin ta ce "Wannan abun da
ka ke yi, zai iya shafar ƙwaƙwalwarka fa" ba ta gama maganar ba, ta ji ya
faɗo a jikinta, ta faɗi a wurin saboda nauyinsa, ƙoƙarin ture shi take yi, dan
ji ta yi tamkar wani ƙaton dutse ne ya faɗo mata.
Ya ɗago idanunsa ya kalleta, ya saka hannu ya shaƙe wuyanta.
Numfashinta ya fara fita sama-sama, ta rirriƙe hannunsa
idanunta suka yo waje.
Walid ne ya faɗo ɗakin da gudu, ya fara ƙoƙarin janye Viper
daga kanta.
A tunaninsa jikin Viper yayi sakin da zai ture shi kawai,
amma ya ji da ƙwarinsa.
A wahale ta ce "Zaka kashe ni fa" a hankali ya
saki wuyanta, Walid ya ɗago shi da ƙyar, ya kalli walid, ya kalleta ya sake
mayar da idonsa kan Walid da ƙarfin gaske ya ce "Walid"
"Na'am Al'amin"
"Walid matata, matata walid! Ɗa na Walid mata ta"
yayi maganar yana wani irin ƙaraji, tare da jan rigar walid da ƙarfin da sai da
ta yage.
"Easy maza, easy yi haƙuri"
"Walid zan haukace, walid kaina zai tarwatse, me zan yi
ne wai, ka fitar mini da yarinyar nan, ba na son ganinta matata walid"
yayi maganar yana girgiza kansa.
Nabila ta tashi da kyar, tana ta haki, ta ce "Zaunar da
shi zan yi masa magana dan Allah"
Walid ya ce "Ɗauki jakarki ki tafi, yi sauri"
Kawai Viper ya shammaci Walid, ya buga kansa da ƙarfi a
jikin bango, take jini ya fara biyo hancinsa, ya faɗi ya suma a wurin.
Nabila ta ƙwala ihu, saboda sautin da kansa ya bayar, da ya
buga kan, Walid ma a rikice ya ɗago shi, amma ko motsi baya yi.
Ayshercool.
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin matsanancin tashin hankali Nabila ta nufe su, Walid ya
rikice, ya rasa me ma yakamata ya yi ya taimakawa Viper.
Cikin azama Nabila, ta ɗaga kan Viper yana kallon sama, ta
ciro hular kanta, ta toshe hancinsa da yake zubar da jini, ya zamana ta gefen
bakinsa yake numfashi.
Cikin kuka ta kalli walid ta ce "A kai shi
asibiti mana, ya bugu da yawa, tun da abun ya kai ga zubar da jini ta
hancinsa"
Walid ya ce "Ba za a kai shin ba, uban waye ya ce ki
kuma zuwa ai duk ke ki ka ja?"
Cikin rashin fahimta ta ce "Ni kuma? Ni me na yi? Zuwa
na yi na bashi haƙuri a kan abun da na yi bisa kuskure, wallahi ban yi masa
komai ba, tarar da shi na yi yana yi wa kansa allura jikinsa yana rawa, na karɓa
amma wallahi ban yi masa komai ba. Ko duk haushin abun da na yi wa ɗan uwanku
ne? Na je station ɗin ai, kuma na yi magana da shi, dan Allah ku yi haƙuri
rashin sani ne ya sanya na aikata abun da na yi masa, abun da ake faɗa a gari a
kansa daban, ni kuma ban san gaibu ba, amma dan Allah ku yi haƙuri" tayi
maganar hawaye wani na bin wani a fuskarta.
Walid ya ce "ya isa haka, tashi ki tafi"
"A haka za a bar shi, ba zaka kai shi asibiti ba?"
"Ta yaya zamu kaishi asibiti ana nemansa a kama
shi?"
Fizge-fizge Viper ya fara yi, yana ƙoƙarin tashi, Walid ya
daddane shi, cikin ɗaga murya ya ce "Walid"
Ya ce "Na'am Al'amin"
"Liti" walid ya ce "Ya shiga banɗaki".
Viper ya sake cewa "Mai laya"
"Na kiyayi mai zamani, Allah ya ƙara maka lafiya"
"Gobe zamu je asibiti da ƙanwarka 'yar madara, sun ce
inducing za su yi mata 'yar madara za ta haihu, ragonta yana ƙauye wurin
Hajiya"
Walid ya ce "Masha Allah, Allah raba su lafiya"
"Walid"
"Na'am mai zamani"
"Cikin nan yana ba ta wahala, nima na ƙagu ta haihu, na
ga yarona, sunan ƙanina nura zan mayar, idan ta kuma haihuwa na saka sunan
Sadik".
Walid ya ce "To Allah ya kawo mana su lafiya da
albarka"
Wani irin ihu ya hau yi, yana ƙoƙarin ture Walid, cikin
ƙaraji ya ce "Walid matata ɗa na, ba zan iya komai ba, ka riƙe madaki, kar
ya illata mini mata, ka riƙe shi walid wai me ka ke yi ne?"
Sosai suke kokowa da Walid, ga hancinsa na cigaba da zubar
da jini, ga damuwa da fita hayyaci a dalilin allurar nan.
Walid ya ce "Sai na ci uban ɗan mama idan ya dawo, bai
ji me na gaya masa a kan kawo maka kayan maye ba, sai ya saka mun yi babu ka
rasa ƙwaƙwalwarka tukuna".
Nabila kuwa iya ƙarfinta take kuka, tsananin tausayinsa ya
mamaye zuciyarta, da ƙyar walid ya danne shi, a hankali jikinsa ya saki, ya
daina motsi, amma yana motsa idanunsa, a buge yake ya fita hayyacinsa amma ba
bacci yake yi ba, abubuwan da suka wuce ne suke dawo masa cikin mayen.
Nabila ta ce "Dan girman Allah ka gaya mini ƙarashen
labarin nan, ina jauhar ina abun da yake cikinta?".
Walid ya ce "Kin ga ni ba wannan ne a gabana ba,
lafiyar ɗan uwana da taya shi ɗaukar fansa ita na saka a gaba, dan haka ki
tashi ki tafi kawai"
Nabila ba ta sake magana ba, ta tashi jiki a sanyaye, ta ɗauki
jakarta, har ta kai bakin ƙofa, ta waiwayo ta sake kallonsa, hakan yayi dai-dai
da buɗe idanunsa, sun yi jawur gwanin ban tsoro, ya tsura mata ido, a hankali
ta juya ta fice.
Cikin maye ya ce "Mai laya"
"Allah ya taimaki mai zamani"
"Ba na son ganin yarinyar nan, zan iya fara kisan kai a
kanta".
Walid ya girgiza kai ya ce "Ba ka taɓa yi ba, kuma ba
zaka fara a kanta ba" surutan da Viper ya cigaba da yi ne, ya tabattar wa
da Walid ba ya cikin hayyacinsa.
***
Ramma ta na zaune, ta na cin farcenta, tana zancen zuci, ta
ji Abdul ya kama hannunta.
Sai da ta firgita, kasancewar tayi zurfi a zancen zuci.
Hannunsa riƙe da nail cutter, ya fara cire mata faratan ya
ce "Ƙazama kawai, da baki ki ke cin farce" janye hannunta ta yi ta ce
"Ni kar ka shafa mini cuta" tayi maganar tana haɗe rai.
"To cuta ta nawa kuma, in dai ina da ita da tuni kin ɗauka
ta can wurin. Duk rashin ji na, ina using protection, a kanki ne kawai nake
gaba gaɗi, shi ma dan na san am safe na killace ki" tsaki ta yi ta kawar
da kanta gefe.
Ya kama hannunta, ya cigaba da yanke mata farcen ta ce
"A banza, wallhi ko haɗiyeni zaka yi, ka fito da ni, ba zan yafe maka
zaluncin da ka yi mini ba"
Bai kalleta ba ya ce "Dama ban ce ki yafe mini ba
ai" ya na cikin yanke mata, ta ga yana ɗan yamutsa fuska, ya gama ya tashi
ya koma ɗaki, ta kalli falon komai tsaf solomon yake gyarawa, a ranta ta ce
"Dama aure ne da ni, ace nan gidana ne ba wannan ƙazantar ba. Tunanin
hakan kawai ya saka idanunta cika da hawaye.
Ta ɗaukko magazines ɗin da ke falon, tana ta kalla, har ta
manta da shi a gidan, ta shiga bedroom ɗin, ta tarar shi a kan gado yana
murƙususu.
Ta kalleshi ta ce "Menene?"
A wahale ya ce "Kira mini solomon" ta juya ta
fita, ta kiro shi.
Ya ɗaga kai ya ce masa ya kawo masa biro da takarda.
Ya kawo masa, yayi rubutu a jiki, ya ce yaje ya sayo masa.
Solomon ya fita cikin sauri, ta kalleshi ta ce "Wai
menene?"
Ya ce "Epigastric pain ne"
"Me kenan" ya nuna mata cikin sa.
Ramma ta ce "Sannu Allah ya sa mutuwa zaka yi na
huta"
Yayi mata shiru, ya cigaba da juyi, ya dunƙule hannunsa yana
dukan gadon a hankali, yana yi yana miƙa alamar yana jin jiki sosai.
Ta tsaya tana kallonsa, gumin da yake yi, ya sake tabattar
mata ya fara galabaita.
Yayi mata nuni da hannunsa ta je, ta ce "In zo in yi
maka me?"
Girgiza kai ya hau yi, yana kiran "Mummy, rahama cikina
am in pain"
"To sannu"
Ta samo jarka da ruwa, ta tofa masa bisimillah ƙafa 19, da
suratul fatiha ƙafa 7, ta hau kan gadon ta ce "To tashi ka sha ruwa"
ya tashi da ƙyar ya karɓa, ya shanye, yayi jifa da jarkar, ya kwanta a kan
cinyarta ya ce "Rahama cikina"
"Allah ne yayi maganinka, a cikin sakans idan ya ga
dama, zai rabaka da rayuwarka, ka ga idan mutuwa zaka yi, ga saɓo kana yi, ga
zaluncin da ka yi mini, Allah ya sa ka mutu".
Abdul ya ce "Da na mutu shahidi, ciwon ciki ne ya kashe
ni, kuma ƙarshe ace ke ki ka kashe ni".
"Ko shahidi ka mutu kan ka shiga aljanna, sai ka shiga
.... Sai kuma ta yi shiru. "Allah dai sai ya ƙwatar mini hakkina a wurinka
na zalunta ta da ka yi"
Solomon yayi knocking, Abdul ya ce ya shigo, ya shigo da
leda a hannunsa, Abdul ya karɓa, ya sakawa kansa butterfly needle, ya saka
ramma ta haɗa allurar da aka kawo, ya ce tai masa.
"Ni ba zan iya ba, tsoro nake ji"
"Tsoron me malama, ciwo zai kashe ni"
"To ni taɓa yi na yi?"
Cikin tsawa ya ce sai ta yi, hannunta na rawa, ta zuba
allurar a cikin butterfly needle ɗin.
A haka ya nuna mata yadda za ta saƙala masa ruwa, yana yi
suna faɗa, ta saka masa ya sa hannu ɗaya ya janyota, ya sake kwanciya a kan
cinyarta.
Yadda yake wash wash da kiran sunanta, sai ya ƙular da ita
kamar ba namiji ba.
"Ni ka daina kiran sunana tun da ba ni na ɗora maka
ba"
"Wash rahama cikina" tsaki ta yi ta ce "Wai
shekarunka nawa?"
"36yrs" yayi maganar yana kallonta.
"Amma an yi asarar ƙuruciya, idan ba ka yi wasa ba kana
cikin wanda annabi ya ce kun yi asara, ka tafiyar da ƙuruciyarka a shirme da
shashanci, a mintuna ashirin ɗin nan da Allah ya ga dama, da yanzu babu kai, me
zaka ce wa Allah, ka sha giya ka kwana kana zina da 'yar da ka raba da uwatta,
ka canza tunani da halaye, ko Allah ya yi maka rahama".
Ya lumshe idanunsa ya yi shiru, bai ce mata komai ba.
***
Nabila kanta tamkar zai tarwatse ita ma haka take ji, so
take ta kamo bakin zaren tallafawa Viper. Babban abun da yake buƙata yanzu
rehabilitation ne, a fara nesanta shi da shaye-shaye, sannan a kwantar masa da
hankali da ƙoƙarin tirsasa masa karɓar ƙaddararsa ta hanyar da ya dace. Sannan
a fuskanci kamo zaren tsaya masa, ya ɗauki fansar abun da aka yi masa ta hanyar
doka, ba ta hanyar da yake tunanin ɗauka ba, sai dai alamu sun nuna mata ba zai
sarrafu cikin sauƙi ba, balle a samu fahimtar juna da shi, sai dai ta ƙudurce a
ranta, duk tsanani da wahalar lamarin, za ta tsaya a kan sa, ko da kuwa sanya
rayuwarta cikin hatsari ne, za ta yi domin taimakon Viper.
Sai dai hakan ba zata yiwu ba, sai ta ji ƙarshen labarinsa,
amma ta yaya?. Da ta tuna yadda yake kururwa yana kiran matarsa, ɗansa sai ta
ji ta karaya, tausayinsa ya ƙara kamata.
Ringing ɗin wayarta ne ya katseta daga tunanin da take yi,
ta ga lambar sumayya, ta ɗauki wayar ta kara a kunnenta.
Sumayya ta ce "Na yi wa Uncle murtala kwatancen
gidanku, zai zo ya same ki, sai ku yi magana".
Nabila ta ce "Kai sumy, ban da ni ki bari na je na same
shi, ni da nake nema?"
Sumayya ta ce "Ya zo ya same ki is more safe, ba wanda
zai kawo wani abu, kin san yanzu rayuwa babu tabbas mussman irin aikinmu".
Nabila ta yi murmushi ta ce "Hakane masoyiyya, na gode
sosai, saura ɗaya aikin"
"Wanne kenan?"
"Waye indabo?"
"Kin ga ki raba kanki da indabon nan, wai me ki ke nema
a kansa ne? Ba dai kin yi masa wulaƙanci kin ƙi gaishe shi ba, menene na
bibiyarsa"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Ba zaki gane ba, ki
taimaka kawai"
"Nabila kamar kina ɓoye mini wani abu fa".
"Ba abun da nake ɓoye miki, mamakinki kawai nake yi,
duk kin canza kina abu kamar mara gaskiya kwanan nan sumayya"
Dummm gaban Sumayya ya faɗi ta ce "Ban gane ba"
Nabila ta yi dariya ta ce "Kar ki manta fa ni lawyer
ce, idan na so zan gane idan ma baki da gaskiya, don't mind me kawai dai na ga
kina ƙoƙarin kawar da maganar indabon nan ne, shiyasa nake tsokanarki, am about
to do something big, zan gaya miki menene daga baya"
"Nabila Please, kar ki je ki yi abun da ba shikenan ba,
ki raba kanki da duk wani abu da zai sake haɗa ki da Aminu Vipern nan, kar ma a
cetare ku ke. Ki bar DSP yayi aikinsa dan Allah"
"Ni ba maganar Viper nake yi miki ba, case ɗin dattijon
nan nake magana a kai, amma ki binciko mini maganar indabon nan, ko na binciko
da kaina".
Sumayya ta ce "To shikenan na ji zan yi, amma ki san in
da zaki din ga zuwa da abun da zaki din ga yi kin ji arfan Abba"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Ji sai ka ce wata uwata,
to na ji sai anjima" ta kashe wayar tana murmushi, a duniya bayan Abba ba
ta tunanin akwai wanda ya kai Sumayya damuwa da ita, da tsoron ta aikata wani
abu, da zai janyo mata matsala.
Bayan sallar magariba, Murtala ya kirata a waya, ya sanar
mata da ya zo, yana ƙofar gidan su.
Ta saka hijjabi ta fita, suka gaisa ya ce "Sumayya ta
ce "Ki na nemana"
"Au ba ta yi maka bayani ba?"
Murtala ya ce "Tayi mini, daga bakinki nake son
ji".
"Haka ne, ka ga wani case na samu, na wani dattijo, an
yi framing ɗin sa, wai yayi wa wata yarinya 'yar aikin da yake gadi fyaɗe, na
je na yi magana da shi, yayi mini bayani, ya ce ba shi bane ba, ɗan yayan matar
gidan ne, so abubuwa da yawa are similar to rahoton da ka bayar kwanakin baya,
shiyasa na ce bari na neme ka, ka ƙara yi mini bayanin yadda abun yake".
Murtala ya numfasa ya ce "Kin san duk abun da aka ce,
harka ta manya ce, sai dai a lallaɓa a yi komai a ɓoye ko ba haka ba, an ce
yaron nan ɗan manya ne, kar mu je ki yi wani abun da zaki sakamu a matsala
fa"
Nabila ta ce "Uncle murtala, ba zan saka kowa a matsala
ba, dattijon nan nake son na taimakawa, kunna mini recording ɗin matar, na sake
ji".
Ya kunna mata recording, ta saurara tiryan-tiryan, Nabila ta
ce "Uncle murtala, case ɗin dai ai wannan, ba shi ne aka ce Naja'atu
Bunkure ta shiga case ɗin ba, ai da na ce zan shiga case ɗin yarinyar".
Ya ce "Shikenan, faɗuwa ta zo dai-dai da zama, amma dan
zatin Allah don't mention my name".
Ta jinjina kai ta ce "Kar ka damu in sha Allah ba zan
yi mentioning ɗin ka ba. Naja'atu Bunkure ko da me take yawo a kanta, sai ta
gaya mini in da case ɗin ya tsaya, ka san ina station ɗin da aka fara case ɗin,
aka ƙwace file ɗin daga hannuna, wai ba zan duba ba".
Haske su aka yi da fitilar mota, Nabila ta tura baki, tana
kare fuskarta, Nasir ya gyara parking ɗin sa, ya fito ya nufo su.
Ta ce "Yaya sannu da zuwa" bai amsa mata ba, ya
kalli murtala ya ce "Malam ya dai, ya aka yi?"
"Yaya idan saurayina ne, haka zaka yarfa ni dan Allah?
Abokin aikin sumayya ne, muna tattaunawa ne a kan wani case".
Nasir ya sake tsuke fuska ya ce "Kuma da daddaren
nan?"
"Eh, saboda shi ɓoyayyiyar shaida ne, da ba zan bayyana
shi ba, ba na kuma son a samu trace, na wani ya ganshi, shikenan uncle murtala
ka gaida gida"
Yayi wa Nabila sallama ya tafi.
Ta cigaba da yi wa Nasir mita, "Gaskiya yaya na
fuskanci saboda kai wasu samarin namu suke tafiya, da haka za a aure mu, kana
zare musu ido, kamar wasu 'yan ta'adda".
"Eh, gara a zare musu idon, su san nan ba wurin da za
su zo su kawo wargi bane ba" kawar da zancen ta yi, ta hanyar bashi
labarin case ɗin dattijon nan, da yadda aka ƙwace file ɗin.
Sosai ya din ga mita, har yayi alwashin rakata sake komawa
station ɗin, a bashi tun da tana lawyer, dole a bata dukkan haɗin kan da take
buƙata.
Bayan ta koma ɗakinta, ta din ga murmushi itakaɗai, abu zai
case zai haɗa ta da Naja'atu Bunkure, "Sai na ga abun da ya ture wa buzu
naɗi kuwa" sai dai walwalarta ta ɗauke, bayan tuno wa da Viper, kar ta
shagala da ramuwar gayya a kan Bunkure ta sakankance ta gaza samo mafita a kan
nasa case ɗin.
Tana buƙatar wanda zata tattauna case ɗin da shi matuƙa,
amma ba ta ga wanda ya dace tayi maganar da shi ba. Dan ko da wasa ba zata
tunkari DSP ba, balle sumayya tsfa zata ce za ta gaya wa Abba, dama ban da su
biyun nan, ba ta wanda ya dace, ta sanarwa wannan gangancin da take shirin yi
ba.
Sai dai kwana ta yi, tana tunanin ko yaya Viper, ya farfaɗo
gaba ɗaya ya warware ko kuma yaya?
Washegari da safe, da DSP suka tafi station ɗin nan, a hanya
yake sanar mata da an yi belin Liti, ta tambaye shi waye ya yi belin Litin, ya
ce mata bai sani ba, waya kawai aka yi masa aka ba shi umarnin ya sake shi.
Nabila ta ce "Nigeria ƙasata"
Suka isa police station, Nasir ya nuna musu id card ɗin sa,
sannan ya nemi su bashi file ɗin da Nabila ta nema, amma suka tabattar masa da
an zo an karɓi file ɗin an mayar da shi babbar headquarter.
Nabila ta ce "No wonder, hakan ya sake tabattar mini da
lallai wanda ya aikata laifin, ɗan manya ne, kuma ba dattijon nan ne yayi
ba" ta cewa Nasir kawai su tafi dama ta san a zaman farko sai an aike da
baba prison, kafin ta gama tattara hujjojinta.
Sai dai duk da haka, Nasir ya nemi a ba su in details,
statement ɗin, da Asibitin da aka kai yarinyar, amma suka ce ba a ba su wannan
umarnin ba, komai da komai yana babbar headquarter.
Suna tafe take ce masa "Kar ka damu yaya, zan baka
mamaki ƙoƙarin da zan yi a kan lamarin nan, zan tattara hujjojina na shiga
kotu" yayi murmushi tare da ccigaba da ba ta ƙwarin gwiwa, ya biya ya
ajiyeta a wurin aiki sannan ya tafi.
Cak ta tsaya a harabar wurin, tana ƙarewa motocin kallo, ta
tsayar da idonta a kan baƙin motocin da ta gani guda uku, sai dai ɗayar ita ce
motar da ta din ga bin ta, har ta tsaya tayi knocking ɗin glass. Ta ƙarasa ta
zagaye motar, ta sake tabattar da ita ce, ta jinjina kai ta shiga.
Ta je office ɗin ta, ta ajiye jakarta, ta fita ta tafi
office ɗin Barrister Habib, a hanya ta ci karo da MD barrister Kabir da wani
babban mutum, da ta taɓa haɗuwa da shi a office ɗin sa.
Cikin girmamawa ta risuna, ta gaishe su, suka amsa,
Barrister kabir ya ce "'yar ƙwalisa in ji habib, an shigo kenan?"
"Eh sir, na biya neman wata shaida ne, ban samu ba ma,
na taho"
Ya ce "Sai haƙuri, haka lamarin aikin dama yake,
wataran nasara wataran sai haƙuri, na ji daɗi da na ga kina mayar da hankali
yanzu kin rage kwalliya".
Mutumin ya zuba mata ido, yana ta murmushi kamar an yi masa
kyautar kujerar makka, dan sai da ta faki idon Barrister kabir, ta galla masa
harara, sannan ta yi gaba.
"Yaya Habib"
Ya ce "Yau kuma?"
Ta ce "Eh mana, yau baƙi muka yi ne?
Ya gyaɗa kai ya ce "Dama wurin nan ai kullum cikin baƙi
yake"
"Wasu motoci na gani, wata farar mota ta waye?"
Ya ƙura mata ido sannan ya ce "Hala na samu demotion ne
zuwa mai gadi?"
Tayi dariya ta ce "Am very sorry, ka san wani
abu?"
"Sai kin faɗa"
"Ka san shi Allah, mai son bawansa ne, da kuma jin ƙan
sa"
Barrister Habib ya ce "Wannan haka yake".
"A wannan karon, ba tare da na yi tsammani ba, akwai
yiwuwar case ya haɗani da Najar bunkure, to kuma ka san ni yanzu kai ne mentor ɗina,
na zo mu yi magana "
Yayi dariya yana mayar da wasu files, drower gabansa ya ce
"Nabila 'yar ƙwalisa, haryanzu ba ki san wacece Bunkure ba ko?"
"And ba na buƙatar na sani, kawai i need your support,
i want expose her hidden face to the world "
"How?"
Nan ta bashi labarin duk abun da yake faruwa, da case ɗin da
yake hannunta.
Ya ce "Nabila"
"Na'am barrister yaya Habib"
Yayi murmushi ya ce "Zaki ga yaya, aradu ki ke shirin
tara da ka fa"
"Na shirya mata".
"Tana da wanda suka tsaya mata matar nan "
"Ni ma Allah ya tsaya mini"
Ya jinjina kai ya ce "Kin gama magana"
Nabila ta ce "Yauwwa barrister, and i want you to
support me, dan Allah ka taimaka mini"
"Ba ƙi nayi ba Nabila, matar nan manyan mutane da
manyan ma'aikata sun kasa ja da ita, ke kin san ba haka nan take ba"
Nabila ta sake gyara zamanta ta ce "Support me, you
will be proud of me"
Ya sauke numfashi ya ce "Duk abun da ki ke buƙata na
taimako, ki yi mini magana kamar yadda na taimaka miki ki ga file ɗin Viper,
zan cigaba da taimaka ki, amma ya zama sirri tsakanina da ke" tayi shiru
tana kallonsa, ji tayi kamar ta yi masa zancen Vipern, sai dai a zuciyarta ta
ji, ba ta gama amincewa da shi ba, kuma ba kowa za ta yi wa magana a kan case ɗin
sa ba, dan haka ta yi murmushi ta ce "Na gode Allah ya saka da alkhairi ya
raya maka zuriya. Amma yanzu ya kake ganin za ayi? Office ɗin ta zan je, a kan
ina son bayanai daga gare ta, da bakin yarinyar?"
"Eh mana, go as a barrister, ke ma lawyer ce, go with
your full confidence"
Tayi murmushi ta ce "Na gode sosai ranka ya daɗe"
ta juya ta fita cikin farinciki.
Sai dai kuma tunanin Viper ya cika mata zuciya, ko yaya
jikinsa? Ya warware gaba ɗaya ko kuwa?
Ba tare da dogon tunani ba, ta ɗau jaka ta fita, ta samu mai
sayar da fruit, ta sai uban kayan marmari ta tari abun hawa ta tafi.
Sai dai ta sha wahala, tana ta bulayi, ga uban kaya a
hannunta, ta kunna Google map, yau sai ya fara yi mata hauka ta ce "Wai
shi wannan ma anya ba aljani bane ba?"
Har ta fitar da rai, kawai ta hango roofing gidan, haka ta
cigaba da tafiya, har ta isa ƙofar gidan.
Duk da tsoro da fargabar waccan shaƙar da ta sha, na neman
kashe mata gwiwa, ta tsananta addu'a tare da neman kariyar Ubangiji.
Jin sallamar mace ya sanya gaba ɗaya suka ɗago suna
kallonta, liti ya zabga ashar ya ce "Ke uban me ya kawo ki nan, munafuka
macuciya?"
Ta ce "Ashe kuma ka fito"
"Ban sani ba, uban me ya kawo ki?"
"Wurin Viper na zo" ta bashi amsa kai tsaye. Ya
tashi tsaye zai zare wuƙa, Walid ya hana shi, ya ce mata "Me zaki yi masa,
kin manta abun da yayi miki ne? Ki bar taƙama da baya kisan kai, zai iya farawa
a kanki, dan yanzu ƙwaƙwalwarsa sai a hankali "
Nabila ta ce "Shi ne dalilin sake zuwana, in ji ya
jikinsa kuma na ji ƙarshen labarin nan"
Walid ya ce "Jiki yayi sauƙi mun gode, amma ki tafi kar
ki sake zuwar mana, saboda zuwan da ki ke yi zamu canza wuri"
Liti ya fusata ya ce "Ke dalla fita"
"Ka daina hantarata, ba wurinka na zo ba. Ni dai ku
taimaka ku haɗani da shi, yakamata na ji da bakinsa ya yafe mink"
"Ke! Ni ki ke gaya wa haka?"
Walid ya ƙara dakatar da Liti ya ce "Ya riga ya yafe
mikin ai"
Ta girgiza kai ta ce "Ban ga alama ba, akwai buƙatar
sama masa nutsuwar ƙwaƙwalwa kafin tunkarar duk wani abu, a ɗan zuwan da na yi,
na fuskanci kuna amfani da ƙarfi wurin tursasa masa karɓar abun da ya zo masa a
yadda yake.
Baku da raunin, da zaku tausasa masa yadda yake buƙata"
Walid ya ce "Kamar yaya?"
"Kamar yadda nake faɗa yanzu, a fara samo ƙwaƙwalwarsa,
ta hanyar daidaita gangar jikinsa, da hana shi ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, a
saita tunaninsa da tunatar da shi shi wanene, ko ba duka ba, ayi ƙoƙarin samar
masa da wani abu na farinciki ko yaya, a gwada canza masa tunani ba ta ƙarfin
tsiya ba, kuma a sama masa likitan da zai din ga duba ƙwaƙwalwarsa"
Walid ya ce "Taɓ, ke zaki iya duk wannan ɗin?"
Cikin ƙwarin gwiwa Nabila ta ce "Ku bani dama, na san
kuma a ba a karon farko ya karɓe ku ya saba da ku ba".
Kafin wani ya kuma magana, ya turo ƙofa ya shigo.
Walid ya ƙure shi da ido, dan kar yayi wa Nabila wani abu,
ko nuna ya ga mutum a wurin bai yi ba, balle ya yi wani abu, ya shige ɗakinsa
ya nemi wuri ya zauna a kan katifa.
Babu fargabar komai, ta bi bayansa, tare da yin sallama a ɗakin,
bai amsa ba kuma bai ɗago ba.
Ta je gabansa, ta durƙusa da gwiwoyinta a ƙasa, ta ce
"Ranka ya daɗe, wurinka na zo fa" ya cigaba da 'yan dube-dube.
"Duk da na san, ba zaka amsa mini ba, amma na san kana
ji na, wannan zuwan da na cigaba da yi, ina yi ne don neman afuwar kuskuren da
na tafka bisa duhun kai, da rashin sani, amma dan Allah ka yafe mini ka yi
haƙuri dan Allah" tayi maganar muryarta na rawa.
"Dan Allah ka yi magana, wallahi na kasa sukuni, a
dalilin jahiltal abun da ya sameka, ban san haka abun yake ba, ka yi magana ka
ce ka yafe mini please"
Still bai yi magana ba, sai dai ya ɗago ya kalleta, hakan ya
sanya ta saurin cire idonta daga nasa.
Ya miƙa mata hannunsa ya ce "Bani"
Jakarta ta ɗaukko ta buɗe, ta ɗaukko wayarsa, ta miƙa masa,
ya saka hannu ya karɓa, sannan ya ce "Sai da nayi kaffara a dalilin
rantsuwa da na yi zan kashe ki, ban kashe ki ba, ki ka sake na sake rantsewa
sai na aiwatar"
"Da kuwa ka ci amanar 'yar madara"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin hanzari ya kalli Nabila, yana mamakin a ina ta san
wannan sunan, dan sam bai san Walid ya gaya mata labarin sa ba.
Ya ƙureta da ido, ta kawar da kanta gefe, ta ce "Eh,
idan ka kashe ni, ka ci amanarta, ta barka ka kusa dawowa hanya, amma ka koma
ruwa fiye da baya. Zan so na ji ƙarshen labarinta, amma kafin nan bari na tafi
yanzu, ga kayan dubiya nan na kawo maka, Allah ya ƙara sauƙi" sai da ta
gama maganar sannan ta ɗago ta kalleshi, still ita yake kallo.
Ta sake cewa "Ina fatan zaka yafe mini laifin da nayi,
rashin sani ne" ta tashi a hankali ta ɗauki jakarta ta fita, tana yi wa
Allah godiya da wannan karon, ba ta sha shaƙa ba, hakan ya sa ta ƙara kin
ƙwarin gwiwar cigaba da gwagwarmayar da ƙuduri aniya.
Bayan fitar Nabila, Viper ya ɗaga kai yana kallonsu ɗaya
bayan ɗaya, Walid ya ce "Ko ba ka yi magana ba, na san menene a ranka, ba
kowa bane ba, ni ne nan na gaya mata labarinka".
Ya tsayar da idonsa a kan Walid ya ce "Saboda me?"
"Saboda dalili mai ƙarfi, cigaba da cusa kanta a
lamuranka cikin duhun kai, tamkar ƙara yawan matsalolinka ne, zuciyar mace ta
na da rauni, fiye da dukkaninmu, ina ganin hakan zai iya yi mana am..... Bai
ƙarasa ba, viper ya katse shi ya ce "Ta yaya? Na ce ta yaya? Meye amfanin
gaya matan, na gaya maka bana buƙatar cigaba da ganin yarinyar nan, sai an haɗa
baki da ita an ƙara rusa ni kenan? Da raunin na su ake amfani a sarafasu a cuci
mutum, halittu ne su marasa imani....
"Raunin 'ya mace, da tausayinta irin na halitta, kar ka
manta shi ya jefa ka a cikin halin da ka ke ciki, idan mace ɗaya zuwa goma sun
cutar da kai, ɗaya zuwa biyu sun yi maka abun da ba zaka taɓa iya biyansu ba,
wanda tausayi da soyayyar da mace ta nuna maka, giɓin da ta bar maka ne, ya
ƙara assasa tunzura zuciyarka ka ke fama da jinyar da muka rasa bakin zaren yi
maka maganinta. Idan zaka yi adalci, ka yi musu hukunci da halin ƙanwata,
Jauhar ko ba dukkansu ba. Yarinyar nan gaskiya ta gaya maka, idan ka yi kisan
kai ka ci amanarta, wannan miyagun ƙwayoyin da ka ke ƙara ɗurawa kanka, su ma
ba ka yi mata adalci ba".
Al'amin da ya ji maganganun Walid sun ishe shi, sai ya miƙe
tsam ya sake ficewa.
Walid ya yi wa Ɗan mama inkiya ya bi bayan sa ya ga ina zai
yi.
***
Ramma ce take dukan gefen fion da Abdul yake
"Abdulyasar Abdul yasar" ya buɗe idonsa da kyar ya kalleta.
"Ka tashi ka yi sallar asuba, gari yayi haske, sallar
ma baka yi" ya ja tsaki ya sake juyawa.
Ta sake cewa "Ka tashi gari fa yayi haske"
"Kin san jiya da daddare fa ban yi bacci ba, ki
ƙyaleni"
Ramma ta ce "Haka ne kam, dama ba ka da lafiya,
wataƙila a cikin baccin za a zare maka rai, ban sani ba ko kana da abun da zaka
gaya wa Allah a kan rashin salla" kan ta rufe baki ya tashi zaune yana
ƙifta ido.
Ta girgiza kai ta ce "Kai yanzu baka shirya wa mutuwa
ba, ka ke rashin mutunci? Allah sarki ɗan Adam abun tausayi" ji yayi
jikinsa yayi mugun sanyi, kamar mutuwar ce ke tunkaro shi, ya je ya yi alwala,
ya fito ya tarar tana gyara gadon da ya tashi.
Wayarsa ce ta fara ringing, ya tashi da sauri, ya ɗauka, ya
saka a kunnensa "Hello mummy"
"Kana ina ne?"
Ya ce "Ina gidana"
"To zuwa anjima ka zo gida, zaka yi magana da babanka,
shugaban jam'iyya ya ce ka je ka ga 'yar sa, ku daidaita kanku, ayi magana dan
ba za su yadda a baka takara ba, baka da aure".
"Haba mummy, aure kuma? Ni wai dole ne auren nan, a
haƙura mana"
"Ban gane a haƙura ba, waye zai yadda ka yi deputy
governor ba ka da aure, lallai ka zo anjima ku yi magana dama yana cewa ni nake
hure maka kunne"
Abdul ya ce "Ba ni da lafiya fa"
"Ka sha magani ka zo, ulcer ce?"
Ya ce "Eh, kuma wallahi ina jin jiki, dan Allah ki
bashi haƙuri zan zo ne"
Cikin damuwa ta ce "Ko na turo a ɗaukko mini kai, ba na
son ciwon cikin nan naka fa"
Ya kashingiɗa ya ce "A'a, zan warware, idan na ji sauƙi
zan zo, sai anjima zan ɗan kwanta" ya ajiye wayar. Tun da ya fara wayar,
ramma ta ƙura masa ido har ya gama.
Ta ce "Ka ga banbancin rayuwar mace da ta namiji ko?
Kaga duk abun nan da ka ke yi, kai an samo maka mata ni mecece makomata?"
Ya kalleta ya ce "Kishi ki ke yi ne?"
"Allah ya rufa mini asiri, na rasa a kan wa zan yi
kishi sai kai, ka wulaƙanta mini rayuwa ka cuce ni, kai ka yi aure ka tara
iyali, ni kuma babu wanda zai kalleni, ka yi mini fyaɗe ka mayar da ni ƙaramar
karuwa, har ciki na ɗauka duk ta ƙazamar hanya ka wulaƙanta rayuwata"
Abdul ya zauna sosai ya ce "Ke ki ka fara wulaƙanta
rayuwarki, da ku ka yi yinƙurin cewa zaku nemi hakkinku a kotu, alhalin ba zaku
iya ja da ni ba"
"Sannu tsohon azzalumi, dama mai kuɗi shikaɗai Allah ya
ce ya ji daɗi a duniya? Yanzu duk wannan abun taƙamarka kana da kuɗi ni 'yar
talakawa ce? In sha Allah sai Allah ya ƙasƙantaka da kai da masu goya maka
baya, suka tsaya maka kake rashin mutunci. Na san akwai ire-irena da yawa yaran
talakawa da kuka zalunta, Allah ya na kallonku. In sha Allah sai Allah ya nuna
maka iyakarka tun a duniya Abdul yasar"
Duk da ya ji zafin maganganunta amma sai cewa yayi "Ko
wanda ya raɗa mini sunan nan, bai kai ki iya faɗar sunan ba Rahama, Abdul
yassar"
Kallonsa tayi tana kuka, haushin kanta yakamata da lokacin
da yake waya, ba ta yi ihu a wayar ta ce a taimaka mata ba sace ta yayi. Yanzu
ko wayarsa ta ɗauka ba zata iya operating ɗin ta ba, kuma ba ta da lambar wanda
ta haddace balle ta kira.
***
Abba yana zaune yana kallon labarai a Aljazeera, Nabila ta
shiga da sallama, yana kashingiɗe, ya tashi zaune yana murmushi ya ce
"Barrister, kin yi mini wuyar gani da yawa fa, kullum na dawo kina aiki,
baki dawo ba aiki ya hana mini arfana sukuni"
Tayi murmushi ta ce "Abba ni kaina ina kewarka, bana
samun zama, yanzu na shiryu ai, ina aiki sosai da sosai, na san addu'a ka ke yi
mini"
Ya ce "Kullum Addu'ata a kanku take, mussaman ke
arfana, Allah ya yi miki jagora a dukkan lamuranki".
"Eh mu ma Allah ba zai tagayyara namu ba" Umma
tayi maganar tana harar Nabila.
Nabila ko a jikinta ta ce "Abba dan Allah abu na zo
roƙonka"
Ya ce "Ina jinki ƴar albarka"
"Abba dan Allah mota nake so, wallahi wahala nake sha
samun napep, ayi ta haɗani da maza, ga zirga-zirga na yi ta kashe kuɗin mota,
kuma haryanzu ni ba na yi wa client ɗina charges mai yawa"
Yayi dariya ya ce "Nawa ki ka tara?"
Tayi shiru sannan ta ce "Ina da 400k"
Ya kwashe da dariya ya ce "400k, sai dai a gyara miki
tsohuwar honda ta"
Cikin shagwaɓa ta ce "Haba Abba, big girl kamar ni, da
tsohuwar mota, ka taimaka Please"
"Babu komai, za a sai mota in sha Allah, amma da sharaɗi
ba na son yawon babu gaira babu dalili, kuma ke zaki din ga zuba manki, ba zan
sai mota na din ga cacar mai ba"
Cikin takaici Umma ta ce "Major mu fa? Muna zaune zaka
saya wa Arfa mota, wannan wane irin rashin adalci ne?"
Ya kalleta ya ce "Da walida zan saya wa mota, ba zaki
faɗi haka ba, ku fa da me? Ga mota nan ana kai ku unguwa a ciki, meye na kishi
da 'yar cikinku? Ku daina haɗa kanku da ita, kun san abun da nake nufi".
Arfa ta tashi ta ce "Abba sai da safe" ta juya
zata fita, ta yi wa Umma gwalo, a ranta ta ce "Saura ma babar su DSP idan
ta ji, sai dai ku mutu".
Ta koma bedroom ɗin ta tana murna, ta ɗauki wayarta, Viper
ya faɗo mata a rai.
Lambarsa da ta saka a wayarta, ta lalubo, ta zubawa ido,
murmushi ta yi, ta kira lambar ta saka a kunnenta.
Yana zaune a kan katifa, yana ta shan sigari, zubawa lambar
ido yayi, ya gaji ya ajiye wayar, ya cigaba da abun da yake gabansa. Ba ta gaji
ba ta din ga kiransa babu ƙaƙƙautawa, har sai da ya hasala, ya ɗaga wayar, amma
bai yi magana ba.
"Har na kusa fushi sannan ka ɗaga, na san da 'yar
madara ce, ko ba ta san mai lambar ba, zata ɗaga kuma za ta saurareni, haka
zalika zata yafe mini laifin da na yi mata. Akwai abubuwan koyi sosai da sosai
a rayuwar ta, da ya ci ace ko ba duka ba, ka yi koyi da wasu, ba ta wulaƙanta ɗan
Adam da tana yi, da ba ta riƙe ka da amana da tausayawa ba. Ina sake roƙonka
yafiya, da kuma fatan samun haɗin kanka, ka ƙarasa mini labarinka da kanka, ina
sha'awar kasancewa wani ɓangare na labarin nan, mai ban tausayi da ratsa zuciya
Viper, sai da safe" tun da ta fara maganar, ya sunkuyar da kai, ya saki
sigarin da take hannunsa, ya sunkuyar da kai hannunsa yana rawa. Ta gama
maganar ta katse wayar, amma ya kasa ajiye wayar.
Sai da liti ya dafa shi ya ce "Maza yane?" Ya ɗago
idanunsa ya kalli liti.
"Kamar Muryar wannan shegiyar yarinyar na jiyo a wayar,
duk Walid ne da wannan sheɗancin"
Ya cigaba da ƙurawa Liti ido, babu abun da yake fata, banda
ya zubar da hawaye ko na mintuna biyar ne, amma ko na sakan ɗaya ya kasa tsawon
shekarun nan.
Murya a sanyaye ya ce "Liti"
"Na'am mai zamani".
"Ina kewar jauhar sosai"
Walid da da yayi musu shiru, dan ya lura daga Viper har liti
haushin sa suke ji, amma maganar da Viper yayi yanzu ta sanya jikinsa ya yi
sanyi, tausayin Viper ya ƙara kama shi.
"Da yanzu yarona ya isa shiga makaranta, wataƙila ma ta
kuma haifa mini wasu"
Walid ya taso, ya dawo gaban Al'amin, ya riƙe hannunsa ya ce
"Ka ƙara haƙuri mai zamani".
"Zuwa yaushe? Ko na ɗauki fansa kamar yadda nake buri
da fata, kashe kaina zan yi saboda ba ni da wata makoma, idan kuwa hakan ba zai
samu ba, zan koma in da na fito na ƙarasa rayuwata".
"Dan Allah maza ka daina irin wannan maganganun, kana
karya mana zuciya wallahi " liti yayi maganar cikin damuwa.
Viper ya girgiza kai ya ce "Ba zaka gane ba"
Kawai ya gyara ya kwanta, gaba ɗaya suka kewaye shi suna
kallonsa.
Nabila kuwa kallon wayar ta cigaba da yi, ta ce "Allah
ya bani nasara a kanka, ya bani ikon taimaka maka".
Kira ne ya shigo wayarta, ta ɗaga ta saka a kunnenta, ta yi
sallama.
"Wa'alaikum Salam da 'yar ƙwalisa".
"Wa ke magana?"
Yayi murmushi ya ce "Bawan Allah ne"
"To, ai kowa ma bawan Allah ne, wanne daga ciki?"
Yayi gyaran murya ya ce "Wani case ne da ni, nake so a
taimaka mini"
Nabila ta yi hamma ta ce "Office zaka zo, ba ta waya
ba" ta katse kiran, dan a zatonta irin samarin nan, ne masu kiran wayar
mata anyhow, duk da Muryar wannan ba ta yaro ba ce.
Wani nannauyan bacci, yayi awon gaba da ita wanda babu abun
da take yi ban da mafarkin Viper, dan sai da ta kusa makara yau.
Kwanaki uku da zuwanta wurin su Viper, ba ta sake zuwa ba,
she's very busy, tana ta off and down na tattara hujjoji, duk da ana ta taɗiyeta,
duk in da za ta bi ta samo shaida, sai a rufe, sai da aka aike da dattijon nan
gidan kaso.
Gashi sai tayi ta sintiri a hanata ganinsa.
Kamar uba da ɗa haka Walid yake ta lallaɓa Viper ya ci
abinci, sai dai ya cakala ya bari, ba ya cin abinci.
Private numbrn nan da ake kiransa da ita ce, ta kira shi,
wayar tana ta ringing liti ya ce "Maza ka ɗaga mana"
"Me zan ce?"
Walid ya ce "Ko ba ka da abun cewa, ka ɗaga kawai"
Ganin ba shi da niyyar ɗagawar, ya sanya Walid ya ɗaga ya
sakata a hansfree.
"Aminu Viper, kwana biyu. Ashe ta dawo maka da wayar.
Alamu sun nuna kwana biyu ka yi sanyi, Kodayake kai sai an sakankance ka ke ɓarna.
Gargaɗi nake sake yi maka, ka nesanta yarinyar nan da ga gareka, za a iya cutar
da kai ta hanyarta".
"Ni nake da ikon yanke hukuncin abun da yake daidai da
rayuwata, babu wanda ya isa ya juya mini rayuwa yadda nake so, ka cigaba da ɓuya
ko ka bayyana kanka, zan yi abun da nake ganin shi ne dai-dai da rayuwata.
Mutumin yayi murmushi ya ce "Aminu Viper, shikenan idan
ka ƙi ji, ba zaka ƙi gani ba ai"
"Babu abun da ban gani ba, dan haka na shirya ganin
koma menene" ya katse wayar.
Liti ya ce "Duk walid ne ya janyo komai, ni na san a
rina, wannan yarinyar idonta kawai zaka kalla ka gane munafuka ce"
Kallon da Viper yayi masa ne, ya sanya shi yin shiru, Walid
yayi dariya ya ce "Ayi dai mu gani, za a gane waye mai gaskiya tsakanina
da ku".
Liti ya ce "Ba wata gaskiya da ka ke da ita, ka dakatar
da mu daga making moves, wallahi mun kusa fita operation kwanan nan"
"Ku fita yaƙi ma ba operation ba"
Haka liti da Walid suka kusa yin faɗa.
Tun ana gobe Nabila zata je wurin Naja'atu Bunkure, suke
waya da sumayya, take bata ƙwarin gwiwa, a kan za ta iya, kar ta ji tsoro.
Da safe sai da ta fara zuwa wurin aikinsu, ta samu barrister
Habib, shi ma ya ƙara mata ƙwarin gwiwa, da yi mata fatan alkhairi.
Cikin ƙasaita take fiya a farfajiyar office ɗin, har ta
ƙarasa, mutane ta tarar jingim. Wanda galibin su mata ne, suna jiran shiga
wurin Barrister Naja'atu Bunkure.
Kai tsaye Nabila ta shiga wurin sakatariyarta, ta nuna mata
ID card ɗin ta, nan da nan ta bawa Nabila wurin zama, na ciki na fitowa ta yi
mata iso zuwa wurin Barrister Naja'atu.
Tun a hanya take maimaita "la hula wala ƙuwwata illa
billa". Har ta shiga wurin Bunkure.
Tayi sallama, ba tare da ta ɗago ta kalli Nabila ba ta amsa
mata, ta ƙarasa ta zauna ba tare da an yi mata umarnin hakan ba.
Kayan jikin Nabila kawai ta kalla, ta fuskanci ba kalar
gajiyayyun da suke zuwa wurinta bane ba.
Ta gyara zaman gilashin fuskarta ta na kallon Nabila.
"Sannu da aiki ma" Nabila tayi maganar tana
murmushi.
"Yauwwa sannu"
Nabila ta ɗaga mata id card ɗin ta ta ce "I am
barrister Nabila Yusuf maitama"
Bunkure ta jinjina kai ta ce "You look familiar to
me"
Nabila ta jinjina kai ta ce "Na yi mamaki ma, da ki ka
iya tuna kamar kin sanni, saboda na san jama'ar ne da yawa. Ni abun da ki ka yi
mini ba zan taɓa mantawa ba har abada"
Bunkure ta ce "Ohh really"
"Yeah and i have a promise to fulfil, a dalilin abun da
ki ka yi mini"
Ta kashingiɗa da jikin kujerarta ta ce "That's very
good, ina son mutane masu yarda da kansu, ba na buƙatar sanin me nayi miki, ko
kuma wani alwashi ki ka yi ba, ga ki ga bunkure Allah ya ida nufi "
Nabila ta ce "Na ji daɗi da ki ka ce Allah, dan kuwa
shi ne gaba da komai, na gode sosai barrister"
"Mentioned not"
Nabila ta gyara zamanta ta ce "Yauwwa, ba komai ne ya
kawo ni ba, na zo ne a kan wani case, duk da ba mu haɗu a court ba, an kai
wanda nake depending prison, amma ban ganki a court ba sai wakilanki"
Bunkure ta ƙarewa Nabila kallo, sannan ta ce "Wane case
ki ke magana a kai?"
"Yarinya da aka yi wa fyaɗe, ki ka ce kin tsaya mata,
ni ce lawyer wanda ake ƙara, na je wurin 'yan sanda ana ta yi mini yawo da
hankali, ina son doctors report, kuma ina son zan ga yarinyar zan yi magana da
ita".
Naja ta yi wa Nabila kallon baki da hankali sannan ta ce
"Kin san a gaban wa ki ke?"
"I am barrister Nabila, ba ruwana da a gaban wa nake,
ina neman hujja ne da zan kare client ɗina"
"Nawa suka baki, ki ka samu ƙwarin gwiwar yin wannan
kasadar? Zan ninka miki, ki ajiye case ɗin, kafin ki kunyata a idon duniya
"
"Watch your words, it can be use against you a kotu,
kin san me nake nufi, you are also a lawyer"
"Who the hell are you?" Bunkure ta yi maganar tana
tashi tsaye, Nabila ma ta tashi tana sake ɗaga mata id card ɗin ta "Sai da
na fara gabatar miki da kaina, sannan na gaya miki meya kawo ni.
Ko dai ki bani abun da nake buƙata kawai, ko kuma na fasawa
duniya wacece ke?"
"Ni ɗin? Yaushe ki ka yi grduating, da me ki ke taƙama
ki ke jin karanki ya kai tsaikon da zaki tunkare ni kina gaya mini maganar da
ki ka ga dama?"
Nabila ta girgiza kai ta ce "Cikin dukkanin girmamawa
ta seniority a aiki, nake faɗar duk abin da nake magana a kai. You were my
mentor before, abun da ki ka yi mini ya tabattar mini you are green snake under
green grass. Keep your eyes open, Barrister bunkure, zan iya baki mamaki a
lokacin da baki zata ba. Zan cigaba da bibiyar case ɗin ramma, da ƙoƙarin wanke
wanda nake karewa har sai na yi exposing ainihin gaskiya ko da kuwa ita ce
ajalina" tun da ta yi face to face da ita, ta ji duk wata fargaba da tsoron
da take ji sun kau.
Ta ɗauki jakarta, ta fita daga office ɗin.
Tsaki Bunkure ta yi ta daki tebur, ta ɗauki wayarta, ta
danna ta kara a kunnenta.
"Yauwwa barrister Kabir ya kake?"
"Lafiya ƙalau manyan ƙasa ya aikin?"
"Normal ne, wacece Nabila a ma'aikatanka?"
Ya ce "Lafiya kuwa? Ya aka yi ki ka santa?
"Wacece ita, a id card ɗin ta na ga a wurinka take
aiki"
Ya ce "Barrister Nabila, a law firm ɗina
take".
"Ta zubawa kanta fetur a jiki, tana kuri, idan na
ƙyatta ashana, ba ita ba har kai, zaka ƙone ƙurmus ka ja mata kunne, ɓera ba ya
taka rawa a gaban mage, ko da kuwa tana kan gargara ne"
Kabir ya ce "Subhanallah, me ta yi?"
"Ka bincike ta, ba na bari ayi mini kuskure biyu, ko
yinƙurin yi aka yi, ina daƙile duk wani abu da zai kawo mini cikas".
Kabir ya ce "Na fahimta, ki yi haƙuri dan Allah zan yi
magana da ita, zan kuma ja mata kunne" ta ajiye wayar tana tsaki.
Cike da annashuwa ta fito daga wurin, tare da jin kanta
tamkar ta yi facing ɗin babban abun tsoronta.
Ta tsaya a gefen hanya, ta ciro wayarta, ta kira Viper, ya ɗaga
sai dai bai yi magana ba.
"Hello, ya jiki? Na san ba zaka yi magana ba, dama so
nake na ji ya jikinka, na so zuwa na ganka amma rana tayi sosai, zan je wani
wuri ne, ka kula da kanka sosai" ta katse wayar, ji yayi tamkar ya aikata
wani uban zunubi, ya din ga bin wayar da kallo, yana tunanin yarinyar nan tana
da hankali kuwa?.
Gida ta tafi cikin matsanancin farinciki, duk da ba su
kwasheta da daɗi ba ita da.
Gida ta tafi ta yi wanka, ta ɗauki wayarta ta kira sumayya,
amma line busy.
Ta ajiye wayar ta kwanta tana bacci.
***
Shiru shiru Abdul bai je kiran iyayensa ba, yana nan yana
fama da kansa, kuma ya hana duk abokansa zuwar masa gida.
Duk da Allah ya isa, da fatan mutuwa da ramma take yi masa,
hakan ba ya hanata tausaya masa, idan ciwon ciki ya murɗe shi, har mamaki take
yi da ya ce mata ulcer ce, dan ita ta ɗauka yunwa ce take kawo ulcer, yaran
masu kuɗi ba sa yi.
Da daddare yana kwance a kan gado, tana zaune a ƙasa tana
karanta wani novel na turanci, da ta ɗauka a falonsa, duk da ba wani ganewa
take yi ba, amma yana ɗebe mata kewa.
Tana ji aka kira shi a waya, ya ce yana zuwa, ya tashi ya
fita.
Bayan ya fita, ta ɗaukko pillow, ta ajiye a ƙasa ta cigaba
da karatunta.
Hamma da take ta yi ba ƙaƙƙautawa ne ya sanya ta gane bacci
take ji sosai, ta tashi za ta rufe ƙofar ɗakin, kasancewar ya bar key ɗin ta
ciki, dan ciwon cikin nan da yake yi, ta samu sassauci daga akuyancinsa.
Sai dai ta buɗe ƙofar falon ba ya nan, ta fito ta wuce
kitchen, ta daɗe a kitchen, ta zubawa fridge ido, komai akwai na morewa rayuw a
gidan, amma gaba ɗaya ba ta jin daɗinsu, saboda ƙazantacciyar rayuwar da take
ciki.
Ta sha ruwa mai sanyi, ta cika cikinta, ta fito falo,
sai dai abun da ta tarar ya sanya gabanta mummunan faɗuwa.
Cikin hanzari ya ture Nina daga jikinsa, ya yi tsilli-tsilli
da ido, yana kallon ramma.
"Abdul wacece wannan?"
"Amm maid ɗina ce, mai aikina ce".
"Kamar yaya, ina solomon ɗin, shi zaman me yake yi? Me
ka ke yi da mace a zaune a gidanka? Abdul kar ka raina mini hankali mana,
karuwa ka ajiye Abdul?"
"Kar ki sake ce mini karuwa, ni ba karuwa ba ce, ke ce
karuwa amma shi ki tambaye shi yadda aka yi na zo gidan nan?" Ta yi tsaki
za ta tafi.
"Abdul ka yi mini magana wace banzar ce wannan?"
Abdul ya miƙe ya ce "ya isa haka, ki je gida za mu yi
magana "
"Ban gane ba, ka gaya mini wacece wannan?"
Bayan ramma ya bi da sauri, Nina ta biyo shi, amma yana
shiga ɗakin, ya mayar da ƙofa ya rufe da key ta ciki.
Ramma tuni ta kwanta wani abu mai zafi ya tsaya mata a rai.
"Rahma, ki tashi mu yi magana dan Allah, zan yi miki
bayani" tayi masa shiru ta ƙi motsawa.
"Dan Allah ki tashi ki ji, zan yi miki bayani"
Ramma ta waiwayo sosai ta kalleshi ta ce "Ba ni zaka yi
wa bayani ba, Allah zaka yi wa bayanin abun da kake aikatawa ba tare da
tsoronsa ba. Ni baƙincikina, muzanta rayuwata da ka yi ne da wulaƙanta ni.
Ka yi zina da wasu, ko wankan janaba baka yi, ka zo ka kuma
afka mini, wannan wace irin rayuwa ce, Abdul yasar ka gama da rayuwata, wallahi
ko baka kashe ni, ina son kashe kaina na huta, dan dai kawai ina tunanin
makomata ne, amma ka cuceni wallahi" tayi maganar hawaye na ta gangarowa
ta gefen idonta.
Hannu ya sa yana share mata hawayen, amma ya kasa ce mata
komai.
Ya numfasa ya ce "Kina ji na?"
"Dalla ƙyale ni, ba abun da zan ji, ni ƙyanƙyamika ma
nake ji, mazinaci ƙazami mara tsoron Allah"
Duk da yadda maganganunta suka yi masa zafi, amma ya daure
ya ce "Dan Allah Rahma ki daina kirana da mazinaci, kalmar nan na yi mini
ciwo sosai. Wallahi tun a kanki ban sake zina ba, yanzu ba abun da ki ke tunani
ba"
Aikuwa kamar ya tunzura ta, ta tashi zaune ta ce "Ni
abun da ka ke yi mini menene? Na faɗa na kuma" ta sauka daga kan gadon
tana huci, cikin ɓacin rai.
***
Naja'atu kuwa tana zaune a bakin gado, tana ta haɗa ƙwayoyi
a cikin roba, ta na zuba ruwa a ciki, shiru ta yi tana tunanin maganganun da
Nabila ta gaya mata, mamakin ƙarfin halin yarinyar take yi, yadda ake shakkarta
da shakkar yin gaba da gaba da ita, ita wannan yarinyar zata yi wa cin mutunci
haka. Me take nufi da za tayi exposing ɗin ta. Ta daki teburin gabanta ta ce
"Wai ma wacece ita?" Ta yi wata ajiyar zuciya ta ɗaga kai, ta shanye
ƙwayoyin cikin robar nan da ta narka.
Nabila ce zaune tare da Nasir, tana bashi labarin yadda suka
yi da Naja'atu Bunkure, yake ƙara ja mata kunne, a kan ta bi sha'anin matar nan
a hankali, kar ta yi mata illa.
Tayi murmushi ta ce "In sha Allah ni zan karya
alkadarin matar nan"
Ya ce "To, Allah ya sa"
Ya amsa da "Amin, na ji an ce kin ce mota ki ke
so?"
Ta jinjina masa kai ta ce "Abba ya saya mini mota,kai
kuma ka din ga zuba mini mai" tayi maganar cikin shagwaɓa. Kasa amsa mata
yayi, sai bin ta da kallo da yake yi, yana murmushi.
Ta ce "DSP ya ake ciki ne, da zancen binciken
viper?"
Ya numfasa ya ce "Ina ta cigaba da bincike, gashi ana
cigaba da matsa mini a kan kama shi, abubuwan ma na rasa yadda zan yi, duk
shaidar da na kama sai ta zille, ace in sake shi, na rasa wannan wane irin abu
ne. Amma dai an kwatanta mini wani yaro, dealer ne na wiwi, wai shi ɗan mama,
idan na kama shi, ba zan bari a san na kama shi ba, sai na dangana da kama
Viper in sha Allah" gabanta yayi mummunan faɗuwa ta ce "To wai suwaye
suke sakawa a saki shaidun naka?"
Ya ce "Ban sani ba, daga sama kawai ake cewa na sake
su".
Ta jinjina kai ta ce "Kuma anya ba su san in da yake
ba, raina maka hankali kawai suke yi ba?"
DSP ya ce "To ko ma dai menene, zan ɓoye bincikena, sai
na dangana da kama shi, na danƙa musu shi, su san yadda za su yi da shi. Ina
nan mun samu bayanan lokutan da yake zuwa an tabattar mana da idan muka kama
shi, zamu iya kama Viper "
Kamar an mintsine ta ta miƙe, ta ce "Bari na koma ɗaki,
zan yi wani uzuri" har da gudu ta haɗa, ta tafi ɗakinta, ta ɗauki wayarta
ta din ga kiran Viper, amma yaƙi ɗagawa, tayi masa missed calls sun fi goma,
amma ko ɗaya ya ƙi ɗagawa, ga yamma ta yi sosai, idan ta fita kan ta dawo
magariba zata iya yi.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Kamar Nabila za ta yi hauka, tana kallon kiran Barrister
Kabir yana shigowa wayarta, amma ta share, taƙi ɗagawa, ƙarshe ma rejecting
kiran na sa ta din ga yi, taƙi ɗagawa babban burinta kawai Viper ya ɗaga
wayarta, amma yaƙi ɗagawa.
Kwana tayi cikin zullumi, da addu'a kar Allah ya bawa Nasir
nasarar kama Ɗan mama, dan a labarin Viper ba ta ji yadda aka same shi ba,
balle ta san ingancin kasancewar sa tare da shi, tare da tabbacin ba zai faɗi
in da Viper yake ba, kodayeke ta san ba zasu taɓa janyo wanda zai cutar da su
ba.
***
Abdul ne zaune a gaban Indabo, sai zazzaga masa faɗa yake
yi, ya haɗe rai yana ta muzurai.
"Ina magana kana shan kunu, Abdul ko ka ƙi, ko ka so
dole ka yi aure, idan ba haka ba, babu yadda za ayi a ɗauki takara a baka, na
gaya maka dan ba zaka yi mini asarar wahalar da na yi shekaru ina yi ba, dole
ka je ka gano yarinyar party chairman ku daidaita, ko baka santa ayi, idan ya
so daga baya sai ka auro wadda ka ke so"
Cikin damuwa ya ce "Daddy, ya za ayi ace na auri wadda
ba na so, ni tun ban ganta ba, ba na sonta wallahi, a bar ni zan kawo wadda
nake so ɗin"
Indabo ya ce "Inaa lokaci kuma ya ƙure maka, arranged
marriage ɗin nan, duk cikin manufa ce irin ta siyasa, dan haka dole ka yi
haƙuri, ka je ku daidaita" Abdul ya yi shiru bai ce komai ba.
Indabo ya ɗora da cewa "Sannan za'a fara haɗa
structures a kowacce mazaɓa, tun yanzu za ku fara campaign kafin ƙaddamar da
takararku" Indabo har ya gama maganganun sa, Abdul bai saki fuska ba, yayi
ya gama ya tashi ya bar office ɗin.
Yana fita P.A ya shigo, ya ce "Distinguish yaya dai
nake jiyo muryarka tun daga waje?"
Indabo yayi tsaki ya ce "Abdul mana, gaba ɗaya yaron
nan ba shi da hankali, wai shi ba zai yi aure yanzu ba, so yake yayi mini
asarar wannan uwar wahalar da na sha muka kawo wannan matakin"
P.A yayi murmushi ya ce "Rabu da shi, mu cigaba da
dukkan shirye-shirye da suka dace, kuma a cigaba da bin malamai, dan Abdul
akwai taurin kai, a kan auren nan zai iya fasa takarar amma a cigaba da
matsawa".
Imdabo yayi tsaki ya ce "Yaya ake ciki? Ya batun
yarinyar nan?"
"Mu na nan muna bibiyarta, sai dai bakin zaren gano in
da Viper yake ne aiki, balle ayi masa tarkon da ita. A binciken da nake yi, shi
wannan ɗan sandan ya kama liti, kwanansa kusan huɗu a hannunsa, aka ce lallai
ya sake shi"
Indabo cikin damuwa ya ce "Waye ya ce a sake shi ɗin?"
P.A ya girgiza kai ya ce "Ban sani ba, haryanzu babu
trace na wanda yake taimaka masa, kuma Viper yana nan a cikin garin nan yana
yawonsa, sai dai gaskiya ƙarƙashin kulawar wani yake duk abin da yake yi "
"Kaii wai wannan wane irin abu ne? Hankalina kullum a
tashe yake, ban san ta ina zai ɓullo mini ya ce zai ɗauki fansa ba, ka san ba
zai taɓa barina ba, shi ma wancan banzan da duk laifinsa ne, ya kasa komai ya
kasa kamo shi ya kasa gano in da yake, duk shi ya ɓata lamarin, da bai tabattar
da Viper ya mutu ba tun a wancan lokacin, ina cikin tashin hankali".
"Ka kwantar da hankalinka distinguish, Viper fa zai zo
hannu, ko da me yake yawo, ka yi haƙuri in Allah ya yarda babu abun da zai faru
sai alkhairi" yayi ajiyar zuciya ba dan ya gamsu da maganganun P.A ba.
***
Daga wurin Indabo Abdul gidansa ya wuce, ya tarar da Ramma
na ta uban bacci, motsinsa a ɗakin ne ya saka ta farka, ya kalleta ya ce
"Baccin nan ba ya isarki ne?" Ta ɗaga masa gira alamar eh.
"Ko ki na da ciki ne?"
"Allah ya kiyaye, ya tsari mahaifata da ƙara ɗaukar
ƙazantarka"
Ya ce "Hmm, ki bari cika baki, ki bari ayi gwaji
tukuna"
Ramma ta ce "Ba abun da za a gwada"
Lambar saif ya kira, ya ɗaga ya ce "Yeah"
"Saif daddy ya ɓallo ruwa fa"
Saif ya ce "Zancen auren dai?"
"Shi fa, wai wata 'yar party chairman, ni tun ban ganta
ba, ba na sonta wallahi dan kawai zan yi takara, sai na auri wata wadda ba na
so, ya dage ya dage, kamar na gudu wallahi".
"Kai fa ka fiye gaggawa, ka bi su a sannu tukuna, ka je
ka ga yarinyar "
Abdul ya ce "Ba ma wannan ba, Nina ta ga yarinyar nan a
gidan nan, tana ta yi mini hauka, ga maganar auren nan idan ta ji, ban san
haukan da za ta yi ba, ni gaba ɗaya na rasa abun yi ma".
Saif ya ce "Lallai ma Abdul, ba ka mayar musu da
yarinya ba, kai baka kasheta ba, ka bar ta to yaya zaka yi da ita?".
"Mu haɗu in anjima a joint kawai"
Saif ya ce "Shikenan, Allah ya kaimu anjiman" yana
kashe wayar ramma ta kalleshi ta ce "Bariki babu riba, dama duk wata hanya
idan ba ta Allah, ai ba mai ɓullewa ba ce ba your excellency, na ga ku duniyar
kawai ku ka saka a gaba, lahira kuma kun bar mana mu talakawa mu nema. Allah ya
bamu a can.
Ni dai in an tashi, a taimakawa 'yan garinmu da hanya, a
gyara mana babban asibitin garinmu, sai kuma makarantunmu, dan Allah kar a
manta da mu"
Yayi murmushi ya ce "Ki na yi mini rashin kunyar za ayi
abun da ki ke so?"
"To ba ma so, dama kuɗin haram bana halal ba" bai
ji haushi ba, ya kwanta a jikinta, yana kashe mata murya, yana kiran sunanta.
"Rahmaaaa" ture shi tayi a fusace ta ce
"Ni ka daina yi mini wannan abun 'yan iskan ba na so"
"Her excellency rahammaaa" yayi maganar kamar mai
shirin yin shagwaɓa.
Wani uban takaici ya cika mata zuciya, ta kasa ture shi, sai
ma cakulkuli da ya fara yi mata, ta dunƙule hannunta tana kai masa duka, amma
ko a jikinsa, dariya ma yake yi, abun nata gwanin ban dariya.
***
Tun da aka idar da sallar asuba, Nabila ba ta koma bacci ba,
ta shirya, gari na yin haske, ta ɗauki jakarta ta fice daga gidan, fuskarta
sanye da niƙabi.
A hanya gari ya ƙarasa waye mata, ta tafi gidan su Viper.
Duk da akwai tafiyar ƙafa sosai, daga titi zuwa gidan, amma
yanzu idan tayi bulayin, tana iya gano gidan. Kasancewar wurin da nisa, gari
yayi haske sosai ta isa gidan.
Ta tarar da su suna ta shirin ɗora karin kumallo.
Walid ya kalleta da mamaki ya ce "Lafiya?"
Ɗan mama ya ce "Mun shiga uku, wannan akwai mayya
wallahi, idan ba kama mu aka yi ba, hankalinta ba zai kwanta ba".
Liti ya miƙe a fusace, ya ɗauki wuƙa a kan taga, ya ce
"Ke ware dan kazakazanki, ko shi bai kashe ki ba sai na kashe ki ni,
jarababbiya kai, uban me ki ke nema a wurinmu? Ke bayan haushinki da nake ji,
har da wannan banzan saurayin naki ɗan sanda da ya din ga azabtar da ni, sai na
yi masa ido ɗaya, ba zai bar aikin ɗan sanda ba sai da tabona".
Walid ya ce "Meya dawo da ke kuma? Me ki ke nema?"
Ta ce "Viper"
"Me zai yi miki?"
"Ina son ganinsa ne"
"Yana cikin yanayi mara daɗi, ki yi haƙuri ki tafi
kawai, ba zaki ji daɗin abun da zaki gani ba"
Nabila ta ce "Komai munin abun zan gani, zan jure"
"Kin ga, ba mutuncinki bane ba, kina 'ya mace, ki dinga
sintiri a gidan nan, wurin mutane irinmu ma, yakamata ki daina zuwa"
"Zan daina, idan na samu abun da nake so, ka ƙarasa
mini labarin jauhar, ni lawyer ce, ina son ya ɗauki fansa ta hanyar da ta dace
ne, kuma niyyar da nake da ita ta alkhairi ce, dan haka na san ba zaku cutar da
ni ba" tayi maganar tana nuna wa Walid id card ɗin ta.
Walid ya ce "Na san ke lawyer ce"
Cikin mamaki ta ce "Ta yaya?"
"A ina na saka aka ɗaukko mini ke?" Sai kuma tayi
shiru tana kallonsa.
"Baki isa na bari ki raɓi Viper ba, muddin ban san
wacce ke ba. Hatta gidanku na sani".
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Nayi mamaki, dama jiya na
kira Viper ya ƙi ɗagawa, wanda ya kama ka, ba saurayina bane ba, yayana ne.
Kuma da shi nake taimakawa a kan neman Viper, yanzu haka ya tabbatar mini da yi
wa wani ɗan mama tarko, ya ce idan ya kama shi, an ce zai samu Viper, sai dai
ban san waye ɗan maman a cikinku ba"
Walid ya ce "Wani tabbaci muke da shi, ba zaki cutar da
mu ba, ko ki ci amanar mu ba, duba da yadda ki ke zambatar ɗan uwanki cikin
aminci"
Nabila ta jinjina kai ta ce "Haka ne, ni zan tsaya a
tsakiya ne, na bi ɓangaren gaskiya, and no matter what, ina da ikon tsayawa duk
wanda nake ra'ayin tsayawa. Amma dan Allah ku bari na ganshi na yi magana da
shi.
Walid ya ce "To"
Liti ya ce "Ni fa ban yadda da yarinyar nan ba mai
laya, ya ya za ayi ta ci amanar ɗan uwanta kuma, ta ce tana tare da mu?"
Walid bai kula shi ba, ya buɗe mata ɗakin da Viper yake
ciki, yana zaune daga shi sai gajeren wando, ko riga babu a jikinsa.
Jiki a sanyaye ya ce "Maganar da ki ka faɗa gaskiya ce,
ƙwaƙwalwar viper ta fara samun matsala, a dalilin damuwa da ta'amalli da
miyagun ƙwayoyi, yana buƙatar ganin likita, amma tayaya? Ina tsoron mu fita da
shi a samu matsala".
Duk ganin ƙirarsa ta razanata, yana zaune, daga zaunen ma
maye kawai yake yi, ga uban karan taba guntu-guntu a wurin.
Kawai ta shiga ɗakin ta nufe shi kai tsaye.
Walid ya ce "Ki daina gangancin tunkararsa yadda ki ka
ga dama, ba ya cikin hayyacinsa fa"
Nabila ba ta saurare shi ba, ta je gaban Viper ta durƙusa,
ya ɗago ya kalleta ya ce "Ban ce ki daina zuwa ba?"
"Ba zan iya ba ne, na fara jin abun da 'yar madara take
ji, idan ta ganka a yanayi mara daɗi, yaya za ta ji idan ta tsinceka a yanayin
da ya fi na baya muni?" Ya zuba wa Nabila ido, wanda hakan ya tilasta mata
kawar da kanta daga kallonsa.
Ta cigaba da cewa "Yakamata ka ƙarasa mini labarin
jauhar, kar na je na sakankance, ta dawo ta ƙwace mijinta, dan a labarinta na
ga daga tausayi soyayya ta ƙullu, kuma nima dai gashi ba na son shaye-shayen
nan, kar na je sai na yi nisa ta ƙwace mini kai, tana ina ne yanzu?" Tayi
maganar tana jiran amsar da zai ba ta.
Ya ƙura mata ido, har sai da gabanta ya faɗi, ta fara
tunanin ko shaƙetan zai yi.
Amma ya jingina da bango yana lumshe ido.
"Talk mana" tayi maganar da sigar rarrashi.
Su liti duk suna window suna ganin ikon Allah, su ihu yake
ta yi musu, yana kiran matarsa, amma yanzu ya nutsu, ko hargowar bai yi mata
ba.
"Na ga haryanzu baka gama dawowa dai-dai ba, bari na je
zan dawo, sai mu yi magana ka din ga ɗaga wayata amma, sunana Nabila Yusuf
maitama. Amma babanmu arfa yake ce mini, ranar arfa aka haife ni, shiyasa nake
da sa'a sosai kuma yana son mamana sosai da sosai, kamar dai yadda ka ke son
'yar madara. Amma dan Allah ka gaya mini da wuri tana ina, kar in zo daga baya,
ka ce baka san zance ba baka sanni ba". Tayi masa maganar cikin sigar
shagwaɓa.
Yayi shiru, ko tari bai yi ba.
Har ta gama surutanta, bai yi magana ba, ta tashi a hankali
ta fito, ta kalli Walid ta ce "Zan je gidan masu rangwamen hankali, na yi
magana sa likitocin ƙwaƙwalwa, idan ta kama dole ayi arranging yadda zai ga
likita, ina matuƙar buƙatar hankalinsa, kafin komai ya yiwu, sannan ku rage
zirga-zirga an matsawa yayana lamba a kan kama shi, kuma ya dage by any means
sai ya kama shi".
Walid ya ce "Shikenan, mun gode da gudunmawarki, sai
anjima" ya jinjina kai ta fice ta tafi.
Suka sake leƙa Al'amin, ya kwanta a wurin, yayi ruf da ciki,
wanda tun bayan sallar asuba suke fama da shi, sai ya fita ya kashe madaki da
Indabo, da ƙyar suka rufe shi a ɗaki, da kokowa, dan kuwa sun sha wahala, duk
da su uku ne, shikaɗai neman gagararsu yayi, amma da Nabila ta zo tana yi masa
magana bai yi wannan hargagin ba.
Sai kusan sha biyu saura ta isa wurin aikinsu, mai yi musu
goge-goge ne ya sanar da ita, Barrister kabir yana ta nemanta, ta ce masa to,
sai da ta shiga office ɗin ta, ta dafa tea a dispenser tana da biscuit a office
ɗin ta, ta haɗa ta karya.
Sai da ta kammala, sannan ta tafi office ɗin Barrister
kabir, yana ta shiri zai fita yana da wani meeting, duk yadda yake yi mata
wasa, idan suka haɗu yau sai ya sha kunu ya ɗaure fuska tamau.
"Sir an ce kana nemana?"
A ƙule ya ce "Au an ce nema? Tun jiya nake kiran
wayarki, baki ɗaga ba, baki biyo ba ki ji dalilin kiran"
Cikin ko in kula ta ce "Sir ban taɓa yin hakan ba,
yakamata ayi mini afuwa ayi mini uzuri"
"Shut up, ba zaki janyo mana magana ba, kin san wacece
matar nan kuwa?"
"But sir, this is my personal trial, ba under law firm ɗin
nan zan yi shari'ar nan ba".
"Ina magana kina magana? Amma da ID card ɗinmu ki ke
amfani ko? You better watch what you are doing, faɗa da matar nan tamkar faɗa
da manyan mutanen nan ne, dan su take yi wa aiki"
Barrister Habib ne ya ƙaraso, yana faɗin "Subhanallah,
lafiya kuwa meyake faruwa?"
Barrister kabir ya ce "Ka san yarinyar nan office ɗin
Naja'atu Bunkure ta je neman magana, wai tayi mata bayanin wani case da yake
hannunta, ina ruwan Nabila da Bunkure?" Idanun Nabila ya cika da hawaye,
tamkar ta fashe da kuka, kowa ya santa da barrister Kabir, suna good time
sosai, amma yau yayi mata ihu a gaban mutane.
Barrister Habib ya ce "Barrister Nabila, garin yaya,
meyasa ba kya shawara waye ya aike ki? Kin san wacece Bunkure kuwa? Gaskiya kin
yi wauta, mu je in ji ya aka yi, barrister yau da kai da daughter taka mu ganku
a rana, amma ayi mana afuwa, ka san yanzu nine abun koyinta, mun shirya tana
son aiki tana ƙoƙari. Ayi mata afuwa".
Kabir ya girgiza kabir ya ce "Rigimarta tayi yawa"
"Ayi haƙuri ke kuma wuce mu je" Barrister Habib ya
sakata a gaba, suna zuwa Office ɗin sa, ta fashe da kuka.
Ya ce "Ahhh ya haka? Kuka kuma karaya tun yanzu?"
Cikin kuka ta ce "Kana ganin abun da yayi mini, ita
wacece Naja'atun ba mutum ba ce ba? She's just my senior kuma ni ba rashin
kunya na yi mata ba, ajiye masa aikinsa zan yi nayi zaman kaina"
Barrister Habib ya yi dariya ya ce "Kin bani kunya,
waye ya ce miki ana gwagwarmaya babu ƙalubale ne? Dole ki shiryawa ƙalubale,
and ki bar maganar resigning ɗin nan ba mafita ba ce ba. Yanzu yaya ku ka yi da
ita?"
Cikin tura baki ta ce "Ni sai na bar wurin nan"
"Kar ki ga laifinsa, maybe kiransa aka yi, aka ja masa
kunne, dan haka ki yi masa uzuri ai bai taɓa yi miki haka ba ai, haba 'yar
ƙwalisa".
Ta zumɓura baki, tana goge hawayenta.
"Yanzu yaya ku ka yi da ita?"
Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Nothing much, alamu
sun nuna babu gaskiya a lamarin nata, dan idan tana da gaskiya, zata gaya mini
aka tsaya a lamarin yarinyar, amma ta kore ni, ta ɓuge da kiran sa.
Sai dai an hana ni ganin shi wanda nake karewar ma, amma dai
ya kwatanta mini gidan ɗaya mai aikin, na je an ce ta tashi ta koma garinsu.
Amma ya tabattar mini da yarinyar 'yar tofa ce, wai wani gari yaloko, amma bai
san ina ba a tofa. Ni ban san ina ne ma tofan ba, balle na nemi gidan su
yarinyar".
Barrister Habib ya yi shiru sannan ya ce "Kin tabattar
a tofan ya ce miki take? A yalokon?"
Ta jinjina masa kai alamar eh.
"To shikenan, ki bani kwanaki i will get back to you.
Amma ki daina garaje, ki din ga bin komai a hankali"
Ta ce "To" ya din ga rarrashinta, har ta huce, ta
tashi ta koma office ɗin ta".
***
Tun da Abdul ya dawo, yake cika yana batsewa, ramma ko kallo
bai isheta ba, ta cigaba da sabgoginta, ko abinci bai ci ba, ya nemi wuri ya
kwanta.
Haushi ya ishe shi, gaba ɗaya ba ta tasa take yi ba, karatun
littafinta ne kawai a gabanta, babu tsammani ta ji ya fizge littafin hannunta.
Ta kalleshi ta ce "Lafiya?"
"Wai ke wace iri ce ne?"
Ta kalleshi ta ce "Kamar yaya?"
"Ke baki damu da ki ga mutum cikin damuwa ba, ki
tambayi meyafaru ba?"
Ramma ta ce "To ina ruwana da abun da ya dameka? Ni
banda damuwar da ka saka ni a ciki? Bani littafina malam".
Abdul ya ƙura mata ido, ta tashi zaune ta miƙa masa hannu ta
ce "Bani dan Allah".
"Me ki ke ganewa a ciki ne?"
Ramma ta ce "Ko ba na ganewa, ai gara na karanta
littafin, da kallon fuskarka ma, bani littafina malam" ta yi maganar tana
haɗe rai.
Wayarsa da take vibrating ya ciro, ya saka a kunnensa.
"Yau Yakamata ka shigo Asibiti, yau zaka yi wa patient ɗin
ka tiyata fa"
Ya ɓata fuska ya ce "Yau ne amma baku tuna mini ba, ni
na manta gaba ɗaya".
"An yi booking ɗin su, da wanda za su ganka, kusan wata
biyu suna jira, ba su samu ganinka ba"
"Zan kira Doctor Anas,ya je yayi am sick, ba zan iya
tiyata ba"
"Amma doctor... Cikin hargowa ya ce "Shut up, abun
da na ce za ayi"
"To shikenan" ya ajiye wayar, ramma ta ce
"Dama kai likita ne?"
"Ban sani ba, sai yanzu ki ga damar kula ni, saboda
baki da imani, ki na kallo ko abinci na kasa ci".
"Kar Allah ya sa ka ci mana, kai har ka na bakin cewa
wani bashi da imani Abdul yasar? Hala tsabar imanin ne ya sa kazo ka yi mini
kurkuku a nan?"
"Ke fa taimakonki nayi, haka ki ka zo kalli yadda ki ka
yi ƙiba, ki ka yi kyau, sai ma mun ci gwamnati, zaki fi haka ƙiba" yayi
maganar yana taɓa damtsenta.
"Ni meye nawa idan ma kun ci gwamantin, in sha Allah ma
ba zaku ci ba, ace a rasa wanda za su jagoranci al'umma, sai mutanen banza masu
lalata yaran mutane " ya ce "Ok, Ai ba a wurinki muke nema ba"
"In sha Allah ba zaka ci ba, ko ƙuri'a ɗaya ba zaka
samu ba"
Abdul ya ce "Ke ki ka sani, na je na ga yarinyar da aka
ce zan aura, kyakykyawa nutsatiyya, tabbatar Allah ba ya karɓar addu'arki"
Da sauri ramma ta kalleshi ta ce "Nutsatiyya, ai ba
zaka taɓa auren macen kirki ba, sai wadda wani ya lalata kamar yadda ka yi. Ai
ko ka ganta a nutse ma, in sha Allah irinka ce zaka aura. Ba zan yi fatan Allah
ya baka lalatacciyar 'ya ba, dan ba ita tayi mini ba, amma in sha Allah sai ka
auri lalatacciya" tayi maganar tana hawaye.
Abdul ya ce "A'a gaskiya ba lalatacciya kamar ke ba,
Nutsatiyya ce sosai, idan na aureta kar ki damu, ba zamu rabu ba, ai ana mugun
tare tun da kin zama 'yar hannu kema.
Ta ce "Kai da Allah, kuma in sha Allah sauran wani zaka
aura"
Abdul ya ce "Nima saurana wani zai aura, balle ba zamu
iya rabuwa da juna ba, mun riga mun saba, ni zan iya aure, amma ke ba zaki iya
ba, kawai mu cigaba da rayuwarmu a haka rahma".
Hawaye wani na bin wani ta ce "In sha Allah, sai Allah
ya kuɓutar da ni daga hannunka azzalumi kawai" Abdul tamkar jin daɗin
tsinuwar da ramma take yi masa yake ji, ta zage shi tayi masa Allah ya isa,
amma hakan ko a jikinsa, sai ma cigaba da tunzurata da yake yi ya ce "Ohhh
kishi a fili, ki dai yi a hankali, kar ki yi zurfi a soyayyata, 'yan mata ne da
ni burjik"
"Eh tun da ga ka bunsuru ba" ta tashi tsaye tana
kuka.
Ya ƙyaƙyace da dariya ya ce "Bunsuru ya ajiye akuya ta
mussaman a gidansa ba" kalmar akuyar tayi mata ciwo, kawai ta fita daga ɗakin
ta bar shi, yana ƙyaƙyata dariya.
***
Indabo yana ta shiri zai koma Abuja, hutunsu na majalissa ya
ƙare, ga shirye-shiryen da ake yi na fara zaɓen fidda gwani, wanda yake ta
fafutuka a tabattar da yarjejeniyar da suka yi na ba wa Abdul takarar
mataimakin gwamna. Sai dai sai fama yake da shi, idan yayi nan sai yayi can.
Naja'atu Bunkure ce ta kira shi a waya, ta ce masa tana
office ɗin sa na gidansa, tana son ganinsa.
Ya san muddin ta yi masa zuwan gaggawa ba bu sanarwa, akwai
damuwa ne, dan haka ya ajiye abun da yake yi, ya fita.
Ya shiga ya zauna yana faɗin "Naja'atu masu ƙasa ya ake
ciki ne?"
Ta kalleshi ta ce "Ina Abdul?"
"Oho masa, yana can tasa shiririta ya tattara ya koma
gidansa da zama"
"Akwai ƙura fa"
Indabo ya ce "Wace irin ƙura kuma?"
"Yaya yayi da yarinyar da ya yi wa fyaɗe?"
Indabo ya ce "Mun yi magana da shi, ya ce mini ya
kasheta"
"Ka tabattar da hakan kuma? Akwai matsala fa. Wata
shegiyar yarinya ta zo office ɗina, wai na bata bayanan in da aka tsaya da
maganar yarinyar, wai zata tsayawa mai gadin nan, hankalina ya kasa kwanciya
jikina yana bani, ba itakaɗai take wannan abun ba, akwai abun da ta taka, duk
da na kira law firm ɗin su na yi musu warning, amma jikina yana bani akwai wata
a ƙasa, kar ta zurafafa ta gano wani abu, dan yarinyar a tsaye take babu alamar
kunya a tare da ita".
Indabo ya ce "Kin daɗe kina magance matsaloli da
rigingimun da Abdul yake ɗaukkowa, amma ya aka yi na ga karaya a tare da ke
yau?"
"Ba karaya nayi ba, ka san hausawa sun ce, rana dubu ta
ɓarawo, ɗaya tak ta mai kaya, na so ƙarasa aikin da kaina, amma ka ce na bari
zai yi maganin abun, ka nemo ɗanka ka tabattar da bai bar wani trace ba, gobe
in Allah ya kaimu zan tafi conference ɗin da shugaban ƙasa ya tura mu, dan haka
ba zan samu damar zuwa gidan su yarinyar ba, dan haka ka nemo shi"
Indabo ya ce "Naja'atu, idan aka samu matsala the blame
will be on you, sakacinki ne"
Naja ta girgiza kai ta ce "Sakacinku dai, na yi iya yi
na ni, yadda ku ka yi da shi, ka sanar da ni"
Indabo cikin hanzari, ya ɗauki wayarsa yana kiran Abdul, sai
dai wayar taƙi shiga gaba ɗaya.
Nabila har wata ramar dole tayi, saboda zirga-zirga, gashi
kwana biyu ba ta je wurin Viper ba, gashi tana cikin damuwa da tsananin son
ganinsa.
Gaba ɗaya yanzu ba ta doguwar shawara, kafin ta tafi gidan
Viper, yau ma haka babu tsammani sai ganinta suka yi rana tsaka.
Duk suka bi ta da kallo, ta kalli Walid ta ce "Ina
wuni"
"Lafiya ƙalau"
"Ya mutumina, ina fatan yana lafiya?"
Walid ya ce "To da sauƙi dai, yana ciki"
Liti ya ce "Wallahi ba zata shiga ba, ke ware, ni fa
ban yarda da yarinyar nan ba".
Nabila ta kalli liti ta ce "Ka kiyaye ni fa, ba ruwanka
da ni, ba wurinka na zo ba, wurin Viper na zo, zan duba lafiyar sa kuma mu yi
magana"
Walid ya ce "Dan Allah liti ka daina haka, mana wai me
ta yi maka ne, ta bayar da haƙurin abun da tayi ai"
Liti ya ce "Ni fa ba a iya yaudarata cikin sauƙi, fita
malama, ba zaki ganshi ba"
"Ba zan tafi ba sai na ganshi, ba ruwanka da ni".
Ya zazzaro mata ido zai yi magana, ya ji an hankaɗe shi daga
bakin ƙofa, Viper ya fito yana ƙanƙance idanunsa.
Suna haɗa ido, ta sakar masa murmushi, mai cike da nuna
farincikin ganinsa, duk kallon na sa tsoro yake bata.
Liti ya ce "Mai zamani mai hakan yake nufi? Kai ma ka
yarda da wannan munafukar, ita fa ta saka aka kama maka ni, aka rufe ni so take
sai an kama ka fa".
Walid ya ce "Kai ɗin uwar me ka ke tsinana masa?"
Duk bai kula su ba, ya taka ya fito ya ɗauki brush da
toothpaste, ya matsa.
"Ina kwana" tayi maganar tana bin bayansa. Bai
amsa ba, ya durƙusa yana wanke bakinsa.
Wayarta da take ta vibrating ta ciro, ta saka a kunnenta ta
ce "Hello"
"Ke Sumayya ce"
"Ohh sumy, kullum cikin sauya lamba kamar 'yar
yahoo?"
"Malama kwana nawa ina nemanki a waya ban same ki ba,
kuma baki neme ni ba"
Nabila ta ce "Sorry na yi laifi"
Sumayya ta ce "Yaya ku ka yi da Naja'atu baki gaya mini
ba"
Nabila ta ce "Ke zan zo gida na baki labari, ina wani
abun ne yanzu, dan na kusa rubuta resigning na ajiye musu tsiyar su, na
fuskanci Naja'atu Bunkure gaba da gaba, naga gani take ita wata jan wuya ce, ko
ban kaita ƙasa ba sai na razanata" gaba ɗaya suka zuba wa Nabila ido,
cikin hanzari Viper ya ɗago ya zubawa Nabila ido, ta katse wayar ta ce
"Meyafaru ku ke kallona ne?"
"Naja'atu Bunkure" ya maimaita yana kallon idon
Nabila.
Cikin rawar baki, saboda tsorata da kallon da yake yi mata
ta ce "Ka santa ne?"
"Mu je waje mu yi magana"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Jikinta ne ya hau tsuma, saboda irin kallon da yake yi mata,
yayi gaba da nufin ta bi bayan shi, amma ta ƙi, ya tsaya ya waiwayo yana
kallonta, ta kalli Walid, ya gyaɗa mata kai alamar ta bi shi.
Kamar mara gaskiya haka ta bi bayansa, sai da suka ɗan yi
nesa da gidan kaɗan, sannan ya waiwayo ya kalleta ya ce "Me ki ke nema a
wurina?"
Ta kalleshi ta sunkuyar da kai. "Ki yi mini magana, me
ki ke nema a wurina? Meyasa ki ke sintirin zuwa in da nake? Idan so ki ke a
kama ni, ki kawo su su kama ni mana, wace irin yarinya ce ke ne?"
Yadda yake maganar cikin hargowa, sai da ta ja da baya,
saboda tsoro.
"Talk! Me ki ke so, waye ya turo ki?"
"Ni ba wanda ya turo ni" ta yi maganar cike da
tsoro.
"Me ki ke nema?"
A sangarce ta ce "Ni ka daina yi mini magana a haka,
tsorata ni ka ke yi, ni ban san me zan ce maka ba"ta yi maganar tana kawar
da kanta gefe.
Ya tsareta da idanunsa, ita kuma taƙi ɗagowa, ta sunkuyar da
kanta ƙasa tana haɗe fuska cikin tsoro.
Ya sunkuyo dai-dai tsawon ta ya ce "Ki bani amsa"
tayi shiru ta ƙi magana.
Hakan ya ƙara hasala shi, ya buga ƙafarsa ya ce "Ki yi
magana kan na saka ki yi ta ƙarfin tsiya"
Cikin rauni ta ce "Na gaya maka, ni babu wanda ya turo
ni, ni na turo kaina, kuma ni tsoro ka ke bani ban san ta ina zan fara ba,
tsorata ni ka ke yi"
Ba ta ƙarasa maganar cikin nutsuwa ba, ta ji hannunsa a
wuyanta. "Naja'atu Bunkure, meye alaƙarki da ita? Ita ki ke yi wa aiki a
kaina, da ita da Indabo ko?" Ba ta yi masa magana ba, sai idanuwanta da
suka yo waje, ga hawaye na bin fuskarta, sai dai kallon da ta yi masa, ya sanya
ƙirjinsa bugawa da ƙarfi, ya saketa ya ja da baya, yana dafe saitin zuciyarsa.
Dai-dai lokacin Walid ya ƙaraso ya ce "Viper meyasa ka
ke haka ne? Ban sanka da cin zarafin mata ba, meyasa ka ke ƙoƙarin farawa
yanzu?" Ya nuna Nabila da yatsansa, amma ya kasa magana sai haki yake yi,
saboda zuciyarsa ta ƙi nutsuwa. Ta ƙura masa ido, tana kuka.
Kawai ya juya ya bar wurin, Walid ya ce "Sannu, kin ga
abun da nake guje miki a kansa ko? Shiyasa na ce ki daina zuwa anyhow. Mun gode
da gudunmawarki ga ɗan uwanmu, amma ki daina zuwan nan, ina tsoron yayi miki
illa wataran".
Ta girgiza kai ta share hawayenta ta ce "Ina da kafiya
wasu lokutan, haryanzu ban ji cewar zan karaya ba, da ya bi ni a sannu, da zan
yi masa bayanin abun da ya haɗa ni da Naja'atu Bunkure. Kawai ji nake ya zame
mini wajibi na taimake shi, ina son sanin ƙarshen labarinsa, har cikin zuciyata
nake son ba shi gudunmawa, na yi masa uzuri, wataran ba zai yi mini haka ba,
bari na tafi. Ayyuka sun yi mini yawa ne sosai, amma ina nan zan je wurin
likitan ƙwaƙwalwar, zan kuma dawowa"
Walid ya girgiza mata kai ya ce "Rayuwarki fa, ke kanki
zaki jefa kanki cikin hatsari"
Nabila ta share hawayenta ta ce "Kar ka damu da ni, shi
ɗin a ceto rayuwar sa da hankalinsa, a ƙwato masa hakkinsa, ba a san amfanin da
zai yi wa al'umma nan gaba ba, ina son kamo bakin zaren lamarin ne, bari na
tafi" ta juya ta tafi.
Walid ya girgiza kai, duk haryanzu bai tabattar da manufar
Nabila a kan Al'amin ba, amma a jikinsa yake jin ba zata cutar da shi ba.
Ya koma gidan su, ya tarar da Al'amin ya cika yayi fam, ya
kalle shi ya ce "Mai zamani ba ka kyautawa gaskiya, shi yaƙi ɗan zamba ne,
ko da turotan aka yi, sai ka bari mu bi komai a hankali, haka Ƙanwata tayi ta
fama da kai, da wannan zafin zuciyar ta ka, ƙarshe ta zame maka sanyin
idaniyarka. Ka din ga bin komai a hankali, bamu san mai gobe za ta haifar ba,
kar ka daki kwano. Ina son mu ƙara zurafafa bincike a kanta, wanda na yi bai
gamsar da ni ba"
"Mai laya"
"Viper"
"Ka ƙyale ni da maganar yarinyar nan"
Walid ya ce "Ba zan ƙyaleka ba, sai ka fuskanci gaskiya
Viper".
Nabila tana tafe, tana mamakin dalilin da ya sanya Viper
yake son kasheta wasu lokutan, amma meyasa ya rikice haka da ya ji ta ambaci
Naja'atu Bunkure?.
Gaba ɗaya al'amuran case ɗin Viper sarƙaƙiyarsu ta yi yawa,
a labarin da Walid ya bata, ba ta ji in da Najar tayi masa wani abu ba,
kodayeke haryanzu labarin bai kammala ba.
Gida ta yi niyyar tafiya, dan kanta ciwo yake yi mata, amma
kwana biyu ba ta haɗu da sumayya ba, kuma gashi ba ta bata labarin karonta da
Naja'atu ba, dan haka ta kira nufi gidan radiyon su Sumayya.
***
Ramma na zaune na karyawa take kallon Abdul, yadda ya sha
kunu, yana video call da wani likita, yana yi masa bayani, a kan wani result na
patient da ya turo masa, yanayin yadda yake bayanin ya tabattar mata da ya san
abun da yake yi. Sai da ya gama sannan ya rufe tab ɗin, ya kalleta ya ce
"Kalli gabanki kar ki lashe ni"
Ta kwaɓe baki ta ce "Ban ga abun lasa a jikinka ba,
jiki duk najasa".
Cikin ko in kula ya ce "Haka dai ki ke zaune da
ni" tayi guntun tsaki, ta cigaba da tauna a hankali.
Can ta sake kallonsa ta ce "Abdul yasar"
Ya ce "Your excellency"
Ta ɓata fuska ta ce "Ba na son wata your
excellency".
"Ke ba abun alfaharinki bane ba, ace ke yarinyar deputy
governor ce ba"
"Malam ka daina zaƙewa ba zaka taɓa ci ba, ai shugaba
nagari ake fata, kai idan ka zama shugaba ai ina ga sai ka halatta zina, tun da
gaka bature, yahudawa ne abun koyinka"
Ya girgiza kai ya ce "A'a iskancin nawa bai kai nan
ba"
Ramma ta ce "Ga wanda bai sanka ba ba, ni tambayarka
zan yi, wai dan Allah da gaske kai likita ne? Mamaki nake yi" yayi mata
banza yana shan tea.
"Taɓ, kura da fatar akuya, ba su san har giya ka ke sha
ba, ashe wataran zaka yi kisan kai, ko ma in ce kana yi. Saboda irinka wasu
mazan suke raka mata asibiti, dan tsaf zaka yi wa matan mutane ɓarna tun da ka
saba" yadda ya dire kofin yana kallonta ne ya sanya ta sha jinin jikinta.
"Meyasa ba ki da ɗa'a?"
"Saboda ɗa'a muhalli ne da ita, nan kuma ba wurin da ya
dace na nuna ta bane"
Ya jinjina kai ya ce "Haka ne, duk matar da na yi
lalata da ita, ita ta kawo mini kanta, kar ki ƙara yi mini irin haka"
"Nima ni na kawo maka kaina kenan ko? Baka da kunya ko
kaɗan, sai dai idan ka gama kumburin ka fashe, har abada mutumin banza ka ke a
idona, 'ya mace ba ta taɓa mantawa da wanda ya kawar mata da mutunci, ko da
kuwa ta hanyar aure ne, balle ta mummunar hanya, irin wadda ka yi mini, wallahi
ban da zuciyar musulunci da tuni na kashe kaina na huta, kaf danginmu babu
mazinaci, amma ni kalle ni yanzu. Tsaki yayi, ya tashi ya zai fice.
"Wallahi duk in da zaka je, Allah ya isata, na nan na
bibiyarka har kabarinka" Dummm ƙirjinsa ya buga, ya waiwayo yana kallon
ramma da ke ta uban kuka.
Bai taɓa dana sanin aikata duk wani laifi da yake yi ba, sai
a kan fyaɗen da ya yi wa ramma. Galibin saɓon da yake yi, tsakaninsa da
Ubangiji ne, ba a taɓa tsayawa gaba da gaba, ana tsine masa da yi masa Allah ya
isa ba, ya sha attempting ya mayar da ita, amma sai ya ji ba zai iya rabuwa da
ita ba, kuma kamar yadda take yawan faɗa, ya riga ya gama lalata mata rayuwa,
ba za ta yi daraja a idon jama'a ba.
Motarsa ya shiga, ya tarar da wayoyinsa a ciki suka kwana, a
buge ya dawo jiya tab ɗin sa ce kawai a cikin gidan, missed calls ɗin
mahaifinsa babu adadi, ga na Naja'atu Bunkure, banda na mahaifiyarsa. Tunani
yake yi ko lafiya ake yi masa wannan uban kiran hakan, shi ya san bai yi wani
laifin ba balle ace.
Haka ya ja mota, ya nufi gidan su, yana jin yadda Allah ya
isan ramma, ke ƙara yi masa amsa kuwwa.
Falon indabo ya nufa, ya na zuwa ya hau shi da faɗa,
"Wane irin rashin mutunci ne zai sanya ka ƙi ɗaga waya tun jiya? Har na
fara tunanin wani abun ne ya same ka? Kana can mashaya kana iskancin naka daka
saba ko? Wallahi ka nutsu ba za ka lalata mini siyasa da shirina a banza a wofi
ba, saboda shashancinka da rashin sanin ciwon kai ba, dole ka san abun da ka ke
ciki ka shiga hankalinka"
Zama yayi ya haɗe rai, yaƙi magana, har Indabo yayi
masifarsa ya gama, sai da ya gama haki, sannan ya ce "Jiya Naja'atu ta zo
mini hankali a tashe, yarinyar da ka yi wa fyaɗe, mutumin da aka ce shi yayi,
wata lawyer za ta tsaya masa, ta je har office ɗin Naja'atu neman in da aka
tsaya a case ɗin. Ina tsoron ranar da abokan adawa za su ɗagomu, ko su bankaɗo
miyagun laifukan da ka ke aikatawa. Yanzu ina ka kai yarinyar yaya aka yi da
ita?"
"Ban sani ba, wace yarinyar nake magana a kai? Yarinyar
da ka yi wa lalatar nake yi maka magana".
"Amm...m...wai ita rahama?"
"Kai ka sani, ina tambayar ka kana tambayata?"
Abdul ya ce "Ba Naja ce ta je ba, zata ba su kuɗi a
rufe zancen ba?"
"Zan kife ka da mari wallahi, uban najar, ba ta je ba
suka ƙi karɓar kuɗin, suka ce sai an karɓar musu hakkinsu ba? Ka ce mini zaka
kashe yarinyar yaya ka yi da ita? Sannna yaya ka yi da uwar yarinyar, muddin
case ɗin ya cigaba aka samu sani leakage mun kaɗe, zan iya asarar wannan
wahalar ta wa, takarar ma ba zaka samu ba".
Abdul ya dubi Indabo ya ce "Amma daddy ka riƙe muƙamai
da dama a garin nan da ƙasar nan, kai yakamata ace ka zama governor nan ba ma
deputy governor ba da ka ke ƙoƙarin ɗora ni a kai ba, ni da ka bar ni da sabgar
siyasar nan takura mini za ayi na kasa sukuni yadda nake so".
Indabo ya jinjina kai ya ce "Taɓɗijan, bilki anya ni na
haifi yaron nan kuwa? Kina jin abun da yake faɗa?"
Ta sha kunu ta ce "Wace irin magana ce wannan ka ke
yi?"
"Ki na jin abun da yake gaya mini, Abdul siyasa lissafi
ce, idan ya ƙwace maka, babu wata fomular da zata yi maka solving duk wani
hardship da zaka shiga. Na gama da jihar nan, sonake ka riƙa mini, sama nake
tunani tawagarmu mu ƙarasa mamaye ƙasar nan, komai a lissafe nake yin sa".
Abdul ya yi ajiyar zuciya ya ce "Yarinyar ta mutu ai,
babarta ce take nan"
"Ka tabattar?"
Abdul ya jinjina kai. Indabo ya ce "Dole aje a nemo
babarta, ita ma a kawar da ita, kar su ɓata mana aiki"
Cikin tashin hankali ya ce "Ita ma wai kashetan za
ayi?"
Indabo ya ce "To me za ayi idan ba a kasheta ba? Sai
asirinmu ya tonu kuma, sannan azo a fara neman mafita?.
And na ɗaga komawata Abuja, sai Allah ya kaimu weekends, kai
kuma zaka tafi jibi in Allah ya kaimu, akwai meeting da shugabannin jam'iyya na
ƙasa da na jiha, sannan akwai meeting na musamman da deligates, dan dai a samu
ayi nasara. Sai ka je ka yi shiri ka bar ni da sauran"
Gaba ɗaya jikin Abdul ya yi sanyi, ya tsare mahaifinsa da
ido.
"Menene kuma ka tsaya kana kallona? Kafin ƙarshen watan
nan kuma za a kai kuɗin aurenka, gidan party chairman kai da 'yar sa".
Abdul ya murza goshinsa, saboda yadda kansa yake sara masa,
gaba ɗaya ya rasa abun yi.
***
A nutse sumayya take kallon Nabila ta ce "Arfa,
idanunki sun nuna akwai damuwa, meyake damunki ne kamar ma fa kuka ki ka
yi" kamar Sumayya ta soso mata wurin da yake yi mata ƙaiƙayi, kawai ta
saka mata kuka.
Sumayya ta ce "Matsalata da ke kenan, shagwaɓa
arfa" ta share hawayenta tana zumɓura baki.
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Ƙila fa ba wani abin
kirki ne ya saki kukan ba, ina jinki ko duk Najar ce, yaya ku ka yi da
ita?"
Nabila ta ce "Wannan ai azzalumar mace ce" nan ta
gaya wa Sumayya yadda suka yi.
Sumayya ta jinjina kai ta ce "To hakan ne ya saki
kuka?" Nabila ta girgiza kai ta ce "Ke na gaji ne, kaina ya ɗauki
caji, kin ga rashin mutuncin da barrister Kabir ma yayi mini duk saboda ita, ni
kamar na karaya ma, amma wallahi ba zan janye ba"
Sumayya ta yi dariya ta ce "Manya gatan wasa, karaya ba
taki ba ce ba, akwai ƙalubale sosai a duk wata nasara da ake son cimma, dan
haka ki yi haƙuri ki cigaba da addu'a, In sha Allah sai kin cika burinki a kan
Naja'atu".
"Wallahi sumy da kamar na karaya, amma ba zan karayan
ba in sha Allah, sai na cika burina"
"Yauwwa mutuniyar Viper" da sauri Nabila ta
kalleta ta ce "Me ki ka ce?"
"Mutuniyar Viper mana, ko shi yanzu kin ɗaga masa ƙafa,
kin haƙura da nemansa kin koma kan fansarki ta naja'atu bunkure?"
Nabila ta ƙurawa fuskar Sumayya ido ta ce "Al'amin mai
dogon zamani" tayi maganar tana murmushi.
Sumayya ta ce "Ban gane ba"
"Kawai shaƙar da yayi mini nake tunawa ne, na kusa
sheƙawa".
"Amma haryanzu ba ki sanarwa DSP ba, yakamata ki
tamakawa aikinsa fa"
Nabila ta ce "Taɓ haka kurum ya gaya wa Abba, ya saka
Abba ya harbe ni da bindiga har lahira, na je wurin ɗan daba, ba dani ba bari
na tafi gida, marata ma ciwo take"
Nabila ta tashi, sumayya ma ta tashi za ta rakata, a
reception suka haɗu da P.A, gaban sumayya ya faɗi, ya din ga bin su da kallo,
ita da Nabila.
"Malam ka kalli gabanka mana, ji jaraba zai saka na faɗi"
Nabila ta yi maganar cikin ɗaga murya tana kallon P.A
Sumayya ta ce "Na shiga uku, haba Arfa, babba ki ke yi
wa haka?"
"To waye ya ce ya kalle ni?"
P.A ya ce "Yi haƙuri, wallahi kallon sani nake yi miki
ne, kina yi mini kama da wata da na sani"
Nabila ta kwaɓe baki, yayin da jikin sumayya ya hau rawa.
Ya ce "Sumayya wurinki na zo fa" gaba ɗaya sumayya
ta rikice, dan kar P.A yayi wani abun da zai sanya Nabila gane wani abun, dan
sharp brain ce da ita sosai.
Nabila ta ce "Bar rakiyar kawai, ni na tafi sai mun yi
waya, kuma ki daina ccacanza lambobi kina kirana, kamar wata mara gaskiya ko
'yar 419, idan na kira layinki ba zaki ɗaga ba, sai ki yi ta canza lamba"
gaban sumayya ya faɗi, mussaman kallon da P.A yayi mata.
Cikin yaƙe Sumayya ta ce "Layina ne yake bani matslaa,
sai mun yi waya".
P.A ya tasa ta a gaba, zuwa news room, in da take aiki, ya
rufe ƙofa ya kalleta ya ce "Wato canza lamba ki ke yi ki yi waya da ita
ko?".
Sumayya ta ce "Ban san me zaku iya yi mata ba, dole sai
na tantance abun zan din ga gaya muku a kanta".
"Haka muka yi da ke? Kin zaɓi ki salwantar da rayuwarta
kenan?"
"Ba zan salwantar da rayuwarta ba, kuma babu abun da
zai same ta sai wanda Allah ya ƙaddara mata, ku bani a hankali ai ina sanar
muku da duk wani abu da take aikatawa kamar yadda ku ka buƙata. Menene na biyo
ni nan kuma, ka yi mini magana a gabanta sai ta gane".
P.A ya ce "Ta gane me? Muddin ki ka bari ta gane, sai
ta zama gawa, an sanar mini ta zo ne, kuma na san muddin ta zo, wani muhimmin
abun ne ya kawo ta. Me yake faruwa? Dan kar ki yi zaton ke kaɗai ki ke yi mana
aiki, duk motsinki kema ana saka mana ido a kai".
Sumayya ta yi ajiyar zuciya ta ce "Zauna mu yi
magana".
Nabila kuwa bayan ta fito harabar radiyon, still motar nan
ta sake gani, wadda aka taɓa bin ta da ita, ta ganta a law firm ɗin su, yanzu
ma gata a gidan rediyon su Sumayya, kuma lambar motar ce ta sake tabattar mata
da motar ce dai.
Wani guntun murmushi ta yi ta ce "Bari dai na ga ƙwal
uwar daka".
***
Ramma ba ta sake ganin Abdul ba sai can dare, ba ta yi
zaton zai kulata ba ma, ta ɗauka fushin da yayi ne ya hana shi dawowa, dan har
ta fara bacci, ta ji motsinsa a bedroom ɗin. Ta buɗe ido ta kalleshi, ta ga bai
kulata ba. "Kayi dare da yawa yau" ya waiwaya ya kalleta ya ce
"Idonki biyu?"
"A'a motsinka ne ya tashe ni"
"Barin gidan nan zamu yi, gobe in Allah ya kaimu"
cikin rashin fahimta ta ce "Saboda me?"
"Wani dalili kawai, zan yi tafiya ne na sati ɗaya"
"Kuma ka tafi ka bar ni nikaɗai?"
Ya ce "Eh babu abun da zai same ki, can zamu koma gaba ɗaya,
bana son a gano ki a nan".
Ta taɓe baki ta ce "Kana nufin dai haka zan cigaba da
zama kenan?"
"A'a ina tunani a kan zaman mu"
Tayi shiru, ta gyara kwanciyar ta, ta cigaba da baccinta.
Juya tayi, ta ganshi a zaune, yana hana haɗa ƙwayoyi, ya ɓalle
wannan ya ɓalli waccan. Matsawa ta yi ta ƙwace ta ce "Ba zaka sha wannan
ƙwayoyin ka mayar da ni jakarka ba, ba zai yiwu ba, wallahi ko na bar maka ɗakin"
a sanyaye ya ce "Ba wanda ki ke tunani bane ba, damuwace ta ɗan yi mini
yawa, bacci nake son na yi" ta saka hannu ta kwashe packets ɗin ta ce
"Kai kamar ba likita ba, anya ma ba likitan bogi bane ba, haryanzu ina
tantama babu likitan kirki da zai yi abun da ka ke yi".
"Ke ba zaki gane ba ne, ki bani kawai idan ba haka ba,
baccin ba zai yiwu ba".
"Aikuwa sai dai kar ka yi" ta watsa su bayan
gadon, ta gyara kwanciyar ta.
***
Nabila tana zaune, tana kaɗa ƙafa tana cin gugguru, ta na
zancen zuci, ta kalli wayarta da take silent, sai haske take yi, ta saka hannu
ta ɗauka, ta saka a kunnenta.
"Hello barka da dare"
A hankali ta ce "Yauwwa"
"Ya gida aiki?"
"Alhamdilillah"
"Na ce ina da ƙorafi, a taimaka mini an ce na je
office, na je sau biyu ba kya nan"
Ta yamutsa fuska ta ce "Wake magana ne?"
Ya ce "Ni ne"
"To kai wa?"
"Bawan Allah, ni ne na kira ki rannan. Wataƙila ina da
magana mai muhimmanci da ke".
Nabila ta yi guntun tsaki ta ce "Da maganar mai
muhimmanci har haka, da ba a waya zaka tsaya kana zagaye-zagaye ba". Ta
katsewayar, tana cigaba da ɓata fuska.
Lambar Viper ta kira, ta na jiran ya ɗaga, har ta sare da
zai ɗaga, ta ji ya ɗaga wayar.
Tayi gyaran murya ta ce "Ka na ji na? Na san ma kana
ji, ba magana zaka yi ba. An ce baka taɓa mata, amma ni kullum burinka ka kashe
ni, ka yi ta shaƙe ni, ko cikakkiyar lafiya ba ni da ita, idan ka yi haƙuri ka
ba a hankali zan yi maka bayanin komai, amma ka fiye zafin zuciya haryanzu
maƙogwarona kamar an shaƙeni da ƙarfe nake ji" ta yi maganar har da kukan
kissa.
Yayi shiru yana sauraren ta.
"Ba zan yi zuciya na daina zuwa ba, har sai ka gaya
mini sauran labarin nan, na ji ina 'yar madara take, ina son saninta, akwai
abubuwan koyi da yawa a rayuwar ta. Zan sake dawowa in sha Allah, amma ka rage
zafin rai dan Allah, mu yi magana ta fahimta"
Nasir ne ya shigo ɗakin unexpected, ta ɗaga kai ta kalleshi,
ya ƙura mata ido.
Ba ta canza daga yadda take ba, ta ce "Sai anjima, zamu
yi magana" ta katse kiran ta kalli Nasir ta ce "Yaya shigowa ba
excuse?"
"Da wa ki ke waya?" Ta gyaɗa kai ta ce "Wani
ne"
"Wani wa?"
"Is confidential"
Ya ƙura mata ido ya ce "Confidential as how?"
"Haba Yaya, client ɗina ne fa"
"Amma ki ke wannan kashe muryar?"
Ta ce "Ikon Allah, to ai he's not just a client,
ammm" ba ta ƙarasa ba ya juya ya fice, ta yi ajiyar ta ce "Ohh ni
Nabila, yaya ai sai dai ka yi haƙuri"
Walid ne ya shigo ɗakin, dawowarsa kenan, ya tarar da Viper,
a ɗakinsa, yana goge wuƙarsa sweazland. Ɗan mama kuma na zaune a gefensa.
Zaro ido ya yi ya ce "Me zan gani haka? Viper waye ya ɗaukko
wannan wuƙar, ya kawo maka?" Al'amin yayi shiru yana jujjuyata a hannunsa.
Ya kalli ɗan mama da yake sunkuyar da kai, aikuwa a fusace
ya saka ƙafa ya daki ɗan mama ya ce "Amma an yi shegen yaro, wallahi baka
da mutunci ɗan mama, uban wa ye ya ce ka ɗaukko masa wuƙar nan?"
Ɗan mama ya ce "To wai ya zan yi dan Allah? Cewa yayi
sai na ɗaukko masa, kuma Oga liti ne ya ɗaukko ya bani, wai operation za su
fita gobe, Madaki yana cikin gari"
Walid ya din ga ɗurawa Ɗan mama ashariya, ya juya ya nufi
Viper, Amma Viper ya miƙe tsaye, ya fito da harshen sa waje ya mayar.
Walid ya nuna kansa ya ce "Ni zaka sakawa ƙarfe?"
"Ƙwarai, muddin ka yi ƙoƙarin dakatar da ni, wallahi
jininka za ta sha, ai na gaya maka ka nesanta yarinyar da ni, muddin ina
ganinta ba ni da wata nutsuwa, dan haka ba ka da ikon, dakatar da ni".
Walid cikin ɓacin rai ya ce "Hanyar da muke ƙoƙarin bi,
ba mai ɓullewa ba ce, ka yi haƙuri"
"Shhhh" ya yi maganar tsare Walid da ido.
"Dalla matsa, ni zaka yi wa barazana, ka je ka yi duk
abun da ka ga dama, na daina shiga harka, tafiya zan yi ku ƙarata da kai da su
litin, mu gani idan hanyar za ta fishshe ku"
Suna cikin faɗa liti ya shigo, suka ya tarar da su, liti ya
ce "Kai walid, ba zaka hanamu abun da muke so ba, ka hanamu motsawa,
wancan banzan madakin, yana ta rashin mutunci a gari, wallahi sai mun ɗauki
fansa" Walid ya fice ya bar musu gidan cikin matsanancin ɓacin rai.
***
Abdul ne da ramma suke tafe a mota, tana ta kallon hanya, ya
yi locking ɗin motar, ga glass ɗin ta tint ne.
"Wai tafiyar nan ba zata ƙare ba, ni fa na gaji".
"Eh, cinikinki zan je na yi na sayar" ta harare
shi, ta cigaba da kallon titi.
Wata unguwa suka yi, babu gidaje da yawa a wurin, sai
tsilla-tsilla, kuma manya manyan gidaje ne, na alfarma a rukunin.
A ƙofar wani ƙaton gida ya tsaya, aka buɗe masa gate, ya
shiga, wasu irin manyan karnuka na ta kai komo a harabar gidan, ya zagaya yayi
parking, ya cire lock ɗin motar, ta buɗe ta fita.
Shi ma ya fito, ya buɗe boot, ya ciro akwatuna, ya ce
"Mu je"
"Yanzu da ka mayar da ni gida, gara ka sake kawo ni
nan?"
Yayi gaba ya ce "Idan karnuka suka cinyeki, kya
taho" ta bi bayansa tana rarraba ido, gida mai kyau na alfarma.
Saman bene suka hau, ya kaita wani katafaren bedroom, ya
ce "A nan zaki zauna, zuwa lokacin da zan dawo, kafin nan na samo
mafita, zaki iya shiga ko ina, an ajiye duk abun da ki ke buƙata, sai dai ko
haraba ba zaki fita ba. Zan ajiye miki waya duk abun da ake ciki, ki kirani ko
idan kina buƙatar wani abu, wayar lambata kawai zaki iya kira".
"Wai dan Allah nikaɗai zaka bari a gidan nan, ni tsoro
nake ji wallahi"
"Ki yi haƙuri mana, ba zan daɗe ba, na ɗan lokaci ne,
zaki yi missing ɗi na ko?" Yayi maganar yana kissing ɗin goshinta. Kuka
take yi sosai, ya rungumeta yana rarrashin ta.
***
Yau ma kaca-kaca Walid ya yi da su Viper, Liti yana
supporting ɗin Viper a kan iya wuya, kawai su afka su ɗauki fansa.
Duk yadda walid ya so fahimtar da su, suka ƙi fahimta.
Nabila ta fara gane kan hanyar zuwa gidan su Viper, kanta
baya kullewa kamar da.
Babu tsammani ta yi karo da Walid, ta ja ta tsaya, ta zata
zai yi mata masifa, ta ce "Ina wuni?"
"Lafiya ƙalau"
"Amm yana ina?"
Ya nuna mata dutsen da yake can gaba, ya ce "Yana can,
amma ki daina wahalar da kanki, taurin Al'amin yayi yawa, an ɗaukko masa
wuƙarsa, zai je ya yi gaba da gaba da madaki yau, ki ƙyale shi kawai"
Ta girgiza kai ta ce "A'a, zan jarraba sa'ata"
tayi gaba ta nufi in da dutsen yake, ba ta ƙarasa ba ta hango shi, a zaune a
gefen bishiya, cikin inuwa yana ɗan kaɗa ƙafa, ya na shan sigari.
Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi ta ce "Barka da
rana" bai amsa ba, ta saka hannunta, ta zare sauran karan tabar hannunsa
ta ce "Ayi mini uzuri, ba na son hayaƙi, mara zuciya na sake dawowa. Dan
Allah kar ka shaƙe ni, magana zamu yi ta fahimtar juna"
Ya ɗaga kai ya kalleta, ya yinƙura ya miƙe, ita ma ta tashi
ta tsaya a gaban sa, ka saurare ni ko sau ɗaya ne, zafin zuciya da gaggawa shi
ya sanya ka rasa da yawan mutane masu muhimmanci a rayuwarka".
Sweazland ya saka mata a wuyanta, ya ce "Gargaɗi na
ƙarshe, ki rabu da ni, ki fita daga rayuwata".
Ta kalli yadda wuƙar ke ƙyalli a saitin wuyanta ta ce
"Sai na ji ƙarshen labarinka, na ji wa ka kashe? Kuma ina jauhar da iabun
da yake cikinta?"
Ya kalleta ita ma cikin ƙwarin gwiwa ta cigaba da kallonsa,
duk da ƙasan zuciyarta a tsorace take.
"Ki daina kallona a haka, meyasa ki ke son ki zama
raunina ne?" yayi maganar muryarsa na rawa.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Jikinta ne ya hau tsuma, saboda irin kallon da yake yi mata,
yayi gaba da nufin ta bi bayan shi, amma ta ƙi, ya tsaya ya waiwayo yana
kallonta, ta kalli Walid, ya gyaɗa mata kai alamar ta bi shi.
Kamar mara gaskiya haka ta bi bayansa, sai da suka ɗan yi
nesa da gidan kaɗan, sannan ya waiwayo ya kalleta ya ce "Me ki ke nema a
wurina?"
Ta kalleshi ta sunkuyar da kai. "Ki yi mini magana, me
ki ke nema a wurina? Meyasa ki ke sintirin zuwa in da nake? Idan so ki ke a
kama ni, ki kawo su su kama ni mana, wace irin yarinya ce ke ne?"
Yadda yake maganar cikin hargowa, sai da ta ja da baya,
saboda tsoro.
"Talk! Me ki ke so, waye ya turo ki?"
"Ni ba wanda ya turo ni" ta yi maganar cike da
tsoro.
"Me ki ke nema?"
A sangarce ta ce "Ni ka daina yi mini magana a haka,
tsorata ni ka ke yi, ni ban san me zan ce maka ba"ta yi maganar tana kawar
da kanta gefe.
Ya tsareta da idanunsa, ita kuma taƙi ɗagowa, ta sunkuyar da
kanta ƙasa tana haɗe fuska cikin tsoro.
Ya sunkuyo dai-dai tsawon ta ya ce "Ki bani amsa"
tayi shiru ta ƙi magana.
Hakan ya ƙara hasala shi, ya buga ƙafarsa ya ce "Ki yi
magana kan na saka ki yi ta ƙarfin tsiya"
Cikin rauni ta ce "Na gaya maka, ni babu wanda ya turo
ni, ni na turo kaina, kuma ni tsoro ka ke bani ban san ta ina zan fara ba,
tsorata ni ka ke yi"
Ba ta ƙarasa maganar cikin nutsuwa ba, ta ji hannunsa a
wuyanta. "Naja'atu Bunkure, meye alaƙarki da ita? Ita ki ke yi wa aiki a
kaina, da ita da Indabo ko?" Ba ta yi masa magana ba, sai idanuwanta da
suka yo waje, ga hawaye na bin fuskarta, sai dai kallon da ta yi masa, ya sanya
ƙirjinsa bugawa da ƙarfi, ya saketa ya ja da baya, yana dafe saitin zuciyarsa.
Dai-dai lokacin Walid ya ƙaraso ya ce "Viper meyasa ka
ke haka ne? Ban sanka da cin zarafin mata ba, meyasa ka ke ƙoƙarin farawa
yanzu?" Ya nuna Nabila da yatsansa, amma ya kasa magana sai haki yake yi,
saboda zuciyarsa ta ƙi nutsuwa. Ta ƙura masa ido, tana kuka.
Kawai ya juya ya bar wurin, Walid ya ce "Sannu, kin ga
abun da nake guje miki a kansa ko? Shiyasa na ce ki daina zuwa anyhow. Mun gode
da gudunmawarki ga ɗan uwanmu, amma ki daina zuwan nan, ina tsoron yayi miki
illa wataran".
Ta girgiza kai ta share hawayenta ta ce "Ina da kafiya
wasu lokutan, haryanzu ban ji cewar zan karaya ba, da ya bi ni a sannu, da zan
yi masa bayanin abun da ya haɗa ni da Naja'atu Bunkure. Kawai ji nake ya zame
mini wajibi na taimake shi, ina son sanin ƙarshen labarinsa, har cikin zuciyata
nake son ba shi gudunmawa, na yi masa uzuri, wataran ba zai yi mini haka ba,
bari na tafi. Ayyuka sun yi mini yawa ne sosai, amma ina nan zan je wurin
likitan ƙwaƙwalwar, zan kuma dawowa"
Walid ya girgiza mata kai ya ce "Rayuwarki fa, ke kanki
zaki jefa kanki cikin hatsari"
Nabila ta share hawayenta ta ce "Kar ka damu da ni, shi
ɗin a ceto rayuwar sa da hankalinsa, a ƙwato masa hakkinsa, ba a san amfanin da
zai yi wa al'umma nan gaba ba, ina son kamo bakin zaren lamarin ne, bari na
tafi" ta juya ta tafi.
Walid ya girgiza kai, duk haryanzu bai tabattar da manufar
Nabila a kan Al'amin ba, amma a jikinsa yake jin ba zata cutar da shi ba.
Ya koma gidan su, ya tarar da Al'amin ya cika yayi fam, ya
kalle shi ya ce "Mai zamani ba ka kyautawa gaskiya, shi yaƙi ɗan zamba ne,
ko da turotan aka yi, sai ka bari mu bi komai a hankali, haka Ƙanwata tayi ta
fama da kai, da wannan zafin zuciyar ta ka, ƙarshe ta zame maka sanyin
idaniyarka. Ka din ga bin komai a hankali, bamu san mai gobe za ta haifar ba,
kar ka daki kwano. Ina son mu ƙara zurafafa bincike a kanta, wanda na yi bai
gamsar da ni ba"
"Mai laya"
"Viper"
"Ka ƙyale ni da maganar yarinyar nan"
Walid ya ce "Ba zan ƙyaleka ba, sai ka fuskanci gaskiya
Viper".
Nabila tana tafe, tana mamakin dalilin da ya sanya Viper
yake son kasheta wasu lokutan, amma meyasa ya rikice haka da ya ji ta ambaci
Naja'atu Bunkure?.
Gaba ɗaya al'amuran case ɗin Viper sarƙaƙiyarsu ta yi yawa,
a labarin da Walid ya bata, ba ta ji in da Najar tayi masa wani abu ba,
kodayeke haryanzu labarin bai kammala ba.
Gida ta yi niyyar tafiya, dan kanta ciwo yake yi mata, amma
kwana biyu ba ta haɗu da sumayya ba, kuma gashi ba ta bata labarin karonta da
Naja'atu ba, dan haka ta kira nufi gidan radiyon su Sumayya.
***
Ramma na zaune na karyawa take kallon Abdul, yadda ya sha
kunu, yana video call da wani likita, yana yi masa bayani, a kan wani result na
patient da ya turo masa, yanayin yadda yake bayanin ya tabattar mata da ya san
abun da yake yi. Sai da ya gama sannan ya rufe tab ɗin, ya kalleta ya ce
"Kalli gabanki kar ki lashe ni"
Ta kwaɓe baki ta ce "Ban ga abun lasa a jikinka ba,
jiki duk najasa".
Cikin ko in kula ya ce "Haka dai ki ke zaune da
ni" tayi guntun tsaki, ta cigaba da tauna a hankali.
Can ta sake kallonsa ta ce "Abdul yasar"
Ya ce "Your excellency"
Ta ɓata fuska ta ce "Ba na son wata your
excellency".
"Ke ba abun alfaharinki bane ba, ace ke yarinyar deputy
governor ce ba"
"Malam ka daina zaƙewa ba zaka taɓa ci ba, ai shugaba
nagari ake fata, kai idan ka zama shugaba ai ina ga sai ka halatta zina, tun da
gaka bature, yahudawa ne abun koyinka"
Ya girgiza kai ya ce "A'a iskancin nawa bai kai nan
ba"
Ramma ta ce "Ga wanda bai sanka ba ba, ni tambayarka
zan yi, wai dan Allah da gaske kai likita ne? Mamaki nake yi" yayi mata
banza yana shan tea.
"Taɓ, kura da fatar akuya, ba su san har giya ka ke sha
ba, ashe wataran zaka yi kisan kai, ko ma in ce kana yi. Saboda irinka wasu
mazan suke raka mata asibiti, dan tsaf zaka yi wa matan mutane ɓarna tun da ka
saba" yadda ya dire kofin yana kallonta ne ya sanya ta sha jinin jikinta.
"Meyasa ba ki da ɗa'a?"
"Saboda ɗa'a muhalli ne da ita, nan kuma ba wurin da ya
dace na nuna ta bane"
Ya jinjina kai ya ce "Haka ne, duk matar da na yi
lalata da ita, ita ta kawo mini kanta, kar ki ƙara yi mini irin haka"
"Nima ni na kawo maka kaina kenan ko? Baka da kunya ko
kaɗan, sai dai idan ka gama kumburin ka fashe, har abada mutumin banza ka ke a
idona, 'ya mace ba ta taɓa mantawa da wanda ya kawar mata da mutunci, ko da
kuwa ta hanyar aure ne, balle ta mummunar hanya, irin wadda ka yi mini, wallahi
ban da zuciyar musulunci da tuni na kashe kaina na huta, kaf danginmu babu
mazinaci, amma ni kalle ni yanzu. Tsaki yayi, ya tashi ya zai fice.
"Wallahi duk in da zaka je, Allah ya isata, na nan na
bibiyarka har kabarinka" Dummm ƙirjinsa ya buga, ya waiwayo yana kallon
ramma da ke ta uban kuka.
Bai taɓa dana sanin aikata duk wani laifi da yake yi ba, sai
a kan fyaɗen da ya yi wa ramma. Galibin saɓon da yake yi, tsakaninsa da
Ubangiji ne, ba a taɓa tsayawa gaba da gaba, ana tsine masa da yi masa Allah ya
isa ba, ya sha attempting ya mayar da ita, amma sai ya ji ba zai iya rabuwa da
ita ba, kuma kamar yadda take yawan faɗa, ya riga ya gama lalata mata rayuwa,
ba za ta yi daraja a idon jama'a ba.
Motarsa ya shiga, ya tarar da wayoyinsa a ciki suka kwana, a
buge ya dawo jiya tab ɗin sa ce kawai a cikin gidan, missed calls ɗin
mahaifinsa babu adadi, ga na Naja'atu Bunkure, banda na mahaifiyarsa. Tunani
yake yi ko lafiya ake yi masa wannan uban kiran hakan, shi ya san bai yi wani
laifin ba balle ace.
Haka ya ja mota, ya nufi gidan su, yana jin yadda Allah ya
isan ramma, ke ƙara yi masa amsa kuwwa.
Falon indabo ya nufa, ya na zuwa ya hau shi da faɗa,
"Wane irin rashin mutunci ne zai sanya ka ƙi ɗaga waya tun jiya? Har na
fara tunanin wani abun ne ya same ka? Kana can mashaya kana iskancin naka daka
saba ko? Wallahi ka nutsu ba za ka lalata mini siyasa da shirina a banza a wofi
ba, saboda shashancinka da rashin sanin ciwon kai ba, dole ka san abun da ka ke
ciki ka shiga hankalinka"
Zama yayi ya haɗe rai, yaƙi magana, har Indabo yayi
masifarsa ya gama, sai da ya gama haki, sannan ya ce "Jiya Naja'atu ta zo
mini hankali a tashe, yarinyar da ka yi wa fyaɗe, mutumin da aka ce shi yayi,
wata lawyer za ta tsaya masa, ta je har office ɗin Naja'atu neman in da aka
tsaya a case ɗin. Ina tsoron ranar da abokan adawa za su ɗagomu, ko su bankaɗo
miyagun laifukan da ka ke aikatawa. Yanzu ina ka kai yarinyar yaya aka yi da
ita?"
"Ban sani ba, wace yarinyar nake magana a kai? Yarinyar
da ka yi wa lalatar nake yi maka magana".
"Amm...m...wai ita rahama?"
"Kai ka sani, ina tambayar ka kana tambayata?"
Abdul ya ce "Ba Naja ce ta je ba, zata ba su kuɗi a
rufe zancen ba?"
"Zan kife ka da mari wallahi, uban najar, ba ta je ba
suka ƙi karɓar kuɗin, suka ce sai an karɓar musu hakkinsu ba? Ka ce mini zaka
kashe yarinyar yaya ka yi da ita? Sannna yaya ka yi da uwar yarinyar, muddin
case ɗin ya cigaba aka samu sani leakage mun kaɗe, zan iya asarar wannan
wahalar ta wa, takarar ma ba zaka samu ba".
Abdul ya dubi Indabo ya ce "Amma daddy ka riƙe muƙamai
da dama a garin nan da ƙasar nan, kai yakamata ace ka zama governor nan ba ma
deputy governor ba da ka ke ƙoƙarin ɗora ni a kai ba, ni da ka bar ni da sabgar
siyasar nan takura mini za ayi na kasa sukuni yadda nake so".
Indabo ya jinjina kai ya ce "Taɓɗijan, bilki anya ni na
haifi yaron nan kuwa? Kina jin abun da yake faɗa?"
Ta sha kunu ta ce "Wace irin magana ce wannan ka ke
yi?"
"Ki na jin abun da yake gaya mini, Abdul siyasa lissafi
ce, idan ya ƙwace maka, babu wata fomular da zata yi maka solving duk wani
hardship da zaka shiga. Na gama da jihar nan, sonake ka riƙa mini, sama nake
tunani tawagarmu mu ƙarasa mamaye ƙasar nan, komai a lissafe nake yin sa".
Abdul ya yi ajiyar zuciya ya ce "Yarinyar ta mutu ai,
babarta ce take nan"
"Ka tabattar?"
Abdul ya jinjina kai. Indabo ya ce "Dole aje a nemo
babarta, ita ma a kawar da ita, kar su ɓata mana aiki"
Cikin tashin hankali ya ce "Ita ma wai kashetan za
ayi?"
Indabo ya ce "To me za ayi idan ba a kasheta ba? Sai
asirinmu ya tonu kuma, sannan azo a fara neman mafita?.
And na ɗaga komawata Abuja, sai Allah ya kaimu weekends, kai
kuma zaka tafi jibi in Allah ya kaimu, akwai meeting da shugabannin jam'iyya na
ƙasa da na jiha, sannan akwai meeting na musamman da deligates, dan dai a samu
ayi nasara. Sai ka je ka yi shiri ka bar ni da sauran"
Gaba ɗaya jikin Abdul ya yi sanyi, ya tsare mahaifinsa da
ido.
"Menene kuma ka tsaya kana kallona? Kafin ƙarshen watan
nan kuma za a kai kuɗin aurenka, gidan party chairman kai da 'yar sa".
Abdul ya murza goshinsa, saboda yadda kansa yake sara masa,
gaba ɗaya ya rasa abun yi.
***
A nutse sumayya take kallon Nabila ta ce "Arfa,
idanunki sun nuna akwai damuwa, meyake damunki ne kamar ma fa kuka ki ka
yi" kamar Sumayya ta soso mata wurin da yake yi mata ƙaiƙayi, kawai ta
saka mata kuka.
Sumayya ta ce "Matsalata da ke kenan, shagwaɓa
arfa" ta share hawayenta tana zumɓura baki.
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Ƙila fa ba wani abin
kirki ne ya saki kukan ba, ina jinki ko duk Najar ce, yaya ku ka yi da
ita?"
Nabila ta ce "Wannan ai azzalumar mace ce" nan ta
gaya wa Sumayya yadda suka yi.
Sumayya ta jinjina kai ta ce "To hakan ne ya saki
kuka?" Nabila ta girgiza kai ta ce "Ke na gaji ne, kaina ya ɗauki
caji, kin ga rashin mutuncin da barrister Kabir ma yayi mini duk saboda ita, ni
kamar na karaya ma, amma wallahi ba zan janye ba"
Sumayya ta yi dariya ta ce "Manya gatan wasa, karaya ba
taki ba ce ba, akwai ƙalubale sosai a duk wata nasara da ake son cimma, dan
haka ki yi haƙuri ki cigaba da addu'a, In sha Allah sai kin cika burinki a kan
Naja'atu".
"Wallahi sumy da kamar na karaya, amma ba zan karayan
ba in sha Allah, sai na cika burina"
"Yauwwa mutuniyar Viper" da sauri Nabila ta
kalleta ta ce "Me ki ka ce?"
"Mutuniyar Viper mana, ko shi yanzu kin ɗaga masa ƙafa,
kin haƙura da nemansa kin koma kan fansarki ta naja'atu bunkure?"
Nabila ta ƙurawa fuskar Sumayya ido ta ce "Al'amin mai
dogon zamani" tayi maganar tana murmushi.
Sumayya ta ce "Ban gane ba"
"Kawai shaƙar da yayi mini nake tunawa ne, na kusa
sheƙawa".
"Amma haryanzu ba ki sanarwa DSP ba, yakamata ki
tamakawa aikinsa fa"
Nabila ta ce "Taɓ haka kurum ya gaya wa Abba, ya saka
Abba ya harbe ni da bindiga har lahira, na je wurin ɗan daba, ba dani ba bari
na tafi gida, marata ma ciwo take"
Nabila ta tashi, sumayya ma ta tashi za ta rakata, a
reception suka haɗu da P.A, gaban sumayya ya faɗi, ya din ga bin su da kallo,
ita da Nabila.
"Malam ka kalli gabanka mana, ji jaraba zai saka na faɗi"
Nabila ta yi maganar cikin ɗaga murya tana kallon P.A
Sumayya ta ce "Na shiga uku, haba Arfa, babba ki ke yi
wa haka?"
"To waye ya ce ya kalle ni?"
P.A ya ce "Yi haƙuri, wallahi kallon sani nake yi miki
ne, kina yi mini kama da wata da na sani"
Nabila ta kwaɓe baki, yayin da jikin sumayya ya hau rawa.
Ya ce "Sumayya wurinki na zo fa" gaba ɗaya sumayya
ta rikice, dan kar P.A yayi wani abun da zai sanya Nabila gane wani abun, dan
sharp brain ce da ita sosai.
Nabila ta ce "Bar rakiyar kawai, ni na tafi sai mun yi
waya, kuma ki daina ccacanza lambobi kina kirana, kamar wata mara gaskiya ko
'yar 419, idan na kira layinki ba zaki ɗaga ba, sai ki yi ta canza lamba"
gaban sumayya ya faɗi, mussaman kallon da P.A yayi mata.
Cikin yaƙe Sumayya ta ce "Layina ne yake bani matslaa,
sai mun yi waya".
P.A ya tasa ta a gaba, zuwa news room, in da take aiki, ya
rufe ƙofa ya kalleta ya ce "Wato canza lamba ki ke yi ki yi waya da ita
ko?".
Sumayya ta ce "Ban san me zaku iya yi mata ba, dole sai
na tantance abun zan din ga gaya muku a kanta".
"Haka muka yi da ke? Kin zaɓi ki salwantar da rayuwarta
kenan?"
"Ba zan salwantar da rayuwarta ba, kuma babu abun da
zai same ta sai wanda Allah ya ƙaddara mata, ku bani a hankali ai ina sanar
muku da duk wani abu da take aikatawa kamar yadda ku ka buƙata. Menene na biyo
ni nan kuma, ka yi mini magana a gabanta sai ta gane".
P.A ya ce "Ta gane me? Muddin ki ka bari ta gane, sai
ta zama gawa, an sanar mini ta zo ne, kuma na san muddin ta zo, wani muhimmin
abun ne ya kawo ta. Me yake faruwa? Dan kar ki yi zaton ke kaɗai ki ke yi mana
aiki, duk motsinki kema ana saka mana ido a kai".
Sumayya ta yi ajiyar zuciya ta ce "Zauna mu yi
magana".
Nabila kuwa bayan ta fito harabar radiyon, still motar nan
ta sake gani, wadda aka taɓa bin ta da ita, ta ganta a law firm ɗin su, yanzu
ma gata a gidan rediyon su Sumayya, kuma lambar motar ce ta sake tabattar mata
da motar ce dai.
Wani guntun murmushi ta yi ta ce "Bari dai na ga ƙwal
uwar daka".
***
Ramma ba ta sake ganin Abdul ba sai can dare, ba ta yi
zaton zai kulata ba ma, ta ɗauka fushin da yayi ne ya hana shi dawowa, dan har
ta fara bacci, ta ji motsinsa a bedroom ɗin. Ta buɗe ido ta kalleshi, ta ga bai
kulata ba. "Kayi dare da yawa yau" ya waiwaya ya kalleta ya ce
"Idonki biyu?"
"A'a motsinka ne ya tashe ni"
"Barin gidan nan zamu yi, gobe in Allah ya kaimu"
cikin rashin fahimta ta ce "Saboda me?"
"Wani dalili kawai, zan yi tafiya ne na sati ɗaya"
"Kuma ka tafi ka bar ni nikaɗai?"
Ya ce "Eh babu abun da zai same ki, can zamu koma gaba ɗaya,
bana son a gano ki a nan".
Ta taɓe baki ta ce "Kana nufin dai haka zan cigaba da
zama kenan?"
"A'a ina tunani a kan zaman mu"
Tayi shiru, ta gyara kwanciyar ta, ta cigaba da baccinta.
Juya tayi, ta ganshi a zaune, yana hana haɗa ƙwayoyi, ya ɓalle
wannan ya ɓalli waccan. Matsawa ta yi ta ƙwace ta ce "Ba zaka sha wannan
ƙwayoyin ka mayar da ni jakarka ba, ba zai yiwu ba, wallahi ko na bar maka ɗakin"
a sanyaye ya ce "Ba wanda ki ke tunani bane ba, damuwace ta ɗan yi mini
yawa, bacci nake son na yi" ta saka hannu ta kwashe packets ɗin ta ce
"Kai kamar ba likita ba, anya ma ba likitan bogi bane ba, haryanzu ina
tantama babu likitan kirki da zai yi abun da ka ke yi".
"Ke ba zaki gane ba ne, ki bani kawai idan ba haka ba,
baccin ba zai yiwu ba".
"Aikuwa sai dai kar ka yi" ta watsa su bayan
gadon, ta gyara kwanciyar ta.
***
Nabila tana zaune, tana kaɗa ƙafa tana cin gugguru, ta na
zancen zuci, ta kalli wayarta da take silent, sai haske take yi, ta saka hannu
ta ɗauka, ta saka a kunnenta.
"Hello barka da dare"
A hankali ta ce "Yauwwa"
"Ya gida aiki?"
"Alhamdilillah"
"Na ce ina da ƙorafi, a taimaka mini an ce na je
office, na je sau biyu ba kya nan"
Ta yamutsa fuska ta ce "Wake magana ne?"
Ya ce "Ni ne"
"To kai wa?"
"Bawan Allah, ni ne na kira ki rannan. Wataƙila ina da
magana mai muhimmanci da ke".
Nabila ta yi guntun tsaki ta ce "Da maganar mai
muhimmanci har haka, da ba a waya zaka tsaya kana zagaye-zagaye ba". Ta
katsewayar, tana cigaba da ɓata fuska.
Lambar Viper ta kira, ta na jiran ya ɗaga, har ta sare da
zai ɗaga, ta ji ya ɗaga wayar.
Tayi gyaran murya ta ce "Ka na ji na? Na san ma kana
ji, ba magana zaka yi ba. An ce baka taɓa mata, amma ni kullum burinka ka kashe
ni, ka yi ta shaƙe ni, ko cikakkiyar lafiya ba ni da ita, idan ka yi haƙuri ka
ba a hankali zan yi maka bayanin komai, amma ka fiye zafin zuciya haryanzu
maƙogwarona kamar an shaƙeni da ƙarfe nake ji" ta yi maganar har da kukan
kissa.
Yayi shiru yana sauraren ta.
"Ba zan yi zuciya na daina zuwa ba, har sai ka gaya
mini sauran labarin nan, na ji ina 'yar madara take, ina son saninta, akwai
abubuwan koyi da yawa a rayuwar ta. Zan sake dawowa in sha Allah, amma ka rage
zafin rai dan Allah, mu yi magana ta fahimta"
Nasir ne ya shigo ɗakin unexpected, ta ɗaga kai ta kalleshi,
ya ƙura mata ido.
Ba ta canza daga yadda take ba, ta ce "Sai anjima, zamu
yi magana" ta katse kiran ta kalli Nasir ta ce "Yaya shigowa ba
excuse?"
"Da wa ki ke waya?" Ta gyaɗa kai ta ce "Wani
ne"
"Wani wa?"
"Is confidential"
Ya ƙura mata ido ya ce "Confidential as how?"
"Haba Yaya, client ɗina ne fa"
"Amma ki ke wannan kashe muryar?"
Ta ce "Ikon Allah, to ai he's not just a client,
ammm" ba ta ƙarasa ba ya juya ya fice, ta yi ajiyar ta ce "Ohh ni
Nabila, yaya ai sai dai ka yi haƙuri"
Walid ne ya shigo ɗakin, dawowarsa kenan, ya tarar da Viper,
a ɗakinsa, yana goge wuƙarsa sweazland. Ɗan mama kuma na zaune a gefensa.
Zaro ido ya yi ya ce "Me zan gani haka? Viper waye ya ɗaukko
wannan wuƙar, ya kawo maka?" Al'amin yayi shiru yana jujjuyata a hannunsa.
Ya kalli ɗan mama da yake sunkuyar da kai, aikuwa a fusace
ya saka ƙafa ya daki ɗan mama ya ce "Amma an yi shegen yaro, wallahi baka
da mutunci ɗan mama, uban wa ye ya ce ka ɗaukko masa wuƙar nan?"
Ɗan mama ya ce "To wai ya zan yi dan Allah? Cewa yayi
sai na ɗaukko masa, kuma Oga liti ne ya ɗaukko ya bani, wai operation za su
fita gobe, Madaki yana cikin gari"
Walid ya din ga ɗurawa Ɗan mama ashariya, ya juya ya nufi
Viper, Amma Viper ya miƙe tsaye, ya fito da harshen sa waje ya mayar.
Walid ya nuna kansa ya ce "Ni zaka sakawa ƙarfe?"
"Ƙwarai, muddin ka yi ƙoƙarin dakatar da ni, wallahi
jininka za ta sha, ai na gaya maka ka nesanta yarinyar da ni, muddin ina
ganinta ba ni da wata nutsuwa, dan haka ba ka da ikon, dakatar da ni".
Walid cikin ɓacin rai ya ce "Hanyar da muke ƙoƙarin bi,
ba mai ɓullewa ba ce, ka yi haƙuri"
"Shhhh" ya yi maganar tsare Walid da ido.
"Dalla matsa, ni zaka yi wa barazana, ka je ka yi duk
abun da ka ga dama, na daina shiga harka, tafiya zan yi ku ƙarata da kai da su
litin, mu gani idan hanyar za ta fishshe ku"
Suna cikin faɗa liti ya shigo, suka ya tarar da su, liti ya
ce "Kai walid, ba zaka hanamu abun da muke so ba, ka hanamu motsawa,
wancan banzan madakin, yana ta rashin mutunci a gari, wallahi sai mun ɗauki
fansa" Walid ya fice ya bar musu gidan cikin matsanancin ɓacin rai.
***
Abdul ne da ramma suke tafe a mota, tana ta kallon hanya, ya
yi locking ɗin motar, ga glass ɗin ta tint ne.
"Wai tafiyar nan ba zata ƙare ba, ni fa na gaji".
"Eh, cinikinki zan je na yi na sayar" ta harare
shi, ta cigaba da kallon titi.
Wata unguwa suka yi, babu gidaje da yawa a wurin, sai
tsilla-tsilla, kuma manya manyan gidaje ne, na alfarma a rukunin.
A ƙofar wani ƙaton gida ya tsaya, aka buɗe masa gate, ya
shiga, wasu irin manyan karnuka na ta kai komo a harabar gidan, ya zagaya yayi
parking, ya cire lock ɗin motar, ta buɗe ta fita.
Shi ma ya fito, ya buɗe boot, ya ciro akwatuna, ya ce
"Mu je"
"Yanzu da ka mayar da ni gida, gara ka sake kawo ni
nan?"
Yayi gaba ya ce "Idan karnuka suka cinyeki, kya
taho" ta bi bayansa tana rarraba ido, gida mai kyau na alfarma.
Saman bene suka hau, ya kaita wani katafaren bedroom, ya
ce "A nan zaki zauna, zuwa lokacin da zan dawo, kafin nan na samo
mafita, zaki iya shiga ko ina, an ajiye duk abun da ki ke buƙata, sai dai ko
haraba ba zaki fita ba. Zan ajiye miki waya duk abun da ake ciki, ki kirani ko
idan kina buƙatar wani abu, wayar lambata kawai zaki iya kira".
"Wai dan Allah nikaɗai zaka bari a gidan nan, ni tsoro
nake ji wallahi"
"Ki yi haƙuri mana, ba zan daɗe ba, na ɗan lokaci ne,
zaki yi missing ɗi na ko?" Yayi maganar yana kissing ɗin goshinta. Kuka
take yi sosai, ya rungumeta yana rarrashin ta.
***
Yau ma kaca-kaca Walid ya yi da su Viper, Liti yana
supporting ɗin Viper a kan iya wuya, kawai su afka su ɗauki fansa.
Duk yadda walid ya so fahimtar da su, suka ƙi fahimta.
Nabila ta fara gane kan hanyar zuwa gidan su Viper, kanta
baya kullewa kamar da.
Babu tsammani ta yi karo da Walid, ta ja ta tsaya, ta zata
zai yi mata masifa, ta ce "Ina wuni?"
"Lafiya ƙalau"
"Amm yana ina?"
Ya nuna mata dutsen da yake can gaba, ya ce "Yana can,
amma ki daina wahalar da kanki, taurin Al'amin yayi yawa, an ɗaukko masa
wuƙarsa, zai je ya yi gaba da gaba da madaki yau, ki ƙyale shi kawai"
Ta girgiza kai ta ce "A'a, zan jarraba sa'ata"
tayi gaba ta nufi in da dutsen yake, ba ta ƙarasa ba ta hango shi, a zaune a
gefen bishiya, cikin inuwa yana ɗan kaɗa ƙafa, ya na shan sigari.
Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi ta ce "Barka da
rana" bai amsa ba, ta saka hannunta, ta zare sauran karan tabar hannunsa
ta ce "Ayi mini uzuri, ba na son hayaƙi, mara zuciya na sake dawowa. Dan
Allah kar ka shaƙe ni, magana zamu yi ta fahimtar juna"
Ya ɗaga kai ya kalleta, ya yinƙura ya miƙe, ita ma ta tashi
ta tsaya a gaban sa, ka saurare ni ko sau ɗaya ne, zafin zuciya da gaggawa shi
ya sanya ka rasa da yawan mutane masu muhimmanci a rayuwarka".
Sweazland ya saka mata a wuyanta, ya ce "Gargaɗi na
ƙarshe, ki rabu da ni, ki fita daga rayuwata".
Ta kalli yadda wuƙar ke ƙyalli a saitin wuyanta ta ce
"Sai na ji ƙarshen labarinka, na ji wa ka kashe? Kuma ina jauhar da abun
da yake cikinta?"
Ya kalleta ita ma cikin ƙwarin gwiwa ta cigaba da kallonsa,
duk da ƙasan zuciyarta a tsorace take.
"Ki daina kallona a haka, meyasa ki ke son ki zama
raunina ne?" yayi maganar muryarsa na rawa.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
"Meyasa zan zama rauninka ne? Wallahi ba cutar da kai
zan yi ba, ba na nufin yin hakan. Idan niyyata kenan a baya yanzu na canza
tunani, dan Allah ka fahimce ni".
Ya sauke numfashi ya ce "Me ki ke buƙata?"
Ta ce "To dan girman Allah mu zauna, sai mu yi magana,
ba dan ni ba"
Ya koma ya nemi wuri ya zauna, ta yi ajiyar zuciya, tare da
ƙara jinjinawa Jauhar.
Ita ma ta zauna, ya ce "Ina jinki"
"Kamar yadda na gaya maka da farko, na yi nadamar abun
da nayi, wallahi ba ni da niyyar cutar da kai ko kaɗan.
Dan Allah ka yi haƙuri, a shirye nake na taimaka maka, na
ƙwato maka hakkinka, da na matarka kai har ma da na yaronka Nura, ko hakan zai
sanya na baya su kuɓuta daga irin abun da ya faru da ku, amma hakan ba zai yiwu
ba, sai ka ƙarasa mini labarin abun da ya faru"
"Bana buƙatar taimakonki, zan yi abun da nake ganin ya
dace"
Ta girgiza kai ta ce "Bari, ɗan hakin da ka raina, shi
ka iya tsole maka ido, ni ko ba dan kowa ba, dan 'yar uwa jauhar, wallahi
labarinta kawai da na ji ta tsaye mini a rai, ina sonta saboda girman Allah,
rayuwarta abun tausayi ce kuma abar koyi, har cikin zuciyata nake jin raɗaɗin
abun da ya faru, ban rayu da ita ba, amma halayenta sun yi mini, sun burgeni
kuma duk in da na zauna, zan buga misali da su. Dan Allah ka yarda da ni, ka
bani haɗin kai"
Kallon hawayen da take yi yayi, ya ji ina ma shi ne ya samu
wannan damar, yake zubar da hawaye ya ji sanyi a ransa. Duk da yadda take ƙular
da shi, amma hawayenta ya sanya zuciyarsa motsawa, da jin kamar ya amince mata,
ko da cutar da shi za ta yi, tun da ta nuna tausayi da ƙauna ga matarsa, haƙiƙa
ta samu wani mutunci a idonsa.
Ta share hawayenta ta ce "Na bibiyi file ɗinka na
shari'a, an rubuta kisan kai ake tuhumar ka da shi, wa ka kashe? Garin yaya ka
yi kisan kai? An kama ka an sake ka, kuma an dawo ana nemanka".
Ya kaɗa kai ya ce "An bar jaki ana dukan taiki ba, sun
fuskanci ƙarfen cikin wuta ne ni, na fi ƙarfin hannu. Shekara ɗaya, biyu, uku,
huɗu, biyar, Naja'atu Bunkure" yayi maganar yana kallon yatsunsa.
Cikin zaƙuwa ta ce "Me ta yi maka?
nima da ka ji ina waya, na yi zancenta, wata yarinya aka yi
wa fyaɗe ta shiga case ɗin ta karɓa, kuma an yi wa wani dattijo sharri wai shi
yayi mata, alhalin ainihin case ɗin wani ɗan babba ne yayi, wallahi abun da ya
sanya na ambaceta kenan a maganata, ba wai aiki nake yi musu ba. Ka yi mini
magana dan Allah. Bana fatan ka ɗauki fansa ta hanyar da ba ta dace ba, ba zaka
taɓa hucewa ba, ka bari rayuwarsu ta tagyayara tukuna.
One of the biggest fear na masu mulki, shi ne rasa ƙwarin
gwiwar su daga mutane, yayin da asirinsu ya bankaɗu mutane suka daina yarda da
su. Indabo yayi ƙarfin da ka tunkare shi kai tsaye, ba zai yiwu ba.
Kisan mummuƙe yakamata ka yi masa, dan Allah ka gaya mini me
Bunkure tayi maka, hakan zai taimaka mini a wurin Shari'a".
Viper ya ce "Ba na buƙatar wata shari'a, ko wani ya
ƙwato mini hakkina, shari'a ita ta fara cin zarafina, babu komai a harkar nan
ta ku, sai zalunci da son zuciya, taimakon wanda ku ke so, da tozarta wanda ya
gaza baku kuɗi duk gaskiyar sa".
Taji daɗin yadda yake yi mata magana, dan bata taɓa zaton
yana magana haka ba.
"A'a kar ka ce haka dan Allah, Dan Allah da gaske kisan
kai kayi?"
Ya ce kalleta ido cikin ido ya ce "Eh, kisan kai nayi,
Naja'atu Bunkure made me confess it"
Ta haɗiye wani abu, ta girgiza kai ta ce "Ba zan taɓa
yadda da hakan ba, labarin Viper da na ji, bai taɓa kisan kai ba, wa ka
kashe?"
Tashi yayi, ya ɗauki wuƙarsa yayi gaba, kamar mayya ta tashi
ta bishi cikin sauri, amma saurinsa ya ninka nata, dan haka ya rigata isa cikin
gidan, kafin ta ƙarasa har ya shiga ɗaki ya rufe kansa.
Ta taga ta tsaya tana leƙawa "Dan Allah ka daina bani
bayani guntu-guntu ka ƙarasa mini, hakan zai taimaka mini wurin sanin ina zan
kama, wa ka kashe dan Allah?"
Ya tsaya ƙyam ya juya mata baya, ya dafa jikin bango,
zuciyarsa tamkar ruwa na tafasa a ƙasan gagarumar wuta, haka wani Irin zafi ya
din ga taso masa daga ƙirjinsa zuwa ƙwaƙwalwarsa.
Nabila ta din ga bubbuga ƙofar, tana yi masa magiya ya buɗe,
amma yaƙi, ta koma ta window, ta ga tuni ya fara ɗurawa kansa allura.
"Dan girman Allah ka bari, lafiyarka da ta
ƙwaƙwalwarka, wannan ba mafita ba ce ba, dan Allah kar ka illata kanka".
Liti ya ce "Zo ki fita, koma uban menene ba ke ce sila
ba, uban waye ya ce ki zo, yau ya tashi da 'yar walwala kawai kin zo kin kuma
tunzura shi".
Cike da tsananin damuwa, da tashin hankali ta baro gidan,
tana tunanin to ita menene laifinta, da suke cewa ita ce sila idan ya ganta
yake burkicewa.
***
Ramma ta zubawa Abdul ido, ya haɗa akwatin sa tsaf, ya
kalleta ya ce "Ƙarfe huɗu jirgina zai tashi, dole na shirya da wuri, akwai
in da nake son zuwa kafin na tafi"
Ta turɓune fuska, tayi masa shiru.
Ya zauna kusa da ita, ya ɗago haɓarta yana kallon fuskarta
ya ce "Ya dai?"
"Ni dai kar ka tafi dan Allah, tsoro nake ji wallahi,
nikaɗai zan zauna a nan dan Allah"
Ya kwantar da murya ya ce "You start missing me?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"Your excellency, ba iya tsoro ne a idonki ba, missing ɗina
zaki yi"
Ta ture hannunsa ta ce "Allah ya kiyaye, ni gaskiya
tsoro nake ji"
Abdul ya ce "Tafiyar nan dole ce, sannan ina son na je
garinku yau, zan ce wa mamanki kina gaisheta"
Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka mayar da ni
mana"
Ya girgiza kai ya ce "Ba yanzu ba"
"Nan gaba zaka mayar da ni?"
"Eh to, sai ƙura ta lafa" tayi shiru tana wasa da
yatsunta.
"Ki yi haƙuri, zan dinga kiranki kullum muna magana,
idan da wani abun ma sai ki gaya mini, na ajiye miki komai na amfani a kitchen,
ai kin iya girki ko?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
Ya ce "Yauwwa your excellency" ya tashi ya shiga
wanka, yana ta shiri, ya zauna a gefen gado yana shafa mai, ta riƙe shirt ɗin
sa tana kuka.
Nan ya lalace a wurin rarrashin ramma, "Wai wannan
kukan duk dan kar na tafi ne?"
"Ni ina ruwana da tafiyarka, tsoro nake ji ne"
"Ƙarya ki ke yi rahama, faɗi gaskiya dai"
"Ni ba na ƙarya" tayi maganar tana murguɗa masa
baki sannan ta ce "Kuma wallahi ka bi mata Allah ya isa" bai san
lokacin da ya ƙyaƙyace da dariya ba, har sai da ya bata haushi.
Har ƙofar falon ta rako shi, tana kallonsa, ya kasa gane
kallon me take yi masa har haka, yayi mata sallama, ya sanya mukulli ya
kulleta, ya ja akwatinsa.
***
Kan Nabila tamkar zai yi bindiga, ta rasa abun da yake yi
mata daɗi, haka ta koma jiki babu daɗi, kanta fal tunani daban daban.
Har ta shirya, zata ci abinci, kawai ta tuna kwana biyu ba
ta haɗu da Nasir ba, kuma ba ya shiga sabgarta, gashi tana son sanin a ina ya
tsaya a binciken Viper, saboda duk yadda za ayi ba ta son ya gano Viper ba ta
gama na ta binciken ba, idan ya so ko kotu za a shiga, ta shiga da ƙwarin
gwiwar ta.
Gaba ɗaya mayar da hankali a kan aikinta ya sanya, ba ta
shiga sabgar yan gidan, hakan ya rage yawan faɗace-faɗace da suke yi da 'yan
gidan.
Ta fito falo, dan ta gaji da zaman ɗaki, abubuwa duk sun
dameta, sai ga Nasir yayi sallama a falo, ta amsa sallamar tana kallon sa, amma
ya basar da ita ya nemi wuri ya zauna.
Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi ta ce "Sannu da
zuwa"
"Yauwwa" ya amsa mata a ciki.
"Wai me na yi maka ne ka ke wani share ni?" Tayi
maganar a shagwaɓe.
Rasa me zai ce mata yayi, yai shiru, ya kawar da kansa gefe.
Ta zagaya in da ya kawar da kan ta ce "Me na yi
ne?"
"Bakomai". "To ka kula ni mana".
Nasir ya ce "Na gaji, kar ki dame ni dan Allah"
"Sai na gaya wa Abba kana hantarata"
Ya ce "Sai kin dawo" ta rausayar da kai ta ce
"To ni dai ka yi haƙuri, dan Allah" ya kalleta ya ce "Ya
wuce"
"Yauwwa DSP, to ya ake ciki ya aikin?" Ya gyara
zamansa ya ce "Alhamdilillah, mu na ta fama ya naki?"
Ta kwaɓe baki ta ce "Babu daɗi, duk na gaji, da fa
ajiye aikin zan yi, aka bani haƙuri" Nan ta bashi labarin abun da
barrister Kabir yayi mata.
Nasir ya ce "Ke baki da haƙuri ne, shiyasa wasu lokutan
ba kya cin ribar abubuwa, ki daina gaggawa"
"Ai abun ne ya bani mamaki, daga zuwana wurinta, har an
kira barrister Kabir an gaya masa, baka ga abun da ya yi mini ba, da cewa na yi
sai na gaya wa Abba ma".
Nasir ya ce "No, ba za ayi haka ba, duk abun alkhairin
da yake yi miki, sai a kan laifi ɗaya ki yi fushi"
"To meyasa zai yi mini tijara a kan wata Naja".
Ya ce "Hakan yana alamta miki cewa, kin ɗaukko
gagarumin abin da sai kin yi kyakywan shiri na gaske".
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Haka ne, ya ake ciki da naka
aikin, yaya batun case ɗin Viper, akwai cigaba kuwa?"
"Wallahi ba wani cigaban kirki, ina da ta fafutuka,
gashi sai hura mini wuta ake yi"
"Kai abun babu daɗi, but you can do it, na yarda da kai
ai".
Mama ce ta fito fuska a haɗe ta ce "Nasir menene
haka?"
Ya ce "Mama a ina?"
"Ban sani ba, uban me ka ke zaune a nan ka ke yi? Ka
dawo gida tun ɗazu, amma ka gagara shiga inda nake?"
Nasir ya ce "Wallahi nayi tunanin bacci ki ke yi,
shiyasa na yada zango a nan muke magana da Arfa, yi haƙuri"
Nabila ko a jikinta, ta sake gyara zamanta ta kwanta sosai a
kan kujerar tana danna waya.
Mama tayi mata wani mugun kallo, ko a jikinta, sai ma wani
irin murmushi da tayi.
Messages aka din ga turowa Viper, da private numbrn nan, da
ake kiransa da ita.
"Muddin ka cigaba da biyewa yarinyar nan, asirinka zai
tonu, kuma zata iya rasa rayuwarta a dalilinka, ba ka da sa'a wasu lokutan, kar
ka bari ta zama raunin da maƙiyanka za su yi amfani da ita, wurin cimmaka har
maɓoyarka" Ya din ga jujjuya wayar, yana sake tunanin waye wannan, kowaye
ya sanshi, ya kuma san in da yake, kuma yana ankare da duk abun da yake yi,
amma meyasa yaƙi bayyana kansa?.
Kiran Nabila ne ya shigo wayarsa,
tana zaune hannunta riƙe da waya a kunnenta tana kiran
lambarsa, babu tsammani ta ji ya ɗaga.
Ta kalli agogon ɗakinta, ƙarfe goma daidai na dare.
"Barka da dare, duk da ba amsawa zaka yi wa ba. Amma
ina fatan kana lafiya?
Na kasa jurewa ba zan ɓoye maka ba, ban ji daɗin yadda na
baro ka ba, muna cikin magana ka tashi ka tafi, kuma ka je ka na yi wa kanka
allura, gaba ɗaya ban ji daɗi ba, dan girman Allah ka rufa mini asiri kar ka yi
wa kanka illa, ka bari mu yi nasara mu kamo bakin zaren. Na san maybe ka raina
gogewa ta, kuma kamar ba zan iya ƙwato maka hakkinka ba, amma na san Allah yana
tare da mu, dan Allah ka daina shan abun da zai yi maka illa, ba na jin daɗi,
na san yayata ma 'yar madara ba zata ji daɗin hakan ba, dan gaskiya sai ta
matsa mini na shigo, daga ni sai a rufe. Saboda son da nake yi mata make son mu
kasance tare, idan na shiga gidanta, kaga gani ga ta, in ƙara koyon halayenta,
in ƙara sonta, amma gaskiya ayi mana adalci, saboda kishi ne da ni sosai da
sosai fa, kuma alamu sun nuna mini kana sonta da yawa"
Kamar mai sauraren karatu, haka ya nutsu yana jin ta, ɗan
mama da yake kusa da shi, har kuma leƙa idonsa yake yi, ya ga reaction ɗin da
zai yi, tare da jinjina rawar kan Nabila, a gaban Viper ko ƙwaƙwaran motsi ba
ta iya yi, amma ta sameshi a waya, sai karairaya take yi tana shagwaɓa.
Ta sauke numfashi ta ce "Bari na ƙyaleka, amma yakamata
na san ƙarshen labarin nan, saboda na san yanayin shirin da zan yi, kuma kar
sai na gama zaƙewa 'yar madara duk kirkinta ta ce ba zan shigo mata gida ba,
dan ni gaskiya idan ba gidanta ba sai rijiya. Sai da safe take care" tayi
maganar tana ajiye wayar, cikinta na kaɗawa saboda ita kanta ta san ba ƙaramar
kasada take yi ba, abun da take yi. Amma hanyar da matarsa ta bi ta iya samun
kansa da farko, dole ita ma ta bi, domin cimma nasara, saboda gaba ɗayansa
hukuma ne, sai da rarrashi.
***
Sanye yake da face mask, yana tuƙi a hankali, saboda yadda
hanyar ta ƙara lalacewa, a ƙofar gidan su ramma yayi parking, ya fito ya tsaya
a waje yayi sallama, amma shiru, ya shiga cikin gidan sai dai tsakar gidan babu
kowa, ƙofofin ɗakin duk a buɗe.
Ya ɗan jira ko za a shigo, ko fita tayi, amma shiru, ba ta
dawo ba.
Ya fita ya tambayi maƙwabta, suka sanar masa kwanaki huɗu
kenan, su ma ba su san in da ta tafi ba, ba ta yi wa kowa sallama ba.
Yanayin gidan ya tabattar masa da ba fitar nutsuwa tayi ba,
ya lissafa shi yanzu kwanaki uku kenan, da mahaifinsa ya kira shi yai masa
magana a kan batun ramma balle ya ce ko mahaifinsa ne.
Yayi shiru yana tunanin to garin yaya haka, ya za ayi ta
fita ta bar gida a buɗe haka babu kowa, tsawon kwanaki huɗu, ba ta yi wa kowa
sallama ba, lallai akwai wani abu a ƙasa, yanzu me zai cewa ramma? Ya tambayi
kansa.
Lallai akwai wani abu a ƙasa, gashi lokaci na nema ya ƙure
masa, ƙarfe huɗu zai tafi.
Saif ya kira a waya, ya sanar masa halin da ake ciki, saif
ya ce "Kuma baka tunanin ko guduwa tayi, ko kuma daddy ne yayi mata wani
abun?"
Abdul ya ce "Bana tunanin haka, shekaranjiya yayi mini
zancenta, da shi ya saka aka ɗauke ta zai gaya mini, na rasa wani lissafin ma
yakamata na yi"
Saifu ya ce "Ka tafi kawai, zan tsaya na sake
bincikawa, in Allah ya yadda ba wani abu".
Ya ce "To shikenan, ina saurarenka dan Allah" ya
ajiye wayar yana cigaba da tunanin lamarin.
***
Abdul yana sauka a Abuja, sai da ya kira Ramma, ya ce mata
ya sauka, sai dai ba ta amsa masa ba sai cewa tayi "Yaya ka baro mini
mama? Tana nan lafiya? Ta tambaye ka yaya nake?"
"Ni ba zaki tambayi ya na sauka ba, sai mama
kawai?"
"Dan Allah ka gaya mini, ko na ji daɗi"
Abdul ya ce "Zan gaya miki da daddare idan na
huta" ya katse wayar yana fargabar ranar da ramma ta san halin da ake
ciki, bai san ya zai yi ba. Ya san duk laifin shi zata ɗorawa.
***
Katafaren falo ne, ya sha ado da kayan alatu na zamani,
manyan mutane ne su uku, zaune a falon wanda kaf ɗin su sanannun fuskoki ne da
su a ƙasa.
Kayan shaye-shaye ne a gaban su, suna sha suna hira, gefe ga
kayan marmari.
"Distinguish ma'aruf Indabo, ya ake ciki ne gaba ɗaya
baka walwala?"
"Komai ma ya dame ni ne, Abdul sai so yake yi sai ya
watsa mini lissafi, da ƙyar na yaƙo shi, ya tafi Abuja, zaman taron nan, nima
gobe in Allah ya kaimu zan tafi birnin tarayyar"
"Ya salam, wai meyasa Abdul yake haka ne? Ya san
wahalar da muka yi kuwa kafin mu zo nan, shi me yake damunsa ne?"
Indabo ya kora ruwan lemon da yake cikin kofin hannunsa, ya
ce "Oho masa, gaba ɗaya na kasa gane kansa, ina tsoron Allah ina tsoron ya
aikata wani abun da zai yi dalilin takarar nan, amma ina nan na kafa na tsre
ina monitoring activities ɗin sa".
"Ohh Allah ya kyauta, ya batun wannan yaron ne da ake
nema?"
Indabo ya girgiza kai ya ce "Hmm honorable kenan,
wallahi kullum da shi nake kwana nake tashi, kamar wani iblishi, ya gagara
kamuwa, na rasa uban da yake tsaya masa, sai dai na samo wata yarinya da nake
son ayi masa tarko da ita, to ita kanta yarinyar ba ta da cikakken saiti, wata
barrister ce, 'yar wani tsohon soja, idan na matsa zata iya tona mana asiri, na
saka ana yi mini monitoring ɗin ta, ta hanyar ƙawarta. Saboda wani furuci da
tayi. Duk dai na ga hanyoyin ba sa yi mini sauri, na san dole yaron nan bakam
yayi mini, at any cost sai na canza dabara, wadda za ta ɓulle mini da wuri, na
kashe Aminu na huta"
Haka suka cigaba da jimantawa, tare da tattaunawa da neman
mafita, suna yi suna shaye-shaye.
Ramma tana duƙunƙune a cikin bargo, karnukan estate ɗin, da
na gidan sai haushi suke yi.
Video call suke yi da Abdul, ta ce "Ba ka ce mini komai
a kan mama ba"
"Mama tana lafiya, ta ce a gaishe ki"
Ta ce "Hmm, to ya take, tana cikin damuwa ko? Tayi
kuka?"
Ya ce "A'a, na bata tabbacin kina nan lafiya, har
hotonki na nuna mata"
Ramma ta ce "A'a hankalinta ba zai taɓa kwanciya ba, ka
manta rashin ɗa'ar da ka yi mata, ranar da ka je ka tabattar mata da kai ka
keta mini haddi, kuma ka tafi da ni, ai a yanzu idan akwai wanda ta tsana bai
wuce ka ba, kodayeke akwai wanda suka yi mata wasu laifuffukan"
Yayi shiru jiki a sanyaye ya ce "Laifin da suka yi mata
irin nawa ne? Ai na nemi afuwarta"
"Ta ina ka nemi afuwarta? Hmm ta ce ta yafe maka ne?
Kai baka ganin girman laifin da ka aikata fa saboda mu talakawa ne kana da kuɗi.
Mama ta sha wahala sosai, gashi duk mun ɗaiɗaice, kaga
ƙanina sani daka je?"
Ya girgiza mata kai ya ce "Ina ga yana makaranta"
"Shikenan, sai da safe, bari na rintse idona ko zan yi
bacci, haushin karnukan nan ya isheni"
Ya ce "Ni kuma sanyi ne nan ya dame ni, da muna tare da
kin bani ɗumin jikinki"
Cikin tsiwa ta ce "Saboda gani heater ko?"
Ya ce "No, jikinki akwai ɗumi sosai, da duk ba zan ji
wannan sanyin ba"
"Sai da safe"
"Dan Allah ki tsaya ban gama ganinki ba"
ta ce "Sai kuma ka yi ai"
"Miƙo bakinki na yi miki kiss"
"Ba na so" tayi maganar bacci yana kwasarta, tana
lumshe ido.
Ya ce "Rahama"
"Na'am" ta amsa tana buɗe ido da kyar. Sai kuma
yayi shiru yana cigaba da kallon fuskarta, har bacci ya kwasheta, yana
kallonta, tausayinta ya din ga ratsa zuciyarsa.
***
Yau weekends, Nabila tana gida, tana kai komonta, ta bayar
da wankinta ayi mata, ta fito harabar gidan tana zagawa, Nasir ya fito da
shirin fita.
"DSP sai ina? Ko zance za a tafi rana tsaka"
"Wurinki zan zo zancen" tayi dariya ta ƙarasa
gabansa ta ce "Ina zuwa yanzu?, La'asar ta kusa?"
Ya kalli agogon hannunsa ya ce "A kan Viper ne"
Cikinta yayi ƙuuu, amma ta maze ta ce "Ya ake
ciki?"
Ya ce "Eh to, na canza dabara ne, a yanayin neman nasa,
mun riga duk mun yi connecting da mutanen unguwar su, an ce yana zuwa gidansa
da ya zauna, to kwana biyu bai je ba. Abokin faɗansa da na kama kwanaki madaki,
an ce ya dawo yana cikin gari, akwai ƙishin-ƙishin na zai iya zuwa unguwar,
neman rigima da shi madakin, duk mun baza komar mu, akwai wurin shayin yaransa,
an ce ma wurin nasa ne, zuwana biyu wurin cikin fararen kaya, an kwatanta mini
wani yaronsa Walid, na haɗu da shi a wurin, amma ko kaɗan ba sa zancensa a
wurin. Da na so na zunguro zancen daba ma, na kama sunansa, cewa suka yi na
tashi na fita. Ina kyautata zaton wannan Walid ɗin ya san in da yake, motsinsa
zan sakawa ido sosai, ana ta yi mini binciken ina yake da zama, da a unguwar
suke zaune, amma tun da Viper ya bar prison, sun daina kwana a unguwar sai idan
za su yi aikin rabawa ƙanan dealolinsu wiwi. Ba zan motsa da wuri na kama shi
Walid ɗin ba ba, kar shi ma ya zille mini, kuma an tabattar mini da ɗan amanrsa
ne, ina dai ta bibiyar su ta hanyar mai unguwa, da wasu daga mutanen
unguwa. Wanda nake baki labarin nan ma ɗan mama, ya daina zuwa arear da aka
gaya mini kai kayan shaye-shayen na su, abun ne dai duk sai a hankali".
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Wani aiki sai mai shi, Allah
dai ya ba da sa'a, sannu da ƙoƙari DSP"
"Yauwwa arfan Abba, bari na tafi"
"To yanzu can ɗin zaka tafi?"
"Eh, zan je in sake zaɓar yarana su shiga unguwar su
madakin a farin kaya"
Ta ce "Shikenan, a sauka lafiya, Allah ya tsare"
ya amsa da Amin, ya nufi motarsa.
Cikin sassarfa, ta nufi ɗakinta, Wayar Viper taƙi shiga, ta
din ga kira amma a kashe.
Hankalinta ya ƙara mummunan tashi, har la'asar wayar viper
ba ta shiga.
Shiryawa tayi ta saka niƙab, ta lallaɓa ta fice, ba tare da
yi wa kowa sallama ba.
Sauri take yi tamkar za ta tashi sama haka take fafaka
sauri.
A hanya aka fara kiraye-kirayen sallar la'asar, har ta
ƙarasa kiran lambarsa take yi, amma shiru bai ɗaga ba.
Ɗan mama ta tarar a tsakar gida, shikaɗai, yana ta shafawa
wuƙaƙe wani abu, da ba ta san ko mene ne b. Ya miƙe yana kallonta ya ce
"Dan Allah suna ina?"
"Su wa?"
"Su viper, da sauran".
Ɗan mama ya ce "Oga Viper ya fita, ya tafi cikin gari
wurin madaki, da shi da Oga liti, Oga walid sun yi faɗa ya fita"
Jikinta na rawa ta ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un, shi Walid ɗin ina ya tafi? Wai ma meyasa Vipern ne yake da taurin kan
tsiya, akwai hatsari a hakan fa "
"Ke, Oga Vipern ki ke faɗar baƙar magana a kan
shi?"
Ta juya zata fita ya ce "Ina zaki?"
"Bin sa zan yi"
Ya waro ido ya ce "Ina?"
Ta tsaya ta kalleshi ta ce "Dabar madakin, ai na san
wurin" zai yi magana, ta fita da sauri sosai.
Shida saura na yamma, ta isa unguwar su madaki, saboda
azalzalar da ta din ga yi wa mai adaidaita sahun da ta hau.
Ta cikin niƙabinta, take kallon unguwar, ba zata taɓa manta,
yadda aka sakar mata karnuka ba, suka kusa cinyeta.
Ta nufi cikin unguwar, sai dai kamar babu mutane, sai ɗaiɗaikun
mutane da suke guje-guje.
Ta tsaya tana neman wand zata tambaya meyake faruwa, amma
kusan kowa ta kansa yake yi.
"Kai ku tafi gida, wannan ɗan tijarar ne ya shigo neman
masifa, mai zamani ne da yaransa, suke faɗa da yaran madaki" taji muryar
wani matashi, yana yi wa wasu yara magana" maimakon ta tsorata sai ta
kutsa kai ta cigaba da tafiya tana fatan Ubangiji Allah ya sa kar wani abu ya
same shi, Allah ya sa ta ganshi.
Tana saka kai wani layi, ta ga an yanki wani a cinyarsa,
jini ya yi tsartuwa, ta gigice cikin tashin hankali ta fara ihu, ji tayi an ja
hannunta da ƙarfi, an shiga da ita wani layi daban.
Ayshercool
0808012143
Cikin matsanancin tsoro, ta rintse idanunta, zuciyarta na
bugawa da sauri sosai.
Da kyar ta iya buɗe ido ta ga wanda ya ja ta, kallo ɗaya ta
yi wa idanunsa ta cire nata, saboda mugun kallon da yake yi mata.
"Uban me ya kawo ki nan?" Mamaki take yi, yaya aka
yi ya ganeta da niƙab.
"Ba magana nake yi miki ba?"
Ta ɗaga kai ta kalleshi ta ce "Haka muka yi da kai?
Meyasa zaka fito, kana da tabbacin idan suka kamaka a wannan karon zasu barka
da rai ne, ba fa za su yadda su sake wannan kuskuren ba, dan Allah kar ka ɓata
mini aiki, dan Allah ka daina fitowa" mayafin da ya rufe fuskarsa da shi,
ya sake gyarawa, ya sake damƙar hannunta, ya din ga ratsa hanya da ita, kowa ya
gudu gida ya ɓuya.
A haka suka ƙaraso titi ya ɗaga wa wani mai baburin
adaidaita sahu hannu, ya yi mata nuni ta shiga, shi ma ya shiga.
Ta kalli yadda duhun magariba yayi, sai a lokacin hankalinta
ya kai kan me za ta ce a gida.
Ya ciro wayarsa, ya danna wata lamba, ya saka a kunnensa, a
hankali yake magana ba ta iya jin me yake cewa a wayar, ya zirawa mai
napep ɗin dubu ɗaya ya kama ƙarfen adaidaita sahun, ya dire ba tare da mai
napep ɗin ya tsaya ba.
Cikin sauri ta leƙa, ta ga wani ya tsaya a babur sanye da
face mask, Viper ya hau suka yi wani wurin.
Tana jin yadda wayarta take ta ringing, amma taƙi ko ɗaukkota,
balle ta ga waye.
Ta gaya wa mai napep in da zai kaita, tuni aka fara
kiraye-kirayen sallar isha'ai, motar Abba ta tarar da ta Nasir, alamar duk suna
gida, gabanta ya faɗi.
Sannu a hankali ta ƙarasa falon, ta tarar da Abba a tsaye,
hannunsa riƙe da waya, take wayarta ta hau vibrating alamar ita yake kira a
waya.
Yayi mta wani irin kallo, da sai da hantar cikinta ta kaɗa.
"Daga ina ki ke?"
Tayi tsuru-tsuru da ido, tana kallonsa.
Nasir ya ce "Magana fa ake yi miki"
"Amm, Abba dama wallahi wata shaida nake so na haɗu da
ita, wani case ne a hannuna shiyasa na fita".
Abba ya ce "Wa ki ka gaya wa zaki fita?"
Mama ta ce "Yaushe za ta gaya mana, tun da bamu isa
ba"
"Wato arfa kullum rashin jinki ƙara gaba yake yi ko?
Idan baki yi wasa ba, hatta aikin sai na hana ki zuwa, an ce tun safe ba kya
gidan nan, wace irin shaida ce haka?"
Nasir ya ce "A'a har azahar tana nan ina ga da la'asar
ta fita"
"Koma menene yanzu yakamata ta shigo gida, ƙarfe takwas
da wani abu tun la'asar?"
Ta sunkuyar da kai ta ce "Dan Allah Abba ka yi haƙuri,
in sha Allah ba zan sake ba"
"Daga yau, ki ka sake fita babu wanda ya sani, zamu
gauraya da ke" ta jinjina masa kai, ta wuce tana yi wa Allah godiya, da
bai yi mata faɗa sosai ba.
Addu'a ta din ga yi, Allah ya sa kar Viper ya aikata wani
abu da za a kama shi, ko kuma ya yi wa kansa illa.
Gashi ba ta samu sun yi magana a kan abun da ya kaita ba, na
shirin da Nasir yake yi na son kama shi ta hanyar Walid ba.
Madaki ne a tsaye yana kallon Al'amin da yake tsaye a
gabansa, duk da duhun dare ne, amma manyan fitilun solar sun haske ko ina da
ina.
Idon Al'amin kamar ana hura wuta, Madaki yayi dariya ya ce
"Mahadi mai dogon zamani, ka ci na wasu gaka kana cin naka. Viper ka ke
maciji mai hatsarin gaske, dodon cinnaku masu ƙaryar kaki.
Barka da sake haɗuwa da kai a dai-dai wannan lokaci, bayan
dogon lokaci bamu yi ido da ido.
Tabbas labarin Mai zamani ba zai taɓa cika ba, sai an ambaci
madaki.
Maza gumbar dutse ya ake ciki ne?"
Yana rufe bakinsa, Al'amin ya soka masa russia a cinyarsa, a
take jini ya fara kwarara a jikin madaki. Madaki ya kalli cinyarsa, ya kalli
Al'amin.
Al'amin ya kalli madaki ya ce "Na san zaka yi mamakin,
yaushe na samu makarin tsafinka, amma na ƙyaleka a raye kana cin karenka babu
babbaka.
Yadda daba ta bar mini mugun tabo a zuciyata, ka rubuta ka
ajiye, kamar yadda ka ce labarin Viper ba zai cika ba, sai an ambaci sunanka.
Ina mai tabbatar maka Viper zai yi maka saran da bai taɓa yi wa wani irinsa ba.
Kamar yadda ka canje ni, ka ke yi wa Indabo aiki, a
madadina, ina da saƙon da zan baka ka bashi. Ka gaya masa ya toshe dukkanin
ramukan da ke gidansa, ofishin sa da duk wani wuri da yake zuwa, saboda maciji
ba ya raina ƙofa komai ƙanƙantarta, kuma ya tsammace ni, ta in da bai taɓa zata
ba, kuma lokacin da bai taɓa zato ba.
Al'amin na rufe bakinsa, madaki ya saka masa ƙarfe a
damtsensa, a take kokawa ta kaure a tsakanin su, sai dai madaki ya kasa sarrafa
ƙafar da Viper ya soka masa wuƙa, rabon da a zubar masa da jini har ya manta,
saboda laƙanin taurin da yake amfani da shi, fitar masa da jinin da Al'amin
yayi, yana nufin laƙanin ya karye, kuma a kowane lokaci, ana iya yi masa rauni
da ƙarfe koma a kashe shi.
Sosai suka din ga yi wa junansu illa da makami, sai dai
Madaki ya fara galabaita, dan haka ya fara ƙoƙarin guduwa, dan ba ya son wasu
su farga cewar ƙarfe ya fara tasiri a jikinsa.
Amma Viper ya hana shi yin hakan, zuciyarsa ta din ga wata
irin tafasa, ya din ga saran madaki, madaki ya saka hannu ya shaƙe Viper, take
Viper ya ji abun da ya taɓa ji idan madaki ya shaƙe shi, tamkar an yi masa
sarƙa da dutse, ya kasa motsi.
Viper ya ji an saka masa wani abu a gefen wuyansa, a take ya
silale ya ya faɗi ƙasa.
Madaki ya ja da baya yana kallon yadd mutumin ya saita shi
da bingida, dan bai ga ta in da ya ɓullo ba.
"Zaka iya tafiya" mutumin yayi magana yana nuna
masa hanya.
Madaki ya ja jiki da kyar, yana ɗingisa ƙafa ya bar wurin.
Wasu mutane manya manya majiya ƙarfi suka ɓullo wurin
"Yaya kun tarwatsa yaran?"
"Eh sir, amma fa har an sanar da 'yan sanda zancen
rikicin sun taho"
"Maza maza ku ɗauke shi ku tafi da shi, ayi masa
treatment, ayi sedating ɗin sa, har a gama yi masa komai, kar ku mayar da shi
maɓoyarsa yanzu, a bari zuwa da safe, idan yaransa sun fita nemansa sai ku
mayar da shi. Su kuma su musa su tabattar sun goge duk wani trace da zai sanya
a gane yazo unguwar nan"
"Ok sir"
Suka cicciɓi Al'amin, suka saka shi a mota, suka ɗauki
wuƙarsa da wayarsa, suka tafi.
Har wajen goma na dare, Nabila tana kiran wayar Viper, amma
ba ya ɗagawa, hankalinta ya fara tashi, ko wani abu ne ya same shi, amma sai ta
tuna, kaɗan da aikinsa ya ƙi ɗagawa mussaman ma da tayi masa laifi yau.
Liti kuwa bayan ƙura ta lafa, ya koma gida, sai dai bai
tarar da Viper ba, sai Walid.
"Wai Viper bai dawo ba?" Yayi maganar yana kallon
Walid.
Walid yayi masa banza.
"Malam magana nake yi maka fa"
"Ban sani ba, da ni kuka fita?"
Liti yayi tsaki ya ce "Bari na san yana hanya shi da ɗan
mama"
Walid ya ce "Ina fatan kun kashe madaki, kun wuce kun
kashe Indabo"
"Ban sani ba"
Walid ya girgiza kai, ya cigaba da abun da yake yi.
Ɗan mama ya shigo shi ma, jikinsa duk jini da alama yayi ɓarna
sosai, ya ce "Oga liti ina Vipern, ina fatan yana lafiya, ni fa tun da
muka afkawa su lakwari, ban sake ganinsa ba"
Liti ya tashi tsaye ya ce "Kamar yaya? Ya haɗu da
madakin ne?"
"Ai ban sani ba, da muka rabu da ku, wani wurin yayi
ai"
"Bari mu jira nan da awa ɗaya mu gani"
Walid ya ce "Hmm"
"To yana nan lafiya, ai ba wani abun ne ya same shi
ba"
Walid ya ce "Na yi maka magana ne?"
"To kama yi mana"
Walid ya ce "Wallahi wani abun ya same shi, sai ranka
ya ɓaci liti, daga kai har ɗan mama muguwar kasada cw da ganganci abun da ku ka
biye masa ku ka yi. Kuma tun da ya kai i yanzu, akwai abun da yake faruwa gara
kawai" yayi maganar yana miƙewa tsaye, ya ɗauki wuƙa ya soke a jikinsa, ya
fice.
"Ɗan mama, Walid fa gaskiya ya faɗa anya ba wani abun
ne ya faru ba?"
"Tashi mu koma, akwai matsala mun yi wauta da muka bar
shi ya yi mana wayo, da ƙyar idan bai haɗu da madaki ba" haka suma suka
tashi, suka fita.
DSP Nasir da kansa ya jagoranci tafiya unguwar su madaki,
bayan kiran da suka samu daga mai unguwa, sai dai da suka je ba su tarar da
kowa ba.
Duk ga alamu nan na faɗan dabar an yi, dan 'yan unguwar sun
tabattar da hakan.
Da safe Nabila har ta gama shirinta, baya ɗaga wayarta, tana
zaune tana karyawa, ta shiga what's app tana duba messages, sai ga wani saƙo,
an turo mata wani voice message, amma bayan an turo lambar tayi blocking ɗin
ta.
"Dan Allah ku taimaka mini, a ƙwato mini hakkina, an yi
wa ɗiyata fyaɗe, na nemi a bini hakkinmu a kotu, amma wata Naja'atu Bunkure ta
ce mana ita lawyer ce, ta ce zata taimake mu, amma wai sai mun janye ƙorafinmu,
ko mu haƙura wanda yayi laifin yafi ƙarfinmu.
Tayi mana tayin kuɗi bamu karɓa ba, yaron ya zo har gida, ya
ci mini mutunci, ya ɗauke mini ramma ya tafi da ita ta ƙarfin tsiya, ban san
ina ya kai mini 'ya ba, ya dawo ya karɓi kayanta, wai nayi haƙuri ta zama tasa.
Ban san meyake nufi ba, dan girman Allah a bi mini hakkina, a nemo mini 'ya ta
bani da ƙarfin ja da su, ni talaka ce, amma dan Allah a dawo mini da 'ya ta mu
ji da ciwo ɗaya na keta mata haddi da yayi, ku taimaka mini dan Allah"
matar ta ƙarasa maganar tana kuka. Da sauri Nabila ta tashi tsaye, ta din ga
kunna voice ɗin tana saurare, wani irin gumi ya fara tsatstsafo mata, ba ta
raba ɗaya biyu, wannan Muryar babar ramma ce, ita ce Muryar da aka saka a
radion su Sumayya.
"To amma waye ya turo mata voice ɗin?" Ta tambayi
kanta.
Buɗe ƙofar office ɗin da aka yi ne, ya sanya ta ɗan nutsu.
Mutumin nan ne da yake zuwa wurin Barrister kabir, babban
mutum ne sosai.
"Na shigo ko na koma a nema mini iso?"
Ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Bisimillah"
Ya shigo ya zauna, ta ɗan risuna ta ce "Sannu da zuwa
sir".
"Yauwwa barrister Nabila, ya kike ya aiki?"
"Alhamdilillah"
Ya ce "Masha Allah, ai na yi wa Kabir magana, shi ya
bani numbernki, kuma na kira kin ce sai na zo office" ta waro ido ta ce
"Dama kai ne? Yi haƙuri dan Allah, ban sani ba na zata kawai masu haɗa
lamba ne"
Yayi murmushi ya ce "Kar ki damu, hakan yana da kyau
ai, ai mace da aji aka santa.
Sunana Wada M karofi, maybe kina ɗan jin sunana"
Tayi murmushi ta ce "Oh yes, dama kai ne M
karofi?" Ya jinjina mata kai ya ce "Eh barrister, ina son ki zama ɗaya
daga cikin lawyoyina, masu kula mini da dukiyata da kadarorina, ina biya sosai,
na yaba da nutsuwarki, na ce da ganinki zaki yi amana, na yi magana da
barrister Kabir ya ƙara bani tabbacin hakan".
Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Haka ne, amma am very sorry
sir, ni bana son irin wannan, a bar ni a hakana kawai"
Yayi murmushi ya ce "A bar ki a hakanki anya kuwa? To
shikenan idan ba za a kula da dukiyata ba, to ni a kula da ni mana" yayi
maganar yana kallon ta.
Murmushi ta yi tana girgiza kai ta ce "Haba sir, manya
ba sa haka fa"
"Subhanallah, na yi miki tsufa kenan?"
"A'a ban ce ba, namiji ai baya tsufa"
"To shikenan, zamu yi waya, bari na barki ki yi
aikinki, idan ta kama ma sai na zo gida"
"To Allah ya kawo ka lafiya ya tsare"
"Amin Barrister na, ga wannan ki sha ruwan roba, ba na
leda ba" yayi maganar yana ajiye mata kuɗi a kan tebur"
"Ina fatan ba cin hanci ka bani ba, hakan ba zai hana
in ta kama na saka alƙali ya ɗaure mini kai ba"ta yi maganar tana
kallonsa.
Ya yi dariya ya ce "Funny you, ni na isa, ayi aiki
lafiya" ya fita yana murmushi.
Yana fita ta ɗauki kuɗin ta ce "Alhamdilillah, tsuntsu
daga sama gasashe, Allah ya kawo amanar baban wasu hannuna, na samu mai zuba
mini mai idan mota ta iso" da sauri ta zube kuɗin, ta sake ɗaukar wayarta,
ta sake jin voice message ɗin nan, tayi sauri tayi saving ɗin sa a gmail ɗin
ta, dan kar ya ɓata.
Kamar ta turawa Sumayya, sai kuma ta fasa.
***
Ramma na kan dining tana karyawa, ta jingine waya tana
kallon Abdul da shi ma karyawa yake yi.
"Rahama kin taɓa gaishe ni kuwa?"
"Waye ɗi na kai da zan gaisheka?"
"Your life saver mana, yadda na ceci rayuwarki, da ki
ka kusa mutuwa"
"A'a da ka sha giya dai ka kusa kashe ni"
Ya sosa kansa ya ce "Ke abu ba ya wucewa ne, sorry
mana"
Ta harare shi ta ce "An ƙi ayi sorryn"
Ya kashingiɗa ya ce "Ɗan cire hannunki, na din ga gani
sosai"
Cikin rashin fahimta ta ce "Ka ga me?"
Ya ɗaga girarsa yana nuna mata ƙirjinta.
"Wallahi Abdul ka ɗuma asara, kai a duniya abu ɗaya
Allah ya saka maka a cikin kanka ne? Haba mana"
"Future governor ki ke gaya wa haka? Zan fa hanaki
first lady, kodayeke wadda zan aura ce zata zama first lady, ke kuma maid ɗin
ta" tayi shiru, tana tauna cornflakes.
"Ki lallaɓa ni na dawo da wuri"
A fusace ta ce "Kar Allah ya sa ka dawo ɗin, in sha
Allah ka tafi kenan, ko jirgin ya faɗi, kai kaɗai ka mutu"
Yayi dariya ya ce "Kin ga sai ki mutu kekaɗai a gidan
nan ba, dan babu wanda ya san na ajiye ki a ciki. Gara ki yi sauri ki janye
addu'ar ki, idan kina son ki fita"
Ajiye kofin tayi, ta fashe da kuka, har da sheshsheƙa.
Ya ce "Is ok, ke ce ba ayi miki abu, sai ki yi ta tsine
mini, ina jin pain fa, am sorry ya isa haka, haba your excellency"
maimakon ta yi shiru, sai ma ta ƙara sautin kukan, nan da nan ya rikice, ya hau
bata haƙuri, amma tayi disconnecting kiran, ta cigaba da kuka.
Ta ɗauki wayar, tun da ya tafi, take gwada kiran lambobi
daban-daban, amma ba ta tafiya sai ta sa kawai. Ta dudduba ko ina, ko da hanyar
da za ta iya guduwa, amma babu ga wata irin kewar mama da sani ƙaninta da take
yi.
Su liti tamkar za su yi hauka, gaba ɗaya suka rikice, da
Viper bai kwana a gida ba, duk in da suke tunanin za su ganshi ba su same shi
ba. Har gidansa Walid ya je, ya haura ta katanga, ya shiga amma ba su same shi
ba, gashi madakin da aka ce ya zo yana unguwar, shi ma yayi ɓatan dabo, an neme
shi an rasa.
Gaba ɗaya hankalinsu ya tashi, mussaman liti, amma saboda
tsananin ƙi faɗi, yaƙi yarda ya karɓi laifin, Walid ya din ga yi musu luguden
ashariya daga shi har ɗan mama, suka yi masa shiru suka ƙi kula shi.
A sukwane Nabila ta tashi daga wurin aiki, bayan cin karo da
batun faɗan daba a tsakanin yaran madaki da na Viper, sai dai babu ɗaya daga
cikin su da ya zo hannu, tsakanin Viper da madaki, al'ummar unguwar na cigaba
da zaman ɗar-ɗar, sakamon rashin tsaro.
Ofishin Nasir ta tafi, babu sanarwa sai ganinta yayi, sai da
hankalinsa ya tashi ya ce "Arfa lafiya kuwa?"
Ta ciro wayarta ta nuna masa posting ɗin.
Ya ce "To wannan ne ya saka ki ka taho har nan?"
Ta ce "Eh, na yi zaton baka sani bane"
Ya girgiza kai ya ce 'No, na sani"
"To yaya ake ciki?" Ya ɗan tsareta da idanunsa
sannan ya ce "Ni duk kin ruɗa ni, ko kece ke binciken nan, sai haka Arfa.
Na je, sun yi faɗan daba, amma babu tabbacin yazo".
"Baka kama shi ba kenan?" Ya jinjina mata kai
alamar eh.
"To ko yaran nasa ba ka kama ba?"
"Lokacin da muka je, sun yi sun watse" wata irin ɓoyayyiyar
ajiyar zuciya ta yi, sannan ta ce "To shikenan, ai ban zaci ka gani ba,
shiyasa na zo da kaina, bari na tafi"
Nasir ya ce "Yanzu mussman ki ka baro aikinki ki ka zo
kawo mini rahoto, arfa mai abun mamaki, zauna na gama abun da nake yi, na rage
miki hanya"
Ta ce "A'a yi aikinka, ina da wurin zuwa" ta lallaɓa
shi ta fice.
Sai dai hankalinta ya rarrabu kashi-kashi, voice ɗin nan da
aka turo mata, babbar shaida ce da zata shiga kotu da ita da ƙwarin gwiwar ta.
Abdul ya kira saif a waya, ya tambaye shi yaya ake ciki ya
ce masa "Wallahi Abdul babu labarin matar nan, duk wani bincike da
yakamata na yi na yi, amma shiru babu labari".
"Lahaula wala ƙuwwata illa billa, Saif akwai matsala me
zan ce wa yarinyar nan idan ta gano mahaifiyarta tayi ɓatan dabo, bayan babu
irin magiyar da ba ta yi mini ba, a kan na mayar da ita"
"To wannan kuma kai ta matsewa, tuntuni da ka san abun
yi a kanta da duk ba a kawo nan ba"
Abdul ya ce "Dole na gano in da mahaifiyar rayya take,
idan ba haka ban san kalar tsinuwar da za ta yi mini ba"
Saif ya ce "Ban gane tsinuwa ba, tsine maka take
yi?"
"Manta kawai" ya kashe wayar, ya din ga kiran
wayar ramma, saboda tun jiya da safe da tayi kukan nan, ba ta sake ɗaga wayarsa
ba, hankalinsa yayi mummunan tashi, ya fara tunanin ko wani abun ne ya sameta,
kar ya je ta yi wa kanta illa, dan da wuƙaƙe a kitchen, kuma tana yawan
iƙirarin cewa zata kashe kanta.
Kusan awanni ashirin da huɗu suka shuɗe, Nabila ba ta samu
Viper a waya ba, can ɓangaren su Walid ma, hankalinsu ya kasa kwanciya, saboda
yawon neman Viper.
Har ta je wurin aiki, ta kasa sukuni, kawai ta yanke
shawarar zuwa gidan da yake.
Tana sauka daga abun hawa, wata mota ƙirar helux baƙa, ta
fito daga hanyar, duk da wurin mota ba ta iya bi, tayi ta tunanin yaya aka yi
mota ta bi ta wurin, ta ƙarasa gidan, tun a tsakar gida take sallama, amma
shiru babu wanda ya amsa, ta nufi ɗakinsa, ta ganshi a kwance a kan katifa,
gefensa ga wuƙarsa da wayarsa da ledar magunguna, yana sanye da riga baƙa
armless, da dogon wando shi ma baƙi, ga damtsensa an yi masa ɗinkin rauni, da
sauran wurare a jikinsa.
Cikin hanzari ta ƙarasa tana faɗin "Subhanallah"
"Viper meyasameka?" Sai dai kamar gawa, ta ƙare
masa kallo, an yi masa askin uwar sumar da take kansa, an yi masa gyaran fuska
tare da rage masa gashin da ya taru a fuskar sa. Yayi wani irin ƙayataccen
kyau, hatta kayan jikinsa ba ƙaramin kyau suka yi masa ba. Wayarta ta ciro ta
din ga ɗaukarsa a hoto.
Ta daddaki gefen katifarsa ta ce "Viper, bacci kake yi
ne? Garin yaya ka ji raunuka haka?" Sai dai shiru ko motsi baya yi.
"Me ka sha har haka ne? Ko sai na ce Master zaka
tashi?" Babu tsammani ta ga yana motsawa a hankali.
"Madarata" Nabila ta ce "Too yau kuma?"
Yayi murmushi idanunsa a lumshe ya ce "Ai a duniya babu
wanda ya raina ni, daga ke sai Walid, kin daina jin tsorona gaba ɗaya zan kama
ki ne" murmushi yake yi sosai, wanda hakan ya bayyanar da tsantsar shauƙi
da soyayyar da yake yi mata.
Surutansa ya cigaba da yi ya ce "Yakamata na gaya miki
wani abu, da yakamata ace kin sani, amma sai kin haihu tukuna, saura kuma ki
isheni da tambaya na san halinki" ya buɗe idonsa a hankali, ya kalli
Nabila da ta zuba masa ido, ya miƙa hannunsa ya riƙo nata ya ce "Zan gaya
miki me na je yi Lagos ne" sai kuma ya saki hannunta yana girgiza kai.
"Laaa, ke ya aka yi ki ka dawo da shi, Walid ƙaraso ka
ga" liti yayi maganar yana shigowa ɗakin.
Gaba ɗaya su ukun suka shigo, suka kewaye ta.
"Da gidan uban wa ki ka kai shi?"
Ta kalli Liti ta ce "Kamar yaya?"
"Gidan uban wa ki ka kai shi?"
A ƙule ta ce "Gidan ubana, tayaya zan iya ɗaga wannan
shirgegen ƙaton"
"Ƙarya ki ke yi haɗa baki aka yi da ke aka ɗauke shi,
wannan kayan na jikinsa ma ba nasa bane ba macuciya"
Walid ya ce "Ya isa dan Allah, Barrister nemansa muke
ko sama ko ƙasa bamu ganshi ba, a ina ki ka gano shi?"
Ta ce "Wallahi yanzu na zo, bana samunsa a waya, yanzu
na zo kawai na tarar da shi a kwance, wallahi ban san ma neman sa ku ke yi ba,
duba wayarsa zaka missed calls ɗina da yawa. Amma dai naga wata baƙar helux ta
fita daga hanyar nan, ban san ta ina suka biyo ba, na riƙe lambar motar a
kaina"
Walid ya ce "Karki damu, na yadda da ke"
"Wallahi mai laya, ka cigaba da sakankancewa da
yarinyar nan, sai tayi dalilin an kashe ku tukuna"
Liti ya ƙarasa gaban Viper ya durƙusa a kansa, cikin zafin
nama, viper ya danƙi wuƙarsa ya saita ta a cikin liti yana wani irin huci.
Liti ya buɗe baki ya ce "Ni zaka sa wa russia
Viper?"
A hankali ya ƙara buɗe idonsa, ya hankaɗe liti gefe ya ce
"Na zata madaki ne" sai kuma ya kalli jikinsa, ya kalli kayansa, ya
kalli damtsensa ya ga ɗinki, ya kalli Nabila ya kalli ɗakin ya ce "Ke a
ina muka rabu da ke?"
Ta ce "A titi, bayan ka dire daga adaidaita sahu".
"Me ki ka yi mini?"
Nabila ta ce "Au kaima ni ka ke zargin na sace ka
kenan?"
Walid ne ya yi masa bayanin abun da ya faru, ya lalubi
wayarsa da sauri yana duddubawa.
"Don't endanger your life again, madaki is still not
your mate, da sauran lokaci" ya ajiye wayar ya sunkuyar da kansa, da yayi
masa nauyi yana tuno abun da ya faru a ranar.
Nabila ta kalli Walid ta ce "Yay walid, yayana yana
zuwa wurin sayar da shayinku, kuma akwai jami'ansa a farin kaya suna zuwa, kayi
taka tsantsan, yanzu aikinsa a kanka yake. Kuma ka kula da wanda suke zuwa
wurin sosai, kar wani information yayi leaking a wurin"
Liti ya ce "Munafuka, wadda take kwarewa ɗan uwanta
baya ne, ku ke tunanin kuma ba zata bar ku ba wataran. Shegen yayan naki
azzalumi, ƙugu kamar gatari"
Nabila ta ce "Allah ya isan sa, kuma ni ba munafuka ba
ce, kuma wallahi idan baka kiyayeni ba, zan kuma sakawa a kama mini kai, sai
igiya tayi saura" tayi maganar tana hararsa ta ɗauki jakarta.
Ta durƙusa a gefen Viper ta kai bakinta, kunnensa ta ce
"Viper, zan tafi zan je wani wuri, zamu yi waya, ka samu ka ci abinci, kar
ka takurawa kanka da tunani da yawa, kar ka sha ƙwayoyin da za su yi maka illa.
Saboda muna son ganinka cikin ƙoshin lafiya da ni da 'yar madara, na ji ka ce
zaka gaya mata wani abu, to nima sai ka gaya mini, tun da nice amarya. Kayan
nan sun yi maka kyau sosai da sosai, ka ci abinci kayi salla ka huta, ka bar
wayarka a buɗe zamu yi magana dan Allah, ka yi mini addu'a zan cigaba da
shari'a da su bunkure, take care dear" ya ɗaga kai ya kalleta, taƙi
kallonsa tayi waje.
Liti ya ce "Makira, duk makircinki sai ya koma
kanki". Ta galla masa harara ta tafi.
***
Abdul yana ta kiran ramma, har ya fitar da ran zata ɗaga,
yaji ta ɗaga muryarta ƙasa-ƙasa.
"Bacci ki ke yi ne?"
Ta ce "Eh"
"Eyya sorry na tashe ki, nake ta kiranki a waya amma ba
kya ɗagawa, lafiya dai ko?"
"Haushinka nake ji ne, zan iya ɗuɗɗura maka ashar,
shiyasa bana ɗagawa"
Yayi dariya ya ce "Yanzu kin huce?"
"Eh"
"To masha Allah, kin tashi lafiya?"
"Eh"
"Duk muryarki wani iri, anya lafiya kuwa?"
Ramma ta ce "Ba wani lafiya, ni na gaji da zaman gidan,
nikaɗai kamar mayya sai tv da haushin karnuka, ni ba prisoner ba".
Abdul ya ce "To yanzu ya ki ke so ayi?"
"Ni koma yane ayi"
Ya ce "To shikenan, zan dawo gobe in Allah ya
kaimu"
"Ba sati ka ce zaka yi ba?"
Ya ce "A'a hankalina yaƙi kwanciya ne, zan dawo gobe in
Allah ya kaimu "
Ramma ta ce "To Allah ya tsare"
"Kin fasa in faɗi a jirgin, kar in dawo?"
"A'a jirgin ya faɗi kai kaɗai ka mutu"
"Muguwa ba Amin ba"
"Ban kai ka mugunta ba ai"
Yayi dariya ya ce "Sai anjima".
***
Washegari ya kama ranar da Nabila zasu cigaba da shari'ar
mai gadi, ta shiga office ɗin ta, ta tarar da wani file a ajiye a kan
teburinta, har ta fara masifar na meye wannan aka ajiye mata a kan tebur.
Ta nemi wuri ta zauna, ta ɗauki wayarta, ta shiga social
media ta rubuta, kuraye masu fatar akuya, an kusa walƙiyya mu ga kowa" ta
yi tagging ɗin Naja bunkure.Washegari ya kama ranar da Nabila zasu cigaba da
shari'ar mai gadi, ta shiga office ɗin ta, ta tarar da wani file a ajiye a kan
teburinta, har ta fara masifar na meye wannan aka ajiye mata a kan tebur.
Ta nemi wuri ta zauna, ta ɗauki wayarta, ta shiga social
media ta rubuta, kuraye masu fatar akuya, an kusa walƙiyya mu ga kowa" ta
yi tagging ɗin Naja bunkure.
M karofi ya kirata, ya din ga yi mata surutu, da neman ta
bashi damar zuwa gidansu, ta ce masa yanzu aiki take yi, bayan sun yi sallama,
ta ja file ɗin tana dubawa.
Sunan Naja'atu Bunkure ne a sama, sannan aka fara bayanin
tarihin rayuwarta tiryan-tiryan, har zuwa fara aikinta, yadda ta taso cikin
rayuwar ƙunci da wahala, yadda ta zama lawyer, bayan fyaɗe da aka yi mata da
ƙanan shekaru, gaɓar da Nabila ke son ganin meyafaru, a nan aka tsaya. Ta daki
tebur, ta din ga jujjuya file ɗin tana tunanin waye wannan ya kawo mata file ɗin
nan, da kyar idan ba shi da alaƙa da wanda ya tura mata voice message ɗin nan.
***
DSP Nasir yana zaune yana rarraba ido a ƙaton falon, da ko
ina sanyin A.C ne ke ratsa shi.
Babu tsammani mutumin ya fito, ya samu wuri ya zauna, cikin
girmamawa Nasir ya ce "Barka da wannan lokaci sir"
"Yauwwa barka, DSP Nasir Yusuf maitama, ɗan uwan
barrister Nabila Yusuf maitama" ya ɗago ya kalle shi.
"Na san zaka yi mamakin kiran da nayi maka ko?"
Nasir "Ƙwarai sir, na san ni dai babu wani abu da ya taɓa
haɗa ni da kai, amma ka saka a nemo ni, kuma ga sunana ka kama, da na
ƙanwata"
Indabo ya gyara zamansa ya kalli Nasir ya ce
"Nabila!"
Cikin rashin fahimta ya ce "Me tayi?"
Ayshercool
0808101243
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin rashin fahimta, Nasir ya ce "Amma Yallaɓai me
tayi ne?"
Indabo yayi murmushi ya ce "Bari mu ɗan ajiye batun ta
a gefe. Aminu Viper, wanda aka fi sani da mai zamani a baya, kai ne incharge of
bincike da ƙoƙarin kama shi haka ne?"
Ya jinjina kai ya ce "Eh sir"
"Na san kana fuskantar matsin lamba, daga wurin na sama
da kai, a kan lallai ka kama Viper. Duk da abun mamaki ne, a baya yana tsare a
prison lokaci guda yayi ɓatan dabo sama da shekara guda ana nemansa".
Nasir ya ce "Haka ne sir"
Indabo ya sassauta muryarsa ya ce "Akwai jiƙaƙƙiya
tsakanina da Viper, wanda barazana ne ga siyasata da mutuncina. Saboda haka na
yanke shawarar yin gaba da gaba da kai mu tattauna wataƙila kafi bawa aikin
muhimmanci, tun da na samanka kawai nake gani, kai bamu taɓa haɗuwa ba, kuma
Alhamdilillah sai na yi sara a kan gaɓa"
ya ajiye masa wata jaka ya ce "Ga wannan ka sha mai,
sannan akwai fuloti mai rai da lafiya a unguwar tudun yola da takardunsa a
ciki, wannan zai zama wani ɗan hasafi, ko in ce ihsani domin ƙara maka ƙwarin
gwiwa, idan aiki ya kammala, ina da kyakykyawan Albishir gareka, muddin Viper
ya zo hannu, ko ma ya bar duniyar baki ɗaya ina da ƙarin Albishir gareka. Ɗana
na shirin zama deputy governor a garin nan, zaɓe mai zuwa. Kuma ka san kujerar
da nake kai, ka san ma'anarta. Zan iya yi maka alƙawarin zama CP na jihar nan,
kai koma na yi maka babban muƙami a ƙasa. Akwai kyautar mota irin ta sanatoci,
da gwamanti kan yi gwanjon su, gida ko fili sai wanda ka zaɓa. Kar ka yi dogon
tunani, ba wai cin amanar ƙasa zaka yi ba, taimakon kai da kai ne, kai ma ka
taimaki gobenka, idan ba haka ba, a haka zaka ƙare kana yi wa ƙasar da ba ta
san muhimmancin ka ba bauta, ka gama babu wani allowance ɗin kirki ka ƙare
rayuwarka a tagayyare" Nasir yayi shiru yana ajiyar zuciya.
"Sai magana ta biyu, Nabila ƙanwarka, akwai wasu
abubuwa muhummai a tattare da ita. Abu na farko na sanya rayuwarta a matsayin
tarkon da zan kama Viper ba tare da ta sani ba, duk da hanyar tana tangarɗa,
amma tabbas ina ƙoƙarin kama Viper ta hanyar ta, ko da kuwa hakan yana nufin
salwantar da rayuwarta ne"
Cikin mamaki da rashin fahimta ya ce "Kamar yaya?"
"Kamar yadda nake gaya maka, ai ba ta hannunku kawai
nake nemansa ba, dan haƙa ƙwazonka, da nemo Viper shi ne zai kuɓutar da
rayuwarta, haka zalika ka taka mata burki a kan shari'ar da take yi, na son yin
gaba da gaba da Naja'atu Bunkure, saboda yin hakan tamkar yin fito na fito da
ni ne, idan ba haka ba, wallahi rayuwarta zata salwanta a banza, ba zan taɓa
bari sunana ya ɓaci a banza ko asirina ya tonu ba"
Nasir ya ce "Amma sir, dole sai an shigar da Nabila
cikin wannan lamarin?"
"Dole ne, muddin kana son rayuwarta, make her withdraw
the case, ta fita daga shari'ar nan"
Nasir yayi sassanyar ajiyar zuciya ya ce "Zan duba naga
menene abun yi"
Indabo ya ce "Yauwwa, a ƙoƙarta, zaku tafi da P.A ɗina,
za ayi wa motarka full tank, ka sanya ido sosai a kan yarinyar nan"
Nasir ya tashi ya ce "Thank you sir"
Indabo yayi murmushi ya ce "In dai muna tare, ka din ga
samun damrmaki kenan, ai ba a zama haka DSP" ya jinjina kai ya juya ya
fita, kansa yana wani irin nauyi.
***
Cikin hanzari Nabila ta fito daga office ɗin ta, ta kalli
mai goge-goge ta ce "Baba, akwai wanda ya shiga office ɗina kafin na zo
ne?"
Ya ce "A'a, shara kawai na yi na goge miki, na
fito"
"Kai ka ajiye mini wani file a kan tebur?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a, ban tarar da komai ba da na
goge teburin" ta jinjina masa kai ta koma, tana cigaba da mamakin waye
haka?.
Ta window ta leƙa taga zuwan barrister Habib, tayi sauri ta
fita, a ƙofar office ɗin sa ya tarar da ita ya ce "Ya dai? Tara ko bashi,
ki ka tsaya mini a ƙofar office" tayi murmushi ta ce "Babu ɗaya,
nemanka nake yi ruwa a jallo ne"
Ya saka mukulli ya buɗe, suka shiga, ya ce "Allah ya sa
ba wata shirirtar ba ce? Nima ina nemanki dama"
"Haba barrister, sai ka ce wata 'yar yarinya, is a very
serious issue"
Ya dubeta ya ce "To yanzu dai, ki yi haƙuri, na fara
karyawa tukuna"
Noƙe masa kafaɗa tayi, tare da girgiza kai.
Ya ce "Ke, kwanan nan fa nayi mata ta biyu, da na sani
ma da ke nayi ta biyun nan, wannan shagwaɓar taki ai sai ki hanani
karyawa"
"Taɓ matarka ta daka ni kenan, ni dai ka zauna Please
muyi magana"
Ya zauna ya ce "Na zauna Nabila menene?"
Wayarta ta ciro ta kunna masa voice message ɗin nan, cikin
mamaki ya kalleta ya ce "Waye ya turo miki?"
Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, shiyasa na zo na
nuna maka"
"To ai tun jiya naso na kira ki, na je garinsu yarinyar
da kaina, har gidan su na je, amma ban tarar da kowa ba, maƙwabta sun tabattar
mini da ta shafe kwanaki ba su san in da take ba, kuma ba ta yi wa kowa sallama
ba" Nabila tayi turus ta ce "Ban gane ba, uwar ta ɓata kenan? Ko kuma
guduwa tayi saboda gudun abun kunya?"
"Shi ne dai ban sani ba"
Nabila ta ce "Na kasa gane kan lamarin nan, to waye ya
turo mini voice ɗin nan, an ce shi wanda yayi mata fyaɗen, ya zo ya ɗauke ta,
to ya aka yi da uwar, waye ya naɗi wannan recording ɗin?".
Barrister Habib ya ce "Gaskiya dai abun tunani ne,
lamarin akwai ɗaure kai, amma kar ki damu, koma waye sauƙaƙa miki aiki
yayi"
"Amma abun da mamaki fa, kuma wanda yayi hakan ba shi
da wata manufa ta yin hakan, ya bayyana kansa mana idan yana da gaskiya koma
waye"
Barrister Habib ya jinjina kai ya ce "Yauwwa, ya ku ka
yi da Alhaji wada M karofi?"
Ta yamutsa baki ta ce "Soyaya muke yi "
"Soyayya kuma? Cewa yayi yana son ki shiga cikin
lawyoyinsa, masu kula da dukiyarsa fa"
Ta ce "A'a gaskiya, ce masa nayi a'a, sai ya ce to shi
na din ga kula da shi, shikenan"
Habib ya ce "Innalillahi, wallahi baki da lissafi
Nabila, kin san waye mutumin nan kuwa? Kin san kuɗin da muke samu a wurinsa
kuwa? Babban mutum ne fa a ƙasar nan"
Ta tashi ta ce "Oho, a hakan ma ai yana bani kuɗi, bana
son dai ya zo gidanmu, naga he's very serious, kar ya zo suyi magana da Abba
ace sai na aure shi, dan yasin bana son tsoho".
Ya girgiza kai ya ce "Ƙuruci dangin hauka, Allah ya
shiryeki"
"Amin, ayi aiki lafiya" ta fice daga office ɗin.
***
Ramma na zaune tana ta gyangyaɗi, ta ji ana murɗa ƙofar
falon, Abdul ya shigo da akwatinsa.
Suna haɗa ido ya sakar mata murmushi ya ce "I am
back" murmushin ita ma tayi masa.
Ya ƙarasa ya zauna tare da rungumeta, yayi kissing ɗin
goshinta ya ce "Kina zaune baki yi bacci ba kina jirana?"
"Ƙarfe tara fa ka ce, amma sai sha biyu, Club ka je
ko?"
"Wallahi ban je club ba, abubuwan da na tarar da yawa a
can, Shiyasa na kuma samu matsala ne da flight ɗin shiyasa, gudowa fa nayi
saboda ke"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "To sannu"
"Yauwwa sweetheart "
Ta ce "Taɓ babu daɗin ji"
Ya ce "Wallahi da daɗi, rantse baki ji daɗi ba da na ce
sweetheart"
"Wallahi ban ji ba"
Abdul ya ce "Ƙarya ki ke yi, santaleln mutum kamar ni,
na kira ki da sweetheart, ki ce ba ki ji komai ba"
"To waye kai ɗin? Sai ka ce wani mutum na
musamman"
Ya kaɗa ƙafa ya ce "Ke kin san matan da suke crushing ɗina
kuwa?"
"To ina ruwana?"
"Kina da ruwa mana, na gaji fa sosai Saboda na san
maybe kina nan kina jirana, ko abinci ban tsaya na saya ba, yanzu zan yi wanka,
sai ki rakani mu duba in da suke 24hrs, mu ci abinci"
Ramma ta ce "A'a, na yi girki ai tun magariba ma na
gama, tun da nan gidan ba mak aiki, kayi wankan ka ci"
Ya ce "Iyee zan ci jagwalgwalo yau, bari nayi
wankan" ya ja akwatinsa, ya shiga bedroom ɗin da take.
A falo ya tarar ta ajiye fulasai.
"Rahama kayan miyan cikin fridge ɗin ba su lalace ba
kenan?"
Ta ce "Eh, har fruit ɗin, na iya reserving ɗin su
ai"
Yana cin abincin yana murmushi, ya ce "Yanzu har
sakwara ki ka yi, gaskiya kina ji da ni, ga shayin ma yayi daɗi sosai"
"Ba wani ji da kai da nake yi, tunani nake ina ma da
guba a ciki, ka ci ka mutu"
Yayi dariya ya ce "Koma dai menene, idan ma da gubar na
ci, ba mutuwa zan yanzu ba, sai kin haifa mana babies, kuma fa zama zaki yi
kiyi kuka idan na mutu. Anyway abinci yayi daɗi sosai, yaya aka yi ki ka iya
girki haka?"
Ramma ta ce "Aikina kenan a gidan Anty maijidda, ta ce
ba ta taɓa yar aiki kamata ba, sai gashi iftila'i ya faru da ni a gidanta, amma
ta kware mini baya, saboda kai ɗan ɗan uwnta ne, ni kuma bata da alaƙa da ni,
ko ganin idonta ban yi ba, wai sai ma umarnin idan mun zo kar a bari mu shiga
da ta bayar, aka canza masu gadi.shikenan bakomai, shi talaka ai Allah yana son
abun sa" tayi maganar tana share hawayenta.
Sai jikin Abdul yayi sanyi, ya ce "Rahama duk laifina
ne, nayi kuskure, kuma duk sharrin giya ne da ruɗin shaiɗan, amma na rage shan
giya ma, kuma wallahi rahama na daina bin mata, da ɗin ma sharrin giya ne da
kuma abokai" tashi ta yi ta bar masa wurin, saboda tuno hanyar da ya bi ya
ci mata zarafi da yayi.
Shi ma gaba ɗaya sai jikinsa yayi sanyi, duk da irin
zaluncin da yayi mata, tana da matuƙar tausayi da imani, duk da yana shan zagi
da tsinuwa, amma wasu lokutan sauƙin hali ne da ita.
A zaune ya tarar da ita a kan gado, tana ta uban kuka, bai
ce mata uffan ba, ya rungumeta yana shafa bayanta, a hankali yake furta
"Am very sorry for what i did, ki yi haƙuri" ya din ga rarrashinta,
har suka kwanta, yana ta magana, amma tunani ne daban-daban a cikin kanta, babu
tsammani ya ji ta ce "Abdul yasar"
"Your excellency"
"Wai dan Allah da gaske ana yi wa maza fyaɗe?"
Ya ce "A'uzibillah, wannan wace irin magana ce?"
"Shekarun baya, kan yayanmu ya mutu, kamar haka na so
naji an ce, wani ne ya ce zai samo masa aiki a Abuja, shi ne yayi masa fyaɗe
yayi rashin lafiya ya mutu, kullum mama ta tuno da shi, sai ta kusa kwana tana
kuka, sai ta daina cin abinci, kusan shekara shida fa, amma ta kasa mantawa.
Kuma dama ba a hannunta yake ba, shi yana wurin babansa a birni. To ni haryanzu
ban taɓa jin an ce an yi wa namiji fyaɗe ba sai mace, shi ne nake tunanin, ko
wani abun suke nufi daban ban gane ba".
Dummm haka Abdul ya ji kansa yayi, ita kanta kalmar ga mace
ma babu daɗin ji, balle ga namiji, sai yanzu ya ƙara tabattar da in dai zancen
ramma gaskiya ne, ya zalunce su. Hakan ya saka ya ji dolensa ya ƙara ƙaimi, ya
nemo mahaifiyarta, ya nemi afuwarta, amma bai ji a ransa zai iya mayar mata da
ramma ba.
"Abdul ka yi shiru, ka gaya mini mana"
"Ke kin ga alamar in da za a yi wa namiji fyaɗe ne? To
ban sani ba ko ana yi, tun da nima yaro ne haryanzu, ban sani ba ko ana
yi"
"Waye yaron?"
"Ni mana"
"Ka fiye abun haushi, da takaici, a'a mahaifa ne
kai" murmushi ya yi yana sumbatar ta.
***
"Mai zamani" Walid ya kira sunan Viper.
Ya ɗaga ido yana kallon Walid.
"Da gaske ka haɗu da madaki? Ko kuma yaransa ne suka yi
maka wannan raunin na damtsenka? Na ji an ce an neme shi an rasa, kuma ban ji
labarin yan sanda sun kama shi ba. Abun duk ya ɗaure mini kai, daga majiyarmu
ta dabarsa, hatta su yaransa ba su san a inda yake ba. Kuma na san abu ne
mawuyaci ku haɗu ace iya illar da yayi maka kenan, bai kashe ka ba, tun da ya
san nemansa ka ke yi, kuma kai ma da ka kashe shi da an ji labari, kuma bana
tunanin zaka iya kashe shi a yanzu".
Viper ya gyaɗa kai, ya ɗaga russia da take hannunsa yake ta
goge ta, yana shafa mata mai.
Ya miƙawa Walid ita, ya karɓa. Ya ce "Meyafaru?"
Al'amin ya ce "Duba da me aka ƙerata?"
Mamaki ne ya kama Walid, tun da suke bai taɓa yi masa wannan
tambayar ba, ya karɓa ya dudduba ta, ya ce "Ƙarfe ne"
Viper ya ce "Duba dai"
Ya sake dubawa ya ce "Ƙarfe ce Viper"
Viper ya haɗa tafukan hannayensa biyu ya ɗaga ya ce
"Allah ya jiƙan maza"
Walid ma ya haɗa ya ɗaga ya ce "Amin, dodo babban
sarki"
Viper ya ce "Shi ya saka aka ƙera mini russia. An yi
amfani da ƙashin ƙwaurin zaki ne, a samanta, ƙasanta kuma azurfa ce haɗe da
ƙarfe, sai kuma aka yi amfani da magunguna wurin ƙarasa haɗa aikinta. Shiyasa
ba ko yaushe nake amfani da ita ba. Ya saka an ƙera mini ita, ita ce makarin
taurin da madaki yake amfani da shi.
Sai dai a lokacin ban ji cewar ya dace na kawar da madaki
farat ɗaya, na kashe shi ba, na cigaba da ajiyeta.
A wannan karon naga yakamata na nu na wa madaki, talala
kawai nayi masa. Saboda shi aka ƙera russia, na gwada aikinta ne a kansa, kuma
tayi tasiri, dan kuwa ta huda shi, ya kuma zubar da jini.
Ƙafar da na soka masa, ta tashi daga aiki har abada, ba zan
kashe shi farat ɗaya ba, sai na gama sabauta rayuwarsa, Indabo ya watsar da shi
a dalilin Rashin amfanin da ba zai yi masa ba. A lokacin da sauran waɗanda yake
cuta, za su farga asirinsa ha karye ya daina tasiri, su ma su fara far masa da
kai masa hari. A haka zan cigaba da yi wa gaɓoɓinsa yankan ƙauna, har sai na
fara jin sanyi a zuciyata".
Walid ya ce "Kan uba, yanzu duk tsawon lokacin nan,
kana da makarin tsafin madaki, ka zauna muke bulayi? Har yayi maka illa ta
biyu?"
Ya sunkuyar da kai sannan ya ɗago ya ce "Tun a baya,
nayi niyyar ɗaukar fansa, amma daga cikin alfarmar da matata ta nema a wurina,
ya haɗa da na bar madaki da Allah, kar na kashe shi, ba ta son nayi kisan kai,
sunana ya ƙara ɓaci, hatta gabarmu sai da ta roƙi na kawo ƙarshenta, idan ban
manta ba, har Abbu ta sako a al'amrin.
Kukanta ne ya tsaye mini a rai, tare da magiyarta, har na ji
a raina na yadda, na haƙura zan kawo ƙarshen gabata da shi, domin in faranta
mata amma.... Sai kuma yayi shiru, ya fara huci, jijiyoyin sa suka fara
kumbura, gumi yana tsatstsafo masa a goshinsa.
Walid cikin damuwa, ya daddaki kafaɗar Viper ya ce "Am
sorry mai zamani, ka yi haƙuri, kayi haƙuri"
***
Nabila na ta rubuce-rubuce a cikin system, ta jiyo muryar
Abba yana "Ina Arfan Abban ne, ko ba ta dawo ba ne?"
Daga ɗakin ta amsa ta ce "Ina nan Abba, gani nan"
ta fito tana murmushi.
Ya ɗago mata key, ya ce "To, ga 206 ɗin ki can an kawo,
duk da na san ba kya son kalar motar"
Wani irin tsalle tayi, ta rungume Abba, ta na
"Subhanallah, wayyo daɗi ina zan saka kaina, Abba dama zaka sai mini
motar? Na zata da wasa fa ka ke yi mini" murmushi ya yi, ya kama hannun
ta, suka fita harabar gidan, wanda suka kawo motar ma ba su tafi ba, Vibe ce
blue black sai sheƙi take yi.
Kawai ta fashe da kuka, Abba ya ce "Ya kuka kuma?"
"Abba na gode, na ma rasa me zan ce ne" 'yan gidan
duk suka fito suna kallon motar, masu tayata murna nayi, masu tsaki suna yi.
Ana haka Nasir ya shigo, ta nufe shi da sauri, tana nuna
masa key ɗin motarta.
"Congratulations, amma tawa zaki ɗauka ni bani
sabuwar"
Tayi dariya ta ce "Ai ba aro ba ɗani, balle
kyauta" dama a karambani, Nabila ta iya mota, a kan ta Nasir, ya karɓi
mukullin, walida ta ce bari ta zo a ɗana su, amma Nasir ya ce mata a'a, su biyu
kawai za su fita.
Suna tafe yana driving, bakinta yaƙi rufuwa.
"Wow na zama big girl, idan zan je trial, sai dai a
ganni a motata, a din ga cewa hajiya, shikenan na huta da hawa ɗan sahu, da
masu warin hammata da zarnin fitsari" ya ƙare mata kallo, sai nishaɗi take
yi tana murmushi.
"Arfa"
"Yes sir"
"Ina son mu yi magana ne"
Ta kalleshi ta ce "To yaya"
"Shari'ar da ki ke yi, da kuma adawa da Naja'atu
Bunkure"
"Ok ina jinka"
"You have to withdraw the trial"
"What?"
Nasir ya ce "For your own good and safety, mace ce mai
hatsarin gaske, kar wani abu ya same ki, Abba ba zai iya jurewa ba, nima kuma
haka ki rabu da matar nan"
Nabila ta ce "Yaya, ni fa dama masu ƙaunata ba su da
yawa a duniya, dan haka ka ƙyaleni, why would that innocent old man suffer just
to cover someone's evil did, ita kuma ta din ga zaluntar mutane, kuma ayi mata
shiri, i can't nima Allah ya tsaya mini".
"Shut up, ina magana kina mayar mini, babu wanda ya
shiga cikin maganar sai ke, tun da ki ga kowa baya tsoma baki a lamarinta, dan
me ke zaki yi? Ki janye shri'ar nan tun ban saɓa miki ba, tun da baki san ciwon
kanki ba. Ya zama dole ki janye, idan ba ƙafar wando ɗaya ki ke so mu saka da
ke ba" ya haƙiƙance yana yi mata masifa. Tayi masa shiru, gaba ɗaya ta
nemi farincikin da take ciki ta rasa, saboda maganar da Nasir yayi, ya gama
zagayawa suka koma gida.
Matan Abba kuwa mussaman mama, ta din ga mita a kan saya wa
Nabila mota, itakaɗai a gidan, amma ya ce gidansa ne, abun da ya tsara shi za
ayi, ba wanda aka tsara masa ba. Lokaci ne yayi da zasu girbi abun da suka
shuka masa a kanta.
Gaba ɗaya sai ta rasa karsashi, ta na ta zumuɗin kiran
sumayya, amma yanzu ta kasa, saboda haushi da mamakin abun da Nasir yayi mata
yanzu.
Kawai sai ta kira Viper, ya ɗaga ya saka a kunnensa.
"Ina wuni, ya jikinka kuwa?"
"Alhamdilillah" sai da ta tashi tsaye jin ya amsa
ta ce "Kai, yau ka amsa mini, masha Allah, Allah ya ƙara maka lafiya da
nisan kwana, ya kare mana kai. Dama na kira ne in ji ya jikinka, kuma" sai
tayi shiru, shima shirun yayi bai yi magana ba.
"To ka tambayeni menene mana? Shikenan ma na san ba
kulani zaka yi ba, sai anjima" ta kashe wayar ta ajiye, ta kwanta tayi
shiru, zuciyarta a cunkushe babu daɗi, ga abun farinciki, amma Nasir ya ɓata
mata. Kawai ta fashe da kuka, ta yi ta gama, ta kwanta ta hau bacci.
***
Yau a kotu, hujjojin da Nabila ta bayar masu kyau ne sosai
da sosai, sai dai lauyan gwamantin da yake kare ɓangaren ramma, sun fita gogewa
suka din ga dankwafar da ita, kuma alƙalin ya din ga ɗaukar side, tare da soke
wasu daga cikin hujjojin Nabila. Ya sake ɗaga shari'ar zuwa wata guda. Ta kalli
dattijon, gaba ɗaya sai ta ji ta fara karaya.
Jiki a sanyaye ta fito, tana fitowa murtala yana tsaye a
harabar kotun yana jiranta.
Kamar ta fashe da kuka ta ce "Yaya murtala kaga yadda
shari'ar nan ke tafiya ko?"
Murtala ya ce "Kar ki damu, ai idan sun san wata, ba su
san wata ba, kamar yadda muka tsara zan tattauna da ke a kan shari'ar yanzu, ki
faɗi hints mai muhimmanci, zamu saka a live program yau da ni da Sumayya, sai
dai duk mai faruwa ta faru.
Cikin damuwa ta ce "Kar fa ku samu matsala a wurin
aiki"
"Manta da su, duk da su ake haɗa baki ai, dattijon ne
ma abun tausayi"
Nabila ta ce "Wallahi ko kallonsa nayi, sai tausayinsa
ya kama ni, bana son na kasa sakawa a wanke shi"
Murtala ya ciro recorder ɗin sa, ya tattauna da Nabila, na
mintuna biyar, a kan shari'ar sannan ya tafi.
***
Indabo tamkar zai kwaɗawa Abdul mari, saboda takaici
"Abdul wai me kake nufi da ni ne? Sai ka yi mini asarar wahalata, uwar me
ka dawo kanon ka yi? Uban wa ka ajiye da ka taho, mutane sun zauna suna
jiranka, kawai a nemeka a rasa, wane irin rashin mutunci ne, da iskanci har
haka? Wato tona mini asiri zaka yi, ka nuna wa duniya ban isa da kai ba
ko?"
"Daddy, uzurin gaggawa ne ya taso mini, wata tiyat.....
"Ubanka da kai da tiyatar, ko tunanin ɗan uwanka da
yake mexixo a tsare baka yi, dole sai ka nuna mini ban isa da kai ba, ka cigaba
kar ka fasa ka kuma kyauta"
Wayar Abdul ta fara ringing, ya cirota ya ga lambar ramma,
ya ɗaga a saka a kunnensa, yayi ƙasa da murya ya ce "Beb"
"Abdul kana ina?"
"Ina gida meyafaru?"
"Tun jiya fa zazzaɓi nake yi, cikina sai ciwo yake ina
amai"
A rikice ya ce "Subhanallah, kina ji na, ki duba side
bed drower, akwai pcm, ki ɗauka ki sha, daga shi kar ki sha komai, gani nan
zuwa kin ji, ki samu ki kwanta" sai da ya kashe wayar, ya tashi tsaye, ya
ankare da katoɓarar da yayi, gaba ɗaya ya manta a gaban wa yake.
"Abdul karuwa ka ajiye gidanka, har take rashin lafiya,
saboda iskanci a gabana kuma kake waya da ita?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a ba karuwa ba ce
Daddy..ammm....
"Abdul, yanzu ba zaka daina sakarcin nan ba, sai abokan
adawa sun farga, sun fitowa da duniya waye kai? Uban wa zai yadda ya zaɓeka,
idan mutane suka san you are womanizer? Kuma har ka ajiye mace a gida, bama ka
yi shahshashancin ta tafi ba. Na haramta maka kwana a waje, duk in da kake ka
dawo gida ka kwana, kuma a cikin watan nan za ayi bikinka, ko ka yarda ko baka
yadda ba".
Abdul ya kalli Indabo ya ce "Dan Allah Daddy ka bari na
kawo wadda nake so na aura, ni wallahi bana son waccan yarinyar, ni ka bari zan
yi maka bayani"
"Babu wani bayani da zan saurara daga gareka, dan nawa
bayanin ne gaba da naka, kuma kaje ko sallami koma wace karuwar ce daga
gidanka, tun kan na biyoka na ci maka mutunci" cikin sauri ya fice, yana
sake kiran rahama, a ransa yake jin sai dai ayi wadda za ayi, ko da kuwa hakan
yana nufin bayyanawa duniya ramma ne.
***
Yana tsaye a jikin bishiya, ya juya wa hanyar da take tahowa
baya, yayi crossing ƙafarsa, hannunsa ɗaya riƙe da taba, ɗaya kuma yana danna
wayarsa. Daga bayansa kawai, sai mutum ya so ya juyo ya ga fuskar sa, suffarsa
ta ƙaƙƙarfan namiji duk a bayyane, saboda yadda damtsensa yake a murɗe, ya cika
hannun shirt ɗin sa, hannunsa ɗaya kuma ya sha ɗinki. Rigar ja sai dogon
wandonsa baƙi.
"You are under arrest, officer ku kama shi" ko
motsi bai yi ba, balle ya waiwayo, ta zagaya ta gefen bishiyar, tana leƙa
fuskarsa, ya ɗaga kai ya kalleta ta ce "Kai baka jin tsoro ne?, ba ka ji
tsoro ba da na ce you are under arrest" ya ɗaga kai ya kalleta ya ce
"Tsoro?"
Ta ce "Eh mana"
"Hmm" kawai ya ce, ya zuƙi sigarinsa, ya kawar da
kansa gefe, ya din ga sakin hayaƙin, in a passionate way"
Ta zuba masa ido, komai nasa na daban ne, kuma na musamman.
"Wurinka na zo"
Ya ɗaga mata idonsa da girarsa ɗaya alamar yana jinta, hakan
ya sanya ta ɗan diririce.
Ya samu wuri ya zauna, ita ma ta zauna, ta kalleshi ta ce
"Sannu ya hannunka? Na ga da sauƙi ma baka da ƙan jiki" ya kalli
ciwon, ya basar, ya sake zuƙar sigarinsa.
Yana sakin hayaƙin, ta fara tari, ya kashe sigarin a jikin
bishiyar, ya ce "Ina jinki".
Tayi gyaran murya ta ce "Raina ma fa babu daɗi,
shari'ar nan da nake yi, so suke su yi mink fin ƙarfi, na fara sarewa kuma hope
ɗin iyalin mutumin duk a kaina yake, ni da na gansu ma sai in ji zan yi
kuka" tayi maganar tana goge hawayenta.
"Ohh, a haka za a tsaya mini? Idan bamu yi nasara ba,
sai mu zauna mu yi kuka?" Ta girgiza kai ta ce "A'a zamu yi nasara in
sha Allah, shaidar fa da na gabatar babbar shaida ce, wani ya turo mini voice
na maman Yarinyar, tana kuka ta ce a taimaka mata, amma wanda ya turo ɗin yayi
blocking ɗina, sai kuma aka ajiye mini wannan a office ɗin" tayi maganar
tana ciro file ɗin tarihin Naja bunkure ta miƙa masa daga cikin jakarta ta
goyo.
Ya karɓi file ɗin ya fara dubawa, ya miƙa mata hannunsa, ya
ce "Bani wayarki" ta ce "Wayata?" Yayi shiru yana kallont,
dan ba zai maimaita ba.
Ta ciro ta cire password ta miƙa masa, ya karɓa yana
dannawa.
Ta zura kai tana leƙa wayar, ta ce "Me kake nema a
wayar?" Ya janye wayar ya cigaba da dannawa.
Kiran Nasir ne ya shigo, ya miƙe mata dan ta ɗaga, ta
girgiza masa kai ta ce "Rabu da shi"
"Ki ɗaga ki gaya masa muna tare, ba nemana yake yi
ba?"
Ta kalleshi ta ce "Ga wayar nan a hannunka, ka ɗaga ka
gaya masa" kafin ta rufe bakinta, ya yi accepting call ɗin, ya kai wayar
kunnensa.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Wata irin zabura Nabila tayi, ta kai hannunta zata karɓe
wayar, amma ya riƙe hannunta yana kallonta, girgiza masa kai tayi da sigar
magiya tana kallonsa.
"Hello. Hello, Arfa" muryar Nasir ta fito rangaɗau
a wayar.
Viper ya ɗaga idonsa yana kallon ƙwayar idonta, ga mugun
riƙon da ya yi wa hannunta da take jin tamkar zai ɓalle.
"Arfa kina ina ne? Hello kina ji na?"
Kallon da Viper yake yi mata, gaba ɗaya sai ta rikice, ga
kusancin da suke da shi, ta ƙara rikicewa. Kasa daurewa tayi ta ce "Wayyo
hannuna"
"Nabila, menene? Kina ina ne?"
Al'amin ya sakar mata hannunta, ya katse kiran, ta ja da
baya tana murza hannunta tana ƙifta ido.
"Amm meye ma sunan naki?"
Ta kalleshi tana turɓuna fuska ta ce " 'yar
madara"
Cikin sauri ya kalleta ya ce "Iyee?"
"To idan ban kai 'yar madara ba, ka din ga ce mini 'yar
suga, ko mazarƙwaila" tayi maganar tana cigaba da murza hannunta.
"Baki shiryawa wannan ranar ba, ki ka yi gammon ɗaukar
abun da baki san a ina zaki sauke ba?"
Ta gyara zamanta ta ce "Nayi mana, ai shi ramin ƙarya
ƙurarre ne. Amma yau da ka gaya wa DSP muna tare, da ka gama kashe ni da
raina, ban gama da aikin gabana ba, ka sake ɓallo mini ruwa.
Zaman kotun nan na yau ya bani haushi, Alƙalin alamu sun
nuna side zai ɗauka, gashi dattijon nan ya musa ya ce ba shi bane ba, sun kafa
hujja da shi ne, wai lokacin da abun ya faru daga shi sai ita, kuma ita da shi
da wata mai aiki ne, amma har gidan ɗayar naje ban same ta ba.
Su kawo ita rammar kotu, ba su kawota ba, ba su da wata
tabbatacciyar shaida, recording ɗin da na gabatar, an soke an ce sai dai uwar
taje da kanta, ni na rasa me ma zan yi wallahi" tayi maganar cikin
matsananciyar damuwa.
Ya nuna mata file ɗin hannunsa ya ce "Waye ya baki
wannan?"
"Ban san waye ba, a kan teburina kawai na ganshi da
safe" ya cigaba da daddana wayarta, ba tare da ya kalleta ba ya ce
"Kin ɗauki hotona, dan ki nuna wa yayanki ya kama ni?"
Ta kalli wayar hannunsa, ta ce "Ai nayi hiding ɗin
hoton, ya aka yi ka buɗe?"
Ya sake kallonta ya ce "Me kike da hotona?"
Nabila ta ce "Saboda in din ga kallonka, ina jin daɗi,
askin nan da aka yi maka kayi mini kyau sosai da sosai ne" tayi maganar
tana murmushi.
"Amm, amma dan Allah ina ka tafi, naji su Oga walid sun
ce, ɓata kayi, wai ranar da muka rabu ina ka tafi? Can ka koma ko? A can aka ji
maka ciwon nan. Na tsorata da naga an yanki cinyar wani, da sun ganni nima
kasheni za su yi ko?"
Gyaɗa kai yayi, ya ce "Kina da system?"
"Eh tana gida amma" ya cigaba da danna wayarta.
"Wai dama kana magana haka? Baka taɓa yi mini doguwar
magana ba sai yau. Hmmm da tabon wuƙarka da ka yi mini zan koma ga Allah, ka
kusa fa kashe ni ranar farko da muka haɗu, ban san laifin da nayi maka ba ka
kusa kashe ni. Amma dai yau ba ka sha komai ba ko? Naga yau ka yi mini
kirki" jefa mata wayarta yayi ya tashi tsaye, ya ce "Ki kula da
kanki, ana bibiyar ki, ana bibiyar wayar da ki ke yi da wata sumayya, akwai
alamar tana bin diddigin abubuwan da ki ke yi, ko kuma ana bibiya bata sani
ba". Ta tashi tana zare ido ta ce "Sumayyan?"
"Wanda yake bibiyarki, shi ya turo miki wannan voice ɗin,
ya baki tarihin bunkure, duk da bai baki complete ba. Yana bibiyar ki ko dan ya
taimake ki, ko kuma yana da manufar da yake son cimma, dan haka ki kula"
Ta dafe ƙirji ta ce "Amma meyasa za a din ga bibiyata
da sumayya? To wa ka ke tunanin yana bibiyata? Ka yi mini bayani sosai da sosai
to me ma nayi za a bibiye ni?. Ya cigaba da tafiya bai bata amsa ba, tabi
bayansa tana cigaba da magana.
Ya tsaya cak, ya waiwayo ya kalleta, tsayawa tayi ita ma,
tana kallonsa tana jiran taji mai zai ce?.
"Kin haɗu da Indabo?"
Shiru ta yi, sai kuma ta waro ido ta ja da baya, ta ce
"Wai indabo ɗan siyasar nan, shi ne dai na cikin labarinka? Na ganshi a
wurin aikin su sumayya, subhanallah shiyasa tun a ganin farko da nayi masa naji
na tsane shi".
"Ya ganki?" "Eh, sai dai ban kula shi ba. Ai
ni bai sanni ba, nima kuma ranar na fara ganinsa, sunansa kawai nake ji, amma
menene?"
Ya girgiza kai ya ce "Shikenan" ya cigaba da
tafiya.
Ta sake bin sa tana ɗan haɗawa da gudu, saboda saurinsa ya
fi nata sosai, "To ka yi mini bayani, ni menene haɗina da shi to?"
"Babu, ki je ki mayar da hankali a kan wannan case ɗin,
idan kin yi wining sai ki dawo, kar na sake ganinki a wurin nan"
Cikin rashin fahimta ta ce "To amma"
"Take your way, ki tafi na ce" yayi maganar yana
nuna mata hanya, ƙyam ta tsaya tana kallonsa, mamaki ne ya cika shi, tsawar da
yayi mata ko a jikinta, ta tsare shi da idanunta masu matuƙar haske, yanayin
yadda take abubuwan ta, ya sake tabattar masa da akwai sangarta a tare da
Nabila.
Ya juya ya tafi, ita kuma ta tsaya cak, tabi bayansa da
kallo, tafiyarsa kawai gwanin burgewa, tafiya yake yi cike da ƙasaita, da
bayyanar da ƙarfin da yake da shi, sai dai shi bai san yana hakan ba, har ya
ƙulewa ganinta, sannan ta juya ta fara tafiya.
Sai yanzu take wasu lissafe-lissafe, tabbas sumayya ta
canza, sun rage yin waya sosai yanzu, kuma ba ta kiranta da layinta sosai
yanzu, kenan da gaske haɗa baki aka yi Sumayya a bibiyeta? To waye yake bibiyar
ta ta? Farar motar nan ce ya faɗo mata a rai.
"To idan kuma an san ina zuwa nan fa, aka tona mini
asiri, ina zuwa wurin mai laifi da ake nema ruwa a jallo. Wace amsar zan bayar
na kare kaina?.
"Wai me ma ya aike ni tun farko? Ina zaman zamana"
tana tafe a hanya, wani irin ciwon kai ya saukar mata, da kyar ta ƙarasa gida.
***
A kwance Abdul ya tarar da ramma, cikin damuwa ya ce
"Rahama ya aka yi baki da lafiya, har na fita baki gaya mini ba?"
Ta yamutsa fuska ta ce "Na zata zan warke ne, ba sai na
sha magani ba"
"Wannan ai ganganci ne, ko dai ciki ne?"
Da sauri ta ce "A'uzibillah, Allah ya yi mini tsari, ai
kai ma ka san ba shi bane ba"
"Duk da haka, sai na gwada" first aid drower ɗin
sa ya buɗe, yayi mata gwaje-gwaje, babu ciki sai malaria.
"Rahama, wurin nan babu sauro a ina ki ka samo malaria
kuma?"
Ta kalleshi ta ce "A jikinka"
Yayi murmushi, ya haɗa allurai, zai saka mata cannula, ta
hau kuka wai ba ta so.
"Rahama kina wahalar da ni, yanzu alluran baki zan yi
ki shanye ko kuwa?"
"Ni hannunka da zafi gaskiya, ka samo wani yayi
mini" ya harareta ya ce "Wani wa? Babu wani mahaluki da zai ganar
mini jikinki a doron duniyar nan, ina kallon shi"
"Eh amma ai kai ka iya kallon na wasu"
"Duk cikin aiki ne, kuma ki yi mini shiru nayi aikina,
ko na caccaka miki allurar har a baki"
Ya saka mata cannula, yayi mata allurai, ya saka mata ruwa,
da duk ya ajiye su a gidan, saboda ramma.
Ya rungumeta a jikinsa, yana shafa saman cannulan, ɗaya
hannun kuma yana matsa jikinta a hankali.
Ya zubawa hannunta ido, daga lokacin da ya ɗaukkota zuwa
yanzu, ta canza sosai da sosai, fatarta tayi kyau, tayi haske. Ramma ba wani
shahararren kyau ne da ita ba, amma yana jinta a kusa da zuciyar sa, duk da ba
wani shiri suke yi ba, duk in da ya tafi tana ransa.
Bai taɓa raping ɗin mace ba, sai a kan ramma, hakazalika bai
taɓa tarayya da virgin ba sai ita. Bai taɓa jin kunya da dana sanin wani rashin
mutunci da ya yi ba, sai a kan abun da yayi musu, yanzu kuma uwa uba, ɓatan
mahaifiyarta, bai san me zai ce mata ba, duk da yana ta ƙoƙarin ganin ya gano
in da take.
Yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Sannu, kan ya daina
ciwo?"
"A'a, amma Alhamdilillah ya rage"
"Masha Allah, ki bani labarin ƙauyenku mana, zan cika
alƙawari, na yi magana da ɗan majalisar ku, lokacin da naje Abuja, zai shigar
da ƙudurin hanyar ku, burtsatse ma da ki ka ce, ina jiran injiniyoyi su gama
lissafi su turo mini, za ayi muku guda uku" ta tashi zaune ta kalleshi ta
ce "Da gaske dan Allah?"
Ya jinjina mata kai yana murmushi, itama murmushin ta yi, ta
ce "Yan garinmu za su ji daɗi, mun gode Allah ya saka da alkhairi, mun
gode sosai, yan garinmu mun daɗe muna koken rashin hanyar nan, amma ba ayi mana
ba, mun gode"
"Yau ba Allah ya isan?"
"Ai wancan abun da ka yi mini daban, wannan ma daban,
amma Allah ya isa tana nan"
Abdul ya yi ajiyar zuciya ya ce "Ki yafe mini mana
sweetheart "
Ramma ta ce "Ka mayar da ni wurin mahaifiyata, ka nemi
afuwarta, amma haryanzu a zuciyata ban ji zan iya yafe maka ba, daga kai har
anty maijidda, da wannan bayahudiyar matar"
Yayi shiru ya sunkuyar da kai, zuciyarsa babu daɗi, ta ɗaga
kai ta kalli fuskar sa, ta ce "Oho, ba zaka bani tausayi ba, ka tuba ga
Allah ka gyara halayenka, dan ka samu kyakkyawar makoma. Ka cigaba hannun ya
fara zafi" bai ce mata uffan ba, ya cigaba da shafa mata hannun.
Ta saka ɗaya hannun ta juyo da fuskarsa, taga idanunsa sun
yi ja, sun bayyanar da tsantsar damuwa.
"To meye kuma?" Ya girgiza kai alamar babu komai.
"Ka tabattar?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
"Shikenan, to kayi haƙuri dai, ni gaskiyata na gaya
maka, baka san zafin abun da ka yi mini bane, amma naga kamar ka ji
haushi"
"Meyasa zan ji haushi, carbi zan sayo ki zauna ki yi ta
jan Allah ya isan son ranki" ta murguɗa masa baki, ta kawar da kanta gefe.
***
Madaki ya zuba wa cinyarsa ido, yadda ciwon da Viper ya ji
masa yayi wani irin mugun rami, maimakon ya yi ja ma, sai ya koma yayi kore,
wasu irin jijiyoyi duk suka ɗaɗɗaga a gefen ciwon, ƙafar ta ƙara riƙewa, ba ya
iya takata sai dai ya dinga jirgata.
Ya kalli babban amintaccen yaronsa ya ce "Lakwari,
ciwon nan fa cigaba yake yi, kenan ta tabatta alkadarina ya karye?"
"Nima na gani maigida, kaga ana ta saka maganin, amma
sai cigaba yake yi. Ba zamu yi saurin yanke hukunci ba, mu bi dare kawai, muyi
makabeli mu ɓace mu yanka gabas, mu koma in da aka fara, ya duba mana, idan da
wani abu da za a yi a kai, idan ba haka ba, mai zamani ya yi maka muguwar illa,
kuma yana sane yayi hakan".
Madaki ya jinjina kai ya ce "Haka ne, babban abun da ya
bani mamaki, bai wuce wanda suka zo suka ɗauke shi ba, ban san suwaye ba. Ta
tabbata yana da waɗanda suke goge laifukan da yake aikatawa, yakamata na sanar
da indabo"
Lakwari ya ce "Haka ne, amma mu fara neman mafita, a
karya dafin nan da ya saka maka, kafin duk wata magana ta biyo baya".
Ya jinjina kai ya ce "Shikenan".
***
Sumayya da murtala ne a zaune a gaban MD sun yi fiƙi-fiƙi da
idanu, gefe ga lawisa a zaune.
"Abun da ku ke yi, da kai da sumayya ya fara yawa a
wurin nan, ko dai ku bi tsarikanmu, da abun da muka ce dan cigaban tashar nan,
ko kuma ku ajiye mana aikinmu. Duk jajircewarku akwai waɗanda suka fiku. Gashi
kun saka hankalin mutane gaba ɗaya ya yo kanmu, saboda recording ɗin da ku ka
saki a duniya da yake bayyanar da zargi ga Naja'atu Bunkure, wands duniya kowa
ya shida mutuniyar kirki ce, mai yi wa mutane hidima".
Murtala ya ce "Tuba muke, muna neman afuwa in sha Allah
ba zamu sake ba"
"Daga kai har ita, wannan ne karo na biyu da kuka
aikata mana laifuka, muna ƙyaleku, na uku kora ce. Yanzu dole mu san yadda zamu
yi mu gyara wannan shirmen da kuka yi" Murtala yayi ta bayar da haƙuri,
sumayya kuwa fafur ta yi shiru, taƙi cewa komai.
Sun fito daga ofishin MD, tana hura hanci, ta tarar da
Nabila.
Sumayya ta ƙarasa ta zauna a kusa da ita, ta ce "Ke
kuma daga ina? Kin je kin haɗa kai da Uncle murtala, mun saka recording ɗin da
yayi miki, a kan shari'ar nan, yanzu aka gama sauke mana kwandon jaraba a ka.
Nabila ta ƙurawa sumayya ido, ta ce "Sumy why?"
Cikin rashin fahimta ta ce "Kamar yaya?"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Don't mind me, mota fa ta
iso, na zo na sanar miki"
Ihun farinciki sumayya tayi ta ce "Are you serious, ko
kuma jirgani ki ke yi?"
"Da gaske nake, amma Abba ya ce ba zan hau ba, sai
driving licence ɗina ya zama ready, kin san shi da ƙa'ida"
Cikin farinciki ta ce "Alhamdilillah, summa
Alhamdilillah yawo ba kama ƙafar yaro, Allah ya saka wa Abba da alkhairi, uban
marayu mai uban ma goyawa yake yi. Amma dan Allah arfat ki kula, ki san in da
zaki din ga zuwa, banda rigima da faɗa da mutane a titi" ta din ga kallon
sumayya, da son tabattar da abun da Viper ya gaya mata, yanzu sai ayi amfani da
ita, a cutar da ita, sam ta kasa yarda gaba ɗaya.
Wada M karofi ne ya kira Nabila a waya, ta ɗaga ta ce
"Hello sir"
"My beautiful angel, ya kike yau bamu gaisa ba gaba ɗaya,
kin ƙi bari mu haɗu, gashi na koma wurin aiki"
Ta ɗan kashe murya ta ce "Ba haka bane ranka ya daɗe,
ka san aikin namu ne babu zama, amma very soon zaka zo har gida mu gaisa"
yayi murmushi ya ce "To shikenan, na san maybe kina wurin aiki, da daddare
zamu yi waya in sha Allah"
"Ok Allah ya kaimu, ka kula da kanka sosai, kar ka yi
aiki ka gaji da yawa"
Yayi dariya ya ce "Thank you my dear"
Sumayya ta ce "Ohh wa kuma ake yaudara, wa aka kwaso
mana?" Nabila ta bata labarin wada M karofi.
Sumayya ta ce "Allah ya sa shi ne mijin, kakarmu ta
yanke saƙa, kin san waye mutumin nan kuwa Arfa? Allah ya tsaga miki farinjinin
manyan mutane, kar ki yi mana buƙulu dan Allah".
Nabila ta tashi ta ce "Taɓ gaskiya ba na son shi, ki zo
gida kiga motarmu"
Sumayya ta ce "Dolena" Nabila tayi mata sallama ta
fito, zuciyarta na cigaba da wasi-wasi a kan Sumayya, har ga Allah tana ƙaunar
sumayya har cikin zuciyarta, ta kasa yadda da abun da Viper ya gaya mata.
Nabila na tafiya aka kira Sumayya a waya, ta ɗaga tayi
shiru.
"Sumayya meyasa ki ke wasa da rayuwar ki, da ta ƙawar
taki ne? Bayan ɗan waken zagaye da ki ke yi, Ki ke kiranta da wasu layukan
daban, shi ne ki ka yi disconnecting ɗin bibiyar kiranki da ita da muke yi
ko?"
"Ni kuma, ban gane nayi disconnecting ba? Wallahi ban
yi disconnecting ba"
"Ƙarya ki ke yi, some hours back, aka yi disconnecting,
zaki ga matakin da zamu ɗauka a kanki da ita, sannan zuwan da tayi me kuka
tattauna?"
Sumayya ta dafe kanta ta zauna, sannan ta ce "Mota aka
saya mata, sai labarin sabon saurayinta da tayi, Alhaji Wada M karofi, sai
ƙorafin rashin nasara da take hangowa a kan shari'ar da suke yi".
P.A ya maimaita "Ki ka ce Alhaji wada M karofi?"
"Eh, shi"
"Ki cigaba da sanya ido a kanta, kina kawo mana rahoto,
akasin haka zaki ga abun da ba kya so " ta kashe wayar ta dafe kanta.
***
"Indabo ya ga yarinyar nan"
Gaba ɗaya suka kalli Al'amin, liti ya ce "Shikenan, ai
na san a rina"
Walid ya ce "Ya aka yi ka gane haka?"
"Mun yi magana da ita sosai yau, ana bibiyar ta, ana
bibiyar kiranta da wata ƙawarta, na yi disconnecting duk wata hanya da za a
cigaba da bibiyar kiranta. Amma rayuwarta na cikin hatsari, kuma idan ta cigaba
da zuwa za a gane inda muke".
Liti ya ce "Shiyasa tuntuni na ce, a sallameta ta daina
zuwar mana nan, amma walid ya nace".
"I think i will sealed a deal with her"
Suka haɗa baki suka ce "Kamar yaya?" Yayi shiru
yana lissafa yatsun hannunsa.
Liti ya ce "Ka yarda da ita ne? Ni haryanzu tantama
nake yi a kanta ne"
Walid ya jinjina kai ya ce "Lallai a tafawa mata"
Viper bai sake ce musu komai ba daga haka, ya tashi ya fita.
***
M karofi yana zaune yana shan shayi, wani jami'in tsaro, ya
shigo da Indabo cikin falon.
Karofi ya kalli Jami'in tsaron ya ce "Zaka iya
tafiya" ya mayar da idonsa kan Indabo ya ce "Barka da zuwa sirikina,
kwana da yawa, muna haɗuwa a Abuja, amma da ni da kai, babu wanda yake ziyarar
wani. Duk ni yakamata ace ina kawo gaisuwa. Bisimillah zauna mana.
Indabo ya zauna, ya kalli M karofi ya ce "M
karofi"
"Ma'aruf Indabo"
"Sabo da kaza fa, baya taɓa hana a yanka ta"
Karofi ya ce "Wannan haka yake, ko a siyasance, ko ma a
normal life"
"Auren 'yar uwata maijidda da kake yi, ba zai hana idan
kayi mini kan kara nayi maka na itace ba, hawainiyarka ta kiyayi ramata"
Yayi murmushi ya ce "Yakamata kayi mini fashin baƙi,
akan wannan kurman baƙin da kake ta karanta mini"
Indabo ya yi wata ƙwafa ya ce "Soyayya da ka je ka fara
da 'yar cikinka, saboda abun kunya, kuma yarinyar da take ta gwagwarmayar sai
ta tona mana asiri, wadda ka tsayawa, wallahi muddin asirin Abdul ya tonu kaine
ba wani ba, kuma sai nayi maganinka a siyasance da duniyance"
M karofi ya ce "Iko sai Allah, kana nufin Nabila wai?
Taɓ ai ni ban taɓa sani ba, banda yanzu da kake gaya mini. Ina da lawyer a law
firm ɗin su, shi naje gani, na ganta naji ina sonta, kai idan nayi niyyar
tonawa ɗanka asiri, da wani zancen ake yi ba wannan ba.
Kuma ni ban yi abun kunya ba, sonta nake yi da aure. Tun da
ƙanwarka ba yar gwal bace, da zata hanani zama da mata ba.
Naji daɗin wannan gargaɗi da kayi mini sosai da sosai, amma
ka kwantar da hankalinka, babu ruwana da shari'arku, nima aikina nake yi. Zaka
iya tafiya idan baka da abun cewa".
Indabo ya tashi, ya kalli idon kankarofi ya ce "Kifi
yana ganinka mai jar koma"
Karofi ya ce "A juri zuwa rafi dai " Indabo ya
fice yana baza babbar riga.
***
Nabila ta sake komawa gidan abokiyar aikin ramma, amma still
bata same ta ba, aka sake gaya mata ta koma garinsu, sai dai samun sunan garin
ma ya gagareta, ta kasa samu.
Tana kwance a kan gadonta, ta buɗe videos da hotunan da ta
yi wa Viper, ta zuba masa ido, tana jin daɗin tsokanarsa da take yi, na cewa
tana son shi, tana son zama kishiyar 'yar madara, mugun kallon da yake yi mata,
ba ƙaramin dariya yake bata ba.
Mussaman da ta samu ya kulata, a haɗuwar su ta ƙarshe, duk
da a ƙarshe, korarta yayi.
Tana kallon hotunan tana murmushi, ta ɗauki ƙaramar wayarta,
ta saka lambarsa ta kira.
Sai da ta kira da ainihin lambarta, sannan ya ɗaga.
"Ohh Allah, kayi saving lambata ne?, Ina ta kiranka da ɗaya
layin amma baka ɗaga ba. Ina ta kallon hotunanka, ina son in yi bacci .
Ka san ranar da nayi maka hotunan nan, har murmushi fa kayi,
ka din ga fara'a murmushi yana yi maka kyau sosai dear. Yaushe zaka ƙarasa bani
labarinka ne? Yakamata ka gabatarwa jauhar ni, a matsayin amarya, zan yi mata
biyayya sosai da sosai, in tayata sonka. Ba zan yi kishi da ita ba, ina sonta
sosai da sosai, dan Allah ko sau ɗaya ka haɗani da ita mana" kamar da iska
take, haka yayi shiru ya ƙi magana.
Ba ta gaji ba, ta sake cewa "Ina ƙaunar yar madara
saboda Allah, dan Allah ka ƙarasa mini labarin ta".
"Meyasa ki ka shigo rayuwata?"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Labarin dogo ne, ba zan ɓoye
maka ba, da dai ina taya Yayana nemanka ne, saboda nayi suna, na rama abun da
Bunkure ta yi mini, na wulaƙanta ni a gaban jama'a. Shi ne na din ga up and
down, har na haɗu da wannan litin, mara kirki".
"Saboda ki yi suna ki ke son taimakona?"
Nabila ta ce "Eh, a da ba, amma jin labarinka gaba ɗaya
ya canza mini tunani, nake jin zan iya yin komai, dan na ga na ƙwato maka
hakkinka, da kai da yar madara, duk da ban san ƙarashen labarin ba. Amma
gwiwata ta fara sanyi, na fuskanci Naja'atu Bunkure nan, tana da goyon baya
daga sama, kuma indabo babban mutum ne shahararre sosai, ina buƙatar support
sosai, kai kuma sai korata kake yi kana hantarata".
"Idan na ƙarasa miki labarin, that means duk tsanani
babu gudu babu ja da baya, zaki tsaya a shari'ata komai wahala da
sarƙaƙiyarta?"
"In sha Allah, i promise it"
Ya sake cewa "Kin tabattar zuciyarki zata iya ɗauka
komai muni, komai daɗin abun da zaki ji?"
Cikin ƙwarin gwiwa ta sake cewa "Eh zan iya"
Viper ya ce "Take your time to think, ki yi comparing
da ƙalubalen da ka iya biyo bayan hakan"
Ta lumshe idonta, hatta muryarsa, mai daɗi ce, duk a buɗe
take saboda bayan naturally yadda take, wiwi da shaye-shaye sun ƙara making ɗin
ta deep.
Ba ta bashi amsa ba, ya kashe wayar.
Walid ya ce "Mai zamani, ka yadda da maganarta kenan?
Zaka ɗauki fansa ta hanyar shari'a"
Mai zamani ya girgiza kai ya ce "Ta riga ta shiga
tarkonsu, kuma na fuskanci ba ta ji ko kaɗan, zata iya salwantar da
rayuwarta". Walid ya yi murmushi mai cike da jin daɗi ya ce "To ɗaya
maganar fa? Zaka gaya mata?"
Al'amin ya kalli walid, yayi shiru bai ce komai ba.
***
Jikin ramma da sauƙi sosai, tana zaune a gefen gado, Abdul
yana bata abinci, gefe ga magungunan ta. Wayarsa da take ringing ya ɗaga ya
saka a hansfree ya ajiye ya ce " 'yar mutanen bunkure, ya ake ciki
ne?"
"Abdul"
"Na'am"
"Ya ka yi da yarinyar nan ne da ka yi wa fyaɗe? Wata
yarinya ta tsaya kai da fata, sai ta wanke dattijon nan, mun yi duk abun da
yakamata, ta koma tana amfani da social media against me, hankali na ƙoƙarin
dawowa kaina, sai sintiri take yi wai lallai sai an kai yarinyar gaban shari'a,
ga wani voice message da yake yawo na uwar yarinyar...... Abdul ya cire wayar
daga hansfree, ya saka a kunnensa, yana kallon ramma.
"Ka gaya mini yaya ka yi da ita? Tana raye ko ta mutu?
Mu san abun da zamu shirya a kan shari'ar, an je gidansu babarta bata nan an
nemeta an rasa"
"Kina ji? Zan zo in anjima yanzu ina wani uzurin
ne" ya kashe wayar, ya kalli Ramma zai yi magana, amma ya kasa saboda
mugun kallon da tayi masa.
"Rahama ki tsaya ki saurare ni ki ji"
"Kayi mini shiru tun ba shaƙeka ka mutu na huta ba,
azzalumin banza da na wofi, in sha Allah sai Allah ya tarwatsa ka da kak kai da
duk masu goya maka baya kuna cutar mutane"
Fafur ta ƙi saurarsa, tayi watsi da kayan karin kumallon, ta
tashi ta bar masa ɗakin.
***
Nabila ta daina shiga harkar Nasir, dan sosai ya sakata a
gaba, da masifar lallai sai ta daina case ɗin bunkure, saboda lafiyar ta da
rayuwarta, ita kuma ta ce babu wanda ya isa.
Sumayya ce ta kirata da wata lamba, ta ɗaga ta ce
"Waye?".
"Ke ni ce"
Nabila ta ce "Yar 419, yau kuma da lambar wa ki ka
kirani, ko aiki ki ke yi a kaina ne?"
"Nabila, bar wannan maganar kin san menene?"
"No"
"Maganarki da muka saka a radio, a kan bunkure, wata
mata ta zo mini, ta ce lallai ke take son gani, akwai information da zata baki
a kan bunkure, ta ce macuciya ce, abun babu daɗin ji, bama itakaɗai ba, akwai
gwarama, mutane sun fara magantuwa fa"
Nabila ta ce "Abubuwa sun fara yi wa kaina yawa, zan zo
har gida na same ki"
Ta ajiye wayar ta dafe kai tana tura baki. Duk da tayi
farinciki da haka, dan kuwa gagarumin cigaba ne, amma gaba ɗaya ba ta yadda da
sumayya ba yanzu, dole tana buƙatar ganin Viper kafin tayi wani yinƙuri.
Babu tsammani ta ga Nasir ya shigo office ɗin ta, ta tashi
tsaye ta ce "Yaya lafiya?"
"Nabila wai ke meyasa a duniya ba kya nemawa kanki
zaman lafiya ne? Gaba ɗaya na kasa gane kanki a 'yan kwanakin nan, menene yake
damunki ne?"
Cikin rashin fahimta ta ce "Me kuma nayi?"
"Comment ɗin da ki ka yi da safe nake magana a
kai" yayi maganar yana ciro wayarsa ya daddana, ya buɗe facebook ɗin sa,
ya tura mata wayar.
Ta kalli wayar, posting ne da hukumar yan sanda tayi, na
cigaba da neman Aminu Viper ruwa a jallo, saboda ayyukan ɓarna da yake cigaba
da yi.
Tayi comment da "Wannan abun kunya ne ga rundunar
tsaron Nigeriya, ace kuna tsare da mutum a prison, a sake shi kuma a dawo ana
nemansa, ba shi ne abun bincike ba, hukumar 'yan sanda, da prison, da ta
shari'a su ne abun tuhuma da zargi" aikuwa mutane suka yi caa a kan
comment ɗin ta, suna reply.
"Yanzu yaya fisabilillahi menene laifina a cikin wannan
comment ɗin nawa, ita hukumar 'yan sandan, dan ayi comment ai suka yi posting ɗin,
kuma gaskiya na faɗa. Akwai ayar tambaya a kan ma'aikatar Shari'a, hukumar yan
sanda da ta gidan yari a kan case ɗin nan, kar ka yi wani tunani daban, ina
goyon bayan gaskiya ne kawai"
"Nabila ba kowane lokaci gaskiya take tasiri a ƙasar
nan ba, yanzu ki ka shigo cikin system ɗin nan, ƙasar nan ta wuce duk yadda
kike tunani".
"Na sani, amma rashin yin wani yunƙuri na kawo gyara,
shi ne ke kawo mana koma baya yaya, ba wai ina goyon bayan Aminu Viper ba ne
ba, menene gaskiyar abun da yake faruwa nake son sani"
Cikin takaici ya girgiza kai ya ce "Idan kin ƙi ji, ba
zaki ƙi gani ba arfa".
Ya ɗauki wayarsa ya juya ya nufi hanyar fita, ya kama handle
ɗin ƙofar office ɗin ya murɗa ya buɗe. Sai dai wanda suka yi ido huɗu da shi a
tsaye ya sanya gabansa wani irin mummunar faɗuwa. Ya raɓa jikin Nasir ya shiga
cikin office ɗin, Nabila ta waro ido tana kallonsa tana kallon Nasir.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Kallonta yake yi ta cikin baƙin glass ɗin idonsa, duk da ya
saka facemask, babu yadda za ayi Nabila ta kasa gane shi.
Nasir ya tsaya ya waiwayo, yana son sake ganin waye, duk da
fuskarsa a rufe take da face mask, amma ya tsaya ƙyam a tsakiya, ya juya wa
Nasira baya, yana fuskantar Nabila.
A hankali ya ƙarasa takawa, yaje ya samu wuri ya zauna a kan
kujera, ba tare da yayi magana ba.
Nabila kuma ta kalleshi ta kalli Nasir.
Nasir ya juya ya tafi, yana fita da saurin gaske ta ƙarasa,
ta rufe ƙofar office ɗin ta saka mata key.
Ta dawo ta kalleshi, ya cire facemask ɗin sa da glass ya
ajiye a kan teburinta.
"Su maciji an fito daga rami, kuma kai tsaye aka yo
wurina, dan Allah meyasa ka ke son lallai sai ka haɗu da yaya Nasir ne?
Da ya gano ka da ni da kai zai haɗa duk ya kama, dan ban san me zan ce masa
ba"
Ta dafe ƙirjinta ta ce "Wayyo Allana, haryanzu zuciyata
racing take yi, ranka ya daɗe irin haka sai ka kirani a waya, ka ce in zo kana
son ganina, amma wannan dirar mikiyar da ka yi mini ohh my God me ma zan ce ne?
Allah ya sa babu wanda ya sanka" ta zagaya ta buɗe fridge ɗin office ɗin
ta, ta ɗauki plate ta ɗoro masa apple, ayaba da lemo ta zo ta ajiye masa.
Ta tsiyayo ruwan zafi a dispenser ta haɗa masa tea mai zafi,
ta buɗe jakarta ta ɗaukko ɗan ƙara min flask, ta juye masa dankali a kan plate
da ƙwai, ta ce "Bisimillah, fara cin abincin sai mu yi magana naga yanzu
safiya ce" yayi shiru yana danna wayarsa.
"Ka ci abinci, wanne zaka fara ci?"
Still bai yi magana ba, har ta fara jin haushi.
"Sweetheart, magana nake fa, 'yar suga na magana"
ya ɗago ya kalleta.
Ta saka hannu ta karɓi wayarsa ta ajiye, ta ɗauki kofin
shayin ta miƙa masa ta ce "Ba dan ni ba, dan Allah ka sha, a gabanka na haɗa,
ban kuma son da zuwanka ba, balle ka ce na zuba wani abu a ciki dan Allah"
tayi maganar cikin kwantar da murya.
Ya saka hannu ya karɓa, sai dai kamar ƙaramin yaro, ya
zubawa kofin ido.
Ta ɗaukko plate ɗin dankalin, ta riƙe a hannunta, ta kalle
shi ta ce "Sha mana" ya tsareta da idanunsa masu ban tsoro.
Ta sauke nata idanun, saboda yadda nasa suka yi mata nauyi.
Ta saka hannu ta kai kofin bakinsa, ya buɗe bakinsa a
hankali, ya fara sha.
Tayi ɓoyayyiyar ajiyar zuciya, ya sauke kofin, ta miƙa masa
dankalin, kamar mai koyon cin abinci, haka yake ɗauka yana ci.
"Yauwwa My dear" yana ci, Adam apple ɗin
maƙogwaronsa, na kaiwa na komowa, sai yayi kamar zai yi magana, sai ya fasa ya
haɗiye maganar tare da abincin, da ƙyar yake haɗiye abincin, a duk lokacin da
ya saka abinci a gaba zai ci, haka yake ji, sai ya cakala ya bar shi, tun su
liti suna lallaɓa shi ya ci abinci, har sun haƙura sun ƙyale shi, sun zuba masa
ido.
"Master, ciwonka ya gama warkewa, Alhamdilillah Allah
ya ƙara tsarewa, ka daina zuwa in da za a cutar mana da kai dan Allah"
Yayi mata shiru, yana cigaba da cin abinci.
"Ko in ƙara gudun AC naga kana gumi" ya girgiza
mata kai alamar a'a.
Tana tayi masa hira, har ya cinye abincin tas.
Ta ce "Alhamdilillah" ta miƙa masa tissue ya goge
hannu.
"Wai dan Allah meyasa kake ta kallona ne? Ko wani abun
nayi?" Nan ma ya girgiza mata kai.
"Kamar bacci ka ke ji fa, ko an sha ne?"
"Me fa?" Yayi maganar yana kallon ta.
Ta ce "Bakomai"
"Aiki na zo yi" ya faɗa a taƙaice.
Ta ce "Aikin me?"
"Computer zaki bani"
Ta ce "Ok, desktop ta aiki ce, bari na baka laptop ɗina"
ta ɗaukki laptop ɗin ta ta bashi, ya buɗe ya fara dannawa.
Ta zauna a kusa da shi, tana kallon mai zai yi, sai dai ta
kasa gane me yake yi ɗin, wasu irin lambobi da alphabets kawai take gani a
screen ɗin system ɗin.
Sunan Yaya Nasir ne ya fito a kan wayarta, ta ɗaga ta kai
kunnneta, tayi shiru.
"Arfa"
"Na'am"
"Waye mutumin da ya zo office ɗin ki?"
Ta kalli Viper sannan ta ce "Baƙona ne"
"Wane irin baƙo?"
Nabila ta ce "Client ɗina ne, ya zo muyi magana ne a
kan wata shari'a meyafaru?"
Nasir ya ce "Gaba ɗaya ban yadda da shi ba"
"Daga fara ganin mutum yau ka ce baka yadda da shi ba
yaya? Ka san shi ne?".
"A'a kawai jikina ya bani wani abu ne, amma akan case ɗin
menene?"
"Is confidential, and against my professional ethics,
ba zai yiwu na gaya maka ba, idan na dawo mayi magana" ta katse wayar.
"Meyasa ki ke tsoron gaya masa ne? Shi ne DSP Nasir ɗin?
Shi a yadda yaken nan matsoraci yake son kama ni, ai karo da karo sai rago, na
raina jarumtarsa"
Ta tsuke fuska ta ce "Ya haka? Yayana ne fa, banda cin
fuska"
Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Da lokacin da nake mai
zamanina ne, aka bashi aikin kama ni, sai na yi masa karayar da zai shafe
shekara yana zaune yana jinya. A yanzun nan da muka haɗu, ba zamu rabu lafiya
ba.
Tarbiyyar Jauhar ce da girma ya sanya wasu abubuwan nake
kawar musu da kai".
Ta ce "A hakan? Yanzun ma fa kana zuwa ka sari mutane,
ka yi faɗa da neman magana"
Ya matso da fuskarsa saitin ta ta, ta ja da baya.
"Lokacin da nake mai zamanina, bana bin ƙofa komai girmanta, sai dai na
kama katanga kamar ɓarawo, bana biyo hanya ayi gaba da gaba da ni. Bana tsoron
kowane irin nau'i na fitina ko tashin hankali, idan aka kwana biyu ban ji ni
cikin rigima ba, sai na ji ni kamar mara lafiya.
Aiki tuƙuru da jajircewa tayi a kaina, ba dan ƙaddara ta
rusa tanadi da burikan rayuwata ba, ta ci kaso mafi yawa na tarbiyantar da
rayuwata a kan tafarki madaidaici. Ki daina haɗa kanki da ita"
Ta lumshe idonta ta buɗe ta ce "Shiyasa na ce tun da
ita 'yar madara ce, ni kuma sai na zama 'yar suganka, amma ka ƙarasa mini
labarin ta dan Allah" ya zauna sosai ya cigaba da danna system sannan ya
ce "Idan na ƙarasa miki labarin ta, hakan na nufin we sealed a deal, da
babu gudu babu ja da baya kenan, komai rintsi komai wahalarsa?"
Ta jinjina masa kai alamar eh.
"A'a ki sake tunani, mussman ranar da zata fasu kina ɓoye
shahararren ɗan ta'adda kamata"
"Kai ba ɗan ta'adda bane ba, ta'addancin da aka yi wa
rayuwarka, shari'a ta kasa tsaya maka ya sanya ka zama haka. A labarinka da oga
walid ya bani, da tun a lokacin da aka kashe yayanka, hukuma tayi abun da ta
dace, da duk ba a zo wannan gaɓar ba.
Muna iya jure rashin makusantanmu ne, saboda ƙarfin imani,
da tuna wanda ya bamu ne ya karɓi abunsa, amma idan wani ya zama sila, na rasa
mutane masu muhimmanci a rayuwarmu, wannan imani na yarda da ƙaddara ya kan yi
rawa a zukatanmu, mu kasa yadda da wanda ya bamu ne ya karɓa. Kai ba ɗan
ta'adda bane ba mai babban suna, cin hanci a doka da shari'a su ne suka
mayar da kai duk abun da ka zama a yau. Ba kowace zuciya ce zata jure tana
kallon wanda ya cutar da ita yana rayuwa cikin kwanciyar hankali, alhalin ita
an bar mata tabo mara warkewa ta jure ba.
Ban ce zan kai 'yar madara ba, amma na fuskanci giɓin da ka
rasa nima akwai makamancin sa a rayuwata, da yake ci mini tuwo a ƙwarya yake
damuna, ina ɓuya in yi kuka wasu lokutan na ji na tsani komai, kamar na kashe
kaina na huta.
Jin labarinka ya sanya, na fuskanci me ka ke ji a zuciyarka.
Har abada duk tsanani ba zan sake kuskuren kallonka a matsayin ɗan ta'adda ba,
kuma zan tabattar wa da duniya haka, da izinin Allah. Sai an gyara fannin
shari'a an murƙushe rashawa da bambancin hukunci tsakanin ɗan talaka da mai kuɗi,
mai ƙarami da babban uban gida, idan ana son rage yawan 'yan ta'adda" tun
da ta fara magana, yake kallonta, duk da tana yi tana zubar da hawaye, hakan ya
tabattar masa da akwai wani pain a zuciyarta ita ma.
Ya juya ya cigaba da danna computer, ta kifa kanta tana goge
hawaye. Ta kwantar da kanta a kan teburin, tana danna wayarta.
Ta ɗaga idonta ta kalli, yadda yake ta sarrafa computer,
bata san me yake yi ba.
Yanzun ma hotonsa take ɗauka tana murmushi, kamar ba yanzu
ta gama kuka ba.
"Master" yayi mata shiru.
Ta sake cewa "Maciji" tai maganar tana dariya.
"Viper, maciji mai hatsarin gaske, yau ka fito daga
raminka, ka zo wurina, sarana ka zo yi ne?" Still bai kulata ba.
Ta tashi sosai ta ce "Da ni 'yar sugar da yar madara,
wacce ta fi kyau ne? Kodayake na san ma ita zaka zaɓa, kafi sonta, amma dai
kyakykyawa ce? Sannan fara ce ko baƙa? Doguwa ce ko gajeriya, ina son in ganta
ka nuna mini hotonta, ko ba zaka bani haɗa ni da ita ba?". Sai da ya dafe
goshinsa, Nabila bata gajiya da surutu, Jauhar akwai lokutan da ba ta kula shi
da hira, idan ba ya cikin mood, shi wannan surutun nata ba zai bari su daidaita
ba.
Ya fizge wayar hannunta, yana dubawa yana danna computer.
"Wai hacking ɗin wani zaka yi ne? Ni baka yi mini
bayanin me ka ke yi ba, sonake ma mu yi magana, amma ka ƙi kulani, sai aiki
kake yi kai kaɗai".
Ya tashi tsaye ya ce "Zan yi salla"
Ta nuna masa toilet, ya shiga yayi alwala, ya fito yayi
sallar azahar, sanann ya kalleta ya ce "Tashi mu tafi"
Ta tashi tsaye ta ce "Ina?"
"In ƙarasa miki labarina, amma bisa sharaɗin da na
gindaya miki da farko, babu gudu babu ja da baya, duk tsanani da wahala"
ta jinjina masa kai.
Ya ɗauki facemask ɗin sa ya saka, ya sanya baƙin glass ɗin
sa ya yi gaba.
Dama yau hijjabi mai niƙab ta sako, dan haka ta saka
niƙabin, ta bishi.
Cikin ikon Allah, chamber babu kowa, duk lawyoyin sun tafi
kotuna, sai massenger da mai gadi.
Suka fito, ta ce "To ina zamu je? Ba zai yiwu ka ƙarasa
mini a nan ba?"
"I have to test you more, before i completely trust
you" daga haka ya tarar musu napep, ya gaya masa in da za su je.
Suna tafe tana ta addu'a, Ubangiji Allah ya kare su, ya
tsare duk in da za su je, Allah kar ya sanya ya cutar da ita, ko wani ya kama
su.
Kasancewar rana ce sosai, layin shiru babu kowa, suka tsaya
a ƙofar wani gate, ya ciro mukulli a aljihunsa ya saka ya buɗe, ya ce ta shiga.
Ta shiga sannan shi ma ya shiga ya rufe ƙofa.
Ta tsaya tana kallon gidan, ya jingina da gate ɗin ya tafi
tunani.
"Waye yake mini kokowa da ƙofa zai karya mini
gate?"
"Ɓarawo ne ya zo sace matar gidan" tayi dariya ta
ce "Da alama ɓarawon nan, bai san gidan wa ya zo ba ko? Ka bari mijina ya
zo ya same ka" tayi maganar tana fitowa daga falon, fuskarta ɗauke da
murmushi da tsohon cikinta.
"Wai da ke muka haɗa kuɗi muka sai rigar nan ne? Ki din
ga ɗaukar mini kaya kina sawa"
Ta tura baki ta ce "Kai da kaya mallakar wuya ne, da
kayan da mai kayan duk mallakin 'yar madara ne" tai maganar tana sakar
masa murmushi.
Nabila ta ce "Ya naga ka tsaya, ina ne nan?".
Yayi firgita ya dawo daga tunanin da ya tafi.
Ya tunkari ƙofar falon, zuciyarsa na bugawa da sauri da
sauri, ya saka mukulli ya buɗe.
Falo ne sosai, komai neat sai dai yayi ƙura sosai.
Ta tsaya tana ƙarewa falon kallo, taji wani abu ya kama
zuciyarta.
"Viper, nan ne gidanka da 'yar madara tana ina? Kuma
baka tsoron azo a kama mu?"
Bai ce mata komai ba yama wuce ya shiga bedroom ɗin, ya
tsaya yana ƙarewa ɗakin kallo, komai ya din ga dawo masa, tamkar mai mafarki.
Tana tsaye, ya fito da wani riyo a hannunsa ya zo gabanta ya
ajiye, yayi kneel down a gaban riyon, ya buɗe ya shiga fesawa kayan turaren
florie. Ya din ga ɗago kayan, na jarirai ne, komai na haihuwa yana ciki intact,
hatta zannuwa zamzam, bagaruwa, pad pampers komai akwai a ciki.
Duk wanda ya ɗago sai ya fesa masa turaren ya ajiye,
muryarsa na rawa ya ce "Ɗaya daga cikin ƙamshi mafi soyuwa a wurin jauhar
kenan".
Gaba ɗaya zuciyar Nabila ta tsinke, gabanta ya tsananta faɗuwa,
ta ɗauki kayan, ita ma ta kai hancinta.
"Yanzu tana ina? Ina kuma jaririn naga kayansa na
jariranta haryanzu?"
Ya ɗaga kai, yana kallon in da Nabila take zaune, ya ga
jauhar kwance a wurin, cikin jini, tana ɗago masa hannun tana la'ila ha illa
la, ya Allah.
Daga nan bai sake sanin in da kansa yake ba, sai ji yayi an
watsa masa ruwa mai tsananin zafi, da ratsa fata a jikinsa.
Ya yinƙura zai tashi a gigice, amma yaji shi a ɗaɗɗaure,
tamkar huhun goro.
Ya buɗe idanunsa da ƙyar cikin matsananciyar galabaita, amma
ya kasa magana, haka zalika wuyansa ya kasa tsayawa.
"Idan ya watstsake, ku cigaba da tuhumarsa, har sai ya
amsa laifin da bakinsa"
"Ok sir"
Suka cigaba da kwara masa ruwa mai zafi, amma sai dai ya
zabura ya ƙanƙame jikinsa, amma babu baki.
Suka kwance shi daga mugun ɗaurin da suka yi masa, sai dai
ana gama kwance shi, ya faɗo ƙasa jikinsa a sake.
Ɗaya daga cikin su ya ce "Haryanzu bai gama dawowa
hayyacinsa ba, ku ƙyale shi tukuna"
Indabo sai kaiwa yake yi, yana komowa a falonsa,ya rasa me
ma yakamata yayi, gefensa ga P.A ga kuma madaki a zaune.
"Wallahi kayi mini hauka madaki, ni ban san zaka yi
mini sakarcin ba. Bambancinka da Aminu kenan, abun da aka saka shi yake yi,
idan ka ga ya canza, to ya hango abun da ya fi naka ne, yanzu idan ya farka ya
tona mana asiri ya kenan?"
P.A ya ce "Honorable, ka kwantar da hankalinka C.P yana
hanyar zuwa nan, zamu ji mai zai ce mana"
Madaki ya ce "Honorable, da ka san hatsarin da yake
tattare da yaron nan, da baka ce haka ba, mugun shu'umi ne. Hodar nan da guba
na haɗata, kisa take yi har lahira, nayi mamaki da aka ce bai mutu ba, ba
laifina bane ba, nayi iya ƙoƙarina".
CP ne yayi sallama, ya shigo falon, suka amsa tare da mayar
da hankalinsu kansa, ya miƙa wa Indabo hannu suka gaisa. Cikin zaƙuwa indabo ya
ce "Yaya ake ciki C.P?"
"Eh to, maganar gaskiya fa ya farfaɗo, kuma yana daf da
watstsakewa a ko wane lokaci. Abun da muka yi guda ɗaya ne, a report ɗinmu, mun
shigar da cewa ya sha kayan maye ne, ya bugu ya halakka matarsa".
Indabo yayi shiru sannan ya ce "Kai naji daɗi, amma
kamar hanyar ba tayi ba sosai, idan ya buɗe bakinsa, zai iya faɗar gaskiya
fa"
C.P ya ce ba zamu bari haka ta faru ba, lokacin da muka je
gidan, mun goge duk wani abu da zai nuna hujjar wani ne ya shiga ya aikata
laifin ba shi ba. Sannan mun ajiye miyagun ƙwayoyi har da hodar iblis, da sunan
mun kama su a gidan. Idan za a fara sharia dole a samo ƙwararrun lauyoyi, kuma
a yi wa alƙalin kyakykyawan gani, ni dai daga ɓangarena komai zai tafi dai-dai
da yardar Allah. Tun da dama ya riga ya shahara kowa ya san ɗan daba ne"
Indabo ya yi ajiyar zuciya ya ce "Haka ne, na gode
sosai da sosai C.P, zaka ga saƙo da yardar Allah, kuma zan cika alkawarin da
nayi, muddin komai ya tafi cikin nasara, amma C.P ba zai yiwu ku yi masa wani
abu, ku kashe shi ba kawai?"
Ya ce "No, muddin wani abu ya same shi, mu kuma zamu
zama abun arziki, saboda sanarwar da kakinmu ya fitar mun tabattar da yana
hannunmu cikin ƙoshin lafiya"
"Shikenan babu laifi, na gode sosai da sosai" ya
sallami C.P ya tafi, ya ce "Aikin Naja'atu ya zo, P.A kira wo mini
ita".
***
"Ka yi magana ka amsa laifinka, ka sauƙaƙa mana kai ma
ka sauƙaƙawa kanka, idan ba haka ba mu zamu bi hanyoyin da zasu sama mana
sauƙi"
Al'amin ya ɗago da kyar, saboda a cikin mayen da yake, suka
yi dukan tsiya, tamkar sun samu jaki, jikinsa ya ƙara mutuwa, kowace gaɓa ta
jikinsa ban da ciwo, babu abun da take yi.
"Ka amsa, ka ce ka sha kayan maye ka kashe
matarka"
Gefen bakinsa duk jini, sun tuɓe shi, daga shi sai vest da
gajeren wando, ya sake ɗaga idonsa, karo na farko yayi magana ya ce "Ina
jauhar?"
"Ban sani ba, ni kake tambaya ina juahar? Bayan ka
kasheta?" Tsaki yayi, ya taƙarƙare ya yinƙura ya tashi tsaye, suka saka
kokara suka daki ƙafafuwansa, ya hantsila ya faɗi a wurin.
Duk abun nan da ake yi, da jibgar da yake ci, shi kawai
mafarki yake yi, jira yake yi ya farka, dan ba ya son baccinsa ya cigaba da
nisa, zai kai Jauhar asibiti da wuri.
A haka aka shafe kwanaki bakwai, amma Al'amin, yaƙi sakawa
ransa cewa gaske ne ba mafarki ba.
Kwanaki bakwan nan, babu wanda ya zo in da yake, ba wai dan
ba a samu masu zuwan ba, an hana kowa ganinsa.
Liti da walid, da sauran jama'arsa babu irin sintirin da ba
su yi ba, amma aka hana su ganin sa.
Mutuwar jauhar, ta karaɗe kowane gidan jarida, unguwanni
zuwa gidaje.
Abbu yayi kuka tamkar zai yi hauka, yayi dana sanin
kasancewar sa mahaifin Al'amin.
Gidansu jauhar kuwa, ba su san sun yi rashi ba, sai da aka
tabbatar da mutuwar jauhar, kowa kuka da zubar da hawaye.
Abbu yana kuka, ya sanya gwiwoyinsa a ƙasa, yana roƙon Baba
ya yafe masa, da ya san Al'amin zai kashe masa 'ya, ba zai yarda a aura masa
ita ba.
Baba ya girgiza kai ya ce "Alhaji Ibrahim, ni wallahi
haryanzu ban ji na yadda Al'amin zai kashe mini 'ya. Akwai abun da ya faru ni
ban yadda shi ya kashe mini jauhar ba"
Abbu ya ce "Wace hujja kake nema ko shaida bayan
wannan? Ni na haifi Al'amin, kuma kowa ya san yana ta'amalli da miyagun
ƙwayoyi"
Cikin kuka mama ta ce "Yaron nan ya cuce mu, bai yi
mana adalci ba, haihuwar ɗa irin jauhar a gidan nan, daga kanta an gama, ba ayi
ba, kuma ba za ayi ba"
Hafsa ta girgiza kai ta ce "Baba nima ina bayan
maganarka, ƴan kwanakin nan, ina zuwa gidanta sosai da sosai, ina haɗuwa da
shi, ita take bani labarin galabar da ta ci a kansa, da bani misalai
daban-daban da aurenta. Son da yake nuna mata a gabana ba ya jin kunyata ko
nauyina, suna matuƙar ƙaunar junansu. Har take gaya mini na tayata da addu'a,
yanzu sigari ce kawai damuwarta da shi, har sai da na ji raina ya biya, da irin
kalar soyayyar da suke yi wa junansu, dan haka gaskiya ban yadda mai zamani zai
kashe jauhar ba, mutumin da idan zata fita baya nan, yake sawa ana bibiyarta
dan kar wani ya kawo mata farmaki, mugwayen karnuka ya ajiye a layinsu, suna
gadinta lokacin da yayi tafiya, duk dan kar a taɓa ta, gaskiya ban yadda
ba".
Anty ma tana kuka ta ce "Babu abun da mai shaye-shaye
ba zai iya aikatawa ba, dan haka ba abun mamaki bane dan an ce ya kasheta,
Allah sarki jauhar wannan wane irin mummunan ƙarshe ki ka yi?"
A fusace Saifu yana kuka ya ce "Kar ki sake aibata mana
gawar jauhar, wallahi ba ta yi mummunan ƙarshe ba, ta bi Allah, ta yi wa iyaye
biyayya, ta yi biyayyar aure, idan ana nuna ɗan aljanna a duniya to jauhar ce,
koma wane irin mutum ne shi, ai ku kuka yi bita da ƙullin da ta aure shi, kuma
wallahi Allah ba zai bar kowane azzalumi ba, ita ta mutu ta huta". Haka
aka din ga musayar yawu, har sai da Baba ya tsawatar tukuna.
Da taimakon Naja'atu Bunkure, suka haɗa kai da lawyoyin
gwamnati, Indabo ya cika su da kuɗi, har da alƙalin kansa. Domin tsayawa tsayin
daka wurin tattara shaidu da hujjoji.
Haka zalika ta fito ta bayyanawa duniya cewa, zata tsaya
tsayin daka, har sai ta ga abun da ya ture wa buzu naɗi, sai an bi wa jauhar
hakkinta, na kisan gilla da viper ya yi wa jauhar, mussaman dama ya riga yayi
suna a harkar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi da kuma harkar daba.
Ranar fara shari'a, haka aka zo da mai zamani a cikin sarƙa,
yana ɗingisa ƙafa, saboda azabar da ya sha a hannun 'yan sanda, a kan ya amsa
cewa shi ya kashe jauhar.
Aka fara gabatar da shari'a, wani lawyer ya gabatar da kansa
a matsayin wanda zai kare Al'amin, bai taɓa ganinsa ba, sai ranar a cikin
kotun.
Aka gabatar da charges ɗin da ake yi wa Al'amin.
Ɓangaren tawagar lauyoyin gwamanti, da su Naja bunkure, suka
din ga gabatar da shaidun bogi, suka kawo ƙwayoyin da suka samu a gidan
Al'amin, tare da kawo bayanan likita, na cewa dukanta aka yi har ta kai ga rasa
ranta, da abun da yake cikinta.
Abun bai tsaya a nan ba, sai da aka kawo malam lawan, bayan
shaƙa masa wasu muhimman kuɗaɗe, ya zo ya bayar da shaidar Al'amin ya saba
dukan jauhar, idan ya je ya sha ya bugu, haka za su yi ta jiyo ihunta yana
dukanta, a ranar ma sun ji kukanta, sai dai ba su yi zaton zai kasheta ba.
Muryar Liti ce ta dawo da Al'amin hayyacinsa, dan duk
surutan da ake yi, bai san me ake cewa ba.
"Ƙarya kake yi dan ubanka, Viper ba ya dukan yar
madara, ba ita ba kowace mace ma baya duka, a matsayin ku na maƙota idan yana
dukanta, meyasa baku kai wa yan sanda ba, ƙarya kake maƙiyin Allah la'ananne,
Viper ba zai taɓa cutar da matarsa ba, ba shi ya kasheta ba" jami'an tsaro
suka yi waje da liti.
Sai dai wani irin ihu da Viper yayi, sai da wasu suka fara
gudu, ya daki katakon gabansa da ƙafarsa ya ce "Ƙarya ne, jauhar tana nan
a raye, gobe zata haihu, matata bata mutu ba"
Da ƙyar aka danne shi, Alƙali ya aika shi gidan prison, tare
da ɗage shari'ar.
Haka ya cigaba da buge-buge, tamkar zai jefar da motar gidan
yarin, sai da suka sumar da shi, sannan suka samu nutsuwa.
Tun daga wannan ihun, bai sake magana ba, ba cin abinci, sai
dai zai yi salla kawai.
Har aka yi zama na biyu a kotu, bai ce uffan ba, duk wasu
hujjoji Bunkure ce ta samar da su, lawyern gwamanti gabatarwa kawai yake yi.
Sai dai juyin duniya, ya yi magana, yaƙi yi.
Bunkure ta je gaban Al'amin ta tsaya ta ce "Amsa ɗaya
kawai kotu take buƙata daga bakinka, kai ka kashe matarka jauhar?"
Ya ƙura mata rinannun idanunsa, ta din ga yi masa wani irin
kallo, mai cike da rainin wayo.
Ya jinjina mata kai alamar eh.
A nan suka buƙaci a ƙarƙare shari'ar, ba tare da wata huɓɓasa
ba, lawyern Al'amin, ya ce ya yarda da duk abubuwan da masu gabatar da ƙara
suka gabatar. Daga haka aka sake ɗaga shari'ar zuwa wata guda.
Wata gudan da sai da ya shafe shekaru biyar a prison, ba a
cigaba da shari'ar ba, ba kuma a sallame shi ba.
Kullum burinsa shi ne ya farka daga mafarkin nan da yake yi,
shi dai ya san matarsa na raye, ba ya cin abinci baya iya bacci, ya koma tamkar
mahaukaci.
Sai dai lokaci zuwa lokaci yana yi musu ihu, da kiran
matarsa, ya kan kira sunan madaki da Indabo.
Lokaci lokaci, ya kan ga aiken abinci, hakan ya sanya ya
ƙara sakankancewa jauhar ce ke yi masa aike, bai sake ganin wani yazo wurinsa
ba, tsawon shekaru biyar ɗin nan.
Rana tsaka aka ce masa ya fita ya tafi gida an sallame shi.
A ƙofar prison ɗin ya tsaya, yana tuna lokacin da ta zo
tafiya da shi, lokacin da aka rufe shi, aka ce an kama shi da cocaine.
Bai tsaya ko ina ba, sai unguwarsu, da ƙafa ya taka ya tafi,
amma ya tarar da gate ɗin a rufe.
Sai yayi tunanin ta koma gida ne, dan haka sai ya fara
tafiya gidansu, dan tabattar wa.
Gidansu ya fara zuwa, rahila da yaranta, gaba ɗaya suka
dare, suka gudu ɗaki tana ihu ta ce "Ka fita ka kore shi, gashi can an
sako shi, Allah wadaran yan siyasa, sun sako masifa da annoba, wanda bai san
halacci ba".
Abbu ya fito ya kalli Al'amin, ya koma kamar wani mahaukaci,
a gigice ya nufo Abbu ya ce "Abbu, ina jauhar? Ta haihu ne? Ina abun da ta
haifa?"
Abbu ya ja da baya ya ce "Kar ka matso kusa da ni,
Jauhar tana gidan uwarka da ubanka, dama ka gaya mini zaka kasheta, kuma ka
cika alƙawarin ka Al'amin, na gode da muguwar sakayyar da ka yi mini, da ɓata
mana sunan zuriya. Ka fita babu ni babu kai, ka nemi wani uban bani ba, na
sallamawa duniya kai, ba zan cigaba da rasa makusantana, mutanen da nake ƙauna
ba saboda kai, ka je na yafeka a duniya"
"Na ji na yadda, amma ina jauhar? Sun ce idan na ba su
abun da suke so, zasu kai ni in da take"
"Sai dai ka bita kabari ka ɗauki ɗan naka, mara
mutunci, ka fita ka bar mini gida, bana ƙaunarka bana ƙaunar ganinka"
"Ba zai yiwu ba, wallahi sai kun fito mini da
matata" ya juya ya fita da gudu, ya tafi dabar su, incomplete building ɗin
da suke zaman shaye-shaye.
Su Walid suna ganinsa, suka rirriƙe shi suna kuka, ya watsar
da su ƙasa, ya ce "Walid, ina jauhar? Na san ta haihu ko?"
Walid ya tashi tsaye ya ce "Viper ka nutsu mana, ya aka
sako ka ne? Ba yadda bamu yi ba, a ƙarasa shari'arka mu ɗaukaka ƙara aka
ƙi"
"Dalla ina tambayar ku, ina jauhar, ko ta koma gidansu,
ku bani kaya na canza na je wurinta, na san hanata ganina aka yi"
Hawaye na zuba a idon liti ya ce "Viper, Ƴar madara fa
ba ta raye, ta rasu"
Al'amin yana zuwa nan a maganar, yayi shiru, yayi fatali da
kayan gabansa, ya fara wani irin haki, yana nema ya kurma ihu.
Nabila tana kuka, ta toshe masa baki tana girgiza masa kai.
Ya saka hannu, ya cire hannunta daga bakinsa ya ce "Ban
cancanci na haukace ba? Ban cancanci na nemi fansa ko ta wane hali ba
kenan?"
Nabila ta girgiza masa kai, kuka ya hanata magana.
"Na kashe matata, ni na kashe jauhar ɗina, halittar da
ta nuna mini tsantsar so da ƙauna"
"Ba kai ka kasheta ba"
Cikin tsawa ya ce "Ni ne, ni na kasheta. Meyasa da Abbu
ya ce mini zai yi mini aure, na ce zan kasheta, ya ce mini Allah ya taimaka?
Meyasa na kasa tuba na daina bangar siyasa da daba, a lokacin da zabra take ta
ankarar da ni illarta, mai yasa sakamakon laifina ya faɗa kan matata?"
"Astagfirullah, Viper kar ka yi saɓo"
"Meyasa ban karɓi ƙaddarata ba tun da farko, na furta
idan aka yi mini aure zan kasheta? Meyasa na jinkirta barin aikata laifi, sai
da na rasa mutane masu muhimmanci a sanadin daba da shaye-shaye. Daba da bangar
siyasa ta yi mini mummunan tabo, na kasa zubar da hawaye ko sau ɗaya tsawon
shekarun nan, meyasa ba zan haukace na huta ba.
Ina son matata, laifina ya shafe ta, ba ta ji ba bata gani
ba, na kasa yadda ta mutu, haryanzu ina ganinta ina ganin ɗana a jikinta. Ko
ban ɗauki fansa ba, ina fatan na haukace, ko na bita na huta. Ina ma jauhar ba
ta sanni ba, da yanzu tana nan tana rayuwa cikin farin ciki, bani da sa'a ko kaɗan
a rayuwata, duk wanda na saka sonsa a raina, sai Daba da bangar siyasa tayi
masa illa"
Huci yake yi, idanunsa suka rine zuwa ja mai ban tsoro.
Ta sake mayar da hannunta bakinsa, ta rufe masa, tana kuka
ta fara furta "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Innalillahi wa
Innalillahi raji'un, Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Astagfirullah wa
atubuilaihi"
A hankali ya fara maimaitawa shi ma, jikinsa na kyarma,
kamar wanda ake kaɗawa gangi.
Nabila ta ce "Ka yi i ajiyar zuciyan da kake
dannewa" ya kama ɗaya hannun nata, ya ɗora saitin zuciyarsa, yana wani
irin haki, wani irin bugu zuciyarsa take yi mai ban tsoro.
A take ya saki wata irin nannauyar ajiyar zuciya, tare da
hawayen da suka maƙale a tsakiyar zuciyarsa tsawon shekaru shida!
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin matsanancin tashin hankali, Nabila tana kuka ta ce
"Viper zuciyarka fa, dan Allah ka nutsu zata daina aiki, idan ta cigaba da
bugawa a haka, ka cigaba da istigfari da maimaita Innalillahi wa Innalillahi
raji'un" tayi maganar cikin damuwa, ƙara danna hannunta yayi a kan
ƙirjinsa, yana wata irin shaƙuwa mai haɗe da haki, numfashin sa na fita
sama-sama.
A jejjere zuciyarsa take bugawa da ƙarfin gaske.
Cikin tausayawa take kallon sa, Al'amin yana buƙatar kafaɗar
da zai kwanta yayi kuka, babu wanda ya fuskanci ainihin matsalar sa, kowa ɗora
masa laifi kawai yake yi, iftila'in da ya faɗa masa, kowa ya dare ya bar shi,
sai abokansa duk da suna iya ƙoƙarin su a kansa, amma ba abun da yake buƙata
suke yi masa ba.
Ji tayi ina ma tana da damar, da zata rungume shi, ta bashi
dama yayi kuka yadda yake so, ko zai samu afuwa a zuciyarsa, tsawon shekaru
shida, yana dakon baƙin ciki da damuwa, kuma ya kasa zubar da hawaye sai a
wannan lokacin.
Haka yayi shiru ya sunkuyar da kai, sai dai bai saki
hannunta ba, hawaye ne kawai yake zuba daga idonsa, taya shi take yi, sai dai
ta rasa me ma zata kuma ce masa, a tsorace take da kar zuciyarsa ta buga.
A hankali ya saki hannunta, ya goge hawayen sa, ya tashi
zumbur, ya tattare kayan ya mayar ɗakin, hatta kayan jauhar suna nan,
lokaci lokaci, su Walid ne ke zuwa su karkaɗe gidan su share, dan idan ya bushi
iska yana zuwa cikin dare, yayi ta tuna irin rayuwar da suka yi.
Yanzun ma yana shiga ɗakin, ƙwaƙwalwarsa ta nuna masa ita
zaune a kan gado, tana shirin dutse, gefe ga boti a kusa da ita a kwance, ya
mimmiƙe yana ta goge jikinsa.
Ta ɗago ta kalleshi tana murmushi ta ce "Manya gatan
wasa, me ake so ne ake ta kallona? Ko fankar ce?" Tayi maganar tana kashe
masa ido.
Gadon ya nufa da hanzari ya kai hannu ya riƙe ta, amma ya ga
pillow ne kawai a wurin.
Ya dafe hannunsa a wurin, daga baya ya fito jiki a sanyaye
ya ce "Mu tafi" Nabila ta saki niƙabinta tana ta kuka, suka nufi
hanyar fita, ya gyara facemask ɗin sa suka fita.
Yana fita yaga wasu daga magidantan layin, a ɗan tsaitsaye,
suka yi ido huɗu da malam lawan, ya zura da gudu ya shige gidansa, ya rufe
ƙofa.
Ya danƙi hannun Nabila ya din ga sauri da ita, maimakon su
bi titi, lunguna suka din ga bi, suna tafe yana haki, yana dafe ƙirjinsa.
A dai-dai wata kan kwana, ya saki hannunta, ya danƙo wani
mutum da yake zaune yana jin radiyo, yana cin karas, zuwa wani lungu.
Nabila ta ce "Me yayi maka shi kuma?"
Ya zaro iraƙi a ƙugunsa, ya saita masa a maƙoshinsa, ya ce
"Bani wayarka"
Jiki na rawa, ya ciro wayar, ya miƙa wa Viper.
"Ka janye mini mutanenka, zan yi walƙiyya, idan ba haka
ba, zan yi maka rami a maƙoshinka"
Mutumin ya diririce, ya ce "Ban gane me ka ke nufi
ba"
Ya ɗaga mutumin ya haɗa shi da bango da ƙarfi, ya ce
"Ka janye mini mutanenku zan tafi, idan na kuma magana, hanjinka zan naɗo
da wuƙar nan"
Mutumin ya ce "Ya aka yi ka gane ni, ka san identity ɗina?"
"Saboda tsohon mai laifi ne ni, ba yau na fara aikata
laifi ba" yana ƙoƙarin zira hannu a aljihu Viper ya riga shi, ya ciro
bindigar da take aljihun mutumin ya ce "Ka yi abun da na ce, ko na harbe
ka"
A razane Nabila ta ce "Viper bindiga ce fa, dan Allah
kar ka yi wani laifin mu shiga uku" bai kulata ba, ya sake saita mutumin
da bindiga.
Ya saka wayar a kunnensa ya ce "Zaku iya tafiya, we
missed the target" ya katse wayar ya ce "Sai ka bani bindigata na
tafi"
Viper ya ce "Ɗaga hannunka, ka wuce mu je" ya tasa
mutumin a gaba, tamkar ya kamo mai laifi, yana gana suna bin sa a baya, da ya
motsa sai ya ji Viper ya ce "Idan ka waiwayo zan fasa kanka da bindigar
nan" haka suka yi doguwar tafiya a haka, sai kuma ya ji shiru.
Ya waiwaya, ya neme su ya rasa, a rikice ya bi hanya, saboda
bindigar sa da take hannun Viper.
Yana shan wata kwana, ya ga abokin aikins a tsaye da
bindigar a hannunsa.
"Gata, tun da ya ritsaka nake biye da ku, a hanya ya
yar da ita, suka yi wani wurin, nayi ƙoƙarin bin su, amma ban cim musu
ba".
"Ohh shit, meyasa ba ka yi making wani move ba, wannan
ai shirme ne kayi"
"No, kar ka gargaɗe mu a kan haka, ka ce sai abun da ka
ce, kai ka ke son ka kama shi da kanka"
Ya fesar da iska ya ce "Kuma haka ne, amma gayen nan ya
bani mamaki, na rasa ya aka yi ya gane ni a cikin fararen kaya.
Kaga fuskarsa?"
"A'a sir, fuskarsa a rufe take ai, ban ganshi ba, ni
bayansa ma kawai na gani".
"Na so naga kammaninsa, ko wataran zamu sake haɗuwa,
suma informer's ɗin banzaye, da ba su sanar da wuri ba. Yi shiru ga oga Nasir
yana kiran waya"
Ya saka wayar a kunnensa ya ce "Hello sir"
"Ya ake ciki ne?"
"We miss the target sir"
Nasir ya ce "Kamar yaya?"
"Kafin mu je, ya bar unguwar, bamu tarar da shi
ba"
Nasir ya numfasa ya ce "Shikenan, ku dawo mu haɗu a
office, sai mu sake shiri"
"Ok sir" ya kalli abokin aikinsa ya ce "Mu
je,ya ce mu koma office"
Viper kuwa wata hanyar ya bi, suka ɓulla can wata unguwar
daban.
Sai dai suna tafe yana ta haki, yana haɗa hanya.
"Viper mu tsaya ka huta, kalli halin da kake ciki, ko
mu samu wani asibiti a duba ka, kar numfashinka ya ɗauke" bai ko nuna ya
san da shi take ba, sai da suka fita titi ya saki hannunta ya ce "Ki koma
gida"
Cikin damuwa ta ce "To kai kuma fa?"
"Ki tafi nace" yayi maganar da kyar, kawai ya tare
wani mai napep ya shige ya tafi.
Jiki a matuƙar sanyaye, ta koma chamber ta ɗauki motarta,
ita kanta ta san ikon Allah ne ya kaita gida, amma kusan gaba ɗaya ba ta
hayyacinta, tarin damuwa ce kawai cunkushe a ranta.
Ba ta san yar madara ba, ba ta taɓa ganinta ba, amma ƙarshen
labarin ya tsaye mata a rai, da wayonta ba a taɓa yi mata mutuwar da ta gigita
ta ta ji ta ba, sai dai jin wannan mutuwar ta gigita ta, ta ɗaga mata hankali.
A cikin zuciyarta take jin ƙaunar matar da ba taɓa gani.
A wannan karon ma tayi kuka mai isarta, ga uwa uba, tausayin
mai gayya mai aikn wato Al'amin, dan ita yar madara ta mutu ta huta, amma shi
da blame ɗin ya dawo kansa, shi ne babban abun a tausayawa. Wayoyinta suka
isheta da ringing, ta kashe su gaba ɗaya ta ajiye.
Ta din ga fatan Allah ya mayar da Viper maɓoyarsa lafiya,
dan ta tsorata da mummunan yanayin da ya shiga.
Sannan haryanzu labarinsa da saura, ba duka bane ba, amma
tana fargabar sake matsa masa son jin ƙarashen labarin, dan gudun kar ya sake
shiga mawuyacin hali kamar yau.
Tana ta saƙe-saƙe, sumayya ta yi sallama, ƙasa-ƙasa ta amsa,
sumayya ta shiga ɗakin tana mita. "Malama kin ce mini zaki zo, amma kin
shanya ni, bayanai ne suke ta fitowa a kan mutuniyar ki, ina son ki gana da
mutanen direct, na haɗa ku, amma ki ka ƙi zuwa"
Ji tayi Nabila tayi mata shiru, ta ce "Arfa meyafaru
ne? Kamar kuka ki ka yi fa"
"Kuka nayi sumayya"
Cikin rashin fahimta ta ce "Kukan me kuma? Ko duk a kan
shari'ar ne?"
"Sumayya komai ma, yakamata nayi kukan ne kawai"
"Arfa yakamata fa ace kin san kin girma, haba abu kaɗan
sai kuka, ki din ga miƙa wa Allah lamuranki mana haba Arfa".
"Arfa, Arfa" suka jiyo muryar Nasir yana ƙwala
mata kira.
Tayi shiru bata amsa ba, ya shigo ɗakin, ya tarar da ita a
zaune, ta jingina da gado.
"Ina magana ki ka yi mini shiru?"
Ta ce "Kaina ne yake yi mini ciwo"
Sumayya ta ce "Yaya ina wuni?"
Ya amsa da "Lafiya ƙalau sumayya, ya aiki?"
"Alhamdilillah"
Ya sake mayar da idonsa kan Nabila ya ce "Waye mutumin
da ya zo wurinki ɗazu a Office ɗin ki?"
Ta ɓata fuska ta ce "Na gaya maka client ɗina ne
ai"
"A'a arfa, na tambayeki wani irin case ne zaki tsaya
masa, kin ce is confidential ban san lokacin da muka fara ɓoyewa juna abun da
ya shafe mu ya shafi aiki ba. Mutumin nan yayi kama da masu aikata miyagun
laifuka, duk da ban ga fuskarsa ba"
Ta girgiza kai ta ce "Allah ya kiyashe ni hulɗa da masu
aikata laifuka, sai dai ko da mai laifin ne, a matsayina na lawyer babu ruwana
da laifin sa, zan bashi kariya ne kawai. A wurinku ne ku ke kama mai laifi, a
wurin lawyer babu ruwansa da mai laifi ko akasin haka, client ɗinmu ne a
gabanmu ba laifinsa ba".
Ya tsaya yayi shiru yana kallonta "Ban gane me ki ke
nufi ba"
Tayi murmushi ta ce "Ba wani abu da nake nufi yaya,
aikinku kamo mai laifi, mu kuma namu aikin binciko gaskiya komai ɗacinta"
Ya jinjina kai ya ce "I see, ɗazu informer's ɗin mu sun
sanar da mu Viper ya je gidansa, da shi da wata da ba a san ko wacece ba, sai
dai kan jami'anmu su je, ya bar unguwar" duk da ƙirjinta yayi dumm. Amma
cikin iya siyasa ta ce "Ikon Allah, lallai wannan Viper akwai shu'umi, ya
cika macijin gaske, wato lokacin da ya ga dama, sai ya baro raminsa ya fito
shan iska, to Allah ya shirye shi. Amma ya batun abokinsa da kake bibiya?"
Nasir ya ce "Nothing much, ya daina zuwa unguwar ma
kwata-kwata, abun har mamaki yake bani, da mun hari wani abu da muke son mu
kama shi, sai abun ya kuɓuce mana, amma muna nan muna ƙoƙari"
Nabila ta ce "Gaskiya abun da mamaki, Allah ya yi
jagora"
Ya amsa da "Amin, Sumayya ki din ga yi wa yar uwar nan
taki faɗa, bata ji ko kaɗan tana neman zunguro mana sama da kara, kasadarta
tayi yawa sosai"
Sumayya ta ce "Ana yi mata fa yaya, ka san halinta da
kafiyar tsiya ne, amma zata daina in sha Allah"
Ya jinjina kai ya ce "Allah ya sa" bayan ya fita
Sumayya ta ce "Arfa, waye yaya yake magana a kai, ina fatan dai ba wani
mai laifin bane ba, ko kuma wani abun ki ke shirin ɗaukkowa ba"
Nabila ta kalleta ido cikin ido ta ce "Kina son na ce
miki viper ne, ki je ki ji daɗin gaya wa waɗanda ki ke ba wa information a
kaina?"
Gaban sumayya ya faɗi ta ce "Information a kan ki
kuma?"
"Eh mana sumayya, ana bibiyata ta hanyarki, kina
bibiyar duk activities ɗina kina sanar musu. To ki gaya wa ko suwaye suka saki,
wallahi babu yadda suka iya da ni, gaba da gaba za su yi da ni, su karɓi abun
da suke so daga wurina, ba wai su fake da ke ba kina ba su information a kaina
ba"
"Nabila waye ya gaya miki haka?"
Nabila ta ce "Jira ki ke yi a gaya mini? Ni na ganoki,
sai dai na kasa yadda saboda ƙauna ba ƙarya ce ba, kuma wanda ya gaya mini ba
zai yi mini ƙarya ba, dan bai sanki ba, balle ya san alaƙarmu da ke. Please
sumayya You can leave, ko ganinki ba na son yi wallahi" Sumayya ta ce
"Nabila, ki tsaya mu fuskanci juna dan girman Allah"
"Babu wata fahimtar juna da ta rage tsakanina da mai
fuska biyu, ni da gaske na yarda da ke, ba zan bari a cutar da ke ba, mussaman
ayi amfani da ni a cutar da ke ba, amma ke gashi ana ƙoƙarin cutar da ni ta
hanyar ki. Koma waye yake bibiyar tawa, ki ce masa ya fuskance ni ya gaya mini
abun da nayi masa. Idan kuma a kan ayyukan da na saka a gaba ne, babu wani
mahaluki da ya isa ya hana ni abun da nayi niyya, ki tashi ki tafi"
Sumayya ta miƙe tsaye, kawai ta ɗauki jakarta ta fita, tana
tafe a hanya tana kuka, sam ba ta san da wasu kalamai za ta yi amfani ba, wurin
fahimtar da Nabila ba, sai dai tayi mamakin gaske, a kan wanda ya gaya wa
Nabila cewa ana bibiyar ta, da Nasir ne ya gaya mata, to da tabbas sai yayi
zancen yanzu a gabanta, kuma sai ya tuhume ta, amma sai dai bai yi hakan ba.
Bayan tafiyar sumayya kuwa, Nabila ƙanƙame pillownta tayi,
tamkar ta samu viper, ta cigaba da zubar da hawaye.
Viper kuwa a galabaice ya ƙarasa gidan da suke, gaba ɗaya
nema yake ya fita hayyacinsa, haki kawai yake yi, zuciyarsa na cigaba da wannan
matsanancin bugun.
Ɗan mama ne kawai a gidan, ya tashi ya riƙo Viper cikin
tashin hankali, ya shiga da shi ɗaki, ya kwanta a kan katifarsa, ya cigaba da
ajiyar zuciya, yana haki, ga wani abu da yaƙi gaba yaƙi baya a tsakiyar
ƙirjinsa.
"Oga Viper, meyafaru ne? Baka da lafiya ne? Meyake
damunka?" Ya jejjerawa Viper tambayoyin, amma babu guda ɗaya da ya iya
amsa masa, ya lumshe idanunsa ya na ta sauke numfashi.
Cikin sauri, ɗan mama ya kira Walid a waya, ya sanar masa
halin da Viper yake ciki.
Walid ya ce "Ka kula da shi, kar ka bari ya sake fita,
gani nan zuwa"
***
Madaki ne zaune a cikin dokar daji, a gaban wani mutum da
shi da yaronsa lakwari.
Ya miƙe ƙafarsa da ciwon jikinta yayi rami, mai zurfi, sai
wani irin kore ruwa ne yake fitowa, wurin ciwon ya kumbura suntum babu kyawun
gani ko kaɗan.
Mutumin ya ƙare wa ƙafar kallo sannan ya ce "Ya riga ya
yi maka illa, tabbas yana da makarin asirinka, dan kuwa ya karya shi ɓara, wuƙa
da kaifi, za su din ga tasiri a jikinka. Cikin tashin hankali da damuwa madaki
ya ce "Yanzu babu wani abu da za ayi a kai, idan ya so a kuma bani wani
asirin?".
"Gaskiya babu, yanzu dai magani zan baka, aje a haɗa
shi da diddigar maƙera, ka yi kwana arba'in ana sakawa ciwon, sai ya warke sai
kuma mu ga da abun da zamu ɗora".
Madaki ya yi shiru, saboda baƙin ciki, lokacin da aka bashi
asirin, an tabattar masa da babu wani wanda yake da laƙanin karyewar asirin,
sai shi wanda ya bashin, wanda yanzu ya mutu sai ɗan sa yanzu dan kuwa shi
kansa ɗan ma bai san makarin asirin ba, dan haka sun yi mamakin yadda aka yi
Viper ya samu.
Sun kamo hanyar dawowa kano, madaki ko iya magana baya yi,
babu tunanin da yake yi, da ya wuce wani mataki zai ɗauka a kan Viper, dan kuwa
karya asirin nan, dai-dai yake da karya alkadarinsa baki ɗaya.
Kiran P.A ne ya din ga shigowa wayar Madaki, sai da yayi da
gaske sannan ya ɗaga, domin kuwa gaba ɗaya ransa a jagule yake saboda tashin
hankali, da fargabar halin da zai shiga, idan aka fuskanci Alkadarinsa ya
karye.
"Madaki, ina ka shiga ne, yau kwanaki kusan huɗu
wayarka ba ta shiga, distinguish ya bayar da muhimmin aiki da kai kaɗai ne zaka
iya yin sa"
Madaki ya yi ajiyar zuciya ya ce "Aikin menene?"
"Idan kana gari ka shigo"
Madaki ya ce "A'a, na ɗan yi wani balaguro ne"
"Duk in da ka ke ka dawo, honorable ya matsa a kan
lallai a kama viper, yarinyar nan yake so a ɗaukko masa"
Madaki ya ce "Wace yarinyar kenan?"
"Wata lawyer ce, wadda na fara yi maka zancen nan"
Madaki yayi wani huci, ya ce "Bari na shigo garin, zan
yi maka magana"
P.A ya ce "Wai madaki lafiya kuwa? Kamar ba ka da
karsashi, meyake faruwa ne?"
"Basar ka ɗauke tunaninka a kan hakan, zan faso idan na
shigo gari" ya katse kiran yayi shiru yana tunani, tabbas ta bakin Al'amin
daga lokacin da suka ga ya daina yi musu amfani zasu watsar da shi.
***
Nabila ta kira layin Viper ya kai sau biyar, dan ta ji halin
da yake ciki, amma ba a ɗagawa, har ta fitar da ran zai ɗaga ta ji an ɗaga
wayar.
"Haba master, ka barni cikin zullumi da tunanin halin
da kake ciki, ka ƙi ɗaga wayata".
"Walid ne"
"Oga walid, yana ina dan Allah?"
"Gashi muna ta fama, jiki ya rikice gaba ɗaya".
Cikin tashin hankali ta ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un, wani abun ne ya same shi ne?"
"Ke zamu yi wa wannan tambayar, dan babu yadda bamu yi
da shi ba, ya ce sai ya fita, wurinki zai zo, zai yi wani aiki, mun yi iya
ƙoƙarin mu mu hana shi, amma ya ƙi saurarenmu, ko kin yi masa wani abu ne ki
gaya mana dan Allah"
"Wallahi Allah kenan, ban yi masa komai ba, office ɗina
ya zo ɗazu....
Walid ya katseta ya ce "Office kuma? Ya ce kiranki zai
yi a waya ku haɗu"
"A'a zuwa yayi, yayi amfani da wayata da computer ta
ta, daga nan ya ce zai ƙarasa mini labarin da ka fara bani, har gidansa muka
je" ta yi wa walid bayanin yadda aka yi.
Walid ya ce "To ki tayamu addu'a, jiki ya rikice, ɗan
sakewar da yayi kwana biyu, ta gushe ya koma yadda yake a da. Salla kawai yake
yi a kwance tun da ya dawo, sai dafe ƙirjinsa yake yi yana haki".
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Oga walid da ka
ƙarasa mini labarin nan, duk da haka bata faru ba, da na san halin da zai shiga
kenan, da ba zan takura masa ya gaya mini ba. Ubangiji Allah ya kawo masa
mafita, Allah ya bashi lafiya, ba zai yiwu na fito yanzu ba, dan Allah ku kula
da shi sosai. Zan zo in ga jikin nasa in sha Allah"
"Shikenan, Allah ya kawo ki" ya kaste wayar, yana
kallon in da Viper yake kwance, hannunsa ɗaya a kan ƙirjinsa, yana ta sauke
numfashi.
***
Duk wasu kalamai da Abdul yake tunanin idan yayi amfani da
su, zai shawo kan ramma, yayi amma fafur taƙi saurarsa, ya kaɗa ya raya, amma
taƙi saurarsa. Da ya addaba mata cikin tsawa ta ce "Wai me kake so ne
Abdul, ai ban yi zaton mugun zaluncinka ya kai haka ba, ka yi mini fyaɗe an ɗora
wa mutanen da suka taimaka mini sharri, wannan wace irin rayuwa ce?"
Ya sake kwantar murya ya ce "Ki fahimce ni dan Allah,
zan yi duk iya ƙoƙarina a kan mutumin nan ya fita a sake shi, dan Allah ki
daina ɗaga hankalinki"
"Dama dole ka ce haka mana, tun da kana ganin ko ta
halin ƙaƙa, kuɗi zasu ƙwatar maka komai, baka tunanin mawuyacin halin da zaka
jefa zukata, baka yi dacen hali ba ko kaɗan" taƙi sauraronsa, sai uban
miyagun maganganu da ta din ga yaɓa masa.
***
Bacci ya gagari idanun Nabila, ta ga tamkar an ƙara wa daren
tsawo, gashi ta kasa bacci, ƙarshe ta tashi tayi alwala ta tayar da nafila.
A gaggauce ta hana baba magajiya aikinta, ana idar da sallar
asuba, ta shiga kitchen ta dafa abun da take buƙata, da duku-duku, ta ɗauki
motarta ta fita.
Jin ƙarar mota ya sanya Nasir ɗaga labulensa ya duba, ya ga
babu motarta, ya kalli agogo, hari sam bai gama waye ba, ya fara tambayar kansa
ina tafi da wannan duku-dukun?.
Gudu ta din ga yi a titi, gani take yi tamkar kafin taje,
wani abun ya same shi.
Gari yayi haske sosai tana hanya, ta ajiye motarta a wani
wuri, ta fito ta tsaya ko zata samu abun hawa, amma bata samu ba, dan haka ta
cigaba da tafiya da ƙafa, gabanta na ta tsananta faɗuwa sai addu'a take yi.
Ta sha tafiya sosai, sannan ta samu abun hawa ta hau, ya
ƙarasa da ita.
Kasancewar da tafiya daga titi zuwa gidan da yake, haka ta
din ga haɗawa har da gudu, har ta ƙarasa tana ta haki, ta shiga da sallama, ta
ƙarasa ƙofar ɗakin, ɗan mama ta hango zaune a gaban Viper, yana ta rarraba ido,
daga shi sai shi a gidan.
Ƙwayoyi ne a hannun Al'amin, gefe ga allura a cikin sirinji,
amma sai haki yake yi mai ban tsoro.
Da sauri ta ƙarasa ɗakin, tana cewa "Wannan ƙwayoyin na
menene?"
Kafin ta ƙarasa ya watsa su a bakinsa, babu ruwa yake
ƙoƙarin haɗiyewa, ba ta san lokacin da cikin tsawa ta ce "Viper meye haka?
Ƙwayoyin meye wannan kashe kanka ka ke son ka yi?"
Bai kulata ba, ya cigaba da ƙoƙarin haɗiyewa, sai dai ya
kasa saboda abun da yake ji ya tokare masa a wuyansa zuwa ƙirjinsa.
Matse bakinsa tayi iya ƙarfinta, tana girgiza masa kai
"Kar ka haɗiye, wallahi hakan ba mafita ba ce ba, dan girman Allah ka zubo
su daga bakinka" hankaɗeta yayi yana ta huci.
Ɗan mama ya ce "Ki daina zuwa in da yake, zai yi miki
illa, wallahi aiken su Walid yayi, ni kuma yayi mini barazana da wuƙa, na samo
masa kuma wanda ya watsa a bakinsa sun yi yawa, sun yi masa ƙarfi"
"To waye ce ka kawo masa, ba sai ka gaya wa Oga walid
ba, ai ka san ba zai taɓa iya kisan kai ba"
Ta sake tunkarar Viper, sai haki yake yi mai haɗe da huci,
tamkar kumurcin, yana motsa bakinsa a hankali, yana son haɗiye ƙwayoyin.
Bakinsa ta sake matsewa, idanunsa sai buɗewa suke yi suna
lumshewa, wanda suka fara narkewa a bakinsa, sun fara rikita masa lissafi.
"Kalleni nan, ka fito da su na ce" tayi maganar
tana zare masa ido.
Ya ɗago a hankali ya kalleta, ta ce "Ka zubo da su, kar
ka haɗiye. So kake ka kashe kanka, idan ka kashe kanka, ɗan wuta zaka mutu,
kuma ko ka je lahira ka mutu ɗan wuta, yar madara kuwa muna saka mata ran tana
aljanna, kaga ba zaka ganta ba"
A galabice, ya buɗe bakinsa, yana zubo da ƙwayoyin da suka
rage a bakinsa, yana ta haki.
Shammatarta yayi, ya ɗauki sirinjin da yake gefensa, ya caka
mata a hannunta, wata irin ƙara tayi, cikin razani, dan ba ta yi tsammanin
hakan ba.
Ɗan mama ya rikice, ya nufo su da sauri, Viper ya kalli in
da ya caka mata sirinjin, ya kalli fuskarta yadda ta fara kuka, sai kuma ya
ankare da abun da yayi.
Sai ya rikice, ya zare sirinjin ya jefar ya riƙeta ya
ce "Zahra, me nayi miki? Yi haƙuri, na daina shan komai, ai nayi
miki alƙawari" yayi maganar yana ƙoƙarin kai hannunsa fuskarta, ya share
mata hawaye.
Walid ne suka shigo tare da liti, suka nufo su, liti ce wa
yake "Me ki ka yi masa?"
Viper ya yinƙura ya tashi, amma ya yanke jiki ya faɗi.
Suka rufu a kansa, suka ɗaga shi da kyar, Nabila ta gaya wa
Walid a halin da ta zo ta same shi.
Walid ya kalli ɗan mama, cikin tsananin ɓacin rai, ɗan mama
ya ce "Nifa bani na kawo masa ba, wallahi ɗaukko masa kawai ya saka nayi,
ban san a ina ya samo abun sa ba"
Suka mayar da hankali a kan Viper, sai dai ba maye kawai
yake yi ba, suma yayi, ga numfashinsa iya ƙirjinsa yake.
Nabila ta ce "Dole fa a kai shi asibiti, ko da hakan
yana nufin a kama mu ne baki ɗaya, lafiyar sa ita ce mafi muhimmanci a wannan
lokacin"
Walid ya ce "Haka ne, amma wani asibiti zamu kai
shi?"
Liti ya ce "Akwai wani asibiti a can bayan gari sosai,
sai dai na kuɗi ne, ina ga kamar can zai fi zama safe"
Nabila ta basu mukullin motarta, ta gaya musu a in da take.
Liti ya karɓa ya tashi ya fita.
Nabila kallonsa take cike da tausayawa, namijin gaske ne,
sai dai ta wata fuskar yana da raunin zuciya sosai.
Da liti ya kawo motar, suka yi kama kama, suka ɗauke shi,
suka shafo tafiyar nan da shi, suka fito titi.
Liti ne yake jan su a motar, ɗan mama da Viper da walid suna
baya.
Asibiti ne mai kyau, sai dai ya yi nisa da gari sosai da
sosai.
Ganin halin da yake ciki yasa suka karɓe shi da gaggawa,
Nabila ta tambayi ya tsarin Asibitin yake, da payment ɗin, aka ce su bari, a
fara ceto ransa tukuna.
Da aka tambayi sunan Al'amin, sai Walid ya ce "A saka
masa Muhammad Nura"
Liti ya ce "Meyasa baka bayar da normal sunansa
ba"
Ya bashi amsa da "Saboda tsaro"
A kan oxygen aka fara ɗora shi, saboda numfashinsa, sannan
aka fara sauran ƙoƙari a kansa.
Walid kallonta kawai yake yi, yadda take a rikice cike da
tashin hankali, babu ma alamar tana fargabar a kamata ko wani ya ganshi, ta
uzzurawa likita da tambayoyi.
Likitan yayi mata bayanin yadda Jinin Al'amin ya hau, ga
bugun da zuciyar sa take yi, fiye da kima kamar yadda ECG ɗin sa ya nuna, he's
at very risk of having heart attack.
"Subhanallah, dan Allah doctor kayi ƙoƙarin ka, na san
Allah ne mai komai, amma dan Allah ka taimaka"
"In sha Allah zamu yi iya a ƙoƙarin mu a kai"
Tayi masa godiya, ta tafi reception ita da litu, suka gaisa
da cashier ta tambayi, me za su yi depositing, na patient ɗin su da aka yi
admitting?.
Ya tambayi sunan mara lafiyan, liti ya gaya masa, ya duba
cikin system ɗin gabansa ya kalle su ya ce "Ai an biya"
Suka kalli juna da ita da liti, liti ya ce "Malam ka
duba sosai, ɗazu muka shigo fa, aka ce mu bari a fara bashi taimakon gaggawa,
ka duba ko masu irin sunan biyu ne".
"Shikaɗai ne me irin sunan da aka yi admitting yau,
Al'amin Ibrahim"
Suka kalli juna da Nabila, liti ya ce "Mu sunan mara
lafiyanmu Muhammad Nura"
"Wanda ya biya kuɗin, sunan da ya bamu kenan, ba shi ne
na ɗaki mai lamba 2 ba? Al'amin Ibrahim ya ce mana, ya turo kuɗi ya ce ayi masa
duk abun da yakamata".
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Nabila ta ce "Malam ya za ayi mu kawo mara lafiya, mu
zo kuma ace mana wani ya biya kuɗinmu, dama haka ake yi, wannan wane irin
abu ne, ka gaya mana bills ɗinmu mu biya, mu bamu san kowa ba"
Ya girgiza mata kai ya ce "No ma, ba zan karɓi kuɗinku
ba, na gaya miki an riga an biya"
"Waye ya biya?"
Liti ya ce "Kai bana son nuƙu-nuƙu, wanene ya biya kuɗin?"
"Nima ban sani ba, management ne suka turo mini
receipt, aka ce kar mu karɓi kuɗinku, an yi settling bills ɗin"
Nabila ta ce "Suwaye management ɗin?" Yayi shiru
yana kallonta.
"Malam kayi mini magana, ka tsare ni da ido, suwaye
management ɗin? Suwaye suka biya kuɗin?"
Liti ya ce "Ki yi magana a hankali, kar ki janyo
hankalin mutane kanmu"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ana bibiyarmu, wanda yake
wannan abubuwan ya san duk wani motsi da muke yi"
Liti ya jinjina kai ya ce "Nima nayi wannan
tunanin"
Nabila ta ce "Mu koma wurinsa, kafin mu san abun
yi" suka koma in da suka baro Al'amin da walid da ɗan mama.
Walid na ganin su ya ce "Yaya? Nawa ne kuɗin?"
Nabila ta ce "Kar ka damu, an biya"
Tayi maganar tana zama a gefen Viper, ta tsurawa fuskarsa
ido, kawai tuno yadda ya din ga kuka ta din ga yi, gaba ɗaya jikinta ya ƙara
sanyi.
Walid ya ce "Ba zaki ga likita ba, wurin da ya caka
miki allura?"
Ta girgiza kai ta ce "Bakomai, ni yanzu ta lafiyarsa
nake yi"
"Amma yakamata ki koma wurin aiki fa, ai muna tare muna
kula da shi"
"No, ko na tafi hankalina ba zai kwanta ba, ba zan iya
aikin ba, bari na jira naga abun da hali zai yi"
Likita ya sake shigowa, yana duba Al'amin.
Ya ce "Alhamdilillah, ina ga ya samu bacci, dan ya
farfaɗo daga suman"
Nabila ta ce "Masha Allah" ji tayi ya taɓa
hannunta, ta kalli hannunsa, ya yi mata alama ta matso.
Ta matsa ta kai kunnenta saitin bakinsa, a hankali ya ce
"Ki gaya masa a cire mini wannan abun na hancina bana so".
"Haba master, baka ga yadda kake numfashi da kyar bane
ba? Dan ya taimaka maka aka saka maka shi, dan Allah ka yi haƙuri ka ji, Allah
ya baka lafiya"
Ya sake cewa "Ki ce musu bana iya bacci, yayi mini abun
da zan yi bacci, kaina zai tarwatse"ta ɗago ta kalli likitan ta ce
"Doctor, ya ce dan Allah ayi masa allurar bacci, so yake yayi bacci baya
iya bacci"
Likitan ya ce "Ai mun yi masa, kuma da jinin ya sauka
zak yi bacci mai yawa mai daɗi in sha Allah"
Ta sake sunkuyawa, zata yi masa magana ya ce "Bana son
baccin, ba na son jinin ya sauka, bani da rabon sake yin su, Allah ya nuna mini
ranar da zan bi matata"
Babu wanda yake iya jin abun da yake faɗa, sai ita, muryarta
na rawa take yi masa magana a hankali cikin nutsuwa.
"Haba Al'amin, mai babban suna, shikenan bawa ba zai yi
imani da ƙaddara ba, tun da ka fuskanci kurakuran da ka yi a baya, ba sai mu
nutsu mu nemi mafita ba, yanzu idan ka mutu maƙiyanka sun ci galaba a kanka
kenan fa.
Dan Allah ina roƙonka ka janye wannan fatan da ka ke yi,
kuma in dai muna tare in sha Allah zaka yi bacci mai daɗi mai cike da nutsuwa
da kwanciyar hankali trust me.
Wallahi i feel your pain, bani na tsinci kaina a halin da ka
ke ciki ba, but ina jin zafi a zuciyata, in sha Allah you won't cry alone, an
cutar da kai, in sha Allah kuma sai in da ƙarfina ya ƙare a kan ƙwato maka
hakkinka, in sha Allah sai nayi sanadin dawo da farincikin ka.
Amma sai ka yi haƙuri, ka yi haƙuri, kayi haƙuri na san da
wahala, da ciwo, an yi maka illa, amma ina roƙonka a wannan karon kar ka
jinkirta tuba, mu yi ta addu'a, Allah ya taimake mu, ka kwantar da hankalinka
ka yi haƙuri, Allah da kansa ya rarrashi masu haƙuri a cikin Alqur'ani"
Yayi shiru yana sauraren Nabila, hawaye yana bin gefen
fuskarsa.
"Madam ya kuma kike kuka, mu da muke son hankalinsa ya
kwanta, jininsa ya sauka?"
Liti ya ce "Rabu da shi doctor, kukan shi ne samun
afuwarsa, mun gode sosai da ƙoƙarin ku.
Cikin kalaman hikima, da tausasawa, ta cigaba da yi wa Viper
nasiha, tare da bashi ƙwarin gwiwa, a kan cigaba da haƙuri, da kuma Addu'a.
Har bayan azahar, Viper bai gama frafaɗowa ba, haka Nabila
ta haƙura ta tafi gida, bayan ta ajiye musu abincin da ta zo da shi.
Sai magariba ta isa gida, Allah ya sa Abba baya nan, balle
ta sha tuhuma.
Message ne ya shigo wayarta, ta ɗauka ta duba.
"Arfa dan Allah kar ki yi mini mummunar fassara, ki
tsaya ki saurare ni mu yi magana, kin ƙi ɗaga wayata, hankalina a tashe yake,
amma ki bani dama nayi miki bayani, dan girman Allah"
Har jikin Nabila yayi sanyi, kamar ta yarda da maganar
Sumayya, sai kuma ta fasa, tayi mata reply da "No peace for wicked person,
kar ki sake tunanin zan yarda da maganarki" ta saka lambar a busy, ta
cigaba da sabgar gabanta.
Ta idar da sallar isha'i, tana zaune tana cin abinci, kawai
Nasir ya faɗo ɗakin, babu ko sallama. Ta ɗaga kai ta kalle shi, amma bata ce
masa uffan ba.
"Arfa"
"Na'am yaya"
"Ina ki ka je yau?" Ta ɗaga ido ta kalleshi ta ce
"Meyasa kake tambayata?"
"Ki bani amsa kawai"
Cikin ko in kula ta ce "Wurin aiki"
"Ƙarya ki ke yi, me ya kai motarki hanyar
ungoggo?"
Ta ajiye cokalin ta ce "Haba DSP, mutum nawa ne suke da
vibe a birnin kano?"
"Ya ina magana kina nema ki raina mini hankali, wurin
aikinki an ce baki je ba"
"Amma yaya ka san aikina ba na zama wuri ɗaya bane ba,
yaya ka ke yi mini tmbaya kamar ka ritsa ƴar ta'adda ne? Wataƙila harkar aiki
ne ta kaini wurin, bibiyata kake yi kenan? Ko kuwa meyafaru ko rashin yadda ya
shiga tsakaninmu ne?"
Ya sauke numfashi ya ce "Gaba ɗaya kwanan nan kin canza
Arfa, na je Division ɗin ungoggo kan wani case, a hanya na ga motarki, dan
lambar motarki ce"
"Abokin aikina ne ya ari motar, suka fita, ta sa ta
samu matsala. Sannan kuma ni ban canza ba, kai ne dai ka canza mini kwanan nan,
ni ban san me nayi maka ba, duk ka tsane ni, ka daina goyon bayan gaskiya, ni
na fara tsoron ko kaima ka fara karɓar cin hanci" tayi maganar tana ƙaƙalo
kukan kissa.
Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "No ki fahimce ni,
ke ɗin ce yanzu dole sai ana saka miki ido, kar wani abun cutarwa ya samar mini
ke, ki yi haƙuri ki daina kuka" a haka ya ɓuge da rarrashin ta, ta nuna
masa komai ya wuce, yana fita tayi masa gwalo, tare da ajiyar zuciya.
Ta ɗaukko wayarta ta ce "Bari na kira na ji ya jikin ɗan
marayan zakina" sai dai wayarsa a kashe, haka ta haƙura.
***
Gaba ɗaya ramma ta fita daga harkar Abdul, abun duniya ya
addabe shi, gashi ya kasa gano in da mahaifiyar ta take, babban tashin
hankalinsa kar ta gano cewar mahafiyarta ta ɓata. Dan bai san wane irin kalar
bori zata yi masa ba.
Ga Indabo ya uzzura masa, dan har an kai masa kuɗin aure, ga
shirye shiryen takararsa na ta ƙara yin nisa, amma gaba ɗaya hankalinsa baya
kan takarar. Abokansa sai mita suke yi masa a kan duk ya canza, ga aurensa an
saka su fara shiri, amma ya kasa mayar da hankali a kai, sun kasa gane kansa
gaba ɗaya.
Babu wanda ya tsaya saurara da bashi amsa a kan surutun da
yake yi.
Yana zaune yana kallo, amma hankalinsa ba a kan kallon yake
ba, tunani kawai yake yi.
Ramma ta ƙaraso kansa ta tsaya, ya ɗaga kai ya kalleta, ya
tashi zaune sosai ya ce "Rahama, ya aka yi ne?"
Ta ƙaraso ta durƙusa a kan gwiwoyinta, hawaye na bin
fuskarta ta ce "Abdul yasar, dan son da kake yi wa Allah da annabinsa, ka
mayar da ni gaban mahaifiyata, naga message a notification ɗin ka, wai aure
zaka yi, dan girman Allah ka mayar da ni wurin uwata da ɗan uwana, na yadda zan
ƙarasa rayuwata, a rushen zan tattara ta na rayu, ba ma na saka ran zan zan yi
aure, na yarda na rayu a haka"
Ya kalli ramma ya ce "Daga ganin message sai ki ce aure
zan yi? Bincike ki ke yi mini kenan? To ni ba wani aure da zan yi ".
Cikin kuka ta ce "Ka daina yaudarata Abdul, ka rabu da
ni, idan kana son iyayenka, na gaji, na gaji na gaji da haƙuri, da fatan zaka
mayar da ni gida, ka ƙyaleni dan girman Allah, ai ka gama morar abun da kake so
zuwa yanzu, kowace irin ƙishirwa ce ka kasheta zuwa yanzu ka rabu da ni dan
Allah " tayi maganar cikin ɗaga murya.
Abdul ya kalleta a tsanake ya ce "Kin manta alƙawarin
da ki ka yi mini ne?"
"Babu wani alƙawari da nayi maka, ni ban san wani
alƙawari ba, ka mayar da ni gida"
"Wallahi ƙarya ki ke yi ki rusa maganar da muka yi da
ke, da alƙawarin da ki ka yi mini"
"Ka yi mini duk abun da ka ga dama, amma ni dai ka
sakeni na koma gida, idan duk matan duniya ne ka je ka aura, ban damu ba, amma
a yanzu tun da dai ka gama da rayuwata dan Allah ka rabu da ni"
Abdul ya tsura mata ido, yadda take kuka wiwi har da majina.
Ya saukko daga kan kujerar, ya zauna a gabanta ya ce
"Rahama kishina fa ki ke yi"
Kamar zata kai masa mari ta ce "Ƙarya ne, Allah ya
kiyayeni ya tsare ni da kishin ƙazamar halitta mara tsoron Allah kamar ka, ni
kishin rayuwata nake yi"
Ya sauke numfashi ya ce "Zan mayar da ke, amma sai kin
cika mini alƙawarina, sannan kin haifa mini ɗa sannan zaki koma gida, kin ga
idan kika haihu duk duniya babu wanda ya isa ya raba ni da ke" yayi
maganar yana share mata hawaye.
"Abdul ba zan taɓa yafe maka ba, na bar ka da
Allah"
"Duk cikin kishina ne, matsayin matar da zan aura
daban, naki ma daban, you are like my guest house, wurin hutawa ta da nishaɗina"
Jiki a sanyaye ta ce "Ka cuce ni Abdul, duk saboda ina
'yar talakan ƙauye, mara gata mara galihu"
Ya girgiza mata kai, ya haɗe bakinsa sa nata, wata irin
ajiyar zuciya take yi, a hankali ya cire bakinsa daga nata, ya kalli idanunta
ya ce "Iya wuya rahama, ina tare da ke, ban ga wanda ya isa ya raba ni da
ke ba. A lokacin da maza da yawa suke gudun matan da suka lalata, ni a dai-dai
lokacin soyayyar yarinyar da na lalatawa rayuwa ta yi mini kamun kazar
kuku".
Jiki babu ƙwari ta cw "A hakan? Wace irin soyyaya ce
zaka yanke mini farincikina ba tare da wani dalili ba, bana sonka Abdul ko kaɗan"
"Ki saurari zuciyarki, kina jin zafin abun da nayi miki
ne kawai, amma kina so na rahama, nima kuma ina matuƙar sonki"
"Da ban yi wa kaina, da mahaifiyata adalci ba, idan na
fara sonka Abdul yasar"
"Zuciyar ki, cike da ƙuruciya, kina ƙoƙarin sakawa
kanki ƙiyayyata ne ta ƙarfin tsiya ne".
"Wallahi wannan ba so bane, ka gama lalata ni, ka samu
abun da kake so, kuma ka ce sona kake, me yayi saura?"
"Kin san abun da na ɗauko ki ki yi mini, kuma na daina
kamar yadda ki ka buƙata. Wuri ɗaya nake kwana da ke nake tashi, amma na daure,
ban sake yi miki ba, kuma na lazumci istigfari kamar yadda ki ka gaya mini. Kar
ki saɓa alƙawarinmu mana. Wa ki ka taɓa ganin ya lalata yarinya ya bita kuma
yana so? Ke kin san waye ni a garin nan da ƙasar nan. Na fiki shekaru, da ilimi
da tarin dukiya, amma gaba ɗaya na bar abun da yake gabana na tattara hankalina
a kanki, ki yafe mini mana sweetheart, ki yarda ki so ni, zan goge laifukana
zan kuma mayar da ke wurin mama in sha Allah"
"To yaushe?"
"Very soon, da zarar kin yafe mini, kuma kin cika mini
alƙawari"
Ramma ta share hawayenta ta ce "Abdul ta yaya zan haihu
da kai, in kalli duniya in ce musu me? Baga mata nan zaka aura ba, ba sai ku
haihu ba?"
"Naki nake so please" yayi maganar yana sumbatar
goshinta, cikin tsananin so da shauƙinta.
***
Yau ma uban sammako Nabila ta yi, ta tafi asibitin da Viper
yake, sai dai ba ta ɗauki motarta ba.
Yanzu ma ɗan mama ta tarar, yana ta sharar uban bacci, babu
liti babu Walid.
Viper kuma yana zaune, ya jingina da bango idanunsa a
lumshe.
Murmushi tayi, tare da farin cikin ganinsa a zaune.
Ta ƙarasa ta zauna ta ce "Yallaɓai, good morning, ya
jiki? Alhamdilillah na ji daɗin ganinka a zaune" sai dai kamar mai bacci,
bai buɗe idonsa ba.
Hannunsa ta kalla, ɗaya da drip, ɗaya kuma kamar lazumi yake
yi. Wani irin farinciki ya kama Nabila.
Wani baƙin abu ta hanga, a gefen pillown sa, ta saka hannu
ta janyo, ta ce "Menene wannan, ko kayan da zaka canza ne?" Tayi
maganar tana buɗewa.
"Wannan rigarka ce?" Buɗe idonsa yayi ya kalleta,
cikin wani irin zafin nama ya fizge rigar daga hannunta, ya hau waige-waige.
Ta ce "Menene? Meyafaru?"
Ya kalli in da ɗan mama ya saki baki yana bacci, ya kalli
taga babu hanyar shiga ko fita ta tagar, ya sake ɗaga rigar.
Baƙar riga ce shirt, mai ɗauke da hoton tambarin dragon a
gefen rigar, bayanta kuma an rubuta wasu alphabets, da bai bar Nabila ta
karanta ba. Duk da jikinsa babu ƙwari haka ya saka ƙarfin sa, ya yayyaga rigar,
yana cigaba da waige-waige.
Cikin rashin fahimta ta ce "Wai me yake faruwa
ne?" Ya girgiza mata kai, ya sake jingina.
Nabila ta kalle shi ta ce "Akwai damuwa fa, jiya an yi
settling bills ɗin ka, sai dai bamu san waye ba, an ƙi gaya mana ko
wanene" ya ƙura mata ido, ta jinjina masa kai, alamar da gaske take.
"Dan Allah ka gaya mini, menene yake faruwa ne, bai
kamata ka ɓoye mini komai ba, tare fa zamu yi gwagwarmayar nan" Sai ya
lumshe idanunsa ma, yaƙi kulata.
"Haba master, yar suganka ce fa, talk mana" a
hankali ya fara kaɗa ƙafa, amma bai yi magana ba.
"Sweetheart" ta faɗa tana dariya ƙasa-ƙasa.
"Sweetheart magana nake fa" sai ya kwanta ya juya
mata baya baki ɗaya.
"Am sorry wasa fa nake yi maka, ya ƙarfin jikinka to,
ina fatan akwai progress, kana samun sauƙi?"
Ya girgiza kansa alamar "A'a"
Ta ce "Ohh ni Nabila ina ganin mulki yau, Allah dai ya
jaddada rahama da Fatima jauhar, ta yi ƙoƙari sosai"
Ya ce "Amin" tausayin sa ne ya sake kama ta, ta ce
"To tashi ka karya, na san yanzu za a zo yi maka allurai, kuma na san kana
jin yunwa"
Bai yi magana ba liti ya shigo da leda a hannunsa, ya kalli ɗan
mama da yake ta bacci, ya dake shi da ƙafarsa ya ce "Tashi, ɗan asara,
idan ma sace shi za ayi, kana kwance ka shanya baki kamar fatarin mata kana
bacci" ɗan mama ya tashi yana mutsutsuka ido.
Jauhar ta kalleshi ta ce "Ina kwana?"
Ciki ciki ya amsa, ya dafa Viper ya ce "Maza ya ne, ya
jikin?"
"Alhamdilillah"
"To masha Allah, ga brush ɗin da toothpaste, ka wanke
bakin, yanzu Walid zai kawo abinci, sai ka yi wanka ka canza kaya"
Ya yinƙura ya tashi zaune, ya ƙurawa ɗan mama ido, sannan ya
ce "Kai waye ya shigo ɗakin nan jiya da daddare?"
"Likita ne, sai mai bada magani Nurse, sukenan"
"Ƙarya kake yi"
Ɗan mama ya ce "Wallahi sukaɗai na gani"
Liti ya ce "Dama ya kwanta yana ta uban bacci, ya za
ayi ya san me ake yi? Ina fatan ba wani abun ne ya faru ba?"
"Babu komai"
Da Al'amin ya shiga banɗaki, sai Nabila ta fita tana waya da
barrister Habib, ya ce lallai yana son ganinta, Sumayya T ladan ta turo wasu
mata, kuma zasu taimakawa aikinta a kan bunkure.
Nabila ta yamutsa fuska ta ce "Ka sallame su kawai,
babu buƙatar na gansu"
"Kamar yaya, abu mai muhimmanci da ki ke nema, ki ce a
sallame su"
"To ai nayi nisa ne, yaushe na bar abun da nake yi na
zo"
"Ki bari koma menene ki taho yanzun nan" to kawai
ta ce masa, ta ajiye wayar.
Ta cikin niƙabinta, take ƙarewa asibitin kallo, wurin
cashier ta sake zuwa, sai dai yau wata mace ce. Suka gaisa Nabila tayi mata
bayanin abun da ya faru jiya, ta buƙaci ta dubo receipt ɗin da aka turo musu na
biyan kuɗin, ta ciro ta bata.
Ta shiga computer ta duba, ta kalli Nabila ta ce "Ban
ga receipt ba, kawai an saka bill settled"
"Ina ne ofishin MD, ko admin na asibitin nan, dole fa a
nemo wanda ya biya kuɗin nan"
Ta ce "Ba sa shigowa da wuri, amma maybe zuwa
anjima"
Nabila ta juya ta koma ɗakin Viper.
Ya canza kaya ya zauna a kan gadonsa.
Har walid ma ya zo, ya buɗe masa wainar shinkafa ta sha
ƙuli-ƙuli, yana lallaɓa shi ya ci.
"Barrister har kin zo ashe?"
Ta ce "Eh oga Walid, na zo tun ɗazu, naje likita ya
duba ni, allurar da master ya caka mini jiya, hannuna ya sage" da sauri
Viper ya kalleta.
Walid ya ce "Subhanallah, Allah ya sauwwaƙe ya ƙara
afuwa"
Ta kalli wainar gaban Viper, ta ce "Oga walid ɗauke
wainarka, na dafo masa abinci.
Ta janyo ledar viva daga ƙarƙashin gadonsa, ta buɗe food
plask, ta ɗaukko mini tea flask ɗin ta, ta haɗa masa tea.
Faten dankalin turawa ne, ya sha ganye sosai da nama, sai
ƙamshi yake yi duk ya cika ɗakin da ƙamshi.
Ta miƙa masa shayin ta ce "Bisimillah ranka ya daɗe,
kaga tea ne, da ɗuminsa sai ka samu cikinka ya warware, kaga tun jiya baka ci
komai ba, ina fatan Allah ya baka lafiya da wuri, mu cigaba da aiki muna
addu'a, in sha Allah sai mun dangana da nasara"
Ya ɗaga kai yayi mata wani irin kallo, ta ce "Ba danni
ba, dan Allah idan baka ci ba ba zan ji daɗi ba, dan kai na girko na kawo maka.
Lafiyarka na da matuƙar muhimmanci a wurina please mana, ka karɓa" ya miƙo
mata hannu, ta saka masa kofin tana kallonsa tana murmushi.
"To yi bisimillah ka fara sha".
Ɗan mama ne yake ta ƙoƙarin yin dariya, amma yana jin tsoro,
ganin yadda aka bar Walid da busashshiyar wainarsa. Liti kuwa ƙyaƙyatawa ya din
ga yi ya ce "Walid, miƙo mana wainar nan, mu ƙaddamar mata"
"Sannu maye, aikuwa ba zaku ci ba, ku ci kanku"
Nabila murmushi ta yi, ta cigaba da yi wa Viper hira, cike
da tausayawa, da bashi ƙwarin gwiwa a kan haƙuri da ƙaddara.
Sannu a hankali yake cin abincin, har ya cinye tas, ya
shanye shayinsa.
Wani murmushin ta sake yi masa, ta ce "Alhamdilillah
ala kulli halin. Allah ya ƙara maka sutura da ingantacciyar lafiya, ya baka
tsawon rai ya bamu nasarar ɗaukar fansar abun da aka yi mana. Har cikin raina
nake jin zafin abun da ya faru da kai, but before then. Please promise me ka
daina z1y ³y2ubar da hawayenka, wanda ka yi ya isa. Kuma kayi mini alƙawarin ba
zaka sake shan ƙwayoyin da za su illata mini kai ba"
Liti ya tashi ya ce "Nikam nayi waje, wannan wace irin
fitsara ce?"
"Ka kalleni mana dan Allah" ya ɗaga kansa ya
kalleta.
Duk da idanunsa sun yi mata nauyi, amma ta ce "Ka ce
Nabila, nayi miki alƙawari ba zan sake shan miyagun ƙwayoyi ba, ba zan sake yi
wa kaina allura ba, zan baki cikakken goyon baya in ɗauki fansata ta hanyar da
ta dace"
"Tashi zan kwanta" ya faɗa a taƙaice.
Duk wannan zubar da ta gama yi, ba su ne a gabansa ba, kawai
ta tashi zai kwanta.
Ta fuskanci aiki ne jawur a gabanta, ba ta sare ba taƙi
tashi, ta kuma ƙi magana.
Ya ture ta, ya raɓa ya kwanta ya juya mata baya.
"Allah ya baka lafiya ya jaddada rahamarsa ga
marigayyiya jauhar".
"Amin ya Allah, na gode" yayi maganar idanunsa a
lumshe.
Tayi murmushi jin ya amsa, ba ya wasa da duk abun da ya
shafi Jauhar.
Walid ne ya rakota, take ce masa "Ku yi haƙuri da wasu
abubuwan da zaku ga ina yi, ina yi ne saboda sama wa ƙwaƙwalwarsa nutsuwa, idan
ba haka ba zai iya rasa hankalinsa baki ɗaya"
Walid ya ce "Karki damu na fahimce ki, ki rabu da liti,
ba kan gado ya cika ba dama".
***
Ramma na kwance a jikin Abdul, yana waya da mahaifiyarsa,
tana yi masa magana a kan haɗa lefensa, ya ce su yi duk abun da yakamata, yau
zai je asibiti ne, zai yi tiyata cikin dare, dan haka yayi busy. Ya kashe
wayar, ramma ta motsa tana ƙoƙarin tashi ya riƙe ta ya ce "Beb, ina zaki
kuma?"
Rai a haɗe ta ce "Na gaji da kwanciyar tashi zan
yi"
Ya tashi zaune ya ce "Haba rahama, nifa duk wani
motsinki ina gane me kike nufi, ai na baki haƙuri, kin san dalilin auren
nan.....
"Ni cewa nayi na damu da aurenka? Ina ruwana ne ni
damuwata na koma gaban iyayena"
Abdul ya ce "Zaki koma, amma sai Allah ya sa kin samu
ciki kin haihu, am doing this for your own benefits, saboda ke duk nake
haka".
"To bana so, ka daina"
"Haba sayyada, ba fa zina zan yi ba aure zan yi, kin ce
in yawaita istigfari Allah zai yafe mini, to ke kuma kin ƙi ki yafe mini, ki yi
amfani da iliminki mana haba sayyada rahama"
"Ba wata sayyada, sayaddar da ka kafawa ƙahon zuƙa sai
ta haifi ɗan shege ko?"
Kawai ya kama dariya, ya ce "Ke dai ba a iya miki, idan
an yi nan sai ki yi can, anjima zan kai ki shan ice cream mu ɗan fita mu
zagaya".
"Ba zan je ba"
Ya ce "Shikenan huta roro, na ɗauki amaryata mu
je"
Tayi tsaki, ta sauka daga kan gadon, ta nufi toilet.
***Bunkure ta fito daga shari'a kenan, ta nufi motarta, ta
tarar da Nabila a tsaye tana jiran isowarta.
Ta tsaya ta kalli Nabila, Nabila ta kalleta ta ce "Na
je office ɗin ki sau biyu, an ce ba kya nan, kin yi balaguro, da ki ka dawo
kuma, bani da isashshen lokaci.
Ina son sanin in da ramma take, ita wadda aka yi wa fyaɗen,
da shi kansa likitan da yayi documenting ya tabattar da an yi mata rape, ba wai
takarda kawai ba.
"Ke, kin fara wuce gona da iri fa, kar ki bari na
waiwayeki, nayi yinƙurin ɗaukar mataki a kanki"
"Wane matakin kenan? Harka ce ta aiki fa, idan kina da
gaskiya menene na ɓoye-ɓoye. Nayi mamakin yadda kina mace, once a rape victim,
amma ki zama tsanin kare masu laifi. Na san kin ga shaidar da na gabatar a
kotu, ta sautin muryar mahaifiyar ramma, kuma ko sama ko ƙasa an nemeta an
rasata yanzu. Shikenan idan kina taƙama da kun saye lawyoyi da alƙalai, ki
shirya motsi na gaba da zan yi.
Sai na bankaɗo duk wani shu'umanci, da zalunci da ki ke yi,
kuma ko a ina kuka ɓoye ramma, sai na tona muku asiri, na tonawa wanda yayi
mata fyaɗe asiri. Kar ki manta ɗan hakin da ka raina....... Bata sake cewa
komai ba ta tafi ta bata wuri.
Wayarta ta ɗaukko ta tura wa Indabo message. "Yakamata
ka motsa a kan yarinyar nan, ta fara wuce gona da iri"
Kasancewar ta sha zirga-zirga, a gajiye ta ƙarasa office ɗin
su.
Wurin Barrister Habib ta fara nufa, tana zuwa ta tarar da
Sumayya da wasu mata su biyu, a Office ɗin Barrister Habib suna jiranta.
Suka gaisa da Habib, ta juya ta fice, zai yi magana, Sumayya
ta ce "Bari na je na same ta.
Ta iske Nabila a office ɗin ta, ta ce "Arfa, tun safe
fa bayin Allah nan suna jiranki, har na zo nima, baki zo ba ina ki ka je ne
haka?".
"Sumayya wai baki da zuciya ne, alaƙa da ke ce bana so,
na menene zaki din ga bibiyata kuma?"
"Nabila, dan Allah ki tsaya mu yi magana, mu fuskanci
juna dan Allah"
"Babu wani abu da zan fuskanta, ni kin riga kin sire
mini, ki fita ki bani wuri, ko ni baki wuri" Sumayya ta tsaya tana kallon
Nabila.
Nabila ta zo zata fice, Sumayya ta riƙe ta, ta ce "Ni
yakamata na fice na baki wuri, na san nayi kuskure amma yakamata ace ko sau ɗaya
kin saurare ni.
Tabbas ina bayar da duk wasu bayanai, da aka nema a kanki,
amma ni baki san a wani hatsarin rayuwata take ciki ba, domin kare taki. Ni
'yar halak ce, zan daina binki dan ki saurare ni, amma zan cigaba da aikin da
aka bani a kanki. Idan kin ga dama, ki saurari matan can, idan kuma kin ga
dama, ki kore su, matsalarki ce ba tawa ba" ta ja da baya, ta buɗe ƙofa ta
fita.
Ta so bin bayan sumayya, amma sai ta fasa, Sumayya ta faɗi
maganganu masu muhimmanci, da yakamata ta tsaya ta ji menene, amma sumayya ba
ta fushi, idan kuma tayi tana da wahalar sha'ani, dan haka bata bi bayanta ba
ta koma wurin barrister Habib da wannan matan.
***
Ƙarfe biyar Al'amin ya koma maɓoyarsu, bayan su Walid suna
ta fama da shi, ya ce a sallame shi, sun ce sai ya gama warwarewa, shi kuma ya
san akwai hatsari zamansa a asibitin, suna fita salla ya fice daga ɗakin, ya
bar Asibitin.
Sai dai yana shiga ɗakinsa, ya tarar da wata baƙar rigar,
irin wadda aka ajiye masa da safe a asibiti, ya ɗaga ta ya juya, irin waccan ce
sak.
Ita ma a take ya yayyagata, ya watsar, ringing ɗin waya ya
ji a ɗakin, ya duba ya ga wata ƙaramar waya keypad, wata lamba ce ke kiran
wayar.
Ya ɗaga ya saka a kunnensa.
"Al'amin Viper, ka daina jayayya da ƙaddararka, bin
wannan ƙaddarar itakaɗaice mafitar da ta rage maka, ka karɓi kayan da muka
baka, ka dawo gida Viper" aka katse kiran, ya bi lambar, amma aka ce
lambar dose not exist. Yayi jifa da wayar ya ja da baya ya tsaya yana huci.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Ya cigaba da zazzare ido, yana kallon ɗakin, ya ɗauki wayar
da ya watsar, ya sake haɗata, ya kuma kiran lambar, amma a sai ace masa lambar
dose not exist.
Ya fita waje, ya zagaye gidan yana dube-dube amma bai ga
kowa ba, ya koma cikin gidan ya ɗauki wayar da rigar da ya yayyaga, ya shiga
banɗaki, ya watsa su a masai ya fito.
***
Nabila kuwa bayan tafiyar sumayya, ofishin Barrister Habib
ta koma, suka sake gaisawa da matan nan, ya ce "Ina sumayyan?"
"Ta tafi gida ne, na ce gani me yake tafe da su
ne?"
Ya kalle su sannan ya kalli Nabila ya ce, maganarki da ki ka
yi, su sumayya T ladan suka saka a radio, a kan Barrister Naja'atu Bunkure, shi
ne ya sanya suka zo, su sanar miki da wasu abubuwa da zai taimaka miki".
Nabila ta ce "Masha Allah, bari na aika baba masinja,
ya sayo musu ruwa da lemo, naga azahar ta wuce, kafin nan nima nayi salla"
Ya ce "To babu laifi"
Tayi salla ta dawo, suka zauna da matan, ɗayat ta fara bata
labarin abun da ya faru "Ni 'ya ce da ni, mun rabu da mahaifinta, tana
wurin babanta, yayi mata auren dole, take ta guje-guje saboda ba ta san mijin.
Ake ta fama har tayi yinƙurin kashe kanta, magana har gidajen rediyo, ta turo
wakilanta, suka tafi da mu can office ɗin ta, ta ce aure ba dole bane ba, dan
haka dole a kashe auren nan. Da fari na so ayi sulhu yarinya ta koma ɗakinta,
tun da bama tare da ubanta.
Na din ga yi mata nasiha, a kan tayi haƙuri, tun da babanta
yana ta tsine-tsine a kan ta bujire masa, ta haƙura ta yarda, amma matar nan ta
ce sai an kashe auren, zata kai ni ƙara hukumar kare hakkin ɗan Adam, ta ɗauke
mini 'ya, ta tafi da ita, sai da aka yi sati biyu sannan ta dawo mini da ita ga
babanta da mijinta suka ƙara matsa mini lamba, bayan ta dawo da ita, yarinya ta
ƙara tuburewa ba ta san zancen aure ba.
Tamkar an canza mini ita, idonta ya buɗe, har mijin 'yar
tawa ta saka aka kama aka rufe, aka kashe auren nan. Yanzu maganar da nake yi
miki, shekru uku kenan, yarinyar nan ta ce aure wani abu ne al'ada da muke
takurawa kanmu a kai, addini bai wajabta mana ba, haka take rayuwarta, sai ta
shafe kwanaki ba ta gida, tana yawonta. Babanta ya sallama mini ita, bayan ya
gama tsine mana daga ni har ita. Har a cikin unguwa ta cigaba da yi wa sauran
ƙasayenta mummunar huɗubar adawa da aure, wai ana tauye musu hakki, kuma
wallahi Naja bunkure ce ta mayar mini da 'ya haka,tana fakewa ne kawai da
taimako, tana zaluntar mutane".
Ɗayar ta ce "Nima kusan hakan ne, wani yaro ɗan masu kuɗi,
ya lalata mini yarinya daga aikenta gidan, jami'an tsaro suka ƙi kama yaron,
uban ɗan ya ce in dai arziki yana rana, zai kare ɗan sa, ba wanda ya isa ya
kama shi ya hukunta. ni kuma jin shirye-shirye da ake yi a kanta, na taimakon
marasa galihu, ya sanya nima na je neman ta taimaka mini. Da farko abu kamar
gaske zata taimaka mini, ƙarshe abun ya juye, aka nemi a mayar da case ɗin wai
sharri muka yi wa yaron.
Wallahi ƙarshe yarinyata fiya-fiya ta sha ban sani ba, yar
shekara goma sha huɗu ta mutu. Wallahi matar nan azzaluma ce, bamu da wurin da
zamu je, mu nemi hakkinmu sai wurin Allah, haryanzu idan zance yayi zance a kan
tayar da maganar abun da ya faru da yarinyata, wanda hakan ba ƙaramin tsaye
mini yake yi ba" tayi maganar tana kuka mai ban tausayi.
Nabila ta tashi ta rungume matar, tana rarrashinta ta ce
"Ki yi haƙuri dan Allah, ki kwantar da hankalinki, Allah ya jiƙanta, kuma
in sha Allah da ikon Allah sai mun kai matar nan ƙasa, zan yi iya yi na, in
bankaɗo duk wani mugun abu da ta aikata muku, kuma sai ta girbi abun da ta
shuka, ku yi haƙuri. Yanzu duk zaku bani adress ɗin ku, zan bi cases ɗin ɗaya
bayan ɗaya, na tabattar da abun da ya faru kafin na san abun yi"
Jikin Nabila yayi sanyi sosai da sosai, da jin abubuwan da
Bunkure take aikatawa, tamkar ba 'ya mace musulma ba, da matan ke iƙrarin ciwon
ƴa mace, na 'ya mace ne.
Har kuɗin mota ta basu, bayan tafiyarsu ta kalli barrister
Habib ta ce "Yaya habib, ka ji wani yahudanci? Ina laifin ta tsaya a kan
iya kashe auren an yi wa 'yar auren dole?"
"Ke ce baki san wacece ita ba sai yanzu, wannan wata ɓoyayyiyar
aƙidarta ce, na bawa mata damar ƙin zaman aure da lasisin karuwanci. Tana saye
yaran da kuɗi, da abun duniya wurin cusa musu wannan mummunan ra'ayin, da koyar
da su daidaiton jinsi tsakanin su da maza".
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, amma duk da haka
Alhamdilillah, na samu hints a kan yadda zan bankaɗo asirin matar nan, and one
more thing kuma" ya kalleta ya na jiran me zata ce.
"Maganar da muka yi da kai kwanakin baya, a kan case ɗin
Aminu Viper"
"Ina jinki"
"Naja'atu Bunkure tana cikin tawagar lauyoyin da suka
tsaya kai da fata a kan shari'ar da aka yi masa. Kuma ka san ita ungulu ce ba
ta jewar banza, dan haka akwai manufa a cikin shiga shari'ar da tayi. Viper ba ɗan
siyasa bane ba, kuma ba shahararren mai kuɗi bane ba, balle ace tsaya masa tayi
a shari'ar. Dan haka akwai ayar tambaya a kan charges ɗin da aka yi masa na
kisan kai.
Take a look at it barrister, an tsare mutum shekara biyar,
an yi masa shari'a sau biyar kawai, an kai shi prison an ajiye babu conclusion
na shari'ar, is je guilty or innocent? Kwatsam an ce ba a ganshi a prison ba,
kuma an cigaba da nemansa, ruwa a jallo, anya akwai gaskiya a lamarin nan
kuwa?"
Ya tsura mata har ta gama, yayi murmushi ya ce "Haka
kwanyar nan take cike da basira, amma aka ƙarar da ita a wurin iyayi da
kwalliya?.
Maganarki gaskiya ce Nabila, amma ina rabaki da case ɗin
Vipern nan, akwai badaƙala sosai a kan case ɗin".
Nabila ta ce "Me da me ka sani a kai?"
"Nothing much, kawai na san dai akwai bita da ƙulli ne
a ciki sosai"
Ta jinjina kai ta ce "Haka ne, bari na tafi gida, yau a
matuƙar gajiye nake" tayi masa sallama, ta tafi office ta ƙarasa shirinta,
ta tafi gida. Ta sake karo da file a office ɗin.
Cikin mamaki ta ɗauka, ta fara buɗewa.
Aka rubuta continuation a ciki.
Cigaban tarihin Naja bunkure ne, bayan rape da aka yi mata,
cousin brother ɗin ta, aka rufe case aka ce abu ne na dangi, bayan ta ƙara
girma tayi aure, ta sha wahala sosai a hannun mijinta na farko, ya azabtar da
ita tamkar baiwarsa, ko haihuwa ba ta yi ba auren ya mutu.
Yayanta ne ya taimaka mata, ya mayar da ita makaranta, tayi
candy, ta shiga jami'a, sai dai bayan rasuwar yayanta, aka rasa mai sponsiring ɗin
ta, ta cigaba. Mahaifiyata na can wani garin tana aure, babanta kuma ya ce ba
ruwansa da ita, tun da taƙi zaman aure.
A lokacin har wurin ɗan majalisar su, ta je neman kuɗin
makaranta, lokacin yana tare da Indabo, indabo ya ce zai bata, amma sai dai ayi
bani gishiri na baka manda. Ta amince tun daga nan, ta zama tamkar matarsa su
watse ya biya mata kuɗin makaranta, babu wani sirri nasa da bata sani ba.
Ta nemi ya aureta, bayan tayi graduation, amma yaƙi, ganin
haka ya sanya, ta samu wani suka daidaita ya aureta, sai dai Indabo ya cigaba
da bibiyarta.
Ta fara aiki a matsayin lawyer mai zaman kanta, Naja tana da
burin yin luxry life sosai, sai dai mijinta yana da rufin asiri amma ba irin
wanda take hange ba, Indabo yayi mata alƙawarin haɗa ta da manyan mutane,
lokacin ya zama ɗan majalisa, wanda zata din ga samun alkhairi da damarmaki.
Kwaɗayi da buri, ya sanya suka koma ruwa da aurenta, ya din
ga kashe mata kuɗi, yana kuma haɗata da manya. A wurinsa ta koyi shaye-shaye.
Tsakanin ta da mijinta babu ragayya ko kyautatawa, duk son da yake nuna mata da
kulawar da yake bata sam baya gabanta.
Ta fara tashe sosai tana shahara, ana programs da ita a
kafafen watsa labarai, ta buɗe ƙungiyar ta ta kanta, bayan joining ɗin
ƙungiyoyin yahudawa, masu da'awar daidata jinsi, reshen Nigeria, ta cigaba da
yi musu aiki ta ƙarƙashin ƙungiyar ta.
Sai dai a haka take miyagun harƙallarta, na yi wa manyan
mutane safarar mata a birnin tarayya, musamman ƙananan yara, da akan yi amfani
da su saboda asiri.
Red handed mijinta ya kamata, chats ɗin ta da wani minista,
na ƙazanta, yayi kuka, amma ko a jikinta, ta ce idan ba zai iya ba ya rabu da
ita. Haka ya saketa, ta samu cikakken gashin kanta.
Ba ta taɓuwa, ko da kuwa tayi laifi, yanzun nan ƙungiyoyin
kare hakkin ɗan Adam zasu shiga lamarinta. Ta din ga binne mutane ta hanyar
bayyana musu kyawawan ayyukanta, da ɓoye na laifin.
Bayan mutuwar aurenta labari ya bazu, mutane suka din ga
tsinewa mijinta, wai ya saki macen kirki, aka yi hira da ita, ta din ga kuka
tana yi tsohon mijinta sharri kala-kala.
End the story.... Aka rubuta a ƙarshen page ɗin.
Wani irin gumi, ya din ga tsatstsafowa Nabila, ta ma rasa
abun yi, da tunanin da yakamata tayi, ba ta bari ta takura ƙwaƙwalwarta wurin
hasaso waye ya kawo mata file ɗin a karo na biyu ba, kawai ta ɗauki jakarta ta
fita.
***
Sumayya ce a tsaye tana kuka wiwi, shi kuma ya zuba mata
ido, ko ƙiftawa baya yi, sai da tayi mai isarta sannan ya ce "Kukan ya isa
haka, meyafaru?"
Ta share hawayenta ta ce "A gaskiya sir, ni na gaji da
aikin nan, na samu matsala da ni da Nabila, ni Nabila ba ƙawata ce kawai ba,
ƴar uwata ce, ta riga ta yi fushi, ba zata saurare ni ba, ni ban san wanda ya
gaya mata ina bibiyarta ba, ga wancan honorable ɗin ya addaba mini, duk motsina
sun sani, sai kuma sun tambaye ni, me tayi me take ciki, banda barazana da suke
yi mini ba yau ba gobe, ni dai dan girman Allah ka yi wani abu a kai, kar ni ko
ita ayi wa wani illa, indabon nan fa ba imani ne da shi ba" ta ƙarasa
maganar tana sake fashewa da kuka.
Yayi murmushi ya ce "Haba ƴar jarida, ya da kuka wiwi
haka da karaya nan da nan? Da kin sanni, kin san zan taimake ki? Baki san ya
aka yi na gane Indabo yana yi miki barazana ba. Har na shigo lamarin ba, dan
haka ba zan bari a cutar da ku ba, dukkaninku a kan gaskiya ku ke, sai dai ita
naga buyaginta yayi yawa.
Ki yi haƙuri ku daidaita, da haka zan cigaba da yi mata
supplying abubuwan da take buƙata a harkar shari'ar nan"
"Sir yanzu fa ka gama cewa buyaginta yayi yawa, sai ce
mini munafuka take yi, babu yadda tsakanunmu yanzu"
Ya ce "No, tayi fushi ne kawai, and ki ƙara kiyayewa
sosai da sosai, ki daina bari tana gane kina bibiyarta".
Sumayya ta ce "Yanzun ma, wallahi ina kiyayewa, ban san
yadda aka yi ba"
Ya din ga rarrashinta, sannan ya saka aka ɗauke ta a mota,
aka mayar da ita gida.
***
Nabila da ƙyar ta isa gida, ta watsar da kayan a kan
gadonta, ta fara kiran wayar Viper, amma a kashe, ta kira ta Walid amma baya ɗagawa,
haka ta haƙura ta shiga banɗaki tayi wanka ta yi alwala ta fito.
Har washegari da safe, Nabila tana neman layin Walid,
hankalinta ya ƙara tashi, tayi tunanin ko wani abun ne ya same shi.
Tana saka kayan abinci a motarta, Nasir ya fito.
Ta ce "Yaya ina kwana?"
Ya amsa da "Lafiya ƙalau, wai ina ki ke zuwa da
kwanukan abinci kwana biyun nan ne?"
Ta ɗago ta kalleshi ta ce "Ci nake yi mana, wataran ai
wuni nake yi bana gida"
Ya ɗage kafaɗa ya ce "Ban sanki da dakon flask ba,
saboda haka kin gwammace ki ci biscuit da sauran kayan ciye-ciye"
"Haba yaya, yanzu ba mota ce da ni ba? Kuma zan je in
ta cin abinci nikaɗai duk ga mutane ne a wuri?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a, amma yanzu ƙarfe bakwai
saura kwata, har shida da rabi kin fita, saɓanin da har goma saura sai ki kai a
gida"
Ta tsaya sosai ta dube shi ta ce "Yaya me kake nufi ne?
Ka daina ɓoye-ɓoye ka fito fili ka sanar mini cewar, tuhumata kake yi, da
aikata rashin gaskiya mana"
Yayi murmushi ya ce "Ai ba a tuhuma sai an tabattar da
zargi my dear"
"Da ka daina zargin, dan wahalar da kanka kawai zaka
yi, ko kuma irin abun naku zaka yi mini na masu kaki" tayi maganar tana
murmushi.
Shi ma murmushin ya yi, ya ce "A sauka lafiya"
Ta amsa da Amin ta tafi.
Tana tafe a hanya sai ga kiran wayar Walid, ta ɗaga wayar ta
ce "Oga Walid, sai kiranka nake yi a waya, shi wayarsa ba ta shiga,
wayarka kuma baka ɗagawa"
Walid ya ce "Bari kawai, kin san halin mutumin naki sai
a hankali ai, jiya bayan tafiyarki, ya kafa mitar sai an sallame shi daga
Asibiti, da mu da likita muka din ga rarrashin sa, yayi mana banza, mun fita
salla ya gudu, baki ga yadda hankalinmu ya tashi ba, na ce musu kawai mu koma
gida, dama ya saba irin haka, ko lokacin da ƙanwata take raye, haka take fama
da shi, idan aka kwantar da shi, da ɗanyen ciwo haka zai bar asibiti sai dai ta
ƙarasa masa dressing a gida ya warke".
Nabila ta ce "Allah sarki, Allah ya yi mata rahama, shi
kuma ya bashi juriya. Kana ji na, zan shigo dan ga abinci ma nayi, yayana ya
fara saka mini ido ne, dole na canza takuna, zuwa azahar zan bar motata a
chamber, zan zo in sha Allah"
Ya ce "To Allah ya kawo ki, dan zuwan naki yana da
amfani, yaƙi cin abinci ya ƙi shan magani, yana kwance kawai tun jiya"
"In sha Allah zan zo, ayi masa sannu" ta ajiye
wayar tana murmushi, rigimar Viper tana da yawa, idan ba ka da haƙuri ba zaka
iya da shi ba.
Har ta fara neman lambar sumayya, sai kuma ta fasa kiranta,
dan har ta manta sun yi faɗa. Kawai ta din ga jin ta wani iri, akwai abubuwa da
dama da take son gaya wa sumayya, saboda kusancinsu da shaƙuwarsu, ta musamman
ce. Sai dai haryanzu tana mamakin dalilin da zai sanya a din ga bibiyarta ta
hanyar sumayya, kuma waye yake bibiyar ta ta.
Sai dai ta fara zuwa courts ɗin da take da trials, ta
gabatar da shari'oi, sannan ta koma asibitin da aka kai ramma, lokacin da aka
yi mata fyaɗe.
Ta nemi a bata copyn report ɗin da aka yi confirming rape
case ɗin, aka ce an bawa ƴan sanda. Ta nemi ganin likitan da ya kula da ita,
aka ce ya tafi ƙaro karatu, a bata lambarsa nan ma aka cigaba da yi mata yawo
da hankali.
Sai da ta gama zagayenta, sannan ta ajiye motar a wani wurin
parking, ta karɓi pass, ta tafi wurin su Viper.
Yau a tsakar gida ta tarar da shi, sun shimfiɗa masa
tabarma, yana zaune yana ya danna wayarsa, sai dai idanunsa sun ɗan yi wuri
wuri ya faɗa, gabansa kuma kwalin sigari ne da lighter.
Tayi sallama duk suka amsa, ya ɗaga kai ya kalleta ya mayar
ya sunkuya.
"Ohhh masha Allah, the most handsome man ever saw, kaga
yadda ka yi kyau sosai da sosai" ta nemi wuri ta zauna a gabansa ta ce
"Manya gatan wasa, fisabilillahi mutum sai ya gudu daga Asibiti ba a
sallame shi ba? Idan kuma bai warke ba fa, ni gaskiya ban ji daɗi ba"
Ba ta saka ran zai kulata ba, ta ce "Ina wuninku, ya
mai jiki kuma?"
Suka amsa da sauƙi.
Walid ya ce "Ba yadda bamu yi da shi ba, amma sai
nemansa muka yi muka rasa"
Tayi dariya ta ce "My, ya kake haka ne, duk muna ta
taka, amma kai ko a jikinka. Wannan sigarin ina fatan ba sha aka yi ba, kaga an
ce jininka ya hau, kuma kana smoking ba zai sauka da wuri ba, an ce mini baka
cin abinci, duk ka rame ai ba zan ji daɗi ba" ta janyo ledar abinci ta ce
"Ka yi haƙuri ban kawo abinci da wuri ba, Yaya Nasir ya fara saka mini
ido" ta ƙarasa maganar tana miƙa masa plate, da cup ɗin da ta zuba masa
kunun alkama.
Ya saka hannu ya karɓa, ya fara ci.
Liti ya ce "Wato mai zamani mune dai ba ma yi maka
gwaninta ko?"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Ka san wani abu?" Ya
girgiza mata kai alamar a'a.
"Ni fa na gaya wa Sumayya, na san tana bibiyata, duk da
jiya ta kawo mini wasu mata, da suka yi mini complain a kan Bunkure, amma mun
yi faɗa da sumayya.
Sannan an sake ajiye mini file a office ɗina, na ƙarashen
labarin Naja'atu Bunkure.
"Ku ka yi faɗa ba ƙawarki ba ce ba?"
"Eh, amma meyasa zata ci amanata?"
Ya kalleta ya ce "Ya aka yi ki ka tabattar da cin amana
ne ya sanya take bibiyarki?"
"Saboda kai ka gaya mini"
"Ban ce tana bibiyarki dan ta ci amanarki ba, kuma baki
da tabbacin da gaske nake ko akasin haka"
Ta gyara zamanta ta ce "A labarinka da na ji, baka
ƙarya dan ka ci amana, kuma bana tunanin zaka fara a kaina"
Ya jinjina kai ya ce "Bani wayarki" ta ɗaukko
wayarta ta bashi, ya nutsu sosai yana ta daddanawa.
"Yayanki ma na ƙoƙarin yi wa layinki kutse, sai dai na
rufe damar hakan. Yana zarginki a kan da shi kansa bai san menene ba. Yayanki
ya ga Indabo yana yi masa aiki a kaina, yana kuma gargaɗin sa a kan abun da ki
ke yi a kan bunkure, na san zuwa yanzu ya matsa miki lamba a kan ki rabu da
ita"
Ta waro ido ta ce "Ya aka yi ka sani? Anya yayan
kuwa?"
Ina bibiyar kiran wayarsa ta hanyar amfani da wayarki,
hakazalika duk wasu maganganu da yake yi, recording ɗin suna kan computer ki.
Wayarsa da Indabo kawai nake bibiya, ba ruwana da sauran harkokin sa.
Ta ce "Subhanallah, amma yaya ya bani kunya, shiyasa
yake ta uzzura mini? Amma nima ka yi hacking ɗin wayata kenan? Kana jin duk
wayar da nake yi da samarina?"
Tsaki yayi, ya jefa mata wayarta. Ya ce "Ina magana
serious kina yi mini shirme?"
Ta ce "To ai kar ka ji ina kalamai ne, ka zo kana
kishi, nifa duk ba son su nake yi ba, kai kawai nake so" tayi maganar da
niyyar sake kunna shi.
Ƙoƙarin tashi yayi, tana dariya ta ce "Yi haƙuri, dan
Allah ka duba mini ƙarashen labarin nan, na Najar bunkure ka gaya mini menene
opinion ɗinka".
"Mu yi aiki kawai, ki daina yi mini wannan
shirmen"
"Ba shirme bane ba fa, ni da gaske nake" ya karɓi
file ɗin, ya cigaba da duddubawa.
Ya ɗaga kai ya kalli walid ya ce "Mai laya"
"Mai zamani".
"Yakamata ku je ku daba mini mahaifiyar Nura, tun da na
fito yakamata ace na je na ganta, amma ba zan iya ba, ban san wace irin karɓa
zata yi mini ba, maybe ita ma irin kallon da ake yi mini, take min"
Liti ya ce "Haba maza, babu lallai gaskiya"
Nabila ta ce "Ina kakarka to? Wadda oga walid ya bani
labarinta?"
"Ta mutu ina prison"
Walid ya ce "Har tare da ita mun je prison, sau biyu ba
a bari mu ganshi. Baiwar Allah nan tashin hankali da damuwa ne, suka haɗu suka
kasheta"
Jiki a sanyaye ta ce "Allah sarki, Allah ya yi mata
rahama, ya sanya sun huta baki ɗaya, da yar madara, da Hajiya, da mamana da
sauran al'ummar musulmi baki ɗaya" suka amsa da Amin.
Walid ya ce "Mamanki ta rasu?"
Ta jinjina masa kai ta ce "Eh, ban ma santa ba, sai dai
hotunanta na gani a wurin Abba"
"Allah sarki, Allah ya jiƙanta"
Liti ya ce "Shiyasa ba kya ji, ina tausayawa mariƙanki,
sun sha wahala da ma ba kowane maraya ne yake ji ba"
"Oganku shi ne na farko a marasa jin, in dai maraya
baya ji" ta yi maganar tana satar kallon Viper.
"Amma Viper, ka sake komawa wurin Abbanka kuwa? Na san
zuwa yanzu ya huce, zai kuma fuskance ka, ka yi masa bayani, shi fa tsakanin ɗa
da iyaye sai Allah" yayi mata shiru.
"Ni ka bani dama naje na same shi, na san zai fahimce
ni"
Ya ajiye file ɗin ya ce"Kar ki kuskura ki fara wannan
gangancin, kar ki kusanci unguwarmu, ko ki ce zaki je unguwar da gidana yake,
idan ki ka yi ɗaya daga ciki, zan yanke aikin da zan yi da ke, kuma hakan zai
iya sanya wa na kashe ki"
"Au ba zaka daina zancen kisan kan nan ba ko? To maza
nima ka kashe ni, na ga wanda zai din ga rarrashinka.
Ta tashi ta ɗauki jakarta, ta tattara kwanukanta, ta ce
"Bari na tafi, kar nayi yamma da yawa, zamu yi magana" tashi ya yi ya
ce "Muje"
"Rakani zaka yi? To muje" suka fita kamar gaske.
"Ina sake gargaɗinki, kar ki sake ki ce zaki nemi gidanmu ki je, ko gidan
su 'yar madara, zaki ɓata mini aiki, duk da na samu labarin sun bar unguwar,
idan kuma ki ka ɓata mini aiki, ba na jin zan iya yafe miki"
Ta ce "Subhanallah, in sha Allah ba zan je ba, amma
yakamata ku daidaita da mahaifinka.
"Ba wannan ne a gabana ba"
"To menene a gabanka? Iyaye fa ba a fushi da su"
"Ki rabu da ni"
Ta ce "To, Allah ya baka haƙuri"
"Ki cigaba da kula sosai da sosai a kan zuwanki wurin
nan, za a iya biyoki har nan, bana tunanin iya wayarki ake bibiya"
Ta kalleshi ta ce "Akwai wata mota da na lura da tana
bina kwanakin baya, amma ba wannan ba. Na faa tunanin anya a cikin yaranka babu
wanda suke sanar da wasu abubuwan da muke yi? Ko kuma wani yana binka ko kuma
ni da ake bi, an san ina zuwa wurinka ba? Suwaye suka ɗaukeka kwana biyu?
Sannan ya aka yi aka san kana asibitin nan, har aka biya maka kuɗin
asibiti"
Ya sauke numfashi ya ce "Kar ki shagala da tunani da
yawa, ki manta da abubuwa masu muhimmanci, ki je zamu yi magana"
Ta kalleshi ta ce "To, amma dan Allah ka ɗaga wayata da
daddare in ji muryarka, ka ji Oga" wani irin mugun kallo yayi mata, ya
nausa ya bi wata hanyar, ita kuma tayi gaba tana murmushi.
***
Ramma na zaune a kusa da Abdul, yana kallon ball, ita kuma
ta kunna radio a wayarta, tana ji.
Ya kalleta ya ce "Dan Allah ki rage radion nan"
"Ina ruwanka da ni ne, ka yi kallonka mana"
"Kin cika mini kunne da radio ne"
"To ita ball ɗin magana ake yi? Ba ihu bane ba
kawai?"
Abdul ya ƙure volume, ita ma ta ƙure volume, ta kara masa
radion a kunnensa.
Yayi mata shiru ya ce "Kya yi kya gama"
Sumayya ce tare da murtala a studio, suka gabatar da
program, kasancewar an samu akasi masu gabatar da program a dai-dai lokacin ba
su samu zuwa ba.
Program suke yi akan abubuwan da suka shafi rayuwa, suna yi
suna karanto saƙonnin masu sauraro.
Murtala ya ce "T ladan, ga wata tambaya daga masu
sauraro, wai an ce a tambayeki, wace irin alaƙa ce tsakanin ki da Nabila Yusuf
maitama, da kullum ba kya taɓa aiki ki tashi, baki ambace ta ba, baki tsokane
ta, ko saka waƙoƙi domin jin daɗinta ba?"
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Barrister Nabila, voice
of voiceless a lady of her words, a hardworking, strong minded young barrister,
she's exceptional, lovely and simple sister of me" tayi maganar tana jin
zafin saɓanin da suka samu a tsakanin su.
Murtala ya ce "Tirƙashi, duk wannan kirarin itakaɗai?"
"Sosai, Nabila mutum ce ta mussaman a rayuwata, ina yi
mata son fisabilillahi"
"To yanzu da saurayinki, da Nabila wa ki ka fi
so?" Ta kwashe da dariya ta ce "Uncle murtala wannan ai haɗa faɗa
ne"
"To yanzu kafin muyi sallama da masu sauraro, gaya mana
kalma ɗaya tak a kan Barrister Nabila"
"Mai gaskiya ce, ina yi mata fatan nasara, ya ɗaukaka
mini ita, ya kuma kare mini ita a duk in da take, ya dauwwamar da ita a kan
gaskiya"
Murtala ya ce "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, Allah ya bar
wannan ƙauna, kafin mu ƙarƙare shirin, mun karɓi takardar wata baiwar Allah da
za a yi wa ɗanta aikin ƙaba, amma ba ta da hali, tana neman taimakon bayin
Allah. Akwai kuma wadda take neman kuɗin sayawa mahaifiyarsu magani mai fama da
hawan jini, muna fatan zaku taimaka"
Nabila kuwa tana driving, ba ma'abociyar jin radiyo bace ba,
amma saboda sumayya take sauraren radio. Hawaye ta din ga sharewa, tare da tuna
abun da ta yi wa sumayyan.
Ramma kuwa cewa ta yi "Allah ya ƙarfafi wannan baiwar
Allah, ya tabattar da ita a gaskiya, kar ya kauce hanya, kamar waccan munafukar
mara imani" Abdul yana jin ta, yayi mata shiru. Ganin bai kulata ba ya sa
ta ce "Ba zaka ce amin ba"
"Ni fa ball nake kallo"
"Allah ya sa a cinye club ɗin da kake yi"
"Ba amin ba" ya ɗauki wayarsa, ya kira admin ɗin
asibitin sa, ya ce a je gidan radion su sumayya, a kai yaron nan ayi masa aiki
kyauta, mai hawan jinin ma a kai ta a bata magani.
Ramma ta ce "Kalle shi kamar na Allah" duk yaƙi
kulata, ta tashi ta nufi ɗaki, ta saka hannu ta kashe tv ta riga ɗaki da gudu,
kawai yayi dariya.
***
Kwanaki biyu, Nabila ta daina samun Viper a waya, sai dai da
ta kira walid, ya tabattar mata da lafiyarsa ƙalau.
Nabila ta fara gazgata zancen Viper, duba da yadda Nasir
yake kashe-kashen kuɗi, ya canza mota ya cigaba da gininsa, kuma salarynsa gaba
ɗaya ba wani shahararre bane ba.
Nabila tana kwance tana waya da Alhaji Wada M karofi, yadda
yake lallaɓata yake yi mata magana, har kunya yake bata.
Fuskar viper kawai take hangowa, yanzu da shi take yi wa
kalaman nan, da tuni ya haɗe rai yana hararta. Bayan sun yi sallama ta ajiye
wayar, Walid ta shigo ɗakin ta ce "Arfa, isa ne ya shigo yanzu, wai ana
sallama da ke a waje"
"Kai, wane ɗan baƙin cikin ne zai hana mini jin daɗi a
magaribar nan? Ni fa ban yi da kowa za a zo wurina ba"
Walida ta ce "Ace ya tafi kenan?"
"A'a gani nan zuwa"
Ta yafa mayafin abayarta, ta fita, a ƙa'idar Abba a cikin
gida suke zance, ganin bai shigo ba, ya sanya ta gane lallai wanda ya zo ɗin
baƙo ne.
Ta zira kai ta leƙa ƙofar gida, dan duba waye.
A opposite ɗin gidan ta ga Viper a tsaye yana kallon ta.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Gaban Nabila ya faɗi, cikin matsanancin tsoro da tashin
hankali, ta din ga waige-waige tare da dubawa, idan akwai wanda ya ganshi, amma
layin babu kowa, sai manyan security light da suka haska ko ina.
Ta sake kallonshi, ta tabattar shi ne, ta ƙarasa in da yake
da sauri ta ce "Viper, waye ya nuna maka gidanmu? Yau kuma ba office ba
har gida?"
"Akwai matsala ne?" Yayi maganar yana ƙara ƙureta
da ido.
"Au tambayata ma ka ke yi? Amma dai ka san yayana
nemanka yake yi ko meyasa zaka zo gidanmu, lallai sai ka tona mini asiri ne?
Waye ma ya nuna maka gidanmu?"
"Shi yayan naki, ki shiga ki gaya masa gani ya zo ya
kamani mana, shikenan ki daina wahalar da kanki da fargaba mana. Kina tunanin
zan yi aiki da wadda ban san wacece ba?"
Ta ce "Yanzu dai duk ba wannan ba, dan Allah mu je daga
wancan lungun, mu yi magana"
Ya sha kunu ya ce "Ban gane muje lungu ba"
"Eh mana, mu je can mu yi magana kar a ganka"
"A'a ni ba zan shiga lungu a daren nan ba"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, to ai ba wani abun
na ce ayi a lungun ba, magana kawai zamu yi kar a ganka nake tsoro"
"Kuma sai ki ce in shiga lungu"
"Na shiga uku, sai ka ce wata 'yar iska, kar ka yi mini
wata mummunar fassara mana"
Viper ya ce "Ke da duk baki yi wannan tunanin ba, ki ka
amince da aiki tare da ni, ki ke iƙrarin zaki taimake ni? Ki tsaya ki saurare
ni" ya yi maganar fuskarsa ɗauke da matsananciyar damuwa. Duk da bai
kasance mai fara'a ba, amma yau akwai damuwa sosai a tare da shi.
"Amma dan Allah waye ya nuna maka gidanmu"
"Ba wannan ne ya kawo ni ba"
"To Allah ya baka haƙuri sir, me yake tafe da
kai?"
"Nura" ya faɗa a taƙaice.
"Waye hakan?"
"Ƙanina Nura guduma, bayan mutuwarsa ina duba
mahaifiyarsa, sai dai bayan an tsare ni ban samu damar yin haka ba, amma su
Walid sukan je amma ba ko yaushe ba, bayan fitowa ta kuma, bani da cikakkiyar
nutsuwa, kuma ina matuƙar jin nauyinta ban je ba, ban kuma saka su walid sun je
ba"
Nabila ta nutsu tana sauraronsa, duk a tsorace take, kar
wani ya ganshi, duk da akwai facemask a fuskar sa.
"Mijin da ta aura bayan baban Nura ya rasu, shekaru
biyu da suka wuce, tana ta fama da rayuwa, ga yaranta guda biyu, a taƙaice dai
jiya da su Walid suka dawo daga garin, sun tabbatar mini da 'yar ta aka yi wa
fyaɗe ita kuma ba a san in da take ba" Nabila ta zabura ta ce
"Kuma?"
"Yarinyar da ki ke bincike a kan case ɗin ta, Naja
bunkure ta shiga case ɗin"
Nabila ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
kalmar nan ko daɗin ji ba ta da shi, dama ita ce? To ba su gano in da maman
take ba?"
"Ina gaya miki kina tambayata, na baki nan da sati biyu
rak, tun da kin ce wanda ake zargi ba shi bane ba, ki fito da mai laifin, ko
kuma ni na fito da shi ta ƙarfin tsiya".
Cikin rashin fahimta ta ce "In fito da mai laifi kuma
ta ina? Nima bulayin nemansa nake ai saboda in wanke client ɗina"
"Sai fa kin nemo shi, ko kuma ki tabattar an yankewa
mutumin nan hukunci dai-dai da abun da ya aikata"
"Amma dai ka san ni lawyer ce ba 'yar sanda ba ko?
Jami'an tsaro sune za su yi maka wannan aikin, ni kuma na tsaya na tabattar
kotu ta yi adalci"
Ya tsare ta da idanunsa ya nuna ta da yatsansa ya ce
"Ke zaki yi, ba wanda zai yi sai ke, ki nemo ainihin mai laifin, ko kuma
ki bari a hukunta wannan mutumin"
"But he's not guilty, he's innocent, ka bari na bi
komai a hankali"
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "No matter what it takes,
ki binciko ainihin mai laifin nan, an cutar da matar nan fiye da yadda ki ke
tunani"
Nan ya warware mata ɓangaren labarin sa na Nura, da ba ta
sani ba.
Rawa ƙafafuwanta suka fara yi, jikinta yayi wani irin sanyi,
ta kasa magana.
"Ki din ga yi mini uzuri wasu lokutan, ni mutum ne mai
tarin laifuka ga mutane, bana son in ga wani a cikin damuwa, ina tsoron ace
matar nan guduwa tayi saboda baƙin ciki, ba haka ba ma, voice message ɗin da ki
ka kunna mini, sai a yanzu na sake tabattar da muryarta ce, ta tabattar da har
gida wanda yayi rape ɗin yaje ya ɗauke 'yar, dan haka ramma tana tare da wanda
ya yi mata fyaɗe, kuma Naja'atu Bunkure ta sanshi, ba dan ta tsayawa yarinyar
ta shiga case ɗin ba, dan ta bawa mai laifin kariya ne".
"Yanzu ka yadda wanda nake karewa ba shi da
laifi?"
"Na sani, amma dole ki yi wani abu, a nemo yarinyar nan
da mahaifiyarta"
Nabila zata yi magana, aka haske su da fitilar mota, ta saka
hannu ta kare saboda hasken fitilar, shi kuwa yayi ƙuri yana kallon fitilar.
Viper ya ce "Ko dai ki gaya masa ya kashe fitilar nan,
ko na haɗa idonsa da na motar na ɗauke musu wuta gaba ɗaya"
Fitowa yayi daga motar ya ƙaraso in da suke, ya kalli Viper,
sai dai a wannan karon ma ya ji wannan faɗuwar gaban. Kallo ɗaya ya yi wa
Viper, ya tuna a in da ya ganshi.
Ya kalli Nabila ya ce "Arfa waye wannan? Irin wannan
samarin kuma ki ka koma kulawa?"
Ta kalli Viper sannan ta kalli Nasir ta ce "Yaya me
yayi maka ne? Na gaya maka tun waccan ranar he's my client"
"Client like how? Shi ne zai din ga biyoki har gida?
Get inside kafin na kwaɗeki a wurin nan" Addu'a take Allah ya sa kar Viper
ya hasala.
Viper ya ciro wata fitila daga aljihunsa, ya haske idon
Nasir, ya matsa daf da shi, Viper ya fishi tsawo sosai ya ce "Talk to me,
like a man, baka din ga yi mata shouting ba"
Ya ja da baya ya kalli Nabila ya yi mata alama da hannunsa
na i will call you.
Ta jinjina masa kai, shi kuma ya juya zai tafi.
"Waye kai?" Nasir yayi maganar cikin dakewa, dan
muryar Viper kawai a bar tsoro ce.
Viper ya juyo, ya kalli Nabila, da ta bashi tausayi, ban da
tana wurin, kuma bai san me abun da zai aikata ka iya haifarwa ba, da sai ya
sakawa Nasir iraƙi sannan ya gaya masa waye shi, kamar yadda ya yi wa tijjani
yayan yar madara.
Ya kalli Nasir ya ce "A man" ya faɗa a taƙaice.
Nasir ya waiwaya, ya kalli Nabila zai fara masifa, amma ta
zura da gudu ta shige gida.
Rufa mata baya yayi, yana masifa har ɗakinta ya bita, yana
yi mata bala'i, ganin yana neman ya tozarta ta a gabam mutanen gidan ya sanya
ta fara kiran sunam Abba da ƙarfi.
Aikuwa Abba ya saukko daga kam benensa yana faɗin "Wai
waye yake taɓa mini yarinyar nan, kai Nasir menene haka? Dukanta zaka yi?
Shekara Ashirin da biyar sai ka kamata kana duka dan rashin mutunci?"
"Abba ba dukanta zan yi ba"
"To me ka yi mata take wannan kururwar haka?"
"Abba gaba ɗaya Arfa ta canza, ta tsiri wasu irin ɗabi'u
na rashin gaskiya, rannan na je ofishin ta, na tarar da ita da wani mutum, gaba
ɗaya bai yi kama da mutanen kirki ba, yauma still ta tsaya da wani a waje,
maimakon cikin gida tana zance, kamar dai wancan mutumin ne, gaba ɗaya bai yi
kama da mutanen ƙwarai ba"
Abba ya kalli Nabila ya ce "Arfa, yayanki a kan gaskiya
yake, ni kaina shige da ficen samarin nan naki, ya fara isata".
"Abba, wallahi ba mutumin banza bane ba, kuma ko
mutumin banza ne, ba wata muguwar alaƙa ya gani tsakani na da shi ba, na gaya
masa client ɗina ne kawai, amma yaƙi yadda kwanan nan komai nayi sai ya din ga
zargina na rasa me nayi masa gaba ɗaya"
"A'a Arfa, Nasir yana cikin masu goyon bayanki a gidan
nan, tun da har ya magantu, to ya fiki gaskiya, ki san irin mutanen da zaki din
ga tsayawa, kuma ki din ga mu'amala da su, yanzu a cikin samarin nan naki,
lallai ki duba mai nutsuwa ya zo in ganshi, nima zan fi samun kwanciyar hankali
ace kina ɗakinki" Nabila ta yi shiru, Abba yayi ta yi mata nasiha, bayan
ya gama ya fita, Nasir ya bi bayansa.
Nasir ne ya bi bayan Abba, suka shiga ɗakinsa ya ce
"Abba, yakamata ka ja wa arfa kunne, wasu abubuwan take yi kwanan nan,
shishishigi a kan wasu abubuwa. Ta sako wannan barrister Naja'atu Bunkure a
gaba, kar ta je ta janyo wa kanta wata matsalar"
Abba ya ce "To ai ni kaga ban sani ba, ban san me take
aikatawa ba wasu lokutan, amma babu komai, zan yi mata nasiha, ka san ba kowane
lokaci faɗa yake tasiri ba".
Nasir ya ce "Haka na, sannan kuma Abba"
"Sannan kuma me, ina jinka"
Ya ɗan muskuta ya ce "Abba dan Allah ka bani auren
Arfa"
Take annurin fuskar Abba ya ɗauke, ya ce "Auren arfa
kuma?"
Ya ɗan yi shiru yana wasa da yatsunsa.
Abba ya numfasa ya ce "Kenan kishi ne ya saka ka shigo
kana yi mata faɗa?" Ya girgiza kai ya ce "A'a Abba, ba haka bane
ba"
"To, Nasir kai ɗa na ne, hakazalia arfa, babu wani
banbanci a tsakaninku, dan haka ba zan so abun da zai cutar da ɗayanku ba. Ba
zan manta abun da mahaifiyarka tayi mini a kan yarinyar nan ba, kuma haryanzu
ina kallon irin ƙiyayyar da take nuna mata, na daɗe da gane kana sonta, amma
ina fatan ta samu wanda hankalinta zai kwanta da shi. Muddin ka aureta
mahaifiyarka ba zata taɓa barinta ta zauna lafiya ba.
Ni bani da matsala da son da kake yi mata, amma ka nemi
yardarta, da ta mahaifiyarka tukuna"
Nasir ya ce "To Abba, na gode sosai" ya tashi ya
bar ɗakin.
Nabila banɗaki ta shige, ta rufe ƙofa ta kira Viper.
"Yanzu fisabilillahi ka kyauta mini kenan? Ka saka an
yi mini faɗa, Allah ne ya rufa mini asiri, dan Allah ka daina zuwa in da nake,
gara ka kirani na zo da kaina"
"Ki je ki yi tunani a kan abun da na saka ki, ki san
abun yi sati biyu kawai ki ke da shi"
"Ya kake bani umarni ne a haka, ka din ga lallaɓani
mana, why are you always bossy ne? Sai da safe zan duba na ƙara effort, ina iya
ƙoƙarina a kai, tauye ni ake yi, ka san ba ni da kowa sai Allah ni, amma ka yi
mini addu'a in sha Allah ni zan kawo ƙarshen bunkure"
"Allah ya sa" ya kashe wayar.
***
Ramma ce ta ƙurawa wayar Abdul ido, ta kalli ƙofar banɗaki,
yana ciki yana wanka, ta miƙa hannu ta ɗauka ta bar ɗakin.
Bai jima ba ya fito daga banɗakin, sai dai ya nemeta ya rasa
a ɗakin, ya fita nemanta, ya tafi kitchen, ya tarar da ita a tsaye a kitchen,
da wayarsa a kunnenta cike da rashin gaskiya.
Babu tsammanni ta ji ya fizgota, ya kwaɗa mata mari, har sai
da ta faɗi ƙasa.
Ya duba call logs ɗin sa, ya ga ba a ɗaga kiran da ta yi ba,
ya kalleta a matuƙar fusace ya ce "Saboda kin ga ina ɗaga miki ƙafa shi ne
zaki tsallake gona da iri, zaki wuce makaɗi da rawa? Bari na koma miki ainihin
Abdul ɗina, kuma wannan huakan da ki ka yi, dai-dai yake da sake nesanta kanki
da iskar 'yanci. Kuma bari na sake gaya miki, babu wani mahaluki da ya isa ya
rabani da ke a duniyar nan ko waye shi, idan kin ga dama ki cigaba da ƙoƙarin
lallai sai kin bar gidan nan, zaki ga yadda zan yi da ke"ya fice daga
kitchen ɗin ya bar a zaune, hannunta riƙe da kuncinta, hancinta har ya fara
zubar da jini, saboda azaba.
Ta rasa me ma yakamata tayi, saboda zuwa yanzu zuciyarta ta
ƙeƙashe, kukan ma ba iya yin sa take yi ba.
Ta ja wuri ta zauna sosai saboda jirin da take ji.
***
Sallama take yi a tsakar gida, ta ce "Na shigo ko na
koma?"
Umma da take ƙofar kitchen ta ce "Idonki kenan arfa?
Yaushe rabonki da gidan nan?"
"Tuba nake umma, ayyuka ne sun yi mini yawa sosai, amma
ayi mini afuwa dan Allah"
Umma ta ce "To Allah ya yi jagora"
"Amin umma, ina sumayya?"
"Tana ɗakinta"
Nabila ta nufi ɗakin sumayya, ta sameta tana ta aiki a cikin
computer, sallamarta kawai ta amsa, ta mayar da hankali ta cigaba da abun da
take yi.
"Sumy, dan Allah ki kalleni mana"
Sumayya ta ɗago ta kalleta ta ce "Idan na kalleki mai
zai amfana miki, ni da nake munafuka?"
Jiki a sanyaye ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, nayi
kuskure abun ne ya bani mamaki ya ɗaure mini kai"
Tuni hawaye ya cika idon sumayya ta ce "A yadda muke da
ke, ban taɓa tunanin wani zai kawo miki aibuna ki yadda ba, ba tare da kin yi
bincike ba, amma kai tsaye ki ka danganta ni da kalmar munafunci, baki san
wahalar da nake ta yi dan kare rayuwarki ba"
Nabila ma sai ta saka kuka ta ce "Dan Allah masoyiyya
kiyi haƙuri ki yafe mini, ɓacin rai ne, kin ga sam baki yi mini bayanin komai
ba, na samu labarin an saka ki kina bibiyata, dole na shiga damuwa kuma ke baki
gaya mini ba"
Sumayya ta dubeta ta ce "Waye ya gaya miki ana
bibiyarki ta hanyata?"
"Ba shi da amfani faɗar, amma dan Allah waye ya saka ki
bibiyeni, ki din ga kai masa rahotona?"
Sumayya ta kalli Nabila da take ta share mata hawaye, Nabila
cikin jin kunya da sanyin jiki, take ta ƙara bawa Sumayya haƙuri.
Sumayya ta numfasa ta ce "Honorable indabo ne"
Nabila ta waro ido ta ce "Indabo kuma? Meye alaƙata da
shi? Me na yi masa?"
Nan Sumayya ta warware wa Nabila yadda suka yi da Indabo,
lokacin da ya ce taje gidansa su yi program.
Hankali a tashe Nabila ta ce "Amma meyasa baki gaya
mini ba Sumayya?"
"Ya za ayi na gaya miki? Ya ce muddin ki ka sani, zaki
iya rasa ranki, kuma na san dole zaki iya aikata wani abu, da zai sanya su yi
miki illa, babban abun da ya bani mamaki bai wuce lokacin da muka yi waya da ke
ba, ki ka ce kin haɗu da Viper, ya ƙara rikicewa gaba ɗaya, amma na tabattar
masa da ƙarya ki ke yi, baki haɗu da shi ba, ina tunanin akwai wani abu a
tsakanin sa da Viper, dan cewa yayi, zai yi wa Viper tarko da ke, ya kama
shi"
Gaban Nabila ya faɗi, gaba ɗaya sai kanta ya kulle.
"To tayaya zan zama tarkon da za a kama Viper? Meye
alaƙata da shi?"
Sumayya ta ce "Ban sani ba, amma dan Allah ki nutsu,
kar ki aikata wani abu da zai saka ya cutar da ke, wallahi rashin imanin
mutumin nan ya wuce tunaninki, ke hatta a wurin aikina akwai masu saka mana
ido, da kin zo sai su kirani, su ce me muka tattauna, har wayar da nake yi da
ke suke bibiya shiyasa nake kiranki da wasu lambobin"
"Na shiga uku, to ni uban me na yi masa? Sumayya da
wace lambar suke kiranki?"
"Private number ce, ba sa kirana da lamba" zumbur
Nabila ta tashi.
Sumayya ta ce "Ina zaki je?"
Tayi waje da sauri ta ce "Zamu yi qaya kawai" a
tsakar gida ta yi wa Umman Sumayya sallama ta fice.
Ƙaramar wayarta ta ɗauko, ta kira Viper, ya ɗaga a rikice ta
ce "Kana nan ne, gani nan zuwa"
"Ke tsaya mana, ki zo ina?"
"In zo wurinka mana ina cikin ruɗani da rashin
fahimta"
"Koma menene ki nutsu, ki yi mini bayani ina
jinki"
"Ni ba wani bayani da zan yi maka, kawai zan zo gani
nan".
Ya ce "Hanya babu kyau, na gaya miki kar ki zo fa"
"To a ina zamu haɗu? Rayuwata tana cikin hatsari, ni
kawai kana ina, na shga uku"
Viper da yake zaune ya tashi tsaye ya ce "Malama ki
nutusu ki yi mini magana, kina cikin hatsari kamar yaya?"
A fusace ya ce "Na gaya miki hanya babu kyau, ana
bibiyarki ko kin manta? Za a fara tracking wuraren da ki ke zuwa yanzu haka. Ki
tsaya ki saurare ni.
"To ina jinka"
"Zan tura miki adress ɗin da zaki same ni, idan kuma ni
in zo shikenan"
Ta ce "A'a kar ka zo"
"Ki samu wuri ki ajiye motarki, zan turo miki adress ɗin
in da zaki same ni".
"To ka yi sauri" ta cigaba da tafiya a motar, tana
waige-waige ko zata ga wani yana bin ta.
Ya turo mata adress ɗin da zata same shi, ta ajiye motarta,
ta bi adress ɗin.
Wurin kamar garden haka yake, ba kowa a wurin, sai manyan
bishiyu, ga wurin sanyi mai daɗi.
Tana tsaye tana waige-waige, ta ciro wayarta, tana ƙoƙarin
kiransa, kawai ta ganshi unexpected a bayanta, sakin wayar tayi ta hau ihu.
"Menene?"
"Ba tsorata ni ka yi ba, sai ka zo kana wani sanɗa da
na zura da gudu fa, ka daina wannan sanɗar".
Ya kalleta ya ce "Idan ban yi sanɗa ba, ban amsa sunan
Viper ba, sai da aji hucina, ko bayan nayi ɓarna a ankare da na zo wuri, gani
menene?"
Ta ƙare masa kallo ta ce "Ɗan beauty"
Ya tsuke fuska ya ce "Neman me ki ke yi mini?"
Cikin damuwa ta ce "Mu zauna, na gaji da tsayuwa"
Suka samu wuri suka zauna, ta ce "Dan Allah Viper meye
haɗina da Indabo? Shi ya saka sumayya take bibiyata. Ta gaya masa yadda suka yi
da sumayya.
Ya numfasa ya ce "To me zan yi miki?"
"Ban gane ba, ka gaya mini meyasa Indabo yake bibiyata,
me nayi masa?"
Cikin ko in kula ya ce "Ya za ayi in sani?"
"Dan Allah ka gaya mini, kai ma fa ka tambayeni ko na
haɗu da shi, me kake ɓoye mini ne? Dan Allah ka gaya mini mana"
"Meyasa liti ya rikice ranar farko da ya ganki, ya
amince ya kawo ki maɓoyata?"
Ta ce "To ya za ayi in sani, ina tambayarka kana
tambayata? Ka gaya mini mana"
Ya ɗago ya tsura mata ido.
"Ka yi magana mana, dan Allah meyasa yake bibiyata, ta
ce ya rikice lokacin da ya ji na ce na haɗu da kai" still bai yi magana
ba.
"Talk please"
Zuciyarsa ya ji tana harbawa da sauri, ya girgiza kai ya ce
"Kamar na ji kin ce mamanki ta rasu ko?"
Turɓune fuska ta yi ta ce "wai ina ta rayuwata, kana
tambayata wani abun daban".
"Nan gaba zaki so jin dalilin da ya sa na tambaye ki,
bana surutun banza ni"
Kamar za ta yi kuka ta ce "To ni yanzu ya zan yi da
wannan indabon?"
Viper ya ce "Ba ruwanki da shi, ni ne dai-dai shi, ki
ji da bunkure karki manta, sati biyu kawai na baki ki yi mini aikina"
Ta narke murya ta ce "Nawa zaka bani ne da ka sakani
aikin, ka san dai ba lawyer gwamanti ce ni ba"
"Nawa ki ke so?"
"Kai nake so" gabansa ya faɗi, da ya tuna Jauhar
sararta ce faɗar haka.
"Kina wuce gona da iri" yayi maganar yana kallon
in da yake facing.
"Daga zuwanka, ka saka DSP ya haɗa ni da Abba, an ce
sai na duba samarina na fito da miji, sai ka aureni, tun da duk kai ka janyo
koma menene"
"Are you serious? Ɗan ta'addan zaki aura kina gidan
masu kaki?"
Ta ce "Eh mana, ka bani dama na zama yar suganka"
Ya ɗora hannunsa a kan ƙirjinsa, ya ce "Ki daina wannan
wasan ba na son sa ko kaɗan, haryanzu ina jin motsin jauhar a cikin zuciyata.
Idan ki na irin wannan maganganun ji nake tamkar na aikata zunubi mai girman
gaske, babu wani abu da zan iya haɗawa da soyayyar jauhar a zuciyata, ki kiyaye
wannan ki daina wannan wasan, kar ya zama gaske".
"Ba ka son yar sugar kenan sai madara ko?"
"Ke ki ka san sugan, ni ba na ta'amalli da shi ma"
"To zuma fa ko mazarƙwaila" ya yi mata shiru.
Ta tashi ta ce "Kar ka so ni ɗin, amma to ni ya zan yi
da wannan indabon bashi da imani, kar ya kashe maka ni"
Viper ya ce 'Idan ya kashe ki ya hutar da ni"
Murguɗa masa baki tayi, ta kama hanyar tafiya. Sai da tai
nisa sannan ya waiwaya yana kallonta.
Ita kanta murmushi ta yi, saboda yau ya sake, babu wannan
alamar ƙuncin da damuwa a tare da shi.
***
Da daddare Nabila tana kan social media, taga wani dogon
rubutu, da aka yi, na jinjinawa Naja bunkure, a kan ayyukan ta na jin ƙai.
Sumayya na ganin posting ɗin, tayi tagging ɗin Nabila.
A take Nabila tayi reposting ɗin post ɗin, tare da caption
kamar haka *Lokaci yayi da yakamata mu san haƙiƙanin ayyukan da Bunkure
foundation ke gabatarwa, shin da gaske dan talaka take yi, ko kuwa dan rufe ɓarnar
masu ido da kwalli kawai take yi?.
Mu duba case ɗin yarinya zulaiha, da ya faru shekarun baya,
wadda ta fuskanci cin zarafi, daga wani ɗan mai kuɗi, bunkure foundation sun
shiga case ɗin domin su tsaya mata, a hukunta shi, amma ƙarshe sai labarin
mutuwar zulaiha muka ji, ta kashe kanta ta hanyar shan fiya-fiya, shi kuma
wanda ya aikata, yana shekarar ƙarshe na kammala karatun degree a ƙasar
Amurika.
Bana ƙwaina sai da zakara, akwai tarin hujjoji da nake da su
a kan maganata.
Jikinta na tsuma, ta yi posting ɗin, ta rufe data.
Tayi addu'oin kwanciya bacci, ta kashe wayarta, har ta rufe
ido maganganun ta da Viper suka faɗo mata.
Lumshe idanunta ta yi, amma maganar sa ta din ga kai komo a
zuciyarta.
*Ba zan iya haɗa soyayyar jauhar da komai ba, dan haka ki ma
daina wannan wasan*
Dafe ƙirjinta ta yi, ta ce "Na shiga uku,
tausayin sa kawai nake ji, da wasa nake yi, me nake ji a raina ne?' ta tambayi
kanta.
Wasi-wasi ne kawai, ta bawa kanta amsa tare da kwanciya.
Washegari da safe bayan sallar asuba, ta kwanta ta sha
bacci, kasancewar lahadi ce, babu aiki.
Sai wajen ƙarfe goma ta tashi, ta yi wanka ta fito ta shirya
ta ɗauki wayarta ta kunna.
Jerin saƙonni ne suka din ga rige-rigen shigowa wayarta,
bayan ta kunna data.
Messages kuwa, ga na barrister Habib, ga na summaya.
Ƙarƙashin post ɗin ta kuwa, comment ya kusa dubu, da masu
kare Bunkure da masu zagin Nabila, kasancewar alherin bunkure galibi mutane
suka sani.
Ta ɗaga kiran wayar sumayya da yake shigowa, ta ce "Ya
ne?"
"Nabila daga tagging ɗin ki a post, kin rikita
media"
Nabila ta ce "Ai makaho ba ya sanin ana kallonshi sai
an taɓa shi, bar su su gama haukan da kare ta, ina nan zan saki maganar ramma
bayan an kuma zaman kotu".
"Amma Arfa kar fa ta yi miki wani abu"
"Ba abun da ta isa ta yi, ai ina da hujjoji "
"Allah ya ƙara tsare ki, zan cigaba da nemo miki
sahihan bayanai a kan ta"
Naja ta kalli posting ɗin ta yi murmushi ta ce "Bari na
nuna wa yarinyar nan ainihin kalata da take son gani.
Kira Nabila ta gani da private number, babu tsoro ko fargaba
ta ɗaga.
"Wane irin move ne haka, kin san mutanen nan ba za su
barki ba ko?"
Nabila ta ce "Kai ka bani aiki ka ce nan da sati biyu,
aka yi sara a kan gaɓa, sumayya ta yi tagging ɗina a kan post ɗin, na ga ya
dace na tofa wani abu".
Viper ya ce "Shikenan, amma ki shirya matakin da za su ɗauka
a kanki"
Nabila ta ce "Ina da kai ai, idan na je aiki zan
kiraka"
Nasir ne ya faɗo ɗakin ta ya ce "Nabila, wai meyasa
baki da hankali ne"
Ta kalleshi ta ce "Me nayi kuma?"
"Ban ja miki kunne a kan Naja'atu Bunkure ba? Kin je
kin tsokanota, gashi an fitar da sanarwa hukumar DSS suna nemanki, an shigar da
ƙararki for defomation of character".
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Ta ce "Ban gane ba, su DSS ɗin uban me na yi musu suke
nema na, kamar wata 'yar ta'adda".
"Shut up, ina magana kina yi mini gatsali, abun da nake
ta ankarar da ke kenan ai, matar nan tafi ƙarfin ki, ba sa'ar yinki ba ce ba,
amma saboda zunzurutun taurin kai, da zigar da ki ke ɗauka, kin cigaba da abun
da ki ka ga dama, da yake ba kya son zaman lafiya"
"Ina son zaman lafiya DSP, kuma duk abun da nake yi da
hujja nake yin sa, dan haka a gaban kotu yakamata ta ƙalubalance ni, ba wurin
DSS ba, uban me nayi mata?"
"Look arfa, matar nan ba zata bi abun da doka ta tanada
ba, dan tana tsoronki, koma menene za ta yi shi ne, dan kawai ta tozarta ki, ta
nuna miki ke ɗin ba kowa ba ce ba, kuma babu abun da wani ya isa yayi. Ko
hurumin DSS ne su kama ki, ko ba hurumin su ba ne, za su yi abun da ta ce ne,
kuma babu mai ƙwatarki"
Kawai Nabila ta saki murmushi ta ce "Ai DSP duk wanda
ya ce ayi wasan jifa, ya san me ya taka ne? Dss ai ba lahira bane ba, a yadda
nake ji na yanzu, hukuncin Allah shi ne abu mai razanarwa da firgitarwa a gare
ni. Ban fara wasan ba, sai da na tabattar da ingancin ƴan wasa na. Ita
taƙamarta tana da manya a sama, da zasu tsaya mata, abun da ta manta da ita da
manyan banzan nata shi ne, ƙanan na ƙasa su suka zama tsaninsu wurin zuwa
ƙololuwar in da suke tafka tsiyar, daga zarar na ƙasan sun yi bore, na saman dolennsu
su shiga hankalinsu, ita ta iya Black market ni ta hanyar shari'a zan nuna mata
kuskurenta legally"
"Shut up a beg, uban me ki ka taka, mara hankali kawai,
zaki tayar wa da mutane zaune tsaye" tayi masa shiru ya fice yana sababi.
Nan fa yan gidan, suka samu topic of discussion, ko a
jikinta, ta gama shirinta tsaf, Baba magajiya ta iske a falo, ta ce
"Yauwwa arfa, dama ke zan zo na kira, babanki na nemanki yanzu da
gaggawa".
Duk da sauri take yi, amma ta nufi ɗakin Abba, ta iske shi
da shi da Nasir, hankalinsa a tashe.
"Arfa, me ki ka je ki ka aikata? Yayanki ya ce kin yi
posting a social media kin tayar da tarzoma jami'an tsaro suna nemanki"
Nabila ta ce "Wallahi Abba ban tayar da tarzoma ba,
gaskiya kawai na faɗa, kuma haryanzu a hukumance ni ban ga cewar DSS su kama ni
ba"
"Ƙaniyarki da ke da hukumar, amma dai kin san ni yanzu
ba da bane ba da zaki je ki tsokano mutane ko, tsokanar taki ma, ki ka kasa yin
dai-dai da ke, sai in da zaki sha wahala, haka kurum ki tayar mana da zaune
tsaye, muna zaman lafiya a ga DSs sun yi mana dirar mikiya a gida, kamar wasu
yan ta'adda".
"Abba ba su da hurumin kama ni, ban ɓata wa kowa suna
ba, gaskiya kawai na faɗa"
"Rufe mini baki, ko na saka ki tsallen kwaɗo yanzun
nan, mara kunya fitsararirriya".
Wayarta ce take ringing, ta ce "Bari na ɗaga waya"
"Hello yaya Habib"
"Nabila kina ina ne?"
"Ina gida, yanzu zan fito wurin aiki"
"Maza ki hanzarta ki ƙaraso, na ga wani rumors yana
yawo, a kan posting ɗin da ki ka yi jiya, wai Dss suna nemanki, duk da ba
officially na ga sanarwar ba, magoya bayanta ne suke ta zuzuta maganar, maza ki
ƙaraso mu riga su ɗaukar mataki"
"To Barrister, gani nan in sha Allah" ta sauke
wayar ta ce "Abba daga law firm ɗinmu ne, bari na tafi"
"Ki tafi ina, an ce ana nemanki?"
"Eh zan je in ji me za su ce ne"
Abba ya kalli Nasir ya ce "Ka kai ta law firm ɗin na
su, duk yadda ake ciki, ka kirani, zan je na ga likita sai na biyo"
Sam Nasir ba haka ya so Abba ya yi wa Nabila ba, ya so ya ja
mata kunne sosai, ya taka mata burki a kan abun da take yi, amma bai yi hakan
ba.
Suna tafe a mota, ba ta kula shi ba, sai waya take yi da
sumayya da murtala, sumayya ta ce zata ƙarasa law firm ɗin su Nabila.
Tana sauke wayar sumayya, kira ya shigo, an rubuta
Confidential a kan lambar.
Ya kalli Nabila, ya kalli wayar, kasancewar Bluetooth ne a
kunnenta, ya sanya ta amsa dan kaucewa zargin sa.
"Hello boss"
Viper ya ce "Ya ake ciki? Sun kama kin ne?"
"So ka ke su kamanin kenan?"
"Am asking? Ya ake ciki?"
"Eh, ba su da hurumin kama ni, yanzu ina hanyar law
firm ɗin mu ne, Oga na a wurin aiki ya ce maza naje, a riga su ɗaukar
mataki".
"Ok, amma you over react, na so ace a sannu ki ka bi
abun, amma yanzu zamu raba hankalinsu biyu, zan yi wa Indabo aike, hakan zai
sanya su kasa tsayar da hankalinsu wuri guda"
Ta kashingiɗa da jikin seat ɗin mota ta ce "Aiken
me?"
"Ke da waye a motar nan?"
"Meyasa ka tambaya?"
"Akwai rashin sukuni da tsoro a cikin maganarki, ke da
wayar"
Nabila ta waro ido ta ce "Kai ya aka yi ka gane, vi....
Saurin katse maganar tayi, da tuna katoɓarar da kusa tafkawa.
Tayi gyaran murya ta ce "Zamu yi magana anjima, yanzu
ina cikin zullumi jami'an tsaro za su kama ni, ka bari na yi salati na nemi
agajin Allah"
Viper ya ce "Ok" ya kaste kiran.
"Da wa ki ka yi waya?"
Ba tare da ta kalli Nasir ba, ta bashi amsa da abokin aikina
ne.
***
Ramma ta takure kanta sosai da sosai, tun da Abdul ya
dake ta, ya fice daga gidan ba ta sake ganinsa ba, itakaɗai take kwana take
tashi, kuma ya ɗauke wayar da ya bata, da take kiransa a ita, hatta system ɗin
sa guda ɗaya da yake ajiye mata, yana koya mata computer ko tayi kallo, dan har
fina-finai na hausa, yake yi mata downloading dan su din ga ɗebe mata kewa,
gaba ɗaya ya haɗa ya kwashe, ƙofar da zata fito da ita, ta sauka daga kan bene
ma zuwa falon ƙasa, duk ya haɗa ya rufe.
Sam ba ta ko iya cin abinci, damuwa ta dawo mata sabuwa fil,
ta rasa abun da yake yi mata daɗi baki ɗaya.
Tana zaune bayan sallar isha'i a bedroom, ta ji ya buɗe ƙofa
ya shigo, a razane ta waiwaya ta ɗan ja da baya.
Ya ɗan tsura mata ido, sannan ya mayar da ƙofar ya rufe, ya
nufi in da take hannunsa da leda.
Ya ajiye ledar, sannan ya zauna a kusa da ita, amma ta sake
ja da baya.
"Guduna kuma ki ke yi yau?" Da ya motsa sai ta
zabura, dan gani take dukanta zai kuma yi.
Shammatarta yayi, ya janyota jikinsa, ya rungumeta a
ƙirjinsa ya ce "Am sorry please, ki yi haƙuri dan Allah" ta yi shiru
ba ta ce masa komai ba.
"Ki yi haƙuri, tsantsar tashin hankali da na shiga ne,
ya sanya na aikata miki abun da nayi, bana son gardama da taurin kai, tun da ki
ka ga na ajiyeki, duk da irin son da nake yi miki, da magiyar da ki ke yi mini,
ban mayar da ke gida ba, akwai matsala ne, mamanki ina zuwa wurinta, na
tabattar mata da kina cikin ƙoshin lafiya, abin da ki ka yi shirin yi, barazana
ne ga rayuwarki. Wallahi regret ne ya hanani dawowa tun da na fita na nutsu,
gaba ɗaya nake cikin damuwa, amma ki yi haƙuri dan Allah"
Tayi lamo a jikinsa, amma taƙi magana.
"Rahama talk dan Allah, ki yi mini magana mana ko na ji
daɗi dan Allah ki yi haƙuri ki yafe mini, son da nake yi miki ne ya sanya na ga
abun da ki ka aikata barazana ne ga cigaba da kasancewarmu tare, ki yafe
mini" ai kamar gunki, taƙi cewa uffan.
Ya ɗago fuskarta, yana kallonta, amma ta sunkuyar da kanta
ƙasa.
Ya janyo ledar gabansa, ya buɗe tsire ne fal a ciki, ya ce
"Ki ci abinci, duk kin faɗa kwana biyu, dan Allah ki yafewa Abdul ɗinki,
ba zan ƙara dukanki ba"
Ta saka hannu ta share hawayenta ya ce "Yauwwa babyna,
ai na zaki yafe mini, kina da yafiya shiyasa nake ƙara ƙaunarki Rahama, Allah
ya yi miki albarka ya shirya miki ni" da ƙyar ya din ga bata abincin a
baki, ta ci kaɗan ta tashi, sam taƙi sakar masa fuska.
***
Nabila suna zuwa law firm ɗin su, Barrister Kabir ya
balbaleta da faɗa, Nasir ma ya taya shi, akan kasadar da ta yi.
Duk da Nabila ba ta son faɗa a rayuwarta, amma ko a jikinta,
ta maze tana cunkusa baki.
Barrister Habib ya ce "Dan Allah ku yi haƙuri haka,
aikin gama fa ya riga ya gama, ta riga ta aikata, sai a san abun yi, kuma
wannan duk ba abu ne na tayar da hankali ba, in dai mutum yana da gaskiya, ai
faɗa ba nasa bane ba.
Nabila shigo office mu yi magana.
Barrister Kabir ya ce "Naga kamar goya mata baya kake
yi Habib, idan kuka janyo abun da ba zaku iya ba, to ku tsaya can, kar ku raɓa
ni a ciki"
"To barrister idan ba a goya mata baya ba, kware mata
baya zamu yi, ma'aikaciyarmu ce, tayi abun da wani bai yi yinƙurin yi ba, ai
kamata yayi a duba, idan akan gaskiya take, a ƙarfafeta, shigo mu yi
magana"
Nabila ta shiga cikin office ɗin sa, ya ce "Good girl,
i like your confident, a lady of her words, kin dage sai kin cimma burinki a
kan matar nan"
Ta ce "Yanzu dai ba wannan ba, meye abun yi, kafin a zo
a kamani, nima su saka a kaini prison a ajiyeni babu Shari'a kamar yadda suka
yi wa Viper"
"Suka yi wa Viper ita da wa?"
Nabila ta ce "Oho mata, shi ma wannan case ɗin ina nan
zuwa kansa, zata gane bata da wayo ai"
Yayi murmushi ya ce "Ba wannan ba, na yi wa Bashir ma
magana, yana hanya, zamu yi maza mu shigar da ƙara, a kan lallai kotu ta
dakatar da kamun da aka ce Dss su yi miki idan ma da gaske zasu kamakin, ba su
da wannan hurumin, sannan su daina yi miki barazana dan kin faɗi albarkacin
bakinki"
"To ayi sauri ayi, dan wani update ɗin zan saki, da ni
take zancen"
Duk da hantarar da Barrister Kabir ya yi wa Nabila, tare da
shi, da sauran lawyoyin law firm ɗin, suka haɗu suka tattara bayanai, da
hujjoji da za su kai kotu, dan hana kama Nabila.
Suna can suna ta ƙoƙari, Nabila suka keɓe da Sumayya, ta
tura mata videon yaron da ya ketawa zulaiha haddi, a cikin abokansa a ƙasar
amurka.
*Wannan shi ne Najib, wanda ya keta wa yarinya zulaiha
haddi, har ta kaita ga rasa ranta, a shekarun baya, shin ina shari'ar ta tsaya?
Ko ya fi ƙarfin doka ne, dokar a kan talaka kawai take aiki?
Kwana kwanan nan, mun ga yadda labarin wani matashi ya cika
dandalin sada zumunta, a kan yadda aka tsare wani matashi shekara goma sha
biyu, a gidan gyaran hali, bisa zargin sa da aikata fyaɗe, sai bayan shekaru
goman nan, a ziyarar da wani bawan Allah ya kai gidan, ya tausaya masa, ya
tsaya masa aka cigaba da yi masa shari'a har aka gano ba shi da laifi, saboda
shi talaka ne ya sanya Bunkure foundation ba ta shiga ire-iren cases ɗin nan,
sai dai na mata kawai? Me zai saka ace mata kawai foundation ɗin take tsayawa
ban da maza? Anya babu wata maganar a ƙasa?.
Wannan ra'ayina ne a matsayina na ƴar ƙasa, wanda yake da
ja, a gaban Alƙali zai ƙalubalance ni, ba wai a din ga yi mini barazana ba*
tayi posting ɗin tana murmushi, ta ce "Sumy na zama celeb fa"
"Zaki ci ƙaniyarki ke da celeb ɗin, kina kan sirɗin
duniya kina rashin mutunci, akwai buƙatar mu nutsa sosai, mu cigaba da samo
hujjoji, dan mutane su yadda da abubuwan da ki ke tonawa, dan na san haryanzu
akwai masu tantama a kai"
"Haka ne, wannan kuma sai idan muka sake tsayawa a
gaban kotu a kan case ɗin ramma"
"Allah ya ƙarfafeki, ya baki sa'a"
"Amin godiya nake masoyiyya"
Sumayya ta ce "Amma Nabila ya za ayi da Indabo ne? Ina
tsoron mutumin nan, kin ga kuma shi babba ne, tun a lokacin na so na kai
report, amma yayi mini kashedi a kan haka, babu ma wanda zai yadda da ni,
saboda muƙaminsa"
Nabila ta ce "Rabani da zancen wannan mutumin, ni yanzu
wannan matar ce a gabana, shi kuma akwai dai-dai shi"
"Wa kenan?"
Nabila ta basar da zancen ta shiga wani.
***
"Indabo ka yi wani abu a kan lamarin nan, lallai a kama
yarinyar nan a koya mata hankali, ban san da me take taƙama ba, ba a taɓa samun
tsageran da yayi mini abun da take yi mini ba, idan fa asirina ya tonu, kuma
naku ya tonu wallahi"
"Kar ki damu, muke da ƙasar fa, babu abun da ta isa
tayi, na riga na bayar da order da ta kamata"
Ta kashe wayar, cikin fushi, tana mamakin ƙarfin halin
Nabila, manyanta ma sun gaji sun ƙyaleta, ba a iya ja da ita, amma yanzu yar
ƙaramar alhaki ta sakota a gaba.
Indabo ya daddana wayarsa, ya saka a kunnensa, "Barka
da wannan lokaci distinguish senator"
"Barka dai, ya ake ciki ne maganar yarinyar? Na ji kun
ce Dss su kamata ya ake ciki, dole fa a toshe duk wata hanya da za a tonawa
bunkure asiri dole a tosheta".
"Sir yarinyar nan fa tana da wayo, kuma tana da wanda
suka tsaya mata, ta tafi kotu, ta ce lallai a hana kamata kuma ba wanda ta ɓatawa
suna, sai dai bunkure ta ƙalubalanceta a gaban shari'a"
Ya numfasa ya ce "Haka ta ce? Wane alƙalin ne? Wace
kotun ce zan bayar da umarni a bi umarninta a ƙi bin nawa"
"Honorable ka gane wani abu, abun nan fa ya haɗa da
social media, ba zai yiwu mu yi abu gabagaɗi ba, su kansu ƙungiyar lawyoyin ba
zasu bari ba, kuma madam tana da magauta a cikin su kansu lawyoyin, za su iya
taimaka mata, idan aka yi over reacting, to asirin da ake gudun tonuwarsa zai
tonu"
Indabo ya ce "Shikenan, na fahimta".
***
Madaki ya kalli ƙafarsa, ya kurma wani irin uban ihu, tamkar
mahaukaciya, Lakwari ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri ka daina wannan ihun,
hakan ba mafita bane ba".
"Ka rabu da ni nayi ihun nan, sai na kashe yaron nan,
abun kunya ne ace kamar ni, ƙasƙantaccen maƙiyina, ya ga bayana ya sabauta
rayuwata, sai na kashe mai zamani na ƙarar da zuriyar su*.
Lakwari ya kalli ƙafar madaki, ta kumbura kamar mai dundumi,
sai wani irin koren ruwa ne yake fita daga cikin ciwon ga wari da yake yi, ga
maganin da aka bashi, aka ce ya din ga sakawa, ya sanya raunin ƙara
jagwalgwalewa, ko iya taka ƙafar baya yi.
"Madaki, ka yi haƙuri mu je asibiti a duba ƙafar nan,
ni fa ban ga alamar ciwon nan yana warkewa ko zai warke da haka ba, ƙara
jagwalewa yake yi".
"Idan na je asibiti asirina tonuwa zai yi, idan
lakwayen nan suka san alkadarina ya karye na shiga uku, kai ka san ta'adin da
na yi ai"
"Haka ne, amma duk da haka yakamata muje asibiti a duba
ƙafar nan, tun da babu sauƙi a ciki" ya din ga lallaɓa madaki har ya samu
ya amince.
Viper yana tsaye tare da su liti, ɗan mama ya shigo, Viper
ya ce masa ya ake ciki?
"Komai normal, saƙonka ya isa cikin aminci da kwanciyar
hankali. Na shiga area na yi bincike sosai, babu wanda ya san in da madaki
yake, amma an tabbatar mini da yana jinya, kuma lakwari ne a tare da shi, sai
dai ba a san in da yake ba"
Viper ya zaro russia, ya jujjuyata a hannunsa, ya kalli ɗan
mama ya ce "Ka nemo duk in da suke, ina son ka samo target mai kyau, in da
zan ritsa lakwari, na san ƙafarsa ɗaya ta mutu zuwa yanzu, zan hari wani wurin
na daban kuma"
"Sai da kai ubangidana, abun da ka ce shi za ayi"
"Bari mu ga respond ɗin da Indabo zai yi, idan ya ga
saƙona"
***
"Hello, barka da wannan lokaci"
"Yauwwa barka sir"
"Ina magana da justice maijidda ɗan rimi ne"
"Eh nice"
"Good, ina fatan kin gane mai magana?"
Tayi murmushi ta ce "Ya za ayi na ce ban gane ba sir,
na gane"
"Masha Allah, akwai ƙara da wata yarinya da sauran
lawyoyi suka shigar gabanki, barrister Nabila Yusuf maitama, a kan ki hana Dss
kamata, da kuma hana yi mata barazana, ki bi tsarin doka ki yi abun da ya dace,
na san dole za a nemi ki yi wani abu ba dai-dai ba, idan ki ka yi akasin abun
da doka ta tanada, zai iya janyo wa ayi seizing license ɗinki, nima umarni aka
bani daga sama"
"In sha Allah sir, zan yi abun da ya dace ba tare da
son rai ba, na gode sosai da sosai"
Ya ce "Yauwwa"
A media kuwa aka cigaba da samun musayar ra'ayi, kowa da
abun da yake faɗa, waɗanda bunkure foundation ta cutar, suma suka samu damar
bayyana ra'ayoyin su, duk da mutanen da suke ganin hassada ta sanya ake yi wa
bunkure hakan sun fi yawa.
Bayan Bunkure ta gama sakankancewa, ta gama da babin Nabila,
sanarwa ta fita, kotu ta haramtawa Dss kama Nabila, ko yi mata barazana a kan
abun da take aikatawa, a matsayin ta na ƴar ƙasa, tana da ƴancin faɗar
albarkacin bakinta.
Indabo kuwa yana cikin majalisa, ya zauna, ya fara ƙoƙarin
buɗe envelope ɗin da aka bashi, aka ce an aiko masa da ita.
Ya buɗe ta ya ƙara ciro wata ƙarama a ciki.
Hoton ciki ya kalla, Simon ne tare da Viper a cikin hoton.
Simon yana daga cikin yaran da Indabo ya lalatawa rayuwa, kuma ya zama ɗaya
daga cikin masu yi masa hidima, a wannan gidan da suke sheƙe aya da shi da
ire-iren sa, da suka sanya neman duniya a gaba.
Wanda shi ne ya kuɓutar da Nura guduma daga gidan, ya saka
shi a mota, ya haɗa shi da wani ya kai shi kano. Shi kuma ya gudu daga gidan,
indabo ya bayar da cigiyar a nemo simon, ya bayar da kwangilar a kashe shi, aka
tabattar masa da an kashe shi, amma hoton ya nuna masa kwanan nan aka ɗauka.
Cikin tashin hankali yake sake kallon hoton, tabbas na
kwanan ne hoton, saboda Viper ya ƙara girma, fuskar nan babu annuri a tattare
da ita ko kaɗan.
"Simon yana raye kenan?" Ya tambayi kansa, ya juya
bayan hoton ya ga an rubuta Viper da jan abu.
Bai san ya tashi tsaye ba, sai da na kusa da shi ya ce
"Honorable, ya aka yi ne? Me kake gani?"
"A'a ba komai, ulcer ta ce ta tashi" ko izini bai
nema ba, yayi waje daga cikin majalisar kamar babbar rigarsa zata harɗe shi ya
faɗi.
***
"Assalamu alaikum, Assalamu alaikum ba kowa a gidan
ne?"
Walid ya ce "Wa'alaikum Salam, barrister yau ke
ce?"
"Ina wuni Yaya walid"
Yayi murmushi ya ce "Lafiya ƙalau, yau kin tuna mini da
ƙanwata jauhar"
Ta ce "Allah sarki, Allah ya sa tana aljanna"
Ya amsa da "Amin"
"Ina ogan yake?"
"Ya tafi caji"
Ta ɗan yi turus ta ce "Caji kuma, kamar wani power
bank?"
Yayi dariya ya ce "Ya ce, ya fita shan iska yana wurin
wancan dutsen"
Ta ce "Ok, bari na je"
"To Allah ya sa yana ƙasa, ba saman ya hau ba"
Nabila ta ce "Idan ma saman ya hau, zan bi shi"
Da tazara daga gidan zuwa dutsen, duk da daga gidan sai ka
zata taku kaɗan zaka yi ka ƙarasa.
Daga nesa ta hango shi, a zaune a ƙasa-ƙasa, ta hango tashin
hayaƙi a wurin.
Ta ƙarasa da ƙyar, dan duk ta gaji, kwali guda ne a gabansa,
ta ƙarasa ta kai hannu ta ɗauke, caraf ya riƙe hannunta. Tsorata tayi, dan
cikin sanɗa ta ƙarasa wurin, amma har ya ankare da ita ya hanata ɗauka.
Ta haɗe rai ta ce "Sakar mini hannu, nan ka gama cewa
zan saka a lungu, shi ne zaka wani riƙe mini hannu?"
"Ni na kawo ki? Ban ce ki daina zuwa ba ma?"
"To ko kirana ba ka sake yi a waya ba, idan ma an kama
ni, ko ma menene ya same ni, ba ruwanka ko?" Tari ta fara yi, saboda
hayaƙi, sakar mata hannu ya yi, tayi sauri ta ɗauke kwalin sigarin da ashanar,
ta tura a jakarta.
Satchet ɗin maganin da ya leƙo a gefen aljihunsa, shi ma ta ɗauke,
tana mita "Wallahi Allah ya hore maka taurin kai, wannan shaye-shayen ne
ba zaka daina ba ko?" Ya ƙura mata ido, saboda jin tana ƙamshin turaren
florie irin na 'yar madara.
"Ina magana kana kallona, baka tausayin lafiyarka,
yanzu duk ƙoƙarin jauhar a kanka ya tashi a banza, yawaita yi mata addu'a,
istigfari da mayar da hankali a kan addu'a, shi zai rage maka damuwa, amma baka
ji, kullum cikin hayaƙi, da shan miyagun ƙwayoyi"
"Faɗa fa ki ke yi mini"
"Au kar na yi maka? Ka daina mana da na yi maka mana,
wannan abubuwan da kake yi ba shi yake nuna halaccinka a gareta ba, ka daina
abun da ka ke yi, ka zama mutumin kirki, shi ne cikar halaccinka a gareta"
Kawar da kansa gefe yayi a hankali ya ce "Angry
bird"
"Ni ce bird ɗin? Wallahi ni ba tsuntsuwa ba ce ba, da
ba ka neme ni ba, ni gani ai na zo, ba a kama ni ba fa"
"Dama na san ba za a kama kin ba ai"
"Haba ya aka yi ka sani?"
"Bani wayarki" ta ciro wayarta ta miƙa masa.
Ya ciro tasa ya danna, sannan ya saka a kunnensa.
Muryar P.A ta fito rangaɗau a waya ya ce "Hello"
Viper ya yi shiru, bai ce komai ba.
Ya sake cewa "Hello", still bai yi magana ba.
"Waye ne ya ɓoye lamba yake kirana, idan ba za ayi
magana ba, zan kashe, waye?"
"Mai zamani ne" waro ido P.A yayi ya ce "Wane
mai zamanin?"
"Zuwa yanzu, na san saƙona ya iske shi, ya shirya, zan
bayyana a lokacin da bai yi tsammanina ba, kuma ya daina wahalar da kansa a kan
lallai sai an kamani, ko da an kama ni, nafi ƙarfinsa, ya kuma jirani aikena na
biyu" ya katse wayar yana ajiyar zuciya.
"Kai, Oga kana burgeni, ka din ga acting kamar a film ɗin
indiya hausa, wai dan Allah, a ina ka ko yi wannan halin naka?"
Ya jefa mata wayarta jikinta.
"Amma wait, wai ne ka ke yi a wayata ne baka gaya
mini?"
"Yaushe zaki fara shari'ata?"
Nabila ta ce "Shari'arka akwai sarƙaƙiya boss, sonake
na gama da ta ramma gobe in Allah ya kaimu zamu koma kotu." Ya jinjina
mata kai.
"To zaka fara bani kuɗin aiki ai, ka ɗan ragen wani
abu, na din ga zuba mai, tun da na je fa aka nuna mini file ɗin ka, nake ta up
and down, ina tattara abun da zan tattara. In sha Allah zan zama sanadin daina
zubar hawayenka"
"Dama kuka nake?"
"A'a murna ka ke yi"
Ya girgiza kai ya ce "Ko matata da muna tare, ta daɗe
kafin ta iya kallona ta yi mini magana, balle ta yi mini baƙar magana, amma ke
kin mayar da ni kamar wani sa'anki, har hantarata ki ke yi"
"Ni ɗin ce na rainaka? Ni na isa wacece ni? Amma dan
Allah sweetheart meyasa ka kusa kashe ni ranar farko da na zo wurinka?"
Ya ɗago ya kalleta ya yi shiru.
"Ka amsa mini dan Allah"
"A lokacin ai kamar mahaukaci nake shiyasa"
Ta girgiza kai ta ce "A'a, wani abu na din ga gani a
idonka, da na rasa menene? Dan Allah meyasa?"
"Ke ban sani ba, tashi ki bar wurin nan"
Ta noƙe masa kafaɗa tana kallon idonsa, abun da ya tsana.
Yayi tsaki ya kawar da kansa gefe.
Turare ta ɗaukko a jakarta, ta toshe hancinta, ta fesa a
wurin. Ba shiri ya waiwayo yana kallon hannunta.
"Gashi yanzu na saka ka waiwayo ai, gashi saya maka na
yi" ya karɓi turaren, ya din ga juya shi a hannunsa yana kallo.
Ta na ƙoƙarin ɗaga wayar da ake yi mata, ta ga hawaye na ɗiga
a hannunsa.
Sai jikinta yayi sanyi gaba ɗaya. "Haba mai babban
suna, a yanzu fa kuka ba naka bane ba, wanda ka yi ya isa, mu cigaba da addu'a
da ƙoƙarin tattara shaidun da zamu shiga kotu da su, dan Allah ka daina bana
jin daɗi.
"Da jauhar na raye, da yanzu na san ta kammala law
school, maybe ta haifi yaronmu na biyu ko uku, ina da tarin burika a kanta, na
kyautata rayuwar ta, ta ji daɗi ta huta, saboda wahalar da ta sha a rayuwarta,
amma wauta ta da rashin hankali, ya sanya ta mutu ta bar ni a duniyar. Lokacin
da duniya ta yi watsi da ni, ake yi mini kallon mara amfani, ta rungume ni, ta
karɓi ƙaddararta, ta kula da ni, a lokacin da nake ƙoƙarin kyatata ratuwarta na
fara bata kulawa, lokacin da na fara gano haske yana tunkaro rayuwarmu, ashe
yayi daidai da lokacin da zan yi girbin ya mummunar hanyar da na zaɓawa
rayuwata, na rasata" yayi maganar yana ƙoƙarin mayar da hawayen sa, amma
suka cigaba da zuba, kamar an kunna famfo.
"Viper, ka yi haƙuri, Allah ya ambaci masu haƙuri a
wurare daban-daban a alƙur'ani, tare da yi musu bushara. Viper Allah ya fi kowa
so da kishin bawansa, wataƙila mutuwar jauhar a wannan lokacin shi ne mafi
alkhairin ta, a duk buɗe ido muka yi muka ganmu a duniya, dan haka ba zamu
tsarawa Allah yadda muke son kasancewa ba a duniya.
Ba kowa Allah ya tsarawa jin daɗi a duniyar nan ba, ai dama
ita duniyar kurkukun mumini ce, aljannar kafiri. Wani ga jin daɗin yana cikinsa
a zahiri, amma a baɗini rayuwar kawai suke yi mara ma'ana.
Yanzu tsohon ubangidanka ga duniyar ya samu, yana jin daɗin
amma nauyin zunubin da yake aikatawa ba zai taɓa barinsa ya rayu cikin
kwanciyar hankali ba. Ba sai mutum ya samu wadata dan ya sha wuyar rayuwa, shi
ne tabbacin Allah yana son sa ba, duk tsananin rayuwa da ka ke ciki, idan har
ya barka da imaninka, kuma ka yi kyakywan ƙarshe, wallahi ya fiye wa ɗan Adam
duk wani abun more rayuwa.
In dai ana samun aljanna a biyayyar iyaye, da biyayyar aure
in sha Allah Jauhar ta samu" ya jinjina kai yana cigaba da zubar da
hawaye.
Ta bashi handkerchief ɗin ta, ta ce "Share hawayen
haka, kaga ni ma ka saka ni kuka, bana iya jure in ga mutum a cikin damuwa ko
yana kuka, alhalin ba zan iya yaye masa damuwar sa ba.
Yanzu ni kaina, duk abubuwan da nan da nake yi, ƙarfin hali
nake yi, zuciyata akwai wani ciwo da yake addabata, ina kuka iya yi na wasu
lokutan, sai dai babu yadda na iya, da abun da ƙaddara ta zana mini" tayi
maganar ita ma tana kuka.
Ya ɗago ya kalleta, ya motsa baki, yana son ya faɗi wani
abu.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin hanzari Viper ya tashi ya tsaye, yana cewa "Kina
ina ne? Meyake faruwa?" Sai dai still shiru ba ta ce komai ba.
Su Walid ma duk suka miƙe tsaye, suna kallonsa.
Walid ya ce "Yaya meyafaru Viper?"
"Ki yi mini magana, kina ina meyake faruwa ne?"
Liti ya ce "Mai zamani menene wai?"
"Yarinyar nan tana cikin matsala"
"Subhanallah, to tana ina ne yanzu?" liti yayi
maganar yana kallon sa.
"Safiya ce yanzu, ko tana gida, ko hanya ko wurin aiki.
Babu yadda za a yi ace a gida ne wani abu ya same ta ta kira ni, da hanya ne
kuma da tuni an kai mata ɗauki, ko dai an ɗauketa ne ko kuma tana wurin aiki,
wuta na ji ta ce"
Hanyar fita Viper ya nufa, Walid ya riƙe shi ya ce "Ina
zaka fita ka je? Ba kai yakamata ka fita ba, liti ko ɗan mama, ɗan maman ma
dai, ka san wurin aikinta ai in da kuka ɗaukkota?"
Ya ce "Eh oga Walid"
"Je ka gano mana menene yake faruwa"
Ya ce "To bari na canza kaya"
Viper ya cigaba da bin layin Nabila yana kira, amma shiru ba
ta ɗagawa.
Nabila kuwa tuni ta fice daga hayyacinta, ba ta sake sanin
in da kanta yake ba.
Masinja ne da shigowarsa kenan, ya ga wurin ya turnuƙe da
hayaƙi, ya shiga dudduba daga ina hayaƙin yake fitowa.
Cikin tsananin tashin hankali, ya nufi ƙofar office ɗin
Nabila, ya din ga bubbuga ƙofar, amma ya ji ta a rufe gam, ya girgiza ya
girgiza amma a rufe, ya fito ya nufi wurin masu gadi, ya na sanar da su wuta.
Suka tashi gaba ɗaya suka rankaya a guje, ɗaya daga cikin su
ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Nabila fa ta shigo aiki, tana
ciki jama'a ku taimaka".
Nan da nan wuri ya cika da mutane, ana ta ƙoƙarin a ɓalle
ƙofar a cirota, a daidai lokacin barrister Habib ya ƙaraso cikin tashin
hankali, kasancewar an kira shi a waya an sanar masa.
Da kyar aka ɓalle ƙofar, wani irin huci mai ɗauke da hayaƙi
ya buso waje suka ja da baya, wani matashi ne ya kutsa kai, ya na nemanta, ya
hangota a yashe a cikin office ɗin ga jakarta da system ɗin ta, da wayarta a
wurin.
Wutar ta mutu ba ta cigaba da ci ba, iya wadda ta kama ce ta
haddasa hayaƙi, da huci mai zafi.
A kafaɗarsa ya saɓo Nabila, yana fitowa barrister Habib ya
karɓi wayar da system ɗin, yayi waje da ita. A motar barrister Habib aka saka
ta, suka nufi asibiti.
Barrister Kabir ma hankalin sa yayi mummunan tashi, ya din
ga kiran waya, Habib ya ce masa sun tafi da ita Asibiti.
Gaba ɗaya hankalin ma'aikatan wurin ya tashi, dan duk jin
kan Nabila da gayunta akwai girmama mutane, ga yawan kyauta da take yi musu.
Viper ya kasa zaune ya kasa tsaye, Liti da Walid ne suke ta
rarrashin sa, amma ya kasa nutsuwa, sai cewa yake tafiya zai yi ya gano halin
da take ciki, suka din ga kiran wayar ɗan mama, amma bai ɗaga ba.
Viper ya ce "Walid, ba zan lamunci a wannan karon
wannan ita ma ta rasa ranta ba, dole fa na gano halin da take ciki"
Walid ya ce "Mun sani, amma ka fara bari mu ji daga
bakin ɗan mama"
Suna tsaka da maganar ya kira waya, Viper ya fizge wayar
daga hannun liti, ya ɗaga ya ce "Kai ana ta kiranka ka ƙi ɗagawa, yaya aka
yi ka sameta?"
"Wuta ce ta kama fa a ofishin ta, lokacin da na je an
buɗe ƙofar an fito da ita, za a tafi asibiti"
"Dalla ba wannan na tambayeka ba, tana ina yanzu a wane
hali take ciki?"
"Eh, sun tafi kaita Asibiti, na bi bayansu a adaidaita
sahu, an kaita wani ɗaki an hana kowa shiga, haryanzu dai ina asibitin,
likitocin dai ba su ce komai ba, amma dai kamar fa ba ta da rai"
Ashar Viper yayi masa, ya ce "Yaya aka yi ma wuta ta
kama a iya ofishin ta kawai? Me hakan yake nufi? Likitoci sun ce ta mutun
ne?"
Ɗan mama ya ce "A'a ni nake tunanin hakan, bata motsi
ko numfashi a yadda naga an sakata a mota wallahi da ƙyar idan ba mutuwa za ta
yi ba"
Liti ya ce "Ɗan mama ko ɗan shegiya, gaba ɗaya yaron
nan gaɓo ne, ya za ayi ka gaya masa wannan maganar?"
Walid ya karɓi wayar daga hannun Viper, ya saka a kunnensa
ya ce "Ɗan mama kana ji na?"
"Eh oga Walid"
"Duk abun da ka ke ciki, ka din ga sanar da mu"
"To oga walid in sha Allah"
"Jikinta wutar ta taɓa ta ne?"
"A'a, ba ta ƙone ba, hayaƙi ne ya yi mata illa, wutar
ma ba ta kama sosai ba"
"To shikenan, muna saurarenka"
Walid ya kalli idon Viper, yadda ya bayyanar da matsanancin
tashin hankali.
"Viper, ka kwantar da hankalinka dan Allah komai zai zo
da sauƙi, in sha Allah ba zata mutu ba, sai ta cika maka burinka"
Jiki a sanyaye ya ce "Walid yanzu shikenan duk wanda ya
raɓe ni, rayuwarsa sai ta shiga hatsari, idan ita ma ta rasa ranta fa, jikina
yana bani set up ne abun nan"
Liti ya ce "Kar ka zargi kanka, dama can wannan ba ta
ji, kuma haryanzu ai bata fara shari'ar ka ba, balle ace saboda kai ne"
Walid ya ce "Ya isa haka liti, kai abu ba ya wucewa a
wurinka"
"Yaushe zai wuce, tun da ta munafurce ni, ta saka aka
kamani"
***
Abba kuwa Allah ne ya tsare bai yanke jiki ya faɗi na, bayan
sanar masa da cewar, gobara ta kama a ofishin Nabila tana Asibiti.
Haka Nasir ma, cikin gigita da tashin hankali, ya nufi
Asibitin da aka ce an kai Nabila.
Likitoci sun hana kowa ya shiga, an cire mata kaya an saka
mata wata gown, ana duba jikinta ko da in da ta ƙone, amma babu, sai dai ga
zuciyarta na bugawa, amma babu numfashi, idan tayi kamar zata yi numfashi, sai
tayi ta tari, hayaƙi na fita ta hancinta da bakinta, sai tayi ɗif.
Gaba ɗaya Abba a rikice ya ƙaraso asibitin, cikin
matsanancin tashin hankali Abba ya ƙarasa asibitin, zuwansa babu daɗewa Nasir
ma ya ƙaraso, Abba ya nemi a bar shi ya ganta, amma aka ce ba a shiga likitoci
na aiki tukuna.
Abba ya ce " 'ya ta ce, ko me za ayi mata ayi a gabana,
idan ma ta mutu ne a bari na ganta, ai ni musulmi ne na kuma yadda da ƙaddara
mai kyau ko mara kyau" suna ƙoƙarin lallaɓa shi ya haƙura kar ya shiga, ya
burkice musu, babu shiri aka bashi damar shiga wurinta.
A kwance ya tarar da ita, ana ta allurai, ya ƙarasa gaban
gadon ta ya zuba mata ido, dama ya lafiyar kura balle ta yi hauka, an sha
wahalar ciwonta na asma sosai da sosai, sai da ta girma ta ɗan samu sassauci,
tayi gado mai wahala, dan mahaifiyarta ce mai ɗauke da ciwon ta gada.
Ya kalleta a kan gado, sai ya ga ta koma masa kamannin
mahaifiyarta sosai da sosai, lokacin da take gadon asibiti ta riƙe hannunsa a
halin rashin lafiya.
Ya riƙe hannun Nabila, ya ga alamar akwai rai a jikinta,
amma a galabaice take, ya daɗe yana yi mata addu'a, sannan ya tashi ya fita
waje.
Barrister Kabir kuwa tuni suka yi reporting wurin Jami'an
tsaro, aka zo aka fara bincike a kan musababbin tashin wutar, abun bai tsaya
iya nan ba, sai da aka tattare masu gadin wurin, aka tafi da su wurin 'yan
sanda domin fuskantar tuhuma.
Sumayya ma tun kan ta ƙaraso asibitin take uban kuka, saboda
yadda aka gaya mata faruwar abun, ta riga ta fitar da rai Nabila tana raye.
Sai da Nabila ta shafe awa biyu, likitoci na procedure
daban-daban a kanta, aka samu numfashinta ya dawo, sai dai a wahale take yin
sa, aka fito da ita daga emergency, aka mayar da ita wani ɗakin.
****
Bunkure ta daki tebur ta ce "Tana raye kenan?"
Mutumin gabanta ya ce "Eh ranki ya daɗe, an samu
nasarar fitar da ita daga wurin, amma na samu tabbacin tana raye, bata mutu ba
sai dai tana cikin mawuyacin hali"
"Babu ruwana da mawuyacin hali, wannan wane irin aiki
ne? Yaya za ayi ni ga yadda muka yi da ku, amma abun da ku ka yi daban?"
"Ba daga mu bane ba ranki ya daɗe, wallahi aiki an yi
shi yadda yakamata, agajin gaggawa aka kai mata shiyasa"
Ta numfasa ta ce "Shikenan, zaka iya tafiya, a asibitin
zan saka a ƙarasata".
***
Hankalin Viper bai dawo jikinsa ba, sai da ɗan mama ya dawo,
ya tabattar masa da a kan idonsa aka fito da ita, tana raye, kuma ba ta ƙone
ba, ko ƙwarzane babu a jikinta.
Nannauyar ajiyar zuciya Viper ya sauke, yana fatan Allah ya
sa hakan, ya kuma bata lafiya.
Hatta 'yan gidan su Nabila, sai da suka tausayawa halin da
take ciki, duk da ba shiri suke yi da ita ba, baba magajiya kuwa kuka ta ɗora
hannu a ka ta din ga yi, ba ta san iya tashin hankalin da zata shiga ba, idan
aka ce ba Nabila.
Sumayya na gefen Nabilan, ta riƙe hannunta tana ta matsar
hawaye, tari ne ya kuma turnuƙe ta, kawai ta yinƙura zata tashi zaune, duk suka
nufo kanta, Sumayya ta riƙeta tana kiran sunanta.
"Viper wuta, wani ya kulle ni ta waje, ku taimaka mini,
Viper wuta" gaba ɗaya sai suka yi sak, suka zuba mata ido.
Abba ya ce "Waye kuma Viper?"
Cikin matsananciyar tuhuma Nasir yake bin ta da kallo, da
yake ta surutai cikin fita hayyaci.
Barrister Habib ma sak yayi, Sumayya ta ce "Abba sunan
wani ɗan daba ne, da take bincike a kan sa, maybe tana ƙadamin aiki a kansa ne
abun ya faru"
Abba ya ce "Na rasa irin Arfa, wataƙila ma a dalilin
wannan kwashe-kwashen nata, aka yi yinƙurin cutar da ita.
Barrister Habib ya ce "Bana tunanin haka sir, maybe
ƙaddara ce kawai, ai tana yawan zancen ɗan daban nan ne, ta ce Yayanta shi ne
incharge na nemansa tana fatan ta taimaka masa"
Nasir duk da ido yake bin su da kallo, yanayin yadda take
surutan, kamar akwai sabo da kuma shaƙuwa a tsakanin su.
A hankali sumayya ta ce "Masoyiyya"
"Na'am sumy"
"Na'am"
"Wuta aka saka mini a office ɗina, da ta tashi, na tafi
da gudu na buɗe ƙofa na ji an rufe ni ta waje"
Abba ya ce "A'a Arfa, Allah ne dai ya ƙaddara tashin
wutar, kar ki zargi kowa"
Nabila ta ce "Abba, ni fa na buɗe office ɗin da kaina,
na bar key a jiki ta waje na shiga, da wutar ta tashi na je na buɗe, na ji an
murɗa key ɗin sau biyu"
Abba ya ce "Ki na cikin hayyacinki, kin farka gaba ɗaya?"
Ta jinjina masa kai.
Ya ce "Alhamdilillah" nan aka din ga jera mata
sannu, duk da tana ta haki a hakan ma.
***
Ramma ce a tsaye, ta shirya cikin doguwar rigar abaya, ta ɗora
mayafin a kanta, Abdul ya bata facemask ya ce "Saka wannan" ta karɓa
ta saka, ya ce "Wow, kin yi kyau sosai beb" ta yi murmushi tare da
gyara mayafinta.
Ya riƙe hannunta, har cikin motarsa, da hannu ɗaya yake
tuƙi, hannunsa ɗaya kuma ya riƙe nata, loka-lokaci sai ya sumbaci hannunta,
yana jin wani irin so da shauƙinta yana ratsa ilahirin jikinsa.
"Ni ka daina shafa mini yawu a hannu"
"Haba Rahama, yawun ƙauna ne fa" yayi maganar yana
satar kallonta.
Ta jingina da seat ɗin motar, ta numfasa ta ce "Yaushe
ne bikinka, ko an yi ne?"
Ya ce "A'a, ya za ai, ayi ba ki sani ba? Wai bata
ƙarasa karatu ba, da an so ayi ne idan ta dawo shikenan ta tare, babanta ya ce
a bari ta gama, saura 2months"
Ramma ta ce "Allah sarki, ni nawa karatun ko oho, na
zama karuwa"
"Haba rahama, dan Allah ki daina wannan maganar, ina da
kyakykyawan tanadi a kan rayuwar ki da iliminki, na san na cutar da ke, amma
zan gyara laifina in sha Allah" tayi masa shiru tana kallon titi.
Dare ne sosai, duk sahu ya ɗauke.
Ya zuba mata ido, a lokacin da take shan ice cream ɗin
gabanta, ya tuna yadda yake ta fama da mahaifinsa, ya tsunduma tunanin ya zai
yi ya sanar da shi batun ramma? Dan sai dai ayi wadda za ayi a kan ramma, amma
bai ji duk iya bala'in da za ayi zai rabu da ita ba, ta kalleshi ta ce "Ka
sha mana" yayi murmushi ya jinjina mata kai, mama ya cigaba da jujjuya
cokalin.
Hakan ya sanya ta fuskanci a cikin damuwa yake, ta ɗebo
icecream ɗin ta kai bakinsa, ya ɗaga ido ya kalleta, ya buɗe bakinsa ya karɓa.
Ya ce "Kin yafe mini dukan da nayi miki, kin daina
fushi da ni?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
"To ɗaya laifin fa?"
"Ban yafe wannan ba" ta bashi amsa kai tsaye.
"Tun da ki ka yafe wannan, wancan ma zaki yafe mini in
sha Allah" ta yi shiru tana kallonsa.
Sai da ta gama ciye-ciyenta son ranta, sannan ya ce ta raka
shi asibitin abokinsa, zai duba wasu marasa lafiya.
A zuciyarsa yake zargin kamar wani cikin ne da ramma, amma
bai tabattar ba, kuma bai ambata ba, balle ta tashi hankalinta, muddin kuma ya
ce zai gwada za ta gane, kuma ta daina yarda da shi, dan ce mata yai, yayi mata
allurar planing, ba zata sake ɗaukar ciki ba sai allurar ta sake ta.
Waɗanda ya yi wa tiyata a asibitin ya duba, sun fito take
tambayarsa "Nan ne asibitinka?"
Ya ce "A'a, Asibitina na can wajen gari, na kan je wasu
asibitocin da aka buƙace ni, na gabatar da aiki, zan kai ki namun ma ki
gani"
Ramma ta ce "Naka dai"
"A'a namu dai, idan komai ya daidaita, ai bikinmu za
ayi, na nuna wa duniya ke, komai ya wuce"
Ta ce "Taɓ kwaɗo"
Babu tsammani yayi karo da wata matashiyar budurwa, hannunta
riƙe da ledar Pharmacy.
"Ke ba kya gani ne?"
"Ban gane bana gani ba, kawai ka zo ka tsaya a hanya,
kana rangwaɗa, da alama kai jin daɗi ne ya kawo ka asibitin ba mara lafiya ne
da kai ba" Ramma ji tayi kamar ta san muryar.
A fusace ya yinƙura zai yi masifa, ramma ta ce "Dan
Allah ki yi haƙuri, mun tsare hanya kam, Allah ya ƙara afuwa ga mara
lafiyan"
Sumayya ta amsa da "Amin" ta harare shi ta wuce.
"Dan Allah ka din ga rage faɗa, har marasa lafiyar ma,
faɗa ka ke yi musu, haba kai kuwa" ƙwafa yayi suka tafi.
***
Sosai Viper yake son kiran wayar Nabila, amma babu hali, dan
ɗan mama ya tabattar masa da ya ga an fito da wayarta, da jakarta da system ɗin
ta, wani mutum ya karɓa, amma alamu sun nuna a wurin yake aiki shi ma.
Viper bai san waye ya karɓi wayar da system ɗin ba, akwai
ayyukansa a cikin system ɗin ta, da suke buƙatar sirri sosai da sosai.
Nasir ya karɓi system ɗin Nabila da wayoyinta a hannun
barrister Habib, sai dai ya kasa buɗewa, dan bai san menene password ɗin ta ba,
har su walida ya tambaya ko sun sani, suka ce ba su sani ba.
Ƙaramar wayarta kawai ya iya buɗewa, sunan confidential ya
fara nema, yayi sa'a ya samo lambar, sai dai ya duba lambar da aka yi saving a
kan sunan, ya tarar da suna babu lamba, ya duba ya duba, amma ya rasa samun
lambar, ya din ga kwafar lambobin wayar, yana dubawa a Truecaller ɗin sa, amma
babu wani suspicious abu da ya samu.
Yanzu tantamar da yake yi a kan Nabila, ya wuce zargi, akwai
abun da take aikatawa na rashin gaskiya, ya ƙallafa ransa sai ya gano, waye
wannan mutumin da ya gansu tare sau biyu.
A kunne ya bar wayoyin, sai dai yadda aka din ga kira babu
ƙaƙƙautawa, tun yana ɗagawa yana saka ran, zai samu wani abu na information,
harya haƙura ya daina ɗagawa.
Nabila ta farga da rashin wayoyinta, ta tambayi a bata
wayoyinta, aka ce mata suna wurin Nasir, ta jira ya zo Asibitin ta ce ya kawo
mata wayoyinta ya ce ba zai bayar ba.
Cikin mamaki ta ce "Amma meysa na san za a neme ni a
wayar?"
Ya ce "Kina fama da kanki, uban me zaki yi da wata
waya?"
Sumayya ta ce "Ke ma dai arfa, uban meye a wayar ne, ki
hutawa kanki ki gama farfaɗowa" kallon Nasir take yi, tana nazarin irin
kallon da yake yi mata, ta fara fatan Allah ya sa ba wani abun ya gano a wayar
ba.
Abba ne ya shigo, suka gaggaisa, ya din ga tsokanar Sumayya
tare da Nabila, ko wurin aiki Sumayya ba ta zuwa, tana liƙe a asibiti da Arfa,
Sai da Nabila ta magantu a kan wurin aikin sumayya amma ta basar da ita.
Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin aka yi, sannan aka buɗe.
Jmau'an tsaro ne da bindigogi suka fara shigowa, gaba ɗaya
suka yi ƙuri da ido, suna kallonsu.
Alhaji wada m karofi ne ya shigo, suka gaisa da Abba, Nasir
ma ya gaishe shi.
Nabila ta ce masa "Lafiya, wannan kama ni za su
yi?"
Yayi murmushi ya ce "Saboda ke ce Sarkin laifi ba, yaya
jiki ashe haka wannan iftila'in ya faru?"
"To ai na ganka da yan sanda me na yi?"
Yayi mata shiru, suka ƙarasa gaisawa da Abba suka gaisa,
Sumayya ta ce "Ina kwana?"
"Lafiya ƙalau T ladan, ya gidan radio?"
"Yana nan sir"
Nabila ta ce "Dama kin san shi?"
Sumayya ta girgiza kai.
Ya ce "Eh ba lallai ta sanni, amma ita muryarta
sananniya ce ai, kuma kina bani labarinta ai, ko ba sumayya T ladan ba
ce?"
Sumayya ta jinjina kai tana murmushi.
Nan yake gaya wa Abba, ai a law firm ɗin Barrister Kabir
yake ganin Nabila suke gaisawa, shi yake sanar masa tsautsayin da ya faru.
Nasir dai ya din ga mamakin yadda karakainar Nabila, ta kai
ga ta ga sanin manyan mutane har haka, bayan ya gama duba ta, yayi musu sallama
ya tafi, Nasir ma da Abba tafiyar suka yi, aka bar sauda da Sumayya, suna
tafiya Saudan ma ta shura takalmanta ta fice, dama ba son zaman take yi ba.
Sumayya ta kalli Nabila ta ce "Nabila na ajiye aikina
fa"
Nabila ta waro ido ta ce "What? Saboda me?"
Sumayya ta numfasa ta ce "Hakan shi ne yafi dacewa
ne"
"Sumayya wannan ai wauta ce, meyasa zaki ajiye
aikin?"
"Na gaji da barazanar da ake yi mini, da tashin
hankalin da ake yi mini, Allah ya taimake ni an shiga tsakanina da indabo, ya
rabu da ni, amma support ɗin da muke baki, da ni da yaya murtala baki ga rashin
mutuncin da ake yi mana ba, ga hantara da tsangwama. Da barazanar kora babu yau
babu gobe, na ajiye musu bakin da Allah ya tsaga ba ya hana shi abun da zai
ci"
Cikin matsanancin damuwa Nabila ta ce "Sumayya baki
kyauta mini ba, da ki ka ɓoye mini wannan babban al'amari haka, ki rasa aikinki
a dalilina, haba sumayya".
Sumayya ta yi dariya ta ce "Kar ki damu, umma ma ta
sani, kuma ta bani ƙwarin gwiwa yaya murtala yana yi mana processing ɗin wani
sabon gidan radio, za su bani aiki da ni da shi, shi ma baro can zai yi, su ci
kansu"
Cikin damuwa ta ce "Sumayya duk da haka ban ji daɗi ba,
idan kuma ba a samu aikin ba fa?"
"Zafa a samu in sha Allah, na bawa yaya murtala cv na,
ya ce mini sun yi murna sosai da jin zan koma wurinsu, sabon gidan radio ne, za
a buɗe dama lawisa a ƙule take da ni, ta ƙara takura mini, saboda mutane suna
yi na, sai su kwaɗa gidan radion su cinye"
Nabila ta numfasa ta ce "Sai mu duƙufa addu'a
masoyiyya, Allah ya sa ki samu ya tabattar da dukkanin alkhairansa"
"Amin, amma Nabila wannan wutar kuwa ba set up bane ba,
ana sane aka sakata ba?"
Nabila ta ce "Set up ne mana, sai da na shiga na zauna
sannan ta kama, na taho na fita kuma, aka sakawa ƙofar key"
"Wa ki ke zargi?"
Ta girgiza kai ta ce "Bana zargin kowa, abun da nake yi
ne dai ba zan bari ba"
"Nabila"
"Na'am sumayya T ladan"
"Haryanzu kina zuwa in da Viper yake kuna haɗuwa?"
Nabila ta kalleta ta ce "Wace irin tambaya ce
wannan?"
"Amsa zaki bani, ba ki tambaye ni ba"
"Ban ga gurbin yin tambayar a nan ba, ko dai haryanzu
yaudarata ki ke yi, aiki ki ke yi wa Indabo a kaina?"
"Ko kaɗan, indabo ma Allah ya yi mini maganinsa, ya
rabani da shi, amma alamu sun nuna kina haɗuwa da Viper, da sunansa ki ka farfaɗo
a bakinki"
"Tuhumata ki ke ko zargi?"
"Babu ɗaya"
"To idan har ba aiki ki ke yi wa wani a kaina haryanzu
ba, to ki bar maganar nan"
Sumayya ta ce "Shikenan, an bar ta"
Likita ne ya shigo, ya kalli Nabila ya ce "Barrister
jiki yayi kyau, jiya doctor yasar ya shigo, ai da na sani nayi masa magana ya
duba jikin naki, idan da wani abu da zai ƙara miki"
"Doctor ni dai dan Allah ka sallame ni, na gaji
wallahi"
"Ki yi haƙuri, zai sake shigowa yanzu, mun yi waya da
shi, zai ga masu hawan jini kan ya wuce, kin san shi abun ne ya haɗar masa, ga
siyasa ga kuma aikin likita"
"Ashe kuwa zaka neme ni ka rasa a asibitin nan, tafiya
ta zan yi na gaji"
"No ba za ayi hakan ba, bari na rubuta miki sallama,
Alhamdilillah ai jiki yayi kyau sosai".
Sumayya ta ce "Mun gode sosai doctor"
Tashin hankalin da Indabo yake ciki a yan kwanakin nan, duk
sai tsufansa ya fito, ko bacci baya iya yi sai ya sha ƙwayoyi, saboda damuwa da
tashin hankali.
Cikin dare ya ga kiran Wada karofi, ransa ya ɓaci kamar kar
ya ɗaga, sai kuma ya ɗaga ya ce "Karofi wani irin wulaƙanci ne ya sanya
kake kirana ƙarfe ɗaya na dare?"
"Kashedi, da kuma gargaɗi, Nabila ta tsallake wannan
tarkon da kuka yi mata, kamar yadda na taka maka burki a kan ƙawarta, ina mai
ja maka kunne a kanta, wallahi wani abu ya samu yarinyar nan, zan yi abun da
baka so"
"Wacece hakan?"
"Ka fi ni sanin wa nake magana a kai indabo, mukiyaye
abun da zai zubar mana da mutunci a idon duniya a matsayin mu na 'yan siyasa
kuma sirikai da ni da kai, ba zan lamunci wani mummunan abu ya same ta ba, mu
cigaba da yaƙar juna ta ƙarƙashin ƙasa kar duniya ta ji wannan labarin ka
kiyaye"
***
Madaki ne ya lallaɓo ya fito daga cikin ɗakin da yake, yana
ta kiran wayar lakwari, amma taƙi shiga.
Walid ya gani a tsaye, yana kallonsa, ya tsaya cak, suna
kallon kallo.
Walid ya yi murmushi ya ce "Duk ƙoƙarin da ka yi, ka
gaza ɓoye mamakinka na ganina madaki, wannan da uban gayyar ka gani sai yaya
kenan?".
"Meya kawo ka wurina?"
"Ahh ai ba abun faɗa bane ba, zuwa na yi na duba ya
yanayin jikinka yake? Ni na hana mai zamani zuwa wurinka, da yazo nan da wani
zancen ake yi ba wannan ba.
Zuwa yanzu na san kana mamakin ina lakwari, kuma ya aka yi
muka san in da kake? Lakwari dai Macijin nan mai ban tsoro viper, ya saya shi a
cikin raminsa, sannan indabo yanzu ba ta taka yake yi ba, dan haka yanzu zaɓi
ya rage gareka kafin mai zamani ya waiwayo gareka, ko dai ka fita ka nemi
madafa, waɗanda ka zalunta su ƙarasa ka, ko kuma yunwa da wannan ruɓaɓiyar
ƙafar taka su ƙarasaka a wurin nan.
Ba zaka yi wa mai zamani wani amfani ba, saboda ya riga ya
gama da kai, iya hakan nan da ya barka azaba ce mai zaman kanta, sannan ka
sani, duk in da ka motsa ka tafi, yana sane da in da ka ke, ɗaukar fansa cikin
ruwan sanyi" ya ƙarasa maganar yana ciro wata zabgegiyar wuƙa daga
ƙugunsa.
Madaki ya zaro ido ya ce "Kar ka matso in da nake, kar
ka zo in da nake" yayi maganar yana dakatar da walid, dan idan yayi
kyakykyawan yinƙuri, ji yake kamar naman cinyarsa zai zaftare ya faɗi.
Babu tausayi, Walida ya kwarfe shi, ya danne shi a ƙasa, ya
zana masa V a gadon bayansa da wuƙar hannunsa.
Ya ce "Ka ce labarin Viper ba zai cika ba, sai an
ambaceka, to kai kuma har ka ƙarƙare rayuwarka kana dakonsa da alhakinsa a
kanka da gadon bayanka. Ka shirya a kowane lokaci zamu iya yi wa waɗanda ka
zalunta cunenka. Kuma ina yi maka Albishir da hukuma ta kama tabar wiwinka da
ƙwayoyi, baka ga tsuntsu ba ka ga tarko madaki"
***
Nabila ce tsaye a falo, tana yi wa Nasir magiya.
"Dan Allah Dsp ka bani wayoyina, ina buƙatar cigaba da
amfani da su, ga ayyukana a ciki, amma ka riƙe mini waya da system ka hana
ni"
Ya kalle ta ya ce "Ba dai da wayoyin ki ke janyo wa
kanki matsala ba, kin yi sallama da su, ba zaki sake riƙe waya a gidan nan ba,
and beside gaba ɗaya ni ban yarda da ke ba, akwai abun da ki ke aikatawa wanda
ki ke ɓoyewa".
"Dan Allah ni ka bani wayoyina, ya za ayi ka karɓe mini
kayan aikina, yaya wai meyasa ka ke yi mini haka ne?"
"Ni ki ke ɗagawa murya haka?"
"To ka bani mana"
Abba ne ya shigo falo ya ce "Haba arfa, daga farfaɗowarki
daga ciwon ki ke ta ɗaga murya har haka, sai numfashin ya sake samun
matsala"
"Abba kayan aikina ya ɗauke mini, ka ce ya bani wayata
da system ɗina"
Mama a ƙule ta ce "Dan ubanka ka bata kayanta, ƙannanka
babu wanda ya isa yayi maka abun da take yi maka, da sun motsa sai hantara da
zagi, amma kalli abun da take yi maka"
Abba ya ce "Tsaya, Nasir meyasa zaka kaeɓe mata kaya ka
hanata?"
"Abba nayi seizing wayoyinta ne for a while, da su take
amfani take janyo mana magana, haryanzu ba a tabattar da musababbin tashin
wutar nan ba, amma zai iya yiwuwa saboda abubuwan da take yi ake neman sabauta
rayuwarta".
Abba ya ce "Haka ne, kana da gaskiya, amma ka yi haƙuri
ka bata, ke kuma ki kiyaye da abubuwan da zaki din ga aikatawa da wayar nan,
idan ba haka da kaina zan ƙwace su aikin ma ki daina yin sa. Bi shi ya baki
kayanki"
Nasir ya numfasa, yayi gaba ta bi bayansa, ya ɗaukko ya miƙa
mata yana kallon idonta cike da tuhuma.
"Wuƙa garin tone-tone take tono wuƙar yanka kanta,
yaya, ina martabaka da martaba zumuncin da yake tsakanina da kai. Bana son
harkar aiki ta zama tangarɗa ga wannan alaƙa da na lissafa maka, bayani ne nake
yi maka da manyan baƙaƙe a kan farar takarda, sai dai ba zaka gane nufina a
yanzu ba, ko dai ka bari a haka, ko kuma lokaci ya zo da fassarar da ba ita
kake buƙata ba, ina fatan idan lokacin ya zo, zaka tuna wannan bayanin nawa,
kuma ba zaka ga abun a bazata ba".
Ayshercool
08081012143
Ta share hawayenta, ta ɗaga kanta ta ga ita yake kallo ta ce
"Ka ce mini ka yi wa Indabo aike, me ka aika masa?"
"Hotona ne"
"Hotonka kuma?"
"Eh, hotona ne da ni da wani yaronsa da yake zaton ya
saka an kashe masa shi"
Ta zaro ido ta ce "Wai shi mutane nawa ya kashe kenan a
rayuwarsa?"
Ya rausayar da kai ya ce "Mutane sun ɗauki duniya fiye
da yadda ki ke tunani. A baya bayan matsalar da nake fuskanta a gidanmu, fatan
da nake yi kullum, Allah ya bani abun yi, ko iya abinci in din ga samu ina ci,
sai da na haɗu da uban gidana dodo, ya haska mini duniya da in da mutane suka
saka gaba. Da na so na yi kuɗi da yanzu ni hamshaƙin attajiri ne.
A lokacin da jauhar take ciyar da ni, da fari babu abun da
yayi mini zafi, gani nake kawai auren dole aka yi mini, sam ba ta gabana, sai
dai abun mamakina da ita, duk abun da zan yi mata bata jin haushi, naga yadda
take sana'a tuƙuru iya yin ta, dan kar mu zauna da yunwa, daga baya nayi
noticing idan abinci ba zai isa ba, sai ta bani ita tayi kame-kame ba ta ci ba,
a lokacin ba wai dan tana so na bane take yi mini haka, ta rungumi ƙaddara ne,
kuma tana tausayina.
Daga baya sai na fara jin kunyarta, lokacin da ta roƙi na
sayo mata omo, naga responsibility ɗina, amma na zuba mata ido take yi, kuma
bata taɓa nuna mini ta gaji ba. Sai dai a lokacin ba ni da wata sana'a sai
sayar da wiwi da ƙwayoyi, yadda take yi mini addu'a Allah ya wadata ni da
halal, ya nesanta ni da haram, ya sanya na ji ba zan iya ciyar da ita da kuɗin
wiwi ba.
Sai a lokacin naga ashe, bayan mutuwar Sadik kukan daɗi
nayi, da na ce na rasa sana'a, dan a lokacin na din ga faɗi tashi, saboda kar
na ciyar da ita da kuɗin ƙwaya.
Da in ciyar da ita da wannan kuɗin, gara na dawo na maze na
ce bani da kuɗi, na san ba ɗaga mini hankali za ta yi ba.
Gashi lokacin tana ta ƙoƙarin rabani da hulɗa da Indabo,
wataran idan na ga wahalar tayi mata yawa, haka nan nake zuwa na tsitsiye
Indabo ya bani kuɗi.
Zuciyata ta sha raya mini, na faɗa mummunar hanya, na samu
kuɗi saboda jauhar ta huta, bana nuna mata hakan a zahiri, amma zuciyata kullum
a takure babu daɗi. Duk da tsamin alaƙar da ke tsakanina da mahaifina, sai da
na din ga jin tamkar na je na ce ya bani aron kuɗi nayi jari, amma na kasa,
mussman tuna halin matarsa.
A lokacin da tausayinta ya fara zama tsananin so a cikin
raina, da tana uzzura mini ko yi mini tashin hankali, da babu abun da zai
hanani kauce hanya, dan yahoo zan fara, kuma kuɗi zan samu sosai da sosai, haka
nan na san in da zan yi dillancin miyagun ƙwayoyi a tsakanin manyan mutane, har
da ƙasashen ƙetare na samu kuɗi, amma ban taɓa burin tara kuɗi da mummunar
hanya ba.
Ina ga lokacin da tayi ɓari ne, bani da wasu kuɗi sai na
wiwi, shi ne aka yi mata magani da su, amma banda haka, ban taɓa ciyar da ita
da kuɗin ƙwaya ba".
"Viper, labarinku abun tausayi, kuma gwanin daɗi, Allah
ya bani ikon zama kamar jauhar, ina sonta sosai"
"Sai dai ki kamanta, ba zaki iya ba, ke mafaɗaciya ce,
matata kuwa kan tayi faɗa sau ɗaya ana daɗewa, shiyasa nake kiyaye abun da zai ɓata
mata rai ya sa tayi fushi, har ta yi faɗa. Na gode sosai da saka ni kuka da ki
ka yi"
"Saka ka kuka kuma?"
"Eh, tun da na rasa jauhar, ban zubar da hawaye
ba"
"Ai kai jarumi ne, bari na tashi na tafi gida, ka yi
mini addu'a, gobe in Allah ya kaimu zamu zauna a kotu"
Ya jinjina kai ya ce "Allah ya bada sa'a, bani
maganina"
"Dan Allah ka daina shan magungunan nan, lafiyarka
fa"
Ya ce "Duba na na menene?"
Ta ciro maganin ta duba, cikin magungunan sa ne na Asibiti,
ta ajiye masa ta ce "Allah ya baka lafiya mai amfani, ya bamu nasara a
kotu, in sha Allah case ɗin ka ne next, ka yi mana addu'a" ya jinjina mata
kai.
Ta tashi ta ɗauki jakarta tana ɗaga masa hannu.
***
Daren yau Nabila tayi ta addu'a, suka yi waya da Barrister
Habib, ya ce su haɗu a kotu.
Ya ƙara mata ƙarfin gwiwa, kafin shiga shari'a, suna tsaye a
harabar kotu, tana dudduba abun da zata tsaya a gaban shari'a da shi.
Nabila ta tsaya a gaban kotu, ta ce my lord, kamar yadda na
gabatar da hujjojina a wancan zaman da aka yi, akwai voice na muryar
mahaifiyar ramma tana kokawa akan a nema mata hakkin 'yar ta.
Haryanzu ina da ja, a kan zargin da ake yi wa wanda nake
karewa, a hirar da aka yi da mahaifiyar ramma, a gidan rediyo, wanda suka yi
iƙirarin ya yi wa ramma fyaɗe, ya sha banban da wanda aka gabatarwa kotu.
Haka zalika, voice message ɗin da yake yawo, na mahaifiyar
ramma, ta koka a kan wanda ya yi wa ƴar ta fyaɗe, ya dawo ya ɗauketa ta ƙarfin
tsiya daga gabanta.
Lauyan gwamanti yayi suka, ya nemi da a gabatar da
mahaifiyar ramma, ba wai kame-kame da abun da babu wanda ya san tushen sa ba.
Nabila nan take ita ma ta buƙaci, a gabatar da ramma, tayi
mata tambayoyi.
Lawyan gwamnati ya ce Ramma na ƙarƙashin kulawar, likitoci
haryanzu, dan haka ba za a gabatar da ita a gaban kotu ba.
Nabila ta sake cewa Wane irin illa aka yi mata, da har zuwa
wannan lokacin za ace ba ta warke ba, a shekarun baya shekara sha uku sha huɗu
ake yi wa mata aure, ba a samun matsala, suna zaune lafiya, a report ɗin da aka
bayar na case ɗin ramma, abun bai zama complicated da za ace tsawon wannan
lokaci tana Asibiti ba.
Lauyan gwamanti ya soki maganar Nabila, tare da neman a
bashi dama ya gabatar da shaidunsa na gaba.
Wata mata ce ta fito, aka tambayi baba mai gadi, ko ya
santa? Ya ce Eh, ita ma mai aiki ce a gidan.
Aka tambayi me ta sani, a game da abun da ake tuhumar mai
gadi da shi, babu kunya babu tsoron Allah, ta bayar da shaidar zir, tare da
tabattar da mai gadi ne yayi laifin, sai bayan da yayi aika-aikar, ta dawo daga
sayen kayan miya, ta tarar da ramma, kuma daga shi sai ramma ta bari a gidan.
Baba mai gadi ya sunkuyar da kai cikin matsanancin ɓacin rai
da mamaki.
Nabila ta ce ya za ayi ace gida kamar wannan babu cctv
camera, akwai buƙatar idan da cctv camera a duba abun da ya faru.
Daga nan Nabila ta nemi a bata damar ta gabatar da nata
shaidar ma, aka bata dama, ta buƙaci wata mata ta fito.
Nabila ta buƙaci matar ta gabatar da kanta, ta gabatar da
kanta a matsayin maƙwabciyar su ramma a can garinsu.
"Me ki ka sani game da abun da ya faru da ramma?"
"Eh to, bayan an dawo da ramma gida, ta cigaba da
jinya, dan sallamo su aka yi daga Asibitin birni, saboda rashin isashshen kuɗi.
Babar ramma ta gaya mini wata mata ta zo ta ce zata taimaka musu, amma sai sun
yarda sun janye shari'ar.
Da suka ƙi, ta ce zasu gani, bayan wasu 'yan kwanaki, wani
mutum ya zo da shi da wasu, ya gaya mata shi ne ya yi wa ramma fyaɗe, kuma ta
ƙarfin tsiya, ya kama hannunta ya tafi da ita"
Nabila ta ce "Ko ta gaya miki sunan wanda ya keta wa
yar ta haddi?"
"A'a, ba su san sunansa ba, ramma ba ta daɗe da fara
aiki a gidan ba, amma ta tabbatar da ƙanin matar gidan ne. Bayan ya sace mata
'ya, ta je birni gidajen radiyo ba a saurareta ba, haka zalika wurin jami'an
tsaro, kawai lokaci ɗaya muka nemeta muka rasa".
"My lord, shaida ta tabbatar da cewa wanda ya yi wa
ramma fyaɗe, ya dawo ya saceta, wanda nake karewa da ake zargi yake tsare,
tayaya zai je ya sace yarinyar. Kuma har zuwa wannan lokacin, ba mu ga ramma a
zaman kotu ba, shin ina ramma take?"
Lauyan gwamanti ya ce bai kamata a karɓi shaidar maƙwabciyar
su ramma ba, tun da ba a kanta abun ya faru ba, dan haka ayi fatali da
shaidarta.
Duk yadda Nabila ta so bayyanar da nagartar hujjojinta, amma
kotu ta din ga soke su.
Nabila tana ji tana gani, aka yankewa dattijon shekara goma
sha huɗu a gidan yari, wata irin bahaguwar shari'a, mara fasali balle ɗigon
adalci, yanke hukunci cikin gaggawa ba tare da kammala tabattar da ingancin
shaidun kowane ɓangare ba, sai dai an basu damar ɗaukaka ƙara.
Yanayin yadda ta fito a gigice kawai zai tabattar wa da
mutum ba a hayyacinta take ba, sumayya da suka zo ɗaukan report ce ta nufeta da
sauri, watsi ta yi da file ɗin hannunta, ta faɗa jikin sumayya tana kuka.
Barrister Habib ya ƙaraso, ya ce "Haba Nabila, wannan
ai sai ki saka ayi mana dariya, akwai appeal a gaba, dan Allah ki nutsu.
Cikin kuka ta ce "Sumayya mu tafi gida, ba zan iya sake
haɗa ido da mutumin nan ba, i try my best, ai kun ga yanayin shari'ar da aka
yi, dama haka aka koyar da mu, an bi Principles na law a wannan shari'ar?"
Sumayya ta din ga rarrashinta, suka sakata a mota, barrister
Habib ya ce "Bari mu kaita gida, Bashir kai ka tafi da motata"
Suna tafe a mota tana cigaba da kuka, Barrister Kabir ya
kira Habib, ya ce "Ya ake ciki ne?"
"Gamu zamu tafi, ba ta yi wining ba, sai kuka take
yi"
Kabir ya ce "Ai dama na gaya mata, waye ya gaya mata
jayayya da mutanen nan abu ne mai sauƙi?"
"Dan Allah kar ka saka ta sare gaba ɗaya, za mu yi
appeal, kuma saboda ita nima zan yi abun nan kyauta fisabilillahi i really
appreciate what she did" ya ajiye wayar yana cigaba da yi wa Nabila
nasiha.
Bunkure ta ƙyaƙyace bayan kammala wayar da ta yi, ta kalli
badi'a.
Badi'a ta ce "An kammala komai kenan?"
"Eh, an ƙarƙare shari'ar a yau, uba ya yi abun da ya
dace, wallahi da bai yi wani yinƙuri ba, sakar musu zan yi su ƙarata daga shi
har ɗan nasa, su ta shafa, amma a wannan karon dole na ɗauki mataki a kan
yarinyar nan, da gaske so take yi sai ta tona mini asiri, dole zan tattauna da
indabo, ya ɗauki mataki a kan ta"
"Amma kina ganin hakan zai yiwu, tun da abu ya shiga
social media, kuma ta fara samun masu mara mata baya?"
"Iyayen gidanta ma, ba su kai ko ina ba, amma an ce
mini an hangeta da barrister Habib, kuma ina kyautata zaton da saka hannunsa a
wani abun da take yi, amma duk na san matakin da zan ɗauka akan dukkansu"
ta ƙarasa maganar tana haɗiye ƙwayoyin da suke hannun ta, ta bi su da ruwa.
Nabila bayan sun kaita gida kuwa, ba ƙaramin kuka tayi ba,
gaba ɗaya sai ta ji ta karaya, komai ya fita daga kanta.
A ɗakin Nasir, ya sameta bayan ya dawo daga aiki, ko da ya
tarar da Nabila ta sha uban kuka, tuntsirwa yayi da dariya, ya ce "Haba
barrister, ina ƙwarin gwiwar ta ki? Har kin karaya haka?. Abun da na yi ta nuna
miki kenan, nake gargaɗinki a kan ki fita daga sabgar nan, ba ke kaɗaice mai
gaskiya a ƙasar nan ba, amma tun da ki ka ga kowa ya ja baki yayi shiru, to
abun ya gagari kundila, amma ki ka ƙi ganewa ki ka cigaba da dagewa, ki gode
Allah da ba su yi wani abu da za su taɓa lafiyarki ba ma" ya gama surutansa
ya fita, ba ta ko kalleshi ba.
Yana fita ta mayar da ƙofa ta rufe, tana ƙoƙarin kiran
Viper, wayar Alhaji wada ta shigo. Ajiye wayar tayi, ta ɗauki ƙaramar ta ta, ta
kira Viper.
Bugu ɗaya ya ɗaga, kawai ta saka masa kuka.
"Meye ne?"
"Kana kallon wulaƙancin da aka yi mini a shari'ar nan,
kaga wata irin shari'a da aka yi mai cike da wulaƙanci da zalunci, wallahi gaba
ɗaya na karaya, na gaji da aikin nan, ina ji ina gani, mutumin da bai ji ba bai
gani ba, zai tafi prison, zuciyata kamar ta fashe na gaji".
"To ni kuma wa zai tsaya wa tawa shari'ar?"
Nabila ta ce "I give up, na karaya" tayi maganar
tana kuka.
"Ke kin isa? Ai tun da muka fara, sai mun kai ƙarshe,
tied your belt against next trial".
"Ni ba zan iya ba, ina ga ma ciwon zuciya ya kama ni,
duk na tsani komai, haka zamu cigaba da tafiya, mai kuɗi ne kawai ɗan gata?
Ƙiri-ƙiri fa aka murɗe komai".
"Sai ki gyara, kar ki gaji, sai kin gama da ni tukuna,
anyway an hukunta wanda ya aikata laifin, saura kuma ki matsa ki gano in da
ramma take da mahaifiyarta"
"Wai kai wane irin mutum ne? Na gaya maka dattijon nan
ba shi yayi laifin nan ba, kuma ni ina zan ganta?"
Ko a jikinsa ya ce "Wannan matsalar ki ce ai, ki ƙarasa
wannan ki zo ki yi nawa"
Katse wayar ta yi, ta ajiye ta cigaba da kuka.
*****
"Lakwari, ka je ka samu P.A ɗin Indabo, ka gaya masa ni
na aikoka, ya uzzura mini da kiran waya, a kan lallai sai na je, wai mai zamani
ya yi masa aike, dan haka dolena na nemo masa shi, haryanzu ban sanar masa da
halin da nake ciki ba, amma ka je, idan ka je wurin P.A ɗin, ka kira ni zam yi
masa bayani".
"Shikenan, amma kana ganin ba za a samu matsala
ba?"
"Ba za a samu ba, daga nan ma sai ka samo mana kuɗin
zuwa asibitin nan, dan na tattara kuɗin hannuna gaba ɗaya na aika a kawo mana
ganye, shi ma kuma na ji shiru, idan ka dawo daga wurinsa ka biya ka duba
mana".
"Shikenan an gama"
***
Nabila kuwa ba a iya Nasir ba, hatta yan gidan suka sakata a
gaba da tsokana, suna yi mata dariya, bisa yadda ta shiga matsananciyar damuwar
rashin nasarar da ta yi, a kotu. Ba ta taɓa yin shari'ar da ta shiga ranta ba
kamar wannan, gashi dai kyauta take shari'ar babu ko sisi, amma duk ta bi ta
damu, hatta hawa social media ya gagareta, saboda yadda ake yi mata dariya, ƴan
koren Bunkure ke cigaba da nuna cewar Nabila hassada take yi wa bunkure, kuma
kwangila ta karɓo a hannun wasu.
Sosai ta fusata, ta hau social media tayi posting, ja da
baya ga zaki ba tsoro bane ba, shirin faɗa ne. Kuma ko bayan shekara dubu,
sunan gaskiya baya taɓa canzawa, a saurari fitowa ta gaba.
Ɓangaren Nasir ma, yana fuskantar matsin lamba sosai daga
wurin Indabo, da kuma manyansa a wurin aiki, a kan kama Viper.
Gefe guda ga fargabar abin da Nabila za ta janyo musu, tun
da ita ba ta so a zauna lafiya, yana matuƙar fargabar Indabo ya yi mata wani
abun.
Gaba ɗaya ta daina walwala, ko fitowa ta daina yi, sai idan
fita zata yi, sai dai a kai mata abinci ɗaki a ajiye.
Ganin ta takura kanta da yawa, Nasir ya sameta yana
rarrashinta, da bata baki a kan ta jure ta karɓi ƙaddara.
"Ba wata ƙaddara da zan karɓa" tayi maganar tana
hura hanci.
"Ke saɓo zaki yi kenan?"
Nabila ta ce "DSP, abun da Allah ya hukunta shi ne
ƙaddara, ba abun da mutum ya ga dama yayi da son rai ko son zuciya ba, ko da me
matar nan take yawo, sai na tona mata asiri wallahi, gara ma ka ƙyale ni da
wannan nasihar"
"Na ƙyale ki, amma idan kin ƙi ji, ai ba kya ƙi gani
ba, tun gashi yanzu kin fara ganin ma, amma ba wannan ba, wai haryanzu babu
wani news da ki ka samo a kan Viper ne? Na ga duk kin yi sanyi, kin daina
taimaka mini"
Ta kalleshi ta ce "Ba dole na yi sanyi ba, ai dama ka
ce na daina saka kaina a abun da babu ruwana, dan haka wannan ma babu ruwana da
shi"
Yayi murmushi ya ce "Haryanzu a fusace ki ke arfa, to
ba ni ne dai Naja'atu Bunkure nan ba, amma yakamata idan da wani hints a
taimaka mini"
Ta kalleshi ta ce "Babu wani hints, ban san komai
ba"
"To shikenan, idan kin huce sai mu cigaba da
maganar" ta harare bayansa har ya fice.
Kasa samun nutsuwa ta yi, ta sake ɗaukar wayarta ta yi
posting, "Idan har mahaifiyar ramma ba ɓata tayi ba, kuma da gaske Bunkure
foundation na kula da ramma ne, to tana ina, al'umma yakamata su samu update a
kan halin da take ciki, kuma shin suna da masaniya a kan ɓatan mahaifiyarta?
Idan eh to ina tafi? Tana tare da 'yarta ne ko kuwa?" Tayi posting ta nemi
wuri ta zauna, lissafi da tunani daban-daban suka din ga kaiwa suna komowa a
cikin ƙwaƙwalwar Nabila.
***
"Indabo, yakamata fa ka sake matsa Abdul, ya gaya maka
in da yarinyar nan take, hankali ya fara dawowa kanmu, yarinyar nan fa ta
matsa, kuma ban ga alamar, zaka ɗauki wani muhimmin mataki a kan ta ba"
"Ya ce mini ya kasheta"
Bunkure ta ce "Ya kashe ta ta yaya? A binciken da na
yi, an tabattar mini uwar yarinyar ba ta garin nan, tafiya ta yi babu shiri,
kuma Abdul ya je gidan fiye da sau ɗaya, bayan ya ɗauke yarinyar, me ya je yi,
ni fa ba na son a din ga gaba ana baya, kar asirinmu ya tonu fa"
Indabo ya numfasa ya ce "Abubuwa sun fara caza mini kai
Naja, ga takarar Abdul da nake ta fafutuka, ga auren nan da ake shirin yi na
shi. Ga ɓangaren ki taki matsalar, duk is a minus case, bababr damuwata yanzu
Viper, aiken da ya yi mini ya tayar mini da hankali, idan ba a kama shi an
kashe ba, hankalina ba zai taɓa kwanciya ba, ga ƴan adawa sun sako mu a gaba,
ga tunanin jafar da yake tsare na rasa wane tunanin ma yakamata na yi"
"Ai wanda ya fi muhimmanci shi zaka yi, wallahi idan
aka cigaba da ƙyale yarinyar nan, muna raina abun da take yi zata bamu mamaki
fa"
Ya jinjina kai ya ce "Na ga alama, kuma ba zan taɓa
bari hakan ta faru ba".
P.A ne ya kaste su, ta hanyar yin sallama, suka amsa duk
suka ɗago suna kallonsa.
Ya kalli indabo ya ce "Akwai matsala fa"
"Again?"
"Ƙwarai kuwa, madaki ne ya yi aike, wai ya samu rauni a
ƙafarsa, yanzu haka ko iya tafiya ba ya yi, ɗazu ya turo yaronsa har ya buƙaci
a bashi kuɗi ya je asibiti, amma wai duk wani abu da yakamata, yana da yaran da
za su iya yi maka"
Indabo ya buga tsaki ya ce "Maganar banza kenan, zuwa
yaushe zan cigaba da rarraba sirrina, wannan yayi mini aiki wancan yayi mini,
kalli yadda haryanzu jarabar ɗan tahaliki ɗaya take ta ɗawainiya da rayuwata.
Na gaji ya je Allah ya kyauta, na nemi wata mafutar"
"Amma kana ganin watsi da shi, ba zai zame mana wata ɓarakar
ba ko barazanar ba?"
"Babu abun da zai zame mana sai wahala, tun da ba shi
da wani amfani yanzu, Viper da na bari ya ci karensa babu babbaka, saboda yaron
dodo ne, ina matuƙar jin tsoron abun da ya sani a kaina, kuma kamar yadda na yi
tsammani, ya san abubuwan da idan yayi magana kashinmu ya bushe, dole fa a nemo
Viper akwai matsala wallahi" yayi maganar yana zazzaro ido cikin tashin
hankali.
Sai da aka kusa sati da yanke hukunci, sannan Nabila ta tafi
wurin iyalan dattijon nan, tare da sake rarrashin su, a kan su yi haƙuri su
ƙara mata lokaci, zata ƙara shiryawa sosai a appeal ɗin da za su yi, tana saka
ran za su yi nasara in sha Allah.
Suka yi ta yi mata godiya, sai da zata tafi, ƙaninsa ya keɓe
da ita, ya ƙara yi mata godiya, sannan ya ce "Dan Allah ki ƙara bincikar ɗan
uwana, kamar fa ya san wanda ya yi laifin, barazana aka yi masa Shiyasa ya kasa
gaya miki komai"
"Barazana kuma, wace irin barazana?"
Ya ce "Eh, akwai ziyara da na kai masa, ya gaya mini
amma ya nemi kar na gaya wa kowa, ya san sunan wanda yayi laifin, da alaƙarsa
da matar gidan, amma bai san ɗan waye ba"
Ta ce "Ya salam, to amma meyasa ni bai gaya mini ba,
babu yadda ban yi da shi ba a kan idan ya san wani abu, ya sanar mini, amma ya
ce mini babu abun da ya sani, sunansa ma bai sani ba, kawai dai ya san ɗan
yayan matar gidan ne".
Ta ce "Subhanallah, shikenan zan san abun yi, a cigaba
da yi mana addu'a"
Ya ce "In sha Allah, kullum cikin yi muku ake, Allah ya
jiƙan magabata mun gode sosai da sosai".
Tana kan hanya saƙon Viper ya shiga wayarta, a kan yana son
su haɗu.
Ji tayi kamar ta maze taƙi zuwa, amma ina, ba ta ji alamar
zuciyarta zata bari ta aikata hakan ba.
Garden ɗin da suke haɗuwa, a can ta same shi, ta tsaya tana
kallonsa ya rage sumar kansa, yayi kyau sosai.
Wata tab ta gani a hannunsa, cikin basarwa ta ce "Ina
wuni?"
"Wayarki zaki bani"
Ta kalleshi ta ce "Wai baka san meya same ni bane? Baka
jajanta mini rashin nasara da nayi ba, abu duk ya dame ni"
"Yanzu ki ka fara, idan har rashin nasara ba zai saka
ki ƙara jajircewa ba, sai dai ki yi kuka"
Nabila ta ce "To idan ban yi kuka ba ya zan yi?"
Ya kalleta ya ce "Babu"
"Waye ya sai maka waya?" Yayi mata shiru.
Ta sake cewa "Haryanzu fa ina da tarin tambayoyin da
baka amsa mini ba"
"Wanne daga ciki?"
"Meyasa Indabo ya ce zai yi maka tarko da ni ya kama
ka? Ni meye haɗina da kai?"
Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Wataƙila ya san kina
zuwa wurina"
"To amma ya aka yi haryanzu bai kama ka ɗin ba? Kuma ni
haryanzu kana ɓoye mini wasu abubuwa"
Ya saka ƙaramar wayarsa a kunnensa, ya ce "Ɗan mama ya
ake ciki?"
"Oga Viper, mun ƙwamuso Lakwari fa, yanzu duk in da
madaki yake, dole ya bayyana, tun da babu mai taimaka masa ko ya kula da
shi"
Viper ya ce "Good job, zan gaya muku what next"
Cikin zaro ido Nabila ta ce "Viper kidnapping?"
"Eh ina son na sauƙaƙa miki aiki ne, shaidu na fara
tattara miki, kafin a fara shari'ata, Madaki yayi jigatar da ba zai iya musa
laifin da ya aikata ba"
"Amma ka gaya mini me ka ke yi da wayoyi? Ka daina yi
mini ɓoye-ɓoye. Sai kin zo kan shari'ata zaki ji koma me ki ke buƙatar ji"
Kamar shashasha haka take kallonsa, gaba ɗaya ta ma rasa me
za ta ce masa.
Ya miƙa mata wayarta ya ce "Angry bird"
"Am confused"
"Sorry"
Kamar ta sake fashewa da kuka ta ce "Zuciyata kamar a
kurku, haka nake jin ta, mai laifi daban yana can yana rayuwarsa, mai karɓar
hukunci daban, wane irin abu ne wannan?"
Viper ya gyaɗa kai ya ce "Kamar dai ni a kwanakin baya,
idan aka kama mai laifi, sai ayi musanye a saki wancan saboda ɗan gata ne, ni
kuma a tsare ni a matsayin mai laifin"
Ta ce "Kuma dai? Wani yayi laifi kai kuma a
tsareka?"
"Mmm, a saka matata tayi ta yawo tana wahala ba, wata
Shari'a sai a lahira, duk rintsi kar ki yadda ayi amfani da ke ki ci amana, ba
kowa ne yake da zuciyar yafiya ba"
Jiki a sanyaye ta jinjina kai, ya ce "You can
leave".
Kusan a tsukin lokacin, Nabila ta zama topic of discussion a
social media, sai dai ba ta karaya ba, wurin cigaba da posting a kan bunkure
foundation.
***
"Abdul tun muna shaida juna, ka gaya mini ina yarinyar
nan take? Ka kashetan ko kuwa? Sannan uban me ya sake mayar da kai gidansu,
bayan ka je ka ɗauki yarinyar, kuma saboda hauka maimakon ka saka ayi? Kawai
sai ka wanke ƙafa ka tafi da kanka ka je ka ɗauki yarinyar, kamar baka san
matsayinka ba? Idan ka san uwar yarinyar nan ma, tana tare da kai, ka gaya
mini, na san matakin da zan ɗauka a kai"
Ya girgiza kai ya ce "Ni ban ɗauki uwar yarinyar ba,
ban san in da take ba"
"Da ka kashe yarinyar yaya ka yi da gawarta?"
Abdul ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Ruwa na jefa
ta"
Indabo ya ja guntun tsaki ya tashi, maganganun da bokansa ya
gaya masa ne suke ta yi masa kai komo a zuciyarsa, wai dutsen da ya gaya masa
zai ci karo da shi, lokaci yayi da shi bai san ya za ayi ba, dole ayi ɗayan
biyu, ko dutsen yayi nasara a kansa, ko kuma su yi mutuwar kasko, amma babu
yadda za ayi, ya iya maganin dutsen nan da kansa.
Nabila fa ta sake jajircewa, da cigaba da ƙoƙarin gano bakin
zaren matsalolin da take tunkara.
Bayan shari'ar ramma, akwai shari'oi da dama a gabanta, amma
wannan c ta fi ci mata tuwo a ƙwarya, sai kuma ta Viper da zata fuskanta.
Kasancewar da sassafe ta je wurin aikin, duk babu mutane, ta
shiga office ɗin ta, ta ajiye jakarta, ta yi addu'a ta zauna, ta buɗe computer
ta fara aiki.
Ƙaurin wayar wutar lantarki ta fara ji, ta ɗaga kanta, ba ta
ga komai ba, ta sunkuyar ta cigaba da aikinta.
Wata irin ƙara wearing ɗin office ɗin ta yayi, ya fara ci da
wuta, a razane ta tashi cikin tashin hankali, ta nufi ƙofa zata buɗe, ta ji an
kulleta ta waje, ta jijjiga iya ƙarfin ta, amma a ƙofar a kulle gam, ga wuyar
wuta sai cigaba da ƙara take yi wuta na kamawa tana tarwatsi.
Da ƙyar ta iya ɗaukko jakarta, ta ciro wayarta, tuni ta fara
gani dishi-dishi, saboda hayaƙi, tari ya turnuƙeta.
Hannunta na rawa, lambar Viper kawai ta iya gani, ta danna.
Ya ɗaga wayar sautin tarinta ya fara ji, tana ta yi haɗe da
haki, da ƙyar ya iya fahimtar ta ce "Wuta" daga nan ya ji ɗif
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin rashin fahimta, yake bin ta da ido, sai dai tamkar
soko, har tayi maganar ta gama, bai iya tofa mata uffan ba, har tayi ta gama ta
karɓi wayoyinta da system tayi tafiyarta ɗaki.
Ɗakin ta rufe, ta shiga duba call logs ɗin ta, amma kaf ba
ta ga kiran Viper ba, wani irin takaci ne ya turnuƙe ta, wato duk siraɗin nan
da ta tsallake da kyar, bai kirata ba, balle ya ji a wane hali take ciki.
'To idan kuma bai san abun da ya faru ba fa?' ta tambayi
kanta. Ta basar ta ce bari ta jira zuwa gobe, taga ko zai kira wayar.
Ƙasan zuciyarta kuma ta din ga hamdala da Allah ya sa bai
kira ɗin ba, dan da ya kira Nasir zai ɗaga ne, kuma ba abun da yayi masa zafi,
zai iya gaya masa waye, idan ya tambayi waye.
***
"Naja wai ko ke ki ka saka aka yi wa yarinyar nan wani
abu ne?"
"Wace yarinyar?"
"Barrister nan? Karofi ya kira ni yana yi mini kashedi,
ina tsoron Allah ina tsoron shu'umancin mutumin nan"
Naja ta ce "Eh, ni na saka aka yi mata haka, dan so
nayi ma ta mutu, na ga kai ka ƙi mayar da hankali ka yi abun da yakamata, ba
zai yiwu ta tona mini asiri a banza ba, mutuncina ya zube a idon duniya ba. Ba
a taɓa samun wanda ya yi yinƙurin kawo mini tangarɗa ba, ka ƙyale shi ka ke jan
ƙafa a kansa ba, sai a kan wannan yarinyar"
A fusace Indabo ya ce "wai meyasa ki ke haka ne Naja?
Duk iya ƙoƙarin da nake yi a kan lamarin nan? Na gaya miki zata iya zama tarkon
da zan kama Viper, kuma ina amfani da ita wurin yi wa yayanta barazana yake yi
wa umarnina biyyaya, lokaci ɗaya karofi ya bijiro, yake yi mini gargaɗi a
kanta, wai sonta yake yi, wataƙila ma yi yake yi dan kawai ya muzanta ni. Amma
gaba gaɗi babu shawara, kin je kin aikata abu, kin saka yana ta kiran wayata
yana nema ya tozarta ni"
"Nifa ban yi danasanin abun da nayi ba, kuma zan cigaba
da bibiyarta sai na ga bayanta, ban damu da abun da zai biyo baya ba muddin zan
tsira, kar ka manta kai ka koyar da ni hakan" ta kaste wayar tana jan
guntun tsaki.
***
A gurguje Abdul ya yi breakfast a wurin ramma, yayi mata
sallama ya fice.
Bayan fitarsa ta daɗe tana kuka, kamar zuciyarta ta fashe
haka take ji, saboda damuwa da tashin hankali, tun tana lissafin adadin
kwanakinta a wurin Abdul, har ta karaya lissafi ya ƙwace mata, tana matuƙar son
sanin halin da mahafiyarta ke ciki. Ta sha attempting ta saka wuƙa ta kashe
Abdul, amma sai ta kasa, ita kanta ta sha yinƙurin kashe kanta, amma tuna
makomarta sai ya sanya ta fasa.
Gashi yanzu sam ba ta iya bujirewa buƙatar sa, rayuwa suke
yi tamkar ma'aurata, ta yi kuka tayi istigfari amma da ya zo ya kalallameta da
zance, sai ta bayar da kai bori ya hau, wasu lokutan idan ta kalli hidimar da
take yi masa, ta gyaran gida, kula da abincin sa, yin wani abu da zai saka shi
farinciki sai ta yi sai ta ji haushin kanta ya isheta.
Abdul kuwa Asibitin su doctor AK ya wuce, ofishin sa ya je
suka gaisa ya ce "Kai ne zaka yi morning kenan?"
Ak ya ce "Eh ni ne your excellency kai fa zuwa yanzu ya
ci ace ka ajiye Lab coat, tun da ana ta ƙishin-ƙishin kai ne zaka zama lamba
biyun garin nan, zaka koma field ɗin dadynka"
Abdul ya ce "Nifa Ak ko lamba ɗayan ƙasar nan na
zama, ba zan iya daina aikin likita ba, ina gudanar da office ina
consultation" suka tafa tare da kwashewa da dariya tare.
Ak ya ce "Sannu doctor excellency, ina ƙanwar ka da
kuka zo tare kuwa? Baka wani tsaya mun gaisa da ita ba, ko dan kar na ƙyasa ka
bani ita, ai ban taɓa sanin kana da ƙanwa ba, na zata kai ne ƙarami"
Abdul ya tsuke fuska ya ce "A wane room patient ɗin
take ne?"
"Ai ta uzzura sai da aka sallameta, amma Alhamdilillah
jikinta yayi kyau sosai, sai dai ka yi mana ward round idan da abun da za a
taimaka mana ayi mana" ya jinjina kai ya juya ya fice daga office ɗin.
***
Tun bayan da ɗan mama ya tabattarwa Viper an sallami Nabila
daga asibiti, yake kallon wayarsa yake jiran kiran wayarta, amma shiru ba ta
kira shi ba, har ya fara tunanin ko ƙarya ɗan maman ya yi masa da ya ce ta
warke an sallame ta.
Shigowar Walid ce ta dawo da shi hayyacinsa, ya ɗaga kai ya
kalle shi, Walid ya ciro wuƙarsa ya zareta daga cikin gidanta, ya kalli Viper
ya ce "Lakwari da gaske yake, na iske madaki, ƙafarsa ba ta takuwa, raunin
da ka yi masa ya zama gyambo a ƙafarsa, ga shaida harafin sunanka na zana masa
a gadon bayansa, yadda shi ma ba za a kammala na sa labarin ba, dole sai an
ambaceka"
Viper yayi kamar zai yi murmushi ya ce "Mai laya"
Walid ya ce "Na kiyayi mai zamani, Allah ya kiyaye mini
kai ɗan amanata"
Viper ya ce "Ina kewar wancan kwanakin, kwanakin da aka
yi rashin ji da gaske, yanzu girma ya fara zuwa duk an daina wasu
abubuwan"
Walid ya yi murmushi ya ce "Rashin jin ai duk ba na daɗi
bane ɗan uwa, duk da kai ƴar madara ta fara saita mana kai, Allah ya karɓi
kayarsa, amma duk da haka ba zan gushe ba ina jinjinawa Nabila, dan ita tayi
abun da muka kasa, albarkacinta mun sake ganin walwala a tare da kai, duk da ba
ta kai ta wancan lokacin ba"
"That angry bird, masifaffiya" ya furta yana
kallon liti ya ji me zai ce.
Aikuwa kamar mai jiran ƙiris hya e "Ba wata tsiya da ta
tsinana masa, sai shegen naci da taurin kan tsiya, mara kunya da ita sai kayan
ƙaton kai kamar injin markaɗe da ƙwala-ƙwalan idanuwa kamar an soya aya, ai
wallahi 'yar madara duniya ce, ga kunya da girmama mutane, wannan tsagerar
kuwa, tana zazzarewa mutane ido, ni har mamakin mai zamani nake yi
wallahi".
Walid ya ce "Ai ita ce daidai da ku, daga kai har mai
zamanin, mu da muka kasa iya masa, ita ai gata nan yana saurarenta"
"Ba wani nan, ni haryanzu ba gama yarda nayi da ita ba,
yar leƙen asiri ce"
Walid ya ce "To tayi leƙen asirin, ai ba asirinka ta
leƙa ba ko?"
"Ware, ban da naga kuna ta tata, da sai na saka
tsumagiya na jiƙa mata jikinta, sai na yi mata mazinacin dukan da ba zata iya
tashi ba, na rama muguntar da yayanta yayi mini a station"
Viper yana gefe yana jin su, wasu lokutan faɗan Walid da
liti nishaɗi yake saka shi, kamar sako da sako.
Nabila wuni tayi da waya a hannu, amma shiru babu kiran
Viper, shi ma haka ne, wuni yayi yana kallon wayar ta sa yana sauraren kiran
wayarta, amma ba ta kira ba.
***
Nasir ne zaune a ɗakinsa, yayi zurfi sosai a cikin tunani,
yana ta tuna wasu abubuwan da suka faru a 'yan kwanakin nan sosai yake jin yana
zargin Arfa tana aikata wani rashin gaskiya, da take ɓoyewa, mussman da ya ji
ta ambaci viper lokacin da ta farfaɗo, ba zai yiwu a ce magagi ne kawai ba,
kuma a yan kwanakin nan tayi watsi da lamarin cewa zata taimaka masa a kan
nemansa balle ya ce tsananin saka abun a ranta ne ya sanya ta farko da sunansa,
amma haryanzu yana son sanin dalilin da ya sanya Indabo ya ce zai yi tarko da
Nabila ya kama Viper, menene haɗinta da shi?.
Nabila tana zaune a kan gado, tana waya da Alhaji Wada, sai
kashe murya take yi, wai ita haryanzu ba ta warke ba, ya biye mata sai sangarta
take yi, kamar ba babban mutum ba yana lallaɓata, tun da ya ce zai kuma zuwa
gida dubiya ta ce masa ai ta warke ba sai ya zo ba.
Sallamar baba magajiya ce ta sanya tayi masa sallama, ta ɗago
ta kalleta da murmushi.
"Yauwwa yar gari, ai dama zuwa nayi na tashe ki, ki
samu ki karya ki sanya wani abun a cikinki, ashe ma kin tashi "
"Eh hajjaju, ina kwana"
"Lafiya lau, ya ƙarfin jiki kuma?"
Nabila ta ce "Alhamdilillah da sauƙi"
"To Allah ya ƙara kiyayewa, ki cigaba da addu'a Allah
ya ƙara tsarewa, dama mu ma addu'a cikin yin ta muke babu dare babu rana,
Hasbunallahu wa ni'imal wakil, ki yawata faɗarta babu adadi, da yardar Allah ba
dai mutum ba sai dai Allah"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Kin faɗa kin nanata mini,
na daɗe da haddacewa ai"
"Kya ci ƙaniyarki da kin daɗe da haddacewa, zamanin nan
na yanzu waya ce miki ana zama haka? Kana da ido ba na ganin gari ba, Addu'a
kake tuƙuru iya yinka, baka san waye maƙiyin fili da na ɓoye ba"
Sosai Nabila take dariya ta ce "Aikuwa maƙiyina yana
ruwa, dan ni kaina ba wani cikakken saiti ne da ni ba in ji Abba"
"Ke ki yi addu'a kawai yar nan, tashi ki je ki samu
abun da zaki ci" ta saukko daga kan gadon, ta fice falo tana miƙa, wayarta
take kallo lokaci lokaci, duk kiran Viper take jira, amma shiru.
Sauda ta kalleta ta ce "'yar asara an fito"
Nabila ta ce "Wallahi kuwa, Allah ya nufa barka da
safiya, bazawara uwar son banza ga gadonki ga na asara"
"Arfa, me ki ka ce?"
"Sauda kin sani sarai bana shiru idan aka gaya mini
babu daɗi, ni yanzu a kan tsini nake, magana ɗaya mara daɗi ki ka yaɓa mini,
sai na yi miki goma mai zafi, ba girmata ba Allah ya sa haifata ki ka yi"
Sauda za ta yi magana, ta jiyo takun Abba yana saukkowa daga kan bene, dan haka
ta haɗiye maganar ta, tana kallon Nabila.
***
Abbu ne zaune a gefen gadonsa, fuskarsa sanye da farin
glashi, ya zubawa hoton hannunsa ido. Shi da Zahra'u ne, da sadik, shi kuma
hannunsa riƙe da Al'amin, bai fi shekaru biyu ba a lokacin, sai dai fuskar nan
ta sa tamau, babu alamar fara'a.
Murmushi Abbu yayi, tun Al'amin yana yaro baya son wargi, ba
shi da faa'a, ya tuna yanzu a jikin hoton ba kowa sai Al'amin, shi ma ga yadda
ya zama, rabon da ya saka shi a idonsa, tun fitowarsa daga prsion da ya zo masa
nan, kusan shekara guda kenan.
"Wai meyafaru ne kamar kuka fa kake yi?"
Ya ɗaga kai ya kalli rahila ya ce "Kuka kuma?"
Ta leƙa ta kalli hannunsa, ta kwaɓe baki ta ce "Kai ta
wani abu kamar ƙaramin yaro, ka ɗauki hoto ka saka a gaba kana kuka, haba kai
kuwa?" Yayi mata shiru bai ce komai ba.
"Abbu, dan Allah magana nake so mu yi da kai"
"Ina jinki"
"Dan Allah ka yi haƙuri ka yafewa Abba, ya koma kasuwa,
sai raragefe yake yi a gari da shi da Nazifi, ina tsoron kar su faɗa wani
mummunan halin, rashin sana'a ga matashi babbar matsala ce".
Ya ƙare mata kallo ya ce "Rahila, nawa ɗan ma da ya
kangare, sallama shi nayi, ba zai yiwu in cigaba da jan ɓarayi a jikina suna
zalunta ta ba, su yi ta yawo babu sana'ar, ai uban su yana raye, ya nemi abun
yi ya ba su"
"Ni kake kallon idona ka ke cewa yarana ɓarayi?"
"Na faɗa rahila, ba ɓarayin bane ba? Wane irin gata ne
ban yi musu ba, ƙarshe rashin lafiya na kwanta aka rasa wanda zai zauna da ni a
cikin su a asibiti, ƙarshe cewa ki ka yi kar na ga laifin su, ba hakkinsu bane
ba, amma ni na riƙe su na ciyar da su, na kula da su, ni nawa hakkin ne? Yanzu
nake ƙara danasanin biye miki, na wofantar da nawa ɗan, kuma ki tattatara su
gaba ɗaya su bar mini gida, dan ba hakkina bane ba riƙon su"
Cikin takaici ta ce "Wallahi ba zan rabu da 'ya'yana
ba, sai dai na tattara da ni da su mu bar maka gidan"
"Allah ya raka taki gona, ya tsare hanya"
Cikin fargaba ta kalleshi ta ce "Au babu ruwanka kenan
in tafi baka damu ba?" Tashi yayi, ya ja tsaki ya mayar da takardun
gabansa ya bar ɗakin.
***
Nabila ta kasa jurewa, hankalinta ya fara tashi, ko wani
abun ne ya samu Viper, duk da bai fiye kiranta ba, sai da ƙwaƙwƙwaran dalili,
amma shirun yayi yawa. Yau take shirye-shiryen komawa wurin aiki, Barrister
Habib ya tabattar mata da an gyara office ɗin ta, an canza mata wani.
Har ta shirya ta tsaya, ta kira lambar Viper.
Yana kwance idanunsa a lumshe, yana ɗan kaɗa ƙafa, ya ji
ringing ɗin wayarsa.
Ganin lambarta sai da ya yi ajiyar zuciya, amma ya zubawa
wayar ido, sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga kuma yayi shiru.
"Hello Viper"
"Salamu alaikum" ya faɗa a nutse.
"Wa'alaikum Salam, kana lafiya?"
"Ƙalau"
Cikin marairaicewa ta ce "Wai baka san abun ya same ni
bane ba? Kwana nawa baka ga kiran wayata ba baka neme ni ba, wrong connection
na wearing aka yi a office ɗina, wuta ta shi, aka rufe ni ta waje fa"
"Na sani"
"Ka sani?"
Ya ce "Eh"
Cike da takaici ta ce "Kuma ka kasa nemana a waya, da
mutuwa na yi fa"
"Allah ya jiƙanki, zahra ma da mutu haƙuri nayi, balle
ke. Sai ki ƙara taka tsantsan da abubuwan da ki ke yi"
Wani ƙululun takaici, ya tokare mata wuya, sosai ta ji zafin
abun da ya ce mata, kawai ta katse wayar.
Walid ya ce "Viper, kamar baka kyauta ba fa" yayi
masa shiru, hakan ya sa shi ma yayi shirun bai kuma cewa komai ba.
Baƙin ciki da ɓacin rai ya sanya, babu wanda ta yi wa
sallama a gidan ma, tayi tafiyarta.
Tana tafe a hanya ta din ga jin wani abu mai kama da kishi,
da ɓacin rai yana taso mata, har ga Allah ba ta san jauhar ba, amma tana son ta
saboda Allah, amma abun da yayi mata yau, ya sanya ta ji ranta ya sosu.
"Meyake damuna ne? Wai son bawan Allah nan nake yi? Na
shiga uku me yake shirin faruwa da ni ne? Idan ta tabatta son shi nake yi, na
yi wauta, to yaya ma za ayi hakan ya yiwu abu daga wasa?" Har ta ƙarasa
wurin aiki, tunani take a zuciyarta. Tayi shiru tana sauraren zuciyarta dan ta
tabattar da abun da take tunani gaskiya ne ko akasin haka, amma bata kai ga
hakan ba, aka ƙwanƙwasa glashin motarta, masu gadi ne suke yi mata barka da
dawowa, tare da yi mata sannu da jiki".
Ta saukko daga motar, suka gaggaisa, sannan ta shiga ciki, a
cikin ma murnar ganinta suka din ga yi suna yi mata sannu.
Ko mintuna talatin ba ta yi a sabon office ɗin ba, barrister
Habib ya ƙaraso.
"Autar lauyoyi, ƙaramar su babbar su, aminiyar sumy,
ƙaramar sauro ka da ƙatuwar giwa, ba giwar ba hatta toron ma kayarwa ki ke
yi"
Nabila ta yi murmushin yaƙe ta ce "Ni har ka bani kunya
ma"
"To yaya jikin naki?"
"Alhamdilillah yayi sauƙi sosai"
Ya ce "Masha Allah, yanzu ya ake ciki da batun shari'ar
nan? Zamu je prison ɗin ne wurin mutumin?"
"Za a bari mu ganshi kuwa?"
Habib ya ce "Za'a bari mana ba dole ba, ai na je
lokacin kina gadon asibiti, ba na son abun da zai kawo tsaiko a harkar shari'ar
gaba ɗaya"
"Kai amma na gode sosai yaya habib "
"Kar ki damu Nabila, ba ke ba, hatta ni na ji haushin
yadda shari'ar nan ta gudana, kuma cin mutuncin harkar shari'a ne, a wannan
karon zamu yi nasara in sha Allah "
"Allah ya sa yaya Habib" suka fito suka hau motar
barrister Habib suka fita.
Nasir da yake bin Nabila a wata motar, ya ga fitar Barrister
Habib da Nabila, ya sake rufa musu baya, sannu a hankali ba tare da sun san
yana bin su ba, sai dai azabar kishi ya sanya ya ji har wani dishi-dishi yake
gani.
A wannan karon Nabila tayi mamakin yadda aka basu damar
ganin baba maigadi, ba tare da an raina mata hankali kamar yadda aka saba ba.
Suka gaisa cikin mutuntawa, duk ya rame yayi wani iri.
"Baba, ina mai sake baka haƙuri, amma ban karaya ba, in
sha Allah zamu ɗaukaka ƙara ne"
Jiki a sanyaye Baban ya ce "Kina ta ɗawainiya, ni idan
babu hali, kawai a bar maganar nan, na bar wa Allah"
Barrister Habib ya ce "No ba zai yiwu ba, ka manta
yadda muka yi da kai wancan zuwan da nayi muka haɗu?"
Yayi shiru ya sunkuyar da kai.
"Ka yi magana mana, mun yi magana da kai fa sosai baba,
ka bata haɗin kai dan Allah, a wannan karon muna fatan ayi nasara, ka yi mata
bayani, saboda ƙoƙarin kamanta gaskiya har nema aka yi a sabauta rayuwarta, ka
yi magana baba, ka yi mata bayanin komai.
Nabila let's record it Incase"
Ta jinjina kai ta ɗaukko wayarta, ta danna recording ta
ajiye.
Cikin tsoro ya ce "Dan Allah to kar ku gaya wa kowa,
kun ga yarana duka mata ne, na aurar da wasu, ina da biyu ƴan mata, an ce
muddin na yi magana abun da ya samu ramma zai same su, koma su rasa rayukansu
gaba ɗaya tsoro nake ji" mamaki ya cika Nabila, dan ita duk bai yi mata
wannan maganar ba.
"Baba, ni na baka tabbacin nan, babu abun da zai samu
iyalanka, ka ba ta cikakken haɗin kai, idan ka bari ta sake faɗuwa a shari'ar
nan, kaga magauta sun yi galaba a kanta, kuma yayan da ka ke yi wa, ka ɓata
musu suna"
Ya jinjina kai ya ce "Ana saura kwana biyu uwar ɗakin
hajiya jidda, tayi waya ta ce aje garin su ramma, ta dawo su haɗu da ɗaya mai
aikin, ayi mata gyaran gida, saboda tana ji da Ramma sosai, tana da biyayya,
kuma bata yi mata sata.
Ranar an ɗaukko ramma, suna ta aiki, zulai ta tafi kasuwa, ɗan
yayar matar gidan ya zo, sunansa Abdul, ban daɗe da fara aiki a gidan ba, dan
babban mutum ne sosai mutumin, in da suka baro, jami'an tsaro ne suke yi masa
gadi. Unguwar nan da suke ne, jami'an tsaro layuka suke gadi, ni kuma aka samo
mini buɗe ƙofa da rufewa a gidan.
Bayan yayi mata, ya tafi zulai ta fito tana kururuwa, bayan
ta dawo daga wurin sayen kayan miya. Bayan mun kai ta Asibiti, magana ta bazu,
aka ce an sallame ni daga aiki, amma za a neme ni, daga baya yan sanda suka je
gidana suka tafi da ni, wai zan ba da bayanin abun da na sani, muna zuwa aka
rufe ni aka ce ni ake zargi, kuma aka yi mini barazana da muddin na ce bani
bane ba yarana na cikin haɗari"
Nabila ta ƙulu ta ce "Amma meyasa baka yi mini wannan
bayanin ba ni, na san ta ina zamu ɓullowa lamarin? Nayi ta wahalar neman shaida
ka kuma ƙi bayani a kotu"
Barrister Habib ya ce "Kwantar da hankalinki, ki yi
haƙuri kin san uba da 'ya'ya"
"Ki yi haƙuri na san nayi kuskure amma a tsorace nake
ne nima"
Ta kalleshi ta ce "Ya sunan mai gidan?"
Ya girgiza kai ya ce "Ban sani ba"
"Ya za ayi ka yi aiki a gidan wanda ba ka san sunansa
ba?" Yayi shiru ya sunkuyar da kai.
Barrister Habib ya ce "Tashi muje, ma ƙarasa sauran
aikin" haka suka fito Nabila tana mita, barrister Habib yana bata haƙuri.
Law firm ɗin suka koma, suka fara arranging ɗin yadda zasu
yi appeal, sun gama ta fito suka haɗu da barrister Kabir, yayi mata sannu, tare
da yi mata kashedi, a kan ta raba kanta da aikata duk wani abu da zai sanya ta
shiga matsala, ta bishi da to, ta fita ta shiga motarta ta nufi gida.
Nasir bai ga wani abu ba a bibiyar Nabila da ya yi yau ba,
amma bai ji zuciyarsa ta gamsu ba, ya sakawa ransa zai yi assigning wani wanda
zai din ga bibiyar masa ita lokaci zuwa lokaci.
***
Su liti suna karyawa, Viper kuwa yana zaune yana yanke
farcensa da nail cutter.
Wayar liti aka kira, ya karɓa ya ɗaga ya ce "Ya
ne?"
"Normal, kwana biyu ba ku shigo gada ba fa"
"Eh ka san yanayin ne, sai muna bayyana muna ɓacewa,
meye labari?"
"Baban Viper ne ya zo rumfa, ya na neman ka, ko kai ko
walid" liti ya kalli walid ya kalli Viper.
"Meyafaru yake nemanmu?"
Ya ce "Ban sani ba, ya dai tambaye mu, ko Viper yana
zuwa wurin, muka sanar masa rabonmu da shi, tun kafin a kama shi, shekara shida
kenan"
Liti ya ce "Normal ne, zan faso fatan rumfa komai
lafiya?"
"Lafiya ƙalau tana ta garawa"
Ya jinjina kai ya ajjye wayar.
Liti ya cigaba da kallon Viper, Viper bai kalle shi ba ya ce
"Ko dai ka yi magana, ko kuma ka daina kallona"
"Allah ya baka haƙuri, na daina kallonka" kamar ya
gaya wa Viper, zuwan mahaifinsa rumfar shayinsu, sai kuma ya fasa ya haɗiye
maganar.
***
Abdul ne yayi sallama a falon, ya shigo a gajiye, ta amsa
sallamar tana tashi zaune daga kwancen da take.
Ya ajiye jakarsa, ya kwanta a jikinta ya ce "Wash"
Ta ce "Sannu"
"Yauwwa sweetheart" ta kama hannunsa, ta cire masa
agogon hannunsa.
"Tashi a cire safar"
"Ki bari na huta na gaji"
Ramma ta ce "Ƙato da kai kana shagwaɓa, wataƙila ma ba
wani aiki ka yi ba kake wani wash"
Ya ce "Kaii, baby kin san mutum nawa na yi wa tiyata
kuwa? Ga kusan asibiti uku naje na ga marasa lafiya"
"To tashi ka yi wanka, ka ci abinci" ya kalleta ya
yi murmushi ya tashi zaune, ya shafa kanta ya ce "Allah ya yi miki albarka
babyna, i so much love you" yayi maganar yana sumbatar goshinta.
Kallonsa take yi, tana son jin matsananciyar tsanarsa a
zuciyarta, amma abu ya gagara, sai wani ma kyau da ta ga yayi mata.
Ya tashi ya tafi bedroom, yayi wanka, Ramma ta goge
hawayenta tana fatan Allah kar ya jarrabeta da son Abdul.
Yayi salla ya fito, ta bashi abinci.
"Beb, in sha Allah komai ya kusa zuwa ƙarshe, zan
bayyanawa duniya ke, ina daf da gayawa babana maganarki, a san yadda za a gyara
lamarin mu cigaba da rayuwarmu, am ready na ɗauki kowane risk mu zauna tare in
sha Allah my rahama"
Tayi ajiyar zuciya tare da murmushi.
"Dan Allah ko sau ɗaya ki ce kina so na mana"
"A'a ni ban iya ƙarya ba"
Ya ce "Zaki yi bayani ne"
***
"Hello masoyiyyata"
Nabila ta ce "Na'am sumy kalar kyau"
"Albishirinki?"
"Kuɗi dubu goma"
Sumayya ta ce "Mayyar kuɗi, ba za a bayar ba"
Tayi dariya ta ce "Fesa mini"
"Arfa ranar monday in Allah ya kaimu, zan fara aiki, ni
da yaya murtala zamu buɗe gidan radion"
Nabila ta miƙe ta ce "Dan Allah masoyiyya"
"Wallahi da gaske, ke Allah ne ya kawo mana mafita, an
bani damar ƙirƙirar programs, har na sami program ɗin da zamu din ga yi tare,
mu ci karenmu babu babbaka, babu mai yi mana barazana da daka tsawa".
"Ke gani nan zuwa gidan naku ma, tare da ni za a buɗe
gidan rediyon nan in sha Allah"
Duk wannan abubuwan da Nabila take yi, ƙarfin hali ne kawai,
zuciyarta na tare da Viper, tunaninsa kawai take yi, tama rasa wane irin tunani
take yi a kansa, ga zuciyarta da take ta azalzalarta da son ganinsa.
Tare da Nabila aka yi bikin buɗe sabon gidan radio, mutane
suka din ga kiran wayar suna yi wa Sumayya fatan alkhairi, tare da tabattar
mata da duk in da ta tafi suna tare da ita.
A program ɗin farko da suka fara yi da sumayya, suka sanya
masa suna ƙeƙe da ƙeƙe.
Tun da sumayya ta gabatar da Nabila, kasancewar masu saurare
sun santa a bakin sumayya, suke ta tura saƙonnin gaisuwa, wasu kuma suna
tambayarta dalilinta na ƙalubalantar bunkure foundation, duk da irin gudunmawar
da take bawa al'umma.
Sumayya ta ce "Masoyiyya, kin ji tambayoyin masu
sauraro mai zaki ce?"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Babu abun da zan ce, sai
su kasance da mu a sabon shirinmu, na ƙeƙe da ƙeƙe. Ba wai bunkure foundation
ba, duk wani abu da ake kitimurmura a cikin sa, ko rashin adalci zamu yi
bajekolinsa a wannan shiri, kuma program zai iya bi ta kan kowa, duk wanda ya
ga kuma an yi masa ba dai-dai ba ya ƙalubalance ni a gaban shari'a.
Manyan shari'oi da aka yi bita da ƙulli a ciki, yadda ake
danne hakkin mara galihu ake tsayawa yaran masu kuɗi, yadda ake wasa da
hankalin talaka, da tauye masa hakki, shi fa wannan program ɗin, kai har da
shari'ar wani gawurtaccen matashi da ya shahara, jami'an tsaro suna nemansa,
sai dai abun mamaki shi ne sai da ya shafe shekaru biyar ba ayi masa shari'a, a
shekara ta shida aka sake shi, kuma yanzu an ce ba bisa ƙa'ida aka sake shi ba
wai nemansa ake yi.
Akwai tarin kwamacla a harkar shari'a a ƙasar nan, a shirin
ƙeƙe da ƙeƙe zamu fayyace abubuwa da dama, na ban mamamki" suka ƙarƙare
program ɗin cikin wasa da barkwanci.
***
Alhaji wada hankali kwance yake zaune yana shan lemo a kofi,
yana kallon indabo da yake ta haƙilo yana magana.
"Karofi, ka shiga gonata da yawa, ka kiyayeni, muddin
kana son yarinyar nan ta rayu, ya zama dole ka takawa shirin nan da zasu fara
gabatarwa burki"
Karofi ya ce "Sabod me? Kai da kake ɗaukar nauyin gidan
radion ka ake abun da ka ke so waye ya hana ka? Ni na ɗauki nauyin program ɗin
dan haka babu ruwanka da abun da ake yi"
"Karofi, ka san na fi ƙarfin kafi ga bayana ko?"
"Ai ka san shi ƙarfen cikin wuta sai da ɗan uwansa
ƙarfe, babban mutum mai kima a ƙasar nan, bai kyautu ace ka na ɓata lokacinka a
kan wata ƙaramar alhaki kamar wannan yarinyar ba.
Auuu ashe fa ta sako wani zance a maganarta, mai kama da
maganar Al'amin Viper, wato mai zamani. Kana tsoron ta tona maka asiri cewa kai
ne ka saka aka kashe matar Viper ko? Ka kwantar da hankalinka ba ta san wannan
labarin ba, idan har ba tana haɗuwa da Viper ba ya gaya mata da kansa"
Wani irin shock indabo yayi, ya sandare a tsaye, jin yadda
Alhaji mu'azzam wada kankarofi yake farke sirrin da bai taɓa tunanin wani
mahaluki ya sani ba.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Indabo da ƙyar ya iya buɗe bakinsa ya ce
"Kankarofi"
"Indabo"
"Wace irin magana kake faɗa ne?"
"Irin wadda ka ji da kunnenka, ka zata daga kai sai waɗanda
kuka aikata laifin ne ku ka sani? Kamar na so na fika iya playing cards ɗina
ko?"
Indabo zai yi magana, Jidda ta shigo wadda ita ce matar
kankarofi, kuma ƙanwar indabo.
"Yaya yana ganka a tsaye ne? Ba dai har tafiya zaka yi
ba?"
Kankarofi ya ce "Eh, ya ce tafiya zai yi, dama ziyarar
ta bazata ce, mu je na taka maka" kamar wawa haka indabo ya bi kankarofi
suka fito.
Ya sake kallon indabo da yake ta rarraba ido, kamar shege a
rabon gado ya ce "Ka fa kwantar da hankalinka, kar ka yi zaton zan gaya wa
wani wannan sirrin tsawon shekaru kenan, ina dakonsa ba wanda ya sani, ko
ma na faɗa bani da wata ƙwaƙƙwarar hujja a kai, ina gargadinka ne kawai ka
kiyayi yarinyar nan".
"Kankarofi"
"Indabo"
"Hawainiyarka ta kiyayi ramata, sanin wannan sirrin ba
shi yake nufin kana da lago na ba"
Kankarofi ya ce "Na sani, na ankarar da kai ne kawai,
na san abun da kake yi, dan haka kar ka tsallake gona da iri".
Indabo kawai ya jinjina kai zai juya ya tafi, Kankarofi ya
ce "Na san zaka yi mamakin yadda aka yi na sani ko? Ba abun mamaki bane
ba, kar ka je ka sakawa kanka damuwa da dogon tunani" bai ce masa komai
ba, ya yi gaba.
***
Abdul yana kwance yana bacci, saboda daren jiya bai yi bacci
ba, ramma tayi bacci, aka kira shi asibiti, sai bayan sallar asuba ya dawo.
Ramma ce ta shiga ɗakin a gigice, tana dukansa a kafaɗarsa.
Ya buɗe idonsa ya ce "Meye haka kuma?"
"Ka tashi"
"In tashi in yi miki me? Rahama ban yi bacci ba fa
jiya, ina asibiti".
A gigice ta ce "Ina ruwana? Abdul ban ga al'ada wancan
watan ba, wannan ma lokaci ya wuce"
"Kuma shi ne zaki tashe ni ina bacci?"
"Dole na tashe ka, me hakan yake nufi ka tashi ka duba
ni, ba zan sake ɗaukar ciki ba, ni ka tashi ka duba ni"
Tashi yayi daga kan gadon, bai ce mata komai ba, ta bi
bayansa tana kiran sunansa, amma ya rigata fita ya kulleta a ɗakin, ya tafi
wani ɗakin ya yi kwanciyarsa.
***
Sosai sumayya take jan jama'a a sabon gidan radion da kama
aiki, da ita da murtala.
Saboda bayan kasancewar ta sananniya, tayi ƙoƙari wurin
samar da sabbin shirye shirye masu ƙayatarwa, wanda za su tafi dai-dai da
matasa da ma dattijai baki ɗaya. Wasu daga cikin abokan aikinta da ta baro a
can, suka din ga yi mata magiyar suma ta samar musu gurbi a in da ta koma, suma
su koma. Yanzu sumayya ba ta da fargabar ta samo rahoto, a kushe ace mata ba
irinsa ake buƙata ba, saboda kawai bai yi dai-dai da abun da wasu suke son ji
ba.
Ranar farko da suka gabatar da program ɗin ƙeƙe da ƙeƙe ita
da Nabila, program ɗin ya yamutsa hazo, dan tayi sukuwa tayi zamiya, ta
ƙarewa bunkure foundation ta tas da hukumar shari'a, tayi bayanin yadda
shari'ar baba mai gadi ta kasance a kotu, tare da jaddada idan har da gaske dan
al'umma suke ayyukansu, ya zama dole a bayyana ina ramma take, idan kuma da
gaske tana asibiti, a bawa lauyoyi da ƴan jarida damar zuwa su ganota, kuma a
kawo bayanin likita a kan abun da yake damunta zuwa lokacin da aka gaza ganinta
a gaban kotu.
Hatta lauyan gwamanti ta din ga challenging ɗin sa, a yadda
suka din ga taka doka yadda suke so.
Nan fa mutane suka din ga tururuwar kiran waya, wasu suna
sharhi, ciki har da wani lauya mai zaman kansa, da ya kira waya, ya tofa
albarkacin bakinsa tare da tabattar da akwai jabun lauyoyi da suke yi wa doka
hawan ƙawara, a yi cuwa-cuwa a danne hakkin mai ƙaramin ƙarfi, a wanke yaran
masu ido da kwalli, ire-iren foundations ɗin bunkure suna da yawa. Ya ƙara faɗaɗa
bayanan da Nabila tayi, tare da fito da wasu abubuwa ma da ita hankalinta be
kai, kai ba.
Nabila ta ji daɗin program ɗin sosai da sosai, dan kuwa ji
tayi, zuciyarta ta rage raɗaɗi da baƙin cikin abun da aka yi musu a kotu.
Bayan kammala program ɗin, still cigaba da kiran wayar a aka
yi, ƙarshe sai kashewa suka yi.
Sumayya ta ce "Mutuniyata kin yi bala'i fa"
Nabila ta ce "Ke ni ɗin ta wasa ce? Ai sai Najar
bunkure ta zubar da hawaye, yanzu ta ƙarƙashin ƙasa zan yi analysis nawa
ƙungiyar take samu na tallafi a wata, da kuma abun da ake spending wurin
tallafwa mutanen da ake iƙirari. Ni ɗin fa ba ta wasa ce ba"
Sumayya ta ce "Ba wani ta wasa ko ba ta wasa ba, dole
mu daga da Addu'a fa, Allah ya tsaremu Masoyiyya"
"Amin dai, amma yanzu meye abun yi?"
Sumayya ta ce "Eh to, kamar yadda ki ke tunanin kawo
ƙarshen bunkure, ni kuma sonake na ci uban indabo, duk da ya fi ƙarfina, amma
zai ga abun da 'yar matsiyata zata iya yi, dan wallahi sai na kusa girgizo shi
daga kan kujerar nan"
Nabila ta kwashe da dariya ta ce "Me yayi miki ne, ki
ke wannan alwashin?"
"Zagin cin zarafi yayi mini, lokacin da ya ce na din ga
bibiyar masa ke, kin san na taɓa zuwa na bayar da wani rahoto, a kan cewa an ce
an yi wani aiki a yankinsa, kuma da na je ban tarar an yi ba, kin ga abubuwan
da aka yi mini a kan hakan? Program ɗin da zamu din ga yi da yaya murtala, irin
su Indabo zamu din ga bankaɗawa asiri. Zamu faɗi abun da suke karɓa na
consituency project duk wata, da kuma ayyukan da suka gabatar a watan, daga nan
ya ragewa al'ummar yankin da ake wakilta, su yanke hukuncin da ya dace"
"Allah ya ƙara lafiya, ƴar gwagwarmaya amma shirin ya
ƙayar da ni, Allah ya taimakemu ya ƙarfafi gwiwarmu masoyiyya. Abun mamaki
shekarun baya bamu taɓa tunanin samun wannan damarmakin ba, sai dai mu yi ta
dama dama"
"Haka lamarin Allah yake, yanzu ya ara mana damar da
muka roƙa, ya rage namu mu yi abun da ya dace da ita"
"Haka ne, Allah ya taimake mu ya bamu sa'a" suka
ce Amin.
Ko da ta koma gida, Walida ce ta fara tararta ta ce
"Arfa, yanzu muka gama jin program ɗin ku, live ku ka yi shi, kina ta ɓarin
maganganu ko tsoro ba kya ji"
Nabila ta ce "Walida, wanda bashi da gaskiya ai shi ne
yake tsoron a faɗeta, bamu fara dan mu daina ba"
"Zaki ga baki fara dan ki daina ba, yaya ya shigo a
ƙalla sau uku yana nemanki, ya kira wayarki ma, kin ƙi ki ɗaga"
"Duk a kan program ɗin da na yi"
Walida zata bata amsa ya shigo, fuskarsa babu annur ko kaɗan.
Ta tsaya tana kallonsa, ya ƙaraso gabanta ya kalleta ya ce
"Arfa ba zaki taɓa yin hankali ba ko? Meyasa ki ke son yin wasa da rayuwar
ki ne?"
"Dsp, rayuwa ta ka ce ai, nikaɗai nake abuna ai,
shiyasa nake takatsantsan kar baya tawa rayuwar, na saka ta wani a
hatsari"
"Zaki rufe mini baki, ko sai na kwaɗa miki mari, ni
kike gaya wa ba kya saka rayuwar wani a hatsari? Duk tayar mana da hankalin da
ki ke yi ba kya gani, yadda ki ke tayarwa da Abba hankali a shekarunsa ba wasa
da rayuwarsa ba ce ba? To wallahi ba zaki kashe mana uba ba, muna da burin
ganinsa a raye".
Aikuwa ta gyara tsayuwarta, ta haɗiye wani abu mai ɗacin
gaske, ƙirjinta na yi mata zafi ta ce "Good, an zo wurin, kar na kashe
muku uba, tun da ni ba nawa uban bane ko? To ku mayar da ni wurin nawa uban
mana, meye na zama ana yi mini gori, how many years for now? kuna yi mini gori,
kai ɗin ma da baka yi yau gashi ka fara, alhalin kun fi kowa sanin bani na zaɓi
hakan ba, da da yadda zan yi, da tuni na bar muku gidanku, ku nuna mini hanyar
gidan nawa uban mana"
Ta baya ya fizgota, ya ɗauketa da lafiyayyen mari.
Gigicewa tayi, jikinta ya hau rawa ta kalli Abba, da ransa
yake a ɓace, fuskarsa babu annuri.
Ya riƙe hannunta, ya zazzaro mata ido ya ce "Me ki ka
nema kika rasa? Me kike buƙata a rayuwar nan da ban yi miki ba da ki ke zancen
mahaifinki, menene shi Nabila?"
Ta sunkuyar da kai tana kuka, ta dafe kuncinta.
"Ki gaya mini, kafin na kasheki, me uban naki ya
tsinanawa babarki ma, balle ke? Uban me ki ke nema a wurinsa?"
"Abba ka yi haƙuri, ba zan sake ba"
"Ba zan yi haƙurin ba, ki gaya mini ta ina na gaza,
menene ba na yi miki"
Mama da jin hargowar su ya sanya ta fito ta tarar da su, ta
ce "Mhmm, ai tsintacciyar mage ba ta taɓa yin mage major, kuma gurbin ido
ba ido bane ba, muna nan da kai wataran sai ta saka ka zubar da hawaye"
Nasir ya ƙarasa ya ce "Abba dan Allah ka yi haƙuri, ba
zata sake ba in sha Allah, kar ka kuma dukanta"
"Shut up! Kai ma har da kai, ina yi maka kallon mai
hankali ashe ba haka ba ne, ku kuke tunzurata take wannan zancen".
Ya ce "Ka yi haƙuri dai Abba, in sha Allah ba za a sake
ba"
Ya saki hannunta ya fice daga gidan baki ɗaya.
Nabila kuwa da gudu ta ƙarasa ɗakinta tana kuka mai cin rai.
***
Ƙarfe sha ɗayan dare, liti yana ƙofar gidan su Al'amin, yana
rarraba ido, babu yaron da zai aika cikin gidan, kowa ya watse.
Ya bubbuga gate ɗin gidan, ya koma gefe.
"Waye?"
"Nine"
Ya buɗe gate ɗin ya kalli liti ya ce "Ya aka yi?"
"Wurin Abbu nazo shi nake nema"
Jin muryar liti, ya sanya Abba gane jama'ar Viper ne, dan
haka ya ce "Mai zamanin yana tsare ai, ka sani kake nemansa"
"Dan uwarka wurin mai zamani na ce maka na zo? Wurin
mai gidan na zo, baka gane ni bane liti ne" yayi maganar yana cire
facemask ɗin fuskarsa.
"Na gane ka, amma a kan me zaka zo nemansa, ka gaya
mini na je na gaya masa"
Wata uwar shaƙa liti yayi masa, ya watso shi waje ya ce
"Shege, kai ka isa in zo wurin maigida ka ce na gaya maka menene sa'anka
ne ni, wallahi idan baka kiyayeni da abun da ya shafi mai zamani ba, sai na
sassaraka na bar wa uwarka tabon daba, makira yar wuta" tamkar gidan
ubansa, liti ya kutsa kai ya shiga gidan.
Ya tsaya a tsakar gidan yana kwaɗa sallama.
Rahila ce ta fito ta ce "Wane mara mutuncin ne haka a
tsakar gidanmu, malam balaggagen gardi ka shigo mana gida".
"Ɗanki ne ya so na shigo, eh sarkin gida nake nema, an
ce ya je gada biɗata, mu kuma tsakainmu da maƙyanƙyasanmu akwai amana, mussaman
maƙyanƙyashin mai zamani, ai dattijonmu ne iya wuya, ace masa gani na amsa
kira".
"Wace irin magana ce kake yi wannan, ni ban gane
ba"
"Gana ce, kuma kin gane mai nake nufi, ki yi mini
magana da mai gidan, ko na shiga na neme shi da kaina"
Abba ya shigo gidan yana zare ido, ya sake cewa liti
"Ka zo ka fitar mana daga gida"
"Gidan ubanka ne ko na mai zamani? Idan gidan ubanka ne
sai na fita, idan kuma gidan uban mai zamani ne nima gidanmu ne"
Rahila ta ce "Wane mai zamanin, ka tafi can ka neme
shi, ka fice ka bar mana gida"
"Ke yar wuta ban saka da ke ba, baƙar sheɗaniya, idan
baki nemi yafiyar mai zamani ba, wuta ɗaya zaki shiga da matar sheiɗan, kai
ware ka yi mini magana da mai gidan" yayi maganar yana zaro makami.
Abbu kuwa bacci yake yi sosai, a cikin baccin ya jiyo muryar
liti, kawai zuciyarsa ta raya masa Al'amin ne, ya zo da mutanensa.
Da sauri ya fito tsakar gida, yana tambayar ko lafiya.
Liti na ganin sa ya mayar da makamin, ya durƙusa ƙasa ya ce
"Abbu barka da dare"
"Yauwwa barka, lafiya ka shigo mana gida a wannan
daren?"
"Liti ne Abbu, an ce ka je namanmu, ko ni ko walid,
shiyasa ban yi sanya ba, na ce bari na gangaro na amsa kira, duk da mu masu
laifi ne, ya kyautu ace muna zuwa muna kawo gaisuwa"
Abbu ya ce "Ikon Allah, meye sunanka na gaskiya
ne?"
Liti yayi murmushi ya ce "Bawan Allah nake ai sarkin
gida, Abdallah ne"
"To ni Abdallahn zan ce, bisimillah shigo mu shiga daga
ciki"
Rahila ta ce "Ya shiga ina? Makami ne fa a jikinsa, sai
yayi maka illa, ya zaka shiga da shi makwancinka?"
Abbu bai kulata ba ya ce "Ƙaraso Abdallah"
Ya bi bayan Abbu, yana baza babbar rigar daya saka a kan
ƙanan kayansa ya kalleta ya ce "Munafuka, haddsana mai raba ɗa da uba,
idan baki yi wasa ba, tun a duniya sai kin tozarta"
Duk tsagerancin Al'amin baya saurarta balle ya zageta, amma
liti sai ƙare mata zagi yake yi.
Abbu ya kalli liti ya ce "Abdallah, dan Allah ko ka san
in da Al'amin yake? Tun da ya zo mini daga prison na kore shi, ban sake ganinsa
ba, ina matuƙar kewarsa da son na ganshi, na san ku ne makusantan sa, ban sani
ba ko kun san in da yake?"
Liti ya ce "Eh to, gaskiya ban san in da yake ba, amma
dai muna haɗuwa"
Abbu ya ce "Ban gane ba"
Liti ya ce "A bar shi hakan da na faɗa, ban san in da
yake ba, amma muna haɗuwa, kuma maganar gaskiya, yana fushi da kai, tun da aka
ce yayi laifin nan baka bashi dama ko sau ɗaya ba, ka saurare shi"
"Wace damar zan bashi, na nema masa auren yarinya girma
da arziki, amma ƙarshe yayi silar rayuwarta"
Liti ya kalle shi ya ce "Haryanzu ka yadda shi ne ya
kashe yar madara?"
"Meyasa ba zan yadda ba, tun da ya furta mini, kuna
gashi yana shaye-shaye"
Liti ya jinjina kai ya ce "Haka ne" ya tashi tsaye
ya ce "Baka shirya ganin sa ba, maybe zuwa gaba kaɗan, amma wallahi mai
zamani, Allah ne yayi da sauran kwanansa a gaba, dan ya kusa kashe kansa, ko
mun lalace fa ku iyayenmu ne, bamu da sama da ku, duk son da mai zamani yake yi
maka, ka fita daga zuciyar sa, ya daina maganarka ranar da na yi masa zancenka
ce mini yayi shi yanzu ba shi da uba, kaga wannan ba dai-dai bane ba, alhalin
ga wani ɗan kut.... Da yafi mai kora shafawa da shi da yan uwansa, suna zaune a
gidan, mu kuma kun sallamawa duniya mu. Bari na ɓace, Allah ya ƙara maka lafiya
da nisan kwana, ka cigaba da yi mana addu'a a duk in da muke, mai zamani zai
samu yanci ya cigaba da gudanar da rayuwarsa kamar kowa, ba tare da yana ɓuya
ba"
Abbu ya miƙe suka fito tsakar gida ya ce "Kayi mini
wani taimako Abdallah, ka tayani kwantar masa da hankali kafin ranar da Allah
zai saka na ganshi dan Allah"
"To in sha Allah"
Ya ɗaukko kuɗi ya bawa liti, liti ya ce "Meyasa zaka
bani kuɗi, ni ba zan karɓa ba, ayi mana addu'a kawai, in sha Allah mai zamani
ya kusa samun ƴanci" yana gama maganar ya fice.
***
Liti ne yake ta kallon Viper, ya numfasa ya ce "Mai
zamani"
"Farin jakada" liti yayi dariya, ya ce "Rabon
da ka gaya mini sunan nan har na manta, kwanan nan kamar kana jin raha, menene
sirrin ne?"
Ya ce "Abubuwa da yawa, ƙwaƙwalwa ta ta samu nutsuwa a
'yan kwanakin nan, sannan na fara jin daɗin yadda nake wasa da hankalin
maƙiyana, ka san sanyawa mutum tsoro yafi kowane horo wahala"
Walid ya ce "Ai mun gode Allah, da bayan tafiyar
jauhar, Allah ya kawo mana Nabila rayuwar ka, haƙiƙa bayan ƴar madara ita ta
ceto mana ƙwaƙwalwarka da tunaninka"
"Ba wani nan, da an yi magana ka fara sako maganar
wannan makirar ba wani, ba uwar da ta tsinana masa"
"Wai anya liti idan aka bi salsala ba daga zuriyar
fir'auna kake ba, kai wai baka yafiya ne"
"Ba zan yafe ba, kace ma nine fir'aunan kawai mana
walid"
"A'a ni ban ce maka fir'auna ba, amma dai baka da
zuciyar kirki"
"Ni rabu da ni, zan yi magana ka hana ni, zaka saka na
manta"
Ya kalli Viper ya ce "Mai zamani, Abbu yaje rumfar
sayar da shayi yana nemana ko ni ko walid" a take ɗan annurin fuskar Viper
ya ɗauke.
Liti ya ɗora da cewa "Na ɗan yi yawo na nemi bayanai,
kar na je ko wani set up ne, amma na fuskanci lafiya ƙalau ne, dan sai na ci
uwar agolan nan na gidanku, da ya kawo mini wargi, mun haɗu da Abbu, ya ce mini
yana son ya ganka, amma na ce ban san in da kake ba, akwai tarin nadama a tare
da shi, dan Allah mai zamani ka sassauta, naka mahaifin ne kawai ya rage mana,
mu yi haƙuri mu yafe masa, na tabattar masa da ka kusa yin 'yanci da yardar
Allah"
"Bani da uba, nawa uban ma mun rasa shi, dama can ba ya
ta tamu, dukkanmu marayu ne, da muke zaune a matsayin ƴan uwan juna, ko na yi
ƴanci, ba zan sake zuwa in da yake ba, na bar shi da waɗanda yake so"
"A'a Viper, su fa iyaye komai za su yi, ba a fushi da
su" harshensa ya zaro waje, ya ɗago sweazland ɗin da take gefensa, ba
shiri liti ya tsuke bakinsa, yayi shiru ba dan ya rasa abun faɗa ba, sai dan
sanin cewa yana sake magana sai ya saka masa ƙarfe.
Message ne ya shigo wayar Viper.
"An yi maka gargaɗi a kan yarinyar nan tun da farko,
amma ka ƙi ji, yanzu ta zama rauninka, sai ka yi aiki tuƙuru, dan kare
rayuwarta!.
***
Nabila ba ta san ya aka yi aka samu lambar wayarta ba,
mutane suka din ga kiranta a waya, wasu na zaginta a kan program ɗin da ta
gabatar, ta taɓa bunkure foundation, wasu na jinjina mata, tare da nuna mata
goyon bayansu, da ta gaji kashe wayar ta yi gaba ɗaya.
Gaba ɗaya kewa da tunanin Viper, suka haɗu suka uzzurawa
rayuwarta, tana ta ƙoƙarin basarwa amma abu yaya gagara kamar yadda dariya ta
gagari kare.
Ta tsaya a gaban mudubi tan ƙarewa kanta kallo, bayan ta
fito daga wanka, ta shiga ƙarewa kanta kallo, kyakykyawar farar fatarta sai
sheƙi take yi.
Idanunta jawur, saboda kuka, gaba ɗaya haushin Nasir take
ji, gaba ɗaya komai yayi mata zafi, ba ta jin daɗin komai.
Message ne ya shigo ƙaramar wayarta, "Mu haɗu a
garden" ta zubawa notification ɗin ido, tayi wata irin ajiyar zuciya,
kamar sanyi ta ji a ranta, da ganin saƙon nasa.
'Wai me nake yi haka ne? Ta tabatta son shi nake yi kenan?
Wace irin ƙaddara ce haka?"
Ta lumshe idanunta, hawaye ya ziraro daga idaunta, abubuwa
da yawa suna damunta, kuma babu wanda take burin ta gayawa sama da Al'amin,
mutumin da bai damu da ita ba ko kaɗan.
Jiki a sanyaye ta shirya, ta saka kayanta, ta kawo facemask
ta saka, ta fice.
Ko da ta je garden ɗin, ba ta tarar da shi ba, ta kira
wayarsa amma ba ta shiga, haushi ya kamata, ranta ya ɓaci, dan da niyyar ta
ganshi ta zo, haka kurum tayi ta ɗokin ta zo su haɗu.
Ta nemi wuri ta zauna cikin takaici, haushin kanta take ji,
yadda ta faɗa soyayya cike da wawanci.
Ta ɗan jima a wurin a zaune, sannan ta tashi, ta ɗauki mota
zata koma gida, ya kirata a waya.
Bai jira tayi magana ba, ya fara "Yayanki yana bin
bayanki, nan da kilometer biyu, akwai wani gidan cin abinci, ki tsaya ki
shiga" ya gama maganar ya katse.
Babu tunanin komai ko musu, ta cigaba da tafiya, sai dai ta
din ga kallon mirror, amma bata ga alamar wani ita yake bi ba.
Ta tsaya a restaurant ɗin, ta shiga ta sake kiran wayarsa,
bai ɗaga ba ya tura mata saƙo "In the next 10 minutes, ki koma motarki, ki
samu wuri ki zauna ki jira"
"Wai dan Allah meyasa...... Katse wayar yayi, ba tare
da ta gama maganar ba.
Ta nemi wuri ta zauna ranta a ɓace, mintuna goma na cika ta
ga saƙonsa.
Ta tashi ta fita, ta ƙarewa harabar wurin kallo, amma ba ta
ganshi ba, ta buɗe motar sai da ta zauna, kawai ta ganshi a cikin motar, da ihu
zata kurma, amma tayi shiru, tana rarraba ido, ta rufe motar ta kalleshi ta ce
"Ta ina ka shigo?"
"Ta ƙofa" ya bata amsa.
"Amma to meyasa kayi ta wahalar da ni?"
"Fita ki zagayo, zan ja motar" ta jinjina masa
kai, ta fita ta zagaya, shi kuma ya koma mazaunin direba, ya bawa motar wuta,
ya ja ta da uban gudu ya bar wurin.
"Ka tuƙa a hankali, tsoro nake ji" bai ce mata
uffan ba, ya cigaba da fafara gudu, sai da ya cimma wani a kan babur, ya sanya
hular kwano.
"Kin san wannan?" Ta girgiza kai alamar a'a.
"Kin tabatta?"
"Eh, ɗazu dai ka na ƙaraso nan, na wuce shi a kan
titi"
Ya jinjina kai ya ce "Ke yake bi, kin wuce ni a mota,
na ga yana binki, ina kyautata zaton ko dai yayanki, ko wani ne ya sa ya din ga
binki"
Ta sauke numfashi ta jingina da jikin dai-dai lokacin da ya
saka hannu a jikin seat ɗin, yana ƙoƙarin shiga wata kwana.
Tudun gashinta ta ɗor a kan hannunsa, ta lumshe ido,
fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa, jikinsa ne yayi wani irin sanyi, yayi
saurin cire hannunsa, ya ƙarasa in da yake son su je.
Shi ma lambu ne wurin, amma babu kowa, sai sanyin bishiyun
wurin, ta fuskanci yana son yanayi irin haka.
"Yaya ake ciki da case ɗin rahama, a ina ki ka
tsaya?"
Kawai ta zuba masa ido, ya yi mata wani irin kyau, ma'abocin
ƙanan kaya ne, shirt ce ajikinsa baƙa da zanen damusa a jiki, sai dogon wandon
jeans, mamaki ma take yi, a in da yake samun kuɗin sayen kaya masu kyau.
Sai ƙamashin turaren florie yake yi, ya yi gyaran fuska, ya
kuma yi saisaye, idanunsa sun rage wannan jan, alamu sun nuna ya ɗan tsagaita
da shan miyagun ƙwayoyi.
"Malama ina magana kin yi shiru kina kallona"
"Yanzu rashin muhimmancina har ya kai na shiga wannan
tashin hankalin, ka sani amma ka kasa nema na ko a waya, ka ce mini sannu, i
almost lose my life fa, a yaya ka ɗauke ni ne? Bani da muhimmanci har haka a
wurinka, haba dear, ni ka san ba zan taɓa yi maka haka ba, ina son rayuwarka,
ina son ganin walwalarka da farincikin ka, ina son na maye maka gurbin jauhar,
da wasa na ɗauki abun, amma ya zame mini gaske. Ka daina nuna mini halin ko in
kula, bana jin daɗi ko kaɗan. Damuwa ce da ni a raina sosai, ina son wanda zan
gaya wa ya saurare ni, wanda zai fahimci haƙiƙanin abun da nake ji"
"Ki shiga hankalinki, bana son wannan wasan da ki ke yi
mini, da zarar aikina da ke ya kammala, kowa zai kama gabansa, ki daina yi mini
irin wannan wasan, na gaji da yi miki kawaici, ba na so"
Cikin ƙarfin halin da rauninta ya hana ta aikata hakan,
hawaye ya fara biyo kuncinta ta ce "Ba wasa nake yi maka ba, ƙaddara ce da
na roƙawa kaina da bakina, ba wasa nake yi maka ba, da fari wasa nake yi, amma
yanzu ya zame mini gaske, ban taɓa tunanin zan iya cewa wani namiji ina son shi
ba, amma kai naga kamar nutsuwar ka ta kai na gaya maka"
Ya ce "A'a karki yaudari kanki, wace nutsuwa nake da
ita?"
"Rauninka mutane kawai ke iya gani, ni kuma nagartarka
nake gani, kamar kai ne zaka zama dai-dai da ƙaddarata"
Wani abu ya ji yana nema ya rinjayi zuciyarsa, mussman da ya
fara ganin fuskar jauhar a cikin ta Nabila tana kuka.
Cikin ƙarfin hali, yayi ta'awizi ya kaurara muryarsa cikin
tsare gida ya ce "Jauhar ɗaya ce, kuma na sameta ta suɓuce mini, babu wata
mace da zata iya maye mini gurbinta, sanya wata macen a zuciyata tamkar cin
amanar 'yar madara ne, a kanta na gama soyyaya, kuma na gama aure, dan haka kar
ki ƙara yi mini wannan maganar, ki nemi wani ki aura, wanda iyayenki za su yi alfahari
da ke da shi, jauhar ma ƙaddara ce ta saka aka bani ita"
Ta share hawayenta ta ce "Nabila mace ce mai aji, aji
ma na gaske, ban taɓa mafarkin fara furtawa wani namiji ina son shi ba, raunin
macen kenan, daga tausayi na faɗa sonka ban shirya ba, kai banda ƙaddara da haɗin
Allah, me zai kai mace kamata yin kasada da rayuwata kamar wata wawuya ina
nemanka ina zaman zamana?.
Sannan ka sani idan akwai macen da nagartarta zai hana a
auri wata mace bayan wafatinta, to Sayyada Khadijah ce Allah ya ƙara mata
yadda, kuma idan akwai macen da soyyayar da ake yi mata, zai hana ayi mata
abokiyar zama, to sayyada Aisha ce radiyallahu anha.
Baka san wace damuwar ce a raina ba, ka zaɓi ka yi mini
haka, ko baka so na, ba haka yakamata ka yi mini ba, bani mukullin motata na
tafi" tayi maganar tana kuka tare da miƙa masa hannu.
Kallonta kawai yake yi, babu in da ta bar 'yar madara a
kamanni, hatta kukan nan da take yi, jauhar kawai yake gani, sai dai Nabila ta
fi jauhar murya, da kilewa kuma ita mafaɗaciya ce.
Loosing control ɗin sa ya kusa yi, da zuciyar sa take raya
masa, ya rungumeta ya rarrasheta, sannan ya ji menene damuwarta, fizge mukullin
motar tayi, ta ƙara gaba tana kuka.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin zafin nama ta juya tana kuka, ta nufi hanyar barin
wurin, har ya ɗaga ƙafa da niyyar ya bi ta, sai kuma ya fasa, dan idan ya bita
bai san me zai ce mata ba, yana kallonta ta hau motarta ta bar wurin.
Bashi da zaɓin da ya wuce shi ma ya bar wurin, sai dai ya
tafi zuciyarsa cike da wasi-wasi, ko cikin duhu aka tara mata dubu, zai cire
'yar madararsa, amma haryanzu ya kasa gane dalilin da ya sanya Nabila take kama
da jauhar, ba kuma wai kama sama-sama baz kamannin ne tamkar an raba kara biyu.
Ya cigaba da takawa a hankali ya bar wurin.
***
"Indabo ina fatan ka saurari program ɗin da wannan sheɗanun
yaran suka gabatar, ka shirya ɗaukar mataki ne, ko kuma ni na ɗauka da kaina?
Na gaya maka ba zan bari wahalata ta shekaru ta tafi a banza ba, in ƙare a
lalace, ƙaramar yarinya ta rusa ni ba, ko dai ka saka a dakatar da program ɗin
nan, ayi abun da ya dace a kanta, ko kuma ni zan ɗauki matakin abun da ya
dace"
Indabo ya kalleta ya ce "Naja, wai yaushe ki ka zama
haka ne? Duk wata matsala tare muke magance ta, amma wannan sai nema ki ke yi
ki zame, ba fa wata babbar matsala bace ba"
"A wurinka ne ba babbar matsala ba, kuma ƙaramar
matsala ita ce take zama babba. Kana jin manyan lauyoyin nan da basu samu dama
a kaina ba da, yanzu sun samu suna ta bata goyon baya, mutane sun fara farga da
abun da take yi, ni na rasa wai waye uban ɗakinta ne waye ya tsaya mata?"
Ya numfasa ya ce "Kankarofi ne"
"What? Kankarofi kuma? Meya kawo shi cikin wannan
maganar?"
"So yake lallai sai ya ga bayana, ya rama abun da ya
faru a baya, maimakon ya rama a siyasance, ba ta haka yake son yi ba, so yake
lallai sai na tozarta"
Naja ta ce "Ikon Allah, to menene ribarsa, alhalin kuna
sirikai?"
"Aurenma da ya auri jidda, duk cikin plan ne na siyasa,
kin san ita siyasa babu maƙiyi na dindindin, kuma babu masoyi na dindindin, mun
zauna jam'iyya ɗaya da shi a baya kamar yadda na taɓa gaya miki. A lokacin nan
mutane suna matuƙar sonsa, duk da ba wani babba bane ba, kuma naga take-taken
ana kiransa ya fito takarar kujerar da nake hari. Na shiga na fita da wasu
mutane, sai da suka fita suka bar mana jam'iyyar, duk da a lokacin ba wani
mayar da hankali yake a kan siyasar sosai ba, gidansu yan kasuwa ne, shi ne
yake taɓa siyasa.
Bayan sun bar jam'iyyar, aka bani takara, shi ma jam'iyyar
da ya koma, suka bashi takara, nayi ta bita da ƙullin siyasa, da yi masa yarfe
kala-kala.
Ni da yan jam'iyyar mu, kasancewar muke da mulki a sama,
muka shiga muka fita, aka murɗe zaɓen, ya ce shi ba zai kai ƙara ba,
jam'iyyarsa suka kai ƙara, amma duk aka kori ƙarar, duk da haka mutane suka so
yi mini bore, shi suke so. Na haɗa kai da shugabannin jam'iyyarmu, muka kunno
masa wuta ta sama, EFCC suka zo har gida suka kama shi, aka yi seazing ɗin wasu
kadarorinsa, da zimmar ya mallake su ba bisa ƙa'ida ba.
Kasancewar ba shi da manyan iyayen gida, bai iya shige-shige
da neman wurin zama da biyayya a wurin manya na wannan lokacin ba, ya sanya sai
da aka tsare shi a prison, ana binciken sa, bayan an sake shi duk da haka aka
ƙwace masa kadarori.
A lokacin mahaifinsa ya ce, baya son sa da harkar siyasa, ko
zai yi ya bari sai bayan ransa, sai ya cigaba da kasuwancinsa, kuma bai taɓa ce
mini uffan ba, sai bayan rasuwar mahaifinsa ya dawo yake taɓa harkar siyasa,
har aka yi masa muƙamin nan, ashe ya ƙwafe wannan abun a ransa, so yake sai ya ɗauki
fansa ta ƙarfin tsiya yanzu"
Naja ta ce "Taɓ, gaskiya kana ruwa indabo"
"Ban gane ina ruwa ba?"
"Au muna ruwa zan ce? Wannan rigimar ai ban san lokacin
da aka yi ta ba, balle ace da ni aka ƙulla a nemi mafita, a kanka yake neman
fansarsa, dan haka ni kar a saka ni a ciki ba zai yiwu ba, haka kurum ana nema
ayi mini tsirara a idon duniya"
"Naja"
"Na'am"
"Haka ki ka ce? Kin san bana tafiya da butulu?"
"Babu in da nayi maka butulci, na bauta maka da ƙarfina
da gangar jikina, abun da nake yi ba butulci bane, iya ruwa ne fidda kai"
Ya jinjina kai ya ce, "Haka ne, na fahimta"
***
Abdul ne a zaune, ya zubawa ramma ido, tamkar mahaukaciya,
gaba ɗaya ta burkice masa, idanunta sun yi jawur saboda kuka, yana kallonta
rabonta da abinci tun jiya, muryarta duk ta dashe saboda kuka, ya ma rasa ya
zai yi mata, yayi tsawar ya zare idon, amma duk a banza.
Ya kaɗa ya raya taƙi cin abinci.
"Rahama" ta ɗago ta kalleshi kamar wata dodanniya.
"Me ki ke so?"
"Ka duba ni, wallahi ba zan zauna da cikin shege ba,
idan shi ne ka cire mini, ka mayar da ni gaban uwata, na gaji da yi maka
biyayya baka da niyyar cika alƙawarin da kayi mini, ban sani ba ko sai ka cika
alƙawarin ka na kasheni sannan hankalinka zai kwanta".
"Yanzu da kanki ki ke cewa a zubar da ciki? Alhalin
lokacin da tsautsayin nan ya faru, mun nemi a zubar a rufe maganar amma ku ka
ƙi"
Kamar ta ɗura masa ashar ta ce "Wancan idan tsautsayi
ne wannan fa? Wallahi Abdul zan kashe kaina in huta, na gaji"
Ya ce "Is ok, shikenan yanzu ko cikin ne babu lallai na
gani, ki bari zan tafi da ke asibiti na yi miki gwaje-gwaje sosai, amma sai kin
yadda kin yi wanka kin ci abinci"
Cikin rashin wayo ta jinjina kai, ya lallaɓata da kyar, ta
yi wanka, ya dafa tea da indomie ya bata, sai dai tana gama ci, ta hau amai.
Ya ce "Kin gani, ulcer ta kama ki, daga jiya zuwa yau
da baki ci abinci ba, shiyasa kina cin abincin ki ka yi amai"
Cikin kuka ramma ta ce "Wallahi ciki ne da ni, ni bani
da wata ulcer "
"In ji wa? Ulcer ai tana saka amai, baki ga nima yadda
take yi mini ba ne? Ai rashin cin abincin ne ya janyo haka, kuma idan ki ka
cigaba da ƙin cin abincin tumbinki ne zai ta rarakewa, komai ki ka ci sai kin
yi amai".
"Dan Allah da gaske kake, ulcer ba ciki ba?"
"Zan yi miki ƙarya ne?" Yayi maganar yana tsuke
fuska.
"To ka rantse da Allah"
"Ba zan rantse ba, ina likita zan yi miki ƙarya ne?
Kuma kan nayi miki allura ban gaya miki allurar tsarin iyali na iya ɗauke miki
al'ada ba, tun da artificial homones ne aka saka a jikinki ba?"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Eh ka gaya mini"
"Amma shi ne ki ke ta yi mini wannan borin ko rahama,
ni ko?"
"Da ka san me nake ji a zuciyata da baka ce ina yi maka
bori ba, na gaya maka mamana mu biyu ne da ita, yayanmu ma ya mutu, ya za ayi
hankalinta ya kwanta ina nan? Kalli tsawon lokacin da na ɗauka ban ganta ba, ka
tausaya mini mana"
Ya saka hannu yana share mata hawaye ya ce "Zan mayar
da ke rahama, sonake sai na sanar da mahaifina komai tukuna, bana son sunanki
ya ɓaci kamar yadda ki ke ta iƙrari"
"Ɓacin suna na nawa kuma? Ai ya riga ya ɓaci"
"Zan gyara shi da yardar Allah babyna"
Sai da yayi ajiyar zuciya da yaga ta ɗan nutsu har ta ɗan
saduda, sai da ta samu bacci, sannan ya tashi ya fita, ya kira saif a waya ya
ce masa su haɗu.
***
A harabar gida Nabila ta tarar da Nasir, tana gama parking
ya fito daga cikin tasa motar ya tareta ya ce "Daga ina ki ke?"
Kamar ta wanka masa mari, a hasale ta kalleshi ta yi shiru.
"Ina magana kin tsare ni da ido"
"Iska na fita sha"
"Wa ki ka gaya wa, sai Abba ya dawo yayi ta faɗa ko?
Kuma wace irin shan iska ne zaki fita ki yi nisa da gida, kukan me ki ke yi
ma?"
"Dan girman Allah ka ƙyale ni" tayi maganar cikin
sauti mai ƙarfi, ta nufi cikin gida da sauri, kamar mahaukaciya sabon kamu.
Ta shiga ɗakinta, ta rufe ƙofa ta wulwula jakar hannunta
tayi jifa da ita, ta samu wuri ta zauna ta dafe kanta, da take jin tamkar zai
rabe biyu.
"Ya haiyyu ya ƙaiyyum, ya zuljalalu wal ikram"
take ta maimaitawa, tunanin ma ta rasa wanne yakamata ta yi.
Viper ya ƙular da ita, amma tafi jin haushin kanta, da ta
iya buɗe baki, ta furta tana son shi, a da ko me za ayi mata, ko da wasa ba ta
taɓa sakawa a ranta zata iya furtawa wani tana son shi ba. To saurayi ya ce
yana sonta ma, wahalar da shi take yi, ko da tana sonsa, saboda ta ja ajinta,
amma wai yau ita ta furtawa wani so, kuma yayi rejecting ɗin ta kai tsaye.
Viper yana da qualities ɗin da ya cancanci a so shi,
ba ta taɓa zaton wasan da take yi zai zama gaskiya ba, dan ita da fari
tsokanarsa kawai take yi, sai kuma matsanancin tausayin sa sa take ji, gashi
tausayi ya juye ya koma mata soyayya shi kuma baya ta tata, ga wannan tsohon
ciwon nata da ta fama. Zuwa yaushe Abba zai fuskanci gurbin ido ba ido bane ba,
duk wani abu da ya faru a baya, bata san an yi shi ba, ba ta san maman nata ba
dama wannan an tabattar mata da bata raye, to mahaifinta fa, komai lalacewarsa
zata so ta ga abun ta, kuma komai ya yi wa mahaifiyarta, wani abu ne da ya wuce
a baya, da ba ta nan ma aka yi shi, to na menene za a gadar mata da wani abu da
ba shi da tushe balle cikakkiyar makama.
Ta zabura ta tashi, ta watso drower littatafanta, ta ɗaukko
hotunan mahaifiyarta, cikakkiyar bafulatanar yarinya ce ba wata babba ba, fara
sol da ita mai dogon hanci, tayi ɗauri irin na mutanen da, ta zubo da dogon
gashinta ta ƙarƙashin ɗan kwalinta, har ka kafaɗarta, dukkanin hotunan uku,
fuskarta ɗauke da murmushi daga yanayin hotunan zaka fahimci ba ta da hayaniya,
kuma mai yawan murmushi ce.
Ta daɗe tana kallon hotunan tana kuka, ta gaji ta kwanta a
kan gado, sai ajiyar zuciya take yi.
Washegari da safe, ta shirya zata tafi wurin aiki, ta shiga
wurin Abba ta gaishe shi, amma ya shareta yaƙi amsawa, sai gajiya tayi, ta
tashi ta fita.
Ko da taje wurin aikin ma, kanta ta kifa a kan teburin
office ɗin ta.
Barrister Habib har yayi knocking ya shigo, ba ta sani ba,
sai da ya daki teburin, sannan ta ɗago.
"Nabila ya dai? Na ji program ɗin ki ya ɗau hankalin
mutane, ki zo a mayar da hankali wurin neman shaidu, kin shigo kuma kin zo nan
kina bacci"
Tayi shiru ba ta ce Komai ba.
"Wai meyafaru ne?"
"Ba na jin daɗi ne"
"Yasalam, sannu kuma kika fito? Kina da tiral ne
yau?"
"A'a, na zo ne dama mu cigaba da aikin shari'ar nan, ai
na sha magani, bari na biyoka office ɗin"
Tare suke aikin, amma sam hankalinta baya kan aikin, ƙarshe
ya ce, su bari sai ta samu sauƙi tukuna.
***
A wani wurin cin abinci saifu suka haɗu da Abdul, suka zaune
saifu ya ce "Mutumina harkar siyasar nan duk ta ɓoye mana kai, wurin
chilling ɗin ma duk ka daina zuwa. Hafsa ta ce tana son ta zo ta ganka, na ce
ko ta je asibiti baka zama, ayyuka sun yi maka yawa, asibitin ma ba wani zama
kake yi ba"
Yayi murmushin ƙarfin hali ya ce "Ya jikin nata?"
"Da sauƙi sosai Alhamdilillah, likitanta ma sun
sallameta, sun ce ta warke, ina ga wani abun ne yake damunta, ta ce kafi dubata
sosai, na rasa wani siddabarun kake yi wa patient suke liƙe maka"
"Saif, mu bar wannan maganar, akwai damuwa fa"
"Ta me?"
"Haryanzu babu labarin mahaifiyar yarinyar nan, gashi
kuma ta matsa mini, kullum cikin kuka take"
Saifu ya ce "Ai fa Abdul ka yi mugun ganganci abun da
ka aikata, ka mayar da ita wurin iyayenta, tun kafin asirinka ya tonu, sunanka
ya ɓaci"
"Saif, ni fa ba ta sunana ya ɓaci nake yi ko akasin
haka ba, ni wallahi burina kawai na cigaba da ratuwata da ita, wani irin abu
nake ji a kanta, da rabani da ita tamkar rabani da rayuwata ne"
"Kai Abdul, ba ka gama ɗibar abun da kake so ba, ko
haryanzu bai isheka ba?"
"Ba wannan nake yi wa ba, ita nake so, tun bayan da na ɗaukota
take bani tausayi, ka san ban taɓa raping ba, sai a kanta, wallahi son rahama
nake yi, so mai tsanani".
Cikin mamaki Abdul ya ce "Taɓɗijan, aurenka ne fa yake
gabatowa, yanzu yaya kenan, gashi ana ta fitina a kan ainihin wanda ya yi mata
fyaɗen, wata lauya ta kafe, sai an fito da ita ta bayar da shaida a kotu. Ina
ga fa dolenka ka gaya wa mahaifinka gaskiya, ya ɗauki matakin da yakamata a
rufe abun nan".
"Ina son gaya masa, amma ina tsoron abun da zai iya yi,
ba zai ɗauki maganar da sauƙi ba"
"To ai kuwa ko da yaya zai ɗauki maganar, haka ne kawai
mafitar"
Abdul ya yi shiru yana zancen zuci.
***
Viper yana zaune, ya tsurawa hoton jauhar ido, yana hararo
kamannin Nabila a cikin kansa.
Walid ya dafa shi, ya ɗaga kai ya kalle shi.
"Ya ake ciki ne? Mutuniyar kwana biyu, yakamata ace fa
shirye-shirye sun yi nisa a kan shari'ar ka, ta ina za a fara?"
Viper ya ce "Fushi take yi "
Walid ya ce "Fushin me? Wani abun ya faru ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Akwai magana a bakinta da
yakamata na saurara, wataƙila zai haska mini abun da kake gaya mini, sai dai ta
bijiro da abun da dole na taka mata burki"
"Wane abu ne?"
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Bakomai"
"Mai zamani, yakamata ka din ga bin komai a sannu, mata
fa dukkansu ba irin jauhar bane, jauhar one in million ce, ba kowace mace ce
zata iya juriyar da ta yi ba, kar ka yi treating ɗin Nabila yadda kake treating
ɗin Jauhar, suna da banbanci"
Yayi shiru, ya cigaba da kallon hoton hannunsa.
"Allah ya jaddada rahama a gareki, ya kyautata
makwancinki my wife " yayi maganar yana shafa haƙoranta na jikin hoton da
yake da shi da ita ne, fuskarsa da ƙuruciya sosai lokacin.
Walid ya ce "Amin" ya karɓe hoton, ya ajiye shi a
wani wurin.
Yayi shiru yana tunanin ko me Nabila take son ta gaya masa?
Ko yanzu tana wani hali? Da gaske son shi take yi, ko kuwa dai still da wasa
take yi? Kukan da tayi ya tabattar mata ba wasa take yi ba.
To su mata babu wuya sun fara son mutum kenan? Ya ga damuwa
sosai da sosai a cikin idanunta da suka haɗu, ya so ya ji menene damuwarta,
amma ta zo da lamari mai girman gaske, son da take yi masa wahalar da kanta
kawai zata yi, yana cikin wannan halin na ɓoye-ɓoye, idan ta fara son shi yaya
zata yi, tun da ba aurenta zai yi ba, kuma shi ba ma wannan ne a gabansa ba
gaba ɗaya.
***
Kusan kwanaki huɗu, amma Abba baya saurar Nabila, fushi yake
yi da ita sosai, gajiya tayi da fushin da yake yi da ita, ga habaici da yar da
magana da ake yi mata a gidan.
Ta shirya tafiya aiki, ta shiga ɗakinsa, ya na karyawa.
"Abba ina kwana" yayi mata shiru ya cigaba da
karyawa.
Ta tashi ta je gabansa ta zauna cikin kuka ta ce "Dan
Allah Abba ka yi haƙuri ka yafe mini, dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini, in
sha Allah ba zan sake maganar babana ba, idan raina ne ya ɓaci aka yi mini
gori, duk sai na ji babu daɗi amma dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini ba zan
sake ba" da fari yayi mata shiru, amma daga baya ya numfasa ya shafa kanta
ya ce "Kukan ya isa haka, na ji na yafe miki, duk da kin sha yi mini
wannan alƙawarin amma ba kya cikawa, yau da mahaifinki wani abun kirki ya
tsinanawa mahaifiyarki, rabuwar arziki aka yi, babu yadda za ayi na nesanta ki
da shi har haka, na yanke duk wata alaƙa tsakaninki da shi. Ki yi haƙuri na san
kina haƙuri da abun da ake yi miki, da zarar kin yi aure shikenan kin wuce
wurin, ki yi haƙuri ki cire maganar mahaifinki a zuciyarki"
Nabila ta jinjina kai, amma ƙasan zuciyarta ba ta ji zata
iya daina maganar mahaifinta ba.
Ta tashi ta fita ta tafi aiki, ita ma ta fita daga harkar
Nasir gaba ɗaya.
Yau ba ta da shari'ar da zata halatta, dan haka tana office
tana ta nazarin shaidunta, da za su yi appeal.
Wayarta ce tayi vibrating, ta ɗaga ta duba "Mu haɗu a
restaurant ɗin da ki ka je, zamu yi magana mai muhimmanci" ta zubawa wayar
ido tana kallonta, ta ajiye wayar. Har mamakin kanta take yi, yadda take abu
babu tsoro take wannan kasadar haka.
Ta ajiye wayar ta kifa kanta, can ta miƙe, ta tattara system
ɗin ta da kayanta, ta tashi ta fito, suka yi karo da barrister Habib.
Ya ce "Yauwwa wurinki zan zo dama, ina son mu je
unguwar da abun nan ya faru ne, ko da wani abu da zamu kuma samu, da bamu haske
a kan shari'ar"
Ta ce "Amm ganin likita zan je ne, ko mu bari sai gobe
in Allah ya kaimu?"
Ya ce "Subhanallah, jikin ne dai?"
"A'a ba wani abun damuwa ne sosai ba, zan dai je na ga
likita ne, yau yakamata na koma dama"
"Ok, to Allah ya ƙara afuwa"
Ta amsa da Amin.
Ta je wurin cin abincin, ta kira wayarsa ya ɗaga.
"Gani na zo ina wurin"
"Ki miƙe sosai ciki, ki tambayi Vip 2" ta ƙarasa
ta tambaya, aka nuna mata, ta buɗe ta shiga.
Yana zaune, ya ɗora ƙafafuwansa a kan tebur, yana sanye da
facemask da facing cap ya rufe fuskarsa.
Fuskarta babu annuri, ta ƙarasa ta ja kujera ta zauna, ta
ajiye jakarta da wayarta, da mukullin motarta, amma ba ta ce komai ba.
A yanayin yadda ta tafi wancan karon, bai zaci da ya ce ta
zo zata kuma zuwa ba.
Tayi masa shiru, tana danna ƙaramar wayarta.
Ya ɗan daki teburin ya ce "Attention, magana zamu
yi"
Ta ajiye wayar ta ce "Ina ji"
Ya ja babbar wayarta, ya buɗe ya ɗaukko tab ɗin sa, ya fara
daddanawa.
Mai kawo abinci yayi knocking, ya kawo ruwa da lemo.
Ya sauke facemask ɗin sa ya ce "Yaya ake ciki da
maganar wancan case ɗin, zuwa yaushe zaku yi appeal ɗin? Sonake ki kammala da
wancan shari'ar, sannan ki mayar da hankali a kan tawa, already ina da shaidu
guda biyu a ƙasa" har yayi maganar ya gama, bata ɗago ta kalleshi ba, wasa
kawai take yi da zobunan hannunta.
"Magana fa nake yi"
"Ina ji ai"
"Ba jin nake buƙata ba, hankalinki zaki bani" iya
idanunta ta ɗaga ta kalleshi tana yi masa wani irin kallo.
"Ina magana a kan yaushe zaki yi appeal, ki zo ki fara
processing tawa, ina da shaidu biyu a ƙasa" still ba ta ce komai ba ta
cigaba da kallonsa.
Zubawa sarautar Allah ido yayi, ya saka mata nasa idon shi
ma, ta gyara zamanta, ta kwantar da hannunta a kan teburin, ta ɗora kanta ta
kwanta ta yi masa shiru.
Ƙasa yayi da muryarsa ya ɗan matsa ya ce "Meyake
damunki ne?"
Kawai ta fashe da kuka, yayi mata shiru, tayi iya yin ta, ta
ɗago ta share hawayenta ta ɗauki jakarta, ta ɗauke wayarta daga gabansa, ta
juya za ta fita.
"Ina miki magana zaki tafi? Ina zaki je ina yi miki
magana?" Yayi maganar cikin tsawa da sai da ta firgita, ta ja da baya tana
kuka.
"Talk" yana mata tsawa tana ƙara sautin kukan
nata.
"Meyake damunki? Kin san haka zaki yi mini, ki ka yi
mini tayin dawowa normal rayuwata? Ki ka ce zaki taimaka mini"
"Ina amfanin tarayya da mutumin da kansa kawai ya sani
kuma yake so? Ba cewa kai baka so na ba? Rashin amsa tayina bai yi mini ciwo
ba, irin halin ko in kula da ka nu na wa rayuwata, hakan na nufin duk da risk ɗin
da na saka rayuwata baka damu ba ko da zan rasa rayuwata. Saboda kana ganina a
haka do you know what am going through ne? To an fasa taimakon naka, i destroy
the deal and i am out of it, ka je kayi duk abun da ka ga dama"
Murmushi ya yi, sai da haƙoransa suka fito, abun da ba ta taɓa
gani ba.
"Angry bird, always angry for no reason, duk saboda na
ce bana sonki, ki ke wannan abun? Ba zan taɓa sonki ba, zuciyata ta jauhar ce
itakaɗai"
"Ai baka burgeni ba, da aka zauna baka bi ta lahira
ba"
Viper ya ce "Ai nayi niyyar bin nata, ki ka hanani,
wannan deal ɗin sai an kai ƙarshensa da ke"
"Komai zaka yi, ba zan sake zuwa in da kake in dai ni
yar halak ce, babu amfani tarayya da mutumin da kansa kawai ya sani" ta raɓa
shi ta wuce ta bar wurin.
Ajiyar zuciya yayi, ya koma ciki ya zauna.
Gida ta tafi, abun duniya duk ya dameta, tana ganin kiran
sumayya, amma ta share ba ta ɗagawa, gaba ɗaya ta zama so silent.
***
Abdul ne yake kallon ramma, yadda take ya shiri, ya ce wai
shirin me ki ke yi haka ne?
"Asibitin ka zaka tafi da ni, ni dai mu je ka duba ni
na tabattar"
"Rahama haryanzu tunaniki ƙarya nake yi kenan?"
"To wa ya sani, tun da haryanzu ban ji na warke ba,
amai yaƙi tsayawa, muje idan ma shi ne kawai ka zubar da shi"
Ya girgiza kai ya ce "A'a ni ba na zubar da ciki
gaskiya"
Ta kalleshi sheƙeƙe ta ce "Yaushe ka fara tsoron Allah,
har ka ke cewa ba ka zubar da ciki?"
"Ai lokacin da zan kama aiki, rantsuwa nayi, ba zan ci
amanar aikina ba"
"Kai har wata darajar rantsuwa ka sani? Ni ka daina yi
mini wasan kwaikwayon nan, kawai mu tafi"
"Rahama mutuwa fa aka yi a wurin zubar da cikin
nan"
"Na ji, bakomai, Allah ya yi mini rahama".
Ya sauke numfashi ya ce "Na ji, zamu je, amma wallahi
ki ka takura mini ba zamu je ba, kuma kar ki dame ni"
Ta haɗe rai ta ce "Zan baka nan da sati ɗaya, idan na
ji shiru zan kuma magana" ta cire mayafinta, ta bar ɗakin.
***
Unguwar gidan aikin ramma take son sake zuwa, kamar yadda
barrister Habib ya buƙata, take ta yi masa yawo da hankali.
Tana daf da shiga mota, ta tsaya tana amsa kiran waya.
"Salamu alaikum, Barrister, walid ne"
Ta ce "Oga walid, ya kake?"
"Lafiya ƙalau, mutumin ne babu lafiya fa, ko zamu haɗu
a wani wurin mu kai shi asibiti a motarki, saboda yanayin tsaro"
Gabanta ya faɗi ta ce "Subhanallah, wani abun ya je ya
sha?"
"A'a, ai rabon da ya sha wani abu, an kwana biyu, ciwon
ciki yake yi, tun yana yi sama-sama, tsakanin jiya da yau har suma yake
yi"
A rikice ta ce "Ya salam, a ina zamu haɗu to? Ina wurin
aiki gani nan"
Da gudu gudu, ta ƙarasa ta hau motar, ta ja, tana tafe tana
waya da su, har suka haɗu, sun ɗaukko shi a adaidaita sahu.
A sume suka saka shi a motarta, hankalinta yayi mummunan
tashi ta ce "Oga walid yana numfashi?"
"Eh yana yi, Suma dai yake ta yi"
"Yanzu wane asibitin zamu nufa? Ka ga wancan ga
matsalar da aka samu"
Suka tattauna suka yanke shawarar kai shi wani asibitin
daban.
Asibitin shi ma a wajen gari yake, amma yayi kyau ya tsaru,
ko ina tsab da shi.
Nan da nan aka shiga da shi emergency, aka fara yi musu
tambayoyi a kan meyasame shi.
Su walid suka yi musu bayani, aka tafi da shi wurin yin
scanic.
Nabila ta fita da sauri, dan ta je ta ji ya tsarin Asibitin
yake, da biyan kuɗin, taga ɗan mama yana ƙoƙarin komawa in da ya baro su.
Ta ce "Sannu ɗan mama"
Ya ce "Yauwwa, an gano meyake damun nasa?"
Tayi murmushi ta ce "Suna ƙoƙarin yin hakan dai, wannan
karon ma ka je ka sanar da su ne su zo su biya bills ɗin asibitin nasa?"
Yayi turus yana kallonta, ya ce "Kamar yaya?"
"Kamar yadda wancan karon kayi, kai ka yi waya aka biya
bill ɗin Viper, dan babu wanda ya san mun je asibiti, yanke muka din ga yi, mu
ƙaddara ma wani ya sani yana bibiyarmu, ana tsaka da treating ɗin sa hankalinmu
yana kansa, ka zame ka fice. Kana kawo masa miyagun ƙwayoyi a duk lokacin da ya
buƙata, abubuwa da yawa idan ba na kusa da shi ba babu yadda za ayi a san su,
wa ka ke yi wa aiki?"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Ɗan mama yayi murmushi, ya ƙara taku biyu gabanta, ya
kalleta ya ce "You better count yourself out of this. Ba ni da niyyar
cutar da Viper, da cutar da shi zan yi, da tuni na yi so bakinki ƙanin
ƙafarki" daga haka ya miƙe ya nufi in da suka baro su walid.
Aka fito da Viper a kan gado, aka ce za a ba su ɗaki, za a
turawa likita result ɗin.
Kamar yadda Nabila ta yi tsammani, an biya bills ɗin, ta din
ga yi wa ɗan mama kallon tuhuma, shi kuwa da sun haɗa ido, sai yayi mata
murmushi, hakan ya ƙara jefata cikin tunani.
Likita ya shigo da file a hannunsa, suka sake gaisawa, ya
tattaɓa cikin Viper, sai dai duk da an yi masa allurai ya samu bacci, da ya taɓa
cikinsa ɓangaren dama, sai da ya zabura ya motsa.
Ya duba scanic ɗin hannunsa, ya ce "Hantarsa ce ta
kumbura gaskiya, amma ƙodojinsa da sauran abubuwa lafiya ƙalau, amma duk da
haka zaku yi x-ray na cikin, mu sake tabattarwa ko da wani abun"
A tsorace Nabila ta ce "Likita hantarsa ta kumbura
kuma?"
"Eh, amma karki damu babu wani abu in sha Allah, idan
aka yi x-ray ɗin, akwai likitanmu da zai zo ya duba shi, ba wani abun tayar
hankali bane ba, zai samu sauƙi in sha Allah"
Walid ya ce "Allah ya sa"
Ɗan mama ya ƙurawa wayarsa ido, sannan ya kalli Nabila, yayi
mata alama da su haɗu a waje.
Ya tashi ya fara fita sannan ta bi bayansa.
Ya ce "Ana bibiyarki, yanzu aka turo mini saƙo, zaki
bani mukullin motarki, zan kawo miki ita gida a matsayin bakanike"
"Nifa ban fahimci duk wannan abun ba"
"Tsayawa dogon bayani, ba zai haifar da ɗa mai ido ba,
ki ga gaggauta muje na raka ki, na ɓulla da ke wata hanyar ki hau napep ki tafi
gida, zan kawo miki motar gida".
"Kamar wani abun kake shiryawa a kaina" ya miƙa
mata wayarsa, ta karɓa ta duba, message aka turo masa aka yi masa bayanin kar
ta tafi a motarta, akwai yiwuwar a kamata, ko kuma ayi mata wani abu.
Bai bari ta yi wa su liti sallama ba, ya fitar da ita daga
asibitin, ya tare mata abun hawa ta hau ta tafi tana mamaki.
Ta koma gida, duk a gajiye, abubuwa duk sun dame ta, tana ta
tunanin ciwon Viper, tayi ta addu'a Allah ya bashi lafiya, sai ta ji ba ta
kyauta ba maganganun da ta gaya masa, haɗuwarsu ta ƙarshe.
"Allah ka bashi lafiya, ka bani ikon cika masa
alƙawarin da nayi masa"
"Arfa"
"Na'am" ta amsa tana daga zaune.
"Ina motarki?" Nasir yayi maganar yana shigowa
cikin ɗakinta.
"Lalacewa ta yi, na bawa bakanike"
"Wane bakaniken?"
"Bakanike dai mai gyara mota"
"An ce an ganki da wasu maza a motar, a can ring road,
sai dai ba a san in da ku ka yi ba, na saka jami'ai a arear in da ake tunanin
kin bi, aka kama wani da motar yanzu haka yana tsare a wurina"
Ta miƙe tsaye ta ce "Wai dan Allah yaya me kake nufi da
ni ne? Motata ta lalace zan yi gammo na ɗauketa a kaina ne, na kira masu gyara
su tafi da ita sai ya zama laifi, na menene zaka saka a din ga bibiyata
ma?"
"Saboda baki da gaskiya arfa, gaba ɗaya kin canza, kuma
ba kya tsoron salwantar da rayuwarki"
"Kalli, kamar da gaske ka damu da rayuwar tawa, ba ta
rayuwata kake yi ba, mafitar ka kawai kake nema Yaya Nasir, amma ai ramin ƙarya
ƙurarre ne ka cigaba da bibiyata. Na roƙe ka ka saki bawan Allah, gyaran mota
kawai na bashi, abun arziki bai kamata ya zama na tsiya ba" ta fita daga ɗakin
gaba ɗaya ta bar shi.
Da daddare ta kira walid, ta ji ya jikinsa, ya tabattar mata
jiki da sauƙi sosai, ya farka ma.
Nabila ta ce "Oga walid, shaye-shayen nan ne fa ya fara
taɓa shi, ya janyo masa wannan matsalar"
"Ai bama sai kin faɗa ba, shi ne ba wani abun ba"
"Dan Allah oga walid ku daina wannan rayuwar, idan ba
haka ba da ƙuruciyarku haka zaku rasa lafiyarku ku mutu, dan Allah" yayi
murmushi ya ce"Karki damu, za a daina in sha Allah"
"Allah ya sa, ayi masa sannu dan Allah"
Ya ce "Zai ji in sha Allah" bayan ya kashe wayar,
ya fita yana mitar ina ɗan mama ya tafi har wannan lokacin bai dawo ba.
A harabar Asibitin ya haɗu da ɗan mama, kamar ya kwaɗe shi,
dan haushin abun da yayi, shi kuma bai gaya masa ainihin abun da ya faru ba, ya
ce masa wani wuri yaje.
"Ka wuce ka je ka zauna da shi, liti ya je nemo wani
magani, ni kuma zan je gida".
"Kar ka je gidan nan oga Walid, hanya babu kyau,
cinnakun nan sun ɗana mana, akwai wani abu a ƙasa ka ɓad da sahu, ka lafe a
wani wurin, akwaisu sosai a hanyar gidan nan"
Walid ya ce "Na fahimta, muddin kaga wani abu da baka
yarda da shi ba, ka kira sanar mini" ya jinjina masa kai.
Nasir yana zaune ya gama cin abincin dare, aka kira shi a
waya.
Ya ɗaga a take, ganin daga office ɗin su ne.
"Yallaɓai yaron nan fa, wasu sun zo sun yi
belinsa"
"Wane yaron?"
"Wanda muka kama, kuma sun ɗauki motar ma"
Tashi tsaye yayi ya ce "What? Meyasa ku ka bari suka ɗauka?
Waye ma ya ce a sake shi?"
"Manyanmu ne yallaɓai" mukullin motarsa ya ɗaukko
ya fito da sauri, kawai ya tarar da motar arfa a gareji.
Bin motar ya din ga yi da kallo, dan ya tabattar ita ce, ko
ba ita ce ba. Bai haƙura ba sai da ya dangana da zuwa ya dudduba ya tabattar
dai ita ɗin ce.
Bai tsaya ba, ya shiga cikin gidan, ya tarar da ita a falo,
suna kallo a falon ita da mutanen gidan.
"Arfa waye ya kawo miki motarki?"
"Ina ga bakanike ne, yaro ne ya kawo mini key ya ce an
kawo motar" tayi maganar cikin ko in kula.
Ganin da mutane a wurin, ya sanya bai ja maganar ta yi tsawo
ba, ya bar falon.
***
Liti yana zaune yana game a wayarsa, likita ya shigo, ya
kalli likitan, likitan ya ce "Sannu ko, ya mai jikin?"
"Da sauƙi"
"Masha Allah, naga ya samu bacci ma, shi ne mai
hepatitis ko? Yayi maganar yana duba file ɗin Al'amin. Kodayeke ma bacci yake
yi, bari ba sai an tashe shi ba, idan aka yi x-ray ɗin na duba shi, idan ya
farka gaba ɗaya" yayi maganar yana taɓa cikin Al'amin. Sai dai yayi shiru
yana kallon Viper, yana ƙoƙarin ganin fuskarsa sosai, dan kamar ya san shi, sai
dai yanayin kwanciyar da ya yi, bai bashi damar yin hakan ba.
Ya kalli file ɗin Al'amin, an rubuta Muhammad Ibrahim. Ya
juya zai fita, ya tsaya ya sake waiwayowa ya kalli Al'amin ya ɗan yi shiru
sannan ya fita.
Yayi iya ƙoƙarin sa wurin tuna a ina ya san shi, amma ya
kasa dan haka dolensa ya haƙura.
***
"Rahama"
"Na'am"
"Zan fita da ke, zamu je asibiti, wallahi idan ki ka yi
misbehaving, ke da ganin mahaifiyarki har abada"
"Idan da zan yi misbehaving, da tuntuni da kake fita da
ni da nayi, amma na fara gajiya da ƙaryar da kake yi mini, na cewa gwargwadon
bin umarninka da nake yi, shi zai sanya ka sada ni da mahaifiyata. Ina tsoron
tonuwar asirina na wulaƙanta a idon duniya, shiyasa bana yi maka ihu, da neman
agaji, sonake ka mayar da ni cikin sirri da rufin asiri, yadda ba zan tozarta
da yawa ba, amma haryanzu na kasa gane in da ka dosa"
Ya ce "Zaki fahimta ne, muddin ki ka yi yekuwa, to ke
zaki kunyata fiye da ni, kuma ni zan iya wanke kaina, ke kuwa zaki tozarta, dan
sai kin samu masu ɗoraki a social media kowa ya ganki, kin san duk abun da
namiji yayi ado ne"
Ta girgiza kai ta ce "Wannan wani banzan tunani ne, na
waɗanda ba su san girman Allah ba, babu al'ada a batun saɓon Allah. Allah bai
ware wutar mace ba, kuma bai ware ta namiji ba, bai ce zai sassautawa wani ba
dan yana wani jinsi idan ya saɓa masa ba, dan haka babu ado da zunubi, idan
al'ada ta nuna maka duk abun da ka yi ado ne, addini kuma ya koyar da kai
tsoron Allah da tsoron azabarsa"
Wato ramma akwai baki, wasu lokutan duk abun da yake ji da
shi, sai ta ƙure shi ta hanyar kafa mishi, hujjoji da addini, dan haka ya ja
bakinsa yayi shiru, suka cigaba da shiri.
Tana sanye da niƙab, a kan dogon hijjabinta, yake nuna mata
wurare a cikin asibitin, wai nan ma branch ne na Asibitin, ba shi ne main
branch ɗin ba, sai dai yayi kyau ya tsaru sosai da sosai.
Washegari da safe Nabila ta je court ɗin da take da trial,
tayi ta kammala, ta samu wurin parking, ta bayar da ajiyar motar, ta hau napep
ta fita asibiti.
"Ki zauna a nan, zan je na fara zagaywa na duba marasa
lafiya na, sai na zo na tafi da ke, in da zan duba ki"
Ta kalleshi ta ce "To ka tafi da ni mana, ni ba wani
abun zan yi ba"
"So ki ke sai wani ya ganki wai?"
"Matsalar rashin gaskiya kenan"
"Eh na ji, ga kayan tea nan, fridge akwai lemuka, ga
kayan kallo nan, ki yi duk abun da ki ke so, ban da fitina, zan rufe ki a nan,
zan je na ga marasa lafiya, sai na yi ward round na dawo"
Ta ce "Saura ka daɗe"
Abdul ya ce "No ba zan daɗe ba in sha Allah" yayi
kissing goshinta ya ce "I love you, ki yi mini addu'a na yi komai cikin
nasara"
"To jeka, kar su gaji da jiranka" haka kurum ya
din ga jin is no safe, ya bar ta nan, kamar wani abu zai faru, ya din ga
waiwayawa yana kallonta, har ya fita ya rufeta a wurin.
Nabila ta shiga cikin Asibitin, tana saanye da hijjabin da
ta ɗora a kan uniform ɗin ta da facemask, sai waya take yi, tun da ta taho,
wata matashiya da ita ma tahowa take yi, suna facing ɗin juna, take bin ta da
kallo. Ji take yi, tamkar ta je ta ɗage facemask ɗin fuskar Nabila taga wacece,
har ta wuce hanyar da yakamata ta tabi.
Wayarta ce ta fara vibrating, ta ɗaga ta ce "Hello
yaya"
"Dalla malama kina ina, gashi ya zo, zai fara ganin
marasa lafiya, ki zo ya fara da ke na mayar da ke gida, amma kin tafi
yawonki" kasa bashi amsa tayi, ta ɗaga kai tana dube-dube, ta nemi Nabila
ta rasa.
Jiki a sanyaye ta shigo office ɗin, saifu kamar ya mareta ya
ce "Wai ina ki ka tafi, yazo ya zauna yana jiranki?" Bata amsa ba, ta
zauna jiki a sanyaye.
Abdul ya ce "Dan Allah ka daina yi mata tsawa, ka san
mara lafiya ce, ba na son naga ana kyarar mini patient, Hafsat ya aka yi
ne?"
"Doctor Abdul, jauhar fa na gani ta saka niƙab ta
wuce"
Ya ce "Wacece haka?"
Saif ya ce "Na fuskanci ba ta warke daga depression ɗin
nan ba, likita ya sallameta, ƙanwarmu da ta mutu fa take magana a kai"
"Wallahi yaya, ka taso mu bi hanyar da ta bi, ka ganta
kaima, ta saka niƙab"
"Kuma da niƙab ɗin ki ka ga jauhar ce?"
Ta ce "A'a, gani nayi kamar na santa, kuma wallahi irin
idonsu ɗaya, ai naga idonta"
Abdul ya yi murmushi, ya fara bin hanyoyin su na likitoci,
wurin daidaita tunanin hafsa, da saka mata nutsuwa.
Nabila tayi sallama. Al'amin yana zaune, ya jingina da jikin
gadon, yana ɗan yamutsa fuska.
Suka gaisa da ɗan mama, shikaɗai ne a wurin, ta ƙarasa
gabansa ta ce "Sannu ya jiki?" Ya jinjina mata kai alamar da sauƙi.
"Kaga ɗaya daga cikin illar shaye-shayen miyagun
ƙwayoyi ko? Kodayeke zuwa yanzu ai ba illa ɗaya ka gani ba, illoli daga dabar
shaye-shaye da bangar siyasa wanne yayi maka rana a cikinsu? Daba da bangar
siyasar a dalilin su, ka rasa makusantanka, ka rasa soyayyar mahaifi da ta ƴan
uwa, illar da aka yi maka, ka kasa karɓar ƙaddararka, ta'amalli da miyagun
ƙwayoyi ya sanya, ka nemi ka rasa imaninka, ka halaka kanka, yanzu gashi
lafiyar ka ta taɓu, gaba ɗaya abubuwan nan babu wanda zaka ɗaga na ce ga ribar
da ka samu a dalilin su, dan Allah ka cikawa yar madara burinta, duk da bata
duniya, ka zama mutumin kirki, ka zame mata sadaƙatul jariya, ya zamana bata
raye, amma tana da kamashon ayyukan alkhairin da zaka yi idan ka zama mutumin
kirki, tun da ita ta ɗaukko hanyar saita rayuwarka bisa hanya mai kyau"
kamar ba zai yi magana ba, sai ya buɗe idonsa ya zuba mata ido.
Ita ma shi take kallo, amma ta yi ƙoƙarin janye nata idanun
daga nasa.
Ya zuba mata ido kamar zai haɗiyeta, hatta maganarta wani
abun idan tayi, kamar Jauhar.
"It all depends on you" ya furta yana cigaba da
kallonta.
Ta ɗago ta kalleshi, "Ke zaki ƙarasa abun da ta yi
niyyar yi, ta hanyar cika mini alƙawarin da ki ka yi mini. Na gode da ki ka
taimaka mini, ban rasa imanina gaba ɗaya ba, tabbas a duniya daba da
shaye-shaye basu tsinana mini komai ba, sai asara kashi-kashi wata na bin wata.
Abu ɗaya nake fata, ko da ba zan rayu ba, naga an hukunta wanda suka kashe mini
mata ba tare da hakkinta ba, shi ne babban fatana, ke ki ka cusa mini
aƙidar in ɗauki mataki ta hanyar shari'a ba hanyar da nake so nake ganin ita ce
dai-dai ba. Ba wai ina roƙonki bane ba, kina da zaɓin yin abun da ki ke ganin
shi ne dai-dai a gareki"
A ƙasan zuciyarta ta ce 'Ai ba zaka canza ba"
Kiran sumayya ta gani a waya, ta ajiye ledar kayan marmari
da ta shigo da su, ta fita amsa waya.
Ba ta san dalilin kiran sumayyan ba, dan haka ta nemi hanyar
da zata nesanta ta, da wurin shige da ficen mutane.
Tabi wata hany, ta ɓulla wani wuri da babu kowa, ta tsaya a
wurin ta ciro wayarta ta ɗaga ta ce "Hello, Sumayya T ladan baki abun
magana, maƙogwaron kakaki radio".
Gaban ramma ya faɗi, jin muryar mace a wurin office ɗin,
sunan wadda aka ambata ne ya daki zuciyarta, Sumayya T ladan, tana jin program ɗin
ta, sai dai a rufe take a cikin office ɗin babu hanyar fita.
"Ba shakka Nabila Yusuf maitama, ni kike kira da ni da
sunan ubana ko?"
"To ai kin rama, ya ne ya ake ciki, ya gidan radio?.
Abdul ya shiga ɗakin da Viper yake, da shi da wata Nurse da
take on duty.
Ya kalli ɗan mama ya ce "Ina mara lafiyan?"
Ɗan mama ya ce "yana banɗaki"
Ya ce "Ok, sister je ki room 4 ki duba mini temperature
yaron nan, kafin na zo" ta ce "Ok sir"
Ya tsaya yana dudduba medication ɗin da aka yi chatting, ya
juya baya yana amsa waya Viper ya fito, ya nemi wuri ya zauna a kan gadonsa, ya
gama amsa wayar ya juyo, idonsa suka shiga cikin na Viper.
Ƙiris ne ya rage bai yar da wayar hannunsa ba, an kusa
shekara bakwai rabonsa da Viper, tun wata haɗuwa da suka yi, ya zo hutu suka
kusa faɗa P.A ya gargaɗe shi a kan hakan, Viper ya ƙara girma, kwarjini ya ƙara
baibaiye shi.
Shi bai san abun da ya faru ba, shi dai ya daina ganinsa a
wurin mahaifinsa, ya ji labarin kisan kai yayi, aka rufe shi, sai kuma yaji
mahaifinsa yana nemansa, kasancewar shi ba mai shiga abun da babu ruwansa bane
ba, sam bai damu da sai lallai ya ji meyake faruwa ba.
Da ido Viper ya yi wa Ɗan mama magana, ɗan mama ya taso, ya
zo, Abdul bai gama tunanin ba, Viper ya zare wuƙar da ke ƙugun ɗan mama, ya
fuzgo labcourt ɗin Abdul, ya zauna a gabansa. Ya kalli ɗan mama ya ce "Ka
gindaya katanga, ba shiga babu fita" ɗan mama ya jinjina kai ya fice, ya
rufe su ta waje.
"Ka yi mamakin ganina ko? Nima mamakin ganinka nake yi,
haka mahaifinka ya adana rayuwarka, ni kuma ya tagayyara tawa, ya bar ni da
yawon ramuka ina ɓoye kaina, tamkar maciji, kodayek macijin ne ni, ina nan zan
yi fitar burtu daga ramin, zan yi masa sara mafi muni, da zai yi ajalinsa"
"Da mahaifina kake yi, ni meye nawa a cikin abun da ya
haɗaku?"
Viper ya saka masa kaifin wuƙarsa a jijiyar wuyansa ya ce
"Kai likita ne, na san ka san ma'anar wannan jijiyar, kuma ka san mai
hudata yake nufi ga rayuwar ɗan adam, idan ka yi wani yinƙuri da bai gamshe ni
ba, zan yi wa jininka magudana zuwa doron duniya. Ya saka hannu ya ciro wayar
Abdul daga gaban labcourt ɗin sa, ya ce masa "Buɗe ta"
Ya karɓa ya buɗe masa, Viper ya karɓa yayi danne-danne a
ciki, sannan ya miƙa masa ya ce "Gashi nan, zan tura masa saƙo mai
muhimmanci ta hanyarka, kafin nan ka gaya masa, zan cigaba da farautarsa babu
dare babu rana, sai na ɗaiɗaita farincikin sa, ni ƙarfen cikin wuta ne, hannun
da yake ƙoƙarin sakawa dan ya kamani, idan nayi masa illa, sai ya nakasa,
nakasa kuma ta har abada. Ƙarfen da yayi yinƙurin yin amfani ya ɗaukko ni,
wutar tayi masa zafin da na riga na narka shi, ba kowane irin ƙarfe ne zai ciro
ni ba. yana gama maganar ya hankaɗa Abdul da hannu ɗaya, sai da ya faɗi ƙasa.
Nabila kuwa babu yadda ba ta yi ba, ta shiga, ɗan mama ya
hanata, ya ce likita ne yake duba shi, ya ce su fito waje.
Ita kuma ga sumayya na jiranta, tana ta tuna mata lokacin
program ɗin su ya kuss, ga barrister Habib yana ta kiranta shi ma, dan haka
kawai tayi masa sallama, ta ce za suyi waya.
Ɗan mama ya ce "Jiya bayan fita ta da motarki yayanki
da kansa ya kama ni fa"
"Ina ta son na yi maka magana, ya aka yi kuma ya sake
ka".
"Waɗanda nake yi wa aiki ne suka karɓo ni, na kawo miki
motar ki gida, na bayar da mukullin aka kai miki ciki"
Nabila ta ce "Suwa ka ke yi wa aikin kenan?"
"Ai sauri ki ke yi, kuma ya saɓa dokar aikin da nake
yi, ki kula sosai yayanki tarko yake yi miki ko ta ina, siled mistake zai iya
kama ki" ta ɗan yi shiru sannan ta jinjina masa kai ta ce "Na
gode"
Cikin ɗakin kuwa da sauri Abdul ya tashi, ya shafo wuyansa
da wuƙar Viper ta fara yankarsa, ya ga jini, ya ja da baya a hankali yana
kallon Viper, ya nufi hanyar fita ya jijjiga ƙofar da ƙarfi, ɗan mama ya buɗe,
ya fice cikin matsanancin hanzari, ɗan mama kuma ya shiga.
Wuyansa ya cigaba da tsatstsafar da jini, ya fita gate wurin
security, ya ce su hanzarta, su shiga amenity 2, su kama wanda yake cikin ɗakin,
babban ɗan ta'adda ne, da jami'an tsaro suke nema" nan da nan suka tashi
da gudu, suka yi cikin Asibitin.
Ma'aikatan suka ce, ya tsaya ayi masa treatment ɗin wuyansa,
ya ce musu a'a, ya je ya buɗe Office ɗin sa, ramma na ciki ta kwanta a kan
couch ɗin ɗakin tana bacci, ya danƙota daga kan kujerar, sai da ta razana, ya
fita da ita da sauri, ta ce "Abdul lafiya kuwa? Menene wai?"
"Akwai matsala ne" ya faɗa lokacin da ya sakata a
mota ya rufe.
Suna tafe a hanya ta ce "Meyasame ka a wuya ne? Wai me
yake faruwa?"
"Wani patient ne mahaukaci, ya yanke ni a wuya"
Cikin tausayawa ta ce "Subhanallah, sannu Allah ya
sauwwaƙe, kuma baka tsaya ka saka magani ba"
"Bakomai, idan muka je gida na saka"
Security kuwa suna zuwa suka tarar da ƙofar ɗakin a buɗe
hanhai, sai dai babu kowa a ciki.
Suka dudduba har cikin banɗaki, amma babu kowa.
Suka je suka rufe gate, aka hana kowa shiga da fita, tuni
aka sanar da jami'an tsaro, Viper kuwa da ɗan mama tuni suka dire katanga, ya
kira su walid ya ce kar su dawo, asibiti babu lafiya, Viper ya haɗu da ɗan
gidan indabo.
Liti ya ce "Maganar banza kenan, kuna daidai ina mu zo
mu same ku?"
Viper ya ce "Ba sai kun zo ba, zamu zo mu same ku"
Sai da ya kai ramma gida, ya zauna ya yi wa kansa dressing,
aka kira shi a waya, aka ce ya je yan sanda za su ɗauki report ɗin abun da ya
faru.
"Kai ba zan sake dawowa wurin nan a yau ba, sai an
tabbatar da security wurin"
Ɗan sanda ɗaya ya karɓi wayar, ya ce "Doctor, to ko
zaka gaya mana wani ɗan ta'addan ne?"
"Aminu Viper ne, wands ake cewa mai zamani da".
"Mai zamani kuma, yallaɓai Viper fa"
"Eh shi fa"
Ɗan sandan ya ce "Ok to" Nan da nan suka kira DSP
Nasir a waya suka sanar masa.
Nabila bata san abun da yake faruwa ba, ta ƙarasa gidan
radion su sumayya, sai da suka yi faɗa da sumayya, saboda lokacin shirin ya ɗan
ja sosai, sai itakaɗai ta fara program ɗin.
Sai da ta nutsu, suka gama faɗan dai-dai lokacin aka dawo
daga talla, sumayya ta gabatar da ita suka ɗora da program.
Yau ma dai program ɗin na su, a kan abun da ya shafi harkar
shari'a ne, kanta tsaye take bayyana ƙulle-ƙulle da rashawar da ta yi katutu a
harkar shari'a.
Nan ta tabattar da cewa zasu yi appeal, a kan shari'ar
ramma, kuma tana fatan hukumar shari'a zata sanya ido sosai a kan yadda
shari'ar zata gudana.
Sumayya ta ce "Yanzu dai kina da hope kenan, a kan
appeal ɗin da zaku yi?"
"Sosai kuwa sumayya, kuma ina nan a kan bakana,
lauyoyin gwamnati da bunkure foundation su gabatar da victim a gaban kotu, kuma
ina da kyakykyawan fata a kan wannan shari'ar, sannan bayan haka akwai tarin
ƙulle-ƙulle da zan warware a wannan zaure, masu tarin ban mamaki"
"To shikenan, da ni da masu sauraro muna dako, duba da
yanayin lokaci, baki samu shigowa da wuri ba, da haka da haka nake cewa muna
nan muna saurarenki, domin jin wane irin ƙulli zaki warware mana.
The lady of her words, the young capacitated barrister,
gugan ƙarfe sha kwaramniya iron lady, kuma boss lady, voice of voiceless
Barrister Nabila Yusuf maitama ayi sallama da masu sauraro"
Dariya Nabila ta din ga yi ta ce "Kirarin nan naki
dariya yake bani Sumyya, ai ke ce voice of voiceless, baki abun magana, a sayar
da a tsage gaskiya, the lady of the century Sumayya T ladan, Allah ya ƙara
kiyaye mana ke, masu sauraro Assalamu alaikum" suka ƙarƙare shirin cikin
nishaɗi da dariya.
Tuni Nasir ya isa asibitin, ya fara investigation, aka ɗaukko
masa file ɗin Viper da aka buɗe, sai dai babu lambar waya a jiki, ya ce meysa
babu lambar wayar mai file, record suka ce, emergency aka buɗe file ɗin, kuma
ba su ne a shift ɗin da aka buɗe file ɗin ba.
Ya saka security su kawo masa littafin da masu shiga da fice
suke rubuta sunan su a ciki, aka kawo masa yana dubawa, babu wani sanannen suna
a ciki, sai dai ya tsaya cak, ganin sunan Nabila a cikin book ɗin.
Nabila kuwa ta ɗauki hanyar titi, bayan ta ɗauki motarta,
tana tafe yau jinta take sakayau, kwanakin da ta yi cikin takaici, zuciyarta
tamkar an wanke mata ita.
Ta kalli glass ɗin motarta, ta ga wata babbar mota ta taso
ta a gaba, idan ta kauce, ta bar hannun ta bawa motar dama ta wuce, sai motar
ta rage gudu, ganin ba zasu bata damar tafiya cikin kwanciyar hankali ba, ya
sanya ta ɗauki titi sosai, ta wuce su, amma suka cigaba da binta by fire by
force ita suke hari!.
(Am sorry for delayed posting, am sick ayi mini addu'a
please)
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Al'amin da ɗan mama suna kwance a cikin ciyayi, in da suka ɓuya
nesa da Asibitin sosai.
Suna ta jin kai komon motocin yan sanda, ɗan mama ya kalli
Viper, ya ga yadda yake rintse idanunsa, yana damƙar ciyayin wurin, ya ce
"Sannu oga Viper, cikin ne? Ko wani asibitin zamu tafi?" Ya girgiza
masa kai alamar a'a.
"To tun da da cannula a hannunka, kaga magungunanka da
na kwaso, naga suna yi maka wannan allurar, ina ga ita ce ta ciwon cikin, bari
na yi maka"
Viper bai ce masa komai ba, ɗan mama ya haɗa allura ya hau
zuba masa a cikin cannula, a hankali viper ya fara buɗe idanunsa, amma kansa ya
fara juyawa, ya kasa magana.
Ɗan mama ya koma gefe, ya kunna sigari yana sha, mintuna
goma Viper ya tafi gaba ɗaya, ya ciro wayarsa ya danna, sannan ya saka a
kunnensa ya ce "Hello sir, eh su yi sauri ya samu bacci, amma yana cikin
ciwo sosai"
Ya ajiye wayar ya cigaba da shan sigarinsa, mintuna arba'in
sai ga wata helux baƙa ta iso wurin, wasu narka narkan ƙarti suka fito, suka saɓa
Viper suka saka shi a cikin motar, ɗan mama ya kama ya hau suka tafi.
Suna tafe a hanya su liti suna kiran ɗan mama a waya, ya
gaya musu yana ina, da shi da Viper, ya din ga raina musu hankali yana yi musu
kwana-kwana, suka din ga zaginsu amma ya ce "Oga walid ka yi haƙuri, wayar
zata mutu babu caji" ya katse wayarz ya cire batirinta gaba ɗaya.
Wani Asibiti suka kai shi, likitoci suka rufu a kansa, suka
dudduba shi, suka ce babu wata matsala zai warke, ba wata gagarumar matsala
bace ba, sai dai dole ya nisanci shaye-shaye idan yana son zama lafiya.
Nasir jiki na rawa ya ɗaukko wayarsa, yana kiran Nabila, sai
dai yayi mata missed calls, sun fi biyar, ko ɗaya bata ɗaga ba, hakan ya ƙara
fusata shi ainun, ficewa yayi ya ɗauki mota ya bar Asibitin, yana ƙoƙarin
gazgata zargin da yake yi wa Nabilan.
Yana ƙoƙarin sake kiran wayarta, sai ga kiranta, ya ɗaga zai
yi magana ya ji muryar da bata Nabila ba, ta wani daban.
"Malam ina mai wayar?"
"Ta haɗu da hatsari, tana emergency na asibitin cikin
gari" wani wawan burki ya ci a tsakiyar titi, wanda sai da ya kusa haddasa
hatsarin shi ma.
"Ta mutu ne?"
"A'a, ana kula da ita, ni ɗan sanda ne, mu muka kaita
asibitin"
"Nima ɗan sandan ne, ka gaya mini ta mutu ko?"
"A'a, muna dai jiran abun da likitoci zasu ce ne"
ana tayi masa horn, amma hankalinsa baya kai, ya fizgi motar ya canza hanya.
***
Ramma kuwa bayan Abdul ya gama wayar ta ce "Ka ce mini
mahaukaci ne ya yanke ka, kuma yanzu na ji yan sanda ne suka kiraka ana zancen ɗan
ta'adda"
"Eh shi ne mahaukacin ai"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kamar na san sunan da ka
faɗa fa"
"Wanne?"
"Mai zamani, amma kuma kamar ba haka ake ce masa ba,
mama ta san shi"
Basar da zancen yayi ta hanyar cewa "Wayyo wuyana"
Cikin kulawa ta ce "Sannu, ka kwanta to"
"To ki zauna sai na kwanta a kan cinyarki"
"Gaskiya ba zaka takura mini ba, wai kai jinyarka sai
ka ce wani jariri, ka yi ta ragwanci, ɗan wannan ciwon sai wash kake, wannan
idan kaga fuska kuka zaka yi kenan?"
"Haba baby, ki tausaya mini mana, da na mutu fa"
Ramma ta ce "Haka nake fata dama"
"Ƙarya ki ke yi " yayi maganar yana janyota, yana
ƙoƙarin kwanciya a jikinta, ta ture shi ta ce "Baka isa ba, idan ka gama
sangartar ka watstsake, mutum ba juriya"
Shagwaɓe fuska yayi, yana kuma kwanciya a jikinta ya ce
"Zafi"
"To sannu"
"Yauwwa baby, i love You, ki kula da ni sosai"
"To samo zani sai na goyaka ƙarewar kula, ka rabu da ni
dan Allah" ƙarshe ta gama mitar ta rabu da shi.
***
Nabila kuwa a emergency, aka gano gocewar ƙashi a hannunta,
sai buguwa da tayi a ka, ta fasa goshi, ga jini na fita daga hancinta, in da
Allah ya taƙaita abun, da seatbelt a jikinta take driving, dan Abba na yawan
gargaɗinta a kan hakan.
Godiya Nasir ya din ga yi wa Allah, da ya tarar bata mutu
ba, daga nan asibitin, ya ɗauketa ya canza mata wani.
Da ƙyar ya iya kiran Abba ya gaya masa, saboda yadda baya ɗaukar
lamuranta da sauƙi.
***
Lokacin da aka kai Viper da ɗan mama gida, su liti
basa nan, sun bazama nemansu, duk da a hanya, sai da jami'an tsaro suka tare
motar, da son bincikar motar, amma ganin masu motar, ya sanya aka basu dama
suka wuce.
Suka kwantar da Viper suka tafi, ɗan mama ya gyara gidan, ya
nemi wuri yayi zamansa hankali a kwance.
Dare yayi sosai, su liti suka dawo, suka tarar da ɗan mama
da Viper yana bacci.
Zabura liti yayi, zai kwaɗe shi, Walid ya hana shi, ya ce
"Ɗan mama, wane irin wulaƙanci ne ka yi mana haka?"
"Oga Walid, wayata ce ta mutu fa, ɗan gidan indabo ne
likitan da ya shiga duba shi, tona mana asiri ya so yayi, a kama mu, muka yi
layar zana, muka dirge, muka samu wuri muka ɓuya, ciwon cikin ya sake tayar
masa, na yi masa wata allura da na ga suna yi masa a cikin kayan magungunan sa,
kawai naga ya ware, shi ne na samu abun hawa, na kai shi wani asibitin, da kyar
na kawo shi gidan nan, hannunsa na saƙalo a kafaɗata muna tafe muna faɗuwa har
gida".
Liti ya ce "Ɗan azzaluma, duk sai da ka azabtar da shi,
ga ciwo yana fama, shegen taurin kai kamar jinjirin jaki, ka gaya mana kuna
ina, ka ƙi da yake ɗan kut....ne kai, ɗan wahala kawai".
Walid ya ce "Dan Allah liti kayi haƙuri, tun da Allah
ya dawo da su gida lafiya"
"Ai yaron ne, wasu lokutan yadda ka san rainon garke,
gaba ɗaya rayuwar sa, babu lissafi"
Ɗan mama ya ce "Ayi haƙuri"
"Kai ni fa ban ma yarda kai kaɗai, ka iya kawo Viper
gida ba, Allah ya sa ba wani haukan kayi, ka kawo mana wani ya ga in da muke
ba"
"A'a oga liti, nikaɗai na kawo shi gidan nan"
"Ware maƙaryaci kawai"
***
"Abdul"
"Na'am daddy"
"Saura wata guda bikinka, babu wani alamar
shirye-shirye da kake yi, kawai dai gaka nan, ta ƙarfi da yaji ka ke son
salwantar mana da wannan damar"
"No daddy ba haka bane ba, ina shiri, amma yau ka ji
news kuwa?"
"A'a wasu lokutan news ɗin nan, hawan jini yake saka
mini, amma meyake faruwa?"
"Na haɗu da Viper fa" miƙewa tsaye Indabo ya yi ya
ce "Wane Vipern?"
Abdul ya ce "Ya naga ka tashi tsaye? Viper dai naka, ya
je ƙaramin branch ɗina, an kwantar da shi har ya kwana"
Indabo ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wai
da me yaron nan yake taƙama har haka, yawo ma yake yi a cikin gari har da zuwa
asibiti? Anya ba harinka yake yi yayi maka wani abun ba, ya sanya ya je?"
Abdul ya girgiza kai ya ce "Bana tunanin hakan,
unexpected muka haɗu, naje da daddare ban gane shi ba, yana bacci, sai yau da
safe muka haɗu, amma dan Allah Daddy, meya haɗaka da Viper har haka, yake
farautarka kai ma kake farautarsa?"
Indabo yayi wuƙi-wuƙi da ido ya ce "Ya gaya maka wani
abun ne?"
"A'a, amma ya ce yana nan zai yi fitar burtu, yana nan
tafe gareka, dan Allah mai ka yi masa ne?"
Indabo ya ce "Babu komai, kawai dai ka san yan daba, ba
alƙawari ne da su ba, babu wani abu da nayi masa" yanayin yadda yake
maganar, ya sanya Abdul gane akwai wani abu a ƙasa, amma ya ɓoye masa, Abdul ya
jinjina kai ya sake cewa "Daddy"
"Na'am Abdul"
"Bayan na auri 'yar gidan party chairman, idan na kawo
wadda nake so, zaka aura mini ita?"
"Wacece kuma a ina take?"
"A'a kafin in gaya maka, zaka yarda na zauna da ita,
kuma ba zaka yi mini faɗa ba?"
Indabo ya ce "To ai haryanzu ba ka yi mini bayani
ba"
"Amm yarinyar da nayi raping tana raye"
"What! Tana raye? Tana ina?"
Cikin sanyin jiki Abdul ya ce "Dan Allah Daddy kayi
haƙuri ɓoye makan da nayi, tsawon lokaci, dan Allah ka yi haƙuri"
"Na ji, na ji, tana ina yanzu?"
Abdul ya girgiza kai ya ce "To ai daddy baka ce komai
ba, dan Allah ka yi haƙuri, na san nayi kuskure, sai da na ce zan kasheta, na
ga ashe kisan kai ba abu ne mai sauƙi ba, dan Allah ka yi haƙuri "
Indabo ya yi shiru sannan ya ce "Na ji, amma yanzu tana
ina? An yi sara a kan gaɓa, hankalin mutane ya dawo kan appeal ɗin da waccan
shegiyar yarinyar zata yi, dan haka dole zata bayyana a gaban kotu, amma da
baka kasheta ba tana ina?"
"Daddy, abun da kawai zan iya gaya maka kenan ban
kasheta ba, saboda ina tsoron matsala ta taso daga baya, amma ba zan iya barin
rahama taje gaban kotu ba"
"Me kake nufi?"
Cikin damuwa ya ce "Ban san me zai iya biyo bayan hakan
ba, rahama tana tare da ni a wuri daban, tsawon wannan lokacin" wani
lafiyayyen mari Indabo ya ɗauke Abdul da shi, ya dafe kuncinsa ya ja da baya.
"Abdul yasar, yaushe ka yi girman da zaka yankewa kanka
hukunci ba tare da sanina ba? Yanzu duk dambarwar da ake yi yarinyar nan na
tare da kai? Audio da yake yawo aka ce muryar babarta ne, da gaske kenan zuwa
ka yi ka ɗauke ta, saboda mahaukaci ne kai, sai ka je da kanka, ba ma turawa ka
yi a ɗaukko maka ita ba, lallai ta tabbata baka da hankali dabba ne kai,
wallahi ba zaka lalata mini siyasa ba duk wannan wahalar da nayi ta tashi a
banza ba"
"Daddy, dan Allah ka fahimce ni".
"Shut up my friend, ubanka zan fahimta ka je ka kawo
mini yarinyar duk in da ka kaita, kafin na casaka wallahi ba zan bari ka tona
mini asiri ba, saboda hauka da wautarka ba, fice ka bani wuri kan na tattaka
ka"
Abdul ya tsuke fuska sai hura hanci yake yi, ya fice, sam
bai ji cewa ko indabo zai jajjaga shi, zai kai masa Ramma ba, ko ya yarda ta
tsaya a gaban kotu ba, sai dai ayi duk wadda za ayi.
***
Bayan farfaɗowar Viper daga baccin da allura nan ta saka
shi, ya din ga mamaki, wace irin allura ce haka, bai takura da kansa da dogon
tunani ba, sai dai yadda ya din ga jin ina ma, ya yi wa Abdul mummunar illa,
kan ya baro asibitin, sai kuma wata zuciyar ta tuna masa, ba shi ne yayi masa
laifi ba. Wata zuciyar kuma ta ce kai ma ba matarka ce tayi musu laifi ba, suka
kasheta.
Ya tashi ciwon cikin da sauƙi, ya yi alwala ya rama sallolin
sa, da daddare ya zauna yana jiran kiran wayar Nabila da daddare, dan ya san ba
zata iya zuciya ba, sai ta kira shi ta ji ya jikinsa, amma shiru ba ta kira ba,
har cikin dare idan ya juya, sai ya duba wayarsa ko ta kira bai sani ba, amma
babu kiranta, shi ma kuma ya kasa kiranta.
Abba kuwa godiya ya din ga yi wa Allah, da likitoci suka
tabattar masa da ba wani abun tashin hankali ne ya samu Nabila ba, ta bugu ne a
ka, kuma babu internal injury, sai hannunta da ta samu gocewar ƙashi shi kawai
za a gyara.
Mama ta hau masifa, ta ce "Ba dai ita yar gata ba, an ɗauki
mota an bata ba, Allah kaɗai ya san tuƙin gangancin da take yi, ko dan ma tayi
burga a titi, gashi ta tayar da mutane tsaye"
Abba ya ce "bata tayar da kowa tsaye ba, babu wanda na
yi wa dole ya zo ya zauna mini da ita, a da ma baku yi ba sai yanzu? Kuma tuƙin
da take yi, ai masaniyar doka ce ita ma, ba wani tuƙi da take yi na ganganci,
jarabta ce kawai Allah ya kawo, kuma ya taƙaita, Magajiya zata yi mini
jinyarta, zuwa a sallameta, ban ce dole ayi mini ba" mama ta ja bakinta
tayi shiru, jin abun da ya ce.
Ya cigaba da kallon Nabila, cikin tsananin tausayawa, kwanan
nan abubuwa sai samunta suke yi, daga wannan sai wannan.
***
Nasir ne zaune a gaban Indabo, fuska babu walwala Indabo ya
ce "Naga alamar aikin nan baka ɗauke shi da muhimmanci ba, idan har ba
zaka iya ba, zan saka a canza mini kai, nayi abun da nake ganin shi ya
dace".
"Ina mai baka haƙuri, amma komai ya kusa zuwa
ƙarshe"
"Idan ma baka kawo shi ba, ni zan kawo".
***
Hafsa ce zaune a gaban baba ta ce "Baba"
Ya ce "Na'am ƴar baba"
"Baba na san ai kai ba zaka ƙaryata ni ba ko?"
"Eh mana yaya zan yi na ƙaryata ki ma?"
Hafsa ta gyara zamanta ta ce "Ai dai ka san na warke
yanzu, bana yawo, ba na shan komai, kuma na warke ai dai ko?"
Ya ce "Alhamdilillah kam, duk na sani hafsat"
"To yadda naga jauhar yau Allah ya nuna mini annabi
haka, ta saka niƙab, da irin tafiyarta, da irin idonta, amma sai da na ganeta,
na so na bi ta, yaya saifu ya kira ni, na nemeta na rasa"
Baba ya ajiye cokalin sa, ya ce "Anya kuwa warkewar nan
hafsa? Yaya za ayi ki ga wanda ya riga ya mutu, kuma ta cikin niƙab ɗin ki ka
iya gane ita ce?"
"Haba Baba, ka san dai yadda nake da jauhar, amma ko
ina ga fatalwarta ce, amma dai da ko da ta zo mini a fatalwa, sai ta tsaya mu
gaisa, bai kamata ta nuna kamar ba ta sanni ba, ina ga haryanzu haushina take
ji, saboda na auri Alhaji mu'azzam yakamata ai ta yafe mini, ba ta ga irin
wahalar da na sha ba, ai ko gaisawa sai ta tsaya mu yi. Ka ce na din ga yi mata
addu'a, ina yi mata fa, amma duk ba ta ga wannan ba, ta share ni, ban san ya
aka yi waliyiyyarka ta koyi wannan halin ba baba" tayi maganar tana kuka
iya ƙarfin ta.
Ya share hawayen da yake shirin gangaro masa, ya ce
"Bata kyauta miki ba, zan yi mata faɗa, amma ina ga zamu koma Asibiti
ganin likita".
Hafsa ta ce "Baba da hankalina fa, ba hauka nake yi ba,
ina sane da duk abun da nake yi fa" Mama ce ta shigo ɗakin ta ce "Ke
mahaukaciya, tashi ki fita ki bashi wuri, ya gama cin abinci dan Allah, kin
saka shi a gaba da sakarci"
Hafsa ta ce "Ni ba mahaukaciya ba ce ba, cutar damuwa
nayi ba hauka ba"
Baba ya ce "Na sha gargaɗinki a kan kiranta da
mahaukaciyar nan, wannan salon ki sake tunzurata ne ai"
"A'a dama ai a tunzuren take" Hafsa ta tashi rai a
ɓace, ta fita tsakar gida tana kiran Anty.
"Hafsa wane irin kira ne wannan? Menene?"
"Kin ga maman su surayya tana ce mini mahaukaciya ko?
Ni fa ba mahaukaciya ba ce ba"
A fusace Anty ta nufi ɗakin Baba ta ce "Wallahi kar ki
sake kiran ya ta da mahaukaciya, idan ba haka ba duk abun da nayi miki ke ki ka
saya"
"Mecece idan ba mahaukaciya ba, ba dai auren cin amana
ba, da son abun duniya ba, ta haɗu da babarta a makirci a matsayin kishiya ai,
ga hauka ga ba auren, sai an yi magana ace depression ne, yarinya ta zama yar
ƙwaya ta haukace"
"Eh bakomai, tun da har ta yi auren ai, ta shiga ta
fito, da babbar budurwa ai gara ƙaramar bazawara, da kike maganar zama yar
ƙwaya, naki ɗan uban menene ba ya sha? Ko kina tunanin bamu san komai ba"
Hafsa ta koma gefe tana kuka, saboda ta tsani taji an kirata
da mahaukaciya, kuma haryanzu idan ta tuna jauhar, da cin amanar da aka yi mata
sai ta ƙara shiga damuwa, tayi ta kuka, ta san hakkin jauhar ne ya sanya ta
tsinci kanta a wannan mawuyacin halin da take ciki.
Baba yana jin su, ya fito a zuciyarsa yana Addu'ar, Allah ya
sa jauhar da mahaifiyarta suna tare a aljanna. Ya fice ya bar musu gidan.
Walid yana ta lallaɓa Viper, ya ci abinci ya sha magani,
gaba ɗaya jin sa yake yi wani iri babu daɗi, ya karɓi kofin shayi yana sha a
hankali.
Ɗan mama ya kunna radion wayarsa, liti ya hau mitar ya cika
musu kunne, ya ce "Dan Allah oga liti kayi haƙuri, labarin wasanni zan
ji"
"Ai sai ka yi"
Tashar su Sumayya ya kai, a dai-dai lokacin da murtala yake
sanar da hatsarin da Nabila ta samu a jiya, bayan kammala program da suka yi ta
tafi, suna barar a sakata a cikin addu'a.
Buredin da viper ya haɗiya ne, ya tsaya masa a maƙogwaro,
tamkar ya haɗiyi dutse.
Liti ya fizge wayar hannun ɗan mama ya ce "Ban gane
hatsari ba, ji ya ma fa taje Asibiti duba Viper, har yaushe ta yi hatsari
kuma?"
Walid ya ce "Babu kusa babu nesa ga Allah, amma dai
dole mu san halin da take ciki"
Liti ya ce "Taɓ yarinyar nan tana shan azaba, dudu
yaushe ta kusa mutuwa a gobara, yanzu kuma hatsari?"
Viper ya din ga murza kofin hannunsa, gumi yana tsatstsafo
masa, amma bai tofa uffan ba.
Ɗan mama ya tashi ya ce "Bari nayi maza nayi wanka, na
je unguwar su na jiyo, wane asibitin take? Ko kuma na je asibitin da ta kwanta
lokacin da tayi gobara, yadda ake ciki dai zan kira ku"
"Saura kuma ka kira mu ka yi mana wannan gaɓancin naka,
kayi mana wauta, ka tsaya ka nutsu, kuma saura ka ce baka da caji a waya"
Ɗan mama yayi murmushi ya ce "Ni na isa, in sha Allah
ba za ayi haka ba"
Walid ya ce "Viper ka ƙarasa ci, in sha Allah babu wani
abu, tun da ba su ce ta mutu ba, an ce dai ta ji raunuka ne kawai" shi dai
bai ce komai ba, ya ajiye kofin shayin.
***
Yanayin yadda Abdul ya shigo, sai da ramma ta ɗan tsorata,
maye yake yi sosai.
Ta tashi ta nufi in da yake, ta ce "Abdul giya ko? Baka
ce mini ka daina shan giya ba?"
Yayi shiru yana ta numfarfashi.
"Kai dai ba zaka taɓa gyara rayuwarka ba, idan ka yi
kamar zaka nutsu, sai ka ƙara fanɗarewa, kayi ta yi mini alƙawari baka
cikawa".
Ya kama hannunta ya rirriƙe, ya ɗaga jajayen idanunsa da
ƙyar ya kalleta ya ce "Rahama"
"Meye?"
"Dan Allah karki rabu da ni, ban san me zai iya faruwa
a gaba ba, ina sonki, ina sonki....Ai zaki yafe mini ko rahama" yayi
maganar cikin maye yana kallonta.
Ta kwantar da kansa a kan cinyarta, tana shafa sumarsa a
hankali ta ce "Kana so na amma ka je ka sha giya, kafi bawa soyayya
muhimmanci a kan tsoron Allah ko?"
Ya girgiza kai alamar a'a.
"Ga lokacin Sallah yayi, amma babu damar ka yi saboda
kana maye, idan ka mutu a haka fa, zan yafe maka ne kawai, ranar da ka mayar da
ni gaban mahaifiyata ka nemi afuwarta"
"Idan nayi hakan, zaki yafe mini, mu cigaba da zama
tare?" Tayi shiru ba ta ce komai ba.
"Wallahi rahama, komai zai faru sai dai ya faru, idan
aka yi ƙoƙarin raba ni da ke, zan ɗauke ki ne na yi gaba da ke, muje mu cigaba
da rayuwarmu tare"
Ta ce "Mhmm Abdul yasar rigima, kayi shiru ka daina
wannan surutun ka samu ta sake ka, kayi salla ba na son ka mutu kana rashin ji,
wasu lokutan dai kayi ta abu kamar mutumin kirki, amma zunubanka da kake
tafakawa ne, sun wuce misali"
"Rahama"
"Abdul yasar"
"Wallahi ba zan yadda a rabani da ke ba, ina sonki
sosai"
"To likita, amma na ce kayi shiru ai"
Ya ce "To na yi" da haka ya din ga sauke numfashi,
yana bacci.
****
Ƙarfe biyu da rabi na dare, Viper yana cikin asibitin da
Nabila take, sawu duk ya ɗauke, yan dubiya babu kowa, daga majinyata, sai
marasa lafiya da ma'aikatan da za su kwana.
Ya jinjina ƙofar ɗakin da Nabila take, ya tura a hankali,
bai ji an yi magana ba, ya sake turawa ya ga duhu, an kashe fitilar ɗakin, ya
shiga ya rufe ƙofar, ya kunna fitilar wayarsa ya haska, baba magajiya na ƙasa
kan carfet tana bacci.
Ya haske Nabila tana kan gado, ita ma baccin take yi, ana
ƙara mata jini.
Ya taka a hankali, ya je gaban gadonta ya durƙusa, an naɗe
mata hannu ɗaya da bandeji wanda ta samu gocewar ƙashin.
Hular kanta ta zame, tun daga farkon goshinta, a cike yake
da gashi mai santsi, kasancewar ba gwanar yin kitso bace, gashin nata a tsefe
yake.
Ya kai hannunsa goshinta, in da aka rufe da plasta, da alama
rauni ne a wurin, ya dawo ya riƙe hannunta ya ce "Get well soon, Allah ya
baki lafiya"
"Viper" ta furta a hankali kamar mai raɗa.
"Angry bird"
"Ya jikinka?"
Ya ce "Na ji sauƙi"
"Yanzu ma na san ba zaka kira ni a waya, ka yi mini
sannu ba, ka tsane ni"
Ya girgiza kai ya ce "Ban tsane ki ba Abla, ina so ki
rayu ne, in cigaba da ganin fuskar jauhar a cikin taki"
"Viper"
"Mmm"
"Zan cika maka alƙawarin ka in sha Allah, duk wuya duk
rintsi, zan tsaya maka sai ka yi 'yanci, duk girman barazanar da zasu yi mini,
zan tabattar da an yi maka adalci da kai da matarka"
"Allah ya baki iko"
Ta sake cewa "Viper"
"Mmm Abla"
"Dan Allah kar ka tafi daga mafarkina yanzu, na san
idan na tashi, ba zan iya zuwa asibiti na dubaka ba"
Yayi shiru bai kuma ce mata komai ba, ta ƙara riƙe hannunsa,
da yafi nata girma sosai.
Jikinta ne ya ƙara saki, ta cigaba da bacci, tana yi tana
surutai, a hankali har ta yi shiru. Ya sake haskata da fitilar sa, irin
innocent face ɗin jauhar ta bayyana a fuskar Nabila. A hankali ya zare hannunsa
daga nata, ya yinƙura ya tashi ya fita daga ɗakin.
Washegari da safe, sai tunanin mafarkin da tayi jiya take
yi, tana tunanin gaske ne, ko kuma kawai mafarki ne?.
Da safe ana ta zuwa dubata, wajen ƙarfe sha ɗaya Nasir ya
zo, lokacin babu kowa kasancewar ranar aiki ce, sai baba magajiya. Suka gaisa,
ya aiki baba magajiya ya rage saura daga shi sai Nabila a ɗakin.
Ya zauna daf da ita a kan gadon, yana kallonta ya ce
"Sannu ya jikin?"
Ta amsa da "Jiki Alhamdilillah, da sauƙi, zuwa gobe in
Allah ya kaimu nake so na tafi ma, i have a lot to do"
Ya ce "Well, tambayarki zan yi, kuma bana buƙatar ki yi
mini ƙarya, saboda zargina ya tabatta gaskiya ne a kanki"
"Wane zargin?"
"Nabila kin san in da Viper yake, kina haɗuwa da
shi!"
Ta kalleshi ta ƙura masa ido amma bata yi magana ba.
"Ina magana kina kallona, na samu rahoton an ganshi a
A.I hospital, naje bamu sameshi ba, amma naga signing ɗin ki, kin je asibitin
me ki ka je yi?"
"Ni ganin likita naje, ka daina zargina tun da baka da
wata hujja, mai asibitin aka tura ni wurinsa follow up, saboda lokacin da aka
sallame ni, bai zo ba"
"Ƙarya ki ke yi Nabila"
"Ni ba ƙarya nake yi ba, ka fara samo tabattaciyar
hujja, kafin ka ƙaryata ni"
Ya jinjina kai ya ce "Zamu gani ai, bayan duk wannan
abubuwan hujja ki ke so na kawo miki? Shikenan zamu gani, amma ki sani aikinki
ba zai baki kariya ba, muddin aka kama ki da laifi, sunanki yar ta'adda kema,
mai ɓoye mai laifi"
"Abun kunya ne ga hukumar yan sanda ace sun gagara kama
mutum ɗaya, da yake iya yawonsa a cikin gari, sai ma a din ga bibiyar wanda bai
ji ba, bai gani ba, ana yi masa baranaza" tsananin fusatar da yayi, ya
sanya kawai ya tashi ya bar ta a ɗakin.
Ta dafe ƙirjinta, saboda yadda yake tsananin bugawa, ta
yanke a ranta dole tayi gaggawar fara shari'ar Viper, kafin ta kammala ta
ramma.
Ya fita babu jimawa, baba magajiya ta dawo, ta karɓi aron
wayarta, ta shiga banɗaki, ta kira wayar Walid, Allah ya taimaketa ya ɗaga.
Ya ce "Barrister ashe tsausayi ne ya faru haka, ya
jiki?"
"Jiki da sauƙi, meyake faruwa ne? Yayana ya ce mini ya
samu labarin Viper ya je asibiti, ina yake ina fatan babu wata matsala?"
"Eh, Yana nan cikin ƙoshin lafiya mun koma gida ma, haɗuwa
yayi da ɗan Indabo a matsayin likitan da ya duba shi, shi ne ya sanarwa
security"
Ta ce "Haba dai? Likitan da ya duba shi kuma? Garin
yaya dole mu ƙara taka tsantsan amma ba abun da ya faru?"
Walid ya ce "Babu abun da ya faru, mun bar Asibitin ma,
muna gida"
"Dole na haɗu da shi, nan kusa Allah ya ƙara
afuwa" ta katse wayar ƙirjinta na cigaba da bugawa.
***
Indabo yana ta sanya ran ya ga ta ina Abdul zai ɓullo, ya
kasa zaune ya kasa tsaye, saboda matsalolin da suke kunno kai, ya rasa wanne
yakamata ma ya fara ƙoƙarin kawarwa.
Kwanaki biyu kenan, ko ya nemi Abdul a waya, baya samunsa.
Kuma bai sake zuwa gida ba, hakan ya ƙona wa Indabo rai fiye da kima.
Viper bai sake neman Nabila ba, ko a waya, dama bata saka
rai ba, dan ta san bata gabansa, idan ta tashi, Walid take kira ta tambaye shi
ya jikin Viper, tana ta neman hanyar da zata bi, ta samu ta ganshi, dan sosai
Nasir yake sanya mata ido yanzu, ya hanata sakat duk motsinta a kan idonsa,
kasancewar motarta tayi damage, an kaita garrage wurin gyara, hatta wurin aiki
shi yake kaita, da farko ya so ya Abba ya hanata fitar ma, amma ta din ga kuka,
taba nuna wa Abba cewa akwai shari'oin da suke buƙatar ta yi attending.
Bayan ya ajiyeta a wurin aiki aƙalla yayi mintuna talatin a
tsaye, ko da zata fito, sai da ya samu ɗaya daga cikin security na wurin, ya
lambar wayarsa, ya ce masa idan ya ga fitar Nabila ya kira shi ya gaya masa, ya
kawo alheri yayi masa sannan ya tafi.
Nabila kuwa a office ta iske barrister Habib, ya shirya tsaf
zai fita, ta shiga da sallama.
Ya amsa mata ya ce "Sannu Nabila, ya hannun?"
"Hannu Alhamdilillah, fita zaka yi ne?"
Ya ce "Eh, zan je shari'a ne"
Ta ce "Mu fita tare, magana nake son mu yi da kai"
ya ce "To shikenan babu laifi" suka fita suka shiga motarsa suka
fice.
Kamar mai aljanu, suna tafe a hanya, ta ce "Ya ajiyeta,
tayi mantuwa, office zata koma, ya ce zai kaita ta ce masa a'a, ta fice ta hau
napep.
Viper ya buɗe ƙofar gidan zai fita, ya ganta a tsaye tana
shirin shiga, ta saka hannu ta ɗage niƙabinta, suka yi ido huɗu ya ɗan tsura
mata ido, ta faɗa sosai.
Ta ce "Ya jiki, ka warware?"
"Mmm"
"Zuwa nayi mu ƙarasa tattaunawa, ka fara yi mini
bayanin shaidun da kake da su a hannu, zan fara gudanar da shari'ar ka, zan
cigaba da yi tare da ta ramma, kafin su halaka ni, accident ɗin nan, da nayi,
takani aka so yi da mota, garin na kauce musu, nayi accident" ya tsura
mata ido, tare da haɗiye wani abu a wuyansa.
(Alhamdilillah ala kulli halin, ina godiya sosai da sosai
addu'oin da ku ka yi mini, bisa ga rashin lafiya da nayi, Ubangiji Allah ya bar
zumunci na gode ƙwarai)
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Viper ya tsaya ƙyam yana kallon Alhaji mu'azzam da ya miƙo
masa hannu.
A rikice Nabila ta ce "Amm eh, ai na ma warware na ji
sauƙi, ka shiga, ka jira ni a office ɗina, yanzu zan dawo"
Viper ya kalli Nabila ya ce "Koma ciki" sai ta
tsaya tana rarraba ido, tana kallonsa tana kallon Alhaji mu'azzam wada.
Wani irin kallo Viper ya yi mata, da ya tilasta mata barin
wurin, tana waiwayawa.
Viper ya saka hannunsa a hannun Alhaji mu'azzam, ya sauke
facemask ɗin sa yana kallon cikin idonsa.
"Dama ana ganinka, ka yi wa hukuma wuyar kamawa? Ya aka
yi na ganka tare da yarinyar da nake so, kuma nake fatan na aura?"
Viper ya tsananta riƙon da ya yi wa hannun Alhaji mu'azzam
ya ce "Ka gaya mata wani abu ne?"
"Kamar me fa?"
"Ka san abun da nake nufi" yayi maganar yana ƙara
tsare shi da ido.
Alhaji mu'azzam ya ce "Kana tsoron wani abu ne?"
"Ba maganar tsoro bane ne ko akasin haka, gargaɗi ne
nake yi maka, idan baka furta ba kar ka fara, nike da alhakin kai ƙarshen
wannan lamarin, idan ka yi wani yinƙuri da zai kawo tangarɗa ga abun da nake
tsarawa, ka san abun da zan iya aikatawa".
Alhaji mu'azzam ya yi murmushi ya ce "Da fari jauhar,
na bar maka ita, a wannan karon kuma Nabila, kar ka zama mai......
"Jauhar ta wa ce, haka zalika Nabila, muddin zan cigaba
da ganin fuskar jauhar a cikin ta Nabila ta haramta a gareka, ba kai ba kowane
mahaluki ma" ya fizge hannunsa daga na Alhaji mu'azzam ya mayar da
facemask ɗin sa ya bar wurin.
Nabila kuwa kai komo ga din ga yi a office ɗin ta, cike da
fargaba da tsoro.
Kankarofi ya turo ƙofar office ɗin Nabila ya shigo, ta tsaya
tana kallonsa yayi mata murmushi ya ƙarasa ya ce "Madam ya na ganki a
tsaye ne?"
Murmushin ƙarfin hali ta yi ta ce "Bisimillah zauna
mana"
Ya zauna ya ce "Ashe tsautsayi ne ya kuma afkuwa haka,
ya ƙarfin jikin?"
Ta ce "Jiki da sauƙi Alhamdilillah"
"Amma dai babu wani mummunan rauni ko?"
Ta ce "Eh, gocewar ƙashi na samu a hannuna, amma
Alhamdilillah da sauƙi"
"To Alhamdilillah, na ji daɗi ƙwarai, ya shari'a
kuma?"
Tayi murmushi ta ce "Mu na ta fama, sai fatan Ubangiji
Allah ya iya mana"
"Allah ya yi jagora, kin ga kamata yayi ace har gida na
je dubiya, daga nan na miƙa buƙata ta ga Abba, ayi komai a kan lokaci, kin ga
babban mutum ne ni, amma soyayya ta saka sai wahalar da ni ki ke yi, kina
sakani sintiri, sai dai na yi ta biyoki office"
Ta ɗan shagwaɓe fuska ta ce "Wahalar da kai kuma?"
Ya kwantar da murya ya ce "Eh mana, ko ba ayi na ne, ya
sanya ake ta bani wahala"
"Matanka fa biyu, ni gaskiya...
"Ba kya son mai mata ko?" Ta jinjina masa kai
alamar eh.
"To meyasa?"
"Wahala ake sha, kuma nan da nan ake sakin wadda ta zo
daga baya, impact ni fa tashin hankali ne ba na so, gidanmu ma uku ne, ina
ganin tashin hankalin da ake yi"
Yayi dariya ya ce "Barrister, dabarar mutum ba ta
sanyawa ya kaucewa ƙaddararsa. Da dabara da wayon mutum na sanyawa ya kaucewa
ƙaddara, da wataƙila haryanzu fatima tana raye da ni ta aura"
"Wacece hakan?"
"No kar ki damu, kawai dai misali nake yi miki, wata
yarinya ce da na taɓa ƙallafa raina a kan aurenta, Allah bai yi ba"
"Baka aureta ba, sai ka auri mata biyu, yanzu da sai ka
yi ta uku da ita ni ta huɗu?"
Sosai ta bashi dariya, saboda yarinyata da kishinta da suka
gaza ɓuya.
"Karki damu, labarin ne akwai sarƙaƙiya, idan ya zo
ƙarshe zan baki. Amma matana ba matsala bane. Uwargidana tana Abuja, amaryata
kuma na kano, ke kuma sai in da ki ke so zaki zauna"
Noƙe kafaɗa tayi, tana ɗan tura baki, har ya gama yi mata
hirar, bai yi mata magana akan Viper ba, duk da ta so ta tambaye shi ko ya san
shi, amma ta ja bakinta tayi shiru, dan da Viper yakamata su tattauna wannan
maganar.
****
Naja'atu Bunkure ce zaune a office ɗin Abdul yasar, ya
hakimce a kan kujera yana saurarenta.
"Abdul, yarinyar nan fa dole ka fito da ita, even for
your own safety, idan fa aka wanke mutumin nan, akwai cakwakiya, bamu san ya
shari'ar nan zata kasance ba, taurin kan nan da kake yi, babbar barazana ce
gareka da mahaifinka Shari'a saɓanin hankali ce"
Abdul ya ce "Ba wata barazana, ai ba yau ki ka saba
goge laifi ba komai girmansa, wannan karon ma ki yi wani abu"
"Nayi iya yi na, da kai da mahaifinka ne kuka ɓata
komai, Abdul idan lamarin nan ya kwaɓe fa, zaku shiga matsala mussaman ma kai.
Kuma an gaya maka shaida kawai zata bayar a kotu shikenan ba wani abu ba"
Abdul ya yi murmushi ya ce "Naja'atu Bunkure, na sanki
fa, na kuma san waye mahaifina, na san abun da zaku iya na san wanda ba zaku
iya ba. Idan aka kuma cutar da yarinyar nan a karo na biyu, ba zan yafewa kaina
ba, ke da kanki kin san kura tayi lafiya, duk da a duk lokacin da zan shiga
Asibiti ina ajiye duk wani iskanci a gefe, in shiga a nutse, amma ke kin san
yanzu na nutsu sosai da sosai, albarkacin rayuwa tare da rahama"
Naja ta tafa hannu ta ce "Innalillahi wa Innalillahi
raji'un, Abdul kidnapping fa kenan, bayan fyaɗe ka saceta kana rayuwa da ita,
wani laifin fa kake aikatawa a kan wani"
"Babu wani laifi da nake aikatawa, da na barta to da
tabbas kun yi mata wata illar, barinta a wurina shi ne zata zauna safe"
"Shikenan, zamu ɗauki duk wani mataki da hukuncin da
muke ganin ya dace"
Ya ɗage kafaɗa alamar ko a jikinsa.
***
Indabo kuwa gaba ɗaya ya kasa zaune ya kasa tsaye, ya rasa
abun da yake yi masa daɗi, tun yana ƙirga adadin shigarsa banɗaki, har ya sare
lissafi ya ƙwace masa.
Gudawar tsoro da fargaba kawai yake yi, tun bayan da Viper
ya kira shi a waya.
Embassy ɗin Nigeria na Mexico ya kira, domin a bincika masa
da maganar da Viper ya kira shi ya gaya masa, idan gaske ce.
Ya ma rasa wa zai kira ya gaya wa maganar, ashe da gaske
yana sane da cewa, da shi yake sakawa ayi exchange a duk lokacin da jafar ya
aikata laifi, to ko da sanya hannunsa aka kama masa ɗa? Amma ya za ayi common ɗan
daban gari, ya saka a kama masa ɗa a ƙasashen ƙetare?.
Waya ya ɗauka ya kira IG, ya din ga masifa, a kan jan ƙafar
da ake yi, wurin kama Aminu Viper, tare da jadadda idan har ba za su yi abun da
yake so ba, zai shiga ya fita a ɗauke shi daga garin kano, a canza wani IG. Tun
da suka kasa kama mutum ɗaya, alhalin yana yawonsa a gari, da aikata abun da
yake so.
Yayi ta bashi haƙuri, tare da bashi tabbacin suna iya
ƙoƙarin su, amma komai ya kusa zuwa ƙarshe. Ya ajiye wayar yana mamakin ya za
ayi, ace senator guda ya tayar da hankalinsa haka a kan ɗan daba guda ɗaya tal
har haka, ya din ga ɓata lokacinsa a kansa.
Yadda indabo ya kira shi, ya tayar masa da hankali, haka
shima ya kira Nasir a waya, ya ce masa nan da kwanaki talatin, idan babu
improvements a aikin nan, zasu karɓi aikin daga hannunsa su bawa wani, kuma
hakan ka iya janyo masa demotion, da rasa wasu damarmaki.
Shi ma haƙurin ya din ga bayarwa, tare da bada tabaccin zai
kama Aminu Viper.
***
Abdul da la'asar ya koma gidansa,ya tarar rahama na wanka,
ya kwanta ya yi ɗai-ɗai a kan gado.
Ta buɗe ƙofa ta fito, ta tarar da shi ta ɓata fuska ta ce
"Abdul meye haka?"
Ya buɗe ido ya kalleta.
"Na gyara gadon, kawai ka hau ka ajiye mini shirginka,
wata uwar jaka kamar wanzami, kalli takalmi har bedroom ba a wancan ɗakin nake
ajiye maka ba?
Lumshe idanunsa ya yi, ta ƙarasa ta kwashe kayan, ta hau kan
gadon ta kwance agogon hannunsa, dan ta san ƙarshe ya cire, ya yar da shi a
wani wurin, ya zo ya isheta da nema.
Ya kai hannu ya fara shafa bayanta, tayi masa banza, tana
cikin ɓalle masa labcourt ya cigaba da shafa gashin kanta, sai da ya kai
hannunsa kan towel ɗin ta, ta buge hannunsa da ƙarfi ta ce "Tashi kayi
sallar la'asar na san baka yi ba" ya buɗe idonsa ya kalleta.
"Eh kana wani manne ido, ka tashi kayi sallar
la'asar"
"Zan yi in anjima, yanzu na gaji"
Ramma ta buɗe baki ta ce "Wace anjiman? Kai ke da
anjiman? Waye ya baka guarantee kai wa anjiman? Abdul wallahi wutar duniya ma
ba zaka iya da ita ba, balle ta lahira, kai a wuta kala nawa kake so a saka ka
ne? Saƙara fa, wutar marasa yin salla, ita ka ke so ka shiga ko? bayan ta shan
giya da neman mata. Ba shiri ya tashi ya ajiye labcourt ɗin ya ce "To
naji, ai dama ban ce ba zan yi ba, zan yi Astagfirullah in sha Allah ba zan
shiga wuta ba, shan giya da neman mata ai kin san na daina" yana maganar
ya nufi banɗaki.
Sai da tayi dariya, Abdul ga tsoro ga iskanci, ta tabatta da
ya samu kyakkyawar tarbiyya, da isashshen ilimin addini, da bai aikata wasu
abubuwan ba.
Taje gaban mudubi ta zauna, mudubin fal da turaruka, da
kayan gyaran gashi da na fata, wasu abubuwan duk shi ya koya mata amfani da su,
har wasu supplement yake bata tana sha. Ita kanta ta san tayi ƙiba ta yi kyau.
Tayi ajiyar zuciya ta fara shafa man.
Ya fito ya tayar da salla, ta ce "A kyautata niyya da
nustuwa idan ana salla, yadda ka yi ta haka zata zo maka a kabari" ta
shirya cikin doguwar riga, yana idar da sallar, ta ɗaukko masa azkar ta ce
"Ungo, ka san shi yawan ambaton Allah, yana hana mutum aikata alfasha, abu
ne mawuyaci kaga wanda yake da kusanci da Allah, yana aikata ɓarna
kala-kala" haka ta saka shi a gaba, ya idar suka je ya ci abinci.
Gaba ɗaya rayuwa da ramma ya sanya ya ji tamkar an canza
shi, zuwa wani na daban, haka kurum yake jin wata nutsuwa a tare da shi.
Mussaman saita shi da take yi a kan ibada, da yawan tsoratar
da shi a kan yin ta, haka yana saka masa nustuwa da kwanciyar hankali, kuma ya
rage aikata tsageranci da rashin ta ido. Hakan ya sanya yake ƙara jin raba shi
da ramma, tamkar raba shi da rayuwar sa ne.
System ya kunna ya ce "Your excellency zo ki ga wani
abu"
"Wanke-wanke zan yi na ɗora abincin dare"
"Karki damu, zan yi mana takeaway"
"Sai dai idan zaka yi wanke-wanken"
Abdul ya ce "Na ji zan yi"
Ta ƙaraso ta zauna, ya rungumeta a jikinsa, sannan ya buɗo
wani form ya ce "Kin san na menene wannan?"
"No"
"Form ɗinki ne na makaranta"
Ta kalleshi ta ce "Makarnta kuma?"
Ya ce "Eh mana, ko ba kya so?"
"Ina so, amma gida zaka mayar da ni?"
"Eh, zaki je ki ga gida, daga nan sai school, boarding
ce, mai kyan gaske, saboda sonake ki nutsu ki yi karatu da kyau, yadda babu
wanda ya ganki, balle yayi miki gori, da kin gama karatu kuma, ƙasar waje zaki
tafi jami'a, shiyasa nake tambayar ki me ki ke son zama, na biya komai, na yi
rubutu, yadda ko bayan raina ba zaki tozarta ba in sha Allah, ko bana raye
karatunki ba zai tsaya ba sai kin kammala in sha Allah"
"Yar uban wace ni da zaka yi mini duk wannan hidimar
haka?"
"Ba yar kowa ba ce, amma komai zan yi miki, ba zai kai
nauyin laifin da nayi miki ba, ba zai biya budurcinki da na karɓa ta ƙarfin
tsiya ba, da kuma rashin darajar da naje gidanku nayi ba, ba zan gaji da cigaba
da neman afuwar ki ba rahama" ta sunkuyar da kai ta yi shiru, hawaye na
zubowa daga idanunta.
Ya saka hannu yana share mata hawayenta ya ce "Ki yi
haƙuri, na san na cutar da ke, dan Allah ki yafe mini rahama, soyayyar nan
kawai da Allah ya jarabbe ni da ita, ta isheni, baki san tarin ƙalubalen da
yake a gabana nake ta ƙoƙarin karewa a waje ba, amma dai ki yi haƙuri dan
Allah" a hankali ta zare hannunta daga nasa, ta tashi ta bar falon tana
kuka.
***
Nabila kuwa da file ɗin Viper ta tafi gida, ta kai shi ɗakinta,
ta cigaba da duba shi daki-daki, tana picking ɗin kurakuran da aka tafka a
cikin shari'ar ta sa. Kai da ganin fasalin shari'ar ka san cewa cike take da
mugunta da zunzurutun zalunci.
Zafi ne ya isheta, babu wuta, ga solar sai ƙara take yi,
kasancewar ranar ba ayi rana sosai ba.
Ta ɗaukko system ɗin ta, da wayoyinta, ta fita gareji, ta
shimfiɗa sallaya, da kayan ciye-ciyenta, ta zauna ta cigaba da aikinta.
Nasir ne ya fito yana waya, ba ta san da wa yake yin waya
ba, sai dai yanayin yadda ya fito yana wayar, bai san tana wurin ba.
"Eh dan Allah, duk yadda za ayi a samo mana hotunansa,
ko guda ɗaya ne, nima na daɗe da wannan tunanin, ban aiwatar ba, amma a yanzu
naga hakan ne kawai mafita, a samo hoton nasa, dan IG ya kira ni ɗazu, shi
kansa distinguish sai da ya kira ni, ni duk na ruɗe, nayi mamakin yadda aka yi
mutum ɗaya ya gagari hukuma. Duk wata hanya da na bi da zan sameshi, sai ta kuɓuce
mini.
Shiru ya yi, lokacin da ya lura da ita a wurin a zaune, ya
ƙarƙare wayar ya saka a aljihunsa.
"Dama har zuwa yanzu baka taɓa ganinsa ba, baka san
kamaninsa ba?"
"Eh" ya bata amsa a taƙaice.
"Hmm"
"Ko zaki bani hoton nasa ne?"
"Ni a su wa?"
"Ke a 'yar kankamba mana, samunki da hotonsa ai ba abun
mamaki bane ba"
Nabila ta yi murmushi, kawai ta cigaba da aikin da yake
gabanta.
****
Mutumin da yake zaune a cikin ofishin sa, ya kalli P.A ɗin
Indabo ya ce "Ɗan sake duba na da kyau mana malam"
P.A ya ce "Na kalleka"
"Shekaru huɗu rak idan Allah ya bani aron rai, suka
rage mini nayi retire, a tarihin aikina, ban taɓa karɓar cin hanci na aikata
son zuciya ba, ban ƙi ba wasu lokutan ina karɓa in yi abun da ya dace, duk da
hakan ma saɓa doka ne. Ba za a haɗa kai da ni ayi rashin albarka ba, a tozarta
harkar shari'a ba, idan na ci amana na tsayawa ƙarya a duniya, wa zai tsaya ni
a kotun Allah idan zai yi mini hisabi, a cikin kai da uban gidanka, waye zai
ƙwace ni? Tambayarka nake yi, na ce waye zai ƙwace ni? Kotun Allah saɓanin
tunanin ɗan Adam ce, kuma wallahi dukkanin mu, sai mun tsaya a wannan kotun,
kotun da bata buƙatar lauya, ɗan sanda balle ka yi tunanin bayar da cin hanci.
Duk da na san badaƙalar da ake tafkawa a cikin harkar
shari'a, na yi mamakin wasu abubuwan da yarinyar nan ta din ga faɗa, yar cikina
ce amma ina sauraron programs ɗin ta, kuma ko kaɗan ban ji haushin yadda take
tsigalewa aikinmu ba, yadda ake amfani da mu, ake aikata abun da ake so. Babu
wani rashawa da zaku bani na karɓa, zan yi abun da ya dace ne kawai, idan kuma
aka sake zan yi abun da rai zai ɓaci. Kai in taƙaice maka doguwar magana zuwa
gajera, daga sama aka yi mini magana a kan lallai nayi abun da ya dace a kan
shari'ar nan, ba a buƙatar kuskure a ciki, kuma ko ba haka ba, ni sonake na
gama aiki na ajiye shi lafiya"
P.A ya jinjina kai ya miƙe tsaye, ya ce "Hakan ma babu
laifi, muna godiya sosai" ya juya ya fita daga office ɗin.
***
Missed call kusan uku Nabila ta yi wa Viper, amma bai ɗaga
ba, sai da ranta ya sosu, ta rasa irin wannan murɗaɗɗen hali nasa, gashi ko
zata yi fushi da shi, na ɗan lokaci ne, ana jimawa ta manta.
Viper kuma fitowar sa kenan daga wanka, ya kalli wayarsa ya
ga missed calls ɗin ta, har guda uku.
Bai kula ba, ya fara ƙoƙarin neman kayan da zai saka, wayar
Walid ta far ringing.
Walid ya ɗaga yayi sallama, ta amsa ta ce "Oga walid
barka da wannan lokaci"
"Yauwwa barkanmu barrister, ya aiki ya jama'a"
"Alhamdilillah, ina ta kiran Viper ya ƙi ɗagawa, wai ni
ko wani laifin nayi masa ya tsane har haka ne?" Walid ya kalli
Viper, sannan ya ce "Wanka yake yi yanzu ya fito"
Ta ce "Ai dama kai kare shi zaka yi, baka taɓa yadda
yayi laifi, ko yayi laifin sai ka kare shi, dama magana nake son mu yi da shi,
kuma na ma fasa barshi kawai, sai anjima"
Da sauri Walid ya ce "A'a ba za a bari ba, ko na haɗa
ki da shi?"
"Ba zai kulani ba ai na sani, shiru zai yi mini kamar
kurma, in dai yana lafiya shikenan sai anjima"
"Kin ga Nabila, tsaya ki ji mana, gaba ɗaya ke ce baki
fahimci Al'amin ba, ba wulaƙanta ki yake yi ba"
"Ba wulaƙanta ni yake yi ba kace? Idan ba wulaƙanci ba,
mai zai sanya ya ce baya so na, wallahi ban taɓa cewa ina son wani ba, ina
zaman zamana, ƙaddara da rashin ya ja ni ya kai ni har in da yake, yayi ta
wulaƙanta ni bai damu da rayuwata ba, amma ko haushi bana ji naƙi zuciya, ko
kwana biyu nayi ban ji ɗuriyarsa ba sai na damu" ta ƙarasa maganar cikin
damuwa, da alama abun ya na damunta sosai da sosai.
"No, Viper mutumin kirki ne, kuma abun so, in dai ka
zauna da shi zaka so shi, saboda yana da halaye masu kyau sosai da sosai, kina
kallon muma da muke tare da shi, wasu lokutan haka yake yi mana, amma muna duba
halaccinsa a garemu ne, kema baki fahimce shi bane"
"Ba wani ban fahimce shi ba, kalli yadda na shiga siraɗin
gobarar nan, na zo nayi hatsari, amma sannu kawai ba wani abu ba, ya kasa ce
mini"
Walid ya ce "Ki yi haƙuri, halinsa ne a haka, amma zan
iya ce miki, bayan iyayenki, akwai wanda ya kai shi shiga damuwar abun da ya
faru da ke"
"A hakan? In kusa rasa raina har karo biyu?" Babu
tsammani Viper ya fizge wayar hannun Walid, ya kashe ya dire masa ita, ya fice.
Walid ya bishi da kallo yana kallon ikon Allah, shi bai rarrasheta ba, kuma ya
hana a rarrasheta.
Ko da ya fice daga gidan, wayarsa yake kallo, yana jin
tamkar ya kirata, har ya ɗaga ya kalli lambarta, sai kuma ya tsaya ya cigaba da
kallon lambar, fasawa yai kawai ya mayar da wayar aljihunsa ya yi gaba.
***
"Arfa, wai meyake damunki ne duk kin wani rame kin
tsotse" Sumayya ta yi maganar tana ƙare mata kallo.
Baba magajiya ta ce "Gara dai ki yi mata, ko ta ji,
taƙi gaya mini meyake damunta, sun samu saɓani da babanta, kuma sun shirya,
amma kwanan nan sai ƙarewa take yi kamar kuɗin guzuri, ko abincin kirki ba ta
ci, duk ta zube sai uban nono da take kayansa kamar ya rinjayeta" Sumayya
ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "Wallahi kuwa baba magajiya, da 'yar ƙibarta
tafi kyau, haba jarumar mu, idan ki ka saka damuwa a ranki, mu wa zai bamu
ƙwarin gwiwar? Muje mu zanta na ji menene ya faru".
Suka tafi ɗakin Nabila, Nabila ta zauna a gefen gado,
sumayya ma ta zauna ta ce "Gaya mini menene? Naji baba magajiya ta ce kun
yi faɗa da Abba, me ki ka yi?"
Ta kalli sumayya ta ce "Sumayya haka soyayya take
dama?"
"Soyayya kuma, ita ta hana ki cin abincin ki ke
ramewa?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba ita ta hana ni cin abinci ba,
damuwoyi ne kashi-kashi suka sha mini kai sumayya.
Da fari nifa zuciyata na azalzalata a kan son ganin
mahaifina, ina son sanin waye shi, ko yaya yake a bani dama na san shi, ni zan
fara bincike ta ƙarƙashin ƙasa da kaina"
"A'a Nabila, kar Abba ya sani ransa ya ɓaci"
"Sumayya ya zan yi, ni ba na son na mutu ban san babana
ba, idan a gidan babana nake, wani abun ba za ayi mini shi ba"
"Naji, zamu dawo kan wannan batun, naji kina maganar
soyayya"
Ta numfasa ta ce "Ƙaddara ta kaini ta baro
sumayya"
Sumayya ta waro ido ta ce "Kamar yaya?"
"Son abun da ba zan samu ba nake yi"
"A'a kar ki ce haka, amma wa ki ke so ɗin tukuna ma
dai"
Nabila ta tashi, ta saka key, ta buɗe wardrobe ɗin ta, ta ɗaukko
file ta zo ta ajiye a gaban Sumayya.
Sumayya ta ɗauka ta fara bubbuɗewa, ta tsaya ta gama dubawa
sannan ta kalli Nabila cikin matsananciyar kiɗima da tashin hankali ta ce
"Ban gane me ki ke nufi ba haryanzu Nabila"
Nabila ta goge hawayen da ya gangaro mata, ta sunkuyar da
kanta ƙasa.
Ta daki kafaɗar Nabila ta ce "Kin san in da mutumin nan
yake, da gaske haɗuwa ku ka cigaba da yi da shi, har ki fara son ɗan
daba?"
"Ɗaga murya zaki yi, ki tona mini asiri Sumayya"
"Nabila wannan hauka ne, ga yaya Nasir a cikin gida,
yana ta haƙilo yana fama, ko ɗazu an kawo mana sanarwa, yan sanda na cigaba da
nemansa ruwa a jallo, duk wanda ya nuna in da yake, ko in da za a same shi,
akwai kyauta, kawai ki ke zuwa in da yake, idan aka kama da ke fa? Menene
sunanki bayan mun gama fitowa duniya muna ɓaɓatu da nuna mu masu goyon bayan
gaskiya ne?"
"Ban damu da abun da duniya za ta ce ba, ko yadda za a
kalleni ba, zan tsaya a bayan gaskiya ne duk rintsi duk wahala. Sumayya zan
tsayawa Aminu Viper, kuma kamar yadda ki ka faɗa tabbas ina haɗuwa da Viper,
kuma na san in da yake, amma ba zan taɓa bari hukuma ta kama shi ba"
Sumayya ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wace
lalacewar ce ta same ki har haka Nabila? Kina ya mace, ki ke zuwa wurin ɗan
daba mashayi, dan ta'adda?"
Ta girgiza kai ta ce "Sumayya ƙaddara ce, kamar yadda
na gaya miki da farko, idan zaki rufa mini asiri ne shikenan, idan kuma tona
mini asiri zaki yi, kina da zaɓin yin wanda ya dace". Ta tashi ta nufi
wardrobe ɗin ta, ta mayar da file ɗin.
"Kai!! Nabila ki canza tunani, ni ba zan bari ki cutar
da kanki, ina kallonki ba"
"Ai ba gaya miki na yi, dan ki bani shawara ba, na riga
na yanke abun da nake ganin shi ne dai-dai"
Sumayya ta ɗauki jakarta ta fice, tana zare idanunta, dan
tabattar da ba mafarki take yi ba, dan bata taɓa tsammanin wauta da haukan
Nabila ya kai wannan limit ɗin ba.
Bayan tafiyarta, Nabila ta duba wayarta, ta ga announcement ɗin
jami'an tsaro, ta ɗauki, jakarta ta saka kayanta, ta faki ido ta fice daga
gidan.
Sumayya kamar za ta yi kuka, ta marairaice a waya ta ce
"Sir dan Allah ka yi wani abu a kai, rayuwarta zata shiga cikin hatsari da
matsala, za ayi mata kallon mutuniyar banza, ɗan ta'adda take shirin kasadar
karewa"
Yayi murmushi ya ce "Sumayya ƙawarki ba ta ji, bar ta
ai ɗaukaka take nema, mu yi mata fatan nasara"
"A'a sir, dan Allah ba zata iya ba"
Kankarofi ya ce "Haka ta ce miki? She can do it, ni na
bayar da file ɗin sa aka kai mata, ki ja da baya ki tayata da addu'a, in da ki
ka ga ana buƙatar taimakona kuma, ki yi mini magana kar ki yi ƙoƙarin dakatar
da ita, wannan gargaɗi nake yi miki" ya kashe wayar.
Sumayya ta ce 'Naga ta ta kaina ni sumayya"
***
Suna zazzaune a ɗakin, suna ta shan sigari, ya ɗaga kai
kawai ya ganta a tsaye a ƙofar ɗakin, tana kallonsu, ko sallamarta bai ji ba.
Ta rame sosai da sosai, duk da fuskarta kawai ake iya gani,
saboda facemask.
Ganin ya tsareta da nasa idanun, ya sanya ta sunkuyar da
kai, waiwayawa su Walid suka yi, su ga me yake kallo, suka ga Nabila a tsaye.
Liti ya ce "Su 'yar anace ce da yamaccin nan ashe"
Walid ya ce "Afuwan barrister, kin zo mun cika wurin da
hayaƙi, gashi ke ba kya son hayaƙi"
Viper ya yinƙura ya tashi, ya ce "Ki tsaya karki shigo,
ki zo kina sumewa mutane sai an ta jagwalgwala ki" yayi maganar yana
nufota, sai da ya tunkarota sosai, sannan ta lura rigar jikinsa sunansa ne a
jiki, an rubuta Viper, da zanen kan macijiya a jiki ta fito da harshenta.
Ya fito ya tsaya, yayi crossing lega ɗin sa, irin ina
saurarenki.
Banza tayi masa ita ma, suka cigaba da tsayuwa, sai dai
tsayuwar bata damunsa, ita kuwa ta fara gajiya, yana zuƙar sigarinsa, yana
fesarwa a gefe.
Hannunsa ta kalla ta zare sauran sigarin ta yar a ƙasa, ya
kalleta amma ta haɗe rai.
"Ina jinki ya aka yi?"
"Alhaji mu'azzam da ku ka haɗu, dama ka san shi
ne?"
"Haka ya ce miki?"
"A'a, tambayarka kawai nake"
"Ki bar maganar sa kawai"
"Saboda me?"
Ya ce "Saboda haka na ce"
"Nifa ina tsoron sai na je gaban kotu, in tarar da wasu
abubuwa da ban san da su ba, na rasa yadda zan ɓullowa lamarin, ka gaya mini
shi menene alaƙarka da shi?".
A hasale ya ce "Na ce ki bar maganarsa ko? Na san shi,
amma sanin waye shi ɗin ba shi da wani amfani".
"Shhhh ka daina yi mini shouting, ka yi shiru ka
saurare ni, aikina nake yi malam" tayi maganar tana kallon ƙwayar idon
Viper.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cigaba yayi da kallonta, ita kuma ta kasa sake ɗaga idonta
ta kalleshi.
Yanayinta ya nuna sosai akwai damuwa a tare da ita.
"Kin fasa cewar ba zaki tsaya mini ɗin ba kenan?"
Ta jinjina masa kai ta ce "Eh, idan ma na fasa,
zuciyata ba zata nutsu ba, alƙawari ne da nayi, yakamata na cika, ko ba dan
kowa ba, dan wadda aka kashe ba da hakkinta ba" tayi maganar ba tare da ta
kalleshi ba.
Ya jinjina kai, a hankali ya furta "Ina zuwa"
Ya koma cikin gidan, tana tsaye ta bi ƙofar da kallo, ya
fito ɗauke da jaka a hannunsa, ya ce "Muje" ba tare da ta san in da
zasu ba, ta bishi. Sai da suka yi nesa kaɗan da gidan, sannan ya ja ya tsaya
ita ma ta tsaya.
Ya samu wuri ya zauna, yayi mata nuni, ita ma ta zauna, ta
sauke tata jakar daga bayanta, hannunta ɗaya an naɗa mata bandeji, in da ta
samu gocewar ƙashin, sai dai hannun rigarta ya rufe wurin.
Ta ciro system ɗin ta, ta ajiye ta ajiye wayarta.
Ya zuba mata ido, bai yi magana ba, sai da ta ɗan ɗago ta ce
"Wace shaidar da wace shaidar ce da kai, and dan Allah kar ka ɓoye mini
komai, saboda kar sai mun je kotu, wani abu da ban san da shi ba, ya taso daga
baya".
"Me ki ke son sani?"
"Shaidunka, da ka ce kana da su"
Ya ɗan lumshe idanunsa, sannan ya buɗe ya ce "Madaki,
duk na yi masa illa, sai kuma babban yaronsa lakwari, duk suna wurina"
"Garkuwa kayi da su kenan?"
"Kusan hakan"
"Laifi ne fa ka aikata yin hakan"
Ya tari numfashinta ya ce "In sake su kenan?"
Ta ɗaga idonta, amma taga kallonta yake yi.
Jikinta ya ƙara sanyi, maimakon ta mayar da hankali a kan
abun da take yi, sai hannunta ma ya hau rawa, wata irin ƙaunarsa ta din ga
fizgarta, ji tayi tamkar ta ɗurawa kanta zagi.
Ya ɗan matsa kusa da ita, yana kallon fuskar system ɗin ta.
Ta takure jikinta, ƙamshin turaren sa da warin sigari suka cika mata hanci.
Murya na rawa ta ce "Viper"
"Mmm"
"Ka sha sigari ko?" Yayi shiru bai bata amsa ba.
"Kar ka bari lafiyarka ta taɓu bamu gama shari'ar nan
ba, kuma kaga ya fara taɓa maka internal organs, an ce hantarka ta
kumbura"
Yayi shiru bai yi magana ba, sai kallonta kawai da yake yi.
"Akwai abubuwa da yakamata ka gaya mini, amma kamar
kana ɓoye mini, yakamata idan kana ɓoye mini ka gaya mini, kar wani abu ya bamu
matsala daga baya"
Har ta fitar da ran zai yi magana ya ce "Kamar
me?"
"Suwaye suke goge laifukan ka idan ka yi? Ranar da muka
je gidanka, ya aka yi ka gane jami'an tsaro a fararen kaya, har muka tsere
musu? Wannan rigar da ka yaga a asibiti ta mecece? Kuma me kake yi da wayata da
kake connecting?"
Viper ya yi gyaran murya ya ce "Wasu tambayoyin ba su
da alaƙa da abun da yake gabanmu, amma na gane jami'in tsaro a farin kaya,
saboda ni tsohon mai laifi ne, ba lokacin na fara aikata laifi ba, dan haka duk
wani nuƙu-nuƙun jami'in tsaro sai na gano shi. Rigar da ki ke magana a kai,
bata da alaƙa da abun da zaki yi a court. Wayarki kuma ina connecting ina duba
wasu location, da tura saƙonni. Mai goge laifukana kuma ban sani ba. Sai kuma
me?"
Nabila ta ce "To shikenan, nan da kwanaki biyu zaka ji
ni in Sha Allah, zan har haɗa abun da nake buƙata, saboda yayana ya sakani a
gaba da yawa"
"Good luck" ya faɗa a takaice, tamkar ta kurma
ihu, ko sannu ya jiki bai iya yi mata ba, dan takaici ta tattare system ɗin ta,
ta yinƙura ta tashi ta ce "Sai anjima" ya jinjina kai.
Jiki a sanyaye take takawa, kamar mara karsashi, ya waiwaya
yana kallonta, yadda take ɗaga hannunta tana saukewa, ya tabbatar masa da kuka
take yi. Sai da yaji zuciyarsa ta motsa, shi gaba ɗaya tausayinta ma yake ji.
Tana tafe a titi, barrister Habib ya kirata, ta ɗaga ya ce
"Nabila kina ina ne?"
"Meyafaru?"
"Wai yayanki yaje ɗaukar ki, an ce masa mun fita, ya
kira ni, wai muna ina?"
Guntun tsaki ta ja, ta ce "Rabu da shi dan Allah"
"A'a kamar yaya na rabu da shi? Kina ina ne, ni ya
addabe ni"
"Wani wuri naje, ina kan hanyata ta komawa gida, ina
son ma ganinka urgent, amma sai Allah ya kaimu gobe"
Ya ce "To Allah ya kaimu"
Ta amsa da "Amin"
***
Naja'atu Bunkure ta dubi Indabo ta ce "A haka ana
wannan yanayin zaka koma Abuja?"
"To idan ban koma ba yaya zan yi, matsaloli sai kuma
cakuɗewa suke yi"
"Dole fa a nemo Abdul, kuma ta wani fannin rashin kashe
yarinyar nan yayi amfani, amma kuma ya tafka shirme da hauka, dan me zai ɗauketa
ya je ya ɓoye, kuma saboda wulaƙanci yaje har gidansu da kansa, dole fa a nemo
Abdul ya fito da yarinyar nan"
"Kin san ya kashe wayoyinsa gaba ɗaya, kin san a haukan
yaron nan ce mini yayi, wai idan ya auri yar party chairman bayan aure zan bari
ya auri wadda yake so, kawai ya yi mini wannan maganar, ban sani ba ita yake
nufi zai aura ko wata oho"
"Taɓɗijan, lallai Abdul wannan karon ya ɗebo ta da
zafin gaske, wallahi sai an yi taka tsantsan kafin a warware wannan shirmen da
yayi"
Indabo ya yakice gumi ya ce "Na rasa makama gaba ɗaya,
ga rayuwarsa na cikin hatsari, ya haɗu da mai zamani, wai yaron da ake ta nema
ido rufe, shi ne yake yawon sa har da zuwa asibiti, tsoro ma nake ji, kar
Vipern yayi masa wani abun"
Naja ta ce "Yanzu neman Abdul, shi ne abu mafi a'ala,
ina tsoron yayi wani abun da zai tona mana asiri"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ni ɗan da na haifa, nake ta
fafutuka a kan rayuwarsa yake neman ya kware mini baya, saboda mace, aishikenan
da ina da wata hanyar da zan fito da jafar, da ƙyale shi zan yi, idan abun da
yake bi a jikin nata ya gundure shi, sai ya dawo hayyacinsa"
Bunkure ta kwashe da dariya ta ce "Barewa bata gudu...
A fusace ya kalleta, ta haɗiye dariyar, tana mazewa.
***
"Nabila ina ki ka je daga wurin aiki? An ce kun fita da
barrister Habib, na kira shi ya ce ba kwa tare.
"Eh, uzuri ne ya kamani, na je prison ganin wanda nake
karewa ne, ko yanzun ma kana zargin wurin Viper na je?" Kawai ya gyaɗa kai
ya fita.
Ta kwanta ruf da ciki, ta buɗe wurin da ta ɓoye videon da ta
yi wa Viper, ta din ga kallon hotunan da video, tana ƙara jin yadda ƙaunarsa
take mamaye zuciyarta.
Ta yi shiru, bata taɓa zaton zata tsinci kanta a irin wannan
yanayin ba, duk yadda take kallon kanta, a matsayin mai class taga namijin da
ya ƙure wa ajinta gudu.
Ta dinga shafa fuskarsa, ta kan screen ɗin wayarta, ta
lumshe ido tana tuno muryar sa, da a zahiri mai ban tsoro ce, amma a baɗini daɗin
sauraro take yi mata, da sanya mata nutsuwa.
Ƙarfe takwas da rabi, tana ofishinta, tana jiran barrister
Habib.
Yana isowa, ta tashi ta tafi, ya ce "Yar ƙwalisa, yaya
aka yi ne? Ya hannu"
Ta zauna ta ce "Hannu Alhamdilillah, yaya Habib"
"Na'am ƙanwa Nabila"
"Kamar yadda baka gajiyawa da ni, na sake dawowa neman
alfarma a wannan karon"
Habib ya ce "To Nabila, me ni ke so?"
"Wataƙila wannan ta zama alfarma ta ƙarshe zan neman a
wurinka, duk da akwai haɗarin gaske, amma yanzu burikana biyu ne, bayan ganin
bayan Bunkure foundation, sai wanke Viper daga zargin da ake yi masa"
Da sauri ya ce "Kamar yaya?"
"Kamar yadda nake gaya maka, bana nufin na sanyaka a
matsala, kamar yadda ka taimakeni kwanaki a kansa, yanzu ma ina neman
taimakonka, dan Allah"
"Nabila, wannan wasa da rai ne fa, ke ya aka yi ki ka
san ba shi da laifi? Tayaya zakinkare mutumin da hukuma take nema ruwa a
jallo?"
Nabila ta numfasa ta ce "Zaka ga ta yadda zan yi, ni
dai haɗin kanka nake buƙata da taimakonka"
Ya girgiza kai ya ce "Nabila matana biyu fa da yara
uku, haka kurum ki saka su zama zawarawa da marayu, na gaya miki case ɗin sa
yayi involving manya haka kurum ki ja mana fitina muna zaman lafiya"
Cikin marairaice wa ta ce "Dan Allah yaya habib, ba zan
bari sunanka ya fito ba, dan Allah copyn file ɗin sa nake so, da aka yi masa
shari'a shikaɗai nake buƙata"
Ya ce "Taɓɗijan, ke kin san uban process ɗin da na bi,
aka baki ki ka gani wancan lokacin, balle yanzu kicw copy ki ke so"
"Dan Allah ka taimake ni barrister Habib"
Yayi shiru sannan ya ce "Gaskiya sai kin bani lokaci,
dan wanan aiki ne da yake buƙatar ɓoyayyiyar gwagwarmayar "
Cikin farinciki ta ce "Zaka nemo mini ɗin?
"Zan jarraba ne na gani idan zai yiwu, ba alƙawari nayi
miki ba"
Ta miƙe cikin farinciki ta ce "Na gode sosai, Allah ya
saka da alkhairi ya raya zuriya"
Ya amsa mata da Amin.
***
Ramma tana ta gogewa Abdul labcourt ɗin sa, ya daɗe a tsaye
yana kallonta, wani irin matsanancin tausayinta ne ya mamaye zuciyarsa.
Ya ƙarasa ya zauna ya ce "Rahama" ta ɗago ta
kalleshi.
"Ina da masu gugu fa, kaiwa nake yi ayi mini, ki ke
wahalar da kanki"
"Ka ce zaka yi tiyata, shiyasa nake goge maka"
Yayi murmushi ya ce "Ai ba da labcourt muke shiga
tiyata ba, kayan tiyata daban suke"
Ta ce "Ok, duk da haka ka saka wani lokacin"
Ya jinjina kai ya ce "Rahama menene babban burinki a
rayuwa ne?"
Ta sunkuyar da kai ta ce "Ka mayar da ni wurin
mamana"
"Na san da wannan, zan mayar da ke, burinki na
rayuwa?"
Ta ɗago idanu ta kalle shi ta ce "Babu"
Ya ce "Kamar yaya? Kowane ɗan Adam yana da buri da yake
son cimma a rayuwarsa"
Rahama ta kashe socket, ta kalleshi ta ce "Wace
rayuwar? Rayuwar da ka gama kassarawa wane buri ne yayi mini saura? Ka mayar da
ni wurin mahaifiyata na ƙarasa rayuwata shikaɗai ne roƙona a gareka, amma ba ni
da wani sauran buri da nake da shi, gaba ɗaya rayuwar ta fita daga raina, babu
abun da yake burgeni yake bani sha'awa".
Abdul ya koma kusa da ita ya zauna, ya ɗan tsura mata ido,
ita kuma ta kawar da kanta gefe ɗaya.
"Dukkanin mai rai baya fitar da rai, da cimma burikansa
na rayuwa, na san ni ne musababbin rushewar naki, amma haryanzu ina dana sanin
abun da na aikata, amma zan cika miki burinki Rahama, zaki koma makaranta kiyi
karatu mai zurfi in dai muna tare in sha Allah, makaranta mai kyau zan mayar da
ke, na gyara makarantun garinku, kuma an karɓi ƙudurin gyaran hanyarku, aiki
yayi nisa na yi muku boreholes kamar yadda nayi miki alƙawari, idan aka kammala
zan nuna miki"
Maimakon ta yi magana, kawai sai ta fashe da kuka.
Cikin damuwa ya ce "Rahama menene kuma?"
"Ni duk bana son wannan abubuwan, kawai na koma gidanmu
na ƙarasa rayuwata, babu wani abu da zan zama a rayuwa da zai katange ni, daga
tsangwamar da zan fuskanta a cikin al'umma, wannan ɗabi'a ce ta hausawa"
"Ina tabattar miki da idan muna tare, babu wanda zai
tsangwame ki, wasu shirye shirye nake yi ne, da sun tabatta in sha Allah zamu
je ki ga mama, amma babu maganar rabuwa tsakaninmu, ba sai na bar ki a tsakanin
hausawan ba ma zau yi miki, ki daina damuwa Please bana so"
Wayarsa ce ta fara vibrating, ya ɗaga ya ce "Yeah Salim
ya ake ciki ne?"
"Wai ina ka shiga ne? Mummy ta kira saifu a waya, wai
an nemeka a waya an rasa, ya ce mini shi ma baya samunka a waya, ni kaina
kwanana biyu kenan ina nemanka yanzun ma ban zaci zan sameka ba, nace bari na
jarraba kiran wannan layin naka"
Abdul ya numfasa ya ce "Akwai damuwa ne Salim, mu haɗu
a gidana na by pass"
"To shikenan, ka san nina har ta gaji da nemanka ita
ma, har clubs ka daina zuwa, gidanka da take samunka ma yanzu baka zama, kuma
ta daina samun wayarka, na ce mata kayi busy ne da shirye shiryen
siyasarka"
Abdul ya ce "Manta da ita, zan je asibiti zan yi tiyata
da daddare, idan na kammala ko kafin na tafi, sai mu yi magana sai mu haɗu"
"To shikenan, sai na ji ka"
***
Walid ne ya ƙarasa in da Viper yake a zaune a kan dutsen
nan, yayi shiru yana nazari.
Ya zauna a kusa da shi ya ce "Sannu da hutawa"
"Yauwwa sannu da zuwa"
"Yauwwa, tunanin me ka ke yi ne?"
Viper bai ba shi amsa ba ya ce "Meye labari?"
"Labari, yan unguwar su madaki, sun addaba wa yan
unguwarmu, naji ɗan mama ya ce zai shiga unguwar, sai kuma na je maɓoyar
madaki, na tarar baya nan, ko dai ya tafi wani wurin bamu sani ba?"
Viper ya ɗan kaɗa kai ya ce "Kar ka damu na san in da
yake"
Cikin mamaki ya ce "Ka san in da yake kamar yaya?"
"Kamar yadda na ce" ya faɗa a taƙaice.
Shiru ya wanzu na wani ɗan lokaci, Viper ya ce "Jibi
yarinyar nan zata shiga kotu, ta kuma ce a kwankin nan zata fara shari'ata, i
need to assist her, a haka ma rayuwarta na cikin hatsari, muddin ta shiga case ɗin
nan matsaloli zasu ninku fiye da baya, akwai buƙatar na taimaka mata
sosai"
Walid ya ce "Haka ne, Allah ya tabattar mana da
alkhairi, ya bamu dukkanin nasara, ka yi yanci mai zamani, ka daina wannan
zaman ɓuyan"
Viper ya dafa kafaɗar Walid ya ce "Mai laya"
"Na kiyayi mai zamani"
"Mu huta wannan zaman ɓuyan zaka ce, idan Allah ya bamu
nasara, in ga kun tsaya da ƙafafuwan ku, na aurar da kai, da wancan sarkin faɗan"
Walid ya ce "A'a, ka yi yanci, muga farincikinka da
walwalarka sun dawo dai, mu dai mu cigaba da gurgura rayuwa"
Viper ya girgiza kai ya ce "Aure yana da daɗi mussaman
idan ku ka yi dace kamar yadda na yi. Ni na taɓa yi na more shi, kuma yakamata
ku yi, idan na bari ku ka ƙarar da rayuwarku a kan hidimata kawai ban yi wa
kaina adalci ba muhsin"
Walid ya ce "Taɓ anya na taɓa jin ka kira ni da ainihin
sunana kuwa?"
Viper ya yi murmushi ya ce "Ka tuna mini da watarana,
da 'yar madara ta sakani a gaba, ta ce sai na gaya mata ainihin sunayenmu, na
ce mata ni Muhammad Al'amin, kai Muhsin, liti Abdullahi. Ta rafka salati, ta ce
kalli yadda duk kuka mayar da sunayenku wani iri, har ma ɗan gara yaya walid,
duk da shi ma wataran mai laya kake ce masa, gaskiya ku canza hali, sunayenku
masu daɗi, amma duk kun canzawa kanku suna. Na ce ;Sunan waye yafi daɗi, tayi
murmushi ta ce na mijina, na ce yauwwa ke ma sunanki mai daɗi an saka miki wani
iyayi daban. Muhsin ku yi aure akwai alfanu a cikin aure, haryanzu na kasa
manta rayuwar cikin aure, na san abu ne da ba zai bar ƙwaƙwalwata ba. Ina son
naga kun samu cigaba a rayuwar ku, ba zan yi alfahari da ku ƙarar da rayuwarku
a kaina ba"
Walid ya kalli Viper ya ce "Al'amin, ko mai muka yi
maka a rayuwa ka cancanta, ai duk ɗan halak baya manta alkhairi, idan kai ka
manta ni ba zan manta ɗawainiyar da ka yi da ni da mahaifiyata ba, haka zalika
mutuntawar da matarka tayi mana"
"Muhsin, mahaifiyar ka, mahaifiyata ce, ka daina saka
wannan a lissafi"
Walid ya ce "Na daina, amma dai sai mun fara aurar da
kai tukuna, farincikin ka da walwalarka su dawo, sannan mu san abun yi mu
ma"
Viper ya girgiza kai ya ce "Bani da ra'ayin kuma yin
aure a rayuwata, wancan ma tsautsayi da ƙaddara ne ya saka aka yi shi"
Walid ya yi murmushi ya miƙe ya ce "Wannan kuma,
ƙaddarar tausayi da soyayya zai saka a ayi shi" har Walid ya yi gaba,
Viper ya miƙe da sauri ya ce "Ina ba zai yiwu ba, jauhar ce kawai a
zuciyata" kawai walid ya ɗaga masa hannu ba tare da ya waiwaya ba ya yi
gaba yana dariya.
***
Salim ya kalli Abdul da ya shigo a gajiye, ya zauna ya ajiye
labcourt ɗin sa a gajiye.
"Yaya ne mutumina, na ganka a wahale"
"Aiki na sha yau ɗin nan, na je asibiti ya kai huɗu, na
duba wanda na yi wa tiyata, sannan na yi wa wasu aikin sai godiyar Allah"
Salim ya yi murmushi ya ce "Sannu, ko in ɗaukko maka
abar ne, ina da ita a mota?"
Abdul ya girgiza kai ya ce "Rahama ta san warin giya,
faɗa zamu yi da ita"
Salim ya ce "Wow, to ko abinci zamu je ka ci?"
Nan ma ya girgiza kai ya ce "Ina da special cook a
gida, yarinyar nan dar ce" yayi maganar yana kashingiɗa.
Salim ya kwashe da dariya ya ce "Allah mutumina, ta
saduda kenan?"
Abdul ya yi murmushi.
"Ina jinka, bani labari"
"Salim, kai ka san komai, tun da ka tafi fa babu
labarin mahaifiyar yarinyar nan, gashi ta matsa mini na mayar da ita gida, ni
ba mayar da itan ne ya dame ni ba, na fara yi wa daddy bayani ko zai fahimce
ni, ya hau ni da faɗa da zagi, kuma wai lallai sai na kai masa ita, sai an
kaita kotu ta bayar da shaida, ni fa na yanke shawarar zan ɗauke ta mu ƙara
gaba, har takarar ma bana so. Wallahi Salim ban taɓa dana sanin aikata wani abu
a rayuwata ba, irin yi wa rahama fyaɗe ba, kuma ban taɓa jin so da ƙaunar wani
abu a raina ba, kamar yadda nake jin son ta, ya mamaye zuciyata ba, Salim
wallahi ba zan iya rabuwa da rahama ba, ba wai ina sonta da jikinta ko wani abu
ba, ita ɗin nake so"
Salim ya ce "Ƙarya ne malam, mun san komai fa"
Abdul ya yi murmushi ya ce "Ita ta sani ai, ba zan yi
maka ƙarya ba"
Salim ya ce "Kar ka damu, na fahimta maganar ka ɗauketa
kayi gaba bai taso ba fa, ka zauna ka yi wa daddy cikakken bayani"
"Salim na san waye mahaifina ciki da bai, muddin na
fito da rahama, zai iya salwantar da rayuwarta, ita kanta mahaifiyarta ina
tantama a kan bashi ne ya ɗauke ta ba, ni kuwa a kan rahama sai dai ayi duk
wadda za ayi"
Salim ya waro ido ya ce "Da iyayen naka? Abdul yaushe
ka koma haka ne? A cikinmu duk rashin nan da kai da Saif kun fi mu mutunta
iyaye ma da jin maganar su mussaman kai, meyasa ka ke son canzawa saboda
mace?"
"Kamar yadda take yawan faɗa, na riga na ɓata
rayuwarta, dan haka ba zan bari a sake tagayyara rayuwarta ba, ina son rahama
irin son da nake son na ƙarasa rayuwata da ita, idan Daddy ya cigaba da
matsawa, ba zan yi wancan auren ba"
Ya girgiza kai ya ce "Ba za ayi haka ba, ka je ka fara
maganar da mahaifiyar ka, ko zata fahimceka"
Ya ce "Taɓ ayi sha'ani kawai, zan je zanji kiran da
yake yi mini amma in fito da rahama dai, gaskiya ban ji zan iya ba"
"Amma fa Abdul mun tafka shirme a gaban uwar yarinyar
nan, anya zata yafe maka kuwa? Ga tsiyar da ka je ka kuma yi daga baya"
Abdul ya numfasa ya ce "Sharrin giya ne, da gigin
arziki da nake ji da shi, nake jin kamar zan iya taka na ƙasa da ni, ni komai
zata yi, mini tayi mini amma ban da raba ni da yarinyar nan".
Salim ya ce "Lallai ka faɗa da yawa mutumina"
"Rahama, akwai haƙuri, duk da ina cin zagi a wurinta da
tsinuwa, amma da ta ganni cikin rashin lafiya, ko damuwa hankalinta yake tashi,
ita take dafa abincin da zan ci, yau har da yi mini guga. Nifa yarinyar da aka
ce za a haɗa ni da ita, gaba ɗaya bata yi mini ba buɗaɗɗen ido ne da ita, gara
a bar ni da rahaman dai, na san koma menene ni ne sila"
Salim ya jinjina kai.
***
Nabila ce a tsaye a gaban court, tana ƙoƙarin fara gabatarwa
da mai shari'a appeal ɗin su, ta kalli barrister Habib, ya jinjina mata kai
alamar bata ƙwarin gwiwa, ta tsaya ta gabatar da kanta cikin harshen turanci,
tare da fara karantowa kotu koken su.
Na kotun ta yi duba da rubutaccen jawabin da suka gabatar, a
kan hukuncin da kotun farko ta yi, bisa ga wasu kurakurai da suke ganin an
tafka a wurin yin shari'ar, na rashin bayyanar wadda abun ya faru da ita a
gaban kotu, da rashin gabatar da medical report ta hannun ɗan sandan da kuma
likitan da ya tabattar da yin laifin ba.
Hakazalika a hujjojin da suka gabatar a kotun farko, akwai
sautin murya, na mahaifiyar ramma tana koken a kawo mata agaji, domin kuwa
wanda ya yi mata fyaɗe ya dawo ya ɗauke ta, idan kuwa haka ne, wanda ake zargi
ba shi ne ya aikata wannan laifin ba, sannan kuma wanda ake zargin ya amsa
laifin ne, a sakamakon barazana da aka yi masa, da haka take roƙon kotun ta
bibiyi shari'ar da kotun baya tayi, ta tabattar da adalci"
Ta miƙa file ɗin aka miƙa gaban mai shari'a.
Suna tafe a mota tare da barrister Habib ta ce "Yaya,
gaba ɗaya jikina a sanyaye yake, gani nake wannan karon ma, ba zan yi nasara
ba"
"Bana son saurin karaya dan Allah, kin manta wadda ki
ke ƙoƙarin tunkara ta fi wadda ki ke yi yanzu? Kuma yanzu hankalin mutane da
yawa ya dawo kanki, ba common mutanen gari ba, har da ma'aikatan shari'a"
"Idan Allah ya sa na yi nasara, akwai gagarumin tonin
silili fa" tayi maganar tana murmushi.
Barrister Habib ya kalleta ya ce "Na me fa?"
"Zaka gani kai dai, ya batun case ɗin Viper, samo mini
copyn shari'ar da na ce?"
"Ai na gaya miki ba aiki ne mai sauƙi ba, ina nan ina
ƙoƙartawa, yanzu idan aka san ina ƙoƙarin samo file ɗin ma, rayuwata na cikin
hatsari"
Ta jinjina kai ta ce "Haka ne, Allah ya ba da
sa'a"
***
"Inadabo, wallahi akwai matsala muddin Abdul bai kawo
yarinyar nan ba, tun da ya ce maka tana wurin sa ya fito da ita mana"
"Naja duk wani ƙoƙari ina yi, bai taɓa bujirewa
umarnina ba sai a wannan karon, yama daina zuwa in da nake gaba ɗaya, bana
samun wayoyinsa"
"Ka san kuwa me nasararta a appeal ɗin nan yake nufi?
Yarinyar nan fa ba zata zuba mana ido ba, dole ka yi ƙoƙari fa a kai"
"Kar ki damu, zan ga alƙalin da kaina"
Bunkure ta girgiza kai ta ce "Ƙoƙarin ka ba a kan
alƙali kawai zai tsaya ba, har da wannan yarinyar, dan ni na yi iya yi na"
Inadabo ya katse kiran, ba tare da ya sake yin magana ba.
****
Babu tsammani, indabo ya shiga falon mai ɗakinsa, ya tarar
da ita tana yi wa Abdul faɗa. Yayi turus, sannan cikin tsananin ƙuluwa ya ce
"Ai dama na sani, ke ki ke goya masa baya, yake rashin mutunci"
"A'a nima fa yanzu na ganshi, nake tambayarsa ba'asin
ina ya shiga, kar ma ka ɗora mini wannan zargin"
"Wato Abdul ban isa da kai ba kenan ko? Nayi maka
magana sai ka ɗauke ƙafarka gaba ɗaya daga gidan ka daina zuwa, ina yarinyar
take?"
Abdul ya yi shiru ya ƙi magana.
"Ka gaya mini in da take, tun ban tattaka ka ba, yau an
yi appeal ɗin shari'ar yarinyar, kuma muddin aka wanke mutumin nan, babu lallai
ka tsira ba tare da asirinka ya tonu ba".
Abdul ya ce "In dai hakan yana nufin na cigaba da
rayuwa da ita, shikenan ni ba komai asirin nawa ya tonu, dan Allah Daddy ka yi
haƙuri, wallahi ba zan iya fito da rahama gaban duniya ba, ban san iya abun da
zaka yi mata ba, kuma bana fatan abun da zai ƙarasa zubar da mutuncinta, dan
kuwa fito da ita gaban kotu kamar cigaba da yayata abun da ya faru da ita
ne"
Tamkar shashasha indabo ya tsaya yana kallon Abdul, babu
kunya babu tsoron Allah Abdul yake gaya masa wannan maganganun.
Ya numfasa ya ce "Babu laifi, ni na san matakin da
yakamata na ɗauka".
***
Nabila ta shiga office ɗin ta, ta zauna ta janyo drower zata
ɗauki biro, ta ga file, ta ɗaukko file ɗin ta buɗe, kawai taga copyn shari'ar
Viper ne a ciki, sai da ta razana ta ja da baya, tana waige-waige.
A razane ta ɗauki waya, ta kira barrister Habib, ya ɗaga ya
ce "Hello Nabila"
"Barrister ka samo file ɗin nan ne?"
"A'a, ina ta ƙoƙari dai a kai, ki yi haƙuri"
"Barrister, file ɗin na gani a office ɗina"
Ya ce "Wane file ɗin?"
"Na shari'ar Viper"
"Iyee, waye ya baki?"
"Nima ban sani ba, a office ɗina na tarar kamar yadda
aka ajiye mini na Bunkure"
"Kar ki gaya wa kowa, gani nan zuwa"
Ta ajiye wayar tana sake dudduba file ɗin.
Ji ta yi an buɗe ƙofar office ɗin ta razana da sauri tana ɓoye
file ɗin, ya rufe ƙofar office ɗin, ya ƙaraso.
Ta ce "Yau ma kai ne da kanka?"
Ya ce "Eh, ko in koma ne?"
"A'a, bisimillah zauna"
Ya samu wuri ya zauna, kamar yadda a wancan karon, tayi masa
hidima, haka ma a wannan karon, ta haɗa masa tea, ta bashi abincinta da ta zo
da shi, ta bashi" wannan karon babu gardama ya karɓa ya ci.
Ta ciro file ɗin ta ajiye masa ta ce "Yau da safe aka
kawo mini shi, ban san kuma wanda ya kawo ba"
Ya karɓa ya bubbuɗe, yana dubawa.
"An fitar da sanarwar cigaba da nemanka jiya, wai
yaranka sun je sun yi faɗan daba, jami'an tsaro na ta cigaba da yayata
nemanka"
Ya girgiza kai ya ce "Ni ma na ji, sai dai ni bani da
masaniyar hakan, na samu labarin faɗa tsakanin yan unguwarmu da yan unguwar su
madaki, ban san ma me ake ciki ba"
"Zan je kotu, na nemi kotu ta hana kama ka, kafin na ɗauki
mataki na gaba"
Viper ya jinjina kai yana kora shayin hannunsa.
Ya ce "Bani system ɗin ki"
Ta ɗaukko, ta bashi ya ciro tab ɗin sa, ya ɗan jima yana
danne-danne, yayin da ita kuma take satar kallonsa kamar yau ta fara ganinsa.
Kamar kar ya tafi ta daina ganinsa, wani irin shauƙi da
farinciki ya din ga ratsa zuciyarta.
"Ki shirya, zamu je ki ga shaidar da nake da shi, idan
da abun da ki ke buƙatar sani"
Ta ce "To shikenan, ka sanya lokaci sai mu je, sai kuma
mu yi ta addu'a".
Ya ɗan daddana tab ɗin hannunsa ya ɗan yi shiru sannan ya ce
"Barka da wannan lokaci, kana magana da mai zamani ne.
Babu buƙatar yin doguwar magana, na san zuwa yanzu ka san
labarin haɗuwata da ɗanka, zuwa yanzu na san duk wani motsinsa, duk in da yake
zuwa na sani, amma ba wannan ba, akwai buƙatar ka bibiyi case ɗin ɗanka da ka
ke musayar sa da ni, a lokacin da yake Nigeria yake aikata laifuka, ina da
babban albishir gareka, Mexico na shirin miƙawa amurka shi, ya fuskanci
shari'a, kuma ina mai sanar da kai kisan kai ne hukuncin abun da ya aikata.
Na san zaka yi mamakin yadda aka yi aka kama Jafar, akwai
buƙatar mu haɗu fuska da fuska nayi maka bayani" ya katse wayar, tare da
tashi tsaye ya ce "Ka zan bar wurin nan"
Ita ma ta miƙe ta ce "Amma....
"Amma me?"
Sai ta tsaya tana kallonsa "Ina son mu yi magana ne,
ina da tambayoyi"
"Ba yanzu ba, am not safe here"
Ta ce "To muje, na raka ka gate nima fita zan yi"
ta tattaro file ɗin, da jakarta suka fito.
Tun kafin su ƙaraso, ya zuba masa ido, duk da fuskar Viper
sanye yake da facemask, amma hakan bai hana shi gane ko waye ba.
Suna ƙarasowa yayi murmushi ya ce "Barrister, wurinki
na zo, ina Abuja aka ce mini kin samu accident, sai dai na samu labarin da
sauƙi jikin, duk da haka na ce bari na zo na ganki, kuma na ganki da baƙo.
Assalamu alaikum" yayi maganar yana miƙawa Viper hannu.
(Ayi mini afuwa ji na shiru, bani da lafiya ne)
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
*Ina ma'abota bibiyar litattafan bright pens, ƙarƙashin
mikiya writers association, marubutan da suka kawo muku CUTARWA, MUNAFUKIN
MIJI, YI WA KAI, A first batch ga second batch, ƘARFE A WUTA, MUTALLAB ya fara
zuwar muku da na sa saloz sai kuma ZAYTOON DA HADARIN GABAS NA NAN TAFE SUMA A
CIKIN WANNAN WATAN, KAR KU BARI A BAKU LABARI.
Waro ido suka yi waje, jin abun da Nabila ta yi wa Viper,
liti ya doko tsalle yana faɗin "Ke! Saken da ki ka samu har ya kai haka,
mai zamanin ki ke yi wa tsawa?"
"Nayi ɗin, kai kuma a suwa?" Tayi maganar cike da
son huce takaicinta a kan liti.
Walid ya yinƙuro ya fito, amma Viper tuni ya danƙi ƙeyar
Nabila, Walid ya yinƙuro, amma Viper ya ɗaga masa hannu, ya yi waje da Nabila.
Sai da ya yi nisa da ita, sannan ya saki ƙeyarta, ta ja da
baya, tana ƙifta idanu.
Ya taka a hankali ya ƙarasa gabanta, ya tsaya ya kalleta ya
ce "Ni ki ke wa tsawa a gaban jama'a ko?"
Ta sunkuyar da kai, tana yamutsa fuska tare da tura baki.
"Karki yi ƙoƙarin tsallake iyaka, ki kaini bango, idan
na yi magana bana son jayayya, ki ƙyale wannan maganar, ki tafi da id card ɗinki
zan tura miki adress ɗin da zaki je, a asibiti ne kiga shaidan da nake da shi,
wato madaki.
Ta ɗago ta kalleshi ta ce "Kai ba zaka je ba?"
Ya girgiza kai ya ce "Tsoro nake ji, na samu labarin
yayanki ya ƙara tsananta nemana kar ya kamani"
Nabila ta ce "Hotonka yake nema, ya ce a samo masa
hotunanka, ina tunanin hotunanka za ayi sharing ace ana nemanka"
Ya ce "Duk neman da yake yi mini ma bai sanni ba, a
confused blind man" yayi maganar tare da yin murmushi. Sai da ta kuma
kallonsa, ganin yana murmushi, murmushin ma a nutse yake yi.
Kallonta da ya yi, ya sanya ta daina kallonsa, ya ce
"Amm kwanaki, kamar akwai maganar da ki ke son ki yi mini, something like
wani abu yana damunki"
"Baka tambaye ni a lokacin ba sai yanzu, ka manta ba
wani abu bane, ya wuce" tayi maganar cikin tsiwa, tana kawar da kanta
gefe.
Kallonta yayi, bai ce uffan ba, ya zira hannu a aljihunsa,
ya ciro wayarsa, ya danna ya saka a kunnensa, ya ce "Kawo mini abun nan,
na ƙasan katifata, ina wajen bishiyar kalgon nan"
Shiru ya wanzu a tsakaninsu, sai ga ɗan mama ya ƙaraso, ya
miƙawa Viper envelope, ya saka hannu ya karɓa ya ce "Zaka iya tafiya"
Ya kalli Nabila ya ce "Gashi, wani abu ne daga aikinki
ne na fara biyanki wani abu, idan komai ya kammala, in sha Allah zan yi miki
kyakykyawan biya"
Ta karɓi envelope ɗin ta jujjuyata, ta saƙala masa a
hannunsa ta ce "Da dan kuɗi zan yi maka aikin nan, da ba zan yi shi ba,
bana buƙatar kuɗinka, a wurin Allah nake neman ladan abun da zan yi maka, ba
wai dan halinka ba"
Shi ma ya jujjuya envelope ɗin, ya ce "Rashin sani, ya
fi dare duhu, abun da yake ciki yafi kuɗi muhimmanci a wurinki, zaki dawo ki
nema da kanki, shikenan a sauka lafiya"
Ta shagwaɓe fuska tana kallonsa, shi ma ita yake kallo, ji
yake kamar ya tambayeta me yake damunta, ta rame, amma ya kasa.
"Kayi haƙuri"
"Da me?"
"Kayi haƙuri ka bani"
Ya zira aljihunsa ya ce "Ai kuma kin yi wa kanki,
maganin mara kunya, wuce ki tafi gida, kan a fara nemanki"
Ta sake marairaicewa ta ce "Dan Allah"
Viper ya ce "Kar ki ɓata mini rai, wuce ki tafi"
"Korata ka ke yi ko? Dan Allah meyasa ka tsane ni ne?
Me nayi maka?, Kalli duk rashin lafiyar nan da nayi, ko sannu fa Viper, sannu
kawai baka iya yi mini ba, abun yayi mini zafi fa"
"Really?"
Ta haɗiye wani abu mai ɗaci, ta gyaɗa kai ta ce
"Shikenan, bari na tafi, in sha Allah zan yi duk abun da ya dace" ta
juya zata tafi ya ce "Amm meye ma sunan naki? Abla ko?" Ta waiwayo ta
kalleshi, ta fara tunanin a ina ma aka taɓa kiranta da wannan sunan?.
Ta girgiza kai ta ce "A'a Nabila"
"Ohh, sunan yayi mini tsayi, just accept it Abla"
Kamar ba yanzu ya gama yi mata wulaƙanci ba, ta ce
"Nice one, na gode sosai" tayi maganar tana ɗaga masa hannu.
***
"Hello, Salim kana ina ne?"
"Bokan turai, ya aka yi ne?"
"Dan Allah gida nake son ka samo mini"
Salim ya ce "Gida kuma?"
"Eh salim, amma ba na son kowa ya sani, a wajen gari
kuma, saboda na san daddy zai saka a fara bibiyata, sun dage lallai sai sun
gano in da rahama take".
"To kai yanzu hakan da ka ke yi kana ganin shi ne
dai-dai?"
Abdul ya ce "Shi ne, dole zan danƙata a wurin iyayenta,
na kai ta makaranta kafin su san in da take"
"Abdul, ina tsoron abun da zai biyo bayan abun da kake
yi ne?"
"Salim, rayuwar rahama nake ƙoƙarin karewa da
ingantanwa, dan Allah ka taimaka mini, kar a kuma cutar da yarinyar nan a
wannan karon"
"Shikenan, babu damuwa za a duba in sha Allah"
"And sirri ne Please, ko saif ba na son ya sani"
"Haba mutumina, ba sai ka jaddada mini ba, you are
safe"
"Thank you"
***
Kankarofi yana zaune a kan gadonsa, yana daddana wayarsa, ya
ci karo da lambar Hafsat. Ya yi shiru yana kallon lambar ta ta, ya shafi saman
lambar yana tuno ta, yarinyar ta nuna masa so, kuma shi kansa ya san ba dan
yana son ta ya aureta ba, amma beside his wealth, ta so shi, ta yi iya ƙoƙarin
ta a kansa, amma ya kasa sakewa da ita, yayi mata adalci, har auren ya mutu.
Amma ita jidda bai ji haka a kanta ba, hasali ma sosai suke
gogawa ita da Safiyya, duk da dama Jidda tsohuwar budurwarsa ce, lokacin tun
suna jam'iyya ɗaya da Indabo, kuma za su yi sa'anni da Safiyya, ita kuwa hafsa
yarinya ce dama. Ya ji ciwon rashin samun auren jauhar da bai yi ba, amma duk
da haka yana yi wa Allah godiya, da ba jauhar ya aura ta wahala suka rabu ba.
Shiyasa ko zai ƙarar da duk abun da ya mallaka, sai ya
tabattar da indabo ya girbi abun da ya shuka, ba ƙanwarsa yake aure ba, ko
babarsa yake aure, bai ji zai iya ɗaga masa ƙafa ba, kisan mummuƙe zai yi masa,
kamar yadda shima indabon yake yi.
Jidda ta ce ta shigo ɗakin, sanye cikin doguwar riga, ta
ƙarasa ta zauna a kusa da shi, ya ce "Ya dai?"
Ta yi guntun tsaki ta ce "Nifa gaskiya na gaji"
"Da me?"
"Haryanzu ana yi mini sintiri a kan rashin mutuncin da
Abdul yayi, yau wannan ya zo, gobe wancan ya zo, duk security ɗin nan, gaskiya
ni kawai ka canza mini gida, mu bar estate ɗin nan, na gaji wallahi"
"Mu bar estate ɗin nan, amma ɗaya gidan kin san na
sister ɗinki ne, a nan suke zama idan sun zo hutu"
"So find another one mana, am tired hell of all this,
abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, tun da abun ya faru ban sake ganin Abdul ba, ga
babarsa ta kira ni tana nema ta gaggaya mini magana, wallahi rashin ramma a
gidan nan, gaba ɗaya bana samun komai yadda nake so, khalifa da ansar haryanzu
suna tambayata, yaushe yarinyar nan zata dawo, sun saba da ita, Abdul yayi mini
hauka wallahi " har ta gama surutanta, murmushi kawai Alhaji mu'azzam yake
yi, bai ce mata uffan ba.
***
"Hello Ambassador Tahir Arabi"
"Distinguish, ya aiki ya Nigeria?"
"Alhamdilillah"
"Masha Allah, dama maganar yaron nan ne"
Indabo ya ce "Na wurina? Jafar?"
Amb Tahir ya ce "Eh shi, wallahi distinguish sai
haƙuri, sun bawa America shi, kuma yana daf da fara fuskantar shari'a, kuma na
lura babu wani abu da embassy ɗin mu zasu iya yi a kai, duk da dai haryanzu
muna cigaba da ƙoƙari"
Indabo ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
Ambassador ba wani abu da za a iya fa ka ce?"
"Wallahi kuwa, ka san kisan kai yayi a amurka ya gudu
Mexico ya cigaba da harkar ƙwayoyi da hodar iblis tsakanin Nigeria da mexico,
yadda aka shirya kama shi, akwai ƙwarewa sosai da sosai, bisa ga wata
yarjejeniya da haryanzu bamu san ta mecece ba tsakanin Amurka da mexico suka
basu shi, wataƙila musayar fursunoni suka yi"
Jiki a sanyaye Indabo ya ce "Na gode sosai da
sosai"
Ya katse wayar ya dafe goshinsa ya rasa abun da yake yi masa
daɗi.
*****
Da daddare Nabila na kwance, tana ta tattara bayanai a kan
shari'ar Viper, sai ƙarfe ɗaya na dare, sannan ta samu sukunin kwanciya.
Ta janyo wayarta, tana duddubawa, ta ga lambar Viper, kawai
ta danna kira.
Bisa ga mamakinta kawai ta ji ya ɗaga.
Ta ce "Viper"
"Mmm"
"Ba ka yi bacci ba?"
"Mmm"
Tayi murmushi ta ce "Me ka ke yi ba ka yi bacci
ba?"
Muryarsa ƙasa-ƙasa kamar mai jin baccin ya ce "Abun da
ya hanaki bacci ne hana ni"
Ta ce "Wai ni? Ai ni soyayya ce ta hana bacci"
tayi maganar tana murmushi.
Viper ya ce "Nima haka, tunani da kewar matata ne ya
hana ni bacci"
"Ai addu'a zaka yi mata"
"Ina yi mata, zafi ya dame ni, ina missing
fankata" yayi maganar very serious yana lumshe idanunsa.
Nabila ta ce "Fanka? Wace irin fanka kuma?
Ya ce "Fankar solar ce, iskarta daidai ba mai cutarwa
ba"
Nabila ta ce "To ko sayo fankar za ayi, ban zaci ana
zafi a wurin nan ba ai"
"A'a nikaɗai nake jin zafin ai"
Tayi dariya ta ce "Ko ƙiba ka yi ne? Zan sayo maka
fanka in sha Allah"
Viper ya ce "Ki ƙyale maganar fankar nan, ba ki da kuɗin
sayenta, ba irin wadda nake buƙata zaki saya ba" yayi maganar yana juyi
tare da gyara kwanciyar sa.
"Ka gaya mini, zan sai maka in sha Allah, wace iri ka
ke so i promise"
Ya ce "Ba zaki iya sayenta ba"
"Ka gaya mini, zan nemota in sha Allah"
Viper ya ce "Ita fankar?"
"Eh mana"
Kawai ta ji yana dariya, har da gyaran murya.
"Kai, dama kana dariya?" Tayi maganar tana tashi
zaune.
Yayi shiru bai ce komai ba.
"Viper"
"Mmm"
"Dan Allah me ka bani a envelope ka ce zan dawo ina
nema da kaina?"
"Ki manta, ya wuce kawai, zan baki address ɗin nan, ki
je ki samu mutumin nan"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "To, kayi bacci mai daɗi"
"Zafi ya dame ni, ba zan iya bacci ba"
Ta ce "Ka tashi liti yayi maka fifita"
"Na gaya miki fanka nake so ai, sai da safe"
"Ai ka ƙi gaya mini wace iri ce, dan dai fanka sai na
saya maka, shikenan yau na ci pass an yi mini dariya"
"Hmm" kawai ya ce.
Ta sake cewa "Viper"
"Kar sunan ya ƙare"
Tayi murmushi ta ce "Sunan daɗin faɗa, Viper, in shot
kuma V.Snake" ta faɗa tana murmushi.
Ta sake cewa "Wai a ina aka yi maka rigar nan, nima ina
so"
"Wacce?"
"Wadda aka rubuta sunanka a jiki"
"Nawa zaki saya?" Gyara zama tayi, jin yana kulata
yau.
"Ayi mata kuɗi, zan saya ko nawa ce, ka san wani abu,
idan Allah ya sa muka yi wining a court, rigar nan zan saka in yi ta yawo ina
murna"
"To, Allah ya bamu sa'a"
"Amin V snake"
Wasu lokutan simple da shi, wasu lokutan kuwa, sai ka rasa
gane kansa gaba ɗaya.
Ta ce "Sai da safe"
"Hmm" kawai ya ce, ta katse kiran.
***
Sanarwa ko ta ina, a kan tsananta neman Al'amin Viper, tare
da alƙawarin kyauta mai tsoka ga duk wanda ya nuna ko ya bayar da information a
kan in da za a same shi.
Nabila ta damu sosai, ga Sumayya ta daina ɗaga wayarta, dan
haka ta shirya tsaf, ta tafi wurin aikin sumayya.
Sumayya na ganinta ta haɗe rai, Nabila ba ta yi fushi ba ta
ƙarasa in da take ta ce "Sumayya ba kya ɗaga wayata meyasa?"
"Ban sani ba, na gaji da wahalar da ki ke saka mu ne,
babu dalili Nabila, daga wannan sai wancan? Gaba ɗaya kin hanamu nutsuwa da
sukuni, ki jijjigo mana wannan masifa muna zaune, wane irin kallo ki ke so ayi
miki, idan aka ga kin koma bawa ɗan ta'adda kariya, hukumar yan sanda na
nemansa ruwa a jallo, ke kina tare da shi"
"Sumayya, baki yi mamakin yadda na sauya lokaci guda
ba? Har kin manta huci da haƙilon da nake yi a kan a kama shi, kwatsam ki ji na
koma na ce zan tsaya masa na bashi kariya, ayar tambaya yakamata ki fara saka
mini, meyafaru?"
Sumayya ta ce "Ba wani in tambayi meyafaru, kawai ki
cire kanki daga wannan sabgar"
Nabila ta ce "Wallahi ba zan ajiye ba, ko me za ayi
mini" kawai ta saki baki tana kallon Nabila.
"Ko dai ki tayani a wannan karon ma, ko kuma ki ƙyale
ni ki zuba mini ido, yanzu ya maganar program"
Sumayya ta ce "Mhmm yana nan, Nabila ni yanzu kin daina
bani mamaki tsoro ki ke bani, yanzu duk bala'in nan, kin san in da Viper
yake"
"Ƙwarai ki gaya wa uban kowa da ki ke so
masoyiyya"
"To, Allah ya taimaka"
"Amin, gama mu tafi ki rakani wani wuri"
Sumayya ta ce "A'a ba zaki kai ni in da za a kashe ni
ba"
Nabila ta ce "Wane irin kashe ki kuma, mu je dan
Allah"
"To ki tsaya na kammala abun da nake yi, sai mu
tafi"
Ta kammala abun da take yi, suka fita, tare da
sumayya.
Tiryan-tiryan suna tafe, har ƙofar ɗakin da Viper ya rubuto
mata, wasu masu sanye da kaki, suka tarar a ƙofar ɗakin a tsaye, Nabila suka
gaisa, ta ciro id card ta nuna musu.
Suka ce ta shiga, amma ban da sumayya, Nabila ta ce
"Ita ma ma'aikaciya ce, yar jarida ce"
Suka ce "A'a kekaɗai aka ce mu bari ki shiga".
Sumayya ta ce "Ba damuwa, zan jira ki a nan"
Nabila ta shiga, ta yi sallama ta tarar da mutum a zaune a
kan gado, hannunsa ɗaya an saka masa sarƙa, ƙafarsa kuma ɗaya an yanke ta.
Ta ƙarasa gaban gadon, ta ja kujera ta zauna, ta kalleshi ta
ce "Sannu malam"
Ya ce "Yauwwa"
Ta ciro id card ta nuna masa ta ce "Sunana barrister
Nabila, na zo ne a kan case ɗinka da Al'amin mai zamani.
Ya ɗago ya kalli Nabila amma bai yi magana ba.
"Ka yi magana, dan ka sauƙaƙa wa shari'a, me ka sani
game da kisan da aka yi wa matar mai zamani?"ya yi shiru ya ƙi magana.
Tayi tayi, amma yaƙi cewa komai, ƙarshe haka ta fito bai yi
magana ba.
Sumayya suna ta hira da security ɗin wurin, Nabila ta fito,
tana ganin Nabila ta tashi ta ce "Kin gama?"
Nabila ta ce "Eh mu tafi"
Suna tafe ta kira Viper a waya, ta ce "Hello V
snake"
"Barrister"
"Naje wurin gayen nan, amma yaƙi magana, nayi nayi,
yaƙi magana"
Viper ya ce "Rabu da shi, zai yi ta ƙarfin tsiya, ki
tafi kawai"
"Ok, na ma taho, amma yakamata yayi magana gaskiya,
bari na ƙarasa gida sai anjima" ta kashe wayar.
Sumayya ta ce "Nabila wai wurin wa ki ka zo ne?"
"Zan yi miki bayani, amma ba yanzu ba"
Ta ce "Ok shikenan"
***
"Rahama kina ji na?"
"Ina jinka"
"Zamu sake barin gidan nan" "Zuwa ka mayar da
ni gida?"
"Wai na mayar da ke gida ki yi me? Ai kin san iya wuya
muna tare, nan zamu bari temporarily, daga can kuma zan kai ki gida, sai kuma
makaranta, a abuja zaki koma da karatu ai"
"Yar ƙauye a Abuja, to ai ban iya turanci ba, ni
gaskiya na fi son makarantar garinmu"
Abdul ya yi dariya ya ce "Ai Shiyasa zaki je Abujan,
zaki iya turanci, kan ki gama ki ƙara gogewa ki zama her excellency
rahama"
"Taɓ abun ma ba tsari"
"Kamar ya babu tsari?"
"Wata zaka aura ai, kuma ni a lokacin mutane zasu ji daɗin
nuna ni suna aibata ni"
Abdul ya girgiza kai ya ce "Muna tare, babu wanda zai
aibata mini ke"
Ramma ta yi murmushi ta ce "Ba zaka iya canza komai ba,
ɗabi'ace ta al'ummar hausawa"
Ya ce "Shikenan, mu bar maganar"
Ta ce "Ya dai fi"
Wayarsa ya ɗaga, ya ɗan gyara zamansa ya ce "Na'am
Mummy"
"Wato Abdul kafi son ka yi ta sakani a tashin hankali
da damuwa ko?"
"Mummy me nayi kuma?"
"Ban sani ba, ka saka babanka yana yi mini kallon ni
nake goya maka baya ka ke yi masa rashin ɗa'a, ka fito da yarinyar nan ka huta
su huta ka ƙi, rashin mutuncinka har ya kai ka ajiye mace kana lalata da ita,
bayan na keta mata haddi,, ga ɗan uwanka can an mayar da shi america, sai abun
da Allah ya yi, shiyasa ake ta fafutukar ka zama gwamnan nan ko a samu ya fito,
amma ka ƙi, ya ka ke so na yi Abdul, in bar muku duniyar ka huta ko?"
Cikin damuwa ya ce "Mummy ki yi haƙuri dan Allah, ki
fahimce ni, ya za ayi na so ki mutu, ba haka bane ba. Wallahi Mumm tsoro nake
ji na fito da yarinyar nan, ayi mata wani abu na daban, dan Allah ki yi haƙuri,
zan zo gida nayi miki bayani, na san zaki fahimce ni in sha Allah. Kuma yaya
jafar zai fito in sha Allah, ki yi haƙuri dan Allah"
"Ai shikenan, ka yi abun da ka ke so"
"A'a ba za ayi haka ba, zan zo har gida nayi miki
bayani" ta katse wayar, yayi ajiyar zuciya yana lumshe idanunsa ya buɗe
yana kallon ramma, da ta yi kamar ba ta jin me yake faɗa a wayar.
"Rahama"
"Na'am"
"An sakoni a gaba a kanki"
"An san ka sace ni kenan?"
Abdul ya ce "Ke fa ba a abun arziki da ke, ke da ban
sace kin ba, da yanzu wani zancen ake ba wannan ba"
"Ai ba da kyakywar manufa ka sace ni ba, kashe ni ka ce
zaka yi"
"Amma ai ban kashe kin ba ko?" Tayi masa shiru ta
cigaba da aikin ta.
****
Nabila ta fito daga banɗaki, kawai ta tarar da Nasir a tsaye
a ɗakinta, ta kalleshi ta ce "Lafiya?"
Ya ɗago mata file ɗin Viper da yake hannunsa, ta bar shi a
kan gadonta tana aiki, ya faɗo mata ɗaki.
"Menene wannan?" Ta ƙarasa gabansa ta saka hannu
zata karɓa, ya janye yana sake tambayarta "Menene wannan Nabila?"
"Babu ruwanka da ko menene, ka bani file ɗina kuma ka
daina shigo mini ɗaki ba tare da iznina ba"
Cikin tsawa ya ce "Ki yi mini bayani kin tsaya kina
wasu kame-kame da wasu maganganun banza da na wofi"
Cikin dakewa ta ce "DSP aikina nake yi, ka fita daga
harkata ka bani file ɗina"
"Nabila, ta tabatta goyon bayan ɗan ta'adda ki ke
yi?"
"Ni bayan gaskiya nake bi, kawai, ka bani file ɗina"
"Nabila kina haɗuwa da mutumin nan, kin san in da
yake"
"Ni ban san in da yake ba, ka bani file ɗina tun ina
ganin mutuncinka"
Shammatarsa tayi, ta kafa masa haƙora a hannunsa, ba shiri
ya sakar mata file ɗin, ta kwashe abun ta tayi waje, ya bi ta da kallo, ya
kalli hannunsa yadda yake tsatstsafar da jini saboda iya ƙarfinta ta cije shi.
Cikin yarfe hannu, ya bi bayanta, sai dai ko sama ko ƙasa ya
nemeta ya rasa a cikin gidan nan.
Zuciyar sa ta daɗe tana mamakin abun da ya gani, amma
haryanzu ya kasa gazgata cewar Nabila tana haɗuwa da Viper, ta san in da yake,
amma me zai haɗata da ƙasurgumin ɗan ta'adda haka tana ya mace, idan kuwa haka
ne, duk hukuncin da doka tayi a kanta shi ba zai ce komai ba, amma ya yanke ya
sake tuntuɓar Abba, ya kirata ya ja mata kunne, a lallaɓata a cikin gida idan
da abun da ta sani, a sasanta abun, kar asiri ya tonu, dan shi kansa abun kunya
ne a gare shi, ace yana can yana haƙilon neman ɗan daba, Nabila na zagewa ta haɗu
da shi a ɓoye.
Da daddare Nabila na zaune a falon Abba, ga Nasir a gefe,
sai kuma shi kansa Abban, tayi shiru ta sunkuyar da kai fuskarta babu annuri.
"Arfa" Abba ya kira sunanta a kausashe.
"Na'am Abba"
"Gaske ne abun da ɗan uwanki ya gaya mini?"
"Abba ai ban san me ya gaya makan ba"
Abba ya gyara zama ya ce "Gaske ne, kin san in da wanda
yake ta haƙilon nema yake? Nabila meye haɗinki da ɗan daba ne? Kina 'ya
mace?"
Ta girgiza kai ta ce "Abba ya za ayi na haɗu da wanda
yan sanda ma suka kasa kamawa, file ɗin shari'arsa kawai ya gani a ɗakina, kuma
ba nawa bane ba, na barrister Habib ne, nima karɓa nayi na duba, ina dudduba
yadda aka gudanar da shari'ar sa a wancan lokacin ne, an ce yayi shekara biyar
a prison ba ayi masa shari'a, kwatsam kuma aka ce an sake shi, aka dawo ana
nemansa sai nake jin kamar akwai wani ɓoyayyen lamari, shi ne nake ta bibiya,
ka san muna program da sumayya, so ina binciken cases makamantan nasa shi ne
kawai, amma sai zargina yake yi, ni ban san meyasa ba"
Abba ya yi ajiyar zuciya ya ce "To kai ka ji abun da ta
ce, me zaka ce?"
Sam Nasir bai ji ya yarda da abun da Nabilan ta faɗa ba,
amma ya ce "Shikenan Abba, tun da haka ta ce"
"Dan Allah ku daina wannan rigingimun, da ba haka kuke
ba, naga tare kuke sharing working experience ɗinku, amma yanzu kuna nema ku
lalata tsakaninku, ni ban ji dama arfa zata iya bin wani ɗan daba ba, tana
ƙyamar irin wannan laifukan, dan haka dan Allah duk ku yi haƙuri Allah ya yi
muku jagora, ya rufa muku asiri"
Nabila ce ta fara miƙewa ta amsa da Amin, ta fice tana
hararar Nasir, shi kuma ya bi bayanta da kallo, sam bai yarda da ita ba.
Washegari aka dawo da motar Nabila, an gyarota fes har fenti
an canza mata, ta ji daɗin dawowar motar nan, dama yawan zirga-zirgar nan ya
isheta.
Ɓangaren sumayya ma, nata program ɗin da take gabatarwa a
kan shirin siyasa, na an yi walƙiyya, yana ta jan dubban masu sauraro,
sakamakon yadda take baje wa mutane komai, game da irin kuɗaɗen da gwamantin
tarayya take bayarwa domin ayyukan raya ƙasa, ta kan ɗauki ƙananan hukumomin
shiyya ɗaya, ta kawo kuɗin da suka samu na wata, na tarayya, na jiha da na
ƙanan hukumomin, da iya ayyukan da aka yi musu.
Sai dai tun da ta zo kan na Indabo, a ƙalla tafi sati uku,
program ɗin a kansa yake, dan sai da ta faro tun daga farkon tenure sa, yadda
take hawa da sauka a kansa, zai tabattar maka akwai wata a ƙasa tsakaninta da
shi. Yan siyasa da dama, sun kawo wa program ɗin hari, da neman a dakatar da
shi, amma hukumar gudanarwa ta tashar suka tabattar da cewa an riga an biya su ɗaukar
nauyin program ɗin, dan haka ba zasu dakatar ba, wanda bai gamsu ba, ko ya ji
an yi masa sharri ko cin zarafin sa, to ya kai kotu.
Da safe Nabila ta fito da motarta, sai ƙyalli take yi, ta
batta a kunne, ta shiga gida ta haɗo kayan breakfast ɗin ta, ta koma cikin
mota, Viper ya kirata a waya.
Ta ɗaga ta ce "Hello V snake"
Cikin dakakkiyar muryarsa ya ce "Kin fita aiki
ne?"
"Ina ƙofar gida ne, yanzu zan tafi ka tayani da addu'a,
yau zan kai kokenmi kotu"
Ya ɗan ja numfashi ya ce "Ki bi ta farkon layinku,
wurin incomplete building ɗin nan, ina nan ina jiran ki"
"Ok sir, gani nan"
Ta ja motar ta ƙarasa in da ya ce mata, a wurin ta tarar da
shi, ya tako a hankali, cikin nutsuwa. Ta zura masa ido tana murmushi ba tare
da ta san tana yi ba.
Ya shigo ya rufe ƙofar, ta kalleshi ta ce "Good
morning"
"Morning" ya amsa ba tare da ya kalleta ba, ya
ajiye mata baƙar leda.
Ta ɗauka ta ciro abun ciki, baƙar riga ce, da sunansa a jiki
Viper, da hoton maciji.
"Wow masha Allah, har an yi mini? Na gode sosai, wai
waye yake yi maka rigunan nan?" Yayi shiru bai amsa mata ba.
Sai kuma ta ce "Sanyin Ac yayi maka normal ko na
rage?" Kawai ya jingina da seat ɗin motar ya zuba mata ido.
Sai ta ɗan rikice ta ce "Menene? Ko wani abun ne?"
Still bai yi magana ba.
Ji tayi tsigar jikinta na tashi, ta ce "Dan Allah ka
gaya mini menene?"
"Ina jin ƙwarin gwiwa a kan shari'ar nan, wanda ke ki
ka bani shi, and at the same time scared, idan rayuwarki ta salwanta saboda ni,
ba zan yafe wa kaina ba, dan rayuwar ki kika saka a haɗari saboda ni, na zo ne
in ce miki good luck"
Duk da ta takura da kallon da yake yi mata, tamkar ta nutse,
ga wata fargaba da bata san ta mecece ba, amma ta dake ta ce "Allah yana
tare da mu, in sha Allah zamu yi nasara"
"Allah ya sa, ko mun yi nasara ko bamu yi ba, ina da
kyakykyawan tukuici gareki"
"Ni zuciyarka kawai nake so, shi ne tukuicin da nake
so" haɗe rai yayi ya ce "You are not serious, ba zaki daina wannan
shirmen ba ko? Wahala zaki yi ta sha kuwa, ba na kallon kowace mace mace idan
ba jauhar ba, ki je ki samu wani ku daidaita" yayi maganar ba tare da ya
kalleta ba, yana ƙoƙarin buɗe ƙofa ya fita, jikinta har yayi sanyi, idonta ya
cika da hawaye" yayi saurin ficewa, ba tare da ya sake kallonta ba. A guje
ta fizgi motar, ta bar wurin, wanda hakan sai da ya bashi dariya, dan ya san
fushi ta yi.
Nabila tana tafe hawaye na zuba daga idanunta, duk ta ɓata
kwalliyar ta, sai taga kamar zata yi nasara, kawai sai ya buntsure, gashi ita
kullum ƙara son sa take yi so mai zafin gaske.
Da haka ta ƙarasa court, ta tsaya ta ƙara gyara fuskarta,
sannan ta fita ta shiga cikin court ɗin.
Nabila ta nemi kotu, ta hana hukumar 'yan sanda kama
Muhammad Al'amin Ibrahim, da aka fi sani da Viper, har sai an yi cikakken
bincike a kan kisan kan da aka yi wa matarsa shekaru biyar da suka gabata,
hakazalika yana neman hakkinsa, na tsare shi shekaru biyar ba tare da yi masa
shari'a ba, a kan laifin da ba shi ya aikata ba. Ta gabatarwa kotu kwafin
shari'ar da aka yi masa a baya.
Duk da ba ma a fara shari'ar ba, amma haka nan ta din ga jin
tamkar ta kama hanyar sauke gingimemen nauyin da yake kanta.
Abun da Nabila bata sani ba shi ne, tuni aka kira Nasir, aka
sanar masa da an ganta da wani, a wurin sabbin gine-gine da ake yi a unguwar,
kamar yadda ya saka CID ta ko ina a kanta.
Ya shiga kitchen ɗaukar lemo a fridge ya tarar da wayar
Nabila a kitchen tana ringing, ita kuma bata kitchen ɗin, ya ƙarasa in da wayar
take, kiran ya yanke. Ya kalli wallpaper ɗin ta Hoton sunan Viper ne, da maciji
a kan wallpaper da wani heart.
Ya saka hannu ya ɗauki wayar, wani kiran ya kuma shigowa.
Kawai ya ɗaga kiran ya saka a kunnensa ya ce
"Waye?"
"Viper ne, mai zamani"
Ayshercool
08081012143
Albishirinku ma'abota bibiyar litattafan bright pens, kamar
yadda ku ka ji daɗin littafin ƙarfe a wuta, to Mutallab ma free pages ya
kammala.
*The story of a thug husband MUTALLAB, as a good parents za
ku bada auren yarinyarki ga ɗan daba ɗan ta'adda? Ban ce ku fara kuka tun yanzu
ba,ban ce ku ji soyayyar ciki kamar a ƙirjinku ake wanzar da ita ba.* *The
story of TIGER and MOH The destiny of CAPTAIN and FIYYA. Finally the eternal
love* *between..The love that separate them and back them together❤🔥😭*
Page 15 last free episode
For more updates follow Mutallab on Arewabooks in sha Allah
❤🔥🥰
Page 15 shine last free pages na labarin, kar ka yi tunanin
ganin wani page ɗin a waje ka yi payment a yi naka into paid group akan 500
kacal, love ɗin da kuke showing yanzu ne zai yi aiki🫠MUTALLAB.
Book 1, 2 &3
500 Naira
0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya
ta nan 08164069385 'Yan Nijar tsarin biyan zai kasance ta *Stock na airtel*. Ku
yi wa wannan layin 84506476 magana sai ta ba ku lambar da za ku turo mata stock
ɗin. Kafin ɗorawa da inda muka tsaya zamu ɗauki hutun zango na sati ɗaya tal😂
maybe har a yi albashi ko masu mining ta fashe musu.
LAST FREE PAGES
Waye Mutallab?
Waye Scorpion?
Wace Safiyyerh?
Waye Daddy?
Mene FS WORLD INVESTMENT COMPANY?
Labarin Mutallab da tarihinsa ya fi wannan da muke ciki
yanzu ai za ku zo jin wannan soyayyar ta ƙuruciya ba?
Mene yake saka a fara daba da shaye-shaye?
Wanne ganganci iyaye suke yi akan yara?
Mece siyasa da cikakken tarihin dimokuraɗiyya?
Za ku su sanin ya ake mulki a ƙasar nan?
Har ku yi supporting yaran ku?
Soyayya na saka shaye-shaye ne ko daba? Me ya sa Mata har
uku suka mutu ta sadanadin MOH me ya sa ya kashe matarsa SAFIYYERH?
YAUSHE SAFIYYERH TA HAIFI YARO?
maza hanzarta yin payment chat with me on WhatsApp
08164069385
BRIGHT PENS... 2ND BATCH 🔥🔥
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Ina ma'abota bibiyar litattafan bright pens, ƙarƙashin
mikiya writers association, marubutan da suka kawo muku CUTARWA, MUNAFUKIN
MIJI, YI WA KAI, A first batch ga second batch, ƘARFE A WUTA, MUTALLAB ya fara
zuwar muku da na sa saloz sai kuma ZAYTOON DA HADARIN GABAS NA NAN TAFE SUMA A
CIKIN WANNAN WATAN, KAR KU BARI A BAKU LABARI.
Cak Nasir ya ƙame, a daidai lokacin da Nabila ta dawo
kitchen ɗin.
"Wa ka ce?"
"Sarai ka ji abun da na ce, kar na sake kiran waya, ka ɗaga
mini, ka bawa mai wayar, zan yi magana da lawyer ta"
Hakan yayi daidai da shigowar Nabila da take tsaye a
bayansa, ya waiwayo ya kalleta, ya miƙa mata wayar yana tsareta da idanunsa da
ya zazzaro su, tamkar zasu faɗo ƙasa.
Ta saka hannu ta karɓi wayar, tayi ƙasa da murya, ta ce
"V ka kashe ni"
"Shhh ki tsaya ki saurare ni"
Ta ce "Tom"
"Yaya zaki yi da batun shaidun nan? kin ce gayen nan
yaƙi magana, ina so zan je in da yake da kaina"
"To ai ka ga ni ban san me ma zan ce ba, ban san wace
hukumar ta ce ta kama shi ba, dole yan sanda zamu shigarwa koken su kama
shi".
"Na fahimta, na san abun da zan yi, dama na zata zai yi
magana ne, ki samu wani abun as shaida, amma na san abun da zan yi masa, zai yi
magana ta ƙarfin tsiya. And am sorry for what i did, na san zan saka ki a
matsala, amma hakan ka iya zama maganin wasu matsalolin naki, dole za a zo
wurin nan, cigaba da ɓoye-ɓoye ba zai haifar da ɗa mai ido ba, no matter what
it takes, duk tsanani da ƙalubalen da zaki fuskanta ki jure, da Allah na
dogara, amma kekaɗai ce ƙwarin gwiwa ta, Please don't give up"
"Kar ka damu, in sha Allah I won't, i promise you
that"
"Thank you" ya katse wayar, hankali kwance ta
kammala wayar, Nasir ya zuba mata ido, yana jiran ta gama, ya ji wace ƙaryar za
ta yi masa, kawai ya ga ta basar, ta cigaba da abun da yake gabanta.
Da ƙarfin tsiya, ya janyo kafaɗarta ya tsayar da ita tana
fuskantar sa, ya ɗaga hannu zai kwaɗa mata mari ya ji muryar Baba magajiya
"A'aaa lalalalaaaaa me zan gani haka, a kul ɗin ka, kar ka kuskura fara me
yayi zafi zaka dakar mini 'ya Nasir" tayi maganar tana nuna shi da yatsa,
Nabila kuwa da gudu ta gudu ta ɓuya a bayanta, tana ƙifta idanuwa.
"Ammm baba magajiya, ki fita daga cikin maganar
nan"
"Ban gane in fita daga maganar nan ba, zaka kassara
mini ƴa ka ɗaga hannu zaka daketa, ƙarfin ka da nata ɗaya ne?" Ai tana
rufe baki, ya ture baba magajiya ya danƙo Nabila ya fara janta.
Tirjewa ta din ga yi, tana zunduma ihu, tana a taimaketa zai
kasheta.
Baba magajiya ta sake biyo su, tana yi masa masifar ya saki
Nabila. Sai da ya kaita tsakiyar falo, sannan ya kalleta cikin ƙunar rai ya ce
"Nabila umarni nake baki, a yanzu yanzu cikin gaggawa ki sanar mini ina
wannan ɗan iskan ɗan daban yake, kafin na tafi da ke na kulle ki, Nabila wace
irin mahaukaciya ce, kina iƙirarin ke mai gaskiya ce, amma kina take doka kina ɓoye
mai laifi?".
"Ni ban taka kowace irin doka ba, bisa doron doka nake
gudanar da aikina"
"Shut up, ki gaya mini in da yake, kafin na saka ankwa
ke na tafi da ke, na je na kulle ki"
Nabila ta ce "Ka kulleni a nayi maka laifin me?"
"Tambayata ki ke sake yi saboda kin raina mini hankali,
ko bayan wannan hujjar wata ki ke nema? Am disappointed on you, kin bani kunya
Nabila, ban taɓa tunanin duk wannan haƙilon da ki ke yi, zaki iya cin amanar
ƙasa ba, kuma ki ci amanata ba"
"Ban ci amanar kowa ba, ni ba maciyiya amana ba ce
ba"
"Ba zaki yi mini shiru ba, sai na tattakaki tukuna? Ki
na ɗiya mace daga gidan daraja da mutunci, amma ki zubar wa da kanki kima, dan
ba zan ce mu ki ka zubar wa ba, ki gaya mini ina ce maɓoyarsa, kafin ke nayi
arresting ɗinki"
"Kayi arresting ɗina like how, DSP lawyer ce fa ni,
lawyer ma mai zaman kanta, ina da ikon kare duk wanda ya zo gabana ya nemi
hakan, duk girman laifin da ya aikata kuwa, balle wannan da makauniyar shari'a
kawai ake yi. Ba ka da ikon kama ni, dan ban aikata laifin komai ba"
Tuni yan gidan suka tattaru a falo, domin jin meyake faruwa,
suke ta wannan uwar hayaniya da yammacin Allah.
Sai dai jin turka-turkar da ake yi, ya sanya su mamaki ba kaɗan
ba, jin abun da Nabila ta aikata, gaba ɗaya sai suka haɗe mata kai, suka din ga
jifanta da miyagun maganganu, na cin zarafi.
Mama ta kada baki ta ce "Ai na san a rina, an saci
zanin mahaukaciya, ba dai major ya ɗaukaketa ya nuna ita ce ya a gidan nan ba,
an zo dai-dai in da nake son a zo, ɗan sa da ya haifa bai ja masa abun kunya
ba, wata a banza gashi ta jawo masa, Allah ya sa ba yawon ta zubar take yi ba
da sunan aiki, ban da haka, ya za ayi ta din ga hulɗa da ɗan iskan gari da ake
nema ruwa a jallo, ta ce shi zata kare mutumin da yayi kisan kai ɗan
ta'adda".
"Allah ba zai nuna mini yawon ta zubar a rayuwata ba,
da ni da 'ya'yan gidan nan, in Allah ya yadda, babu wanda zai yi yawon ta
zubar"
"Maman ki ke gaya wa haka Nabila?" Yayi maganar
yana nuna ta da yatsansa.
Ko a jikinta ta ce "Zata iya kallon sauda, ko su
siyama, ta ce suna yawon ta zubar? Ko yi suke na san ɓoyewa zata yi ba zata faɗa
ba, sai ni 'yar Allah ba ni da ba ita ta haife ni ba, ai na daɗe ina yi mata
kawaici kai ma ka sani" Baba magaji sai haƙuri take bayarwa, Nabila kuwa
bakinta yaƙi mutuwa, da sun faɗa take mayar musu, mama ta ce wa Nasir, ya rabu
da ita ya jira major ya dawo, ya ɗauki duk matakin da yakamata a kanta, kar ya
matsa tayi masa wani Sharrin amma duk abun da yakamata ayi mata na doka, a ɗauki
mataki a kanta.
***
"Abdul, so kake sai baƙin ciki ya kashe ni, ya kashe
mahaifinka, mu bar maka duniyar ka rayu kai kaɗai ko? Tun da aka ce masa an
mayar da jafar amurka, hankalinsa yaƙi kwanciya, wataƙila hukuncin kisa ne a
kansa, jininsa yayi mummunan hawa, an bashi hutu ma zaman majalisar nema yake
ya gagare shi, kai ana ta fama ka samu ka zama deputy governor ɗin nan, yanzu
ko maganar bikinka ka daina yi, yau an ƙara watanni uku a kan lokacin bikin,
amma ko ka bibiya meyafaru ya ake ciki? Babu ruwanka saboda ka ajiye yar mutane
kana lalata da ita, so kake sai asirinka ya tonu mu shiga uku baki ɗaya, da
wanne ka ke son mu ji? Wancan case ɗin ko kuma naka da ake ta bibiyarka ana
lallaɓaka ka ke rashin mutunci?"
Ya girgiza kai ya ce "Mummy, ba haka bane ba, wallahi
tsoro nake ji na fito da rahama, na san babu lallai abun ya tsaya a iya bayar
da shaida a kotu, ina tsoron daddy ya yi mata wani abun, kin san halin sa, idan
kuwa aka kuma cutar da ita, ba zan iya yafewa kaina ba, saboda nayi nadamar
abun da na aikata"
"Ka yi nadama amma ka ajiye musu yarinya, ka ke lalata
da ita? Wace irin nadama ce haka?"
Ya ɓata fuska ya ce "Ni ajiyeta kawai nayi, ba lalata
nake da ita ba"
"To yanzu dai na ji, amma tana ina? Ni ka gaya mini,
nayi maka alƙawarin babu wanda zai cutar da ita, har mahaifin naka ma, ba zan
bari ya cutar da ita ba"
Ya ce "Gaskiya Mummy na san lallaɓa ni ki ke yi, kiyi
mini wayo, amma na san tsaf zaki bayar da ita"
Ta ce "Laaa ƙarya nake yi maka kenan Abdul?"
Ya girgiza kai ya ce 'To, zan dai dawo in gaya miki, amma ba
yau ba, bari na tafi Asibiti zan je"ya tashi ya ɗauki jakarsa.
"Ba zaka je ka duba mahaifin naka ba?"
Abdul ya ce "Zan je, yanzu na kusa makara ne, kuma ina
zuwa zai yi mini zancen yarinyar nan, sai na dawo tukuna" ya fice daga ɗakin.
***
Viper ya ƙurawa madaki ido, da duk yayi wani iri, babu
wannan kwarjinin da ban tsoron da yake da shi, babu shaye-shayen ƙwayoyin da ya
saba, gaba ɗaya sai tsufansa ya fito sosai da sosai.
"Madaki, yanzu na tabatta har labarin madaki ya shafe,
Viper ba zai bar zuciyarka ba, ko dan wannan ƙafar da aka yanke, kodayeke
taimakonka nayi, ni na fika imani, ba dan haka ba, wannan ƙafar cin jikinka
zata cigaba da yi.
Na turo lawyer ta, ku yi magana, amma ka ƙi, ni ba ta taka
nake yi ba, kai ka san kasheka ba wahala zai bani ba, da kai da muƙarabbanka,
amma ba ta kai nake yi ba, zan yi amfani da kai ne, na dangana da Indabo, dan
haka ka shirya yin magana ko baka shirya ba?"
"Ban shirya ba, kuma ba zan shirya ba, kayi kaɗan mai
zamani, haryanzu ba ka kai in da zaka ga bayana ba, maƙiyina bai isa ya ga
bayana ba"
Viper ya ce "Baya kuwa na riga na ganshi, tun da da
hatimin sunana zaka mutu a gadon bayanka, na san duk abun da zan yi maka, ba
zan huce ba madaki, ni zuciyata ka yi wa illa, amma zan iya kamantawa. Kar ka
manta lakwari ma yana hannuna, sannan shi ya ji wuyar da ya shirya yin magana,
dan haka ko ka yi magana, ko kar ka yi tare zata kwaɓe muku, idan yayi tamkar
ka yi ne"
Ya ciro wani jan gari, mai fatsi-fatsi a cikin yar leda, ya ɗago
wa madaki shi, ya ce "Da irin wannan, ku ka yi amfani wurin hanani kataɓus,
ku ka yi mini illa ko?" Madaki yayi shiru, yana bin hannun Viper da kallo.
"Bari na yi maka amfani da ita, na ga wani irin hali na
shiga kuma wane irin nishaɗi ka ji, lokacin da kake cin zarafina" Viper ya
miƙe tsaye, Madaki ya zazzaro ido, amma Viper haka ya sheƙawa madaki garin nan.
A take kansa ya fara juyawa, ya shiga girgiza kansa.
Viper ya ce "Ina son ku ɗauke shi, ku kai shi kusa da
tsohuwar dabata, in da yaran nan da yake cin zarafi yake yi wa kisan gilla,
wanda ya sanya tsananin tsoronsa a zukatansu, idan dare yayi ku yasar da shi a
can, gari ya waye su ganshi a wurin, da ƙafa ɗaya su tabattar da cewa alkadarin
sa ya karye, ƙaryarsa ta ƙare.
***
Nabila na kwance, ƙirjinta na ta bugawa, jiran dawowar Abba
kawai take yi, ba ta san me Nasir zai gaya masa ba, ba ta san a yaya zai karɓi
maganar ba. Tana ta maimaita "la haula wala ƙuwwata illa billah"
bacci ne ya fara fizgarta, ta ji tsayuwar motar Abba, wajen ƙarfe goma na dare,
zumbur ta tashi ta tsaya, ta tafi window tana leƙe-leƙe, har wurin goma na
dare, shiru ba ta ji an kira ta ba.
Ta ɗauki wayarta, ta kira Viper, bugu ɗaya ya ɗaga, ya ce
"Ya ake ciki?"
"V am scared" tayi maganar tana fitar da numfashi
cike da tsoro.
"Meye yake baki tsoron?"
"Ban san me Abba zai ce mini ba, tsoro nake ji, Abba
bai iya fushi ba, bana tunanin zai fahimce ni cikin sauƙi, na shiga uku"
tayi maganar tana fashe masa da kuka.
"Shhhhh, Abla" ta ji kiran sunan har tsakiyar
zuciyarta.
"Mmm"
"Shi ramin ƙarya ƙurarrre ne, duk yadda ki ka kai ga ɓoyewa,
dole sai ya fasu wataran, shiyasa na kawo ƙarshen zargin da yayanki yake yi
miki. Haɗuwar da muka yi da ke, sai da aka gaya masa, yana bibiyarki ko ta ina
tasa mafitar kawai yake nema. Ki nutsu ki cigaba da addu'a, babu abun da zai
faru in sha Allah, you are my only hope as i told you before, idan ki ka karaya
ni ya zan yi?" Yayi maganar cikin rarrashin da bata taɓa tunanin ya iya
ba.
"Ba zaka gane ba, amma zan cigaba da addu'a, sai da
safe" ta kashe wayar tana dafe ƙirjinta, saboda yadda yake bugawa.
***
P.A ne ya shiga bedroom ɗin Indabo, bakinsa ɗake da sallama,
ya amsa masa ya ƙarasa ya zauna, ya ce "Barka da wannan lokaci"
"Barkanka dai P.A"
"Ya ƙarfin jiki kuma?"
"Jiki Alhamdilillah, da sauƙi sosai, maybe gobe in
Allah ya kaimu zan shiga Abuja"
P.A ya ce "Yakamata ka ɗan dakata da shiga Abujan
nan?"
Ya kalli P.A ya ce "Saboda me? Hutuna ya ƙare ai"
"Ƙishin-ƙishin na ji, maganar kuɗin scholarship ɗin da
na harkar sadarwa, balli na daf da tashi, EFCC zata bincike ku" zumbur
indabo ya tashi zaune ya ce "Kai a ina ka ji?"
P.A ya ce "Majiya mai ƙarfi, amma ka kira shugaban
marasa rinjaye, a wurin P.A ɗin sa na ji maganar, kuma ba jita-jita bane
ba"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, P.A wai ya aka yi
abubuwa suke ta taɓarɓarewa ne haka?"
P.A ya ce "Nima abun ya fara bani tsoro, amma ka
dudduba ka bincika mu ji"
"Ai ni har bana son kiran waya, duk wanda na kira akwai
kalar masifar da zai gaya mini. Kuɗin nan fiye da rabi duk a kan ƙoƙarin ganin
jafar ya fito ne, idan ba hali sai na lallaɓa na mayar, amma zan yi magana da
ministan sadarwar da na ilimin, mu tattauna, koma dai na saka su bincika
mana".
"Bayan nan, mutane fa suna ta surut a kan program ɗin
da yarinyar nan take yi, na walƙiyya wallahi mutane sun fara dawowa daga
rakiyarmu, na rasa uban da yake ba ta wasu information ɗin da take faɗa a
kanmu"
"Kaga P.A, dan Allah ka ƙyale ni haka, gaba ɗaya
maganganunka ba alheri yau, tashi ka tafi dan Allah"
P.A ya ɗan yi shiru, sannan ya tashi ya fita.
***
Yanayin da Abba ya fito falo, ya tabattar musu da ba lau ba,
fuskar nan a murtuke babu annuri.
Ya kalli baba magajiya ya ce "Kira wo mini Nabila"
sai da suka kalli Abba, jin ya ambaci Nabila, maimakon Arfa da ya saba kiranta.
Nabila na kwance baba magajiya ta shigo ta sameta, ta ce
"Arfa, babanki yana kiran ki" sai da ƙirjinta ya buga da ƙarfi, ta yi
ajiyar zuciya ta ce "To, gani nan zuwa" baba magajiya ta fita daga ɗakin.
Da ƙyar Nabila ta tashi, ta nufi falon, ƙirjinta na ta
bugawa da sauri.
Kusan kowa ya hallara a falon, ita kawai ake jira.
Ta ƙarasa ta durƙusa a gaban Abba, ta ce "Abba
gani"
Mama ta ce "Munafuka ga ladabin kura"
Umma ta ce "Ki yi shiru, karya haɗa da ke".
"Dama irin tarbiyyar da na baki kenan? Ki je ki dinga
bibiyar 'yan iska a waje?"
Gabanta ya faɗi, ta ɗaga kai ta kalli Nasir ta koma ta
sunkuyar da kai.
"Har muka yi zaman kudancin Najeriya, muka gama ki ka
yi jami'a, duk baki lalace ba sai yanzu? Ina ke ina bibiyar ɗan daba, ɗan
ta'adda kuma ɗan iska da hukuma take nema? Kin zama 'yar iska lalacewa ki ke so
ki yi ko, ko ma in ce ki ka yi?"
Falon yayi tsit, baka jin sautin komai, ƙarar gudun A.C, sun
yi cirko-cirko suna kallon Nabila.
Tuni ta fashe da kuka, jin yadda maganganun Abba, ke
dukanta.
Abba ya ce "Nasir ya gaya mini komai, da duk bana
yadda, yanzu sakamakona kenan a wurinki ko? Sakamakon tarbiyya da ilimin da na
baki kenan, ki ƙare a ɓoye mai laifi, azo kama shi a haɗa da ke, ki tozarta ni
ki zubar mini da mutunci"
Cikin ƙulewa mama ta ce "Wane sakamako ka ke saka ran
samu daga tsintacciyar mage, ai ba zata taɓa mage ba, shiyasa nayi ta ƙoƙarin
ankarar da kai tun a baya, uban wani ba ya zama na wani, yanzu duk da fifikon
da ka nuna mata, bai hanata nuna maka, ita 'yar kunama ce ba, duk gidan nan
babu wanda yake janyo maka magana sai ita, yayanka suna zaune lafiya amma ita
kullum cikin ɗaga mana hankali take"
Baba magajiya ta ce "A'a fa, dan Allah ki sassauta
maganganun nan, sun yi tsauri da yawa"
Nabila kuwa da a zahiri ta nuna tashin hankali da nadama,
cikin zuciyarta kuwa babu alamar hakan, ta yakice gumin fuskarta da yake ta
tsatstsafo mata ta ce ""Abba ba mummunan sakamako bane ba, abin da ka
tarbiyyantar da ni a kai ne, gaskiya ita ce nake tsaye a kai. Yakamata ayi mini
adalci aji ta bakina, ba a goyi bayansa kawai ba ace ni ce bani da gaskiya ba.
Wallahi Abba ni ba bibiyar yan iska nake ba, aikina kawai nake yi".
Mama ta ce "Har wata gaskiya ce da ke....
Abba ya ɗaga mata hannu, ya dakatar da ita, ya ce "Ya
isa haka, ki tashi ki je, bana ko son ganinki, ki je ki yi abun da ki ke ganin
shi ne dai-dai, tun da a kan gaskiyar ki kike"
Cikin tashin hankali ta ce "Abba baka son ganina fa ka
ce, me aka gaya maka har haka a kaina ya sanya ka yanke mini wannan hukuncin
"
"Abun da ki ka aikata aka gaya mini, muddin kina neman
zaman lafiya da gudun ɓacin raina, dole ki bawa ɗan uwanki cikakken haɗin kai,
ya gudanar da aikinsa, ki fita daga wannan lamarin, kafin a saka ki cikin masu
laifi a kama da ke.
Duk wahalar da yaron nan yake yi, kina ji kina gani, amma
kika ja bakinki ki ka yi shiru, har barazana ake yi masa na kora, muddin bai
kama mutumin nan ba, amma ki ka zagaye ki ka je ki ka ƙulla alaƙa da shi, kin
fara bani tsoro Arfa"
Cikin matsanancin tashin hankali ta ce "Amma Abba ni
kuma menene makomata? Yakamata ka ji ta bakina abba, na karɓi aikin nan ka
fahimce ni Abba"
Bai tsaya sauraronta ba ya ce "Sai dai kin nuna mini ba
ni na haife ki ba, na gode" yayi gaba zai bar falon.
Cikin tashin hankali, ta riƙe ƙafarsa ta ce "Haba
Abbana, idan har zan rayu kana fushi da ni, me yayi mini saura a duniya? Ka yi
haƙuri zan yi abun da ka ce" ta yi maganar tana kuka mai ratsa zuciya,
tana sheshsheƙa kamar ta shiɗe, amma ya fizge ƙafarsa yayi gaba.
Yana bari falon, tamkar su cinyeta ɗanya, suka yi kanta da
surutu, kowa na tofa albarkacin bakinsa.
Tashi ta yi tsaye, ta goge hawayenta, cikin ko in kula, ita
ma ta bi wata hanyar ta bar musu falon, cikin sigar kwa ci kanku.
Ɗakinta, ta shiga ta buɗe drower, ta fito da wasu takardu ta
zube su a kan gado, ta kunna system ɗin ta da take caji a gefen gadon, lokaci
guda kuma ta ɗauki wayarta tana dannawa.
Jin motsin mutum a bayanta, ya sanya ta waiwaya da sauri.
A tsaye ta ganshi bakin ƙofa, fuskarsa babu walwala balle
annuri.
Mayar da hankali ta yi, za ta cigaba da danna wayarta, Nasir
ya tako zuwa gabanta, ya tsaya ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Kin shirya
aikata abun da Abba ya umarce ki ko kuwa? Ina zan kama Viper"
Cikin hanzari ta tari numfashin sa ta ce "Ban ce shirya
ba, kuma ba zan shirya ba, daga nan har gaban abada,ka je can ka neme shi, yaya
Nasir ka fita ka rabu da ni dan Allah".
Cikin matuƙar mamaki yake bin ta da kallo, "Yanzu duk
kukan da ki ka yi a falo, ƙarya ki ke yi kenan?"
A hasale ta ce "Ina ruwanka, idan ma kukan ƙarya ne ko
na gaske, ka yi aikinka in yi nawa. Ba dai ka je ka gaya masa ƙarya da gaskiya
abun da ka ke so ba? Shikenan, amma kar ka sake yinƙurin shigar mini aiki, idan
ba haka ba komai yana iya faruwa, wallahi ba zan fasa abun da na yi niyya ba,
idan kuma ka cigaba da takura mini, zan baka mamaki ka taka a hankali kar ka faɗo
cikin aikina"
Hannu ya saka, ya ɗagota daga kan gadon ya ce "Menene
zai faru, wani irin mamaki zaki bani? Me zai faru nake son ki gaya mini. Kina
da hankali kuwa Nabila? Kin san doka amma kina taka ta yadda ki ke so? Da me ki
ke taƙama ne haka? Sai da na zauna na nutsu, nake tunani, kenan duk hanyoyin da
nake bi, dan na samu na kama mutumin nan, ke ce ki ke toshe su ko? Ki ke taka
doka yadda ki ke so Nabila"
Ta waro masa idanunta ta ce "Doka ko? Ni iya
takata na yi, kai kuma cin zarafinta ka ke ƙoƙarin yi, ka ƙyale ni babu ruwanka
da ni, ka yi naka aikin na yi nawa duk wanda yayi galaba shikenan. Idan ka ga
dama ka je ka sake gayawa Abba abun da duk yayi maka a kaina, wallahi babu gudu
babu ja da baya, ban fara dan ina saka ran dainawa ba, ba tare da na yi nasara
ba. Ka rabu da ni muje a kan Sharrin da ka yi mini, ina bin ɗan daba a
waje" hankaɗata yayi kan gadon, yana wani irin huci, zuciyarsa na yi masa
zafi, yayi wata irin ƙwafa yana bin ta da kallo. Cikin hanzari ya fice ya bar
mata ɗakin, saboda idan ya cigaba da tsayuwa, zai iya yi mata abun da ba
shikenan ba. Ta yinƙura ta tashi zaune tana haki, tana kallon ƙofar da ya fita.
Yana fita ta dafe kanta, saboda yadda yake wani irin sara
mata, ta kira Sumayya a waya, sai da ta kusa katsewa sannan ta ɗaga.
"Salamu alaikum"
"Wa'alaikum Salam, sumayya dan Allah kina ina ne?"
"Gida, ban daɗe da dawowa ba ma"
"Dan Allah idan kin huta ki zo gida, ina son na ganki,
ina cikin matsala ne, ba zama a bari na fito ba"
"Subhanallah, wace irin matsala kuma?"
"Ni dai ki zo dan Allah"
"Shikenan, bari na canza kaya na zo kawai"
***
Tamkar an ɗora masa gingimemen dutse a kansa, haka ya buɗe
idanunsa da ƙyar, ya na ƙoƙarin tashi, ya ce "Masa oga kar ka tashi, ka
huta tukuna"
Madaki ya ɗaga kai da kyar, ya ganshi a dabarsa ya ce
"Ya aka yi na zo nan?"
"Yaran mai zamani ne, suka kawo ka, suka ce wai gaka
nan ajiya, zai waiwayeka, amma oga ya na ganka da ƙafa ɗaya, sai nemanka muke
yi da kai da lakwari babu wanda ya san in da kuka shiga?"
Ya kalle shi ya ce "Akwai wanda suka san na dawo?"
"Eh mana, su fidda na kogo, duk suna nan aka kawo ka,
labari ma ya fara zagawa cewar an cire maka ƙafa ɗaya"
"Wani taimako nake so ka yi mini, amma bari sai na
wartsake, kaina kamar an kunna wuta a cikinsa, kamar ana narka mini ƙwaƙwalwa,
bari abun nan ya sake ni"
"To shikenan, sannu"
*****
Sosai Nabila take yi wa sumayya kuka, tana gaya mata
abubuwan da suka faru.
"Nabila, shiyasa tun da fari na ja miki kunne, babu
wanda zai tsaya ya saurareki balle ya fahimce ki, gaskiya ina bayan Nasir, ko
dan rayuwarki, yakamata ace kin ajiye wannan shirmen da ki ke yi, ni babban
tashin hankalina haukan da ki ka yi wai son shi ma ki ke yi".
"Laifi ne dan ka tsayawa wanda aka zalunta?"
"Aka zalunce shi a gidan uban wa, mutumin da ya yi
kisan kai? Kisan kai fa yayi. Kuma babban tashin hankalin son sa da ki ka fara
yi. Ba zaki taɓa ganin laifinsa ba, mutuncinki ya zube a banza, a din ga yi
miki kallon mutuniyar banza, wallahi hukuncin da Abba ya ɗauka a kan ki, yayi
dai-dai duk wani abu na shaida ko hujja, ki tattara ki ba wa Yaya Nasir, a kama
shi kowa ya wuce wurin, kan ki janyo wa mutane magana, ni ba a kyauta mini ba,
da bai haɗa woyoyinki ya ƙwace ba, ya bar ki da su" Ta ƙura wa Sumayya
ido, yadda ta ɗauki zafin nan, babu alamar za ta tsaya ta fahimce ta, kawai ta
yi mata shiru, ta gama masifarta, ta tashi ta fita.
Tayi shiru, gaba ɗaya ta rasa abun da yake yi mata daɗi, ta
ji gaba ɗaya duniya tayi mata zafi, rana zafi inuwa ƙuna, ta rasa ina zata
kama, wurin wa za ta je taji sauƙi.
Gari ya waye, Nabila ta shirya tayi ficewarta wurin aiki, ba
wanda ta kula, ta yi ficewarta ta tafi.
Ofishin barrister Habib taje, ta jira shi, ta samu wuri ta
zauna, tana jiransa.
Kallo ɗaya yayi mata, ya buɗe ofishin sa, ya ce mata
"Taso"
Ta tashi ta shiga, suka zauna, ya kalleta ya ce "Ina
jinki yau kuma menene?"
Nan ta kwashe komai ta zauna gaya masa.
Ya ce "Ai dama na gaya miki, dole ki fuskanci ƙalubale,
ki yi haƙuri, komai zai wuce, gobe in Allah ya kaimu kotu zata zauna a kan case
ɗin su rahama, sannan zan cigaba da duk wani ƙoƙari na baki dukkanin goyon
bayan da ki ke buƙata, amma mu cigaba da addu'a"
"To yaya Habib, kai kaɗai ne ka fahimce ni, kotu na
yanke hukunci zamu shigar da ƙarar kotu ta tilasta wa bunkure foundation fito
da ramma, tare da gurfanar da ainihin wanda ya aikata laifin".
"Ki yi haƙuri ƙanwata, nasara na tare da ƙalubale, ina
yi miki fatan alkhairi da fatan nasara".
A sanyaye ta ce "Na gode"
"Amma Nabila, a ina zaki yi generating shaidun da zaki
shiga kotu da su, a kan case ɗin Viper? A ina zaki ganshi?"
"Na ma ganshi, na riga na tanadi duk abun da nake
buƙata, domin fuskantar shari'a"
"You can do it my dear, kuma in sha Allah za ki yi
nasara, akwai yiwuwar zan je na samu major da kaina, nayi masa bayani"
Ta girgiza kai ta ce "No need, kar ka je, hakan ba zai
sauya komai ba"
Ta miƙe ta nufi hanyar fita, tana duba message ɗin da ya
shigo wayarta.
"Mu haɗu a garden, idan baki da aiki"
Tayi masa reply da "On my way".
Yanayin yadda take tafe, tana jefa ƙafa, ya tabattar masa da
a cikin damuwa take.
Tana zuwa gabansa kawai ta nemi wuri ta zauna, ba tare da ta
ce masa uffan ba.
Ya samu wuri ya zauna a gefenta ya ce "Ya aka yi
ne?" Ta girgiza masa kai alamar babu komai.
"Akwai mana, fuskar ki ta nuna"
"Kowa yaƙi fahimta ta, Abba yayi zazzafan fushi da ni,
wai sai na bawa yaya Nasir haɗin kai ya kama ka, ya je ya gaya wa Abba ƙarya da
gaskiya, sam Abba yaƙi saurarara ta, sumayya taƙi fahimta ita ma, barrister
Habib ne kawai ya fahimce ni, Vi na rasa ya zan yi, zuciyata zafi take yi mini,
Nasir ya cuce ni, ya haɗa ni da Abba"
"Yanzu zaki ba shi haɗin kai ya kama ni kenan?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya ba, ba zan iya bari a
kama ka ba".
"Meyasa?" Ta ɗaga kai ta kalleshi ta ce "Ka
sani ai"
"Ban san komai ba"
Cikin basarwa ta ce"Kawai ina so ayi wa matarka adalci
ne, kuma a hukunta wanda suka yi maka laifin"
Ya ce "Gwargwadon yaya ki ke son yar madara?"
"Gwargwadon yadda nake son ka"
"Ki ke son wa?" Yayi maganar ƙasa-ƙasa.
Kasa jurewa tayi, duk jikinta yayi sanyi, ta kasa kallonsa,
gashi ya matso daf da ita sosai.
"To ungo share hawayen" yayi maganar yana bata
handkerchief ɗin sa.
Ta karɓa, amma ta kasa gogewar, ta cigaba da kuka.
"Dan Allah kar ki karaya, ina ƙara jaddada miki, da
Allah na dogara da ke na dogara, amma idan kin ga matsin yayi yawa, ki bayar da
kai bori ya hau, ki bashi dama ya kama ni" ta girgiza kai ta ce "A'a,
ba zan iya bari a kama ka ba" tayi maganar tana sheshsheƙar kuka.
"To ya isa haka kukan, ga wata 'yar ƙaramar kyauta zan
baki" yayi maganar yana sake bata envelope ɗin da ya bata wancan karon.
Ta saka hannu ta karɓa, tana goge hawayen, tana buɗewa
ƙananan hotuna ta ciro guda biyu, wadda ta yi tozali da ita a jikin hoton ce,
ta sakata razana, ta kalli hoton, ta kalli Viper ta shafa fuskarta ta ce
"Wace wannan?"
"Ni ma ban sani ba"
"Yaya zaka bani abu ka ce mini ka ce baka san wace ba?
Wannan....wann... Kai wannan ba ni ba ce ba, bani ce a jiki ba, yaushe aka yi
wannan hoton ban sani ba? Kai wallahi bani ba ce ba, wacece wannan meyasa take
kama da ni" ta yi maganar tana kallonsa, idanunta yake kalla, amma bai yi
magana ba.
"Kayi mini bayani, ka yi magana wacece wannan"
tayi maganar kamar zata zare, tana riƙe rigarsa tana zazzaro masa ido.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
KU KASANCE DA LITATTAFAN BRIGHT PENS A SECOND BATCH, NA
ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL).
MUTALLAB (NIMCYLUV)
ZAYTOON (ZEE KUMURYA) DA HADARIN GABAS (NAZEEFA SABO NASHE)
Idanunta yake kallo, jikinsa a sanyaye amma yayi shiru bai
yi magana ba.
"Kayi magana, ka gaya mini wacece wannan? Bani ba ce a
jiki, amma meyasa take kama da ni? A ina take?"
Still bai yi magana ba, ƙara tsananta riƙon da tayi masa ta
ƙara yi, cikin matsanancin kuka tashin hankali da ƙaraji, take jijjiga shi ta
ce "Ka yi magana, ka gaya mini wacece meyasa take kama da ni? Kuma a ina
take?"
Viper ya ce "Ban santa ba, tsintar su nayi, naga ya
dace kema ki gani, ban taɓa jin kin ce kina da yar uwa da ku ke ciki ɗaya ba,
amma kamarku ta ɓaci da ita, shiyasa na ga ya dace na baki ki gani"
"Ka san wacece, ka saba yi mini wasa da hankali wasu
lokutan, Please na roƙe ka, don't play with my emotions, ka gaya mini dan
Allah" tayi maganar tana kallon ƙwayar idonsa.
Ya ɗan jima yana kallonta, kan ya saka hannu ya cire
hannunta daga riƙon da tayi masa, yana riƙe da hannunta ya ce "'yan
gidanku yakamata ki tambaya bani ba"
"Tayaya zan tambaya? Alhalin a duniya babu abun da Abba
ya tsana sama da nayi masa zancen mahaifina, ban san dalilin wannan mummunar
ƙiyayyar ba, sun yi abun su ya riga ya wuce, amma ya nesan ta duniyata da
mahaifina, duk wata hanya da zata saka na san in da yake, Abba ya tosheta wai
ba wani abu da zai tsinana mini. Wani abu ne mai ciwon gaske da yake addabar
zuciyata, ka fama mini ciwon da yake zuciyata, kuma ka bar ni a duhu, ka
taimaki rayuwata wallahi ko Wacece wannan tana da alaƙa ta kusa da ni"
Viper ya ce "How, an ce kowane mutum akwai irinsa guda
uku a duniya...
"Ba wani guda uku, wannan kamar nice a jikin hoton,
kamannin nan sun yi yawa, ka wayar mini da kai dan Allah"
"Me ki ke so na ce, duk abun da zan faɗa miki ƙarya zan
yi miki, ki je gidan abun da suka ce miki shikenan"
Ta fizge hannunta, ta yinƙura zata tashi, jiri ya kwasota ta
hau tangaɗi, ya riƙe ta, ta ɗan yi shiru ta samu nutsuwa, ta juya ta bar wurin.
***
Ramma kuwa kwana suka yi, Abdul yana juye-juye, ciwon
cikinsa ya tashi, ko baccin kirki ba su yi ba, sai bayan sallar asuba ya ɗan
lafa masa, ya din ga tofa fatiha da bisimillah tana bashi yana sha.
Yana kwance a kan cinyarsa, tana ta shafa masa ruwan tofin a
kan cikin, tana shafa masa, ya riƙe hannunta yana mayar numfashi.
"Sannu Abdul" ya jinjina mata kai alamar yauwwa.
"Wai wannan ciwon cikin, ka dudduba kanka sosai mana,
kana likita amma ka din ga wasa da lafiyarka, kalli yadda ka ke shan wahala dan
Allah"
"Tausaya mini ki ke yi?"
Ramma ta ce "Duk rashin imanina, idan ban tausaya maka
wannan wahalar ba, ya zan yi, idonka har ja yayi saboda wahala".
"Rahama ina ga ciwon cikin nan ne zai yi ajalina, har
ƙasashen waje na je, an kasa gano menene"
Dummm ta ji ƙirjinta ya buga, jin abin da ya ce, amma ta ce
"Dan Allah ka daina wannan maganar, ka din ga addu'a ka cigaba da shan
magani"
"Rahama baki san me nake ji ba ne, ina shan wahala
fa" yayi maganar yana miƙa, tare da lanƙwashe yatsun ƙafarsa, hawaye na
bin gefen idonsa, saboda azabar ciwo"
"Dan Allah ni ka daina wannan maganar" ya juya
yayi ruf da ciki.
"Idan na mutu zaki yafe mini?"
Ta ce "Wataƙila, ai ni dama bana fatan na je gaban
Allah ina neman hakkina a wurin wani, ko wani yana nema a wurina, a duniya nake
fatan Allah ya saka mini abun da ka yi mini, da kai da wannan jakar
matar"ya yi murmushi ya ce "Hakan ma na gode, alfarma ɗaya da zan
nema, dan Allah rahama kar ki zubar mini da cikin nan, ina matuƙar son abun da
yake cikinki"
"Wallahi sai na zubar tas, sai ya bi rariya, ni ka
daina yi mini magana kamar wasiyya wasiyya, dan na tausaya maka"
Sai da yayi dariya ya ce "Abubuwa ne suke ta hargistewa
Rahama, komai ya cukurkuɗe, ban san ya abubuwan za su kaya ba, ina ta ƙoƙarin
baki kariya ne iya yi na, duk da ni mai laifi ne" yayi hamma ya ce
"Idan ya lafa sai na ji daɗi, gashi bacci nake ji, ke ma na hana ki
bacci"
Yayi maganar yana shafo fuskarta, ta saka hannu ta sauke
hannunsa, ta shafa kansa ta ce "Kayi baccin, ko ka samu relief" ya
juyo yana fuskantar cikinta, da yake shafe a jikinta ya ce "Bari na yi
magana da yarona" maganar ta sa tayi daidai da jin motsi a ƙasan mararta.
A haka bacci ya kwashe shi, ta zuba masa ido, tana jin
tausayin sa, gaba ɗaya ya rikice saboda ita, ta ƙara lura da shaye-shaye da
rashin tarbiyya ne kawai yake ingiza shi yake rashin mutunci.
"Kayi haƙuri Abdul, amma komai ya kusa zuwa ƙarshe da
yardar Allah"
*****
Walid ne ya magantu, dan tun shigowar Viper ya lura kamar
yana cikin damuwa, ya ce "Mai zamani, ya ake ciki ne? Jikin ne ko wani
abun ne ya faru?"
Ya numfasa ya ce "Na yi abun da ka ce, Nabila"
Walid ya ce "Masha Allah, ya ake ciki?"
"Ba ta da masaniya a kan hakan, things are complicated,
ta shiga matsala daban daban, ta samu matsala da gidansu, an ce lallai ta bawa ɗan
uwanta dama ya kama ni, she's almost alone, kamar ban kyauta ba, na ɗora mata
abun da ya fi ƙarfinta"
Walid ya girgiza kai ya ce "Ƙaddara ce ta haɗa ku, kuma
she's not alone, tana tare da kai, muna cigaba da addu'a in sha Allah, komai
zai dai-dai ta, ba ta gaya maka komai game da labarinta ba?" Viper ya
girgiza masa kai.
"Bata bani ba, amma na bata hoton, na ce taje ta
tambayi yan gidansu"
"Ina jin alamun nasara, in sha Allah ka kwantar da
hankalinka"
Viper ya amsa da Allah ya sa.
****
Nabila kamar mara laka, ta fito daga wanka, jikinta ɗaure da
towel, ta jiƙo kanta da ruwa, idanunta sun yi jawur, saboda ta yi kuka sosai da
sosai.
Kawai ta ɗaga kai ta ga Nasir a tsaye a ƙofar ɗakin, ta ƙara
haɗe rai, ta ƙarasa tsane jikinta.
"Nabila, lokaci yana cigaba da ja, kuma ke nake jira,
haryanzu baki ce mini komai ba, ki gaya mini in da zan samu mutumin nan, ina ɗaga
miki ƙafa ne saboda Abba, kuma nima ina jin nauyin aikata miki hakan"
Buɗe wardrobe tayi, ta ɗaukko phant da breziar ta jefo kan
gado.
"Magana fa nake yi miki"
Tayi masa banza, ta ɗaga breziar tana ƙoƙarin fara sakawa.
"Nabila wai baki da hankali ne? A gaban nawa zaki saka
kaya?"
"Ni na kawo ka? Ko ka manta bin maza nake yi? Ba abun
da zai hanani saka kayana, ai yanzu ba kunyar wani nake ji ba"
Galala ya bi ta da kallo, jakar da ta fita da ita, ta janyo,
ta ciro ƙaramar wayarta da take vibrating ta ciro ta ɗaga ta ce "Hello
V"
"Are you safe?"
"Yes Alhamdilillah"
"It seems you are bit disturbed"
"No at all"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Kin tambaya ɗin?"
"A'a, ai bai dawo ba, yayi tafiya ne, ni yanzu ina
jiran abun da zai kasance a kotu ne gobe in Allah ya kaimu, and su oga Walid su
shirya, zasu kasance cikin shaidun da zamu gabatar a kotu fa"
"Shikenan, zan gaya musu"
"Yauwwa, gobe in Allah ya kaimu daga kotu zan wuce
wurin 'yan sanda, a kan case ɗin ka, Allah ya sa......
"Nabila, wai me ki ka zama ne?" Nasir yayi maganar
yana tunkararta zai fizge mata waya, ta ja da baya ta ce "Wallahi ka zo in
da nake sai na saki towel ɗin nan, na saki ihu ai kai ka zo in da nake, get out
from sight, wallahi Nasir ko me zaka yi ina kan bakana, ni, ko wani kaga zai yi
mini ƙazafin da ka yi mini, yakamata ka tare mini, amma ka ɓata ni a wurin
mutumin da bani da tamkarsa, wallahi ka cigaba da matsa mini kai ma sai na ɓata
maka suna a gidan nan, ka fita daga rayuwata ba ɗan daba ba, ko uban wa zan
kare ni naga zan iya. Ka je ka yi aikinka nima na yi nawa, kai ma ai amfani ake
yi da kai, ake son kama shi ba dan taimkon al'umma ka ke son kama shin ba, get
out please" yadda jikinta yake rawa take nema ta saki towel ɗin, muddin ta
saki ba shi da kalaman da zai kare kansa da su.
****
Indabo ya kalli Abdul da yake zane yana wasa da mukullin
motarsa ya ce "Wai meye ne, na ganka kamar wani mara lafiya?"
Ya ce "Bakomai, ka yi haƙuri na san maganar
yarinyar.....
"A'a, ai ba maganar yarinyar nan zan yi maka ba Abdul,
ka yi abun da ka ga dama, yau saura sati biyu ɗaurin aure ko wurin yarinyar da
zaka aura duk ka kyauta. Magana ce zan yi maka a kan kuɗaɗen da nake sanya wa a
account ɗin ka, balli na nema ya tashi, an naɗa kwamiti bincike a kan kuɗaɗen
nan, shi ne nake son ka dawo mini da shi, na mayar kan balli ya tashi asiri ya
tonu"
Abdul ya yi sororo yana kallon Indabo .
"Kake kallona kamar shashasha, ka dawo mini da kuɗi na
ce, na mayar musu dama na ɗan jinkirta ne, idan komai ya tafi daidai ayi yaƙin
neman zaɓenka da su, amma zan tanade su a kusa, da na ji ƙishin-ƙishin na
mayar da su"
Abdul ya ce "To, zan dawo da su" ya tashi ya fita.
Bayan fitar Indabo P.A ya shigo, ya samu wuri ya zauna, suka
gaisa da Indabo.
Indabo ya ce "Yaya me ka gano?"
"Eh, ana bibiyarsa gidan sa na lay out, ba kowa a ciki,
duk gidajen shaƙatawarsa, baya nan abokansa duk na neme su, na bibiye su, amma
babu alamar sun san zancen yarinyar ma, amma na in da yake kwana ne, haryanzu
ba a gano ba, ka san wayo ne da shi, wasu lokutan a asibiti yake kwana, amma
sannu a hankali ana cigaba da bibiyarsa"
"Abdul ban san ya aka yi ya zama haka ba, yanzu idan na
matsa tsaf zai yi wani rashin hankalin, yanzu ka duba ka gani, saura sati biyu
fa auren sa, amma gaba ɗaya hankalinsa baya jikinsa, idan na matsa masa a kan
yarinyar nan hauka zai yi mini, shiyasa nake bin sa a sannu, zai zo hannuna sai
ya ci ubansa"
P.A ya ce "Distinguish akwai matsala fa"
"Wace irin matsa kuma? Kullum cikin kiran matsala ka ke
kwanakin nan"
Ya gyara zamansa ya ce "Distinguish, yarinyar nan
sumayya T ladan, sai buɗa maka aiki take yi, kuma duk yan siyasar nan a kanka
ta fi cin kashinka, yanzu wasu matasa daga yankinmu, sun kafa wata ƙungiya suna
wayar da kan jama'a, wai za su rubuta takarda kiranye za su yi maka, ka dawo
gida babu abun da kake tsinana musu sai kwashe musu kuɗi"
Indabo ya kalleshi ya ce "Kai ka taɓa ganin wanda aka
yi wa kiranye a Nigeria? Rabu da su, ƙaryar banza ce, yanzu muna da abubuwan da
suka fi wannan muhimmanci".
P.A ya ce "A'a honorable, kar a fara a kanmu, matasan
nan fa da gaske suke yi, ka san yanzu muna zamanin social media ne, har cikin
ƙauyuka suke bi, da gaske kiranye zasu yi mana"
"Ka je ka haɗa sojojin bakan da muke da su, a basu kuɗi,
su je su karemu, da daƙile abun, sannan a saya musu fili a kafafen watsa
labarai, su shiga su karemu"
P.A ya jinjina kai ya ce "Shikenan, babu laifi za ayi
hakan"
****
Nabila kusan raba dare ta yi, tana kallon hotunan matashiyar
da yake hannunta, ta takura ƙwaƙwalwarta, wurin yin tunani, ko ita ce a jikin
hoton, amma ita dai ba ta san lokacin da aka ɗauki hotunan ba, tabbas ta san ta
nuna hotunan nan, akwai sabon rikici, sai dai ta shirya karɓar duk abun da zai
faru, amma sai ta san wacece a jikin hoton.
Gaba ɗaya ta ɗauki gaba da yan gidan, ba wanda take kulawa,
ko abincinsu ba ta ci.
Ta shirya tsaf cikin uniform ɗin ta, ta shirya ta fice.
Nabila ce a tsaye a gaban kotu ta nemi kotu ta bata damar
gabatar da shaidun da take da su, wanda ba ta gabatar ba a kotun baya.
Kotu ta bawa Nabila dama, Nabila ta taso wata mata, matar ta
zo ta tsaya a gaban kotu Nabila ta ce "Hajiya ko zamu iya sanin
sunanki?"
"Sunana hajara wali"
"Wacece ke a wurin rahama?"
"Ni mahaifiyarta ce, 'ya ta ce"
"Ko zaki iya yi wa kotu bayanin meyafaru"
Mahaifiyar ramma, tayi bayani tiryan-tiryan.
"Kin san wannan?" Tayi maganar tana nuna mata
dattijon.
"Eh, tare da shi muka yi ta ɗawainiyar zuwa kai rahama
Asibiti"
"Shi ne ya dawo ya ɗauke ta?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba shi bane ba, wancan matashi
ne"
Nabila ta ce "Yanzu ina rahama take?"
Cikin kuka ta ce "Ban sani ba, tun da ya ɗauke ta ban
sake ganinta ba".
"Kafin ya zo ya ɗauketa meyafaru?"
Ta goge hawayenta ta ce "Wata mata ce ta zo ta ce mu
karɓi kuɗi, a rufe maganar, na ce ban yadda ba, hakkin 'ya ta nake nema, shi ne
bayan ta tafi ya zo ya ɗauke ta, bayan kwana biyu ya dawo ya ce mini na bashi
kayanta, ta zama mallakinsa"
"Ko zaki iya gaya mana sunan matar?"
lauyan gwamnati, ya nemi kotu ta dakatar da Nabila,
tambayoyinta na ƙoƙarin ƙetare iyaka.
Ya taso zuwa gaban majaifiyar ramma ya ce "Hajiya wanda
ya zo ya tafi da itan, bayan ya tafi da ita, meyasa baki sanar da jami'an tsaro
ba?"
"Na sanar da su, amma suka ce na je gida za su neme
ni"
"Da basu nemeki ba kin koma?"
"Na koma har na gaji, amma babu wani cigaba"
"Sai aka neme ki aka rasa, ko sama ko ƙasa"
"Bibiyar abi mini hakkin 'ya ta da nake yi, ya sanya
aka fara yi mini barazana, shiyasa na bar gidan" ya yi wa kotu godiya ya
koma ya zauna.
Nabila ta sake komawa gaban kotu ta kalli dattijon nan ta ce
"Baba a kotun baya, ka amsa kai ne ka yi wa rahama fyaɗe, shin da gaske
kai ne ka yi mata fyaɗe?"
Ya girgiza kai ya ce "Cewa aka yi idan na ce bani bane
ba, abun da ya samu rahama zai samu 'ya'yana".
"Meyafaru ranar da abun ya faru?"
"A ranar aka ɗaukko ramma daga ƙauye, akwai ƙanin matar
gidan ya zo a buge, ya tambayeni matar gidan sun dawo, na ce masa a'a, amma ya
shiga, bayan wani lokaci ya fito ya ɗauki motarsa ya tafi. Sai bayan zulai ta
dawo daga sayayya, ta fito tana ihu, ta ce na zo na gani, muka tarar da ramma a
kwance a ɗakin girki, cikin jini"
Nabila ta ce ta gama tambayoyin da zata yi, mai shari'a ya ɗaga
shari'ar zuwa sati biyu domin yanke hukunci.
Suka fito tare da barrister Habib da mahaifiyar ramma, da
yaran dattijon, ta ce "In sha Allah, mune ke da nasara, hukuncin da kotu
zata yanke zata yi mana adalci"
Barrister Habib ya ce "In sha Allah, komai ya kusa zuwa
ƙarshe"
Nabila ta ce "Zai dai zo, burina kawai a wanke baba,
daga nan mu ɗora da cigaban shari'a" iyalan dattijon suka din ga yi mata
godiya.
FEW DAYS BACK
Cikin tsananin mamaki, kankarofi yake kallon Nabila. Ya ce
"Barrister, ke ce da kanki a office ɗina? Ya aka yi ki ka san wurin
nan?"
Tayi murmushi ta ce "Ba abun mamaki bane ba, matambayi
ai baya ɓata, yau gani a ofishin masu ƙasa"
Ya ce "Allah ya sa ba laifi nayi ba aka zo kama
ni?"
Ita ma murmushin ta yi masa ta ce "Yan sanda ai su ne
suke kama mutum" ya bata izinin zama.
Ta samu wuri ta zauna ta ce "Na yi sa'a, kana kano baka
tafi Abuja ba kenan?"
"Eh, ina hutu ne, amma haryanzu mamaki nake yi, yadda
aka yi ki ka tako da kanki, ki ka zo har in da nake"
Ta numfasa ta ce "Ka san komai dalili ne yake kawo
shi"
"Haka ne, bari na saka a kawo miki abu mai sanyi"
Ta ce "A'a, Alhamdilillah tambayoyi ne nake da su a
gareka Yallaɓai"
"To gimbiyata ina jinki"
"Case ɗin da nake yi, na yarinya da aka yi raping, ashe
a gidanka aka yi. Na sake komawa na lura da sunan street ɗin sunanka ne, kuma
na tambaya aka nuna mini gidan aka ce naka ne. Abun ya ɗaure mini kai, sai dai
na jajje amma ban samu abun da nake so ba, matar gidan ta koreni, kusan sau
biyu ma, yaya aka yi haka yallaɓai?"
Yayi murmushi ya ce "Waye ya ce miki gidana ne?"
"Sir gidanka ne mana, Mu'azzam wada kankarofi street,
kuma aka nuna mini gidan aka ce gidanka ne, sir ban yi tsammanin haka daga
gareka ba, ɓoye mai laifi a ɗorawa wanda bai ji ba bai gani ba mai
gadinka?"
"Nabila, ina iyakar ƙoƙarina, am even supporting you,
baban yaron nan abokin adawata ne, matata kuma akwai yara a tsakanin mu, bai
kamata na tona mata asiri haka anyhow ba"
"Amma yarinyar mutane da aka zalunta fa? Maigadinka da
aka rufe ba da laifinsa ba fa? Wannan ba hujja ba ce ba, what if ɗanka aka yi
wa haka? Haba yallaɓai"
"Nabila, lamarin ƙasar nan ya wuce duk in da ki ke
zato? Dole sai mutum yana lissafi, amma in tambaye ki mana? Waye ya ajiye miki
tarihin Bunkure a Office ɗin ki? Waye ya tura miki message ɗin babar ramma? Duk
kina tunanin wannan, ko kuwa kawai sabgarki ki ke yi?" Waro ido ta yi tana
kallonsa.
"Mayar da idanun madam"
Cikin mamaki ta ce "But how?"
"Through barrister Habib my dear. Ba zan tona wa yaron
asiri kai tsaye ba, saboda ubansa ne tushen lalata shi, ba kuma nayi haka ne
dan na ɓoye laifinsa ba, ina jan ƙafa a lamarin ne, saboda ki gano komai a
sannu, yadda babu mai zargina, duk da akwai jiƙaƙƙiya tsakanina da ubansa.
Mahaifiyar ramma na tare da ni, ni na saka aka ɗauketa, tun
kan a illata ta saboda case ɗin nan. Zan haɗa ki da ita, zata yi miki bayanin
komai, amma ki daina zargina a kan ɓoye mai laifi, am supporting you, program ɗin
ma da ki ke yi am supponsoring the program sweetheart, ki daina zargina please,
tabbas a gidana aka aikata laifin, kuma ina iya ƙoƙarina a kai madam. Ki je ki
cigaba da aikinki, zan cigaba da ƙoƙarina in taimaka miki"
Saroro tayi tana kallon kankarofi kamar sokuwa.
"Akwai alamar gajiya a tare da ke, ki je zan saka Habib
ya kai ki in da take"
"Amma duk tsawon wannan lokacin, kuka rufe ni ka ke yi
mini yawo da hankali?"
"Akwai dalili ne, amma ki yi haƙuri dan Allah, a
dalilin haka aka saka miki wuta a office, aka kusa taka ki da mota, duk dan ina
tsayawa ina tsawatar wa ne, akwai hatsari a abun da ki ke yi nesa ba kusa ba,
shiyasa nake taimaka miki ta ƙarƙashin ƙasa, amma kiyi haƙuri" ba ta ce
masa uffan ba, ta ɗauki jakarta za ta fita.
"Ina baƙonki kuwa? Idan kun sake haɗuwa ki ce ina
gaishe shi" ta tsaya ta waiwayo ta ce "Wane baƙon kuma?"
"Viper" ya amsa mata kai tsaye.
"Ka san Viper?"
Kankarofi ya ce "Na san shi, akwai labari mai sarƙaƙiya
ne, amma kar ki matsa, ki bi a hankali, zai kawo ƙarshen labarin, kamar yadda
ya faɗa, a sauka lafiya abar ƙaunata" ba ta iya magana ba, ta murɗa ƙofar
ta fice.
Tun a hanya ta kira barrister Habib, take yi masa masifa, a
kan abun da ya yi mata, ya din ga yi mata yawo da hankali da nuna bai san komai
ba.
Sai da suka haɗu, yayi ta bata haƙuri, yana ƙara yi mata
bayani, kankarofi yayi mata kwarjinin da bata tsigale masa ba, amma ta yi wa
Habib ta tas.
****
Nabila tana tafe tana kallon hotunan hannunta, ta kira Viper
ya ɗaga ta ce "V ina wuni?"
"Lafiya ƙalau, ya ake ciki?"
"Ina hanya zuwa zan yi"
"To, Allah ya kawo ki lafiya"
****
Ramma ta tsurawa Abdul ido, ya ce kunun gyaɗa yake so, yana
sha yana waya, ya ajiye kofin kunun ya ce "Daddy ni dai dan Allah ka yi
haƙuri, wallahi ba zan iya fito maka da rahama ba"
Ashariya Indabo ya din ga zabga masa, ya ce "Wallahi
zan saka jami'an tsaro su kama ka, su ci ubanka, uwar yarinyar nan ta bayyana a
kotu, an ambaci sunanka, duk da ba a faɗi cikakke waye kai ba, ga maganar kuɗi
na yi maka, duk ka yi kunnen uwar shegu da ni, Abdul kana son ka gama da duniya
lafiya kuwa? Dole sai ka tozarta ni?"
"Daddy ba tozartaka zan yi ba, makomar rahama nake
dubawa ita ma....
Wata ashar ɗin indabo ya lailayo, kamar ba babba ba, ya gama
masifar, Abdul ya ajiye wayar ya dafe kai.
"Kai ma da naci kamar me, ka fitar da ni mana, ko ma me
za ayi mini ayi mini, sai ɓoye ni ka ke yi kamar ciwo, ni kaina tun ina masifa
har na gaji, haba dan Allah" tsaki ya ja, ya tashi ya bar mata dining ɗin.
***
"Abba ya yi tafiya, yau nake saka ran dawowarsa, zan
nuna masa hoton nan, na ji mai zai ce, tun da kai kaƙi gaya mini wacece?"
"Yaya shari'ar ta kasance?"
"Alhamdilillah, babar ramma ta je kotu ta bayar da
shaida, ina jin alamar nasara in sha Allah"
"Mhmm, a ina aka ganta?"
"Ta gudu ne wani wuri ta ɓuya, daga baya da taimakon
barrister Habib, muka ganota"
Viper ya jinjina kai ya ce "ya nawa, ni ya ake
ciki?"
"Shiyasa na zo ai"
"Ok"
"Kamar yadda na fara gaya maka jiya, dole ina buƙatar
su oga walid, da wannan bugaggen a kotu su bayar da shaida"
"Wane bugaggen?"
"Oho ni na san sunansa ma? Amm sannan sai ka yi haƙuri,
duk wasu rashin ji da ka yi, sai mun yi exposing ɗin su a kotu"
"Rashin ji kamar yaya?"
Ta kalleshi ta ce "Kamar yadda ka yi mana, sara suka,
ƙulla wiwi black market duk da ka yi"
Haɗe rai yayi ya ce "Amma ba prison zan koma ba
ko?"
"Idan ta kama ai dole ka koma"
Ya ce "What? Gaskiya ki yi yadda zaki yi, ba zan koma
prison ba, wanda nayi 5yrs fa?"
Ta zumɓura baki ta ce "Ni na ɗaureka, sai abun da ya
kama kawai, bari na je gidan, na ji wadda zamu yi da su, sai anjima"
*****
Nabila ta tafi ɗakin Abba, domin amsa kiran da yayi mata, ta
tafi bakinta ɗauke da addu'a, ta shiga ɗakin da sallama, suka amsa ban da Abba
da yayi shiru ransa a ɓace.
Ta je ta durƙusa ta ce "Abba gani"
"Nabila ban isa na gaya miki magana ki ji ba ko?"
Tayi shiru ta sunkuyar da kai.
"Dole sai kin nuna wa duniya cewa ban haife ki ba ko
Nabila? Kin nuna mini iyakata, ban isa na nemi alfarmarki ba kenan ko Nabila?
Sai kin tozarta ahalin nan gaba ɗaya ko Nabila?"
Ta girgiza kai ta ce "Abba bani da wannan burin, kuma
wallahi ba zan taɓa aikata wani abu da zan janyo maka zagi ba. Amma dan Allah
Abba a yanzu, ka yi mini wani taimako, saboda zatin Allah kar abun da zan nema
ya ɓata maka rai"
Ta miƙa wa Abba hotunan, da Viper ya bata, ta ce "Dan
Allah Abba wacece wannan? Ni dai na san ba ni ba ce ba, dan Allah Abba ko kana
da masaniya a kan ta jikin hoton nan.
Abba ya saka hannu, ya karɓi hotunan yana dubawa.
Ya gama ƙarewa hotunan kallo, ya ce "A ina ki ka samu
hotunan nan?"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "A office ɗina na
gansu"
A take Abba ya fara yayyaga hotunan, cikin kuka ta ce
"A'a Abba, dan girman Allah ka gaya mini idan ka san ta jikin hoton, Abba
ba ka ga yadda kamaninmu suka ɓaci ba, dan Allah Abba ko sau ɗaya ka nuna mini
wani a dangin mahaifina dan Allah Abba" ƙarasa yayyaga hotunan yayi, ya
watsa mata cikin matsanancin ɓacin rai ya ce "Ki koma in da aka baki
hotunan, su gaya miki koma wacece, ubanki kuma ga hanya nan, ki bar mini gida
ki tafi yawon nemansa, yayi miki abun da ban yi miki ba, tashi ki bar gabana
kan na tattaka ki, da uban naki ya damu da ke, da zuwa yanzu shi ya nemi in da
ki ke".
Anty ta ce "Haba major, dan Allah ka yi haƙuri kar ka
yanke wannan tsatstsauran hukuncin a kan ta, kayi haƙuri dan Allah " gaba ɗaya
jikin Nasir yayi sanyi, ganin yadda take ta uban kuka.
Cikin tsawa Abba ya ce "Ki tashi daga gabana, ki tafi
ki bar mini gida, ki je ki nemi ubanki, amma ki bar mini gida kar na sake
ganinki a gidana"
Wata irin ajiyar zuciya ta din ga yi, ta yinƙura ta tashi da
kyar, ta bar ɗakin, ta koma ɗakinta ta kifa a kan gadonta, ta fara sabon kuka,
shi kuwa Abba wace irin zuciya ce da shi haka? Ko menene a tsakanin sa da
mahaifinta, yakamata ace ya wuce, ta san ya gama yi mata komai a rayuwa, yayi
playing role ɗin uwa, yayi na uba a rayuwarta, amma duk da haka gurbin ido ba
ido bane ba.
Baba magajiya ce tayi sallama, ta ƙarasa kan gadon, ta dafa
kafaɗarta ta ce "Haba Arfa, ke a rayuwarki ba zaki iya haƙuri da tawakalli
ba, tun da ya nuna miki baya son zancen nan ba sai ki haƙura ba, shekara nawa
ana abu ɗaya kin ƙi ki gane ki haƙura".
Nabila ta tashi zaune, idanunta sun yi jawur ta ce
"Baba magajiya"
"Na'am arfa"
"Kema laifina ki ke gani?"
Baba magajiya ta yi shiru tana kallonta.
"Ki bani amsa mana, laifi nayi dan na nemi sanin in da
mahaifina yake na ganshi ko sau ɗaya? Baba magajiya mahaifi fa, a duniya na san
Abba ko baki yayi mini, sai ya kamani, bana nufin yi masa butulci ko tozarta
shi, amma ina son sanin babana, baba magajiya dan Allah ina da wata yar uwa ne?
Ke kin san komai, hoto aka bani da wata a jiki irina ɗaya da ita sak, ko yar
uwata ce, dan Allah ki gaya mini. Ni idan kin san in da zan ga babana ki gaya
mini, ko sau ɗaya na je na ganshi na dawo dan Allah"
Baba magajiya ta girgiza kai ta ce "Ni ban san komai
ba, lokacin da na zo gidan nan, an gama dambarwar da za ayi, na zo, ni bani da
wani labari a kan mahaifinki"
Nabila tayi murmushi mai ciwo, hawaye na bin fuskarta ta ce
"Haryanzu kallon yarinyar da ki ka raina ki ke yi mini ko, shiyasa ki ke
tunanin bani da wayo ko? Shekaru ashirin da biyar a doron duniya, ai na girmi
ki yi mini wayo baba magajiya, amma shikenan, ai Abban ya ce na je ne nemi
babana, zan neme shi kuwa in sha Allah "
Baba magajiya ta waro ido ta ce "Baki san gatse ba
Arfa?"
Nabila ta jinjina mata kai alamar eh, ta mayar da kai ta
kwanta.
Baba magajiya ta ce "Arfa na san har da damuwar matsi
da takura da ake yi miki a gidan nan, ya sanya ki ke damuwa da son ganin
mahaifinki, ni dai roƙona da ke, ki yi haƙuri idan da rabo zaki haɗu da
mahaifinki ko danginsa, amma dan Allah dan Annabi, kar ki bari ku samu saɓani
da maitama"
Nabila ta yi mata shiru, dan gani take yi babu wanda zai
fuskanci halin da take ciki.
Tamkar zuciyarta Abba ya yaga, haka take jin zuciyarta, idan
ta tuna yadda ya yayyaga hotunan nan, sai dai har a lokacin tana ganin hotunan
yarinyar mai kama da ita a cikin idanunta.
****
Duk da Nabila bata
jin daɗin komai na duniyar, jin ta kawai take yi gata nan dai, haka ta cigaba
da up and down a kan muhimman abubuwan da ta saka a gaba.
Ta sake shigar da koke gaban hukumar'yan sanda, ta nemi su
kama madaki da wasu daga cikin yaransa, bisa zargin kisan matar Viper, shekaru
shida da suka gabata.
Yau tana da program a gidan radio, kuma yanayinta ya nuna wa
Sumayya tana cikin matsananciyar damuwa, sai dai ta shigo a ƙurarren lokaci,
zasu fara gabatar da shirin, dan haka ba ta samu damar yi mata tambayar meyake
damunta ba.
Nabila tayi iya ƙoƙarin ta, wurin ajiye damuwa a gefe, suka
fara gabatar da program.
Sumayya ta kalli takardar hannunta sannan ta ce
"Jita-jita ta cika gari, cewa kin shigar da koke gaban kotu, a kan lallai
kotu ta hana hukumar'yan sanda kamar shahararren ɗan ta'addan, da addabi wani
yanki na garin nan, kuma akw zargi da kisan matarsa, duk da yadda hukumar ta
'yan sanda, take nemansa ruwa a jallo?"
Nabila ta kalli sumayya da rinannun idanunta, tayi mamakin
yadda sumayya tayi mata wannan tambayar, a tsakiyar program ɗin su haka, saboda
ba magana ce da ta fita ba, balle ta ce an yi Jita-jita a kai. Sumayya ma ta
tsare ta da ido, alamar tana jiran amsa.
Tayi wani irin murmushi ta ce "Ba ɗan ta'adda bane ba,
mutum ne kamar kowa, kuma ɗan ƙasa da ya dace ya samu duk wani 'yanci da kowane
ɗan ƙasa ya dace ya samu. 'yan ta'adda na yawonsu a gari, an san in da suke, an
san in da za a same su, hakkinsa muke nema a kotu, ba shi ya kashe matarsa ba.
Na san mutane za su yi mamakin yaya aka yi mai dokar bacci ya ɓuge da gyangyaɗi,
amma a bibiye ni a cikin shari'ar da zamu gudanar".
"Amma ba kya ganin hakan kamar taka doka ne, zaki yi
amfani da damarki ta lauya ki taka doka, ki kare mai laifi?"
"Sam, dokar da aka wulaƙanta, da ita nake son yin
amfani wurin gyara kuskuren da aka yi. Tayaya mutum zai shafe shekaru babu
Shari'a, daga baya alƙali da saka hannunsa da umarninsa da komai, a sake shi
bisa doron doka da ƙa'ida, kuma daga baya a zo ana nemansa. Shin wanke shi aka
yi daga laifin? Ko kuma akwai wani ɗaurin ɓoye da yakamata a warware? "
Tayi maganar tana ƙure sumayya da ido.
Sumayya ta kalli agogo, lokaci ya cika, ta na tsaka da
sallama da masu saurare, Nabila ta tashi ta fice, tana kammalawa, ta tashi ta
bi Nabila, amma tuni ta ja motarta ta bar wurin.
Ta koma tana sauke numfashi, kiran kankarofi ta gani, ta ɗaga
wayar suka gaisa, ya ce "T ladan, meyasa ki ka yi wa Nabila wannan
tambayar a tsakiyar program?"
"Sir nayi ne, dan tun yanzu ta kare kanta a wurin
mutane, kafin abu ya bayyana su yi mata kallon, maciya amana mai fuska biyu
"
"Sumayya waye ya gaya miki ana iya wa ɗan adam ne? Ba a
taɓa iya wa mutum, dan haka ki kiyaye gaba, yayi wuri ki fallasa abun haka gaba
ɗaya, amma babu laifi, baki yi kaifi ba, hakan zai ƙara mata ƙaimi"
Sumayya ta ce "Ok sir, na gode" ta ajiye wayar ta
yi shiru, ita a zahiri tayi hakan ne, ko Allah zai sanya Nabila ta ji nauyin
dubban al'ummar da suke goyon bayanta, ta sassauta koma ta haƙura da batun
Vipern nan, amma ba ta ga alamar hakan a tattare da ita ba.
Abbu kuwa a zabure ya miƙe tsaye, jin program ɗin da yayi,
shi ba wani ma'abocin jin radio bane ba, yau kawai ya kunna yana saurare, ya ji
shirin ya ƙayatar da shi, haka zalika muryar barrister, kamar sananniya ce a
gare shi.
Sai dai jin sun yi maganar Viper, ya sanya ya tashi a kiɗime,
tare da ɗaukar radion ya fito tsakar gida.
Rahila ta ce "Ya dai na ganka a firgice haka?"
"Wani shiri na gama saurara, wata lauya ta shigar da
koken kotu ta hana kama Aminu, ko gidan radiyon zan je, wataƙila su sun san in
da yake"
Ta kwaɓe baki ta ce "Ina rabaka da sabgar yaron nan,
idan sun san in da yake me zaka yi masa? Salon ka sanya kanka a masifa, wanda
ake nema ruwa a jallo da laifin kisan kai? Ka ganshi ka yi masa me? Guduwa fa
yayi daga gidan yari"
Ya ƙura mata ido, kawai ya girgiza kai, ya kashe radion ya
fice.
****
Nabila tana driving, wani abu ya tsaye mata a maƙogwaronta,
kukan ma gaba ɗaya ta kasa saboda baƙin ciki da ɓacin rai.
Katafaren gate ɗin aka buɗe mata, ta shiga da motarta, tayi
parking, ta sauka ta nufi cikin gidan.
A falo ta tarar da mahaifiyar ramma, tana ganin Nabila, ta
tashi da fara'arta, tana yi mata sannu da zuwa.
Nabila ta zauna cikin yaƙe, suka gaisa, kamar kullum yau ma
mahaifiyar ramma, kallon Nabila take yi, kamar ta haɗiyeta, ita dai ban da an
yi mata gargaɗi, da tuni ta faɗi abun da yake ranta, dan ta tantance abun da
take tunani, sai dai an gargaɗeta a kan aikata hakan, dan haka ta ja bakinta ta
tsuke.
"Mama ina fatan dai babu wata matsala ko? Ki cigaba da
haƙuri, in sha Allah an kusa dawo miki da ramma, kuma hujjoji nake son kammala
tattarawa, na gano ainihin mai laifin, za a gabatar da shi a gaban kotu, idan
da wani abu ki gaya mini"
Ta girgiza kai ta ce "Ba wani abu, ina ta godiya
Ubangiji Allah ya baki nasara, na gode sosai da sosai da ke da Alhajin da ya
taimake ni, ina godiya Allah ya biya ku, ya ƙara miki zaman lafiya da
mijinki"
Nabila ta ce "Ai ba mijina bane mama"
"A'a ba Alhajin ba, Aminu"
Cikin mamaki Nabila ta ce "Aminu kuma? Nifa ban taɓa
aure ba, ba ni da aure" tayi maganar tana murmushi.
Babar ramma ta ɓoye mamakinta, kar kwaɓarta tayi ruwa ta ce
"Au, ai na zata kina da aure ne, Allah ya kawo miki nagari, ya baki mai
sonki da gaskiya, Allah ya tsaya miki, kamar yadda ki ke ta ƙoƙari a
kanmu"
Nabila ta ce "Amin mama, dan Allah a cigaba da yi mana
addu'a, addu'aeku, ita ce ke tasiri a rayuwarmu"
Maman ramma ta ce "In sha Allah, addu'a yanzu aka
fara"
Nabila ta ce "Na gode sosai" ta tashi ta nufi
hanyar fita, babar ramma ta bi ta da ido, dan ranar farko da ta fara ganin
Nabila, ban da an gaya mata kafin ta zo, an yi mata bayani, da babu abun da zai
hanata kurma ihu, ta ce taga gawa.
Tana driving sannu a hankali, ta tsaya ta sai abun da zata
ci a gida, dan ba sabgar su take shiga ba.
A harabar gidan, ta wuce Nasir, ya zuba mata ido, duk ta bi
ta rame, saboda ta saka jaraba a ranta, ko kallonsa ba ta yi ba ta wuce. Duk
sai ya damu da ramar da ya ga tayi, amma yana nan a kan bakansa sai ya kama
Viper, ko zata mutu dan haushi.
"Ga agolancin ga yawon ta zubar, ga ta'addanci, gashi
an gandame an riƙa a gida babu aure, abun bai yi miki yawa ba kuwa Nabila"
Sauda tayi maganar tana dariya.
Ta sake cewa "
An baki damar ki gusa ki bamu wuri, saboda baƙin naci, kin
liƙe mana a gida, tun da ba zaki tafi ba, ki iya kanki, muna son ubanmu, ba
zaki kashe mana da baƙin cikin ki a banza ba"
Nabila ta tsaya cak, tare da murnar Sauda ta takale ta, ko
banza ta rage zafi idan ta yaɓa mata magana.
"Ke da ki ke son uban naki, sai gashi kin gagara zaman
aure, kin ƙi karatu balle hankalinsa ya kwanta. Ai sauda zaki yi mini gorin
aure ne, a lokacin da ke ki ka iya zama a gidan naki mijin. Kuma karki manta da
ni agola ce mai 'yanci, a dalilina igiya biyu aka sauke wa babarki ta aure,
idan ku ka cigaba da matsa mini, ragowar ɗayan ma sai na tsinketa, sai ku ji daɗin
zawarci tare ga uwa ga 'ya. Yawon ta zubar kuma, ina da abun bayar wa yayi mini
rana, kema idan ki na so ki bayar nonsense"
Sauda ta tashi a ƙufule, Nabila ta ce "Kin san dai ba
dakuwa zan yi ba, dama koma wa ki ka yi ki ka zauna"
Sauran wanda suke wurin, suka tuntsure da dariya, dan yadda
Sauda ke zuba mulki da rashin mutunci a gidan nan, Nabila ce kawai maganinta.
****
Cikin mamaki Abdul ya ɗago ya kalli indabo, saboda marin da
ya kwaɗa masa.
"Ina na kai mini kuɗi Abdul?"
Abdul ya yi shiru yaƙi magana.
"Ka gaya mini in da ka kai mini kuɗi, kafin na tattaka
ka a wurin nan? Yarinya da ka fito da ita, da kar ka fito da ita, matsalarka
ce, ba zaka kashe ni da ɓacin rai ba, sai na samo wani wanda ba zai watsa mini
ƙasa a ido ba, ina ka kai mini kuɗi?"
Mahaifiyar Abdul ta ce "Abdul wai ba magana ake yi maka
ba? Ina kuɗin da ya zuba a account ɗin ka, da sunan campaign kuma ya muka yi da
kai a kan yarinyar nan?"
Abdul ya numfasa ya ce "Na yi wa 'yan garin su rahama
gyaran makarantu da hanyoyi, na yi musu boreholes, sai kuma registration da
nayi mata na karatu bar zuwa jami'a" ya faɗa kai tsaye.
Salallami suka hau yi, da tafa hannu.
Indabo ya ce "Abdul, kuɗin ka kwasa ka ƙarar a kan
garin yar matsiyata da karuwa?"
Ya girgiza kai ya ce "Daddy ba karuwa ba ce ba, koma
menene ni ne mai laifi, fyaɗe nayi mata, nayi hakan ne, dan na goge
laifina"
A fusace Indabo ya rufe shi da duka, ga ƙiba ga hawan jini
yana fama, a take ya hau haki, da kyar P.A ya janye shi daga jikinsa.
"Ƙarya ma kake yi, ka fito mini da kuɗina, sai na yi
seazing ɗin asibitocinka, da duk wata kadara daka mallaka, da wadda na mallaka
maka, ni zaka tonawa asiri, wallahi baka isa ba, kuma zan saka a nemo mini
yarinyar ko ina ka kai ta, zan yi maganinka daga kai har ita".
"Dan Allah daddy kar ka cutar mini da ita, ba tayi
laifin komai ba, ni zaka hukunta"
Ashariya ya din ga zabgawa Abdul, yama rasa me zai yi, kuɗin
da suka yi sama da faɗi da su, domin campaign bisa ga yarjejeniyar idan an yi
nasara zasu mayar da kuɗin da uwar riba, ga balli na neman tashi, dama kuɗin
mutane ne na wasu hukumomi a ƙasa, ga balli na neman tashi, kuma Abdul ya yi
masa hauka.
P. A ya ce "Kayi haƙuri, kar ka je wani abun ya sameka,
ka rabu da shi, zamu san abun yi, mu fara kashe case ɗin can na gaban kotu
tukuna".
"Na fara tunanin anya Abdul ɗa na ne? Ƙiriƙiri ya zaɓi
mace a kaina, ni zai tozarta?"
P.A ya ce "Jarabta ce da kuma ƙuruciya ke damunsa"
"A shekara talatin da shidan ne ƙuruciya?" P.A ya
din ga bashi haƙuri yana lalaɓa shi, Abdul kuwa tunu yayi ficewarsa.
*****
Madaki na zaune a cikin ɗaki, ya din ga jin hayaniya, da
iface-iface ana sara suka a ƙofar gidan da yake.
Wani daga yaran sa ya shigo da kyar, ya ce "Madaki, yan
ƙofa ne fa suka zo gidan nan, muna ta fama da su, sai ƙoƙari suke lallai sai
sun shigo gidan nan, su sareka"
Madaki ya tashi ya ƙwalalo ido, sai dai kan yayi magana, sun
faɗo gidan, sun kai su bakwai, suka zo ka hau shi da sara da suka, wasu na waje
na faɗa da yaran madaki.
Duk da akwai ƙarfin zuciya, yana ta ƙoƙarin kare kansa, amma
sai yaji jikinsa kamar an canza masa wani, duk yayi wani iri babu ƙwari, suka
din ga saransa, ƙarshe suka janyo shi daga cikin gidan, suka din ga jan sa a
ƙasa tamkar abun banza, duk da iya ƙoƙarin da yaransa suka yi, su ƙwace shi,
amma abu ya ci tura, tsofaffin yaran Viper, da yan unguwar su, da ya din ga
shiga yana addabawa ya hana su sukuni, su suka yi gangankon ɗaukko shi, suka yi
masa laga-laga, suka din ga yawo da shi, lungu da saƙo, daga ƙarshe da ƙyar
jami'an tsaro suka kawo masa ɗauki, suka tarwatsa matasan, suka ɗauke shi a
galabaice, dan ba su zaci yana raye ba, suka kai shi Asibiti.
*****
"My Abdul" ta yi maganar tana murmushi, cikin
hanzari ya ɗago, dan bai zaci daga bakin ramma maganar ta fito ba.
"Meyafaru ne? Gaba ɗaya na ganka a cikin tashin
hankali?"
"Rahama abubuwa sun ƙara cakuɗe mini, barin ƙasar nan
zamu yi"
Cikin mamaki ta ce "Mu bar ƙasar nan, mu je ina?"
"Rahama abubuwa ba zasu tafi yadda na tsara ba, zamu
bar Nigeria"
"Ban gane ba, uwata fa?"
Abdul ya ce "Zan saka a kawo miki ita, yanzu visa za
ayi miki, amma sai na fara barin garin nan da ke"
"Abdul, ni fa gani nake wannan guje-gujen, duk ba zasu
kaimu ba, kayi haƙuri ka yi abun da mahaifinka ya buƙata mana"
Ya kalleta ya ce "Na kai ki kotu ki gaya wa duniya, ni
ne nayi miki fyaɗe? Ba wannan ne ya dame ni ba, abun da zai biyo bayan shaidar
da zaki bayar shi ne abun jin, dan haka ki nutsu kiyi abun da na ce kawai"
Murmushi ta yi masa da ita kaɗai ta san ma'anarsa, ta wuce
shi ta tafi kitchen.
****
Daga Naja'atu har Indabo fuskokinsu ɗauke da damuwa, Bunkure
tayi ƙwafa ta ce "Gaba ɗaya hankalina a tashe yake, lallai gaskiyar
hausawa, ɗan hakin da ka raina, shi ne yake tsole maka ido, yarinyar nan dai ta
dage sai ta ga bayana, idan asirina ya tonu, ban san wane irin kallo zan yi wa
al'umma ba. Abdul duk shi ya janyo wannan abun.
P.A ya ce "Duk ku kwantar da hankalinku, babu wani abu
da zai faru, kamar yadda ka yi umarni, dattijon nan zai shiga silent, yanzu
uwar yarinyar ta rage, ita muke binciken in da take, kuma ita ma zamu ganota in
sha Allah, Abdul ma muna daf da gano, wurin da ya ɓoye yarinyar nan"
Indabo ya girgiza kai ya ce "Ban san in da Abdul ya
koyi wannan baƙin taurin kan ba, magana ta fito fili, an ce a binciki
ministocin da muka ƙulla harƙallar kuɗaɗen nan da su, na san kuma dole sai
sunana ya fito, wai ya kwashe kuɗin nan, ya yi wa yan ƙauye ayyukan raya ƙasa,
na rasa uban abun da ya samu a jikin yarinyar talaka mara galihu, ya nace mata
take abun da ta ga dama har haka"
Bunkure ta sauke numfashi ta ce "P.A ya batun barrister
Nabila?"
"Kamar yadda na gaya muku, sponsiring ɗin ta ake yi, na
gwada sakawa a kamo mini ita, amma hakan ya gagara akwai jami'an da suke bin
ta, wanda ba san suwaye ba, kuma da alama ita kanta ba ta san suna bin ta
ba"
Indabo ya ce "Kar ku ja da nisa, kankarofi ne, babbar
buƙatar sa ya ga ya kai ni ƙasa, ya rama abun da nayi masa, kuma yayi kaɗan".
*****
Nabila na zaune a ɗakinta, tunanin ma ta rasa wanne yakamata
ta yi, kawai ta ga Nasir ya shigo ɗakin, ba ta ko motsa ba, balle ya sanya ran
za ta kula shi.
"Nabila"
Ta ɗaga ido ta kalleshi. "Da gaske ke ki ka nemi a hana
kama Aminu Viper"
"Eh" ta faɗa a nutse.
"Nawa aikin ki ke burin ɓatawa kenan, me nayi miki haka
ne?"
Ta kalleshi ta ce "Ba kai nake fatan ɓatawa aiki ba,
duk wani mara gaskiya sai na ɓata masa aiki. Gaba ɗaya ka canza i miss my old
DSP, the only person that understand me" tayi maganar tana tashi ta bar
shi a ɗakin.
Tana office ɗin ta, tana son zuwa duba jikin malam garba,
tana son zuwa wurin 'yan sanda, tana son ganin Viper, ga kuma maganar Abba da
ta tsaye mata, da ya ce taje ta nemi ubanta, ta bar masa gida.
Kenan Abba ya goyi bayan ɗan sa, shi ma a wannan karon ya
nuna mata, gurbin ido ba ido bane ba.
Turo ƙofar office ɗin aka yi, ta tashi zaune sosai daga
kashingiɗar da tayi, tana tunanin ina ta taɓa ganin baƙon nata.
Ya samu wuri ya zauna, suka gaisa, ya ce "Baki gane ni
ba ko?"
Ta jinjina kai ta ce "Gaskiya dai"
"Haka ne, magana na zo mu yi da ke mai muhimmanci"
Nabila ta ce "Ok, ina jinka"
"Saƙo ne daga wurin distinguish Ma'aruf Indabo, na zo
mu yi magana mu fuskanci juna da ke"
Nabila ta yamutsa fuska tana kallonsa.
"Muna yi miki tayin ki fanshi kanki da kanki ne, kan
abun da ba a so ya afku"
"Ɗan yi sauri, ina da wurin zuwa"
P.A ya ce "Maganar da na zo da ita, ta fi abun da zaki
je yi muhimmanci, muna son ki janye shari'ar nan ta batun fyaɗe nan, case ne
tsakanin ki da Bunkure, kuma ko yanzu kin cika burinki a kanta, akwai maƙudan
kuɗaɗe muddin ki ka aikata abun da na ce"
Nabila ta ce "Malam na yi maka kama da shashasha ne? Da
Bunkure nake case ɗina, meye nasa a ciki? Bibiyar rayuwata da ya saka aka din
ga yi, da ƙoƙarin kashe ni, duk bai ishe ku ba, shi ne zaka zo mini da maganar
bunkure? Wallahi idan kaga na bar case ɗin nan, to an hukunta ainihin mai
laifin ne, kuma muddin wani abu ya same ni, kai ko mutuwa nayi, ina da manya
manyan hujjoji a kan sa, da suke a hannun wakilai ne, akwai wanda za su ɗora,
in sha Allah sai na bayar da misali a Nigeria, an fara hukunta masu riƙe da
madafun iko, da iyalansu, ba wai doka a kan talaka kawai ba, everyone is equal
before the law"
"Haka ki ka ce?"
"Hala kurma ne kai?"
Ya ce "To bari mu gani, yaro bai san wuta ba sai ya
taka"
"Na santa farin sani, tun da na ɗaukko ƘARFEN CIKIN
WUTA, da ya gagari hannaye da yawa"
P.A ya kalleta ya ce "Me ki ke nufi?"
"Zaka fahimta nan ba da jimawa ba"
Yana fita tayi tsaki, ta ɗauki jakarta ta fita, a nan ta bar
motarta, ta hau abun hawa ta tafi gidan Viper.
Yana tsakar gida, daga shi sai ɗan mama a gidan, suna hira.
Sun daɗe suna kallon juna, sannan ta ƙarasa ciki, ta samu
wuri ta zauna ba tare da ta ce masa uffan ba.
Ya samu abu ya zauna, ya ce "Ya ake ciki, meye
labari?"
"Ko ka neme ni, kwana biyu ina cikin damuwa da tashin
hankali, amma ko a jikinka"
Ya tsuke fuska ya ce "Menene?"
"Vi"
Ya Kalle ta, tare da ɗage girarsa ɗaya.
"Ka dubi girman zatin Allah, ka tausaya mini, ina ga
ciwon zuciya na daf da kamani, kowa ya ja da baya ya juya mini baya, Abba ya
yayyaga hotunan nan ya watsa mini, ya ce naje na nemi ubana na bar masa gida,
daga shi har yan gidanmu, babu wanda yake kula ni. Gashi a tsakiyar
program sumayya ta hau yi mini tambaya a kanka, yanzu ta ko ina mutane sai
attacking ɗina suke yi a media, saboda case ɗinka, client ɗina malam garba wai
ya yanke jiki ya faɗi na je na duba shi, na tarar wai ya samu stroke, yanzu P.A
ɗin Indabo ya bar office ɗina da tashi barazanar, kuma haryanzu ka ƙi gaya mini
dalilin da ya sanya Indabo yake bibiyata. Na rasa ya zan yi me zan yi ne? Kamar
na gaza, ba wanda zan je na samu duk na gaya wa damuwata, dan Allah Viper ka
gaya mini wacece ta jikin hoton nan, ina jin kamar ina da alaƙa da ita, tun da
ni dai na san ba ni bace ba, dan Allah idan akwai wani abu da ka sani ka gaya
mini, atleast na rage wata damuwar".
"Na gaya miki ban san komai ba, 'yan gidanku zaki
tambaya"
"Na gaya maka ba zasu gaya mini komai ba, so kake sai
na mutu ban san babana ba, idan kana da yadda zaka yi ka taimake ni dan Allah,
ko hakan ne alfarmar da ya rage da zaka yi mini a rayuwa" tayi maganar
tana haɗa hannayenta biyu cikin sigar magiya.
"Ana kiranki a waya"
"Ni ba ta waya nake yi ba, ka taimaka mini dan
Allah"
"Ki ɗaga wayarki " yayi maganar yana kallon ta.
Ta ɗaukko wayar, ta ga lambar barrister Habib ce, ta ɗaga
wayar ta ce "Hello"
"Na duba office ba kya nan, Allah ya yi wa malam garba
rasuwa yanzun nan" miƙewa ta yi tsaye, ta saki wayar, ta tashi za ta nufi
hanyar fita, jikinta yana rawa.
Cikin zafin nama, Viper ya tashi ya riƙe ta, gaba ɗaya ta
gigice, ta ce "Sun kashe shi, wallahi kashe shi aka yi"
Ya ce "Waye? Waye ya kashe shi?"
"Malam garba, wayyo Allahna, meyasa na karɓi
shari'arsa, na janyo ya rasa raywarsa a banza, bani da sa'a wayyo Allah
zuciyata" wata irin miƙa tayi, kamar zata zare, ta fara kokowar ƙwace wa
daga hannun Viper, tana kallon hanyar waje.
Ya ƙara riƙeta ya ce "Abla, tsaya ki ji, ki nutsu"
Magana take son yi, amma numfashinta ya din ga sama yana
ƙasa, hannunta da ya riƙe, ya din ga jin bugun zuciyar ta da sauri-sauri.
Ya ciro wani abu a jikinsa, ya saka mata a gefen wuyanta,
gaba ɗaya jikinta ya saki.
Ya kalli ɗan mama ya ce "Ka kira mutanen nan a waya, su
aiko da mota, a kaita Asibiti"
Ɗan mama yayi saroro ya ce "A ina ta ajiye motar
tata?" Viper ya ƙura masa ido, ya ce "Au, ammm wasu mutanen?"
"A tunaninka duk abun da ka ke yi ban sani bane? Zaka
kira su ko ni na kira su?" Ɗan mama yayi wiƙi-wiƙi da ido, cikin tsoro da
mamaki".
"Am talking to you, and you are looking at me" ba
shiri ɗan mama ya ciro waya yana kallon Viper.
****
"Abdul yau ka addabe ni, kamar nayi maka dukan tsiya
haka nake ji"
"Sorry baby, kin san kullum ke ta musamman ce, i so
much love the natural you".
Ramma ta ce "Wallahi ka isheni, duk ka dame ni"
"Wallahi wani mafarki nayi da bai yi mini daɗi ba, ya
bani tsoro".
Ramma ta ce "Maganin wanda baya addu'a"
"Wallahi ina yi, har karatun Alqur'ani nake sakawa
fa"
Ta ce "To Allah ya bada lada, yanzu ka bani wuri na je
nayi wanka, zan yi salla".
Ya tashi zaune ya ce "Mu je, daga nan sai ki ɗan dafa
mana wani abun, yunwa nake ji"
Yayi maganar yana ɗagota, daga kwancen da take.
A tsakiyar gado suka din ga ciye-ciye da shi da ramma, suna
yi yana tsokanarta, tana gaya masa baƙar magana yana dariya.
Tamkar ya mayar da ramma cikin sa haka yake ji, kuma ya kasa
ɓoye mata hakan, suka kwanta ya gama damunta, bacci ya kwasheta.
Juyi ta yi zata gyara kwanciyarta, ta ga Abdul a zaune, ya
saka wayarsa a gaba, ya ɗora hannu a ka, yana wani irin kuka tamkar ɗan ƙaramin
yaro.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
Tashi ramma tayi, ta ce "Abdul, wai menene meyafaru
ne?" Yayi mata shiru ya cigaba da kuka.
"Dan Allah kayi magana mana, ko mutuwa aka yi
muku?"
Yayi mata shiru bai yi magana ba, ta kai hannu zata ɗauki
wayar, amma ya janye wayar ya kashe.
Kawai ya yinƙura, ya ɗauki mukullin motarsa, ramma ta miƙe
ta riƙe shi ta ce "Ina zaka je ne?"
"Fita zan yi"
"A wannan yanayin da ka ke? Idan wani abu ya sameka fa,
dan Allah koma menene kayi haƙuri, zuwa Allah ya kaimu gobe, dan Allah ka
haƙura da fitar nan" jifa yayi da mukullin, ya koma ya zauna ya cigaba da
kuka.
Ta zauna a kusa da shi, cikin damuwa ta cire masa hannunsa
da ya rufe idanunsa ta ce "Abdul, kalleni menene wai?"
Ya sake sunkuyar da kai, kamar ita ce baya son haɗa ido da
ita. A hankali ya kwanta a jikinta kamar ƙaramin yaro, ta rungume shi sosai,
tana shafa kansa ta ce "Koma menen kayi ta nanata Innalillahi wa
Innalillahi raji'un, zaka samu sassauci in sha Allah" wata irin ajiyar
zuciya ya din ga yi, wanda sai da ya bata tsoro.
"Rahama" ya kira sunanta da kyar a galabaice.
"Dan Allah ko na fuskanci hukunci, kar ki manta da ni,
na san koma menene zuwa ki gama karatunki, zan fito"
"Tom" ta faɗa a sanyaye, dan wasu lokutan har
tausayi yake bata, gaba ɗaya Abdul ya saduda, duk wannan iskancin da rashin
mutunci ba ya yin su.
"Rahama kin ce mini kina da yaya da ƙani ko? Har su ina
son in ɗauki nauyin su"
Ramma ta ce "Ba na gaya maka yayana ya mutu ba, sai
ƙanina sani"
"Da gaske ki ke fyaɗe aka yi masa ya mutu?"
Ta ce "Oho ina na sani, ba ka ce mini ba a yi wa maza
ba, ni kamar haka na so na ji an ce, wai za a samo masa aiki, yaje Abuja aka yi
masa, amma mama ba ta taɓa zama ta gaya mini yadda abun ya faru ba, ko tunawa
ba ta son yi, idan ta tuno da shi tayi ta kuka"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ban san me zai faru ba, amma
dan Allah duk tsanani kar ki rabu da ni, ki zama mai yi mini uzuri da tausaya
mini dan Allah, Allah ma baya kama wani da laifin wani"
Ramma ta ce "Da bana yi maka uzuri, da bana tunanin
zamanmu zai zo i yanzu, ka daina wannan kukan dan Allah kunya kake bani"
tayi maganar da sigar tsokana.
Ya ƙanƙameta ya cigaba da sheshsheƙar kuka.
"To ɗan jariri, ya isa haka, cikin dare kawai mutum ya
tashi yana kuka, ko ka je ka yi alwala kayi salla".
"Ba zan iya ba, ba zan yi karatun sallar dai-dai
ba"
"Kaga amfanin ibada ko, idan bawa ya tuna da Allah,
lokacin da yake cikin yalwa, Ubangiji yana tuna wa da shi lokacin da yake cikin
ƙunci, ka cigaba da addu'a, Allah ya yaye maka damuwar ka doctor Abdul
yasar" yayi lamo kamar kyanwa a jikinta, ba tare da ya kuma magana ba.
****
A hankali Nabila tayi juyi, tana ƙoƙarin gyara kwanciyarta
kawai ta ga Viper a zaune a kan kujera, yana danna waya. Ta ƙura masa ido tana
kallon sa.
"Wannan kallon haramun ne, ki daina yi mini wannan
kallon" yayi maganar ba tare da ya kalleta ba. Ko ƙifta ido ba ta yi, ta
cigaba da kallonsa.
Ya waiwayo sosai yana fuskantar ta, ya ce "Ya aka yi
ne? Ya jikin?"
Ta ɗaga hannunta, ta kalli drip ɗin da yake shiga, ta ce
"Vi"
"Mmm"
"Ina ne nan?"
"Wurin sayar da mutane" yayi maganar yana cigaba
da danna wayar.
Ta lumshe idanunta ta buɗe, ta ce "Kamar bacci nake yi,
kuma kamar a zahiri ne, dan Allah da gaske malam garba ya mutu?"
Viper ya ce "Eh, ya mutu"
Ta girgiza kai, tana kuka daga kwance ta ce "Ai
shikenan, ya mutu bai shaƙi iskar 'yanci ba, ban cika masa alƙawarin da nayi
masa ba, da yaya zan kalli iyalinsa? Kullum da shi nake kwana nake tashi a
zuciyata, ya mutu da mummunan tabo a zuciyarsa da rayuwarsa, ban cika masa
alƙawarin da nayi masa ba, na gaza na kasa" tai maganar tana fashewa da
matsanancin kuka.
"Ke, wai baki da tawakalli ne? Shikenan ke ba zaki
mayar da lamarinki ga Allah ba? Wani ya ce ke ki ka kashe shi ne?"
Ƙara sautin kukan ta yi, ta ce "Ya ka ji da aka kashe
matarka, ya zuciyarka tayi da aka ƙala maka laifin kisanta? Haka iyalan malam
garba suke ji, da wannan ɗacin da baƙin cikin ya mutu, kuma ni ban yadda da
wani stroke ne ya kama shi ba, wani abun suka yi masa" Viper ya janyo
kujerarsa gaban gadon sosai, ya matsa daf da ita, ya ce "Ki yi
haƙuri" ta kalli cikin idonsa ta ce "Kai yakamata na bawa haƙuri nayi
alƙawarin saka kotu ta wanke malam garba, a gurfanar da ainihin wanda yayi
laifin, amma ya rasa rayuwarsa ina kan ƙadamin aikin, na fara tsorata kamar ba
zan iya ba Vi"
Ya girgiza kai ya ce "Zamu cigaba da ƙoƙari, ba zamu
gaza ba, ba zamu sare ba, zamu yi nasara in sha Allah, idan kina cewa kin
karaya, nima karaya nake yi" ta ja wata irin ajiyar zuciya ta kalli rigar
jikinsa.
"Vi"
"Mmm"
"Me kake ɓoye mini ne? Ba irin wannan rigar ka yaga
lokacin kana Asibiti ba, mai tambarin dragon ɗin nan ba?"
"Ki daina saka ido, kina ƙirga mini kaya, son rigar
nake yi" hararsa tayi ta ce "Am not kid"
"You are" yayi maganar very serious.
Wani ne ya shigo ɗakin Nabila, yana shigowa ya ce
"Viperrr" ya kira sunan yana jan sunan, tare da dunƙule hannunsa, ya
miƙawa Viper, Viper ya dunƙule nasa suka haɗa.
Ya ce "Ya madam, ta tashi? Barrister ya ƙarfin
jiki?"
"Ba sauƙi" ta faɗa tana tura baki.
Duka suka kalleta, ya ce "Subhanallah, ba sauƙi fa,
garin yaya meyafaru?"
Ta nuna Viper, ta ce "Baya son na warke, bai iya jinya
ba sam" dariya ya yi ya ce "Maza gumbar dutse, ina Viper zai iya
jinya dama, ki manta da shi, zaki samu sauƙi in sha Allah, meyake damunki
yanzu?"
Ta girgiza kai ta ce "Babu komai, ƙirjina ne yake nauyi
kawai"
"To ki cire damuwa daga ranki, zai daina in sha
Allah"
Ta ce "Ok sir, na gode sosai" yayi rubuce-rubuce a
file ɗin hannunsa ya fita.
"Vi"
"Mmm"
"Wai ina ne nan? Kuma waye wannan ɗin?"
"Asibiti da likita"
Nabila ta ce "Ai na san asibitin ne, ina son tafiya ne,
zan je na ga malam garba"
Viper ya kalleta ya ce "Kina da abun gaya wa iyalinsa
ne?" Jiki a sanyaye ta girgiza masa kai.
"To sai ki daina maganar zuwa"
"To ina son na gaya wa yan gidanmu ina Asibiti, kar a
neme ni"
"Wa zaki kira? Wanda ya ce ki bar masa gida ki je ki
nemi babanki, ko kuma yayanki da yake yi miki bita da ƙulli? Ko kuma sauran yan
gidan da suke yi miki kallon yar hana ruwa gudu? Ba wanda ya damu da ke, mutum ɗaya
ne, kuma a halin yanzu an gurɓata masa tunani, na taɓa tsintar kaina a cikin
wannan halin. Mata guba ne mai masifar dafi da saurin kashe wanda suka hara.
Annabi Sallallahu alaihi Wasallam yayi gaskiya, da ya ce Bai bar wata fitina a
bayansa da take cutar da maza ba a bayansa sai mata, banda haka me zai sanya
mace ta raba ɗa da uba?" Yayi maganar jijiyoyin kansa na kumbura, idanunsa
suka yi ja, suka ciccika da hawaye, tuna mahaifinsa da ya yi.
"Ni ba guba bace ba, idan ka yi wa dukkan mata ka kira
mu da guba, baka yi mana adalci ba, yakamata ko albarkacin jauhar mu ci, ka din
ga kallon wasunmu ne gurɓatattu, kamar yadda kuma a jinsinku yake da akwai gurɓatattu"
Yayi shiru tare da sunkuyar da kai, saboda sake soso masa
wurin da yake yi masa ƙaiƙayi.
****
Indabo yana zauna yana karyawa, tare da matarsa, kawai Abdul
ya faɗo tsakiyar wurin da suke cin abincin.
"Meye haka Abdul, baka iya sallama ba baka iya gaisuwa
ba"
Indabo ya ce "Ko giyar ka je ka sha, ka yi shaye-shaye
ne?"
"Na daina shan giya da miyagun ƙwayoyi, tun bayan da
rahama ta shigo rayuwata, ta haskar baƙar bayahudiyar rayuwar da kuka
tarbiyyantar da ni a kai, kodayeke gara ma ni shan giya ne da neman mata kawai,
but am so much disappointed on you, nayi dana sanin kasancewar ka mahaifina.
Dama a tsatson talakawa na taso, talakawa futuk sai ya fiye mini wannan
mummunar rayuwa da iftila'in kasancewar ka mahaifina"
"Abdul, uban naka ka ke gaya wa haka? Duk iya ƙoƙarin
da yayi na ƙarar da rayuwarsa wurin ganin ya gina ku, ka zo gabansa kana gaya
masa wannan maganar?"
"Mummy! Wace irin gina rayuwarmu, gangar jikin da aka
gina da zunzurutun haramun da jinin mutane? Haba mummy da alama mafitarki kawai
ki ka nema, ya sanya ki ka auri Daddy, wallahi mu 'ya'yanki baki yi mana adalci
ba, kuma a yau ba sai gobe ba, zan bar ƙasar nan, na nesanta kaina da ku, tun
kafin asirinka ya tonu a idon duniya abun da ka yi ya shafe ni, gara in kalli
duniya a hukunta ni da laifin fyaɗe da nayi, da a hukunta ni da mummunan laifin
da ka aikata, ga waya nan ka karɓa ka saurari saƙonka"
Yayi maganar yana miƙa masa wayarsa, Indabo ya saka hannu ya
karɓa, yana dubawa.
Wani audio ya fara buɗewa, sai dai jin muryar wanda yayi
message ɗin kawai, ya rikita masa lissafi, ya fara gumi hannunsa ya hau rawa.
"Wanna saƙon ba naka bane ba, na mahaifinka ne. Duk da
ina da access na yadda zan same shi, amma yafi dacewa na tura masa saƙon ta
hannunka, sai yafi karɓar sa da muhimmanci. Lokaci yayi da zamu daina buga
wasan 'yar ɓuya da kai indabo, zamu yi wasa na ƙeƙe da ƙeƙe, saboda ina daf da
barin ramina da nake ɓoye, na cigaba da addabar rayuwar ka ta kowane hali. Idan
ka muzgunawa Nabila, tamkar jauhar ka taɓa mini, taɓa jauhar kuwa taɓa zuciyata
ne kai tsaye. Dan zan yi wasa irin wanda ka ke so ayi.
Ka so ta zama tarkon da zaka yi amfani da shi ka kamani, shi
kuma Allah ba azzalumin sarki bane ba. Ɗanka ya yi wa rahama fyaɗe ƙanwar Nura,
da ka lalatawa rayuwa ka kashe, ka ɗorawa wani daban, kuma ka bishi ka saka an
kashe shi. Abun da baka sani ba shi ne, ina da cikakkiyar shaidar mummunar ɗabi'ar
da ka ke aikatawa, ta lalata rayuwar matasa da sunan sama musu aikin yi.
Sannan ni na saka aka kama ɗanka Jafar, a Mexico in da ya
gudu neman mafaka bayan yayi kisan kai, haka zalika yanzu ma da saka hannuna a
mayar da shi amurka.
Yanzu haka miyagun ƙwayoyi da hodar iblis ɗin da aka loda
maka a jirgin ruwa, za ayi safararsu ta ruwa, za a kama su a gaɓar tekun italy.
Kamar yadda nayi maka aike na farko, ina tare da Simon kuma shi ya bani wannan
saƙon naka".
Jiki na rawa ya buɗe videon, shi ne a cikin videon, yana ta
kokowa da Nura guduma, wasu irin ƙarti majiya ƙarfin gaske, suka riƙe Nura,
yana kururuwa yana ƙoƙarin ƙwatar kansa, amma abu ya gagara, kuma ba iya fuskar
Indabo ba ce a videon, har da wasu daga cikin manya a ƙasa.
Da ƙyar Indabo ya iya ɗaga ido, ya kalli Abdul, ya haɗiye
wani irin abu mai yaji da ɗaci, ya kasa magana. Abdul kuma ya ƙure shi da ido,
yana jiran ya ji mai indabon zai ce.
Mahaifiyar Abdul tayi shiru, suka yi tsuru-tsuru.
"Na tabattar ba sharri aka yi maka ba, kai ne a jikin
videon nan, naga baka buɗe sauran audios ɗin ba, amma ya tabattar da cewa,
mutum goma ne suke da videon, muddin ka cigaba da takura musu, sai sun sake shi
a duniya, kuma sai an ɗauki mummunan mataki a kanka, babban takaicina me zan
cewa rahama, yarinyar da nake nema ta yafe mini, ashe akwai babban aiki a
gabana jawur, kai kayi silar mutuwar ɗan uwanta, tayaya mahaifiyarta zata yafe
mini ta bari na cigaba da rayuwa da ita?"
"Abdul ka cigaba da rayuwa da wa? Tona wa mahaifinka
asiri zaka yi? Satin bikinka ya kama kana nufin zaka yi aure kuma ka ajiye
karuwa?"
"Rahama ba karuwa ba ce, aurenta nake yi, kuma yau zan
tattara na bar garin nan da ita, da wannan abun kunyar da ka aikata"
Indabo ya ce "Aurenta ka ke yi kamar yaya?"
SOME MONTHS BACK.
Abdul ne ya shigo, ya tarar da rahama a rakuɓe, a jikin
gado, idanu duk sun kumbura saboda kuka.
"Wai ba zaki raba kanki da wannan kukan ba? Aikuwa kina
tare da wahala, dan kuwa yanzu ki ka fara, tashi ga abinci"
Ta ɗago ta kalleshi ta ce "Ba na ci, ka ƙyale ni na
mutu, ai tun farko cewa kayi zaka kashe ni, menene na ajiye ni kana tozarta
rayuwata, saboda kawai ina 'yar talaka? Talauci ne ya saka na fita aikatau, da
burin yin karatu, mahaifiyata ba zata iya ɗaukar ɗawainiyata ba, ban da haka
killace ni zata yi a tare da ita, ba zata bari ma ka ganni ba balle ka keta
mini haddi" ta yi kneel down ta ce "Dan girman Allah ka kasheni na
huta"
"Ke naji, kin cika mini kunne da koke-koke, zan mayar
da ke"
Ta girgiza kai ta ce "Ko ka mayar da ni, ba zan yi
daraja ba, abar ƙyama zan zama, kawai ka kashe ni, ka kaiwa mama gawata dan
Allah"
Abdul ya zauna a kusa da ita ya ce "Ya isa haka kukan,
ki ci abinci zan san abun yi" kwanaki biyu, tana jiran ya kashe ta, ko ya
mayar da ita amma shiru, gashi tun da tayi ɓarin nan, da ya zo mata zata fara
kuka kamar ranta zai fita, tana yi masa magiyar ya daina wulaƙanta mata rayuwa.
Cikin marairaicewa ta same shi, ta durƙusa a ƙasa ta ce
"Ka ce zaka mayar da ni gida, kuma baka mayar da ni ba"
"Rahama ba zan iya mayar da ke ba, zan ta tunaninki ne,
kawai na ji ina damuwa da ke, ki haƙura kawai" cikin kuka ta ƙare masa
zagi, amma ko a jikinsa.
Washegari ya ɗauki Salim, ko saifu bai gaya wa ba, suka tafi
gidan su ramma.
Mahaifiyar ramma na ganin Abdul, ta tashi cikin ƙarfin hali
ta ce "Ina ka kai mini 'ya ta? Ka dawo mini da 'ya ta"
Abdul ya ce "Mama masalaha na zo muyi, ɓarna an riga an
yi ta, dan Allah ki yi haƙuri ki bar mini ramma, ki bani aurenta" Sai da
Salim ya kalle shi, dan bai san abun da zai ce kenan ba.
"Allah ya tsare, cuta ka riga ka gama cutar da mu, kai
da Allah, amma ka dawo mini da 'ya ta"
Ya girgiza kai ya ce "Kar mu yi haka, a rufa wa juna
asiri, kun ɗauki aure da muhimmanci sosai, ta ce babu lallai tayi daraja,
ƙyamarta za a din ga yi, dan haka ki yi haƙuri dan Allah, ki aura mini
ita"
"Wallahi ba zan taɓa aura maka ita ba, gara ayi ta
tsangwamarmu, zan riƙa a bata na kula da ita, kuma zan cigaba da nema mata
hakkinta, har zuwa ƙarshen numfashina"
Ya miƙe ya ce "Shikenan, tana gaishe ki, ki kwantar da
hankalinki, tana cikin ƙoshin lafiya" ya ajiye mata kuɗi suka fice, ta
bishi tana ya zo ya karɓi kuɗinsa amma yayi mata banza suka tafi.
Salim ya din ga yi masa masifa a mota "Amma dai baka da
hankali ko? Ka yi wa yarinyar fyaɗe, mu zo gaban babarta mu yi rashin mutunci,
kuma mu dawo ka ce zaka aureta, wai ma ka gaya wa su daddy ne?"
Abdul ya girgiza kai ya ce "A'a, yarinyar ce take bani
tausayi irin sosai ɗin nan, virginity is very important to woman's, i took it
away just like that, she's very young and innocent, ina jin babu daɗi, na san
yadda zan ɓullowa lamarin"
Tare da Salim suka cigaba da shige da fice, suka samo wani
wan baban ramma, Abdul ya danƙara masa kuɗi, babar ramma bata sani ba, aka ɗaura
musu aure, sai bayan an ɗaura ya je ya din ga yi wa babar ramma masifa, wai
Allah zai rufa wa ramma asiri, amma tana ƙoƙarin tonewa, da ta samu ma mai kuɗi
da kyau kamar wannan ya saurari yar ta ta, a wurin ɗan birni kamar Abdul ai
ramma a bar ƙyama ce.
Cikin kuka ta ce "Wallahi balarabe ba zai yiwu ba, ban
san wani zancen aurar da ramma ba, lokacin da nake wahala ta da ya ta da me ka
taimake ni, ina har gonar su ta gado ka cinye".
"Oho miki, koma menene rashin iya takaucinki, da son
abun duniya ya sanya ki ka kaita aikatau" da kansa ya shiga ya kwaso wa
Abdul kayan ramma, ya sake ba wa babar ramma kuɗi, ya ɗauki kaya suka tafi.
Suna tafe Salim ya ce "Ranar da asirinka ya tonu ban
sanka ba wallahi, ko kuma ka gama abun da zaka yi, salin alin ka sakar musu
'ya"
Abdul ya ce "Ban aureta dan na saketa ba, sai dai ayi
wadda za ayi"
Ya je ya samu ramma, ya kai mata kayanta, da goro da alawa
ya ce "Gashi nan, hankalinki ya kwanta an ɗaura mana aure yau" cikin
mamaki ta kalleshi ta ce "Aure kuma kamar yaya?"
"Ba damuwarki kenan ba? Ke ba zaki auru ba? To an ɗaura
yau, yayan babanki wai malam bala, shi ne ya ɗaura mana aure"
"Wane irin aure ne babu istibura'i? Cewa nayi ina sonka
ne ma?"
Ya ce "Meye istibura'i?"
"Sai nayi jini uku a addinance, dan tsaftace mahaifata
kan ka aureni, tun da zina kayi da ni, kuma ni bana sonka".
Abdul ya kalleta ya ce "Allah ya nuna mana wata ukun,
kuma ni ina sonki ai, Shikenan an wuce wurin".
Ramma tayi kuka a kan wannan wulaƙanci da Abdul yayi mata,
da nuna mata tsantsar isa da gadara, ta fara yi masa misbehaving ta daina
tsoronsa, amma ko a jikinsa, sai dai zamansu tare ta gane yana da wasu ɗabi'u
na tausayi da sauƙin kai, rashin tarbiyya da ilimin addini ne kawai yake ɗawainiya
da shi, bai sake nemanta ba, sai da ta cika watanni uku, kamar yadda ta buƙata.
Idan tana yi masa masifar ba dan Allah ya aure ta ba, ya kan
ce mata "Ba dan ina sonki ba, babu dalilin da zai sanya na zauna da ke
watanni uku ina kallonki, kina gindaya mini sharuɗa ina ƙyale ki".
****
Mahaifiyar Abdul ta ce "Aure ka yi bamu sani ba Abdul,
rashin muhimmancin namu har ya kai haka?"
Ya kalleta ya ce "Ko zan mutu ba zaku yadda ku aura
mini rahama ba, zaku yi iƙirarin yar talakawa ce, ba tare da la'akari da ɓarnar
da na akata mata ba. Kuma sakawa zaka yi a kasheta, sannan mutumin nan da ka
saka aka kashe, ba ruwana babu saka hannuna a ciki. Zan ɗauki matata mu bar
garin nan, dan Allah kar ka neme ni, takara kuma ka bawa wani, ba zan iya
ba" ya ɗauke wayarsa, mahaifiyarsa ta bishi tana ƙwala masa kira, amma
yayi waje.
***
Viper ne ya shigo ɗakin da Nabila take, tana zaune ya shigo
da waya a kunnensa ya ce "Eh na je wani wuri ne, ɗan mama ya dawo gidan
nan ne, ya gudu na neme shi na rasa, ya kuma kashe wayarsa"
Walid ya ce "A'a bai dawo ba, ko laifi yayi maka ka ce
zaka hukunta shi?"
Yayi murmushi ya ce "Laifi yayi, kuma duk in da ya
shiga zan nemo shi, zamu gauraya da ni da shi"ya katse wayar ya ƙarasa
gefen Nabilaya zauna.
"Vi"
"Mmm"
"Wai dan Allah ina ne nan? Ina son na tafi gida
ne"
"Ai ba zaki koma gida ba, kin zo kenan"
Dariya tayi, dan ta zata da wasa yake yi.
"Daga fitarka ka sha sigari ko?"
"Eh"
Nabila ta ce "Au eh, baka jin kunya wai ka amsa ka
tsaye, sai ƙauri ka ke yi, ba na son ƙaurin abar nan ko kaɗan wallahi"
Ya tsura mata ido, ya girgiza kai ya ce "You can't be
her"
"Who?"
Ya lanƙwasa ƙafarsa ɗaya a kan gadon ya ce "Jauhar, ba
ta taɓa nuna warin sigarina da wiwi yana damunta ba, sai dai ta ce ; Master kar
a sha da yawa, dan Allah a sha kaɗan, idan nayi shaye-shaye na dawo, ta bani
ruwan wanka, ta bani wankakkun kaya, ta fesa mini turare, sai daga baya na
fahimci, warin wiwi ne ba ta so, amma bata taɓa yi mini complain ba. Yanzu bana
iya shan komai, na yadda ƙwaƙwalwata da lafiyata suna da amfani, ko dan ganin
bayan wanda suka cutar da mu. Ke kuwa masifaffiya ce, always angry, ki ka gaya
mini ina ƙaurin taba"
"Sai na zama irin ta zaka so ni? Gaskiya ba zan iya
shiru ba, ni kawai ka daina gaba ɗaya"
Viper ya ce "Ai babu wannan maganar tsakanina da ke, na
gaya miki ki daina wahalar da kanki" ya yi maganar yana miƙa mata wayarta.
Karɓa ta yi tana hararsa ta ga sunan sumayya ta ce "Ba
zan ɗaga ba"
"No, ki ɗaga baki san me za ta ce miki ba"
Ta ɗaga ta saka a kunnenta ta ce "Ina jinki"
"Nabila kina ina ne?"
"Menene?"
"Kawai malama kina ina?"
"Ki gaya mini meyafaru? Nayi nisa ne"
Sumayya ta ce "Mahaifin Viper, ya zo gidan radionmu, ya
ce yana son zai yi magana da ke, na ce masa zan haɗaku, zan yi miki
magana"
Nabila ta ce "Are you serious dan Allah da gaske?"
"Wallahi da gaske nake yi miki"
"Shikenan, in sha Allah zuwa gobe in Allah ya kaimu,
zan zo zamu haɗu, kin karɓi lambarsa?"
"Eh na karɓa"
"Shikenan in sha Allah zan zo" ta katse wayar, ta
ga wani irin kallo da yake yi mata.
"Vi snake, menene? Abunka ne ya zo yana nemana,
wataƙila.....
"Silent. Kar ki kuskura ki fara, ke gaba ɗaya baki da
lissafi, idan wani trap ɗin ne fa?" Yayi maganar cikin hargowa.
"Bari na zama kamar jauhar, ba zan biye maka ba ai
yanzu, hukuma sai da rarrashi, hadari malafar duniya. Tsakanin ɗa da mahaifi
sai Allah. Nifa duk da ina da labarin abun da babanna yayi wa mahaifiyata, fata
nake yi na ganshi, haka zaka cigaba da rayuwa ba dangi, kaikaɗai sai su oga
Walid, sai kuma Ni" ta yi maganar tana murmushi.
"Ka bari mu haɗu da Abbu dan Allah, na san maybe
nemanka yake yi, so yake ya ganka, haba sweetheart, namijin duniya, kar ka saka
muyi babu, kai ba uba nima haka, kayi haƙuri dan Allah, ka manta da komai My
Vi. Magana fa nake yi an yi mini shiru, talk mana, ko sarautar ce ta motsa?
Master magana nake" tsigar jikinsa ta mimmiƙe ya juya yana kallonta.
"Ban taɓa kallon wani abu na ji ina son shi ba, sai kai
Vi, duk a dalilinka na rasa ajina da jin kai na 'ya mace. Gashi ka yi ta
hantarata, baka tausayina ko kaɗan.
Ɗan nuna mini hoton 'yar madara mana, ko sau ɗaya ne"
"Hotonta mai tsada ne, yarinya mai haƙuri da aji"
"Ni kuma masifaffiya mara aji, daga nan kuma sai
me?" Ya fuskanci kawai kunna shi take yi.
Ya ajiye mata wata leda, ya ce "Gashi nan, abinci ne,
za a kawo miki kaya"
"A'a nifa ban gane ba, gida fa?"
Ya miƙe tsaye ya ce "Ba sa buƙatar ki, na fi su buƙatar
ki a yanzu, muddin wani abu ya sameki, ni aka jiƙawa aiki"
Nabila ta ce "Ban gane ba, garkuwa zaka yi da ni?"
"Na ma yi" yayi maganar tare da ficewa.
****
Hanklin can gidan su Nabila ya tashi, bayan an shafe kwana
na biyu, ba a san in da take ba, Abba ya maze kamar ko a jikinsa, amma
hankalinsa a matuƙar tashe yake. Nasir ma ya din ga up and down, haka ma
sumayya dan sai da ta gaya wa Kankarofi an nemi Nabila an rasa.
Ta gaya wa Nasir cewa, ranar da ta ɓata sun yi waya, bayan
la'asar kuma da alama tana cikin ƙoshin lafiya.
Nasir ya ce "Abu ne mawuyaci ace barin gidan nan tayi,
wataƙila mutanen da take addabawa ne suka sace ta"
Aka din ga kiran wayarta, amma a kashe.
Kwana na uku, Nasir ya kira wayarta, ta shiga, amma ba a ɗagawa.
Dan haka ya saka layin a tracker, ya fara tracking in da
wayar take, sai dai ga mamakinsa, wayar tana cikin garin kano.
****
Abdul tamkar zai haukace, duk wani lungu da saƙo na gidan ya
duba, amma bai ga ramma ba, ya dudduba ko ina da ina, amma bai ganta ba. Ya
kira wayarta amma a kashe.
Taka jikinsa ya hau tsuma, ya tabattar da cewa Indabo ne ya
saka aka ɗauke ta, jikinsa na rawa ya ɗaukko mota ya fito, tare da sakawa a
ransa komai zai faru sai dai ya faru, amma sai indabo ya fito masa da matarsa,
ko kuma shi da kansa ya tona musu asiri kowa ya huta.
****
Nasir yayi mamakin surƙuƙin wurin da yake indicating in da
wayar Nabila take, da shi da abokan aikinsa, ƙarshe ajiye motar suka yi, suka
din ga shiga wurin da ƙafa, suna cigaba da dubawa.
A tsaye suka tarar da shi ya juya baya, hayaƙi yana tashi.
Nasir ya ce "Malam waye kai?"
Sai da ya ja sakanni, sannan ya juyo a hankali, hannunsa ɗaya
da wayar Nabila, ɗaya kuma riƙe da sigarinsa, gaban rigarsa ɗauke da sunansa
Viper da hoton maciji a jiki.
"Al'amin Viper, ko ka ce mai zamani"
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA
Cikin matsanancin mamaki, Nasir ya cigaba da takawa zuwa
gaban Viper, ya ɗan bayar da tazara tsakaninsa da shi.
Nasir ya ce "Dama kai ne Vipern?"
Ya ɗan kaɗa kai ya ce "Ni ne Viper, abun mamaki ko? Haɗuwar
mu biyu, amma baka san ni ne ba, haryanzu ina mamakin wane irin aiki jami'an
tsaron ƙasarmu su ke yi, kodayeke ƙulafucin cin hanci ne yake rufewa galibinku
idanu, ku danne masu gaskiyar cikinku, ko ku sauya musu ra'ayi domin neman
mafitarku kawai"
Nasir ya ƙare masa kallo ya ce "Ina 'yar uwata take?
Ina Nabila?"
Viper ya jujjya wayar Nabila sannan ya ɗagawa Nasir ita ya
ce "Baka buƙatar yi mini wannan tambayar, tun da ka samu wayarta a
hannuna"
"Tana ina?"
"Tana wurina ƙarƙashin kulawata, na fiku buƙatar ta,
ina buƙatar ganinta a raye domin nayi surviving, dan haka za ta cigaba da zama
a ƙarƙashin kulawata, har zuwa lokacin da ya dace"
A fusace Nasir ya ce "A matsayinka nawa, am arresting
you, ba zan bar wurin nan ba, sai na kama ka"
Viper ya kalle su gaba ɗaya 'yan sandan su biyar ɗin ya ce
"Bisa wace dokar? Ko bisa umarnin indabo da ka karɓar wa kuɗi, zaka kama
ni?. Viper ya zaro takarda a aljihunsa ya ce "Na sami wannan takardar yau
da safe, kai ma kuma ka je ka bincika, kotu ta hana hukumar 'yan sanda da
kowace hukuma kama ni, har sai an kammala bincike, dan haka ba ka da wannan
ikon, hannunka bashi da ƙwarin ɗaukar ƙarfen cikin wannan wutar, ba zaka jure
ba, muddin ka taɓa kuwa, zaka yi ƙunar da zata yi dalilin rabaka da
hannun"
Nasir ya fizgi takardar hannun Viper, jikinsa na rawa, ya
hau karantawa, tabbas Viper da gaske yake, kotu ta bayar da umarnin hana kama
shi.
Nasir ya riƙe takardar, ya zaro bindiga a jikinsa, ya ce
"Idan kuma na kashe ka a wurin nan fa, waye ya sani?"
Viper ya nuna masa mutanen bayansa ya ce "Ku 'yan sanda
ai ba dukkanku ne masu amana ba, wane tabbaci ka ke da shi cewa mutane huɗun
nan na bayanka, ba zasu tona maka asiri cewa ka kashe ni ba? Beside kana sakin
bullet ɗin bindigar ka, kaima za a kashe ka, tunaninka a banza na zo nan na
jiraka? na san kana tracking ɗin wayar, shiyasa na jira ka zo ka iskeni"
Ya ciro ID card ya ɗaga wa Nasir ya ce "I am an NIA
officer, and also a former thug, ni ba da bindiga zan yi maka illa ba, ƙarfe
zan saka maka, a ɗan daba na zan yi maka illa, ba jami'i ba.
Sauke bindiga Nasir yayi, ya ce "NIA officer how?"
"Kamar yadda ka gani. Maganar Nabila kuma, bari na gaya
maka wani abu, na san kana sonta amma ta haramta a gareka, muddin ina ganin
fuskar matata a ta Nabila, aurenta ya haramta a gareka, ba kai ba kowa ma.
Nabila tana wurina, kuma zan mayar da ita wurin mahaifinta, wannan shi ne
tukuicin da zan yi mata, bisa ga jajircewarta da ceto rayuwata"
"Mahaifinta like how? Me ka ke nufi da hakan?"
"Hoton da na bata, ta kai muku ku yi mata bayani, amsar
da ku ka bata, ta sanya na yanke shawarar yin abun da ya dace" Nasir zai
kuma magana, wani ya ƙaraso wurin da babur, sanye da riga mai tambarin NIA
(National Intelligence Agency) Viper ya hau babur ɗin, suka bar wurin.
Dafe kai Nasir yayi, yana tunanin wannan wane irin
rikitaccen al'amari ne, tayaya riƙaƙƙen daba ya zama jami'in cibiyar samar da
bayanan sirri da leƙen asiri? Ya aka yi kuma ya san mahaifin Nabila, anya
wannan duk ba wata shiryayyiya ba ce ba?.
"DSP yakamata fa mu bar wurin nan, ni gaba ɗaya ban
yadda da mutumin nan ba, i don't think we are safe here" bai ce uffan ba,
ya yinƙura ya tashi suka bar wurin.
****
Gida Nasir ya nufa, a wahale, cike da damuwa da tashin
hankali, yama rasa ta ina yakamata ya fara, meyakamata yayi.
Ya za ayi hukuma kamar wannan, ta bar jami'inta yana tafka
rashin mutunci son ransa. Yayi shiru yana tunanin yadda wasu abubuwan suka din
ga faruwa, ya aikata laifi, amma a bi a goge duk wani trace da zai nuna shi
yayi, ko kuma a gano shi.
Babban abun da ya ƙara baƙanta masa rai, shi ne umarnin
kotu, na hana kama Viper, ana tuhumar mutum da laifi, har na kisan kai, amma
ace kotu tayi umarnin dakatar da kama shi a kan me?.
A ƙofar gidan su, ya tarar da manya-manyan motoci har da na
'yan sanda, cikin sauri ya yi parking, ya shiga cikin gidan domin ya ga mai
yake faruwa, baba magajiya ta sanar masa major ne yayi baƙi.
Hankalinsa bai kwanta ba, ya nufi ɗakin Abba, dan tabattar
da abun da yake faruwa.
Ya tarar da Alhaji mu'zzam kankarofi, tare da wasu jami'an
tsaro, da kuma Abba a falonsa.
Abba ya ce "Yauwwa, ƙaraso Nasir" ya ƙarasa ya
shiga, ya zauna suka gaisa.
Abba ya ce "Ka gane wannan ai ko?" Yayi maganar
yana nuna masa Alhaji mu'azzam.
Nasir ya ce "Eh ya je asibiti duba Arfat"
"Ashe babban mutum ne ni ban sani ba, ya ce Nabila tana
ƙarƙashin kulawar hukuma, saboda rayuwarta na cikin hatsari, wanda take karewa
ya rasu, ba a san me zai iya faruwa da ita ba"
Kamar shashasha Nasir ya tsaya yana bin su da kallo, shi
kuma meya kawo shi cikin wannan lamarin? Tare da Viper suke harƙalla kenan?
Amma da kamar wuya ace kamilin mutum da ya san doka, kamar sa ace yana hulɗa da
mutumin banza kamar Viper.
"Mu'azzam wada kankarofi, mai bawa shugaban ƙasa
shawara na musamman a kan harkar tsaro" ya faɗa yana kallon Nasir da ya ga
yana yi masa wani irin kallo mai cike da tuhuma".
Major ya ce "Haryanzu ina mamaki, da ka ce kai ne dai
wada kankarofi, ni na zata suna ne kawai ya zo ɗaya"
Alhaji mu'azzam ya ce "A'a, ni ne dai, a rayuwata ina
son 'yanci da walwala, dan haka ban fiye son takura ba, ko yawo da gayyar
jami'an tsaro ba duk in da zani.
Na san ka ɗauki zafi a kan abubuwan da Nabila take aikatawa,
na kasada, amma ni burgeni tayi, kuma daga ranar farko da na ganta a law firm ɗin
su, nake bibiyarta, nake taimakonta, akwai ire-iren ta, brave citizens, da cin
hanci da ƙarfin iko, ya sanya ake tauye su su kasa kataɓus, a kanta na ce bari
mu jarraba ayi supporting ɗin ta, mu ga wace irin baiwa da gudunmawa zata bai
wa ƙasa, and Alhamdilillah ko iya haka tayi rawar gani "
Major ya jinjina kai ya ce "Haka ne sir, amma abun da
aka yi ya isa haka, ina son a dawo mini da 'ya ta, abun da tayi Allah ya
amfana, ni aikin ma a haƙura da shi, tayi aure. Ba zan lamunci zuba mata ido,
tana kare rayuwar ɗan ta'adda ba. Aikinta na neman kawo mini rabuwar kai a
cikin iyali. Ga ɗan uwanta yana fafutukar neman mai laifi, ita kuma tana kare
shi ba. Sunanta ya ɓaci a idon duniya ba, ina buƙatar ta dawo a haƙura
kawai"
Alhaji mu'azzam ya ce "Am sorry to say sir, Nabila ta ɗaukko
aikin da kammala shi ne kawai mafita, da ceto dubban al'umma, za ta aikata abun
da da yawa sun yi yunkurin yi, amma ba su yi nasara ba. Bani da ikon dawo maka
da ita, umarni ne na musamman kareta da lafiyar ta"
Abba ya numfasa ya ce "Na ji, amma Allah ya amfana haka
nan, a dawo mini da 'ya ta, ban ga dalilin da zai sanya, a ɗaukar mini yarinya
ba da iznina ba a ɗaga mini hakali har haka ba"
Alhaji mu'azzam ya ce "Na san an yi maka laifi, shiyasa
muka zo har gida baka haƙuri, kuma ta ɗan samu mini attack ne mun kaita
Asibiti, daga baya kuma muka lura da matsanancin haɗarin da rayuwarta take
ciki, ka ɗan bamu lokaci"
Nasir kamar yayi maganar Viper, amma yayi shiru, kenan da
gaske Viper yake shi jami'in sirri ne, ko kuma wata kitumurmurar ce?.
Abba suka yi ta jayya da Alhaji mu'zzam, haka ya haƙura, sai
dai bai ji zai yi shiru da maganar nan ba, dole a dawo masa da 'yar sa.
Bayan tafiyar su, mutanen gidan suja din ga tambayar
meyafaru, Abba ya gaya musu ba wani abu, a kan Nabila ne, tana wurin hukuma
saboda tsaron lafiyarta.
Masu jiran su ji baƙin labari, duk ba haka suka so ba, baba
magajiya kuwa addu'a ta cigaba da yi, tare da fatan Allah ya sa Nabila na cikin
ƙoshin lafiya.
Sumayya ce ta zo gidan, cikin matsananciyar damuwa, ta tarar
da Abba yana shirin fita, suka gaisa ya ce "Kin biyo sahu ko
sumayya?"
"Eh Abba, hankalina ya kasa kwanciya, ni har a radio na
sanar a tayamu addu'a bamu ganta ba, na kasa sukuni gaba ɗaya"
"Ki kwantar da hankalinki, yanzun nan baƙi suka tafi,
wai tana wurin hukuma saboda tsaron lafiyarta, wai wani saurayinta da ya zo
dubata kwanaki, wai mai bawa shugaban ƙasa shawara a kan harkar tsaro".
Take Sumayya ta gane waye, ta ce "To Abba ya tabattar
maka tana lafiya?"
"Eh, ya ce suna bata kariya ne, ashe ba saurayin ta
bane kawai, ni dai kam na gaji da wannan aikin, ajiye shi zata yi ta fitar da
miji, na yi mata aure, ko ni na fitar mata"
Sumayya ta ce "A'a Abba ka yi haƙuri, aikin yana da
muhimmanci, zan cigaha da kiranta, Allah ya sa na sameta"
"Allah ya sa, dan bana tunanin zasu bari ta ɗaga
waya".
***
Ko da Abdul yayi parking a harabar gidan su, bai ko tsaya
rufe motar ba, ya shiga cikin gidan kamar yayi fuka-fukai ya tashi,
"Mummy" ya din ga ƙwala wa mahaifiyarsa kira.
"Menene wai ka ke kirana haka?"
"Ina Daddy?"
Ta kalleshi rai a ɓace ta ce "Ya tafi ya gurfana a
gaban kwamitin da aka naɗa, na binciken kuɗin da kake neman ka janyo masifa a
kansu"
"Mummy ba wannan ba, dan girman Allah ki gaya mini idan
shi ne ya sa aka je aka ɗauke ramma"
Sheƙeƙe ta kalle shi ta ce "Wacece hakan?"
"Matata mana"
"Wai Abdul baka jin kunyar faɗar wannan maganganun ne?
Har wani tutiya kake yi dan ka auri karuwa? Wannan aure da zaka yi alfahari da
shi ne, kana wani matarka?"
Abdul ya ce "Mummy, meyasa a ƙasashen ƙetare, ko wasu
sassan na duniya, idan suka lalata yarinya, ko su gama watsewar su, suke dawowa
su aure su, mu kuma sai mu tafka ɓarna mu koma mu ce zamu yi wa Allah wayo, na
san ba zan taɓa auren macen kirki ba, dole ragowar wani zan aura, gara wannan
ragowata ce koma menene ni na janyo"
"Abdul, ka tsaya a gabana ka ke gaya mini wannan
maganganun banzan? Ina uwarka"
"Ni dai dan girman Allah idan ku kuka ɗauke mini mata,
ko dawo mini da ita, wallahi ba zan iya rayuwa mai daɗi babu rahama ba"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ka je kayi duk
abin da zaka yi Abdul"
"Mummy dan Allah Daddy ne ya saka aka ɗauke mini
ita"
"Ban sani ba, ka bishi Abujan ka tambaye shi" ta
juya ta koma ɗakinta, a matuƙar fusace.
****
Wata irin runguma, Ramma ta yi wa mahaifiyarta, suka fashe
da kuka baki ɗaya.
"Ramma, kina lafiya bai cutar mini da ke ba?"
Ramma ta jinjina mata kai tana kuka, suka ƙara ƙanƙame juna.
Barrister Habib ya ce "Kukan ya isa haka, a gode wa
Allah, dan Allah ku yi wa Nabila Addu'a, da ita da malam garba, shi an bishi an
kashe a prison ɗin, amma ita Nabila an kauwwameta, ana tsaron lafiyarta"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, sai da mutumin nan
ya rasa ransa?" Maman ramma tayi maganar cikin tashin hankali.
Jiki a sanyaye ramma ta ce "Yanzu malam garba ya rasu?
Wayyo Allana, Allah ya sa mutuwa hutu ce a gare shi"
Suka Amsa da Amin.
Mama ta kalli barrister Habib ta ce "Na gode sosai da
sosai, Allah ya saka muku da mafificin alkhairi, idan ka samu ganinta, ka ce
mata na gode, na gode Allah ya saka mata da mafificin alkhairi, ya jiƙan
magabatanta, yadda ta share mana hawaye, ka da Allah ya bar nata su zuba"
Ya ce "Amin, amma ni kuma fa"
"Kai ma haka tare da Alhajin da yake ta ɗawainiya da
ni"
Barrister Habib ya ce "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, bari
zamu cigaba da magana da jami'an tsaron, za a kama ainihin mai laifin, za a
hukunta shi da yardar Allah, duk wata shaida muna da ita a kansa" suka din
ga yi masa godiya, ya wuce ya fita.
Suka ƙara rungume juna, mama ta ce "Lokacin da yarinyar
nan take tabattar mini da zata dawo mini da ke, ban zaci da gaske take ba, da
zan ganta har ƙasa zan durƙusa na yi mata godiya"
Ramma cikin kuka ta ce "Mama ina Sani?"
"Mutumin nan da ya saka aka ɗaukkomu, ya kai shi
makarantar kwana, ta kuɗi"
"Mama wai waye shi? Meyasa ya ɗaukko ki?"
"Yana da nasa dalilin, amma ban sani ba"
*MONTHS BACK*
Nabila sai sauri take yi, takalminta mai tsini yana ƙara,
tana neman network, domin yin magana da sumayya, har ta dangana da rukunin
ofisoshin da ba kowa a wurin.
"Hello, ke Sumayya T ladan, ba network ne, yanzu na
samu wuri, ya ake ciki munafukan al'umma"
Sumayya ta ce "Nabila ki daina ce mana munafukai, aiki
muke fa"
"Ba wani aiki, tsegumi wanda aka saka ku, da wanda ba a
saka ku ba, duk ku ke samowa ku kwatsawa al'unma komai daɗinsa da ɗacinsa"
"Zan ɗura miki ashariya wallahi"
Nabila ta ce "Sorry T ladan, masoyiyyar Nabila, bani
labari"
Da sauri Ramma ta ajiye littafin hannunta, jin an ambaci
sumayya T ladan, da sauri ta ƙarasa gaban window tana zura kai.
"Baiwar Allah, baiwar Allah kin ganni ta nan baiwar
Allah" Nabila ta hau waige-waige, taga ta ina ake magana.
"Baiwar Allah wadda take waya, dan ki ƙaraso wurin
tagar nan"
Cikin dakewa Nabila ta ƙarasa, ta ragar jikin window Nabila
ta ga ramma, ta ce "Lafiya kuwa?"
Ramma ta ce "Ki taimake ni, kamar yadda Allah ya
taimake ki dan Allah, na ji kina faɗar sunan yar jaridar nan, mai aiki a
radio"
Nabila ta ce "Eh ya aka yi, kin santa ne?"
"Ban santa ba, taimakona zaki yi, dan Allah ku sanar da
jami'an tsaro idan kuna da dama, wani ne yayi mini fyaɗe, ya sace ni ya aure
ni, ba da sanin mahaifiyata ba, ban san a wane halin take ciki ba"
"Yayi miki fyaɗe ya sace ki? Garin yaya?"
Nan ramma ta gaya mata komai, Nabila ta ce "Innalillahi
wa Innalillahi raji'un, kin san irin neman da muke yi miki kuwa? Ni nake
shari'a a kan case ɗin ki, har ya fita yana yawo da ke, amma baki yi masa ihu
ba, a ƙwace ki?"
"Tayaya zan yi masa ihu yana aurena? Kuma idan nayi ihu
tamkar na ƙara tonawa kaina asiri ne, wanda ya sanni, da wanda bai sanni ba,
sai kowa ya san abin da ya same ni, shi ne mai asibitin nan, shi yayi mini fyaɗe,
sai an bi a hankali idan ba haka ba, ba zai taɓa rabuwa da ni ba, dan Allah ki
taimaka mini dan Allah, ina son na je na ga mahaifiyata"
Nabila ta ce "Tsaya, yana baki ci da sha, ko yana
dukanki da cin zarafi?"
Ramma ta ce "A'a, baya yi"
"Yauwwa Alhamdilillah, a ina yake ɓoye ki?"
"Ban san ina ne ba"ta yi maganar tana kuka.
Samo abu na rubuta miki lambata, ki faki idonsa, ko saƙo ki
turo mini, sai ki goge, nayi miki alƙawarin zaki kuɓuta in sha Allah"
Nabila ta bata lambarta, ta nufo hanyar tafiya, tana yi wa
Allah godiya, yadda kayanta suka tsinke a gindin kaba, saboda tsananin addu'a
da take yi.
Daga nan ta koma ƙofar ɗakin Viper, ɗan mama ya hanata
shiga.
Kamar yadda suka tsara, Ramma ta yi mata message, Abdul na
wanka, Nabila ta bawa Viper, ta ce masa wata lamba take so, a duba mata
location ɗin ta.
Yana dubawa ya ce "Wannan ai lambar ɗan gidan indabo
ce"
"Waye Indabo?"
"Mutumin da ya kashe mini jauhar"
Nabila ta rufe baki cikin tsananin mamaki.
"A ina ki ka sameta?"
Ta ce "Kar ka damu, manta kawai" sai da kanta ya
sara, ta ina zata fara yi masa wannan mugun jawabin mara daɗin ji, indabo ya
kashe Nura guduma, kuma yanzu ɗansa ya saceta, bayan yayi mata fyaɗe.
Wurin barrister Habib ta je, ta sanar masa da abin da ya
faru, sun daɗe suna mamaki, barrister Habib ya ce "Wannan lamarin ba zamu
miƙa shi kai tsaye ga 'yan sanda ba, dan bamu san a hannun wa zamu danƙa ba,
yana buƙatar sirri sosai da sosai, kar wani yayi mana katsalandan ya ɓata mana
aiki".
Bayan Nabila ta gano Alhaji mu'azzam, shi ya sama musu wanda
suka cigaba da tracking in da ramma take, ta hanyar bibiyar lambar Abdul, har
zuwa lokacin da aka yi nasarar gano in da take, jami'an tsaron Civil defense,
suka je suka ɗaukkota
****
Nabila na tsaye na leƙen window, ta kasa gane a ina take,
wurin shi ba jeji ba, shi dai gashi nan.
Ta koma ta nemi wuri ta zauna, Viper ya shigo da sallama, ta
amsa masa, ya je gabanta ya tsaya, ya ajiye mata ledar abinci ya ce "Gashi
nan ki ci ki sha magani"
"Vi"
"Mmm"
"Dan Allah ka mayar da ni gida, ina da abubuwan yi da
yawa, yakamata na je ta'aziyyar malam garba, na rarrashi iyalinsa na basu
haƙuri, bisa ga gazawata, dama ni ban taɓa shari'a na samu nasara ba, kullum faɗuwa
nake yi, bani da sa'a" ta ƙarasa maganar cikin damuwa.
"Dama yaushe masifaffen mutum zai yi sa'a?"
"Na ji, amma ka mayar da ni gida, ni ban san me ma zan
cewa yan gidanmu ba, kwana biyu bana gida, dama ana yi mini iƙirarin bin maza,
ban san me zan ce musu ba"
Viper ya ce "Na gaya miki, na fisu buƙatar ki, zaki
cigaba da zama a nan, har sai kin kammala aikina"
"Wai na cigaba da zama kamar yaya? Sai in din ga keɓewa
daga ni sai kai, ka san dai bai dace ba, idan mace da namiji suka haɗu na
ukunsu shaiɗan ne, ka san bai kamata ba"
Ya sunkuyo dai-dai fuskarta, ya tsura nata jajayen idanunsa,
da suke razanata wasu lokutan, zaro harshen sa yayi waje, wanda sai da ta
tsorata, saboda ganin tsayin harshensa. Ya ɗan ja numfashi ya ce "Lokacin
da ki ke sintiri a gidan da nake, kina neman suna, baki yi tunanin na ukunmu
shaiɗan bane sai yanzu? Sai dai kece macen kuma shaiɗaniyar, idan zamu shekara
dubu, baki isheni kallo ba, wadda take halalina ma, sai da.... Sai kuma ya yi
shiru.
Ya cigaba da cewa "Kamar yadda na gaya miki, duk wata
mace idan ba jauhar ba, namiji ce a idona"
"Katako kake gani ba namiji ba" tayi maganar cikin
ƙunƙuni.
"Ban taɓa ganin abin da ya raina ni ba kamar ke? Amm
dama zan gaya miki, ina ganin zan canza lawyer, saboda na lura baki da sa'a ko
kaɗan, gashi baki wani goge ba, nafi son wanda zai din ga abin da nake so. Idan
na biye miki, sai na koma prison, kuma ƙila nima a bini a kashe a can, kamar
yadda aka kashe wannan mutumin, dan haka zan canza lauya".
Ɗagowa tayi tana kallon Viper, cikin tsananin mamaki da
takaicin abin da yake fitowa daga bakinsa.
Fuskarsa a ɗaure, alamar da gaske yake yi.
"Bayan duk wannan wahalar da na riga na sha? Ka san
zaka ɗauki wani lauyan, amma ka wahalar da ni, nake ta dagewa ina ƙoƙari a kan
shari'ar ka na kasa zaune na kasa tsaye?"
Viper ya ce "Eh, muddin zaki cigaba da yi mini rashin
kunya, tabbas zan sake saka miki ƙarfe wataran, kamar yadda na saka miki da
farko, na gaji kin kasa kawo ƙarshen lamarin, kullum sai surutu da shirme ki ka
iya"
Tamkar ta kwaɗe shi, haka wani abu ya cunkushe mata ƙirji,
kawai ta kifa kanta a kan gwiwarta.
"Abla, ɗago ki ga" banza tayi masa taƙi ɗagowa.
"Kin san magana ɗaya nake yi" ta ɗago idanunta, da
suka yi sharkaf da hawaye.
Ya ajiye mata takarda a gabanta, takardar umarnin kotu ce,
da ta hana kama shi, ɗagowa tayi ta kalleshi, ta rasa ihu zata yi na murna ko
kuma me? Kawai ta cukuikuye takardar, ta jefa masa a ƙirji, ta sauka daga kan
gadon tana cigaba da kuka"
Murmushi ya yi ya tashi ya bi bayanta, cikin kuka ta
ce "Amma a haka kake cewa zaka canza lauya?"
Ya ce "Sorry, am just kidding"
"A haka ake wasa Vi?, fuska a ɗaure ana zare ido?
Tayaya zan gane wasa kake yi?" Tayi maganar tana kuka cike da shagwaɓa.
Ya ce "Viper baya manta halacci, ba kuma ya saɓa
alƙawari, ko da zaki yi failing sau dubu, ba zan taɓa barin ki ke kaɗai ba,
alƙawari ne da na ɗauka"
Nabila ta ce "Look at you, i even save your life, amma
da haka zaka yi mini albishir da 'yar ƙaramar nasarar da nayi" ya girgiza
kai ya ce "Ba ƙaramar nasara ba ce Congratulations, and barrister Habib ya
yi miki message, Civil defense sun ɗaukko rahama" a take ta waro ido ta ce
"Dan Manzon Allah, da gaske?" Ya jinjina mata kai, alamar eh.
Rikicewa tayi, ta durƙusa tayi sujudu shukur, ta tashi, ta
shiga kaiwa tana komowa ta ce "Alhamdilillah, ko yanzu na mutu, na cika
wani sashe na alƙawarin da nayi, Allah sarki malam Garba, Allah ya yi masa
rahama, ni me ma zan yi ne dan daɗi Vi?"
Murmushi take yi, tana kuka, tana ta zarya a ɗakin, kamar
zata zare, shi kuma sai bin ta yake da ido. Ta je ta tsaya a jikin bango, ta
jingina tana sauke numfashi.
Ya sake takawa, ya ƙarasa in da take ya saka hannunsa ɗaya
ya dafe bango, yana cigaba da tsareta da ido.
"Thank you for saving my life 'yar suga" duk da ta
takura, amma bai hanata yi masa murmushi ba.
Kallonta yake yi, yana tunanin a yaya zata ɗauki ƙaddarar da
take bibiye da ita? Ko zata iya jurewa, ko zata gaza kamar yadda yayi? A
hankali ya ce "Wannan babbar nasara ce ki ka samu, kamar yadda nayi
tsammani, ba kya gori, kamar yadda Jauhar take, na zata da na ce zan canza
lauya, zaki yi mini gori, amma ba ki yi ba.
Akwai tambayoyi da ki ka yi mini a baya, da wasu wanda nake
son na yi miki.
Da fari meyasa nayi yinƙurin kashe ki karon farko da na
ganki? Meyasa ki ka ga ruɗewa a fuskar liti da walid da suka ganki? Meyasa na
din ga korarki idan ki ka zo wurina, nake yi miki barazanar mutuwa? Meyasa su
liti suka amince su kawo ki wurina, duk da babu mahalukin da suke bawa damar
hakan? Meyasa Indabo ya ke ƙoƙarin yi mini tarko da ke? A yanzu ko a baya, ba
za a rasa mutanen da suka nuna miki sanayya ba, alhalin baki san su ba
right?" Ta tsare shi da ido tana jiran amsohin tambayoyin.
"And as my lawyer, akwai abubuwan da yakamata na sanar
da ke, but before then, Abla ni da ke ƙaddara ce mai ƙarfin gaske ta haɗa ni da
ke, dan haka dole mu yi haƙuri, mu karɓeta a yadda ta zo mana, saboda pain ɗin
da zaki shiga, zai iya fin wanda ni na tsinci kaina a ciki"
Tayi tsuru tana kallonsa.
Ya zaro wani hoto a aljihunsa, ya miƙa wa Nabila.
Hannunta na rawar rashin sanin wace ƙaddarar ce, ta sanya
hannu ta karɓi hoton, wata 'yar ƙaramar ƙara ta saki, ta saki hoton a ƙasa,
jikinta yana rawa, ta kalleshi ta ce "Soka ke sai na haukace sannan zaka
daina yi mini wasa da hankali, menene wannan? Ni bani bace wannan, ni yaushe na
sanka har muka yi wannan hoton tare?" Tayi maganar a firgice, tana neman
ta raɓa shi ta wuce, amma ya riƙeta a jikin bango, idanunsa suka cika da hawaye
ya ce "Matata ce a jiki, ita ce jauhar, 'yar madarata, mace mafi soyuwa a
gare ni, matar da ba zan manta halaccinta ga rayuwata ba, matar aljanna da
kullum nake fatan na farka daga mummunan mafarkin da nake yi, na farka na ganta
a kusa da ni, Nabila meyasa ki ke kama da matata?" Jikinta ne yake wata
irin rawa, ta zazzaro ido tana kallon sa.
Buɗe ƙofar ɗakin aka yi, suka waiwaya gaba ɗaya suna kallon
ƙofar, Alhaji mu'azzam ne ya shigo tare da barrister Habib, da kuma ɗan mama,
da yake laɓewa a baya, yana leƙowa.
Cikin mamaki Viper yake bin Alhaji mu'azzam da kallo, ba
tare da ya saki Nabila ba.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
Cak Viper ya tsaya yana bin kankarofi da kallo, zuwa kan ɗan
mama da yake ta zazzaro idanu.
Kankarofi ya haɗiye wani abu mai ɗaci, saura ƙiris ya yi
loosing control ɗin sa, saboda yanayin da ya ga Viper da Nabila.
Viper ya a janye hannunsa a hankali, ya tsaya a tsakiyar ɗakin,
su kankarofi suka shigo.
"Meya kawo ka in da nake?" Yayi maganar a
kausashe.
"Haba ƙanina, mayar da wuƙar mana, abun rabo ya ƙare,
miƙa hannu na menene, bai kamata ace zuwa yanzu muna cigaba da wannan abubuwan
ba, ko da ran jauhar, ko babu mallakinka ce, matarka ce dan haka ba zan din ga
bibiyarta ba, balle yanzu da babu ranta, ka sassauta wannan kishin dan Allah.
Ga Anas, wato ɗan mama yaronka na hannun damanka, da duk wani nasarar aiki da
muka yi a kanka, ya faru ne saboda ƙoƙarin sa, sai dai kan mu kai ga bayyana
maka komai, ashe ka gano shi, ya gudo wurina hankali a tashe, ya ce na taimake
shi, ba zai iya jure hukuncin da zaka yi masa ba, na zo on his behalf, na bayar
da haƙuri kuma nayi maka bayanin komai"
Viper ya bi ɗan mama da wani irin kallo, ɗan mama ya ce
"Na shiga uku, dan girman Allah Oga Viper kayi haƙuri, tursasa mini aka
yi, wallahi bani da niyyar cin amanarka, ban taɓa cutar da kai ba, ka san ina
yinka, kamar yadda ka ke yi na, kayi mini rai saboda Allah"
Alhaji mu'azzam ya ce "Ya isa haka Anas, ni yakamata na
wanke ka" duk maganar nan, Viper idonsa na kan ɗan mama, ɗan mama ya sake
maƙalewa a bayan Kankarofi ya ce "Gaskiya daga nan kayana zan tattara na
gudu Cadi, kallon nan da yake yi mini, tsoro yake bani, bana tunanin zai yafe
mini, da ƙyar idan bai saka na gana da Russia ba"
Kankarofi ya riƙo hannun ɗan mama, suka ƙarasa gaban Viper,
ya numfasa sannan ya ce "Lokacin da uban gidanka yana raye, Dodo, ka fi ni
sanin waye shi, ka fini sanin hatsarinsa da imaninsa. Babu wanda ya bawa damar
sanin sirrikan da yake da su, kuma ya sani sai kai.
Duk da shi ma mai aikata laifi ne, amma yana yi wa hukumomi
amfani sosai wurin kama masu laifi, daban-daban.
Ya baka horo na musamman, ta yadda yake gane masu laifi,
komai kamalarsu, yadda yake iya gane idan akwai kayan laifi a wuri, bai tsaya
nan ba ya saka aka baka horo na musamman, a kan fasahar na'ura mai ƙwaƙwalwa.
Manyan ƙasar nan na mu'amala da shi sosai da sosai, dan ya
san duk wasu hanyoyi da za a iya shiga da fitar da kayan laifi, ciki da wajen
ƙasar nan, ba tare da ta an kama kaya ba, sukan haɗa kai da shi, su bashi
dukiyoyin su, ya yi musu kasuwancin ƙwayoyi da sauran kayan laifi, ya ruɓanya
musu riba a shekara".
Viper ya ce "Duk meye amfanin dawo da abin da ya riga
ya wuce, abin da na riga na sani, kar ka aibata gawar uban gidana"
Kankarofi ya ce "Ba aibata shi nake yi ba, kayi haƙuri
na sadaka da gaɓar da nake son na kai ka. Dodo yayi shirin yin murabus, bayan
ya koyar da kai manyan abubuwa, da ka iya zama makamin rusa wasu daga cikin
manyan hanyoyin aikata laifuka da ba kowa ya sani ba.
Daf da zai mutu, ya danƙa amanarka ga manyan mutane da ya
yarda da su, ciki har da shugaban hukumar NIA na wancan lokacin, ya basu
tabbacin zaka iya basu gudunmawa ta kowane ɓangare, sukaɗai ne hukumar da ya
yarda ya damƙa amanarka a hannunsu, duk da kasancewar baka ji, amma kai babban
makami ne, ka san manyan sirrukan da bayan shi babu wanda ya sani.
Bayan mutuwar dodo, sun buƙaci kaje su baka horo, kayi aiki
da su, amma ka ƙi, saboda zuciyarka da tunaninka na kan ɗaukar fansa a kan
madaki, kuma rashin yadda ya sanya ka sake cewa ba zaka je ba, dan baka da
tabbacin ta wace hanya zasu yi amfani da kai.
Bayan aurenka da jauhar, bayan na shiga damuwar rashinta,
wataran muna hira da cousin ɗina, wanda shi ne aka danƙa amanarka a wurinsa,
muna hira, yake bani labarinka, a nan na gano cewa lallai kai ne ake magana a
kai, na cigaba da matsa masa, a kan lallai suyi ƙoƙarin su ga sun ɗauke ka,
zaka yi musu amfani sosai, a lokacin ina fatan silar aikin, ka daina wani abun,
kuma ka samu hanyar kula da Matarka.
Har bincike na saka aka kuma yi mini sosai a kanka, a nan na
gano kana aiki da Indabo, abin ya ɗaure mini kai ya bani mamaki.
Bayan wani lokaci, ban san meyafaru ba, na samu labarin ka
je ka basu haɗin kai, an kama ɗan gidan indabo a Mexico, da laifin safarar
cocaine, duk da babu wanda ya sani, amma ni ina da hanyar samun bayanai na a
kanka.
Na cigaba da fatan Allah yasa daga haka su hilace ka, ka
amince da aikin nan, amma sam baka da intrest a kan haka.
Wasu lokutan Hafsa kan bani labarin, irin soyayya da ƙaunar
da ka ke yi wa jauhar. Kwatsam na samu labarin mutuwar ta, wai ka sha miyagun
ƙwayoyi ka kasheta, sai dai sam ban ji na yarda ba.
Daga yadda na bibiyi case ɗin silently, naga sam babu
adalci, a yadda aka gudanar da binciken da gurfanar da kai ɗin ma a gaban kotu,
kuma na samu labarin abokin gabarka, Madaki shi ya maye gurbin aikinka, a wurin
Indabo.
Ni na saka aka kamo Anas ɗan mama, aka matsa mini shi, yadda
yakamata kasancewar sa, yana cikin tsagerun dabar Madaki.
Shi ya tabattar mana da Madaki ne ya karɓi kwangilar kasheka
a wurin Indabo, amma azal ɗin ta hau kan matarka.
A lokacin shugaban ƙasa ya samu nasara a tenure farko, kuma
yayi mini S.A ɗin sa na fannin tsaro, haka zalika ya tafi da ɗan uwana a
matsayin shugaban hukumar NIA.
Sosai nake biyan ɗan mama, ya koma wurin su Walid, tun suna
korarsa, suna hantararsa, har suka saki jiki da shi a dabar su, duk da
kasancewarsa yaron madaki, suka bashi cikakkiyar kariya daga Madaki, yana
reporting duk wani motsinka a gareni, da kuma hukumar NIA, hakazalika ni ne
nake tura maka saƙonni. Tabbas nayi amfani da kai dan cimma nawa muradin a kan
indabo, kuma taimakonka nayi, sauran abin da ya faru ka sani, ni nake sanya a
goge duk wani sahun laifi daka aikata, ta hanyar amfani da jami'an Civil defense,
kan daga baya, hukumarku ta karɓi ragamar cigaba da kula da kai, tare da turo
maka gayattar dawowa ka cigaba da aiki da su ta hanyar ɗan mama, da yake ajiye
maka rigunan aiki, ina nema masa afuwa, shi ma umarni aka ba shi da dole ya
bi"
Viper ya din ga haɗiyar wani yawu mai zafi, yana son yayi
magana, Nabila ta dafe kanta ta ce "Wannan wane irin abu ne wai, gaba ɗaya
sai juya mini kaina ake yi, na kasa gane komai, wai menene haka" tayi
maganar cikin ɗaga murya, tana dafe kanta. Viper ya juya ya koma in da take, ya
durƙusa ya ɗauki hoton Jauhar da yake ƙasa, kawai Nabila ta tafi zata faɗi,
idanunta a lumshe, ya riƙe ta, amma ya kasa magana,a hankali ya ja ta, ya mayar
da ita kan gadonta.
Ta ce "Bana gani, duhu nake gani, kaina zai fashe"
kankarofi ya nufo gadon, amma Viper ya ɗaga masa hannu, ya ce "Excuse us
please"
Kankarofi ya tsaya yana kallon Viper, Viper ma ya ƙura masa
ido.
Barrister Habib ya ce "Ina son zan yi magana da
ita"
Viper ya ce "Ka jira tukuna" Kankarofi yayi musu
alama, da su fita, haka duk suka fice.
Nabila ta dafe kanta, ta cigaba da kuka, ya ce "Wai
kukan me ki ke yi haka?"
"Ni ka rabu da ni dan Allah, ka ƙyale ni, so ka ke na
haukace, gaba ɗaya kun ruɗa mini kai, sai ƙara bijiro da wasu abubuwa ku ke yi
da ban san da su ba, ni ka rabu da ni".
"Ki tsaya ki saurare ni"
"Ba zan saurareka ɗin ba, ba na son jin komai, ni ka
rabu da ni"
"Am talking and you are misbehaving" yayi maganar
cikin tsawa.
A razane ta dafe kanta, ta faɗo daga kan gadon, ta takure a
wuri guda tana kuka.
Ya tashi ya sake dawowa gabanta, amma ta hau jifansa, da
abun da duk ta samu a kusa da ita. Shiru yayi yana kallonta, yana tuna lokacin
da jauhar ta burkice masa, da yayi mata laifi, ta din ga jifansa da kwanuka,
yayi ajiyar zuciya ya kira wayar Asibiti. Mintuna kaɗan likita ya shigo, ya
tarar da Nabila kamar mai shirin zarewa, ya yi mata magana, amma tayi masa
shiru.
Ya fita ya dawo da allura, ya kama damtsenta zai yi mata,
taƙi tsayawa, sai da Viper ya riƙeta aka yi mata, sannan jikinta ya saki ta hau
lumshe ido.
"Viper, garin yaya ta zama haka lokaci guda? Ba ta fara
samun sauƙi ba?"
Viper ya ce "Ta ɗan samu damuwa ne, idan ta farfaɗo ta
samu sauƙi, kawai a sallame mu"
Likitan da yake sanye da wandon sojoji ya ce "Viper,
discharge kuma? Why? Ba haka aka shirya ba, tana ƙarƙashin kulawar hukuma, kai
fa shegen taurin kai ne da kai, sai ka janyo wata matsalar tukuna?"
Viper ya ce "She's not safe here, zamu bar wurin
nan"
"Zuwa ina kuma? Akwai wanda zai shigo cikin barrack, ya
zo asibiti yayi mata wani abu ne?"
"John, i want her to be discharged"
John ya ce "Ko nayi discharging ɗin ta, ka san ba zata
bar wurin nan ba, sai an bamu izinin hakan. Let me help you put her to bed,
she's already sleeping on the floor" wani irin mugun kallo Viper ya yi
masa, ya ce "Ohh sorry" ya juya ya fice.
Viper ya sunkuya yana kallonta, fuskarta ta koma ja, sai
tsatstsafar da gumi take yi, da gani baccin na dole ne kawai saboda allurar da
aka yi mata.
Zai iya cewa ya bai taɓa ganin mace mai naci, da tsantsar
jarumta, kamar Nabila ba.
Duk da baya son taɓa ta da yake yi, amma dolensa ya ɗagata
ya mayar da ita kan gadon, ya gyara mata kan gadon, ya juya ya fito.
A waje ya tarar da Alhaji mu'zzam da barrister Habib, da ɗan
mama a zazzaune.
Ya taka ya ƙarasa gaban Alhaji mu'azzam, ya ce "Meyasa
ka zaɓi irin wannan lokacin, ka gaya mini wannan maganganun a gabanta? Na gaya
maka ni zan kawo ƙarshen wannan lamarin, tun da ni ya shafa, abu ne mai nauyin
gaske da ɗaukarsa ba lallai ya zama abu mai sauƙi a gareta ba. Dan haka bana
buƙatar ka a cikin abin da ya shafeni ya shafi abin da ya shafe ni. Wadda ta haɗa
ba rabonka ba ce ba, ban san dalilin da zai sanya ka din ga bibiyar rayuwata ba
kamar kana bi na bashi ba"
"Muddin za a bayar da labarin jauhar, dole mu'azzam zai
fito a ciki, ban cigaba da bibiyarka dan ina neman wani abu a wurinka ba, na
bibiyeka na taimake ka ne, domin mu taimakawa juna, daga ni har kai, buƙatata
ta biya kaima taka haka, naga bayan indabo, kai kuma ka ɗauki fansar tozarci da
zaluncin da aka yi maka.
Ban da ƙaddara ta Ubangiji, na rigaka ganin jauhar, kuma
aurenta nayi niyyar yi, amma Allah ya nufa matarka ce, na so jauhar so na
haƙiƙa, amma na kawar da kai, duk na shiga tashin hankali jin irin mutumin da
ta aura, yanayin zamanku daga baya ya sanya na samu kwanciyar hankali, kisanta
da abin da aka yi maka ya bani ya sanya na tausaya muku nake bibiyarka.
Nabila ma na rigaka ganinta, ni ba a garin kano na fara
ganinta ba, tun a Abuja wurin da aka basu rantsuwar zama cikakkun lauyoyi. Sai
da na kusa rasa hankalina da tunanina, saboda tsananin tashin hankali da ruɗewa,
har sai da na zata ko matsalar ƙwaƙwalwa na samu, saboda damuwar kisan gillan
da aka yi wa jauhar.
A lokacin ban yi ƙasa a gwiwa ba, na tashi yin bincike a
kanta, har zuwa wannan lokaci, nake bibiyarku daga kai har ita. Muddin ba
butulci zaka yi mini ba, na taimakeka Aminu, ko nayi maka laifi a wani wurin,
wani wurin na taimake ka". Sai da ya gama tsaf Viper ya ce "Na nemi
taimakonka ne? Wane irin taimako ne kayi mini kana yawo da hankalina, ka yi
mini shi a munafunce? Ka din ga wasa da hankalina kana ɓoye kanka? Madalla da
abin da ka yi, amma ina buƙatar abin da ka ke yi ya tsaya a iya nan, Nabila da
abin da ya shafi rayuwar ta hurumina ne, daga nan idan ta farfaɗo zan bar wurin
nan da ita"
"Waye ya baka wannan damar? A ƙarƙashin kulawata take
ba taka ba, naje na samu mahaifinta ma, na sanar masa da hakan, sai dai kai ka
bar nan wurin, amma Nabila na tare da mu"
"Don't cross the boundaries! Ban ƙi ayi mutuwar kasko
ba, ba na wasa da duk abin da ya shafi marigayyiya, a kanta ba abin da ba zan
aikata ba, idan da na koma na ɗauki wannan rigar ce, zan cireta na ajiye, kar
ka sake kusanto in da nake, bana buƙatar taimakonka"
Kankarofi ya ce "Jauhar ce mallakinka, Wannan kuma
Nabila ce"
"Na gaya maka Nabila ta haramta ga kowa muddin ina
ganin fuskar matata a jikinta" Viper ya yi maganar yana zazzaro ido cikin
matsanancin kishi, jijiyoyin kansa suka ɗaɗɗaga.
Cikin hanzari ɗan mama ya fito, ya shiga tsakanin Kankarofi
da Viper, barrister Habib gefe ya koma, dan gaba ɗaya Viper tsoro yake bashi.
Hankalin sojojin wurin ne, ya fara dawowa kansu, suka
tattaso suka nufo su, Viper sai huci yake yi.
"Easy oga, ka fahimci al'amarin nan dan Allah, wallahi
Yallaɓai mai ƙaunarka ne, ba ya nufin cutar da kai, ba ƙaramin taimako ya yi
maka b.....
"Shut up! Da na ƙyaleka ban ce maka komai ba, ka ke
gaya mini maganar banza, ka kuma yi mini magana, sai na tatsule ka a wurin nan,
menene na cigaba da bibiyar rayuwata dan na auri wadda ya so ya aura, menene
amfanin haka?"
"Wadda ake yi domin ta, ta bar duniya, ba shi da wata
mummunar manufa a kanka, ka fahimci hakan oga dan Allah"
Ya nuna ɗan mama da yatsansa, alamar kashedi.
"Viper wai me ka ke yi haka ne? Oga ne fa da kansa a
wurin nan, ka ke ɗaga masa murya ka ke faɗar maganganu"
Viper ya ce "Bana buƙatar sa a rayuwata, ya bar wurin
nan, ko kuma ni yanzu na bari"
Ɗan mama ya koma wurin kankarofi ya ce "Dan girman
Allah sir kayi haƙuri, wallahi Viper yana da kirki, kar ka ce zaka cire
hannunka, tsabar kishi ne kawai, kar ka ce sai ka na son Nabila sai ka
aureta"
Kankarofi ya ce "Yaron ba shi da kunya, ba kuma shi da ɗa'a,
ban yi zaton haka daga gare shi ba"
Ɗan mama ya ce "Wallahi Viper yana da ɗa'a da biyayya,
kawai ka san soyyaya ba ta da gwani ko jarumi, na san dai yana da taurin kai da
azabar fushi, amma wallahi duk faɗansa yana da kirki, kar ka manta, da shi nake
kwana nake tashi muke rayuwa. Amma ba haka yake ba, dan Allah kar ka cire
hannunka a kansa, zan yi maka proving abin da na gaya maka, ai na san
maganinsa, zai nustu bari ya gama hargowar".
Ana ta fama da Viper, ya ce sai ya bar Asibitin da Nabila.
Liti ne ya ɗaga wayar Walid, ganin kiran ɗan mama ne ya ce
"Kai dan ubanka, ina ka shiga kwana biyu baka nan, baka sanar mana ina ka
tafi ba, Viper duk ya addabe mu, ko wani rashin gaskiya ka fara ne?"
Ɗan mama ya ce "A'a oga liti, akwai matsala ne, ina oga
walid?"
"Yana banɗaki matsalar me? Tsokana ka yi ko me? Kana
ina ne?"
"Ina cikin barikin sojoji"
Liti ya ce "Iyee, ba wurin yan sanda ba sojoji? Ɗan
mama me da me ka ke sha ne? Sojoji fa ka ce? Me ka yi musu?"
"Dan Allah ku zo, da kai da Oga walid, ku kaɗai ne zaku
yi solving case ɗin nan"
Liti ya ce "Kai, duk iskancina, ban taɓa tsokanar
wannan mutanen ba, da babu Allah a ransu, haka kurum su tumurmusa ni a banza,
su sauya mini kamanni, Allah ya ƙwatoka, bari Walid ya fito ko zai iya ƙwatoka,
dama ya fi ni imani da tausayi, ko shi ko Viper, dama shi ya saba da jure
wahala. Dukanka suka yi ko kuma karairayaka suka yi?"
Ɗan mama ya ce "Ba ɗaya, matsala aka samu ne"
"To Allah ya yi maka maganinta, ya tsayar iya kanka,
Allah ya sa idan su Walid ɗin sun zo su ganeka, ba su sauya maka fasali ba, su
mayar da kai gorilla ko wata halittar ba"
Walid ya ƙaraso, ya karɓi wayar daga hannun liti cikin
tashin hankali ya ce "Ɗan mama, kana ina ne? Meyafaru meya kai ka wurin
sojoji ne?"
"Oga walid, lafiya ƙalau fa, wani case ake yi, ina tare
da oga Viper, ku yi sauri ku zo dan Allah, kar ya aikata wata ɓarnar, ku kaɗai
ne zaku iya shawo kansa"
Walid ya ce "Kai da Viper kuma a cikin barikin Sojoji?
Garin yaya?"
Liti ya miƙe ya ce "Viper kuma? Ka gani ko? Viper wasu
lokutan baya lissafi ko shawara, kawai ya ɗibi jiki ya tafi, Allah kaɗai ya san
me ɗan maman yayi musu, ya janyo an kama shi"
Walid ya katse wayar ya ce "Muje dai mu ji menene, ka
san babu yadda za ayi Viper ya bar ɗan mama ko wa ya tsokana kuwa"
Liti ya ce "Ai da yake ba mutunci ne da shi ba, kwana
nawa muna nemansa, da ya tafka tsiyarsa kai tsaye kuma sai ya nemi Viper ba mu
ba" haka suka tafi, liti yana ta masifa.
Al'amin na ɗakin da Nabila take, shikaɗai ya kasa ya tsare,
ya zuba mata ido, tana ta bacci. Tun da aka yi wannan dambarwar yaƙi fita, gani
yake yana matsawa zasu ɗauke Nabila.
Ji yayi an buɗe ƙofa, ya waiwaya.
Wasu manyan sojoji suka shigo, ɗaya ya ce "Viper, taso
muje ko"
"Muje ina? Am not going anywhere"
"Meyasa ka ke haka ne, kar ka saka mu yi faɗa da kai
fa"
Viper ya ce "Wace azaba ce ni ba a gana mini ba, ba zan
je ko ina ba, ban san me kuka haɗa kai da mutumin nan, ku yi mana ba" da
ƙyar suka lallaɓa shi, suka fita zuwa wani sashe na barrack ɗin.
Suna shiga wurin, ya ga liti da Walid, sai dai still ya ga
kankarofi, take ransa ya kuma ɓaci, yana mamakin taurin kai da rashin zuciya
irin na kankarofi.
"Me kuma zan yi maka? Me kake so kuma yanzu?"
Walid ya miƙe ya ce "Mai zamani"
Viper ya ɗaga masa hannu ya ce "Mai laya"
Walid ya ƙarasa gaban Viper ya ce "Mai zamani, easy
mana cool your temper" yayi maganar yana ɗan dukan ƙirjin Viper.
"Meyasa yake bibiyata, dan na auri matar da ya so
aura?" Yayi maganar cikin damuwa.
"Ta rasu fa yake bibiyarka, da tana raye ya bibiyeka
ne?" Viper ya yi shiru.
Walid ya ce "Kishi ne yake damunka, an fara yi mana
bayani, bawan Allah nan, ya taimaki rayuwar ka ta fuskoki daban-daban, ka nutsu
ka kwantar da hankalinka, mu taimaki rayuwar Nabila. Ba zai yiwu ta cigaba da
zama a nan ba, tun da Asibiti ne, kayi haƙuri a samu kauwammanen wuri a ajiye
ta, idan ya so kaima ya zamana kana tare da ita. Wancan abokin aikinta ne, kuna
buƙatar ƙawarta 'yar jarida, da sauran su, kai a tunaninka effort ɗin ta kawai
ya isa ya sanya ku yi Wannan nasarar? A Nigeria fa muke, dole sai da wa ka sani
wa ya sanka, ka danne koma me kake ji, mu fuskanci gaskiya.
Butulci da manta alkhairi ba halinka bane mutumina, ka ajiye
kishi a gefe, muna buƙatar a bi mana hakkin jauhar, muna buƙatar yi wa Nabila
tukuici da abu mai muhimmanci, idan ka ɓata aikin nan saboda taurin kai, ba ka
yi musu adalci ba, ciki har da ita da mu kanmu da muke tare da kai" Viper
ya ja jiki ya zauna a hankali.
Liti ya ce "Ɗan mama duk zaman da muka yi da kai, ashe
aikin munafunci ka ke yi, amma kuwa ka yi asara dan wannan ba aikin yi bane ba,
kuma saboda tsabar ƙwarewa, ko da wasa baka taɓa gaya mana ba. Ni dama na daɗe
ina zargin baka da gaskiya"
****
Miƙa tayi sosai tana addu'a, ta ji kamar gadon da take kai,
ya sha bamban da wanda ta kwanta a kai, ta tashi zaune a hankali, ta ganta a
cikin wani katafaren bedroom, bisa wani ƙaton gado.
Tayi tsuru da ido, tana tunanin ko mutuwa tayi.
Wata mata ce tayi sallama, ta ce "Kin tashi? Ga banɗaki
nan idan zaki yi alwala ki yi wanka ki rama sallolin da ake binki".
Nabila ta ce "Ina ne nan baiwar Allah? Ko mutuwa nayi
ne?"
Matar ta ce "A'a, wanda suka kawo ki, zasu zo su yi
miki bayani, ga kaya nan ko zaki canza".
Ta tashi a hankali tana addu'a, ta shiga banɗakin, ta yi
wanka, ta yi alwala, ta fito ta din ga salloli, daga iya abin da ta iya tunawa,
ga wata irin yunwa tana ji, gaba ɗaya ta kasa tantance meyake faruwa gaba ɗaya.
Matar ta dawo, ta kawo mata abinci, amma Nabila ba ta taɓa
ba, ta takure a gefe.
Viper ne ya shigo, ta ɗago kai ta ƙura masa ido, har ya
ƙarasa gabanta, ya zauna ya ce "Sannu, ya jikin?"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kamar nayi kuskuren
yinƙurin taimaka wa rayuwarka, kana ƙoƙarin rusa tawa, ta hanyar ganin ka
haukata ni, me nayi maka haka? Kuma ina ka kawo ni nan?"
"Ba ki yi kuskure ba, domin kuwa kin yi sara ne a kan
gaɓa, kuma zaki alfahari da ƙaddarar da ta haɗa ni da ke"
"In yi alfahari bayan na haukace ko?"
Viper ya girgiza kai ya ce "Ba zaki haukace ba,
tambayoyin da nayi miki, haryanzu nima ina buƙatar samun amsarki, sai dai bani
da tabbacin samun amsarsu duka.
Amma bari mu gani, ko a cikin abin da zan gaya miki zamu
gano bakin zaren, rayuwata kamar ƙwallon ƙafa take, daga wannan ƙafa zuwa
wancan, daga wannan tudu zuwa wancan rami.
A haƙiƙanin gaskiya, ban yi shekaru biyar a gidan yari
ba". Nabila ta waro ido tana kallonsa.
"Nayi zaman gidan yari, cikin tsananin razani, cikin
matsananciyar damuwa da ƙuncin zuciya, tare da fatan Allah ya sa da an mayar da
ni kotu, a yanke mini hukuncin kisa, na huta, amma ranar da aka saka a cigaba
da shari'ar ta wuce ba a cigaba ba.
Azaba da wahalar da nake sha a gidan, bai ɗaga mini hankali
ba, kamar yadda halin da nake ciki, bai hana wasu din ga ƙoƙarin nemana da
mummunar ɗabi'a ta neman maza ba, ciki har da ma'aikatan wurin.
Abin da su madaki suka yi amfani da shi suka shaƙa mini, ya
cigaba da affecting ɗina.
Azaba da takura, ya sa na zame musu mahaukaci, na danne
wanda suke cewa sarkin gida, na kusa janyo maƙogwaronsa waje, nayi masa dukan
mutuwa, saboda sun zata dolo ne ni, duk da sun san labarin waye ni, prsion ɗin
ta sha banban da wadda ake kaini.
Suka ajiyeni a wani wuri, suka din ga gana mini azaba, wai
nayi yinƙurin yin kisan kai, ba wanda ya duba abin da ya neme ni da shi. Aka
ajiyeni, babu wanka, babu wanki, babu ci babu sha, sai azabar duka. Wurin ga
ƙazanta da rashin tsabta, a haka kuma a kan fito da ni, ace za a saka ni aikin
wahala.
A halin da nake ciki, na tsinci wani ɗan ƙarfe, da zai iya
zama makami, na farwa wani, dan fuskar madaki na gani, sai da aka ƙwace shi da
kyar, na huda masa wuya, sannan naga ashe ba shi bane ba, ƙwaƙwalwa ta ce ta
fara samun matsala, banda kururuwar da nake yi wasu lokutan, ina kiran matata
da ɗa na, tare da alwashin kashe madaki. Aka rabani da sauran fursunoni, aka ce
na haukace.
Watarana, cikin dare ina kwance, na san idona biyu, amma
bakomai nake ganewa ba, fatana na farka daga baccin da nake yi, na ganni tare
da matata.
Kawai wani mutum ya saka mukulli ya buɗe in da nake, ya fara
lalubena, duk a galabaice nake, kwana uku ba abin da aka bani na ci, sai na
tsaya naga me zai yi mini, kar nayi masa wani abun, na je ƙwaƙwalwata ce take
gaya mini shirme, kamar yadda ta saba. Sai na ji bai nufi yi mini lalata ba, kawai
ya soka mini wani abu, kamar allura a cinyata, ya fara zuba mini wani abu mai
tsananin zafi a jikina, ruwan allurar na shiga, ina jin kamar ana fizgar naman
jikina, a take na kurma ihu, na tashi na shaƙe shi, ina dukansa, ina cewa shi
ya kashe jauhar, sai na kashe shi. Ina dukansa jikina yana ƙara sanyi, kamar
ana zare mini laka.
Aka zo aka raba ni da shi, nayi masa jina-jina, ni kuma na
faɗi a wurin, basu bi ta kaina ba, suka fice da wancan. Ina kwance na ji wani
abu mai sanyi na bin hancina, a taƙaice dai, kasheni yayi yinƙurin yi mutumin.
Washegari ina kwance kamar gawa, ina jin duk abin da ake yi,
amma ba zan iya motsi ko magana ba, aka ɗauke ni, aka ce za a kai ni Asibiti,
ayi mini magani, ashe wasa farin girki, maimakon a kaini asibiti, sai aka yi
wani wurin da ni.......
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
"Bana iya gane ina ake, saboda a matuƙar galabaice
nake, amma naji a jikina, yakamata ace idan asibiti ne ya ci ace an je, duk da
bana sanya ran zan rayu, a maganar da mutanen motar suke yi, jini nake ta
fitarwa ta hancinca, ga azabar yunwa da datti, na gidan yari, tufafina tamkar
mahaukaci, dan a mazaunin da aka ajiyeni kenan.
Aka yi parking ɗin motar, aka canza mini wata, wadda nake
kyautata zaton ambulance ce, dan a ciki aka toshe hancina da bandeji, saboda
jinin da nake zubarwa, aka saka mini ruwa, muka cigaba da tafiya. Tun ina jin
maganganun da ake yi a motar, tafiya taƙi ci taƙi cinyewa, har na daina gane
komai, na buɗe ido na ganni a wani wuri, a kan gadon asibiti, an tuɓe kayan
jikina, sai gajeren wando, na tashi a gigice cikin matsananciyar kiɗima, ina
ihu saboda ban san meyafaru da ni ba, na farka ina zaton zan ga madaki da
jauhar, ina hana shi cutar da ita, wani ɓangaren ina tunanin ko ina prison ne,
wani yayi galaba a kaina. Sai dai na ji ni a ɗaure da ankwa dukka hannayena, na
din ga ihu saboda yadda naman jikina yake yi mini wani irin azababben zugi,
kamar ba zan rayu ba.
Wasu mutane da ban san suwaye ba, suka zo kaina, da allurai
suka yi mini, ɗaya daga cikin su ya ce "A cigaba da kula da shi mu gani,
will he survive the poison, duk yadda zaku yi, ku yi ƙoƙarin ceton rayuwar
sa" haka na sake fita hayyacina na farka, sai dai a wannan karon, ban ji
wannan raɗaɗin ba.
Aka cire mini ankwa, aka tashe ni zaune, aka kawo mini
abinci, kamar mayunwacin kare, haka na dirarwa abincin nan, kamar zan haɗa da
kwanon saboda yunwa, ina ci ina jin kamar ana yayyanaka kayan cikina da wuƙa,
amma azabar yunwar da nake ji, ya sanya naƙi daina ci, sai dai ban gama ci ba
na din ga amai, haɗe da jini, wai duk cikin side effect ɗin allura da aka yi
mini ne, kashe ni aka so ayi.
Ba a sake bani abinci ba, sai ƙarin ruwa da allurai, mutanen
wurin ba kowa ke jin hausa ba, ni kuma bana magana, suna bani damar yin salla,
aka fara koya mini cin abinci.
Ba wanda na tambaya dalilin kai ni wurin nan, kuma babu
wanda yayi mini bayani, a haka har na shafe wata guda cif.
Duk yadda suka so nayi magana, bana yi, sai dai wasu lokutan
ina rasa tunanina, na din ga ganin madaki da jauhar a zahiri, na din ga
yinƙurin shaƙe duk wanda yake kusa da ni. Sai da na ɗan samu nutsuwa, aka aske
mini gemuna da sumar kaina gaba ɗaya, aka kuma saka mini ankwa, aka rufe mini
ido, aka sakani a mota, aka bar wurin da ni.
Wani wurin aka sake kai ni, mu huɗu ne a wurin, kowa da
wurin da ake ajiye shi tamkar ceil. Na fauskanci nikaɗai ne musulmi babu
bahaushe, sai ƙabilu, kullum bayan nayi sallar asuba, da sassafe haka za a
kaimu wani wuri, ana bamu training na azabatarwa, wanda ka iya zama ajalin
mutum.
Idan muka gama, zamu saka wasu riguna, masu tambarin dragon,
za a kaimu wani wuri, in da ake bamu darasi, malamanmu turawa ne, class ɗin mu
huɗun nan ne, kowa da computer sa, ayi mana darasi ta online. Waɗanda suke kula
da mu, wasu irin zaratan ƙartin sojoji ne, sun kai su goma sha biyu, a kan mu
huɗu kawai.
Azaba ta ishe ni, ban ga alamar za a mayar da ni gida ba, na
gaji, gaba ɗaya na rasa ina rayuwata ta dosa, bani da wani burin da ya wuce na
mutu na huta. Za a bamu abinci mai kyau, a bamu abin sha mai kyau, amma azabar
da ake mana ta ishe ni. Wataran ana tsaka da bamu training, na fizgi bindigar
wani, nayi yinƙurin kashe kaina, suka riƙe ni, aka ɗauke ni aka kai ni wani ɗaki,
da ban zaci zan fito da rai ba. Sai da na kwana bakwai a ɗakin, ko class bana
zuwa. Ranar na takwas, ogansu ya zo ya same ni, yake tambayata meye matsalata
na yi yinƙurin kashe kaina.
Na ce masa su mayar da ni garinmu, ina son ganin matata.
Ya ce mini muddin ina son komawa gida, sai na basu haɗin
kai, na yi wa ƙasata aiki, sun san ni yaron dodo ne, kuma akwai amfanin da zan
yi musu, dan haka dole na mayar da hankali a kan training da kuma karatun da
nake yi, kuɗi aka ware masu nauyi, saboda mu yi wannan karatun.
Na ce ni ba zan yi ba, su kasheni kawai su daina wahalar da
rayuwata.
Ya ce ba zasu kashe ni ba, in yi abin da suka umarceni, idan
ina son na ga matata. Sai na tambaye shi, matata na raye? Ya ce tana raye, zan
ganta idan na daina taurin kai, nayi abin da ake so. Kuma ko ina so ko bana so,
ubangidana ne ya nema mini wannan aikin, tun kan ya mutu, dan haka sai dai na
mutu a process ɗin, tun da na san sirruka masu muhimmanci da zasu taimaki ƙasa.
Na din ga tunanin, wane irin laifi na yi wa dodo, zai zaɓa mini wannan azabar,
sai dai tsananin ɗoki, da daɗin bakin zan ga matata, ya sanya na saduda, gashi
suka saka mini ido sosai da sosai, saboda suna iƙirarin bani da lafiyar
ƙwaƙwalwa, kuma bana ji.
Wata makaranta muke yi a russia, ilimin na'ura mai ƙwaƙwalwa
kawai ake bamu, duk da na san abubuwa da yawa ni, ta online muke makarantar, a
training ɗin nan aka koya mana duk wani nau'i na haɗawa da wargaza bindiga,
ilimin makamai, leƙen asiri, da duk wani nau'i na abin da ya shafi harkar
tsaro.
Suka ce mini ƙwazona, shi zai bayar da damar komawata
garinmu, har naga matata, na roƙe su ko a waya, a haɗani da matata tun da sun
ce tana raye, suka ce ba zasu haɗamu ba, zan ɓata musu aiki.
Na zage damtse, lokutan jarrabawa, ina cikin overollers, ina
tashi da points masu kyau, na fara sabawa da wahalar training, jikina duk ya
murɗe, sai dai babbar matsalata bana cikakken bacci, bana iya bacci, da na rufe
idona, zan ganni a falo, tare da jauhar madaki zai kasheta, gaba ɗaya sai na
tubure musu, na hau ihu. Ko abincin da nake ci, bana cin sa ta daɗin rai,
saboda damuwa da tunani. Abokan karatuna a kan basu damar shan giya, har mata a
kan kawo musu, amma ni duk ba wannan a gabana.
Tun ina lissafi da sanya ran ƙarewar wannan wahala, naga
babu rana babu wata, na zauna nayi tunani, babu yadda za ayi, jauhar na raye a
gurfanar da ni a gaban kotu, a tuhume ni da laifin kisan kai, naga kawai raina
mini hankali suke yi, sai kuma wata zuciyar ta ce mini ai mafarki nake yi, sai
dai na rasa wanne ne mafarkin wanne ne zahirin?.
A haka na shafe shekaru a wurin nan, ban taɓa barin kewayen
in da muke ba, na rayu da matsanancin ƙunci da damuwa a zuciyata, wasu lokutan
sai an yi mini allurar bacci nake iyawa.
A haka muka kammala karatu, sauran ukun aka ce, za ayi
posting ɗin su, in da ake son su gabatar da ayyukansu, ni kuma sai an yi
settling issue ɗina. Mun zama sojojin leƙen asiri.
Ni dai jinsu kawai na din ga yi, sauran suka din ga murna,
aka shirya mana walima, sauran duk sun saba da su, ni duk yadda aka so ja na a
jiki, a yi raha da ni, a saba ban yadda ba, dan ni kaina na san rabi mai
hankali rabi mahaukaci nake. Abokan karatuna kuwa, basa shiga harkata, dan duk
lokacin da ƙwaƙwalwa ta ta haska mini fuskar madaki, a jikin ɗaya, sai na kusa
kashe shi, dan duk da training ɗin da aka bamu, na fi su ƙarfi nesa ba kusa ba,
kuma ba addinmu ɗaya ba, ba ƙabilarmu ɗaya ba.
Sai da na ji haushin dodo, duk da baya raye, na ji ya sakani
a masifa, duk da ina fatan sanya indabo, biyan bashin abin da ya aikata ciki
har da kisan dodo.
Ana gobe za a mayar da ni kano, ina ta murna zan koma naga
jauhar, naga ɗana, dan na san a lokacin ya yi wayo, ban san meyafaru ba, ko me
suka yi mini ba, sai farkawa nayi, na ganni a prison. Hakan ya ƙara burkita
ƙwaƙwalwa ta, na fara tunanin wani mafarkin na kuma yi, na din ga kiran sunayen
shugabbaninmu da suka bamu training, ina cewa su zo su cika mini alƙawarin da
suka yi mini, su haɗa ni da jauhar ɗina da ɗana kamar yadda suka yi mini
alƙawari, gashi ko za a kashe ni, ban san sunan garin da aka kaini ba.
Gandirobobi, suka yi mini dukan tsiya, wai na cika musu
kunne da hauka, matar da na kashe da hannuna, bayan na sha na bugu, na amsa
hakan a kotu, yanzu kuma na zo na ishe su da shirme. Suka yi mini dukan tsiya,
amma na kasa daina kururuwar kiran sunaye da magiyar su haɗani da jauhar, gaba ɗaya
na zama mahaukaci, ni kaina a lokacin na yadda ni mahaukaci ne. Wasu lokutan
idan na buɗe jikina, ina ganin tabon raunuka da wahalar da na sha a wancan
garin, amma fafur aka nuna hauka nake yi, da sambatun ƙarya.
Tun da suka tabattar mini ni na kashe jauhar, na ƙara rasa
tunanina, damuwa da tashin hankali suka koma sabbi fil.
Kusan watanni uku, cikin dare ina kwance, dama ɗakina daban,
aka tashe ni aka ce na fito, na fita na bi bayan wanda suka kira ni, aka fitar
da ni wajen gate, wai an karɓi court order na tafi.
Na tsaya ina kallonsu, ina mamakin wane mafarkin kuma na
sake shigowa, suka rufe gate ɗin prsion ɗin, suka bar ni a tsaye.
Zuciyata ta raya mini maza kafin na farka daga baccin, na je
na ga jauhar, ko zan farka dai na ganta.
Na fara tafiya a duhun nan, har garin Allah ya waye. rana ta
ɗaga, na isa unguwar mu, ban manta hanya ba. Sai dai Abbu ya tabattar mini da
jauhar ta mutu, ni na kasheta, na tafi na bar masa gida.
Mutanen unguwa suka din ga kallona, har da masu gudu.
Babu tunanin komai ko tsoro, bayan na je dabarmu, su Walid
suka karɓe ni, suka kuma tabattar mini da cewar na rasa Jauhar.
Na burkice musu, amma suka riƙe ni suna kula da ni, kawai
sai ga sanarwa daga hukumar 'yan sanda, wai a kamo ni, a raye ko a mace, da
fari suka ce na gudu daga prsion, daga baya kuma wai an sake ni ba bisa ƙa'ida
ba.
Walid ya ce "Kome za ayi, ba zasu yadda a sake mayar da
ni a kulle ba, sun san ba zan taɓa kashe 'yar madara ba.
Na tarar da su da ɗan mama, na san shi tun da na taɓa yi
masa rauni, shi ne ya bayar da gidan da muke zaune muke ɓoye.
Idan nayi kamar na gaya musu, rayuwar da nayi ana bani
training, sai na tuna aikin sirri ne, an gargaɗemu a kan haka, kuma bani da
evidence ni kaina bani da tabbacin cewa a gaske nayi wannan rayuwar.
Bana iya bacci, bana iya cin abinci, ga azababben ciwon kai,
ga nauyin ƙirji, kawai na koma shaye-shaye fiye da da, duk da a wurin training
ina shan sigari da wiwi, sai dai bana shan miyagun ƙwayoyi, ko giya.
Amma bayan tabattar da mutuwar jauhar, na cigaba da
shaye-shaye ina fatan ko haukacewa nayi, na manta da duk wata rayuwa, wadda
nake tunanin gaske ce ko mafarki, amma kayan cajin basa ɗaukata.
Ganin ɗan mama na din ga yi tamkar Nura, dan ba zai fi
sa'ansa ba, ya din ga yi mini biyayya, hakan ya sanya nake son sa sosai, saboda
su Walid kullum cikin faɗa muke, suna hana ni shaye-shaye.
Shi kuwa samowa yake yi ya kawo mini, a hakan idan na bushi
iska, sai na tafi gidana na dura ta katanga, na kan yi iya ƙoƙarina nayi kuka,
amma bana iyawa, sai dai na yi ta jin ƙunar rai da bugun zuciya.
Na kan yi yinƙurin zuwa na ɗauki fansar abin da madaki yayi
mini, amma su Walid su hana ni, suka samo mini waya keypad suka bani incase ina
buƙatar wani abu, basa nan, ɗan mama shi yake yi mini duk wata hidima, kawai
wannan mutumin ya fara kirana, yana ƙara dagula mini lissafi. Kayan
shaye-shayen ya zama basa ɗaukata, sai dai nayi ta tamɓele, suna iya ƙoƙarin su
a kaina, amma ba sa yi mini abin da nake so.
Damuwa shaye-shaye suka ƙara tsunduma ni a wani hali, har
nake yinƙurin kashe kaina. Ashe duk wannan abun, mutanen nan suna bibiye da ni,
da duk wani motsina, na din ga ƙoƙarin jami'an tsaron kawai su kamani, su yi
duk yadda za su yi da ni, amma da nayi laifi, dan goge hanyar da za abi a kama
ni.
Walid ya zo ya bani labarinki, na ce ƙarya yake yi, cutata
zai yi. Bai haƙur ba, ya kawo mini ke, kawai ƙwaƙwalwata ta bani cewar, an haɗa
baki da ke an shirya wani abun ne, dan a kuma yi mini wani mugun abun, hakan ya
saka na sanya miki ƙarfe ko zan ga ainihin wacece ke, dan na san jauhar ba ta
kaiki girma ba, ba ta kaiki waye ba, kuma babu yadda za ayi ta ganni ta kasa
gane ni.
Amma da ki ka faɗi, ciwonki ya tashi, sai na ga kin koma ita
sak, duk da ina jin haushin mata wasu lokutan, amma a sanadinta nake tausayin
su, saboda tunawa da ita, na sai kayan treatment ɗin ta na asma, nake ajiyewa
ina kallo, ina ganin kamar zata dawo. Shigowar ki rayuwata, ya ƙara rikita mini
lissafi, Walid ya ce na sanar miki irin kamannin da ki ke yi da matata, na baki
labarina, amma naƙi.
Na cigaba da barazanar kashe ki, saboda na kasa tantance
jauhar ce ke ko ba ita ba ce, nayi ta ƙoƙarin avoiding ɗinki, kar na aikata ɓarna,
saboda babu in da ki ka bar ta, sai kuma daga baya na ga zuwanki wurina, yana
rage mini damuwa, kamar ke kin fahimci halin da nake ciki.
Rigar da ake ta bibiyata da ita, ta wancan aikin ce, dan an
tura mini saƙon zasu tafi da ni, na ƙi kulawa, sai daga baya da na amince da
ke, na ga dole ina buƙatar security ko dan lafiyar ki, na amince zan tafi nayi
aikin, amma sai na samu nasara a kotu. Aka ce za a ɗaukar mini lauyoyi da zasu
kare ni, zasu nemi a basu ni, su suyi na su binciken, su yi mini hukunci na ce
ban yarda ba, ina da lauya, tsaro kawai nake buƙata a tsare mini lafiyarki.
Suka yarda da hakan, amma da zimmar zan fara yi musu aiki.
Daga nan barrack ɗin kano, suka zo suka tafi da ni, aka bani
kayan aiki, ciki har da tab ɗin hannuna, da rigar aiki da ki ke ganina da ita,
sai dai ba kowa ya san ma'narta ba, ciki har da su Walid.
A yanzu haka ina karɓar salary, kuma ina aiki da NIA,
ƙoƙarin ki ne zai sanya, na yi free na cigaba da aikina, akasin haka kuma, zan
iya komawa prison ne, babu ranar fitowata, duk da ba zan ce ma ban yi shekarun
nan a prison ba, tun da kauwwame ni aka yi, aka hanani dukkanin walwala.
Nabila tayi ƙuri da ido tana kallonsa, cike da tsantsar
mamakin duk wannan rashin mutunci, da cin mutuncin doka, a Nigeria ake aikata
shi. Wani abun idan bai zo kanka ya faru ba, sai ka rantse da Allah ƙarya ne ba
zai faru ba. Har gara shi, da aka fitar da shi daga prison ɗin, taimakon sa aka
yi ta wani fannin, wasu kuwa canza musu gari ake yi gaba ɗaya, suje su yi
rayuwarsu, saboda tsabar masifa, a prsion ɗin ma bin sa aka yi za a kashe. Gaba
ɗaya rayuwar Viper gaba a baya take, sai dai ita ma tata rayuwar kusan haka.
"Abla, talk please, jami'an tsaro na nemana, zan je a ɗauki
statement, kuma dole sai da ke zamu tafi, dan Allah ki daidaita nutsuwar ki,
yanzu rayuwata tana hannun Allah, tana hannunki, nayi rejecting support ɗin da
za a bani a hukumance, na zaɓi cika miki alƙawarin da nayi miki, ba zan ja da
baya na barki ba"
Ta ɗago idanunta da suke tsiyayar da hawaye ta ce
"Wacece ni? Kuma wacece jauhar?"
"Ki na ji na? Shiyasa tuntuni nake jinjina yadda zan yi
miki bayanin nan, ki nutsu ki karɓi ƙaddara a duk yadda zata zo miki"
Nabila ta ware masa manyan idanunta, da suka yi jawur, ta ce
"Ba ni ce jauhar ba, to ni wacece? Ko jauhar 'yar uwata ce? Dan girman
Allah ka kaini gidansu na ga ko iyayenta ne, wataƙila muna da alaƙa"
Ya girgiza mata kai ya ce "Babu tabbacin kina da alaƙa
da ita, bata taɓa gaya mini cewar tana da wata 'yar uwa ba, ce mini tayi itakaɗai
mahaifiyar ta ta haifa a gidan, ta fita. Amma ke babu abin da ki ka sani game
da mahaifiyarki, da ahalinta?"
Ta ja wata irin ajiyar zuciya ta ce "Idan ya kasance
jauhar yar uwata ce, kenan ina da 'yar uwa ban taɓa ganinta ba, ban rayu da ita
ba? An cutar da ni, wallahi an zalunce ni"
Viper ya ce "Kar ki ce haka, ki bari sai mun tabattar
tukuna, kuma wannan amsar dole 'yan gidanku ne za su bayar da ita, amma mu fara
gamawa da wannan case ɗin, kiyi haƙuri"
Tari ta fara yi, tana kuka ta ce "Ni gaba ɗaya baka yi
mini adalci ba, ka ɓoye mini abubuwa da yawa, da yakamata na sani, sai yanzu
zaka gaya mini. Ni ka rabu da ni ma ka ƙyale ni, ina ga nima haukacewar zan
yi"
Duk yadda Viper ya sauke jin kansa, yake rarrashinta, ta
burkice masa, ta ce idan an ga dama a ɗaure shi da igiya, case ɗin nasa ma ta
fasa, ƙarshe haka ya tashi ya rabu da ita.
***
"Badi'a, anya ba zan gudu na bar ƙasar nan ba, ina daf
da yin faɗuwar baƙar tasa, wannan yarinyar ta dage sai ta ga bayana ta kaini
ƙasa, ya zan yi ne?"
Badi'a ta ce "Naja, wallahi ki ka bari yarinyar nan ta
ga bayanki, kin ɗuma asara"
"Badi'a, kowace hanya ta toshe ta ko ina, duk masu goya
mini bayan, sun ce wannan karon lamarin yafi ƙarfin su, shi kansa Indabo yana
can Abuja, yana fuskantar tuhuma, EFCC sun dakatar da wasu daga cikin
kadarorinsa, yana cikin tashin hankali, na rasa yadda zan yi".
"Wallahi kina guduwa asirinki zai tonu, ki jira kiga
iya gudun ruwansu, tun da haryanzu ba su ce komai ba, ba su tona miki asirin
ba"
Kamar ta fasa ihu ta ce "Yanzu jira zan yi sai sun fito
sun tona ɗin? Ke kin san ba zasu bar ni ba, lallai ɗan hakin da ka raina, shi
ke tsole maka ido, babu ƙoƙarin da ban yi na kawar da yarinyar nan ba, amma abu
ya gagara, amma duk da haka ba zan zuba ido ba, sai na san abun yi".
***
Abdul kuwa ya yi sintiri tsakanin Kano da Abuja, babu adadi,
amma ya kasa ganin Indabo, hakan ya sanya ya tabattar wa da kansa cewar Indabon
ne ya ɗauke ramma.
Duk yadda mahaifiyar ramma, ta bugi cikinta, ramma ta nuna
mata babu abin da ya faru, Abdul ajieta kawai yayi, duk da ya ce ya aureta.
Maman ramma ta ce "Har na ji sanyi, dole a zo a raba
auren nan, dama ba da yardata kawunki ya aurawa wannan tsohon mara mutunci ke
ba, saboda kuɗi da tsinannen son abin duniya yayi mini haka. In sha Allah yaron
nan sai Allah ya tozarta shi kamar yadda ya tozarta mu, sai Allah ya wulaƙanta
shi, kamar yadda yayi mana" jin Addu'a ramma tayi har cikin zuciyarta, dan
sai da cikinta ya motsa, tayi shiru bata amsa da Amin ba, ta san duk inda yake
yana can hankali a tashe.
"Amma ramma, kin tabattar ba abin da ya haɗaki da
mutumin nan? Mutumin da yayi miki fyaɗe shi ne zai aure ki kawai ya ajiye
ki?"
Cikin tsoro da rashin gaskiy, ramma ta ce "Eh, ɓoye ni
yayi saboda kar asirinsa ya tonu, cewa aka yi da ya kashe ni ma, shi ne bai
kashe ni ba. Kuma wai ya biya mini kuɗin makaranta na cigaba har jami'a"
"Allah ya kiyaye, ba ma buƙatar duk wani abu daga
hannunsa, da haka zai yaudaremu, in sha Allah sai an hukunta shi, barrister nan
tayi mini wannan alƙawarin, sai an gurfanar da shi, ya girbi abin da ya shuka,
ga kisan kan da suka yi wa wannan tsohon, da suka ƙalawa sharri, Allah dai ya
watsa shi, daga shi har wanda suke goya masa baya"
Ramma ta kawar da zancen, ta hanyar cewa "Mama wai a
nan zamu yi ta zama?"
Ta ce "A'a, nima wannan Alhajin ne ya saka aka ɗaukko
ni wai idan aka bar ni, nima za a iya cutar da ni, ban san zuwa yaushe zamu
zauna a nan ɗin ba, amma ina ga da komai ya daidaita sai mu tafi" Ramma ta
jinjina kai.
Maman ramma ta bi ta da ido, ganin yadda duk jikinta yake a
sanyaye, ta kalli fatar ramma yadda tayi haske take ta sheƙi.
"Rahama"
"Na'am mama"
"Wai me ki ke ci ne a hannun nasa, na zata a wahale zan
ganki, ki gaya mini tsakani da Allah idan akwai wani abu"
"Mama babu komai fa, nifa tun da ya ajiye ni baya
ƙasar, sai masu kula da ni" mama ta jinjina kai kawai, ba ta sake magana
ba.
Viper ya haƙura da azabar kishin da yake ɗawainiya da shi,
aka yi zama na musamman da shi da Alhaji mu'zzam, da shugabannin sa, aka sake
jaddadawa Al'amin, Alhaji mu'azzam tainakonsa yayi, kuma tare da haɗin kan
Alhaji mu'azzam komai ya tafi daidai, kasancewar sa babban mutum a ɓangaren
harkar tsaro.
Sai kuma aka yi masa alƙawarin ba shi duk wata kariya, da
shi da Nabila, tun da haka ya zaɓa, amma muddin suka yi failing a shari'a a
kotu, babu wani abu da za a kuma sake yi masa. Ya ce ya amince, babu gudu babu
ja da baya Nabila ce lauyar da zata tsaya masa.
Sai dai Nabila gaba ɗaya ta hargitse, Viper ya kasa gane
kanta, gashi an gayyace shi hukumar yan sanda, ya je ya bayar da bayani, amma
Nabila fafur ta ce ba zata je ba.
Sanarwa kuma ta fita, muddin Viper bai kai kansa ba, order
kotu zata koma arrest order.
Nabila na zaune, zuciyarta a cunkushe ta rasa abin da yake
yi mata daɗi, lallai tana buƙatar ganin Abba, ko ta halin ƙaƙa Viper ba shi da
niyyar yi mata bayanin abin da take son ji.
Ta ga wayarta a gefen gadon da take kai, tayi sauri ta ɗauka,
ta kunna tana dudduba saƙonni.
A What's app ta tarar da message, wai gari ana ta yaɗa
rumors, cewar Viper ya saceta, ba a san in da take ba, wasu suna Allah ya ƙara,
wasu suna yi mata addu'a.
Ta buɗe message ɗin Nasir, ta saurari voice message ɗin da
ya turo mata.
"Haryanzu wanda ki ke iƙrarin karewa, bai bayyana a
gaban hukumar yan sanda ba, idan ya wuce wa'adin da muka bashi, order kotu zata
sauya, ga shela da ake ta yi, na cewar ya sace ki, ba a san in da ki ke ba, ko
a nan sunanki ya ɓaci, am did on you.
Knocking aka yi, tayi shiru, dan ta zata Viper ne, ta ajiye
wayar.
Wani narkeken mutumi ne ya shigo, tare da barrister Habib,
da sumayya, da kuma Walid.
Zama tayi sosai tana kallonsu, sumayya ta ƙarasa ta zauna a
kan gadon ta ce "Nabila, ya kike kina cikin ƙoshin lafiya?" Nabila ta
jinjina mata kai.
Mutumin ya ce "I salute you barrister, kallabi tsakanin
rawuna" yayi maganar cikin gurɓatacciyar hauss, amma da alama ya ji hausa.
Ta ɗan yi murmushi yaƙe, ta kalli Walid ta ce "Oga
walid"
"Na'am barrister, ya ki ke ya ƙoƙari?"
"Alhamdilillah" ta din ga bin su da ido, dan bata
san dalilin zuwan su duka ba.
Walid ya ce "Barrister, na san mun yi miki laifi, tun
da fari na so Viper yayi miki bayani, amma yaƙi, kin san shi wasu lokutan da
taurin kai, kuma na san kin yi haƙuri da shi, amma dan Allah ki janye batun
cewar ba zaki tsaya masa ba, ki yi haƙuri dan Allah, ba zamu iya jure ganinsa
ya koma prison ba, kiyi wani abu a kai, wanda kuke ƙalubalanta, suma ba zasu
zauna haka ba, dole zasu yi ƙoƙarin yin wani abu suma, ki taimaka"
Ɗaya mutumin ya ce "Duk wani support da zamu ba shi a
hukumance, yaƙi yarda, ke kaɗai ce hope ɗin sa, kar ki ce a'a, kiyi haƙuri, a
ƙarasa wannan case ɗin, sai koma menene ya biyo baya"
"Meyasa ya ɓoye mini abubuwa irin wannan?"
"Tsarin aikinmu ne a haka, haryanzu ke kaɗaice lauyar
sa, ke ki ka sani, su kansu yanzu da muka zo tare ba komai suka sani ba, ga
abokin aikinki, dole kina buƙatar sa, ga ƙawarki kina buƙatar ta, ga abokansa
da sun san komai"
Barrister Habib ya ce "Ga case ɗin ramma ma"
Mutumin ya ce "Yess, ke fa yanzu idon duniya yana
kanki, ba laifinsa bane, kin san ba mai yawan magana bane ba, kuma tsarin
aikinmu ne, yanzu abin nan da ya gaya miki, zai iya zama da hukuncin kisa a
kansa, banda mun san a situation ɗin da yake"
Walid ya ce "Yana asibiti ma, ciwon cikin nan da yayi
kwanaki ya kuma tayar masa, hantarsa ta kumbura, yana asibitin sojojin nan da
aka ɗaukko ki"
Nabila ta numfasa, ta ce "Muje zan ganshi, kuma ina son
zuwa office ɗina, zan koma aiki"
Mutumin nan ya ce "Is ok, zaki koma bakin aikinki, amma
a ƙarƙashin kulawar mu, ƙasarmu na san rayuwar Viper"
"Amma ku ka bari ya kusa haukacewa, aka ɓata masa
suna" mutumin yayi murmushi ya ce "We are trying our best now"
Sumayya ta ce "Nabila ina son magana da ke fa"
"Ni da nake kare ɗan ta'adda, me ki ke so a
wurina?"
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Arfan Abbanta, an buga
dake an barki, batutuwa ne masu muhimmanci, amma sai kin saukko tukuna"
A cikin wata rantsatsiyar mota, aka ɗauki Nabila da sumayya,
da barrister Habib, suka tafi.
Liti ya ƙarewa ɗan mama kallo ya ce "Ɗan mama, ni
haryanzu mamaki nake yi, yaushe Viper ya san wannan mutanen bamu da labari ne?
Wai naga sojoji ne suke kula da shi, duk ka munafunce mu"
"Nima ban san meyasa ba"
"Ƙarya kake yi munafiki, ka san komai, meye haɗin Viper
da sojoji? Ko ka gaya mini ko na ɓulaka da wuƙa"
Ɗan mama ya ce "Wallahi oga liti muka yi misbehaving,
zanemu za ayi daga ni har kai a barikin nan, dan Allah kayi haƙuri ka rufa mana
asiri"
"Ni haryanzu tsoro nake ji, idan ba haɗa kai aka yi da
kai, ake son a kashe mu ba, ko a haɗamu a cikin yan boko haram ace duk su ne
ba, gaba ɗaya baka da imani ɗan mama, tsawon lokaci kana jakadancin
munafunci"
Suna cikin maganar, su Nabila suka shigo wurin, ba wanda ake
bari ya shiga wurin Viper, su liti ma a waje suke.
Aka ce Nabila ce kawai zata shiga wurin Viper.
Ta taka a hankali ta shiga, ta tarar yana kwance, likita
yana yi masa allura ta cikin cannula.
Suka gaisa da likitan, ya gama yi masa ya fice, ta zauna ta
kalleshi ta ce "Effect na shaye-shaye yana ta bibiyarka" ya yi shiru
yana kallonta.
"Idan ɓoye mini waye kai, ba laifinka bane tsarin
aikinka ne, ni kuma ɓoye mini wacece ni, laifinka ne da wasa da hankalina.
Ba zan watsar da alƙawarin da nayi maka ba, gobe in Allah ya
kaimu zamu je station, zamu bayar da statement, amma bisa ga sharaɗi ɗaya da
sai ka yadda da shi"
Ya lumshe idanunsa ya buɗe yana kallonta.
"Am talking to you".
"Viper zaki sawa sharaɗi?"
"Your freedom depends on me, so watch your tounge"
"Send me back to prsion if you like, i am still Viper,
the most dangerous snake"
"A heartless spy"
Ya yinƙura ya tashi zaune yayi murmushi ya ce "I admit
it, am heartless"
"Dole ka amince da sharaɗina Viper, akasin haka
kuma........
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
Shiru tayi ganin irin kallon da ya yi mata, a take jikinta
ya hau rawa, ta haɗiye maganar da take son yi.
Ya jingina yana kallonta ya ce "Ina jinki, sharaɗin
menene?" Ta girgiza kai ta ce "Shikenan kawai, yakamata mu fara zuwa
mu sake ganin madaki, an ce yana asibiti, a hannun jami'an tsaro, yakamata mu
je mu ganshi, kafin mu haɗu gaba ɗaya a gaban yan sanda"
"Menene sharaɗin naki?"
Ta ɗan kalle shi ta ce "Bakomai, ya wuce kawai" ta
yinƙura zata tashi, ya mayar da ita ya zaunar da ita, yana bin fuskarta da
kallo.
"Kawai kin zaɓi ki wahalar da ni, saboda kin ga ina
lallaɓaki ko?"
Ta girgiza kai Viper ya ce "Haka ne mana, i can give up
the trial, na koma prison kawai, i can do it"
Jiki a sanyaye ta ce "Am just curious to know who i am,
ina son sanin mahaifina, da 'yan uwana idan ina da su, amma bana fatan ace ina
da alaƙa jauhar matarka"
Da sauri ya ce "Why?"
"An gaya mini mahaifina yana da mata da yara, ya auri
mahaifiyarmu, muddin jauhar yar uwata ce, zai iya yiwuwa cikinmu ɗaya, ta mutu
ba tare da na taɓa ganinta ba" tai maganar tana zubar da hawaye.
"Kin ga babban dalilin da ya sanya, na cigaba da ɓoye
miki abubuwa da dama, you will lose confidence. Babu tabbacin kina da alaƙa da
jauhar, kuma dolena cika alƙawarin da nayi miki, ki kwantar da hankalinki"
kamar ya tunzurata, ta cigaba da kukan.
Yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Bana barin 'yar madara ta
zubar da hawaye, muddin kina kuka a gabana, matata nake gani, zan iya
rungumarki at any time na ce zan rarrashe ki, ki rufa mini asiri kar ki saka na
aikata ɓarna, kin ga daga nan kuma ba lallai na tsaya a nan" da sauri ta
ja da baya tana kallonsa, tsaf zaka rantse ka ce baya magana.
Ta ce "Ammm yaushe zamu je mu ganshi?"
Viper yayi murmushi ya ce "Za ayi mini allurai anjima,
sai mu je kawai"
Nabila ta ce "Ka ji sauƙi ne?"
"Idan aka yi mini allurai ina jin daɗin jikina, daba da
shaye-shaye sun yi mini mugun tabo, illoli ko ta ina"
"Kayi ta istigfari, Allah ya yafe maka ya sassauta
maka, bari na je waje" ya jinjina mata kai alamar to.
Ta fito ta tarar da su, ta kalli barrister Habib ta ce
"Yaya, zamu je mu ga ɗaya daga shaidun da muke da su ne, gobe in Allah ya
kaimu zamu je wurin jami'an tsaro"
Habib ya ce "To shikenan, jikinsa sa sauƙi amma?"
Ta jinjina kai alamar eh.
Sumayya ta ce "Ni dai sonake naga Vipern nan, amma
Allah bai yi ba, zan koma ana nemana, amma Nabila na gaya miki mahaifin sa yana
ta sintiri, yana so na haɗaki da shi, neman ɗansa yake ido rufe"
Jiki a sanyaye Nabila ta ce "Ki rarrashe shi, yayi mana
afuwa zuwa mu kammala shari'ar nan, Viper ba zai yadda su haɗu yanzu ba".
"Amma Arfa meke damunki ne? Ko wani abin suke yi miki
da ba kya so?"
Nabila ta girgiza kai hawayen da ta ke ƙoƙarin tarewa, suka
zubo mata.
Hankali a tashe Sumayya ta ce "Nabila menene?"
Nabila ta ja hannunta suka koma gefe, ta ce "Sumayya,
matar Viper da aka kashe, ina kyautata zaton ina da alaƙa da ita"
Sumayya ta ce "Ta ina?"
"Yanzu na san ko na ce ya bani hotonta, ba zai bani ba,
idan ki ga ganta rantsewa zaki yi, ki ce ni ce a jikin hoton"
"Ke Nabila bana son shirirta dan Allah, saboda soyayya
ta rufe miki ido, har kin fara kalen dangi"
A hasale Nabila ta ce "Sumayya yaushe zaki din ga ɗaukar
maganganuna serious ne? Kodayeke shikenan, daga baya idan komai ya bayyana,
zaki gane idan ma ƙarya nake, idan ma gaskiya nake faɗa, ki je kiran da ake yi
miki" Sumayya ta bi Nabila da kallo har ta bar wurin.
Suna tafe a hanya, Nabila take tunanin lokacin da take
takurawa Nasir, tana tambayarsa me zata yi, wanda zai saka tayi suna sosai ta
zama kamar bunkure, ya ce mata ta nemo masa Viper. Ta din ga bin yadda abubuwa
suka din ga faruwa daki daki, ita kanta ta san ƙudura da ikon Allah ne kawai da
ya ƙaddara sai ta haɗu da Viper. Da ta din ga lissafa rashin hankali da wautar
da ta din ga yi, tana yawon nemansa, yana iƙirarin kasheta, amma tana nace tana
bibiyarsa kamar mayya har zuwa wannan lokaci, abun lamari ne na Allah kawai.
"Amma daga can, yakamata muje ku gaisa da mahaifiyar
ramma"
Ya ɗago ya kalli Nabila ya ce "Bana son haɗuwa da
mutanen da na sani, suna yi mini kallon ɗan ta'adda"
Nabila ta girgiza kai ta ce "Ba kowa ne yake yi maka
kallon hakan ba, abin da yakamata ne, mussaman da iftila'in nan ya faɗawa
ramma" yayi shiru bai ce komai ba.
Har ɗakin da madaki yake aka kai su.
Tare da Viper suka shiga, suka tarar da shi a kwance, duk
jikinsa sara da suka, da rauni, ɗakin sai wari yake yi. Babban abin da ya bawa
Nabila mamaki bai wuce duk jikin madaki raunukan nan sun yi kore ba, maimakon
ja, irin na ciwo. Hatta fuskarsa sara ne, kamanninsa sun sauya daga shi sai ɗan
wando.
Nabila ta dubi jami'an tsaron da suke tsare da shi ta ce
"Yanzu a haka yake? Ana duba shi kuwa?"
"Eh, likitoci na duba shi, yana da ciwon suga ne, dan
haka wannan raunukan ba zasu warke ba, sai dai ayi ta treatment a haka".
"To wannan tayaya zamu je da shi kotu, yana magana ma
tukuna?"
Madaki ya buɗe ido da kyar, yana kallonsu.
Viper yayi murmushi, dan ya san ba ciwon suga bane kawai,
russia da yayi amfani da ita, wurin karya sihirin da yake amfani da shi ne ya
janyo haka, duk wani rauni da ya ji, muddin da ƙarfe ne, ba zai warke ba.
Wancan karon ma Viper shi yayi sponsoring yanke ƙafar madaki.
Viper ya ce "Ya kake kallonta, haryanzu kana tunanin
wadda ka kashe ce ko? Nayi mamaki da na turo maka ita da farko, ka iya jurewa
baka yi wani abu ba. Kodayeke namiji idan ya kai namiji, baya tsoro baya nuna
gazawa.
Ina yi maka albishir da sai ka ruɓe a raye, kafin ka mutu,
dan idan ka mutu yanzu hutu ne. Naka ƙarshen ya fi na kowa muni. Baka aikata
alkhairi ba, baka bar wani baya mai kyau ba, babu ɗa babu jika, sai tarin
zunubi da haƙoƙƙin mutane. Ga lokaci ya ƙure da zaka bi su yawon neman yafiya.
Ka zo a banza zaka koma a wofi, ina fatan sunana da yake gadon bayanka ba zai
ruɓe ba, zaka koma ga Allah da shi, duk da kome zan yi maka, ba zan huce
zaluncin da ka yi mini kashi-kashi ba.
Da farko yayana, na biyu ubangidana, mafi muni kuma matata
da ɗa na, wata shari'ar sai a lahira, duk abin da zan yi maka, ba zan bi wa yar
madara hakkinta ba, Allahn da yayi ta shi zai saka mata" yayi maganar
muryarsa na rawa. Madaki ya ƙure su da ido.
Nabila ta girgizawa Viper kai, cikin matsanancin tausayin
sa, juyawa yayu yana haɗiye hawayen da yake shirin zubo masa.
"Vi, shaidar da muke da shi, ɗaya yana kwance ba zai ma
taɓa yi mana amfani ba, ba magana zai yi ba, dole muna buƙatar wata ƙwaƙwƙwarar
shaidar"
"Kamar wa kenan? Wa zamu samo?"
"Muna buƙatar, ko daga cikin maƙwabtanku, ko makamancin
haka"
Viper ya ce "No, ki rabu da wannan mutanen, mu bari
gobe in Allah ya kaimu sai mu ga yadda za ayi".
"Muna buƙatar iyayen jauhar a case ɗin nan"
"Meyasa?"
"Saboda shaidunmu su zama masu ƙarfi, bana son a ja
shari'ar da yawa" yayi mata shiru bai sake cewa komai ba.
Nabila har system ɗin ta aka kawo mata daga wurin aiki,
barrister Habib ya kawo mata.
Tayi mamakin yadda tun da ta kunna wayarta, daga gidansu
babu wanda ya neme ta.
Dan haka ta kira Abba, sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga.
Ta ce "Abba ina wuni?"
"Lafiya ƙalau Nabila, yau kin tuna da ni kenan?"
"A'a Abba, wayar ba ta hannuna ne, yau aka bani
ita"
"Kin ga abin da taurin kanki ya janyo mana ko?
Ƙiri-ƙiri an ɗauke ki, an kai ki in da ban sani ba, da sunan an kauwwame ki,
ban isa na ganki ba"
Cikin mamaki Nabila ta ce "To ai Abba Sumayya ta zo in
da nake, barrister Habib ma haka, kuma dama na ce zan koma bakin aiki, ina son
zan dawo gida"
"Ai kin ga da baki bijirewa umarnina na cigaba da kare
mutumin banza ba, da ba ayi haka ba. Ki je Allah ya taimaka" ya kaste
wayarsa. Nabila ta bi wayar da kallo, ta rasa abin yi gaba ɗaya.
Nasir kuwa ya kasa ya tsare, muddin Viper bai bayyana a
gaban yan sanda ba, sai ya kama shi, ya ɗaura aniyar ko ta wani hali sai ya kai
Nabila ƙasa da Viper, Viper yake son nuna wa iyakarsa, ko dan saboda wulaƙanci
da gadarar da yayi masa.
****
Sumayya ce da safe ta buɗe gidan radiyo da safe, tana amsa
gaishe-gaishe, masu sauraro suke tambayarta ina Nabila da gaske an yi garkuwa
da ita.
Sumayya ta ce "Haƙiƙanin gaskiya, ba wanda yayi garkuwa
da Nabila, yanayin jiki da jini, ayyuka sun yi mata yawa, kuma ba ta ɗan jin daɗi,
dan haka da komai ya lafa za a ji ta dawo"
Message ɗin Nabila ta gani, a kan su haɗu a police station,
tana son su zama witness, zasu je da Viper a ɗauki statement ɗin sa.
Sumayya ta riga su Nabila zuwa, da ita da murtala.
A wata irin zuƙeƙiyar mota aka kawo Nabila, da Viper da su
Walid.
Nabila ce ta fara fitowa, su Walid ma suka fito.
Sumayya ta ce "Ki ka ce na zo da wuri, amma sai yanzu
ku ka ƙaraso"
"Malama ba wani daɗewa fa muka yi ba, yaya murtala ina
kwana"
Ya ce "Lafiya ƙalau, ya ki ke ya hidima"
Alhamdilillah.
Sumayya ta ce "Ina Vipern ne? Wanne shi a nan?"
Tayi maganar tana nuna su Liti.
Nabila ta yi murmushi ta ce "Wane mutum, yana cikin
motar, sai ya gama mulkin zai fito"
"Kai ni nayi neman suna, naje na gaishe shi"
Nabila ta yi dariya ta ce "Idan yayi miki halin, zaki
gane baki da wayo, ki bari zai fito da kansa.
Motar barrister Habib ma ta iso harabar wurin state CID ɗin,
yayi parking ya fito, suka gaggaisa, amma madugun yana ƙame a cikin mota, yana
kallon su ta cikin glass.
Can kuma da ya gama abin da Allah ya nufe shi da yi,
ya fito daga motar.
Ƙaton tabon da yake gefen wuyansa ya tabattar wa Sumayya shi
ne Viper, duk rawar ƙafar da take yi zata ga Viper yau, sai bakinta ya mutu, ta
zubawa sarautar Allah ido.
Ɗan ƙarewa harabar wurin kallo yake yi, yana tuna adadin
zuwansa wurin nan, tun jauhar na raye yake zuwa, da aka kasheta ma, nan aka
kawo shi, aka din ga gana masa azaba.
Tinkis-tinkis, ya fara tafiya yana bayar da faɗi.
Barrister Habib ya miƙa masa hannu, suka gaisa ya ce
"Ya jikin, an ce mana baka ji daɗi ba jiya"
Viper ya ce "Eh, ina ta fama da hanta, sai fatan Allah
ya sa mu yi kyakywan ƙarshe"
Ɗan mama ya ce "A'a Master ba yanzu ba in sha
Allah" Viper ya galla masa harara.
Liti ya ce "Wannan zaƙal zaƙal ɗin da ka ke yi, ba zai
hana aci ubanka, a hukuntaka ba, gara ai maka hukunci a duniya, tun kan ka je
lahira da laifin munafunci"
Nabila ta ce "Viper, ga yar uwata, sumayya T
ladan"
Ya jinjina kai ya ce "Yarinyar indabo" yayi
maganar yana mayar da hankalinsa kan Walid da yake yi masa magana.
Zata yi magana, Nabila ta hana sumayya magana.
Nasir ne ya shigo, wurin shima, da tasa tawagar, yana tafe
ana sara masa, yana wani basarwa.
Sai da ya ɗan tsaya suka yi kallon kallo da Viper.
Sumayya ta kalli damtsensa na hagu, nan ma wani tabon ne, da
alama an taɓa yi masa ɗinki a wurin, gefen kansa ma, ya wani shata kai ka zata
aski ne aka yi masa a haka, amma sara ne. Kai da ganinsa ka san an sha
gwagwarmaya.
Nabila ta ce "Vi, dan Allah na san kai ba mai magana
bane, sai abin da na amince kayi magana zaka yi, banda hasala da saurin fushi
dan girman Allah, kar ka yi wani abu da zaka janyo mana matsala Please".
Shafa ƙeyarsa yayi yana kallonta.
"Bamu da ƙarfi, bamu da tsumi bamu da dabara, sai a
wurin Allah, muyi ta addu'a"
Ya jinjina mata kai, suna tafe, ya ga ta koma jauhar,
lokacin da tayi belinsa da kyar, ta riƙo hannunsa suka bar wurin suna kuka.
Ɗan sandan ya kalle su ya ce "Waɗan nan fa?"
Nabila ta ce "Ni da wannan lauyoyin sa ne, wannan 'yan
jarida ne, wannan kuma suna cikin shaidunmu"
Mutumin ya jinjina kai, can aka fito da lakwari, ya rame ya
fita hayyacinsa tamkar lagwani, aka riƙo ƙugunsa, aka fito da shi.
Viper ya ƙure shi da ido, yana jin tamkar ya ƙwaci bindiga
ya harbe shi.
Ɗan sandan ya kalli Viper ya ce "Ina tayaka murna, kotu
ta hana kamaka, duk da ba a nan take ba, an danne bodari ta ka" yanayin
zaman da Viper yayi, kai baka ce da shi ake magana ba.
"Meye cikakken sunanka?"
Nabila ta ce "Sunansa Al'amin Ibrahim"
Nasir da yake wurin ya ce "Bashi da baki ne?"
"Doka ta bashi damar yin shiru, lauyoyin sa su yi
magana" ya kalli Nabila ta kalle shi.
Aka juya aka karɓi sunan lakwari ma.
"Menene ƙorafinka?"
Viper ya kalli Nabila, ta jinjina masa kai ya ja wasu second
ya numfasa ya ce "Sun shiga gidana, da misalin ƙarfe uku saura na daren
alhamis, shekaru shida da suka gabata, suka shaƙa mini abu, suka kashe matata,
ta hanyar kayar da ita a kan cikinta, bayan sun bugar da ni".
Nasir ya ce "Amma shaidu sun tabattar da cewa kana
ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, su ka sha ka kasheta"
Viper yayi shiru yana kallonsa, Nabila ta ce "Wane
shaidun kenan? Nan ba zaman kotu muke yi ba, statement muke bayarwa"
Nasir ya kalli Nabila, tamkar an canzata zuwa wata daban ba
Nabilansa ba, yadda take yi masa martani da zuciya.
"Meye haɗinka da su, da har suka shiga gidanka suka
kashe maka mata?"
Viper ya nuna lakwari, ya ce "Shi zaka tambaya, ban san
laifin da nayi musu ba"
Aka tambayi lakwari, amma lakwari ya kada baki ya ce
"Viper ƙarya yake yi masa, ba su shiga gidansa ba, basu kashe masa mata
ba"
Taka ya fara harzuƙa, amma Nabila ta dakatar da shi.
Walid ya ce "Yallaɓai, mune abokan harƙallar Viper,
tare muke sha da fataucin wiwi, Viper ya kan sha ƙwayoyi amma ba ko yaushe ba,
kuma mu abokansa da maƙwabtansa shaida ne, na matarsa ta saita shi a hanya,
kafin su kasheta, dan kuwa a lokacin sai da Viper ya hana sayar da wasu kalar
ƙwayoyi, a unguwar da yake da kewayenta".
Nasir ya kalli Walid ya ce "Ikon Allah, daina
shaye-shaye fa ba abu ne mai sauƙin da ka ke tunanin, abu ne da zai daina farat
ɗaya ba. Abu ne da yake buƙatar dogon lokaci, wani ma har da likitocin
ƙwaƙwalwa kafin mutum ya daina, ta yaya zamu yarda da cewar Aminu ya daina
shaye-shaye kuma bai yi shaye-shaye ba a wannan ranar?"
Liti ya ce "Sun je Asibiti da matarsa, ni na raka su,
aka ce za a yi mata inducing, bamu koma gida ba sai bayan ƙarfe goma na dare,
suka ajiyeni suka wuce gida a adaidaita sahun wani ɗan unguwarmu.
Viper bashi da wani wurin zuwa sai wurinmu, bashi da wasu
abokai sama da mu, tare muke shaye-shaye, irin abu ɗaya muke sha, dan haka
Viper baya cikin nutsuwar sa, bai yi shaye-shaye ba ranar, suna fargabar
inducing da za ayi wa matarsa".
"Malam shi mai shaye-shaye, kullum yana buƙatar samun
sauyi, da samun abin da zai bugar da shi, fiye da wanda yake amfani da shi, dan
haka zai iya yiwuwa ya samu wani abun bai sanar muku ba"
"DSP Nasir, ya sunan abin da Viper ya sha ne ya bugu ya
kashe matarsa?"
"Hodar iblis ce, aka haɗata da wasu sinadarai, kuma a
binciken da muka yi, an taɓa kama shi da cocaine a gidansa"
"Tayaya karabutin ɗan daba zai iya ta'amalli da cocaine
a ganshi a haka? Ina gwaje-gwajen likita da yayi, ya tabattar da cewar ya ga
cocaine a jinin Viper? Ko kuwa kawai da ka ake cewa ya sha cocaine?"
"Wanda kuke tuhuma, bai amsa cewar shi ya aikata ba,
kin san hakan dai-dai yake da baku da hujja"
Ɗan mama ya ce "Mu na da ita" gaba ɗaya suka kalle
shi.
"Ina daga cikin yaran madaki tsageru, Viper ya taɓa
illata ni, daga baya yayi mini nasiha, ya biya kuɗin da aka yi jinyata.
Kwangilar kisan Viper aka bawa su madaki, aka haɗa musu da
abin da suka kashe shi, saboda sun ce ba zai mutu ta daɗi ba, saboda yana da
ƙarfi sosai.
Da madaki, da lakwari, da wani ana ce masa ɗan fari, da
gulafa, su huɗu su ne suka je gidan Viper. Kuma saka su aka yi, wani ne ya saka
su".
"Waye wanin?"
"Ban sani ba, su za a tambaya, amma ina da hujja, duk
da ɗan fari an kashe shi, amma gulafa lagos ya gudu bayan an biya shi kuɗin
aikinsa"
Yan sandan suka ce "Ɗan mama ma ya shiga cikin suspect,
tun da a gabansa aka shirya komai, bai sanar da hukuma ba"
A take Viper ya rikice ya ce "Ba zai yiwu ba, babu
ruwan ɗan mama a cikin wannan maganar"
Ɗan mama ya ce "Oga Viper, kar ka damu, zan zama cikin
shaidu"
Liti ma rikicewa yayi, ya ce "Ɗan mama wane irin shirme
ne wannan kayi haka?"
Nabila ta ce "DSP, ba fa zaman kotu muka zo ba, bayar
da statement muka zo yi"
"Ɗan sanda baya wasa da duk wani abu da zai iya zama
hanya ce ta kama mai laifi, hanyar da kuka ɗauka ma, idan baki yi wasa ba, zata
sadar da ku zuwa ga baƙar duhuwa"
Ɗan mama ya ce zai yi magana da Nabila, yayi mata raɗa a
kunnnenta, hakan ya sanya ta yi ajiyar zuciya ta ce "Na fahimta sosai, in
sha Allah muke da nasara".
Sumayya kanta tayi mamakin yadda Nasir gaba ɗaya ya canza,
muraran ya fito da adawar da yake yi da Nabila. Ta sake keɓewa da barrister
Habib, suka yi rubuce-rubuce, suka gama bayar da statement, suka tashi suka
fita harabar wurin.
Hankalin Viper ya ƙi kwanciya, ganin an kama ɗan mama, sai
da Nabila tayi masa bayani, sannan ya ɗan samu nutsuwa.
Nabila na fitowa, Nasir ya sha gabanta ya ce "Ki zo ki
wuce mu tafi gida"
Nabila ta kalle shi ta ce "Wane gidan kuma?"
"Gida nawa ne da mu? Ko kin zaɓi Abba ya cigaba da
fushi da ke? Ki je wurin da ba wanda ya san in da ki ke? Abba ya iya yarda ki
tafi wurin da bai sani ba, ya ƙyale ki da halinki, hakan duk bai dame ki
ba?"
Nabila ta girgiza kai ta ce "Ko kaɗan, Abba baya fushi
da ni, zigar da kake yi masa ne da kai da mahaifiyarka, ya sanya ya ɗauki zafi,
amma na san yafi kowa fahimta ta, kuma zai fahimce ni. Kuma a barikin sojoji
nake zaune, duk lokacin da ka buƙaci ganina zaka ganni, daga nan wurin aiki za
a kai ni, barrister Habib sumayya, duk suna zuwa wurin da nake. Dan haka ka
daina aibata ni, da cigaba da danganta ni da mummunar ɗabi'a, dan na san abin
da ka ke yinƙurin yi kenan".
Viper ya ƙaraso in da suke tsaye, ya ce "Ga abokin
aikinki nan, zaki iya bin sa ki je office, in sha Allah you are safe"
Ta jinjina masa kai ta ce "Zamu je mu ga ramma ma, daga
nan na ji ina aka tsaya da batun kama mutumin nan, amma yakamata ka je ku gaisa
da ita, kaga yarinyar ma, tun da kai yaya ne a wurinta, a yan uwanta babu wani
wanda yake zuwa wurinta"
Viper ya ɗan gyaɗa kai ya sakar mata wani irin murmushi ya
ce "Zan je in sha Allah, tun da ke ce lauyata, kuma lauyar su, abin da ki
ka ce ai shi nake yi ko?" Sai da Nabila ta tsaya tana kallonsa, cikin
mamaki.
Ya sake cewa "zaki iya tafiya, take care, my only
hope" yayi maganar yana cigaba da yi mata murmushi, Nasir kuma ya sandare
a wurin kamar katako.
Nabila ta ce "To daga nan ina zaka je? Kar ka yi wani
wurin"
"Za a zo a ɗauke ni, ki tafi kawai tare da su Walid
zamu tafi".
Cikin damuwa ta ce "Kar na tafi fa su kama ka".
"Babu hannun da zai iya kama wannan ƙarfen ba, ku tafi
kawai" Nabila ta tafi tana waiwayensa.
Tsananin mamaki ya kama Nasir, kenan Nabila son mutumin nan
take yi, abin da ya gani a idonta, tsantsar soyayya ce.
Ya tsura mata ido, har ta shiga mota, ita da sunayya su ka
bar wurin, murtala ya hau babur ɗin sa ya tafi, Viper mayar da idanunsa kan
Nasir ya ce "Malam, akwai mutanen da suke ajiyar Allah ne, duk tsanar nan
da ka yi mini, na riga na fi ƙarfinka, babu yadda zaka yi da ni, takura mata da
hura mata wuta a kaina, da ƙuntata mata a kaina, ba zai haifar maka da komai
ba, sai zunzurutun ƙiyayyarka a wurinta. Ka san meyasa dalili biyu ne, a yanzu
a wannan duniyar da nake ciki tafi kowa sanin waye ni, kuma babu wani abu da
take tausayi kamar ni, kuma ka san menene ma'anar tausayi a wurin mace. Abu na
biyu kuma wannan, mussaman saboda na haɗu da kai na baka, na cigaba da yawo da
shi".
Ya zaro envelope daga aljihunsa, ya ce "Na bata saƙo,
ta kai muku gida, kun yi burus da ita, kun yi mata furucin ta je ta nemi
mahaifinta, na gaya maka na fiku buƙatar ta, kuma lokaci yayi da zan biyata
ladan aikin da tayi mini, ko kun shirya hakan ko baku shirya ba, dan haka
shawara ta rage ga mai shiga rijiya".
Ya danƙawa Nasir envelope ɗin ya ce "Gashi nan, mu haɗu
a zama na gaba, ko kotu, ko a mafitar makomar Nabila" ya juya ya nufi in
da su Walid suke.
Nasir ya rasa meyasa baya iya kataɓus idan yana gaban Viper,
yayi ta ci masa mutunci yana tsaye yana kallon sa.
Liti kamar yayi kuka, ya ce "Ɗan mama, ɗan kut......
Saboda hauka da yarinta, ya ja an kama shi, uban waye ya gaya masa zaman wurin
nan lafiya ne? Allah kaɗai ya san izayar da zasu yi masa, yanzu za a haɗa shi
da masu kisan kai, na jakai zasu din ga naɗa masa wallahi wawa kawai"
Viper ya ce "Mu tafi"
"Mu tafi ina mu bar wannan banzan?"
Walid ya ce "ashe dai kana son sa?"
"Ba wai son sa nake yi ba, tausaya masa kawai nake yi,
gaba ɗaya gaɓo ne"
Viper ya dafa kafaɗar liti ya ce "Duk cikin plan ne, ka
kwantar da hankalinka, ba abin da zai same shi in sha Allah"
***
Sumayya suna tafe a hanya, suna hira da Nabila, ta ce
"Subhanallah, Nabila kin ga wata ƙira ta manya, ga mulki wai kuma ɗan
daba, gaskiya ya ci sunansa Viper, bala'i"
"Ya maganar mahaifinsa da ki ka yi mini?"
"Na gaya masa saƙonki ai"
Nabila ta ce "Idan mun gama da wurin su ramma, zan
ganshi"
Sumayya ta ce "Da gaske, zaki haɗa shi da
Vipern?".
Nabila ta ce "Eh, zan haɗa su, zan yi uniting uba da ɗa,
ko me hakan zai janyo kuwa"
"Kina nufin akwai matsala kenan?"
Nabila ta ce "A'a karki damu"
Da hanzari Ramma ta ƙarasa suka rungume juna da Nabila,
Nabila ta ce "Rahama, barka da arziki ban samu na zo na duba ki ba"
"Bakomai Anty, na gode sosai da sosai Allah ya saka
miki da alkhairi"
Nabila suka gaisa da maman ramma, ta ce "Rahama ga
masoyiyyar ku, Sumayya T ladan"
Ramma ta ce "Anty sumayya ya aiki?"
Sumayya ta ce "Alhamdilillah, ya fargaba kuma, Allah ya
kiyaye gaba"
Maman ramma suka gaisa da barrister Habib ma, tana tayi masa
godiya, ta ɗaukko wa Nabila takarda, an yi stapling ɗin ta, ta ce "Gashi
aka kawo, tasatasan da aka yi wa ramma ne, da aka ɗebi jininta, bayan an
kawota, aka ce kar a buɗe ke za a bawa, tun da ke ce lauyanta"
Nabila ta karɓa ta na faɗin "Ai yana daf da zuwa hannu,
mun gama sbirya komai ta buɗe takardar tana dubawa, komai na ramma lafiya
ƙalau, sai dai ga tes ɗin ciki ya fito rangaɗau".
"Ina fatan babu matsala dai ko? Babu ƙanjamau ko wani
abu?"
Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Eh komai lafiya, amma
rahama ɗan zo mana"
Ramma ta tashi suka koma gefe, ta kalli ramma ta ce
"Rahama kin san kina da juna biyu?"
Ramma ta jinjina kai alamar eh.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un"
"Dan Allah anty kar ki gaya wa mama"
"Rahama dole a mata, dole ta sani fa"
Cikin kuka ramma ta ce "Dan Allah ki rufa mini
asiri"
Ta kamo hannun ramma suka dawo falon, ta kalli mahaifiyar
ramma ta ce "Maman ramma, da gaske kin tabattar ya aureta?"
Jiki a sanyaye ta ce "Haka wan babanta ya gaya mini,
meyafaru?"
"Akwai matsala, sakamakon nan ya nuna akwai ciki
fa"
Sosai Nasir yake gudu, cikin matsanancin tashin hankali,
ganin hoton da Viper ya bashi, hotonsa shi da jauhar.
Ko rufe motar bai yi ba, ya fita ya faɗa cikin gida.
Sai da Abba baya nan, ya din ga kallon hoton, cikin fargaba,
kenan wannan ce ake dambarwa a kan kisanta? Saboda yanayin yadda suka yi hoton,
ya tabattar da mata da miji ne. Lallai akwai gagarumar matsala.
"Wai wannan wane irin mutum ne? Kenan ya san komai,
shiyasa yake ziga Nabila? Akwai Matsala......
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
Nasir ya cigaba da jujjuya hoton, ya fita ya tafi sashen
mama, ya tarar da ita tana cin abinci, amma ya rasa me zai ce mata.
"Lafiyarka kuwa?"
"Eh lafiya ƙalau, shigowa nayi kawai mu gaisa"
"Kuma sai na ganka a haka kamar mara gaskiya, gaisawar
da muka yi da safe fa?. Amm ya ake ciki ne? Ka haɗu da ita ɗin?"
Ya jinjina kai ya ce "Eh mama, mun haɗu ƙarewar rashin
kunya, tare suka je da gayen"
"Hmm ai na sha gaya wa mahaifinku, gurbin ido ba ido
bane ba, ai yanzu gashi nan ya fara gani. Ni dai ka yi iya yinka kar yarinyar
nan tayi galaba a kan ka"
Ya jinjina mata kai kawai ya fita.
Wiwi ramma take kuka, mamanta ta ce "Ramma, kin
munafunce ni, na ce miki babu abin da yaron nan yayi miki, ki ka ce mini eh,
amma kawai sai na tsince ki da ciki? Baki kyauta mini ba"
Ramma cikin kuka ta ce "Dan Allah mama ki yi haƙuri,
bana son ki shiga damuwa ne"
Barrister Habib ya ce "Hajiya, ina ga mu bi komai a
hankali, Nabila menene watannin cikin, kuma kwana nawa da ɗaura musu aure, tun
da an ce ai lokacin da ya saceta da ciki, ya ci ace zuwa yanzu ta haihu.
Ramma tayi wiƙi-wiƙi da ido tana kuka.
"Kiyi magana dan ubanki"
Nabila ta ce "Yi mata a hankali, rahama meyafaru da
wancan cikin?"
Ramma ta kasa magana, ta cigaba da kallon mahaifiyarta da ta
hasala.
Nabila ta yi ta rarrashinta, amma taƙi magana fafur.
Sumayya ta ce "Nabila, ku bi a hankali, zata yi magana,
amma yanzu yakamata a rabu da ita, zuwa lokacin da zata samu nutsuwa tayi
magana"
Maman ramma ta ce "Har zuwa yaushe kenan, dan girman
Allah ku yi mini rai a cire cikin nan"
Barrister Habib ya ce "Haba Hajiya, baki bari an cire
na farko ba sai wannan, dan Allah kar ki takura mata, ki ce sai ta yi miki
bayani ko makamancin haka, ki yi haƙuri"
Maman ramma ta dafe fuskarta tana hawaye, ta ce wannan wace
irin wulaƙantacciyar rayuwa ce, an cutar da ni an wulaƙanta iyalina"
Nabila ta ce "Mama jarrabawa ce, kowa da yadda Allah ya
tsara masa, muddin muka taɓa cikin nan, zamu iya shiga matsala, tun da da
izinin wakilinta ya aureta, babbar damuwar mu a nan shi ne, ayi masa hukuncin
abin da ya aikata mata, amma ki yi haƙuri dan Allah"
Nabila ta cigaba da rarrashin ta, tare da taimakon su
sumayya.
Sai da suka gama da mahaifiyar ramma sannan suka fito, suna
ta jajanta lamarin, Sumayya ta ce zata tafi gida, Barrister Habib kuma zai
mayar da Nabila, Nabila ta ce "Sumy, ki turo mini lambar mahaifin Viper
please"
Sumayya ta ce "Ok, amma ni haryanzu baki gaya mini
tayaya ki samu alaƙa da matarsa ba"
Nabila ta girgiza kai ta ce "Ai ni yanzu na daina
dagewa lallai idan na faɗi abu sai an yadda da ni, lokaci zai warware
komai"
"Shikenan, ba zan matsa miki ba, zamu gani, amma Nabila
nayi mamakin ganin Viper, lallai ya ci sunansa Viper, wallahi na zata zan ga
wani karabutin mutum kawai, kalleshi masha Allah, lallai wannan su suke yin
dabar gaske"
Nabila ta ce "Malama ya daina daba fa, ki daina zancen
dabar nan Please, ya tuba"
Sumayya tayi murmushi ta ce "Allah ya baku haƙuri, sai
mun yi magana"
"Ok, bye" suka yi sallama.
****
Sannu a hankali ta cigbaa da zaro kwalaban maganin tari, da
satchet ɗin magungunan mura a ƙarƙashin gadonsa, kwalabe sun kusa ashirin,
jikinta sai tsuma yake yi.
Da kyar ta iya amsa sallamar da Shahida take yi a tsakar
gida, ta fito jiki a sanyaye tamkar munafuka.
"Mama ya dai? Na ganki kamar a tsorace meyake faruwa
ne?"
Alama ta yi wa shahida da hannu da ta shigo, ta ƙarasa cikin
ɗakin Abba, ta nuna mata tulin kwalaben maganin tari masau hatsarin gaske.
Shahida ta dafe kai ta ce "Mama kin gani ko? Na daɗe
ina gaya miki amma kin ƙi yarda"
Rahila ta ce "Duk laifin babanku ne, tun da ya kore shi
daga kasuwa shi da Nazifi, ya rasa abin yi ya shiga wani hali, ni da nake ta
fatan nayi masa aure"
"Mama Abbu fa ba shi da laifi, yayi iya ƙoƙarin sa a
kansa, ya zai zauna da su, suna cutarsa"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na shiga uku ni
Rahila"
"Ina Amira ne?"
Tamkar ta fashe da kuka ta ce "Amira yau kwananta biyu
bata gidan nan, ban san in da take ba, na yi wa babanku ƙaryar tana gidan Yaya,
Shahida na shiga uku"
Jiki a sanyaye ta ce "Mama baki shiga uku ba, ni fa
daga kotu nake, na kai Anwar ƙara ya sauwwaƙe mini, ba zan iya ba na gaji"
A razane ta ce "Ya sauwwaƙe miki? Shahida baki da hankali, a wannan
ƙadamin da ake ciki zaki kaso aurenki, ya ki ke so nayi, sai duniya tayi mini
dariya?"
"Mama, kin kasa gane in da na dosa, wai so ki ke sai na
halaka ne, saboda kawai yana da kuɗi, nayi haƙuri fa iya haƙuri, ke fa uwata
ce, haƙurina ya ƙare, Allah da zan iya tunkarar Abba, da sai na tunkare shi na
sanar masa".
"Shahida uban naki zaki tunkara da wannan maganar?
Saboda baki da kumya?"
Cikin tsiwa ta ce "Idan ba irin Amira ki ke so na zama
ba ki ƙyale ni dan Allah"
Rahila ta kwantar da murya ta ce "Ki rufa mini asiri
Shahida, shi wannan ya fara shaye-shaye, waccan bin maza, shi Nazifi ya gudu
kudu neman kuɗi, ban ma san a duniyar da yake ba, ke kaɗai ce a ɗakin aure nake
jin daɗi, kar ki gurguɗe auren nan, ki ƙara tona mini asiri, ba ya ce miki yana
neman magani ba? Baki san me Allah ya ɓoye a lamarin nan ba, ga tarin dukiya
yana da ita, sai ki ga ke kin haihu da shi, ki haifi namiji, wannan dukiyar ta
zama tamu"
Ta kalli Rahila cikin takaici ta ce "Na haihu ta yaya,
mama shekara uku fa, wane irin magani ya kasa nema a kan sauran matan da ya
rabu da su? Ashe aurensa tara ni ce ta goma ya ɓoye mana, ga shaye-shaye ga cin
mutunci har da duka wasu lokutan, wallahi ba za a kashe ni da raina ba, gara na
auri talakan tulus in samu nutsuwa da kwanciyar hankali" Rahila ta ɗora
hannu a ka, ta din ga kurma ihu, tana kukaz Shahida ko a jikinta, ta tashi ta
shige ɗaki ta bar ta.
***
Abin duniya duk ya damu liti, da yayi juyi ya ga babu ɗan
mama sai yayi ta tsaki, da daddare ma kasa bacci yayi, sai tsaki yake yi.
Walid ya ce "Sarkin gida"
"Mai laya"
Walid ya ce "Wai ya ne?"
"Wallahi tunanin yaron nan nake yi, Allah ya sa ba suna
can suna jibgarsa ba, ka san ba imani ne da su ba, kuma ga sauron wurin
nan"
Walid ya yi dariya ya ce "Allah liti, kai ne kake
tunanin halin da ɗan mama yake ciki? Dama ka damu da shi har haka?"
Liti yayi tsaki ya ce "Wallahi ban san ya aka yi ya
shiga raina haka ba, ka san ya iya ladabin makirci, wallahi da ya dawo wurinmu,
rashin Nura ya sanya nake yin sa"
Viper ya yi gyaran murya ya ce "Ka yi haƙuri duk
laifina ne, amma in sha Allah ba zai wulaƙanta ba zai fito"
"Idan ma cewa kayi ba zai fito ba, ya tafi kenan
dai-dai ne Ogana"
Viper ya ce "Zai ma fito, ni kaina nayi mamakin yadda
ya shiga raina, Allah sarki ɗan uwana Nura, Allah ya sanyaya makwancinsu da shi
da mahaifiyata, da Sadik, da uban gidana dodo, da kuma matata a bar ƙaunata, da
dukkanin wanda muka rasa" suka amsa masa da Amin.
Liti dai bacci gagararsa yayi, sai tsaki ya din ga yi yana
juyi.
Gidan da Nabila take, aka gabatar mata da wata macen soja, a
matsayin mamallakiyar gidan, ba ta gari ne ya sanya Nabila take zaune a gidan
tare da masu aikinta.
Nabila ta zata zata ga matar masifaffiya, kasancewar an ce
soja ce, amma taga ba haka ba, tana da matuƙar kirki da sauƙin kai.
Nabila ta din ga jujjuya lambar mahaifin Viper tana son ta
kira, amma tana tsoron tijarar Viper, kasancewar ya gargaɗeta a kan haka, tana
cikin tunanin, sai ga kiran Viper sai da ta kusa katsewa ta ɗaga ta ce
"SPY"
"Idan ki ka sake suka ji abin da ki ke faɗa, zasu iya
kashe ki, ban da ogana da ya zo wurnki da su Walid, babu wanda ya san kin san
ni waye"
"Yanzu har su Oga Walid basu sani ba"
Ya ce "Mmmm"
"Taɓ, sannu"
"Yauwwa, ya rahama da mamanta? Ina son zuwa da gaske
kamar yadda ki ka ce, na ga halin da suke ciki"
Nabila ta ce "Akwai matsala, ciki ne fa da rahama"
"What ciki ta yaya?"
"Ya za ayi in sani, ciki dai, maman hankalinta ya tashi
sosai da sosai, ta ce sai an zubar, wallahi na rasa yadda zan yi, gashi ta ƙi
magana rahaman, muna son mu ji, kafin ya aureta cikin ya samu ko bayan ya
aureta, amma na fi kyautata zaton bayan auren ta samu cikin, duk da bamu san
meyafaru da wancan cikin ba da ta samu bayan ya mata fyaɗe"
Viper ya haɗiye takaici, ya tsani ya ga an ci zarafin mace,
mussaman mahaifiyar ramma da aka watsa mata yara gaba ɗaya babu wani wanda ta
amfana an watsa rayuwar su, kuma abin mamakin uba da ɗa ne suka lalata mata
rayuwar yara"
"Bani adress ɗin in da suke zan je" yayi maganar a
kausashe cikin damuwa.
"Ka bari muje tare, ina ga idan rahaman ta ganmu tare,
ta yi magana, kayi haƙuri na san ranka a ɓace yake, amma babu yadda muka iya da
ƙaddara" yayi shiru yana huci.
A raunane ta ce "Viper"
"Mmmm"
"Idan na mutu baka sadani da mahaifin jauhar ba, wanda
nake kyautata zaton ina da alaƙa da ita ba, ba zan yafe maka ba"
Dummm haka ya ji maganar Nabila ta dira a tsakiyar
zuciyarsa.
Viper "Kin san me ki ke faɗa kuwa? Ta ina ki ke da
alaƙa da jauhar?"
Tuni ta fara kuka ta ce "Abubuwa da yawa, na fara
sarewa, tun kan na ganka nake mafarkinka, bayan ban sanka ba, ban taɓa ganinka
ba, ina da ciwon Athma da take gada nayi daga mahaifiyata, ita ce take da
ciwon, familyn su na Jalingo da yawansu, Asma ciwonsu ne, ita ma ka ce ciwonta
ne. Akwai abubuwa da dama, ba zan ɓoye maka ba, Wallahi idan Allah ya karɓi
rayuwata baka sada ni na mahaifina ba, ba zan yafe maka ba" ta ƙarasa
maganar tare da kashe wayarta.
***
Abba ya kalli Nasir ya ce "Nasiru, ya aka yi ne, an ce
tun ɗazu ka ke nemana, na je wani wuri ne, ya aka yi?"
"Na haɗu da Arfa"
Abba ya ɗan yi sak, sannan ya ce "Tana lafiya" ya
jinjina masa kai alamar eh.
"Haryanzu ba ta yi regreting abin da tayi ba kenan,
shirun da nayi mata da zuru duk bata saduda ba kenan?"
"Babu alama, tare da ɗan daban suka je CID jiya"
"What? Aka ce mini tana barrack wurin yarinyar nan
Halima goza, ina sane da duk halin da take ciki ai"
Nasir ya ce "Tare dai na gansu, tare da wasu 'yan daban
ma, da sumayya"
Abba ya yi shiru cikin takaici, wai 'yan daba.
"Nabila ba ta da hankali, kuma bana tunanin zata yi
shi, zan je na taho da ita, duk wadda za ayi sai dai ayi, basarwa kawai nake
yi, amma hankalina yana kanta"
"Abba" ya kalli Nasir.
"A harabar wurin, ga abin da shi wanda take karewar ya
bani"ya miƙawa Abba envelope.
Cikin matsananciyar faɗuwar gaba, ya kalli Nasir ya ce
"Hoton da ta kawo mini wancan karon dama ba Photoshop bane?, Har na fara
tunanin waye ya gaya mata wani abu"
"Abba ka san babu wanda ya isa yayi fatali da umarninka
a cikin gidan nan"
Muryar Abba har rawa take ya ce "Shi wannan ɗin waye a
jikin hoton?"
"Shi ne gayen, matarsa ce, ita ce ake shari'ar a kanta
ai, ake zargin ya kasheta"
A zabure Abba ya tashi tsaye jikinsa yana rawa ya ce
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, kuma Nabila saboda mahaukaciya ce, ta
tsaya masa take fafutukar a wanke shi, Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
Nasir kira mini Nabila a waya yanzun nan".
Nasir ya ciro wayarsa daga aljihunsa, ya kira lambar Nabila,
amma line busy.
Ya ce "Abba line busy" Abba jikinsa na ta ɓari, ya
ciro ta sa wayar, ya jefawa Nasir, ya ce "Kira ta maza" sai dai tun
tana cewa line busy, aka ce wayar a kashe take.
"Abba ta kashe wayar"
"Nasiru, tashi ka ɗaukko mota mu tafi barrack"
"Abba a daren nan, wajen gari ne wurin"
"Ka tashi na ce!" Yayi maganar cikin tsawa.
"Abba dan girman Allah kayi haƙuri, ka san ba zasu bari
mu shiga yanzu ba, dan Allah ka yi haƙuri sai Allah ya kaimu gobe da wuri sai
mu tafi.
Anty da ta fara bacci, a bedroom ɗin Abba ta fito ta ce
"Major lafiya kake ɗaga murya a daren nan?"
Nasir ya ce "Bakomai"
Har Abba zai bar falon, ya dawo ya nuna wa Nasir hoton ya ce
"Waye wannan ɗin ne wai?"
Nasir ya ce "Abba, na ce maka shi ne ɗan daban da nake
nema, aka ce na kama, yarinyar jiki ya kashe.... Abba ya ɗaga masa hannu ya
dakatar da shi, ya shige ɗaya ɗakin nasa ya kulle ƙofa.
"Nasir meyake faruwa ne?" Anty ta sake tambayar
Nasir cikin damuwa.
"Bakomai"ya sake bata amsa a taƙaice ya fice.
Abba ya ɗaukko wani hoto tun Black and white, da hoton wata
matashiyar budurwa a jikin bukka ta buɗe haƙora tana dariya, aka yi mata hoton.
Ya haɗa da hoton da Nasir ya bashi, gabansa ya tsananta faɗuwa
ya ce "Anya ban tafka kuskure ba kuwa? Hukuncin da na yanke bai yi muni
ba? Kana naka Allah ya na nasa. Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na yanke
hukunci cikin fushi, bayan shekaru Allah ya jujjuya ƙaddara yadda yake so, ki
yafe mini mairamu" yayi maganar cikin matsanancin rauni.
Kwana Abba yayi a zaune, yadda ya ga rana haka ya ga dare,
cikin tashin hankali da rashin sanin abin yi, ya din ga jinjina girma da
ƙudurar Ubangiji.
***
Sojar nan sai mita take yi wa Nabila, ta ƙi sakin jiki ta
karya.
Ƙarfe bakwai da rabi, Viper ya je gidan, suka gaisa da
Madam, ya ce "Nabila ta shirya, za su fita"
Madam Goza ta ce "Ka karɓo permisson ne?"
"Eh sun sani, wurin aiki zata je, muna ta shirin shiga
court"
Ta jinjina kai ta ce "Best of luck"
Ya amsa da thank you.
A wata haɗaɗiyar mota helux mai fentin sojoji, aka ɗauke su.
Da ƙyar Nabila ta iya ce masa "Ina kwana"
Shiru yayi bai amsa ba, ita ma ta ja bakinta ta tsuke.
Gaba ɗaya fuskarta mamaye da damuwa, kamar ma ba ta samu
isasshen bacci ba.
"Meyasa ki ce ba zaki yafe ba, idan ban haɗaki da
iyayen jauhar ba, Allah ya isa fa ki ka yi mini kenan"
Cikin rauni ta ce "Ya ka ke so na yi, ka ƙi fahimta ta,
Allah ke da yau da gobe, balle ka ce akwai lokacin da ka zaɓa, ka nuna mini
iyayenta".
Ya numfsa ya ce "Kalmar tayi mini nauyi sosai, kasa
bacci nayi" ta yi masa shiru, tana kallon window tana share hawayenta.
Ya kamo hannunta ɗaya, ta kalleshi da sauri, ta fara ƙoƙarin
ƙwace hannunta.
"Ki daina kuka, jauhar ɗina nake gani, kar nayi ɓarna
dan Allah"
"Cika ni, ni ba ita ba ce, ni maganin kukana
Allah"
Ko a jikinsa ya ce "Kar ki ce zaki yi kishi da ita,
wahala zaki sha"
Shiru ta sake yi masa, tana duba wayarta.
Nasir ya turo mata message "Ki ɗaga wayata, zamu zo ni
da Abba" kasje wayarta tayi, saboda a jikinta ta ji Nasir ƙarya yake yi.
****
A rikice maman ramma ta tashi, ganin Nabila tare da Viper,
ta nufe shi da sauri ta fashe da kuka.
Riƙeta yayi, jikinsa a sanyaye yana tuno Nura guduma, ya ɗagota
yana share mata hawaye ya ce "Mama, ki daina kuka dan Allah, na san ni mai
laufi ne, rabona da ke na daɗe, amma ƙaddara ce ta janyo duk hakan".
Cikin kuka ta ce "Murnar ganinka nake yi Aminu, ashe
zan sake ganinka? Ni da Hajiya mun zo wurinka sau uku, tun daga ƙauye amma ba a
bari mu ganka, Allah bai ƙaddara zaku sake ganawa da ita ba"
Aminu ya ce "Allah sarki, ki yi haƙuri ke gashi Allah
ya ƙaddara ganawarmu ai" yayi maganar yana zaunar da ita a kan kujera.
Nabila ta gaisheta, ta amsa tana kallon Nabila tana kallon
Viper, gashi an hanata magana.
"Jauhar a ina ki ka gano shi? Ya aka yi ki ka san muna
da alaƙa da shi?"
Viper ya ce "Nabila ce wannan, ita ce lauyar da zata
tsaya mini nima, kuma take ta ƙoƙari a kan shari'ar rahama. Komai da ake ciki
tana gaya mini, ina son na zo na ganki na gaishe ki, amma kin san jami'an tsaro
nemana suke yi, kuma ina tsoron ki yi mini kallon ɗan ta'adda da ya kashe
matarsa"
Cikin ɗaurewar kai ta ce "Wai ni fa na rikice, tayaya
Jauhar ta koma Nabila kuma?"
Viper ya ce "Zancen dogo ne, yanzu mu fara gamawa da
batun rahama" yana maganar ramma ta fito cikin hijjabi.
Mammaki ne ya kama shi, har ya tafi prison yarinya ce ƙarama
sosai, amma yanzu ta zama wata uwar mata, tayi ƙiba, tayi haske sosai.
Cikin matsanancin tsoro, ta gaida Viper, ita gaba ɗaya taoro
yake bata tun lokacin da ta taɓa ganinsa a asibiti da kuma lokacin da ya zo
gidansu"
Viper ya yi mata alama da ta zo.
Ta ƙarasa gefe kusa da Nabila ta zauna.
"Maganar me ake so ki yi ki ka ƙi yi? Sai kin yi magana
za a iya ƙwatar miki hakkinki"
Jiki na rawa Ramma ta kalleshi, amma ta yi shiru. Tsura mata
ido yayi ba tare da yayi magana ba, babu shiri ta fara bayani tiryan-tiryan.
Nabila ta ce "Taɓɗijan, wannan case ɗin akwai
sarƙaƙiya, cikin jikinta na halal ne ai"
Maman ramma ta ce "Dan girman Allah ku taimake ni a
zubar da cikin nan, yaron nan ba shi da tarbiyya ko kaɗan, babu ɗan da zai yi
alfahari da shi a matsayin uba, ni dai bana buƙatar sa".
Viper ya ce "Na goyi bayan haka, yakamata ta koma
makaranta ne, ta fuskanci rayuwarta da ƙalubalen rayuwa"
Ramma ta fashe da kuka, Nabila ta ce "A'a dan Allah ku
yi haƙuri, laifi ne na kisan kai, ko kin yadda a zubar?" Tayi maganar tana
kallon ramma.
Ramma ta girgiza kai ta ce "Mama dan Allah ki yi
haƙuri, nayi masa alƙawarin ko an kama shi, ba zan zubar da cikin ba, dan Allah
ki bari na haihu, ya ce mini mutuwa ake yi idan aka zubar da ciki" tayi
maganar cike da yarinta da wauta.
Salati suka hau yi, Viper kawai ya jinjina kai.
Ya tashi ya ƙarasa gaban Ramma, ta sake takurewa gabanta na
tsananta faɗuwa.
Ya ce "Kin san yayanki Nura ko da ya mutu?" Ta
jinjina masa kai alamar eh.
"Baban wannan mutumin da yayi raping ɗin ki, ya ci
mutuncin ki, shi ne ya yi sanadiyar mutuwar sa, bayan ya yi masa fyaɗe ta wurin
bayan gidansa, idan kin zaɓi ki rufa masa asiri ba zaki bayar da haɗin kai ayi
abin da ya dace ba, ba kanki kawai ki ka cutar ba, har da marigayi ɗan
uwanki"
Toshe baki ramma tayi, tana bin Viper da kallo, jin maganar
tasa kamar almara, sai yanzu wasu abubuwan suka din ga dawo mata.
Nabila ta ce "Vi da ka sani baka gaya mata a haka
ba"
"Muddin aka tafi a haka, zata baki kunya a wurin
Shari'a, alamu sun nuna zata iya ruf masa asiri"
Ya kalli maman ya ce "Mama, zamu tafi, akwai uzururruka
da zamu yi amma zan dawo, ki yi haƙuri, na san na fama mana wani ciwo mai wuyar
warkewa.
Ta jinjina masa kai ta ce "Gara da ka yi mata hakan, na
gode Aminu, Allah ya kula da kai ya tsare mana kai. Kema Allah ya rufa miki
asiri duniya da lahira". Tayi maganar tana kallon Nabila, bakinta fal
maganganu, da tambayoyi, sai dai gargaɗin da aka yi mata ya hanata tambayar,
amma har a wannan lokacin zuciyarta na bugawa cikin tsananin tashin hankali da
mamaki, a duk lokacin da ta ga Nabila, mussaman a yanzu da ta gansu tare da
Al'amin, kuma ya ce mata ba Jauhar ba ce.
****
Abdul yana tare da su Salim, ya sha ya bugu yayi mankas, dan
abin da yake yi kenan ya samu sassauci, gaba ɗaya nema yake ya haukace saboda
rashin sanin in da ramma take.
Salim ya miƙe yana ƙoƙarin kama shi su tafi, kawai suka ga
an kewaye su, wasu mutane sanye da kaya personal.
Ba su yi musu wani dogon jawabi ba, suka kama su gaba ɗaya
suka tafi da su.
Indabo yana Abuja, zuwa kano ya gagare shi, duk da zaman
Abujan ba daɗi yake yi masa ba, kotu ta yi seazing ɗin passport ɗin sa, babu
damar fita ƙasashen waje, har sai an kammala bincike, kwamiti biyun da aka
kafa, na binciken kuɗaɗen da aka karkatar, duk sunansa ya fito a ciki, ga kuma
tuhuma daga ɓangaren EFCC.
Gefe guda kuma, a Kano mutanen yankinsa na shirin yin abin
da ba a taɓa yi ba a Nigeria, shi ne yi masa kiranye, ya dawo daga Abuja ba su
gamsu da wakilcin da yake yi musu ba, ya rasa wane tunani yakamata ya yi, wace
mafitar yakamata ya fara nema.
Ana tsaka da haka aka kira shi a waya, aka sanar da shi an
kama Abdul, ba a ma san wace police station ɗin aka kai shi ba, abokansa ne
suka sanar da kama shi.
Hakan ya ƙara gigita shi, da tayar masa da hankali, ya fara
shirin tahowa Kano.
****
An so a kai ruwa rana kafin a bawa Abba damar ganin Nabila,
sai dai kasancewar shi ma retired solder ne, aka bashi damar hakan. Sai dai
suka tarar da Nabila bata nan. Gaba ɗaya Abba ya rikice, ya din ga faɗa ya ce
"Shi ba haka aka yi masa bayani ba, an ce za a riƙe masa 'ya ƙarƙashin
kulawar hukuma, dan me zai zo ace bata nan"
"Sir, bawa yarinyar nan kariya baya nufin mu yi ta ɓoyeta,
akwai ayyukanta da take gabatarwa na aikinta. Sun fita an yi mata rakiya zuwa
wurin gudanar da aikinta, rayuwarta na cikin haɗari ne".
"Rayuwarta na cikin haɗari, sai a kauwwameta a cikin
barrack ma tukuna, ba 'yan sanda ne yakamata su bata kariyar ba ma, menene haɗinta
da ku kuma?"
"Akwai dalili mai girma, da ba zamu iya gaya maka ba
sir"
Ya sake kallon Nasir, ya ce "Kira mini ita"
Nasir ya sake kiran wayar Nabila, wayar na hannun Viper,
Nabila kuma ta shiga cikin ma'aikatar Shari'a tare da barrister Habib.
Ɗaga wayar ya yi ya saka a kunnensa "Arfa, tun jiya ake
kiranki a waya kin ƙi ɗagawa, Abba yana son ganinki lallai kina ina
yanzu?"
Kai tsaye Viper ya ce "Na tafi kaita wurin
mahaifinta"
A sukwane Abba ya kalle shi, saboda a hansfree wayar take,
ya ce "Waye wannan?" Abba ya karɓe wayar jikinsa na tsuma ya ce
"Who are you, waye ya baka wannan damar? Kana ina? Ina 'ya ta?"
Cikin girmamawa Viper ya ce "Am sorry sir, wannan
alƙawari ne da nayi wa Nabila, a matsayin hakkinta na aikin da tayi mini. Na
baku damar sanar da ita komai, saboda ban san dalilinku ba, amma ka bata damar
ta je ta nemi mahaifinta.
Nima ina buƙatar sanin, menene alaƙarta da matata".
"Stop it, kar ka kuskura ka kai Nabila wurin wannan
mutumin"
"Am very sorry sir"
Cikin tashin hankali Abba ya ce "Ku san yadda zaku yi,
ku dakatar da mutumin nan, ku gaya mini in da yake ya dawo mini da ya ta, bamu
yi da ku ku bari tana yawo da yan daba a gari ba.
Viper ya tsurawa Nabila ido, tana nufo motar, ta ƙaraso ta
buɗe motar tana yi masa magana.
"Lafiya kake kallona haka?"
"Shigo muje wani wuri, zamu ɗauki su Walid mu
tafi"
Jiki a sanyaye ta ce "Ina?"
"Zaki gani" ta ce "To"
Ta shiga motar ta zauna, hakanan sai ta ji jikinta yayi
sanyi, kamar an zare mata laka.
A ransa ya ce "Yau komai zai zo ƙarshe in sha
Allah"
Indabo ne a hukumar yansandan farin kaya, kamar zararre,
yana ta masifa da tambayar ba'asin menene dalilin da ya sanya aka kama masa ɗa.
Da ƙyar aka lallaɓe shi ya zauna, "Honorable, ana
zargin ɗanka da aikata laifin fyaɗe, tare da ɓoye yarinya ba da sahalewar
iyayenta ba, sannan bayan mun kama shi, mun same shi da miyagun ƙwayoyi ciki
har da waɗanda aka haramta shigowa da su ƙasar nan, wanda ta'amalli da su
babban laifi ne"
"Wannan duk ƙage ne da yarfe da son ɓata mini suna da
siyasata, sharri aka yi masa, bai aikata ba, ku sakar mini ɗa kawai"
"Distinguish senator, kai babban mutum ne a ƙasar nan,
kar mu yi ta jayayya da kai dan Allah. Duk wasu shaidu da hujjoji da ake buƙata
muna da su, shi ya aikata laifin, dan haka kotu ce take da damar wanke shi ko
kuma hukunta shi, kayi haƙuri aikinmu muke yi.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
"Ban gane aikinku ku ke yi ba, wane irin aiki ne babu
evidence, kawai ku kama mutum ku rufe shi?"
"Distinguish, na sanar maka yaron nan fa muna da
evidence a kansa, ciki har da videon da CCTV camera ta ɗauka, lokacin da yaje
gidan, dan haka musu ba naka bane ba. Babbar shawarar da zan baka bai wuce ka
je ka nema masa manyan lauyoyi da zasu tsaya masa ba" gaba ɗaya jikin
Indabo yayi sanyi ƙalau, cikin mamaki da tsantsar tashin hankali ya ce "Ka
ce kana da videonsa lokacin da ya shiga gidan?"
"Ƙwarai kuwa, da cikakkiyar hujja da aka bamu muka kama
shi, kuma wadda ya aikatawa abin, tana tare da hukuma, kuma ta tabattar da
hakan da bakinta, dan haka zamu gurfanar da shi a gaban kotu kamar yadda kotun
ta buƙata"
Indabo ya cire hular kansa da ya ji gumi na barazanar ture
ta daga kansa, ya shafi shimfiɗaɗen sanƙon da gwagwarmaya ta raba tsakanin
gashin kansa, yana sauke numfashi yayin da bugun zuciyar sa ke ƙara hauhawa
tamkar ta tsaga ƙirjinsa ta fito.
"Ina Abdul ɗin yake?"
Jami'in ya ce "Mu je na kai ka ka ganshi" yayi wa
indabo jagora, har zuwa in da aka rufe Abdul, yana ta tangaɗi, sai da ba iya
mayen yake yi ba, har da magagin ciwon da yake sakaɗarsa, sai dai mayen da yake
yi ya hana shi gane takamaimai abin da yake danunsa.
"Abdul yasar" Indabo ya kira sunansa cikin tashin
hankali, ganin a wurin da aka ajiye shi, ɗan ƙut a takure, duk wurin babu
tsafta, har gari prison ɗin da ɗan uwansa yake a ƙasar waje, a kan wurin nan da
aka ajiye Abdul.
Abdul na jin muryar Indabo ya taso, cikin maye ya ce
"Daddy dan Allah ka fito mini da ramma, kar na mutu ban ganta ba, ban ga ɗa
na ba, akwai ɗa na a cikin ta, dan Allah ka yi mini rai, ka dawo mini da ita
rahama rayuwata ce"
"Dalla rufe mini baki, soko bita zaizai yarinyar da ta
tona maka asiri, ta tabattar da kai ka yi mata fyaɗe ka ke nema, saboda baka da
hankali, ita tayi silar shigarka wannan halin da ka ke ciki"
Abdul ya ɗaga idanunsa da kyar, ya ce "Rahaman? Ta fara
so na fa, kai wannan zance ne, rahama ba zata taɓa yin haka ba, kai ka saceta
kawai ka fito da ita, tun kan na faɗi komai, a bani mata ta kawai mu bar garin
nan, kan na fasa ƙwai mai wari" yayi maganar yana zamewa a hankali ya faɗi
ƙasa, saboda ciwon cikin da ya murɗe shi.
Indabo ya ce "Abdul, kai Abdul anya yaron nan lafiyarsa
ƙalau ku fito da shi a san abin yi".
"Lafiyarsa ƙalau a cikin maye yake, zai miƙe ya ware
ne, kar ka damu"
Indabo ya ja jami'in suka koma gefe, ya ce "Officer
babu yadda za ayi ne? Zan bayar da ko nawa ne, ku sakar mini shi dan
Allah"
"Am so sorry sir, hakan ba zai taɓa yiwuwa ba, ana sane
da duk wani motsinmu, kayi haƙuri lauyoyin dai yakamata ka ɗaukar masa"
Indabo yayi shiru bai sake cewa komai ba, ya fice ya bar wurin.
Yana komawa gida mahaifiyar Abdul ta tare shi cikin damuwa
da tashin hankali ta ce "Yaya ake ciki? Ina Abdul ɗin yake?"
Ya girgiza mata kai ya ce "Da gaske an kama shi, wannan
karon bana tunanin kuɗi da sanayya za su yi amfani, kuma wannan duk munafuncin
kankarofi ne, da ni yake zancen"
Hannu ta ɗora a ka, ta fara kurma ihu "Na shiga uku
naga ta kaina, shikenan gaba ɗaya yaran rayuwarsu ta tarwatse, babu wanda zan
mora? Wannan wane irin abu ne?"
Indabo ya ce "Kiyi haƙuri mana, ai matsalar Abdul da
sauƙi, nan gida Nigeria ne, komai zai zo da sauƙi da yardar Allah, ki yi haƙuri
ki daina wannan kukan" da kyar ya din ga rarrashinta, gaba ɗaya hankalinta
ya tashi.
***
Ramma na kwance, jikinta ya ɗauki zafi, ga tarin damuwa,
mama sai faɗa take yi mata, tana kiranta mara hankali, saboda furucin da tayi,
a kan kar a zubar mata da ciki.
Mama ta cigaba da jaddada mata abin da baban Abdul ya yi wa
Nura tana kuka, wanda hakan ba ƙaramin taɓa zuciyar ramma yake yi ba. Haka nan
ta ji ta kasa hukunta Abdul da laifin da babansa ya aikata, ita burinta ɗaya a
hukunta shi a kan ci mata zarafi da yayi, shi ma ƙasan zuciyarta tana fatan a
sassauta masa, mussaman ta ɓangaren alkhairin da ya yi wa garinsu, da kuma
yafiyarta da ya din ga nema babu yau babu gobe. Ta din ga tunanin ko yana cikin
wani hali yanzu oho.
Sai dai duk da haka, abin da aka yi wa yayan nata ya daketa,
ya taɓa zuciyarta nesa ba kusa ba.
***
Gaba ɗaya Abba ya tashi hankalin sojojin nan, a kan lallai
su nemo masa yar sa a take, ba sai bayan wani lokaci ba.
Lallai su kir wannan ɗan daban, ya dawo masa da yarinyar sa.
Nasir kuwa gefe ya koma yayi shiru yana nazari tare da
takaicin daɗewar da aka yi Nabila tana raina masa hankali.
Ya kama liti, aka sake shi, ya yi target ɗin Walid, kwatsam
ya daina zuwa wurin saida shayi, yayi target ɗin ɗan mama shi ma ya suɓuce
masa, yanzu ya ƙara tabattar da Nabila shigo-shigo babu zurfi tayi masa, ta din
ga rusa masa aiki, ashe mama son sa take yi, da take ta ankarar da shi a kan
Nabila, amma ya kasa ganewa. Sai dai duk da haka, ya kasa tsayawa ya ji
haushinta sosai, sai haushin Viper. Ya tsane shi ta kowace fuska, saboda yadda
yake tozarta masa careersa ta aiki, kuma ya yi imani da cewa shi ne yake ziga
Nabila yake yaudararta da wannan hotunan da daɗin baki, take kare shi, saboda
ya ga yana da makamin yin hakan.
Nabila a hanya suka ɗauki liti da kuma Walid, Nabila ta ce
"Oga walid ina kwana?"
"Lafiya ƙalau, ya aiki?"
"Alhamdilillah"
Viper ya kalli yadda ba su kula juna da ita da liti ba, yayi
gyaran murya ya ce "Kin yi wa Abdallah fa laifi"
Ta ce "Waye hakan?"
Ya ce "Liti mana"
"Nayi masa me?"
Ya ce "Kin saka an kama masa ɗan mama, kasa bacci yayi
jiya, gashi dama shi ma kin taɓa sakawa an kama shi. Kin saka sa da suka je CID
suka kai masa abinci, suka zo in da muka haɗu"
Cikin tsiwa Nabila ta ce "Ni na matsi bakin ɗan maman
na ce yayi magana, to ya fashe ya huta mana"
"Viper ka daina haɗa ni da yarinyar nan, zan iya
karairayata ba ta da kunya"
Viper ya ce "Easy mutumina, a din ga yi wa 'yar madara
kara mana"
"Dan Allah ka daina haɗata da waliyiyyar baiwa, babu haɗi
kashi da fura".
"Waye kashin waye furar?"
Daga gaban motar ya waiwayo a fusace ya ce "Ke ce
kashin, ke kin isa ma na haɗa ki da jauhar, mutuniyar kirki, yar aljanna, ai
wallahi an cuci yar madara idan na ana haɗata da ke, shi kansa Vipern ƙular da
ni yake yi, yadda yake kula ki. Kamar nayi muku dukan tsiya, ai wallahi an ci
amanar 'yar madara. Kuma ba zai aure ki ba, sai dai ki je can ki auri wannan suɗaɗɗen
yayan naki, tun da an ce sonki yake yi. Yar madara an yi an gama, kuma ba za a
sake ba wallahi"
"Aikuwa sai dai baƙin ciki ya kasheka, Allah a saki
Anas, a kama ka"
Walid ya ce "Dan Allah liti kayi haƙuri, kai a duniya
kamar kuturu saboda naci da nanata magana"
"Kaga ka ƙyaleni na yi mita ta, ina raye ana cin amanar
yar madara mai bani taliya da cincin ga ladabi sama da ƙasa, kawai sai wasu
abubuwa yake yi yana sakarwa wannan fuska. Ni wallahi idan aka dame ni, na fasa
kai ku wurin, ku je ku nemi wurin da kanku"
Walid ya ce "Allah ya baka haƙuri, Allah ya huci
zuciyar ka"
"Eh naji Amin, yarinya sai taurin kai da nacin tsiya,
itakaɗai a cikin maza, zaratan 'yan daba, kamar ba mace ba. Yar madara da ko haɗa
hanya ba ta iya yi da maza"
"Ni yakamata ka gaya wa haka Abdallah ba Nabila ba,
idan ka ci zarafinta kamar juhar ka yi wa, ni kuma taɓa jauhar taɓa ni ne kai
tsaye yakamata ka kiyaye"
Liti ya ce "Easy maza, tuba nake ba zan sake ba in sha
Allah"
Nabila kuwa tuni ta fara kuka, ta ji haushin maganganun da
liti ya gaya mata, Walid ya din ga bata haƙuri, liti yayi musu banza. Viper sai
ya tsinci kansa da kasa bata haƙuri, maganganun liti suka yi tasiri a
zuciyarsa, ya ga tamkar cin amanar jauhar yake yi. Sai dai kuma yana tsananin
tausayin Nabila, so take yi masa da gaske ba na wasa ba.
Wayarsa ce ta fara ringing, ya ciro ya ɗaga.
"Viper kana ina ne?"
"Na je wani wuri ne"
"Maza maza ka dawo, idan ka san kana tare da yarinyar
nan barrister ka dawo da ita, mahaufinta ya zo yana ɗaga mana hankali"
Viper ya ce "Muna tare, amma mun yi nisa gaskiya, zan
turo muku, address ɗin da muke, a bashi"
"Viper" sojan ya kira sunansa da ƙarfi.
"Am sorry sir, am ready to face the consequences of my
actions, ba zan iya dawowa yanzu ba" ya ajiye wayar. Nabila ba ta kula shi
ba, balle ta ji da wa yake waya.
Sai dai yana gama wayar, ta ta wayar ma ta fara ringing, ya
miƙa mata, ta ɗaga.
Cikin girmamawa suka gaisa da mai kiran wayar ta ce "Eh
muna tare bari na bashi"
Ta miƙa wa Viper wayar.
Ya kalleta yana jiran jin ba'asin waye.
"Ka karɓa mana" tayi maganar tana kallonsa.
Ya saka hannu ya karɓa, ya saka a kunnensa ya ce
"Salamu alaikum"
Cikin matsananciyar rawar murya ya ce "Aminu, Al'amin
ni ne, Al'amin ka yi mini magana dan Allah" sauke wayar yayi, yana yi wa
Nabila wani irin kallo, take ta sha jinin jikinta, wani fitsarin tsoro ya cika
mata mara, wani irin kallo yake yi mata mai cike da tuhuma da kuma tambayoyi.
"Ban gargaɗe ki a kan abin da ki ka aikata ba?"
Walid ya ce "Menene kuma?"
"Dan me, meyasa ki ke da taurin kai, mutumin da ya ce
baya buƙatar ɗan ta'adda a cikin rayuwarsa zaki haɗa ni da shi, ban gargaɗe ki
ba?" A take Walid ya fuskanci in da zancen ya dosa.
"Ba magana nake yi miki ba" Viper ya yi mata tsawa
cikin maɗaukakiyar murya.
Fashewa tayi da matsanancin kuka, ta takure a jikin ƙofra
motar tana kiran suna. Abba cikin matsanancin razani da tashin hankali. Ƙoƙarin
buɗe ƙofar ta din ga yi, dan gara ta buɗe ta dungura tayi waje, da wannan
tashin hankalin da yake yi mata.
"Viper zata fita fa ka hanata" liti yayi maganar
cikin tashin hankali.
Sojan da yake jan su, ko a jikinsa ko kallonsu bai yi ba,
balle ya saka musu baki.
Allah ya sa an yi locking motar.
"Hey stop here, let's reverse, take us back to
barrack"
"A'a ba zamu koma ba, abin da zai saka mu koma, ka sake
mayar da mu baya, abin da tayi dai-dai ne, ka yi haƙuri kawai malam".
"Mai laya, dan me zata nemi lambar mahaifina ta haɗa ni
da shi, kin je kin haɗu da shi kenan ko?" Ta girgiza kai cikin tsoro tana
kuka.
Walid ya ce "Mai zamani, dan Allah ka nutsu, ka yi
haƙuri, mutumin nan zai yi reverse fa, ka hana shi dan Allah da kyar ya shawo
kan Viper, suka cigaba da tafiya.
Abbu kuwa miƙewa yayi a razane, yana ta tsuma, yana sake
kiran layin Nabila, amma ya ji an kashe wayar.
Bai gaji ba ya cigaba da trying, amma shiru ba ta shiga,
Ihun rahila ya jiyo a waje, ya fito da saurin gaske, ya tarar da Abba a buge,
yana ta ball da ita a tsakar gida.
Shahida ta maƙale a bango, sai ihu take yi tana neman ɗauki,
da sauri Abbu ya ƙaraso, ya hankaɗe Abba gefe, sai dai tuni Rahila ta riga ta
suma, saboda yadda ya din ga dukanta da ƙafarsa.
Abbu ya ce "kai yanzu kana son ka gama da duniya
lafiya, uwar taka ka ke duka saboda lalacewa?"
Shahida ta ce "Wai kayansa ta kwashe masa, shi ne yake
daketa"
Kururuwar da maƙwabta suka jiyo, tuni suka fara shigowa, aka
kwasheta aka tafi da ita Asibiti.
***
Tafiya suke Nasir na ta fafara gudu, amma Abba mita yake yi,
gani yake kamar Nasir baya sauri.
Yayi shiru ya kashingiɗa, ya tafi tunani.
JALINGON JIHAR TARABA. can cikin wani jeji, da ke ƙarƙashin
ƙauyen gamyel.
Ƙatuwar harabar gida ce, mai da sashe sashe ne a cikin
gidan. Mai ɗauke da bukkoki.
Akwai tarin turaku da ke ɗaure da shanu, a wasu sassa na
gidan, daga wani sashe na gidan, matashiyar yarinye ce, 'yar shekara goma sha
biyu, take surfa gero, ɗaya ɓangaren kuma wata matashiyar mace ce take iza
wuta.
Cikin harshen fulatanci ta ce "Chubaɗo, kina ganin har
na gama tuwon nan, mu yi aikin furar nan da daddare?"
Matashiyar yarinyar da take fara tas, da siririn billenta na
fulani, ta ce "Eh mana, bari ma ki ga na ƙara sauri" sai kuma ta ɗan
yi jimm ta ce "Dada, kamar kukan karsana nake ji, ko dai haihuwa za ta yi,
bari na je na ga meyafaru"
"Kul kar ki kuskura, kin san baffanki ya hanaki shiga
turken shanu ko? Sai kin je makarai sun sake make ki a turken nan ko? Hanzarta
ki gama, na san idan Habibu na nan, zai je ya duba".
Ta cigaba da dakan geron, sallamar da aka yi ya sanya duk
suka tsaya suna amsawa.
Chubaɗo ta risuna ta ce "Baffa sannu da zuwa"
"Yauwwa chubaɗo, aiki ake yi ne?"
"Eh baffa"
Ya ce "Sannu, ramata sannu da aiki"
Matar ta ce "Yauwwa, sannu da zuwa" tayi maganar
tana ƙoƙarin ɗaukko tabarma ta shimfiɗa masa.
Yasar da taɓaryar hannunta tayi, ta fyalla waje da gudu, jin
an kira sunan maitama a wajen.
Tana fitowa, maitama ya saki akwatin hannunsa, ya ƙarasa ya
rungumeta yana murmushi.
Cak yaran da suke murnar ganinsa suka tsaya, ba su ba har da
manyan da suke wurin, ganin abin kunyar da jibo ya aikata wato maitama.
Ita kanta Chubaɗo sai ta ga abun wani iri, tayi sukuri da
kai tana sunkuyar wa.
Ya ce "Masha Allah, mairamu kin girma, ya ki ke"
"Lafiya ƙalau hamma, ya birni?"
"Birni Lafiya ƙalau tana gaishe ki" ta ɗauki
jakarsa ɗaya, shi ma ya ɗauki ɗaya, ya riƙe hannunta suka shiga gida.
Baffa da yake shan fura, ya ɗago ya kalle su, ya mayar da
kansa ya sunkuyar ya cigaba da shan fura.
Jibo ya ƙarasa gaban baffa, ya durƙusa ya ce "Sannu
Baffa na dawo"
Baffa ya ce "Sannu"
"Yauwwa"
Ramata ta ce "Jibo sannu da zuwa"
Ya ce "Yauwwa sannu"
Chubaɗo ta shiga ɗaki ta shimfiɗa masa tabarma, ta ce
"Ka zauna, bari na sake gyara maka ɗakinka, nayi ta mafarkinka, ashe ka
kusa dawowa" yayi murmushi ya zauna, ta ɗebo masa ruwan randa, ta kawo
masa, ta buɗe bukkarsa da shekara guda kenan, rabonsa da ita tana sake gyara
masa.
Babu wanda ya kuma kula shi, shi kuma ko a jikinsa, ya
cigaba da hira da chubaɗo.
Ta ɗauki ƙoƙo, ta tafi gidansu Habibu, da kanta ta shiga
tsakanin shanu, ta tatso masa madara, mai ɗumi ta kawo masa, sai rawar kai take
yi.
Baffa yana fita aka sanar da shi abin kunyar da jibo ya
tafka, na rungume chubaɗo. Hakan ba ƙaramin ƙona wa Baffa rai yayi ba, ya zubar
masa da ɗan ragowar mutuncin daga dawowarsa, bayan wanda ya zubar masa a baya,
yazo ya fara gwada yahudanci da baƙar ɗabi'ar da ya koyo.
A fusace ya dawo gida, ya sake tarar da Jibo, yana ta hira
da chubaɗo kamar wata sa'arsa. Yana yi mata tambayoyi a kan abubuwan da ya koya
mata a baya, dangane da karatun boko da na addini, cikin ikon Allah bata manta
ba, har sunanta da nasa, da haɗa baƙi duk bata manta ba.
Sosai yake murna, kan ya jiyo muryar Baffa yana faɗa
"Maitama, dama abin da ka je ka aikata kenan daga dawowarka, saboda
yahudanci a gaban mutane ka rimbaci chubaɗo, saboda rashin mutunci"
Jibo ya ce "Baffa chubaɗo fa ƙanwata ce ciki ɗaya,
shekara guda rabona da ita, menene laifi a cikin hakan? Kuma naga ai ba wani
girma ne da ita ba"
"Zaka rufe mini baki, ko sai na rushe maka kai da
sandar nan? Tashi kema daga kusa da shi, kana naɗa miki duka. Ka tashi mu je arɗo
yana son ganinka yanzun nan, har labarin zuwanka da abin da aikata ya je masa.
Kalle ka har ka fara tsufa, sa'aninka duk sun yi aure, sun kusa ma fara aurar
da 'ya'ya kai kuma kana nan kana gararanba, kana shashanci"
Jibo ko a jikinsa, ya ce "Nima dawowata yanzu har da
maganar auren na dawo"
"A ina zaka yi auren?"
"A can in da nake ne"
Baffa ya ce "To bayahudiyar zaka aura kenan, masu
bawali a tsaye, to sai su yi maka waliccin auren, tashi mu tafi" tashi
yayi ya bi baffa, ko da suka je fadar arɗo, tuni wasu manya a rigar sun taru
suna jiran su.
Aka hau jibo da faɗa, da jaddada kiransa da bayahude, kuma
suka ce lallai ya tattara ya bar musu gari, kamar yadda aka yi yarjejeniya da
shi da farko.
Jibo ya gyara zamansa ya ce "Idan har kuna son na bar
garin nan, sai dai ku bani mairamu chubaɗo, na tafi da ita, dan ba zan je na
rayu nikaɗai ba alhalin ina da 'yar uwa ba, tun da ku kun sallama ni"
"Babu wanda zai baka chubaɗo, kuma sai ka bar rigar
nan, ai duk zuwa muna gaya maka, bama buƙatar ka tun da abin da ka zaɓawa
rayuwarka daban"
Ya ce "To shikenan, amma ku sani duk ƙasar nan babu
wanda ya bawa wani ikon ya kori wani, muddin ba zaku bani chubaɗo ba, ku bar ni
na din ga zuwa ina ganinta, idan kuma kun ƙi, kun san ƙasa nake yi wa aiki, za
a aiko yahudawa kuma su kore ku, su kwashe shanunku" sai kuma duk suka yi
saroro.
Ya ce "Eh idan mun tashi zuwa kiwo, babu wanda yake
hanamu shiga duk in da muke so da shanu, muyi kiwo, saboda yan ƙasa ne mu, amma
idan ku ka ce zaku kore ni, to fa kuma za a kore ku daga rigar nan, kuma a
ƙwace muku shanu". Gaba ɗaya sai suka sha jinin jikinsu, sai kuma suka
koma rarrashin sa da neman sulhu.
Maitama wanda suke kira da jibo, cikakken sunansa shi ne
Yusuf, mahaifiyar su Allah ya yi mata rasuwa, a ƙalla ta haifi yara tara amma
duk mutuwa suke yi, shi ne na huɗu, har an fitar da ran zata sake haihuwa, ta
samu ciki ta haifi mairamu ake ce mata chubaɗo.
Kowa ya ɗauki son duniya ya ɗorawa chubaɗo, mussaman ma shi.
A can yawon kiwon shanu, ya faɗa wani ƙauye, ya tarar ana
makaranta, turawa na koyar da yaran garin karatun boko. Abin ya ƙayatar da shi,
ya fara shiga cikinsu, ya shiga cikin ɗalibai, kullum ya fito kiwo, sai ya je
ƙauyen nan, komai kyauta ake ba su, da kayan rubutu da karatu.
Gashi da ƙwazo, ya shafe wata shida yana zuwa ba a gane ba a
gida, daga bisani wani a rigarsu ya gano shi, ya je ya faɗa. Ai tamkar za a
cinye shi, aka ce kiwon ma ya daina zuwa gaba ɗaya.
Baffa ya koma fita da dabbobin da kansa, sai dai yana
ficewa, shi ma maitama yake saka ƙafarsa ya fita, ba boko ba har da karatun
allo yake koya a garin.
Baffa duk son sa da yara, sai da ya saka aka zane masa
maitama, amma washegari ya gudu ya koma can ƙauyen ma gaba ɗaya. Yake kwana a
masallaci, abin da zai ci ba wahala yake ba shi ba, kullum gidan mai garin ana
bayar da abinci sau uku a rana.
Innarsu babu irin nasihar da ba ta yi masa ba, da rarrashi,
amma yaƙi.
Hnakali ya tashi rashin ganin maitama, aka wakilta ƙarti
suka tafi ɗaya garin,arɗo ya ce a ɗoro masa Jibo a ka a dawo masa da shi.
Sai dai can garin suka hana kama Jibo, abu ya nemi ya zama
rigima da fitina, sai da aka shirya zama na musamman tsakanin malaman dagacin
ƙauyen, da ƴan rigar su jibo, a kan a samu fahimtar juna, su bar Jibo yayi
karatu, su ma idan suna buƙata zasu iya kawo wasu yaran, a cigaba da yi musu
karatu, amma suka ƙi suka ce ba sa son yahudanci.
Abu sai da jami'an tsaro suka shiga, suka ce sai Jibo yayi
karatu, ba tare da an cigaba da tsangwamar sa ba.
Da kyar aka samu masalaha, sai dai can a riga suka ce, sai
dai ya bar musu rigar su, babar sa ta din ga kuka tana yi musu magiyar kar su
korar mata ɗa.
Idan bai ga dama ba, idan ya tafi sai juma'a yake dawowa,
kan ya dawo innarsu ta ɗan tanadar masa busashshiyar fura, man shanu, nono, ta
ce ya tafi da su, kar ya ji yunwa, haka kurum ta ji ita dai tana son abin da
yake yi. Ta fuskanci ƙalubale sosai da sosai, ana cewa ita take goya masa baya,
duk lokacin da ya zo, idan zai tafi sai chubaɗo tayi ta kuka saboda sun shaƙu.
Tana da shekaru huɗu, haka zai zauna da ita, yana koya mata
idan baffa ya ƙyalla ido ya ganshi, ya ɗauke chubaɗo yayi ta yi masa masifar
kar ya lalata masa yarinya shi dai ya je ya ƙarata.
A haka aka zaɓi ɗalibai har da maitama, aka ce za a kai su
makarantar kwana.
Nan ma an sha gwagwarmaya, kan maitama ya tafi.
Chubaɗo na da shekaru shida, Allah ya yi wa mahaifiyar su
rasuwa, maitama yana can makaranta. Da ya zo hutu ya sha kuka, ya shiga tashin
hankali da kiɗima mai yawan gaske.
Da aka nutsa, suka sake ce masa sai dai ya zaɓa, ko boko ko
ya dawo yayi aure, amma ya ce boko, suka ce to ya bar musu riga. Bai damu ba,
bai kuma daina zuwan ba.
Baffa ya auri ramata, ta riƙe mairamu hannu bibbiyu kamar
ita ta haife ta. Sai dai tun tana ƙarama, take fama da matsalar numfashi, sai
dai ko maganar asibiti ba ayi, sai dai ayi ta banka mata hayaƙi, wai iskokai
ne, cike da jahilci. Ga kuma matsalar iskokai da take fama da su.
Maitama ya ɗauke ta, ya kaita asibiti babu wanda ya sani,
likitoci suka tabattar da athma ce da ita, wanda irin ciwon ne ya kashe
mahaifiyar su.
Sai da aka kusa ƙaramin yaƙi a zuriyar, saboda kai mairmu
Asibiti da yayi.
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, maitama ya yi degree, ya
tafi aikin soja, amma duk sunansa Bayahude a wurin mutanen rigar.
A yanzun ma haka suka ƙyale shi, bayan yi musu barazanar
saka yahudawa su ƙwace musu shanu su kore su daga riga.
Har magana yake yi wa mairamu da turanci, kuma tana iya gane
wani abun.
Ya fara kashe bakinsu, bayan da ya fara basu 'yar shinkafa
kyauta.
Lokacin aurensa da kyar suka je masa walicci, sai dai da
suka ga birni sun rikice da yawa, ya so a bashi mairamu amma fafur suka hana
shi.
Shekaru suka cigaba da ja, chubaɗo na da shekaru goma sha
uku a duniya, tsantsar kyawunta, ya fara baiyyana, samarin ƙauyen sun fara kawo
hari, saboda kyakywar gaske ce, sai dai da yawa suna tsoron larurarta ta
matsalar numfashi da suke cewa aljanu ce.
Duk lokacin da Maitama ya zo garin, sai ya kawo mata kayan
sawa, na kwalliya, wanda babu wata yarinya da ta taɓa amfani da su a rigar. Ya
kan bugi cikinta duk wanda ya ji ya nuna yana sonta, sai ya je yayi masa
barazanar saka yahudawa su kama shi, su mayar da shi ƙarfe.
Ya kan kawo mata litattafai, ya sayo mata radio, ya gaya
mata lokutan da ake gabatar da wasu shirye-shirye a radio na yara.
Watarana da ta zama ranar mabuɗin sada chubaɗo da
ƙaddararta, ta bi 'yan matasan matan da suke fita can bakin hanya sayar da
nono, domin ta je ta ga motoci, ta fita da shanu, ta fake da haka, dan Baffa
baya barinta ta je ko ina.....
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Fitar ta yi wa mairamu daɗi sosai da sosai, dan ko kiwo zata
fita, ba ta yi hanyar barin garin, balle ta fito bakin hanya.
Suna zazzaune, shanunta na gefe na kiwo, sai nishaɗi take
ji, tana ƙissima ta nan hanyar hammanta yake wucewa, idan zai zo riga, ko kuma
ya tafi. Yayi mata alƙawarin komai daɗewa zai zo ya ɗauketa daga riga, ya tafi
da ita can in da yake, ita ma ta ga gari, amma ba zata ji daɗin tafiya ta bar
baffa da dada ba. Gashi rashin jituwar hamman da baffa baya yi mata daɗi, sai
dai tana fatan barin rigar, tana son tayi karatu irin na hammanta, babban abin
da yake ƙara burgeta da yi mata daɗi, shi ne idan ya zauna yana koyar da ita
karatun addini, yana bata tarihin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam, da
sahabbansa wanda yake matuƙar ratsata da sanya mata nutsuwa da farinciki.
Idan ta tafi birni, wurinsa ta san kullum sai ya bata
tarihin Manzon Allah da wasu annabawan. Kuma ta huta da takurar baffa, a kan
rashin fitowar manemanta, da an fara magana sai abu ya lalace, ya fara zancen
ko iskokai ne suke hana maganar, ya saka ayi ta banka mata hayaƙi, dan an saka
hayaƙi kuma sai ta hau suma, hakan ya sanya suke ƙara yadda da hakan. Bayan
haka bijirewar jibo na zaman riga da zaɓar boko da barazanar da yake yi, ya
ƙara sanya samarin garin nesanta kansu da Chubaɗo.
"Chubaɗo, tunanin me ki ke yi ne?" Firgigita ta
farka tana murmushi ta ce "Bakomai, daɗi nake ji, yau gani a bakin hanya,
ina ta kallon motoci" sauran yan matasan suka din ga yi mata dariya, dan
su suna zuwa, ita ce dai baffa baya barinta zuwa ko ina.
Wani mutum suka hango yana tunkarosu, hannunsa riƙe da
galan, gashi matashi a ƙalla zai shekara ashirin da bakwai, a ganinsu babba ne,
amma sanye da ƙananan kaya, wanda hakan baƙo ne a wurin su.
Yayi musu sallama suka amsa, ya ce "Yan mata dan Allah
ina zan samu ruwa? Motata ta ɗauki zafi, a can baya na bar ta, kuma ina son zan
yi salla, ruwan sha ne kawai a mota ta"
Dukkaninsu kowa ya ce "Bai sani ba"' ban da chubaɗo,
da tayi ƙuri da ido tana kallon kayansa, hamma yana saka irin kayan, kenan shi
ma bayahude ne?.
Ya ja ya tsaya cikin damuwa yana waige-waige, da alama kuma
a gajiye yake.
Kamar daga sama cikin siriryar muryarta ta ce "Na sani,
amma ruwan rafi ne, kuma a ɗan ciki ne" tayi maganar tana nuna masa
hanya, yanayin hausar ya tabattar masa da cikakkiyar bafulatana ce, duk yan
matan babu mai mayafi, suna sanye da kayan saƙi da ɗan kwali.
Duk suka waiwaya suna kallon chubaɗo.
Ya ce "Yauwwa yar albarka, nuna mini wurin"
Cikin harshen fulatanci, suke gargaɗin ta a kan meyasa zata
bi kaɗo, daga ganin sa yau.
Ta ce "A tarihin Annabi da hamma yake bata, Annabi yana
taimakon mutane, kuma babu kyau wulaƙanta mutane" ta wuce gaba ya fara bin
ta a baya.
Tayi gaba ba tare da ta ce masa uffan ba, tana ta kaɗa 'yar
sandarta, tana cilla ƙafarta cikin nishaɗi.
Ya ce "Ba a kusa ba, na gaji" ta tsaya ta waiwaya
ta ce "To kawo abun ka zauna ka jirani, sai na ɗebo maka".
Ya ce "A'a mu je" suka cigaba da tafiya, sun yi
tafiya sosai, sannan suka ƙarasa rafin, ya durƙusa yayi alwala, ya ɗebi ruwa a
galan ɗin da ya zo da shi.
Yana satar kallonta, gaba ɗaya ba ta da wata damuwa, tana ta
wasa da layar da take wuyanta ta sauko har kan ƙirjinta, hannu ɗaya kuma tana
wasa da sandarta.
Ya gama suka nufi komawa, ya ce "Ya sunanki ne?"
"Mairamu"
Ya ce "Masha Allah, sunana Bashir, ina yawan wucewa ta
hanyar nan, ba taɓa zaton akwai mutane ba, ko daga wani wurin ku ke zuwa?"
Ta ce "A'a rigarmu na can ciki"
Ya ce "Masha Allah, mu je na sai nonon na sha, idan zan
wuce na din ga tsayawa mu gaisa, ba zan manta da taimakon da ki ka yi mini
ba"
"Ba ni nake sayar da nonon ba, ni rako su kawai nayi,
shanuna nake kiwo"
"Au har kiwon shanu ki ke yi? Lallai ke jaruma ce"
suka yi maganar lokacin da suka dawo in da ya tarar da su, ya sa nono mai yawa
sosai, ya basu kuɗin.
Ya ce "Mairamu, sai na sake dawowa, ni ɗan garin azaren
jihar Bauchi ne, ta nan nake wucewa, sai mu din ga gaisawa na gode sosai Allah
ya saka da alkhairi" ta amsa da amin.
Suka koma gida, sai da aka gaya wa ramata mariƙiyar chubaɗo,
ta bi wani kaɗo ta raka shi rafi, ramata tun daga ranar ta hanata bin su.
Bashir ya daɗe yana wucewa, idan ya tambaye su ina mairamu,
sai su ce masa an hanata zuwa. Ya ce idan sun je su gaishe ta.
Sukan gaya mata, sai da ta ce musu to, amma bata ɗauki hakan
da muhimmanci ba.
Maitama ya sake zuwa rigarsu, sun fafata da baffa sosai, a
kan ya bashi mairamu, amma ya hana shi, ya ce shi aure zai yi wa yarsa, ba za a
kaita cikin kafurai ba.
Ga surutu ya fara yawa a kan rashin aurar da chubaɗo duk da
irin kyau da Allah ya bata.
Maitama ya kawo mata ƙatuwar radio da carsets, na wa'azi da
tarihin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, ya koya mata yadda ake amfani
da ita.
Da daddare ƙawayenta da maƙwabtansu, zuwa suke su taru ta
kunna musu, suyi ta saurara, idan wannan ya ƙare a saka wancan.
Wani zuwa maitama ya zo da matarsa da ya aura, har da yara
biyu da ta haifa, a wannan karon suka fara zuwa garin tare.
Duk da haushin maitama da suke ji, sun karrama matarsa da
yaransa sosai da sosai, sai dai a fili ta nuna ƙyamarta ga rigar, da nuna ita
ba zata iya zama ba.
Mairamu kamar ta haɗiye yaran nan, tayi ta ɗaukar ƙaramar
tana goyawa, tamkar ta haɗiye su, da kyar suka yi sati ɗaya.
Watanni shida suka shuɗe, mairamu ta sake bin ayari, zuwa
bakin hanya wadda ta tasamma zama ƙaramar kasuwa.
Ana ta hada-hada, kawai ta yanke jiki ta faɗi, numfashi ya
sarƙeta, ya zamana ko motsi bata iya yi.
Gaba ɗaya hankalinsu ya tashi, suka rasa yadda za su yi da
ita, kamar an yi masa wahayi, sai ga motar Bashir, ya zo wucewa ya tsaya zai
sayi nono ya wuce, ya hange su sun yi cincirindo a wuri ɗaya.
Ya sauka ya fita, yana zuwa ya tarar da chubaɗo a baje a
ƙasa ko motsi bata yi.
Cikin tashin hankali yake tambayarsu, meyafaru da ita? Suka
gaya masa faɗuwa tayi.
Saroro suka yi, ganin ya taɓa ta, ba ta motsa ba, sai wani
irin numfashi mai sauti daga ƙirji da take yi.
"A garin nan kuna da Asibiti ne?" Suka ce
"A'a, sai dai wurin mai magani"
Bai yi sanya ba, ya ɗauki mairamu, ya sakata a motarsa, ya
ce wasu daga cikin su su bishi, su tafi kaita Asibiti.
Hama ce ta ce masa "A'a mufa rigarmu ba a zuwa
asibiti" duk aka rasa mai bin sa, kawai ya shige motar ya ja ya tafi da
ita.
Cikin tashin hankali, suka kwashi kayansu, suka koma riga.
A lokacin maitama yana gari, ai kuwa cikin kiɗimewa, aka yi
ayari suka taho bakin hanya, amma babu Bashir babu alamarsa.
Ramata kuwa tuni ta fara kuka tana salati, tana Allah ya
rufa mata asiri ya sanya a ga mairamu, ba ita ta haifeta ba, amma akwai soyayya
da shaƙuwa a tsakanin su.
Sai dai suka dawo bakin hanya, amma babu Bashir babu chubaɗo,
sosai Baffa ya din ga yi wa ramata faɗa, ta din ga kuka kuwa.
Maitama ya ce su bari zai je asibitocin hanya ya duba, in
dai da gaske kamar yadda sauran suka faɗa, asibiti ya ce zai kaita, to zai
ganota.
Baffa ya ce lallai sai dai su tafi tare, suka rankaya suka
din ga duddubawa, ƙarshe a wani asibiti a nan jalingo suka gano mairamu.
Maitama ya fara yi wa mutumin masifa, a kan dan meyasa zai ɗauke
ta ya tafi da ita.
Bashir ya ce "Ku yi haƙuri dan Allah, na san na ɗaga
muku hankali, cikin yaran an rasa wanda zai biyo ni, na tarar da su da ita a
gefen hanya, ba ta numfashi shiyasa kawai na ɗauke ta zuwa asibiti, in da muka
fara zuwa suka turo mu nan"
Baffa ya din ga faɗan shi baya zuwa asibiti, bai yadda da
wannan abun ba, a ɗaukko masa 'yar sa ya tafi da ita.
Maitama ya ce "A'a ba za ayi haka ba".
Chubaɗo ta galabaita sosai da sosai, baffa ya cigaba da
mitar, sai an bashi 'yar sa, za a kashe masa 'ya duk an ɗaura mata wasu kwanuka
a fuskarta.
Likitoci suka ce, ba zasu bayar da chubaɗo ba, ba ta warware
ba, aka din ga kai ruwa rana da baffa, da kyar aka lallaɓa shi, ya ce yar sa ba
zata kwana a wurin ba.
Yamma sosai, Maitama yana son mayar da baffa gida, amma ba
zai yiwu ya bar mairamu a asibiti ba, da mutumin da bai sani ba, ga lokacin
babu waya.
Ya lallaɓa baffa, ya kai shi tasha ya ce komai dare zai dawo
masa da mairamu gida.
Sai dai ya ga Bashir ba shi da niyyar tafiya, ya ce
"Abokina mun gode da taimakon da kayi mana, zaka iya tafiya fa"
Bashir ya ce "Ba zan iya tafiya na bar ta a halin nan
ba, zan yi ta wasi-wasi ne. Dan ban manta alkhairin da tayi mini ba watanni
baya" ya bashi labari.
Nan hira ta ɓarke, yake bawa maitama labari, cewa shi
coustom ne, ƙarshen wata yake komawa Bauchi hutu, yanzun ma gida zai tafi ya
tsaya sayen nono, ya tarar da chubaɗo babu lafiya.
Har yake bashi labarin, ainihi shi ɗan kasuwa ne, ya fi son
harkar kasuwancin sa, amma aka turasasa masa wannan aikin, duk a takure yake.
Shi ma maitama yake bashi labarin shi soja ne, nan da nan
suka saba, suka din ga hira, kasancewar jikin da ɗan sauƙi.
Yake gaya masa burinsa a kan mairamu tayi karatu, amma
baffansu baya so, soyake lallai sai ya aurar da ita, ga shi bata da cikakkiyar
lafiya.
Suka kwana tare ta farfaɗo sosai aka bata magani, maitama ya
ce ya samu dama, tafiya zai yi da mairamu can garin da yake aiki, a Benue
state.
Haka aka yi, asubar fari suka hau motar Bashir, ya je tasha
in da ake hawa motar garinsu, ya bayar da saƙo a gaya wa Baffa, Bashir ya rage
musu hanya, maitama yayi ta yi masa godiya sannan suka rabu.
A hanya ya sake jaddadawa mairamu, zai tafi da ita gidansa
da yake zaune, taji daɗin hakan, sai dai ta wani fannin ta ji kewar gida, yadda
aka rabota da garin babu ko sallama.
A cikin barrack gidan sa yake, matarsa kawai sai ganinsa
tayi da mairamu, dan hatta kayan sakawa a hanya ya saya mata.
Bayan ya huta take tambayarsa, lafiya ta ganshi da ita, ya
sanar mata ta dawo nan da zama, nan ta ce bata yarda ba, shi kuma ya ce to ta
koma gidansu, shi zai rayu da ƙanwarsa.
Ta ɗauki gaba da fushi da shi, shi kuwa ko a jikinsa, chubaɗo
bagidajiya ce a birni, ba ta iya komai ba, ta din ga ganin abubuwa kamar ba a
duniya ake ba, maitama da kansa ya din ga koya mata abubuwa.
Baffa ya rikice kamar yayi hauka, bayan samun saƙon maitama,
na ya tafi da mairamu.
Mairamu daga ita sai maitama, sai yaran gidan take mu'amala
da su, hatta amfani da kayan wanka komai shi ya koya mata.
Satinta uku a garin, babu alamar musulmai a in da suke, duk
sati maitama yake kaita ganin likita, saboda matsalar ta. kwatsam sai ga
Bashir. Abun ya basu mamaki nesa ba kusa ba, wai duba mairamu ya zo.
Nisan tafiyar kawai maitama ya din ga hangowa, suka karɓe
shi, suka karrama shi sosai da sosai, ya din ga murnar ganin mairamu ta samu
lafiya. Sai da ya kwana a garin sannan ya koma.
Sai dai bayan wata guda ya sake dawowa, a lokacin maitama ya
saka mairamu a makarantar boko, karatun addini kuma, yana koya mata a gida.
Duk wani aikin gida, mairamu tana yi wa matar hammanta, amma
sam bata gani, kawai ta tsaneta.
A wannan karon, maitama ya rutsa Bashir, a kan ya gaya masa
dalilin zuwan da yake yi, bai yi ƙwauron baki ba, ya sanar masa son mairamu
yake yi.
"Kana mutumin birni, tayaya zaka auri bafulatanar daji,
yarinya ƙarama?"
Ya ce masa shi babu komai zai iya yana son ta a haka, sai
dai da magana ta yi magana, ya sanar masa yana da mata biyu.
Maitama ya ce yayi haƙuri, ba zai iya aura masa mairamu ba,
duk da matashi ne, ko talatin bai yi ba, amma yana da abin hannunsa, ya ce
yarinya ce yar ƙauye mara wayo wahala kawai zata sha.
Sai dai mairamu, bai gaya mata yana son ta ba, amma maitama
ya lura da yadda take murna idan ya zo.
Sai dai hakan bai hana shi, sake niƙo gari ya zo Benue ba,
saboda mairamu. Maitama ya sake jadda masa, ba zai bashi mairamu ba, ya ce shi
in dai zai zo ya ganta shikenan, haka ya cigaba da sintiri.
Wani zuwa da yayi, ya bata wasiƙa lokacin da ya zo, ta zauna
ta karanta ta kasa, saboda manyan turanci ne, ta kai wa hammanta ta ce ya
karanta ya fassara mata, ita ba ta san me aka rubuta ba.
"Kalaman soyayya ne" ya bata amsa. Sai tayi shiru
tana mamakin wace irin soyayya kuma?.
Tana kewar baffa da kuma dada, amma tana jin tsoron gaya wa
hamma yayi fushi.
Sai da ta shafe watanni biyar, sannan maitama ya je riga,
aikuwa ya sha takaici, dan ƙiris ya rage baffa yayi masa baki, ya ce ya dawo
masa da 'ya ya aurar da ita, kar ta lalace.
Maitama ya ga idan ya dawo da ita, ba zata cigaba da samun
kulawa ba, saboda yadda suka jahilci zamani da cigaban da ya zo da shi.
Ya ce "To yanzu akwai mijin da zaka aura mata ɗin?"
"A'a amma zan samo mata"
"Ni ina da wanda zan aura mata, idan ka yarda ya zo ya
nemi aurenta" ya ce bai yarda ba.
Aikuwa maitama ya ce ba zai dawo da ita ba, in dai a garin
nan za ayi mata aure, idan ya tafi ba zai dawo ba har abada, kuma ba zai sake
ganin mairamu ba.
Ba shiri ya amince, ya turo masa mijin da ya samo matan.
Yayi tattaki har azare, yayi bincike sosai a kan bashir, ya
tarar da familynsu mutanen kirki ne, shi kansa nagartaccen mutum ne, har wurin
da yake aiki, sai da ya je duk ya kammala binciken sa, sannan ya koma ya tuntuɓi
mairamu idan tana son Bashir, tayi shiru ta sunkuyar da kai, hakan ya sanya ya
gane in data dosa.
Ya nemo Bashir da kansa, ya gaya masa halin da ake ciki,
amma ya ce zai bashi auren mairamu, idan ya amince da zai riƙeta amana, ya kula
da lafiyarta da iliminta, a duniya ba shi da kowa sai Allah sai mahaifinsa da
mairamu, itakaɗai ce yar uwassa.
Bashir ya ce ya amince kuma yayi masa alƙawarin haka.
Ya tura shi wurin baffa, nan ma sai da aka yi wani darun, ya
ce ba zai bayar ba, da shi aka haɗa baki, jibo ya gudu da maitamu, maitama ya
tsaya, tsayin daka, Baffa ya bayar da auren mairamu ga Bashir.
Ya dawo da ita aka yi biki da ɗaurin aure, aka kai mairamu
gidan Bashir da yake jihar Bauchi.
Matan Bashir sai da suka kusa yi masa bore, jin zai auro
musu, yarinya ƙarama bafulatanar daji, amma ya ce babu gudu babu ja da baya.
Ba wata shaƙuwa suka yi da Bashir ba, dan haka wata irin
matsananciyar kukyarsa ta din ga ji. Washegari kaita, ya tara matansa a
falonsa, ya gabatar musu da mairamu.
Sai dai sun sha jinin jikinsu, ganinta jawur kamar ƙosai,
dai-dai gwargwado kyakykyawa ce ta gaske, kuma yarinya sharaf.
Shi kansa ba wani babba bane ba, amma ya ajiye mata uku
rigis, yayi musu nasiha sosai, ya ja amaryar sa ɗaki.
Ita ma yayi ta yi mata nasiha, yana yi yana gaya mata
kalaman soyayya, ta ja gefe ta duƙunƙune a mayafi, saboda kunya.
Ko riƙe hannunta taƙi yadda ya yi, ya nuna mata yaransa, a
lokacin yaransa huɗu, biyu maza biyu mata.
A da kan ya auro, mairamu faɗa da kishi a tsakanin su, kamar
sun cinye junansu, amma tun da yayi aure suka haɗe masa kai.
Mairamu na da tsananin biyayya, da safe sai ta durƙusa ƙasa,
zata gaishe shi. Suna da mai aiki, idan aka gama abinci, za ta je ta ɗaukko
masa, amma ba zata taɓa cin abinci a gabansa ba, saboda kunya.
Ana gobe zai bar ɗakinta, ya cika kwana bakwai, sannan wani
abu ya shiga tsakaninsu.
Kasancewar kowa ɗakinta ciki da ƙaton falo ne, banɗakuna
biyu ne a tsakar gida, sai kuma banɗakin da yake cikin ɗakinsa falle ɗaya.
Amma a ɗakinta ya kwana, cikin dare yana ƙoƙarin taimaka
mata, ta kintsa, uwar gidan ta dalle su da fitila a tsakar gida, ta din ga zuba
habaici da rashin mutunci.
Da sassafe ta zo ƙofar ɗakin ta ce ya fito, tun da yau
girkinta ne.
Sai wajen la'asar, ya samu sukunin sake shiga ɗakin chubaɗo,
ya tarar da ita a kwance, abincin ma da aka kawo mata ba ta ci ba.
"Fulanina, sannu ya jikin?"
Ta ƙunshe fuska ta ƙi magana.
"Ba ki ci abinci ba, me zan sayo miki ki ci?" Ta
girgiza masa kai alamar babu.
Ya kwantar da murya ya ce "Tashi na baki abincin a
baki, ai za ki ci ko fulanina"
Fafur taƙi sai ma ta saka masa kuka wai gida, ya mayar da
ita gida. ya tashi ya fita ya sayo mata tsire fal, da fanta ya kawo mata.
Ya din ga rarrashinta, da ƙyar ta daina kukan, ai ba ta
saurari nama ba, ta din ga ɗaɗɗakar fanta.
Yayi murmushi ya ce "Ka ga bafulatanar Bashir, da ga
yanzu na gano lagonki, fanta ce maganinki" sai kuma ta sunkuyar da kai
tana murmushi.
Sai da ya shafe wata guda a Bauchi, ya kaita can garinsu
azare, da yake shi ba a can yake zaune ba, a can ya samu ya ɗan sake da ita
sosai, dan sai da suka kwana uku, sosai danginsa da yan uwansa suka karramata.
Mamaki take yi yadda yake salihi, a gaban mutane, ake yi
masa kallon mutumin kirki, yake sunkuyar da kai, amma ida suka keɓe yayi ta yi
mata fitsara da rashin kunya.
Wata irin soyayya yake yi mata, wadda bai iya nuna mata a
waje ba, dan da gaske yake jin sonta a cikin ransa, chubaɗo akwai haƙuri da
biyayya, ya samu har ta ɗan fara sakewa da shi, yayi kamar ya ce zai tafi da
ita in da yake aiki, dan dab da za ayi bikin su, aka mayar da shi Naija state.
Da ya fara yi mata wani abu dan soyayya da kyautatawa, sai
ta ce ya bari, saboda tana son ta shiga aljanna.
Ya dubeta ya ce "Waye ya ce idan na yi miki tausa, ko
dafa miki ruwan wanka, ba zaki shiga aljanna ba? Jin dadin biyayyar da ki ke yi
mini, ya sanya nake yi miki abin da zaki ji daɗi kema"
"To zan shiga aljanna?"
"In sha Allah, hannuna a naki zamu shiga"
Ta rausayar da kai ta ce "Wataƙila babar saifu ta
hanaka, ta ce na ta hannun zaka riƙe ita da amarya, ku tafi ku barni" tayi
maganar cikin kishi da yarinta.
Yayi dariya ya ce "Kowaccenku, zan riƙe hannunta mu
shiga tare in sha Allah"
Mairamu bata aikin komai, gidan ma kusan ba wanda yake wani
aiki a gidan, saboda suna da masu yi musu aiki.
Da fari tana so ta ɗan sake da matan gidan, amma suka nuna
mata bata isa ba, hatta masu aikin ma wani gani-gani suke yi mata.
Sai dai saifullahi ne mutuminta, shi ne ya kan shigo ɗakinta,
har su ci abinci tare da shi.
Tun da Bashir ya koma aiki, suka mayar da mairamu tamkar
baiwarsu, suka din ga sakata ayyuka na wahala, suka dakatar da mai aikinsu, ita
ce wanke-wanke, shara raino wankin yara da kuma girki.
Gashi har a lokacin da ƙauyanci da ƙuruciya a kanta.
Maƙwabta suka din ga ziga su, wai ƴar aiki kawai aka kawo
musu, ban da haka ina wannan bagidajiyar zata iya kula da miji.
Ranar da zai dawo, duk sun sha ado da kwalliya, mairamu kuwa
futu-futu dan wuni tayi tana aiki.
Duk zumuɗin ya zo ya ganta, bai ji daɗin ganinta a haka ba,
da ya shiga ɗakinta sai da ya ce mata ƙazama. Haƙuri kawai ta bashi ta yi
shiru.
Ranar da ya dawo ɗakinta, ta yi kwalliya, hakan yayi masa daɗi
sosai da sosai, babban abin da ya basu mamaki, bai wuce jiyo dariyar Bashir da
mairamu ba, suna yi mata kallon sokuwa, amma ta saka miji a ɗaki suna ɓaɓɓaka
dariya.
Tambayarta yake yi "Da a baki fanta, da nagge wanne ki
ka fi so?"
Ta ce "Kai Nagge mana"
Ya ciro check, ya rubuta Naira dubu ashirin irin ta da a
jiki, ya ce "Nan dubu ashirin ne, da na baki wannan, da na baki nagge
wanne ki ka fi so?"
Tayi dariya ta ce "Aradu na fi son nagge" suka
tuntsure da dariya ya ce "Baki da wayo, wannan kuɗin sai ya sai miki nagge
biyar"
"Wannan ɗin, takadda ce fa kawai gaskiya na fi son
nagge"
Bashir ya ce "To da ni da nagge wanne ki ka zaɓa?"
Ta waro ido. Ya ce "Sai kin zaɓa fa"
Ta faki idonsa ta ce "Nagge"ya riƙeta yana yi mata
cakulkuli ya ce "Me ki ka ce?"
"Kai na zaɓa" tayi maganar tana dariya.
Mairamu ba ta taɓa kai ƙarar wani wurinsa ba, su kuwa ba sa
rasa Sharrin da zasu yi mata, wani ya yadda wani ya rabu da su.
Ba ta taɓa cewa ya sai mata wani abu ba, duk da yana jaddada
mata, duk abin da take so, ta tambaye shi.
Maitama ya zo gidanta bayan auren, sai dai yayi farinciki da
yadda ya tarar da mairamu, babu yunwa babu ƙishirwa, akwai kulawa sosai da
sosai.
Duk da kashedin da Bashir yayi musu a kan mairamu ba ta da
cikakkiyar lafiya, bai hana idan baya nan su azabtar da ita ba su tura ta gaban
hayaƙi ba.
A gidan Bashir ta fara al'ada, shi ma sai da matan suka yi
ta ƙanan maganganu, dan sun zata ciki ne da ita.
Ana haka Allah ya yi wa baffa rasuwa, babu wanda ya sani,
dan sai da yayi watanni uku, sannan maitama ya sani, ya saka aka gaya wa
Bashir.
Chubaɗo ta sha kuka, kamar babu gobe, ta shiga matsananciyar
damuwa da tashin hankali.
A haka ta shafe shekara guda cif, dada ta zo mata, ta ji daɗin
hakan, sai dai sai da suka kuma yin kukan rashin baffa.
Dada ta din ga rarrashin mairamu, dan ta fuskanci yanayin
zamanta da abokan zamanta babu daɗi, amma gidan akwai kulawa komai na buƙata
akwai.
Sai da ta shekara biyu, ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba, ko a
jikinsa, ita dai tana ta addu'a, Allah ya sa ita ma ta haihu, dan yar da aka
haifa hafsa kamar ta ce a bar mata, duk da idan ta ɗauka ayi ta yi mata
habaici.
Aka kuma canzawa Bashir wurin aiki, ya samu ƙarin matsayi,
ga aiki ga kaswuanci, ya sai wuri a kano, ya fara gini, saboda yana ƙaunar
garin kano, yana son idan ya gama, su koma can, ya nemi transfer ya dawo arewa
gaba ɗaya, dan a kano ya auri matarsa ta biyu, kuma garin ya burge shi.
Watarana da safe, ana shirin karyawa, jaririya hafsa ta fara
rarrafe, mairamu ta ce "Ki kula kar hafsa ta ɓaro kunu a jikinta"
aikuwa tana rufe baki, hafsa ta sheƙo kunu a jikinta, ta ƙone, tun a ranar suka
laƙaya mata maita.
Haka kurum ta fara rashin lafiya, abu yaƙi ci yaƙi cinyewa,
ga Bashir ba ya gari, aka rasa mai kaita Asibiti, abu har da suma, ciwonta kuma
ya tashi, sai masu aiki ne suka kaita Asibiti, a tsukin lokacin Bashir ya dawo,
ya sha baƙin ciki da ɓacin ran abin da suka aikata.
Duk ta rame ta yi duhu, ya mayar da ita Asibiti da kansa,
aka tabattar masa da tana da juna biyu. Ya din ga murna kamar ba a taɓa yi masa
haihuwa ba, sai dai yayi shiru da bakinsa, da ya tashi komawa aiki, ya ce da
ita zai tafi.
Suka yi surutansu da masifarsu, suka gama.
In da aka mayar da shi aiki, can wani gari ne a kudancin
Najeriya, a lokacin rabonta da hammanta, kusan shekara duk ta damu tana son
zuwa ganin gida, ya ce ta bari idan ta kusa haihuwa, zai mayar da ita gida ta
haihu ta yi arba'in.
Lokacin maitama shi ma babu zama, daga wannan gari zuwa
wancan gari, har ƙasashen da ake yaƙe-yaƙe a Afrika ake tura su aiki, dan haka
bai samu sukunin sake zuwa wurin mairamu ba, sai dai kullum tana zuciyarsa.
Tana yawan yi wa Bashir zancen makaranta, ya ce zai mayar da
ita, yana sane, dama target ɗin sa, ta haihu ko ɗa ɗaya ne, sai ya sakata a
makarantar.
Ashe matansa sun ƙwafe tafiyar da ya yi da ita a ransu, sun
ƙullace su, dama a hakan a rashin wayon nata, da azabar da suke yi mata, gani
suke yi ta mallake shi abin da take so kawai yake yi.
A can garin kuwa, yana bata kulawa iya yin sa, amma laulayi
ya sakata a gaba, ciwonta kuma kusan kullum cikin tashi yake, shi yake yi mata
komai yake kula da ita, cike da ƙauna da tausayawa, bai taɓa gajiyawa da ita
ba, sosai yake tausayinta, ba ta da wasu dangi, da za ace su zo su kula da ita,
ko ya kaita tayi rainon cikin a can, dan har ga Allah ba zai iya kaita rigar
nan tayi rainon cikin a can ba.
Idan ya samu lokaci, yana zuwa can gidan, ya yi kwanaki ya
dawo, cike da addu'a da fatan Allah ya sauketa lafiya.
Cikinta na da wata takwas, ya je gida, tun da ya je, gaba ɗaya
tamkar an shafe masa duk wani tunani da ya shafi mairamu, yazo da kwanaki biyu,
aka turo masa da takardar transfer, an mayar da shi aiki jigawa.
Bai ko sake komawa garin da ya baro marainiyar Allah ba, ya
je yayi reporting a wurin aikinsa na Jigawa.
"Abba, ina ga canza hanya zamu yi, akwai go slow sosai
a nan, maganar Nasir ta dawo da Abba daga tunanin da yake yi.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Major yayi wata irin nannauyar ajiyar zuciya, ba tare da ya
ce komai ba.
Nasir ya ce "Abba"
"Nasir, ko ma ta ina ne ka bi, fatana kawai na cimmusu,
shi kansa yaron na ji dalilin sa na shiga sha'anin iyalina ba tare da izinina
ba".
Nasir ya ce "Ina ga hakan baya rasa nasaba, da ta jikin
hoton da na kawo maka" Abba yayi shiru bai sake cewa komai ba.
Viper kuwa muryar Abbu ce ta cigaba da amsa kuwwa a cikin
kunnuwansa, ya din ga jin muryarsa har cikin ƙirjinsa. Gefensa Nabila ta na ta
kuka, ba yadda ya iya, ya ji zuciyarsa babu daɗi sam.
Ya matsa murya ƙasa-ƙasa ya ce "Ki daina yi mini wannan
kukan, na gaya miki ba na so ko?" Shiru tayi masa ta cigaba.
"Babu buƙatar mu je in da zamu je, kina kuka a haka,
idan kuma mu koma ne shikenan"
Cikin kukan ta ce "Ni ku tsaya ku sauke ni, koma ina ne
ba zan je ba"
Ya ce "Saboda me?"
"Yanzu ku ka gama ci mini mutunci da kai da abokanka,
bani da kamun kai, ina yawo a cikin maza, kai kuma dan na haɗaka da mahaifinka,
ya zama tashin hankali, har ka manta har da fushin iyaye ya jefa ka a musibar
da ka ke ciki, daga ƙoƙarin sasanta ku, wataƙila komai ya zo mana ma da sauƙi a
dalilin hakan, amma kalli yadda ku ke cin fuskata, wallahi ƙaddara ce ta kawo
ni in da ku ke, har gaban iyayena na bari nayi karatu, ban lalace ba, kuma ban
saki jiki da maza ba, duk aikin ƙaddara ne, da ƙoƙarin ceto rai, amma bakomai
na gode"
Sai kuma jikin liti yayi sanyi, Walid kansa bai ji daɗin
abin da suka yi wa Nabilan ba.
Walid ya ce "Yi haƙuri Nabila, dan Allah ki ke yi ba
dan halin su ba, kuma Allahn yana gani, shi ne zai biya ki, idan ki ka gama
shari'ar nan, duk ki watsar da su ki yi ta kanki, kar wanda ki ka sake nema.
Wallahi ni ina gani, kuma ina yabawa abin da ki ka yi"
Liti ya ce "Walid ba a haka, wannan ai ziga ce, ke yi
haƙuri haushi ki ka bani ne"
Zazzage jakarta ta fara yi, saboda numfashinta baya sauka
cikin ƙirjinta sosai, saboda kukan da ta yi.
Viper ya taimaka mata, ya ɗaukko mata inhaler ya saka a
bakinta, sau biyu ya fesa mata, ta saka hannu ta karɓa ta mayar ta saka a cikin
jakarta, tana share hawaye.
Message ya rubuta mata a wayarsa, ya tura ta ta, ya miƙa
mata ta karanta, ɗagowa ta yi ta kalle shi, suka haɗa ido, ta galla masa harara
ta gyara zamanta, tana kallon taga.
***
Asibiti kuwa sai da aka je da 'yan sanda, sannan suka karɓi
rahila, shi kuma Abba aka je aka kamo shi.
Tuni labari ya karaɗe gari, yaro ya yi wa uwassa duka, a kan
tayi masa faɗan daina ta'amalli da kayan maye.
Hannunta na hagu ta samu karaya, har guda biyu, ga gefen
wuyanta da ya kumbura yayi suntum saboda duka.
Abbu ya ce "Daga hannun yan sanda sai dai su san yadda
za su yi da shi, dan ba zai sake zamar masa a gida ba, ya koma hannun ubansa.
Abun takaici sai dangin rahila suka fara ƙananan maganganu
wai da ɗansa ne, ba zai ce zai kore shi ba, tun da abin ƙaddara ne, bai wuce
kan ɗan kowa ba.
Abbu ya ce "Ai ba ɗan nawa bane, nawa ɗan ma da ya ƙi
ji bai ƙi gani ba, dan haka ba zai yi mini kisan kai a gida ba, tun da ya iya
dukan uwarsa wataran ai ni zai daka"
"Yo Allah na tuba kisan kan, ai kai ba ka yi wa wani
gorinsa ba, tun da dai kai ma naka ɗan yayi, kuma in sha Allah, Allah ba zai
nuna mana wani yayi kisan kai a zuriyar mu ba"
Abbu ya ji zafin maganar da ƙanwar uwar rahila ta gaya masa,
amma ya haɗiye yayi shiru, bai ce uffan ba ya fice ya bar su.
***
Ramma abin duniya ya isheta, wata irin kewar Abdul take yi
kamar babu gobe, Abdul ɗan gayu ne kuma ɗan hutu, tun da ta ji an ce an kama
shi, sai ta ji gabanta na tsananta faɗuwa, da zata yi masa adalci roƙonta da ya
din ga yi, ta yafe masa yakamata ta yafe masa, da fari ta zata idan aka kama
shi, aka hukunta shi zata huce, amma sai ta ji ba haka ba, tausayin sa ma take
ji.
Gashi mahaifiyarta, ta saka ta a gaba, ko saurararta ma ba
ta yi yanzu, ta kuma dage a kan lallai idan tana son su zauna lafiya, to sai an
zubar da cikin nan, da ba zata taɓa yarda ta haɗa zuriya da marasa mutuncin
mutane irin su Abdul ba. Gaba ɗaya dauɗa ce take bin zuriyarsa babu na Allah
cikin su, mussaman zaluncin da aka yi wa ɗan ta Nura, wanda hakan yake ƙara
tunzurata ta ji tamkar ta yi wa ramma shegen duk ko zata huce.
***
A nesa kaɗan da ƙofar gidan suka yi parking, Viper ya ce
"Bari na je tukuna na dawo, ku jira ni ina zuwa"
Walid ya ce "To shikenan, babu matsala"
"'yar sugar am talking fa" yayi maganar yana
kallon ta.
Haɗe rai ta yi ta share shi, tana ta tura baki, tana son
tayi masa tsiwa, amma ta kasa sai harararsa da take ta gefen ido.
A zuciyarsa ya ce "Allah ya bamu ikon cin wannan
jarrabawa" ya sauka daga motar, ya nufi gate ɗin gidan, yana yaba cigaban
da suka samu, dan wannan gidan na su ya fi na cikin gari kyau da suka baro,
nesa ba kusa ba.
Ya tsaya a bakin gate ya fara bubbugawa.
Wani yaro ne ya buɗe, yana cewa waye, Viper ya ce "Ka
je ka ce ana sallama" yaron ya ce "To" ya koma cikin gidan,
mintuna kaɗan Tijjani ya fito, kawai suka yi arba da Viper, ya kalle shi, shi
ma ya kalle shi.
"Me ka zo yi mana gida kuma?"
"Wurin Baba na zo"
"Zai fi kyau ka kira shi da sunansa kawai, ba sai ka yi
masa kara ba, bayan ka kashe masa 'ya"
Kai tsaye maganar ta soki, tsokar da ke tsakanin ƙirjin
Viper wato zuciya, amma ya dake ya ce "Ina son ganin Baba, ka yi mini iso
wurinsa"
"Ba zan yi ba, baka da abin da zaka gaya masa....
"Shhh Viper ya faɗa, a lokacin da ya ɗaga wa Tijjani,
rigarsa.
Ya hangi ƙyallin iraƙi a ƙugun Viper "Haryanzu ina nan
a yadda ka sanni, in saka maka ƙarfe, in tsallake ka, na shige gidan nan, ba
zai zama sabon abu ba, a abin da na saba aikatawa ba, ka shiga ka yi mini iso
da mai gidan" gummm tijjani ya rufe bakinsa.
Baba kuwa ya san da zai yi baƙo, sai dai bai san wanene ba,
dan an kira an tambaye shi ne kawai yaushe za a same shi a gida, ya bayar da
wannan lokacin.
Yana zaune a falonsa, yana karanta jarida, Tijjani ya shigo
yana zazzare ido.
Mama ta ce "Lafiya kai da waye a wajen ne?"
Wata irin zazzafar ajiyar zuciya ya sauke, ya ce "Mijin
jauhar ne a waje, wai yake son ganin Baba" gaba suka yi sak suna bin sa da
kallo, a gigice Abba ya tashi ya ce "Wace jauhar ɗin? Waliyiyya dai? Kana
nufin Al'amin?" Ya jero masa dukkanin tambayoyin lokaci guda.
Zakiyya ta ce "Ya zo yayi mana me, ko kuma ya ce me?
Shi har yana da kunyar sake tunkaro mana gida, alhalin ya kashe mana 'ya? Kenan
da gasken dai sakinsa aka yi, yake yawonsa a gari yadda yake so?"
Hanyar fita Baba ya tunkara, Tijjani ya riƙe shi, ya ce
"Dan girman Allah baba kar ka fita, yanzun ma da makami a jikinsa, kar
yayi maka illa, ba fa mun san meya kawo shi ba.
Can waje kuwa, Saifu ne ya dawo, ya ajiye motarsa ya fito ya
nufo shiga gida, kawai ya ga Al'amin a tsaye.
Kamar mai mafarki, haka ya ƙarasa gaban gidan, yana kallon
Al'amin.
Ya ce "Kamar mai zamani mijin jauhar?" Viper ya
kalle shi, bai ce komai ba.
"Me ka zo yi mana gida, saboda rashin kunya da rashin
ta ido, sai yanzu bayan shekaru shida, ka zo ka kalli fuskokinmu, kaga wani
hali ka sanya mu a ciki, bayan sakayyar da ka yi mana, aka ɗauki 'ya mafi
haƙuri da tarbiyya a gidanmu a ka baka, duk tausayinta da soyayyarta gare ka
bai hana kashe ta ba, ka zo ka yi mana gadarar iyayen gidanka sun sanya an sake
ka ne kamar yadda ka saba?" Yayi maganar idanunsa na cika da hawaye.
"Har duniya ta naɗe, ka bar mana mummunan tabo a
zukatanmu, tabon da ba zamu taɓa yafe maka ba, babu yadda ban yi da ita a kashe
auren nan ba, amma taƙi ta dage, ita na rabu da ita tana son aurenta, ta san
zaka shiryi, zaka daina duk abin da ka ke yi, amma kalli irin ƙarshen da tayi
duk a dalilin rashin imaninka, wallahi ba zamu yafe ba" Viper ya ƙurasa
masa ido, ya rasa abin da zai ce masa, duk da a baya ba wani shiri suke yi ba,
amma yana ɗagawa saifu ƙafa, saboda yadda jauhar take yin sa, take yawan zancensa
da shi da hafsa, mussaman ma shi. Tabbas ya cancanci ya shanye duk wani abu da
za a gaya masa yau, komai ya samu shamuwa watan bakwai ne ya janyo mata.
Cike da ƙosawa Nabila ta ce "Ni fa gaskiya na gaji, wai
me yake faruwa ne?"
Walid ya ce "Ki ɗan ƙara haƙuri kaɗan, za ki ga koma
menene"
Babu yadda Tijjani bai yi ba, amma fafur baba yaƙi tsayawa,
yayi waje a sukwane.
Viper yana ido huɗu da mahaifin jauhar, kawai sai ya karaya,
gabansa yayi mummunan faɗuwa, bugun zuciyarsa ya ƙaru, jikinsa yayi sanyi
ƙalau, ji yake yi kamar ƙafafuwansa na neman gazawa da ɗaukarsa, bai san ma da
wane idon zai kalli baba ba, bai san me zai ce masa ba, rabonsa da shi tun kan
mutuwar jauhar, da ya kawo musu ziyara da daddare, har Viper ya kusa abun
kunya, bai san baba yana gidan ba, ya shigo yana mitar "To uwar son kuɗi,
yau ba oyoyon babu ɗan karairayar, Allah ya sa ba neman kuɗin ki ka ƙule a ɗaki
ki na yi ba" tana gaban baba, amma kamar ta nutse, sai da ya shiga falon
ya ga baba, kamar ya juya ya koma saboda nauyinsa da ya ji.
Baba yayi murmushi ya ce "Ka sanya a ranka ban ji komai
ba, ni babu abin da na ji"
Da kyar ya iya shiga suka gaisa, sun jima suna hira, har
baban ya ba wa jauhar ruwan tofi da ya karɓo mata, wai saboda haihuwa. Ya na ta
murna da ɗokin, zai ɗauki jika ta wurin jauhar.
Da Baba zai tafi, Viper ya raka shi, ya cigaba da yi masa
nasihar ya nutsu, ya zama mutumin kirki, saboda yana daf da zama uba, yayi
ƙoƙarin zama uba nagari ga abin da za a haifa masa.
Viper yayi masa alƙawarin hakan, tare da tabattar masa, duk
wani abu da zai gusar masa da hankali, ko yayi ɓarna, yana ta iya ƙoƙarin sa a
kan dainawa, kuma cikin ikon Allah ya rage kaso mafi yawa. Baba ya nuna masa
jin daɗin sa a kan haka, tare da yi masa addu'a.
Ba ayi sati da zuwa gidan ba, tsautsayin nan ya faru, kuma
ko a kotu, bai ga Baba ya je ba.
Viper cikin mamaki, ya ga Baba ya rungume shi, ya ce
"Sannu Al'amin, sannu da zuwa" ya riƙo hannunsa, ya buɗe gate ɗin
gidan, yana jan hannun Al'amin.
Saroro tijjani da saifu suka bi baba da kallo, duk tsawon
lokacin da ya shafe, yana gaya musu bai yadda Al'amin zai kashe jauhar ba, ba
su yadda da gaske yake ba, dan ya ce musu babu wata gamshashshiyar hujja a kan
hakan.
Suka ankarar da shi cewa, yana ta'amalli da miyagun ƙwayoyi,
dan haka ba abin mamakin bane ba, amma ya ce shi dai har zuciyarsa bai amince
da hakan ba.
Har tsakiyar falonsa ya shiga da shi, cikin murna da
farincikin ganin sa, ya ce "Zakiyya, ku kawo masa ruwa, sannu Aminullahi
amintaccen Allah, dama zan sake ganin ka bayan na rasa Waliyiyya? Sannu
Aminu" kawai Viper ya durƙusa a kan gwiwoyinsa, ya riƙe hannayen Baba, ya ɗaga
ido ya kalle shi, ya ce "Wallahi baba ban kashe jauhar ba, ban kashe
waliyiyya ba, me tayi mini me zai sanya na kasheta? Idan da wanda zai tafka
asarar mutuwarta to ni ne, ni ne nan baba, zan yadda idan aka ce nine sila,
amma da hannuna ban kasheta ba baba, ba ni na kashe maka jauhar ba, na san
duniya ba kowa zai yadda da hakan ba, amma na san ko yaya, kai zaka yarda da ni
Baba, wallahi ban kasheta ba, nayi burin kashe kaina nima, ko dan kaucewa sake
haɗuwa da kai, ban san me zan ce maka ba, ban san da wasu kalmomi zan yi amfani
ba, kawai dai ban kasheta ba"
Cikin rauni, da dattaku, Baba ya rungume Viper a kan kafaɗarsa,
yana dukan bayansa cikin sigar rarrashi, ya ce "Ko kowa bai yadda ba,
wallahi ni shaida ne Aminu, ni na san me na gani, na san me na ji daga bakinta
a kanka, kar ka damu, na san me ka ke ji, na taɓa tsintar kaina a yanayi mai
kama da naka, ina fatan Allah ya yi wa jauhar rahama, Allah ya sa halinta na
gari ya bi ta"
"Nayi asarar mace Baba, ta bar ni da raunin da ba zai
taɓa gogewa a zuciyata ba, ba zan fasa zargin kaina da ni ne silar mutuwar
jauhar ba, taurin kai da jinkirta barin aikata laifi, shi ya janyo mini haka,
ina kewar matata" tamkar ƙaramin yaro, haka ya kwantar da kansa a kafaɗar
Baba yana kuka, kukan da ya daɗe yana fatan Abbunsa ne ya fuskance shi ya bashi
wannan damar.
Baba ma kukan yake yi, ya ce "Haka Allah ya tsara, ka
yi haƙuri, mu duka na haka ne, zaman jiranta muke yi. Bayan an kama ka, mijin
yayarta hafsa da ya so ya aureta, shi ya zo ya same ni, ya ce mini in ci gaba
da addu'a, Allah ya bayyana gaskiya, amma ba kai ka kashe jauhar ba, abin ne
akwai sarƙaƙiya, duk da ni dama tun farko ban yadda zaka kashe mini 'ya ba. To
kuma daga baya ita ma hafsan zaman yaƙi daɗi, suka rabu".
Viper ya ɗago ya kalli Baba cikin mamaki, ya ce "Shi ne
ya zo ya ce maka bani na kashe jauhar ba?"
Baba ya jinjina masa kai, ya ce "Eh, shi ya gaya mini
haka"
Viper ya sauke numfashi ya share gumin da ya haɗa da hawaye,
da handkerchief ɗin sa.
Gaba ɗaya cirko-cirko mutanen gidan suka yi, suna mamakin
baba, yadda ya sake da Al'amin, wataƙila ma ƙarya kawai yake ta zuba masa, dan
kawai a tausaya masa.
Viper ya ce "Na zo da wata tambaya da nake buƙatar
amsarta baba"
Baba ya ce "wace tambayar ce?"
"Baba jauhar mutum nawa ce?"
Cikin mamaki baba ya ce "Kamar yaya?"
"Tana da wata 'yar uwa ne, da suke ciki ɗaya?"
"A'a itakaɗai ce"
Ya jinjina kai ya ce "Akwai lauyata, da muka zo tare,
zaku tattauna da ita, wadda ita ce tambayata da nake son ka amsa mini" ya
tashi tsaye, ya nufi hanyar fita.
***
"Kankarofi, zuwa yanzu ina fatan hankalinka ya kwanta
baka da wata damuwa ko?"
Ya kalli indabo ya ce "Ba ni da ita Indabo, kawo
ƙarshenka, babbar nasara ce, da rage mugun iri a ƙasa ko ma na ce duniya baki ɗaya"
"A'a, bari murna karenka ya kama zaki, da saura tukuna
baka kawo ƙarshena ba, kuma kawo ƙarshena tamkar kashe maciji ne, baka sare
kansa ba"
Kankarofi ya ce "Ko ban sare kansa ba, ya tashi, na
rage masa karsashi da ƙarfin mugunta da zalunci. Kuma in sha Allah wannan
kujerar da ka cimmata, ta hanyar zubar da jinin mutane bisa zalunci, da amfani
da rayuwar talaka ka cimmata, ka wofantar da su ka tagayyara rayuwar su, sai ka
barota, sai ka kuma fuskanci hukunci.
Yanzu haka ana shirin tsayar da kadarorinka, a kai gaban
shari'a bisa laifin sata wato cin amanar ƙasa, bayan babban tattalin arzikinka
da aka kama, na miyagun ƙwayoyi a Italiya. Ka san Waye yayi maka aikin kama ɗanka
da kama maka dukiya? Viper! Abin ya baka mamaki ko? Wani banbarakwai, da yake
ce maka ya saka an kama ɗan sa ka daɗe kana mamaki, da ganin ƙarya yake yi.
Dodo babban sarki ya fi ka lissafi, da shu'umanci indabo, sirrinka da ya sani,
ya san zaka kashe shi, ba za ku bar shi da rai ba, da shi da tawagarsa, shiyasa
ya ƙara jan Viper, ya sanar masa da duk wani abu da yakamata ya sanar masa. Duk
tsawon lokacin da Viper ya shafe tare da kai... Yayi shiru yana kallon Indabo.
"Spy ne, hatta yadda ka ke samun return da kai da
tawagarka, a kan tashe-tashen hankulan da ake yi a ƙasar nan, yadda ku ke
safarar makamai ta ɓarauniyar hanya cikin ƙasar nan, Viper ya sani, dodo ya
gaya masa, aikin contract rundunar tsaro ta bashi a kanka, kasancewar waccan
gwamnati duk gayyar tsiya ce irinka, ya sanya ba su iya yi muku komai ba.
Sannan Viper bai shafe shekaru biyar a gidan yari ba, yana
can yana karɓar horo na musamman a kan zama cikakken jami'in leƙen asiri. Idan
ku kuna amfani da doka, wurin tozarta ƙasa yadda ku ka ga dama, mu ma muna iya
amfani da ƙarfinmu ta ɓarauniyar hanya mu yi wa ƙasa aiki. Ina fatan yanzu ka
fahimci BODMAS ɗin da Viper ya gaya maka. Kar fa ka zarge shi, sam shi ma wasu
abubuwan bai san da su ba, tsuntsu biyu na jefa da dutse ɗaya.
Sosai ƙafafuwan Indabo suka fara karkarwa, saboda mamaki da
tashin hankali.
"Ka hanzarta, ka je ceil ka duba ɗanka, kar wahala ta
kashe shi, dan ya saba da hutun da aka samar masa ta hanyar zubar da jinin
dubban matasa, a kan harkar daba bayan ka basu miyagun ƙwayoyi, ka gina ɗanka,
gashi dai ka bashi ilimin, yana amfanar mutane, gefe guda kuma ya gado duk
miyagun halayenka, kuma a haka ka ke ƙoƙarin ɗora shi a kujerar mataimakin
gwamna, shi gwamna kai senator, ku cigaba da azabtar da mutane, tun da shi
mulkin gadon gidanku ne, you are not serious, Allah yana son bayinsa. Kuma ina tayaka
murna, saura wata guda kacal ayi recall election, mutanen yankinka za su yi
maka kiranye, abin da ba a taɓa yi a tarihin ƙasar nan ba, sai a kanka" ya
ɗauki glass cup ɗin ya bar falon.
***
Mamaki ne ya kama Nabila, ganin idon Viper yayi jawur, gidan
da ya shiga bai yi kama da na mutanen banza ba, balle ta ce ko shaye-shaye ya
shiga yi, hakan ya tabbatar mata da kuka yayi.
Ya kama hannunta, ya ja ta zuwa cikin gidan, kasa yi masa
magana ta yi, ta cigaba da bin sa.
Tijjani da saifu da suke tsakar gida, darewa suka yi, suka
ja da baya suna zazzaro ido, ganin wadda Viper ya shigo da ita.
Zakiyya kuwa iya ƙarfinta ta saka uban ihu, ta zura da gudu ɗaki,
tana dambe da ƙofa taƙi rufuwa, saboda razani da tsoro.
Nabila tsaywa tayi tana kallon dattijon, wanda shi ma ya
ƙame wuri guda yana kallonta, tun daga sama har ƙasa.
Ta baya Nabila ta ji an yi mata wata irin runguma da ƙarfi.
Hafsa ce, ta ce "Jauhar, sai da na gaya musu na ganki
rannan a asibiti, da na je ganin doctor Abdul yasar, amma suka ce bani da
hankali"
Jiki a matuƙar sanyaye, Nabila ta rungumeta ita ma, duk da
ba ta san wacece ba.
Hafsa cikin kuka ta ce "Kin haihu? Ina jaririn naki
yake? Mastern ne ya kai ki asibiti? Kin ga aurena ya mutu ko? Na sha wahala a
gidan Alhaji mu'azzam".
Nabila ta ɗaga kai ta kalli Viper, ta mayar da idonta kan
dattijon, amma ta kasa magana, sai lumshe idanunta take yi, tana rufewa tana
fatan jin amsar tumulin tambayoyin da ke bakinta, ba tare da ta iya furta ko
tambaya ɗaya ba, dan ji take yi, tamkar an kanannaɗe mata harshenta.
A tare Major da Nasir suka fito daga mota, cikin ikon Allah
suna fitowa, suka yi arba da liti da walid a tsaye a jikin motar da suka zo.
Nasir ya ce "Yauwwa Abba gasu nan, ina Viper yake, ina
ku ka kai Nabila?"
Liti ya ce "Ba a sani ba, kai a wa zaka zo kana yi mana
tsawa?"
Ya kalli liti ya ce "Ni ka ke gaya wa haka?"
"An gaya maka ɗin"
Major ya ture Nasir ya ce "Ina 'ya ta take, waye shi
yaron a cikin su?"
Nasir ya ce "Abokansa ne"
"Shi yana ina? Meya kawo mini 'ya nan yayi mata?"
Major ya yi maganar a matuƙar hasale.
Walid ya ce "Suna cikin gidan can" yayi maganar
yana nuna musu gidan da Viper ya shiga da Nabila.
Major ya tunkari gidan, liti ya ce "Wallahi bin su zan
yi, kar wannan mai kunnuwan ya je yayi musu wani abu"
Viper ya ce "Baba wannan ita ce tambayar da na zo maka
da ita, nake neman amsarta"
A hankali baba ya fara takowa, yana maimaita
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, subhanallah wa bi hamdihi, adada
khaliƙihi, wa rida nafsihi, wa zinatu arshih" yana miƙa hannun sa, yana
ƙoƙarin taɓa Nabila.
Da ƙarfin tsiya, Nabila ta ji an ja ta baya, har ta na
ƙoƙarin faɗuwa ƙasa, major ya nuna Baba da ɗan yatsansa ya ce "Kar ka
kuskura, baka da wannan ikon, babu wanda ya baka wannan damar, tsohon macuci ma
ci amana"
A hankali baba ya ce "Yusuf maitama"
Major ya ce "Bashir lamiɗo" suka kalli juna.
Baba ya ce "Bai kamata haɗuwarmu ta kansace a haka
ba"
"Babu wani abin kirki da yakamata a tsammata daga
azzalumin mutum, mara imani da tausayi irinka, haɗuwar da ta fi wannan muni ita
yakamata muyi. Ke kuma wuce mu tafi, da kin san wanenen wannan tsohon najadun
da abin da ya aikata wa babarki, da baki yi marmarin ganinsa a rayuwarki ba,
wuce mu tafi kafin nayi ƙasa-ƙasa da ke. Kuma da na san kana garin kano, da da
nayi retire ban zo kano na zauna ba"
Baba ya sha gabansu ya ce "Maitama, babu in da zaka je
sai ka gaya mini ita kuma wannan wacece, duk da ko baka faɗa ba, na san 'ya ta
ce, amma nauyin laifin da nayi maka bai kai zunubin da aikata mini ba, wacece
wannan?"
Major ya ce "'ya ta ce ta halak, wadda ba ta da uba, ba
ta da wani gata sai na Allah sai nawa, ni ne uwa kuma ki ni ne ubanta, babu uba
a tarihin rayuwar ta, na cireka a rayuwarta gaba ɗaya, dan haka kar ka sake
saka wa zuciyarka wannan 'yar ka ce".
"Amma maitama ka san zan iya shari'a da kai a kan abin
da ka aikata mini. Ka san me ka ce mini shekara ashirin da shida da suka
wuce"
A fusace Major ya ce "Ka daɗe baka yi ba, ni yakamata
na yi shari'a da kai, shekaru ashirin da shida baya, bisa cin amana da kisan
kai, zan iya cewa kai ka kashe 'yar uwata, dan haka ba abin da zaka tsinana wa
rayuwar Nabila, wanda ban yi mata ba"
Ƙara Nabila ta saki, ta silale ƙasa, nufarta suka yi gaba ɗaya,
Nasir ya durƙusa zai kai hannu kan Nabila, amma Viper ya hankaɗe shi gefe, ya ɗagota.
Galala ya buɗe baki, ganin yadda ya kusa kai wa ƙasa saboda
hankaɗewar da Viper ya yi masa.
Baba ma kan Nabila yayi, amma major ya durƙusa, zai karɓi
Nabila daga hannun Viper.
Nabila kuwa kanta ne ya juye, wani irin jiri ya ɗebeta, ta
faɗi ƙasa, wani irin kuka take yi daga cikin zuciyarta.
Viper ya riƙe ta gam, ya kalli major ya ce "Yallaɓai a
ganina, kamata yayi ku yi wa Nabila bayanin wacece ita, meyake faruwa, bai
kamata ta shiga cikin saɓanin da ku ka samu ba, abu ne da yake a tsakanin ku,
da ya faru shekarun da suka gabata.
"Wanene kai?"
"Mijin ta jikin hoton da na bayar a kai maka".
"Mmm mijin wadda ka kashe" major yayi maganar yana
kallon idanun Viper.
Su Saifu da suka fara leƙowa ɗaya bayan ɗaya cikin tsoro,
saifu ya ce "Baba ka yi mana bayani meyake faruwa ne? Mu da kai mun san
jauhar ta mutu, to wannan kuma wacece?"
***
Chubaɗo tun tana sanya ran dawowar Bashir, har ta fara
sarewa, ta fara tunanin ko wani abin ne ya same shi, ba ta iya yi wa kanta
komai sai da kyar, saboda nauyi da girman cikin da yake jikinta, abu kaɗan sai
haki, gashi babu wanda ta sani a garin, ko ta san wani ma, babu yadda za a yi
ta iya magana da su, ita ba yarensu take ji ba.
Cikin ta ya shiga wata na tara, ba ta iya cin komai sai dai
ta wuni a kwance, salla ce kawai take tayar da ita.
Kwanan cikin bakwai da shiga watanni tara, ta fara jin
alamun ciwon naƙuda, ga ƙuruciya, gashi ba ta san kan abin ba, dan haka ba ta
gane meyake faruwa ba.
Ciwo ya ci gaba da ƙaruwa, tamkar zata bar duniya, sai da ta
kwana biyu a haka, babu mataimaki sai Allah.
Cikin dare abu ya ta'azarra, ta rasa in da zata sanya ranta,
tana jin yadda abu ya tokare ƙasan mararta, amma yaƙi fitowa, tayi kukan ma abu
ya gagara ta tashi tsaye, ta durƙusa, ta kwanta kowanne ya gagara ta rasa abin
da za ta yi ta ji daɗi.
Ta ji fitsari ya matseta, ta tafi banɗaki amma ya fara zuba
a tsakar gida ashe faya ce ta fashe, ga ta ga banɗakin ta kasa shiga, ƙafafuwan
ta suka sage a wurin, dolenta ta durƙusa a wurin, ta fara nishi.
Tana jin kan jariri ya fito, amma gangar ciki ta ƙi fitowa,
ta yi iya yin ta abu ya gagara, ga numfashinta na ƙoƙarin ɗaukewa, kawai ta
nemi wuri ta kwanta daga durƙushen da take, ta zubawa sarautar Allah ido.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Wani irin nishi ne ya fara taho mata, ta yinƙura zata tashi,
amma ta kasa tashin, tun tana yi kaɗan kaɗan, har ta fara yi da ƙarfi, da tayi
wani ƙwaƙƙwara, santaleliyar jaririya ta faɗo jawur da ita, duk da mairamu a
galabaice take, haka ta yinƙura, ta tashi zaune, ta kalli jaririyar yadda take
ta wutsul-wutsul tana ƙoƙarin yin kuka, amma ruwan da yake fitowa daga bakinta,
ya hanata yin kukan yadda yakamata.
Ta janyo zaninta, ta fara goge wa jaririyar cikin bakinta,
tana kuka yarinyar na kuka, ta rasa yadda za ta yi da ita, ga zaren mabiyiyya a
jikinta, bai faɗo ba, gashi ba ma ta san ta yadda zata raba yarinyar da zaren
ba, wani irin mugun ɗaurewa, mararta tayi, tare da bayan ta, a take ta fara
sabon nishi, ciwo ya dawo sabo, tana tsoron tayi muƙursusu, ta danne jaririyar
hannunta, amma da masifa tayi masifa, ajiye yarinyar ta yi a gefe, ta cigaba da
jijjiga kanta, jin da gaske wani abu ne yake ƙoƙarin sake fito wa daga jikinta,
ya sanya ta tashi ta durƙusa, ga mamakinta wata yarinyar ce ta sake fitowa tare
da mabiyiyyar da suke ciki da komai, tayo waje, sai dai ita wannan tana ta
tsanyara uban ihu, kamar ana cire mata idanu.
Ta zauna da kyar, da zuba musu ido cikin tsananin so da
ƙauna take ce wa "Yanzu Allah duk nawa ne wannan? Allah na gode maka,
Allah na gode sosai da sosai Allah ka raya mini su duka, ka shirya mini su, duk
wannan nawa ne" tayi maganar tana murmushi tana kallonsu, sai dai kuma ta
fashe da kuka rashin sanin yadda za ta yi da su.
Ƙoƙarin jan jikinta take yi ta tashi, ta ɗauke su, amma abu
ya gagara saboda uban jinin da yake zuba daga jikinta.
Haka ta koma ta kwanta cikin ƙazantar da haihu a ciki, tun
tana ƙoƙarin ɗaukko su, har ta daina gani hankalinta ya gushe.
Ba ta da maƙwabta in da take, wani mutum ya wuce ƙofar
gidan, ya shiga daji ya yi itace, ya ɗoro a kan keke, da zai wuce ya ji kukan
jariri, da ya dawo ma haka. Har zai wuce ya fasa, ya sauka ya tsaya ya hau
bubbuga ƙofar gidan, amma shiru, ga kukan yana ji, ɗaya da sauti mai ƙarfi,
wani kuma yana tashi kaɗan-kaɗan kamar kukan jaririn mage.
Ya gaji da bugu, kawai ya kutsa kai cikin gidan, ja yayi ya
tsaya, yana kiran yesu, ganin mace kwance dama-dama a cikin jini ita da yara
har biyu ɗanyar haihuwa.
Da gudu ya fita nesa da gidan kaɗan, in da yake da mutane,
ya tattaro mutane, suka tafi gidan.
Sai a lokacin mata suka yanke cibiyar, aka naɗe yaran da ita
uwar, aka tafi da su Asibiti.
Likitoci suka buƙaci jini, a tsakanin mutanen, suka yi
voulanteer suka bayar, aka din ga saka mata, yara kuma aka ce madara, nan ma ba
su yi ƙasa a gwiwa ba, aka nemo madarar ba wa yaran, a lokacin duniya na
kwance, babu ƙabilanci da gudun taimako.
Sai da ta kwana uku a asibiti, ba ta san in da kanta yake
ba, dan daga baya jijjiga tayi, bayan an kaita asibitin.
Ga yaran aka ce dukansu su biyun, pnuemonia ce da su, dan ta
ɗaya har ta fi muni ma, taƙi yin kuka yadda yakamata.
Bayan chubaɗo ta farfaɗo, da kyar, ana so ayi magana da ita,
babu hali, ita ba ta jin yaren su, su ma kuma ba sa jin nata, gashi sai dai
tayi ta bin su da kallo, kamar tana son gane wani abu.
Sai da tayi sati biyu a asibitin cif, aka sallameta, suna ta
tambayar ta, ina ne gidan su, ina mijinta, amma ba baki sai kuka, har suka fara
tunanin ko yaran dakan kuka ne, wato marasa uba.
Suka mayar da ita gidanta, suka cigaba da kula da ita,
wannan ya kawo mata abinci, wannan ya kawo mata kayan sakawa ita da yaranta, da
safe da yamma haka mata suke zuwa, ayi wa yaran wanka, da ruwa mai zafi, sai
dai tsakaninta da su ido, sam ba ta jin yarensu, su ma ba sa jin nata.
Suka daina damuwa da sai sun san wacece, kawai suka cigaba
da hidima da chubaɗo, ta zauna cigaba da jiran Bashir, tana tunanin ko wani
abin ne ya tsare shi, ta dawo ta fara jin tsoro ko ya mutu ne a hanya ba ta
sani ba, gashi ba ta da kuɗin mota, ba ma ta san hanya ba, balle ta koma gida.
Ita kanta ta ƙi lafiya, ga damuwa ga kewar gida ga raino, ba
ta san kan abubuwa ba, ga jijjigar da ta yi, ta taɓa mata ƙwaƙwalwa.
Kusan duk sati sai an kai yaran nan asibiti, saboda yanayin
jikinsu, mussaman ta farkon, duk zuwan matan nan ba sa gane su, sai ta wajen
kukansu, ɗayar ba ta da kuzari sosai, amma ita chubaɗo tana kallon abinta take
banbance su, ta san wadda ta fara haifa.
Sai dai da daddare ta kan ɓuya tayi kuka, dan har da wata
dattijuwa, da take tayata kwana, tana tayata kula da jariran.
A haka tayi arba'in, a danginta dana Bashir babu wanda ya
sani, shi ma kuma a can, matansa babu wadda ta kuma yi masa zancenta, maƙwabta
idan sun tambayi matan gidan ina chubaɗo sai su ce musu ta tafi gida haihuwa.
Wani mutum ne ya buga ƙofa tare da yin sallama, chubaɗo ta
zabura, ta san duk yadda aka yi mai sallamar muslmi ne, ta zari hijjabi ta
fita, ta tarar wani abokinsa ne, Tahir, suka gaisa, ya ce "Ya aka yi na
ganki a nan? Jiya na haɗu da Bashir, an mayar da shi jigawa har ya cigaba da
aiki, kuma na zo nan, na tarar da ke, ke me ki ke yi a nan, gidan nan aka bani,
nima nan aka dawo da ni aiki, zan duba abun da babu na gyara"
Cikin damuwa ta ce "Au dama yana nan lafiya?"
Ya ce "Eh mana, jiya muna tare da shi a jigawa ma"
Cikin sanyin jiki ta ce "Dan Allah idan ka koma ka ce
ya zo ya tafi da ni, na haihu bani da lafiya"
Ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, meyake damun
Bashir ne?" Ya shiga ya ga yaran yayi musu addu'a, a haka har suka yi
magana da ɗaya daga cikin matan da suke taimaka mata.
Cikin takaici, ya ɗauki kuɗi mai yawa ya bata, yayi wa
mutanen godiya, ya ce a ranar zai juya, ya je ya samu Bashir, ya ji dalilin sa
na aikata wannan rashin mutunci.
Sai dai kana naka Allah ya na nasa, a hanya yayi haɗari ya
mutu.
Jin shiru, har sati biyu, chubaɗo ta tattara yaranta, ta bar
garin ba tare da masu kula da ita sun sani ba, ita tana fama da rashin lafiya
yaran ma haka, da kurmanci da kwatance, aka kaita tasha, ta din ga cewa Taraba
jalingo, aka sakata a mota, ta bayar da kuɗin, a cikin wanda abokin Bashir
Tahir ya bata.
A galabice ta ƙarasa rigar su, dare ya riga ya yi, tun daga
titi da ƙafa har cikin riga, ga yara, suna ta numfashi da kyar, ita ma sai haki
take yi ta ƙarasa.
Ta je ta tarar da gidansu babu kowa a ciki, ta buɗe ɗakin
maitama ta kutsa ciki, ɗakin duk ƙura, haka ta baje yaran suka kwana a ciki,
sai wayar gari mutanen garin suka yi suka ga chubaɗo da yara.
Ta tambayi ina dadarta, aka ce mata ta mutu, ruwa ne ya tafi
da ita, sun je kai amarya ɗaya rigar maƙwabtan su.
Ta ƙara kiɗimewa, halin da take ciki ya ƙara ta'azzara,
jikinta ya ƙara rikicewa.
Ga yara babu lafiya, kamar almajira, haka ta cigaba da
rayuwa a gidan itakaiɗai, sai dai a shanunsu, da suke wurin baban su bello, ɗan
uwan baffa, ana bata madara, idan sun yi tuwo suna bata ko kunu.
Ba yadda ba su yi da ita ba, suka tambayeta yaya ina auren
ba, ta dawo riga ta zauna, amma taƙi faɗa.
Yan garin suka din ga zunɗenta, wai kwaɗayi ne da zunubin
Jibo, duk ya janyo mata.
Yara maimakon su din ga girma, sai suka din ga yanƙwanewa,
duk suka lalace kamar yaran aljanu, gashi wasu lokutan tayi ta shirme, ba ta
iya gane meyake faruwa saboda jijjigar da tayi, gashi kullum cikin haki take,
ga jego kuma babu cikakkiyar kulawa. Yara kuwa kullum cikin amai da gudawa
suke, da tari da sarƙewar numfashi, sai dai a basu jiƙe-jiƙe da hayaƙi, aikuwa
suka ci-gaba da tsula gudawa ba ƙaƙƙautawa.
Sai da suka yi wata biyar, kwatsam Allah ya kawo maitama
garin, dan shi kansa bai san da mutuwar ramata ba, sayayya yayi ya zo ya
gaisheta, dan duk da baffa ya rasu, ba zai manta da alkhairi da kuma hidimar da
tayi da chubaɗo ba. Ya shafe watanni baya ƙasar, an tura su yaƙi can libiya,
dan matansa ma sun fara tunanin ko an kashe shi a can, shiyasa bai samu ya je
yaga chubaɗo ba, fatansa dama daga nan jalingo ya kwana biyu ya tafi Bauchi ya
ga Chubaɗo.
Sai dai abin da ya tarar ya ɗaga masa hankali, mairamu ta
koma baƙa, da ta ganshi ma sai da ta ɗan yi shiru sannan ta tuna shi.
"Mairamu shi Bashir ɗin ne ya turo ki riga ki zo ki yi
jego?" Ta girgiza masa kai.
"Ki yi mini bayanin, menene ya faru, kan na zane
ki"
Cikin rawar murya, ta gaya masa komai tiryan-tiryan, ba
ƙaramin mamaki ne ya kama shi ba, abin kamar almara ya din ga tunanin anya
Bashir yana hayyacinsa.
Ya ɗauketa da yaran ya nemi a garin wata ta raka su asibiti,
dan ya san za a kwantar da su, amma aka rasa mai yadda, ya ɗauke su zuwa
asibiti, sai dai kwananta biyu a asibitin, aka tura su Gombe, saboda zuciyarta
ta taɓu, tun lokacin tana da ciki.
Ya sha faɗa sosai a wurin ma'aikatan lafiyan, suka din ga
cewa a haka kamar yana da ilimi amma yayi wannan shirmen, aka yi sake tamowa ta
kama yara ƙanana, ita kanta uwar yunwa ce a jikinta, ga complication na jijjiga
da suka gano, bayan sun yi mata tambayoyi, ga kuma zuciya ta taɓu.
Shi dai bai ce komai ba, aka basu kwanciya.
Shi ne yake kwana da chubaɗo, da taimakon nurses yake kula
da ita, suka ce lallai ya samo mata mace, jinya dole sai da mace.
Ya rasa yadda zai yi, ya koma garin da ya fara karatu, su
sun samu cigaba sosai, ya ce a samo masa wadda zata yi masa jiyyar ƙanwarsa ya
biyata, aka samu wata 'yar dagaci, da aurenta ya mutu mai suna magajiya, ta ce
ita ko kyauta za ta yi, ba ta manta ɗawainiyar da ya din ga yi da mahaifinsu
ba.
A haka ya daddafa, ya koma can gidansa, ya sanar da matansa
abin da yake faruwa, Allah ya sauwwaƙe kawai suka yi masa, ba tare da wata tayi
karar bin sa ta duba mairamu ba.
Ya ɗaukko babban ɗansa Nasir, ya taho da shi, ya zo ya
duba mairamu, da jariranta, da suka yi masa kyau a ido duk da ba su da lafiya.
Abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, ɗayar kamar ba zata yi rai ba, ga
shi chubaɗo na fama da kanta, ga rainon yara marasa lafiya. Suka wayi gari ɗaya
ko numfashi ba ta iya yi, aka saka mata oxygen, ƙarin ruwa sai da aka aske mata
gashin kanta, sannan aka saka, jininta ma da za'yi gwaji, ta mararta aka samu
jinin.
Aka bawa maitama ɗayar aka ce ya kaita wani asibiti, ita ma
a saka mata oxygen nan space ya ƙare, ita ma kuma tana buƙata.
Yana tafe a mota, baƙin ciki da takaicin abin da bashir yayi
masa ya hana shi sukuni, kamar ya jefa yarinyar ta taga, gaba ɗaya ya ji
haushin yaran yake ji, ya din ga dana sanin rashin jin maganar baffa.
Kawai zuciya ta ɗebe shi, ya canza akalar motarsa, ya nufi
Bauchi.
Yana tafe a hanya, yarinyar babu kuka, babu komai, sai shan
hannunta da take yi, duk da tana ta haki. Bai manta ba haka uwar ma aka yi ta
fama da tana jaririya, amma aka ƙi kaita Asibiti. Yana tuƙi yana yi yana
kallonta, tayi bacci ta tashi, ta sha hannunta, ko uffan sai da ya tsaya ya sai
ruwa ya bata.
Saboda tsabar masifa da wahala, yaran da ya kai su fara
zama, amma suna kwance duk yunwa da zawo ya cinye su. Ya ja tsaki a fili.
Har ƙofar gidan ya isa, cikin matsananciyar sa'a, da ya aika
aka yi masa sallama da Bashir ya ga ya fito yana gari, sai da ya ga maitama,
sannan ya tuna da wata halitta wai ita mairamu.
"Ka bani kunya ka bani mamaki Bashir, meye ribar abin
da ka aikata ka wulaƙanta mini 'yar uwa, ka tozarta ta? ta haihu a wulaƙance,
ka ci amanata, amma na bar ka da Allah, ga wannan nan, ita ce mai alamar zata
rayu shima wataƙila, yar ka ce na kawo maka, yar uwata ba zata mutu tana yi
maka wahala kana gefe ba, kana tsula rashin mutunci.
Kuma, ka gaya mini menene matsayar aurenku a yanzu? Tun da
ta ce baka saketa ba"
Bashir ya kalli maitama, ya kalli yarinyar da take ta bacci,
ya ce "Na saki mairamu, Saki ɗaya Allah ya haɗa kowa da rabonsa, 'ya ta
kuma na karɓa Allah ya raya mini"
Cikin tashin hankali ya kalli Bashir ya ce "Ka saketa,
ba sakin ne ya bani haushi ba, amma laifin me tayi maka?" Bashir ya
girgiza kai alamar babu.
Maitama ya haɗiye yawu mai matuƙar zafi da ɗaci, ya so ya
sanar masa yaran biyu ne, amma sai ya kasa saboda tsananin mamaki. Kuma ya san
wadda ya baro, wannan yarinyar kafin ya koma ta rasu, saboda ta galabaita da
yawa, dan haka ya ga babu amfani gaya masa, ya ce "Na gode Bashir da
wannan tukuici, ya taka ce dama, an bar maka halak malak, zan nesan ta ka da
mairamu nesantawa ta har abada, kuma in sha Allah duk wani sukuni da nutsuwa da
ake samu da walwala a sanadin aure ba zaka same shi ba, kai da Allah da ni da
zuriyarmu ba zaka sake ganin ire-iren mu ba, in sha Allah zamu ƙaddara babu
wata alaƙa, ko wani abu da ya jiɓanceka a rayuwarmu" A hankli yarinyar ta
buɗe idanunta, ta ƙura wa maitama, sai kuma ta wangale masa dadashinta tana
dariya, tare da jan numfashin ta da kyar.
Maitama ya juya ya nufi motarsa, yana jin tamkar ya fasa
ihu, Bashir kuwa ji yayi sakin mairamu kamar ya saukewa kansa wani nauyi ne, ya
shiga da yarinyar gida, cike da ƙaunarta.
Bashir yana tafe a mota, kawai tausayin mairamu ya lulluɓe
shi, sai kuma ya din ga tunanin da ya sani, bai ɗauki yarinyar nan ya bashi ba,
ita menene laifinta, dariyar nan da ta yi masa, sai ta tsaye masa a ƙirjinsa,
ya kasa mantawa, ganin ita ma a galabaicen take, ya sanya ya din ga addu'a
Allah ya sa yarinyar ta mutu, dukkansu ma su mutu kowa ya rasa, shikenan babu
sauran alaƙa a tsakanin sa da Bashir.
Yana komawa da daddare, aka din ga tambayarsa ina Husna
take, ya jikinta, dan dama Hassana da hussaina kawai ake ce musu, a asibitin,
ta ce ba ta san sunan su ba. Dan ita wannan yaran kawai take cewa, kasancewar
su yaran fari.
Mairamu na kan gado na fama da ƙarin jini, ta ji nurses na
tambayar "Ya jikin haussaina"
Mairamu ta ce "A'a, ba ita ba ce, babbar ce ya tafi da
ita, ƙaramar tana nan"
"Allah ya yi mata rasuwa a hanya, har an binneta ma,
shiyasa ban dawo da wuri ba"
Duk da ƙirjinta ya buga da ƙarfi, amma ta dake, a matsayin
ta na bafulatana, bai kamata ta nuna damuwa a kan ɗan fari ba.
Maitama ya sha mamaki, da ya ga jaririyar da ya bari ta fara
farfaɗowa, bai taɓa tunanin zata ƙara mintuna talatin ba ta mutu ba. Da an
tambayi ranar da aka haife su, nawa ga wata, sai mairamu ta ce ba ta sani ba,
ita dai ta san ranar arfa ne.
Maitama ya tambayeta, ainihin sunan da za a saka wa
jaririyar.
Ta ce duk sunan da ya saka shikenan, kasancewar yana son
sunan Nabila, sai ya saka mata Nabila, ya ce "Tun da ranar arfa aka haife
ta bari mu saka mata sunan 'yan gayu, arfa"
Tsananin tausayin Nabila da wahalar da ta sha, ya sanya ya
fara yi mata wata irin soyayya, da fari ba dan tafi jigata ba, ya so ace ya haɗa
har ita ya kai wa uban su, shi ya kula da ƙanwarsa, tun da ba shi da mutunci,
amma idan ya tuna yadda yarinyar da ya baro, ta kalleshi har da ƙarfin hali
dariya, sai ya ji babu daɗi a ransa.
Hutunsa ya riga ya ƙare, dan haka ya ɗauki chubaɗo, ya tafi
da su illori, in da yake aiki a lokacin.
Ya mayar da ita asibitin sojoji, sai dai ya lura da yadda
idan chubaɗo ta zauna take yawan shiru, ta saka damuwa a ranta sosai.
Cikin kulawa ya ce "Mairamu, ke da ake fatan ki samu
lafiya, menene kuma na tunani da saka damuwa a rau?"
Ta ce "Bakomai, yarinyar nan har ta mutu, babanta bai
taɓa ganinta ba, ina ga ko shi ma mutuwa yayi ba a sani ba" duk tsananin
kunya irin ta ta, hakan ya tabattar masa da damuwar rashin 'yar ta ne da kewar
mijinta yake damunta, haka yayi ta rarrashinta, ƙasan zuciyarsa yana jin, ba
zai iya yafe wa Bashir ba.
Aka sallame su, suka koma gida, baba magajiya ke yi wa arfa
komai, da taimakon Nasir, da kullum yana liƙe da arfa, yana raino.
Sai a lokacin ya yi wa Nabila hakika, sai dai an hana
mairamu cin jan nama a lokacin.
Yayi mata suturu, ya yi wa Nabila kayan sakawa masu kyau na
zamani.
Sai da babar Nasir ta magantu a kan "Wai dan Allah ina
uban yarinyar nan, da ka ke ta wahala, tun da ka dawo da su, bai zo ya duba ta
ba, ai hakkinsa ne"
Ya bata amsa da ba ta da uba, ni ne uban.
Can Bauchi kuwa, Bashir matansa sai ganinsa suka yi da
jaririya, suka tambaye shi wannan ƙarmasashiyar 'yar fa a ina ya samo ta.
"'yar wurin waccan yarinyar ce, yanzu yayanta ya kawo
mini ita, dan ya tura mini takaici, ni nama manta da ita gaba ɗaya, na karɓi
kayata ina son abata".
"To kai ya zaka yi da jaririya, saboda rashin mutunci
da zalunci, sai a ɗaukko wannan yar mitsitsiyar yarinyar, duk a tsotse ta kusa
mutuwa a kawo maka, kai amma mairamu azzaluma ce, kalli ƙashin haƙarƙarin
yarinyar, kamar fara sai uban fari da gashi kamar horo".
Ya sake gyara ta a cikin zani, ya kalli Zakiyya ya ce
"Zakiyya, ko ke zaki shayar da ita, tun da kin ga shayarwa ki ke yi"
Ta buga tsalle ta ce "Wallahi ba zata ba wa 'yar mayu
nononta ba, wannan yarinyar abar tsoro, ta tsotse mini jini a banza, wallahi ba
zan bayar ba"
Uwargidan ta ce "Dama ni ban haihu kwanan nan ba, dan
haka bani da abun bata, ban da jakanci irin na mutumin daji, kawai ku wofantar
da jaririya haka, Allah wadaran naka ya lalace"
Ƙarshe sai azare ya koma, aka kaita Asibiti, aka lalubi mai
shayarwa a dangi, sai dai danginsa ba ƙaramin zagi suka yi wa su chubaɗo ba,
bayan da ya gaya musu rabuwa suka yi aka dawo da yarinyar.
Wadda ta karɓi 'yar ta ce 'Kai kuwa basiru, me yarinyar nan
tayi maka, ka saketa? Duk haƙurinta da biyayyarta" yayi shiru, dan shi
kansa ba shi da amsar tambayar da ta yi masa.
Illori, arfa ta murmure tsaf, idan maitama yana yi mata
wasa, yayi ta ce mata gawa taƙi rami, chubaɗo ta gaji, ta ce wa magajiya, dan
Allah ta ce wa hammanta, ko za aje a duba ko baban yaran mutuwa yayi, ko wani
abin ne ya same shi.
Da ta gaya masa, sai ce mata yayi babu buƙatar hakan, dan ba
zai iya kallon mairamu, ya bata saƙon sakin da Bashir yayi mata ba.
Har Arfa tayi watanni tara, mairamu na jinya, matan maitama
suka ɗora mata tsana, baya ta tasu sam, komai chubaɗo komai ita, magajiya kuwa
ta ji daɗin zama, ta zauna tare da su, ta ci-gaba da rainon Nabila cikin
soyayya da ƙauna.
Dare ɗaya chubaɗo ta tashi numfashi ya sarƙe, suka ɗiba suka
yi asibiti, kwananta biyu a asibiti ta daina magana, ta kasa tashi.
Hankalin maitama ya ƙi kwanciya, ya rasa abin da yake yi
masa daɗi, ya rikice ya kasa zaune ya kasa tsaye.
Kwana na biyar, ya zo dubata, ta buɗe idonta, ta kalle shi,
ta miƙa masa hannu, ya kama hannun nata, ya durƙusa a gaban ta, ta ce
"Nabila" karon farko da ta kira sunanta.
Sai kuma ta sake ce wa "Bashir" shi ma karon farko
da ta kira sunan sa a rayuwarta, "Allah ya sa 'ya ta ta samu lafiya, ka ɗaukko
mini ita"
A hankali ta lumshe idanunta, ya zata bacci tayi, ashe
tafiyar kenan.
Ga shi namiji, ga shi soja, amma ya kasa jarumta, ya rikice
tamkar hankalinsa zai gushe, ya ji mutuwar chubaɗo, fiye da yadda ya ji mutuwar
iyayensa.
Bayan rasuwar ta, ya yi niyyar sallamar magajiya, amma matan
suka nuna masa ba zasu riƙe Nabila ba, kai tsaye babar Nasir ya fara danƙarawa
saki, baba magajiya ta yi ta bashi haƙuri, ta ce zata ci gaba da zama ta kula
da Nabila.
Bayan wani lokaci ya haɗu da wani ɗan garin su Bashir, yake
gaya masa ai kwanaki wata 'yar wurinsa mara lafiya ma ta rasu, hakan ya saka
maitama zata ko jaririyar nan ce, amma yar wurin zakiyya ce da take shayarwa
taƙi haɗawa da Nabila, ta mutu.
Ya ƙallafa soyayyar Nabila a ransa, gani yake yi tamkar
chubaɗo ce, ga pneumonia ta koma mata Asma, bai yi mamaki ba, dan dama larurar
mairamu ce. Hakan ya ƙara sanya wa yake kaffa-kaffa da ita.
Gashi saboda yawo tsakanin dazuzzukan barrack a garuruwa, da
maitama yake yawo da su saboda wurin aiki, Nabila ta kwashi aljanu, dan dama ba
ta jin magana ko kaɗan, hakan ya ƙara mata baƙin jini a gidan, gashi ba ta taɓuwa.
fitinar Nabila ta mussaman ce, saboda larurarta, ga tsalle-tsalle, da
iface-iface da an taɓa ta ba wuya ta faɗi, ko kuma asma ta tashi. Ba ta aikin
fari balle na baƙi.
Da ta isa shiga secondary school, ta ce ita boarding take
so, babu yadda maitama bai yi da ita ba, ta dage ta ce ita sai boarding. Haka
aka kaita boarding jss1 cikin ƙedaren arna ƙabilu, a ajinsu ta haɗu da sumayya,
ita kaɗaice bahaushiya musulma. sai ya sanar musu larurarta, saboda kar a samu
matsala.
Da farko faɗa suka fara yi, daga baya ya zama ƙawance,
sumayya ba ta da hayaniya, Nabila kuwa akwai fitina da neman magana.
Mahaifinta ya rasu, coustom ne a hatsarin mota, wan
mahaifinta ne ya kawo ta boarding, idan aka yi hutu kamar kar su rabu, Sumayya
a mayar da ita Kano, Nabila kuma tana nan garin su na Bayelsa lokacin, Maitama
ya zama major.
Ya saba da ƙanin mahaifin Sumayya, wataran idan hutunsu ba
yawa, a gidan su Nabila take zama, komai tare yake yi musu.
A makarantar akwai tsirarun musulmai, da malamin da yake kai
koyar da su ilimin addini.
Idan an yi hutu ma, akwai malamin da yake zuwa gida, koyar
da Nabila karatu.
Nabila ta ce ita ma soja take son zama, Abba ya ce ba ta isa
ba, har kuka ta yi, wai ita a lallai sai ta zama soja, ga samarin inyamuran
nan, suka yi mata caaa lokacin da ta zama budurwa.
Abba ya ce ba zata yi soja ba, ta ce law zata yi.
Suka haɗa kai da sumayya, wai Benin zasu tafi jami'a, Abba
ya ce bai yarda ba, saboda ba ta da cikakkiyar lafiya. Tun suna sakandare idan
ciwo ya tayar wa Nabila, sumayya ce take jinyarta.
Ganin ya hanata zama soja, yanzu kuma ta kawo issue na ga
makarantar da take so, ya ƙyaleta, ita ma sumayya ɗan uwan babanta yana ta
ƙoƙari, ya ce sumayya ba zata je Benin ba, major ya lallaɓa shi, ya ce su yi
musu addu'a.
Ɓangaren Bashir kuwa, jaririyar sa ya saka mata fatima
jauhar, kamar ba shi da wata 'ya sai ita, Allah ya jarrabe shi da son yarinyar
nan.
Ana yayeta ya je ya ɗaukko ta, cike da makirci, mama ta karɓa
ta ce ita zata riƙe, saboda ta ƙara samun fada a wurinsa, dan kuwa ya ƙara
samun rufin asiri lokacin, dan sun koma kano ma, yana ƙoƙarin barin aiki ma.
Bawa aiki da kasuwanci muhimmanci, haɗi da sakaci da ibada,
sallolin farilla kawai ake samun yi, babu azkar da neman tsari, hakan ya sanya
matan Bashir samun damar ci gaba da yi masa asiri, kowacce so take ace babu ya
ita.
A ƙarƙashin zuciyarsa yake jin wani irin nauyi a cikin
zuciyarsa, kamar akwai wani babban bashi a kansa, da yakamata ace ya sauke,
amma ya rasa menene.
Bashir yayi aure-aure, amma su zakiyya na hana su zama, su
kansu mugunta suke yi wa kansu, amma sun kasa galaba a kan junansu.
A wayance, tun jauhar tana ƙaramar yarinya, take fuskantar
izaya kala-kala, amma Bashir ba ya iya magana, duk da yana matuƙar tausayin
jauhar.
Bai taɓa zancen kaita wurin babarta ba, ko kaita garin su
ba, sai dai hoton ta, da ya nuna mata.
Nabila ta kammala makaranta, jin zasu koma kano, kamar ta
taka rawa, dan tana tunanin rabuwa da Sumayya, saboda shaƙuwar da take tsakanin
su.
A Kano tayi bautar ƙasa, ta fara aiki, duk da ba wani zama
take a gidan major ba, ta tashi ana nuna mata ƙiyayya muraran a gidan, daga
baya ta fuskanci major ba shi ya haifeta ba, dan haka ta saka shi a gaba, da
tambayar ina babanta, tun da ya ce mamanta ta mutu, sai dai ta kan fuskanci
mummunan ɓacin rai, a duk lokacin da ta tambaye shi.
Tun tana yarinya, major ya gargaɗi Magajiya da Nasir, a kan
kar a kuskura, Nabila ta san cewa su biyu aka haifa, duk da ya samu labarin
mutuwar ɗayar, kuma yayi mummunan gargaɗi a kan yi wa Nabila duk wani zance da
ya danganci mahaifinta, domin ya yanke duk wata alaƙa tsakaninta da mahaifinta
har abada.
Ta na yawan mafarki da wata mai kama da irinta sak suna wasa
tare tun tana yarinya, idan ta farka tana jin tsananin ƙaunar yarinyar da suke
wasan tare, idan ta gaya wa baba magajiya, sai ta ce mata shirmen mafarki ne da
iskokanta.
Sai dai daga baya ta daina mafarki da ita, daga baya kuma
bayan ta girma sosai, ta cigaba da mafarkinta, har cikin zuciyarta take jin
matsananciyar ƙaunar wadda take gani a baccin nata. Sai dai yadda take ganinta
daga baya bayan ta girma, cikin damuwa take ganinta, tana nuna mata inuwar wani
mutum a cikin sarƙa.
Ta samu baba magajiya ta ce "Wai ni baba anya ba 'yan
biyu ba ce ba? Yarinyar da nake mafarki ba ta girma ta zama kamar ni".
"A'a yan dozen ne ba biyu ba, gane-ganenki ne na
makaran kanki, suke buɗe miki ido, dama ai tun kina yarinya ki ke yi" ta
shiriritar da maganar.
Wataran suna camp, ta sake mafarki da yarinyar, tana kuka
tana nun mata na cikin sarƙar, ta farka a razane sai ta ji kamar muryarta a
zahiri tana kiran sunanta "Nabila" tsakiyar dare ta tashi zata fita,
aka riƙeta da kyar.
Ta daina mafarkin mai kama da ita, sai inuwar wannan mutumin
a cikin sarƙa, da take gani babu yau babu gobe a cikin baccinta.
Da kyar Nabila ta kalli Viper, ta na suffanto inuwar wanda
take gani a cikin bacci.
Motsa bakinta take yi, tana son tayi magana, amma ta kasa ta
ɗago hannunta da kyar tana nuna Viper, amma bakinta ya hau karkarwa.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Bakin Nabila ya cigaba da karkarwa, idanunta suka fara
ƙoƙarin kakkafewa.
Liti ya na tsaye daga baya a jikin bishiyar umbrella da take
tsakar gidan, wani irin tausayin Nabila da jauhar har ma da Viper ya mamaye
shi, har gara ma Viper, shi yanzu idan da sabo ya riga ya saba, ita kuwa an
rabata da 'yat uwatta, an nesanta su da juna, kuma ta rasu ba su haɗu ba, sosai
ya ji nadamar abubuwan da ya din ga yi wa Nabila.
A hankali Viper yake ɗan girgizata, yana kiran sunanta
"Nabila, me yake damunki?"
Su Zakiyya da suke ɗaki kuwa, gaba ɗaya suka yi sak, dan sun
san su ne kanwa uwar gamin abin da ya faru.
Baba ya miƙe hannu zai taɓa Nabila, major ya riƙe hannunsa
ya ce "Bashir, haryanzu ina nan a kan bakana, babu kai babu abin da
mairamu ta bari, ba zan taɓa baka Nabila ba, kuma ka cire a ranka Nabila ba
'yar ka ba ce ba"
"Yanzu maitama abin da ka yi kana ganin daidai ne? Baka
gaya mini yarana biyu ba, ka kawo mini ɗaya ka nesanta ni da ɗaya? Zan iya
ƙararka fa a kan abin da ka yi mini"
"Shut up! Ko kuma ni na yi ƙararka ba, da ka kashe mini
'yar uwa, ai dai na kawo maka ɗayar ko, ka aura wa ɗan daba ya kasheta, kai ka
sani" Viper ya yinƙura da Nabila a hannunsa, sai wata irin miƙa take yi,
ya nufi waje da ita.
Bayansa suka biyo, Bashir sai share hawaye yake yana kiran
"Aminu ina zaka kaita ka tsaya na ga 'ya ta".
Cikin ɗaga murya, major yake yi wa Viper magana, a kan ya
tsaya, Nasir kuwa kasa shan gaban Viper ya yi, gaba ɗaya suka bi shi. Sojan da
ya kawo su, yana ganin Viper ya fito, ya buɗe masa mota, ya saka Nabila a ciki.
Saifu ya riƙe shi ya ce "Ina zaka kaita, dole fa ka
tsaya a gama wannan tarzomar"
"Cika ni" Viper ya yi maganar yana kallon saifu.
Saifu ya cika shi ya ja da baya.
Viper ya kalle su ya ce "Zan mayar da ita asibitin
barrack, idan na bar muku ita a nan, zan iya yin laifi tun da tana ƙarƙashin
kulawar jami'an tsaro ne.
Walid taho mu yi gaba, su taho tare da liti"
"A'a shi dai su taho tare"
Zakiyya ta ce "To a tafi babu wata mace, mu tafi gaba ɗaya
mana" kafin Viper ya bata amsa, Hafsa ta ture shi, ta shige cikin motar,
yanayin yadda ta shiga kawai zaka gane kan babu daɗi.
Ya kalli saifu ya ce "Ka shiga ka riƙeta mu tafi"
Hafsa ta ƙanƙame Nabila, tana kuka ta ce "Yaya saifu,
rannan ba ce muku naga Jauhar a asibiti ba, aka ce bani da hankali, to ai gashi
yanzu ta dawo ba ta mutu ba"
Walid da Viper suna gaban mota, sai da Walid ya waiwayo
gwanin ban tausayi, bai manta hafsa a da ba, yar gayu 'yar ƙwalisa, jawur da
ita ta sha mai, amma yanzu duk ta koma baƙa ta firgice.
Har suka isa barrack, Nabila tana wannan miƙar bakinta yana
rawa, viper ya ce a ƙarasa da su asibitin sojoji, saifu ya ce "Anya wannan
abun ba aljanu ba ne?"
"Ba wani aljan" Viper ya faɗa a daƙile.
Sai dai suna isa, aka ɗauki Nabila aka shiga da ita, Viper
ya yi wa ma'aikatan alama, da karba bari kowa ya shiga in da take.
Tafiya ce mai nisa sosai, daga gidan baban Nabila zuwa
asibiti, amma har suka zo, jikinta a sandare yake, dai dai idan ta motsa tayi
miƙa kawai.
Alluran bacci kawai aka yi mata, sai drip na babu gaira babu
dalili, kusan ko ina a jijiyoyin hannunta akwai tabon hudar cannula.
Major ya fara tambayar ina aka kai masa 'ya, aka ce masa an
hana kowa ya shiga in da take. Cikin hasala ya ce shi ma fa tsohon ma'aikaci ne
kamar yadda yake gaya musu, dan me za ace ba zai shiga ba.
Aka ce masa ba bisa umarnin sojoji aka hana kowa shiga
wurinta ba, bisa ga umarnin likitoci ne.
Baba ma ya ƙarasa tare da tijjani, yana kiran wayar saifu,
dan ya gaya musu, a in da aka kwantar da Nabila, bayan su haɗu, saifu ya sanar
masa an hana kowa shiga.
Baba bai damu da irin mugun kallon tsanar da major yake yi
masa ba, babban burinsa kawai ya sake tozali da kyakywar fuskar 'yar sa, mai
kama da jauhar Waliyiyya, kuma kamannin mairamu chubaɗo.
Walid ya kalli liti, da kamar ya koma kamar ɗan tsakon da ya
faɗa ruwa, duk yayi tsuruu da shi, kamar mara gaskiya.
"Ya dai liti?"
"Walid zuciya da saurin fushi ba su yi ba"
"Meyafaru?"
"Yarinyar nan wani irin mugun tausayi ta bani, wallahi
kamar na yi kuka, tabbas na daɗe da gane ba ita ce jauhar ba, tun da damu aka
yi jana'izar ta, hausin abin da wancan banzan yayi mini mai ƙugu kamar an miƙo
kare ta taga, da rashin kunyarta da shishishigi da take yi wa Viper, ya sanya
na ji na tsaneta, haka kurum idan yana saurarenta, sai na ji kamar ya na cin
amanar jauhar ne, ko bayan mutuwar ta, bai kamata ya kula wata mace ba"
"Abin da nayi ta nuna maka kenan liti, amma ka ƙi
ganewa, kullum cikin yi mata rashin mutunci ka ke, ji maganganun da ka caɓa
mata muna tafe a hanya. Ai a duniya idan zaka yi ƙiyayya ka yi ta sama-sama
haka ma soyayya amma kawai ka je ka yi ta hantararta, ashe abin da yayi jauhar
shi ya yi Nabila"
"Amma kamar su ta yi mugun ɓaci fa, ni fa na daɗe ina
kokwanton idan ba fatalwar jauhar ba ce, halayensu da na din ga nazarta na
fuskanci wannan sai a hankali, gaba ɗaya sun sha banban ta fuskar halayya, amma
hatta muryarsu iri ɗaya, sai dai ta jauhar ta fi sanyi da nutsuwa, wannan kuwa
tsabar tsiwa da masifa ce a cikin ta ta muryar, Allah sarki Allah ya jiƙan 'yar
madara". Walid ya amsa da Amin.
Major kuwa ganin Bashir ya kafe ya nace, ya sanya ya Kalle
shi ya ce "Bashir, ka kama hanyarka ka bar wurin nan, wallahi ko me zaka
yi, ba zan ba ka Nabila ba, kar ma ka yi tunanin ayyana kanka a matsayin
mahaifinta"
"Maitama babu in da zan je, har sai ya ta ta farfaɗo,
kuma sai ka bani kayata na tafi da ita"
"Ita ma ka je ka aurawa ɗan daba ya kasheta kenan"
Bashir ya ce "Ko ma wa zan aurawa, 'ya ta ce, ina da
iko a kan aba ta"
Saifu ne ya din ga ba su haƙuri, a kan su yi haƙuri su daina
abin da suke yi.
Viper kuwa yana zaune a cikin ɗakin, da take tana bacci,
yayi alwala ya gabatar da salla, sannan ya nemi wuri ya zauna yana danna
wayarsa.
Ya ɗago ya kalleta jin ta yi tari, bacci take yi, amma
yanayin fuskarta ya nuna ba daɗin baccin take ji ba sam.
Sosai Nabila take kama da jauhar, babu yadda za ayi ka ce ba
mutum ɗaya ba ce ba, sai ka rayu da jauhar, ka dawo ka rayu da Nabila, zaka
fuskanci su na da banbanci.
Amma mafi yawa they have so many things in common.
Ya mayar da kansa kan wayarsa, ya ci gaba da daddanawa, bai
fargaba kawai ya ga ta tashi tsaye, ta fizge ƙarin ruwan, jini yana zubowa daga
hannunta.
Da azama ya tashi, ganin idanunta a rufe ko gani ba ta yi,
ta nufi hanyar fita daga ɗakin.
Shan gabanta ya yi ya ce "Ina zaki je?" Da kyar ta
buɗe rinannun idanunta ta kalle shi, ta je uban tsaki, ta raɓa shi za ta wuce,
amma ya riƙe ta, ya danne hannunta da yake zubar da jini.
Ya ce "Abla, menene? Meyake damunki?" Ta tsaya
ƙyam sai rangaji take yi kamar wadda ta sha ta bugu, tana lumshe idanunta ta na
buɗe su.
"Abla" ya sake kiranta a hankali.
Kamar wadda ta farka daga bacci ta kalle shi, ta ce
"Mafarki ne ko, ai ba gaske ba ne ko?" Kan ya kai ga ba ta amsa, ta
kalli kayan jikinsa, ta kalli na ta, ta shafa fuskarta, ai sai ta saka kuka, ta
fara kiran Abba da ƙarfi, tana ƙoƙarin ture Viper tayi waje.
"Shikenan, ya isa ki nutusu, bari ayi masa magana ya
shigo ki ganshi, amma mu je ki zauna tukuna" kamar mahaukaciya sabon kamu,
haka Nabila ta din ga misbehaving.
Viper ya yi waya, ya ce a ba su damar su shigo su ganta.
Sai ga su duk sun shigo, ga hafsa saifu da Tijjani, major da
Bashir na rige-rigen shigowa, sai kuma su liti da walid da Nasir.
Bin su ta din ga yi da kallo, Hafsa ta ƙarasa gaban gadon
Nabila ta ce "Waliyiyya, sannu kin tashi? Ina ɗan jaririnki yake? Shikenan
yau sai ki koma gidan Master, ku ci gaba da shan soyayya" ƙuri Nabila ta
yi mata da ido, dan ba ta santa ba sai a ɗazu ta taɓa ganinta.
Major ya ce "Arfa, ya jikin naki?" Tayi shiru ta
sunkuyar da kai.
"Arfa Abba ne fa, ba ki gane ni ba ne?"
Bashir ya zagaya ta gefenta, yana ƙare mata kallo, cikin
matsananciyar soyayya da ƙauna.
"Yarinyata, ki kalle ni, ni ne mahaifinki" yayi
maganar cikin matsanancin rauni.
Nabila ta ɗaga kai, ta kalle shi sau ɗaya, ta kawar da
kanta, tabbas ta ɗokanta da son ganin mahaifinta, ba irin alwashin da ba ta yi
ba, na idan Allah ya sa yana raye, su ka haɗu, babu ruwanta da Al'ada sai ta
rungume shi, ko a yaya yake, sai dai kash! Ba ta ji daɗin a yadda mahaifin na
ta ya kasance ba, duk da ba ta san mahaifiyarta ba, amma uwa uwa ce, ba ta ji
daɗin abin da ta ji game da tarihin zaman su ba.
Nasir ya ce "Nabila, ki yi magana mana"
Major ya sake cewa "Arfa, ki kalle ni mana? Meyake
damunki?"
"Ni ku daina nuna ku na so na, ba kwa so na ba kwa
ƙaunata, meyasa za ku yi mini haka? Ni menene laifina a tsakanin ku? Ace ina da
'yar uwa ban ganta ba, ba ta ganni ba har ta koma ga Allah, kun san me nake ji
kuwa? Ban san uwata ba, 'yar uwata kuma ta mutu ban taɓa ganinta ba, duk ba kwa
so na, kun fifita tsamin alaƙar ku a kai na, ta mutu fa ba zan ganta ba kenan.
Abba tsananin son da ka ke yi wa 'yar uwakka ya sanya ka yanke wannan hukunci,
ni yanzu ba ka yi tunanin a wane halin nake ciki ba, da na rayu kamar wata
mujiya, ba wani ɗan uwa da zan ɗaga in kalla ya na so na tsakani da Allah"
tayi maganar tana wani irin kuka mai matuƙar sauti.
"Shikenan da ban haɗu da Viper ba, ba zan san ina da
'yar uwa ba, Abba ka ɓoye mini, kai kuma babana, duk burin da na ci na in
ganka, gwiwata ta yi sanyi, meyasa ka yi wa mahaifiyarmu haka, da ba ka yi haka
ba, da babu lallai a raba ni da 'yar uwata, ban fa taɓa ganinta ba, shikenan ta
tafi har abada"
Ta miƙe tsaye a kan gadon, tana neman hanyar sauka.
Viper ya ce "Meye haka ne ki ke yi? Ina kuma zaki
je?"
"Ka kira mini sumayya dan Allah" tayi maganar
cikin sigar magiya.
"Sumayya kuma? Me za ta yi miki?"
"Ni dai ka kirawo mini ita"
"Magariba ta yi, ba za a kirata ba sai da safe"
Likita ne ya dawo, ya ce duk a fita a ƙyaleta, a stage ɗin
nan da take, za ta iya samun matsalar ƙwaƙwalwa, a ƙyaleta ta huta.
Matsananciyar nadama da jin kunya, suka mamaye Bashir yanzu
shikenan Nabila ba ta farincikin ganinsa.
Shi ma major, damuwa ce ta mamaye ilahirin fuskarsa, wani
irin dana sani yake yi, na raba Nabila da jauhar da ya yi, wato duk wayon bawa
ƙaddara ta riga fata.
***
Gidan su jauhar, tun bayan da Zakiyya ta yaudari maman
saifu, ta aurawa Alhaji mu'azzam Hafsa, dama haɗin kan na su ya lalace, kullum
cikin faɗa da tashin hankali suke, sai ka ce ƙanan yara, gaba ɗaya tarbiyyar
yaran sai a hankali, ba wanda yake ganin uwar wani da gashi sai tasa.
Bayan tafiyar su Major, Zakiyya ta ce "Ke kin ga wani
ikon Allah, wallahi saura kaɗan na haukace, na ɗauka gamo na yi, yanzu duk
tsawon wannan lokacin dama jauhar 'yan biyu ne?"
"Wallahi kuwa, abin da mamaki ba kaɗan ba, kuma wani
ikon Allah, ba ya zancen uwar su, tun wancan lokacin"
Zakiyya ta ce "Eh, amma ai yana kallon hotonta wasu
lokutan, wai dan Allah maman saifu, wurin wani malamin ki ka kai Bashir, da
aikin nan ya ci shi, ya manta da chubaɗo gaba ɗaya daga rayuwarsa, ashe a
tagayyare haka ta haife su?"
A ƙule ta ce "Ban gane wurin wani malami na kai shi ba,
muka kai shi dai, ke da yarinyar nan ta rayu a gidan nan, ai da wallahi
kashinmu ya bushe, yadda ya din ga rawar kan nan, ya nemi ya mayar da mu borori
a kan bafulatanar daji, kawai a daina wani tone-tone"
Zakiyya ta ce "Uhumm ai shikenan, zan ga yadda dramar
nan za ta ƙare, shi ya ɗauki zafi shi ma wan uwarta ya ɗauka, amma abin da ya
bani mamaki na kasa ganewa shi ne, yaya aka yi mijin jauhar ya samo ta, a ina
ya ganota ya kawota nan ɗin?"
"Oho sanin gaibu sai Allah"
Su ka ci gaba da hira, su na mamakin yadda al'amuran suke
cike da sarƙaƙiya da ban mamaki.
***
Nabila kamar tana tura magani, haka take shan youghurt ɗin
gabanta, ta na yamutsa fuska, fuskar tayi jawur, Viper ya zuba mata idanunsa ko
ƙiftawa ba ya yi.
"Kin ce ke youghurt, ku ma kin ƙi sha"
Hawaye ya gangaro kan fuskarta ta ce "Ka takura mini
ne, babu yadda zan yi, dan Allah ka nuna mini hoton 'yar uwata na sake ganinta,
idan an tuna ba zan taɓa ganinta ba, wallahi sai na ji zuciyata ta buga da
ƙarfi ban santa ba, amma wallahi ina son ta, meyasa tuntuni ban sanka ba ka haɗani
da ita ba?"
Ya shafi fuskarsa cikin dakiya ya ce "Allah ne bai
ƙaddara ba"
"Kenan kai nake mafarkin tana nuna mini a cikin sarƙa?
Yayi ƙuri da ido yana kallon ta.
"Wallahi Vi da gaske nake son ta, ashe haka ka ji, kai
da ka santa ya ka ji da ka rasata, gara ma kai ni fa ban santa ba ma, tsakani
da Allah iyayen nan nawa sun kyauta mini?" Tayi maganar tana rushe masa da
matsanancin kuka.
Allurar gefen gadonta, ya ɗauka ya buɗe ya zuƙe ta, ya ce
"Kwanta ki bani hannunki na yi miki, sun shigo za su yi miki ki na
salla" ta kalleshi tana sheshsheƙar kuka.
"Kar ki damu, ɗan ƙwaya ne ni, kuma ɗan daba na saba
riƙe sirinji da allura.
Ya buɗe cannulan ya fara yi mata allurar, a hankali jikinta
ya fara sanyi, ya kwantar da ita.
"Tun daga lokacin da na fuskanci bijirewa ƙaddara na
nufin halaka ta dindin ko samar da damejin da ba shi da hanyar gyaruwa, ya
sanya na yi saranda, na bawa ƙaddarar damar ci gaba da jujjuya akalar
rayuwarmu, domin na fuskanci ƙaddarorinmu na da alaƙa da juna. Tamkar na kashe
kaina, haka na ji bayan rasa matata, ni har hauka na yi ai, na kuma yi ƙoƙarin
sake sabauta rayuwata. Kar ki tafka irin kuskuren da na yi, nake ta fama da
dana sanin da ba shi da wani amfani a gare ni, ina guje miki aikata haka.
Ki yi haƙuri ki rungumi ƙaddara, ki karɓi mahaifinki kuma ki karɓi mariƙinki,
ki sasanta tsakaninsu" cikin muryar jin bacci ta ce "Maza wasu ba su
yi ba, Allah sarki babarmu 'yar fulanin riga, abin tausayi"
"Idan kuma abin da ya same ta ya na da alaƙa da
jinsinta fa, su suka aikata komai, mu daina zargin jinsinmu da cutar da ɗaya,
kawai mu mu zama adalai a kowane lokaci, da mahaifinki da major duk ba na
yarwa. Zan iya rantse miki ban san mahaifinku da wani mugun hali ba, mutumin
kirki ne, duk da ba ni hali na kirki, amma auren 'yar sa da na yi, ɗa ya ɗauke
ni ba siriki ba"
Ta buɗe idanunta da kyar, cikin raɗa ta ce "Spy, wai
nasiha ka ke yi mini? To ka fara yi wa kanka, zan iya rantse maka, Abbu mutumin
kirki ne, bamu haɗu a zahiri ba, a waya muka yi magana amma dattijon arziki
ne" ta yi maganar daidai lokacin da bacci yayi awon gaba da ita.
Dare ya fara yi, Viper ya fito daga sashin in da ɗakin
Nabila yake, daga major har Baba duk suna nanz har a lokacin ba su tafi ba.
Viper ya ce "Ina ganin zaku iya tafiya gida, zuwa in
Allah ya kaimu da safe, tun da an ce ƙwaƙwalwarta na buƙatar hutu, kar ta
rikice gaba ɗaya. Amma dai yakamata ku sasanta kanku kafin Allah ya sanya ta
sake farfaɗowa".
Major ya kalli Viper rai a ɓace ya ce "Ai kai ne kanwa
uwar gamin komai, dan me zaka ɗauke ta, ka kai ta wurin wannan mutumin mara
tsoron Allah, ita ma ya bari rayuwarta ta wulaƙanta kamar yadda ya wulakanta ta
uwatta, kuma saboda rashin tsoron Allah ya aura maka yarinyar da ba ta ji ba,
ba ta gani ba ka kasheta, kuma saboda zalunci ka dawo ka sanya ta tssya maka,
take baka kariya, alhalin ka kashe yar uwatta, wane irin abu ne wannan?. Duk a
dalilinka zumuncin da yake tsakanin yaran nan, ka watsa shi, ba ta jin maganar
kowa sai ta ka, idan abin gaskiya ne, meyasa ni ba ka je ka same ni a gida, ka
yi mini bayani ba kawai ka ɗauke ta ka kai wa wannan mutumin"
Maganganun Major sun yi wa Viper zafi sosai, yayi ƙuri da
ido yana kallon major, amma bai yi magana ba.
Baba cikin mamaki ya kalli major ya ce "Ka ga wani iko
na Ubangiji da yadda yake jujjuya al'amura yadda ya so, duk guje-gujen naka, da
Allah ya ƙaddara, Nabila ce za ta tsaya wa mijin 'yar uwatta, ka yi ƙoƙarin
tsayawa a kan iliminta da tarbiyyarta, amma Al'amin ba mutumin banza ba ne ba,
haryanzu ban yadda zai iya kashe mini 'ya ba, kar ka ƙara danganta shi da kisan
kan jauhar"
Saifu ya ce "Baba ka daina wannan maganar fa, ba ka da
tabbas ya aikata ko be aikata ba"
Liti ya ce "Ji wani ɗan wahala kuma, to ai sai ka jira
kotu ta tabattar da shi ya aikata, tun da shari'a za a fara kwanan nan. Mu mu
ka yi rayuwa a gidan Viper a tsakanin sa da Jauhar. Mun san yanayin
zamantakewar su, tsabar ƙauna ko sunanta ba ya iya faɗa sai 'yar madara, sai ka
jira kotu tukuna, kafin ka yi wannan maganar"
Shiru saifu yayi, dan ya san halin liti farin sani, 'yan a
mutun mai zamani ne.
Da kyar da siɗin goshi, aka samu suka tafi gida, shi ma sai
da su ka tabbatar da Nabila tana cikin tsaron da babu wanda zai gudu da ita,
dan kowa zargin kowa yake yi.
Viper a makwancinsa, yana ta jujjuya al'amarin ya san akwai
sauran ƙura a gaba, major ya ɗauki zafi sosai da sosai, kuma haɗin kansu ne zai
ba wa Nabila nutsuwar ci gaba da gudanar da shari'ar da take yi a cikin
nutsuwa.
***
Sumayya duk wani abu da ya shafi Indabo, haka take yaɗa shi
a kafafen watsa labarai ba tare da tsoro ko fargaba ba, ba shi kaɗai ba,
mussaman Alhaji mu'azzam yake sanyawa ake nemo mata manyan rahotanni na bankaɗa
tare da cikakkiyar hujja a kan miyagun harƙallolin da ake yi a ƙasar nan. Sai
dai kash, ko an bankaɗo babu wani abu da talaka zai iya yi a kai face Allah ya
isa. Dan ƴan siyasar sun din ga ƙoƙarin kare kansu kenan, lokutan zaɓe su sake
lallaɓowa tare da fara ayyukan babu gaira babu dalili, da raba tallafin abin da
bai kai kaso goma a cikin abin da suke wawaso na al'aumma ba. Sai dai a wannan
karon al'ummar sun yi rawar gani wurin yin abin da ya dace, karo na farko a
Nigeria da ake ƙoƙarin yi wa sanata kiranye. Duk da irin barazana da matasan da
suke jagorantar abin suke yi, amma suka dage babu gudu babu ja da baya, dan
tuni sun miƙa wasiƙa ga hukumar zaɓe ta ƙasa a kan son yi wa Indabo kiranye.
Hakan ya ba wa wasu matasan daga sassa daban-daban na ƙasar nan ƙwarin gwiwa da
ganin cewa ashe za su iya kawo canji ga waɗanda suke wakiltar su su ma.
Alhaji mu'azzam mutum ne na mutane, dan haka mutanensa su ka
din ga kiransa a kan ya fito takara.
Dama harin kujerar inda
Bayan kammala program ɗin ta, ta ga kiran waya.
Lambar Nabila ta gani, ta ɗaga ta ce "Ke ya ne, program
na kammala ko numfashi ban shaƙa ba, kin doko mini kira"
"Ta na asibitin barrack, ta na buƙatar ganinki da
gaggawa" ƙuuu cikin sumayya ya yi ƙara, muryar Viper ce, a duniya Allah ya
yi masa kwarjini, muryarsa da ta ji kawai gabanta ya faɗi. Kashe wayar ya yi,
bayan kammala gaya mata saƙon.
A gurguje Sumayya take ƙoƙarin kammala ayyukanta, dan ya je
ya ji me ya sami Nabila.
A jiya da major ya koma gida, kasa gane kansa matansa suka
yi, dan babu wadda ya kula, kuma ya ce baya buƙatar kowa ta zo masa turaka.
Sai Nasir suka tutsiye, su na tambayar sa, ina su ka je jiya
wuni guda ba sa nan.
Nasir ya labarta musu komai, gaba ɗaya suka yi shock. Anty
ta ce "Dama mahaifin Nabila yana raye?"
"Eh, mun ganshi jiya ma, ɗan daban nan Viper da ake
nema, 'yar biyun Nabila ya aura ya kashe, kuma saboda shirme take kare shi, shi
ya ɗauke ta ya kaita wurin mahaifinta" al'amarin yana buƙatar nutsuwa kan
a warware shi, dan ba kowa ne zai iya fahimtar bayanin ba sama-sama.
Ko da sumayya ta je, ba wanda ya hanata shiga, da ta tambayi
in da Nabila take, Nabila na ganinta ta miƙe tsaye, fuskarta ta kumbura suntum
saboda kuka.
Ta rungume sumayya ta ci gaba da kuka, Sumayya ta ce
"Subhanallah, Nabila waye ya mutu? Kin ga yadda ki ka rame fuskarki ta
kumbura kuwa?"
Cikin kuka ta ce "Sumayya na ga babana jiya" waro
ido sumayyan tayi ta ce "A ina?"
"Viper ne ya kai ni, Sumayya ashe yar biyuna ya aura
aka kashe, duk wannan haƙilon da nake yi, 'yar uwata aka kashe"
Sumayya ta ƙurawa Nabila ido, ta ce "Anya kanki ɗaya?"
"Kai na ɗaya Sumayya, amma ai kin san lokacin da nake
ce miki ina mafarki da mai kama da ni, ki ke yi mini dariya, wallahi sumayya
ina da 'yar uwa da ban taɓa ganinta ba, a kanta nake shari'ar Viper"
"Nabila, gaba ɗaya kin rikita ni, ban gane in da ki ka
dosa ba wallahi, gaba ɗaya na rikice" Viper ne ya turo ƙofar ɗakin ya
shigo.
Jiki na rawa sumayya ta gaishe shi ya amsa, ta kalli Viper
ta ce "Vi ka yi wa sumayya bayani, ta ƙi yadda ta kuma kasa gane bayanin
da na yi mata"
"Wa zai fuskanci wannan bayanin naki at once dama, ki
ƙwarara jikinki, ki yi haƙuri ki daina wannan kukan, yana daga dalilin da ya
sanya tun farko ban gaya miki ba"
Sumayya za ta yi magana, Abba ya turo ƙofa ya shigo da
sallama, suka amsa masa. Sumayya ta gaida Abba ya amsa mata, suka gaisa da
Nasir ma.
Viper ya yi masa barka da zuwa, amma ya yi masa shiru.
"Arfa, kin ji sauƙi ina son a sallame ki, mu koma gida
ne" kawar da kanta gefe ta yi, ba ta kalle shi ba.
Sumayya ta ce "Nabila Abba ne fa"
Ta ɗaga kai ta kalli Sumayya ta ce "Abba disappointed
me, meyasa ya ɓoye mini ina da 'yar uwa, gashi ta mutu ban taɓa ganinta ba...
"Wai mahaifiyarki ma ba rasuwa ta yi baki taɓa ganinta
ba?" Viper ya yi maganar a kausashe.
"Amma jauhar ta yi tsawon rai ai, meyasa aka hukunta mu
da laifin babanmu"
Nasir ya ce "Nabila Abban ki ke gaya wa haka?"
Major ya yi shiru, kawai ya tashi ya fita.
Sumayya ta ce "Nabila meyasa ki ka yi haka? Baki kyauta
ba, duk ɗawainiyar da ya yi da mu, hakan da ki ka yi ba dai-dai ba ne ba. Idan
aka sallame ki, dole mu je ki ba shi haƙuri.
Kiran gaggawa aka yi wa sumayya, ta tashi ta tafi, cike da
mamaki da tunani daban-daban a cikin zuciyarta.
Bayan tafiyar major, sai ga Bashir, har da kayan abinci
niƙi-niƙi sun zo duba Nabila.
Tana zaune, a kan gado, Viper yana gefe yana waya, yana
ganinsu ya kashe wayar, ya risuna suka gaisa da Baba.
Ƙarasawa yayi gaban gadon Nabila ya zauna ya ce "Sannu
ya jikin naki?"
Ƙura masa ido ta yi, amma ta kasa masa uffan.
Ya zauna ya dafa hannunta, amma ta janye ta sunkuyar da kai.
Bashir jiki a sanyaye ya tsaya yana ci gaba da kallon
Nabila.
Viper ya ce "Ina ga ko zaka ɗan bata lokaci, kafin
Nabila ta ganka, tana ɗokin da muradin ganinka, abin da ta ji ne dole za ta ji
wani iri, amma in sha Allah za ta maye maka gurbin jauhar.
"Na san ni mai laifi ne, amma ƙaddara ta riga fata,
wallahi tamkar an shafe ni tunanina a cikin kaina, haka na manta da mairamu.
Yaya za ayi ace ka auri mace ka manta da ita, ban san meyafaru ba a lokacin.
Kuma ni maitama bai gaya mini ku biyu ba ne, amma ki yi haƙuri ki yafe mini dan
Allah" ya kalli Viper ya ce "Bari na je, hafsa ma za su zo dubata
yanzun nan in sha Allah" Viper ya tashi ya raka shi har harabar Asibitin.
Nabila ta jingina da jikin bango ta lumshe idanunta, hawaye
na bin gefen idonta, Viper ya dawo ya tarar da ita.
"Ba ki kyauta ba abin da ki ka yi? Duk ɗokin ganin
mahaifin naki, abin da ki ka yi kin kyauta kenan?"
"Ba ka san me nake ji ba ne?"
"Ko ma me ki ke ji ba ki kai ni ba, abin da ki ke yi ba
ki kyauta ba, ke zaki jajirce ki daidaita wannan rashin jituwar da yake
tsakaninsu, ki rungumi mahaifinki"
Ta zuba masa ido hawaye na bin idonta.
"Menene kuma? Kukan be isa ba haka?"
"Vi" tayi maganar muryarta na rawa.
"Abla"
"Ka ga abin ƙaddara ko? Ƙaddara ce ta sanya na din ga
bibiyarka"
Ya ce "Haka ne"
"Kwatsam na fara sonka daga wasa, na yarda da
maganarka, ba zan taɓa jauhar ba, kuma idan na ci gaba da sonka ban yi zumunci
ba na ci amanar 'yar uwata. Zan fara jin kunyrka a matsayin ka na mijin yayata,
ba soyayya tsakanin mu yanzu, zan yi iya ƙoƙarina na ga an ƙwatarwa 'yar uwata
hakkinta, kuma na ga an wanke ka daga zargin da ake yi maka. Na gode sosai da
sosai da ƙoƙarin da ka yi mini".
Ayshercool
08081012143
*HADARIN GABAS*
*ATTENTION! ɗan tsaya 'yar uwa, shin ki na karanta littafin HADARIN GABAS??? Tafiya ce
ta mussaman mai tsayawa a zukatan masu karatu, ba yaƙini nake da shi ba,
tabbaci nake da shi, tsaruwa da ma'anar littafin Hadarin gabas ya zarta tunanin
mai karatu, Hadarin gabas daga alƙalamin NAZEEFA SABO NASHE.
Ku tuntuɓe ta domin samun damar karanta wannan littafin.
+234 803 374 8387
Abu na farko da zamu buk’ata daga wajenka shine mahaifar
matarka, Ma’ana ba zaku haihu da matarka
ba.” Imaam ya ‘dago yana kallonsa Ya ji kansa ya wani sarà masa, amma sam ya
kasa masa musu… Alwan yana murmushi ya ce “Ka kirata ku yi shawara…” Ya fice ya
bar masa wajen. Da sauri Imaam Ya kira Safna. Tana d’agawa ta ce “Yaya? Imaam
Allah yasa dai baka musu taurin kai ba?” Ya saki huci ka’dan ya furta “Ba zan
iya abinda suke so ba….” “Zaka iya Imaam, ka yi koma me suke so? Yanzu fa ba
abinda baa yi saboda ku’di, ana ya Kai Kai, mutum yana kwanciyar da y’ar
cikinsa, da Uwar data haifeshi ma saboda ku’di, ana luwa’di da ma’digo saboda
ku’di, ana bada Uwa ko y’a Yaya ko k’anwa, K’ani ko wa? Duk saboda ku’di, don
haka ka yi ko me suke so Moddi Saboda ku’di… bana son musu…” ta fa’da tana zame
kanta a duk sunayen da ta ambata, bata k’i ya yi komai ba in dai zai samar musu
da ku’di, bata damu ta ji shara’din da suka bashi ba. Imaam Ya saki ajiyar
zuciya, sai ya ji ya samu k’warin gwiwar bayar da mahaifarta tunda ita ta
jawowa kanta ta ce ya yi komai saboda ku’di. A zuciyarsa Ya dinga jin baya so,
amma harshensa ya kasa amince masa ya furta baya so d’in. Ya kalli Alwan da Ya
shigo d’akin idanunsa a kansa shima ya ce “Yaya Aboki? Ka yarda ko a’a? Abu
guda dana sani baka isa ka San sirrinmu sannan ka bijire mana ba…..
Cab’di kin fara bibiya ko har yanzu… Hadarin gabas dai da
zafinsa yazo akwai cakwakiya anan gaba… Za’a yi kuka za’a yi dariya za’a sha
soyayya a cikin littafin nan. Hanzarta ki fara Ina Imaam Muhammad Moddibo Ya
kai kansa?
Daga Alƙalamin Nazeefa sabo Nashe.
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Abin da Nabila ta faɗa ya sanya Viper jin ƙirjinsa ya
tsananta bugawa.
Ta sake cewa "mu yi zumunci kawai, zumuncinmu ya ɗore,
amma yanzu na fahimce ka, da ka yi ta jaddada mini, ba zan taɓa zamo wa jauhar
ba" zai yi magana.
Hafsa ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo da sallama, hannunta
riƙe da leda cike da kayan marmari, ta ƙarasa tana murmushi.
Bayanta saifu ne yake biye da ita, tana zuwa ta dungurar da
ledar ta zauna a kusa da Nabila ta ce "Waliyiyya kin warke ya jikin?"
Nabila ta yi murmushi, ta fuskanci Hafsa 'yar uwatta ce, dan
tana kama da ita kaɗan, ta ce "Jiki Alhamdilillah".
Ta kalli Viper ta risuna ta ce "Ina wuni"
"Lafiya ƙalau yaya hafsa" ya kirata da yadda
jauhar take kiranta.
Sai ta yi murmushi ta sake kallon Nabila ta ɗora hannunta a
goshin Nabila ta ce "Ba kya zazzaɓi ma, kin warke sai mu tafi da ke gida
ko? Ko gidanku zaki koma ke da shi? Har gidan naku nake zuwa ba a sani ba, baba
ya ce idan na kuma zuwa Yaya tijjani ya zane ni"
Saifu ya kalli Nabila ya ce "Yaya jikin naki?"
Nabila ta ce "Na ji sauƙi Alhamdilillah"
"Allah ya sauwwaƙe, ga hafsa nan ita ma yar uwammu ce,
yakamata ace duk an gabatar miki da yan uwanki, amma sai Allah ya sa kin
warware, zan je duba wani abokina, idan na dawo zan zo na ɗauke ta. Ina amfani
da wannan damar wurin baki haƙuri, da nema wa mahaifinmu afuwarki ki yi haƙuri
dan Allah. Sannan ku yi haƙuri da abubuwan da za ta yi, tana misbehaving wasu
lokutan, tana fama da matsalar ƙwaƙwalwa ne, ta damu a kawota wurin ki ne"
"Baba ya ce kar ka sake ce mini mahaukaciya, ni da
hankalina dan Allah jauhar na yi kama da mahaukaciya?" Hafsa tayi maganar
kamar zata yi kuka.
Nabila ta girgiza kai ta ce "Ko kaɗan" Saifu ya
juya ya tafi, ba tare da wani ya kula wani tsakanin sa da Viper ba.
Bayan ya fita Hafsa ta ce "Jauhar ina jaririnki
ne?"
Viper ya ce "Ba jauhar ba ce ba" ta kalli Nabila
ta kalle shi ta ce "Ita ce mana"
Ya ce "Kalle ta da kyau dai" ta sake ƙurawa Nabila
ido, ta kalleshi ta ce "Jauhar ce mana, ina ɗan naku to?"
Ya ce "Tambayeta"
Nabila ta ce "Ta tambaye ka dai"
Viper a hankali ya ce "Ya rasu"
Ta ɗan yi shiru ta ce "Shi ba zai dawo ba kenan kamar
yadda ita ta dawo, to yaushe zata samu wani cikin, ina son na ga ta haihu
wallahi, ka san baba cewa yake yi, idan ku yi aure ku haihu da ƙuruciyarku, sai
su zama kamar ƙannenku" gum Nabila tayi jin katoɓarar da Hafsan tayi.
Gaba ɗaya suka yi mata shiru, ta kalli Nabila ta kalli Viper
ta ce "Baku gaya mini ba"
Viper ya kalli Nabila ya ce "Abla tana magana, yaushe
zaki sake samun wani cikin ki haihu?"
Nabila ta ce "Na shiga uku"ta yi maganar tana
sunkuyar da kai, sai ya faɗi magana ya wani maze kamar ba shi baz wannan
nannauyar maganar tayi masa sauƙin faɗa haka yana kallonta.
Ya basar ya ce "Ina mijinki ne?"
"Ni bani da aure, rabuwa muka yi, uwargidansa ta hana
shi kula ni, sai dai ya ɗauketa su tafi yawo su bar ni a gida. Nayi ta kuka na
gaya wa Anty, amma wai na yi haƙuri, na zo na daina bacci, na je asibiti aka
bani wani magani na kwana biyu, tun daga ranar da nayi bacci na ji daɗi, na din
ga kai wa wani mai chemist yana bani ina sha, har ya fara ƙara mini da wasu ina
sha.
Gaba ɗaya baya yi mini irin yadda ka ke yi wa jauhar, idan
na zo gidanku naga yadda ku ke yi, in yi ta kuka, kuma fa anty ce ta din ga
bani magani dan ya aure ni, amma wallahi ina son shi, na din ga shaye-shaye da
ban san shi nake yi ba sai daga baya. Zama yaƙi daɗi ya sake ni. Bayan ya sake
ni fa sai da ya auri wata kuma ta zauna ita ba ayi mata irin yadda aka yi mini
ba. Na cigaba da shaye-shaye damuwa ta yi mini yawa, mai chemist yayi mini haɗin
wata ƙwaya ya ce zan manta da damuwata ashe ƙwaƙwalwa ta ya taɓa mini sai aka
ce wai na zama mahaukaciya. Amma nima na san alhakin ki ne ya kama ni, ki yafe
mini dan Allah ƙanwata"
Nabila da tausayin Hafsa ya sanya ta fara hawaye, ta kalle
ta ta ce Jauhar zuciyarta daban ce, ta musamman ce. Ita ai kusan kun gama yi
mata komai da ku ka aura mata sanyin idaniyarta.
Turo ƙofar ɗakin aka yi hafsa ba ta waiwaya ba, amma ta
tsorata gabanta ya faɗi, jin ƙamshin turaren Alhaji mu'azzam ya cika ɗakin.
Sallama ya yi suka amsa masa, ta ɗaga kai a hankali, suka yi
ido huɗu da shi, gabanta ya sake faɗuwa, zai iya cewa tun da ya saketa bai sake
ganinta ba sai yanzu.
Jan jikinta tayi, ta haye gadon da Nabila take.
Ya miƙa wa Viper hannu, amma Viper ya tsaya yana kallon sa,
Nabila ce ta ɗan gyaɗa masa kai, a hankali ya miƙa masa hannu, suka yi
musabaha. Ya ja wata kujerar ya zauna.
Ya ce "Barrister ya jikin?"
"Alhamdilillah" ta amsa a hankali.
Ya kalli Viper ya ce "Ashe ka kawo ƙarshen labarin da
kanka?"
Viper fuskarsa babu yabo ba fallasa ya ce "Eh na
kawo"
"Na san kan labarin ya ƙarƙare da sauran rina a kaba,
ina yi muku fatan alkhairi. Nabila zuwa yanzu kin san wanene ni, da dalilin da
ya sanya na din ga bibiyarki, ta tabbata jauhar Sister ɗinki ce ko? Duk na san
mahaifinki, ban yi garajen sanar da shi komai ba, saboda binciken da nayi a
kanki, babu ta in da ya nuna jauhar da ke akwai alaƙa, ashe akwai ɗin dai. Na
tayaki murna"
Nabila ta jinjina kai ta ce "Na gode sosai, Jauhar da
ni twins ne, abubuwan ne da tsayi sosai amma bani da bakin yi maka godiya Allah
ya saka da alkhairi. Ga wannan ita ma tana cikin 'yan uwana, sunanta
hafsa"
Ya kalli hafsa da tayi tsuru, yayi murmushi ya ce "Na
santa ai, hafsa mun san juna ko?" Hafsa ta kalleshi, kawai ta dira ta ɗaya
side ɗin, ta zari takalmanta za ta fita, Nabila ta ce "Ina zaki je?"
Ba ta juyo ba ta ce "Waje zafi nake ji, kar ki da mu
ina da hankali ba wani wurin zan je ba" ta kai bakin ƙofa walid ya turo
ƙofa ya buge mata goshi.
A rikice ya ce "Ya salam, yi haƙuri dan Allah, ban dan
kin taho ba" ta yi murmushi ya ce "Bakomai ai babu zafi tayi waje.
Suka shigo ɗakin, suka gaisa da Alhaji mu'zzam, ya tashi da
hanzari ya ce "Bari na je waje na amsa waya, daga nan zan wuce, amma ina
son zama da ku, a kan shari'ar nan amma ina zuwa dai" Alhaji mu'azzam ya
fice daga ɗakin.
Kawai suka ga Viper ya saka dariya, gaba ɗaya suka zuba masa
ido, Nabila tunani take yi, anya ta taɓa ganin dariyar Viper haka.
Walid ya ce "Mutumina meyafaru ne ka ke dariya, dariyar
da rabonka da ita tun 'yar madara na raye"
Ya ce "Muhsin, wani abu ne ya bani dariya"
"Akhbirni mutumina, meyafaru ne?"
Ya tsagaita ya mayar da dariyar murmushi ya ce "So
mugun wasa ne, mai saka ma'abocinsa yi masa biyayyar dole ko bai shirya ba,
babu wata waya fa da zai amsa, ya bi matarsa ne kawai, maybe yana kewarta"
Nabila ta ce "Ita ce Hafsan da oga walid ya bani
labari, dama zancen Alhaji mu'azzam take yi?" Viper ya jinjina mata kai
alamar eh.
"Ikon Allah, yanzu duk tsawon wannan lokacin kun san
komai, ku ka rufe ni"
Viper ya ce "Yanzu ai gashi kin sani".
Can bayan ɗakin Nabila ta zagaya, hawaye na zubowa daga
idanunta, ta tsaya tana ta share hawayenta, ta jima a tsaye tana share hawayen,
sannan ta juyo da niyyar komawa, kawai ta ga Alhaji mu'azzam a bayanta a tsaye.
Tsuru-tsuru ta yi kamar mara gaskiya.
"Haba hafsa, ko gaisuwa babu, tamkar dodo daga ganina
sai ki hau gudu? Ya goshin naki?"
Cikin inda inda ta ce "Lafiya ƙalau, babu zafi"
Alhaji mu'azzam ya ce "Ya kumbura fa, kuma ki ce babu
zafi?" Ta ɗaga kai alamar eh.
Ya taka a hankali zuwa gabanta, ya mamaye ta da ƙamshin
turaren sa, ta kalleshi, yana sanye da yadi ash mai tsada riga da wando, Alhaji
mu'azzam akwai kwalliya da ado.
"Kin ga wata sabuwa daban mai kama da jauhar ko?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a jauhar ce".
"Ba jauhar ba ce, wannan sunanta Nabila. Hafsat"
ya kira sunanta a hankali.
Tsigar jikinta ta tashi, taƙi kallonsa.
"Meyake damunki ne? Kin rame kin yi duhu, ba gayunki
kamar da, meyafaru haka?"
Kawai kuka ya ƙwace mata, har da sheshsheƙa. Jauhar yake so
ba hafsa ba, amma yana tausayin ta mussaman da ya ganta yanzu. Daga baya ya
fuskanci ba wai kuɗinsa kawai take yi wa ba, tana matuƙar son sa.
Amma shi kansa bai san ya aka yi ya din ga misbehaving ba,
kuma a lokacin ƙanwar indabo tsohuwar budurwarsa jidda tana ta bibiyarsa ya
aureta.
Handkerchief ɗin sa ya ɗaukko, ya fara share mata hawayen.
Ƙoƙarin rasa nutsuwar sa ya fara yi, ita ma ganin idan ta cigaba da tsayuwa, za
su iya ɓarna, dan har wani tsuma take yi, soyayyar sa ƙamshin turaren sa, da
maganganun da ya fara yi mata, narka mata zuciya yake yi, hakan ya sanya ta
buge hannunsa daga fuskarta, ta raɓa shi ta bar wurin.
***
Abdul yana kwance a gadon asibiti, hannunsa ɗaya da ankwa,
mahaifiyarsa na gefe tana ta uban kuka, tamkar an ce mata gawar Abdul ce a
gabanta. Ga Indabo can yana fuskantar hukunci. Jami'an tsaro na son ɗaukar
statement dan a shiga kotu, amma ko magana ba ya iya yi, idan ya yinƙura sai
aman jini.
Bunkure ma kamar zata haukace, dan ko ta wani ɓangare tana
samun suka, kuma babu sassauci. Mutane sun fara juya mata baya, tare da gazgata
zancen Nabila da tayi a kanta a kwankin baya aka din ga attacking ɗin ta.
Nabila ta bar Asibiti, ta koma gidan madam Halima.
Viper ya dage da yi wa Nabila nasiha, tare da tausarta, a
kan ta karɓi mahaifinta, tayi haƙuri sannan ta nemi gafarar major shi ma, dan
bai cancanci abin da tayi masa ba.
"Ni ka ƙyale ni dan Allah, in ji da raɗaɗin rashin 'yar
uwata da hake addabar ruhi da gangangar jikina, koma menene ya faru laifinsu ne
na kasa samun nutsuwar karɓar dukkaninsu".
A fausace ya hau ta da faɗa "Are you out of your sense,
rayuwata ba ta zama darasi a gare ki ba? Duk abin da ya faru a tsakaninsu, ke
ina ruwanki ne a ciki? Could you imagine mahaifinki na yi mini kuka a kan na
shawo masa kanki ko sau ɗaya ki yi masa kallon uba, ya riƙe ko da hannunki ne,
ya ji daɗi? Ya rasa jauhar, babu tsammani kin bayyana a gare shi, ba tare da ya
san ki na raye ba, amma kin ƙi saurarsa ina ruwanki da abin da ya riga ya wuce?
Wallahi ko kaffara ba zan yi ba da yar uwakki ce ba zata yi haka ba, jauhar ta
daban ce, mai tausayi da jin ƙai ce. Na san da ke aka yi wa abin da aka yi mata
a kaina bijirewa zaki yi. Da haƙuri da siyasa ake cin ribar zaman duniya ba
fushi da shirme ba. Kin nuna rashin jin dadin ki abin da aka yi miki da farko
daga baya kuma sai ki saukko ki haƙura ai"
Sumayya da tana wurin, ita kanta sai da ta tsorata da faɗan
da Viper yake yi.
Nabila kuwa kuka take yi wiwi, wasu lokutan gara faɗan Abba
da na Viper, gaba ɗaya sai ya razanata ya saka ta rasa abin da yake yi mata daɗi.
"Ki tashi ki shirya, zamu je ki nemi afuwarsa, sannan
mu je mu ga ɗan mama, da su Rahama"
Haka Nabila ta shirya, sumayya tana ta mamakin samun abin da
zai iya tsorata Nabila ya sakata kuka, bayan Abba.
Yau ma a ƙofar gidan su jauhar, aka yi parking, tare da
sumayya suka zo, da sallama suka shiga.
Baba yana gareji, yana ba wa saifu sallahun wanke masa mota,
Nabila suka shiga.
Cak ya tsaya yana kallon su, da sumayya da Nabila.
Kallo ɗaya Sumayya ta yi wa Baba ta gane baban Nabila ne.
Rikicewa yayi ya nufota duk da jikinsa a sanyaye ya nufeta,
idanunsa cike da hawaye.
Yana ƙarasowa ta faɗa jikinsa tana sakin wani irin kuka mai
karya zuciya.
A hankali ta ce "Baba" tana kuka yana kuka, kamar
wani zai ƙwace masa ita, haka ya ƙanƙame Nabila, yana kuka har da majina.
Sumayya da take tsaye ita ma fashewa ta yi da kukan, cikin
matsanancin tausayin su, ta san irin artabu da ƙalubalen da Nabila ta din ga
fuskanta a kan rashin uba, a gidan major yadda suke kiranta da tsintacciyar
mage wai babu wanda ya san babanta, Nabila ba ta da wata magana da ta wuce
fatan ganin mahaifinta, ta ji ina ma ita ma tana da rabon sake ganin mahaifinta
a rayuwa.
Viper yana hango su daga waje, ya sunkuyar da kansa hawaye
na cika masa ido, cike da fatan ina ma shi ne ya sake ganin Jauhar ta bayyana a
rayuwarsa ba tare da ya yi tsammanin hakan ba.
Nabila ta ce "Sumayya ga babana, kin ga babana"
"Na gan shi Nabilata, Ina tayamu murnar ganin Baba,
burin da muka daɗe muna fatan Allah ya cika mana"
"Ki yafe mini 'ya ta, abin da ya faru ba da son raina
ba ne ba, wani abu ne da ba zan ce ga a yadda ya faru ba, na san mai laifi ne a
gareku da mahaifiyarku, ke kaɗai ki ka rage mini a cikin su, dan Allah ki yi
haƙuri ki yafe mini" yayi maganar cikin matsanancin kuka.
Ya rungumi Nabila zuwa cikin gidan, sumayya na biye da su,
yaran gidan duk su ka kewaye su, wasu na taya su kuka wasu na kallon su.
Ya ce aje a ce wa Al'amin ya shiga.
Nabila ta kwantar da kanta a kan cinyar baba, tana cigaba da
kuka.
Bayan Viper ya shigo su ka gaisa da Baba, ya kalli sumayya
ya kalli Viper ya ce "Anya Aminullahi wannan ma ba tawa ba ce?"
Viper ya yi murmushi ya ce "Duk naka ne Baba, an
baka"
"Na san fuskarta ne, ta na kama da wani wanda na sani,
amma ba zan iya tuna waye ba? Ya sunan mahaifinki?"
Sumayya ta share hawayenta ta ce ba ni da wayon sanin
mahaifina, amma dai sunansa Tahir ladan.
A take ya yi sak, ya ce "Wane Tahir ladan ɗin? Coustom
ne?"
Sumayya ta jinjina masa kai ta ce "Ka san shi?"
Yayi shiru ya ce "Tare mu ka je ɗaurin aurena a
jalingo, abokin aikina ne, lokacin da aka yi mini transfer daga in da na bar
mairamu shi ne ya koma, ya je yayi reporting a wurin aiki, ya koma yayi
hatsarin mota ya rasu.
Viper ya ce "Kenan dai duk 'ya'yan naka na kawo
maka"
Kamar ƙaramin yaro ya kalli Sumayya ya ce "Ni babanki
ne, ke ma 'ya ta ce ai, na gode Aminullahi, Allah ya saka maka da mafificin
alkhairi"
Viper ya ce "Baba da ka yi haƙuri da kukan nan haka,
saboda su ma su samu ƙwarin gwiwar yin haƙuri, mu gode wa Allah kawai"
Ya jinjina kai yana maimaita Alhamdilillah.
Baba ya din ga shafa kan Nabila, amma hawayensa suka kasa
tsayawa.
Zakiyya tare da maman hafsa su ka shigo ɗakin da sallama, su
na kallon yadda ya saka su Nabila a gaba yana kuka.
Viper ya na ganin Zakiyya ya haɗe rai, tamkar ya ga abin
ƙyama.
Su ka zauna su ka din ga surutai marasa ma'ana, marasa tushe
balle makama. Tare da taya su kukan cike da makirci.
"Baba ina hafsa?" Nabila ta tambaya da kyar.
"Ta je gidan kakaninta da su ka haifi
mahaifiyarta".
"Baba shikenan ban san jauhar ba, ba kuma zan ganta ba,
ban san mama ba, ita ma kuma ban santa ba, mun rayu a wurare daban-daban, ba mu
san juna ba" tayi maganar tana sake fashewa da kuka.
Cikin sigar rarrashi ya ce "Hakan hukuncin Allah ne, ki
yi haƙuri, mu masu tarin laifi ne a wurinki, mussaman ni, na san ni ne baban
mai laifi, duk da major ma mai laifi ne, bai kamata ƙiyayyar da yake yi mini ya
sanya, ya nesanta ni da ke ba, ya kawo mini yarinya amma bai kuma waiwaiyarta
ba, amma Alhamdilillah na ji dadin yadda ya kula mini da ke"
Viper ya numfasa ya ce "Baba yakamata mu koma haka, da
su"
Baba ya ce "Aminullahi, dan girman Allah ka bar mini
ita"
"Ka yi haƙuri, ai aikin gama ya riga ya gama, tun da
har komai ya riga ya bayyana, sai da na saka hannu na ɗauki excuse sannan na
fito da ita, shi ma bisa uzurin aiki za ta yi, kuma ka ga a hannun Abba aka yi
yarjejeniya a ka ɗauketa, da niyyar ba ta kariya, har a kammala shari'ata,
addu'ar ka muke fata".
"Yanzu ka na nufin mijin 'yar uwatta take karewa, Allah
al-hakimu, Allah ya bayar da nasara, yayi muku jagora dukkaninku"
Su ka amsa da Amin gaba ɗaya.
Baba ya ce ya bari su ci abinci, Viper ya ce "Lokacinsu
a ƙididdige yake, idan su ka saɓa akwai matsala"
Har gaban mota ya rako su, yana rungume da Nabila kamar zai
mayar da ita cikin sa.
Su ka je bakin motar, ya riƙe hannun sumayya, ya riƙe na
Nabila, ya kasa tsayar da hawayensa, ya kalle su ya sake fashewa da kuka ya ce
"Ku yafe mini dan Allah, ku ci gaba da haɗa kanku, Allah ya yi muku
albarka, Allah ya jiƙan mahaifinki ke kuma Allah ya jiƙan mahaifiyarki da
jauhar"
Su na kuka su ka shiga motar, su ka ja, su na tafe a hanya,
Viper bai rarrashe su ba, dan ba wani ƙwarewa ya yi a hakan ba, ya yi musu
shiru, su ka yi ta kukan, ya ce a fara kai sumayya gida, sannan su koma barrack
washegari sai su je wurin su ramma.
***
Major ya sha mamakin yadda Nabila ta nuna fushi take yi da
shi, taƙi saurarsa.
Mama kuwa sai ziga shi take yi, ta ce "Dama ga ubanta
yaushe za ta saurare ka, ai kai ka gama yi mata amfani kuma, shiyasa tuntuni da
yaranka ka kama, da ya fiye maka" shi dai bai furta komai ba, amma abin ya
din ga cin zuciyarsa.
Rahila ma aka sallameta daga asibiti, bayan an yi mata ɗorin
karayar hannunta, sai da Abbu ya dage ya ce sai Abba ya bar masa gidansa, aka
kaɗa aka raya ya ce ba zai ci gaba da riƙe shi ba, idan kuma ta dage sai ya
zauna, to sai dai ta bi shi su bar gidan.
Shahida ma ta dage a kan raba aurenta, da fari Abbu bai sani
ba, amma bayan ya takurata, da ta gaya masa bai tausayawa halin da rahila take
ciki ba, yayi mata tas, ya ce sai an raba auren, ba za a saka masa 'ya a halaka
ba.
***
Sumayya ta labartawa ummanta abin da yake faruwa, sumayya na
ce mata jalingo, ummanta ta ce ta san mahaifin Nabila, amma ba wani sani ba, ta
dai san abokin aikinsa ne.
Madam halima ta gaya wa Nabila Viper ya zo, yana jiranta su
fita.
Kallo ɗaya ya yi mata, ya san ba ta samu isasshen bacci ba,
fuskar nan babu walwala.
"Ina kwana" tayi maganar a hankali.
Ya tsura mata ido, ita kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa.
"Akwai sauran damuwa ne? Kin haɗu da mahaifinki ba shi
ne fatanki ba?" Yayi maganar yana kallon ta.
Ta girgiza masa kai.
Ya ce "To me ya yi saura kuma?"
"Kewar yar uwata, da tunanin yadda zan daidaita Baba da
Abba, kowanne ya na da muhimmanci a gare ni, amma Abba ba zai saurare ni ba,
saboda Nasir ba zai daina ziga shi ba, saboda haushin tsaya maka da na yi, zai
ta ziga shi a kan lallai ya yadda kai ka kashe jauhar, ba ni da gaskiya ina
tsaya maka"
"Ƙalubale ne ma hakan, amma yakamata tun ba yanzu ba ki
san kuka ba magani bane ba, na san duk ni ne silar komai, shigowa ta rayuwarki,
ki yi haƙuri"
"Ba kai ka shigo rayuwata ba, ni na shiga taka, ko in
ce ƙaddara ce, amma in sha Allah zan yi iya yi na, sai an hukunta wanda su ka
kashe 'yar uwata, ku ma na tabattar da an kwance sarƙar da aka sanya wa mijinta
alƙawari ne na yi wa kaina" ta yi maganar tana share hawayenta.
Ya jinjina kai ya ce "Allah ya ba da sa'a"
"Amin" har ya yi gaba zai fita, ta ce
"Viper" ya tsaya ya waiwayo.
Ta ƙarasa gabansa ta ce "Ina son ka ji abin da na ji a
lokacin da na rungumi mahaifina, ina son ka yi amfani da nasihar da ka yi mini,
a kan kanka. Mahaifinka yana da muhimmanci a rayuwarka"
"Wannan ni ya shafa, ba ke ba, dan haka babu ruwanki a
ciki"
Ta ɗan yi murmushi ta ce "Ina roƙonka ne a matsayina na
ƙanwarka, ba lauyar ka ba, ina fatan ka kasance cikin rahamar Allah kamar yadda
nima ka ankarar da ni nawa kuskuren" Ajiyar zuciya ya yi, ya fice ta bi
bayansa.
Haka kurum su na tafe a mota, yake tunanin da gaske yanzu
Nabila a matsayin yaya ta ɗauke shi kawai?.
Harabar wurin 'yan sandan cike da motoci.
A can su ka tarar da sumayya, mahaifiyar ramma ma ta je
wurin ita da ramma, Alhaji mu'azzam ya saka an kai su.
Nabila tana matuƙar jinjinawa gudunmuwar da Alhaji mu'zzam
ya ba su, ya cancanci yabo da godiya, amma goga Viper hakan ko a jikinsa, balle
ya nuna masa yabawar sa da jin daɗin sa.
Suka gaggaisa, ramma da ƙyar ta iya gaida Viper, saboda
matsanancin tsoronsa da take ji.
Su liti tuni sun je wurin, dan sun kai wa ɗan mama abinci.
Sumayya ta zauna su ka sake tattauna wa da ramma, kasancewar
su na jiran ƙarasowar su Abdul da lauyoyin sa a ɗauki statement ɗin su duka.
Sumayya ta naɗi wani sashi mai muhimmanci, na tattaunawar su
da ramman, wanda zai yi wa Sumayya amfani haka Nabila, mussman ta ɓangaren
Naja'atu Bunkure.
Viper kuwa cikin isa yake yawonsa a headquarter yan sandan,
ya je ganin ɗan mama da kansa.
Sumayya ta dubi Nabila ta ce "Nabila, haryanzu ina
mamakin yadda aka yi ki ka haɗu da Viper, ikon Allah ashe duk wannan haƙilon a
kan sister ɗinki ki ke yin sa, amma Nabila idan ba shi ne ya kashe Jauhar ba,
wanene?"
Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Mu haɗu a kotu kawai
sumayya, abubuwan su na da girma da faɗi sosai"
"Meye wani sai mun haɗu a kotu, ki ƙarasa mini, kin bar
ni a cikin duhu da zullumi Abla, kamar yadda na ji ana kiran ki, Nabila gayen
nan kuwa ba son ki yake yi ba?"
Nabila ta numfasa ta ce "Sumayya, ba ki yi ƙarya ba, ni
ina son Viper, na kamu da sonsa ba tare da na shirya hakan ba, dan da farko dan
na taimaki rayuwarsa ya dawo hayyacinsa ya sanya na ce ina son sa, sai dai ban
yi aune ba, na faɗa son shi da gaske. Saboda Viper mutum ne na musamman ya kai
a so shi, kin san meya ƙara jefani cikin ƙaunar sa da gaske?"
Sumayya ta ce "Sai kin faɗa"
"Zamantakewar sa da ya yi da jauhar" Nan Nabila ta
fara ba wa sumayya labarin abin da ba ta sani ba, matakan da ta bi wurin haɗuwa
da shi, zuwa labarin sa da Walid ya bata.
Ramma ta yi shiru ta na sauraron su, kawai ta din ga jin,
idan jauhar tayi haƙuri da Viper mutum mai ban tsoro ta zauna da shi, ta yi
wannan gwagwarmayar lallai idan aka yi haƙuri Abdul ma zai iya shiryuwa.
Wani ɗan sanda ne ya leƙo, ya ce su shiga, sun ƙaraso. Gaban
ramma ya faɗi, maman ramma na can ta na shan hantsi, Nabila ta yi mata magana
ta ce ta taso.
Gaban ramma ya tsananta faɗuwa, aka yi musu jagora zuwa
ofishin da za a ɗauki statement ɗin.
A ciki su ka tarar da Viper a zaune, har da manyan mutane
abokan Indabo da su ka zo, ga mahaifiyar Abdul yasar a wurin ita ma.
Ai su na shiga office ɗin, Abdul ya miƙe, kallonsa ramma ta
yi, ya rame sosai da sosai, ba wai rama ta damuwa ba, rama ta ciwo.
"Rahama" ya kira sunanta a raunane.
Mugun kallon da Viper ya yi mata ne,ya sanya ba shiri ta
nemi wuri ta zauna.
Tashi ya yi ya nufi in da take, wani ɗan sanda ya daka masa
tsawa, amma bai saurare shi, ba ya nufi ramma. Ƙafa Viper ya saka masa, abin ka
da mara lafiya, ya tafi luu zai faɗi, Viper ya riƙe rigarsa ya hana shi kai wa
ƙasa.
Aka saka ɗan sanda ya janyo shi, ya zaunar da shi, tuni
ramma ta fara kuka.
Kawai ya zuba mata ido ko ƙiftawa ba ya yi.
"Abdul da ma wannan ce yarinyar da ka ke ta wannan
haukan a kanta, duk matan garin nan? Wallahi ka bani kunya" mahaifiyarsa
tayi maganar a ƙule.
Aka tambayi ramma sunanta ta faɗa, aka nuna mata Abdul aka
ce "Kin san wannan?"
Ta jinjina kai alamar eh.
"Waye shi?"
"Mijina ne" ta faɗa kai tsaye.
Gaba ɗaya su ka Kalle ta, cikin takaici mamanta ta ce
"A gidan uban wa ya zama mijin naki?"
Nabila ta tashi ta je gaban ramma, cikin raɗa ta ce
"Dan Allah ki nutsu rahama, ki yi bayanin komai, saboda a ƙwatar miki
hakkinki"
Aka sake tambayar ramma "Meye alaƙarki da shi, me ya yi
miki?"
Tayi shiru ta na kuka taƙi magana.
Abokin Indabo ya ce "Ni fa ina ga wannan abun duk da
masalaha aka yi, aka sasanta abun nan, dan gudun ɓacin sunan yarinyar nan, tun
da akwai aure kuma abin nan ya wu....
"Shut up, ba rikicin jam'iyya ba ne ba ko na siyasa, a
ƙwatarwa yarinya hakkinta mu ke buƙata" Viper ya yi maganar cikin tsawa.
"Aminu Viper, mai bunu a ƙugu ba ya kai gudunmuwar
gobara, ka bari ka fara kashe wutar gabanka, kafin ka zage ka na ɗaga jijiyoyin
wuya, haryanzu ɗa na ya na da gatan da za a iya shafe ko ma me ya aikata, mu ka
zaɓi ayi masalaha".
"Gobarar da nake ƙoƙarin kai gudunmuwar kasheta, ai ku
ne gobarar, dan kun fi ni shiga matsala da hatsari, a ɗauki statement a gabatar
da ƙararmu a gaban kotu "
"Ya isa haka, nan fa gaban hukuma ne, ba teburin caca
ba. Ke ki yi magana mu na jiranki" Ɗan sandan yayi maganar yana kallon
ramma.
Da ta ɗaga kai ta kalli Abdul, sai ta ji ta karaya.
"Talk" Viper ya daka mata tsawa, ta zabura ta
rirriƙe Nabila ta na kuka.
A hankali Abdul ya ce "Ku daina yi mata tsawa, yes i
rape her, na amsa laifina"
"Ba ka da hankali, lauyoyin ka ba su gargaɗeka a kan
kar kayi magana ba?"
Nabila cikin rarrashi, ta ce "Rahama ki yi magana, dan
Allah kar ki bari tausayi ya yi tasiri a zuciyarki, ki yi magana"
Cikin kuka ramma ta ce "Ai ya nemi yafiyata, kuma da
gani ba shi da lafiya, dan Allah a sassauta masa, ko a bari wataran idan ya
warke sai na yi magana".
Ayshercool
08081012143
Abu na farko da zamu buk’ata daga wajenka shine mahaifar
matarka, Ma’ana ba zaku haihu da matarka
ba.” Imaam ya ‘dago yana kallonsa Ya ji kansa ya wani sarà masa, amma sam ya
kasa masa musu… Alwan yana murmushi ya ce “Ka kirata ku yi shawara…” Ya fice ya
bar masa wajen. Da sauri Imaam Ya kira Safna. Tana d’agawa ta ce “Yaya? Imaam
Allah yasa dai baka musu taurin kai ba?” Ya saki huci ka’dan ya furta “Ba zan
iya abinda suke so ba….” “Zaka iya Imaam, ka yi koma me suke so? Yanzu fa ba
abinda baa yi saboda ku’di, ana ya Kai Kai, mutum yana kwanciyar da y’ar
cikinsa, da Uwar data haifeshi ma saboda ku’di, ana luwa’di da ma’digo saboda
ku’di, ana bada Uwa ko y’a Yaya ko k’anwa, K’ani ko wa? Duk saboda ku’di, don
haka ka yi ko me suke so Moddi Saboda ku’di… bana son musu…” ta fa’da tana zame
kanta a duk sunayen da ta ambata, bata k’i ya yi komai ba in dai zai samar musu
da ku’di, bata damu ta ji shara’din da suka bashi ba. Imaam Ya saki ajiyar
zuciya, sai ya ji ya samu k’warin gwiwar bayar da mahaifarta tunda ita ta
jawowa kanta ta ce ya yi komai saboda ku’di. A zuciyarsa Ya dinga jin baya so,
amma harshensa ya kasa amince masa ya furta baya so d’in. Ya kalli Alwan da Ya
shigo d’akin idanunsa a kansa shima ya ce “Yaya Aboki? Ka yarda ko a’a? Abu
guda dana sani baka isa ka San sirrinmu sannan ka bijire mana ba…..
Cab’di kin fara bibiya ko har yanzu… Hadarin gabas dai da
zafinsa yazo akwai cakwakiya anan gaba… Za’a yi kuka za’a yi dariya za’a sha
soyayya a cikin littafin nan. Hanzarta ki fara Ina Imaam Muhammad Moddibo Ya
kai kansa?
Ku kasance da littafin hadarin gabas.
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Gaba ɗaya su ka yi shiru su na kallon ramma, mamaki ya hana
mamanta magana, ya yin da tsananin baƙin ciki tamkar Viper ya yi ball da ita
haka ya ji.
"Gara ma ku yadda ayi sulhun nan, dan idan aka je kotu,
kunya za ku sha, tun da ma dai ya auri yarinyar nan ba sai a lallaɓa ba, ya
rufa mata asiri, tun da wannan yarinyar jaraba ce kawai irin ta yara maza amma
sam ba ajinsa ba ce ba".
Cikin dakiya maman ramma ta ce "Da ba ajinsa ba ce ba,
meyasa ya haike mata bai nemi ajinsa ba, mara tarbiyya da ba shi da mutunci, ba
wani taimaka mata da zai yi, auren nan kashe shi za ayi ban san da shi
ba".
Lauyan Abdul ya ce "Hajiya, ki daina maganar auren nan
fa, kowa ya san wan mahaifin yarinyar nan ne ya aura masa ita, kuma shi ne
waliyyinta dan haka ba ki da hujjar cewa aure bai inganta ba".
Nabila ta ja Ramma waje, ta kalle ta ta ce "Rahama
meyasa za ki yi mana haka? So ki ke ki lalata mana shirinmu?"
Cikin kuka ramma ta girgiza kai ta ce "Tausayi yake
bani, ya ce in yafe masa dan Allah a sassauta masa"
"Ki na son mijinki kenan, a bar muku aurenku?" Ta
girgiza kai alamar a'a.
"Magana zaki yi mini, abin da ki ke so dole shi zan yi,
a matsayina na lauyarki.
Idan kin ce a yafe masa, kar ki manta rashin hukunta shi ba
zai zama izina ga na baya ba, kuma ga sace ki da yayi ba tare da izinin
magabatanki ba, ga malam garba ya rasa ransa, duk domin a kare shi daga zargi,
ga kuma uwa uba abin da mahaifinsa ya yi wa yayanki har ya rasu Nura
guduma".
Ramma ta numfasa ta share hawayenta ta ce "Wallahi na
Sani Anty, ba kuma wai dan abin ba ya sosa mini zuciya ba ne ba, a duniya ba na
tunanin akwai abin da na taɓa tsana a rayuwata sama da Abdul yasar, idan na ce
a tsaurara masa saboda laifin mahaifinsa, ban yi masa adalci ba, mahaifinsa ne
ya yi wasu laifukan. A zamana da shi na san ba shi da cikakkiyar lafiya, kuma
mutum ne wanda al'unma su ke amfana da ilimin sa, da kuma dukiyarsa. Bayan haka
ba wai son sa nake yi ba, abin da yake cikina nake tausayawa, menene makomarsa
idan na kasa yafewa mahaifinsa, ni dai aka yi wa lafin, ni an riga an gama
cutar da ni, Abdul sanannen mutum ne, sunansa ya na ɓaci zai shafi ɗa na, kuma
ina matuƙar son abin da yake cikin nawa, dan Allah ki fahimce ni, ba wai ƙasa
zan watsa muku a ido ba, ko za ayi masa hukuncin a hukunta shi a sassauta masa
tun da ya yi nadama"
Rirriƙe Nabila ta yi, ganin Viper ya tinkaro su idanunsa
jawur fuskarsa a haɗe. Kafin ya ƙaraso, Nabila ta tare hanya ta ɓoye ramma a
bayanta.
"Wace irin banzar yarinya ce ke? Baki damu da
mutuncinki ba? Duk zullumi da fagabar da mahaifiyarki ta shiga, bai dame ki ba?
Mutuwar ɗan uwanki ba ta dame ki ba kenan?" Yayi maganar yana zazzaro mata
ido.
Nabila ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, ka yi haƙuri ka
tsaya ka ji, point ɗin ta abin dubawa ne, kuma ba ya nufin bai dame ta ba, abin
ya dameta kuma ba ta nufin, wai kar a hukunta shi ne, a'a sassauci ta nema
masa"
"Silent Nabila, duk wannan abin laifinki ne, guda nawa
take, haryanzu ba ta shekara sha takwas ba, tayaya za ta yanke decision da
kanta, as her lawyer, ke yakamata ki yi magana ba ita ba"
"Ko mun je court, dole sai ta yi magana, idan ban lallaɓata
na fahimceta ba, ta yi kwaɓa a kotu a gaban alƙali, case ya ɓaci, domin za ayi
amfani da maganarta, dan Allah ka yi haƙuri"
Viper ya ce "Ba wani haƙuri da zan yi, ta wuce ta je ta
bayar da statement na abin da ya faru, kafin na shaƙeta a wurin nan"
"Kai fa ka gama cewa so mugun wasa ne, idan ka ci gaba
da zafafawa, za ka ji kunya fiye da yadda ka ke zato, she's on her adolescent
period, ka san irin rayuwar da suka yi tare ne? A wannan stage ɗin da ƙwaƙwalwa
ake sarrafa irin su rahama, ba da zuciya da zafin kai ba. Ko dai ka bari nayi
aikina har a kai ga nasara, ko kuma zafin kanka ya sanya komai ya lalace, tun
da ta na son mijinta. Ni misali ce a wurinka, babu barazana da masifar da ban
gani ba, amma hakan bai canza mini ra'ayi ba. Haka zuciyar mace take".
Nabila ta mayar da idonta kan ramma ta ce "Rahama, ko
kin yi magana, ko ba ki yi magana ba, mu na da full evidence da yake tabattar
da cewa Abdul ya yi miki fyaɗe, ya sace ki ba tare da izinin magabatanki ba, ga
razanarwa da ya yi wa mahaifiyarki"
"Na sani anty, ban kuma ce kar a hukunta shi ba, duk
tausayinsa da nake ji ina da nauyin tabon cin zarafin da ya yi mini. A sassauta
masa kawai na ce, ba shi da cikakkiyar lafiya, sannan a duba goben abin da yake
cikina" Nabila ta share mata hawayen fuskarta, ta ce "I promise you
that, yanzu wuce mu je ki yi bayani"
Nabila ta ja hannun ramma, sai rakuɓewa take yi, dan kar
Viper yayi ball da ita kamar yadda ya ce.
Su ka koma ofishin, summaya ta bi ramma da ido gwanin ban
tausayi, nan ciki ma tun da su ka fita, ake yi wa Abdul magana, amma yayi shiru
ya ƙi magana.
Ramma ta zauna, Nabila na tsaye a kanta, ta sunkuyar da kai
ta ƙi kallon Abdul. Nan ta din ga amsa tambayoyin da aka yi mata ɗaya bayan ɗaya.
Aka waiwayi Abdul, lauyoyin sa su ka ce ba su yadda ba,
sharri ne aka yi masa.
Nabila ta ce "Wannan wani salo ne na tatsar iyayen sa,
ku ma mafitarku kawai ku ke nema, da neman wahalar da shi, amma duk wata
cikakkiyar shaida mu na da ita, duk wata ƙwarearku muddin ba cin hanci za ku
bayar ba, to tabbas wahalar banza za ku yi"
"Babu abin da ya yi miki zafi" ɗaya lauyan ya yi
maganar a kausashe.
Abdul yasar ya ce "Dan Allah kar aje a wahalar da ni,
ni dai na yi dan Allah ku bar ni haka"
Nan dai aka yi ta muhawara da musayar yawu, Abdul ya nemi a
bashi ko mintuna goma ya yi magana da ramma, amma Viper ya ce ba za'a bayar ba.
Nabila ta ce "Mijinta ne fa, haryanzu da aurensa a
kanta, ka ɗauki komai a hankali mana"
Wani ofishin aka kai Abdul tare da ramma, bai tsaya jin
nauyi ko kunyar ɗan sandan da yake kansu ba, ya rungumeta ƙam a jikinsa, yana
wata irin ajiyar zuciya.
Cikin kuka ta ce "Ka yi haƙuri Abdul, alƙawari ɗaya zan
yi ƙoƙarin cika maka, ganin cewa cikin jikina bai salwanta ba, ka yi haƙuri dan
Allah"
"Rahama, ni mai laifi ne, na daɗe ina aikata laifuka
iri-iri ba a hukunta ni, sai a kanki, da ki ka zama ƙaddarata, rahama so masifa
ne, kwanakin da na yi babu ke kamar zan yi hauka. Tsare mahaifina a Abuja, bai
yi mini zafin rasa ki da na yi ba. Na san hakki ne yake bibiyata, ni ko da za a
hukunta ni, dan girman Allah ki yafe mini, wallahi yanzu na fi tsoron Allah da
irin hukuncin da za ayi mini. Kin kwaɗaitar da ni, da nuna mini muhimmancin
tsoron Allah, Astagfirullah".
Na ta hannun ta saka ta zagaye gadon bayansa ta ce "Ina
ma ba ta haka ƙaddara ta haɗa mu ba, da zan jarraba jurewa na zauna da kai, na
yi kamar yadda na ji tarihin rayuwar matar Viper, duk da na santa amma ba ni da
wani wayo sosai lokacin. Ka yi haƙuri hukunta ka kawai shi zai rage mini raɗaɗin
da nake ji, da tabon da ku ka yi wa ahalinmu"
Ya jinjina mata kai ya ce "Na fahimce ki, zan so jin
tarihin rayuwar matar Viper, duk da shi na sani, shi ya yi wa mahaifina aiki,
ban san wace irin tsatstsamar alaƙa ce a tsakaninsu ba, har yake son ɗaukar
fansa ta ƙarfin tsiya a kaina ba. Idan kin kawo mini ziyara prison sai ki bani
labarin" tayi shiru ba ta ce masa komai ba.
"Zan ba wa lauyana lambar wayar su saifu, su tuntuɓi
lauyar ki, a damƙa miki kuɗinki, da kuɗin kula da kanki da zuwa asibiti da
rainon yarona, yayi maganar yana shafa cikinta da ya ɗaga kaɗan.
Ajiyar zuciya kawai take ta saki, ya ɗagota a hankali yana
kallonta, ita ma ta yi rama sai dai fatarta ta ƙara kyau.
"Dan Allah ko an yanke mini hukuncin, dan Allah rahama
kar ki bari a raba aurenmu, na san ba lallai na yi tsawon rai, ciwo nake har da
aman jini, dan Allah kar ki bari su rabani da ke, dan Allah"
Ramma ta gyaɗa kai ta ce "Allah ya sa kar su fi
ƙarfina"
"Amin sweetheart" ba ta yi aune ba, ya haɗe
bakinsa da nata cikin tsananin kewarta.
Ɗan sanda ya kawar da kai gefe, duk dambarwar bala'in da aka
gama yi, bai dame su ba.
Ya dafo kafaɗarta su ka fito, Viper ya na tsaye, kamar ya
fashe, Babar ramma ce wa take "Wallahi Aminu ka yi mata duk hukuncin da ya
dace, ban taɓa tunanin ramma za ta aikata abin da ta yi ba".
Nabila ta ce "Mama ni fa na fuskanci ramma, wallahi ki
ka bar ta da shi, za ki iya dawowa daga baya ki yi da na sani, ku yi haƙuri na
yi magana da ita na fahimceta"
Can ma babar Abdul masifa take yi, "Wace irin jaraba ce
haka Abdul, yarinyar da su ka gama tozartaka yanzun nan, shi ne ka wani dafo
kafaɗarta ka na ƙus-ƙus?"
Babu wanda Abdul ya kula, ya sunkuya dai-dai kunnenta ya ce
"Dan Allah rahama kar ki auri wani, sai dai idan mutuwa na yi, ina sonki
your excellency" murmushi ne ya suɓuce mata, ta ƙwace kafaɗarta, ya yi
murmushi ya ƙarasa wurin yan sandan da su ka zo da shi.
'yan sanda su ka tabattar musu da cewa za su kai su kotu,
bayan sun kira Naja'atu Bunkure ita ma sun ɗauki statement ɗin ta, domin kuwa
har da ita su Nabila shigar da ƙara.
Kunnen ramma Viper ya riƙe, ba wani riƙon kirki ya yi mata
ba, amma kamar ta yi fitsari.
"Ashe ba kya ji ba ki san ciwon kanki ba ko? Ba kya
tausayin kanki ba kya na mahaifiyarki, babu yayanki sunanki ya ɓaci, amma duk
hakan bai ishe ki ba ko? Idan ki ka kuma misbehaving, ko kuma ki ka sake yin
wani abu da sunan a raga masa, sai kin bi shi prison ɗin"
Nabila ce ta din ga yi masa magiya, da kyar ya saki kunnen
ramma, da take ta uban kuka.
Nabila ta yi ta rarrashinta, ta saka su a mota, tare da ba
wa mahaifiyar ramman haƙuri, a kan kar ta je ta ce za ta yi mata faɗa a kan
abin da ta aikata, lamari ne na sun yi zaman aure mata da miji, babu wanda ya
san irin zaman da suka yi, da haka su ka tafi, Nabila su ka yi sallama da
Sumayya.
Ita kuma tare da Viper su ka tafi ma'aikatar Shari'a, sai
dai ya cika ya batse dan daga ita har rammar a ƙule yake da su, gani yayi ma
kamar Nabila goyon bayanta ta yi, idan ya yi wasa, biye wa Ramma za ta yi, su
kasa taɓuka abin arziki a kotun.
"Vi" ta kira sunansa. Bai amsa ba, ba ta damu ba,
tun da ta san ya na jin ta.
"Ka yi haƙuri, ba na nufin yin wani abu da zai ɓata
muku rai, amma ka kalli abin da na yi cikin tsanaki, ban ji dadin abin da ka yi
wa rahama ba. Sai kuma abu na gaba, ina sake yi maka tuni game da mahaifinka,
ya na cikin tsantsar damuwa, jiya na daɗe ina waya da shi, ya na buƙatar ka a
cikin rayuwarsa, kai ne sitiyarin da ya rage, na saita gidanku, ya na kewarka,
kuma ya na neman afuwarka" yayi mata shiru, ita ma ta na gama yi masa
bayani, ta fice.
****
Major ya na zaune a ofishin sa na gidan gonarsa, ya jera
hoton Nabila, da na chubaɗo da kuma na Jauhar da Viper da Nasir ya kawo masa.
Duk rabonsa da jauhar, tun ta na jaririya, amma babu in da
kamaninta su ka bar na Nabila.
Hakazalika babu in da su ka bar kamanin chubaɗo, mamaki ya
din ga yi yadda aka ce masa jauhar ta na raye, bayan an tabbatar masa da ta
rasu. Kuma ya san wanda ya gaya masan ba zai yi masa ƙarya ba. Amma da ya san
za ta rayu da bai kai wa Bashir ita ba, duk haɗawa zai yi ya riƙe su, amma
saboda tsabar rashin mutunci bayan azabtarwar da Bashir ya yi wa chubaɗo,
ƙarshe ya rasa abin da zai yi wa 'yar ta sai haɗa aurenta da ɗan daba, wanda ya
yi ajalinta, kuma yanzu wai Nabila take kare wanda ya kashe ta ɗin, kuma har ya
na goyon bayan kare wanda ya kashe yarinyar, a take ya ji ya ƙara tsanar
Bashir, gaba ɗaya yayi dana sanin saninsa a rayuwarsa, ya rusa musu dukkanin
farinciki da walwala.
***
Ma'aikatar Shari'a ta sahalewa Nabila damar tsaya wa Viper a
kotu, dan haka bakinta ya saka rufuwa, saboda murna.
Sumayya kuwa tuni ta watsa hirar da su ka yi da ramma, yadda
ta yi bayanin, yadda Naja'atu Bunkure ta din ga yi musu sintiri a kan lallai,
su karɓi kuɗi su yi shiru da bakinsu.
Hakan ya ɗauki hankalin mutane, wasu su na cewa ƙarya ne,
hayar yarinyar aka yi, domin ɓatawa Bunkure suna, wasu kuma su na Allah wadai
da abubuwan da ta aikata.
Hannun Bunkure na karkarwa, ta ke karanta takardar gayyatar
da aka yi mata hukumar 'yan sanda, amma ta yayyaga takardar, ta watsar ta na
huci, babu wata hanya da za ta bi, ta fitar da kanta, duk ma su tsaya matan
take zuba rashin mutunci, duk sun watse sun barta.
Viper ya na zaune a falon madam Halima, ya na ƙarasa aiki a
wayarsa, kafin ya tafi.
Nabila ta fito ta tarar da shi, ta ɗauka tuni ya tafi, tun
da ba su dawo ba, sai magariba, har wurin aikinta su ka je, ta haɗu da
barrister Habib, sannan abokan aikinta sun ƙara mata ƙwarin gwiwa sosai da
sosai.
Ta zauna a kujerar gefensa, ta ce "Vi" ya amsa da
"Mmm" ba tare da ya kalleta ba.
Ta ƙura masa ido, ta na tunanin ta ina za ta fara cire
ƙaunar bawan Allah nan daga cikin zuciyarta, a yanzu haka cikin tsananin sauri
zuciyarta take bugawa, ya yi kyau sosai da sosai, duk da ba ma'abocin fara'a ba
ne, amma a nutse yake gudanar da aikin. Bai damu da kallon da take yi masa ba.
Ganin ba zai ce komai ba ya sanya ta ce "A ina ka ke
kwana ne yanzu?"
"In da ki ka sanni"
"Ba za su baka wuri a barrack ka zauna ba, zamanka a
wurin can, akwai hatsari fa"
Ya girgiza kai ya ce "Wuri ne mai tarihi a rayuwata, ba
zan iya barin su Walid suka ɗai a wurin ba"
"Ka na da alƙawari wasu lokutan"
"Wasu lokutan fa?"
Ta ce "Ka na da zafi sosai" ya gyaɗa kai kawai.
Shiru ya yi ya na kallon wayar, sai kuma ya ɗago ya na
kallonta, "Meyafaru?" Ta yi maganar a hankali.
Ya girgiza mata kai sannan ya ce "Yaushe za ki je gida
wurin Abbanki?"
Nabila ta ce "Ina son zuwa, saboda ina kewarsa, a
duniya ina matuƙar ƙaunar Abbana, duk da na yi farinciki da ganin mahaifina,
amma so da shaƙuwar da nake yi wa Abba ya mamaye ilahirin zuciyata, amma a
ƙadamin da ake yanzu, Abba ya na matsanancin fushi, ban ga alamar sassauci a
tare da shi ba, kuma akwai ziga da ga ɓangaren Nasir, da mutanen gidan.
Ai na kira shi mun yi magana, ya ce muddin ina son
farincikin sa dole na bar shari'arka, tun da kai ka kashe 'yar uwata, kuma sai
na fita harkar mahaifina dan ba mutumin kirki ba ne ba. But na ga kamar akwai
magana a bakin babana, amma ban ga alamar Abba zai ba shi damar hakan ba, ya
sake ɗaukar zafi sosai da mutuwar jauhar.
Am confused now, na rasa me ma yakamata na yi, har ga Allah
ina son mahaifina, kuma Abba ma ina ƙaunarsa, na yi ƙoƙarin fahimtar da shi,
amma yaƙi fahimta ta, dama ni na mutu na huta ba jauhar ba, ina nema na sare na
gaji wallahi"ta yi maganar tana share hawayenta.
"Ita jarrabawa ba a cewa an gaji, keep trying you will
succeed " yayi maganar ya na miƙa alamar gajiya. Ya kashingiɗa da jikin
kujera ya lumshe idanunsa.
Sosai ya ƙara kyau a idonta, ba ta san lokacin da murmushi
ya suɓuce mata ba, a hankali ya motsa ya tashi ya ce "Ki cewa madam Halima
na tafi, sai da safe"
"Allah ya tsare hanya, ka gaishe da oga walid"
Ya jinjina mata kai ya fice. Wurin da ya tashi ta ƙurawa ido
ta yi shiru cikin damuwa, da ta warware wannan matsalar sai wannan,a haka tayi
bacci a wurin, ba tare da komawa ɗaki ba.
Da Viper ya koma gida, sai ya kasa bacci, juyi kawai ya din
ga yi a kan katifarsa.
Ya ɗaukko wayarsa ya duba lambar Nabila, ya din ga kallon
lambar, sosai take ba shi tausayi, duk da ta tashi cikin gata, rayuwarta na ɗauke
da ƙalubale na musamman, ya sarawa juriyarta da gwagwarmayar ta.
Ya san da Jauhar ce, babu lallai ta iya jure duk wannan
abubuwan, ba ta son tashin hankali, duk wani abu da zai janyo mata damuwa ba ta
fiye son sa ba.
Nan ya sake jinjina girman Ubangiji, ya ci burin sanya
Jauhar zama lauya, dan ya samu ta rage tsoro da kuma taimaka masa, a kan wasu
abubuwan, dan ya san al'umma za ta amfana da ita, kwatsam burinsa bai cika a
kanta ba, Allah ya karɓi a bar sa, kuma kwatsam ya haɗu da 'yar uwatta a
matsayin cikakkiyar lauya, kuma kowacce ta taka muhimmiyar rawa a rayuwarsa,
rawar da ba zai taɓa mantawa da ita ba. Duk da Jauhar rayuwarsa da ita ta
mussaman ce, amma shigowar Nabila rayuwarsa ta ƙara haska masa, zai iya zama mutum
ya nemi hakkinsa. Sai da maganganunta na baya bayan nan, haka nan su ke sukar
zuciyarsa lokaci zuwa lokaci, cewa da ta yi, su yi zumunci kawai. Ya lumshe
idanunsa a hankali tare da ɗora wayar a kan ƙirjinsa.
***
Alhaji mu'azzam ne a tsaye tare da Baba su na tattaunawa.
"An so zuwa tun a last week ɗin, amma Allah bai yi ba
ina Abuja, ashe Nabila 'yar uwar jauhar ce?"
Baba ya ce "Eh, 'yan biyu ne amma ya aka yi ka
sani?"
Ya numfasa ya ce "Tun shekaru uku baya, na ganta a
Abuja, na cigaba da bibiyarta, amma a iya binciken da na yi na tarar da Jauhar
ba ta da wata 'yar uwa. Ba na son zuwa gidan nan, saboda jin nauyin abubuwan da
su ka faru.
Haƙiƙa na ci gaba da bibiyar rayuwar Viper bayan mutuwar
jauhar, kuma kwatsam na ga Nabila ta shiga rayuwar sa, shi ya yi ta yi mini
kashedin, kar na kuskura na sanar wa wani har ita Nabilan, ta na kama da
matarsa, na ƙyale su, sai kuma nake samun labarin ya kawo maka ita ina taya ka
murna"
Baba ya ce "Na gode, Na gode sosai da sosai Allah ya
biyaka da gidan Aljanna, tabbas ba ni da bakin yi maka godiya" sun daɗe su
na tattaunawa kafin ya tafi.
Nabila na ta shiri, za a fita da ita a kaita wurin aiki, sai
ga kiran waya, ba ta san lambar ba, amma ta ɗaga su ka gaisa da mutumin ya ce
"Sunana barrister Nazifi Bala, lauyan Abdul yasar ma'aruf Indabo"
Nabila ta yamutsa fuska ta ce "Yaya aka yi?"
"Eh dan Allah lokaci za ki bamu, ki taho da ramma, zamu
tattauna da Abdul za'a damƙa miki dukiyarta"
"Wace irin dukiya kuma, ni fa ba na son salon yaudara
da cin hanci, idan ku ka bamu corruption zamu karɓa, but use it against you
guys"
Barrister Nazifi ya ce "Ba corruption ba ne ba"
Ta ce "Shikenan, zan zo nan da ƙarfe sha biyu na rana,
amma ba zan zo da ramma ba, ban san me za ku yi mata ba"
Ya ce "Shikenan, ta zo itakaɗai ɗin"
Ba ta je office ba, ta tafi gidan su sumayya, sun sha hira
da umman sumayya, umman ta din ga yi mata addu'a, tare da yi musu fatan
alkhairi da addu'oi.
Yanzu tare su ke komai da Sumayya, Sumayya na biye da Nabila
domin samo labarai kala-kala.
Babban abin da ya ba wa Nabila mamaki, bai wuce ganin Saifu
a wurin ba.
Cikin mamaki ta ce "Wannan ba a gidanmu ka ke ba, yaya
saifu ko?" Ya miƙe ya ce "Nabila, me ki ke yi a nan?"
"Ni ce lauyar rahama, wadda Abdul ya yi wa fyaɗe, me ka
ke yi a nan?"
Jiki a sanyaye ya ce "Abdul abokinmu ne, tare muke da
shi"
Cikin takaici Nabila ta ce "Tare da ku ya yi garkuwa da
yar mutane kenan bayan ya yi mata fyaɗe? Kun san in da ya ɓoye ta, amma ku ka
rufa masa asiri? 'yar uwar Viper ce, sister ce a wurinsa yanzu ba su da kowa
sai Allah sai shi"
Sai yanzu Abdul ya samu amsar sa, ya rasa dalilin da ya kawo
Viper cikin shirgin ramma, da ya zo ya na ta zaƙewa.
Cikin ƙarfin hali ya ce "Ba su san duk abin da na
aikata ba, ki zauna ki ji menene. Amma saifu a ina ka santa?"
"Ƙanwar nan ta wa da Viper ya kashe jauhar, 'yan biyun
ta ce, bamu sani ba sai just recently" ya jinjina kai ya ce "Ga
lauyana, na ga ke ce lauyar rahama, kuma jikina ya bani zaki yi amana, dan haka
kuɗi nake son mu damƙa miki, na kula da rahama, zuwa lokacin da za ta haihu,
dan Allah a duba asibitin da za a kaita dan kula da rainon cikin, kar wani abu
ya same su. Ban sani ba ko zan rayu ko ciwo zai yi ajalina dan Allah ki tsaya
iya yinki ki kula da ramma ta yi karatu, na lalata rayuwarta, ko ba duka ba, ina
fatan ta zama wani abu a rayuwarta"
Ita kanta Nabila duk da ta ɗauki zafi sosai a kan shari'ar,
amma ta fahimci abubuwa da dama bai san an yi su ba, Nabila ta karɓi kwafin
takardun, ta ce masa za ta je ta yi nazari, idan ta ga da yiwuwar saka hannu,
za ta saka ta karɓa.
Su ka fito tare da Saifu, cikin damuwa ya ce "Nabila,
dan Allah meyasa ki ke tsayawa wanda ya kashe mana 'yar uwa, Vipern nan mutumin
banza ne, maimakon ki tsaya a ƙwato mata hakkinta, amma ki ka ɓuge da a wanke
shi?".
Nabila ta ce "Idan da wanda ya aikata laifi bai wuce
mahaifinmu ba, da ya ɗauki aurenta ya ba shi, alhalin ya san ga halin sa ba,
amma duk da haka, shi ma mahaifinmu bai yadda shi ya kasheta ba, meyasa ku ku
ka kasa yadda da hakan?"
Saifu ya ce "Idan ba shi ya kasheta ba waye? Dama kowa
ya san ɗan shaye-shaye ne ya sha ya bugu ya halakata amma kalli yadda yake yawo
a gari"
Kawai ta yi murmushi ta ce "Da yawa kallon mara inani
ake yi mini, duk mai son sanin haƙiƙanin abin da ya faru, mu kasance a kotu
sati mai kamawa, amma yanzu dole zan bika, ina son tattaunawa mai muhimmanci da
shi, a kan shari'ar da zan fara ta Viper da kuma game da rayuwar mahaifiyata da
'yar uwata a gidan".
Ya yi shiru ya na kallon Nabila, kamar ranta akwai wani abu,
amma a sanyaye ya ce ce "Babu laifi mu je" ya tafi a motarsa, ita
kuma a wadda aka kawota.
Su na tafe a mota, ta tsinci kanta, da kallon hotunanta na
kammala makaranta, tare da Major.
A duniya ta shaƙu da major, duk da yadda yake cin ƙaniyarta,
a duk lokacin da ta aikata ba dai-dai ba, dan ta zuba rashin ji.
Shi ne uwa shi ne uba, duk da ta shaƙu da magajiya, amma
major na musamman ne, hatta lokacin da ta fara al'ada, a makaranta ta na jss 2,
tayar musu da hankali ta yi, sai da aka kira major ya je har makaranta, ya ɗauke
ta su ka koma gida, ya kai ta asibiti ya zauna ya ƙara yi mata bayani. Duk abin
yake yi, aka ce ga wani abu da ya shafeta, zai ajiye ya je kanta.
Zaman kudancin Najeriya ya sanya Nabila gaba ɗaya ba komai
take ɓoye wa Abba ba.
Ranar graduation ɗin ta, dubu ɗari biyar ya ba ta, hotunan
da suka yi kawai, suka ƙara tabattar da akwai shaƙuwa a tsakanin su.
Ta shafi screen ɗin wayar, ta ce "You will forever
remain in my heart, kar ka yi fushi Abbana, ka bani lokaci kaɗan kawai".
Viper ya na zaune, ya kunna aiki ya na aikin tracking ɗin
wasu kayan laifi da ake ƙoƙarin barin kano da su, notification ɗin sa ya nuna
masa Nabila ta nufi hanyar gidansu. Mamaki ne ya kama shi, me za ta je yi ba
tare da ta gaya masa ba? Kawai jikinsa ya ba shi akwai wani abu.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Ku kasance da littatafan bright pens, second batch.
*ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)*
*MUTALLAB (NIMCYLUV)*
HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)*
*ZAYTOON (ZEE KUMURYA)*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA
MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO
TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake
dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne
maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya
jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana
son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara
, ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da
k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada
matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana
kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko
baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga
kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a
kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar
Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin
kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku
kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana
shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki
shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar
daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta
sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to
yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su
Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar
mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance
bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa
Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta
kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa
ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina
tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa
kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko
wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya
bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari
dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai
gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan
numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan
number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta
hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf
likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Sake kallon wayarsa ya yi, ya ga location ɗin wayarta ya na
harba hanyar gidan mahaifinta.
Kasa nutsuwa ya yi da hakan, kawai ya tashi ya sanya kaya ya
fita.
Saifu ya riga su Nabila ƙarasawa, Allah ya sa Baba bai kai
ga fita ba.
Saifu na sanar masa, Nabila ta na hanya, bakinsa ya ƙi
rufuwa, ya fasa fita, ya ce a haɗa mata kayan abinci.
Ya ce "Saifullahi ita da wa za ta zo nan ɗin?"
Saifu ya ce "Itakaɗai ce, kai take son gani"
Cike da fara'a ya ce "To Allah ya kawo mini ita lafiya
cikin aminci"
Ana haka Nabila ta yi sallama, hafsa ta fito da gudu daga ɗaki,
ta rungumeta ta na "Oyoyo ga jauhar"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Nabila dai, ba jauhar
ba" ta yi shiru ta na kallon Nabila.
"Kin ƙi yadda haryanzu ko?" Ba ta sake cewa komai
ba, ta ci gaba da kallon Nabila, ta na ƙoƙarin gano dalilin da ya sanya za ace
mata ba jauhar ba ce ba.
Baba da kansa ya fito ya tari Nabila, har zuwa ƙaton
falonsa, ta zauna su ka sake gaisawa, babu kunya Zakiyya da maman saifu su ka
biyo bayanta har ɗakin su ma.
Su ma ta gaishe su, su ka amsa su na kallon ta kamar baƙuwar
halitta.
"Ya ki ke aikin naki?"
"Lafiya ƙalau Alhamdilillah"
"Ina ɗaya 'yar ta wa?"
Nabila ta ce "Ta na wurin aiki, ni ma zuwa nan ɗin faɗo
mini kawai ya yi na taho"
Ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ne, yaushe za ki kammala
aikin ne, ki dawo ki zauna tare da ni, in dinga kallonki ina jin daɗi tare da ɗebe
mini kewar jauhar"
"Baba ko na kammala, zan zo dai na ɗan yauta maka amma
ba zan iya dawowa gidan nan na zauna ba, idan na dawo nan gaba ɗaya Abba fa?.
Na zo ne na nemi bakin zaren saita tarwatsatsiyar alaƙar da cikinku babu wanda
yayi tunanin gyarata duk a sanadiyyar hawa dokin zuciya da ku ka yi.
Baba, kai mahaifina ne, major kuma rayuwata ne, kuma ka san
waye shi, a fannin tsatstsauran ra'ayi da kafiya, a wannan karon ya sake ɗaukar
zafi da yin fushin da har ya nemi ko dai na rabu da kai, da shari'ar mijin
jauhar, ko kuma babu ni babu shi, saboda ya na ganin jauhar ba ta samu kyakywar
rayuwa daga gareka ba, ka aurar da ita ga ɗan daba, wanda ya yi ajalinta.
Tabbas na rayu dogon zamani, cike da muradin son sanin waye
mahaifina, sai dai gaba ɗaya na sare, gwiwata ta yi sanyi, tun bayan da na
saurari labarin abin da ya faru.
Sai dai hakan ba zai hanani sauke hakkina a matsayina na 'ya
ba, yanzu warware mini wasu abubuwan, zai taimaka mini a kan shari'ar nan, kuma
ya taimaka mini wurin wanke ka a wurin Abba. Dan Allah ka fahimce ni, ba wai
ina fatan na ƙure ke ba ne ba, mafita nake nema, saboda ni ce a tsakiya muddin
aka ci gaba da tafiya a haka, rayuwata aka saka a tsakiya dukkaninku kuna da
muhimmanci a gare ni, kuma babu wanda zan iya zaɓa na bar ɗaya. Dan Allah baba
ka warware mini abubuwan da su ka shige mini duhu. Me mahaifiyarmu ta yi maka,
ka barota a garin da ba ta da kowa sai Allah sai kai, meye dalilin da ya sanya
ka aura wa jauhar mai zamani, duk da ka san waye shi?"
Baba yayi shiru, sai hawaye da yake gangarowa daga cikin
idanunsa.
Zakiyya ta ce "Ke kuwa abin da ya riga ya wuce, menene
na gutsura magana, abin da ya faru ya riga ya faru, sai fatan Allah ya kiyaye
gaba".
Nabila ba ta kulata ba ta ce "Talk please"
Ya numfasa ya ce "Nabila, na ga ƙoƙarin ki da ki ka yi
saurin saukkowa daga fushin da ki ka yi, ki ka saurareni, kawunki ya yi mini
laifi, amma zan iya cewa koma menene ni na janyo.
Kuma na so na yi magana da shi ta fahimtar juna, sai dai
tsawon wannan shekarun, major bai canza a yadda na san shi ba, yanayin sa ya
tabattar mini da ba zai taɓa ba ni dama ya saurare ni ba, tun da amana ce ya
bani na ci.
Haƙiƙa na so chubaɗo, so na gaskiya, ga ta 'yar ƙauye ba ta
da wayewa sosai, amma ina samun nutsuwa da kwanciyar hankali a tare da ita,
babu hayaniya ba ta da tashin hankali da kan ƙara, ta na da matuƙar haƙuri da
biyayya. Ita kuma zuciya na son mai kyautata mata, hakan ya sanya ko a cikin
dangina, ba na ɓoye son da nake yi mata, da na zauna hirarta kawai nake yi na
ji daɗi.
Ba a iya cikin gidana ba, hatta a yan uwana, sun fara nuna
mini cewar ina zaƙewa a kanta, dan sai da aka fara haɗa ni da mariƙiyata a
lokacin nan, cewa na tattarare a wurinta, ta yi mini asiri.
So da tausayinta ya sanya na ɗauke ta, na tafi da ita garin
da nake aiki, saboda ta haihu a tare da ni, na ba ta dukkanin kulawat da ta
dace, sai dai daga zuwa hutu, ban san meyafaru ba na manta da chubaɗo gaba ɗaya
a cikin kaina ba, na kan yi mafarki da ita, amma da na tashi sai na manta me na
gani. Ina yawan ƙoƙarin tuna wani abu mai muhimmanci a tare da ni, amma sai na
kasa.
Na karɓi transfer ta, na cigaba da aikina, sai watarana da
na je azare, ƙanwata ta yi mini maganarta, sannan na tuna da ita, sai dai a
lokacin sunanta kawai da ta kira, na ji kamar na kurma ihu, na ji a duniya babu
abin fa na tsana sama da chubaɗo, ko kiran sunanta ba na son na ji an yi.
Har zuwa lokacin da major ya kawo mini Jauhar, na furta masa
sakin chubaɗo ƙasan zuciyata na ƙuna saboda takaici, amma a zahiri ko a jikina.
Sai dai na ɗauki soyayyar duniya, na ɗorawa Jauhar, saboda
babu in da ta bar chubaɗo a kamanni da kuma haƙuri.
Bayan dogon lokaci, kamar wanda ya farka daga bacci haka na
tashi cikin tashin hankali, na tariyo abubuwan da su ka faru, na shirya na tafi
Jalingo ba tare da sanin kowa ba, na je rigar su chubaɗo. Sai dai mummunan
labarin da na iske ya kaɗa ni, wai major ya tafi da ita can in da yake, amma da
ita da yaranta duk sun mutu.
Ban kawo cewa 'yan biyu bane ku, na yi zaton kawai shirme
ne, na mutanen karkara, mussaman su da ba hausa ce ta wadace su ba.
Su ka tabbatar mini da chubaɗo ta rasu, dan maitama da kansa
ya je ya sanar musu da mutuwarta.
Tsananin tashin hankali ya sanya na yi hatsari a hanya, na
samu karaya hannu da ƙafa, da raunuka sai da na yi jinya kamar ba zan rayu ba.
Na yi kukan rashin chubaɗo, kuma na yi kuka da nadamar abin
da na yi.
Na bibiyi in da major yake aiki, amma duk wata kafa da zata
sada ni da shi ya toshe ta, ban san adadin zuwana Jalingo ba, har a shekarun
nan na je, suka ce mini tun da ya je su ka ce masa na je nemansa, har rana mai
kamar ta yau bai sake zuwa ba. Waɗanda na ɗan sani a rigar ma duk sun rasu, duk
aure-aure na, har yau ban samu mace kamar chubaɗo ba, ita na aura domin
soyayya, uwargidana auren zumunta, ta biyu saboda aikina uwargidan da fari taƙi
bi na, chubaɗo kuwa soyayya ce ta sanya na aureta".
"Au to mu da ka auremu ba dan ka na sonmu ba, ai da
sallamar mu ka yi tuntuni, ashe mu zaman kare a karofi mu ke yi"
"Aifa tun da mu zaman 'ya'ya mu ka yi, ashe zaman
larura ka ke yi da mu wadda ka ke so, zuciyarka take muradi daban"
Saifu ya ce "Dan Allah mama menene haka? Duk wannan fa
girmanku ba ne ba, abubuwan duk da ku ka aikata duk bai ishe ku ba?"
Mama ta ce "Rufe mini baki, kafin na mangareka"
Baba ya numfasa ya ce "Tabbas zaman larura, zaman
'ya'ya nake yi da ku, lokuta da dama ba na gane kaina, kawai dai rayuwa gata
nan ne dai ina yi.
Haka jauhar, akwai abokina sadis Allah ya jiƙansa, shi ya
ankare da halin da nake ciki, duk soyayyar da nake yi wa jauhar, ba na iya kataɓus
ko da za a dafata a sha romonta, ya ce yakamata na binciki rayuwata, kamar
akwai abin da yake damuna. Na ce masa ni ba zan bi bokaye ba, ya ƙyale ni, ya
ce mini ba bokaye ba, in nema wa kaina tsari, amma ko a jikina, ni lissafin
matan da na tara, da yara yadda zan riƙe su na kula da su, shi ne kawai
damuwata in nemi kuɗi.
Ga kuɗin akwai su, amma ba na iya morawa jauhar, ina
kallonta da yagaggen tufafi, ta na aiki kamar baiwa a cikin gidan mahaifinta
amma ba na iya cewa komai.
A cikin ƙannena, ɗaya da ta na cikin masu adawa da Chubaɗo,
ta kwanta ciwo, na je dubata ta riƙe hannuna ta na kuka take neman afuwata, ta
ce mini haushin rawar kan da nake yi a kan chubaɗo ya sanya ta haɗa kai da
Maimuna, su ka yi mini asiri, da sunan chubaɗo bayan an yi mana farraƙu, aka
zuba asirin a cikin toka, su ka kai cikin ruwa mai tafiya, wai yadda ruwan nan
ya tafi da tokar ta ɓace, haka ya tafi da tunanin chubaɗo a kaina. Sannan su ka
koma, su ka yi mini sihiri, aka binne a maƙera, yadda ake rura wuta a maƙera,
haka zafin ƙiyayyar da na yi mata yake ruruwa a zuciyata duk lokacin da aka
kira sunanta.
Babu wani mahaluki da na sanar wannan maganar, na haɗiyeta a
cikina. Na daina yawon aure-aure dan ba za a bari su zauna ba, sannan duk wadda
na aura, ta na da tata kalar matsalar. Wasu abubuwan ba na sanin ana yi wa
jauhar, Jauhar ba ta iya tambayata abu, ko kawo mini ƙara.
Duk 'ya'yana su na rayuwa kamar yaran sarakai, pant wanda
'ya mace za ta saka, sai na saya, pad ɗin da za su yi amfani da ita ta jinin
al'ada, ta na cikin budget ɗin da nake yi duk wata, amma ba na iya magantawa
'yar marainiyar yarinyar da duk cikin yarana babu wanda nake jin daɗinsa, babu
mai tausayi da imaninta, amma ba na iya maganta mata komai. Ko da su ka rushe
maganar auren jauhar, duƙufa na yi addu'a, haka kurum kuma na ji na karkata na
aminta da aurawa jauhar Al'amin. Ko a lokacin da na amsa aura wa Alhaji
mu'azzam ita, na amince ne domin ta huta ta samu nutsuwa a can, tun da ni na
gaza samar mata da kwanciyar hankali a matsayina na uba, wallahi nauyin
laifukan da na aikata ina jin su a tsakiyar ƙirjina Nabila, rayuwa kawai nake
yi, amma babu abin da yake yi mini daɗi, mussaman idan na tuna laifukana ga
chubaɗo da jauhar, na san ni mai laifi ne, ki nema mini afuwa a wurin
Abbanki"
Hafsa ta yi wuf ta ce "Wallahi lokacin nan, wani abu
aka saka a bakin wata mage, aka binneta da ranta, wai ba zaka ce komai ba, idan
aka ce a aura wa jauhar Mai zamani, da maman su saifu, da Anty. Sai kuma Anty
da matar gidan su mai zamani, su ka din ga kai ni wurin wasu mutane, ana bani
abubuwa wai saboda Alhaji mu'azzam ya aure ni, amma na gaya wa jauhar komai ai,
kuma na ce ta yafe mini, jauhar ai na gaya miki duk yadda aka yi, ki ka ce kin
yafe mini, amma kar in gaya wa kowa" tayi maganar tana kallon Nabila.
Kamar ƙaramin yaro, saifu yake kuka.
Zakiyya ta ce "Hafsa ki rasa wanda za ki yi wa sharri
sai uwarki, a gidan uban...
Maman saifu ta katseta da cewa "Uban waye bai san ki na
biye-biyen bokaye ba?"
"Idan ma na bi gara ni, a kan ku wanda ku ka haɗa kai
ku ka yi wa chubaɗo ai"
Nabila ba ta ce komai ba, ta miƙe, ta ɗauki jakarta da
wayarta ta na wata irin tsuma, kafin Zakiyya ta yi yinƙurin ba wa Nabila hanya,
tuni ta angijeta ta wuce.
Saifu ya bi bayanta ya na kiran sunanta, Baba kuwa bai iya
motsawa ba, ya dafe fuskarsa ya cigaba da zubar da hawaye.
Hafsa zama tayi ta kwanta a jikinsa, ita ma ta na kukan.
Zakiyya da maman saifu kuwa kamar za su dambace.
Viper ya kawo kai, Nabila ta nufo barin layin, sojan da ya
kawota ya biyo ta ya na yi mata magana, amma kamar ta kurmance. Shan gabanta
Viper ya yi ya na tambayarta meyafaru.
Saifu ne ya nufosu, Viper ya riƙe hannun Nabila. Saifu ya
tsaya nesa kaɗan ya na kallon Viper, ya kalli Nabila ya kalli saifu, bai ce
komai ba ya ce wa sojan ya ƙaraso da motar su tafi.
Babu gardama ta shiga motar, sun fara tafiya ta ce
"Wurin Abba za ka kai ni"
"Meyasa? Meyasa ma ki ka zo ba tare da kin sanar da ni
ba?" Shiru ta yi masa, yanayinta kamar na mai shirin fita hayyacinta.
Tsaki ta ja ta ce "Dan Allah ni kawai ka kai ni wurin
Abba kawai".
"Amma kin san halin da ake ciki ko? Ya za ayi a mayar
da ke gida a wannan yanayin?"
Cikin kuka ta ce "Ni wurin Abba kawai zan tafi, ji nake
ma kamar haukacewa zan yi"
Gaba ɗaya tausayi Nabila ta bawa Viper, ya ce "Me za ki
je ki yi masa ne?"
Ya gyara zamanta ta dube shi ta ce "Viper, shekara ɗai ɗai
ɗai shekara ashirin da shida mutum ya na yawon asiri, could you imagine wai
asiri aka yi wa baba ya manta da mahaifiyarmu, aka zo ta mutu aka koma kan
jauhar, wai abin har da ƙanwarsa kai, jauhar ta yi haƙuri Allah ya sa ta na
aljanna, wallahi da ni ce idan ban haukace ba, guduwa zan yi na bar gidan, ko
ma na tsani baban namu, ina kallon ka na wahaltawa 'yan uwana amma ni ka tsane
ni, Allah sarki manana da 'yar uwata, wallahi kamar haukacewa zan yi Vi, ni
kowa ma ya kasa fahimtar halin da nake ciki" tayi maganar ta na kuka ta
kasa zama wuri ɗaya.
"Kin ga zauna sosai, ai na san me ki ke ji, ni ma ina
ji ai"
Ta na kuka ta girgiza masa kai ta ce "A'a ba ka
ji"
"Ina ji mana, ai na fiki sanin jauhar da wacece
ita"
"Har da matar gidanku wai aka yi asiri, a kan baba ya
amince jauhar ta aure ka"
Ya ce "Na sani"
"To ita meya kawo ta cikin wannan maganar matar gidan
naku?"
"Ƙawar babar hafsa ce" ya ba ta amsa.
Ta marairaice fuska ta ce "Dan Allah abubuwan nan ba su
yi mini yawa ba? Gaba ɗaya na rasa me ma zan ce, ta ina zan yi wa major wannan
bayanin, ba ma zai saurare ni ba, amma baba abin tausayi ne, gaba ɗaya matan
nan sun raina shi, ba su da kirki kai wayyo Allana ni na Nabila, da ma tun ina
jaririya tamowar ta kashe ni kowa ya huta"
Sai da Viper ya ji kamar ya yi dariya, amma ya gimtse,
tabbas Nabila ta na namijin ƙoƙari jaruma ce ta gasken gaske.
Kamar yadda ta buƙata, gidan major ya kaita, duk da ya san
ya saɓa doka, amma ta na buƙatar yin abin da zai sakata nutsuwa.
Mamaki ne ya cika 'yan gidan, ganin Nabila a gidan.
"Me kuma ya kawo ki gidan nan?"
Ba ta saurare su ba, ta nufi ɗakinta, wasu daga kayan Sauda
ta gani a ɗakin, har an gaje mata ɗakin.
Kamar mahaukaciya, ta fara watso kayan waje ta na huci.
"Ke Nabila wai meye haka ne? Ba an ce kin gano ubanki
ba, uban me ya dawo da ke gidan nan kuma? Ko ba kin zaɓi wasu daban a kan shi
wanda ya yi wahala da ke ba ne?" Mama tayi maganar ta na haƙiƙancewa.
Baba magajiya ce ta shigo da sauri, ta rungume Nabila cikin
farinciki.
Nabila ta ce "Baba magajiya, finally na ga abbana, sai
dai 'yar biyuna Allah ya yi mata rasuwa"
Baba magajiya ta ce "Alhamdilillah, Allah ya ƙara
tabattar da nasara"
"Ki zo ki fice daga gidan nan, kin tafi mun huta, kin
sake dawowa ki koma gidan ubanki mu ma mu sakata da mu huta da yaranmu"
Nabila ta ce "Ai ni da ke samamkal, duk ba gidan ubanmu
ba ne ba, har gara ni na da ke"
Mama ta ce dole sai Nabila ta bar gidan, tun kan Major ma ya
dawo ya ganta.
Baba magajiya ta ce "Da dai kun yi haƙuri ya dawo ɗin,
tun da babu wanda ya san abin da ya dawo da ita".
Sauda ta ce "Ki rufewa mutane baki, 'yar karere kawai,
ke ma kamata yayi ai ki tattara komatsanki ki bar mana gida, tun da amfaninki
ya ƙare"
Sosai faɗa ya kacame, Nabila ko a jikinta, ta gyara ɗakinta
tas, ta nemi mukullin motarta ta rasa, kai tsaye sashen Abba ta nufa, ta nemo
mukullin motarsa ɗaya, ta fito.
Duk yadda su ka yi ƙoƙarin hanata ɗaukar motar su ka kasa,
saboda yadda su ka lura da fuskarta babu mutunci.
Gidan Gonar Major ta nufa, ta na ta zabga addu'a domin ta yi
nasara a kansa ta samu ya saurareta, dai dai su ka yi saɓani, domin kuwa baya
nan.
Su na tsaye su na ta mayar da yadda aka yi, su ka saka baba
magajiya a tsakiya, su na kiranta da munafuka. Cikin rashin jin dadi Walida ta
ce "Bai kamata ba baba magajiya fa dattijuwa ce, kuma ba ta san komai
ba"
"Dalla rufe wa mutane bakinki a wurin"
Sallamar Major ce ta sanya su ka yi shiru.
"Meyafaru ake waye munafuki menene?"
Cike da ƙwarin gwiwa mama ta ce "Wai Nabila ce ta dawo
gidan nan"
Ya ce "To sai aka yi yaya?"
"Ai abin ne da mamaki, duk dambarwar da aka yi babu
kunya ta dawo gidan nan, motarka fa t ɗauka ta fita, ni dai na ce bar gidan nan
kafin ma ka dawo ka tarar da ita".
Ya kalli mama da ta haƙiƙance, ya ce "Saboda tare mu ka
haɗa kuɗi mu ka gina gidan?" Turus ta yi ta na kallonsa.
"Ina ruwanku da ita?"
Sauda ta ce "Amma Abba, abubuwan da ta yi maka fa, kuma
kai ka ce kar ta dawo maka gida, muddin ba ta yi abin da ka ce ba...
"Ni na gaya miki haka? Idan ma hakan ne na naɗa wani
wakili a cikinku ne da na ce idan ba na nan a yanke hukunci makamancin
wannan?" Su ka yi tsuru-tsuru.
"Duk in da za ta je ta san ba ta da kamar nan, ciki har
da gidan uban na ta, ni nake da ikon sallamarta ko na ƙyaleta a gidan nan, duk
in da za ta je ta dawo, babu ruwanku da ita"
Sauda ta ce "Amma Abba ta ɗauki motarka"
"Eh ta wace ai, ba wani abu" yayi maganar dai-dai
lokacin da Nabila ta shigo.
Su ka yi kallon kallo da Abba, ya wuce ya nufi ɗakinsa, bin
bayansa ta yi ta na kiran sunansa, amma ya yi mata shiru.
Sai da ta dangana har bedroom ɗin sa, wanda a nan ya tsaya,
ya juyo ya kalleta bai ce komai ba.
"Abba" ya kalleta.
"Abba dan Allah ka yi mini magana mana, ko zan samu
ƙwarin gwiwar sanar maka da abin da na zo maka da shi.
"Kin gama fushin kenan?"
"Abba ka fahimce ni, ka yi mini uzuri dan Allah. Na
kasa sarrafa zuciyata ne a wannan lokacin, ka yi mini uzuri ni ma 'yar uwata na
rasa.
Na je wurin baba mun yi magana ne, dan Allah Abba.
"Stop it please, in dai maganar mahaifinki ce ba na son
jin komai menene, sannan ki je ki cigaba da kare wanda ya kashe 'yar uwakki
saboda rashin kishin kai".
"Abba ba shi ya kasheta ba...
"Ba shi ya kasheta ba ke ce kenan? Azzalumin mutumin
nan, bayan kashe mini 'yar uwa, yar da ta bar masa ma, ya kasa riƙeta babu abin
da za ki gaya mini a kan mahaifinki na yarda Nabila, Kodayake laifina ne, da na
kai masa ita, ni dama ke na kai".
Jiki a sanyaye ta ce "Abba...
"Get out Nabila, ba na son ganinki ma, fita ki bani
wuri" ta haɗiye wani abu mai mugun ɗaci, ta fice daga ɗakin nasa.
Ɗakinta ta tafi, kawai ta nemi wuri ta kwanta, baba magajiya
ta kawo mata abinci, amma ta ce ba zata ci ba.
Washegari da sassafe, Viper ya isa ƙofar gidan su Nabila, ya
tsaya ya na kiran wayarta, Nasir ya fito da motarsa.
Bai kula shi ba ya ci gaba da kiran Nabila, ta ɗaga ya ce
"Ina waje" mintuna kaɗan ta fito cikin shirinta na fita aiki.
"Ina kwana"
"Lafiya ƙalau, ba wata matsala dai ko?"
"Akwai mana, meyasa za ka tambayeni, kai ma ka san
akwai muje kawai"
Wani irin azababben kishi, ya turnuƙe Nasir, ya fito daga
motarsa ya tunkaro su.
"Nabila, ki na nufin kin fifita son zuciyarki a kan
abin da Abba ya gaya miki?"
Nabila ta ce "Mu ƙaddara haka ne, meye naka a
ciki?"
"Mutumin da ya kashe 'yar uwakki, haryanzu ki na kan
bakanki na kare shi kenan?"
"Kai ma da ka samu dama, kashenin za ka yi, domin cikar
naka muradin. Yaya Nasir kallonka kawai nake yi, kuɗin da aka baka domin ka
kama shi, wasa da rayuwata da ake yi, ba tare da ka sanar mini ba, ko ƙoƙarin
bani wata cikakkiyar kariya ba, duk fa kallonka nake yi" saroro ya yi ya
na kallon Nabila.
Viper ya riƙe gefen kwalar Nasir, ya risunar da muryarsa ya
ce "Kar ka manta, ni ba karabutin ɗan daba bane kawai, hatta evidence na
kuɗin da aka baka, ina da shi. Dan haka ka ajiye kishi a gefe sauran mutuncin
da ka ke da shi a idonta ya zube. Nabila ta wa ce, ko da kuwa ita ma zan
kashetan ne"
Nasir ya kalli idon Viper, Viper ya kalle shi.
"Na fi ka gwagwarmaya da ganin wahalar rayuwa, dan haka
ba wani zare ido, da wani abu makamancin haka da zaka yi mini da zai tsorata
ni. Ka daina shiga harkata dan ka ganni tare da ita, idan ka ci gaba kuma abin
da zai biyo baya ba zai yi mana daɗi ba".
Tsagwaron kishi ne yake damun Nasir, kamar zuciyarsa zata
tarwatse haka ya na kallonsu, suka hau mota su ka tafi.
***
Abbu ya na zaune ya na ta lissafi na shekara, nawa zai fid
da zakka da sauransu. Hankalinsa ya yi zurfi sosai a tunanin.
Rahila na gefe ta na ta yi wa shahida masifar, an raba auren
su, ta dawo gida su na haɗa kafaɗa.
Shahida ta ce "Auren da da shi, gara babu, ni wallahi
ba na dana sani".
"Ai dama ba zaki yi ba, nan gaba za ki fahimci abin da
nake gaya miki"
Wayar Abbu ce ta fara ringing, sai da ta yi sau kusan uku,
sannan ya ɗaga.
Jin muryar babban mutum ya sanya ya nutsu, su ka gaisa.
"Daga nan hedkwatar hukumar hisba ne, mun kamo 'yarka a
cikin sabon gari, shekranjiya da daddare, kuma a binciken da aka yi, an gano ta
na ɗauke da juna biyu, kuma ga cutar ƙanjamau, dan haka mu na buƙatar ka zo mu
na son ganinka"
Abbu ya ce "Ba ni ne mahaifinta ba, ta baku lambar
babanta ba ni ba ne ba" ya gama wayar, Rahila ta ce "Na ji ana
maganar hisba, ka ce ba kai ne babanta ba"
Ya ce "Eh, 'yar ki da ki ka ce mini ta na gidanku, ita
aka gano a sabon gari, da ciki da kuma ƙanjamau, dan haka na ce a nemi
mahaifinta ba ni na haifate ba"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na shiga uku na
lalace, ciki da ƙanjamau kuma? Wayyo Allana"
Tashi ya yi ya fice ya bar mata falon.
***
Garden ɗin da suke haɗuwa da Nabila a da, can su ka tafi.
Ta kalle shi ta ce "Meyasa ka kawo ni nan"
"Ina jin nishaɗi idan na zo irin wurin nan, sannan wuri
ne mai sanya nutsuwa, ki ɗan huta kawai" wani irin daɗi ne ya ratsa
Nabila, ganin yadda ya nuna damuwarsa a kanta ƙarara, sai dai ta basar da ta
tuna alƙawarin da ta ɗauka.
Hannunsa riƙe da leda su ka ƙarasa cikin garden ɗin, ta
zauna ƙamshin furannin wurin na ratsata, haka kurum ta ji zuciyarta na narkewa
da ƙaunar mijin 'yar uwatta ta, da take ganin kamar ba ta kyauta ba cin amana
ne yin hakan.
"Vi"
"Abla"
"Abba yaƙi fahimta ta, ya kore ni, ya ce muddin ina son
zaman lafiya, to sai na bar shari'arka, na rabu da mahaifina".
Viper ya gyaɗa kai ya ce "Ya ɗauki zafi da yawa ne,
amma zai saukko, ba ya bari kin kwana a gidan ba?"
"Eh, jiya da na dawo ma na tarar ya na faɗan babu
ruwansu da ni, ina ga so su ka yi ya kore ni ma, duk sun gaje mini kaya, har da
motata"
Ya ce"Sorry"
Ta numfasa ta ce "Ka na addu'a kuwa, a kan Allah ya
bamu sa'a?"
Ya ce "Eh, ina yi"
"Masha Allah, amma fa dole mu ƙara, kuma ka yi haƙuri
dole za mu yi exposing wasu abubuwan da ka yi a kotu"
Ya ce "Kamar yaya? Ba dai aikina ba?"
Tayi murmushi ta ce "Ba wannan ba, rashin jin da ka yi,
da alaƙarka da indabo, ka san babban kuskuren da ka yi? Biye wa Nura guduma da ɓoyewa
likitoci ainihin abin da ya same shi. Da sun yi documenting hakan zai bamu
ƙwarin gwiwa da cikakkiyar hujjar dalilin da ya sanya rigima tsakaninka da
Indabo. Yanzu dole abin ɓoye ya fito fili, muddin lakwari ya kuma denying kashe
jauhar, shaidar ɗan mama kaɗai ta yi rauni, dole duniya ta san da videon
nan".
"Ki na nufin Videon Nura? No ba zai yiwu ba, cin amana
kenan da karya alƙawari".
Ayshercool
08081012143
Ta girgiza kai ta ce "Ba ina nufin lallai sai videon ya
fita ba ne ba, ka fahimce ni.
Indabo sun san me muke shirin yi, ba fa za su ƙyale mu ba,
bar ganin hankalinsa ya na kan ɗan sa da kuma tuhumar da ake yi masa, ya na da
muƙarrabansa, ya na da iyayen gidansa da waɗanda siyasarsu ta dogara da shi, ba
za su taɓa zuba ido su na kallonmu ba.
Duk wani tanadi da shiri da yakamata mu yi, dole mu yi shi,
ko da kuwa ya na nufin faɗar abubuwan da ka aikata. Dan ba kowa ne zai ɗauki
cewar akwai wata alaƙa tsakanin ɗan daba da mutum kamar sanata ba, har ta kai
ga ya kashe maka mata ba. Dole sai mun shirya da shaidu da hujjoji fa, ba da
ƙanan lauyoyi zan kara ba, na sani manyan lauyoyi ne iyayena a harkar aiki,
muddin aka kai ga gaɓar da sunan Indabo zai fito a cikin shari'ar nan. To fa
tsuguno ba ta ƙare ba, dan haka kurum su lakwari ba za su kashe maka mata
ba, kuma dole za su yi ƙoƙarin kare kansu, ko mu bamu faɗa ba, su za su iya faɗar
wasu abubuwan da suke da alaƙa da ka yi daba da kuma dillancin miyagun ƙwayoyi,
wanda laifi ne ga dokar ƙasa, da za na iya fuskantar tuhuma"
Viper ya yi shiru jikinsa a sanyaye ya ce "Da sauran
rina a kaba kenan? haryanzu ban gama karɓar sakamon laifukana ba kenan"
yayi maganar cikin damuwa ya na ɗan murza zoben hannunsa.
Cikin kulawa da matsanancin tausayin sa ta ce "In sha
Allah komai zai warware, ai babu abin da ya fi ƙarfin Allah, kuma shi mu ke
gaya wa. In sha Allah abubuwan da su ka faru, kaffarar laifukan ka ne, in sha
Allah sai an tuhumi indabo a kan mutuwar jauhar, muddin sunan sa ya fito a
kotu, to shi ma za mu yi ƙararsa ne, fatana Allah ya bamu nasara" yayi
shiru ya na tunani.
"Vi" ta kira shi a hankali. Ya ɗaga kai ya kalleta
amma bai yi magana ba.
"Ka ce wani abu mana"
"I have nothing to say"
"Idan ka karaya ni fa? Dan Allah ko yaya na ga alamar
ƙwarin gwiwa a tare da kai mana, kar ka saka na karaya mana Please" ya ɗaga
kai ya kalleta ya ce "Duk mai nema, dole ya sanya rai a samu ko rashi, duk
wanda ya riske ni, zan karɓa da murna na gode wa Allah"
"Duk da haka, yakamata bawa ya kyautatawa Allah zato,
burina ɗaya tak ya rage a duniya da nake fatan cika shi, shi ne ƙwato muku
hakkinku, da kai da jauhar, ko da hakan ya na nufin ƙarshen rayuwata.
Ina ta gudanar da bincike na a ɓoye, ina tattara bayanai,
hatta report ɗin likitoci a kan mutuwar ta, ina processing na karɓa. Alhaji
mu'azzam ya na taimaka mini sosai da sosai"
Nan da nan annurin fuskar sa ya ɗauke, rai a ɓace ya ce
"Shi kuma me ya kawo shi cikin wannan maganar?"
"Komai ma mana, ka san abubuwa da yawa ban da taimakon
Allah, ya sanya ya na tare da mu ya na taimaka mana, da tuni an kaimu ƙasa an
ga bayanmu, bawan Allah nan ya cancanci yabo wallahi" banza ya yi mata
yaƙi yi mata magana.
"Ni idan Allah ya sa aka kammala shari'ar nan, lallaɓawa
zan yi na yi aure, su Baba idan za su shirya da major to, idan sun ƙi ina ɗakin
mijina ina yi musu addu'a Allah ya yafe musu ya sanya su gane"
"Amma kin manta mijin 'yar uwakki ne?"
Nabila ta ce "Na sani mana, dama ba jauhar ya fara so
ba? Kuma ai yanzu ba ya tare da hafsan idan ba zai mayar da ita ba ni sai na
aure shi, ko na auri barrister Habib, ko ma duk wanda Allah ya sa ya samu,
Allah ya zaɓa mini mafi alkhairi ya bani wanda zai kula da ni" ta na cikin
maganar ya miƙe ya bar wurin. Tashi ta yi ta bishi, amma har su ka shiga mota
su ka fara tafiya bai kulata ba.
"Vi ka yi haƙuri idan laifi na yi maka mana, ka wani haɗe
rai ka sha kunu kamar boss" gefe ya ci gaba da kallo.
"To ni dai yanzu ba tsoronka nake ji ba duk muzuran da
za ka yi mini, da dai na fi jin tsoronka" ya juyo ya yi mata wani irin
kallo, take ta tsuke bakinta ta ce "Am sorry".
***
Ramma laulayi ya sakata a gaba, ba ta iya cin abinci, komai
ta ci sai amai, duk da ƙasan zuciyar mahaifiyarta babu daɗi ta na tausaya mata,
amma a zahiri yadda rammar ta fifita abin da take so, a kan cin zarafin da aka
yi musu, ya fi komai baƙanta mata rai, da ta tuno hakan sai ta ji ranta ya ƙara
ɓaci.
Alhaji mu'azzam ne ya je gidan, duba su ramma, su ka gaisa.
Ya ce "Hajiya ku yi mini uzuri fa, ayyukan ne da yawa
sosai sai godiyar Allah, kwana biyu ban samu na leƙo ku ba"
Maman ramma ta ce "Wallahi babu komai Alhaji, ai muke
da godiya Ubangiji Allah ya ƙara arziki ya sanya a fi haka"
Ya ce "Amin, mun yi magana da Nabila ta ce babu wata
matsala, amma ya na ga rahaman kamar a cikin damuwa ne?"
"A'a babu komai, kawai dai ba ta jin daɗi ne"
"An je asibiti ne?"
"Eh lafiya lau".
Ya ce "To Alhamdilillah ai Nabila ma ta ce mini ta na
hanya, ina son jin ya ake ciki, zuwa yanzu yakamata ace ai an fara shari'ar,
tuni a tura shi prison" gaban ramma ya faɗi, duk yadda ta so ta takura
zuciyarta ta ji ta tsani Abdul a yanzu kasawa take yi, tausayinsa ya kanannaɗe
mata zuciya baki ɗaya.
Ba a jima ba sai ga Nabila ta iso, Ramma na ganin Nabila ta
ji farinciki ya mamayeta, saboda itakaɗai ce take fahimtar ta, take lallaɓata
ba tare da ta ƙosa ko ta hantareta ba.
Duk su ka gaggaisa, Alhaji mu'azzam ya ce "Barrister ya
ake ciki ne? An ce an ɗauki statement da komai, me ake jira ba a gurfanar da
shi a gaban shari'a ba?"
Nabila ta ce "Eh na je na tuntuɓa, ina ta bibiyar
lamarin shi Abdul ɗin ba shi da lafiya sosai, haryanzu ya na fama, ya na kwance
a asibiti ma, ya na karɓar treatment. Duk ina son na je na duba shi, dan na
tabattar"
"Yakamata, ki je da kanki, kar ayi wata cuwa-cuwar ko
kuma ƙarya yake yi"
"A'a ba ƙarya yake yi ba, ba shi da cikakkiyar lafiya
dama" sai kuma ta yi saurin tsuke bakinta, ganin duk sun waiwayo su na
kallonta, musamman mama da ta galla mata wata uwar harara.
Kankarofi ya ce "Too, ikon Allah me yake damunsa
haka?"
Ta ɗan saci kallon mama, jiki a sanyaye ta ce "Ciwon
ciki ne mai zafi"
Ya ce "To Allah ya bashi lafiya, ayi Shari'ar nan, a
ƙwatar miki hakkinki da ke da mahaifiyarki"
Nabila ta juya harshe zuwa turanci, ta ce "Yallaɓai,
ina tsoron yin shari'ar nan yarinyar nan ta bamu kunya, wallahi ta na son
mijinta, daga ita har shi su na son junansu"
Waro ido ya yi ya kalli Nabila ya ce "Haba dai?"
"Ka ga abin da su ka yi a station kuwa? Ga mutuminka ya
ɗauki zafi a kan lamarin nan, ka san fansa yake so ko ta halin ƙaƙa, a zuciye
yake da su, nayi-nayi ya ƙi fahimta, ka san ba ta da wani tsayayye yanzu idan
ba shi ba, ya kafe ya dage, dan kamar zai daketa, ga ciki kuma na rasa yadda
zan ɓullowa lamarin nan"
Kankarofi ya jinjina kai ya ce "Lallai akwai ƙura, to
dama ni nawa support ne, na yi supporting ɗin ku, financially na baku security,
decision kuma wannan naku ne, Ubangiji Allah ya bayar da sa'a duk abin da ku ka
yanke, ni dai-dai ne a wurina"
Nabila ta ce "Shikenan, hakan ma mu na matuƙar godiya,
Allah ya saka da alkhairi ya sanya a fi haka"
Ya amsa da "Amin Barrister, ai aikinki ya na kyau
Ubangiji ya ƙaro mana irinku a cikin al'umma, kin sake komawa wurin mahaifinki
kuwa, na je masa sau ɗaya, haryanzu ina jin nauyinsa ne abin da nayi".
"Kar ka damu, ai ba mutum ne mai damuwa ba, iyaka idan
ka na buƙatar ya dawo maka da matarka ne shikenan, sai na tayaka biko" ya ɗago
ya kalli Nabila ya yi shiru, sai kuma ya miƙe ya tashi ya yi musu sallama.
Nabila ta ce "Rahama, ki na cin abinci kuwa duk kin
rame"
Maman tayi caraf ta ce "Ina fa za ta ci, ta ɗauki
soyayyar ɗa namiji ta saka a zuciyarta, ba ta tausayina ba ta kallon a masifar
da ya saka mu a ciki wata da watanni ina yawon yadda za ayi na ganta, hankalina
a tashe"
A marairaice ramma ta ce "Mama ya ce nemanki yayi ya
rasa, shiyasa bai dawo da ni ba, saboda za a iya kashe ni, dan a kare shi kuma
wallahi ni ba soyayyarsa na saka a raina ba, a kan me zan so wanda ya keta mini
haddi"
"Rufe mini baki, ko na zaune ki, soyayyata ki ka saka a
ranki ai ko? Tun safe yanzu sha ɗaya na safe, ba ki fito kin nemi abin karya
ba, ki na kwance ki na tunani"
Nabila ta katse hirar da"ba zai yiwu ba, tashi mu je ki
dafa abinci da hannunki, mu fita shan iska, kya samu ki huta ke ma"
Ta saka ramma a gaba, su ka shiga kitchen, ta ce mata ita ba
ta son ko ƙamshin abinci, ita ba za ta iya cin komai ba".
Nabila ta ce "Dubiya za mu je, mijinki ya ce lallai ya
na son ganinki, idan kuma ba kya so shikenan" ai babu shiri ramma ta zage,
ba tare da ta san tayi hakan ba, ta yi girki, zuwa azahar su ka yi salla,
Nabila ta ɗauke ta su ka fice.
Har asibitin da Abdul yake su ka je, jami'an tsaro na ƙofar
wurin a tsaye.
Nabila su ka shiga tare da ramma, ƙirjinta sai dukan uku-uku
yake yi.
Shi da wani su ka tarar da shi, su ka gaisa da mai jinyar
wato Salim wanda abokinsa ne kuma ɗan uwa dan su na da alaƙa, Nabila ta ce
"Lauya ce ni, ko za ka iya bamu wuri for some moment" ya ƙarewa
Nabila kallo, ya ce "Na gane ki ai" daga haka ya tashi ya fice.
Abdul ya na kwance, ya na bacci, ya na sanye da wando
3quater da vest, fuskar nan ta yi fayau saboda ciwo.
Ramma har tsuma take yi, ta na bin sa da ido.
Nabila ta ce "Bari na je waje na jira ku" ta fice
daga ɗakin ita ma.
Kamar jira take Nabila ta fita, ta ƙarasa da hanzari ta saka
hannu ta riƙe hannunsa ɗaya, ɗayan kuma ta ɗan jijjiga shi ta ce "Doctor,
Abdul tashi ni ce" a hankali ya juyo, ya buɗe ido, da sauri ya kalli ɗakin
ya kalleta ya ce "Rahama, ke ce ya aka yi ki ka zo nan?"
"Anty Nabila ce ta kawo ni"
"Wannan lauyar ta ki?" Ta jinjina masa kai alamar
eh.
Abdul ya ce "Ai na ga kamar ta na da tausayi, ba kamar
wannan mai zamanin ba mara imani"
Ramma ta ce "Yayana ne fa, shi kuma yar uwar matarsa
ce, yan biyunta ce"
"Ke ma kin san ba shi da kirki, ko tausayinmu ba ya ji,
am missing you sweetheart" yayi maganar yana janyota jikinsa.
Luf ta kwanta a ƙirjinsa, ta ce "Ya jikin naka?"
"Wallahi ba zan ɓoye miki ba, babu sauƙi, ni kawai a
kaini kotun, idan a can prison ɗin zan mutu shikenan, idan ina da rabon na
rayu, gara ayi a kai ni na fara lissafin shekarun da zan yi"
Cikin rauni ta ɗago ta kalleshi ta ce "Dan Allah ka
daina cewa zaka mutun nan, idan ka tafi binka zan yi, ko bacci ba na iya yi, na
rasa abin da yake yi mini daɗi"
"Dan Allah da gaske rahama? Ki na so na kenan? Wallahi
ciwon nan nawa har da damuwa, hepatic tuberculosis ke damuna, TB ta kama
mini hanta, ikon Allah ne kawai zai saka na rayu, saboda shaye-shayen da na yi
ne na san ya haddasa mini hakan"
Ramma ta ce "Zaka rayu in sha Allah, ka daina irin
wannan maganar, ka na karya mini zuciya" tayi maganar tana hawaye.
Ya tallafi fuskarta, ya ce "Rahama dan Allah kan na
mutu ki ce ki na so na, ko sau ɗaya ne"
"Wai ba zaka daina zancen mutuwar nan ba, wallahi zan
daina zuwa idan za ka din ga wannan maganar"
Ya ce "To na daina"
Ta goge hawayenta ta ce "Ga abinci na kawo maka, ai za
ka ci ko?"
"Ba na iya cin abinci, amma tun da ke ki ka kawo,
dolena na ci ai, your excellency rahama Abdul yasar"
Murmushi ta yi, ta ɗaukko flask, ta zauna a kusa da shi, ta
fara ɗebowa ta na kai wa bakinsa.
Ci yake yi ya na kallonta, ba zai iya misalta abin da yake
ji a kanta ba, na soyayya.
Hannu ya saka ita ma ya na bata, sai su ka so manta halin da
suke ciki.
Ta gama, ta raka shi banɗaki, ya yi alwala, ya dawo ya zauna
ya tayar da salla.
Duk abin nan Nabila na zaune ta na danna waya, ta yi shiru
ta na kallon ƙofar ɗakin, da alama ma sun manta da ita ne a wajen, ta jinjina
kai lallai mata da miji sai Allah.
Ban da Abdul ya na da gata, ya za ayi ma a kawo shi wannan
asibitin jinya, kamar ma ba wanda ake tsare da shi ba.
Nabila na ɗaga kai ta hango babar Abdul na tahowa, tare da
security ɗin ta, hannunsu da fulasai.
Abdul kuwa bayan ta gama ba shi abinci, sai ya marairaice
wai dan Allah ta yi masa wanka, wai da kansa yake yi, baya bari kowa yayi masa,
kuma idan yayi baya fita.
Ya lallaɓata da daɗin baki, ta saɓa hijjabinta, su ka tafi
toilet.
Maman Abdul na zuwa Nabila ta tashi, ta ce "Sannu da
zuwa, bari ayi musu knocking tukuna, ya na da baƙuwa ne" kallon banza ta
yi wa Nabila, kawai ta buɗe ƙofar ɗakin.
Abdul ya na kwance ruf da ciki, ta yi masa wanka, ta na
shafa masa man zafi a bayansa.
Tashi ta yi cikin tashin hankali, ramma ta ja da baya, ta na
zazzaro ido, tare da ƙoƙarin sanya hijjabinta.
"Me zan gani haka, wannan matsiyaciyar yarinyar har
asibiti me ki ke yi a nan, ke wace irin 'yar isaka ce ne?"
Abdul ya ce "Mummy ba 'yar iska ba ce, mata ta ce
fa"
"Rufe mini baki ko na ɗauke ka da mari"
Nabila ta ce "Hajiya, ba ramma ce ta kawo kanta ba, shi
ya nemi ya ganta ta hanyar lauyansa, su ka roƙi alfarma na kawota, amma ba 'yar
iska ba ce"
"Rufe mini baki, banda munafunci, kun haɗa baki a kan
lallai sun kun kassara mini iyali, kun dage sai kun kulle mini ɗa, kuma saboda
iskanci kin kawota ta na yi masa karuwanci, ƴar ƙanƙanuwa da ke kin iya
bariki"
"Mummy dan Allah ki daina aibata mini mata, wane irin
karuwanci fisabilillahi. Ni fa ina buƙatar matata a kusa da ni"
Ta ƙarewa ramma kallo, ciki ne a jikinta ya fara tasawa.
"Me nake gani a jikinta kamar ciki ma? Amma dai ba na
ka bane ko?"
Abdul cikin damuwa ya ce "Dan Allah Mummy ki daina
aibata mini mata, ba dan ni ba, ina son matata, idan laifi ne na yi musu laifi,
dan Allah ki daina aibata mini ita, ina jin zafi sosai" galala ta buɗe
baki ta na kallon Abdul.
Nabila ta ƙarasa ta danƙo hannun Rahama, ta ce "Zo mu
tafi"
Riƙeta Abdul ya yi, ya na yi mata magana ƙasa-ƙasa.
"Na gode sosai da sosai your excellency tun da aka kama
ni, ina cikin baƙin ciki da damuwa, amma na yi farinciki sosai da sosai, na
gode rahama. Allah ya saka da mafificin alkhairi, ki cigaba da yi mana
addu'a"
Jan shi mahaifiyarsa take yi, amma ya yi ƙam da rahama, ya
na yi mata magana a kunne.
Jinjina masa kai kawai take yi, idanunta na cika da hawaye.
Hankaɗe ramma ta yi ta na ce mata munafuka, Nabila ta riƙe
ta, ta kalli maman Abdul ta ce "Ki bi a hankali, wannan zafafa ƙiyayyar ba
naki ba ne ba, rayuwar ɗanki na hannun Allah ta na da alaƙa kuma da Rahama, duk
wannan fusatat da ki ke yi akwai rabo a tsakanin su, gara ki kwantar da murya
ki lallaɓata da iyayenta, dan wannan abun da yake yi a kanta, ba soyayya ce
kawai ba jarrabawa ce".
"Wallahi ƙarya na bi matsiyata yan ƙauye ina roƙonsu,
shi ma asiri su ka yi masa"
Nabila ta ce "Idan ke ba ki bi su ba, shi gashi ya
lalace ai a kan yar ƙauyen"
"Ke ki iya bakinki ko na kifa miki mari, na saka ayi
dukan tsiya"
"Barrister ce ni, tsaf hakan zai saka ke ma a yanka
miki tikitin tafiya in da mijinki da ɗanki ke shirin tafiya".
Ramma kuka kawai take yi, Abdul kuwa ya kasa magana, sam bai
ji haushin abin da aka yi wa mummyn ba, shi matarsa ce kawai damuwarsa.
Nabila su na tafe a hanya, ta ce "Rahama za ki iya yafe
wa Abdul yasar?" Ramma ta kalli Nabila amma ta yi shiru.
"Ki na son mijinki ko?" Still shirun ta yi ta na
wasa da yatsunta.
"Ki gaya mini masalaha nake son a nemo"
"Ba na son shi, kawai tausayi yake bani"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Rahama kenan, menene son
menene tausayin, ki na tsoron abin da zai biyo bayan amsar da zaki bani ne
kawai. Abin da ki ke so dole shi za ayi, idan ki na son mijinki, ki gaya mini a
nema masa sassauci ko ma ki yafe masa, ku yi rayuwar aurenku, na san yadda zan
ji da Mama da Vi"
Ramma dai ta yi shiru, ba ta iya cewa uffan ba.
Tunani ta tsunduma, yadda suka kasance tare yau tare da
Abdul, "Dan Allah rahama kar ki bawa kowa zuciyarki har na fito, zuciyarki
tawa ce nikaɗai"
"Ba zaka yi shiru ba, sai na saka maka sabulun nan a
baki, da kyar ka ke magana sai haki ka ke yi"
Ya marairaice ya ce "Dan Allah ki bar mini
zuciyarki"
"Nawa zaka saya?"
Yayi murmushi ya ce "Ai darajar zuciya, ba a iya
musayarta da komai, sai zuciya 'yar uwatta"
"Ji yadda ka ke magana, kamar a film juya ko na zuba
maka dundu ni"
Ya lumshe ido ya ce "Dundun ƙauna ne" murmushi ne
ya suɓucewa ramma, ba tare da ta shirya ba, Nabila kawai ta kalle ta, ta
girgiza kanta.
A falo su ka tarar da Viper, fuskarsa babu rahama babu
annuri, tuni Ramma ta tsure, Nabila kuwa ta sha jinin jikinta.
Cikin dakewa ta ce "Vi sannu da zuwa, dama zaka biyo
nan ne? Na zata tafiya kawai ka yi"
Miƙewa ya yi tsaye ya ce "Daga ina ku ke?"
"Amm...mm" ganin ta na neman ƙaryar da za ta yi
masa ta kare kanta, ya sanya shi ɗago mata wayarsa.
"Duk in da ki ka je ina gani, kuma na jira Emanuel, ya
gaya mini in da ya kai ku, Me ki ke shirin yi ne, me ki ke shirin aikatawa? Are
you human being, kamar ba mace ba? Idan ita ba ta da hankali ke fa? Dan me za
ki ɗauke ta ki kaita wurin wannan ɗan iskan yaron? Me ki ke shirin aikatawa ne?
Yadda da na yi da ke ya sanya nake jin za ki iya ragamar komai yadda ya dace,
amma na rasa in da ki ka dosa. Ko ke ma kin sauya layi daga in da na sanki, ta
kanki su ka biyo kenan saboda case ɗin ya sha ruwa? Rahama ba za ta taɓa zama
da wannan yaron ba, kuma dole a hukunta shi"
Maman rahama ta ce "A'a Aminu, a bi komai a hankali, ta
na ƙoƙari ai"
Nabila ta kalli ramma ta ce "Jeki abinki rahama, Allah
ya huta gajiya"
Ta kalli Viper ta ce "I so much respect humanity,
yardar da ka bani, yanzu babu ita ka na doubting a kaina, saboda kawai na kai
rahama wurin mijinta. Idonka ya rufe fansa ka ke so ko ta halin ƙaƙa shiyasa ka
ke son sai an hukunta Abdul da laifin da ya yi da wanda ba na sa ba.
Hukuntaka da aka yi da laifin da ba naka ba ya sanya na
tsaya kai da fata, tun ban san ina da alaƙa da kai ba, a kan ƙwato maka
hakkinka. Ko hukunci za ayi, iya laifin da Abdul ya yi kawai za a hukunta shi
da shi.
Ina rashin karɓarka da al'umma su ka ƙi yi a lokacin da ka
ke buƙatar su, shi ne musababbin sake shigarka mawuyacin hali? Da na ƙyamace
ka, ko na gujeka da a wani stage ka ke yanzu? Kar ka manta har yinƙurin kashe
ni ka yi ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba, an nemi rayuwata wuri daban daban
saboda kai, amma hakan bai sanya na haƙura na ƙyaleka ba.
Kar ka manta a yadda ka ke, aka ɗauki auren 'ya aka baka,
shikenan mutum ba zai yi kuskure ya tuba a karɓe shi ba, sai a ɗauki laifin
nasa kawai a saka a gaba.
Zunzurutun kuɗi miliyan nawa ya kashe a garinku, kuɗin da a
sanadinsu, ubansa ya na can ya na fuskantar tuhuma, ya biya kuɗin makarantar
ramma har jami'a, kuɗin rainon cikinta da abin da za ta haifa, hatta kuɗin kula
da al'amuransu na yau da kullum ya bayar, duk dan ya wanke laifin sa,ni da ku
mun san banda ƙaddara rahama ba ta isa zuwa in da Abdul yake ba, son da yake yi
mata jarrabwa ce kawai. Ban da an tsaya mana mu ma, Abdul ya na da gatan
da za a iya sakinsa, kawai dan mun samu manya sun shiga abin ne, amma ya zaɓi a
hukunta shi, muddin rahama za ta yafe masa.
Mama ke ma fa uwa ce, kuma Allah ya taɓa Jarabtar ɗanki da
kauce hanya, ke ki ka zaɓa masa zama hakan? Duk da yanayin abin da ya faru, da
Abdul sakaci da tarbiyyarsa ne, amma za a iya kamanta rahama da jauhar, Annabi
Sallallahu alaihi Wasallam ya ce ka yi sanadin shiriyar mutum ɗaya, ya fi a
baka jajayen raƙuma guda ɗari. Ba mu san me Allah ya ɓoye a lamarin nan ba, ga
juna biyu a tare da ita, ku na nan ta yi masa alƙawarin ya je ya gama prison ya
dawo ta na jiransa. Duk wannan abun fa zai iya yiwuwa wata jarrabawar ce daga
Allah muma yake yi mana, Abdul fa bawansa ne shi ma, kuma ya na kishin abin sa,
ci gaba da jansa dan Allah ya ara mana dama ba zai haifar da ɗa mai ido ba.
Amma ina mai neman afuwar ku, ba ina nufin shari'ar Abdul ta
sha ruwa ba ne, sam sonake ayi tunanin mafita.
Yallaɓai Al'amin, Allah ya baka haƙuri ni babu wanda ya bani
wani cin hanci, ba kuma ƙoƙarin cin amanarka nake yi ba. Zan yi iya yi na Abdul
zai je prison in sha Allah, muddin hakan zai samar muku da nutsuwa" ta
ƙarasa maganar a nutse, ta ja da baya ta fice.
Ramma ta na tsaye ta na ji, gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi,
ta fashe da kuka, ganin yadda ta ja aka ɓatawa Nabila rai.
Sojan da yake ba wa Nabila kariya, ya bi ta ya na yi mata
magana, amma ta share shi, a ranta ta ce "Tsohon munafiki kawai"
Napep ta tara, ta nufi gidan Abba.
Maman ramma na shirin yin magana, Viper ya rigata, ya ce
bari ya tafi.
A ɗaki ta iske ramma, ta yi mata ta tas, ta ce "Ramma
ba kya tausayina, ɗa na ya rasa ransa a banza, a gabanki yaron nan saboda
rashin tarbiyya, ni kaina so yayi da ya haike mini, amma yanzu kin fifita shi a
kaina, na gode rahama"
Tabbas da zuciya za ta yi mata adalci, to da ba ta fara
ƙaunar Abdul ba, amma ita haryanzu ta fi yarda tausayin sa take ji, ya ake so
ta yi da rayuwarta ne.
Viper na fita, sojan ya fara gaya masa tafiya ta yi, ya ce
ya rabu da ita, su tafi kawai.
Da daddare Viper ya din ga kiran wayar Nabila, amma ta ƙi ɗagawa,
hakan ya tabattar masa da ta yi fushi ne.
Gidan major babu wanda ya kulata, babu wanda ta kula sai
baba uwani, ta shirya ta tafi gidansu sumayya, sun daɗe su na tattaunawa, ta na
yi mata nasiha da ba ta ƙwarin gwiwa.
****
Monday morning 9:30a.m
Tsaye take a gefen wani gini, tana ƙarewa harabar kotun
kallo. Yadda aka cika harabar da manya da ƙananan motoci ne, ya sake tabattar
mata da manyan shari'oi za a gudanar a yau.
Ta din ga kallon agogon hannunta, tana kallon gate ɗin
shigowa harabar kotun.
Motar gidan yari ce ta shigo, aka yi parking ɗin ta, sai dai
tsayuwar motar babu daɗewa wata danƙareriyar motar, ta shigo harabar kotun.
A ƙalla an kai mintuna goma da parking ɗin motar, sannan aka
buɗe bayan motar, wata mata ta fito, sanye cikin coat.
Mutanen da ke harabar wurin, suka nufeta, wasu suka karɓi
jakarta, ana ta yi mata fadanci, cikin girmamawa.
"Ya Allah kai ne Allah, kai ne buwayi gagara misali,
Ubangiji da babu wani kafinsa, kuma babu wani a bayansa. Allah na san mutanen
nan sun fi ƙarfina ta ko ina, amma kai ne abun dogarona, na san ba za ka bani
kunya ba. Allah sun fi ƙarfina ka fi mini ƙarfinsu. Allah ka yi mini
kunfayakununka a kan shari'ar nan, hasken gaskiya ya shafe duhun ƙarya, duk da
ina da masu goya mini baya, amma Allah goyon bayanka nake buƙata" ta jima
a tsaye tana karanto addu'a, tare da yi wa Allah kirari.
A hankali ta furta "What a hectic trial, Ubangiji ka
iya mini" cikin nutsuwa, ta fara taka takalminta mai tudu, ta nufi shiga
cikin kotun, da takunta mai kama da na ƙasaita, shigarta ta lawyoyi tayi
matuƙar yi mata kyau, tana tunkarar ƙofar shiga, zuciyarta na tsananta
bugawa,tana fatan Allah ya shiga lamarin ta.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Sannu a hankali ta ke ƙoƙarin shiga cikin kotun,
"Nabila" ta jiyo muryar sumayya a bayanta.
Ta waiwaya, sumayya ta ƙaraso ta ce "Ya aka yi ki ka
riga ni zuwa?"
"Oho miki dai"
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Best of luck my dear,
Allah ya ba da sa'a"
Nabila ta ce "Amin sumayya, amma a tsorace nake, wannan
shi ne trial mafi haɗari da nake tunanin zan fuskanta a rayuwata"
Sumayya ta ce "Haba mutuniyar, tsoro ba naki ba ne ba,
ke jaruma ce i trust you dear, mu je kawai"
Su ka ƙarasa su ka shiga cikin kotun.
Su na nan zaune, Alhaji mu'azzam ya shigo, barrister Habib
ma ya ƙaraso, sai ga murtala, su liti da Walid, cikin mamaki sai ga Nasir ma
duk a cikin kotun daga baya sai ga mai gayya mai aikin shi ma ya iso kotun.
Ƙirjin Nabila na ta bugawa, amma ta tsananta maimaita
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, la haula wala ƙuwwata illa
billah"
Ana ta gabatar da shari'oi, aka kira ƙarar su Nabila.
Tashi ta yi cikin nutsuwa, ta fita gaban shari'a.
Ta tsaya ta gabatar da kanta a da cikakken sunanta, da kuma
wanda take karewa.
Lauyan da yake kare lakwari, ya fito ya gabatar da kansa, da
wanda yake karewa.
Nabila ta nemi a karantowa masu laifi, laifin da ake tuhumar
su da shi, a nan ɗan sanda mai gabatar da ƙara, ya karantowa lakwari laifin da
ake tuhumar sa da shi, da Madaki, duk da madaki ya na gadon asibiti ya na
jinya.
Aka karanto tuhumar da turanci, cewar ana zarginsu da shiga
cikin gidan Aminu Viper, su ka kashe mata da ɗan da kuma ɗan yake cikinta.
Kotu ta waiwayi lakwari domin jin ta bakinsa, bayan an
fassara masa ƙusnhin tuhumar da ake yi masa, cikin harshen hausa.
A nan take lakwari ya musanta zargin, kamar yadda ya musanta
a wurin 'yan sanda, da kuma yadda lauyansa ya jaddada masa kafin zuwan su kotu,
domin kuwa ba ƙaramin kuɗi aka ba wa lauyoyi ba, a kan su yi duk mai yiwuwa ayi
ta jan Shari'ar har ta lalace.
Daga haka kotu ta ɗaga cigaba da shari'ar, zuwa sati biyu
domin bayyanar shaidun kowanne bangare.
Viper daga in da yake zaune, lakwari kawai yake kallo, ko
ƙiftawa ba ya yi, zuciyarsa na raya masa kawai ya kashe shi ya huta, yanzu da
haka za ayi ta jan ƙafa a shari'ar nan a ɗauki dogon lokaci ba a kammalata ba?
Zuciyar sa azalzalarsa kawai take yi, ya na jin tamkar ba zai iya jira ba.
Ya na kallon lakwari, taswirar abin da ya faru a daren da
jauhar ta mutu, na ƙara dawo masa a cikin ƙwaƙwalwarsa, yadda ya kasa kataɓus,
ya na ji ya na kallonta ta na miƙo masa hannu.
Knasa ne ya yi wata irin sarawa, ya tashi cikin hanzari ya
fita daga cikin kotun, gaba ɗaya fuskarsa ta sauya, tsantsar baƙin ciki da ɓacin
rai, haɗi da tashin hankali ya mamaye ilahirin fuskarsa, tuni idanunsa su ka kaɗa
su ka yi jawurrr.
Nabila ta na daga in da take ta bishi da kallo, ta san a
rina, wani irin tausayin sa ya kamata, kamar ta tashi ta bishi, sai kuma ta
tuna fushi take yi da shi, dan haka kawai ta basar.
Walid ne ya tashi ya rufa masa baya, liti ma biyo su yayi.
Walid ya cimma sa cikin hanzari, ya na kiran sunansa.
Bai tsaya ba, Walid ya riƙe rigarsa ta baya, ya juyo ya ture
shi, amma ya sake riƙe shi.
"Mai laya" ya furta muryarsa na rawa.
Walid ya ce "Mai zamani"
"Idan zuwana wurin Shari'ar nan zai din ga fama mini
gyambon da yake cin zuciyata ina ga zan haƙura kawai"
Walid ya ce "Ba zamu haƙura ba, bakin rai bakin fama,
sai in da ƙarfinmu ya ƙare da yardar Allah"
Wata baranda Viper ya samu, ya zauna, ya miƙe ƙafafuwan sa,
ya na jin yadda kansa yake ci ga ba da sarawa bugun zuciyar sa na ƙaruwa.
Liti ya zauna a kusa da shi, ya dafa kafaɗarsa ya ce
"Haba maza, zuwa yanzu yakamata ace fa ka saba da jurewa, ka yi
haƙuri"
Viper ya kalli liti ya ce "A ganinka ragwancina ya yi
yawa ko? Ba ka san me nake ji ba, yau da jauhar mutuwa kawai tayi Allah ya karɓi
rayuwarta, zan yi mata addu'a na haƙura na dangana, sai dai zan rayu da begenta
a raina. Abdullahi a kan idona fa aka kasheta, ban iya aikata komai ba, a kan
cikinta na watanni tara ta faɗi, ta na kiran sunana, ba ta ji ba ba ta gani ba
fa" Viper ya yi maganar cikin ƙunar rai, ya na sauke numfashi.
"Mun sani mai zamani, amma ka ƙarfafi gwkwarka, ko ita
ma ta samu ta yi abin da ya dace".
Ya sauke numfashi ya ce "Wannan karon, muddin aka kuma
yi mini abin da aka yi mini a baya, zan ɗauki matakin da nake ganin ya
dace"
Nabila su ka fito tare da Sumayya, Sumayya cikin damuwa ta
ce "To a haka za ayi shari'ar, yau ai ba a yi komai ba"
"Ba a yi wa shari'a gaggawa, mace ce mai ciki ba a san
me za ta haifa ba, a sannu a ke bi, ba aikin jarida ba ne ba, jakadun yaɗa
gulama kwando kwando"
Duka wasa sumayya ta kai mata, a lokacin da barrister Habib
ya fito, tare da Alhaji mu'zzam su na magana.
Viper ya na cikin mota, ya na jiran Nabila su tafi, kawai ta
shiga motar barrister Habib, tare da Sumayya.
Bai ce uffan ba, ya yi umarnin a ja motar su tafi.
Gidan da su ramma su ke, su ka je, Nabila ta ɗauki ramma ta
ce za ta fara zuwa awo, maman ramma na matuƙar jin nauyin Nabila, dan haka ta
ƙyaleta da ita.
Hatta likitan da zai yi mata awon, Abdul ne ya gaya musu
wanda zai yi mata, dan kar a cutar da ita. Asibitin abokinsa ne, su na ta hira
da sumaya, ramma ko uffan ba ta iya cewa, hankalinta kacokan ya na kan ya jikin
Abdul, dan baban fatanta bai wuce yau ma Nabila ta kaita wurinsa ba.
Su na shiga wurin likitan, ta ga ya zuba mata ido, ko
ƙiftawa ba ya yi.
Nabila haushi ya kamata, ta ce "Lafiya kuwa?"
Ya ce "Ahh lafiya ƙalau, wani cikin ki ka samu
kenan?"
"Ban gane ba, matar abokin ka mu ka kawo, Abdul yasar
da ya ce kai za ka yi mata awo"
Ya ce "Ok Allah sarki, Abdul yasar, ai ya haɗu da
larura shi ma, gashi wai ba a zuwa dubiyarsa, ai mun yi mamaki yadda aka yi ya
yi aure babu labari" yayi maganar cikin kame-kame ya na kallon Nabila.
Ganin ta haɗe rai, ya sanya ya ce "Wacece matar ta sa a
cikin ku?" Yayi maganar yana kallon ta ita da sumayya.
Nabila ta nuna masa ramma, ya waro ido, Ganin ƙaramar
yarinya, bai matsa da tambaya ba, ya ɗauki details ɗin ramma, ya tura su
gwaje-gwaje.
Bayan sun dawo ya dudduba ya ce "Ya aka yi matar likita
take fama da ƙarancin jini har haka, kuma ga shi ta ce ba ta iya bacci, menene
yake damunta haka?"
Ya tattara hankali a kanta ya ce "Menene yake damunki
ba kya iya bacci? Ko dan doctor ba shi da lafiya ne? Ki yi haƙuri zai warware,
in sha Allah. Amma dan Allah ki din ga cin abinci yadda yakamata, ki sha
magungunan ki, dan kanki ya daina ciwo, kuma ki din ga isashshen bacci, idan ba
haka ba, jininki zai hau ki yi jijjiga ƙwaƙwalwarki ta taɓu"
Ramma ta jinjina masa kai, yayi counseling ɗin ta sosai, Su
ka yi masa godiya, har sun miƙe, ya ce "Baiwar Allah dan Allah yi haƙuri,
wai ba Zahra ba ce ba matar Al'amin, da yake ce miki 'yar madara? An ce ya
kashe ki, ranar da ku ka zo nan, na ce washegari za ayi inducing ɗinki, kuma
yanzu na ganki a raye"
Nabila ta yi masa wani marayan murmushi ta ce "Ba ni ba
ce ba"
"Yaya za ki ce mini ba ke ba ce ba? Ki na ce master fa,
ya na ce miki 'yar madara. Idan za ku zo awo, har da abokansa, wani Walid da
wanenen na manta sunan su, ranar har ki ke cewa ya goya ki ba zaki iya tafiya
ba kin gaji. Na yi miki scanic ya ce na gaya masa da wa ɗan yake kama ke ko
shi? Baki gane ni ba, doctor muktar ne fa. A tsohon asibitina fa na gadon ƙaya
da ku ke zuwa".
Nabila ta yi murmushi, hawayen idanunta ya gangaro. Ta ce
"Ka taɓa ganin wanda ya mutu ya dawo? Twin sister na ce, ba ni ba ce
ba" sai kuma ya yi shiru ya na kallonta, ya ce "Ikon Allah, Amma ban
taɓa ganin identical twins da kamaninsu ya ɓaci fiye da kima ba kamar ku, amma
ban taɓa sanin ta na da twin sister ba, mu na hira da su sosai. Duk da mijinta
ba shi da fara'a, amma muddin yaga na ba ta kulawa ta musamman sai ya saki jiki
da ni ya yi ta mutunta mini.
Haryanzu ina mamakin yadda aka yi ya kashe ta duk da irin
soyyayar nan da yake yi mata, kamar ya haɗiyeta.
Ga ta da sanyin hali, komai ta ce master yarinya mai haƙuri
da girmama mutane"
Nabila ta katse shi, ta hanyar cewa "Bari mu je doctor,
mun gode sosai da sosai".
Sai dai su na fita, ta saka musu kuka, Sumayya ta ce
"Haba Nabila menene haka? Ya da kuka kuma"
"Wallahi sumayya duk lokacin da na tuna ban taɓa ganin
jauhar ba, wallahi sabon baƙin ciki nake shiga, sai dai ina jin daɗin duk wanda
na haɗu da shi, halinta na kirki yake gaya mini"
Ramma ta ce "Ki yi haƙuri ki daina kuka, mu yi mata
addu'a, mama na yawan gaya mini, lokacin yaya Nura ya na da rai, kullum ya je
sai ya bata labarinta, har ta na ce masa ya samo mata, za ta saka Yaya Aminu ya
yi masa aure. Ana faɗar kyawawan halayenta, kamar dai yadda ki ke kema"
Duk da kuka Nabila take yi ta ce "Haba, dan Allah nima
ina da kirki rahama? Za a iya faɗar alkhairina idan bana raye nima, ba za a din
ga cewa masifaffiya ce ni ba?"
Ramma ta jinjina kai ta ce "Ki na da kirki sosai Anty
Nabila, daga ke har Anty sumayya"
"Viper fa?" Shiru ramma ta yi ta na kallonta.
A tare Nabila da sumayya suka hau dariya, Ramma ma ta ɗan
biye musu ta murmusa.
Nabila ta ce "Kar ki ƙullace shi, shi ma mutumin kirki
ne, zuma ne kawai sai da wuta, ki yi ta banka masa addu'a, zamu shawo kansa in
sha Allah.
***
Viper ya na kwance ya na ta juyi a kan katifa, ba kalar
rarrashi da ban bakin da su Walid ba su yi masa ba, amma yayi shiru bai kula su
ba. Ga wani malulun takaici da ya ƙule shi, Tun bayan da ya shiga iftila'in
rashin Jauhar, babu wanda yake jin rarrashin sa ya na ratsa shi, kamar Nabila,
gashi saboda wulaƙanci, ta na kallonsa, ya na kallonta, amma tayi banza da shi,
ta hau motar da ake fita da ita saboda tsaron lafiyarta amma ta yi burus, duk
da ta na kallonsa a ciki, kuma ta san ita suke jira.
Jin takaici ya cika masa zuciya, ya sanya ya tashi ya kunna
sigari, ya koma gefe ya na ta busa hayaƙi a nutse, sai dai sam ya kasa samun
sassauci a ransa.
Ya lumshe idanunsa, ya na hango jauhar.
Ta kalle shi, yadda ya zuba mata ido, ta na yi wa wani
mayafi aikin bead.
"Mazajena ya aka yi ne?"
Guntun tsaki ya ja ya na daga kan doguwar kujera ya ce
"Gaskiya na gaji, haba ke baki san me nake ji ba ne ba, wallahi kara uku
na sigari ɗaya safe ɗaya rana da dare kamar wani magani, gaskiya yayi mini kaɗan,
gaba ɗaya kin takura mini rayuwa kin hanani sukuni haka ake yi, ba sai ki bari
na je na sha a waje ba, idan ma ba kya so na sha a gabanki ne ba" yayi
maganar yana jin haushin kansa, yadda ta kirshe shi a gida, kamar wani ɗan ta
wai ba zai fita ba, hadda ƙayyade masa iya adadin abin da zai sha"
Murmushi ta sakar masa, duk da faɗa yake yi, gashi dai ba ɗaure
shi ta yi ba, amma ya na zaune ya na masifa, saboda ya san ya na fita ranar ba
tausa ba hira, ba zata saurare shi ba sai ta wana shi.
Ta ƙarasa gaban kujerar ta na masa murmushi, ta na kallon
yadda ya wani maze ya na kumbura, ba kuma iya rashin shan sigarin ne ya sanya
yake ta faɗa babu gaira babu dalili ba, period take yi shi ne abin da ya ƙara
sanya shi faɗan, yake cika ya na batsewa.
Ta shafi sumarsa ta na murmushi ta ce "Manya gatan
wasa, tuba nake yi, kaina bisa wuyana, ban yi hakan dan takura walwalarka da
nishaɗinka ba, lafiyarka nake yi wa. Ayi mini afuwa a daure a lallaɓa da kara
ukun nan, zan soya maka wainar fulawa mai ɗan karen daɗi, fanka kuwa sai ka
kasheta dan kanka, panel ɗin ya samu isasshen hasken rana, ba zaka kwana cikin
zafi ba, za ka samu wadatacciyar iska, a maimakon sigarinka da na hanaka, ai ka
na so ko?" Tunstirewa ya yi dariya ba tare da ya shirya ba, ya janyota jikinsa
ya ce "Wai ke mai wayo ko?"
Ita ma dariyar ta yi ta ce "Ai na san ba faɗan sigarin
kawai ka ke yi ba, tari idan ka yi master na san me ka ke nufi"
"Aishikenan, ɗaukko abin mayafin da na tayaki, ko kuma
wani abun zan yi miki"
Ta ce "Inyee duk murnar fankar ce za a tayani aikin
bead ɗin da ake watsar mini"
Ya ce "To kin yi wa kanki, na fasa tayakin"
"Bakomai zauna ka ci gaba da kallona, hakan ma ya
wadatar da ni ɗan aljanna na"
Murmushi ne ya suɓuce wa Viper, lokaci guda ya na haɗiye
hawayen da suke ƙoƙarin zubo masa.
Ya saki sauran sigarin hannunsa, ya na sauke numfashi a
hankali.
"Allah ban san dalilin da ya sanya ka karɓi jauhar, ka
shigo da Nabila rayuwata ba, amma duk abin da ka yi dai-dai ne. Astagfirullah
wa atubuilaihi Allah ya yi miki rahama ya sada ki da annabin rahama
matata"
***
Gidan su Nabila kuwa tun da Nabila ta zo, aka yi wannan
fashe-fashen, tonon sililin, gidan ya ƙara rikicewa, Zakiyya kamar ta tsine wa
Hafsa faɗar abubuwan nan da ta yi. Faɗa da tashin hankali ya ƙara kacame wa a
gidan, Baba kuma ya ƙaurace musu gaba ɗaya, ya daina shiga shirginsu, ya daina
cin abincin su, ya din ga kaɗaice kansa daga shiga cikin su.
Wata irin sabuwar damuwa ta addabe shi, dana sani ta aure
shi, ya din ga jin tamkar ya mayar da hannun agogo baya ya gyara wasu abubuwan
da su ka shuɗe. Gaba ɗaya nauyin Nabila yake ji, gashi tun da ta tafi, ba ta
sake waiwayarsa ba, gashi ya na matuƙar son ganinta, amma babu hali dan
nauyinta yake ji, dan a zatonsa fushi ma take yi da shi. Gashi kamar yadda ta
faɗa lallai akwai buƙatar samun daidaito a tsakaninsa da major.
***
Nabila ta gaji da yawa, kai tsaye gidan major ta wuce, ta
saka mukulli ta buɗe ɗakinta, babu wanda ya kulata sai baba magajiya, tare su
ka yi ta hirarsu, ta na ba ta labarin yadda shari'a ta kasance a falo.
Mama sai hararta take yi, tamkar idanunta, za su faɗi Nabila
ko a jikinta.
Unexpected Nasir ya shigo ya tarar da ita a falo, duk ta
rame sosai da sosai.
Kamar ya shareta ya wuce, sai kuma ya kasa, ya ce "Ashe
an fara shari'ar?"
Kamar ba za ta yi magana ba, sai kuma ta numfasa ta ce
"Ai ba ashe ba ne DSP, tin da ka halarci shari'ar kai ma"
Ya yi murmushi ya ce "Haka ne, to ayi dai mu gani"
"In sha Allah za ku ga alkhairi, muddin da jinin major
Yusuf maitama a jikina, zan ci gaba da tsayawa a kan gaskiya, kuma zan yi
nasara in sha Allah" ya kalleta ta basar ba ta kuma magana ba.
Nabila na ta son ta kira Viper, ta ji yaya yake, kuma ta
bashi labarin likitan nan, amma ta basar da ta tuna da maganganun da ya caɓa
mata.
Washegari da wuri ya tafi gidan madam Halima ya na muzurai,
a zatonsa Nabila ta na can, amma madam ta ce "Ba ta dawo ba fa tun jiya,
Nabila ta na wasa da rayuwarta, ba ta san a iya haɗarin da take ciki ba, an ba
ta security amma abin da ta ga dama take yi"
Viper ya gyaɗa kai ya ce "Zan yi mata magana"
Ya duba wayarsa, ya duba location ɗin ta, ya ga ta na gidan
Major.
Nabila kuwa da safe da ta shirya, ta je ta samu Abba ta
gaishe shi, ya amsa mata sama-sama ta tashi ta fita.
Ƙarfe sha ɗaya na safe, ta na asibitin da Abdul yake kwance.
Cikin sa'a mahaifiyarsa ta na nan, ta na ganin Nabila ta
tsuke fuska, ta na tambayarta uban me ya kawo ta.
Abdul ya ce "Mummy ki tsaya mu je menene mana?"
"Ba za a ji ɗin ba, uban me za ta zo da shi na alkhairi
wannan"
Nabila ta numfasa ta ce "Magana ce mai muhimmanci na zo
zan yi da kai"
Ya kalli Mummy ya ce "Dan Allah ki yi haƙuri, ki bari
mu yi maganar nan, bamu san ta zo da shi ba" tashi ta yi ta fice ta na
tsaki.
Nabila ta ja kujera ta zauna, ta kalleshi ta ce "Ya
jiki kuma?"
Ya amsa da "Alhamdilillah"
"Na biya wurin likita, ya ce ana samun improvement a
ciwon naka, yanzu kuma damuwa ce ka saka a ranka tayi maka yawa. Ɓangaren
rahama ma, na kaita awo wurin likitan da ka ce, a kaita"
Cikin sauri ya ce "Komai lafiya ko?"
"Ba na ce ba, tun da ta yi complain da cewar ba ta iya
bacci, ga ciwon kai, jininta ya yi ƙasa saboda ba ta cin abinci"
Cikin damuwa ya ce "To meyasa?"
Nabila ta ce "Abu ɗaya ke damunku kai da ita, sai dai
kafin mu zo nan, mu fara tattaunawa a kan tubalin dalilan matsalolin da suka yi
wa muradinku ƙawanya.
Zan fara da yi maka tambayoyi ka bani amsa, ta haka ne kawai
za mu kamo bakin zaren. Zamu yi magana ne a matsayin mutum da mutum, ba wai a
matsayin lauya da mai laifi ba"
Ya jinjina kai ya ce "Ina jinki"
"Na san ka na cike da jin takaicin yadda Viper ya ƙara
dagewa kai da fata, a kan lallai a hukuntaka, amma ka san Viper kafin
yanzu?"
Ya gyaɗa kai ya ce "Na san shi, yaron mahaifina
ne"
Nabila ta ce "Wane irin aiki yake yi masa?"
Ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Abin da ya shafi harkar
daba ne"
Ta ce "Good, meyasa kai ba ka yi masa, duk da na san ka
fi Viper morar mahaifinka, kai ya kai ka waje ka yi karatu shi kuma ya bashi
ƙwaya da makami, ya bar shi a sake a cikin al'umma?
Ko kuma shi ba shi da ƙwaƙwalwar dai idan an biya masa kuɗin
karatu, ba zai iya ba?"
Abdul ya yi shiru.
"Mahaifinka ya yi wa Viper laifukan da su su ka zama
kanwa uwar gamin ruruta wutar ƙiyayyar da yake yi wa mahaifinka ce ta gangaro
zuwa kanka.
Na san ka san meyafaru da Nura guduma zuwa yanzu, duk da ba
abu ne mai daɗin da zan ta nanata shi ba, hakazalika ban sani ba ko ka san abin
da mahaifinka ya yi wa Viper. A kan case ɗin Nura ya aika a kashe Viper, amma
aka ɓuge da kashe matarsa, wadda take twin sister ɗina, kuma aka rufe shi
shekara biyar da zargin shi ne ya kasheta" cikin tashin hankali da mamaki
yake bin Nabila da kallo.
"Ta yaya ka ke tunanin Viper zai iya yafe wannan
tozarci da aka yi masa, Ramma ƙanwace a wurinsa, ya na da dangantaka da ita ta ɓangaren
uwa, shikaɗai ne yake tsaye a kansu, yake taimaka musu. Ya na ɗora alhakin
mutuwar Nura a kansa, dan haka ya na jin dole yayi duk mai yiwuwa ya yi
supporting ɗin su.
Ni ya damƙawa ragamar shari'ar rahama, kamar yadda ragamar
ta sa shari'ar ma take hannuna. Da zafina har cikin zuciyata nake son na ga an
hukuntaka, saboda abin da ka aikata ya tsaye mini. Ga rape, ga tozarta uwar
yarinya, ka sace mata 'ya, ka yi amfani da dukiya wurin aurenta ta ƙarfin
tsiya. Aka kama wani daban aka ɗora masa laifin, ƙarshe ma aka kashe shi, duk
dan a kare ka. Banda waccan azzalumar matar mai rufe kura da fatar akuya da
take zaluntar mutane, Naja bunkure wadda na yi wa kaina alƙawarin tona mata
asiri. Sai dai abin da na gani ya bani mamaki, daga gareka da kuma rahama, na
bibiyi wasu abubuwan da su ka faru babu saka hannunka.
Amma dagiyar da muke yi, kowa da gaskiyar sa, twins sister
na ban taɓa ganinta ba, duk da wani labari ne daban, amma ko ba komai, na shigo
cikin labarin nima.
Yanzu abin da nake so da kai, gaskiya ni na karaya, ka
tattauna da lauyoyinka, mu yi zama na musamman a kai mu shari'a law, saboda ka
samu sassauci ko yaya a hukunta ka dai hankalinsu ya kwanta, ina tunanin
makomar Rahama da abin da yake cikinta, they really need you. Ka cire girman
kai da duk wani abu, ka roƙi alfarmar Viper da mahaifiyar rahama, ita dan ta
rahama a ƙyaleka ba sai an hukuntaka ba. Ta na ta yi mini magiyar a sassauta
maka.
Amma ya ka gani"
Abdul ya ɗan yi shiru, ƙarshen ƙasƙanci dai ace ya durƙusawa
Viper, yaron mahaifinsa da ba sa ga maciji ƙasƙantaccen ɗan daba, amma ba shi
da wani zaɓi sama da hakan.
Ya numfasa ya ce "Na amince da hakan"
Ta ce "To Alhamdilillah, ba amincewarka ba kawai, ka
tattauna da lauyoyinka. Ni kuma zan san yadda zan shawo kansa, a yi zaman
tattaunawar ka san murɗaɗen mutum ne, da ba ya sarrafuwa cikin sauƙi, amma dai
ka yi shawara"
Ya amsa da "Shikenan, na gode sosai da sosai, da
ƙoƙarin da ki ke yi mana, dan Allah ki gaida mini da rahama, ki ce na ce dan
Allah ta kula mini da lafiyar su, ta daure ta din ga cin abinci "
Nabila ta yi murmushi ta ce "In sha Allah"
***
Aka shafe sati guda, Nabila da Viper ba su haɗu ba, ta koma
gidan major ta yi zamanta, mutanen gidan babu mai iya tanka mata.
Viper ya sha mamakin yadda Nabila ta watsar da shi gaba ɗaya,
idan ya ɗaga waya kamar ya kirata sai ya fasa ya ga kamar ya faɗo. Ita kanta
daurewa kawai take yi, ba ƙaramin azalzalarta zuciyarta take yi, a kan ta kira
Viper ba, ko ta je in da yake ba, amma ta dake.
Lauyan Abdul ya kira Nabila a waya, ya sanar mata da sun
amince ayi zaman sulhun.
Nabila ta na zaune a office ɗin ta, ta na tunanin yadda za
ta shawo kan Viper a kan lamarin ramma.
Ta cire kayan jacket ɗin ta, daga ita sak dogon wando da
shirt, ta ɗora ƙafafuwanta a kan tebur, ta ajiye popcorn a wata container, ta
na ci kaɗan kaɗan ta na tunani.
Buɗe ƙofar ya yi ya shigo, tare da yin sallama ƙasa-ƙasa.
Ita ma a cikin ta amsa masa, ta ɗauke idanunta daga kansa,
ta maze.
Har ya ƙarasa gaban teburinta, ba ta motsa ba.
Ya daddaki teburin, ta ɗago, ya kalli ƙafafuwanta ya
kalleta.
So ta yi tayi burus da shi, sai dai ya yi mata kwarjini, ta
sauke ƙafafuwanta, ta na yamutsa fuska.
Ya matso kanta ya tsaya, ya yi gyaran murya ya ce "Kin
koma asibiti wurin yaron indabo, me ki ka je yi? Next week idan Allah ya kaimu
cigaban shari'ata, ya ake ciki?"
Ta kalleshi ta ce "Ya ka ke bibiyata kamar wata ɓarauniya
ne? Na je wurin Abdul, za mu sake zama da su na musamman, kafin mu shiga kotu.
Shri'arka kuma normal ne, ban karɓi cin hanci daga wurin kowa ba, na tanadi duk
abin da yakamata".
Sarai ya gane magana take gaya masa, da take nuni da abin da
ya sanya ta fushi, amma ya basar ya ce "Zaman me kuma za a kuma yi a kan
shari'ar ta, ba kotu kawai za a kai mu ba, me ake jira ko wani abin dai ki ke
kuma shiryawa ban sani ba. Sannan ki na kasada da rayuwarki yadda ki ka ga
dama, ba ki san ta ina za a iya kawo miki hari ba amma ki na yawo yadda ku ka
ga dama a gari"
Tashi ta yi tsaye ta ce "Allah zai kare ni, ramma kuma
idan ka na kokwanto a kai na, ka canza mata lauya, ka daina zargina babu
dalili, ka na yi mini masifa" tayi maganar ta na nufar hanyar fita.
Kamar ya riƙo kyanwa, ya janyo ta ta baya, ta dawo gabansa
su na fuskantar juna.
Hakan ya bata damar shaƙar warin sigarin da yake yi, wanda
daga nesa ba aji, saboda turaren da ya saka.
Ya ɗago mata jacket ɗin ta, da take shirin fita babu ita, ya
na ci gaba da tsareta da idanunsa.
Da idonsa kawai ta gane meyake nufi, amma in da yake kallo a
jikin nata ya ƙara razanata, jikinta ya hau rawa.
Ya ɗora mata rigar a kafaɗarta, ya ja da baya, wata irin
kunya ta mamayeta, dan kai tsaye ƙirjinta ya zuba wa ido.
Da ƙyar ta aro jarumtar da ta ce "Vi wiwi ka sha
ko?"
Ya waiwayo ya tsura mata ido, ta ɗauke kanta ta ce "Kar
ka mayar mana da aiki baya"
Ta yi maganar ta na ƙoƙarin buɗe ƙofar office ɗin ta fita
hannunta riƙe da rigar.
"Idan ki ka fita ba ki rufe jikinki ba, ranki zai yi
mummunan ɓaci".
Ta waiwayo ta ce "Malam know your limit, ka daina ba ni
umarni yadda ka ke so" tayi maganar tana hararsa.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Ba ƙaramin haushi ne ya kama Viper ba, ba fitsarar da Nabila
ta yi masa ce ta baƙanta masa rai ba, yadda ya kasa sarrafa kansa, har ya
shagala da kallon abin da ba halalinsa ba ne ya fi komai ɓata masa rai.
Sai dai wani irin matsanancin kishi ya taso mata, ganin da
gaske a hakan ta fita, bin hanyar ya yi ya fita, ya tarar da ita a reception ta
saka rigar, su na magana da Barrister Habib.
Barrister Habib ya na ganinsa ya yi murmushi ya ce "Yau
ziyara ka kawo mana, barka da wannan lokaci" yayi maganar yana miƙa masa
hannu.
Nabila ba ta saka ran zai kula Barrister Habib ba, amma ta
ga ya miƙa masa hannu, su ka gaisa Viper ya bi hanyar fita ya fice.
Nabila kuwa murmushi ta yi, ganin yadda ta kunna shi, ko ba
komai ita ma ta rama.
****
Alhaji mu'azzam tun da ya sake haɗuwa da hafsa bayan rabuwar
su, kawai ya ji ya na matuƙar jin tausayinta, har ga Allah ya na son Nabila ma,
sai dai ya san Viper ba zai taɓa barin sa ya aureta ba, ko da zai samu aurenta
sai an kai ruwa rana, amma matuƙa tausayin hafsa yake ji.
Ya na ta bibiyar unguwar ko zai samu ya ganta.
Ranar da ya sake zuwa wurin Baba kuwa, Allah ya taimake shi,
ya ganta ta dawo daga islamiyya, dan kuwa islamiyya ta koma, idan ta je
makaranta ta na samun sassauci daga damuwar da take damunta.
"Baba na dawo"
"Sannu da zuwa" Baba yayi maganar ya na kallonta.
Ta saka kai za ta wuce, duk da yadda Alhaji mu'azzam yake ta
kallonta.
Baba ya ce "Hafsatu ba ki ganni da baƙo ba ne?"
"Na ganshi"
"To ba zaki gaishe shi ba?"
Ta kalleshi ta zumɓura baki ta ce "Ina kwana?"
Baba ya ce "Kwana kuma da yammacin nan?"
Alhaji mu'azzam ya ce "Hakan ma na gode, lafiya ƙalau
ya makaranta?" Ba ta amsa ba ta shiga cikin gidan.
Ya na so ya yi wa baba maganar hafsa, mussaman da ya samu
labarin, ta samu matsalar ƙwaƙwalwa, amma ya kasa.
Bayan baba ya shiga gida ya hau ta da faɗan abin da ta yi
kawai ta fashe masa da kuka ta ce "Baba ni ko son ganinsa ba na yi ne,
amma ai na gaishe shi, ni na tsane shi ne"
Baba ya waro ido ya ce "Hafsatu, ba a cewa an tsani
mutum, ko ba komai auratayya ta taɓa haɗaku, ba ki san mai zai faru gaba ba, ki
daina haka"
But Zakiyya ta fito ta ce "Baban saifu, Alhaji mu'azzam
ɗin ne ya zo, ko bikonta ya zo yi?"
Hararta Baba ya yi, kawai ya wuce turakarsa, daga ita har
Babbar su saifu ya watsar da su, ko turakarsa su ka je korarsu yake yi.
Da yaransa kawai yake harkokinsa, shi ma kuma ba dukkansu
ba, saifu ne sai Hafsa, mussaman hafsa da yake jin tausayinta.
Zakiyya ta saka Hafsa a ɗaki, a kan yadda za su lallaɓa a
sasanta ta koma gidan Alhaji mu'azzam, A take ta ce Allah kar ta ko shi ne
autan maza ba za ta koma gidansa ba, ita yanzu islamiyya za ta yi ta zuwa, ta
zama malama ta din ga yi wa addini hidima har ta mutu.
"Wallahi baki isa ba hafsa, ka ji baƙar muguwar
yarinya, yi wa addinin hidima ba sai ki yi a ɗakin mijinki ba, wallahi sai kin
koma, ba zaki yi mini baƙin ciki ba"
"Wallahi ba zan koma na ci gaba da zaman boranci ba, ai
tun farko dama ba so na yake yi ba, ki ka saka dole ya aure ni, wallahi ba zan
koma ba"
Zakiyya ta rasa yadda za ta yi da ranta, ta shirya ta tafi
gidan su Viper, wurin ƙawar cin mushenta rahila, dan lambar wayarta ba ya
shiga, rabonta da ita, tun ta na Asibiti bayan Abba ya daketa.
Sai dai ta tarar da ita cikin damuwa da tashin hankali ita
ma, shahida ta kashe aure, Amira an sake gwaji babu HIV sai ciki, ta zubar da
cikin ta gudu, ga Abbu ya kori Abba daga gidansa, Naziru kuwa tun da ya tafi
kudu ba ta sake ganinsa ba, sai labari da aka kawo mata ya zama riƙaƙƙen ɗan
iska a kudun.
"Rahila yanzu ina zamu saka ranmu, maigidanmu fa duk ya
yi watsi da mu, yanzu ya gano ɗaya yar ta sa hankalinsa ya na kanta, soyake ya
lallaɓa ta dawo hannunsa, gashi daga gani ba ta da kunya. Ba na son Alhaji
mu'azzam ya san da ita ya ce ita ma so yake yi, hafsa ta kasa komawa ɗakinta,
ta ɓangaren ki babu wani zazzafan malamin ne?"
"Zakiyya da alama ruwa ya ƙare wa ɗan kada. Dan yanzu
asirin ba cin mazajen yake yi ba, har su ma yaran. Gaba ɗaya yarana sun ɗaiɗai
ce sun tsiyace babu wani mai ɗan dama-dama sai shahida, Abba ya ɓaci da
shaye-shaye tuburan"
Zakiyya ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
wannan shaye-shayen ya zama bala'i. Ni fa da depression da shaye-shayen ne su
ka haɗu su ka saka hafsa hauka" nan su ka ci gaba da jajanta wa juna.
***
Da daddare Nabila na shirin kwanciyar, take kallon wayarta,
ji take yi tamkar ta kira Viper, dan ta san ta gama ƙular da shi, amma ta dake
taƙi kiransa.
Washegari da safe ta tura masa message da "Mu haɗu a
CID da ƙarfe goma, saura ka ƙi zuwa, wani abin ya biyo baya ka ce an bani cin
hanci"
Jujjuya wayarsa ya din ga yi ya na kallon saƙon nata.
Gaba ɗaya su ka haɗu kusan lokaci guda, daga ita har Viper
kamar ba su san juna ba, sai basar da juna suke yi.
Babar Abdul sai cika take ta na batsewa, kamar ita aka yi wa
laifi, ta na kallon ramma da take ta rufe cikinta kallon banza.
Abdul kuwa satar kallon matarsa yake yi, kallo ɗaya ya yi
mata ya tabattar da maganar Nabila na ƙarancin jini da kuma damuwa a tattare da
Rahama, gashi duk ta rame ga pimples ƙanana sun feso mata saboda ciki.
Tausayinta da ƙaunarta su ka mamaye shi, ya ji ina ma su na
tare, ya ciyar da ita da ingantattun abinci masu gina jiki, da kulawa ta
musamman.
Ɗaya daga cikin lauyoyin Abdul ya sake gabatar da kansa
sannan ya ce "Mu na godiya da amincewa da ku ka yi ku sake zama da mu,
domin a duba a ga abin da zai yiwu na mafita da kuma masalaha a kan wannan
case".
Mahaifiyar Abdul ta ce "Go direct to the point. Su faɗi
ko nawa su ke so, idan ma kuɗin da ya ba su bai ishe su ba, zamu ba su kuɗi, su
ƙyale mini ɗa a nema masa lafiya. Dan na gaji da wannan sintirin ba yau babu
gobe ana wulaƙanta ni da ni da yarona saboda wata ba ƙauyuyiyar yarinyar"
Cikin ƙunar rai babar ramma ta ce "Uwa uwa ce, babu
banbanci tsakanin abin da ki ke ji a kan ɗanki da wanda nake ji a kan 'ya ta.
Da mazajenku sun sauke hakkin da Allah ya ɗora musu na
al'umma, mussaman na karakara da babu yadda za ayi yaranmu su fito birni
aikatau dan nema mana abin da zamu rufa wa kanmu asiri, balle yaranku marasa
kirki da tarbiyya su keta musu haddi. Da sai dai can su haɗu da watsatsu irin
su su lalace, ba dai da yaranmu ba.
Ba komai kuɗi zai iya saya ba, an riga an cuceni, ko a
hukunta ɗanki ko ba a hukunta ɗanki ba, ya riga ya cuce ni, ubansa ya kashe
mini ɗa, ɗanki ya keta wa ya ta haddi, ya dawo ya nemi nima ya keta mini haddi,
ya jaddada mini shi ya yi wa 'ya ta fyaɗe na yi abin da zan yi ya ɗauke ta ya
tafi da ita. Ubansa kuma ya ci gaba da bibiyar mu da yinƙurin sakawa a kashe
ni, dan na nemi hakkin 'ya ta, uwa ce fa ni sukenan yaran uku, uba ya salwanta
mini rayuwar ɗa, ɗanki kuma ya kassara rayuwar 'ya ta, kuma ki na gaya mini
nawa zaki bani, ki je can da tsiyarki, ɗa ne na ji ɗan sunna ne, za ta haife
shi a kawo muku tsiyarku, amma ba zan bar wurin nan ba sai ya sakar mini
'ya" ɗif kowa ya yi yadda maman ramma take kuka mai ƙarfi, wanda yake
fallasa asirin zunzurutun baƙin ciki da takaicin da yake cikin zuciyarta.
Ramma ta ƙanƙame mama, ta na jin tamkar ba ta yi wa kanta
adalci ba, ba ta yi wa mahaifiyarta ba.
Nabila ma gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi, a hankali Abdul ya
saukko daga kan kujerar da yake, ya je gaban babar ramma ya durƙusa a kan
gwiwoyinsa sai dai ya kasa ɗaga kansa, kuma ya kasa magana.
A hankali kuma ya ce "Tabbas ahalina sun zama tamkar
wata muguwar kibiya, da ta rusa miki dukkanin ginin rayuwarki da ta yaranki.
Idan rahama za ta iya tunawa kwanki kaɗan su ka rage na
nemeta na rasa, ta farka ta ganni ina kuka cikin dare. Na yi kuka ganin abin da
mahaifina ya aikata, abin ya bani tsoro. Sai dai ina neman afuwarku, dan Allah
kar a hukunta ni da laifin da babana ya aikata, a hukunta ni da iya wanda na yi,
ba zan iya ɗaukar hukuncin laifukansa ba.
Dan girman Allah mama ki yi haƙuri, yadda ki ke iƙirarin ke
ma uwa ce, ko sau ɗaya ki kalle ni a matsayin ɗanki, idan ya tsinci kansa a
halin da nake ciki, ya tuba yayi nadama, watsar da shi za ki yi, ko kuma
rungumarsa za ki yi ki ci gaba da yi masa addu'a da fatan shiriya?.
Na cutar da ku, kuma na san jarrabawa ce, Allah ya jarabce
ni da matsanancin son rahama. Ina nan a kan bakana, a hukunta ni, zan karɓi
hukuncin da duk aka yi mini, amma dan Allah kar ku ce na saki rahama wallahi ba
zan iya ba. Sannan dan Allah mama kar ki tsani abin da rahama za ta haifa,
wallahi ɗan halala ne, kar laifina ya shafe shi, shi ma ya zama
lalatacce".
Ya kalli in da Viper ya ke ya sunkuyar da kai ya ce
"Duk da ina ganinka tare da mahaifina, ban san iya girman alaƙar da take
tsakaninku ba, ban san laifukan da ya aikata maka ba, babu sanya hannuna, ban
sani ba. Amma duk da haka kai ma ina baka haƙuri, dan Allah kar ka hukunta ni
da laifukansa, dan Allah kar ka ce na saki rahama. Ka san me nake ji, tun da ka
taɓa tsintar kanka a makamancin halin da nake ciki, ba ƙarya nake yi ba da nake
nanata muku, ina son rahama, dan Allah ku daina cewa na rabu da ita, ko in
saketa, idan ciwon na bai kashe ni ba, tsana da tsangwamar da ku ke yi mini zai
iya halaka ni"
"Amma Abdul ka yi asara ka bani kunya, yanzu duk a kan
mace ka ke wannan abin? Yanzu halin da mahaifinka yake ciki da ɗan uwanka bai
sanya ka yi kuka ka kira wa kanka mutuwa ba sai a kan mace?"
"Mummy waye silar shigata wannan halin, laifukan waye
su ka ƙara yi wa rayuwata ƙawanya, daddy mahaifina ne, ya yi iya ƙoƙarin sa a
kaina, amma laifukan da ya aikata sun shafe kimarsa, babu abin da zan iya yi a
kan abin da ya aikata face na yi masa addu'a, kuma ya saduda ya nemi yafiyar waɗanda
ya zalunta"
Shiru Viper ya yi ya juya ya fice, haushi ne ya kama Nabila,
wace irin zuciya da Viper hake ne.
Maman ramma ma shirun tayi, ya riƙe hijjabin rahama, cikin
marairaicewa ya ce "Dan Allah ki saka baki rahama, ki ce su yafe mini, kar
su rabani da ke ba zan iya ba"
Ban da uban tsaki, babu abin da take yi.
Nabila Viper ta bayan Viper ta biyo ta na mita.
"Haba Vi, abin da ka ke yi ba ka kyautawa, haba dan
Allah, ai atleast ko ba zaka amince ba ka tofa wani abun ko" shiru ya yi
bai yi magana ba, bai kuma waiwayo ba.
Nabila ta zagaya, sai ta ga ya na share hawaye da
handkerchief, ta fuskanci duk lokacin da za ayi maganar abin da ya shafi
jauhar, ƙarara yake karaya, wasu lokutan sai ya zubar da hawaye. A kullum ta na
jinjina girman ƙaunar da yake yi mata.
"Vi menene kuma? Kukan me ka ke yi"
"Leave me" ya faɗa ya na kawar da kansa gefe.
"Amma atleast yakamata ka ce wani abu ai"
"I say you should leave me, muddin ina kallonsa ina
tuna Indabo ne mahaifinsa, ba zan taɓa aminta ayi duk wani abu da zai sanya ya
samu sassauci ba. Sai dai ya yi gaskiya na san abin da yake ji, dan har gara
shi da ni, ni abin da nake so ɗin ubansa ya yi mini silar rasa shi, ba na fatan
ya shiga mawuyacin halin da ni na shiga a silar rashin abin da yake so. Ba kuma
zan iya watsa wa mahaifiyar rahama ƙasa a ido ba, dan haka ba zan sake cewa
komai ba, abin da mahaufiyarta ta yanke shikenan"
Jikin Nabila ya yi sanyi, hakan ya na nufin ya saukko, ya
sassauta abin da ya ƙudurta a kan Abdul, sai dai ba kowa zai gane hakan ba, sai
wanda ya san shi ya saba zama da shi.
A hankali ta koma ofishin, ta tarar still maman ramma ba ta
ce komai ba, sai kuka da take ta yi.
Nabila ta ce "Ina ga, yakamata a bamu ko 3days ne, mu
yanke shawarar ƙarshe"
A haka su ka watse, Abdul ya so yayi magana da ramma amma
sai haƙura ya yi.
Bayan Viper ya koma gida, ya din ga tunani, sosai ya ga
tsantsar nadama da damuwa a idon Abdul, wanda da mutane mai izza da jin kansa,
ga gayu da hutu, amma shi ne duk ya koma haka saboda soyayya.
Ɗan mama kuwa an sako shi, kawai sai ganinsu su ka yi ya
dawo, liti ya saka shi a gaba, ya na tambayarsa waye ya sako shi?.
Ɗan mama ya ce "Dama ni ai ba laifin komai na yi ba,
kawai shaida ne ni dan mugunta aka garƙame ni".
"Ɗan mama ka ji tsoron Allah, ko waɗanda ka ke kai wa
munafuncin ne su ka karɓo ka"
"A'a sakina kawai aka yi"
Nabila kuwa Alhaji mu'azzam kankarofi ta kira, ta gaya masa
halin da ake ciki a kan lamarin ramma.
Ya ce "To ke ya ki ke gani barrister?"
"Sonake ka yi wa Viper da maman ramma magana, su yadda
aje shari'a court kawai, tun da ya yi nadama, ko dan ɗan da yake cikin
ramma"
Kankarofi ya ce "Ni a su wa zan yi wa Viper magana, taɓ
babar rahaman dai wannan gayen ai sai dai ke ɗin, haka kurum ya din ga yi mini
kallon banza ba zai yiwu ba"
"Na sani ya na da zafi, amma mutum ne mai sauƙin
kai"
"A'a ban ga alama ba, ke dai ki ji da shi, zan yi wa
mahaifiyar rahama magana" suka yi sallama a kan haka.
Alhaji mu'azzam da kansa ya je gida, ya din ga rarrashin
maman ramma ya ce "Na san an yi miki laifi, amma yanzu sai mun so za a
cigaba da yayata abin da ya sameta. Wasu lokutan sai an jarrabaka ka ke samun
ni'ima. Ba dan abin da ya faru ba da babu lallai na sanku, balle na taimaka
muku.
Da babu lallai garinku su samu albarkacin rahama, ta na son
mijinta, idan har ki na son farincikin rahama, ki daure ki yi haƙuri, an san
duk wanda aka ce wa ya yi haƙuri an cuce shi ne.
Amma abin da zai sanya namiji ya yi wa mace fyaɗe ta dawo ta
na sonsa ba ƙarami bane ba, su suka zauna da juna, Allah kaɗai ya san irin
zaman da su ka yi ta fara son abin ta.
Ki yi haƙuri, ki yi haƙuri ki yafe masa kamar yadda ya nema,
yayi nadama na je na ganshi ai, saboda na taimaka muku, matata ƙanwar ubansa
yanzu ta bar mini gida, wai na tozarta ɗan uwanta, kuma rahama mai aikinta ce,
ba irin bautar da ba ta yi mata ba, kuma ban tsaya muku dan ina son ɗaukar
fansa a kan ubansa ba, na tsaya muku ne a matsayina na uba, wanda na haifa
nima, ba zan so ayi mini haka ba, amma ki yi haƙuri, ba kuma dole zan yi miki
ba ba a yafiya dole, amma ba ki san me Allah zai yi miki ba albarkacin yafiyar
ba. Abin alfahari ne a sanadin rahama Allah ya shiryi Abdul" ya daɗe ya na
yi mata nasiha mai ratsa zuciya.
Ta amince da a kai ƙarar shari'a Court, dan Abdul ya samu
sassauci.
Amma hakan bai yi wa babar Abdul daɗi ba, a gaban Alƙali aka
karantawa Abdul laifinsa, a chamber alƙali a ka yi shari'ar, domin privacy ɗin
rahama da identity ɗin shi kansa Abdul ɗin.
Ana karanta masa laifin, Abdul ya amsa, Alƙali ya ce a kai
masa shi prison, bayan sati uku a dawo ya ci gaba da saurarar ƙarar.
Waro ido Rahama ta yi, ta san Abdul ba zai iya zaman prison
ba, babu yadda lauyoyin Abdul ba su yi ba, a kan a bayar da belin Abdul, amma
Alƙalin nan ya murtuke ya ce babu wannan.
Babarsa ta ce "Shi ya janyo wa kansa, dama haɗa baki
aka yi, aka zo shari'a court, dan a kulle shi a tozarta shi"
Aka taso ƙeyar Abdul, Rahma ta kasa damuwarta da ruɗewa,
ya kalli maman ramma ya risunar da kansa.
Ta bakin lauyoyin sa, suka yi wa su Viper godiya, bisa
alfarmar da aka yi musu, aka gabatar da shari'ar kotun addinin Muslunci.
***
Nabila na office ɗin ta a zaune, Sumayya ta turo ƙofar ta ce
"Suprise"
Nabila ta ce "Ko ma ki yi mini sallama malama"
Sumayya ta ce "Ba zan yi ba"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Ki ci kanki"
Sumayya ta ce "Nabila ana ƙoƙarin hana gudanar da
recall election, an kuma sake ɗagawa ba ki ji raina ba"
Nabila ta kwaɓe baki ta ce "Mhmm, ai na san a rina, sai
dai idan ba a ƙasar nan muke ba, na ji ana maganar EFCC za su sake shi, amma
haryanzu babu wani tartibin bayani a kan laifukan da ake tuhumarsa da shi"
Sumayya ta ce "Za kuwa mu yi raising alarm a social
media, lallai ayi mana bayanin meyake gudana ina kuɗin al'umma suke?"
Nabila ta kwashe da dariya ta ce "Ɗansa ya wawushe fiye
da rabi, ya yi wa matarsa hidima, Ai Allah ba azzalumin sarki bane, kuma wani
ikon Allah yaƙi faɗar ɗansa ne ya wawushi kuɗin"
"Ya za ayi ya faɗa, dama fa ware su aka yi dan yayi
campaign, shi kuwa yayi campaign a in da ya dace. Wai ina mutuniyar ki Naja'atu
Bunkure ne?"
"Oho mata na daina jin ɗuriyarta, ina nan ina tattara
ƙorafe-ƙorafe a kanta, zan kai ma'aikatar Shari'a, she's not suppose to
practice law at all, her licensed must be seazed in sha Allah"
Sumayya ta duba wayarta ta ce "Ke ni fa tare nake da
baƙo, bari na yi masa magana ya shigo".
Babu tsammani Sumayya ta shigo tare da wani mutum, da ko ba
a gaya wa Nabila ba, kamaninsa ya bayyanar mata da waye.
Babu in da Viper ya bar kamanin mahaifinsa, shi ma haka yake
dogo mai jiki, akwai alamar hutu a tare da shi, daga yanayin suturar jikinsa.
Babu shiri Nabila ta miƙe, ta ce "Abbu sannu da zuwa,
Sumayya ai da ni ki ka yi wa magana sai mu je mu same shi.
Ta gyara masa kujera, ta ce "Bisimillah" sai dai
ya daskare a wuri guda ya na kallon Nabila.
"Jauhar ya na ganki a nan kuma?"
Sumayya ta ce "Ba jauhar ba ce ai, wannan Nabila
ce"
"Ya za ki ce mini ba jauhar ba ce ba?"
Nabila ta ɗan yi murmushi, ta ce "Abbu ni sunana
Barrister Nabila Yusuf maitama, ita kuma sunanta Fatima Bashir Azare. Ka zauna
dan Allah" ya zauna a hankali ya na bin Nabila da kallo.
Ta kawo masa ruwa, ta nemi wuri ta zauna ta ce "Abbu ya
gida ya iyali?"
"Alhamdilillah, amma idan ba jauhar ba ce ba, ya aka yi
ki ke kirana da sunan da iyalina suke kirana da shi?"
"Saboda na san tarihin rayuwar Viper, an sanar da ni
komai"
Ya jinjina kai ya ce "Kin yi abin da ya tabattar mini
da be ke ce Jauhar ba"
Nabila ta ce "Me na yi?"
Ya ce "Jauhar ba za ta taɓa kiransa da sunan da ki ka
kira shi ba na Viper"
Nabila ta ce "Afuwan Allah ya sa ba laifi na yi
ba?"
Abbu ya ce "Ko kaɗan, ba ki yi laifi ba, amma ina cike
da mamakin yadda ya zamana ba ke ce jauhar ba, duk da a zahiri ban ga bambancin
naku ba"
Nan Nabila ta labarta masa kaɗan daga abin da yakamata ya
sani, game da alaƙarta da jauhar. Ta numfasa ta ce "Abbu, duk da mu
yaranku ne, kun fi mu tunani da hangen nesa, amma iyayenmu maza kuna tafka
kuskure.
Da mahaifiyar Viper ta na raye, ko a gabanta ya kashe
jauhar, da ya dawo ba za ta kore shi ba.
Har mahaifin jauhar ya ce bai yarda zai kashe masa 'ya ba,
amma Abbu kai ka kasa karɓar Viper. A lokacin da ƙaddara ta kai ni cikin
rayuwar Viper, ya fid da ran samun sassauci a rayuwa. Ga ƙwaƙwalwars ta taɓu ga
shaye-shaye fiye da da da ya din ga yi.
Allah ne kawai ya bani sa'a a kansa, daga shi sai abokansa
da su ka riƙe shi, su ka karɓe shi su ka sadaukar da ta su rayuwar, saboda su
rayu da shi.
Na yi iya ƙoƙarina a kansa ya dawo in da kake, amma yaƙi
sosai yake fushi a kan abubuwan da su ka faru"
Abbu ya yi shiru, cike da jimami da kaico a kan wasu abubuwa
da ya aikatawa rayuwar ɗan sa.
Ya numfasa ya ce "Haka ne, haƙiƙa ni mai laifi ne a
rayuwar Al'amin, duk da ni na haife shi, na cancanci na nemi gafararsa, dan sai
daga bayan nan na fuskanci a lokacin da ya lalace, watsi da na yi da shi, ba
shi ne masalaha ba.
Amma dan Allah babu yadda za ayi ku taimaka ku haɗa ni da
shi. Zan yi duk mai yiwuwa na ga na gyara kuskuren da na aikata a baya. Sannan
duk wani support da ake buƙata in sha Allah zan bayar".
Nabila ta numfasa ta ce "Ina haɗaku zai sauke mini
kwandon masifa, duk wani ƙoƙari da nake yi a kan shari'ar ku, zai iya mayar
mana da hannun agogo baya. Ranar da na haɗaku a waya ma, sai da muka yi faɗa da
shi sosai.
Sannan duk da ka na mahaifinsa, idan na haɗaku na saɓa
yarjejeniyar privacy ɗin sa, da aka ja mini kunne a kai. Abu ɗaya zan iya ce
maka, shi ne ka din ga halartar kotu wurin gudanar da shari'ar sa, kuma a
sakamu a addu'a, sannan in sha Allah zan cigaba da ƙoƙarin shawo maka
kansa"
Abbu ya yi shiru sannan ya ce "Na yi kuskuren biye wa
zigar mace, da hawa dokin zuciya na wofantar da ɗa na, na riƙe na wani, ƙarshe
na zama mara kima a idanunsu. Ki ba wa Al'amin haƙuri, ki gaya masa abbu ya na
kewarsa".
"In sha Allah zan sanar masa, kuma komai zai dai-dai
ta, na yi maka alƙawarin bibiyarsa da ci gaba da tausar sa, kamar yadda ya
jagoranci haɗa ni da mahaifina"
Ya jinjina kai ya ce "Na gode muku sosai da sosai,
Ubangiji Allah ya biya ku da gidan aljanna, 'yar jarida ke ma na gode
sosai"
Sumayya ta yi murmushi ta ce "Na gode sosai Abbu"
Nabila ta tashi ta ce "Abbu ba ka sha ruwan ba, na saka
order ma a kawo maka abinci"
Yayi murmushi ya ce "A'a Alhamdilillah, bari na sha
ruwan dai, kasuwa zan tafi"
Nabila ta ce "Allah ya tsare hanya, in sha Allah za mu
zo har gida mu gaishe ka"
Ya ce "Da kuwa na yi farinciki da haka. Ai daga ke har
Sumayyan, na zata zan ga manya, na ganku duk 'yan yara matasa, Ubangiji Allah
ya dafa muku yayi muku jagora baki ɗaya, Allah ya raya mana ku, ya tsare ku
daga Sharrin mai sharri"
Su ka raka shi har gaban motarsa, sai sanya musu albarka
yake yi, ya buɗe motar, ya ɗaukko kuɗi ya ce "Ga wannan kwa sha ruwa, na
gode sosai"
Nabila ta ce "Haba Abbu, ai Addu'ar da ka yi mana ma ta
isa, mun gode sosai da mu da Viper a cigaba da sanya mu a addu'a"
"Addu'a kullum cikin yin ta ake yi, amma sai kun karɓa,
sai dai idan kyautar Abbun ce ba kwa so" da kyar su ka karɓa, ya yi ta yi
musu godiya ya tafi.
Bayan sun koma ofishin Nabila, Sumayya ta ce "Ohh su
Abla sai ɓare-ɓare ake yi, an ga siriki"
Nabila kawai ta girgiza kai, ta din ga jinjina maƙudan kuɗin
da ya basu kyauta, mutumin da zai iya bayar da wannan kyautar kuɗin, lallai
mutum ne mai rufin asiri.
***
Laraba ta bawa ranar samu in ji hausawa, ta kasance ranar da
za a ci gaba da sauraren shari'ar Viper.
Kotu ta cika iya cika, da masu ƙara waɗanda ake ƙara,
lauyoyi 'yan jaridu ƙungiyoyi kotun cike fal.
Bayan an kira ƙarar su Nabila, aka fito da lakwari da aka
aike da shi magarƙama a wancan zaman da kotu ta yi.
Babban abin da ya bawa Nabila mamaki, bai wuce ganin
barrister Naja'atu Bunkure a cikin kotun ba, duk da ta ji gabanta ya faɗi, amma
ta dake ta adana mamakinta a zuciyarta.
Ta fito ta gabatar da kanta, aka fito da lakwari, Nabila ta
nemi Walid ya fito.
Walid ya fito ya tsaya, ta dubi Walid ta ce "Ko zaka
iya bayyana wa kotu sunanka?"
"Sunana Muhsin Hassan, wanda ake kira da Walid".
Ta nuna masa lakwari, ta ce "Ka san wannan?"
Ya jinjina kai ya ce "Eh na san shi"
"Ka san laifin da ake tuhumarsa da shi?"
"Eh na sani, laifin ki san kai ne na matar Al'amin da ɗan
cikinta"
"Ka tabattar?"
"Eh na tabattar"
"Za ka iya shaidawa kotu abin da ya faru?"
Walid ya gyara tsayuwarsa ya ce "Ranar da za a kasheta,
ni na aro babur ɗin adaidaita sahu, kamar yadda Al'amin ya buƙata, da ni da shi
da abokinmu liti, mu ka je asibiti. Likita ya dubata ya ce ta wuce lokacin
haihuwar ta, dan haka za ayi inducing ɗin ta, amma idan bai yi ba tiyata za ayi
mata.
Ta ce tana son cin ƙosai, muka yi ta yawo bamu samu ba, na
yi alƙawarin zan nemo ƙosai da sassafe na kai mata, daga nan mu ka ajiye su a
gida, mu kuma muka wuce.
Da sassafen da na je, na tarar da layin a cike da jami'an
tsaro, wai an yi kisan kai"
"Ka ga gawar jauhar da ciki?"
"Eh, a kan idonmu aka fito da ita an rufeta a cikin
ledar gawa, ta na zubar da jini".
"Waye ya kira jami'an tsaro ya sanar da su abin da ya
faru?"
Walid ya ce "Ban sani ba gaskiya"
Nabila ta yi godiya, Bunkure ta taso ta gabatar da kanta a
matsayin lauyar lakwari, sannan ta yi suka ga shaidar Walid, cewa shaida ce mai
rauni, tun da bai tabattar da ganin lokacin da lakwari ya kashe jauhar ba.
"Ya mai girma mai shari'a, ina son kotu ta bani dama,
zan yi wa Al'amin wasu tambayoyi"
Viper ya fito ya tsaya, ya na tuna abin da ta yi masa a
wancan lokacin.
"Malam Al'amin, a haka ba ka yi kama da malamai ba,
balle ace wa'azi ka yi wa su lakwari ba su ka ji haushi, suka kashe maka mata
ba.
Me zai haɗa mutum kamar ka da mutane irin su lakwari har su
shiga gidanka, su kashe maka mata? Ko ka na ta'amalli da miyagun ƙwayoyi ne kai
ma?" Tayi maganar tana tsare shi da idanunta.
Ayshercool
08081012143
Har Nabila ta zaburo za ta yi magana, Baba ya ce "Amma
kamar ƙoƙarin tabattar da mutuwar jauhar ake yi, wannan tambayar abin da ya
shafe mu ne personal issue ne"
Nabila ta yi carf ta cafe, da sukar abin da Bunkure ta
aikata.
Da haka dai aka saurari wasu daga cikin shaidun na ranar,
aka sake ɗaga shari'ar.
Viper ya din ga jin jikinsa wani iri, sai da ya fito ya
tsaya su na gaisawa da Baban su jauhar.
Bayan Nabila ta fito daga cikin kotun, ta samu wuri tana
amsa waya, babu tsammanni Nabila ta ji an janyota baya, an riƙe damtsenta.
Ta waiwaya ta ga Naja'atu Bunkure, ta yi wa Nabila wani
munafukin murmushi ta ce "Sannu da ƙoƙari barrister Nabila, lallai na
yadda da kirarin da ƙawarki take yi miki, na a lady of her words, the voice of
voiceless. Kin yi alwashin kai ni ƙasa, ki na ta faɗi tashin ganin kin ga
bayana. To kafin ki ga nawa bayan ni zan ga naki, sai na tabattar miki da wanda
ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi.
Zan kunna miki wutar da sai ta ƙonaki har lahira, abu mai daɗi
da ya sauƙaƙa mini komai shi ne, samun labarin ke yar uwar matar Viper ce, ki
na kare mijin yar uwakki, da kuma neman hakkin jininta da ya riga ya tafi a
banza a wofi, zan illataki da wutar zahiri da ta baɗini ta zuci, sai na tona
asirin miyagun ayyukan Viper sun koma kansa, na kassara Rayuwarki yadda zai
zame muku baƙin ciki goma da ashirin, kamar yadda ku ka tarwatsa nutsuwarmu da
ni da uban gidana Indabo"
Nabila ta saka hannu, ta buge hannun Bunkure daga damtsenta,
sannan ta hankaɗata iya ƙarfinta ta nunata da yatsanta ta ce "Jinin 'yar
uwata ya fi ƙarfin ya tafi a banza, ƙarya ki ke yi, kuma wutar da ki ke shirin
kunnawa, reshe ne zai juye da mujiya, dan kuwa ke zai koma ya ƙona, daga ni har
Al'amin ƙarafa ne a cikin wuta da babu abin da wutar da ki ka kunna ta isa ta
yi mana. Jinin yar uwata bai tafi a banza ba, duk wanda ya saka hannu wurin
zubar da jininta, sai jinin jauhar ya zame masa mummunar gubar da sai ta kai
shi lahira".
Nabila ta daki ƙirjinta ta ce "Gani gaki Naja, ki
tsammaci abin da zatonki da hangenki bai taɓa tsammani ba" tayi maganar ta
na nuna Naja'atu.
Sumayya ce ta hango abin da yake faruwa, Viper ya na can ya
na magana da Baba cikin girmamawa, ya na tsugunne Baba ya riƙe hannunsa, ya na
ta yi masa nasiha da bashi ƙwarin gwiwa, Alhaji mu'azzam har mamaki abin ya
bashi, dama haka Viper ya iya ladabi.
Karaf idanun Viper su ka sauka a kan na Abbu, da bai san ma
Abbun ya zo kotun ba, gabansa ya yi mummunar faɗuwa, Baba ne ya kalli in da
Viper yake kallo, shi kansa bai lura da mahaifin Vipern ba sai yanzu.
Cikin hanzari ya nufe shi, shi ma ya nufo shi cikin sauri,
Viper kuwa kawar da kansa ya yi daga kallon Abbu, zuciyarsa na ci gaba da
harbawa da sauri.
Suka gaisa Abbu ya ce "Malam Bashir kwana da yawa,
kawai sai samun labari mu ka yi kun tashi, babu ko sallama"
Baba ya ce "Wallahi kuwa, ai na yi laifi ayi mini
afuwa, ashe ka zo zaman shari'ar Al'amin, kuma kawai sai ka ga Nabila ita ce
lauyarsa"
Abbu ya ce "Abin ya bani mamaki sosai ya ɗaure mini
kai, duk wannan abun ashe Jauhar ta na da 'yar uwa, ban taɓa sani ba, ta hanyar
yar jaridar nan ƙawarta sumayya muke magana, ta kaini wurinta, wallahi na
razana sosai, Allah na zata marigayiyya ce"
Baba yayi murmushi ya ce "Allah kenan, mai jujjuya
lamarinsa yadda ya so"
Viper ya bar wurin da zai ci gaba da ganin Abbu, saboda
yadda zuciyarsa ke neman tsinkewa, sai azalzalarsa zuciyarsa take yi ya ƙarasa
wurin da Abbu yake.
Can ya hango Sumayya ta danƙo hannun Nabila, sai surutai
take yi, fuskarta ta koma ja, da alama ranta ne ya ɓaci.
Nufar su yayi da sauri, ya na tambayar su ko lafiya.
Sumayya ta ce "Faɗa su ka yi da Naja'atu Bunkure"
Cikin mamaki ya ce "Faɗa kuma?"
"Eh"
Ya ce "Meya haɗa su?"
"Wallahi ban sani ba, ƙarar da aka yi bayan taku na
tsaya saurara, na yi picking wani abu a cikin rahotannin da zan yi yau, kawai
da na fito na gansu su na cacar baki"
A nutse ya kalli Nabila da take ta huci ya ce "Meya haɗa
ki da ita?" Shiru Nabila ta yi ta kasa magana.
"Ina tambayar ki menene?" Still ta kuma yin shiru,
sai sauke ajiyar zuciya take yi.
Ya ce "To wuce mu tafi"
Ya sakota a gaba su ka fito harabar kotun, a wannan karon
har da Alhaji mu'zzam kankarofi suke tare da su Abba, Abban ya gabatar wa da
Alhaji mu'zzam Abbu mahaifin Viper.
Gaba ɗaya hankalinsu ya dawo kan su Viper, da su ka taho
fuskar Nabila sam babu annuri.
Rige-rigen tambaya su ka fara yi, ko lafiya Nabila take cika
ta na batsewa.
"Ya aka yi ne, meyafaru?" Baba ya tambayeta cikin
kulawa.
Kawai ta durƙusa ta fashe da kuka.
Viper ya ce "Wai ke wace irin yarinya ce, wannan ai
halin yarinta ne, barrister ce fa ke, a harabar kotu ki zauna ki na kuka saboda
wauta da abin kunya?"
Alhaji mu'azzam ma ya ce "Nabila menene, kar ki ɗaga
mana hankali mana"
Abbu ma cewa ya yi "Idan yanayin yadda shari'ar ya
gudana ne bai yi miki ba, ki yi haƙuri mu je a ci gaba da addu'a da neman ɗaukin
Ubangiji"
Abbu na fara magana, Viper ya yi ɗif, ya juya ya bar wurin.
Abin da Viper ya yi ya ƙara wa Nabila takaici, cikin mamaki
Baba ya ce "Ya haka kuma?"
Abbu ya girgiza kai ya ce "Rabu da shi kawai, komai
yayi mini na cancanci hakan"
Still wani mamakin ya sake cika Alhaji mu'azzam, ya na
mamakin wane irin mutum ne Viper haka, baban na sa ma.
A dai-dai lokacin liti da Walid su ka ƙara so gaban Abbu, su
na zuwa suma durƙusawa su yi a gaban Abbun, cikin matuƙar girmamawa su na
gaishe shi tare da Baba.
Abbu ya dafa kafaɗunsu ya na amsawa.
"Ya ƙoƙari ya fama da Al'amin"
Walid ya yi murmushi ya ce "Babu fama Abbu"
"Ina ta godiya Ubangiji Allah ya saka muku da mafificin
alkhairi, dan Allah a ci gaba da bashi haƙuri, ace ya yafe wa Abbansa"
Liti ya ce "In sha Allah"
Walid ya kalli Nabila da take kuka ya ce wa Sumayya "Me
ya sameta?"
"Shagwaɓa mana" Sumayya ta bashi amsa ta na kallon
Nabila.
"Mai zamani ne ya yi mata wani abun kenan?"
"A'a faɗa su ka yi da Naja'atu Bunkure, ban san me ta
yi mata ba dai"
Liti ya ce "Ai matar nan shegiya ce, wani abun ta
ƙudurce a ranta za ta aikata, mussaman yanayin tambayoyin da take yi a kotun
nan"
Abbu ya ce "Ki kwantar da hankalinki, kar ki damu kin
ji jauhar, in sha Allah za ayi nasara"
Baba ya ce "Nabila dai".
Abbu ya ce "Ni jauhar nake gani, duk ɗaya ne a
wurina"
Alhaji mu'azzam ya yi murmushi ya ce "Nabila akwai
ƙoƙari da jajircewa, sai faɗa da tsiwa, unlike jauhar, so calm ba ta da
hayaniya"
Abbu ya ce "Dan Allah dai ko da tsayayye wannan ma mu
na riƙo, a taimake mu a bamu, ta maye mana gurbin jauhar da muka rasa".
Dumm gaban Alhaji mu'azzam ya buga, Baba kuwa ya ce wa Abbu
"Ai a yanzu dai wannan ba ni da iko da ita, akwai ƙura a kanta".
Nabila ta ce "Baba ni na tafi"
"To kya tafi ki na kuka Nabila, ko in tafi da ke can
gida?" Ta girgiza kai alamar a'a ba zata bi shi ba.
Ya ce "Hafsa kullum cikin zancenki take Nabila, yanzu
ina zaki tafi?"
"Gida wurin Abbana"
Ya ce "Dama ai Abbanki ne, ban ce nawa ba ne ba"
Alhaji mu'azzam ya ce "Ko mu tafi na ajiyeku a
hanya?"
Liti ya ce "A'a ga mota can da security ɗin da suke
kula da ita ai, zamu rakata"
Alhaji mu'azzam ya yi murmushi, ƙiri-ƙiri Viper suke taya wa
kishi, sun manta da saka hannunsa aka ba wa Nabilan security.
Baba ya ce "To Allah ya kiyaye hanya, ina nan tafe
wurin Abban naki, ki gaida mutanen gidanku"
Sumayya ta ja hannunta su ka yi gaba, Abbu ya kalli Baba ya
ce "Ni ranar da na fara zuwa office ɗin ta, na zata Jauhar ce, ta yi mini
wani bayani da ban gama fahimta ba, yaya aka yi Jauhar take da yar uwa bamu taɓa
sani ba?"
A lokacin Abba ya warware masa komai, har yadda aka yi auren
Jauhar da Al'amin, da yadda ya mayar wa da Alhaji mu'zzam kuɗin aurensa, da
tsamar da suke yi yanzu da Major a kan Nabila, ya na son ya karɓi 'yar sa, ko
yaya ya zauna da ita kafin ta yi aure, amma ya san major ba zai taɓa bari ba,
ita kanta ba zata yadda ba dan ya ga tsanar iyalinsa muraran a idon Nabila.
Abbu ya ce "Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya yi
gaskiya da ya ce bai bar wata fitina a bayansa mafi cutar da maza ba, dai daga
mataye.
Sai yanzu na ƙara yadda da mata su ne ƙashin samar da duk
irin al'ummar da suke so, na gari ko kuma akasin haka.
Wallahi Alhaji Bashir, ina cikin matsananciyar nadamar
wofantar da rayuwar Al'amin, a ganina haka ne mafita, matar nan ta din ga
zigani ina hawa kai, 'ya'yana na cikina su ka rayu kamar bayi, duk rufin asiri
da nake da shi amma rayuwar Al'amin ta ƙare a haka. Ina baƙin ciki haɗuwata da
shi ta ƙarshe da ya dawo daga prison, ya na tambayata ya aka yi da matarsa, ban
saurare shi ba balle na yi masa uzurin ba zai iya kashe jauhar ba. Na ji kunya
da kai a matsayin ka na mahaifinta ba ka aminta zai kasheta ba. Na tafka
kura-kurai duk a dalilin rashin dace da mace ta gari".
Sai su ka ɓuge da hira, da jajantawa juna, sosai su ka yi wa
Alhaji mu'azzam a kan gudunmuwar da ya ba wa rayuwar Nabila da Viper.
Har gidan Abba su ka kai Nabila, sannan su ka watse, sumayya
ma ta tafi wurin aikinta.
Azahar ce lokacin, kuma dama ba salla za ta yi ba, ta na
period, ta tafi falon Abba.
Ya na tare da Mama, Nabila ta yi sallama, Abba ya amsa, mama
ta haɗe rai.
Ta dire jakarta, ta ware veil ɗin kanta, ta haye kan doguwar
kujera ta kwanta.
Mama ta yinƙura za ta yi magana, amma Major ya kalleta,
hakan ya tilasta mata haɗiye maganar da ta yi niyyar yi.
Nabila ta ci gaba da kuka, amma Abba bai kulata ba, ta ce
"Abba wai ba zaka kula ni ba?" Ya yi mata shiru.
Tashi mama tayi ta bar masa ɗakin, ganin magana take yi da
shi mai muhimmanci Nabila ta zo ta kwanta tana kukan rashin mutunci.
Doguwar ajiyar zuciya da ta sauke, ya sanya ya kalleta,
bacci ta yi, hakan ya tabattar masa akwai gajiya a tare da Nabilan.
Ya gyara mata hannunta, ya na kallon fuskarta, wadda take
sak ta chubaɗo.
Kawai ya din ga hango ina ma duka ya ɗauke su ya riƙe, da
Nabila da Jauhar, ɗaya lauya ɗaya likita, da sai ya fi alfahari da hakan, amma
haryanzu bai ga alfanun tsaya wa Viper da Nabila ta yi ba, duk da kasancewarsa ɗan
daba, kuma da ya ɗan bibiyi abin da ya faru, babu wani history mai kyau a kan
Viper, ban da dillancin ƙwaya da sara suka, sai kuma tserewa daga prsion bayan
an kama shi da laifin kisan kai, kuma wai daga baya an hana kama shi.
****
Mahaifiyar Abdul ta kasa nutsuwa gabaki ɗaya, ta na ta
ƙoƙarin yadda za a bayar da belin Abdul a sake shi, amma abu ya ci tura, duk da
irin tayin kuɗaɗen da ta sanya aka din ga yi wa masu ruwa da tsaki a kan
shari'ar ɗan nata, amma kuɗi su ka ƙi tasiri, alamu su ka nuna da gaske so ake
a hukunta Abdul.
Ba ita ba, hatta abokan Indabo, sun yi iya yin su amma aka
nuna musu ba za yiwu ba.
Sau ɗaya ta je ta ga Abdul, hankalinta ya yi mummunan tashi,
gashi dai a wuri na musamman yake, ba wai haɗa shi aka yi da sauran fursunoni
ba, amma gaba ɗaya ya fita daga hayyacinsa.
Ya ƙara ramewa, gashi mutum ne mai kufan gashi, saboda haka
tuni gashi ya cika masa fuska. Duk da ana kula da shan maganinsa ya na samun
abinci, amma ba irin wanda yake so ba.
***
Da la'asar Nabila ta tashi, ta yi wanka, ta ɗauki abin da za
ta ɗauka za ta fita.
Baba Magajiya ta tare ta ta ce "Arfa, duk yadda major
yake kaffa-kaffa da ku, mussaman ke yake saka miki ido da kula da ke, amma ya
zuba miki ido, ki na shige da ficenki, mutanen gidan nan har da maƙwabta su na
ta surutu a kan hakan, yakamata fa ki kula ki yi wa kanki faɗa".
"Baba magajiya, Abba ya san ko nan da bangon duniya zan
fita, Abba ya na da yaƙinin ba zan lalace ba, ba zan yi abin da zan cutar da
kaina, ko na janyo masa abin kunya ba. Kar ki manta har ƙasar ƙetare na fita na
yi karatu ban lalace ba, in sha Allah ba zan baku kunya ba"
"Abin kunya na nawa kuma, banda wanda ki ke aikatawa
yanzu? Kwana a in da ki ka ga dama, yawo da ƙaratan 'yan daba me ya rage
kuma?"
Nabila ta kalli mama cikin nutsuwa ta ce "Hajiya mama
yaushe ki ka fara damuwa da ba na kwana a gida ne? Tun yaushe ki ke yi mini
fatan abin kunya? Ni ban aikata abin kunya ba, ba kuma na fatan na aikata,
Nasir shi ne mai abin kunya a ƙugunsa, da ya canza mota ya gama gini, yake
wadaƙa da kuɗi wanda ya wuce samunsa ba ki tuhume shi ba, Abba ya yi yinƙurin
tuhumarsa ki ka hana ki ka kare shi.
Ki daina shiga harkata tun kafin na nuna wa duniya waye ɗan
naki"
Baba magajiya na takaicin yadda mama ta daɗe da zubar da
mutuncinta da tun Nabila na jin nauyinta ta na girmamata, har an kai ƙadamin da
ta daina ɗaga mata ƙafa.
Bayan ta fita wayar Viper ta kira, liti ya ɗaga.
Ta ce "Ina mai wayar?"
"Bacci yake" ya amsa mata kai tsaye.
Ta ce "Bacci da yammacin nan, shikenan"
Rabon Nabila da gidan har ta manta, liti ta tarar da ɗan
mama a tsakar gidan su na hira, amma rabin hirar ɗan mama zagi kawai yake sha a
wurin liti.
Amsa sallamar su ka yi, Nabila ta ce "Ɗan mama ka yi
free kenan?"
"Eh belina aka bayar ai, dama za mu tattauna da ke,
nima zan iya bayar da shaida"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Shikenan, ina Oga?"
Ya na cikin ɗaki, ya na ta aikin danna waya.
Nabila ta yi murmushi ta shiga ta tarar da shi, ya tashi
daga baccin, ya na zaune ya na ta danna tab. Gefensa duk abin sauran sigari da
ya sha.
Ta zuba masa ido, ya cigaba da abin da yake yi, sai da ya
kammala sannan ya kalle ta ya ce "Daga ina ki ke?"
Ta kwaɓe baki ta ce "Gida"
"Wai meyasa ba kya ji ne? Ke duk wani abu da za ki
aikata, ace ba ki kyauta ba, kin san shi kuma za ki aikata. Kin sani sarai you
are not safe, an kai ki in da zaki zauna, an baki wanda za su din ga fita da
ke, saboda tsaronki, amma sai yawonki ki ke yi yadda ki ka ga dama, tarar aradu
da ka fa ki ke yi?" Tayi shiru kamar gaske ta na saurarsa.
"Meya haɗa ki da Naja'atu Bunkure, har ku ka yi faɗa ɗazu
a court, kar ki je da gayya take yi miki abin da za ki yi reacting, ta samu
kafar cutar da ke"
Nabila ta ja numfashi ta ce "Ni matar nan za ta kalli
tsabar idona, ta ce mini wai jinin 'yar uwata ya tafi a banza? Ban san ya aka
yi ta samu labarin cewa jauhar sisterna ce ba. Da fari na fara karaya, jin
yadda take zaƙulo tambayoyi a kotu, duk da na yi tsammanin hakan, amma abin da
ta gaya mini, tamkar ta yi mini allura ne, jinin jauhar sai ya zame musu
bala'i ya zame musu guba mai mummunan hatsari"
Ya ajiye tab ɗin ya ce "Haka ta ce Jinin matata ya zuba
a banza?" Ta jinjina masa kai.
Ya numfasa ya ce "Haryanzu su na wasa da ni, daga ita
har ubangidanta, daga nesa suke hangena a cikin wutar, zatonsu hannayensu za su
iya jure zafin da na ɗauka su ɗaukko ni, na san abin yi"
Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Ko ni sai na ba wa matar nan
mamaki, shashasha kawai"
Yayi shiru yana juya maganar, da jin zafin abin da Nabila ta
ce Bunkure ta faɗa, kamar ita aka gaya wa.
Kamar wadda aka mintsina ta ce "Yauwwa kai kuma"
ya juyo ya kalleta tamkar uwar da take shirin yi wa ɗanta faɗa.
"Viper ka bani haushi, zan iya cewa abin da ka yi ya
kusa fin abin da Bunkure ta yi mini" tsuke fuska ya yi ya na kallonta.
"Ai ko za ka cinye ni ɗanya sai na faɗi abin da ya kawo
ni. Abbu da kansa ya je Office ya same ni, ba aike ba a kanka, ni na ce ma ya
zo kotu ya din ga ganin yadda shari'ar take gudana, ya damu ya damu saboda kai,
amma a gaban mutane, a gaban kowa da kowa ka yi tafiyarka ka bar shi, me ka aikata
kenan? Nuna wa duniya cewar mahaifinka bai isa da kai ba ko kuwa? Kai ka ce har
da bijire masan da ka yi Allah yake jarabtarka, so ka ke wani bala'in ya same
mu ne a sanadin wulaƙanta iyaye?.
A cikin Alƙur'ani mai tsarki sau nawa Allah ya maimaita yi
wa iyaye biyayya? Ka daina kallon ya yi maka laifi, kai sai Allah ya hukuntaka
da ƙaurace masa da ka ke yi. Nan fa ni ka zaunar da ni ka na yi mini nasiha,
kai meyasa ba za ka yi aiki da nasihar ba"
"Ke shut up! Kullukum ra'in, wa kullukum mas'ulun an
ra'iyatihi, sau nawa Abbu yayi wannan tunanin a game da ni? Ya wofantar da mu
ni da ɗan uwana, an kashe shi ya ce ni ne sila, a duniya ina cikin 'ya'ya masu
tsananin ƙawazucin iyayensu.
Kin san sau nawa daga gidana kan sallar asuba nake tafiya
unguwarmu, dan ayi sallar asuba a idar ya wuce na ganshi na ji ƙamshin turaren
sa, saboda ƙamshin ya na tuna mini lokutan da su ka gabata mu ka rayu cikin
farin ciki da son juna.
Babu nasiha tsakanina da shi, babu rarrashi sai zagi hantara
da kuma kora, alhalin ina kallon ya na ta haƙilon alkinta rayuwar yaran
matarsa? Ni kuma ina yawo babu sana'ar kirki da zan kula ma da matar da ya aura
mini, ki na tunanin ko na fi kowane ɗa lalacewa a duniya, idan mahaifiyata na
da rai watsar da ni za ta yi?. Kin san sau adadin zuwan da nake yi in da yake
ya na korata, kamar wani kare, kin san cin mutuncin da ya yi mini a lokacin da
na baro prsion na je in da yake, ya kore ni ya ci mutuncina wai ba ya ƙaunar
ganina na kashe jauhar, me ya rage nake nema a wurin Abbu ne tun da ya furta ba
ya ƙaunar ganina? Har cikin zuciyata ina son mahaifina amma ba zan ɓoye miki
ba, gaba ɗaya ya sire mini, uwata da ta mutu ma Allah ya raya ni, ɗan uwana mai
tausayina da aka kashe shi, shi ma Allah ya raya ni. Dan haka zan iya rayuwata
ko babu Abbu. Da ya tallafi rayuwata da wataƙila duk wannan azabar ban sha ta
ba a rayuwa. Ki gaya masa ya rayu da waɗanda yake so, halarta wurin shari'ata
ma na yafe ya zauna ya huta, Allah zai wanke ni"
Nabila ta yi masa ƙuri da ido, har ya yi gama, idanunsa su
ka yi jawur kamar an zuba masa gauta, dama ga sigari ya sha.
Ta ja ajiyar zuciya ta ce "Ni da kai ta wata fuskar
tamkar jirgi ɗaya ne ya kwaso mu, amma sai dai akwai in da ƙaddarorinmu su ka
sha bamban.
Vi" ta kira shi a sanyaye.
Ya kawar da kansa gefe, ya na ta sauke ajiyar zuciya.
"Ka kalle ni mana magana za mu yi"ya ƙi waiwayo
wa.
Ta zagaya saitin in da ya kawar da kansa, hawaye ya cika
masa ido.
"Vi dan Allah kar ka yi kuka, ka yi haƙuri, amma
kasancewar ka abu mafi soyuwa a wurin 'yar uwata ina fatan har a lahira ka
kasance da rahamar Allah, ban yi maka wannan maganar dan na ɓata maka rai ba,
lokuta da dama sai Allah ya jarrabi bawansa kafin ya yi masa wani tagomashi na
alkhairi. Dan Allah ka yi haƙuri, amma ba zan haƙura da rarrashin ka ba, a kan
ka daidaita da Abbu. Iyayenmu duk da sun dace da mataye na gari, da ba su aikata
wani abun ba"
Ya haɗiye wani abu mai ɗaci ya ce "Tashi mu je na mayar
da ke barrack, na san kan ki koma duhu yayi, kuma idan na sake ganin kin zo nan
sai na ɓallaki na gaya miki"
"Ba zan sake zuwa ba, but smile mana dan Allah, kar mu
tafi ka na huci, na ga ka ɗauki zafi da yawa"
Viper ya sake tsuke fuska ya ce "Tashi mu tafi"
kamar yarinyar goye, ta maƙale kafaɗa ta marairaice ta ce "Dan ka yi
murmushi Vi, ba na son wannan mood ɗin naka" tashi ya yi tsaye, ya ɗaukko
face mask ɗin sa ya saka su ka fita.
Su na tafe a hanya, ta na ta yi masa hira, tun ya na basarwa
har kuma ya saki jikinsa, har da yin murmushin.
Nabila ta sha faɗa wurin madam Halima, saboda rashin jin ta
da taurin kai, na yadda take wasa da rayuwarta.
Madam Halima babu hausa sosai, gashi wai a dole sai ta yi wa
Nabila faɗa, sai da Viper ya yi murmushi, dan Nabila ba ta san faɗa, ta haɗe
rai.
***
Abdul ya cika sati uku a gidan kaso, amma duk ya firgice
kamar ya kwashi shekaru a tsare, duk da halin da yake ciki, bai hana shi ganin
ramar da matarsa ta yi ba, ga cikinta ya fara tasawa babban fatansa shi ne
Allah ya sa tun da an ce za ayi masa sassauci ramma kar ta haihu ya na tsare.
Ba tare da sake yin wani dogon jawabi ba, kasancewar ya riga
ya amsa laifinsa, lauyoyin sa su ka nemi a ƙara sassauta masa, tun da ya amsa
laifinsa ba tare da ya wahalar da shari'a ba.
Alƙali ya yanke hukuncin a yi wa Abdul bulala ashirin, a kai
shi gidan yari tsawon watanni biyar, da aiki mai wahala, sai kuma tara ta
zunzurutun kuɗi naira miliyan biyar.
Kasancewar a chamber alƙali ake shari'ar, ba a cikin kotu
ba, mahaifiyar Abdul ta marairaice a kan ya ƙara sassauta masa.
Alƙalin ya dubeta ya ce "Madam, mutanen nan fa sun yi
muku adalci, da ba kotun shari'a su ka kawo ƙarar nan ba, ke kin san laifukansa
sun fi ƙarfin hukuncin da aka yi masa, dan haka babu wani sassauci ko ɗaga ƙafa
da za a kuma yi masa. Ku je ku yi ta haifar yara babu tarbiyya ku na sakin su a
cikin al'umma su na fasadi a bayan ƙasa, ba tare da kun damu ba, iya yarinyar
da ya ketawa haddi ba 'ya ba ce? Tarar ma idan ba zaku biya ba, sai ya je yayi
zaman shekara bakwai a gidan yari, hakan ya zama izina da kuma darasi ga
saura"
Ana gama zaman, Nabila ta janye ramma daga kotun, aikuwa su
na tafe ta na kuka, mussaman jin za a dake shi, ga kuma aiki mai wahala an ce
yayi a gidan yarin.
A waya Nabila ta kira Viper ta ce masa ta tafi da ramma
barrack, washegari ta mayar da ita wurin mama, saboda ta ɗan samu nutsuwa.
Mama kuwa duk da ba haka ta so ba, amma ta samu sassauci
daga baƙin ciki da kuma raɗaɗin da zuciyar ta take yi mata.
Ganin gigicewa da tashin hankalin da majaifiyar Abdul ta
shiga, maman ramma ta ce "Kamar haka, haka na shiga tashin hankali,
lokacin da ya ketwa 'ya ta haddi, kuma na rasa mai taimakona, Alhamdilillah ko
iya haka na samu raguwar wata azabar da nake ji".
***
Rahama ta kasa bacci, ta kasa cin abinci, nan Nabila ta ƙara
tabattar da soyayya bala'i ce wani lokacin. Duk wannan bala'in da ake yi a
kanta, ita hankalinta ya na kan mijinta.
Haka Nabila ta yi ta aikin rarrashinta. Washegari ta kashe
wayoyinta, ta ɗauki ramma aka kai su prison.
Sai dai aka sanar musu, Abdul ba zai iya fitowa ba,
Albarkacin ID card na aiki, da yadda Nabila ta fara tashe, aka ba su damar
shiga cikin prison har ɗakin da Abdul yake.
"Subhanallah" ramma ta furta, ganinsa a kwance ruf
da ciki, bayansa a farfashe saboda bulalar alƙali da ya sha.
Ta ƙarasa in da yake da sauri, ya ɗago da kyar, jikinsa ya
na karkarwa saboda zazzaɓi, Abdul zai iya cewa da wayonsa babu wanda ya taɓa
dukansa, amma yanzu ga shi ya sha duka, hakan ya haifar masa da zazzafan zazzaɓi.
"Abdul" ta faɗa a raunane ta na kuka.
"Rahama zafi, bayana kamar ana ƙona ni"
"Ka yi haƙuri Abdul, dan Allah ka yi haƙuri, ban ma san
me zan ce ba" tayi maganar cikin kuka.
"Ai an sassauta mini, ta wani fannin na ji daɗi da wuri
zan fito in sha Allah, ni zan karɓi haihuwar ki da kaina" yayi maganar
yana kwanciya a jikinta.
Ta haɗiye yawu mai zafi, ta ce "Abdul da sun bi ta
tawa, da na daɗe da furta musu na yafe maka, babu yadda mu ka iya, ƙaddaramu ce
ta zo a haka. Amma ka yi haƙuri na yi maka alƙawarin duk rintsi idan ka fito in
sha Allah mu na tare"
Ya ɗago da kyar ya kalle ta ya ce "Are you sure, kar ki
saka mini rai fa"
"Na tabattar in sha Allah"
"Wallahi ina sonki sosai rahama"
Nabila ta na tsaye ta na kallon ikon Allah.
****
Viper ya na ta shiri zai je wani aiki na musamman cikin
sirri, wayarsa ta fara ringing, bai damu da duba waye ba kawai ya ɗaga.
"Aminu Viper"
"Ma'aruf Indabo" ya amsa masa kai tsaye.
Indabo ya ce "Ban yi mamakin saurin ɗaukar muryata da
ka yi ba, kai a nan ka dage ka haɗa kai da kankarofi a kan lallai sai kun ga
bayana, yanzu ka kafe kai da fata, saboda yar matsiyata ƙanwar Nura guduma, an
kai mini ɗa gidan yari, to bari murna karenka ya kama Zaki mai zamani. Za a
sake ni daga ɗaurin talalar da aka yi mini, sannan ka shirya abubuwan da ka iya
biyo baya da ba ka yi tsammani ba. Za a ci gaba da zaman kotu a kan shari'ar
matarka, amma ka sani reshe ka iya juyewa da mujiya, ka tsammaci abin da ba ka
taɓa zatonsa ba a kotu".
"Gargaɗi ka ke yi mini? Ko alhinin kar asirinku ya tonu
a kotu, idan gargaɗi ka ke yi mini kar na kama sunanka, ka kwantar hankalinka,
ai an san da wuyan biri ake ɗaure shi a ƙugu, kai tsaye waɗanda su ka kashe
matata kawai za a hukunta, sannan ka din ga sassauta lafazinka idan ka na
magana da ni, saboda ni ke da makami mai linzamin ƙarasa tarwatsa rayuwar
iyalinka, idan ka ƙi ji ba ka ƙi gani ba. Na san babu abin da za ayi maka ko da
kuwa an ambaci da saka hannunka a ta'addancin da aka yi mini. Zan yi dragging ɗin
ka zuwa kogon da ramina yake ne, na yi ta azabtar da kai da dafina, zuwa abin
da hali zai yi. Amma ina P.A ɗinka yake ne? Kwana biyu ba a ganin gilmawarsa
yakamata ka yi tunani a kan wannan" ƙit ya kashe wayar.
Ayshercool
08081012143
Viper ya ɗan ja lokaci ya na kallon wayarsa, ya na tunanin
mai indabo yake shiryawa, da har ya samu ƙwarin gwiwar kiransa ya na yi masa
surutan iska. Kodayake bai kamata ya ce surutan iska ba, domin kuwa a rashin
imani irin na indabo babu abin da ba zai iya aikatawa ba.
Lambar Nabila ya yi ta kira, amma a kashe ba ta shiga, dan
haka ya haƙura ya ci gaba da shirin fita.
Ramma ta yinƙura ta ce "Bari mu tafi, na san ba dan
albarkacin Anty Nabila ba, babu yadda za ayi a bari na shigo har na ganka,
Allah ya baka lafiya ya baka ikon cin jarrabawar nan. Ba an hukuntaka da an
tsaneka bane ba, ina fatan tuban da ka yi ya zama taubatan nasuha, kuma wahalar
nan Allah ya sa ta zame mana kaffara baki ɗaya mijina" ya ɗago ya kalleta
ya ce "Kai, rahama baki taɓa kirana da sunan da na ji yayi tasiri har
cikin zuciyata kamar yau ba, da har nake jin eh lallai kin yafe mini ba. Yanzu
kin yadda ni mijinki ne?"
Ta yi ƙasa da muryarta ta ce "Ai zamantowarka mijina
tuntuni na yarda da wannan, da ban yadda wannan cikin ya samu ba" murmushi
ne ya suɓuce masa, ta tashi ita ma ta na murmushin, ta fita daga ɗakin har ta
fice ya na daga ruf da ciki ya na kallonta, duk wannan wahalar da yake sha, ko
sau ɗaya bai ji wani abu daga son da yake yi mata ya ragu daga zuciyar sa ba.
***
Nabila ta biya ta ajiye ramma a gida, sai dai ramma ta
fuskanci mama ta sassauta fushin da take yi da ita, saboda ta ɗan samu sassauci
saboda hukunta Abdul da ta ga an yi.
Barrack Nabila ta koma, dan ita kanta ta ɗan tsorata da
musayar yawu da su ka yi da Najar bunkure, dan ta san ba imani ta cika ba, amma
da ta tuna da furucinta na cewar Jinin jauhar ya tafi a banza, sai wani
nannauyan abu ya soki ƙirjinta.
Kusan da ciwon mara ta wuni, daurewa kawai take yi, su ka ci
abincin dare tare da madam Halima, ta na ta ba wa Nabila labarin yadda aka
kashe mijinta, da yadda ta zama soja.
Nabila ta ce "Taɓ sannu da ƙoƙari Mummy"
Madam ta ce "Daughter ke ma fa za ki iya zama sojan
nan, ki zama military lawyer. Ga Mijinki soja na musamman ke ma haka"
Ta kalleta ta ce "Waye mijin nawa?"
"Ahh Viper mana"
Nabila ta ce "Taɓ ba zan iya ba, gara na auri civilian
irina, ni fa idan ki ka ɗauke tsiwa daga nesa nesa, ko gadin ƙofa ba zan iya
balle wani soja, ko 'yar agaji ba iyawa zan yi ba. Da ne da bani da hankali na
ce wa Abba soja zan zama, ya ce ban isa ba, daga baya na fuskanci da na zama
sojan, ba za ayi abin arziki ba"
Madam ta ce "Haba dai, kar ki bayar da ni mana, and
kuma ba soyayya ku ke yi da Viper ba, ba shi ne zai aure ki ba?"
"In ji wa? Mijin sister na ne fa"
"Ehenn your sister is late, and ba haramun bane a
addinin musulunci, soyayya fa ku ke yi ina kallonku"
Nabila ta ɓata fuska ta ce "Mummy ba ki gani dai-dai
ba, ni fa marata ce take ciwo, gashi zuciyata sai tashi take yi kamar zan yi
amai"
Madam ta ce "Sannu, ko za ki je ki kwanta?"
Abu kamar wasa Nabila ta gagara bacci, sai da madam ta kaita
clinic, aka yi mata allurai ta dawo ta kwanta.
Cikin dare madam Halima ta tashi ta na sallar dare, ta din
ga jin ringing ɗin wayar Nabila a falo, ta fito ta kashe, ta ga Vi snake.
Ta ɗaga ta ce "Snake ka ke kiran yarinyata cikin dare
haka me za ta yi maka?"
Viper ya yi murmushi ya ce "Important issue ne shiyasa
na kirata"
"Salon ka hanata bacci, ba ta jin daɗi ne, bamu daɗe da
dawowa daga clinic ba, ta samu bacci menstrual cramps ne yake damunta, ta na ta
ciwon mara ta sha allurai dai, har da kuka dan sangarta. This your wife is not
brave at all, lazy citizen"
Murmushi Viper ya yi ya ce "Thank God ke ki ka faɗa ba
ni ba, ayi mata sannu sai da safe".
"To shikenan sai anjima" ta kashe mata wayar ta
ajiye.
Da safe ta ga Nabila ta shiryo cikin uniform ta ce "Kin
ji sauƙi za ki iya zuwa aikin ne?"
Nabila ta ce "Eh Mummy, da sauƙi sosai"
Ta ce "To Alhamdilillah, come and have your
breakfast".
"I have no appetite, zan samu wani abu na ci, zan haɗu
da Joseph a bakin gate, zan tafi". Suka yi sallama Nabila ta fita.
Babu shari'ar da za ta halarta, dan haka ta na office ɗin
ta, ta na ta aiki, zuwa ƙarfe sha ɗaya na safe, ta ji yunwa ta addabeta, ta
ajiye aikin ta fita.
Ta fita babu daɗewa sai ga Viper ya zo.
Ya tarar ba ta nan, amma yadda ta bar ƙaramar wayarta da
jakarta ya tabbatar masa da ba nisa tayi ba.
Ya ƙarasa gaban teburin, ta ajiye cake ga kofin tea da
madara da milo, da alama tea za ta sha, ya janyo drowern teburin, nan ma ya
iske gugguru da tarkacen alawoyi. Ya girgiza kai, a dai-dai lokacin ta buɗe
Office ɗin ta shigo, hannunta riƙe da leda.
Ta ce "Binciken me ka ke yi mini waye ya baka iznin
shigo mini office ma?" Tayi maganar tana ƙarasawa.
Ya ɗago ya kalleta ta ga idanunsa jawurrr.
"Ba ciwon mara aka ce ki na yi ba, amma ki ke cin
wannan kayan zaƙin?" Yayi maganar ya na tsareta da idanunsa.
"Waye ya ce ina ciwon mara?" Tayi maganar ta na
zaro ido.
"Madam, na kira jiya da daddare ta ce kun je asibiti,
and yanzu kalli tarkacen abin da ki ke ci, ko tausayin kanki ba kya ji. Duk
ranar da ki ka zo haihuwa zaki yi bayanin wannan zaƙin da ki ke ci ba yau ba
gobe saboda basir"
Murmushi ta yi ta ce "Ba sai in zan haihun ba, adopting
ɗin baby kawai zan yi, banda haihuwa dan tsoro nake ji, akwai wahala, idan ma
zan haihu irin ɗayan nan is ok"
"Saboda ke haka aka yi miki? Ko kuma dan ke ki ka tsara
wa kanki rayuwa?"
Ta ce "No ai yarjejeniya za mu yi da babyna kafin mu yi
aure, banda haihuwa" ƙura mata ido yayi, ya na lumshe su a hankali.
Ta ce "Bari na wuce, kai ma sai na sammaka, ko ya aka
yi ma ka san cin zaƙi na saka basir.....
Kan ta ƙarasa maganar ya ce "Am once married"
Ta ce "Eh haka ne, matsa na wuce to, bobon zan sammaka
ko za ka ci gugguru. Wato bincike ma ka yi mini, duk ka kwaso mini kaya, ka
ajiye a kan tebur" tahowa yayi zai faɗo a jikinta, ta ja baya kaɗan a
tsorace. Ya dafe teburin ya na sauke numfashi.
Jiki a sanyaye ta ce "Vi" ya ɗago jajayen idanunsa
a wahalce ya kalleta.
"Again? Me ka je ka sha ne? Na za ta ka daina gaba ɗaya,
sai abin da ba a rasa ba. Ka yi shaye-shaye kuma ka taho hanya ba ka tsoro wani
abu ya sameka? Me aka yi maka ma ka je ka sha kayan maye? Waye ya ɓata maka
rai"
Ya kuma jan numfashin, ya na lumshe ido.
A hankali ya ce "Am so much thirsty, ina shan baƙar
wahala, saboda daina ta'amalli da kayan maye. Idan ƙishirwar shan ta taso mini,
sai na ji kamar zan bar duniya idan ban sha ba, is not that easy rabuwa da
shaye-shaye" yayi maganar kamar zai faɗi ya na lumshe ido.
"Me ka sha?" Ta tambaye shi cikin damuwa.
Fito mata da dogon harshensa ya yi, duk ragowar farin ƙwayar
da ya sha.
Ta ce "Guda nawa ka sha?"
Ya ɗago mata yatsunsa guda uku.
Ya ce "Uku ne kawai, ban sake yi wa kaina allura ba ai,
tun da ki ka shigo rayuwata, ki ka bani ƙwarin gwiwa da tabbacin zan iya sake
rayuwa kamar kowa.
Kin san da ba sa ɗaukata, yanzun ma ban yi tunanin za su ɗauke
ni ba, sai da na zo nan gabanki, kawai su ka fara ɗibata, dole sai sun tona
mini asiri" yayi maganar yana murmushi tare da layi.
Ta numfasa ta ce "Muje ga kujera ka kwanta" juyawa
ya yi yana neman kujerar, ta riƙe hannunsa, har kan kujerar.
Ya hau ya kwanta a kai, ya na lumshe ido.
Ta kalle shi ta ce "Idan ka sake shan kayan maye, sai
na gaya wa 'yar madara, dan ka san ba ta mutu ta barka a kan wannan tafarkin
ba"
Ya ce "A'a Abla"
"Idan ka kuma sha sai na gaya mata, duk ka ɓata mini
rai ban ji daɗin ganinka a haka ba. Kamar ma na yi kuka wallahi"
"Sorry ba zan sake ba in sha Allah" yayi maganar
bacci nannauya ya na kwashe shi.
Ta tashi ta koma kan teburinta, dan cin abinci, ta na yi ta
na gudanar da aikinta, ƙarshe ta ture system ɗin ta kifa kanta ta hau bacci,
domin daren jiya ba ta samu isasshen bacci ba, saboda ciwo.
***
"Yaron nan ya fara bani tsoro, wai tambayata yake yi,
in da P.A yake, ina tsoron kar na je ya san wani abu fa"
"Indabo, ka kwantar da hankalinka, babu abin da ya
sani, kuma babu abin da zai faru, kawai zunzurutun barazana ce"
Indabo ya girgiza kai ya ce "Babu lallai barazana ce,
shegen yaro ne fiye da yadda ka ke tunani. Ga waɗancan asararrun jarababbun
yaran sun sako ni a gaba, yanzu Kanon nake son shiga amma har fargabar hakan
nake ji, amma hakanan zan je na gano Abdul.
Wallahi zaman prsion ɗin Jafar bai ɗaga mini hankali ba,
kamar na Abdul. Gidajen yarin Nigeria da babu gyara, babu kula a haka yaron nan
yake rayuwa, wai a haka an yi masa sassauci saboda wata banzar yarinya,
kodayeke ko ma menene shi ne ya janyo wa kansa ai"
Mutumin ya ce "Ka yi haƙuri distinguish, yaran namu ne
ka haife su, amma ba ka haifi halinsu ba, kuma duk kankarofi ne kanwa uwar
gami, tun da shi ne yake amfani da ƙarfin ikonsa, ya hana ruwa gudu ko ta ko
ina"
Cikin takaici Inadabo ya ce "Could you imagine Alhaji
Sada, yaron nan kuɗin da ake tuhumar nan tawa a kai, ware su aka yi saboda
campaign ɗin sa, amma saboda sakarci wai ya tattare kuɗin a kan tsinanniyar
yarinya 'yar ƙauye, kuma hakan bai yi musu ba, sai da suka kai shi gidan yari,
har da duka. Shi kansa alƙalin ba zan bar shi ba dan uwatar. Wani baƙin ciki da
takaici da maimuna take gaya mini, wai yarinyar ciki ne da ita, ta cewa Abdul a
zubar wai ba za a zubar ba, gaba ɗaya mutuncina da kimar siyasata ya zube, ban
da Abdul ɗa na ne, da sai na yi masa aiken da babu dawowa. Amma ina nan ina
shiri, Sai an kashe banzan yaron nan Viper, duk wata fitina shi ne yake ƙara
kunnota. Gashi yarinyar nan 'yar jarida twins ɗin matarsa ce, daga rahotannin
da na samu. Shiyasa farkon ganina da ita na tsorata, na saka aka yi mini
bincike a kanta, amma gaba ɗaya nasabarta ba ta yi alaƙa da shi ko waccan matar
ta sa da aka kashe ba. Saboda mugun rainin wayo, shi ma wancan wawan, wai ya na
bincike amma a gidansu yarinyar na haɗuwa da Viper bai sani ba, shi ma sai na ɗauki
mataki a kansa"
Honorable Sada ya ce "Duk dai ka yi haƙuri ka kwantar
da hankalinka, ai mun gama shirya komai, aiwatarwa ce ta rage. Kuma muna da
tabbacin za a sami mafita"
Indabo ya jinjina kai da alamar gamsuwa da maganganun
honorable Sada.
***
Barrister Habib ne ya shiga office ɗin Nabila, ya tarar da
Viper a miƙe a kan kujera ya na bacci, Nabila kuma ta kifa kai ta a kan tebur
ta na bacci.
Gaba ɗaya sai ya ji babu daɗi, wani irin matsanancin kishi
ya na taso masa, duk da ya san ko da me yake yawo, Viper ya fi ƙarfin yayi
takara da shi, duk haryanzu bai gane in da suka dosa ba, daga ita har Vipern,
amma kusancinsu yayi yawa.
Ya ja da baya ya mayar da ƙofar ya rufe, ya na rufewa Viper
kuma ya buɗe idonsa, ya bi ƙofar da kallo, ya mayar da idonsa kan Nabila da
take baccinta a nutse, kamar ta samu gado.
Ya daɗe ya na kallonta, sak 'yar madararsa yake gani, duk da
akwai tarin banbancin halaye tsakanin Nabila da jauhar, amma akwai abubuwan ta
da suke burge shi, she's very straightforward, very silly and arrogant.
A hankali ya tashi ya kalli agogo, ya fice yaje ya yi salla,
har ya dawo Nabila bacci take yi, kodayeke ba abin mamaki bane ba, ko lokacin
da yana tare da jauhar, idan tana period kamar mai laulayin ciki, bacci
ciye-ciye da saurin kuka.
Ya daddaki teburin da ta kwantar da kanta, amma shiru ba ta
motsa ba, "Ke wani daren za ayi miki ne?" Still ba ta motsa ba.
Bayanta ya zagaya ya ja kujerar da take kai baya kamar za ta
faɗi, razana tayi tare da yin wani ɗan marayan ihu.
Ya ƙura mata ido ya ce "Ki tashi haka mu yi maganar da
ta kawo ni"
"Na ji amma ka ajiye ni mana kar na faɗi"
A hankali ya mayar da kujerar, amma ya sunkuyo ta bayanta
dai-dai kunnenta, kamar zai yi magana, sai kuma yayi shiru, ta din ga jin
saukar numfashin sa a jikinta.
Kame jikinta tayi, ta ce "Bari na wanke fuskata, sai mu
yi maganar" ta tashi ta nufi toilet.
Ta dawo ta zauna ta kalleshi ta ce "Ka watstsake?"
Ya ɗaga mata gira.
Ta ce "Alright, ina jin ka, meyafaru?"
"Inadabo ya kira ni jiya, kuma tabbas tun da ya kira
ni, akwai abin da ya taka yake jin ƙwarin gwiwa, har ya kira ni, amma menene
shirinki ke yanzu?"
Nabila ta jinjina kai ta ce "Alhamdilillah, dai-dai
gwargwado muna da abin da ya sauwwaƙa, Bunkure na ta dragging ne to sai ta faɗi
ɓarnar da ka aikata a baya"
"Nabila ba fa zan koma prison ba" yayi maganar
very serious.
Ta waro ido, sai kuma ta ɓata fuska "Nabila kuma
garangatsau ba Ablan"
"Am very serious, kin san masifar gidan yari, ba fa zan
koma ba"
Nabila ta ce "Easy, in sha Allah ba abin da zai mayar
da kai prsion, amma Vi"
Ya kalleta. Ta kwantar da murya ta ce "Ina ganin
yakamata mu fara zuwa kana ganin likitan ƙwaƙwalwa sab...
Haɗiye maganar ta yi, saboda ganin kallon da ya yi mata.
"Kallon mahaukaci ki ke yi mini kenan?"
Da sauri ta girgiza kai ta ce "No, ba kallon mahaukaci
nake yi maka ba, za su taimaka maka ne, ka daina ta'amalli da kayan maye gaba ɗaya,
tun da ka na trying kai ma, za su taimaka maka, zuwa wurin likitan ƙwaƙwalwa ba
ya na nufin mutum ya haukace bane ba".
Shiru ya yi yana kallonta. "Please Vi, kar ka ce A'a
zaka iya daina shaye-shaye gabaki ɗaya, idan muka dage da zuwa wurin likitoci,
dan Allah kar ka ce A'a ka ji"
"Ba zani ba"
"Dan girman Allah, kar ka yi mini haka ka taimaka dan
Allah, ka ji Vi, na jinjinawa ƙoƙarin da ka yi, na rage kaso mafi rinjaye a
shaye-shaye, amma za su taimaka maka, dan Allah ka yarda mu je"
Tashi ya yi tsaye, ya ce "Tashi mu tafi" ba ta
sake yi masa maganar ba, suka tafi.
****
Sanarwa ce ta fita, na ɓatan P.A ɗin Indabo, nan da nan da
taimakon Sumayya, da murtala, aka cigaba da yaɗa ɓatan nasa babu ƙaƙƙautawa,
kamar yadda Viper ya nemi su yi hakan, ta hannun Nabila.
A yau ma kotun a cike take da ɗan Adam, domin kuwa daga
cikin shari'un da suke ɗaukar hankali, har da ta Amini Viper.
Viper ya zama shaida na ƙarshe da Nabila za ta gabatar wa
kotu.
Ya fito ya tsaya, Nabila ta tsaya a gabansa, ta jinjina masa
kai alamar ƙwarin gwiwa.
Ta numfasa ta ce "Malam Al'amin, ko zaka iya bayyana wa
kotu, abin da ya faru a ranar da ka ke zargin waɗan nan mutanen da shiga
gidanka, su kashe maka mata" Tana kai maganar ya tari numfashinta da
"Ba zargi nake yi ba na tabattar"
"To meyafaru?"
Ya yi ajiyar zuciya ya ce "Ina kwance na fara jin motsi
a saman katanga, na taso na fito falo, aka haske ni da fitila. Na tambayi waye,
ba na iya gane suwaye, sai gilmawar mutane, na ji an daki ƙafafuwana da wani
abu mai nauyi.
Kafin na yinƙura, na ji tsinin allura a wuyana, na yinƙura
zan kuma tashi, aka daki ƙafafuwana, suka daddane ni, su ka ɗaure mini
hannayena da ƙafafuwana.
A lokacin Madaki ya sauke takunkunmin fuskarsa, da shi da
lakwari, na kasa motsi, gaɓoɓina su ka fara sanyi.
Idona biyu amma na kasa motsa ko ina a jikina, a dai-dai
lokacin matata jauhar ta fito. Bayan yi musu magiyar su rabu da ni, Madaki...
Sai kuma ya yi shiru, ya na haɗiyar yawu.
Nabila ta jinjina masa kai alamar ya cigaba.
Lakwari ya riƙe gashin kanta, Madaki ya hankaɗata, Madaki
kuma ya sanya mata ƙafarsa, ta faɗo a kan cikinta. Su ka buga mini a kaina daga
nan ban sake sanin meyafaru ba. Ya ƙarasa maganar a sanyaye.
"Ka tabattar ka ga mutuwar jauhar?" Ya jinjina kai
alamar eh.
Nabila ta kalli alaƙali ta ce "Ina fatan wannan kotu
mai adalci, za ta yi duba da shaidu da hujjojin da mu ka gabatar, ta tabbatar
da adalci wurin hukunta ma su laifi"
Aka waiwayi bunkure, kan ko ta na da abin cewa, ta tashi ta
ta ce ta na da tambayoyi ds za ta yi wa Viper.
Ta zo gabansa ta tsaya, ta kalleshi ya kalle ta, ta yi
murmushi ta ce "Al'amin, binciken jami'an tsaro da ya gabata a kan kisan
matarka, sun tabbatar da cewa, kai ka sha kayan maye, ka halakka matarka da
hannunka, amma sai gashi ka na zargin wasu da shiga gidanka su ka kashe
matarka"
Ta sake kallonsa a tsanake ta ce "Ka na ta'amalli da
miyagun ƙwayoyi, eh ko a'a?" Viper ya yi shiru ya na bin idonta da kallo.
Nabila ta nemi a dakatar da Bunkure, saboda ƙoƙarin sanya
Viper amsa laifi ta ƙarfin tsiya, sai dai ba a karɓi ƙorafin ba, aka ce ga ci
gaba.
"Ko ba ka amsa da bakin ka ba, amsar eh ce.Ya mai girma
mai shari'a duniya kowa ya shaida Al'amin Viper ko in ce mai zamani,
gawurtaccen ɗan daba ne da ya gagari al'umma, har a bayan tserewarsa daga gidan
yari, ya ci gaba da aikata miyagun ayyukansa, na sara suka da dillancin miyagun
ƙwayoyi".
"Objection my lord, barrister Naja'atu ta na kare waɗanda
ake zargi ne, ko kuma ɗorawa mai ƙara laifuka da hanyar karkatar da shari'ar
kan wani abu daban".
Aka gargadi Naja'atu Bunkure, ta ɗaukko wani file ta ɗaga ta
ce "A bincike da yan sanda su ka tattara, akwai binciken likitoci, da
gwaje-gwajen da aka yi masa bayan mutuwar jauhar, wanda a jininsa aka gano
sinadarin wata allura, da ake amfani da ita a asibiti, wadda sai da matakai
masu tsauri ake amfani da ita. Bayan haka akwai sauran ƙwayoyin da aka gano
sinadaransu a cikin jininsa, wanda hakan yake tabattar da shi ya sha ya bugu,
ya kashe matarsa da kansa. Da wannan nake roƙon kotu ta wanke waɗanda ake zargi,
a hukunta wanda ya aikata laifin"
Tsit kotun tayi, wani irin gumi ya tsatstsafo wa Viper, ba
shi ba hatta su Walid, sun shiga cikin matsanancin tsoro da fargaba, ga su Abbu
da mama hatta Alhaji mu'azzam da duk wani majiɓancin shari'ar, suka shiga cikin
damuwa da tashin hankali.
Nabila ta kalli Bunkure, Bunkure ta kalli Nabila tana
murmushi.
Nabila ta ce "Zan so kotu ta banu dama, na gabatar da
doctor Muktar sharfaɗi"
Aka ba ta dama, sak Viper ya yi, ya na tunanin shi kuma me
doctor Muktar zai yi a nan.
"Doctor ka gabatarwa da kotu kanka"
"Sunana doctor muktar sharfaɗi, ni ne likitan da na
duba marigayiyya jauhar, na tabattar da inducing ɗin ta za a yi a asibitina,
kuma ni aka samu na tabattar da mutuwarta a asibitin gwamanti na shiga asibitin
safe.
A report ɗin da na bayar, babu duka a jikinta ko kaɗan, faɗuwa
ce, ta rasu ɗan cikinta ma ya mutu.
Sai dai zan yi wani karambani, ban san wane irin bincike
barrister ta yi akan allurar da take magana a kai ba, wannan allura ta na fara
aiki ne mintuna biyar zuwa bakwai da yin ta, kuma tana tafiyar da ji da gani da
consicous ɗin mutum gaba ɗaya, babu yadda za ayi wanda ya yi amfani da wannan
magungunan ko alluran, ya iya sanin meyake yi, har ta kai ga ya yi kisan kai,
kashe jiki suke yi gaba ɗaya Banbancin mutum da matacce numfashi ne kawai"
Nabila ta numfasa, ta je gaban teburinta, ta ɗaukko wata
envelope ta fito da wasu hotuna, ta ɗaga su ta ce "Mai girma mai shari'a,
waɗannan su ne hotunan farko da jami'an tsaro su ka ɗauka, bayan ƙorafin da
maƙwabta su ka shigar, na cewar sun ji ihun jauhar cikin dare, wayewar gari
kuma sun yi ta bugu ba a buɗe gidan ba.
Idan aka yi duba da hotunan, Al'amin kwanciyar da yayi ruf
da ciki, hannayensa a kan gadon bayansa, ya na nuni da cewa tabbas ɗaure shi
aka yi.
A wannan hoton kuma, idan aka duba wurin ƙafafuwansa
kasancewar ba dogon wando ne a jikinsa ba, akwai shaidar an yi traumatizing
wurin, akwai alamar shaidar ɗauri a wurin.
Idan har binciken jami'an tsaro dai-dai ne, kamar yadda
Barrister Naja'atu ta faɗa, to ya tabatta toxicating ɗin Al'amin aka yi aka
kashe matarsa.
Idan kuwa har shi ne ya kasheta, zai iya zama tsautsayi ne,
dan idan niyyar kasheta ya yi, zai daketa ne, ko jikinta ya nuna wani nau'i na
cutarwa. Amma daga bayanan doctor Muktar, da hotunan da na gabatar, ina fatan
Al'amin ya fita daga zargi, kuma za ta hukunta waɗanda suka aikata laifin"
Da ido kawai Viper ya din ga bin Nabila, dan bai san yadda
aka yi duk ta tattara waɗannan shaidun da hujjojin ba, sai a yanzu ya ƙara
jinjinawa basirarta da hangen nesa.
Alƙali ya yi rubuce-rubuce Alƙali ya ɗauki lokaci ya na yi,
daga baya ya ce ya sake ɗaga shari'ar zuwa wata guda, domin yin zama na ƙarshe
domin yanke hukunci.
Kamar wata celebrity, haka Nabila ta fito daga cikin kotun,
su Abba suka kewaye ta, kowa ya na tofa albarkacin bakinsa, su na jinjina wa
ƙoƙarin da ta yi.
Viper gefe ya koma ya tsaya ya na kallonta, yadda farinciki
ya mamaye fuskarta.
Sumayya ta saka mata abin magana, ta na tambayarta, yaya
take ganin gudanawar shari'ar.
"Babu abin da zamu cewa Allah sai godiya, muna sanya
ran samun adalci, a wannan shari'ar".
Hatta su liti ma, kasa ɓoye farincikin su su ka yi.
Viper bai tsaya ba, yau ma saboda Abbu ya na wurin, ba ya
son duk abin da zai haɗa shi da shi.
Daga nan duk su ka watse, Baba ya na ta son lallaɓa Nabila
ta dawo wurinsa, amma yadda ta nuna ba ta so, ya sanya ya ƙyaleta.
"Thank you very much, for standing by my side, and show
me way, to live another life as a different person, a really appreciate Abla,
thank you once again take care. Al'amin"
Murmushi ne ya suɓuce mata, sai kuma ta ɗan tsuke fuska a
hankali ta furta "Alaƙarmu za ta zo ƙarshe, da zarar na kammala wannan
shari'ar"
Ayshercool
08081012143
Duk da abin da ta ƙudurce a ranta, amma ta karanta message ɗin
nan, ya fi sau ashirin.
Haryanzu tana tantama a kan hukuncin da ta ɗauka, na rabuwa
da shi da zarar ta kammala shari'a, amma itakaɗaice mafita a ganinta, saboda ta
na ganin soyayya da Viper tamkar cin amanar 'yar uwatta ne, babban abin da za
ta yi, a matsayin ba ta santa ba, shi ne ta tabbatar da an ƙwato mata hakkinta,
kuma an wanke Viper daga zargi.
Viper kuwa su na tafe, Liti ya yi wani irin ihu, ya ce
"Kan uban nan, yarinyar nan ta yi bala'i, ashe haka kanta yake ɗaukar
wuta, kamar me. Kai ka ga wata karakaina da shige da fice da ta yi, ashe ta san
abin da take yi"
Ɗan mama ya ce "Oga liti, ka manta lokacin da ka din ga
korarta, Allah ne ya sa Oga walid bai yi saurin korarta ba, ya bari ta ci gaba
da zuwa, ina ga a wannan gaɓar babban yaya za mu sarawa, Mikiya mai hangen
nesa, amanar Oga Viper kuma babban yayan marigayiyya, an buga da kai an
barka"
Walid ya yi murmushi, ya ce "lokuta da dama, abin da
haƙuri bai bayar ba, akasinsa ba ya bayarwa. Kai yanzu da mun koreta, da idan
Allah ya ƙaddara za ta tsaya masa, sai mun je mun nemota, idan kuma lauya zamu ɗaukar
masa babu lallai mu samu yaƙinin ba za a saye shi da kuɗi ba ya cutar da mu ba.
Wallahi hardwoker ce Nabila, gashi babban abin da yake
burgeni da ita da Jauhar, sun iya kwantar da kai, su yi galaba a kan abu,
Nabila ba ta da tsoro da ni wani ne, sai na karrama yarinyar nan. Kuma kai
yanzu ka ji kunya, irin abin da ka din ga yi mata"
Liti ya ce "Na ji ɗin, amma duk da haka ai ba ta da
kunya muguwar fitsararirriya ce"
"Liti ka daina rinjayar da laifukan mutum a kan
alkhairin sa mana, kowane ɗan Adam tara yake bai cika goma ba. Ita jauhar ɗin
ce maka aka yi ba ta tsiwa, ka tambaye shi ka ji to, ba ta yi wa kowa amma ta
na yi masa, ko ƙarya nayi?" Yayi maganar yana kallon Viper.
Viper ya yi murmushi ya na tuna yadda ya sha jifa da kwanuka
a hannun Jauhar.
Nabila kai tsaye take abubuwan ta, babu ɓoye-ɓoye ko kara,
Jauhar kuwa cikin ruwan sanyi, a ɓoye take ladabtar da shi.
Walid ya ce "Ko ma yaya ne, ni Jauhar tawa ce, Nabila
ma haka, kowacce ta taimaki rayuwarmu. Ba dan Allah ya kawo Nabila ba, da tuni
mai zamani ya samu taɓin hankali, ko kuma ya kashe kansa, kalli yadda muka din
ga fama da shi, saboda yi wa kansa allurai. Amma tana faɗowa rayuwarsa, ta
saita shi, kai ba iya lauya ba ce ba, har role ɗin likita tayi playing, kalli
multiple attempts na kasheta, da intimidation da ta din ga fuskanta, amma ta
dage ta jure, ko yau ta barka, ta biya Jauhar ina yin ta sosai, ina yi mata
fatan iyayenta su samu fahimtar juna, ita ma ta samu nutsuwa, a zo ayi bikinku
mu huta" yayi maganar yana kallon Viper da bai ce uffan ba.
Liti ya ce "Ba wani nan, ba fa zai sake yin aure ba,
kawai ya haƙura ya shiga ittikafi da yi wa addini hidima har ƙarshen rayuwarsa,
saboda wani takaici nake ji, idan na ji an yi zancensa da wata ba jauhar ba.
Dama ba damuwa yayi da wata sabgar mata ba, zai iya lallaɓa
rayuwarsa a haka, ko mai girma Al'amin" Kawar da kai Viper ya yi yana
dariya, iya shege ɗan liti yake ji, wai ya shiga ittikafi.
***
Yau aka ɗaukko ɗan uwan ramma Sani daga makarantar kwana da
yake yi a Dutse, kamar su haɗiye juna da shi da ramma.
Ya ce "Yaya na kasa gane yaya ki ke ma, rama ki ka yi
ko ƙiba, kin wani goge, ashe zan ƙara ganinki, nayi kuka sosai har na fid da
ran sake ganinka ma"
Tayi murmushi ta ce "Nayi kewarka sosai da sosai da kai
da mama, na yi kuka iya yi na, ban taɓa zaton zan sake ganinku ba, amma
Alhamdilillah ala kulli halin, ya makarantar?"
"Lafiya ƙalau, ni fa kusan shekara ban dawo kano ba,
idan an yi hutu a gidan wani abokin honorable nake zama, wanda ya saka aka kawo
mu nan aka ajiye, wannan karon na saka aka roƙe shi tun da an ce mini an ganki,
kin ga kayan alatun da ake bani ramma, A dalilinki kalli daɗin da muke ciki, da
muna ƙauye muna fama har da cin dafaffiyar tafasa mun sha wahala sosai"
ramma tayi murmushin yaƙe.
"Yaya bayan tafiyarki fa, kin ga kwaltar da aka shimfiɗa,
tun daga tasha har cikin tofa an yi tituna aka gyara makarantu, amma dai kin je
ƙauye ko da ki ka fito, kamar yan birni, har da fitilun sololi aka saka mana,
ga ruwa"
Ramma ta girgiza kai ta ce "Ban je ba, tun da na fito
ina nan" Suka din ga hira da ita. Dawowar Sani, ba ƙaramin daɗi ta yi wa
ramma ba, sosai yake zama su yi hira ya saurareta, saɓanin mama da yanzu
sama-sama take da ita.
Shi dai tun yana kallon ramma, yana mazewa har ya magantu ya
ce "Yaya wai aure ki ka yi ne da gaske, kamar yadda kawunmu ya ce ya aurra
da ke?"
Ta kalleshi ta ce "Me ka gani?"
"Gani na yi kin kusa haihuwa" ya bata amsar da ta
kusa sanyata nutsewa, yanzu duk ɓoye-ɓoyen nan da take yi, sai da Sani ya ga
cikin nan.
Ta ce "Eh da gaske ne"
"Ikon Allah, to ina mijin naki yake, ni gaskiya ban so
yayi miki irin wannan auren ba, na ci buri da yawa a kan aurenki"
Ramma ta katse hirar, ta ce masa za ta je ta kwanta, bacci
take ji.
Ta je ta haye kan gado ta kwanta, ta din ga kallon ɗakin,
duk albarkacin abin da ya faru da ita ne, ta samu wannan ni'imar, da tana
rayuwa a ƙasƙance cikin talauci, amma yanzu tana cikin ni'ima duk da ƙaddarar
da ta kawota wannan bugiren ba irin wadda ake fata ba ce.
Ta ji yadda abin da yake cikinta yake motsawa, ta shafi
cikin a hankali, tana tunanin Abdul.
Da tunanin halin da yake ciki yanzu, ko ciwonsa ya warke
Allah masanin gaibu, dan ba ta da wata hanya ta ganinsa, idan ba Nabila ce ta
wayance da kaita awo, ta kaita wurinsa ba.
***
Nabila ta halarci program ɗin su, da su ka saba yi da
Sumayya, Sumayya ta din ga yi mata tambayoyi a kan shari'ar da take gudanarwa
ta Viper, nan Nabila ta din ga fito da wasu bayanai da mutane da yawa ba su san
da su ba, iya abubuwan da suka ji a kan sa a bakin Mutanen gari, da na jamu'an
tsaro kawai da shi suke amfani su yi masa hukunci.
Har tarihin yadda ya shiga daba a dalilin kisan ɗan uwansa
da rashin ɗaukar mataki, sai da ta bayar, duk da ta ɓoye duk wani abu da ya
shafi familynsa.
Abbu yana tafe a mota, yana driving yake sauraren shirin,
sai tsananin mamakin abun ya kama shi, mussman ɓangaren shekara biyar da ya yi
a prsion, ba tare da an yi masa shri'ar ba, aka sake shi, kuma aka koma wai ana
nemansa wai an sake shi ba bisa ƙa'ida ba.
To zaman me ya yi na shekara biyar ba ayi masa shari'a, a
ƙaddara yanzu a yanke masa hukuncin laifinsa, da lissafin waccan shekara biyar ɗin
za ayi, ko banda ita? Haka ya tafi gida, ya na ta lissafi daban daban a cikin
zuciyarsa.
Ji yayi kamar ya nemi Nabila, amma sai ya rabu da ita, gaba ɗaya
topics ɗin da suka yi discussing sun ɗauki hankalinsa sosai da sosai, tare da
mamakin yadda fannin shari'a da tsaro ya lalace ya taɓarɓare da cin hanci da
rashawa, kawai wa ka sani waye ya sanka.
Maganganunta suka ci gaba da ɗaukar hankalinsa, da take kira
ga iyaye, da al'umma da hukumomi su guji watsi da yaransu dan suna rashin ji,
idan yaro yayi laifi, iyaye su bar hukuma ta hukunta shi, idan an sako shi, su
rungumi abin su, su ci-gaba da addu'a da yi musu nasiha, ta din ga bankaɗo
illar da watsar da yaron da ba ya ji da iyaye suke yi, a waje kuma su samu mai
rungumar su, komai munin halinsa dole su yi masa biyayya.
Gaba ɗaya Abba bai taɓa tsammanin Nabila ta na da hankalin
da za ta yi bayanai masu muhimmanci har haka ba.
Jikin Nasir ya fara sanyi, mussman yadda ya ga ko ina zancen
Nabila ake yi, da yadda shari'a ta fara karkata, ƙoƙarin haifar da abin da bai
yi tsammani ba.
Abba ya samu Nasir a gida, ya ce "Nasiru, ka ji program
ɗin Arfa kuwa?"
Ya ce "A'a Abba, meyafaru?"
"Maganar yaron nan ɗan daba da ta ƙallafa ran kare shi,
alamu fa sun nuna kamar yana da gaskiya. Koma dai ba shi da gaskiya, akwai
zalunci a cikin abin da aka yi masa".
Nasir ya ce "Haka ne, amma duk da haka mu jira a kai
ƙarshen shari'ar, tun da yana da iyayen gida, maybe akwai masu tallafa musu har
da Nabilan a kan shari'ar"
Abba ya ce "Haka ne, amma duk da haka, ɓangarorin
shari'a a ƙasar nan da gyara, yaya za ayi a ajiye mutum shekara biyar babu
Shari'a, to zaman meyake yi ba a yanke masa hukunci ba? Kai Allah ya
kyauta" duk jikin Nasir ya bi yayi sanyi.
*****
Viper yana ta son ya kira Nabila, amma bai san me zai ce
mata idan ya kirata ba, dan haka ya din ga jujjuya wayar, yana kallon lambarta.
Babu tsammani, ya kalli liti ya ce "Abdallah"
"Na'am mai zamani"
"Yaushe rabonka da gida ne?"
Jin tambayar yayi wani iri, "Kusan shekara ɗaya da
rabi"
"Yakamata ka je ka gaishe su, mussaman kai da iyayenka
suke a raye, ba kamar ni da Walid ba".
Liti ya ce "Kai ma ai Abbu yana da rai"
"Ina magana kana mayar mini?" Viper yayi maganar
yana tsuke fuska.
"Easy maza, ni wallahi wannan munafukar tsohuwar ce ta
saka na daina zuwa gidan, tayi ta hantarata tana ziga Alhajinmu, shi ma fa
korata yayi, maminmu na kallo, ba ta ce komai ba. Ai ni da gidan nan idan ba
wannan algungumar tsohuwar ce ta baje tayi bacci ba, gaskiya na daina zuwa, ga
tsinuwa da take yi mini, dan ma Allah ya sa Alhaji ta haifa ba ni ba, da sai na
kwashe ƙasusuwan ƙafarta na watsar da ita"
"Yakamata mu buɗe wani sabon babi na rayuwa ne
Abdullahi, mu gyara wasu daga cikin kura-kurai waɗanda za su iya gyaruwa, akwai
yiwuwar idan mu ka yi nasara a kotu, na koma can kudu da aiki, koma na bar
ƙasar gaba ɗaya, ba zan taɓa tafiya na bar ku ba tare da wani ƙwaƙwƙwaran
madogara ba"
Walid da tun ɗazu yake wanki bai ce komai ba, ya ce
"Aikin me ka ke yi wai? Kuma meyasa zaka tafi kudun?"
Viper ya yi murmushi ya ce "Zan yi muku bayani a gaba,
amma dole muje ka gaida iyayenka, ka ba su haƙuri liti"
"Dan Allah maza ka bar zancen nan, nima fa yakamata su
nemi yafiyata fa, mussman algungumar tsohuwar nan"
"Ba zaka daina ce mata algungumar nan ba ko?"
Liti ya ce "Saboda fa Alhaji ya yi mata biyayya ta saka
ya kore ni, wai zan lalata mata sauran jikoki, lokacin ma fa ba wani nisa nayi
a shaye-shaye ba, amma wani ƙanin babanmu ya ce wai alhakin yaransu ne, da
babanmu bai haɗa da su, ya kai ƙasar waje karatu ba, shegu kamar su suke tara
masa kuɗin. Ni Allah yasa ma ba asiri suka yi mini na je na dawo ban iya komai
ba, sai holewa"
Walid ya ce "Ko ba komai, ai ka hau jirgi"
Liti ya kwashe da dariya ya ce "A banza amma"
Ɗan mama ne ya faɗo cikin gidan, suka kalle shi gaba ɗaya,
liti ya ce "Menene kuma?" Yayi tsuru-tsuru yana kallonsu.
"Kai dalla menene wai?"
Ya numfasa ya ce "An kashe brothern Viper, wannan na
gidan na su Abba" sai da Viper ya zabura, ya kalli Ɗan mama ya ce
"What? How?"
Ɗan mama ya ɗan girgiza kai ya ce "Faɗa su ka yi da
wasu a can unguwar bello wai a kan kare, shi ne suka ƙyale shi, sai da ya dawo
daga yawon cajinsa, suka sassara shi, suka saka shi a buhu, suka kai shi gefen
Black ocean kududdufin nan na cikin unguwa suka watsar. Ashe kwana uku ana
nemansa ba a ganshi ba"
Miƙewa Viper ya yi, jikinsa yana tsuma, kamar zai fita daga
hayyacinsa ya ce "Yaushe ya fara shaye-shaye har yake bin yara marasa ji?
Kuma jiya a kotu, ban ga alamar akwai Matsala a tare da Abbu ba"
Ɗan mama ya ce "Taɓ ai an kwana biyu, yana zuwa rumfar
shayinmu, wurin su ɗan kada ai, yana shaye-shaye".
Takalmansa ya shura zai fita, cikin matsanancin tashin
hankali, Walid ya riƙe shi, ya ce "Ina zaka je?"
"Meye haka, cika ni mana na je na ji meyake faruwa?
Kuma suwaye suka yi masa wannan zaluncin"
Walid ya ce "Babu in da zaka je, a sabga irin tamu, duk
wani ɗan gang, ya san irin haka na iya faruwa da shi, muddin bai tuna ba, ko ma
mutum ya tuba, ko a kashe ne ko kuma a kashe shi"
"Walid, Abba ba zai iya daba ba, ina ganin shaye-shaye
kawai yake yi, wane irin kisan zalunci ne wannan da rashin imani? A sassara
mutum a zuba a buhu aje a zubar?"
Liti ya ce "Ni ku matsa mini, na yi sujudar godiya ga
Allah, gabasa ake kallo ko daga nan Arewa ma zan iya yin ta? Daɗina da kai wasu
lokutan kana da wani ɓoyayyen rauni, da ya kan kusa cutar da kai Viper. Matar
da ta rufe muku ƙofa, aka hallaka ɗan uwanka, shekarun da suka gabata, sharrin
da ta aika ne, ya dawo mata kanta a kan ɗanta ita ma, cin amanar da ta yi, ita
ma Allah ya ɗanɗana mata, Allah Allah ne, dan haka babu ruwanka".
"Liti kai mahaukaci ne? Ko kaza aka kashe wa mutum bisa
zalunci, abin tashin hankali ne, mai rai a sassara shi, a saka a buhu, a kai a
yar fa"
Walid ya ce "Yanzu idan ka je gidan me zaka yi musu?
Salon ta ce kai ne ma ka saka aka kashe shi, ka san halinta ai, babu in da zaka
je, taje Allah ne ya kamata".
Fafur suka hana Viper fita, ya koma cikin ɗaki, ya ɗaukki
wayarsa ya kira Nabila.
Ta ɗaga tayi sallama ta ce "Vi ya ne?"
"Amm ki tambayi ƙawar nan taki Sumayya, ko labarin
kisan da aka yi wa wani yaro Abba a unguwarmu, ya je mata dan Allah ina son a ɗan
bikcika".
Ta ce "Subhanallah, ban sani ba, bari na kirata na
ji"
"Yauwwa yi sauri, dan Allah idan gaske ne, Joseph ya
kai ku station ɗin da case ɗin yake hannunsu, ku jiyo mini ya ake ciki?"
Ta ce "An gama ranka ya daɗe, amma ya sunan wanda aka
kashe ɗin?"
"Ɗan matar Abbu ne, sunansa Abba idan ya kama ku je
gidanmu, ku ƙara tabattar mini".
Mamki ya cika Nabila, amma ta ɓoye mamakin nata ta ce
"In sha Allah zamu je" ya katse wayar cikin matsanancin jimami.
Walid ya ce "To wai meye amfanin hakan da ka yi? Meye
naka a ciki Viper?"
Al'amin ya girgiza kai ya ce "Yaya ku ke abu kamar ba
tsoffin 'yan hannu ba? Yanzu faɗan ɗaukar fansa zai ɓarke a tsakanin
unguwannin, kuma ina gudun abin da ya faru da ni, ya sake faruwa a kan wani,
ina son na bibiyi abin a kama waɗanda suka kashe shi, na tabattar da an hukunta
su, domin ya zama izina. Kuma ko ba komai, musulmi ne, kuma mahaifina ne ya
riƙe shi, an yi masa kisa mai muni, abin da taɓa zuciya"
Sai kuma suka yi shiru, liti ya ce "Haka ne, maganarka
dutse, amma gaskiya ba zaka je ba, ba ruwanka daga nan kayi masa addu'a, idan
komai ya lafa sai a san abin yi"
Viper ya ja tsaki, tare da girgiza kai.
Walid ya ce "Menene kuma?"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Walid, babu wani alfanu ko
jin daɗi a rayuwar daba da shaye-shaye, duk kalle mu dai, babu wanda wannan
rayuwar ta amfana da komai, face tabon baƙin ciki da tsantsar nadama. Akwai
tarin ƙalubale, muddin za a ci gaba da tafiya a haka"
Walid ya ce "Haka ne, sai fatan Ubangiji Allah ya yafe
mana ya shiryar da mu baki ɗaya".
Kamar yadda Viper ya buƙata, Nabila tare da Sumayya, suka
tafi binciken da ya ce, jami'an tsaro suka tabbatar da faruwar Al'amarin.
Sumayya ta je har gidan su Viper, kamar sai dai ba su tafi
tare da Nabila ba.
A rumfar zaman makoki, ta hangi Abbu, ta ƙarasa tayi musu
gaisuwa, Abbu ya taso, suka sake gaisawa, ya ce "Sumayya ya aka yi
ne?"
"Nabila ce ta kirani, Viper ya ce lallai mu zo a
tabattar da abin da ya faru, ban san dai dalilinsa na yin hakan ba"
Ya ɗan yi shiru ya ce "Shi da kansa?"
Ta ce "Eh" nan ya sake yi mata bayanin abin da ya
faru, maganar da yake yi mata ma, mahaifiyarsa na Asibiti allurar bacci kawai
ake yi mata, tamkar zata haukace, saboda yadda aka kawo gawar Baba, jikinsa ya
fara zagwanyewa, jikinsa ko ina sara, hannunsa ma daban aka kawo shi.
Sumayya ta tattara rahoton abin da ta samu, ta sanarwa
Nabila, kuma ta samu na sanarwa a gidan rediyo.
Sosai batun ya ɗauki hankalin jama'a, Duk ita kanta Nabila,
sai da ta ce Alhakin Viper ne, amma ta kaɗu matuƙa jin irin kisan tozarcin da
aka yi wa Abban duk a silar ƙwaya. Kamar yadda ta wallafa a shafinta, suna nan
suna zuba ido, su ga matakin da jami'an tsaro za su ɗauka, wurin cafke waɗanda
suka aikata laifin.
****
Rahila dai abin da ya samu Abba ya zame mata masifa, ta
daina magana ta daina cin abinci, ba ta gane kowa sai kuka, idan aka jima kuma
ta yi ta kurma ihu, tana kururwa tana kiran ɗana Abba, Abba bai mutu ba, sai
dai a daddaneta ayi ta yi mata allurar bacci.
Haka Shahida zata rungumeta, tayi ta kuka, ga Amira ta
shilla ta yi nata wuri, tun da Abbu ya ce ba zai karɓeta a gidansa ba.
*****
Yau da yamma Viper ya je barrack wurin Nabila, sai dai tun
kafin yayi magana, ta fuskanci matsananciyar damuwa a tattare da shi.
Ta ce "Vi meyafaru ne?"
"Abin da ya faru da yaron nan Abba ne ya yi bala'in
tsaya mini Abla"
"To yaya za ayi, sai addu'a, amma in ganin kamar har da
hakkinka abin da ya same su"
Viper ya girgiza kai ya ce "Ba na tunanin haka, haka
kurum abin ya tsaye mini. Shikenan dai makomar ɗan shaye-shaye ko ɗan daba. Ko
ka kashe ko a kasheka, ko a kashe maka wani makusancinka, da zai bar maka
mummunan tabo a zuciya, babu riba sam a wannan harkar".
Ta gyaɗa kai ta ce "wannan haka yake, amma ka godewa
Allah da ya sanya ka farga da wuri, har ka ke ta ƙoƙarin tuba ga Allah, ina
fatan Allah ya karɓi tubanka"
Ya amsa da "Amin ya Allah, kuma kema ina yi miki godiya
sosai Abla, kema kin bayar da gudummawa sosai da sosai a cikin rayuwata, kamar
yadda sisternki jauhar ta yi mini, Allah ya saka muku da mafificin
alkhairi"
Tayi murmushi ta amsa da Amin, duk wannan basar da abubuwan
da yake yi, ashe yane sane da duk alkhairin da ake yi masa.
"Amm ya maganarmu ta zuwa asibiti, me ka yanke a
kai?"
Ya jinjina kai ya ce "Zani in sha Allah"
Faɗaɗa murmushinta ta yi, ta ce "Alhamdilillah ala
kulli halin, amma na yi murna na ji daɗi sosai da sosai, Allah ya tabattar da
alkhairi"
"Amin"
"To menene next, idan an kammala shari'a, sannan ya
zamu yi da batun indabo? Shi Shikenan ya ci bulus kenan, idan aka hukunta su
madaki shikenan?"
Al'amin ya haɗiyi yawu, ya ce "Shi wannan iya
jarrabawar da yake ciki ta ishe shi, ko iya yanzu ya san tasa ta ƙare, akwai
jarrabawa a rashin mulki, tarwatsewar iyali kamar yadda na fuskanta. Bore daga
magoya baya ga karayar arziki an kama kayansa a ƙasar waje da yaransa, ga
tuhuma da yake fuskanta a cikin gida da sauransu, bana buƙatar wani ya hukunta
indabo ni ne zan hukunta shi"
Ta waro ido ta ce "Dan girman Allah mun kusa zuwa gaɓar
ƙarshe, kar ka mayar da mu baya ka ɓallo mana wani babban aikin dan
Allah".
"Haba akwai bambanci tsakanin Al'amin ɗan daba da kuma
jami'in tsaro, na san abin da nake yi, ki kwantar da hankalinki"
Nabila ta ce "Anya kwanciyar hankalin nan kuwa?"
"Trust me mana" yayi maganar yana murmushi.
Ranar Litinin, Nabila da Viper da rakiyar Sumayya, suka kai
Viper Asibitin ƙwaƙwalwa, domin ya ga likita.
Ba su wani sha wahala ba, ya samu dukkanin kulawar da yake
buƙata, hatta history na yadda ya fara shaye-shaye, sai da suka yi wa likitan
bayani, aka tura shi yin wasu gwaje-gwaje.
****
Kwanaki suka ci gaba da shuɗewa, wasu daɗi wasu akasin haka,
ana tsaka da alhinin mummunan kisan gillar da aka yi wa Abba, Rahila ba ta gama
dawowa dai-dai ba, aka sake sanar da ita, an kama Nazifi a Lagos, tare da
manyan 'yan fashi, hakan ya ƙara tunzura nutsuwar ƙwaƙwalwarta.
Kwanci tashi asarar mai rai, aka sake shafe watanni guda
curr, Ramma kullum cikin lissafi take, yaushe Abdul zai fito daga tsaren da
yake.
Yau kotu ta fi ko yaushe cika, ana jiran hukuncin da kotun
zata yanke.
Ƙarar su Viper ce ta uku da aka kira, bayan dogon
rubuce-rubuce da Alƙali ya yi, da bayanai ya shiga karanto hukuncin da za a
yanke wa su Lakwari.
Shekarun ɗaurin rai da rai, kowannensu, sannan kotu ta yi
umarnin a cigaba da binciken in da sauran waɗanda su ka tafka ta'asar tare
suke.
Wata irin ajiyar zuciya Nabila ta sauke, hawaye suka din ga
zuba daga idanunta, ba zata taɓa manta wannan rana ba, domin kuwa wannan ita ce
mafi ƙololuwar nasara da ta samu.
Viper ma sunkuyar da kansa ya yi a wurin, hawaye ya kasa
barin idanunsa, duk da Madaki yana can gadon Asibiti, bai san ma waye a kansa
ba.
Ana gama yanke hukuncin ta yi waje, da Sumayya ta fara arba,
suka rungume juna, Nabilan sai kukan farinciki take yi.
'yan jarida ne suka baibaiye ta, suna yi mata tambayoyi,
amma Sumayya ta ce su ƙyaleta ba ta cikin nutsuwarta.
Walid ne ya fito tare da Viper, yana ta rufe fuska da
handkerchief, babu abin da yake iya sanya shi hawaye a take, sai tuna jauhar,
'yan jarida shi ma suka yo kansa, amma ya rufe fuskarsa, Liti ya ce "Ko me
zaku tambaya ku tambayeni, ba zai iya magana ba"
"A'a da shi muke son yin magana"
"To ba zai yi ba, munafukai kamar baku ku ka din ga
zuzuta lamarin baz da faɗar ƙarya da gaskiya, wallahi idan ba ku bi a hankali
ba, sai aikin nan ya kai ku wuta, saboda yaɗa fasadi da sharrin da k...
"Kai liti wai waye ya tambayeka ne?" Walid ya
dakatar da shi.
Baba yana tsaka da rarrashin Nabila, ta daina kukan da take
yi, ya ga Viper ya fito, ya nufe shi, yana zuwa ya rungume shi ya na "Ina
tayaka murna Aminullahi, Ubangiji Allah ya wankeka yau, ni dama na faɗa ba zaka
iya kashe mini jauhar ba, Allah ya yi maka albarka".
Abbu yayi tsuru daga gefe, yana son yin magana, amma ya kasa
wata irin kunya ta mamaye shi.
Alhaji mu'azzam ma gefe ya koma yana murmushi, amma bai
tunkari in da Viper yake ba.
Viper ne da kansa ya tunkari in da yake tsaye, ya je gabansa
ya miƙa masa hannun sa.
Sai da Alhaji mu'zzam ya waiwaya, ko ba shi yake miƙowa
hannun ba.
Ya ga dai shi yake bawa hannu, ya miƙa masa hannu suka yi
musabaha.
Viper ya rungume shi, ya yi ajiyar zuciya ya ce "Na
gode, ina sane da dukkanin gwagwarmaya da ka yi a kaina, duk dan saboda
soyyayar da ka ke yi wa jauhar, da kuma ƙoƙarin ɗaukar fansa ta hanyata. Ka yi
amfani da ni, ka cimma burinka, ba butulu ba ne ni, da na rintse idanuna daga
kallon abin da ka ke yi mini, ina matuƙar kishin matata ne.
A karo na babu adadi, ina mai sake baka haƙuri, ka yi haƙuri
da Nabila kamar yadda jauhar ba ta kasance taka ba, Nabila ma haka, mussaman da
ake barin halak dan kunya, a wannan karon ma ita ma ɗin tawa ce. Na gode sosai
da gudunmuwar ka".
Alhaji mu'azzam kawai ya yi murmushi ya ɗan daddaki bayan
Viper ya ce "Ina tayaka murna, maganar Nabila kuma, ba a sanin ma ci tuwo,
sai miya ta ƙare".
Nabila kuwa hankalinta ne ya kai kan Naja'atu Bunkure da
take yi wa 'yan jarida bayanin cewa, za su ɗaukaka ƙara.
Ta gama bayanin ta nufi motarta, Nabila ta nufi in fa take,
Sumayya ta riƙe ta, amma ta fizge ta nufi Bunkure.
Ayshercool
08081012143
Tsayawa Bunkure ta yi cak, tana jiran Nabila ta ƙaraso,
Nabila ta ƙarasa gabanta tana wani irin huci, kamar fusatacciyar damusa. 'yan
jarida na ganin haka, abin nema ya samu, yuuuu suka ɗiba suka nufe su, da abin
magana da camerori.
"Ina fatan yanzu kin tabattar da jinin 'yar uwata ba
zai taɓa tafiya a banza ba? Kuma matsayin da ki ke taƙama da shi, ki ka ce ba
zan taɓa taka shi ba, ashe ba matsayin ba na arziki bane ba, na gode Allah da
ki ka haska mini ko ke wacece, ban ci gaba da yi miki makauniyar soyyaya ba.
Abin alfahari shi ne kayi amfani da damar da Allah ya baka, wurin kyautata wa
mutane, yadda ko bayan ranka zaka yi alfahari da hakan, ba yin mugunyar shuka
ba, da sharrinta zai ta bibiyarka har bayan ranka ba.
Na ji ki na iƙirarin ɗaukaka ƙara, to baki da wannan
lokacin, ga copyn ƙorafin da zan shigar a kanki nan, ga hukumar shari'a, kuma
ina fatan ta soke lasisinki da na ƙungiyar ki, ta ƙwatowa al'umma hakkinsu da
ki ke dannewa, ta hanyar rufe kura da fatar akuya, ki na kare yaran masu kuɗi,
kina tozarta masu ƙaramin ƙarfi. Bakk da lokacin ɗaukaka ƙara, zai fi kyau ki
mayar da hankali a kan yadda zaki karenki" Nabila ta dangwara mata wani
file, tare da yi mata kallon banza.
Tabbas tarihi ya maimaita kansa, domin kuwa sowa aka ɗauka
da tafawa Nabila, yayin da ta bar Bunkure baki buɗe ta rasa abin cewa,
ƙanƙanwar bayanta, da da auren wuri tayi, da ta kusa haifar Nabila, duk yadda
ake girmamata kamar wata abar bauta, ita yau Nabila ta dizga kuma ta kayar a
shari'a, wani malolon takaici ya ƙuleta, ta watsar da File ɗin, za ta shige
cikin mota. Wani abokin aikinta ya ce "Kul, kar ki yar ki tafi da shi ki
je ki duba, ki ga ta ina zaki ɓullowa lamarin".
Nabila kuwa wurin Barrister Habib ta waiwaya, da ya kammala
wata Shari'a ya fito, yana ta yashe mata baki, "Congratulations our legit
barrister"
Cikin murmushi mai haɗe da farinciki, ta ce "Na gode
barrister, Allah ya saka da mafificin alkhairi. Har duniya ta naɗe ba zan manta
da kai ba, a lokacin da yan uwa abokan aiki suke yi mini kallon mara hankali,
na ɗaukko dala babu gammo, ka tsaya tare da ni, tare da bani ƙwarin gwiwa da
gudunmawa ta kowacce fuska"
Yayi murmushi ya ce "Honorable Mu'azzam Wada kankarofi
shi ya dace ki yi wa wannan yabon, duk ƙoƙarin sa ne ya kawo haka"
Ta dubi Alhaji mu'azzam ta ce "Honorable, ban san me
zan ce maka ba, sai dai ina fatan idan kujerar sanata alkhairi ce a gareka,
Allah ya baka, ina kyautata maka zato, halacci da taimakon da ka yi mana,
Ubangiji Allah ya shaida ya kuma biyaka, bamu da baki, ko wani kalami da zamu
yi amfani da shi, da zamu yi gamshashshiyar godiyar da za ta wadaci hidimar da
ka yi mana, mun gode sosai da sosai"
"Babu komai Nabila, yi wa kai ne, kun cancanci hakan
ne, daga ke har Al'amin"
Walid ya ce "Shikenan Alhamdilillah, zaman rami ya
ƙare, mun yi 'yanci, kumurcin cikin rami zai yi yawonsa freely a gari, Allah ya
sa kuma kar ya addabi al'umma da sara" murmushi Viper ya yi.
"Yaya" suka ji an faɗa daga nesa, suna juyawa
Shahida ce ta taho da gudu, ta ruƙunƙume Viper tana kuka.
"Yaya dama zan sake ganinka? Yaushe rabon da na ganka a
rayuwata, ashe zan sake haɗuwa da kai?"
Wani irin sanyi ne ya ratsa Viper, duk da ba wani good time
yake yi da Shahida ba, amma atleast yar uwassa ce ta jini, kuma duk da irin cin
kashin da aka din ga yi masa a gidan su, sosai take nuna masa tausayi da jin
ƙai"
Rungumeta ya yi, sai dai ya rasa mai ze ce mata.
Ta ɗago tana kuma ƙare masa kallo, ta ce "Na je prison
ban san adadi ba, ba a bari na ganka, ina yawan yin kuka, idan na tuna halin da
ka ke ciki, ɗazu na ga text ɗin Abbu, wai na taho kotu an wankeka daga zargin
da ake yi maka, ni ban san yana ganinka kuna haɗuwa ba, na yi kewarka sosai
yayana"
Ya riƙe hannayenta ya ce "Kin yi saurin girma Shahida,
ƙarama ce ke fa, lokacin da aka tsare ni"
Zata yi magana ta haɗiyeta ta ƙarfin tsiya, sakamakon arba
da ta yi da Nabila, cakumar rigar Viper ta yi, tana nuna masa Nabila.
Ya ce "Menene?"
"Ba ta mutu ba?"
Ya ce "Eh, amma ta dawo ne ta halarci taron kotu, ta ga
yadda za a hukunta waɗanda suka kasheta, yanzu zata koma"
Nabila ta ce "Kaiiii"
Kiɗimewa Shahida tayi cikin matsanancin tsoro, Walid ya ce
"Viper kai fa ka iya wasan banza wasu lokutan, ba fa ta san ainihin abin
da ya faru ba, sai ka saka ta suma ai"
Baba ya ce "Na ga alama ai, Shahida wannan ba Jauhar ba
ce ba, twins sister ɗin ta ce Nabila" tayi ƙuri da ido, tana kallon
Nabila.
Liti ya ce "Ke kin taɓa ganin wanda ya mutu ya dawo
ne?"
Ganin Nabila ta samu nutsuwa, 'yan jarida suka cigaba da
addabarta a kan tayi magana, tambayar da ta fi ɗaukar hankalinta, har ta ji
zata iya amsata ita ce "Wane irin farinciki ki ke ciki a yau, ganin kin yi
nasara a wannan shari'ar?"
Tayi murmushi ta ce "Alhamdilillah, nayi farinciki
sosai da sosai, dan wannan ce nasara mafi girma da na samu, tun bayan zamana
cikakkiyar lauya mai zaman kanta, kuma in sha Allah yanzu aka fara.
Sai dai na sadaukar da wannan nasara tawa kacokan, ga babana
maganin kukana, abin alafharina baya goya marayu ginshikin da na jingina da
shi, ya zame mini tsananin da na taka na cimma wannan nasara. Mutumin da ya
saita ni a kan wani buri da ban taɓa tunanin ina da shi ba, kuma zan ci karo da
shi ba, yau gashi wannan burin ya cika wato Major Yusuf maitama mai ritaya, ina
alfahari da kai dattijon arziki matuƙa gaya. Ina fatan al'umma za su ci gaba da
bamu goyon baya ɗari bisa ɗari wurin kawo gagarumin gyara da sauyi, a fannin
shari'a da kuma harkar tsaro. Kuma ina fatan matasanmu maza da mata zamu
nisanci shaye-shaye da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi".
Yanayin yadda Nabila take magana, ya sanya Viper ya kalli
Shahida ya ce "Jauhar zata iya magana haka doguwa a gaban mutane cike da
ƙwarin gwiwa ba tare da tsoro ba?" Shahida ta girgiza kai ta ce
"A'a"
"To Nabila daban jauhar ma daban, wannan 'yar biyunta
ce"
"But how, ban taɓa sanin tana da sister ba ai"
Viper ya ce "Is a long story"
Abbu abin har mamaki ya bashi, yadda a wannan karon, Viper
ya sake da Shahida, duk da a baya, duk da irin shishishigi da take yi masa,
baya saurarar ta.
Viper ya gabatarwa da Nabila Shahida, Nabila ta ce "Ai
naga kamar haryanzu tsorona take ji, bari idan ta sake ta ƙara tabattar da ba
jauhar ba ce, sai mu yi magana"
Wata ƙatuwar helux ta shigo harabar kotun, baƙa ƙirin sai
ƙyalli take yi.
Ta yi parking a gaban su Nabila, da Abbu, wasu zaratan ƙarti
ne suka saukko, su na sanye da riguna baƙaƙe da tambarin dragon, bayan rigar
kuma hoton maciji ne da sunan Viper.
Murmushi ne ya suɓucewa Viper, suka jeru suka din ga gaisawa
sa shi ɗaya bayan ɗaya, suna yi masa congratulations da rungumarsa, yana amsawa
cikin sakin fuska.
Suka gaggaisa da su Abba, sai dai girmamawa ta musamman suka
yi wa Alhaji mu'azzam.
Viper ya ɓalle rigar jikinsa, rigarsa ta ciki irin ta su ce.
Ɗaya daga cikin su, ya ce "Oga yana son ganinka, shi ya
ce mu zo mu tafi da kai we need to celebrate with you"
Ya jinjina kai ya ce "Ok to" ya kalli Baba ya ce
"Baba bari na tafi, Nabila za a mayar da ita gida, idan na nutsu za ayi
maganar in da yafi security ta koma, idan kuma za ta ci gaba da zama da madam
shikenan. Shahida, zan zo gida zan yi miki gaisuwa ban in sha Allah.
T ladan ina godiya sosai da sosai" ya ƙarasa maganar
yana jinjina musu hannu, ya ce "Mai laya zamu yi magana, mu haɗe a
chamber" yayi maganar yana danƙar kwalar ɗan mama ta ƙeya ya tura shi
cikin motar"
Liti ya ce "Wai yaushe zaku daina munafurtarmu daga kai
har ɗan maman, waɗan nan jibga-jibgan kamar kai su kuma suwaye, menene alaƙarka
da su?"
"Tambaye su mana" Viper ya yi maganar yana nuna
masa su.
Ya kalli Nabila, yayi mata alama da hannunsa na zai kirata a
waya, tare da kashe mata ido ɗaya. Murmushi ta yi ta ɗaga masa hannu, a daidai
lokacin ya rufe motar suka ja, suka bar wurin.
Nabila ta kalli Abbu jikinsa duk a sanyaye, Baba yana ta
bashi haƙuri, ta ce "Baba da kai da honorable, yakamata ku shiga cikin
lamarin nan mussman kai, a sasanta Viper da Abbu, wallahi nayi nayi da
shi yaƙi, da na fara maganar yake haɗe rai"
Abbu ya ce "Na san kin yi iya ƙoƙarin ki Nabila, ki
daina matsa masa, kin san murɗaɗɗen mutum ne, mai taurin kai, amma mai raguwar
zuciya, duk wannan abin da yake yi, zai saukko, zan ci gaba da haƙuri, har zuwa
lokacin da Allah zai sanya ya saukko".
Viper ne a tsaye a wani katafaren office, wani narkeken
mutum ya miƙe, ya ƙarasa wurin Viper, suka yi musabaha, ya rungume Viper ya ce
"Congratulations my man"
Viper ya ce "Thank you Sir"
"Congratulations once again Al'amin"
"Thank you very much sir"
"Yarinyar nan fa ta bamu mamaki sosai da sosai, bamu taɓa
zaton za ayi wining case ɗin ba, saboda case ne mai hatsari da sarƙaƙiya, amma
thank God, Congratulations once again"
Ya kalli ɗan mama ya ce "Anas" ɗan mama ya ɗan ɗago
yana risunawa.
"Yaushe zaka tafi training ne?"
"Dan Allah sir ka yi haƙuri, ni ba sai na yi training ɗin
nan ba, a bar ni kawai"
Yayi murmushi ya ce "Viper ka ji abin da ya ce?".
Viper ya ce "Bai isa ba sir, dole ya tafi"
"To kai Anas, ko Viper bai faɗa ba, dolenka Anas, ai ka
riga ka yi aiki da mu, you can leave, zan ganka" ɗan mama ya fice.
Ya mayar da idonsa kan Viper ya ce "Viper, komai ya zo
ƙarshe, yaushe zaka koma bakin aiki gaba ɗaya?"
Viper ya ce "Ina son a ɗan ƙara mini lokaci, tun da ina
gudanar da aikina daga nan, ina da abin da nake son ƙarasawa ne"
Ya ƙaraso ya dafa kafaɗar Viper ya ce "Kamar haryanzu
kana cikin pain Viper, amma yakamata ka tattara hankalinka wuri guda, a baka
abin da za a baka ka cigaba da rayuwarka, amma duk abin da ka yanke shikenan,
ina yi maka fatan alkhairi, zamu cigaba da baka dukkanin gudunmuwar da ka ke
buƙata"
Suka sake gaisawa da Viper ya fita.
*****
Bayan Nabila ta koma gidan madam Halimaz tayu wanka ta canza
kaya, madam sai murna take tayata saboda nasarar da suka samu, kai tsaye gidan
Abba ta tafi, ta nufi benensa cikin matsanancin farinciki da murna, suna tare
da Nasir, da wasu daga cikin yaran gidan da matansa.
Gaban Abba taje ta zauna, tana ta murmushi bakinta yaƙi
rufuwa, gaba ɗaya suka tattara hankalinsu a kanta.
Dogon skirt ne a jikinta, da over size t-shirt ta Viper,
tayi rolling da veil, ta ƙarasa gaban Abba ta durƙusa ta ce "Major Abba,
na samu nasarar da ban yi zato ba, Alhamdilillah kotu ta wanke babban mai
laifin da nake karewa, bayan da aka gano ba shi da laifin da ake zarginsa"
Fuskar Major babu yabo babu fallasa ya ce "Na tayaki
murna"
"Abin da nake ta gaya maka kenan Abba, tun farko ba ka
tsaya ka fahimce ni, nayi maka bayani ba"
Ya girgiza kai ya ce "Nabila, ni fa duk wani abu da ya
shafi mahaifinki ba ƙaunarsa nake yi ba. Da bai aura mata ɗan daba ba, da duk
haka bata faru ba, ai yana da wasu yaran, meya hana su ya aura musu shi, sai
ita, saboda ba ta da galihu, ni fa mutuwar yarinyar nan, ƙara mini ƙiyayyar
mahaifinki ta yi, and na baki zaɓi idan zaki zauna a nan ne ki zauna, idan kuma
wurin mahaifinki zaki koma, ki sauka lafiya ki yi abin da ki ke so, you are
allowed to make decision"
Jiki a sanyaye Nabila ta saki hannunsa, ta kalleshi ta ce
"Abin har ya kai ga haka Abba? Ban taɓa tunanin akwai ranar da za ta so,
ka sanya na ji wani abu a raina, mai kama da ba kai ne mahaifina ba"
Ya dubeta a tsanake ya ce "Amma ke kin tabattar da
duniya ba ni na haife ki ba"
Ta girgiza kai ta ce "Ban nuna wa duniya ba kai ka
haife ni ba, amma ina neman afuwarku baki ɗaya" ta tashi gwiwa a saɓule ta
bar ɗakin.
Ta sha kuka sosai da sosai a ɗakinta, sam ba ta ji daɗin
abin da Abban ya yi mata ba.
Ta koma ɗakinta ranta babu daɗi, tana jin kamar dan ba Nasir
ne yayi nasarar ba, shiyasa Abban yake yi mata haka, ba wai dan yana jin
haushin Babanta ba kawai"
Baba Magajiya ce ta din ga rarrashinta, tana ba ta haƙuri,
wayarta ce ta fara ringing, ta duba taga Viper ne.
Ta ɗaga tare da goge hawayen da yake kwance a fuskarta.
"Hello vi"
"Ina waje"
"Ai ba na barrack ina gida"
Ya ce "Na sani, location ɗinki ya nuna mini, am
tracking you ai"
Ta ce "To ina zuwa"
"Baba Magajiya, bari na je waje ana nemana"
"To shi sirikin nawa ne?"
Nabila ta ɓata fuska ta ce "Wane siriki kuma? Ai
wallahi baba magajiya duk kallonku kawai nake yi, babu wanda ya yi mini kara a
gidan nan, na zuwa in da mahaifina yake gaba ɗaya ma kamar kowa gaba yake yi da
ni"
Magajiya ta ce "Haba dai Arfa, wallahi dan babu yadda
zan yi ne, amma ina matuƙar son yin hakan, amma kin ga ga a halin da ake ciki
ne, kar nima na yi wani laifin"
Nabila ta ce "Shikenan" ta tashi ta fita.
"Vi snake" ta faɗa tana murmushi.
"Kukan me ki ka yi kuma? Wai dan Allah ke a rayuwarki
ba kya gajiya ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Ni kaina na san saurin kukan nan
yana cutata, ba yadda zan yi ne"
Ya ɗage kafaɗarsa ya ce "Ya gajiya kuma?"
"Alhamdilillah, babu gajiya"
"Bangajiya na dawo na yi miki, kuma na ƙara jaddada
godiyata a gare ki"
Ta numfasa ta ce "Kar ka damu, kaina na yi wa ai"
"Gaskiya ne, gobe in Allah ya kaimu zamu koma wurin
likita ko?"
Ta jinjina kai ta ce "Eh gobe in Allah ya kaimu
ne"
Viper ya ce "Ina son 1hr kacal a lokacinki idan mun
dawo" kawai ta gyaɗa masa kai.
"Wai ya na ga jikinki a sanyaye ne, kamar ba wannan
ranar ki ke jira ba? Meyafaru ko wani abin kuma nayi?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
Ya sake kallon fuskarta yadda take ƙifta ido cikin damuwa.
"Abla" ta ɗaga mayanyan idanunta ta na kallonsa.
"Menene kuma?"
"Abba ba zai yadda su sasanta da Baba ba, na rasa wace
irin zuciya ce da shi, wai haushin sa ya ƙara ji, da ya aura maka jauhar,
meyasa a cikin yaransa bai aura wa wata a yaransa ba, sai ita, saboda marainiya
ce babu mai tsawatar masa. Shikenan haka zan zauna a tsakiya gaba ɗaya komai ya
fita daga raina" ta yi maganar tana ƙoƙarin mayar da hawayen da ke shirin
zubo mata.
"Yanzu ni ne dai matsalar kenan?"
Ta ce "A'a, ba kai ba ne ba, ya ma ƙi saurarata balle
in yi masa bayani. Yanzu a haka zan ci gaba da zama a gidan nan, Abba ya kware
mini baya a gaban mutanen gidan da ba sa so na, ko kuma can gidan mahaifina zan
koma, na zauna a cikin waɗanda suka muzgunawa mahaifiyata da 'yar uwata. Zamana
a cikin barrack na ɗan lokaci ne, kuma saboda kai ne, da komai ya kammala dole
na bar zaman wurin, gaba ɗaya zuciyata a cunkushe take na rasa mai ma zan yi,
na zata da an kammala shari'a komai zai zo da sauƙi, ashe tsugunno ba ta ƙare
ba"
Ya gyara tsayuwarsa ya ce "Ni ne matsalar a nan, zan
kuma san abin yi na warwareta in sha Allah, ki yi haƙuri komai zai
daidaita"
Ta ce "Tayaya kenan, ka san halin Abba kuwa?"
"Eh mana, hali mai kama da nawa ko? Zan san abin yi, ki
je mu haɗu gobe in Allah ya kaimu"
****
Nasir ya rasa abin da yake yi masa daɗi, mussaman yadda
Nabila tayi nasara a kotu, duk sai ya sha jinin jikinsa, gashi sai ya ga kamar
Abba ya sauya masa.
Da asuba Abba yana sauraren labaran asuba, aka sako Muryar
Nabila, tana murna da godiya ga Allah, bisa nasarar da suka yi a kotu, tare da
sadaukar da nasarar ta ta gare shi baki ɗaya.
Yayi shiru yana saurarenta, ƙasan zuciyarsa yana cike da
farinciki, sai dai haushin mahaifinta, ya hana shi sakewa ya ji daɗin hakan.
****
Ramma ta ɗauki wayar mama ba ta sani ba, ta kira Nabila,
suka gaisa Ramma ta ce "Anty Nabila, mama ta ce wai kun yi nasara a kotu
ko?"
"Eh rahama, Alhamdilillah"
Ta ce "Masha Allah, ina tayaku murna sosai da sosai
Allah ya ƙara nasarori"
"Amin rahama, mun gode sosai ya jikinki, lokacin zuwa
awo bai yi ba ai ko?"
Ta ce "Eh saura sati biyu"
Nabila ta ce "To Allah ya raba lafiya"
Sai kuma tayi shiru, ta kasa faɗar abin da ya sanya ta
kiratan"
"Rahama ko akwai wani abu ne"
Jiki a sanyaye ta ce "A'a dama...."
"Dama me? gaya mini babu wani abu"
"Cewa na yi kin je wurin doctor ne? Ya warke?"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Allah sarki ƙanwata, na
fahimce ki, ki yi haƙuri sai Allah ya kaimu lokacin awonki, daga nan sai mu je
ki ganshi, kin san halin yayanki, daga ni har ke sai ya tijaramu ba
ruwansa"
Ta ce "To na gode sosai Anty Nabila"
"Kar ki damu, ki cigaba da addu'a, da kula da kanki da
cin abinci da shan magani, in sha Allah komai zai wuce"
Ramma ta ce "Ina yi, na gode sosai" suka yi
sallama.
*****
"Viper, wai ɓoye-ɓoyen me ku ke yi mana ne kai da
wancan munafukin yaron, ku na ƙulla wani abu da bamu sani ba, Menene alaƙarka
da sojoji. Gashi kullum cikin danna wanan wayar ka ke, wadda ba a gane komai
sai lambobi da locations, me ka ke yi?" Liti yayi maganar yana tsare Viper
da ido.
"Shaƙeni sai na gaya maka"
Walid ya ce "Ba maganar shaƙewa ba ce ba, maganar
gaskiya ce, ka gaya mana me ka ke yi wanda ba mu sani ba?"
"Sirri ne, ba a faɗa"
Liti ya ce "Ƙarshen sirri dai ace ƙungiyar asiri ka
shiga ko? To komai sirrinsa gaya mana, mu yanzu har akwai wani sirri da za a ɓoye
mana?"
Kallonsu ya din ga yi ɗaya bayan ɗaya ya jinjina kai, ya ce
"Idan kun matsa na gaya muku, zan gaya muku amma wallahi a yanzu,na gaya
muku sai kuma kun yi irin abin da nake yi, komai wahalarsa da azabarsa"
Walid ya ce "Azaba wacce ce ba mu gani ba, mu na
jinka"
Liti ya ce "A'a tsaya gaskiya, ya ce wallahi fa, ina
dalili ban san wace kalar azaba ce da wahala ba, ni dai na haƙura riƙe kayanka,
ba na son ji ɗan mama ya gaya mini, dan na ga tare ku ke ƙulle-ƙullen"
"Shi ma ba zai gaya maka, saboda yana cikin tsaka mai
wuya yanzu, sanin abin da nake yi ya tilasta masa yin irin aikina, ina ga ma ba
zaka sake ganinsa ba, yana can a tsare, cikin satin nan zai bar gari"
"A kai shi ina kuma?"
"Liti yayi maganar yana kallon Viper"
Viper ya yi murmushi ya ce "Irin ƙaunar da aka nuna
mini, ta azaba, ita zan yi masa domin inganta rayuwarsa, abin da zan yi masa
kenan na tabattar masa da na ji daɗin halaccin da ya yi mini"
"Ta hanyar gana wa mutum azaba? Ni dai ba da ni ba dan
Allah, ka riƙe halaccinka"
Walid ya ce "Ina jinka, gaya mini koma menene"
"Ya fa rantse mai laya, ka san halin Viper, tun da ya
rantse abin babu sauƙi, ni dai a bari na fita sai a faɗa"
Walid ya ce "Munafuki so yake fa ya ji koma menene ɗin"
Viper yayi murmushi ya ce "Ni dai na rantse, shawara ta
rage taku"
Liti ya ce ba ya son ji, Walid kuma ya dage sai ya ji.
Ƙarshe dai ya ci gaba da yi musu yawo da hankali ya ƙi gaya
musu.
***
Kamar yadda suka shirya, washegari suka tafi Asibiti ganin
likita, suna tafe a hanya take gaya masa ramma tana yi masa murnar samun nasara
da ya yi a kotu.
Kawai ya ce "Hmm"
"Hmm kuma kamar yaya?"
"Kawai ina tuna wautar da yarinyar nan tayi ne"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Kar ka zargeta Vi, so ne
sila, amma yanzu idan ya fito yaya za ku yi da su ne, dan ko da me ku ke yawo
ba zai saki rahama ba, ban taɓa tunanin ana irin wannan son a gaske ba
gaskiya"
Ya ce "Abin da mahaifiyarta ta yanke kawai, ni dama
babban fatana a hukunta shi, maganar aurensu ni bani da abin cewa"
Nabila ta ce "Vi dan Allah ku yi haƙuri, ku yafe wa
gayen nan, yayi nadama kuma wallahi suna son junansu da rahama, ku bar masa
kayyasa, tasa ce"
"Ba za a bashin ba, bashi da nasaba mai kyau"
"Vi sai ya ci albarkacin ku, nasabar tasa ta gyaru,
wallahi ni gaba ɗaya karya mini zuciya ya yi, dan Allah a bar masa ita, yana
sonta sosai"
"Anƙi"
"Vi baka san menene so ba, ba ka san zafinsa da
wahalarsa ba"
Ya ce "Eh ban sani ba, kuma bana fatan na sani. Ke da
liti ban san wanda ya fi wani raina ni ba, shi ya ce ba zan sake yin aure ba,
na shiga ittikafi, ke kin ce ban san so ba, ina ga ni duniyata daban, ba a
jinsin mutane nake ba"
Sosai Nabila take dariya ta ce "To mutum ne kamar boss,
kullum rai a haɗe kullum cikin tsare gida, dole a yi tunanin baka jin komai, da
ya shafi soyayya"
Tunawa yayi da Jauhar ta taɓa gaya masa magana makamanciyar
wannan.
"Ba na tunanin akwai wanda so ya azabtar kamar ni, a
lokacin ban san menene shi ba.
Ranar da na fara ganin jauhar, ta ganni rungume da liti
cikin jini, ta ƙwala ihu ta suma.
Haka kurum gabana yayi mummunar faɗuwa, na je na ɗagata na
ga ta suma, tun daga ranar nake yawan mafarkinta, da na tuna a yanayin da ta
ganni, za ta yi zaton kisan kai nayi, sai na ji babu daɗi na damu, har zuwa
lokacin da Allah ya haɗamu a inuwa ɗaya, tsarki ya tabatta ga Ubangiji mai
jujjuya al'amura yadda ya so, a lokacin da ɗan Adam bai taɓa tsammanin faruwar
abin ba. Allah ya jiƙan Zahra"
Jiki a sanyaye Nabila ta amsa da Amin, tare da jin begen ina
ma ko sau ɗaya ta ga jauhar a rayuwarta, tana matuƙar jin daɗin yadda ake faɗar
kyawawan halayenta.
Viper ya ga likita kamar wancan lokacin, ya bashi
shawarwari, sai dai a tattauanawar da suke yi ne, likita zai gano bakin zaren,
sai dai fafur Viper ba ya son magana, sai dai Nabila ta yi ta ɓaɓatun itakaɗai.
Bayan sun fito sai da suka je gidan su Ramma, suka gaisa,
Viper da maman suka din ga hira, Nabila kuma suka shiga ɗaki da ramma.
Sai azahar suka bar gidan su ramma, Nabila ta yi ta
rarrashin ramma, ta kwantar mata da hankali.
Bayan sun fito wani store ya kai Nabila, ya ce ta ɗauki duk
abin da take so.
Ta kalleshi ta ce "Meyasa ka kawo ni nan, ina fatan ba
biyana kuɗin aikin da na yi zaka yi ba, ka riga ka biyani, haɗa ni da mahaifina
bana buƙatar komai daga gareka, komai na yi maka kaina na yi wa"
"Ai bani da abin biyanki, dake da iyayenki, bani da
abin biyanku, wani ihsani ne kawai, wani abu da na daɗe ina burin in ga ina yi
wa jauhar, a lokacin ba ni da halin hakan, amma tun da gaki sai na yi miki a
madadinta"
Tayi murmushi ta ce "Na gode sosai da sosai Vi, amma
idan ka yi mini haka, zan ga kamar ka biyani ne abin da na yi maka, maganar
gaskiya ba zan iya yadda ka yi mini sayayya ba, domin hakan tamkar cin amanar
jauhar ne, kuma kaga Jauhar daban ni Nabila ma daban".
Ayshercool
08081012143
Shiru yayi yana dubanta, domin ya tabattar idan da gaske
take, sai dai yanayin fuskarta ya tabattar masa da gaske take yi ba wasa ba.
Basarwa yayi ya ce Shikenan su tafi, amma deep down ya ji
zafin abin da ta yi masa nesa ba kusa ba, he wish 'yar madararsa tana raye, da
ya san ita ba zata watsa masa ƙasa a ido ba, kamar yadda Nabila ta yi yanzu ba.
Dan rashin kunya, su na tafiya a hanya kuma, ta na yi masa
hira da surutu, ganin ya yi mata banza, ya sanya ta ja bakinta ta tsuke, kuma
ta tabattar fushi ya yi.
A hanya ya sauka, ya bar ta da Joseph, ya mayar da ita gida,
shi kuma yayi nasa wuri.
****
Washegari da yamma, Abba yana gidan gonarsa, yana office ɗin
sa, ana ta fitar da ƙwai na kaji, da na sauran tsuntsaye ƙaton gidan gona ne
sosai da sosai, gidan gonarsa na cikin manyan gidajen gona da yake fitar da
ƙwai, har maƙwabtan garuruwa. Da su kansu kajin da kifaye, ban da sauran
dabbobi.
Masinja ya sanar da shi ya yi baƙo, Abba ya ce a shigo da
shi.
Mintuna kaɗan aka buɗe ƙofar Office ɗin aka shigo, ajiye
biron hannunsa ya yi yana kallon Viper.
Viper ya yi sallama, Abba ya amsa a hankali yana ci gaba da
kallonsa.
Ya ƙaraso ya tsaya, ya gaida major cikin girmamawa kamar
yadda suke yi a tsakaninsu masu ɗamara, hakan ya tabattar wa Major akwai wani
abu tattare da baƙon nasa. Ya bashi dama ya zauna.
Viper ya ce "Duk mun taɓa haɗuwa ba na da tabbacin ko
ka gane ni, amma bari na sake gabatar maka da kaina, sunana Al'amin Ibrahim,
wanda 'yar ka Nabila ta tsayawa a kotu, kuma mijin 'yar uwar Nabila da Allah ya
yi wa rasuwa"
"Mijin wadda ka kashe dai, da babanta bai san ciwonta
ba ya ɗauketa ya aura maka. Ta yaya zan kasa ganeka, da ka ɓata mini shirina na
shekara da shekaru ka ɗauki Nabila ka haɗata da babanta, mutumin da bai martaba
rayuwar uwarta da ta 'yar uwatta ba har ya iya aura maka ita ka kasheta".
"Ba ni na kasheta ba, kamar yadda kotu ta tabattar kuma
ta wanke ni, ina roƙonka saboda Allah, kar laifin da ba namu ba ya shafe ni da
ni Nabila, mussman ma ita.
Makamancin abin da ya faru da Jauhar, irinsa ne a rayuwata,
da ya jefa ni cikin ƙaddara. Duk wannan mummunar rayuwa da nayi, ta samo asali
ne daga rashin samun ingantaccen bangon da zan jingina rayuwaya da shi, sai da
ƙaddara ta saka aurena da Jauhar, ba zan taɓa mantawa da ita ba har duniya ta
naɗe, kuma ban kashe jauhar ba.
Kamar yadda kotu ta tabattar, duk da na fuskanci mutum ne
kai irina, muna amfani da ƙwaƙwƙwarar shaida da muka gani a zahiri ne, ba dan
haka ba, ba zan so na baka wata gamshashshiyar hujja da shaida da zata tabattar
maka da Nabila a kan dai-dai take, kamun da aka saka ɗanka yayi mini ba bisa
ƙa'ida bane ba.
Da fari hukumar'yan sanda ce ta bashi umarnin, daga baya
kuma an bashi maƙudan kuɗi dan ya kama ni, hakan ya sanya ya din ga ɓata Nabila
a idonka. Duk ban gaya maka wannan abun da raba maka kan iyalinka ba, roƙonka
kawai nake yi, ka daina fushi da Nabila, duk da ganin mahaifinta da ta yi, a
duniya ba ta da wani wanda ta shaƙu da shi take ƙauna sama da kai. A madadinta
ina mai ƙara baka haƙuri, domin kuwa na san duk ni ne silar komai, amma dan
Allah na roƙe ka, ka yi haƙuri ka yafe wa Nabila da mahaifinta, ci gaba da
fushi da ita, zai kua jefa rayuwarta a cikin damuwa"
"Ka gama?" Major ya yi maganar yana kallon Viper.
Viper ya yi shiru bai ce komai ba.
"Na ji na kuma gode, amma ka tashi ka tafi, ka ɓata
ruwa ba domin ka sha ba, ka ɓata mini haɗin kan iyali"
"Abba ban ɓata maka kan iyali ba, son abin duniya ne ya
rinjayi Nasir, ya ƙara ta'azarra al'amarin, ina sake baka haƙuri, saboda Nabila
kar azo ta shiga wani halin" ya na gama maganar ya tashi tsaye ya fice
daga ofishin.
Bayan fitarsa Major ya yi shiru yana kallon ƙofar da ya
fita, da nazartar maganganun da ya yi.
Gaba ɗaya Viper ya daina kiran Nabila a waya, ita ma kuma ba
ta neme shi ba, hakan ya ƙara tunzura shi, ganin yadda ta watsar da shi gaba ɗaya.
Major ya so ya yi wa Nabila maganar zuwan Viper in da yake,
amma yayi mata shiru ya rabu da ita.
*****
Satin awon Ramma ya zagayo, Nabila ta je ta ɗauki ramma,
suka je asibiti. Aka yi mata awo aka duddubata, komai nata lafiya ƙalau.
Su ka tsaya suka yi sayayya, suka tafi prison. Ramma sai
murna take yi tana jin daɗi za ta ga Abdul.
Saboda yadda Nabila ta zama popular yanzu, duk in da ta
shiga an santa, tana samun alfarma, yau ma har ciki aka shiga da su.
Aka je aka fito musu da Abdul, yana ganin ramma ya saki
murmushi, ita ma murmushin ta sakar masa, ta miƙe tsaye ba tare da ta san ta
miƙe ba.
Nabila ta ce "Bari na baku wuri, idan kun gama ma
gaisa" ta fita waje, bai damu da gandiroban da yake wurin ba, ya rungume
abar sa.
Ta ce "Doctor ya jikin ka warware?"
"Inyee an daina gantsara mini sunana, Abdul
yasar"
Ta saki murmushi ta ce "Ko dan saboda wannan ai
yakamata na fara saye sunan" tayi maganar tana nuna masa cikinta, da ya
kai watanni shida ya fito sosai.
Murmushi yayi ya zira hannunsa cikin hijjabinta, ya shafa
cikin nata.
"Ina fatan dai wurin awon babu wata matsala da babyn
namu?"
Ta ce "Anty Nabila tana kula da ni sosai, tana kai ni
awo"
"To ki na cin abincin da shan maganin dai ko?"
Ta jinjina kai ta ce "Eh, kawai dai ina son na ga ka
fito ne, ina cikin damuwa tsareka a wurin nan"
Ya kalli wurin ya ce "Kar ki damu, ai na riga ma saba
kuma ba wata wahala nake sha ba your excellency, kewarki nake tayi ne dai
kawai, amma yaya zasu bar mu mu cigaba da zaman aurenmu?"
Ta rausayar da kai, ta ce "To gashi nan dai, ban san ya
ake ciki ba, basu sake cewa komai ba. Ina son in roƙi Anty Nabila, ta ɗan ƙara
lallaɓa mini su, amma nauyinta nake ji".
Ya ja hannunta suka zauna, ya ce "Ni zan roƙeta, ko
sake durƙusawa zan yi a gabansu na basu haƙuri, ni dai su bar mini ke babyna,
da ke jaririnmu mu rayu tare ko Rahamana?"
Ta jinjina masa kai, ta numfasa ta ce "To yaya yanayin
abincin kana samu ka ci kuwa?"
"Eh mana, komai nawa normal kawai dai ina tsare ne, ki
kwantar da hankalinki, ki rainar mana babynmu, ina fatan lokacin da zan fito
yayi dai-dai da lokacin da zaki haihu, a karɓi haihuwar nan da ni. Na so ni zan
kula da ke ayi rainon cikin nan da ni"
"To yaya zamu yi, kana naka Allah ya sa shi ne dai-dai,
Allah ya fito mini da kai lafiya"
Abdul ya dafa kafaɗarta ya ce "Naki ne ni?" Ta
jinjina masa kai cikin jin kunya tana murmushi.
"Naki ne ni rahama, ƙaddararmu ce ta zo mana a hagunce,
amma mun gode masa Allah ya sassauta mana, ya sanya su barmu mu yi rayuwarmu ta
aure"
Ta ce "Amin, bari ta zo ku gaisa, mu tafi, na san yanzu
za su ce mu tafi"
Ya marairaice ya ce "Haba dai, kwata-kwata yaushe ku ka
zo, ban gaji da ganinki ba, yayi maganar yana sumbatar goshinta.
Gandiroba ya ce "To sharokhan baban soyayya, lokaci
yayi"
Abdul ya yi murmushi ya ce "Ai shi sharokhan na shi
film ne, ni kuwa soyayya ce ta zahiri, dan haka ni na fi shi ma" yayi
maganar yana dariya.
Nabila ce ta dawo, suka gaisa da Abdul, sai dai da ta ga
farinciki a fuskokinsu, sai ta ji daɗi.
"Ina godiya sosai da sosai, rahama ta gaya mini yadda
ki ke kula mini da ita da babyna, Allah ya saka miki da alkhairi"
Nabila ta ce "Amin, ai yi wa kai ne, rahama ƙanwata ce,
ina jin daɗin ganinta cikin farinciki. Nayi mamakin yadda aka yi ka yi mata
laifi kamar wannan kuma ka iya dasa soyayyarka a cikin zuciyarta. Meye sirrin
ne?"
Yayi murmushi ya ce "Ita zaki tambaya ai"
Ramma ta harare shi ta ce "Ba wani sirri, ban da faɗa
me ka iya?"
"Soyayya" ya bayar da amasa kai tsaye, da sai da
ramma ta ji kamar ta nutse.
Suka yi dariya, ya sake cewa Nabila "Dan Allah na ga
kamar ke kina tausaya mana, dan Allah ki rarrashi mama, ki ba ta haƙuri su bar
mana aurenmu dan Allah"
Nabila ta sauke numfashi ta ce "To bani da ta cewa ne,
idan na matsa yayanta hayayyaƙo mini zai yi, amma zan lallaɓa ta ɓangaren mama
na cigaba da shawo kanta, in sha Allah komai zai wuce"
Ya ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka da
alkhairi. Idan da wani abu ko kuɗi sun yi kaɗan, ayi mini magana"
Nabila ta ce "Kai wane irin kuɗi sun ƙare, wannan
maƙudan kuɗi har haka, akwai kuɗi sosai in sha Allah ba wani abu"
Ya ce "To shikenan, muna godiya sosai barrister, babyna
sai yaushe kuma?" Ramma ta galla masa harara, amma bai fasa ba, ya riƙe
hijjabinta, ta waiwayo ta fizge ta na murguɗa masa baki.
Shafar sumar kansa ya yi, yana dariya, suka fice ita da
Nabila.
Suna tafe a hanya, Nabila ta ce "Ramma har mamaki ku ke
bani da ke da Abdul, dan Allah me Abdul ya yi miki, har ki ka fara sonsa, duk
da girman laifin da ya aikata miki?"
Ramma ta jinjina kai ta ce "Na san da yawa ba za su
fahimce ni ba, za a zata ko kwaɗayin wani abu ne na hannunsa, ko kuma wani abu
nake yi wa, wanda ni har muka rabu ban san menene auren ba, kawai dai ina jin
daɗin shiryuwar sa a dalilina. Kuma yana da wasu nagarta, wanda shi kansa bai
san yana da ita ba. Da ya samu isashshiyar tarbiyya, ba zai yi wasu abubuwan
ba.
Ya nuna tsantsar nadamarsa, gani nake idan na rabu da shi,
zai iya koma wa ruwa, duk da da gaske, yake tuba a kan abubuwan da yake
aikatawa. A matsayin ya aureni, ya tabattar mini da ya aure ni, babu irin zagi
da rashin mutuncin da ban yi masa ba, amma ko a jikinsa, bai taɓa damunsa ba,
kawai zai yi abin da ya ga dace yayi domin ya kyautata mini, ko na yaba ko na
kushe bai dame shi ba.
Sannan daga halayensa masu kyau, yana da tausayi da taimako,
mutum ne mai kyauta ta ban mamaki, kuma ya san aikinsa sosai da sosai, ina duba
wannan abubuwan ne, amma ni kaina na san ta wani ɓangare kamar ban kyauta wa
kaina da mama ba"
Nabila ta ce "Kar ki ce haka, wannan shi muke kira da
jarrabawa, Allah ya jarabce ka ya ga yaya zaka yi? Bar ganin Abdul ba ya ji,
wallahi sai ki ga saboda yawan kyautarsa da taimakonsa, ya sanya Allah ya din
ga ji da shi, maybe shiyasa ya sanya tsautsayin nan a tsakaninku, domin ya
rabauta ya tuba, yadda ya daina zina within shot period of time da ku ka zauna,
ya cancanci a yaba masa daga ke har shi, ina fatan Allah ya tabattar da
alkhairi a zamanku, ya sanya sanadin shiriyar sa kenan, idan Allah ya tabattar
da zamanku, ki yi ƙoƙari ki rufa masa asiri, ki zauna da shi da zuciya ɗaya, ki
yafe masa".
Ramma ta ce "In sha Allah Anty, na gode sosai da sosai,
Allah ya nuna mana aurenku ke ma, da Yaya Al'amin"
Nabila ta kalleta ta ce "Da wa? Wannan yayan naki ai
sai Jauhar ɗin, Allah ya bashi mace ta gari dai ba Nabila ba" Cikin mamaki
Ramma ta ce "Amma Anty Nabila saboda me? Wallahi yana da kirki, yana da faɗa
ne dai kawai"
"Wasu dalilai rahama, ki manta kawai, ba soyayya muke
yi ba dama, kawai dai nima yayananne"
Jiki a sanyaye ta ce "A'a shi sonki yake yi"
"Yaya aka yi ki ka sani, shi ya gaya miki?"
"Ni a wa zai gaya mini, bai gaya mini ba, amma wasu
lokutan irin kallon da Abdul yake yi mini, yake yi miki. Idan mutane sun kai
goma a wuri, duk wanda zai yi magana ba zai damu ba, amma da kin fara magana,
zai tattara nutsuwar sa da hankalinsa a kanki. Ko wani abin ki ke yi daban,
yana kallonki ta ƙasan idonsa"
Kwashewa da dariya Nabila ta yi, ta ce "Kai rahama,
haka ki ke saka masa ido kina kallonsa, ke duk a ina ki ka san hakan shi ne
so?"
"Wurin doctor, amma Wallahi yana sonki"
"Daina rantsewa rahama, Viper mace ɗaya tak yake so a
duniya, kuma yanzu ba ta raye, babu kuma macen da za ta iya maye gurbinta, dan
haka ki manta kawai"
Rahama ta ce "Shikenan, tun da kin ce haka, amma ai
kamarku ɗaya ita, kema yana sonki, ina ga dai ke ca ba kya sonsa kawai"
Rahama tayi maganar cikin sanyin jiki sosai, dan tana son ta ga sun yi aure,
dan sun dace sosai.
****
Abubuwa suka din ga damun Major, game da maganganun da Viper
ya gaya masa, sai ya kasa haƙuri, ya kira Nasir ɗakinsa.
Ya dube shi sosai sannan ya ce "Nasir tambayarka zan
yi, kuma ina so ka ji tsoron Allah, ka gaya mini gaskiya"
Ya ce "To Abba in sha Allah"
"Waye ya saka neman yaron nan da Nabila ta kare?"
Ya numfasa ya ce "Abba maitaimakin CP ne"
Abba ya ce "Da kuma wa?"
"Shikaɗai ne Abba"
"Gaskiya na ce ka gaya mini, waye ya baka kuɗi a
matsayin cin hanci, ya ce lallai ka nemo shi? Kar ka yi mini ƙarya, ka san nima
tsohon ma'aikaci ne"
"Ba kuɗi aka bani ba, senator ma'aruf Indabo ne"
"A kan me zai saka ka nemo masa wani ɗan daba, menene
alaƙarsa da ɗan daba yana sanata?"
Nasir ya girgiza kai ya ce "Nima ban sani ba Abba"
"Baka sani ba, kawai ka karɓa ka fara yi, Nasir idan
baka ji tsoron Allah a kan aikinka ba, a tsiyace zaka shekara talatin kana
wahala, ka gama aiki ka zama abin tausayi.
Na fara yadda wasu abubuwan kai ka ta'azzara su, kamar
Nabila ta fika gaskiya".
"Abba mutumin fa ɗan daba ne, da yake zubar da jini, da
aikata miyagun laifuka"
Major ya ce "To meyasa ba ku nemi kama shi a kan laifin
da yake aikatawa ba, wani zai ja ka gefe ya kuma tunzuraka, ba tare da ka san
abin da ya haɗa su ba, Nasir ka san aikinka kuwa? Kaga tashi ka je kawai
jeka"
Ya buɗe baki zai yi magana major ya ce "Jeka ba zan
sake magana da kai a yanzu ba, ina dai tunatar da kai muddin ka gauraya halal ɗinka
da haram, babu in da zaka je wallahi. Kuma ka ji tsoron Allah, kar masu ƙarfi
su din ga amfani da kai, a kan marasa ƙarfi, saboda kana saka wannan kakin
lokaci ne" Sosai kunya ta kama Nasir, saboda yadda asirinsa yake nema ya
tonu, na ya karɓi cin hanci, ya din ga matsawa Nabila da ƙoƙarin daƙileta a kan
nata aikin.
***
Cikin dare hasken farin wata ya gauraye ko ina, Viper na
tsaye a bakin window, yana shan sigari, hannunsa ɗaya yana kallon wayarsa,
kwanaki shida kenan rabon da su yi waya ko ya sanyata a idonsa, babban mamakin
da ta bashi, yadda ƙiri-ƙiri ya nuna mata yayi fushi, amma ko ta sake neman sa.
Haka kurum ya ji ya ƙara fusata.
Ya harɗe ƙafarsa, yana ci gaba da shan sigarin, kawai sai
watarana ta faɗo masa, Jauhar ta tsare shi a gida, ta hana shi fita ko ina,
kuma ta bashi kara uku na sigari kawai.
Cikin dare ta yi bacci, ya tashi ya fita tsakar gida, ya
shiga banɗakin tsakar gida, ya sha son ransa, ya daɗe hayaƙin ya ragu, sannan
ya koma ɗakin ya kwanta.
Ashe tun da ya tashi ya fita, tana kallonsa, yana kwanciya
ta tashi ta matso kusa da shi, ta saka hannu ta matsa bakinsa, ta sinsuna, dan
ta tabbatar masa ta san me yayi, ba ta ce masa komai ba, ta juya ta kwanta.
Kamar wanda ta kama yana alfasha, yayi tsuru-tsuru, ya rasa
me ma zai ce mata, kawai ya basar. Aka jima yana ƙoƙarin ya rungumeta, dan ya
mantar da laifin da yayi, ta tashi ta bar masa gadon, ta yi alwala ta tayar da
salla.
Asubar fari ba ta tashe shi ba, yaje masallaci ya dawo, a
gida yayi azkar, ya din ga 'yan kame-kame, amma taƙi kula shi, har gari ya
waye, sai da ya gaji ya ce "Ni fa guda uku na sha kawai ba da yawa
ba"
Ta kalleshi ta ce "Me fa?"
"Sigarin" ta ɓata fuska ta ce "Hakan ya
tabattar mini da zaka iya cin amanata wataran, ka yi abu ban sani ba"
Ya girgiza kai ya ce "Ai uku ce kawai ba wata mai yawa
ba, ki ke wani haɗe rai "
"To Allah ya baka haƙuri, na ga kamar na matsa
maka" daga haka ta ci gaba da sabgarta.
Ranar ba ta hana shi fita ba, ya zauna bai fita ba, ko zata
huce, har da yi mata aikin gida, amma ya kasa cewa ta yi haƙuri, ta tabbatar da
ya sha jinin jikinsa, duk ya damu, amma ya kasa ba ta haƙuri. Duk sallolin
ranar a jam'i ya yi su.
Kafin ya dawo daga sallar isha'i, ta sha kwalliya, yana
dawowa ta rungunmi abin ta, kamar ba fushi tayi da shi ba, iya punishment ɗin
nan da tayi masa, sai da ya ji kamar ya shekara a prison. Jauhar akwai iya
dealing ta cikin ruwan sanyi, a lokacin babu wani abin da yake shakka irin yi
mata laifi, saboda ta riga ta sanshi, ciki da bai ta san hanyoyin hukunta shi.
Sakin guntuwar sigarin yayi, ya koma ɗaki ya kwanta ya cigaba da tunaninta.
Da haka wani nannauyan bacci ya ɗauke shi, sai dai
kasancewar da ita ya kwanta a ransa, sai ya din ga mafarki da ita, mafarki mai
cike da shauƙi da nishaɗi irin na ma'aurata.
"Master salla fa, zaka rasa sallar asuba." tayi
maganar tana shafa sumar kansa.
Ƙanƙameta ya ƙara yi, yana tura kansa cikin wuyanta, da yake
fitar da daddaɗan ƙamshin turaren da yake matuƙar son jin tashinsa daga
jikinta.
"Viper wai ina zaka shiga a cikin pillown nan ne? Wai
ko dai ka sha wani abu bamu lura ba, tun ɗazu fa muke tashinka, ka tashi mu yi
salla dan Allah"
A hankali ya motsa, ya buɗe idonsa ya ga hasken fitilar
solar, ya haske ɗakin, sai a lokacin ya lura da ya ƙanƙame pillow.
Yayi miƙa tare da yin salati, ya kalli liti da yake tsaye a
kan sa ya ce "Akwai gas ne?"
"A'a ɗan kaɗan ne sosai, sai an yi refiiling ma zamu
iya dafa karin kumallo".
"Ɗora mini ruwa, ku yi sallarku zan yi wanka"
"Wai Viper meyake faruwa ne kwana biyun nan, ko ka fara
dawowa bil adama ne? Ni ina cewa ka yi wa addini hidima meyake faruwa"
Ashar Viper ya yi masa, ba shiri liti ya ce "Allah ya
baka haƙuri, ya ƙara lafiya"
Walid kuwa dariya yayi, ya ce "Allah ya ƙara, uban son
jin ƙwaƙwaf".
Bayan sun karya Baba ya kira Viper a waya, ya ɗaga suka
gaisa, ya ce "Aminullahi, dan Allah idan baka komai zuwa azahar ina son
ganinka"
"To Baba in sha Allah zan zo, nan gidan zan zo na same
ka?"
"Eh dan Allah"
"Zan zo in sha Allah"
"Yauwwa Allah ya yi maka albarka"
Viper ya amsa da Amin.
Ɓangaren Nabila ita ma kwanaki bakwan nan da suka yi, ba sa
magana da Viper, abin ya dameta, ƙishirwar son ganinsa ta addabeta, ga ayyuka
sun fara yi mata yawa, 'yat shaharar da tayi ta kwanan nan, ya sanya take ta
samun cases ko ta ina.
Ban da masu nuna suna sonta, manyan mutane da suke sonta da
aure.
Yau da mafarkin da tayi ta tashi a zuciyarta, mafarki tayi
da mai kama da ita, wadda take da tabbacin jauhar ce.
Tana nuna mata inuwar mutumin da yake ɗaure cikin sarƙa a
baya, yanzu babu sarƙar, sai dai daga yanayin inuwar tasa, kamar a galabaice
yake, duk da babu sarƙar sai tangaɗi yake yi.
Tana murmushi ta cigaba da nuna mata shi, ta nufi in da take
nuna mata, sai dai da ta waiwaya ba ta ganta ba, tana ƙoƙarin ƙarasawa in da
mutumin yake, kawai ta farka daga baccin.
A hankali ta furta Viper, a gurguje ta shirya, tayi ta
trying lambarsa, amma yaƙi ɗagawa, ta din ga jin ko me zai yi mata, yakamata ta
kira shi, ta ji ya yake.
****
Ko da Viper ya je gidan su Jauhar, ya tarar da motoci a
ƙofar gidan, bai damu da ko me ake yi ba, ya kira Baba ya ce masa gashi nan
yana ƙofar gida.
Baba ya ce ya shiga kawai, ya ƙarasa ya shiga, babu wanda ya
kula a mutanen gidan, sai hafsa da suka gaisa ya shiga ɗakin Baba.
Alhaji mu'azzam ya tarar, da Abbu, da kuma shi kansa Baban.
Gefe ya samu ya zauna a ƙasa ya gaishe su, sai dai da ya zo
kan Abbu kamar an yi masa dole, haka ya gaishe shi.
"Ya gida ya ƙoƙarin Kuma?" Baba ya tambayi Viper.
"Lafiya ƙalau Alhamdilillah"
"Ina yan uwan naka?"
Viper ya ce "Su na gida, nikaɗai na zo".
Baba ya ce "babu laifi, Al'amin"
"Na'am Baba"
"Na san zaka yi mamakin kiranka da muka yi, babu
tsammani da wuri haka.
To bakomai bane ya janyo, Nabila ta same ni, tayi mini wata
magana ne, kuma nima naga hakan yakamata, duba da yadda abubuwa suka wakana.
Al'amin su iyaye, ba a fushi da su, kuma duk lalacewarsu
iyaye ne, balle babu lalacewa a cikin iyaye, yakamata ka sasanta da mahaifinka,
yanzu ina jauhar, ina mahaifiyarka, ina ɗan uwanka, ko da kuɗi ba zaka sake
ganinsu a gidan duniya ba. Dan haka ka yi haƙuri, mun san mu masu laifi ne a
wurinku, amma ku yi haƙuri a yafe ya wuce dan Allah ba dan halinmu ba".
Viper ya yi shiru, kamar mai nazari amma bai ce komai ba.
Abbu ya ce "Al'amin, nauyinka da nake ji, ya sanya na
kasa nemanka gaba da gaba na nemi afuwarka, na san in dai dan halina ne, da
abin da na aikata maka, ba zaka sake kallona a matsayin mahaifi ba, amma ba dan
halina ba domin Allah.
A ƙaddarar rayuwarmu, na ɗauki darasi da dama, daga illar da
mutum zai yi wa rayuwarsa, shi ne auren mace domin buƙatarsa kawai, ba tare da
tunanin abin da gobe ka iya haifarwa ba.
Duk da ni a zatona dan gobenku na auri Rahila, amma ta ci
amanata, kuma nima na san da laifina na rashin bibiya da tantance abin da take ɗora
ni a kai, amma dan Allah ka yi haƙuri Al'amin, ka yafe mini ka dawo gida mu yi
rayuwa a ɗan abin da yayi mini saura na rayuwata"
Alhaji mu'azzam ya ce "Viper, ka yi haƙuri dan Allah,
duk wani abu da ya faru, ya wuce tun da bawan Allah nan shi yayi silar zuwanka
duniya, kuma wani abin idan bai yi maka ba, wani yayi maka, yana cikin tashin
hankali da damuwa sosai"
Viper ya numfasa ya ce "Ko a baya ni ban ƙi Abbu ba,
ina matuƙar ƙawazucinsa da son kasancewa tare da shi, Abbu shi ne ya ƙi ni ya
kore ni, amma tun da yanzu ya nemi na dawo shikenan, ya riga ya wuce. Amma ni a
yanzu na girmi zaman gida, ba zan iya rabuwa da su Walid ba, sai na tabattar da
rayuwarsu ta inganta suma, kamar yadda suka rayu da ni lokacin da kowa yake
mini kallon mara amfani.
Kuma idan na koma gidan nan, zai iya cigaba da haddasa
husuma, wanda ni kuma bana fatan hakan".
Abbu ya ce "Hakan ma na gode Al'amin, Allah ya ƙara
shirya mini kai, dan Allah idan ka samu dama, ko zuwa gobe in Allah ya kaimu ka
zo gida, ina son mu yi wata muhimmiyar magana da kai"
Viper ya jinjina kai, Baba ya ce "Bari a kawo abinci mu
ci baki ɗaya"
Al'amin ya ce "Baba ayi mini uzuri dan Allah, ana
jirana ne, ayi mini afuwa" ya fita ya sanya takalmansa ya tafi.
Rarrashin Abbu suka din ga yi, saboda yadda jikinsa yayi
sanyi, dan gani yake yi, kamar da wani abun a ran Al'amin haryanzu, duk da ya
san halinsa farin sani, ba kowane lokaci ake iya gane yanayin sa ba.
***
Washegari Nabila ta kira Abbu a waya, domin ta ji ya ake
ciki, ko Al'amin ɗin ya saukko?.
Abbu ya ce "Kin san ɗan nawa hukuma ne sai da rarrashi,
ya ce dai ya wuce, amma bai tsaya mun ci abinci tare ba, yau dai ina jiransa,
ina son ya zo zamu yi magana da shi, idan ya zo kin ga sai na ɗan ƙara saka ran
ya saukko ko?"
Sai ya ba wa Nabila tausayi, ta ce "Abbu ka kwantar da
hankalinka, Viper yana sonka haryanzu, shi ba abubuwan da ka yi masa ne suka
dame shi ba, korar da ka yi masa ce kawai ta tsaya masa, amma tun da ya ce maka
ya yafe, ya yafe ɗin ne, dan Allah ka kwantar da hankalinka Abbu, idan ma bai
zo ba na yi maka alƙawarin kawo maka shi har gida in sha Allah"
Abbu ya ce "To shikenan, na kwantar da hankalina, Allah
ya saka miki da alkhairi"
"Amin bakomai Abbu, sai anjima"
Shahida ita tayi girke-girken zuwan Al'amin, Rahila na gefe
tana kallonsu, sai yan surutai take da ƙanan maganganu saboda ƙwaƙwalwarta ta
riga ta taɓu, amma har aka yi sallar magariba Viper bai zo ba.
Hakan ya ƙara sanya Abbu karaya nesa ba kusa ba, domin kuwa
yana da muhimmiyar magana da yake so su yi.
Shahida tayi ta ci gaba da bashi haƙuri, amma a washegari ma
still babu Viper, babu dalilinsa, tun Abbu yana sanya ran ganinsa har ya sare.
****
Viper yana ganin kiran Nabila, amma ya shareta.
Message ta turo masa "Ka ɗaga wayata, is an
emergency"
Sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga yana hura hanci.
"Vi wai dan Allah meyake damunka ne, kai mutum nawa ka
yi wa laifi kai ko neman yafiyar ma baka yi, kai shikenan komai naka babu
sauƙi, Abbu ya nemi afuwarka, amma ka yi burus, ya ka ke so yayi ne?.
Idan shi ma ya mutu sai ka huta, ni dai nayi iya yi na,
sauran na bar wa Allah, ban san ya zan yi maka ba kuma, Abbu yana Asibiti ya
yanke jiki ya faɗi, ana addu'a Allah ya sa ba ɓarin jikinsa ne ya taɓu ba, yana
ta kirana a waya, yana gaya mini kamar baka yafe masa ba, ya nemi ka je ka ƙi
zuwa, to yanzun ma Viper idan ka yi ra'ayi ka je, idan ba ka yi ra'ayi ba
shikenan, ni fara gajiya da halinka"
Ba tare da ta kashe wayar ba, ya ajiye wayar, yana duba
agogon hannunsa, sauran awa ɗaya ya shigo garin Kano, ranar da ya baro wurinsu,
aka tura shi Jos, kuma yana sane da kiran da Abbun yayi masa, dajin da yaje ko
network babu.
Sai dai ƙirjinsa ya din ga bugawa, hankalinsa yayi mummunan
tashi, ya shiga fargaba da zullumin rasa abu mai muhimmanci a rayuwarsa karo na
babu adadi.
Ayshercool
08081012143
Har zai sake bin Nabila a waya, kawai ya tuna yadda ta ɗaga
masa murya, ya ɓata masa rai ƙwarai da gaske, kawai ya fasa kiranta ya kira
Walid a waya.
Walid ya ɗaga ya ce "Mazaa ka ƙaraso ne?"
"Ina hanya, yarinyar nan ta kira ni ta ce Abbu yana
Asibiti, ka je ka bincika mini"
Cikin tashin hankali Walid ya ce "Asibiti kuma? Wane
Asibitin? Nabila ce ta gaya maka?"
Viper ya ce "Ban san wane asibitin ba ne, ka tambaya
mini kawai ka bincika mini, idan ma mutuwa yayi kawai ka gaya mini ba wani
abu"
"Ahh no, in sha Allah yana raye, tambeyata yana wani
Asibitin?"
"Manta da ita, ka duba mini kawai"
"Ok yanzu kuwa in sha Allah"
Allah ya sa yana wurin shayinsu, dan haka ya tashi ya tafi
gidansu Viper, ya rasa wa zai aika gidan, Shahida ta fito hannunta riƙe da
leda.
Gaida Walid tayi, ya amsa. Ya ce "Ya ake ciki, mai
zamani ya kirani, ya ce an kwantar da Abbu a asibiti na zo na bincika
masa"
Ta kalle shi ta ce "Dan Allah da gaske shi ne ya ce ka
zo ka bincika masa?"
"Eh mana, yanzu muka gama waya da shi ma"
Ta ce "Damuwar yaƙi zuwa, ya sanya Abbu ya faɗi, Abbu
yana ta roƙon ya yafe masa amma yaƙi damuwa da hakan" tayi maganar tana
share hawaye.
"Kin ga ki daina kuka, ya gaya mini ya zo sun haɗu a
gidansu jauhar, har Abbu ya buƙaci ya zo su yi magana, wai wani wuri aka tura
shi a Jos, wurin ko network babu, shiyasa bai zo ba, amma wani Asibitin
ne?"
"Can zan je yanzu, in da muke ganin likita ne"
suka rankaya suka tafi, yana ta bata haƙuri.
Ga mamakinsa a can suka tarar da Nabila da Sumayya, har da
Murtala abokin aikin Sumayya.
Suka gaisa da Nabila, cikin damuwa Nabila ta ce "Oga
walid, Vi ba ya kyautawa ko kaɗan, wane irin abu yayi haka fisabilillahi?"
"Allah ya baku haƙuri, mun gode sosai da kulawarku a
kan babanmu"
Nabila ta ce "Ai ba dan shi muka yi ba, dan Allah muke
yi, dan kuma ƴar uwata, ayi mutum sai zafin rai, komai ba zai yi a hankali
normal kamar kowa ba"
Walid ya ce "A'a fa, muna fa kawar miki da kai duk da
haka, kar ki ƙure mu Barrister, ba fa haka Jauhar take yi mana ba"
Nabila ta ce "Taɓ ai ita wannan, idan ana ganin ɗan
aljanna a duniya sai a nunata, ina zan iya, wataran sai baƙin ciki ya kasheni.
Kayi ta yi wa mutum magana, amma ya gagara responding ma, ya ƙame yana
harararka"
Yayi murmushi ya ce "Yanzu yaya mai jikin?"
"An yi masa alluran bacci ne, an ce mu jira kar wanda
ya shiga sai bayan 2hours tukuna, amma jikinsa Alhamdilillah. Nima sumayya ce
ta gaya mini ba shi da lafiya, sun yi waya da wannan sistern ta shi" tayi
maganar tana nuna Shahida.
Tun da Nabila ta fara magana Shahida take kallonta, a nan
take ƙara gano bambancin Jauhar da Nabila, Jauhar ba zata taɓa reacting a
hasale haka ba, komai girman laifin da ya yi mata kuwa. Wannan kuma a tsaye
take, ba ta ɗaukar komai a hankali.
Har mamakin yadda take faɗar maganganu a kan yayanta take
yi.
Viper ya sake kiran Walid a waya, "Ya mutu ne ko
kuwa?"
"A'a lafiyarsa ƙalau, yana samun kulawa ta
musamman"
"Walid, dan Allah kar ka ɓoye mini, ba wani abu ka gaya
mini kawai, ba yau na saba ji ba" yayi maganar haɗe da wani irin
wahalallen numfashi na razani.
"A'a wallahi da gaske nake yi maka, muna tare da Nabila
ma, ko na baka ta tabattar maka"
"A'a, tura mini adress ɗin, yanzu zan ƙaraso in sha
Allah"
Shahida dai gefe ta koma ta zauna, tana ta kallon Nabila,
babu yadda za ayi ka ce ba Jauhar ba ce ba.
"Haryan ƙoƙarin tantancewa ki ke yi ne?" Ta ji
maganar Walid unexpected.
Ta ce "Eh wallahi, haryanzu na kasa yadda, abin mamaki
yake bani"
Yayi murmushi ya ce "Haka ne"
Sai da aka yi kusan awanni uku, sai ga Viper, tamkar an
hankaɗo shi, ya yi duhu sosai da sosai, idanunsa jawur, yana zuwa Walid ya miƙe
ya nufe shi.
"Walin yana ina?"
"Yana cikin ɗaki, likitoci sun ce kar a shiga" ai
take ya ture Walid, ya nufi ɗakin, ana kar ya shiga, amma ko waiwayowa bai yi
ba ya shiga.
Wata nurse ya taho ta ce "Ya za ku bari ya shiga,
isasshen bacci ake so yayi"
Walid ya ce "Dan Allah ki yi haƙuri, yanzu a kan ku
hana shi shiga, duk sai ya tayar mana da hankali, ku ƙyale shi dan Allah".
Viper kuwa gaban gadon Abbu yaje ya durƙusa, ya ɗora
hannunsa a kan cikinsa, ya tabattar da yana numfashi, sai dai still ya kasa
yarda, gani yake kamar Abbun ya mutu ne.
Ya cigaba da ta tattaɓa duk wasu sassa a jikin Abbun, domin
tabattar da yana raye.
Caraf ya ji Abbun ya riƙe hannunsa, ya ce
"Al'amin"
"Na'am, sannu ya jikin naka?"
"Na ce ka zo, amma kaƙi zuwa, ko dai haryanzu baka yafe
minin bane ba, k yi haƙuri, idan baka yafe mini ba na mutu a haka, na san sai
Allah ya tambayeni, tun da kana da hakki a kaina"
"Dan Allah ka daina maganar nan, kaima sai ka tafi ka
barni? Ba ƙin zuwa nayi ba, aiki aka tura ni wani daji can jos, shiyasa ba wai
ƙi nayi ba"
Ya kalli Viper ya ce "Aikin menene haka?"
"Zan gaya maka amma sai ka warke tukuna in sha
Allah" yayi maganar yana shafa saman hannun Abbun.
"Matso na rungumeka nima, nayi kewarka sosai"
Viper ya gyara zamansa, ya ɗora kansa a ƙirjin Abbu. Ya ɗora
hannunsa a kan sumar Viper ya ce "Lallai kana cikin maraici, da jauhar na
nan ba zan ganka da wannan sumar ba, Allah ya yi mata rahama" Viper ya yi
shiru ya kasa magana.
"Al'amin"
"Na'am"
"Kana ganin idan muka nemi auren yar uwar jauhar za su
bamu? Ina son yarinyar ita ma"
Viper ya ɗago ya ce "Ka samu ka koma baccinka, zan je
na yi salla"
Abbu ya ce "To, ka ci abinci ma, ina ga Shahida ta kawo
abinci, sauran yaran nawa duk su ci abinci, na ji daɗi yadda duk suka zo suka
tsaya tare da ni, Alhaji Bashir ma bai daɗe da tafiya ba, na ji daɗi sosai da
sosai."
"Tom, amma ka yi shiru" ya fita.
Ya tarar daga Nabila sai Walid, da Shahida, liti ma ya zo
duk suna zazzaune.
Yana fitowa suka fara tambayar sa, ya jikin Abbun.
Fuskarsa babu walwala ya ce "Da sauƙi har ma mun yi
magana, bari na je na samu wuri na yi sallar la'asar"
Nabila na nan zaune, jira take yi, Alhaji mu'azzam take yi
wa kwatance, zai zo ya duba Abbu.
Bayan mintuna talatin, liti ya amsa waya, ya kalli Nabila ya
ce "Viper ya ce ki je"
"Ina?"
"Wallahi ban sani ba, sai dai ki kira shi"
Sai da ta ja lokaci kamar ba zata tashi ba, sai kuma ta
tashi, tana tunanin ta ina ma za ta ganshi da zai ce ta je, me ma za ta yi
masa.
Tana tafe tana waige-waige, kawai ta ganshi a can wani wuri
yana amsa waya, ƙarasawa tayi, ta tsaya ya gama wayar, da alama wayar ta shafi
aiki ne, yayi ya kammala sannan ya waiwayo ya kalleta.
Yanayin kallon da yake yi mata, sai da ta tsorata kamar zai
kai mata duka, ya tsuke fuska sosai ya fuskanceta, sannan ya ce "Daga rana
mai kamar irin ta yau, ko a waya, ko a zahiri idan ki ka kuma yi mini shouting,
ko gaya mini duk maganar da ta zo bakinki, i will mercilessly deal with you, i
am not your mate" motsa baki tayi za ta yi magana, amma ta kasa, ya juye
mata ya koma mata Vipernsa sak, fuskar nan sam babu annuri.
Amma ta sake tattaro jarumtarta ta ce "Ba shouting na
yi maka ba, gani nayi idan ba haka nayi maka ba ba zaka zo ba, kuma...
"Keep quiet malama, idan ma na zo idan ban zo ba ina
ruwanki?" Ta ɗago ta kalleshi, ya sake tsareta da idonsa, dolenta tayi
ƙasa da kanta.
Ya nuna ta da yatsansa ya ce "This is my last warnin,
idan ki ka sake zaki sha mamaki, wuce mu je" zungui-zungui tayi gaba, ya
biyo bayanta, zuciyarta kamar ta fashe dan haushi, deep down kuwa a zuciyarsa
kewarta yake yi, yanayin yadda tayi masa magana, da yadda ta daina kiransa ne
ya ƙara tunzura shi, amma ya ji daɗin ganinta a wurin mahaifinsa da yadda ta
nuna damuwarta.
Tun daga nesa liti ya hango su, ya san babu arziki faɗa suka
yi, ya zo ya zauna Shahida ta zuba masa abinci ta bashi.
Liti sai tambayar ƙwaƙwa yakw yi wa Viper, a kan aikin me
yaje yi.
Suna zazzaune sai ga Alhaji mu'azzam ya zo ya duba baban
Al'amin, aka yi sa'a ya ɗan sakar masa fuska, suka yi magana a kan rashin
lafiyar Abbu.
Har suka keɓe suka yi magana, a kan aikin da yaje yi, tare
da shi Viper aka kai ɗan mama can kudancin Najeriya, in da zai karɓi nasa horon
na musamman, sai dai bai kai na Al'amin tsauri da takura da kuma daɗewa ba, shi
shekara guda kawai zai yi.
Suka gama maganar, Kankarofi yayi musu sallama zai tafi,
Nabila ta ce "Honorable dan Allah ku ajiyeni a hanya, na samu abin
hawa"
Kankarofi ya ce "Babu damuwa, ina motarki ne?"
"Ta lalace ta zama gwangwani"
Ya ce "To Allah ya mayar da sabon alkhairi, amma babu
risk a a hawanki public vehicles, ina masu fita da ke?"
"Ai na gama aikina, ba wani abu da zai same ni in sha
Allah" sai ya lura kamar tana sane, basarwa yayi ya ce "Shikenan
muje" yayi musu sallama amma Viper bai sake cewa komai ba.
Wami abu mai zafi ya tsayawa Viper, ganin sun jera ita da
Alhaji mu'zzam sun yi gaba, amma ya dake ya shanye, yayi shiru ya maze, dan
idan ya ce zai tanka ɓatacciya za ayi.
Yana Asibiti har dare, Liti ya ce "Boss ka koma gida,
mu sai mu kwana da Abbun, ka je ka samu ka huta"
Viper ya ce "Ba zan iya tafiya ba, gani nake idan na
tafi komai zai iya faruwa, gara na kwana da shi kawai".
Walid ya ce "Ba gamu ba, babu abin da zai faru in sha
Allah"
"I am sorry, ka bar ni kawai"
Walid ya ce "To shikenan, na ga dare ya fara yi, bari
na raka Shahida gida, sai na dawo"
Viper ya ce "To a sauka lafiya"
A hanya Shahida take ƙara bawa Walid labarin yadda aka kashe
Abba, ya jajanta masa sosai da sosai, saboda abin gwanin ban tausayi, sa'ar da
aka yi shi ne an kama yaran da suka kashe shi ɗin.
Bayan ya dawo tare suka kwana su uku tare da Abba, yana kan
gado, suka yi shimfiɗa a ƙasa, suna hirarrakin su ƙasa-ƙasa dan kar su takura
masa, har aka jima kuma su ka yi bacci.
Viper kuwa idonsa biyu, ransa a matuƙar ɓace da abin da
Nabila ta yi masa, ga kuma kewarta da take ta addabar ruhinsa.
Abbu kuwa kallonsu yayi, yadda suka jere su uku a ƙasa a
kwance, ya sake jinjina girman ikon Allah. Dukkannin su, kowanne gidansu daban,
ba su haɗa wata alaƙa ta jini ba, sai ta rashin jin su, amma sun riƙe juna da
tsantsar amana, da ƙauna.
Da ya motsa dukkaninsu ƙoƙarin su, su ji meye damuwarsa me
za su yi masa, sai ya ji ina ma ace duka nasa ne.
Da haka gari ya waye, suka takura Viper ya je gida ya yi
wanka sai ya dawo su ma su tafi.
Haka aka yi, ya tafi ya je yayi wanka, ya ɗan huta, ya ga
message ɗin Nabila "Assalamu alaikum, ya mai jiki? Ba zan samu zuwa yau
ba, daga wurin aiki zan je ganin likita, idan kuma na kammala da wuri zan zo in
sha Allah, ayi masa sannu" guntun tsaki ya ja, ko arzikin gaisuwa ma bai
samu daga gareta ba sai surutu.
Lokacin da ya koma, Shahida ta kawo abincin rana, suna zaune
a ɗakin Abbu, ya samu har ya tashi zaune ya yi wanka, ya ci abinci.
"Ka dawo?"
"Eh ya jikin"
"Alhamdilillah"
Shahida ta gaishe shi ya amsa, liti kamar wanda aka matsa
sai cewa yayi "Wai babarku ba ta san an kwantar da Abbu bane, naga tun
jiya ba ta zo ba"
Shahida ta ce "Ai tun da aka kashe Yaya Abba, ita ma ba
ta da lafiya, shiyasa ba ta zo ba"
Walid kamar ya zabga wa Liti mari, ko ina ruwansa oho.
Viper ya ce "Muhsin yakamata kuma ku je ku huta".
"Eh bari mu ci abinci tukuna, ko a gidan ka bar mana
abin da zamu ci?"
Viper ya harare shi, ya ce "In dawo jiya, yau kuma na
hau yi muku girki"
"Dama can ma ai mu muke yi, bayar da order kawai ka ke
yi, sai ma idan an yi kai ta cewa bai yi daɗi ba"
Walid ya ce "Yaushe ma ya fara cin abincin, sai da
Nabila ta shigo rayuwarsa, yanzu carryover wanda bai ci ba yake yi". Abbu
kallonsu kawai yake yi yana murmushi, yana mamakin yadda suka iya zama da
Al'amin, gashi dai ba dolensu ba, amma da shi da halinsa suke iya zaune da shi.
Suka ci abincin suka tashi suka fita.
Viper ya ce "Shahida ta tashi ta tafi gida, tun da
akwai wata mara lafiyar a gida, ba ta yi musu ba, ta tashi ta tafi.
Abbu ya kalli Al'amin ya ce "Aminu yaran nan suna
matuƙar ƙaunarka, sai suka ƙara shiga raina, Allah ya ƙara muku haɗin kai"
"Amin, amma meye ya kashe wa Shahida aure? Ina fatan ba
wani rashin kyautawar tayi ba"
Abbu ya girgiza kai ya ce "Nima ban san ainihin abin da
yake faruwa ba sai yanzu, uwatta ce ta bawa mai kuɗi, da akwai wanda take so,
ta ce ita ba shi take so ba, mai kuɗin zata aura".
"Abbu kuma ka bari?"
"Ya zan yi mata, ta dage tana nuna mini 'yar ta ce, sai
kwanan nan Shahidan ta same ni, wai ita ta kai shi kotu, Khul'i za su yi, ya
sauwwaƙe mata, na tambayeta dalili ta ƙi faɗa, na kira shi mijin nata ya ce shi
ma bai san dalilin ta ba, sai da na ritsa uwarta, sannan take gaya mini wai ba
shi da lafiya, tsawon shekaru ukun da suke zaune" guntun tsaki ya ja, ya
ce "Da ina nan gaskiya ba zan bari ayi wannan abin ba, yanzu shikenan ta
zama bazawara"
"To yaya zan yi, makaranta dai nake so ta zo ta koma,
gaba ɗaya tausayinta nake ji, halinta ya sha bamban da na uwatta da yar uwatta,
ba yadda muka iya da ƙaddara".
Viper ya yi shiru bai sake cewa komai ba.
Abbu ya sake numfasawa ya ce "Yakamata na gaya maka
abin da nake son na gaya maka, kar lokaci ya ƙure mini"
Al'amin ya tattara hankalinsa a kan Abbu.
"Zuwa yanzu Al'amin babu wani wanda ya san kan
kasuwancina sosai, duk wanda na janyo sai yayi ƙoƙarin cutar da ni. Sannan
akwai gadonka na mahaifiyarka da kuma ɗan uwanka, sun zama manyan kadarori, kar
karɓi abinka ka tallafi rayuwarka, kuma ina son ko bayan babu raina, ka cigaba
da jujjuya harkar kasuwancin nan, kar abun da zan bar maka ya ƙare ba tare da
ka tsaya da ƙafarka ba"
Viper ya gyara zamansa ya ce "Babu in da zaka mutu ka
je"
Abbu ya yi murmushi ya ce "Faɗa kawai ka ke kaima"
Ya rausayar da kai ya ce "Abbu already ina aiki, ni ba
zan iya kasuwanci ba"
"Aikin me?"
"Sojoji nake yi wa aiki, ba zan iya haɗawa ba, ko zan
haɗa ma, sai dai wani ya riƙe mini, wasu alfarma nake nema ka yi mini"
Cikin sauri Abbu ya ce "Na menene?"
"Na farko, ina so ka taimaka ka jagoranci Abdallah,
liti ka mayar da shi wurin mahaifinsa, a nema masa afuwa, dan na san nine silar
barinsa gida baki daya, ko ba ni bane, na taka muhimmiyar rawa a hakan.
Abu na gaba kuma, a yanzu Walid ba shi da kowa sai Allah sai
ni, maraya ne, yan uwansa ba sa ta tashi, duk masu ƙaramin ƙarfi ne. Ina
roƙonka ka sanya mini shi a harkar kasuwancinka, ka bashi babban gurbi, sannan
ka aura masa Shahida" shiru Abbu yayi yana kallon Viper.
Ya cigaba da cewa "Na san zaka ga abin wani iri, amma
bana zaɓen tumun dare, daga ni har su muna ta ƙoƙarin gyara kura-kuranmu, mu
sake sabuwar rayuwa ne. Kuma Walid mutum ne mai amana, ba zai taɓa ci maka
amana ba, duk rintsi duk wahala, Walid ba ya cin amana, ni na yarda idan ma ba
zaka saka shi a kan naka kasuwancin ba, ka bashi gidana ɗaya, a sayar da sauran
kayana, a koya masa harkar kasuwancin katakon, sannan ka aura masa Shahida. Ba
kuma dan na cutar da ita ko rayuwarta ba, zan iya yi maka rantsuwa da Allah, ko
Walid ba shi da komai, Shahida ba zata wahala ba, ina ƙara tabattar maka da mai
amana ne. Shi liti shagon shayinmu yake so, ya ce ko na mutu shi zai gajeta tun
da shi ne ya rayata ba ni ba, ya je ya ƙarata da ita, Walid ko duk wani abu da
na gada za a ƙarar, dan Allah a bashi ba zan iya biyan bawan Allah nan
ba".
Abba ya jinjina kai ya ce "Na ga alama, shikenan babu
damuwa idan ma ya fi hakan za ayi masa, sai dai ita Shahidan ka yi magana da
ita idan ta amince, ka san halin mata kar ayi abu, azo a ji kunya"
Viper ya ce "In sha Allah ba za a ji kunya ba, Walid
mutum ne mai haƙuri da kawaici, kuma mai amana"
"To shikenan, ba zan taɓa maka kayan gadonka ba, amma
zan ɗauke shi a kasuwa, zan bashi auren Shahida muddin ta amince, ni ma na
shaida ɗawainiyar da yake yi da kai, Allah ya tabattar mana da alkhairi".
Likita ne ya shigo yayi musu bayanin jikin Abbu da sauƙi,
jininsa ne ya hau sosai, kuma an samu ya sauka, zuwa washegari za a iya
sallamarsa.
Maƙwabta da abokanan kasuwancin Abbu suna ta zuwa duba Abbu,
suna ta so su magantu da ganinsa tare da Viper, ya ƙara girma, da kwarjini
sannan akwai alamun ƙarin nutsuwa a tattare da shi.
*****
Bunkure ta kasa zaune ta kasa tsaye, saboda rashin sanin
abin yi, dan tun bayan da Nabila ta damƙa mata kundin ƙorafe-ƙorafen da zata
kai ma'aikatar Shari'a a kanta, ta rasa yadda zata yi. Gashi ma'aikatar
shari'ar duk waɗanda ta sani yanzu ba sa nan, an yi musu canjin wurin aiki,
tana ta kasa kunne ta ji ta ina za a nemeta.
Tsananin damuwa ya sanya ko baccin kirki ba ta iya yi, sai
ta sha tayi mankas tukuna.
Duk da abokan aikinta, na ta ƙarfafa mata gwiwa, da nuna
mata cewa za ta iya fuskantar ƙalubalen da yake gabanta. Ga mutane duk sun dawo
daga rakiyar Foundation ɗin ta, kuɗaɗen da suke tallafawa ƙungiyar domin
taimakon mutane, duk sun daina saboda sun gano cewa cuta ce.
A dalilin Nabila, mutane da yawa suka samu 'yancin yin
magana, tare da sanarwa duniya tallafin da aka nema da sunansu, ko aka basu,
ana dawowa a karɓa, wasu kuma ma ba a basu.
Sosai social media da gidajen rediyo, maganar bunkure ta
yamutsa hazo, ko ina zancen ake yi.
****
Washegari aka sallami Abbu daga asibiti, suka koma gida.
Shahida na ɗakinta, tana kwance tana karatun Alqur'ani,
Viper ya ƙwanƙwasa mata ƙofa, ta yi masa iznin shiga, ya shiga ya zauna, ya
dube ta ya ce "Kin gama idda ko?"
Ta jinjina masa kai, ba tare da ta ɗago ba.
"Magana nake son mu yi, shawara ce, ba dole zan yi miki
ba, zaki iya cewa a'a idan abin bai yi miki ba"
Ta jinjina masa kai.
"Na san zaki ji abin wani banbarakwai, amma ba zan yi
miki zaɓen tumun dare ba, kuma ba dole zan yi miki ba, ina son Abbu ya haɗa
aurenki da Muhsin ne, abokina Walid. Na san zaki yi mamaki, ko ki ji babu daɗi,
saboda duba da yanayin mummunar rayuwar da muka yi a baya. Dama kowane mutum
tara yake bai cika goma ba, duk wani halin kirki na mutum, sai an tarar da shi
da wani hali da ba a so, kuma yanzu muna ta ƙoƙarin gyara ɓarnar da muka yi ne
a baya. Ina baki tabbacin Muhsin mutumin kirki ne, kuma zaki ji daɗin zama da
shi, ya fi ni nagarta da halacci, da zunzurutun haƙuri. Kema kuma na san
mutuniyar kirki ce, a dalilinki ina fatan ya ƙara shiryuwa, amma ina baki
tabbacin zaki iya dukan ƙirji a gaba, ki ce kin yi dacen mijin aure. Amma ba
dole nake yi miki ba, na tuntuɓe ki ne dai da maganar, kafin nayi masa, idan
kuma ba kya son sa babu wani abu shikenan shawara ce".
Sai da Shahida ta ji dummm, tabbas Walid ma tsohon ɗan sara
suka ne, kuma bata san shi da wata sana'a ba, amma kwana biyun nan da take zuwa
asibiti, suka ɗan zauna tare, akwai nutsuwa da dattaku a tattare da shi, kuma
karo na farko kenan, da Al'amin ya yi ƙoƙarin yin wani abu a kan rayuwarta, ta
san ba zai cutar da ita ba, dan haka ta numfasa ta ce "To yaya duk yadda
ka yi dai-dai ne, in dai ka amince, nima na yarda".
"A'a kar ki yi mini haka, ki gaya mini abin da yake
zuciyarki, ko kuma dai na fara turo shi ya nemi yardar ki da kansa, amma magana
ta domin Allah bamu iya soyayya irin wadda ku ke so ba, sai dai ki koya masa,
kin san mazaje we are always serious" yayi maganar yana ɗan murmushi.
Ita ma murmushin ta yi tana sunkuyar da kai.
Nan ya cigaba da koɗa mata nagartar Walid, da ƙoƙarin da ya
din ga yi wa rayuwarsa.
Za ta iya cewa, ba ta taɓa zama sun yi hirar kirki mai tsawo
da yayan nata ba sai yau.
Da daddare ya bar gidan, ya tafi can gidan da suke zama,
Walid suna ta faɗa da liti, a kan liti yayi musu wanki, ya ce ba zai yi ba, ya
saka Viper ya dawo da ɗan mama yayi, tun da ya fi jin maganar sa, dama ɗan mama
ne yake yi musu.
Viper ya ce "Rabu da shi mai laya, kai ka kusa shiga
daga ciki, a din ga haɗa kayan ka masu datti a bayar wanki, ka bar Liti"
"Wace zata aure shi, bai iya komai ba sai saka aiki,
daga kai har shi?"
Viper ya ce "Seriously, Walid Abbu zai baka auren
Shahida, abin da ya rage maka kawai ka nemi yardarta" waro ido Walid yayi
ya ce "Wane Walid ɗin?"
Liti ya yi shewa ya ce "Sai dai kai maigida, Allah ya
ja zamaninka ka daɗe ka yi ƙarko irin na dabino, Allah dai ya saka da
alkhairi"
Walid ya ce "Kai fa mahaukaci ne wasu lokutan, uban
waye zai bamu aure a haka? Mai zamani ka daina wannan wasan"
Viper ya kwanta ya ce "Ba wasa nake yi ba, da gaske
nake, ka nemi soyayyarta kawai, aure zan yi muku, Abbu ma ya san zancen. Kai
kuma liti sai dai ka nemo da kanka, tun da na san kai ba gwaninta ake yi maka
ba"
Walid ya ce "Dan Allah a daina wannan wasan, wai waye
ma zai bani wani aure? Dan Allah ka bari ta samu mutumin kirki ta aura"
Viper ya tashi zaune, ya dafa kafaɗar Walid ya ce "Kai
ma mutumin kirki ne, shiyasa ba zan so wata ta samu ba, alhalin ga ƙanwata, ku
daidaita kawai sai da safe" yana gama maganar ya kwanta.
Walid ya zauna kamar soko yana rarraba ido, Liti kuwa dariya
ya din ga tuntsirawa, saboda har gara Viper ma da Walid, dan shi kamar ma
tsoron mata yake ji, shi ko da wasa bai taɓa tare budurwa ba.
Liti ya din ga tsokanarsa, yayi masa banza ya kwanta, hango
Shahida yake yi, yarinya nutsatsiya yar gayu, wai kuma ta aure shi shi dai abin
bai yi masa tsari ba.
Washegari za su je duba Abbu da yamma, kamar ya fasa zuwa,
saboda gaba ɗaya kunya ce ta kama shi.
Kasancewar Viper ya riga su tafiya, ya sanar wa Shahida, su
Walid za su zo duba Abbu, dan haka ta shirya, za su yi magana ita da Walid ɗin.
Duk abin nan, rahila ba ta san me ake shiryawa ba.
Sai bayan la'asar, su Walid suka zo, duk yadda yake ɗan
sakin jiki da Abbu su yi hira kasa yayi, ya din ga mutsu-mutsu, kamar ya nutse
a ƙasa, liti yana ankare da shi, kamar ya yi dariya.
Liti ya ce zai je ya dawo, ya fita ya yi nasa wuri, bayan
sun yi wa Abbu sallama, a ƙofar gida Viper ya ce "Na yi mata magana, za ta
fito ku yi magana, mu haɗe a jungle"
"Dan Allah Viper ka ce da wasa ka ke yi, ni wallahi ban
san me zan ce mata ba, wallahi kunya nake ji"
"Malam yakamata ka girma, ka yi mata tatsuniya if you
like" zai sake magana, suka yi ido huɗu da Shahida, ta fito cikin doguwar
rigar abaya maroon.
Viper ya yi gaba yana murmushi, Walid ya ɗan diririce.
Ta ƙaraso tayi masa sallama ya amsa, ta saci kallonsa, dogo
ne shi ma, sai dai bai kai Viper jiki da tsawo ba, kuma yana da haske sosai,
sai dai laɓɓansa baƙi ƙirin, idanunsa kuma jajaye, yana da dogon hanci da gemu
kaɗan ba mai yawa ba.
"Sannu ya jikin Abbu?"
"Da sauƙi Alhamdilillah"
"Amm na san wataƙila mai zamani ne ya takura miki, idan
ba kya so na, ki rabu da shi kawai, Allah ya zaɓa miki miji nagari, rigimarsa
ce kawai ta saka ya ce wai zai aura mini ke" yadda duk yake a rikice ne ya
sanyata murmushi ta ce "Yaya Muhsin, mu yi addu'a mana, bamu san me Allah
ya ɓoye ba, mu nemi zaɓin Allah, in dai nima zaka kula da ni, ka din ga lallaɓa
ni kamar yadda ka ke yi masa ai ba wani abu" sunkuyar da kai ya yi yana
murmushi, sai dai kamar ya zuba da gudu dan kunya. Bai fi mintuna goma ba, yayi
mata sallama.
Da ya koma can gidan da suke, kamar wanda ya aikata zunubi,
liti ya saka shi a gaba, ko murmushi yayi, sai ya ce tunanin Shahida yake yi,
ya hana shi sakat.
Da daddare Shahida ta kira Viper, ta tambaye shi ya suka je
gida. Maimakon ya bata amsa, sai ya miƙa wa Walid wayar.
Tayi masa ya yaje gida, sannan ya ce zai ɗauki lambarta a
wurin Viper.
Washegari da sassafe, Viper ya shirya ya fice ya bar su, dan
yai zai koma wurin likitan ƙwaƙwalwa, kuma yana son ya ga Nabila.
***
Ƙarfe tara na safe, Nabila ta fito falon madam Halima,
hannunta riƙe da jakarta, da court ɗin ta, kawai ta ga Viper a falo, suna
magana da Madam.
"Mummy good morning"
"Morning sweetheart, kin fito?"
"Eh, Good morning" tayi maganar tana kallon in da
Viper yake, bai amsa ba, ya ci gaba da magana da Madam.
Kitchen ta nufa, kusan mintuna biyar, madam ta tashi ta
shiga ɗakinta, Viper ya bi bayan Nabila.
Sai da ta tsorata da ganinsa unexpected.
Wuri-wuri ta yi da ido tana kallonsa.
Ya sauke ajiyar zuciya ya yi ya ce "Abin da ki ka yi
mana kina ganin kin kyauta ko? Nayi tafiya mai hatsari, ya na je ya na dawo,
bai dame ki ba? Kin yi mini laifi amma ba ki iya bani haƙuri ba, yau zamu koma
asibiti you don't even care to call me. And a gabana ki ka bi kankarofi, duk
dan ki tura mini takaici".
Tayi shiru ta ɗan kalle shi ta ce "Ba faɗa ka ke yi
mini ba, komai ka yi ta hantarata"
Ya ce "Ke ki ke yin abin da zan hantarekin ai. Akwai
muhimman batutuwa da yakamata muyi discussing, kawai kina wani fushi mara
dalili.
Ana ta matsa mini lamba, za ayi posting ɗina wurin aiki, da
zarar na kammala aikin da nake yi a kan Indabo, ina son ayi aurenmu dai-dai
lokacin da zan tafi aiki"
"Kai da wa?"
"Ni da waye a nan wurin?" Yayi maganar yana
tsareta da idanunsa.
"Allah ya baka madadin matarka da ka rasa, ba zan iya
aurenka ba Vi, i fulfill my work on you, amma mu bar wannan maganar
Please"
Sai da ya nazarceta sannan ya ce "Ƙarya ki ke yi mini
da ki ka ce ki na so na kenan?"
Ta ɗan ja da baya, saboda tsoron yadda idanunsa suka fara
sauyawa ta ce "Ko ma ya ne, kai ka fara discouraging ɗina, a lokacin da ka
yi fatali da tayina, ka ce mini ba wannan maganar, bayan jauhar baka kallon
kowace mace. Nima kuma na gamsu da hakan ba zan iya auren mijin 'yar uwata ba.
Amma Alhamdilillah na cimma burina a kanka, tun da ka dawo yadda take fata kafin
ta mutu".
"Ba kya so na kenan? Ba zaki aure ni ba?" Ta
jinjina masa kai, tana kawar da kanta gefe alamar eh.
Juyawa ya yi, ya fara takawa, wayarsa ta fara ringing, ya
cirota ya saka a kunnensa ya ce "Na'am"
A razane ya ce "What Walid ɗin? How?"
Ayshercool
08081012143
Cike da gigicewa ya ce "Gani nan, kar ka sanar da
kowa"
Saboda rikicewa, sai ma ya rasa ina ne hanyar fita, sai daga
baya.
Nabila ta ce "Vi menene? Meyafaru?" Bai kulata ba,
yana ƙoƙarin fita, Madam Halima ta ce "Au nan ka biyota, na zata tafiya ka
yi ai" sai dai yanayin fuskarsa ya nuna mata akwai damuwa.
"Viper menene? Meyake faruwa ne?"
"Walid, gayen nan da muke zuwa da shi, na baro su a
gida, ya fita yin refiiling, shi ne bai koma ba, Abdallah ya bi hanya ya tarar
da cylinder gas ɗin a gefen hanya, da takalmansa da agogonsa, that means ɗauke
shi aka yi" tuni kamanin Viper suka canza, saboda tashin hankali.
Yana ƙoƙarin fita, madam ya ce "Wait Viper, tattara
hankalinka ka nutsu, tunani al'amarin nan yake buƙata da nutsuwa, ba gaggawa
ba.
Yanzu na san Joseph ya ƙaraso, zai fita da Nabila, ya kai ka
ku je a tabattar da abin da yake faruwa, sannan ka kira Oga ka sanar masa da
halin da ake ciki" ya jinjina kai ya wuce cikin hanzari ƙirjinsa na bugawa
da sauri.
Da sauri Nabila ta ce "Bari na bi shi Mummy, kar ya je
yayi wani abun, kin san shi da zuciya da wutar ciki"
"Kya ma gama gulmarki ne daughter, Allah ya bayyana shi
cikin aminci" ta amsa da Amin.
Kafin ta ƙarasa har ya riga ya shiga mota, sai da ta haɗa da
sauri, sannan ta ƙarasa ta shiga baya, kasancewar gaban motar ya shiga.
Tana shiga ta ji Viper yana waya "Liti kar ka matsa
daga wurin, gani nan zuwa, kuma kar ka gaya wa kowa, ka kira wayarsa ne?"
"A gida fa ya manta ta a kan window ya fita"
"Shikenan gani nan zuwa"
"Nabila na ta son tayi masa magana, amma ta san a ƙule
yake da ita, dan haka ta ja bakinta ta tsuke"
A haka suka isa dai-dai wurin da liti yake, yana ta
buge-bugen waya.
Yana zuwa ya tarar da Liti a hanyar shiga rukunin
kamfanunnukan da a bayan su gidan nasu yake, bai taɓa komai ba, yadda ya tarar
da takalman walid, da cylinder gas da agogonsa a yashe.
Viper ya yi shiru, yana nazartar wurin, Joseph ma fitowa ya
yi, suna dudduba wurin, ya kalli Viper cikin broken English ya ce "Oga, da
alama sai da aka yi kokowa da shi kafin a tafi da shi"
Su na nan tsaye Viper yana duba wayarsa, sai ga motar Civil
defense sun zo wurin, su ka yi wa Liti tambayoyin da yakamata, suka yi
investigation a wurin. Su ka yi ta bawa Viper haƙuri, da ƙoƙarin kwantar masa
da hankali.
Jiki a sanyaye Nabila ta ce "Ka yi haƙuri, in sha Allah
yana cikin ƙoshin lafiya, bari na tafi"
"Ki shiga mota, mu ajiye ki, zan bi bayan civil defense
ɗin nan, na ji me ake ciki"
Ta jinjina masa kai, ta shiga mota suka tafi suka ajiyeta a
wurin aiki.
"Idan kin kammala, ko za ki je wani wurin, ki kira ni
kar ki fita, i don't think you are safe".
Nabila ta ce "Ok shikenan na gode"
Abu kamar wasa, aka shafe kwana biyu, babu Walid babu ɗuriyarsa,
hakan ya ƙara ɗaga hankalin Viper fiye da tunani, tun yana ɓoye-ɓoye, har
maganar ta fita, sai da ya sanar da Abbu. Duk da ba wata shaƙuwa tsakanin ta da
Walid, amma ta san shi da yayanta, kuma yana nuna damuwa da abin da ya shafe
su. Sosai hankalinta ya tashi, Abbu kansa da shi ake ta zarya.
Alhaji mu'azzam ma sai kwantarwa da Viper hankali yake yi,
liti ya fi kowa shiga damuwa, dan kuwa har wata irin muguwar rama yayi, a
ƙa'ida shi ne yakamata yaje yayi refiiling ɗin, ya tsaya jan jiki, Walid ya
zuciya ya tafi ya yo, tsautsayin ya faɗa masa. Duk in da ake tunanin samun
Walid, an duba ba a same shi ba, Liti har wata irin rama yayi.
Duk ƙaunar Viper da Abinci, baya gabansa, ba ya iya ci,
saboda damuwa da tashin hankali.
Gashi yana ta gargaɗin Nabila a kan yawo anyhow, dan ya san
tun da aka farmaki Walid, a kowane lokaci za a iya sake kai ma wani na kusa da
shi hari.
Misalin ƙarfe biyu da rabi na dare, yana zaune ya kasa
bacci, yana ta tasbihi, yana fatan Allah ya kuɓutar masa da Walid, wayarsa ta
fara ringing.
Cikin azama ya ɗaga, ya saka a kunnensa ya yi shiru.
"Ban yi mamakin jin idonka biyu ba, saboda sai da na
duba, na duba na tabattar da wanda na kama, shi ne na kusa da zuciyarka, da taɓa
shi zai tabattar maka da ina sane da kai, ban manta da kai ba".
"Ina ka kai Walid, kar ka bari sabgar nan ta juye zuwa
wani abu daban, ka fito da shi, duk in da ka kai shi"
"Ta daɗe ba ta juye ba, ka manta tare ku ka din ga yi
mini aiki a baya, ai ina ganin kamar shi haryanzu ba shi da wani muhimmin tabo,
da bangar siyasa tayi masa kamar kai.
Ai talaka ba shi da wani amfani, ban da ku yi mana hidima,
amma kun dage zaku kai ni ƙasa, zan saki Walid ne, a lokacin da wa'adin zaman
Abdul yasar ya ƙare a gidan yari. Sannan zan sake duba abu mai muhimmanci a
gareka, na yi masa ɗaurin talala, yana raye amma kamar matacce, kamar yadda ka
saka aka ɗaure mini ɗa a ƙasashen waje. Na samu labarin kana aiki a kaina, sai
ka ga bayana, gani gaka, ɗan halak ka fasa".
Viper ya ce "Wannan shi ne kuskure na biyu mafi muni da
ka aikata Indabo. Ni da kai muke harƙalar nan, kuma batun ɗanka, hukunci aka yi
masa dai-dai da abin da yayi. Ina mai gargaɗinka da kakkausar murya ka saki
Walid, idan ba haka ba zan razana duniyarka da abin da baka taɓa zata ba,
awanni arba'in da takwas kawai ka ke da su, kuma ka fara ƙirgawa daga
yanzu" yana gama maganar ya kashe wayar, ya dafe kansa, cike da wata irin
nadama da danasanin biye wa Indabo ya din ga aikata ɓarna.
Wato a duniya idan amfaninka ya ƙare kai ba a bakin komai ka
ke ba, meyasa zai ɗauki Walid maimakon ya ɗauke shi, tun da da shi yake yi, ba
Walid ba.
Da sassafe Viper ya tafi barrack, saboda Nabila, yana tsoron
ita ce next target na indabo, tun da tare suke yin komai da ita, sai dai tayi
noticing rama da kuma damuwa a tattare da shi.
Tana ta shiri, yana falon madam yana jiranta, gani yane da
ya kawar da kai, komai na iya samunta.
"Vi" ya ji ta kira sunansa.
"Ka karya sai mu fita" ya girgiza mata kai bai ce
komai ba.
Ta fuskanci damuwa na ƙara saka shi miskilanci da rashin
magana.
Nabila ta sake marairaicewa ta ce "Dan Allah ka ci ko
kaɗan ne, duk ka yi wani iri"
"In ci Abinci ban san halin da ɗan uwana yake ciki ba?
Shi ya ci? Duk a dalilina, shikenan duk wanda ya raɓe ni a haka rayuwarsa za ta
ƙare a wahala da tashin hankali, menene laifin Walid ne?"
Cikin rauni ta ce "Na sani, na kuma fahimce ka, amma
hakan babu abin da zai canza. Addu'a da ci gaba da jajircewa ce kawai za ta
kawo mafita, ka yi haƙuri dan Allah Vi ka saka wani abu a cikinka" ya ƙura
mata ido na wani ɗan lokaci, kawai ya tashi tsaye ya ce "Idan kin gama ki
same ni a mota" sosai tausayin sa ya mamaye mata zuciya.
Jiki a sanyaye ba tare da ta samu ta yi breakfast ɗin ba, ta
bi bayansa.
Da suka kai ta wurin aikin ma, har ta shiga ta ji kamar ana
bin ta, ta waiwaya ta ga shi ne ya biyota. Ba ta ce masa komai ba, ta shiga
office ɗin ta ya bi bayanta.
Kujerar cikin office ɗin ya samu ya zauna, bai kulata ba,
ita ma ba ta ce masa komai ba, ta ci gaba da aikinta, gani yake yi yana kawar
da kai, wani abun zai sameta ita ma.
Har ta gama aikinta na ranar yana zaune, sannan Liti ma ya
saka an mayar da shi cikin barrack.
Duk yadda ya bi wayar Indabo abu ya gagara, sai taƙi shiga,
gashi gani yake yi kamar babu wani ƙoƙari da ake yi a kan neman Walid ɗin.
Kwatsam Nabila na shirye-shiryen tafiya, ya sake jarraba
wayar Indabo, cikin sa'a ta shiga kuma ya ɗaga, Viper ya miƙe cikin zafin rai
ya ce "A karo na ƙarshe, ina Walid yake?"
"Babu wata barazana da zaka yi mini Viper, sharuɗɗa zan
saka maka, wanda dole sai ka bi su. Na farko ka saka wannan yarinyar ta janye
ƙorafin da ta shigar a kan Bunkure a ma'aikatar Shari'a, sannan ka tattaro duk
wani bincike da ka yi a kaina, na yinƙurin tona mini asiri, da wannan wayar da
ka ke amfani da ita ka bani, sai a saki Walid, idan ba haka ba wannan banzar
yarinyar ita ce next target ɗina a kanka, sai na saka an wulaƙanta ta,
wulaƙanci mafi muni na tagayyara rayuwarta, fiye da yadda ka ke tunani" Viper
ya ɗaga kai ya kalli Nabila da take kallonsa, amma ba ta san me ake cewa ba.
Viper ya ce "Saboda abin da nake shiryawa a kanka ne ya
sanya ka kashe P.A?"
Indabo ya ce "Eh, ban damu da a in da ka samu labarin
hakan ba, iyaka na san ba ka da wata cikakkiyar shaida a kan ni ne kashe shi,
duk wanda ya ci amanata, sai na kawar da shi. P.A ya ci amanata ya haɗa kai da
kai, domin yana ganin ya zame ya bar ni shi ne zai sanya ka ƙyale shi".
Viper ya sauke numfashi mai zafi, cike da dana sanin, sanin
Indabo a rayuwarsa ya ce "Idan kuma ina da shaidar kisan kan da ka yi wa
P.A da hannunka fa?"
"Gwargwadon yadda ka ci gaba da zurafafawa, gwargwadon
yadda zan ci gaba da hura wutar da ka ke ciki, ba dai kana yi wa kanka iƙirarin
ƙarfen cikin wuta ba, idan ba zaka ɗakku da hannu ba, zan ci gaba da iza wutar
da ka ke ciki, sai ta kai matakin da zata narka ka"
Viper ya datse laɓɓansa na ƙasa, ya fesar da wani zazzafan
numfashi, ya ce "A ina zan kawo maka abin da ka buƙata?"
"Zan turo maka adireshin wurin, kuma ba kana bayarwa za
a sake shi ba, sai na ba wa ƙwararru sun tabattar da ingancin abin da ka bayar,
kuma a yau ba gobe ba, yarinyar nan ta janye maganar Bunkure"
"Na ji, zan yi abin da ka ce, amma yarjejeniya ɗaya
idan ka saɓa, wutar da kake ƙoƙarin narkani da ita, kai zata ƙona" Indabo
ya katse kiran.
Viper ya kalli Nabila, ta ce "Vi wai lafiya?"
"Zamu je ma'aikatar shari'a, ki janye ƙorafin da ki ka
shigar a kan Naja'atu Bunkure"
A razane Nabila ta ce "Saboda me?"
"Saboda haka na ce" yayi maganar a fusace.
Nabila ta ce "Akwai dalili dole, ka gaya mini, idan ba
haka ba zan iya janyewa ba gaskiya, gaba ɗaya wahalata a kan lamarin matar nan
na ɓata lokacina, kawai kuma sai na janye?"
"Sai kin janyeta, babu wani bayani da zan yi miki,
dolenki ki janye" yayi maganar yana kallon Nabila, yana hasko cikin bala'i
da tashin hankalin da zai shiga, idan aka taɓa ta.
****
Goye yake da Jaka a bayansa, a dajin Allah shikaɗai, sai
waige-waige yake yi.
A kan babura da manyan bindigu, wasu mutane suka ɓullo, suka
zagaye shi.
"Ka ajiye jakar, ka ɗaga hannayenka sama" wani
yayi masa umarni.
Ya ajiye jakar, ya ɗaga hannayensa, ɗaya ya karɓi jakar, ya
zazzage, ya dudduba ya ce "Kayan ne"
Wani daga cikinsu ya ce "Za a aika shi ne?"
"A'a kai ba a ce ba, jami'i ne, asirinmu zai iya
tonuwa, mu ware kawai".
Suka ja baburansu, suka yi gaba, suna tafiya aka turo masa
saƙo.
"Ke je dutsen da yake in da kuke, ka ɗauki
gawarsa" kamar mahaukaci, haka Viper ya sake gigicewa, daga in da aka saka
shi kai kayan, bai isa in da Walid yake ba, sai bayan awanni uku.
Yana zuwa ya lura da ba a lokacin aka yar da shi a wurin ba,
kamar ya kwana a wurin, an ɗaure masa hannu da ƙafafuwa, an tura masa tsumma a
baki, an ɗaure wuyansa da wayar cable, ga jikinsa ko ina a farfashe saboda
duka.
Fuskarsa ta kumbura suntum, duk jini, ƙanan ƙwari sai bin sa
suke yi.
Kamar yaro ƙarami, Viper ya fashe da kuka yana kwance Walid,
ya kwance wayar da take wuyansa, ya ɗaga shi yana kuka, yana kiran sunansa.
Ya ƙanƙame shi a jikinsa, kawai ya ji zuciyarsa na bugawa, a
hankali.
Zumbur ya miƙe, yana ambaton Allah, ya goya shi a bayansa,
gani yayi idan ya tsaya buge-bugen waya, zuciyarsa zata daina bugawa, haka ya
kwashi tafiya, har rukunin kamfanunnukan nan, ya ce su taimaka masa su kai
Walid Asibiti.
Kai tsaye barrack ya tafi da shi, ya kai shi asibitin cikin
bariki, babu wani jinkiri aka rufu a kansa, yana da rai bai mutu ba, sai dai
babu tabbacin ya tashi.
Duk da Nabila tana cike da ɓacin rai da damuwar sakata janye
ƙorafi da yayi, ba tare da ya yi mata bayanin komai ba, amma tana ganin saƙonsa
na yana Asibitin cikin barrack tare da Walid, ta tashi tana tsuma, ta saka
hijjabi ta fita.
Yanayin da ta ganshi ne ya karya mata gwiwa. Ta ce "Vi
ya ake ciki?"
"Yana ciki sai dai babu ya rayu" yayi maganar yana
zubar da hawaye.
"Kayi haƙuri vi, ka kwantar da hankalinka, in sha Allah
Walid zai tashi da ikon Allah"
Sai ita ta kira su Alhaji mu'azzam, da Liti ta sanar musu an
ga Walid.
Babu jimawa wurin ya ɗinke da jama'a.
Hatta Abbu yana wurin, Shahida ma kasa zama tayi, sai da ta
biyo Abbun.
Abbu sai shi ya kama hannun liti, yana ta rarrashin sa, gaba
ɗaya ya firgice, an tuɓe Walid daga shi sai gajeren wando, duk jikinsa shaidar
duka, aka yi dressing ɗin raunukan jikinsa, aka ɗebi jininsa ana ta
gwaje-gwaje.
Duk wani abu da za a buƙata wurin bincike, sai da suka ɗauka,
kafin a taɓa shi.
Ɗaya daga cikin likitocin ya fito, ya ce "Ku kwantar da
hankulanku, Alhamdilillah. He's responding to treatment. Vitals ɗin sun dawo
normal, in sha Allah muna saka ran ya farka a kowane lokaci. Idan ya farka zamu
tura shi sauran gwaje-gwaje.
Sai a lokacin suka ɗan samu nutsuwa.
Cikin dare aka kira Viper wurin ogansa, Ya sha faɗa a kan
abin da ya yi ba tare da ya sanar musu ba. Shi dai yayi shiru, dan a halin da
yake ciki, babu umarnin wanda zai iya tsayawa saurara, ya sha faɗa duk da yayi
bayanin abin da ya faru a yanzu.
Ya numfasa ya ce "Jami'anmu sun tafi, za su dawo da
wayar, duk wanda aka kama da wayar ɓatar da shi zamu yi, cin amanar ƙasa da
ƙoƙarin tonon asiri ne, duk wanda aka kama da wayar ba jami'inmu ba" Viper
dai yayi shiru, domin an ce ya saurari punishment ɗin da za ayi masa.
****
Sai da Walid ya kwana a Asibiti, ya wayi gari, sannan ya
motsa ya farka.
Liti ne ya ga ya motsa hannunsa, ya tashi da sauri, ya nufe
shi yana zazzare ido yana kiran sunansa.
Walid ya buɗe ido ya kalli Liti, ya yinƙura zai tashi Liti
ya ce "Kai kar ka tashi, a asibiti kake"
Ya ɗaga kai yana kallon ɗakin, Viper ya ƙaraso, yana cewa
"Mai laya, kalleni ka gane ni?"
Murmushi ya yi ya ce "Na kiyayi mai zamani"
Viper ya rasa me ma zai yi dan farinciki, ya zuba masa ido,
yana haɗiye ƙwalla.
"Na kasa tashi ku ɗaga ni"
Viper ya sako hannu ya ɗago Walid, sai da ya yi ƙara saboda
ji yayi kamar su na kakkarya shi.
Liti ya ce "Wai dan Allah meyafaru, suwaye suka ɗauke
ka?"
"Jama'ar Indabo ne, wai sai na gaya musu abin da Viper
yake shiryawa a kansa. Na ce ban sani ba, na daku tun da suka ɗauke ni, a ɗaure
nake, sai ranar da suka shaƙe mini wuya da cable na zata mutuwa ma nayi
wallahi"
Viper ya ce "Muhsin, ka yi haƙuri, duk ni ne sila ka
yafe mini dan Allah"
Walid ya ce "A'a rashin jinmu ne dai sila"
Likitoci sun yi mamakin ganin Walid a zaune yana ta magana.
Sai dai aka yi masa wanka, aka saka masa kaya, ya ci abinci,
aka je aka yi masa hoto, aka tarar da karaya a hannunsa na dama.
Da yamma Viper yaje har gida, yake gaya wa Abbu yanayin
jikin Walid, suka yi ta murna, Shahida tana son ta ce masa tana son sake zuwa
duba Walid, amma ta kasa.
Babban abin da ya tsaye mata, bai wuce jin yadda yake bawa
Abbu labari cewa Walid ba shi da uwa ba shi da uba, ba wa ba ƙani, shikaɗai
yake gararambarsa, dangin iyayensa ba masu zuciya bane ba, duk ba su da ƙarfi,
amma babu wanda ya damu da shi a cikin su.
Lokacin da Viper ya yi wa Shahida tayin auren Walid, ita dai
ba ta ji tana son shi ko akasin haka ba, amma abin da Viper yake gaya wa Abbu,
na cewar maraya ne gaba da baya, sai ta ji wani irin matsanancin tausayinsa, ya
cika mata zuciya. Ta ji zata iya kowace irin sadaukarwa, domin rayuwa da shi.
Sai dai ta sha mamaki jin cewa wai har ya farfaɗo ya tashi
yayi magana, dan lokacin da ta je, baya cikin hayyacinsa.
A cikin daren ranar, aka yi wa Walid ɗori a hannu, wajen
ƙarfe biyu aka fito da shi, liti ya ce Walid sai ya matsa masa saman gadonsa
sun yi squating, tun da shi ne zai kwana da shi, kar yaje yana bacci a zo a
sake sace shi bai sani ba.
Abin ka da an kwana biyu babu bacci, yana hawa gadon, sai
bacci, Walid kuwa zugi ya hana shi bacci, tun bayan da alluran da aka yi masa
suka sake shi.
Da Viper ya zo ya tarar da su, fizgo liti ya so yi daga kan
gadon, amma Walid ya hana shi.
Duk wata sangarta da rashin mutunci, idan suna tare liti ya
iya ta, amma idan aka fita fagen rashin mutunci na 'yan daba, babu wasa.
Viper ya ce "Shahida na gaisheka, ta ce ayi maka
sannu"
Kawai yayi murmushi yana kawar da kansa gefe.
"Au ba zaka ce kana amsawa ba? Aishikenan. Ni dai ina
ta sake yi wa Allah godiya, da Allah sa ka farfaɗo, da ka mutu ba zan yafe wa
kaina ba, kuma da tarayyar mu, ba ta da wani amfani, Allah ya ƙara tsare mini
ku, ya baka lafiya".
Walid ya ce "Tarayyar mu tayi mini rana ni, Viper nifa
abin da ka yi mini, ban ga wani abu da zai sameka na ja da baya na barka, babu
shi. Ka yi mini da aljihunka da jikinka, da lafiyarka babu wanda baka wahalata
mini....
"Ka daina wannan maganganun, bau ne past ya riga ya
wuce, kuma ni mahaifiyarka tawa ce, a haka na ɗauki abin"
Yayi murmushi ya ce "Mai zamani, wanda zai tsaya maka,
a lokacin da baka da komai, ka ke neman taimako, ba tare da tsangwama ko
tunanin samun wani abu daga gareka ba, baka da babban masoyin da ya wuce shi,
shiyasa da kai da mai gida dodo, ba zan gushe ba ina yi muku fatan alkhairi, da
roƙa mana gafarar Allah"
Viper ya ce "Nima hakan take ai, a duniya yanzu bani da
tamkarku, da kai da wannan garujen" yayi maganar yana nuna liti.
Walid ya kalli liti yana dariya.
"Ya fi ni shiga tashin hankalin rashin ganinka, baya
bacci, baya iya cin abinci wai ina zai saka kansa, babu kai ɗan mama"
dariya suka yi tare, liti kuwa bai san suna yi ba.
****
Ƙaton ɗaki ne babba sosai, ɗauke da computers, da wasu
na'urori, Viper yana zaune a kan computer da shi da wasu a cikin wurin.
Wani video ya kunna, aka saita a jikin majigi, Videon babu
murya, amma Imdabo ne a ciki, yayi wasu maganganu, P.A yana ja da baya, kawak
ya harbe shi sau uku da bindiga.
Viper, mutumin nan yaƙarsa sai da techniques, ba za su taɓa
bari a hukunta shi a cikin ƙasar nan ba, ya aka yi ka samu Videon?.
"Eh kamar yadda na gaya maka da farko ne, P.A ɗin sa ne
ya samo mini wasu informations ɗin a kansa, saboda a zaman kotu ya ɗauka za a
ambaci sunansa, yayi hakan da a wanke shi.
Lokacin da Indabo ya buƙaci ganinsa, na bashi cameran, na ce
ya saka a gaban rigarsa, zan din ga ganin komai, ni kaina ban yi zaton zai
kashe shi ba".
Mutumin ya dafa kafaɗar Viper ya ce "Ka kwantar da
hankalinka, na san yadda ka ke ji a zuciyarka a kan mutumin nan, kuma na san
legally ba zasu hukunta shi ba, tun da yanzu ayi shiru da maganar tuhumar da
ake yi masa. But you have my support hundred person, either legally or
illegally sai mun ɗauki mataki a kansa. Saboda ba shi da amfani a cikin al'umma
ko kaɗan, da kunya ace irin wannan ne suke mulkar al'umma, amma ba wani abu in
sha Allah"
Cikin damuwa Viper ya ce "Sir na baku recording na
wayar da muka yi da shi, yarinyar da zan aura, tana cikin hatsari sosai da
sosai, ban san me zai iya yi mata ba, ba zan iya jurewa ba idan ya taɓa ta, ga
aikinta da ta sha wahala a kai ya salwanta"
"Bai salwanta ba Viper, kuma ina baka tabbacin babu
abin da zai sameta, babu kuma abin da zai samu wani naka, kar ka damu"
Viper ya jinjina kai yana jin ƙwarin gwiwa.
Asibiti ya koma wurin Walid, ya tarar da Shahida, ta
yayyanka masa ayaba a kan plate, ta ajiye masa yana ɗauka da hannun hagu yana
ci, yana ganin Viper ya zabura, kamar wanda yake aikata rashin gaskiya, sai da
Viper ya so yayi dariya, amma ya maze.
A haka Nabila ta zo ta tarar da su, tayi masa sannu, Walid
yayi ta yi mata godiyar suna ɗawainiya da shi.
Nabila ta ce "Vi ai su suka sha ɗawainiya, dan Allah
tun da ka farfaɗo ka saka shi ya ci abinci Please, haryanzu baya mayar da
hankali, duk ya rame. Ya fi yi mini kyau lokacin da kumarinsa"
Walid ya ce "Vi an ce ka din ga cin abinci ka
rame"
"Zan zageka da kai da Vi ɗin"
"Allah ya baka haƙuri, an hanamu faɗar master, Vi ɗin
ma an hanamu, to ai shikenan"
Nabila ta rausayar da kai ta je bayan Viper ta yi ƙasa da
murya ta ce "Zamu je ganin likita kar mu makara fa" ɗagowa yayi ya
kalleta, kamar ba zai tashi ba, sai kuma ya tashi ya nufi hanyar fita.
Fitarsu ke da wuya ya tsaya cak, ya waiwayo ya kalleta ya ce
"Kar ki sake ƙoƙarin yi mini yawo da hankali, ko kuma nuna kin damu da ni,
bana son yaudara" yayi maganar yana nunata da yatsansa.
"I don't fake it, kai baka san halin da ka saka ni ba,
lokacin da na nuna maka so saboda Allah. Na ji da farko i fake it, daga baya
kuma da gaske na ƙaunace ka Vi, yakamata ƙwaƙwalwarka ta tunatar da kai,
abubuwan da ka yi mini, kuma ka gaya mini. A gabanka abokinka har ce mini yayi
bani da class, ina yawo a cikin maza, duk dan ina sonka, ina fatan daga kaina,
zaka din ga kiyaye abin da zaka gaya wa mace, mata bama mantuwa.
Duk motsin da nayi ban taɓa burgeka ba, kullum cikin kyarata
ka ke yi, amma haryanzu ina yi maka kallon abu mai muhimmanci a gareni,
mussaman kulawar da Jauhar ta samu a wurinka, ka yi mini afuwa Vi, bana fatan
ƙuntata zuciyarka".
Cikin tsananin dakiya da jarumta, ya jinjina kai, ya ce
"Na fahimta"
Duk yadda ya so cire Nabila daga zuciyarsa abu ya gagara,
sai a lokutan nan, da ta fara yi masa wulaƙanci ya ga ashe ya shaƙu da ita,
shaƙuwa ba ta wasa ba.
Cikin ikon Allah Walid ya samu kulawa sosai da sosai, gashi
ba shi da ƙan jiki, nan da nan jikinsa ya fara warkewa, sai dai ya kan manta da
ba shi da lafiya, idan yana riƙe da wayarsa, Shahida tana turo masa saƙonnin,
babban abin da ya ƙara yi wa Shahida daɗi, ita kanta kunyarta Walid yake ji,
balle yayi kule-kulen mata, saɓanin mijin da ta rabu da shi, saboda yana da kuɗi,
yan mata kowa ma kulawa yake yi, kishi kamar ya kasheta, gashi ba abin da yake
iya amfana mata.
***
Sallamar da ake ta dokawa a tsakar gida ne, ya sanya
dattijon mutumin, sauke farin tabarau ɗin fuskarsa ya ce "Waye ne?"
Ya bankaɗo cikin ɗakin ya ce "Nine, ko har an manta da
ni ne, nake ta sallama aka yi shiru?"
Dattijon ya ce "Ina fa, waye ya isa ya manta da sarkin
gida? Maraba lale da Abdallah"
Liti ya ƙarasa ya na faɗin "Likkafa ta ci gaba, gida ya
sha gyara"
"Yau kai ne a gidan ka tuna da mu kenan?"
"Ai kullum kuna raina, na san ina zuwa dattijuwarka za
ta tayar mini da hankali, ta saka ka kore ni"
"Hmm sannu, na samu labarin ɗaya uban naka yayi free,
kotu ta wanke shi ko?"
"Aiba shikaɗai ta wanke ba, har mu, ai bamu da wata
nutsuwa idan yana cikin damuwa. Ban ga tsohuwar nan ba, ko ta rasu"
"A'a ni uwata ba ta mutu ba, tana nan ƙalau, sun fita
da gyatumarka"
Liti ya ce "Lallai ta sha miya, amm Alhaji, dama na zo
baƙi ne, wata bazawara ce take so na, shi ne ta turo iyayenta, suka zo nema
mata aurena wurinka, tana fatan zaka bata ni"
"Ikon Allah, ita bazawarar"
"Eh, amma dan Allah kar ka yarfa ni, ko ka tona mini
asiri ka ce wai ba na ji, abu ne da aka yi shi ya wuce, yanzu na shiryu na
daina, dan Allah kar ka ce musu wai bana ji, kaga sirikaina ne"
Alhaji ya yi dariya, ko bayan shekara dubu, Abdallah ba zai
canza hali ba,duk da Ya lalace yana son abin sa, amma gwaggo mahaifiyarsa ke
nema tayi masa baki, saboda soyayyar da yake yi masa, kuma hakan yana da alaƙa
da tsanar da ta yi wa babar litin ya ce "To Baba, ba zan yarfaka
ba"
Liti ya fita waje, yayi musu iso, Abbu ne tare da Baba,
mahaifin jauhar, da kuma Viper.
Alhaji ganin Liti da manyan mutane, ya tashi ya karɓe su
cikin girmamawa. Bai fi sau biyu ya taɓa ganin Viper, yanzu da kyar ya gane
shi, saboda lokacin da ya san shi yana da ƙuruciya sosai.
Nan Abbu ya gabatar masa da kansu, tare da gaya musu abin da
ya kawo su, a kan yayi haƙuri, ya yafewa Liti, tun da yanzu duk sun watsar da
shirirtar da suka yi a baya, dama har da ƙuruciya.
Nan Alhaji yake sanar da su, yadda ya kai liti ƙasar waje
karatu, amma ya dawo an koro shi, sai ma shaye-shaye da ya koyo, ga rashin
kunya da yake yi wa kakarsa, wanda hakan ya ƙara tunzura shi a kan litin.
Viper ya ce "In sha Allah Alhaji, Abdallah ya shiryu ba
zai sake ba, dan Allah ayi mana afuwa, ayi haƙuri"
Alhaji ya ce "Dama baku muke ƙi ba, halayenku ne ba ma
so marasa kyau, Ubangiji Allah ya ƙara rufa mana asiri"
Nan kuma hira ta ɓarke a tsakanin su Abbu, tare da tattauna
manyan matsalolin da ya jefa yaran nasu ga halaka.
Bayan sun gama da gidan su liti, suna tafe, tausayin Walid
ya mamaye zuciyar Viper, su duk sun daidaita da iyayensu, shikuwa ba shi da
kowa, sai Allah sai barbaɗaɗɗun danginsa marsa amfani. Yayi Addu'ar Allah ya sa
Shahida ta rayu da abokin nasa cikin aminci da mutuntawa, mussaman da ya ga ya
fara sakewa da Shahidan.
Maganar Baba ce ta dawo da shi hayyacinsa da ya ce "In
sha Allah, gobe zan je gidan Major, mu yi wadda za mu yi, ya bani 'ya ta, na
ƙarasa riƙonta na aurar da ita, na fuskanci bai san zuru ba".
Ayshercool
08081012143
Abbu ya ce "A'a Alhaji Bashir, abi komai a hankali,
zamu je mu same shi sai a tattauna".
"Alhaji Ibrahim, na san na yi wa maitama laifi, amma
yadda yayi reacting ban ji daɗin hakan ba. Gaba ɗaya ya tsaya mu fuskanci juna
yaƙi, ya mayar da ni kamar maƙiyinsa nima fa a ƙa'ida yayi mini ba dai-dai
ba".
Sai a lokacin Viper ya ce "Baba dan Allah ka yi haƙuri
ku sasanta, wannan rashin jituwar taku, yana taɓa Nabila sosai da sosai.
Kuma haryanzu tana cikin barrack a zaune, ta rasa yadda ma
zata yi dan Allah ku yi haƙuri ku sasanta".
Baba ya ce "Ba ƙi na yi ba Aminullahi, na bashi
duk wata dama, a matsayin sa na wanda yake uba a gareta, kuma ya raineta, idan
ya gaji ni ya bani abata, nima na rayu da ita ko yaya"
Viper ya ce "Haka ne, kana da gaskiya. Amma ka yi
haƙuri dai, a bi komai a sannu, aje a same shi, ayi masa bayani, na san zai
fahimta in sha Allah" haka Viper ya ci gaba da rarrashin sa.
Alhaji kuwa hira suka ɗora da Liti, kamar ba barin gida
yayi, kusan shekara guda bai ganshi ba. Ya din ga bashi labarin gwagwarmayar da
suka sha, da halacci da kirkin matar Viper, tare da ba shi labarin yadda Nabila
ta shigo rayuwarsu, ashe 'yar uwar marigayiyya ce.
Sallama aka yi a tsakar gida, Alhaji ya amsa, Liti kuwa ya
tsuke fuska.
Sai da mahaifiyarsa tayi turus da ta ganshi, ta ce
"Abdallah yau kuma kai ne a gidan"
"Saboda ba sunan babanki bane ba, kuma ba sunan mijinki
bane ba, shiyasa ki ke faɗar sunan yadda ki ka ga dama kamar ke ki ka raɗa
masa, to sunan mijinki usmanu ki ka faɗa" tsohuwar da suke tare ta yi
maganar a hasale.
Ta mayar da idonta kan liti ta ce "Sannu ɗan nema, kai
kuma sai yau Allah ya dawo da kai, shanshani mai ƙafar gantali"
"An saka mini sunan kirki, saboda wani sunan mijinki,
kin ɓata mini suna wani liti. Kuma nan fa ke ki ka saka aka koreni, ba dole na
tafi ba, ni wallahi na zata ma kin mutu"
"Salamatu ce zata mutu ba ni ba, babarka ba"
"Kowa ma dai sai ya mutun nan, duk ƙulafucin mutum da
duniyar kuwa"
Alhaji ya yi gyaran murya ya ce "Baba gwaggo ce fa,
mahaifiyata ce" liti yayi shiru yana hararta.
Mahifiyrsa kuwa kallonsa take yi, ta zata tafiyar da yayi,
zai sake lalacewa ne, dan abin yana damunta, amma sai ta ga kamar ya ɗan nutsu,
babu askin banza, gashi normal shiga yayi, kuma babu alamar buguwa a tattare da
shi.
Har yamma yan tare da mahaifinsa, saboda ya fi shaƙuwa da
shi, yan uwansa duk mata ne suna gidan aure, shi ne kawai namiji.
Da yamma aka gama abincin dare, aka zuba masa, ya saka
fulasan a leda ya ce tafiya zai yi.
Alhaji ya ce "Ina kuma zaka je?"
"Can in da nake mana Aljaji"
"Au sake barin gidan zaka yi?"
Liti ya ce "A'a, dama zuwa nayi ai na gani, idan zaku
haƙura ku yafe mini to, idan kuma naga za a sake tozarta ni, idan na cika
wandona da iska nayi gaba, in tafi ikko. Amma Alhamdilillah na ji daɗi da naga
ba a hantare ni an koreni ba, wurin yan uwana zan koma, Walid ba shi da lafiya
yana Asibiti, ni nake kwana da shi, amma zan dawo ai. Na gode sosai da ku ka
yafe mini"
"Dama ba tsanarka muka yi ba babana, halayen da ka ke
yi ne bama so, amm Alhamdilillah daga kai har uban ɗakin naka, naga nutsuwa a
tattare da ku, Allah ya ƙara shirya mana ku"
"Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, na gode sosai da sosai
Alhaji"
Alhaji ya ce "Jeka Allah ya bayar da sa'a" ya amsa
da Amin.
Gwaggo ta fara masifa ta ce "Au barinsa zaka yi ya
tafi? Kana kallonsa?"
"Gwaggo ki yi haƙuri dan Allah, ba kowane lokaci ƙarfi
da fushi yake amfani a wurin tarbiyya ba, wasu lokutan rarrashi da addu'a suke
buƙata.
Yanzu barin gidan da yayi, ba wai hakan ne ya saka ya ɗan
nutsu ba, addu'a ce kawai, kina ji da tasirin wata yarinya a rayuwar
abokinsu"
"To shi ma ayi masa auren mana, tun da ya fara tsufa
yana shashanci"
Ficewa Liti yayi, dan idan ya biye mata, lokuta da dama a
baya lokacin yana kan ganiyar shaye-shaye, ya sha yinƙurin ɗura mata ashariya,
ko kuma ya sureta ya buga da ƙasa, saboda a cewarsa tana yi masa shishishigi da
munafunci.
*****
Saƙo ne ya riski Naja'atu Bunkure, a kan cewar ma'aikatar
Shari'a ta soke lasisinta, har sai an kammala bincike a kanta.
Hankalinta yayi mummunan tashi, ta kira Indabo a waya cikin
tashin hankali, yana ɗagawa ya ce "Ya kuma aka yi?"
"An soke lasisina daga ma'aikatar shari'a, wai sai an
kammala bincike a kaina, dama ba ta janye ɗin ba?"
"Kuma dai? Ta janye ƙarar fa, sai da na tabattar da
hakan, kuma yanzu nima nake samun labarin wannan shegen yaron da na saka a
kashe, dan ya ƙara zama jan kunne ga Vipern, bai mutu ba, wai yana raye a
asibiti"
"To ni ina ruwana, licensed ɗi na fa aka yi siezing,
wane irin abu ne wannan, duk wahalar da na sha kafin na zo wannan gaɓar, sai da
na kai ƙololuwa sannan zan yi faɗuwar baƙar tasa, wannan mummunan ƙarshen,
wallahi ba zai yiwu ba"
"Ki yi haƙuri ki daidaita nutsuwar ki, zan san abin yi,
ki yi haƙuri ai hakan ba zai yiwu ba sam" kashe wayar tayi, tana jin yadda
kanta yayi mata wani irin mugun nauyi, ta ma rasa me za ta yi ko ta ce gaba ɗaya.
***
Walid jiki yayi kyau sosai, Viper yana gefensa yana yi masa
magana, amma hankalinsa yana kan wayarsa da yake dannawa da hannu ɗaya.
"Ɗan marayan zakina, ya jiki, ina son na zo na ƙara
dubaka, amma ina jin kunyar yaya, kuma ga mama babu lafiya ita ma"
"Kar ki damu, ina samun saƙon gaisuwarki ai, jiki
Alhamdilillah da sauƙi"
"Allah ya ƙara tsare mini kai"
"Amin ke ma haka"
"Amma Yaya ya gaya maka na taɓa aure, har shekara
uku?"
Walid yayi mata reply da"Har ɗaurin aurenki mun je ni
da Walid a madadinsa a lokacin yana tsare a gidan yari"
"Lallai kun cika abokan amana, ina son abotarku. Amma
kana ganin babu ƙwara a ciki, kaga kai ba ka taɓa aure ba, ni kuma na taɓa"
Walid ya ce "Ko kaɗan, Viper ba zai haɗani da abin da
ya san akwai cutuwa ba, kuma ni ba wannan nake dubawa ba, nima kin san irin
rayuwar da muka yi a baya, kuma ni ba wani mai ƙarfi bane ba, buga-buga ce dai
muke yin ta, amma kin ga ke kuma 'yar gayu ce, matar manya ce, ina fatan hakan
ba zai zama da shiga hakkinki ba"
Voice message ta yi masa, ya rage volume yana saurara ta ce
"Babu wannan maganar, ni kawai sonake nima ka so ni kamar yadda ka ke son
Yaya Al'amin, ka ji my, Allah ya sa kai nawa ne nikaɗai, kuma ka daina ce mini
Shahida gaskiya, sunan soyayya zaka samo mini nima" ta ƙarasa maganar tana
dariya, dan ta san ƙarshenta, sauka zai yi daga online ɗin.
Aikuwa haka yi, ya rufe data yana murmushi, sai suka yi ido
huɗu da Viper, da ya gaji da magana ya zuba masa ido, sai yayi sauri ya ajiye
wayar yana ɓoyeta kamar yayi rashin gaskiya.
Viper ya ce "Wai me ka ke yi a cikin wayar ne?"
"Tilawa" yayi maganar yana mazewa.
"A'a karatun kalaman da tayi maka kake yi wa tilawa
kenan, ai fa Walid an fara soyayya babu sarki sai Allah, muna zaman zamanmu
Viper ka saita masa hanya, yake ta zaƙewa"
Viper ya ce "Ai naga alama, me take gaya maka ne har
haka?"
Liti yayi farat ya ce "Wai ɗan marayan zaki, wani
gursumemen gardi, kwana yake yana murmushi"
Viper ya yi murmushi ya ce "Na ji daɗin hakan sosai, ɗan
uwana na cikin farinciki, Allah ya tabattar mana da alkhairi. Kai kuma goga wa
zaka samo mana ne mu aura maka?"
Liti ya ce "Mhmm, wani zance mara amfani tsohuwar nan
ta gidanmu take yi, da na lalace cewa tayi a koreni, Alhajinmu yana sangarta
ni, saboda ba ta son uwata. Amma akwai jikarta da take son uwatta, ta gama
lalacewa yarinyar nan na girmeta, amma saboda tsabar yawo da gantalin bin maza,
duk ta fara tsufa wai a haɗamu aure"
Viper ya ce "A'uzubilalimatillahi"
Walid ya ce "To meye a ciki, ku rufa wa juna asiri
shikenan"
"Wa za a rufa wa asirin? Wallahi da budurcina ba zan
auri lalattaciya ba, ta gama bayar da free services a kwararo ba, Allah ya
kiyaye"
"Walid ya ce "A gidan uwar wa ka ke da wani
budurci, mace ne kai? Kai ma fa a lalacen nan kake, shaida ɗaya zan yi maka
bama kula 'yar kowa"
Ya ce "Yauwwa to barka, a bar ni da ɓalla ƙarafa da
caji, amma banda shashanci, dama aure ta taɓa yi da sauƙi, amma ta gama gantali
wai a bani, kai tsohuwar nan ba ta ƙaunata"
Viper sai da yayi dariya, jin yadda liti yake ta ɓaro zance.
Tashi ya yi ya fita, yana son ganin Nabila sosai da sosai,
amma ya fara tsorata da abubuwan da take yi masa, ya kasa gane da gaske take yi
ba ta son shi, ko kuwa dai kawai rigima ce irin ta ta.
Wayarta ya kira, sai dai sai da ya fara harzuƙa sannan ta ɗaga,
murya ƙasa-ƙasa ta yi masa sallama.
"Kina ina?"
"Na je gidanmu ne"
"Meyasa ki ka fita? Ban gaya miki kina cikin barazanar
rashin tsaro ba?"
A hankali ta ce "Joseph ne fa ya kai ni" tayi
maganar kamar a shagwaɓe.
"Meyafaru muryarki tayi ƙasa?"
Nabila ta ce "Bana jin daɗi ne, bani da lafiya"
"Meyafaru?" Ya faɗa kamar an yi masa dole.
"Ka san an yi ƙura ne jiya, ina ta fama da tari, ban yi
bacci ba sosai, sai kuma na tashi da ciwon kai"
Ya ɗan lumshe idanunsa ya ce "Asibiti fa?"
"Na sha magani a gida, zan kai rahama awo gobe in Allah
ya kaimu zan ga likita daga nan"
Ya ce "Ok take care, idan da wani abu let me know"
Ta ce "Ok na gode sosai, a gaida Oga walid"
Ta ajiye wayar tana jin wani iri a jikinta, tunani take yi,
ko ya daina sonta ne, ya ajiye maganarta a gefe kamar yadda ta nema?.
Shi ma sauke wayar ya yi, yana jin yayi kewar rigima
da shagwaɓarta, kenan da gaske dai ba ta son sa kenan? Bai taɓa tunanin idan
yayi mata maganar aurensu, za ta ce ba zata aure shi ba.
****
Ramma ciki ya tsufa sosai, kullum cikin lissafi take, yaushe
Abdul zai fito, gashi sati huɗu ake bata a wurin awo, wani abun tana ji tana
gani, tana so, amma babu yadda ta iya, sai dai ta haƙura tayi shiru. Saboda
tana tsoron tayi wani abun mama ta hantareta, dan sam ba ta ƙaunar cikin nan.
Ramma ta san da Abdul ba a tsare yake ba, da zata ga gata da
kulawa, amma tana matuƙar jin daɗin yadda Nabila take nuna mata kulawa da
damuwa da ita da sumayya.
Yau bayan ta kai ta awo, suka biya aka yi sayyayar kayan
haihuwa.
Daga nan ta kaita wurin Abdul, yau ma kamar kar su rabu,
sauransa wata ɗaya ne ya fito daga prison, bakin ramma har kunne saboda murna.
Washegari da yamma, Alhaji mu'azzam ya zo gidan, mama ta karɓe
shi, kamar yadda ta saba har take tambayarsa yaushe za su koma ƙauye, sun zo
sun zaune masa a gida.
Ya ce "Haba Hajiya, ai kin girmi rayuwar ƙauye yanzu,
ko dan asirin rahama, ba zaku koma ƙauye ba, kema kuma ina fatan Allah ya baki
mijin aure, kema ki yi aurenki a nan birni ki huta".
Maman ramma ta ce "Ashha, ga 'ya har da tsohon ciki
nayi aure, ai aure kuma yanzu sai dai naga ana yi wanda nayi Allah ya sanya
albarka"
Alhaji mu'azzam ya ce "Saboda me, shekarunki nawa
ne?"
"Na kusa arba'in idan ma ban yi ba, tun ina shekara sha
uku aka yi mini aure"
"Kuma ki ce kin wuce aure, a'a ai aure garkuwa ne"
Yayi waya aka shigo masa da wata shirgegiyar akwati, ya saka
aka kirawo masa ramma.
Ya ce "Sannu rahama, kin kusa shiga watan haihuwa
ko?" Ta bashi amsa tana sunkuyar da kai ƙasa.
"Babu wata matsala dai ko? Nabila na kai ki awo, naga
an ware ni a gefe ni, ke da ita kuke abinku" ta sunkuyar da kai tana
murmushi.
"To Allah ya raba lafiya, ga kaya nan, naki da na
jariri unisex ne kayan babyn, Allah ya raba lafiya"
Maman ramma ta ce "Haba Alhaji, ɗawainiyar tayi yawa,
jiya fa sun sayo kaya da Nabila"
"Wannan mijinta ne ya bayar da kuɗin, wannan kuma ni a
matsayinta na 'ya ta na saya mata. Kar ki manta a gidana fa koma menene ya
sameta, dan haka ko me zan yi wa rahama, ba zan goge muku abin da aka yi muku
ba, dan haka ba wani abu bane ba, Allah ya raba su lafiya"
Mama tayi ta yi masa godiya, kamar ta shige cikin sa.
*****
Nasir ya dawo daga aiki, ya ga manyan motici suna shiga
street ɗin su, abin ya bashi mamaki, ya ƙarasa da motarsa, ya ga a ƙofar gidan
su, suka yi parking.
Abbu ne ya fara fitowa, mamaki ne ya cika Nasir, ya fara
tunanin a ina ya san fuskar nan, Alhaji mu'azzam ma ya fito, hannunsa riƙe da
waya.
Sauran motoci biyun convoy ɗin Alhaji mu'azzam ne.
Ya fito daga tasa motar, a dai-dai lokacin da Baban su
Nabila ma ya fito.
Ya ƙarasa suka gaisa da su, Alhaji mu'azzam ya ce
"Yauwwa dama baban naka nake kira, na gaya masa zan zo masa da baƙi
yau"
Nasir ya ce "Masha Allah, tun da ya san da zuwanku,
bisimillah mu shiga"
Suna ƙoƙarin shiga, sannan Viper ya fito daga mota, ɗaya
daga cikin sauran motocin.
Nasir yana jinjina tsabar taƙama da jin kan Viper, shi ba
kowan kowa ba, sai a yanzu ya gane in da yake tunanin sanin Abbu, kamarsa ɗaya
da Viper, sai ya lura irin tafiya ɗaya yake yi da mahaifinsa, sai dai shi
harkar daba ce ta ƙarawa tasa tafiyar taƙama.
Major na jin sallamar baƙi a falonsa, ya miƙe cikin
farinciki yana yi musu maraba, sai dai yayi tururs da ya gansu tare da Bashir.
Fuska babu walwala ya ƙarasa karɓar su.
Alhaji mu'azzam ya yi gyaran murya ya ce "Duk da baƙin
naka, wasu sanannu ne, wasu kuma baka sansu ba, wannan shi ne mahaifin Al'amin
Viper, wanda ya auri 'yar uwar Nabila, wannan kuma Al'amin, wannan kuma baban
su Nabila, kamar yadda ka sani.
Mun zo ne a tare da shi, mu sake baka haƙuri a kan abin da
ya faru, dan Allah kayi haƙuri ya wuce, ko dan samun nutsuwar ita
yarinyar".
Major ya kalli Alhaji mu'azzam ya ce "Ka kuwa san abin
da yayi mini? Har duniya ta naɗe ba zan manta ba. Babu ƙoƙarin da ban yi ba na
yafe masa na manta, amma na kasa, mussaman idan ina tuna yadda yarinyar nan ta
mutu da sunansa a bakinta, duk tsananin kunyar bafulatana, amma ba ta son
laifinsa, sosai take nuna son mijinta, amma ta wulaƙanta mini yar uwa ya
tozarta ta, ya barota a dajin Allah ba ta san kowa ba sai shi. Na bashi yarinya
amma ya aurawa ɗan daba ya kasheta"
Alhaji mu'azzam ya ce "Ashsha! A bar tuna baya major,
shi fa yaron nan da ka ke magana a kai, ga shi a zaune a gabanka, ga mahaifinsa
ba zai ji daɗin ka din ga jifansa da irin wannan maganganun ba. Ni nan ni na
fara neman auren Jauhar, Allah bai yi ba ta auri Aminu, amma zan iya ce maka, a
duniya jauhar ma da ƙaunar mijinta ta bar duniya, saboda yar uwatta da na aura,
kan yi zancenta da rayuwar gidanta. Kawai sharrin yan siyasa ne da rashin ji da
yayi tsautsayi ya faru, idan zan gaya maka gwagwarmaya da wahalar da ya shiga
bayan mutuwarta, to a matsayinka na uba, sai ka zubar da hawaye. Nabila dai ita
ce da ta shiga rayuwarsa ta taimake shi, Al'amin ba ƙashin yarwa bane ba, amma
ka yi binciken ka kaima, kar laifin mahaifinsu ya shafe shi dan Allah"
Abbu yayi gyaran murya ya ce "Ranka ya daɗe, ita
duniyar guda nawa take, duk da Alhaji Bashir yayi mini bayanin komai, bai ishe
mu darasi da mamaki, ace duk da ka nesanta yaran biyu, da juna Nabila ta afka
rayuwar Al'amin ba tare da ta san waye shi ba? A duniya ina gaya maka idan
mutum bai yi dacen mace ba, sai addu'a kawai.
Ka ganni nan, da sanya hannayena bibbiyu, a lalacewar ɗa na,
bayan mutuwar mahaifiyarsa na auri ƙawarta, ina saka ran ta kula mini da
'ya'ya, amma a ƙarshe saboda makirci irin na ɗiya mace, sai da ya zama
tsakanina da Al'amin babu jituwa, kamar maƙiyina, dan Allah a bar tuna abin da
ya wuce"
Bashir ya ce "Maitama na san duk abin da zan gaya maka,
ba yadda zaka yi da ni ba, amma a irin yadda na auri Chubaɗo na fara rayuwa da
ita, ka san ban aureta dan na cutar da ita ba, ƙaddara da makircin mata, ya
sanya abin da ya faru ya faru, tun da ko da na aureta ka san ba mutumin banza
ne ni ba.
Na haɗu da sharrin mata ne da suka yi mini sihiri a kan
mairamu, a gaban Nabila suka din ga faɗar abin da ya faru, amma dan Allah ka yi
haƙuri, ka yafe mini"
"Ba wani sihiri, dama mutum ya tara mata ya zauna ba
addu'a, ba neman tsari, ba dole kowane abu ma mata su yi wa mutum ya kama shi
ba"
Abbu ya ce "A dai yi haƙuri, ya wuce dan Allah"
"To yanzu me ku ke so?"
Baba ya ce "Ina son ka bani Nabila ne, haryanzu ina
kewar Jauhar, dan Allah ka bani 'ya ta"
Wani mugun kallo ya yi wa Bashir, ya ce amma dai ba ka san
me ka ke cewa ba ko? Nima da na rasa 'yar uwata haƙuri nayi na faullawa Allah.
Kai Alhaji mu'azzam yaya muka yi da kai, ba cewa ka yi da ta kammala shari'a
zaka dawo mini da 'ya ta ba? Kawai sai ku zo mini da wani zancen daban, Nabila
tun da Allah ya haɗaku, duk lokacin da take so, ta je ka ganta, amma wallahi ba
zan bayar ba".
"Maitama kar mu yi haka da kai, ka bani 'ya ta ka
tausaya mini mana"
"Ita ma ka kaita su yi mata asirin kenan? Ba zai yiwu
ba wallahi, kuma kai Alhaji mu'azzam, kai mun yi da kai zaku dawo mini da 'ya
ta ai".
Alhaji mu'azzam ya ce "Haryanzu da sauran issue ne,
amma za ta dawo, tun da ai haryanzu tana zuwa nan ɗin"
Abbu ya ce "Amma dai muna fatan ka yafe masa, a manta
da abin da ya faru a baya?"
"Ya wuce, mantawa kuma wannan ba lallai ba, 'ya kuma a
ƙyale mini 'ya ta, Allah ya sa mu dace"
Alhaji mu'azzam ya ce "Hakan ma Allah ya saka da
alkhairi, kuma tun da ka ce duk lokacin da take so taje taga mahaifinta, Allah
ya saka da alkhairi ya huci zuciyarka"
Major ya numfasa ya ce "Amin"
Baba ya tashi ya ƙarasa ya miƙa wa Major hannu, ya ce
"Ina ƙara neman afuwarku da ahalinku, a kan abin da nayi muku, ku yi
haƙuri ku yafe mini"
Major kamar ya maze, ya haƙura ya miƙa masa hannu suka
gaisa, Abbu ya din ga Alhamdilillah, Allah ya ƙara muku fahimta.
Viper kuwa dama tun da suka fara hayaniya, ya fice ya koma
ƙofar gida.
Major ya ce "Bari na kira muku mutanen gidan ku gaisa,
da mariƙiyar Nabilan"
Ya tashi ya sauka falo, ya ce "Magajiya, ki zo ga
mahaifin Nabila ne ya zo, kai Nasir ina babarku, ku zo ga mahaifin Nabila da
mijin 'yar uwatta ku gaggaisa"
Jikin Nasir yayi mugun sanyi, wani irin kishi da fargabar
dalilin zuwan Viper da mahaifinsa ya tsaye masa.
Aka gabatarwa da Baba kowa, ya din ga yi musu godiya da
fatan alkhairi.
Bayan tafiyar su, sannan Nabila ta dawo, ake gaya mata su
Baba sun zo, ta ji babu daɗi rashin tarar da su, sai dai ta yi wa Abba godiya,
jin cewar ya yafe wa mahaifinta, kuma ta san duk jajircewar Viper ce.
Ta samu Abba, ta din ga yi masa godiya, da nuna masa
farincikinta, a kan yafewa mahaifinta da yayi.
Abba ya ce "Eh na yafe masa, amma ban yadda da maganar
ki koma gidansa ki zauna ba, ban yadda da wannan ba".
Nabila ta ce "Nima dama ba zan koma can ba, amma na
gode sosai da sosai da ka yafe masa".
Da daddare bayan ta yi sallar isha'i, ta kira Viper, yana
ganin kiranta ya ɗaga, ta ce "Hello Vi"
"Mmm"
"Ashe kun zo gidanmu bana nan, baka gaya mini zaku zo
ba, da na dawo da wuri, naga shiryawar Baba da Abbana" yayi shiru bai ce
koma ba.
"Na san wannan duk ƙoƙarin ka ne, na gode sosai da
sosai, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi, Allah ya jiƙan 'yar madara da
jaririnta, ya baka abin da ka ke nema duniya da lahira na gode, na gode"
"Godiyar ta isa haka, nima na gode"
"Ba ta isa ba Vi, ban san me ma zance maka, da zai
tabattar da irin godiyar da nake son yi maka ba, na gode sosai da sosai"
"Nima na gode sosai "
"Tom sai da safe"
"Nabila"
"Na'am"
"Haryanzu kina nan a kan bakanki ha zaki aure ni
ba?"
"Dan Allah mu daina wannan maganar Vi, a wuce ta dan
Allah, ni na riga na gaya maka matsayata, mu yi haƙuri da wannan maganar"
Ya ce "Ok, babu laifi" ya katse kiran wayar.
*****
Walid ya warke sarai, hannu ya miƙe, sai dai da Viper ya yi
masa zancen Abbu zai ɗauke shi, a kasuwa a nuna masa harkar kasuwanci, sannan
ya bashi jari, a fara maganar aurensa da Shahida.
Walid ya kasa magana yayi shiru yana kallon Viper.
Viper ya ce "Menene kuma? Ko ba wannan sana'ar ka ke so
ba? Idan da wani abun da ka ke so ka faɗa, sai a san abin yi"
Walid ya ce "Anya gatan nan bai yi mini yawa ba Mai
zamani? A bani jari kuma a bani auren 'ya?"
"Ware, ka cancanci fiye da haka mai laya, yanzu
yakamata mu je ko wurin ƙannen mahaifinka ne, saboda su nema maka auren
Shahida, ni kuma zan je Lagos ne aiki"
"Lagos kuma mai zamani, babu kai babu ɗan mama"
Al'amin ya numfasa ya ce "Tafiyata can na cigaba da
aiki, ya fi alkhairin zamana a nan. Dama na yi zaton ko Nabila zata aure ni ne,
amma ta ce ba ta so na, dan haka zan yi tafiyata kawai, na yi aikina na fi
samun kwanciyar hankali da manta wasu abubuwan"
"Viper, daga kai har Nabila kuna son junanku, kawai dai
rashin fahimta ne. Kaga Jauhar a sadaka ka auret, baka san duk wata wahala da
ake sha, wurin neman aure ba. Yanzu ne zaka yi fafutuka da gasken gaske, idan
ba haka ba ka bari ta auri wani babu lallai ka iya jurewa"
"In biye mata tayi ta wulaƙanta ni?"
"Ba wulaƙantaka take yi ba, kai ka fara watsar da
tayinta a farko, ka din ga nuna mata da farko, an ce mata ba sa mantuwa, amma
ka yi haƙuri ka nemi aurenta, Abbu ya nema maka
Aurenta" Viper dai yayi shiru bai ce komai ba.
*****
Major ne ya kira Nabila, ta same shi a ɗakinsa, ya ce
"Yauwwa babanki ya turo mini baban yaron nan da ya auri 'yar uwakki, wai
yana son ya aure ki, zasu kawo kuɗin aure, na ce sai na yi magana da ke, kina
ganin kin yarda da nutsuwarsa a yanzu zaki iya aurensa?"
Nabila ta yi shiru. "Magana fa nake yi miki Arfa"
"Gaskiya Abba ni ba zan iya aurensa ba"
"Saboda me?"
Ta girgiza kai ta ce "Ni dai kawai a bar maganar nan,
ka ba su haƙuri"
"To uban meyasa ki ka gayyato shi rayuwarki, so ki ke
ace ni na zigaki ko?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"Tashi ki je, Allah ya shiryeki" ta tashi
sumi-sumi, ta tafi sai dai kuma haka kurum ta din ga jin tausayin Viper.
Sumayya ta kira take labarta mata abin da ya faru, Sumayya
tayi shiru, ta ma rasa me za ta ce mata.
"Sumy ya ki ka yi shiru?"
"Nabila me zan ce miki, abin da ki ka yi zalunci ne, ya
za ayi ya sakankance, yana sonki zai aureki, amma ki ce ba kya son sa?"
"Point of correction, nake son sa dai, amma ba yake so
na ba"
Ƙarshe sai da suka kusa yin faɗa, suka rabu tsiya-tsiya a
wayar.
Sumayya da kanta ta kira Abbu, suka gaisa ta fara bashi
haƙuri, a kan abin da Nabila tayi.
"Bakomai kar ki damu Sumayya, ai macece idan ma tayi
haka ba tayi laifi ba, na san halin kayana sarai"
"Abbu Nabila na ganin Ba ya sonta ne, kawai dai zai
aureta saboda tana kama da jauhar ne"
Abbu ya ce "Na fahimceki, ita ma kuma haka, yanzu dai
zan ba su lokaci, shi kansa ya zuciya yanzu haka yana hanyar Abuja, can aka kai
shi ba Lagos ba kuma, ya ce auren ma ya haƙura, amma ta nan ɓangarenki, dan
Allah ki ɗan lallaɓata, ni idan ta kama ma sai na zo da kaina, ba zan so ya
tafi yaje ya zauna haka babu auren ba"
Jiki a sanyaye Sumayya ta ce "To shikenan Abbu, in sha
Allah"
Ta sake kiran Nabila, tana gaya mata yadda suka yi da Abbu.
Nabila ta kada baki ta ce "Dan Allah Sumayya ki ba wa Abbu haƙuri, ba wai
ina ƙyamar ɗan sa bane ba, amma ina yi masa fatan alkhairi a duk in da yake,
Allah ya bashi mace madadin Jauhar".
Ayshercool
08081012143
A ƙule Sumayya ta ce "Kina ganin hakan da ki ka yi shi
ne dai-dai? A gidan uban wa ki ke tunanin zai samo madadin matarsa? Ke kin san
baki isa ki ƙi aurensa ya bari ki zauna lafiya ba"
Nabila ta ce "Lafiya ƙalau zan zauna in sha Allah, kar
ki damu da ni Sumy, Allah ya nuna mini aurenki"
"Nabila kar ki mayar da abin nan wasa, ya ki ke tunanin
mahaifinsa zai ji, kin yi rejecting ɗin ɗan sa?"
Sumayya, wai kina ina lokacin da na din ga gwagwarmaya, ina
nuna wa mutumin nan so yana wahalar da ni?"
"Ramawa ki ke kenan?"
"Da zan rama abin da Vi yayi mini, ko kallonsa ba zan
iya yi ba, kawai dai ba zan aure shi bane"
"Munafuka, kina wani kiransa Vi, kina wulaƙanta musu ɗa,
nan ki ka roƙi Allah ya baki kowane irin miji ne, mutum ya nuna yana sonki,
amma kina wahalar da shi, zaman gidanku da wannan cin mutuncin ne da ake yi
miki bai ishe ki ba, ki ƙarata"
Nabila ta ce "Bakomai, na ji na yadda"
****
Alhaji mu'azzam ne a ƙofar gidan su Hafsa, ya fi mintuna
ashirin yana surutu, amma Hafsa ta yi masa banza ta ƙi kula shi.
"Hafsa" ta ɗago ta kalleshi.
Ya ce "Meyasa ba zaki yafe mini ki koma ɗakinki
ba?"
"Meyasa zan koma in da ba a buƙatata? Gara na barka waɗanda
kake ƙauna".
Ya ce "Na san ban kyauta ba, amma ki yi haƙuri, zan
gyara kuskurena" murguɗa baki tayi, ta sake juya masa baya.
Murmushi ya yi a ransa ya ce "Komawar ki gidana ita kaɗaice
mafita a garemu baki ɗaya" a zahiri kuma ya ce "Shikenan sai da
safe"
Ba ta kula shi ba, kawai ta shige cikin gida ta bar shi a
wurin.
Yayi murmushi ya furta mace kenan, duk yadda ake ganin
girmansa da mutuncinsa a ƙasa, yana ta bin yarinya ƙarama tana wana shi.
****
Viper ne a tsaye a banɗaki, ya sakarwa kansa ruwa, a hankali
ya kammala wankan ya fito, jikinsa duk babu ƙwari.
Ya shafa mai, yayi shirin kwanciya bacci, gaba ɗaya abin da
Nabila tayi sai cin zuciyarsa yake yi.
Yana jera kayansa a cikin wardrobe, yana tuna tarbiyyar
Jauhar ce, da ta hana shi watsar da kaya ko ina, duk yadda ya ga dama, da har
ta koya masa rashin son baza kaya ko ina.
Ɗan ƙaramin hotonsu ne shi da ita ya faɗo, ya durƙusa ya ɗauka
ya zauna a gefen gado yana kallo. Kamaninta sun ɓaci da ita da Nabila.
Ya kalli jikinsa, ya tuna yadda komai dare idan ya gama
yawonsa ya dawo, sai ta haɗa masa ruwa mai zafi yayi wanka, tun ba ya so bar ya
zo ya saba, ta shafe shi da mai sannan ya kwanta bacci. Gashi ba ta taɓa gajiya
da duk wata rigimar sa, sai dai idan yayi mata laifi, to fa ba ruwan wanka,
balle shafa mai da tausa, hirar ma ba zata yi masa ba.
Kayan shafe-shafen gyaran fatarta kuwa, wataran haka take
zaunar da shi, shi ma ta shafa masa wai yayi kyau.
Ya ɗan saki murmushi ya ci gaba da kallon hoton, ya ce
"Kin bar ni da tabo mai tsananin zafi a cikin zuciyata, sai wahala nake
yi, ga twin sister ɗinki ta ce ba ta so na, ke kaɗai ki ke so na babyn
robana" yayi maganar kamar taɓaɓɓe.
Ya nemi wuri ya kwanta, rayuwarsu ta baya na dawo masa,
Addo'in kwanciya bacci, ita take yi masa idan bai yi ba, yawan yi masa ya sanya
ya haddace su tsaf a kansa.
Ya tuna ranar da tana cikin yi masa addu'a, ta idar ta tofa
masa, ta shafa sumarsa ta ce "Mai zamani, yaushe zamu je aski ne?"
Ba shiri ya buɗe ido ya ce "What me ki ka ce?" Ta
hau dariya ta ce "Viper"
"Viper ko?" Yayi maganar yana matsa kumatunta.
Cikin shagwaɓa ta ce "Sorry yaya master"
"In sake jin ki faɗi wannan sunayen, ni da ke ne, matso
to rarrashe ni na yi bacci, ki sake yi mini wata addu'ar"
"Naƙi ɗin, tun da ka ci zalina, ka san dai ka fi ni
ƙarfi, amma ka matse mini kumatu"
Ya ce "Eyya, to ni zo na rarrasheki ki yi baccin "
"A'a ba na son wannan rarrashin, mun yi faɗa, yau ina
farkon gado, ina ƙarshe"
Yayi dariya yana gyara kwanciyar sa, ya ce "Da shegen
son jikinki, ina nan zaki mirgino ki same ni ne"
Ta riga shi yin bacci, aka kawo wuta unexpected, ya ashe
ƙwan ɗakin a kunne yake, ya tattara nutsuwar sa, da hankalinsa a kanta, bacci
take yi sosai, da alama baccin gajiya ne, dan har alarm ɗin ta ya buga na
lokacin sallar dare, ba ta sani ba.
Ya tashi ya je ya sha ruwa, ya kashe fitilar ya kwanta, ya
rungumeta a jikinsa, yana jin wani irin abu game da ita, na mamaye kowane sashe
na zuciyarsa.
Cikin magagin bacci ta ce "Master"
Ya ce "Mmmm"
"Ya Allah ka shirya mini shi, Allah ka yaye masa wannan
shaye-shayen, Allah kar saka ya dawo gareka yana aikata ɓarna, Allah ka bashi
halal, ka bashi juriya da jarrabawar rayuwa. Allah ina son mijina a haka, Allah
ka sanya yana da rabon shiriya" a cikin bacci take ganin kamar tayi salla,
take ta jerin wannan addu'oin a fili.
A hankali ya dawo daga tunanin da yake yi, ya kalli hoton ya
ce "Wannan ce juriyar da ki ke roƙa mini, juriyar rashin ki 'yar
madara" ya ajjye hoton ya canza kwanciyarsa, yana jin yadda zuciyarsa take
yi masa zafi.
Bacci ne ya kwashe shi, sai dai yau a maimakon Jauhar, da
Nabila yayi mafarki, cikin yanayi na ma'aurata, ko da ya farka ya makara sallar
asuba, tsaki ya yi ya tashi, tare da furta jarababbiya, ko meya kawo ta
baccina"
Ta ƙarfin tsiya yake son sanya wa kansa jin haushin Nabila,
amma abu ya gagara, wata irin kewarta ce ma take damunsa, gaba ɗaya tunanin
mafarkin da yayi, yaƙi barin kansa.
Wato nutsuwa da kwanciyar hankali ba abin da ba ya sanyawa,
a lokacin da yake cikin ha'ulai'in tashin hankali, ko kusa baya wani tunani,
balle ya kwanta ya yi wani mafarki, ba ma haka ba, baccin ma ba iya yin sa yake
yi ba, balle yayi wani mafarki.
Yanzu kuwa hankalinsa a kwance yake a cikin nutsuwa, ya
shirya ya auri Nabila da zarar komai ya daidaita, saboda ya san yana buƙatar
hakan, amma lokaci ɗaya ta hau dokin naƙi, wai ba ta son sa.
Ɓangaren Nabila ma, yanzu zaman gidan major bai fiye yi mata
daɗi ba, duk sun ƙara tsangwamar ta, yanzu ta fi zama a barrack, ta fi jin daɗin
zaman wurin madam, sai dai kuma da an kwana biyu sai ta ji gida take son
komawa.
Tana zaune ta idar da sallar asuba, ta yi azkar, ta kifa
kanta tana ƙarasa azkar ɗin, bacci ya kwasheta, dan kuwa yanzu bacci rabi da
rabi take yin sa, saboda tunanin halin da Viper yake ciki, tana ta addu'a da
fatan Allah ya sa kar ya koma halinsa na da.
Kawai tayi mafarkin farkon haɗuwarsu da Viper, a lokacin da
yake Vipern sa, tamkar mahaukaci, ya soka mata wuƙa a ciki. Ihu ta kurma
ta tashi tsaye tana dafe cikinta.
Baba magajiya ce ta shigo ɗakin a razane, Abba yana daga
saman benensa ya jiyo ihunta, sun saba da irin wannan ihun na Nabila wasu
lokutan, amma kwana biyu tayi lafiya.
A sukwane ya saukko shi ma, ya shiga ɗakin nata, ya tarar
baba magajiya ta riƙeta, sai kuka take tana riƙe cikinta, tana dubawa ko zata
ga jini.
"Menene kuma?"
"Viper ne ya caka mini wuƙa, a kai ni Asibiti"
"Wane Viper kuma, kalli dai a ina ki ke?" A
hankali take ƙarewa ɗakin kallo, ta kalli jikinta ta ga lafiya ƙalau.
"A garin shegen kwashe-kwashen ki, kin kwaso abin da
zai hanaki bacci, bayan kwaso masu farautar rayuwarki, kin yi azkar ma
kuwa?" Ta jinjina masa kai, ta nuna masa wayarta da sautin karatun
Alqur'ani yake tashi ƙasa-ƙasa.
"Nemi wuri ki kwanta ki huta" ta ƙarasa kan gadon,
tana ajiyar zuciya.
A ranta ta ce "Vi fushi ka ke da ni har haka?" ta
lumshe idanunta, ƙirjinta na ci gaba da bugawa cike da matsanancin tsoro.
Wajen ƙarfe sha ɗaya na rana ta gama shirinta, ta fice zuwa
wurin aiki.
Tana zuwa ta tarar da Walid tare da Liti suna jiranta.
Cikin mamaki ko gaisawa ba su yi ba, ta ce "Allah ya sa
lafiya na ganku, ba wani abin ne ya same shi ba ko?"
Walid ya ce "Kwantar da hankalinki, babu abin da ya
same shi, yana nan ƙalau"
Ta ce "To Alhamdilillah" ta jagorance su zuwa
cikin ofishinta, bayan sun gaisa Walid ya ce "Na san zaki yi mamakin
zuwanmu, duk da ba abin mamaki bane ba, amma dole ki ganmu.
Nabila dan Allah me Viper yayi haka ki ke wahalar mana da ɗan
uwa, kin san komai zai iya faruwa ƙin auren nan nasa da ki ka yi, idan ba ke ɗin
ba wacece zai je ya aura su zauna lafiya?"
"Ni ɗin ma babu lallai mu zauna lafiya" ta bashi
amsa.
"Amma meyasa ki ka ce haka?"
Nabila ta ce "Halin Viper ai sai dai Jauhar ɗin, kuma
ma duk ba wannan ba, gani nake cik amana ne kamar ban kyauta ba, ace na auri
mijin Jauhar, dan Allah ku yi haƙuri, ku bashi haƙuri, na san a fusace yake da
ni, tun da nayi mafarkinsa yana caka mini wuƙa"
Walid ya ce "A'uzibillah lallai kam ya tabatta Mai
zamani yana fushi da ke, amma dan Allah ki yi tunani, ki taimaki rayuwar ɗan
uwanmu"
"Oga Walid ina jin kunyarka, dan Allah mu bar wannan
maganar"
Walid ya ce "To shikenan, amma dai dan Allah ki yi
tunani a kai"
Nabila ta yi murmushi ta ce "To Oga walid in sha Allah
za ayi"
Ɓangaren Viper kuwa, abu kamar wasa, ya damu da rashin
Nabila sosai da sosai, wasu lokutan sai ya shiga what's app ɗin sa, yana
sauraren Voice message ɗin ta. Gashi ba yau ba gobe cikin mafarkinta yake, abin
har ya fara bashi tsoro, domin kuwa abin ya fara yawa.
Tabbas yana buƙatar sake yin wani auren, dama Nabilan ce ya
saka rai, kuma gashi ta ce ita ba zata aure shi ba.
****
Kwanci tashi asarar mai rai, Abdul ya cika wa'adin da aka ɗebar
masa, na zaman gidan yari, tun safe mahaifiyarsa ta haɗa motoci ta tafi ɗaukar
sa.
Ɓangaren ramma ma ji take yi kamar salla, saboda a
lissafinta yau ne fitowar Abdul, sai dai Nabila ba ta ce masa komai ba. A ɓangaren
sa ma Abdul ɗin, murna yake yi na fitowarsa, ko ba komai ya fuskanci ƙalubale
na gaba, na samun damar ci gaba da rayuwa da matarsa, kuma gashi ya fito dag da
lokacin cikar EDD ɗin ta.
Ramma ta kasa zaune ta kasa tsaye, mama ta fara bacci, ta ɗauki
wayarta, ta tafi ɗakinta ta rufe ƙofa, ta kira lambar Abdul. Cikin sa'a kawai
ta ji muryarsa.
"Doctor"
"Babyna da wayar wa ki ka kirani?"
"Shi ne ka fito ko ka neme ni, ina ta zullumi da
lissafin yaushe zaka dawo?"
"To ta ina zan neme ki, ba waya a hannunki yanzu, ni
kuma tun da na dawo Mummy ta kafa ta tsare, ba zata bari na fita ba, amma kina
raina wallahi, EDD ɗinmu ya kusa cika ko?"
Ta ce "Eh, duk na gaji wallahi, cikin yayi mini nauyi,
na ƙagu na haihu na huta"
"Dan Allah kar ki saka damuwar sai kin haihu abin ya
dame ki kin ji sweetheart?"
"To doctor, ka huta lafiya"
"Ina batun hutu, na so da na dawo a gidana zan zauna,
in ci abincin da ki ka dafa, mu kasance tare cike da so da ƙaunar juna, na yi
missing ɗinki da yawa fa, yanzu dai ga abinci ga komai, amma duk ba wannan nake
buƙata ba, ke nake buƙata a kusa da ni"
"Kaga sai anjima, ba zaka yi wannan zancen da ni
ba"
"Au haka ma zaki ce, shikenan anyway in sha Allah a
satin nan duk yadda ake ciki, zan zo na ganki"
Suka yi sallama cike da kewar juna.
Abdul ya saka ranar da zai zo ganin rahama, sai dai ta rasa
yadda za ta sanar wa mama, gani take kamar ba zata yadda ba.
Dan haka ta kira Nabila ta gaya mata, Abdul yana so ya zo ya
ganta, ko zata gaya wa mama, ita tana jin tsoron ta gaya mata, Nabila ta ce ba
damuwa.
Ta kira mama a waya, suka gaisa Nabila ta ce "Mama,
mijin rahama zai zo ya ganta, zai ga kayan sayayyar da na yi mata, da kuma
yanayin jikinta, ina fatan ban yi laifi ba, na bashi adress na ce ya zo nan
gida"
Mama ta ce "Mhmm ba ki yi laifi ba, ba wani abu"
"Yauwwa mama na gode sosai, a ci gaba da haƙuri dai dan
Allah"
Ta ce "Ba komai"
Ramma da ciki ya sanya, wataran idan tayi wanka, ko mai ba
ta shafawa, amma mama na kallonta, har da su fesa turare, da saka kwalli da
shafa man leɓe mai kala, ita dai ba ta tanka mata ba ta rabu da ita.
Yaro ne ya shigo, ya ce "Wai Abdul ya zo yana
waje"
Ramma ta ce masa "To ana zuwa" ta saci kallon
mama, taga tayi banza da ita, ƙarshe ma ta tashi ta bar falon.
Hakan ya bata damar tashi tana jan ƙafa da kyar, ta fita
harabar gidan.
Yana tsaye cikin yadi ash, kansa babu hula, ya goya hannunsa
a bayansa yana kallon gidan, yana jinjina wa Alhaji mu'azzam, ya taimaki su
ramma, mussaman da ya tuna gidansu na ƙauye da ko ƙofa babu.
"Me ka ke kallo ne?" Ya juyo ya kalleta.
Duk ta kumbura ta cika, ga uban ciki tana ja da kyar,
hangowa yayi kamata yayi ace tana makaranta, ko idan cikin ne, ace a gidanta na
aure take, gaba ɗaya sai jikinsa yayi sanyi.
Ya kalleta ya ce "Sannu uwar biyu"
Ta harare shi ta ce "Wane irin biyu kuma? Ɗayan ma ya
aka ƙare, sannu da zuwa. Lallai prison ta karɓe ka, ka ƙara haske sosai ka yi
kyau"
"Hmm ina daɗi a prsion, ke dai ayi sha'ani kawai"
Ramma ta yi masa jagora, suka ƙarasa cikin sitting room ɗin
da yake harabar gidan.
Ta shiga cikin gida, ta ɗaukko masa abincinta, da ruwa da
lemo ta kawo masa ta ajiye.
Tana ta ƙoƙarin yadda za ta juya ta zauna, kawai ya zaunar
da ita a cinyarsa.
Riƙe cikinta tayi ta ce "Wayyo Allana, kai ba ka ga
halin da nake ciki ba, da na bige ciki fa?"
"Haba dai, na san abin da nake yi ai, na fiki son cikin
nan fa" ya ɗaga rigar jikinta, cikin nan yayi girma sosai da sosai.
Cikin matsanancin shauƙi da ɗokin son ganin abin da zata
haifa, ya ce "Sannu your excellency, Allah ya raba ki da cikin nan lafiya,
na gode Allah da na fito kafin haihuwar ki, ni zan karɓi haihuwar nan, na
rigaki ganin babyn"
"Taɓ, a'a gaskiya, ba zaka karɓa ba, ni wallahi tsoro
ma nake ji"
Abdul ya ce "Ba wani tsoro, ki kwantar da hankalinki,
ai na san ke mai yawan ibada ce, mu yi ta addu'a Allah ya sauƙaƙa miki. Yaushe
zamu je sayayyar kayan baby ne?"
"Ka manta mun sayo ni da Anty Nabila, Alhaji mu'azzam
ma ya sayo wasu ya kawo"
Abdul ya ce "To Allah ya saka da alkhairi, Anty Jidda
sun haɗa kai da Mummy, suna ta yi mini faɗa, saboda ke wai ba ni da zuciya, ni
kuwa in dai a kanki ne, ba zan yi zuciya ba duk tsanani, ni dai a bar mini ke,
mu yi rayuwar aurenmu cikin kwanciyar hankali".
Ramma ta yi shiru ba ta ce komai ba, ya numfasa ya ce
"Zuba mana abincin mu ci tare, ina fatan dai ke ki ka dafa?"
Ta jinjina masa kai, tare suka ci abincin, sai dai sai da ya
so ya wuce gona da iri, ramma ta ankarar da shi a in da yake.
Ya ce "Rakani mu je na gaida mama"
Sai da ta ɗan yi jimm, sannan ta shiga gaba ya biyota a
baya, aka yi sa'a maman tana falo a zaune.
Abdul ya shiga da sallama, ya durƙusa har ƙasa yana
gaisheta, ta kawar da kanta gefe sannan ta amsa masa.
Daga haka ya miƙe ya ce "Na tafi to, sai anjima"
Mama ta ce "To ka gaida gida"
Da suka fito Ramma tayi zaton zai nuna ya ji babu daɗi,
yadda ta amsa masa, amma bai nuna mata ba, sayayyar da ya yi mata ya bata, yayi
mata sallama ya tafi.
Ramma ta kasa gane kan mama, haushinta take ji ko kuma yaya,
gaba ɗaya ta ɗauke mata. Abdul yana son kiran waya yayi magana da ramma, amma
ta ce kar ya kira wayar mama ce, shi kansa shakkar ramman yake ji.
Kotu ta bayar da umarnin a kamo Naja'atu Bunkure, tun da
taƙi gurfana ta kare kanta bisa ga tuhume-tuhumen da ake yi mata.
Viper ya dira a garin Kano, da misalin ƙarfe huɗu na yamma,
a can gidansu da suke zaune yaje ya sauka, ya tarar daga Walid har liti duk ba
sa nan, yayi wanka ya huta, sannan ya shirya ya tafi cikin gari.
Ya tarar Abbu baya nan, kawai Rahila ta fito ta ce
"Sannu munafi mara mutunci" ya tsaya yana kallonta.
"Eh, na ce sannu munafuki, saboda algungumi ne kai,
baka tsoron Allah, shi ne ka haɗa kai da babanka, zaka aura wa Shahida ɗan iska
kamar ka, to baka isa ba, Shahida gidan tsohon mijinta zata koma"
Viper kamar ya tanka mata, amma sai ya rabu da ita ya fita.
Yana nan a ƙofar gidan daf da magariba, sai ga Abbu ya dawo,
tare da Walid, Walid ne yake jan motar, Abbu yana gaba suna hira.
Walid ya din ga yi wa Viper horn,ya taso ya nufo su, Abbu ya
ce "Ya aka yi ka dawo kuma? Ni na yi ɗa dama baka dawo yanzu ba"
Viper ya yi murmushi ya ce "Ai ba daɗewa zan yi ba,
yanzu ma idan aka ce na koma tsaf zan tafi"
Abbu suka fito daga motar, Walid ya ba wa Abbu mukullin ya
ce "To Abbu sai Allah ya kaimu gobe"
Abbu ya ce "A'a, kira wo mini Abdallah a waya, ya
ƙaraso shi ma ku ci abinci tukuna"
Suka yi alwala, suka je suka yi sallar magariba suka dawo,
suka yi shimfiɗa a ƙofar gida suka zauna, har ƙarfe tara na dare suna tare,
wajen tara da rabi, Viper ya ce su tafi zai taho.
Abbu ya din ga bawa labari jin daɗin zamansa da Walid,
saboda biyayyarsa da riƙon amana, kuma ya ga sun fuskanci juna da shi da
Shahida, dan haka baya son a wani ɓata lokaci, saboda Rahila na ƙoƙarin ɓata
lamarin.
Haka suka cigaba da tattauanawa, a kan yadda shirin bikin
zai tafi.
Liti kuwa Alhaji ya ce sai ya koma makaranta ko per time ne,
sannan kuma zai kai shi kasuwa.
Liti ya ce "Amma dai da daddare idan na dawo, an je
rumfar shayi"
"Wai rumfar shayin nan, ba cewa aka yi kayan
shaye-shaye kuke sayarwa a ciki ba?"
"Wallahi mun daina sayarwa, harkar shayi da indomie da
sauransu ake yi a wurin, kuma wannan rumfa tana da tarihi domin tunawa da
marigayiyya Jauhar matar Viper, ba zan bari rumfar nan ta mutu ba. Kuma a yanzu
haka wallahi yaranmu sun kai biyar da suke cin abinci a wurin, ni kula nake yi
da ita, akwai amana ai, duk in da na je da daddare sai na je rumfar nan"
Alhaji ya ce "To, Allah ya tallafa"
Ya amsa da Amin.
***
Kwana na biyu kenan ramma ramam tana ta zubar da ruwa, ta
rasa yadda za ta yi, gashi mama yanzu ba wani sakar mata fuska take yi ba, dan
haka ba ta gaya mata ba, ba ta zata hakan wata matsala ba ce, dan haka ta ja
bakinta tayi shiru.
Sai da Nabila ta bushi iska, ta je gidan, take gaya mata, Ba
ƙaramin ƙuluwa Nabila tayi da abin da mama take yi ba, ta karɓi lambar Abdul,
ba tare da ta saurari mama ba, ta kira shi ta sanar masa, a sukwane ya ce gashi
nan.
"Ina zaka je kana zauna kana cin abinci kuma?"
"Mummy asibitina zani, aikin gaggawa ne ya taso"
"Yaushe ka dawo har ka koma aikin da zaka ce mini wani
aikin gaggawa? Da da kake tsare waye yake aikin?"
"Ki yi haƙuri na je na ji menene" ya ajiye cokalin
ya yi gaba. Ya kira lambar Nabila ya ce ta ɗaukko ramma su haɗu a asibitinsa
kawai.
Nabila ta fito falo ta ce "Mama zan tafi da ramma
asibitin royal, can asibitin mijinta, ba ta da lafiya ya ce lallai a kaita shi
ma ya tafi, kwana biyu tana zubar da ruwa"
Sai kuma ta tashi a kiɗime, ta ce "Ramma naƙuda ki ka
fara baki gaya mini ba?"
Ramma tayi shiru, ta ce "Ai akwai tofinta, da kayan
haihuwa da na haɗa, ko da su za a tafi, ko haihuwar ce?"
Nabila ta ce "A'a bari muje kawai, tun da ba ciwo take
ji ba, idan haihuwar ce sai muyi waya ki taho"
"A'a ba haka za ayi ba, mu tafi kawai bari na ɗaukko
mayafina" tana shiga ɗaki, sai ma ta rasa wa zata kira, kawai ta kira
Viper tana gaya masa.
Ya ce "Ai yau da daddare nake son zuwa da ni da Abbu ku
gaisa, amma gani nan zan biyoku asibitin"
Ko da suka je asibitin, a harabar wurin suka tarar da Abdul,
yana ta kaiwa da komowa, suna isowa, ya nufe su, Nabila ta kamo hannun ramma,
ta fito daga cikin motar, tana takawa da kyar, duk da ta saka pad, amma ruwan
da take zubarwa duk ya ɓata mata jiki.
Wheel chair ya ɗaukko da gudu, ya ajiye suka ɗora ramma a
kai, ya tura ta cikin asibitin.
Tuni ya kira doctor Muktar, wanda abokinsa ne, kuma shi ya
yi wa ramma awo.
Bayan fitar Abdul, doctor Muktar ya yi wa ramma scanic, ya
kalleta ya ce "Yaushe rabon da cikin yayi motsi?"
Ta ɗan shiru ta ce "Tun jiya da safe"
Abdul ya dawo ya ce "Muktar, yaya ake ciki ne?"
Ya gyaɗa kai ya ce "Low amniotic fluid, a shirya OR
kawai, ayi mata EMCS"
Ya ce "Ya subhanallah, amma ya babyn" ya faɗa a
rikice.
Muktar ya ce "Meye haka? Wato saboda wannan taka ce shi
ne zaka wani ruɗe? Dan Allah ka nutsu mana, normal in sha Allah, ka shirya ka
yi assiting ɗina, sai a ciro babyn, ka kira anesthetic ɗin"
"Abdul meya same ni?" Tayi maganar kamar zata yi
kuka.
Ya ƙarasa ya riƙe hannunta, ya ce "Ki kwantar da
hankalinki, tun yaushe ki ke zubar da ruwan nan?"
"Ni na manta, ka gaya mini Meya same ni?"
"Ruwan da babynmu yake ciki ne yayi masa kaɗan, saboda
rashin sanarwa da wuri da ba ki yi ba, duk ruwan ya zube, yanzu tiyata zamu yi
miki a ciro shi"
Ramma ta fashe da kuka ta ce "Yanka ni za ayi kenan,
wayyo Allah tsoro nake ji"
Ya ce "Ki yi haƙuri, babu wani abu in sha Allah"
Ya kalli muktar ya ce "Doctor Muktar, ko zaka yi wa
mamanta bayani, suna falon office ɗina" ya jinjina kai ya fita.
Doctor Muktar yana zuwa, ya tarar da Nabila da mama, ya ce
"Matar master, sannu fa"
"Matar master ai ta rasu"
Ya ce "Ai ni duk abu daga nake gani, amma ya aka yi ta
gama awo successfully, matsala ta taso ku kasa faɗa sai da ta zama worse? Kwana
kusan biyu tana zubar da ruwa fa"
Nabila ta ce "Wallahi ba ta faɗa bane ba doctor "
Ya ce "Aishikenan, yanzu tiyata zamu yi mata ta
gaggawa, amma babu wani abu in sha Allah" maman ramma ta dafe ƙirji ta ce
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu ina ramman take?"
"Ki kwantar da hankalinki, yanzu kafin a shiga da ita,
zaku ganta in sha Allah, ke Nabila taho muje ko da abin da zaki yi mata".
Suna barin wurin sai ga Viper, ya tarar da mama na matsar ƙwalla.
Ya ce "Lafiya ya ake ciki?" Nan ta gaya masa abin
da suka ce, a rikice ya nufi cikin asibitin, ba ya ƙaunar duk wani abu, da zai
shafi mai ciki.
Ba tare da ya yi knocking ba, ya shiga ɗakin, har Abdul ya
sanya wa ramma rigar tiyata, ya rungumeta yana ta rarrashinta tana kuka, wai
tsoro take ji.
Tsit suka yi suka zuba masa ido, ramma na ƙoƙarin barin
jikin Abdul.
Nabila ce suka shigo tare da doctor Muktar, ya bata consent
form, da za a saka hannu ayi wa ramma aiki.
Doctor Muktar ya ce "Allah ya taimaki master, kwana
biyu " ya miƙa wa Viper hannu suka gaisa.
Al'amin ya ce "Ina ganinka gabana ya faɗi doctor
Muktar, a wancan karon matata a wannan karon ƙanwata, ya ake ciki menene
matsalar?"
"Ahh ba wata damuwa, in sha Allah, aiki zamu yi mata,
ruwan da yaron yake ciki ne yayi masa kaɗan"
Ya jinjina kai ya ce "Allah ya raba su lafiya"
Ya kalli ramma da fuskarta ta jiƙe da hawaye ya dafa kanta
ya ce "Rahama" karon farko da ya kira sunanta, ta ɗago ta kalleshi.
"Ki yi haƙuri ki kwantar da hankalinki kin ji? In sha
Allah babu wani abu, za ayi miki aiki lafiya a gama lafiya, ki yi ta addu'a, ki
daina wannan kukan, kar jininki ya hau"
Ta ce "Yaya tsoro nake ji, yankani za ayi"
"Ai ba zaki ji zafi ba in sha Allah"
Nabila ta maze kamar ba ta ga Viper ba, kamar yadda shi ma
ya maze.
Ta ce "Ga consent form da aka ce a cike, wa zan bawa
ne?"
Ta miƙa wa Abdul, ya saka hannu zai karɓa, Viper ya karɓe
form ɗin ya na tsareta da idanunsa, ya ciro biro a gaban rigarsa ya saka hannu.
Abdul kawai ya zuba wa sarautar Allah ido.
Ya ajiye form ɗin bayan ya saka hannu, ya miƙa wa ramma
hannunsa, ta saukko daga kan gadon, ya kalli doctor Muktar ya ce "Ina ne ɗakin
tiyatar?" Ya jagorance su, su na tafe yana tuna 'yar madara, su na zuwa
bakin ƙofar mama ta ƙaraso.
Ta ce "Ramma, Allah ya fito da ke lafiya, Allah ya sa
ayi a sa'a"
Abdul ya ƙaraso, Viper ya kalle shi, ya miƙa masa hannun
rahama, Abdul ya kama hannunta, suka shiga cikin tiyata, tana yi tana waiwayowa
tana kallonsu.
Ayshercool
08081012142
Abdul ya shiga da ramma cikin ɗakin, ya taimaka mata ta
kwanta a kan gadon tiyatar, ya shiga ya canza kayansa zuwa na tiyata, sai
rarraba Idanu take yi, cikin matsanancin tsoro.
Aka shirya ta tsaf, Abdul ya ce a kuma scanic, Doctor Muktar
ya ce no need. Duk wani examination da zai yi wa ramma, sai Muktar ya hana shi,
ya ce masa ya riga ya yi.
Aka duba Vitals ɗin ramma, komai normal sai palpitations,
zuciyarta na bugawa da sauri da sauri, suka din ga rarrashinta, suna kwantar
mata da hankali.
Aka yi mata abin da yakamata, aka kwantar da ita, aka ce ta ɗaga
ƙafafuwan ta, ta ce ba zata iya ba, suka rufe yadda zata ga me suke yi, ta miƙa
hannu ta riƙo na Abdul.
Doctor Muktar ya ce "Anya ba korarka zamu yi ba, malam
ka nutsu ka mayar da hankalinka mana"
Ramma ba ta san me ake yi ba, ta ji kamar ana yi mata
shocking dai, kuma ana jijjigata. Gashi sai surutu suke yi mata, suna mata hira
mai ma'ana da mara ma'ana.
Ta ce "Doctor Abdul"
"Yes my dear"
"Ban taɓa ganinka a cikin kayan tiyata ba, sai yau da
Allah ya yi kai zaka yanka ni"
Ya ce "To ya ki ka ga, sun yi mini kyau?"
Ta ce "Sosai ma, duk sun fi yi maka kyau".
Muktar ya ce "Ban da son kai fa, tsakani da Allah na
fishi kyau"
Ramma ta ce "Anya kuwa? Doctor ashe doctor Muktar ne ya
yi wa Anty Jauhar matar Yaya Aminu awon ciki, kuma shi ya tabattar da
rasuwarta"
Abdul ya ce "Haba dai?"
"Wallahi tambaye shi ka ji"
Muktar ya ce "Baka ga yana ta lallaɓa rahama ba, gayen
nan na tausaya masa, ko yanzu kafin mu shigo, naga damuwa a tare da shi, ana
gobe za a kashe ta, na gaya masa ya tanadi kuɗi, idan inducing bai yi ba, yayi
failing C.S ne, gayen nan ya ce ko nawa ne, zai nemo su, na daɗe ban ga
zunzurutun so da ƙauna ba sai a wurin su, kuma kalli ikon Allah ga 'yar uwatta
nan da take kawo Madam awo, kamar su ɗaya sak"
Shiru Abdul yayi, bayan da Muktar ya ciro jaririn cikin
rahama, jibgegen yaro, fari ƙal alama ya daɗe ma da mutuwa, fatarsa ta fara
macerating, sai dai kyakykyawan gaske ne, ga gashi cunkus a kansa, har goshinsa
zuwa girarsa gashi ne.
Abdul ya kalli doctor Muktar, amma ya girgiza masa kai, yayi
masa alamar yayi shiru.
Ramma ta ci gaba da magana, doctor Muktar yana bata labarin
Viper da Jauhar.
Ta ce "Wai haryanzu ba a ciro ɗan ba?"
"Babyn naki ne, ƙato to, amma yanzu za a ciro shi in
sha Allah"
Ta ce "Allah ya fito mini da shi lafiya, na bi na ɗaga
hankalina, ashe CS ɗin ba abin tashin hankali bane ma"
Maman ramma na can waje, tana jera salloli tana addu'a,
Allah ya sa a fito mata 'yar ta da lafiya.
Viper kuwa kamar ya haɗiye Nabila, sai satar kallonta yake
yi, duk da ta basar da shi, amma zuciyarta azalzalarta take yi, ta kula shi, ta
yi kewarsa sosai amma ta maze, ta kira Sumayya ta gaya mata suna Asibiti wurin
ramma.
Ramma ta ji shiru-shiru, ba a ce mata ga ɗa ba, ta ce
"Nifa ban ji yayi kuka ba, idan kun ciro shi, ku nuna mini shi mana"
Muktar ya ce "Ai sai mun gama, an kai ki ɗakin hutawa
sannan zaki ganshi"
Ta ce "Ka haɗa kai da abokinka sai ya rigani ganinsa,
shikenan ai"
"Wai dama kina magana haka? Kullum idan aka kawo ki
awo, kanki a ƙasa kina ɓuya"
Tayi murmushi ta ce "Idan na yi shiru, zai shiga damuwa
ne, shiyasa nake magana"
Muktar ya girgiza wa Abdul kai, saboda yadda ya karaya
jikinsa yayi sanyi, ya ƙallafa ransa da ɗora buri a kan abin da ramma za ta
haifa, daga fitowarsa ya sai sa da rago, saboda ya ce ko me za ayi, ko a faɗa
sai dai ayi, amma babban shagalin bikin suna zai yi.
Ya nananɗo jaririn a zani, ya fita daga cikin tiyatar
jikinsa a sanyaye.
Gaba ɗaya suka nufo shi, suna jera masa tambayoyi.
Maman ramma ta ce "Yaya ina rahaman? Mutuwa tayi?"
Ya girgiza musu kai alamar a'a.
Viper ya ce "Kayi magana mana menene?" Yayi
maganar yana ƙoƙarin karɓar jaririn.
Ya karɓe shi, ya buɗe shi, ya ga bashi da rai.
Take jikin Viper ya sanyi ya ce "Innalillahi wa
Innalillahi raji'un. Yaron ba shi da rai, kamar ma ya kwana biyu da rasuwa,
amma mama da wa yaron nan yake yi miki kama" yayi maganar yana nuna mata
fuskar jaririn.
Ta ce "Kaii, kamar Nura ce ai wannan, wallahi kamar su ɗaya
sak, bani shi na gani, ina ma yana da rai, wayyo Allana" ta karɓi jaririn
tana kallonsa, hanci har baka ƙato mai kyau, amma babu rai.
Abdul ya koma ya jingina da jikin bango yana kallonsu kawai,
jikinsa gaba ɗaya ya yi sanyi, yama kasa komawa ɗakin tiyatar.
Sai da Nurse ta fito ta ce masa, ana nemansa, sannan ya
shiga, ya tarar an gama ɗinketa, har an sakata bacci, aka fito da ita daga
tiyatar, suka nufeta, suka tarar bacci take yi, dan yadda aka fito da ita kamar
matacciya.
Aka kaita post-op room, aka kwantar da ita.
Doctor Muktar ya kalle su ya ce "Haƙiƙanin gaskiya, tun
da ku ka zo na yi mata scanic, naga yaron ya mutu, bana son ɗaga muku hankali
ne, ta ƙara karaya kafin ayi aikin, rashin sanar da batun zubar ruwan nan ne,
da wuri ya ƙara ta'azarra lamarin. Amma Alhamdilillah ita tana nan ƙalau, mun
tura lab ayi post-op pcv, mu gani idan jinin jikinta ya isheta normal ne, idan
kuma akwai buƙatar a ƙara shikenan, amma dan Allah a rarrashe ta, a bata
baki"
Mama da su Nabila suka yi ta yi masa godiya.
Viper ya ce "Yakamata ka zo mu je a binne shi ko"
Jiki a sanyaye ya ce "Dan Allah a jira ta farka, ta
ganshi, idan aka rufe shi ba ta ganshi ba, za ta ji babu daɗi"
Viper ya jinjina kai, mama ta miƙa wa Viper yaron, ta tafi
gaban gadon ramma da take ta bacci, tana kallonta tana shafa kanta cike da
tausayawa.
Viper ya riƙe yaron sosai, ya zuba masa ido, ya tuna shi ko
gawar masa ɗan ma bai gani ba, kamar dai Abdul ɗin nan haka ya din ga zumuɗi a
kan haihuwar da yake saka ran ayi masa, amma a ƙarshe duka biyun ya rasa su.
Shirun da ya yi yana kallon jaririn, Nabila ta san me yake
tunawa, saboda yadda ya tattara nutsuwar sa kacokan a kansa, yana ta sauke
numfashi.
Nabila ta miƙa wa Viper hannu, ta ce "Ba ni shi nima na
ganshi"
Mugun kallon da ya yi mata sai da ta ja da baya, ya koma
gefe ya zauna, rungume da gawar yaron.
Alhaji mu'azzam ba ya gari, ya aiko yaronsa da yake yi wa su
ramma hidima, idan da wani abu da ake buƙata.
Nabila idan idonta dai-dai yake gane mata, har da harara
Viper yake ta aika mata.
Abdul kuwa sai da ya zubar da hawaye, a cikin zuciyarsa yake
jin ƙaunar yaronsa, gashi dai babu rai ya zo, amma sosai yake jin son sa a
ransa.
Mummy ce ta addabe shi da kiran waya, ya gaji ya ɗaga ta ce
"Kana ina ne?"
"Ina Asibiti Mummy"
"Na ji muryarka ƙasa-ƙasa wani iri, menene?"
"Rahama na yi wa C.S, ta haihu ɗan babu rai".
"To kuma shi ne me? Ba zaka raba kanka da harkar
mutanen banza nan marasa mutunci da suka ɗaureka ba ko? Ka dawo gida babanka
yana hanya zai shigo Kano, yana son ganinka, tun da kai ba ka ga dacewar ka je
in da yake ba"
"Mummy, ɗa na fa na rasa, an yanka 'yar mutane,
haryanzu ba ta farfaɗo ba, kawai na kama hanya na tafi na bar su, anya na yi
musu adalci kuwa?"
A fusace ta ce "Ni ka ke gaya wa haka Abdul?"
"Ki yi haƙuri, ba wai rashin kunya bane ba, ko gaya
miki magana ne ba, amma duk fa abin da ya samu rahama ni ne sila, zuwa anjima
in sha Allah zan dawo, ina jiran ta farfaɗo ne"
Ya katse wayar, yana mamakin son kai irin na iyayensa.
Ramma ta farfaɗo daga baccin da take yi, suna ta jera mata
sannu, kafin ta amsa ta kalli Nabila ta ce "Anty Nabila ina jaririn
ne?"
Nabila ta ce "Bari a kirawo Abdul ɗin"
Aka kirawo Abdul, ya shigo cikin kulawa yana yi mata sannu.
Ta ce "Ina babyn?"
Ya zauna a gefen gadon ya ce "Ki na ji rahama, ki yi
haƙuri da duk abin da Allah ya hukunta mana, babyn bai zo da rai ba, da alama
ya ma kwana biyu da mutuwa a cikinki, sai mu yi haƙuri"
"Wayyo Allana, Innalillahi wa Innalillahi raji'un,
yanzu duk wannan wahalar da na sha amma ya mutu"
Mama ta ce "Ke ramma, ba musulma ba ce ke? Ba za ki yi
tawakalli ba?"
"Mama na sha wahala fa, amma ya mutu" ta yi
maganar tana kuka.
"To dan ubanki sai ki dawo da shi, ke da ki ka samu
kanki lafiya ƙalau ba zaki gode wa Allah ba?"
Ramma ta kasa jurewa ta fashe da kuka, Abdul ya yi shiru ya
ma rasa me zai ce mata, shi kansa kukan yake son yayi, saboda ya saka rai sosai
da sosai.
"Rahama" Viper ya kira sunanta.
"Na'am" ta faɗa tana ɗaga kanta ta kalleshi.
Ya ƙarasa gaban gadonta ya ce "Ba a jayayya da ikon
Allah kin ji ko? Mamanki da ta rasa Nura haƙuri tayi, nima na rasa ɗa na da
matata da tsohon cikin da na ƙallafa rai a kansa, amma ko ganinsa ban yi ba, na
rasata na rasa ɗan, dan haka ki yi haƙuri ki yi masa addu'a"
Ya nuna mata jaririn nata, ta kai hannu ta taɓa fuskarsa ta
ce "Shikenan, Allah ya jiƙansa ya sa ya huta"
Abdul ya ce "Amin, ki yi haƙuri kin ji madam, Allah ya
kawo mai amfani, ki kwantar da hankalinki, dan a samu ki warke da wuri" ta
jinjina masa kai.
Viper ya saka yaron a kwali, ya ce wa Abdul, "Mu je a
binne shi ko?"
Abdul ya jinjina kai, har magariba Nabila na tare da su
rahama, ana ta rarrashinta, daga baya tayi musu sallama ta tafi gida.
Sai da Viper ya tabattar da su mama basa buƙatar komai,
sannan ya tafi.
Muktar ya daɗe yana ba wa Abdul labarin Viper da matarsa, da
yadda aka liƙa masa kashe matar ta sa, har yake gaya masa yaje kotu ya bayar da
shaida a kan shari'ar, tare da nanata Naja'atu Bunkure ba ta da imani.
Abdul ya yi shiru yana tunani, tabbas duk abin da Viper
yayi, tirsasa masa aka yi, an cutar da shi da yawa, dole ya tsane shi.
Jikinsa a sanyaye ya koma gida, yana hasko cewa shi ɗansa
kawai ya rasa, duk ya damu ya shiga cikin tashin hankali, amma shi Viper da
matar da ɗan ya rasa, kuma aka ɗaure shi aka tauye masa hakkinsa. Da haka ya
ƙarasa gida.
Yana zuwa gidan ya shiga falon Mummy, suna tare da Indabo,
yana cin abincin dare.
Ko zama bai yi ba, ta hau shi da faɗa, ta in da ta shiga ba
ta nan take fita ba, tana kiransa mara zuciya da bai san ciwon kansa ba.
Cikin takaici da mutuwar jiki, ya ce "Mummy ɗa na fa na
rasa, haihuwa aka yi mini ɗan ya koma, kuma ɗa na halal ɗan sunna. Mummy idan
iyayen rahama sun saka an rufe ni, meye na ɗa na a ciki? Yadda ki ke jin so da
ƙaunarmu, haka nake ji a raina, ɗa na ne ya zo babu rai, amma baki tausaya mini
ba, baki jajanta mini ba sai faɗa ki ke yi mini ya zan yi ne?"
Indabo ya ce "Abdul" Abdul ya kalle shi ya ce
"Zo nan" Abdul ya ƙarasa gaban digning ɗin ya ce "Gani"
"Zauna mu yi magana" Abdul ya ja kujera ya zauna
yana sauraren indabo.
"Yanzu Abdul duk abin da ka haddasa, duk bai dameka ba
ko? Ka wulaƙantar mini da kuɗi, a kan shashashar 'yar ƙauye, ka yi asarar
takarar da nake ta fafutukar na tsayar da kai, dan na san ina tsayar da kai, za
ayi caa a tona asirinka, a sake ɓata mana suna, yanzu ni na riga na san na yi
asarar takarata duk saboda wawancinka, kuma still baka yi regreting ba, kana faɗar
maganganu kana cikin hayyacinka kuwa Abdul? Tun wuri tun da ta haihu, shikenan
ina son lallai ka rabu da yarinyar nan, ka fita harkarta, ka zo ayi settling
maganarka da yar party chairman haryanzu muna da sauran chances, a next tenure
za a iya baka minista, ni kuma in san abin yi. Dan haka lallai ka saketa tun da
dama ba wanda ya san ka aureta"
Ya kalli mahaufinsa cikin matsanancin takaici ya ce
"Daddy, yadda Jafar yake Mexico a tsare, ranka yake maka zafi saboda an
tsare maka 'ya, haka maman rahama take ji, koma fiye a duk lokacin da ta tuna
na keta wa 'yar ta haddi.
Ba dan na zaɓi rahama a kan ku iyayena ba, amma sai da
rahama ta shigo rayuwata, na fuskanci gaba ɗaya rayuwata jarrabawa ce,
kasancewarku iyayena, babu wanda ya tsawatar mini da shaye-shaye, ko sauran
laifuffukan da nake aikatawa ba, kuna kallon hakan a abu ne da zan daina a
gaba, rayuwar cikin turawa ya sanya na zama haka. Ban ƙara tabattar da zamanku
iyayena jarrabawa ce ba, dai da na nuna maka videon mummunan aikin da ka
aikata, amma hakan bai wani dame ka ba, kuma bai girgiza Mummy ba, saboda
duniyar ce kawai a gabanku, ni kuwa tuni rahama ta ankarar da ni fifikon
Lahirata a kan duniya saboda ita ce dahir.
Na miƙa lamurana ga Allah, la'akari da Annabin Allah ma,
Annabi Ibrahim alaihi salam, Allah ya jarrabe shi a kan mahaifinsa, haka an
jarabci Annabi nuhu da ɗansa, kowane bawa da irin ƙaddararsa, wallahi ku ka ci
gaba da matsa mini, zan bar gidan nan, zan je na ci gaba da rayuwata
kawai"
Indabo ya kwantar da murya ya ce "Haba Abdul, duk
wannan abubuwan da kaga ina aikatawa, duk dan mu yi surviving ne, na inganta
rayuwarku, kuma abin da ka gani abu ne da ya riga ya wuce, na daina aikatawa,
kowane ɗan Adam akwai irin laifin da yake yi wa Allah, kuma Allah mai rahama ne
da jin ƙai"
"Amma Allah ba abokin wasanmu bane, da dan muna taƙama
da mai rahama ne da jin ƙai, zamu din ha aikata zunubai yadda muka ga dama, mu
ce gafurun rahimu ne ba. Kuma ace ɗan Adam baya kunyar saɓawa Ubangiji, Daddy
har kisan kai fa ka ke saka wa a yi"
Indabo ya ce "Wa na ce a kashe?"
"Matar Aminu Viper, dan ɗan uwan rahama ne matata, aka
kashe matarsa da ɗansa, ita laifin me ta aikata?"
"Shi ne yake hure maka kunne kenan? Shiga gonata yayi,
na ce aje a koya mass hankali, tsautsayi ya faɗa kan matarsa"
Hawaye na bin fuskar Abdul ya ce "Kun samu ssɓani
saboda yayi barazanar tona maka asiri na abun da na yi wa yayan rahama, ka tura
a kashe shi, aka kashe matarsa, kuma sai aka ɗora masa laifin.
Daddy su iyaye ba a canza su, kuma ba a wulaƙanta su, ko da
kuwa mushirikai ne, shiyasa tun a wancan lokacin na yi shiru na ci gaba da yi
muku biyayya, kamar yadda Annabi Ibrahim alaihi salam yayi. Amma muddin ku ka
ci gaba da takura mini, a kan rabuwa da rahama, zan bar gidan nan gaba ɗaya.
Allah ne ya tashi kama ni, ya sanya na keta mata haddi ya jarrabe ni da son ta.
Allah ne ha so ni da rahama, na haɗu da rahama, kuma shigowarta rayuwata ta zo
mini da tarin alkhairi, ni duk abin da suka yi mini, ban ji haushi ba, domin
kuwa ma sassauta mini suka yi, dan Allah ku bar ni na ji da zafin da zuciyata
take yi mini dan Allah" yayi maganar yana haɗa hannayensa alamar magiya.
Har Mummy za ta yi magana, Indabo ya ɗaga mata hannu, Abdul
ya wuce yana share hawaye, yana jin zuciyarsa na wani irin zafi saboda tuna
wasu abubuwan.
*****
Viper ya tafi tare da Abbu ya duba ramma a asibiti. Abbu sun
yi hira sosai, dan sai da hirar ta tuna masa da marigayiyya matarsa babbar su
Viper zahra'u.
Abdul yana ta zarya a kan rahama, baya damuwa da shan
ƙamshin da mama take yi masa, hatta medications ɗin ta, shi yake serving.
Duk abin da ake buƙata haka yake yi mata, baya nuna gazawa,
dama yana zuwa mama ke bar musu ɗakin.
Ranar da Abbu ya zo duba ramma, Nabila ma tana nan, yana
ankare da su daga ita har Viper, babu wanda yake kula wani, yayi musu shiru bai
ce musu komai ba.
Sai da Ramma ta kwana biyar a asibiti, sannan Abdul ya yadda
a sallameta, babu wani abu da yake damunta, ta samu sauƙi sosai da sosai.
Nabila na zaune a ɗakinta, a kan gado, ta baje takardu tana
duddubawa tana nazarin shari'oin da take da su.
Abba yayi sallama a ɗakinta, ta amsa masa ta miƙe tana faɗin
"Abba Allah ya sa ba laifi nayi ba?"
"Saboda kin saba da aikata laifuffuka ba" ta ɗan
yi murmushi.
Ya zauna a gefen gadonsa ya ce "Maganganu ne da ni nake
son mu yi" yayi maganar yana kallon jikin wardrobe ɗin ta, duk ta liƙe shi
da hoton maciji da stickers na Viper.
Ta ce "To Abba ina jinka"
"Yanayin alaƙarki da ɗan uwanki Nasir, dan Allah ina
son komai ya wuce, ba na son gabar da ku ke yi sam"
"Abba ba gaba nake da shi ba, kawai ika mamakin yadda
ya din ga kware mini baya ne, yana haɗa
ni da kai"
Major ya ce "Na sani Arfa, amma Nasir ba ƙashin yarwa
bane, kin san kowane ɗan Adam tara yake bai cika goma ba, kuma abin da ya
aikata shi ake kira da rauni, irin na ɗan Adam"
Nabila ta jinjina kai ta ce "Haka ne"
"Yauwwa dan Allah ya wuce ki yi haƙuri"
"To Abba, in sha Allah ya wuce, Allah ya yafe mana baki
ɗaya, yanzu ka yarda gaskiyar da ka tarbiyyantar da ni a kai a kanta nake
dagewa, shiyasa wasu lokutan ake ganina kamar mara ji, ko mara ɗa'a ko"
Yayi dariya ya ce "Na yarda, Allah ya ci gaba da dafa
miki"
Ta amsa da "Amin"
"Abu na gaba, babanki ya ce na gaya miki, An tsayar da
ranar auren sisternki, ƙarshe watan nan, za a sake ɗaura aure, ta koma gidan
tsohon mijinta, Alhaji mu'azzam"
Nabila cikin farinciki ta ce "Alhamdilillah ala kulli
halin, na ji daɗi sosai da sosai nayi farinciki, Allah ya sanya musu albarka ya
daidaita su" ya amsa da "Amin, to ke ya naki batun ne? Kin ce ba kya
son yaron nan, babansa sai magiya yake yi yana roƙo, ga Sumayya mamanta ta yi
mini magana, wani ya fito ya ce shi kuɗin aure zai kawo, ke kuma kin ja bakinki
kin yi shiru, baban yaron nan ya damu lallai a ba wa ɗan sa ke"
Jiki a sanyaye Nabila ta ce "Haryanzu Abbu bai haƙura
ba? Wallahi ina jin nauyinsa sosai da sosai, amma ba zan iya auren Vi ba"
"Meye kuma vi?"
"Au Al'amin"
"Haryanzu yana shaye-shayen ne da harkar daba?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a, ai yanzu soja ne, kuma yana
zuwa asibitin ƙwaƙwalwa, duk ya rage yin wasu abubuwan, kawai dai ba na son sa
ne"
"Ita kuma wallpaper ɗinki, da wannan liƙe-liƙen na ɗakinki,
duk cikin tsanar ta sa ne?"
Cikin jin kunya ta ce "A'a Abba, kawai dai ina sakawa
ne, a lokacin ina da hope na ganin na saka kotu ta wanke shi daga zargi"
Abba ya tashi ya ce "Gaskiya ne, to ni dai duk hukuncin
da babanki ya yanke ba ni da ta cewa, tun da na ga shi ma yana yin yaron, ni na
fita sai na dawo"
"A dawo lafiya"
"Allah ya sa"
*****
Rahila ta ɗaga hankalinta sosai, ganin da gaske Walid da ba
shi da komai zai aura wa Shahida, babu irin zagin da ba ta yi wa shahida ba,
amma tayi bore ta ce ba ta so, amma Shahida ta ce ita ta ji ta gani.
Abbu ya ce "Ke dama ban isa sa ke ba, Shahida kuwa 'ya
ta ce, dan haka ina da ikon zartar da duk wani hukunci a kan ta, idan bai yi
miki ba, zaki iya tattara kayanki ki ƙara gaba, dan albarkacin ta kawai ki ke
ci ki ke zaune a gidan nan" haka suka yi faɗa kaca-kaca, ƙarshe Shahida
sai komawa tayi cikin ɗaki tana kuka.
Da daddare da Viper ya je gidan, ya ga Shahida kamar ba ta
walwala, yake tambayarta ko lafiya.
Cikin damuwa ta ce "Dan Allah yaya, ka roƙa mini Abbu,
na ji ya ce saboda ni mama take zaune a cikin gidan nan, dan Allah ka ba shi
haƙuri, na san tun ba yau ba, yana matuƙar haƙuri da ita, amma dan Allah yayi
haƙuri, ba ta da cikakkiyar lafiya kuma idan ya rabu da ita, babu in da za ta
je, dan Allah yayi haƙuri"
Viper ya ce "Kar ki damu, barazana yake yi mata, kin
san shi da tausayi, da kuma fushi wasu lokutan, amma in sha Allah ba zai rabu
da ita, duk a kan maganar aurenki ne ko?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
"Ba zigaki nake ki bijire mata ba, amma ki samu miji
irin Walid, sai kin daɗe kina tonawa, tun da ki ka ga Abbu ya amince shi ma, ba
mutumin banza bane ba"
Shahida ta ce "Haka ne Yaya, ni dan Allah ma ka yi masa
magana, wai ba zai yadda a bashi aurena, kuma a bashi wurin zama ba, wai haya
zai kama, kuma ya dage sai ya yi mini kayan lefe ko babu yawa. Naga ba ƙarfi ne
da shi ba, kuma ni ina duk abin buƙata. Budurwa ce ni ba bazawara ba, amma yaƙi
yadda"
"Muhsin bai yarda da gazawa ba, wannan wata aƙida ce da
muke da ita, ko zamu yi a raina, mun fi son mu ƙoƙarta, amma ki kwantar da
hankalinki, zan yi magana da shi in sha Allah, kuma da mun kammala shiri, ba
jira zamu tsaya ba da an kawo kuɗin aure lokaci za a tsayar, duk abin da ki ke
buƙata ki gaya mini"
Shahida ta amsa da "To yaya in sha Allah "
Wasa-wasa girma ya hau kan Viper, ɓangaren ramma shi ne,
haka gidansu, ga liti ga Walid, kowa Viper.
Al'amin sai da ya fara tausayawa Abdul, Abdul bai furta a
bashi ramma ba, amma yadda yake sintiri kullum a tafe, ya ƙara tabattar da
gaisuwa yake gami da roƙon iri, a kan a bashi matarsa.
Ita kanta mama ta ɗan fara saukkowa, ta zuba musu ido. Dan kuwa duk da jaririn ya
mutu, sai da ya yanka san da ya saya ya ce idan ta haihu za ayi mata amfani da
shi.
Duk da kayan da take da su, sai da yayi mata sayayya fal, na
kayan sakawa.
Ranar da ya kawo, ta din ga yi masa godiya, ya tambayeta, me
take so ta karanta zai yi processing komawarta makaranta.
"Nurse nake son zama"
Yayi murmushi ya ce "Shikenan, sai mu ƙarfafi
asibitocinmu, mu kula da su sosai da sosai, amma rahama zaki dawo gidana sai ki
yi karatun?"
Ramma ta ce "Ai ka san wannan ba maganata ba ce ba,
maganar mama ce da yaya Aminu, amma kuma idan na dawo gidanka ai ba zan samu
yin karatun ba, an ce ba a ɗaukar masu ciki"
Abdul ya ce "No, sai mu yi planing zuwa lokacin da zaki
kammala"
Ta ce "Anya kuwa, yadda ka ke son yara, kar in je ka
canza shawara"
"Haba rahama, kin fi kowa sanin halina, ni ɗan Adam ne,
amma ban fiye yi wa mutum ƙarya ba dan ya yarda da ni, duk son yarana dolena na
jure, kema na ga na inganta rayuwarki na kafa ki"
"To ka bari yaya Aminu ya dawo, ya koma wurin aiki ne,
amma ka fara yi wa Daddy magana tukuna"
"Waye daddyn?"
"Alhaji mu'azzam mana, ko da nayi aiki a gidansa, ai
haka ake ce masa"
"To shikenan, zan yi masa magana in sha Allah, kin san
za a mayar da aurensa da yayar Nabila Hafsa".
"Ai ban santa ba, ni lokacin anty Jidda na fara aiki a
gidan"
Abdul ya ce "Ok haka ne, ta koma gida ma, wai sai ya
saketa duk a kan case ɗin mu, ni kowa ya ƙarata, a bar mini matata kawai"
Tayi murmushi suka cigaba da hira.
Nabila sai da tayi ta rarrashin Hafsa, a kan tayi haƙuri ta
koma gidan Alhaji mu'azzam, dan fafur cewa tayi ba ta sonsa.
Kasancewar duk ƙarshen wata, sai tayi sayayya taje ta gaida
Baba, hakan ya saka sun shaƙu sosai da hafsa, sai dai sauran mutanen gidan babu
ruwanta da su, idan aka cire saifu, shi ma suna gaisawa.
Tare suka ta shirye-shirye, Hafsa tana cewa ita babu wani
gyara da zata yi, lokacin da aka yi na farin ma, bai yi mata amfani ba balle
yanzu.
Amma Nabila da taimakon sumayya suka ce, sai ta yi gyara da
da yanzu ba ɗaya bane ba, zamani ya riga ya canza.
A lokacin Shahida ma Walid ya kai kuɗin aure, kuma Hafsa
ƙawar Shahida ce, kasancewar iyayensu aminai ne. Watanni biyar aka saka, saboda
babu yadda Viper bai yi da Walid ba, ya dage ya ce shi sai yayi mata lefe ko
yaya yake, kuma sai ya kama gida. Shi ba ruwansa da bazawara ce, ba zai so ace
shi aurensa na fari, ace ya naɗe hannu komai sai dai ayi masa ba.
Viper ya ce masa ya gyara nasa gidan, su zauna sai ya din ga
biyansa kuɗin hayar.
Walid ya ce "Ai sakankancewa zan yi, na san naka ne,
idan ma ban biya hayar ba, ba zaka damu ba, kuma zan ta damuwa gidan zai din ga
tuna mini ƙanwata Jauhar, kuma kai a ina zaka zauna, idan ka yi naka
auren?"
Viper ya ce "Ina da wurin zama ai ni, ko ka ƙi, ina
wani gidan, na ji ba zan saka maka hannu ba, ka gyara shi da kanka, kayi lefen,
amma ba zaka kama haya ba gaskiya ba"
Da kyar Walid ya amince da hakan, sai dai Liti ya zage kamar
kayan lefensa zai tara, kuma Nabila suke turawa kuɗi take haɗa kayan, ita kanta
Shahidan ba ta san da haka ba"
Sai dai daga Hafsa har Shahida sun dawo daga rakiyar
iyayensu, na shirmen bin bokaye, domin sun tabattar da ba hanya ce mai ɓullewa
ba.
Kasancewar Sumayya na ta'amalli da mutane daban-daban, a
dalilin harkar aikinta, ya sanya ta nemi lambar maman dr., Domin haɗawa Alhaji
mu'azzam da kuma ango Walid amayarsa. Tun da ita mace duk in da take sai da
gyara. Kuma masu iya magana suka ce, idan kana da kyau ka ƙara wanka.
A cikin wata gudan
nan, ba ƙaramin kyau Hafsat tayi ba, sai sheƙi tayi gwanin sha'awa, duk da ba
ta da jiki, amma maman dr. Ta tsatsota, ta cika tayi fam, tayi ƙiba dai-dai
misali, amma duk lokacin da Alhaji mu'zzam ya zo sai sun yi faɗa. Gashi can
gidansa uwargidansa ta sako shi a gaba a kan ya ce zai dawo da hafsa, rashin
mutunci na yau daban na gobe daban, gaba ɗaya ta ƙaurace masa, yadda Jidda ma
ta fita, so take ta rayu itakaɗai a gidanta, shi kuma ya ce bata isa ba, yana
da wadata da lafiyar da zai auri mace fiye da ɗaya.
Ya din ga ganin tamkar ranaku ba sa sauri, duk lokacin da ya
je wurinta, da kyar yake saita nutsuwarsa, saboda kyan da tayi, da wani irin
sihirtaccen ƙamshi da take yi. (Domin gyara da kankaro naku mutuncin kuma a
naku gidajen auren, ku garzaya ku tuntuɓi maman dr. Likktar mata domin kar ayi
babu ku 07069711327)
Viper yana zaune yana duba status ɗin sa na waya, yana son
ya halarci ɗaurin auren hafsa, dan haka yana saka ran ana idar da sallar asuba
zai nufo Kano, duk da ɗaurin auren na azahar ne sai an saukko daga masallaci.
Status ɗin Nabila da ya yi muting ya shiga, na farko Addu'a
ce, kamar yadda ya zame mata ɗabi'a, yawan sanya addu'oi da shot videos na
malamai.
Na gaba kuma, videonta ne, an yi mata lalle ja da baƙi, sumayya tana cewa our dear barrister marasa
galihu, jin ki yafi ganinki, our anti serious beb" ta kwaɓe fuska tana
harar Sumayya.
Ɗaya Videon kuma, Ita da sumayya ne da amarya hafsa, da wasu
daga cikin yayyen su mata.
Haushi ne ya kama shi, ya san wataƙila duk mazan da suke
cikin wayarta sun ga status ɗin, doguwar riga ce a jikinta, ta ɗora mayafinta a
kanta, shigarta decent amma shi abin da idonsa yake gani, gani yake kowama ya
gani.
A irin fitinarta, duk abin da Hafsa take amfani da shi na
gyara, sai ta ce sai ta sammata.
Nabila kuwa tana saurar tashar su Sumayya, At the same time
tana chatting, Sumayya na shirye-shiryen rufe tashar, ta fara sanar da ɗaurin
auren hafsa, sannan ta ambaci na Nabila da Al'amin, a babban masallacin juma'a
na BUK wanda za a ɗaura bayan an idar da sallar juma'a.
Ayshercool
08081012143
Miƙewa Nabila ta yi tsaye, tana tunanin kamar ba ta ji sosai
ba.
"Wane irin wasan banza ne haka sumayya take yi
mini?" Tayi maganar tana mamaki.
Wayar Sumayyan ta hau kira, amma wayarta a kashe, jikinta na
rawa ta fito falo, amma ta tarar kowa ya kwanta, ko ina a rufe.
Ta koma ta hau kiran Umman Sumayya, amma ita ma ta ta wayar
a kashe.
Ta saka wa zuciyarta zolaya ce kawai Sumayya take yi mata,
dan tun da aka yi musu lallae take cewa tayi kyau kamar ranar tarewa a gidan
Viper.
Sai dai wannan ya wuce wasa, ta rasa meyakamata tayi, ta din
ga fatan Allah ya sa mafarki ne ba gaske ba.
Gaba ɗaya ta kasa bacci, sai dai yadda ta kasa baccin nan,
haka Nasir ya kasa, da yayi juyi ya kalli invitation ɗin auren Nabila, sai
gabansa yayi wata irin mummunar faɗuwa, cike da baƙin ciki da damuwa.
Ya so Nabila tun tana 'yar ƙarama, tun tana yawo ba riga, ba
ta san ciwon kanta ba, yana matuƙar tausayinta, yana taya major ƙaunarta,
saboda maraicinta, ga rashin lafiya ga kuma ƙiyayyar da mutanen gida suke yi
mata.
Wahalarta babu wadda bai sha ba, kaita makaranta, yawon
visiting kaita Asibiti idan Major baya nan, duk wata gudunmawa da ya san zai
iya bayarwa domin ta ji daɗi yana yin su.
Duk rashin jin ta da karaɗinta baya damunsa, babban burnsa
ya ganta tana cikin faranciki, mussaman idan yayi la'akari da hadisan Annabi
Sallallahu alaihi Wasallam, da suka yi magana a kan kula da maraya, idan ya
tuna mamanta ta rasu, ba ta san waye babanta ba, sai matsanancin tausayinsa ya
ƙara shigarta.
Bayan Major ba ta da wasu da yadda da su take ƙaunar su,
sama da shi da Sumayya, koma Yaya Nasir ko Sumayya, duk wata wauta da taɓara da
zata yi, baya gajiya, da hakan matsanancin son ta ya shiga ransa, sai dai mama
ta riga tayi masa kandagarki da Allah ya isa a kan Nabila, tsawon lokacin nan
baya iya kula kowacce mace, saboda Nabila, sai dai duk wannan son da yake yi
mata, lokaci ɗaya kuɗi suka rufe masa ido, ya tafka mummunan kuskuren da ya
rushe waccan kyakkyawar alaƙar da take tsakaninsu, har ta kai tana yi masa
kallon maƙiyinta a yanzu.
Da Asuba Viper ya nufo Kano, Abbu ya kira shi a waya, suka
gaisa ya ce "Ka taho ɗin ne, zaka halarci ɗaurin auren?"
"Eh in sha Allah Abbu, ai ina hanya ma, na biyo sojoji
mun taho"
"Akwai kuɗi a wurinka ne?"
Viper ya ce "Eh, amma kamar nawa?"
Abbu ya ce "Dubu ɗari biyu"
"Eh ba za a rasa ba"
"To da ka dawo ka taho gida da kuɗin, ina son
ganinka"
"To in sha Allah, ina nan tafe"
"Allah ya kawo mini kai lafiya"
Viper ya yi murmushi ya ajiye wayar.
Sai dai babu daɗewa Walid ma ya kira shi, ya ɗaga ya ce
"Mazaje ya ne?"
Walid ya ce "Mai zamani"
"Mai laya?"
"Za ka zo ɗaurin auren yayar Nabila ne?"
"Eh in sha Allah"
Walid ya ce "To ka yi sauri"
"Me zaka bani, ba sai bayan juma'a ne ɗaurin auren
ba?"
"Eh kawai dai ka yi sauri"
Viper ya ce "To aiko mini da fuka-fukai na tashi
sama"
Walid ya yi dariya ya ce "To in dai zaka yi sauri ai
shikenan"
*****
Wayewar garin Allah, Ana idar da sallar asuba, Nabila ta
tafi ɗakin Abba, ta tarar bai ma dawo daga masallaci ba, ta samu wuri ta zauna
tana jiran dawowarsa.
Yana yin sallama ta tashi tsaye, ta ce "Abba, ina
kwana?"
"Lafiya ƙalau, kin tashi lafiya?"
"Abba ni fa ban yi bacci ba, Sumayya ce ta yi mini wani
wasan banza da ya ɗaga mini hankali, wallahi ido biyu na kwana cikin zullumi da
fargaba, na zata mafarki ne ma zan farka, amma dai na ga gaske ne"
Ya zauna yana faɗin "Subhanallah, wane irin wasa ne
haka, da ya hana barrister bacci?"
"Ɗaurin auren hafsa ta sanar, kuma sai na ji ta faɗi
sunana da na Viper, wai za a ɗaura mana aure"
Major ya ce "Ikon Allah, kuma kin kira wayarta?"
Ta ce "N kirata wayar a kashe, na kira ta Umma ma, amma
ba ta shiga duka"
Abba ya jinjina kai ya ce "Abin da mamaki gaskiya, bai
kamata ta yi miki wannan wasan ba gaskiya, amma ki je ki samu ki yi bacci, na
san da wasa take yi miki, wurin ƙarfe goma sai ki shirya ki tafi can gidan naku
wurin bikin, na ji Antynki da su Magajiya duk suma za su je"
Ta ce "To Abba" sai ta ji ƙwarin gwiwa, ta je ta
nemi wuri ta kwanta, sai ta samu bacci ya ɗauke ta.
Tana farkawa, Sumayya ta fara kira, wayar ta shiga amma
Sumayya taƙi ɗagawa, hakan ya ƙara fusata ta.
Ta fita kitchen, tana gaya wa baba magajiya abin da tayi
mata cike da takaici.
Baba magajiya ta ce "Kun fi kusa, ina fatan Allah ya
tabattar mana da alkhairi"
"Ba amin ba, ba da shi ba alkhairin"
Baba magajiya ta ce "Au zaki ga ba da shi ba, ni dai
ina yin sa, duk da ya ce kar na gaya miki, ranar da suka zo, dubu goma ya bani,
ya ce na sha lemo, a samarinki waye ya taɓa saurarata"
A shagwaɓe ta ce "Ni fa ba saurayina ba ne ba"
"Oho miki dai, ni dai Allah ya zaɓa abin da ya fi
alkhairi"
Nabila ba ta sake cewa komai ba, ta hau bubbuɗe kwanuka, ta
buɗe fridge ta ɗauki gasarar alkama, ta dama kunu da ita, ta ɗebi doya ta dafa
ta ɗebi miya ta koma ɗaki.
Ta fara karyawa, ta shiga facebook, saboda tana buɗe data,
notifications suka din ga shigowa ba ƙaƙƙautawa.
Ai tana shiga da invitation ɗin ta fara cin karo, ana ta yi
mata Allah ya sanya alkhairi, ba ta san lokacin da ture kofin kunun ba, ta
tashi da sauri, har tana tuntuɓe, ta shiga ɗakin major tana zazzare ido.
Ta tarar da shi tare da telansa, ta ce "Abba ka ga
fa" tayi maganar tana haska masa fuskar wayarta.
Ya sallami telan sannan ya ce "Zauna mu yi magana"
Ta zauna jikinta yana tsumar rashin sanin abin yi.
"Nabilatul arfa, tun da mahaifiyarki ta rasu ta bar
mini ke, nake kula da ke cikin ikon Allah, tamkar ita nake kallo, ban taɓa yi
miki wani abu da zai cutar da ratuwarki ba. Kuma na daɗe ina baki dama na
aikata duk abin da ki ke so, muddin ba gani nayi zai cutar da ke ba, babu irin
ƙalubale da bamu fuskanta ba daga ni har ke, amma na toshe kunnuwana, domin
ganin kin rayu cikin farin ciki da jin daɗi.
Wannan hukuncin mahaifinki ne ya yanke shi, duk yadda na kai
ga nuna miki so da ƙauna, ya fi ni iko da ke, ko da a gaban shari'a ne, na ce
ya bani dama na tattauna da ke a kan yaron nan, ya bani amma ki ka nuna ke
fafur ba kya son sa.
Kafin na amince da maganar Al'amin, na yi bincike a kansa
fiye da yadda ki ke tunani, wurin aikinsa, wurin mahaifinsa, duk wani motsi na
rashin jin sa sai da aka bani labari. Na zauna da abokansa, sun bani labarin
yadda ki ka shiga rayuwar sa, da duk abin da ki ka din ga yi, rayuwarsa da yar
uwakki, wanda shi kansa bai sani ba.
Irin rayuwar da ya yi da 'yar uwakki, duk na bincika, gefe
guda babansa na ta bi na yana yi mini magiyar a shawo kanki, Allah ma'aiki kar
ya koma rayuwarsa ta baya.
Honorable Mu'azzam Wada kankarofi, shi ma bai ɓoye mini
komai ba, shi ya ƙara ƙarfafa lallai ayi auren nan, zaku zauna yana sonki kina
sonsa, ke kuma naga gaba ɗaya shirme ne a kanki da wauta, dan haka muka yanke
wannan hukunci.
Sumayya ba wasa ta faɗa ba, katin aurenki ne, kuma ina fatan
zaki yi mana biyayya baki ɗaya"
Ƙurawa Abba ido ta yi, ji take kamar almara, kawai kuma ta
fashe da kuka "Abba ka fa ce ba zaka yi mini auren dole ba, haba
Abba"
"Wannan ai ba na dolen bane ba"
"Haba Abba, na dole ne mana, ba sai an tambayi mutum
yana so ko ba ya so ba, kuma ka tambayeni na ce a'a kawai kuma sai a ɗaura"
Ya ce "Eh gaskiya ne, ban kyauta ba, za'a kai ƙarata
kenan, na taɓa masu shari'a"
Yanayin yadda yayi maganar ya sanya ta gane zolayarta ma
yake yi, bai ɗauki hakan serious ba. Hakan ya saka ta ƙara sautin kukanta har
da sheshsheƙa.
Abba ya ce "Maza yi ta yi, in dai kukan banza ne, dama
tun kina zanin goyo halinki ne, idan ki ka isheni kuma, na zane miki
jikinki"
"Abba ba na son shi fa, gaba ɗaya baya so na, ai an
baka labarinsa da Jauhar, ya ce duk duniya itakaɗai ce mace, ba fa ya so na ko
kaɗan, Wannan auren dole ne Abba"
"To Arfa a kaini gaban me Shari'a a tuhume ni da laifin
child abuse, na yi wa barrister auren dole, amma sai ki haɗa da ni da ubanki
duk ki kaimu ƙara. Kai waye a nan wurin ku kira mini magajiya ta zo ta ɗauki
yarinyar nan daga gabana, kafin na casata a wurin nan"
Ƙarshe ya tashi ya bar ta a wurin, tana ta gursheƙen kuka,
kamar an sanar da ita mutuwar tsohuwarta.
****
Ƙarfe sha ɗaya Viper ya shiga gida, Abbu ya ce "Dama
tuntuni kai nake jira, ka ƙaraso mu karya"
Viper ya yi murmushi, yana jin daɗin tattalin nan da Abbun
yake yi masa.
Ya ce "Abbu ya su Walid kuma?"
Abbu ya ce "Yaran kirki, Abdallah babansa ya kai shi
kasuwa, wurin sayar da sarƙoƙi da kayan shafe-shafen mata, ya ce a kama masa
shago, idan ya gane kan harkar sosai, yaƙi zama muna tare da shi a kasuwarmu,
wai shi ba ɗan daudu ba, me zai yi da wani kayan shafe-shafen mata. Na daɗe ban
ga rigimammen mutum kamarsa ba, yanzu haka ma suna kasuwa ne kayanmu zasu iso,
daga nan za su yi mini wani aiki, da yanzu ka gansu a nan. Na je gida mun yi
magana da mahaifinsa na ce yayi haƙuri ya ƙyale shi, tun da ga in da hankalinsa
ya karkata".
Viper ya ce "Liti akwai rigima, wanda bai san halinsa
ba ba zai iya zama da shi ba"
Abbu ya ce "Ai naga alama, akwai barkwanci"
"Idan yana yin mutum kena ba, amma ga wanda bai san shi
ba, goga ne, a lokacin muna mazaje, muna ji da rashin ji, ya fi Walid karsashi,
'yan daba idan sun kai goma, zai ratsasu shikaɗai ba ya tsoro ba kuma ya san
wargi"
Abbu ya rausayar da kai ya ce "Na so ace tuntuni na
farga, na ja ku a jiki ku duka, da kai ɗin da su, na riƙe ku na kula da
iliminku, na kaiku kasuwa, da yanzu Allah kaɗai ya san me zaku zama, su waɗanda
nake kallon su ne shiryayyun na ɗauki ɗawainiyar su, gashi a ƙarshe ba wanda ya
more su, na yarda da ɗa da dukiya ba a yi musu mugunta, yanzu gashi ku ɗin da
ake kallon marasa ji, yanzu al'umma sun fara amfanar ku, ba zan manta da
honorable wada kankarofi ba, bawan Allahn nan ɗan halak ne, gashi ka zama soja
kana aikinka, Allah ya ƙara dafa muku"
Viper ya ce "Amin"
Abbu ya ce "Amma ya aka yi ka ke da kuɗi tsakiyar wata,
ai ni da na ce ka taho da 200k da idan ka ce babu, zan ƙara nuna maka amfanin
haɗa kasuwanci da aiki ne, an ce albashin naku, ba shi da yawa".
Viper ya yi wata irin dariya ya ce "Ko a cikin sojoji,
irin aikinmu na musamman ne, kuma mai hatsarin gaske, ina da salary mai kyau,
zan zaɓi garin da nake so a bani gida, kuma za a bani abin hawa, ba a buƙatar
rashin gskiya ko a samu irinmu da halin cin amanar ƙasa, idan aka kama mu da
haka, babu shari'a kisan kai ne kawai. Shiyasa irinmu a sojoji ba su da yawa ko
kaɗan"
Cikin mamaki Abbu ya ce "Wai bayan fitowar ka har ka yi
training ɗin ko kuwa? Kuma wane iri ne aikin naku a sojoji?"
"Ina gaya maka kashe ni za ayi, ba a faɗa kawai dai ka
saka a zuciyarka ɗanka soja ne, mai muhimmancin gaske ga ƙasarsa, kuma a kowane
lokaci zaka iya rasa shi, dan haka ka yi mini addu'a kawai"
Abbu ya ce "In sha Allah sai ka yi retire da kanka daga
aiki, ba za a kashe ka ba" haka Abbu ya din ga jan sa da hira, har lokacin
salla ya ƙarato.
Abbu ya ɗaukko masa sababin kayan kar, dark blue ɗin shadda,
riga da wando, da hula. Ga sabon agogo da takalmi.
Ya ce "Wannan fa?"
Abbu ya ce "Wurin ɗaurin aure zamu je, ba na son yawon
da ku ke yi da ƙanan kayan nan, kamar ba yaran hausawa ba, dan haka su zaka
saka"
Shafa kayan ya yi, yana tuna abar ƙaunarsa, Jauhar, a
lokacin da ta bashi kyautar kaya ranar sallar idin ƙaramar salla.
Su Walid ne suka yi sallama a waje, Abbu ya ce ace su shigo,
suka shigo sanye da fararen kaya, liti ya riƙo hularsa a hannu.
Abbu ya ce "Abdallah, ya ka cire hular ka ga
yadda ka yi kyau a cikin kayan kuwa?"
Ya ce "Abbu, hular ce ta ɗame mini ƙeya nake ta gumi
shi ne na cire"
"Ai fa rashin sabo ne"
"Mai zamani, Abbu ne fa ya ɗinka mana kaya" liti
yayi maganar yana nuna masa kayan jikinsa.
Walid ya ce "Mai zamani haka ka ke kyakykyawa, rabon da
ka yi kyau kamar haka, tun ranar aurenka da marigayyiya"
Abbu ya gyarawa Walid zaman tasa hular, ya ce "Yauwwa
ko ku fa 'yan samari, Allah ya nuna mini aurenku duka" suka kasa cewa
Amin.
Wani farinciki ne ya mamaye zuciyar Viper, ganin yadda Abbu
yake nuna wa su Liti ƙauna, wanda ya san duk dan saboda shi ne, shi yanzu a
duniya abin da zaka yi masa, ka saka shi farinciki, ka so mutanen nan uku kamar
yadda yake ƙaunar su, ya san a duniya ba shi da abin biyansu.
Haka suka ɗinguma a mota, suka tafi masallaci, domin yin
salla da halartar ɗaurin Alhaji mu'azzam.
A sahu ɗaya suka yi salla da Alhaji mu'zzam, suna ta yi masa
Allah ya sanya alkhairi.
Bayan an idar da salla, babban abin da ya ba wa Viper
mamaki, bai wuce ganin abokan Abbu da yawa a wurin ba, da kuma wasu daga cikin
'yan uwansa, bai kawo komai a ransa ba, suka gaggaisa, suna taya shi murnar
wanke shi da kotu tayi, wasu kuma na zuzuta kyan da yayi, wasu kuma suna yi
masa Allah ya sanya alkhairi, shi dai duk bai gane kan abin ba, ana ta ɗaura
aure, aka zo kan na Alhaji mu'azzam, aka ɗaura aurensa da Hafsa.
Bayan an kammala na su, aka nemi waliyayyan Al'amin, saroro
yayi yana kallonsu, ganin Baba yana kallonsa yana murmushi, haka Major.
Ya waiwaya, har da su doctor Muktar, da Abdul yasar a wurin.
Sai da aka ɗaura aurensa da Nabila, sannan ya fuskanci abin
da yake faruwa.
Walid ya cire hular Viper, ya shafa kansa ya ce "Angon
Nabila ka sha ƙamshi, yau dai Allah ya yi Allah ya sanya alkhairi"
Yayi saroro yana kallonsu, liti ya ce "Mun iya Suprise
ko? Sai ka bamu tukuci yasin, idan ka cire kayan nan ni zaka bawa, in saka
ranar auren Walidi, ko Allah ya sakani a damshinku"
"Mai laya yaushe aka shirya wannan abin, ita Nabilan ta
amince ne?"
Liti ya ce "Oho muku, mu dai an haɗa kai da mu, an
ƙulla sunnar ma'aiki, ai yanzu rumfar shayi har da banner dalilin aure zan
saka. Idan aka biye muku, wahalar da mu kawai zaku yi ta yi, yanzu sai ku
ƙarata ku sasanta kanku"
Aka fito daga masallaci, Viper sai jin sa yake tamkar ba shi
ba, abin kamar almara.
Alhaji mu'azzam ya ƙarasa ya miƙa wa Viper hannu ya ce
"Na haƙura na janye, na kuma yarda Jauhar taka ce, Nabila ma taka ce, ba a
takara da kai Viper, duk da ka fuskanci ƙalubalen rayuwa da yawa, amma ina da
yaƙinin Allah yana sonka, yadda yake tafiyar da lamuran rayuwarka. Ina yi maka
fatan alkhairi, Allah ya baku zaman lafiya mai ɗorewa"
Viper ya riƙe hannun Alhaji mu'azzam, amma ya kasa magana
sam.
Major ma zagayo wa yayi, ya dafa kafaɗar Viper, ya ce
"Yadda na samu labarin ka riƙe Jauhar amana, dan Allah ga 'yar uwatta nan
ma, Allah shi ya san dalilin da ya sanya ya karɓi jauhar a lokacin da ka ke
matsanancin son ta, ya musanya maka da 'yar uwatta, wataƙila da bai ɗauke
Jauhar ba, babu yadda za ayi Nabila ta ga mahaifinta, komai sila ne, kuma duk
abin da Allah ya yi dai-dai ne, ba a tambayarsa dan me? Allah ya baku zaman
lafiya"
Viper ya risunar da kai ya ce "In sha Allah Abba, na
gode sosai"
Abbu ma ƙarasowa yayi, ya ce "Al'amin, a karo na biyu
na sake nema maka auren 'ya, kuma Alhaji Bashir ya sake bamu, a rana mai kamar
irin ta yau aka ɗaura maka aure da jauhar, yau ba ta raye, an sake ɗaura maka
aure da Nabila, dan Allah Al'amin ka riƙe musu 'ya da mutunci da amana"
Kawai ya fara zubar da hawaye, duk da yayi iya ƙoƙarin sa
wurin mayar da hawayen, amma abu ya gagara, kawai ya lumshe idanunsa ya basu
damar su zuba.
Major ne ya ce "Ya haka kuma? Amare ke kuka ba angwaye
ba, dan Allah kar ka bayar da mazaje mana, soja ne fa kai".
Jiki a sanyaye Walid ya ce "Ai a duk lokacin da za ayi
wani abu da zai tuna masa da Jauhar duk taurin zuciyar sa da ƙarfin halinsa sai
ya yi kuka, haryanzu ya kasa jurewa, duk yadda za a bayar da labarin yadda suka
rayu, idan ba wanda ya gani ba ba zai gane ba"
Major ya ja shi ya bashi handkerchief ɗin sa, yana duddukan
kafaɗarsa yana rarrashinsa, Abbu ya ce "Al'amin dole fa ka yi haƙuri, kayi
haƙuri, duk lokacin da ka tuna Jauhar ka yi mata addu'a. Sannan dole ka koyi
danne zuciyarka, idan ba haka ba, zaka iya sanya wa Nabila kishin 'yar uwatta,
zuciya ba ta da ƙashi".
Kallonsu kawai yake yi, idan ya ce ba ya murna da farincikin
wannan auren, ƙarya yake yi, amma zuciyarsa ta tsinke, da yaga yana sake ɗaura
wani auren, Jauhar ɗin sa ba ta duniya, a lokacin da yake tare da ita, gani
yake duk wani leƙe-leƙe da ake faɗa na namiji a kan mace, itakaɗai ta ishe shi
rayuwa.
Suka kewaye shi suna ta rarrashin sa, abin da ya ƙara yi
masa daɗi da sanya shi farinciki, bai wuce yadda shi da ake ƙyama a da, amma
aka tara wannan mutanen saboda shi, kuma duk suka kewaye shi, kowa yana ƙoƙarin
rarashin sa, lallai babu abin da ya fi zama mutum na gari.
Alhaji mu'azzam ya ce "Ko sai mun dangana da wurin
amaryar za ta rarrashe shi? Dan naga tafi kowa iya shawo kansa"
Major ya ce "A'a bar amaryar nan, ka san ba ta san da
bikin ba sai jiya da sumayya ta sanar da daddare, can na baro ta a falo tana
kuka, fushi ma take da ni, ina ga ranar Litinin za a kawo mini sammaci daga
kotu, na taɓa masu ƙasa na yi wa barrister auren dole, amma na gaya mata ni da
kai zata kama, tun da tare muka yi laifin" yayi maganar yana nuna Alhaji
Bashir .
Suka yi dariya baki ɗaya. Duk da a ƙurarren lokaci Sumayya
ta sanar da ɗaurin auren Nabila, Auren ya samu hakarta ɗaruruwan jama'a, manya
da ƙananan mutane, mussaman waɗanda suke supporting ayyukanta, har da wakilai
daga gidan gwamnati, manyan lauyoyi da baristoci, har da kwamishinan shari'a,
da alƙalin alƙalai na jiha. Da yawa saura kwana biyu uku suka samu invitation ɗin,
kuma an halarta sosai da sosai.
Ba ƙaramin daɗ Major ya ji ba, ganin irin jama'ar da Nabila
ta tara, a ransa yayi mata addu'a Allah ya sa yadda ta riƙe gaskiya a kan
aikinta, da ta tara wannan jama'ar, Allah ya sa ranar mutuwarta ta tara fiye da
haka.
Shi kansa Babanta ya yi farinciki, mussman yadda ake ta
yabonta, da jinjinawa yadda ta zamo matashiyar yarinya, mara tsoro da jajircewa
a aiki.
Nabila kuwa har Abba ya tashi ya shiga bedroom ɗin sa, yayi
wankansa ya shirya tafiya ɗaurin aure, tana bayan kujera a zaune tana kuka.
Gaba ɗaya shi dariya ma take bashi, dan haryanzu kallon
yarinya ƙarama sosai yake yi wa Nabila.
Baba magajiya ta je tana rangaɗa mata guɗa a ka, amma tana
guɗa Nabila ranta na ƙara ɓaci, baba magajiya har da rawa, da yi mata waƙoƙin
amare irin na da.
Nabila ta koma ɗakinta, sai ga kiran Sumayya, ta ɗaga wayar,
Sumayya ta kwashe da dariya tana amarya ba kya laifi.
"Da ke aka haɗa baki aka yi mini haka ko Sumayya, ki je
kanki ki ka yi wa" Sumayya dariya har da tuntsurawa ta san a rina, rigima
da daru, za a sha su akan abin da aka yi wa Nabila.
****
Maman ramma kuwa ta tattara ramma da Abdul ta saka musu ido,
dan ta fara jin nauyin sa, irin yadda yake hidima da rammar, a da tayi zaton
ƙoƙarin sayeta yake son yi da abin duniya, amma sai taga ba haka ba, zunzurutun
soyayyar kawai yake yi wa ramman.
Yau daga wurin ɗaurin auren Viper, gidansu ramman ya wuce.
Tsayawa ramma tayi tana ƙare masa kallo ta ce "Ka ga
yadda ka yi kyau kuwa?"
"Daga wurin ɗaurin auren yayanki nake"
Ramma ta ce "Haka mama take gaya mini, ai shekaranjiya
babansa ya zo, ya daɗe a gidan nan suna hira da mama, yake gaya mata halin da
ake ciki, yau za a ɗaura musu aure, amma daga ita har shi ba wanda ya sani, na
ce ikon Allah kamar film"
"Wallahi rahama ya bani tausayi, kin san duk wannan
muzuran da yake yi, da shan ƙamshi, amma ya din ga kuka a wurin ɗaurin auren
nan, kamar yaro ƙarami, wai ashe wadda ta rasun ya tuna, wallahi sai da na yi
masa kuka, muktar ya ce mini duk yadda nake sonki, da nuna miki kulawa, ba zai
kai kwatantkwacin son da yake yi mata ba, da na tuna mahaifina ne sila, wallahi
sai na rasa in da zan saka raina. Ya ma yi ƙoƙari yake ɗan iya kula ni a 'yan
kwanakin nan, dan hau har gaisawa muka yi"
Ramma ta ce "Yaya zamu yi, ai ƙaddara ta rigayi fata
sai addu'a"
Sai da aka yi sati guda, sannan Alhaji mu'azzam tare da
hafsa suka ɗaga zuwa babban birnin tarayya Abuja.
Gidan Hafsat na Abuja mai kyawun gaske, ya fi wanda ta zauna
da ita da uwargidansa a can Kano, sai dai taƙi sakin jiki da shi.
Jirgin yamma suka bi, gefin magariba suka sauka.
Da ya ɗan matsa kusa da ita, sai ta maze ta matsa tana haɗe
rai, dan haka ya rabu da ita.
Da daddare da kyar ta yadda ta ci abinci, shi ma ba da yawa
ba.
Ya riƙo hannunta zata ƙwace, ya riƙe gam, ya ce "Haba
hafsatuna, ni ne fa, ki yi haƙuri dan Allah, ki bani dama na gyara kuskuren da
nayi miki a baya, Please" tayi shiru, ba ta ce masa komai ba, saboda ta
kasa manta mummunan halin da ta faɗa a wancan karon a dalilin aurensa.
Da kyar ya lallaɓata, kamar budurwar da ba ta san komai ba,
sai dai a wannan karon ita kanta ta san da banbanci, dan a wacan karon, banda
tsabar kayan tsubbu, da abubuwan da ba ta san ko na menene ba, da su aka yi
mata gyaran jikinta.
A wannan karon kuwa, ta san da banbanci, domin kuwa maman
dr. Ta kankarota ta kankaro martabarta a idon mijinta, dan a wancan karon ko
maganin sanyi ba ta yi amfani da shi ba, sai kayan tsubbu da abubuwan da ƙawaye
suka din ga ba ta shawara a kai.
Shi kansa yadda ya yi appreciating ɗin ta a wannan karon, ya
sha bamban da lokacin da tana budurwa.
(07069711327 ga masu buƙatar kayanta, su na iya tuntuɓarta
kai tsaye, she's always available for you)
*****
Viper kuwa kimanin sati biyu kenan, tun da Allah ya sa aka ɗaura
aurensa da Nabil, babu wanda ya nemi wani daga shi har ita, kuma hakan ya ɓatawa
kowannensu rai.
Abba ya sanar mata, da babu ita babu yawo, idan ba wurin
aiki ba, dole sai da izinin Al'amin.
Rashin kiranta da bai yi a waya ba, ya tabbatar mata da sam
ba ya ƙaunarta, auren dolen ne dai kawai, shi ma ya nemi ya aureta ne kawai
saboda mafitarsa.
Kasancewar hidimar bikinsa, tare da na Walid za a haɗa, ya
sanya yayi delay na komawa aiki, domin sanin shirye-shirye da yakamata yayi.
Yana son ya tambayeta, abin da take buƙata na harkar biki,
amma ya shareta.
Ta koma wurin aikinta, ana ta yi mata Allah ya sanya
alkhairi, aka din ga tambayarta meyasa ba ta tafi hutu ba, ta ce ɗaurin aure
aka yi, ba ayi biki ba.
Aka din ga bata gudunmuwar biki, ta in da ta zata, da in da
ba ta ma zata ba.
Kawai tana zaune a office taga alert ɗin dubu ɗari biyar, da
sunan Al'amin da komai.
Sai a lokacin ta kira wayarsa, ya ɗaga amma yayi shiru.
"Naga ka turo mini kuɗi"
"Ki fara sayen abin da ki ke buƙata na lefe, zan sake
turo wasu, na san wannan ba za su isa ba".
"Ni bana so" ta faɗa a daƙile.
"Menene ba kya son?"
"Kuɗin, ni ka bani account number na dawo maka da
su"
Wani malolon takaici ya ƙule masa zuciya ya ce "Bani da
lokacinki, ki same ni a gidan su rahama, sai ki dawo mini da kuɗin" ya
kashe wayarsa.
Ba tare da tunanin komai ba, ta miƙe ta fara harhaɗa
kayanta.
Da ta isa gidan su ramam, Maman ramma ta ce "Amarya ke
da kanki, ina ta cewa Aminun ya zo ya kai ni gidanku, amma haryanzu shiru"
Nabila ta ce "Dama baya nan? cewa fa yayi na zo na same
shi a nan"
"A'a ya dai ce zai zo, amma bai ƙaraso ba tukuna"
yanayin fuskar Nabila da ta gani babu fara'a, ya sanya ta din ga yi mata
nasiha, tayi haƙuri ta rungumi mijinta su zauna lafiya kamar yadda yar uwatta
tayi.
Ita kuwa Nabila gani take, ba zasu gane ba, ba su san waye
Al'amin bane.
Ita a tata wautar, da gaske zuwa ta yi ta mayar masa da kuɗinsa,
sam bai iya rarrashi ba, ba ta san tarko ya yi mata ba.
Awanta guda a gidan, ya zo, kuma yaƙi shigowa cikin falon,
ya ce ta je ta same shi a sitting room ɗin harabar gidan.
Ta tashi ta ce "Mama ina zuwa" ta fita ta ƙarasa ɗakin.
Sai dai tana arba da shi, duk wannan fitsarar da take ji da
ita, ta nemeta ta rasa, sai tsoro da fargaba da suka mamayeta. Lallai miji yafi
gaban wasa.
Ya ɗago ya kalleta, doguwar riga ce a jikinta, sai mayafin
rigar. Gaba ɗaya Nabila ba ta da wayo, ko kaɗan, abin da ba ta sani ba, ba wai
dawo masa da kuɗi ne ya kawota ba, son ganinsa ne ya kawo ta, ba tare da ta yi
lissafin hakan ba.
Ya kawar da kansa ya ci gaba da danna wayarsa.
"Ka bani account number ɗinka, na mayar maka da kuɗinka,
ni bana buƙatar komai daga wurnka, ba zaka taɓa iya bani abin da nake so
ba".
Ramma ta yi sallama da ƙaton faranti, shaƙe da kayan abinci,
ta gaida Al'amin ya amsa, ta kalli Nabila da ke tsaye ta haɗe rai, ba ta ce
komai ba ta fita.
Ta fara ƙosawa da tsayuwar da take yi, ya miƙa mata
hannunsa, ba tare da ya Kalle ta ba ya ce, "Bani wayarki na saka miki
account number ki dawo mini da kuɗina" babu musu ta ƙarasa ta miƙa wayar,
ya yi amfani da hakan, ya janyota jikinsa.
Wata ƙaramar ƙara ta saki, jikinta ya hau tsuma, ta kalli
fuskarsa, babu alamar wasa a tattare da shi, wani irin kallo yake yi mata da ba
ta san a yaya zata fassara shi ba.
Ayshercool
08081012143
So take ta motsa ta ƙwace daga jikinsa, amma ta gagara ga
kallon da yake yi mata, gaba ɗaya ya gama razanata.
"Ni zaki dawowa da kuɗina ko?" Tayi tsuru-tsuru ta
kasa magana.
"Yakamata ki san akwai banbanci yadda kike mu'amalanta
ta, a baya da kuma yanzu" ya ƙare mata kallo, babu tsammani ta ji ya
mirginata, ya danneta.
Baki ta buɗe zata yi ihu, sai kuma ta yi saurin yin shiru ta
ce "Dan girman Allah ka yi haƙuri, Viper meye haka?"
"Shekara ashirin da shida Nabila, kin ce ba kya son
aure, amma tsakanin ni da auren wanne ne ba kya so?"
Ta ɗan yi shiru ta ce "Kai"
"Ni ko?" Ya nanata mata yana kallonta, amma tayi
shiru tana ƙoƙarin yin kuka.
"Amma kina son auren?" Sai ta girgiza masa kai
a'a.
To bari na tantance, tsakanin ni da auren wanne ki ka fi
buƙata.
Ya ƙare mata kallo, ya kai hannunsa kan zip ɗin rigar
abayarta, mai ɗauke da ƙaramin zip a gaban rigar.
Hannunta bibbiyu ta riƙe hannunsa, tana girgiza masa kai,
cikin matsanancin tashin hankali da ruɗewa.
Amma sai da ya buɗe shi, farar fatarta ta bayyana.
"Saboda kin raina ni, baki ɗauki aurena da muhimmanci
ba, a haka ki ke yawo da aurena a kanki, daga ke sai wannan mayafin, kalli
kanki ko ɗan kwali babu. Yayi maganar yana ɗan jan dogon lallausan gashinta na
fulani.
"Dan girman Allah Viper, ka rufa mini asiri, ka san nan
gidan mutane ne, dan Allah ka yi haƙuri kar ka tozarta ni"
Ya ce "Ni na kawo ki?"
"A'a kai ka ce na zo, shi ne na zo"
"Ki ka zo domin ki yi mini rashin kunya, ki nuna mini
ban isa ba. Menene abin da ki ke so da ba zan iya baki shi ba?"
Cikin rauni ta ce "So da kulawa"
"Ban iya ba" yayi maganar yana tsare idanun ta da
nasa.
Sai kuma ya numfasa ya ce "Idan ki na son so da kulawa,
sai kin zama kamar Jauhar"
"I can't, ni ba Jauhar ba ce, Nabila ce ni, ba zan iya
zama kamarta ba, shiyasa na ce bana son auren nan.
Dan Allah Vi ka ɗaga ni, kayi mini nauyi numfashina zai ɗauke,
ka san ina da matsalar numfashi, ka yi mini rai ka yi haƙuri, kar ka tozarta ni
a gidan mutane, na daina duk abin da baka so dan Allah ka yi haƙuri ka ɗaga
ni" kuka take wiwi, kamar yayi mata wani abu, idanunta har sun fara ja,
fuskarta tayi pink, idan ba gizo idonsa yake yi masa ba har da majina a hancin
Nabila, gaba ɗaya ta firgice.
Sai da ya ji kamar yayi dariya ya fasa, ya ɗagata, ta tashi
a zabure zata bar wurin ya ce "Zauna" ba shiri ta zauna tana ta haki
tana share hawaye.
Ya miƙa mata wayarta ya ce "Rubuta mini abubuwan da ki
ke buƙata na biki, yanzu ki tura mini" hannunta na ta karɓa ta ce "Ba
na son komai" ya ɗaga kai ya kalleta ta ce "Wanda ka turo ya
isa"
"Ki rubuta abin da zaki buƙata ki turo mini"
Ta buɗe wayarta, ta rubuta masa 5K ta tura masa. Ya sake
kallonta, muddin ya biye wa halin Nabila, da zazzafan ciwon kai zai tafi.
Ya ɗan yi gyaran murya ya ce "Zuba mini abincin nan na
ci" kamar ta kurma ihu, ta matsa ta zuba masa, haɗaɗɗiyar shinkafa da miya
ce da salad.
Ta miƙa masa, ya ce "A baki matata take bani"
Duk wani halin takura, haka Viper ya yi mata shi, duk wannan
tsiwar da kankambar na Nabila, sai gashi ta nutusu.
Ya ci ya ƙoshi, ya tashi tsaye ya karɓe wayarta, ya shiga
ciki suka gaisa da maman ramma, ta ƙara yi masa Allah ya sanya alkhairi ya ce
"Mata bari na wuce, zan ajiyeta a gida"
"To shikenan Aminu, Ubangiji Allah ya sanya alkhairi
ayi ta haƙuri dai, ka san lamarinmu mata sai an haɗa da haƙuri, Allah ya baku
zaman lafiya, sai kuma Allah ya kaimu lokacin biki"
Ya ce "To shikenan na gode" ramma jin ya ce tare
za su tafi da Nabila, ya sanya ta tafi taje tayi mata sallama.
Ta tarar da Nabila ta yi kicin-kicin, ramma ta ce "Anty
Nabila ashe tafiya zaku yi, ki gaida gida, in sha Allah zan zo har gida na
gaishe ki, tun da dama, ciki ne yake hana ni fita, ina son mu yi magana"
Nabila ta ɓoye damuwarta, ta ce "To sai kin zo"
hargitsewar gashin Nabila, ya fallasa abin da ya faru, ramma zata yi magana
Viper ya ɗaga labule ya ce "Taso mu tafi"
Tana ta cika tana batsewa, ta ɗauki jakarta, ta na jan
mayafinta tana rufe gaban gashinta, ta fita ta wuce shi fuuu.
Ramma sai da tayi dariya, ta kwashe kayan ta kai cikin gida,
ta zauna babu daɗewa, Abdul ya kirata a waya ya ce mata ya zo.
Ɗakin da su Viper suka zauna, suma suka zauna, Abdul ya ce
"Ƙamshin turaren yayanki nake ji"
Ramma ta ce "Eh, zuwa yayi bai daɗe da tafiya ba da shi
da amaryar sa"
Abdul ya yi murmushi, ya ce "Rahama dama maganar
makaranta ne, kin ga da boarding na biya miki, amma yanzu ba zai yi ba, ga
lokaci yana ƙurewa, sonake kina yin arba'in kawai ki fara zuwa makaranta, amma
kin ga ba zai yiwu mu yanke hukunci ba dole sai mun gama magana, sai mu gaya wa
mama, amma ya ki ke gani?"
Ta numfasa ta ce "Ai bani da wani zaɓi, hakan ma yayi
Allah ya tabattar mana da alkhairi".
Ribbon ɗin da yake gefen kujerar ya ɗaukko, ya ce
"Wannan fa?"
Rahama ta ɗan yi shiru, ta ce "Kai, ina ga na yaya
Nabila ne, ta manta shi ya faɗi"
Ya juya ribbon ɗin ya ce "Dama ribbon yana faɗowa
ne?"
Tayi dariya ta ce "Ina zan sani, ina ga faɗa ma dai
suka yi, na ga ranta a ɓace"
Abdul ya jinjina kai ya ce "Kuma har da cire ribbon,
lallai if care is not taking, zata fara laulayi a waje kan a tare, ai da kin
sani kin bashi ribbon ɗin, ki ce masa gashi sun manta"
Ramma ta waro ido ta ce "Shi zan ma bawa ba ita ba, eh
lallai ka shirya ya tumurmusa ni kenan, wai wa ya ga na bashi ribbon ɗin nan na
faɗi haka, da hararar da zai yi mini kawai ta ishe ni fargaba da tashin
hankali.
Sukayi dariya, suka cigaba da hira.
Suka yi hira, zai tafi ramma ta ce "Mama ta ce tana son
ganinka"
"Allah ya sa ba laifi nayi mata ba"
Ta ce "Ban sani ba gaskiya, ba ta gaya mini ba"
Ya ce "To, Allah ya sa ba hana ni zuwa zata yi ba, ta
ce sintirina yayi yawa ba, muje in ji".
Jiki a sanyaye ya bi ramma zuwa wurin mama, suka gaisa yau
fuskarta ba laifi.
Bayan sun gaisa, ya fara yi mata maganar, processing ɗin
makarantar ramma da yake yi.
Mama ta ce "To dama nima na kira ka ne, domin jin ya
ake ciki? Maganar aurenku, idan kana sonta haryanzu, ka zo ka yi magana ta
tare, ka daina wannan sintirin haka, sai ta ci gaba da makarantar a can"
gaba ɗaya suka kalli mama.
Ba su taɓa zaton abin zai zo da sauƙi har haka ba.
Abdul ya ce "Mama, kin yarda Rahama ta tare a gidana,
kin janye na rabu da ita?" Yayi maganar yana kallon ramma yana sake kallon
mama.
Ta ce "Eh, ya na iya da ikon Allah, ka je ka yi shirin
tariyarta, ni dai ina fatan ka riƙe amana, kuma ka ji tsoron Allah" gwiwa
bibbiyu, a ƙasa ya din ga zuba godiya, yana yi wa maman addu'a. Hakan kuma ya
samo asali ne, daga zuwan Abbu, ya ɗan yi hira da ramma, kuma Viper ya yi masa
bayanin komai, ya din ga yi mata nasiha, da ankarar da ita, wataƙila na dan
iftila'in nan ba, da ba ta zo birni ta zauna ba. Ta kuma tausayawa halin da
yaran suke ciki su biyu, ta yafe wa Abdul ɗin.
****
Nabila kuwa da suka fita, da motar Abbu ta ganshi, ya ɗauke
ta a mota, ya nufi gida da ita, kamar kurame, suka yi jugum-jugum a motar,
Viper ne ma yake sauraren radio, Nabila kuma ta sha kunu.
Ya ja yayi parking ba tare da ya ce mata komai ba ya fita,
tana nan zaune ya dawo da ledoji a hannunsa, ya ci gaba da driving ɗin sa, har
gida ya kaita, zata buɗe motar ta fita ya ce "Ji mana" ta kalleshi.
"Ɗauki wannan ledar taki ce, kamar an yi mata dole, ba
ta san menene a ciki ba, ta ce "Na gode"
Ta tsaya ko da wani umarnin da zai bayar, ya zuba mata ido
wani abu yana fizgar zuciyarsa a kanta.
Ya ce "Zaki iya tafiya"
Ta buɗe motar ta fita, wanda hakan a kan idanun Nasir,
zuciyarsa kamar ta yi bindiga saboda baƙin ciki da matsanancin kishi.
Shiga gida tayi tana rarraba ido, kamar za a gane abin da ya
faru.
Ta ajiye ledar, mai ɗauke da gurasa da tsire fal a ciki.
"Dole ka bani cin hanci mana, bayan ka gama lalube ni,
ai dama dan abin da ka aure ni kenan" tayi maganar tana hararar kayan.
****
Amarya Hafsa kuwa nata zuba capacity a gidan Alhaji
mu'azzam, ko tari ta yi sai ya tambaye ta idan wani abu take buƙata.
Nabila suna waya da Hafsa, Hafsa ta ce "Amarya"
"Rabani da wata amarya, ke ce dai amaryar"
"Kema amaryar ce ai, ai ina sake jaddada miki, ki riƙe
likitar matar, malamar daidaita al'amuran gidan aure, maman dr. Kayanta babu
algus Nabila, ta gyara wa ango ke"
Cikin ƙosawa Nabila ta ce "Kin ishe ni wallahi da
maganar nan, an daɗe ba a gyara ɗin ba, idan na n tafi a haka ya koro ni"
"A'a A'uzubilalimatillahi bama fatan haka, ba zaki tafi
a haka ba, gyara zaki sha, ina kyautata zaton daga abin da ya yi mini illa a
aurena, amfani da magani cikin duhun kai, da rashin sanin abin da ya dace na yi
amfani da shi, kin san mace sai da gyara"
"Hafsa"
"Na'am"
"Dan girman Allah ki barni da abin da yake damuna"
Hafsa tayi dariya ta ce "Menene yake damun naki wai har
haka?"
Nabila ta ce "Ai ba zaki gane ba, bar ni kawai"
Hafsa ta yi dariya ta ce "To Allah ya kawo miki mafita, amma ko kin ƙi sai
an gyarawa mai zamani ke tas, ba zamu kai ki a haka ba"
"Saura mahadi ba mai zamani ba"
Bayan ta gama waya da Hafsa, Ramma ce ta kirata, take gaya
mata abin da mama ta ce, ta ce Abdul ya yi maganar tariyarsu.
Sannan ya yi mata zancen makaranta, sosai farinciki ya kama
Nabila, sai yanzu maman ramma ta yi abin da ya dace, domin kuwa da ta zuba ido,
ko da saninta ko babu saninta, za su ci gaba da haɗuwa ne ita da Abdul.
Suna gama maganar ta kira Hafsa take ce mata "Turo mini
lambar maman dr."
"Har kin canza shawara kenan?"
"A'a ni ba ni zan yi amfani da shi ba, turo mini kawai
a gyara mini 'yar ƙanwata"
Ɓangaren major yana ta shirin aurar da Nabila, Baba ma yana
ta tanadin abun da yakamata. Duk lokacin da ya tambayi Nabila menene shirinta a
kan bikin, me take buƙata, sai ta ce ita babu komai duk yadda aka yi shikenan.
Shi kansa Viper yana son tambayar Nabila, in da yakamata ta
zauna, saboda yanayin aikinta, zata bi shi Abuja ne, ko ta zauna a Kano, amma
sabgar gabanta kawai take yi, ba ta ko bi ta kansa, shi ma ya tattarata ya
watsar da ita.
****
Jami'an tsaro har gidan Naja'tu Bunkure suka je, amma cikin
rashin sa'a, ba ta nan tayi ɓatan dabo, an nemeta an rasa.
Sai dai an yi katarin samun miyagun ƙwayoyi a gidan nata,
ƙwayoyin ma irin na manyan kai, dan har da su hodar iblis a cikin.
A gidan har da irin allurar da tayi iƙirarin Viper ya yi wa
kansa ya kashe Jauhar.
Ga wasu irin maƙudan kuɗaɗe da aka samu a gidan, wasu in
naira wasu kuma dollars har ma da riyal na ƙasar Saudiyya.
Hakan ya ƙara sanya wa aka baza komar jami'an tsaro, a kan
lallai a kamota duk in da ta shiga.
Sumayya ce jagorar sanar da abin da ya faru, da Bunkure ta
aikata, dan hakan ne ya kan janyo hankulan al'umma, su bibiyi cases irin haka,
su ga wani mataki za a ɗauka, domin kuwa a program ɗin da suke yi da Nabila,
sun ƙara wayarwa da al'umma kai sosai da sosai a kan cewa, dokar ƙasa ba a kan
talaka kawai take aiki ba, everyone is equal before the law, duk Wanda aka
zalunta, ko da ba zai yi nasara ba, ya nemi hakkinsa, ba masu madafun iko ne a
ƙasar kawai suke da 'yancin walwala da jin daɗi ba kawai.
Gidan su Viper, duk wani wanda ta san zata haɗa Abbu da shi,
a kan ya fasa aura wa Shahida Walid, ta haɗa shi da shi, amma ya hau dokin
naƙi, ya ce babu gudu babu ja da baya. Duk yadda ita kanta Nabilan, tayi
ƙoƙarin nusar da ita, babu aibu a auren taƙi ganewa, muraran take nuna wa Walid
tsana da ƙiyayya, ga kuma ciwon hauka da wasu lokutan idan ya tashi, ta din ga
zunduma ihu kenan, tana kiran sunan Abba, da Nazifi, da kuma Amira da ba ma ta
san a in da take ba.
Wasu lokutan kuma ta din ga ƙwala wa Zahra'u kira,
mahaifiyar Viper tana koke-koke.
Abdul yanzu da Alhaji mu'zzam yake shawara, ko Viper, dan
Viper ya ɗan saki jiki da shi, ya daina harararsa, gidan da ya kai ramma na
ƙarshe, da can ya ce zai canzawa furnitures, amma Alhaji mu'azzam ya ce yayi
wajen gari da yawa, ya nema mata wani, kuma ya bari su yi wa ramma kayan ɗaki.
Abdul ya ce "Haba dai, da kayan lefen rahama, da kayan ɗakinta
duk zan yi mata, ni duk abin da zan yi mata na kyautatawa ba ya sanya wa na
daina jin nauyin laifin da nayi mata, yana rinjayata, dan haka dan Allah ku bar
ni na yi mata abin da ya kamata".
Shikaɗai yake shirinsa, sai Saifu da Salim, dama su ne
abokan cin mushensa.
Indabo ya kaɗu matuƙa gaya, da jin irin neman da ake yi wa
Bunkure, da kuma kayan laifin da aka kama a gidanta, gashi ko ta wani ɓangare
yaran nan sun ƙi taɓuwa, daga Sumayya har Nabila, kankarofi ya yi masa sarƙa da
duk lokacin da zai yi wani yinƙuri ko motsi a kan su, sai sarƙar ta ƙara shaƙe
shi.
Gefe guda Alhaji mu'azzam, yana ta ci gaba da yaɗa
manufarsa, ta son tsayawa takara, kuma ya samu goyon bayan al'umma sosai da
sosai, mussaman matasa, domin kuwa su ya ɗiba sosai da sosai a tafiyar tasa.
Lokacin biki na ta ƙaratowa, babu wata jituwa da fahimtar
juna a tsakaninsu, babu wanda yake neman wani, shirye-shiryen biki ma, sai dai
ya tambayi Sumayya, ba ya son ya yi wani abu da zai gaza, yana son ya yi wa
Nabila duk abin da ya dace na aure, amma baƙin taurin kai da babu gaira babu
dalili ya hanata ta nutsu da shi.
Nabila kuwa ta riga ta sare ne, gani take yi kawai Viper zai
aureta ne ya zauna da ita, saboda tana kama da Jauhar, dan haka gani take ba
zata taɓa burge shi ba.
Ranta ba ƙaramin ɓaci yake yi ba, idan ta tuna da ta taɓa
sauke kunyarta da ajinta na ɗiya mace, ta nuna masa soyayya, amma ya watsa mata
ƙasa a ido.
Sallamar Sumayya ce ta dawo da Nabila hayyacinta, ta nemi
wuri ta zauna.
Nabila ta amsa mata ta ce "Ke ce a tafe Sumy"
"Eh ni ce, halinki ne ya ishe ni"
"Wanne daga ciki?"
Sumayya ta ce "Kowanne ma. Ɗazu muka yi magana da
Viper, yake mini maganar idan da wani event da zaki yi, hakan ya ƙara tabattar
mini da cewa kina nan kina yin wannan baƙin halin naki. Nabila wannan fa kamar
iyayenmu ki ke watsawa ƙasa a ido fa.
An riga an ɗaura auren nan, duk wani bori kamata yayi ki
ajiye shi a gefe, amma ace shi ne yake ta fafutukar shirin bikin, an kusa yin
tariya amma ko gyaran jiki kin ƙi ki fara, wannan fa kamar ƙoƙarin bijirewa su
Abba ne"
Nabila ta gyara zamanta, ta kalli Sumayya ta ce
"Sumayya, kowa ya kasa fahimta ta, kallon mara kirki kawai ake yi mini,
shi meyasa ba a ganin laifinsa ne?
Kin san halin ko in kular da yake nuna mini ne ma? Baya so
na, ya ce dole na zama irin jauhar, idan ina son na rayu da shi cikin daɗin
rai, ni kuma ba zan taɓa iya zama Jauhar ba, meysa ba zai rayu da ni a matsayin
Nabilata ba?
Beside gaba ɗaya ba na gabansa, ba ya so na, tayaya zan yi
zaman aure da mutumin da shi ya fara cewa ba ya so na"
"Ke kuma kin yarda baya son naki? Meysa zai nemi ya
aureki alhalin baya sonki, kawai wannan wani abu ki ke yi, na salon ramuwar
gayayya kawai, amma kin san Viper yana sonki. Kawai mutum ne miskili, kuma murɗaɗɗe,
amma ko ba duka ba, ki jarraba wasu daga halayen Jauhar mana.
Ki lallaɓa shi, ki bi shi a sannu komai zai zama
normal".
"Ni ba na buƙatar rarrashin da kulawa ne Sumy, sai dai
in ta bin sa, saboda ga bita zai-zai. Wallahi sai dai a shekara a haka"
"Ke kut..." Sumayya ta ɗura mata ashariya.
"Bakomai na ji na gode, ko zan yi koyi da Jauhar, nima
ya koyi zama da ni a Nabila"
Sumayya ta sake sassauta murya ta ce "Ki yi haƙuri
Ablan Vi, namijin kenan ai, sannan tausasawarki macen kenan, wai kar ki manta
ke fa ki ka iya gwagwarmayar yawo a cikin jeji, da sake ƙoƙarin saito akalar
rayuwarsa zuwa dai-dai, sai wani zaman aure da shi ne zai baki wahala?
Mutumin da ya saka miki kaifi, amma ki ka kafe, ki ka yi
galaba a kansa, shi ki ke fargabar zama da shi, haba tawan"
Nabila ta ce "Sumy, kar ki saka na saukko, na sake
zubar da kaina mana"
"Ba haka ba ne Arfa, idan ma kin zubar da ajin wa ya
san an yi, mijinki ne fa.
Ya kirani ya tambaye ni me ake buƙata, zai tura miki kuɗi,
ayi maganar gyaran jiki dan Allah abla ki yi haƙuri, ki kwantar da hankalinki.
Yanzu ki kira shi ku yi magana dan Allah"
Nabila ta girgiza kai ta ce "Na san gayen nan kamar
yadda na san yunwar cikina, tsaf zai yarfa ni"
"Ba zai yarfa ki ba, kira shi ki kashe masa murya dan
Allah"
Ta lallaɓa Nabila, ta kira wayar Viper.
Sai dai yana tsaka da aiki, wayar ma ba ta tare da shi, dan
haka bai san ta kira ba.
Nabila kuwa ta din ga mita, ta ce Sumayya ta saka ta zubar
da class ɗin ta.
Ta dai lallaɓa Nabila, a kan ta amince a fara gyaran jiki.
Sai dai ta ƙule sosai da yadda ya ƙi ɗaga wayarta.
Viper bai samu kansa ba, sai daf da magariba, salla ce kawai
take tashinsa daga aiki.
Ya gama aiki, aka tura shi wani wuri aiki, dan haka sai a
lokacin ya ga missed call ɗin Nabila, sai da mamaki ya kama shi, bai kirata ba,
sai da yaje gida.
Ya zauna ya nutsu, sannan ya kirata, ta zubawa wayar ido,
kamar kar ta ɗaga, kuma ta san idan ba ta ɗaga ba, abu ne mai wahala, yayi na
biyu.
Sai da ta kusa katsewa, sannan ta ɗaga.
"Da ba ki yi niyyar ɗagawa ba kenan?"
"Ai nima sai biyu ina kiranka ba ka ɗaga ba, na ji yaya
aka yi?" Wani irin takaici ne ya kamata, wai yaya aka yi, kawai ta ce masa
babu komai.
Ya ce "Ok" ya kashe wayarsa, ba kuma dan ya so yin
hakan ba, yana matuƙar kewar hirarta, amma ya fuskanci akwai aiki ja a gabansa.
Mummyn Abdul ta fusata da jin cewa, wai Ramma zata tare,
yadda Abdul ya ga take-taken mummynsa da na Indabo, sai ya tsorata, duk da irin
son da yake yi mata, ya haƙura ya yanke shawarar ya kaita boarding ƙura ta lafa
tukuna, ko kuma ta fara makaranta a wurin mama.
****
Nabila sai gata take gani ko ta ko ina, kowa kawo gudunmuwa
yake yi, gadonta ma biyu ne, Abba yayi mata, Baba ma yayi mata, sai ƙoƙarin yi
mata kaya suke yi na alfarma.
An samu dai ana ta gyaran jiki, maman dr. Sai tsatso Nabila
take yi, sai dai Nabila sam baya gabanta kawai dai tana yi ne.
Sai dai bikin da tariyar na gabatowa, Nabila fargaba na ƙara
kamata, domin gaba ɗaya tsoron auren take ji.
Viper ya ce shi ba ya son harkar partyn nan, sai dai ita
idan za ta yi shikenan.
Sumayya ta tambayeta, amma Nabila ta ce ba za ta yi komai
ba, Sumayya ta ce ba ta isa ba, ba zata hana su shagali a bikinta ba.
Ga shirin bikin su Walid, ga na su.
Ramma kuwa Abdul ya cewa Alhaji mu'azzam, ya nemi mama ta
bari ramma ta fara makaranta a gida, daga baya ayi tariyar, saboda yana tsoron
abin da ka iya biyo baya.
Nabila babu wani da yake tsyae a kanta, yake yi mata playing
role ɗin uwa yadda yakamata, baba magajiya ta zama dattijuwa, mutan gidansu
kuma ba wani shiri suke yi ba, dama dai Anty ce, ita ma dai ba wani shaƙuwa ce
sosai a tsakanin su ba.
Babu mai wani rarrashinta, da nuna mata ƙabali da ba'adin
auren, Madam halima kayan kitchen ta saya wa Nabila, kaya na gani na faɗa masu
kyan gaske, ta zo har gida ta kawo mata.
Umman sumayya ce ma ta yi ƙoƙarin rarashin Nabila, da yi
mata nasiha a kan rayuwar aure. Ita ma tana ta faɗi tashin hidimar bikin
Nabila.
Viper yana gidansa da zai zauna, gida ya ɗauki kyau, ana ta
gyare-gyare.
Sumayya ta kira shi a waya, ya ɗaga suka gaisa ta ce
"Kana gari ne?"
Ya ce "Eh"
"Dan Allah ko zaka taimaka ka zo ka duba Nabila, tana
Asibiti babu lafiya, an kwantar da ita".
"Asibiti kuma, meya sameta haka?"
"Wallahi 'yan kwanakin nan duk ta saka damuwar auren
nan a ranta ne, baba magajiya ta ce dai kuka tayi, sai zazzaɓi sai kuma
numfashi yake ɗaukewa"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Wane asibitin ne?"
"In da take ganin likita ne dai"
Ya ce "Shikenan, na gode sosai"
Ya ajiye wayar yana tunanin, duk wannan abun saboda ƙiyayyar
da take yi masa ne har da rashin lafiya, dama so yana komawa ƙiyayya?
Walid ya ce "Ango ya ne?"
"Nabila ce a asibiti babu lafiya, duk saboda ƙiyayyar
da take yi mini"
Liti ya ce "Ƙiyayya kuma?"
"Ƙiyayya mana, me zan kira shi idan ba ƙiyayya ba, me
na yi wa Nabila har haka ne?"
Walid ya ce "Viper, mu gaya wa kanmu gaskiya, magana ta
domin Allah kai ka fara ɓata lamarin nan, ko ba ka san mutum, bai kamata ka
gaya masa ba, amma kalli abubuwan da ka din ga yi mata na wulaƙanci dan ta ce
tana sonka, shi ma wannan ɗan abin kazar uban, ya din ga rura wutar, aka din ga
hantarata, kuma a lokacin duk ba ta yi fushi ba, ta din ga bibiyarka.
Ka rasa Jauhar, kuma Nabila
ba zata taɓa zama jauhar ba, amma su na da wasu halayen in common, da na
Jauhar kai tsaye a bayyane suke, Nabila kuma wasu halayen nata kamar irin naka
ne, ka gyara ɓarnar da ka yi"
Liti ya ce "Ban san abubuwa za su juye haka ba, har ga
Allah da na tsaneta, amma daga baya gaskiya ita ma tana da kirki, ba dan haka
ba, abubuwan da muka din ga yi mata, da tuni ta watsar da mu"
Viper dai bai sake cewa komai ba, ya fita, suka biyo bayansa
domin su tafi Asibitin tare.
A ɗakin da Sumayya ta gaya masa an kwantar da Nabila suka
ƙarasa.
Baba Magajiya na zaune, Na lallaɓa Nabila ta sha magani,
amma taƙi idanunta jawur saboda kuka.
Walida ma na ta rarrashinta,
su Viper suka yi sallama suka amsa musu.
Baba Magajiya ta ce "Ango sannunku da zuwa"
Suka gaisa da ita, Walida ma gaishe su tayi, ta tashi ta
fita.
Liti ya bita da kallo, ya ce "Walid zo muje waje"
"Mu yi me?"
"Ka taso mana mutumina" ya ja Walid suka fita.
Baba Magajiya ma fita tayi ta basu wuri, ya tsaya kawai yana
kallonta, ita kuma ta sunkuyar da kai taƙi ɗagowa.
Ya zauna a gefen gadon yana ci gaba da kallonta.
"Menene matsalar ki ne?"
A hankali ya sake cewa "Yanzu duk ƙiyayyar da ki ke yi
mini ɗin ce ta kai haka? Ko fir'auna ne ni, ƙarshen abin da zaki yi kenan,
wannan sai ki saka iyaynmu su karaya su zata ko azzalumi ne ni.
Ko ba komai yakamata ki kyautata mini zato, amma shikenan
Allah ya baki lafiya, ya saka kaffara, amma yakamata ki bani chance kafin ki yi
judging ɗina"
Tayi murmushi mai ciwo ta ce "Wani chance kuma Vi, bani
da gurbi a zuciyarka, ba kuma zan taɓa yi ba, ka gaya mini fa, na riga na sani,
Jauhar ce kawai a zuciyarka"
Ƙura mata ido yayi, cikin mamaki ya ce "Nabila, kishi
ki ke yi da Jauhar?"
"Koma menene ai kai ne ka janyo, ina matuƙar ƙaunar yar
uwata, duk da ban santa ba, ban taɓa ganinta ba, amma kai da kanka zaka koya
mini kishi da ita, Jauhar kawai ka ke so"
A nutse ya ce "Ke ma ki koyi zama da ni, zaki samu
matsayi mai girman gaske a zuciyata"
"Babu buƙata, saboda ba Jauhar ce ta nemi soyayyarka
ba, dama can kana sonta, ni kuwa fa? Muddin aka ci gaba da tafiya a haka, to
tabbas zan fara kishi da ita. Idan kuwa na yi kishi da jauhar nayi asara, 'yar
uwata da ban taɓa gani ba, na shiga gidan da ta gina ta bari, kuma ina kishi da
ita, ban yi wa kaina adalci ba, ban yi wa kaina ba, muddin na fara kishi da
jauhar, kuma alamu sun nuna mini haka ne zai faru, muddin na aureka, shiyasa
tuni na yanke shawarar fasa aurenka.
Yau nayi kukan maraicin uwa da rashin yar uwata da ban sani
ba, gashi kuma zan shiga gidan da ta mutu ta bari, in rayu da mijin da ta gama
wahala da shi, kuma ya tabattar mini da cewa babu gurbin wata mace a zuciyarsa,
meyasa babu wanda yake irin tunanin da nake yi ne" magana take yi iya
gaskiyar ta tana kuka, mai haɗe da sheshsheƙa.
"Sati uku rak ya rage ki tare a gidana, ina roƙonki, ki
bani dama. Ba zan iya daina maganar jauhar ba, sannan na fuskanci kuskuren da
nayi, ki bani dama na gyara"
"Ka makara, kawai dai zan karɓi ƙaddara ne, dan tun
lokacin da ka ce baka so na, na kuma tabattar da jauhar yar uwata ce, nake
addu'a babu dare babu rana, Allah ya cire mini sonka daga raina, ya nesanta ni
da kai"
Rungomota yayi jikinsa, yana kallon idanunta, domin ya
tabattar da idan da gaske take, ta daina son sa.
Ya shafa gefen wuyanta, jikinta zafi saboda zazzaɓi, ga wani
ƙamshi mai sanya zuciya nutsuwa na tashi daga jikinta.
Ƙoƙarin ja baya ta fara yi, ganin yana kusanto da fuskarsa
ga tata.
Ayshercool
08081012143
Sake ƙasa yayi da muryarsa, ya ce "Ina sake roƙonki, ki
bani dama, kin yi mini kuskuren fahimta ne kawai, ban san yaya zan yi miki
bayani ba, amma za ki ga komai a aikace"
Bakinta ta motsa za ta yi magana, amma a dole ta haɗiye
maganar, biyo bayan dogon harshensa da ya saka a kan laɓɓanta.
Bayan su Walid sun fita, ya kalli liti ya ce "Ina
jinka, me zaka ce mini?"
"Wai wannan farar yarinyar yar uwar Nabilan ce
ne?"
"Eh"
"To kuma har muka fito ba ka yi mata magana ba, ka san
dai ka fini faraa'a da kalar masu kirki"
"In yi mata magana in ce mata me? Ko dai sonta ka ke yi
ne?"
"To wa ya san mini ma, amma ɗan yi mata magana, gata
can sai waya take yi "
Walid ya ce "In yi mata magana in ce mata uban me? Kai
ka yi mata mana, tun da sonta ka ke yi. Babanta dai tsohon soja ne, wallahi
kayi masa shirme sanyawa zai yi kuratan nan, su yi maka dukan jaraba na gaya
maka"
Liti ya ce "Ta Allah ba taka ba, kuma a yanzu zan nuna
maka banbancina da kai" kawai ya nufi in da Walida take waya, tana ta
surutu da wata ƙawarta mai kwaliya, tana son tayi booking na bikin Nabila.
Ta kammala ta juyo, ta ga Liti a tsaye.
"Sannu dai"
Ta ce "Yauwwa, ya gida ya shirye-shirye na ganku tare
da wanda Arfa zata aura, ina kyautata zaton abokansa ne"
Ya girgiza mata kai ya ce "'yan uwansa ne mu"
Tayi murmushi ta ce "Masha Allah, Ubangiji Allah ya sa
zamu gani"
"Amin, ashe tana da ƙanwa babba kamar ke, ai mu ita
kawai muka sani"
"Ai muna da yawa ma, ba a fiye ganinmu bane, daga
makaranta sai gida".
Liti ya ce "Masha Allah, ai haka ake so, ki ce tare
zamu yi hada-hadar biki, to Allah ya sa a gama lafiya, sunana Abdallah"
Ta jinjina kai ta ce "To yaya Abdallah, sunana maryam
ana ce mini Walida"
Walid kuwa satar kallonsu yake yi, yadda liti ya nutsu yake
baza capacity a gaban budurwa, kai ba zaka ce shi ne yake wani iya shegen ba,
sai gashi yana ta hira da shi da walida, abin da haryanzu Walid ba ya iya sakin
jiki yayi sosai da Shahida.
Duk da Nabila ba ta saki jiki gaba ɗaya da Viper ba, amma ta
ɗan ji sauƙin damuwar da take ciki, amma har a lokacin faragaba ba ta bar
zuciyarta ba.
Sai da ta kwana biyu aka sallameta, ta ɗauki hutu a wurin
aiki, ta ma daina fita gaba ɗaya, sosai Nabila ta zama so silent, dan ma
Sumayya na tare da ita, tana ƙarfafa mata gwiwa.
Abbu suna ta shirye-shirye, suna zaune da shi da Viper da
daddare, Shahida ma an gama gyara gidan da zata zauna, Abbu ya yi mata sababbin
furnitures. A weekend za a kawo kayan lefe.
Viper ya dubi Abbu, yadda yake ta kashe kuɗi babu
ƙaƙƙautawa, dan haka yake cewa auren yara uku zai yi.
Ga Viper, ga Walid ga kuma Shahida.
"Abbu muna ta godiya Allah ya saka da alkhairi"
Abbu ya ce "Da aka yi me?"
"Kuɗin da ka ke ta kashewa a kanmu"
"Amfanin neman kenan ai Al'amin, kuma a baya ai ban yi
muku ba, Allah dai ya sanya alkhairi"
Viper ya amsa da Amin, sannan ya ce "Abbu wata alfarma
nake son sake nema a wurinka dan Allah"
Abbu har so yake Viper ya nuna yana son yayi masa wani abu,
hakan na sanya mishi nustuwa, ya ji cewa lallai ya yafe masa.
"Ka ga ramma yar uwata ce, kusan ita da mahaifiyarta
sukaɗai suka rage a ɓangaren mahaifiyata, da nake kallo ina jin daɗi. To naga
ba tsufa tayi ba, kuma zamanta haka is not safe, na ce dan Allah idan da dama,
ban takura maka ba, dan Allah ka aureta.
Hakan zai fi sama mata nutsuwa, tun da shi aure garkuwa ne
ga mace, duk tsufanta kuwa.
Abbu ya shafi gemunsa yayi murmushi ya ce "Yanzu dai ka
bari na fara kawar da ku tukuna, ayi wannan maganar"
"Eh ai dama ba yanzu ba, na san da hidindimu a gabanka,
idan Allah ya sa komai ya daidaita nake nufi"
"To ɗan gidan Abbu, Allah ya tabbatar mana da
alkhairi"
Al'amin ya ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya ƙara
arziki"
Saura sati ɗaya biki, Viper ya aiko su Walid wurin Nabila,
suka yi sa'a Walida ta dawo daga aike.
Suka gaisa da su Walid, Liti ya ce "Walida, wurin
sisternki muka zo an aiko mu, ko zaki yi magana da ita"
"Me zai hana" mintuna goma, sai ga Nabila ta fito,
amma yanayin da suka ga Nabila, duk sai jikinsu ya sake yin sanyi, babu wannan
karsashin nata, jikinta duk a sanyaye.
Haka suka gaisa sama-sama, suka ce Viper ne ya aiko su da
kaya su kawo mata.
Ruwa da lemo ne carton hamsin, ga buhun fulawa har da kuɗi,
wai ta ƙara a abin da za ta yi hidimar biki da shi.
Tun da yaje dubata a asibiti, bai sake nemanta ba, ita ma
kuma ba ta neme shi ba, ta so kiransa a waya, amma ta fasa ta jira Abba ya dawo
ta nuna masa.
Faɗa ya hau yi, a kan yadda yake ta ɗawainiya da ɗorawa
kansa nauyi, ya kira Abbu yana mita Abbu ya ce "Haba ranka ya daɗe, ni ban
ma san an yi ba, kuma abu ne da yakamata ya yi, dan haka ai babu laifi, amma
ayi haƙuri idan mun yi laifi"
Major ya ce "Ai an riga an zama ɗaya, a din ga
sauƙaƙawa juna, wallahi mun tanadi komai na shirin bikin nan, bayan uban kuɗi
da ya din ga turo mata na haɗa kayan lefe"
Abbu ya ce "Kar ka damu fa, auren fari sadaka aka bashi
ai, sisinsa ba ta yi ciwon kai ba, wannan kuwa ya daki jikinsa yayi, sai ya fi
riƙewa da kyau"
Major ya ce "Aishikenan, Ubangiji Allah ya sanya musu
albarka baki ɗaya"
Saura sati biyu biki, Abbu ya kai Major da Baba gidan
Nabila, flat ne mai kyawun gaske, a cikin unguwar jambulon da ke Kano.
Tun duniya na kwance, lokacin da baban su Viper ya fara
tashen kuɗi, mahaifiyar su ta sanya ya saya wa Al'amin da Sadik gidaje, ta ce
saboda maza ne, idan ya sai musu ya taimake su.
A haka kuma da ɗan abin da take samu a hannunsa, da yan
sana'oin ta, ta din ga sayen filaye tana ɗan ajiyewa.
Aka zo ita ta rasu, Sadik ma ya rasu, dan haka Al'amin bayan
gidan da yake da shi, da babu yadda ba ayi da Abbu ya sayar ba yaƙi, Rahila ma
tayi ƙulafucin gidan ta gaji.
Miliyoyi aka din ga ambatawa gidan ya sayar yaƙi, yanzu
gashi ya yi rana, aƙalla Viper yana da gidaje huɗu, da manyan filaye biyu, dan
ma ya bi gonar da yake da ita a ƙauye, ya saka an sayar tun Jauhar na raye.
A auren nan Viper ba ƙaramin jin jiki yayi ba, duk da Abbu
yana taimaka masa, amma kuɗaɗen hannunsa duk sun ƙare, a haka sai da aka sayar
da filinsa ɗaya, saboda shi yake taimakawa Walid ma.
A duk lokacin da ya tuna a yadda ya auri Jauhar, da a
al'adance zai iya cewa auren sadaka, sai ya ji tausayinta, ko da wasa ba ta taɓa
nuna masa, ta ji zafin irin auren da aka yi mata da shi ba.
Liti duk da yana supporting ɗin Walid shi ma a kan shirin
bikinsa, gefe guda yana ta karɓar kuɗi a hannun babansa, ya ƙara ƙawata wurin
shayinsu aka mayar da shi joint.
Kasancewar Viper ya kwana biyu bai je wurin ba, ranar da
Liti ya addabe shi ya je, sai da ya zubar da ƙwalla.
JAUHAR MEMORIAL JOINT. Haka aka rubuta a wurin, sannan ga
kan famfo ɗaya da aka janyo, liti ya ce "Ga sadaƙatul jariya, mun yi wa
ƙanwarmu da ni da Walid, alkhairin Allah ya isketa har cikin kabarinta, ƙoƙarin
inganta rayuwarka da tayi, ba kai kaɗai ta yi wa ba, har da mu".
Cikin wurin duk an rubuta, dan Allah ku karanta wa
marigayiyya Jauhar ƙulhuwallahu ƙafa uku, Allah ya jiƙanta da sauran musulmi
baki ɗaya.
Idan Viper ya ce yana da kalamai, ko wani abu da zai yi,
domin nu na godiyarsa ga bayin Allan nan da suka kasance da shi, a halin
tsanani da na jin daɗi, to ya yi ƙarya.
Su Abba sun yaba gidan Nabila ba kaɗan ba, manyan ɗakunta
uku, da falo biyu, ga komai a wadace dai-dai misali.
Duk da ba a rasa 'yan tsegumi ba, da aka je jere, da suka
din ga gulmar, a iyayi irin na Nabila, da yadda ta din ga dating manyan mutane
masu kuɗi, ba su yi zaton zata ƙare a wannan gidan ba, duk da shi kansa yadda
ake cewa ɗan daba ne, sun zata mara galihu ne da abin yi, dan sun raina kansu
da suka ga gidan da ɗan daba zai saka amarya a ciki.
Nabila dai ta kama wuridin ya haiyyu ya ƙaiyyum bi rahmatika
astagis, aslih lii sha'ani kullahu, wala takilni ila nafsi, ɗarfatu ainin.
Domin samun mafita a kan maganar aurenta da Viper.
*****
Rana ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, aka fara
gudanar da biki, shi kansa Viper yayi rama saboda rashin hutu. Dinner da kamu,
duk amare ne suka je ba angwaye, Nabila ta yi kyau sosai, farar fatarta tayi
kyau da kaya da kuma kwalliyar da aka yi mata, haka ma Shahida ta sha kyau.
Sumayya ma sai kai wa da komowa take yi, tayi kyau sosai da
sosai.
A hada-hadar kai komon biki, liti suka ƙara sabawa da
walida, har da karɓar lambarta.
Walid ya ce "Zaka gane kurenka, ka gama yi wa Nabila
rashin mutunci, ka zo kana bin ƙanwarta, Allah ya kawo mata lokacin
ramawa"
"Kai dai ɗan baƙin ciki ne, saboda Allah ya kawo maka
lokacin aure, duk sai ku tafi ku bar ni, to baka isa ba".
An ci an sha, an yi biki lafiya aka kammala lafiya, da yamma
aka fara shirin kai amare.
Nabila na ta kuka, ba kuma wai dan zata bar gidan nan ba,
kawai ji take auren Vipern tsoro yake bata ba na wasa ba.
Abbu ya yi wa Viper da walid nasiha sosai da sosai, haka
Shahida ya gargaɗeta a kan kar ta biye wa mahaifiyarta, ta ɗorata a kan keken ɓera,
ta kashe mata aure.
Ranar da aka ɗaura auren su Walid, a ranar Viper ya yi
walimarsa, tare da abokansa, wanda dama su Walid ne, sai kuma sojoji.
Amma ba a manta baya a harkar, dan hatta tsofaffin yaransa
'yan cau-cau, da marasa ji sai da suka halatta, sai dai a wannan karon, ba
rashin hankali aka yi ba, kamar yadda na auren jauhar ya gudana ba, kowa
taitayinsa ya shiga, mussaman da sojoji suka cika wurin.
Nabila ta rirriƙe sumayya tana kuka, ita ta zauna da Nabila,
har bayan isha'i, kowa ya watse, ta kira wands zata aura, Faruk wanda ɗan uwa
ne ga Alhaji mu'azzam.
Amma fafur Nabila ta hanata tafiya, sai da Viper ya shigo.
Kamar yadda ya saba komai nasa daban, shikaɗai ya shiga
gidan, sai da Sumayya ta tafi ya rufe gidan, ya tsaya yana ƙarewa gidan kallo,
ko ina hasken fitilar solar.
Ya tuna lokacin da ya je wa jauhar, butsu butsu, Walid ne ma
ya takura masa, ya haɗo shi da kayan dauɗarsa ya rako shi. Ɗan guntun murmushi
ya yi, ya shiga ya iske Nabila a bedroom, ta ƙunshe kanta da mayafi.
Ya ce "Ki taso ki yi alwala mu yi salla" a hankali
ta motsa, ta saukko daga kan gadon, idanunta duk a kumbure, rabon da ya ganta
tun a asibiti, ko ta waya ba su sake magana ba.
Ta je ta fara yin alwala, shi ma yayi ya fito, amma ya ga ta
ja ta tsaya a gefe.
Sai da ya raɓata ya tayar da sallar sannan ta bi bayansa,
bayan sun idar yayi addu'a gwargwadon abin da ya iya.
Ya janyo mata ledojin da ya shigo da su, ya ce
"Bismillah ga abinci, me zaki ci a nan?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba komai"
"Saboda me?" "Na ci abinci a gida"
Kawai ya ce "Ok"
Da ya motsa sai ta zabura, gaba ɗaya ta takura kanta, ta
hana kanta sukuni.
Ya tashi ya bar mata ɗakin, sai bayan awa guda, sannan ya
koma, ta kwanta a ƙasa ta lulluɓe jikinta da lafayarta, sai dai tana jin
motsinsa ta sake zabura ta tashi zaune.
"Ki je ki kwanta, tun da bacci ki ke ji" sai da ta
ɗan yi jimm, sannan ta tashi taje ta kwanta.
Ya ɗaukko sabon bargonta ya ƙara mata, tana kallonshi yana
rage kayan jikinsa, zuciyarta na tsananta bugawa tana rarraba ido, yana juyowa
suka haɗa ido, tayi wuf ta shige cikin bargo.
Yana kashe fitila, ta tashi zaune, yana kallonta, ya zo ya
samu wuri a farkon gadon ya kwanta, amma taƙi kwanciya.
A ransa ya jinjina hali irin na Nabila, ya san dai ba ta isa
hana shi abin da yayi niyya ba, amma tabbas zai sha fama da taurin kai. A
yanayi irin na Nabila, da ta rayu cikin ƙabilu, har ta bar Nigeria ta je tayi
karatu, da yadda take gudanar da rayuwarta, sai ka zata a waye take, koma mutum
yayi mata kallon mutuniyar banza, amma zunzurutun tsoro da tashin hankalin da
yake tattare da ita, ko taɓata yayi sai ta kusa tara masa jama'a, abin da ba ta
sani ba shi ne, zai iya shanye koma me yake ji ya rabu da ita. Kamar dai a
zamansa da jauhar, da sai da ya fara gani a idonta, duk da shi akwai sabo sosai
da sosai a tsakanin sa da ita.
Ta sauran hasken da yake shigo ɗakin yake kallon yadda take
gyangyaɗi a zaune, har ta gaji ta tuntsura, amma da ya juya sai ta tashi.
Gidan ango Walid kuwa, halin ya ci gaba da gwadawa, shi ba
tsoro ba, shi ba matsananciyar kunya ba.
Bayan sun yi salla sun idar, ya gabatar mata da kaza da ɗan
abin da ya sauwwaƙa.
Ba ta ci sosai ba, su ka ɓuge da hirar yadda biki ya gudana.
Ganin ta ɗauki kayanta ta shiga toilet, ya sanya ya bata
wuri, yana sake ƙare wa gidan kallo, cike da nishaɗi.
Da ya koma ta canza kaya, zuwa doguwar riga, ta bacci, da
hijjabi.
Sai wani raɓe-raɓe yake, kamar mai shirin aikata zunubi.
Bacci ne yake shirn ɗibarta, saboda a gajiye take.
Kwanciya Walid ya yi a bayanta, da kayansa na angwancin da
komai, duk da yadda rigar ta dame shi, sai da ya ji uwar bari ya cireta.
Ƙamshin turaren da take yi ne, yake ta ci gaba da fizagarsa,
sai godewa Allah yake yi, wai yau shi ne yayi aure.
A hankali ya kai hannunsa kan na Shahida, kamar mai taɓa
wuta, ta buɗe idanunta, taga ɗakin ya gauraye da duhu.
Ta ɗan motsa kaɗan tana ƙara jinjina tsagwaron kunya irin ta
Walid.
"Shahida"
"Na'am"
"Dan Allah ki na so na, ko kin aureni saboda kawai
Viper ne ya baki umarnin hakan?"
Sautin murmushinta ya ji, ta ce "Ba na ce ka daina faɗar
sunana ba, idan ka faɗa sai na ji kamar ba ka so na, saboda yaya Aminu kawai ka
aure ni"
Da sauri ya ce "A'a ina sonki sosai, waye zai ce ba ya
son mace kamar ki?"
"Kai manaz tun da kana faɗar sunana"
Ya ce "Na daina, sweetheart ki ka ce na ce ko?"
Sosai take yi masa dariya, ta ce "Au ni na ce ma, ba kai ka yi niyyar
kirana haka ba"
Walid ya ce "Daga cikin zuciyata ya fito, ki yi haƙuri
wallahi duk ban iya irin wannan bane ba"
Shahida ta ce "Yaya ya gaya mini ai, ku mazaje ne, ba
ku iya soyayya ba, amma ni gaskiya ka koya" tayi maganar a shagwaɓe.
"In sha Allah, zan sayo littafi ki din ga karanta mini
kullum ina haddacewa" tayi murmushi tana jin yadda yake ta wasa da yatsun
hannunta.
"Shahida ban taɓa tunanin rayuwa zata canza, har na yi
iyali ba, babu abin da zan ce wa Allah sai godiya, kuma babu abin da zan cewa
Viper, sai Allah ya sa ya gama da duniya lafiya, bani da bakin da zan yi masa
godiya, ya mayar da ni cikakken mutum"
"Ramawa kura aniyarta aka yi, ku kuka fara riƙarsa a
yadda yake, ku ka mayar da shi mutum, Allah ya ƙara haɗa kanku"
"Amin sweetheart" dariya ta yi masa jin ya ce
sweetheart.
Walid ya gama noƙe-noƙen da jin kunyar, ya raya darensa.
Sai dai ya shiga lissafi, duk da shi dai bai san dawan garin
ba, amma kamar akwai banbanci tsakanin budurwa da kuma bazawara, amma bai mayar
da hankali a kan tunanin hakan ba, saboda kukan da Shahida take yi, ya din ga
bata haƙuri kamar wadda ya tafkawa laifi, har sai da ya bata tausayi.
Washegari da safe ma, ita tana jin nauyinsa, shi ma sai
sinne kai yake yi, lokaci lokaci yana sakin murmushi.
Liti kuwa da kyar yayi bacci, saboda babu Walid babu Viper,
yayi ta mita, wai suna can tare da bargo mai numfashi da sabuwar katifa, shi
yana nan ya kasa bacci.
Da sassafe Liti ya kira Walid a waya, Walid bai watstsake
daga bacci ba ya ɗaga ya ce "Lafiya?"
"Au haka ma zaka ce? Koma kira ni ka ji yaya
nake?"
Walid ya ce "Haifarka na yi da zan kiraka da sassafe na
ji yaya ka ke?"
"Allah sarki ni, wato kai yanzu ka yi 'yanci, yayi
kyau, na ce ba, ka rage mini kazar ko kuma yaya?"
"Eh, ta na wurin mai zamani ka kira shi ka karɓa"
Liti ya ce "Ai da shi muka fara yin waya, Abuja fa zai
tafi yau"
Da sauri Walid ya tashi zaune ya ce "Haba dai?"
"Wallahi haka ya ce mini, cikin dare aka tura masa
saƙo, gashi har aka gama bikinsa ɗan mama baya nan"
"Amma shi aikin nasu babu hutu kenan? Mutum yayi aure
amma ace ya fito washegari"
"Kai ma dai ka faɗa"
"Bari na kira shi" sun yi sallama da liti, amma ya
kasa kiran Viper, saboda kunya, shi tunani ma yake idan ya koma kasuwa ko zai
iya kallon Abbu.
Gidan Ango Al'amin kuwa, bayan sallar asuba Nabila ta koma
bacci, ganin Viper bai dawo ba.
Ƙarfe tara ta tashi, still baya ɗakin, ta kulle bedroom ɗin,
ta shiga banɗaki ta yi wanka, ta duba jakarta ta ɗauki brush ta wanke bakinta.
Ta canza kaya ta fita falo, tana kallon gidan.
Kitchen ta leƙa, ta tarar har ya dafa tea, tana tsaye ta ji
ya buɗe ƙofar falo, falon ta dawo a dai-dai lokacin da ya shigo.
Ta ɗan maze ta ce masa "Ina kwana?"
"Ban ganshi ba" ya amsa mata, tare da wucewa
digning, ya ajiye ledar hannunsa, ya dawo in da ya barta ya ce "Ga abin
breakfast can, kazarki kuma da baki ci ba, tana kitchen.
Ni an turo mini saƙo tun cikin dare, ƙarfe sha biyu zan bi
jirgi na koma Abuja.
Ba ta san lokacin da ta ce "Saboda me?" ba.
"Harkar aiki"
"A kawo ni juya yau kuma ka tafi, yaushe zaka
dawo?"
"Ina ruwanki da lokacin da zan dawo? Dama ai ba ƙaunar
ganina ki ke yi ba, tun da an aura miki annoba, idan na matsa sai ki
sarara"
Cikin kuka Nabila ta ce "Ai dama na sani, a haka ka ke
cewa na baka chance ɗin, ko na baka chance ɗin, na san babu wani da zai canza,
ba na gabanka, ba ni da wani muhimmanci a tare da kai, am regretting this
marriage"
Shareta ya yi ya wuce cikin ɗaki, ita da ta nuna ba ya
gabanta, ko menene na ɗaga hankalinta kuma, dan kira shi wurin aiki oho mata.
Duk da a zahiri shi ma bai so hakan ba, amma dolensa ya tafi
muddin yana son yin galaba a kan Indabo, ta wani fannin kuma, yadda Nabilan ke
treating ɗin sa, gara ya tafi kawai ya rabu da ita.
Da fari kuka ta zauna tana yi, daga baya ta ga kamar ta faɗo
ne, sai ma ya rainata, shi bai damu da ita ba, ita kuma ta damu da tafiyar sa.
Ta haɗa abin kari tana karyawa, kamar ta na cin magani, ya
sake fitowa ya fita, aka jima sai gashi da kayan abinci niƙi-niƙi.
Ƙarfe sha ɗaya ya sameta a ɗaki, ta ɓuya tana matsar hawaye.
Kamar bai gani ba, ya ajiye mata kuɗi ya ce "Na san
maybe zaki yi baƙi, ga kuɗi nan, idan kina buƙatar wani abu, na san kirana a
waya abu ne mai wahala, zaki iya kiran wanda ki ka ga ya dace kin yarda da shi,
ya kirani ya sanar mini" har ya bar ɗakin ba ta ce masa uffan ba.
Ya saɓa jakarsa ya fita, zuciyarsa na yi masa zafi, yanzu
yana ƙoƙarin gazgata Nabila ba ta ƙaunarsa.
Tafiyarsa babu jimawa kuwa baƙi suka din ga zuwa, dan haka
sai damuwar ta ta ta ragu, sai dai ana watsewa komai ya dawo mata.
Walid kuwa hankali kwance ya ci gaba da shan sharafinsa da
amarya Shahida.
Ranar da zai koma kasuwa, ta sha dariya har da riƙe ciki,
wai kunya yake ji ya fita kasuwa ya haɗu da Abbu ma.
Da kyar ya samu ya fita, Allah ya sa ranar Abbu bai je
kasuwa ba, sai dai duk bayan mintuna kaɗan, yana maƙale da waya yana kiran
Shahida, sai da ya ji kamar ya janyo yanna ta yi ya koma gida.
Sai da liti ya gaji ya fara zage-zage da faɗar maganganu,
Walid kuwa yayi masa banza, sai daga ƙarshe ya ce "Zafin gwaurantaka ke
damunka, ba zan kula ka ba"
Sannu a hankali baƙi suka fara ɗauke ƙafarsu daga zuwa gidan
Nabila, hakan ya fara damunta, ga Viper tun da ya tafi babu ko flashing, hakan
ya ƙara ƙona mata rai, ita kuma ta kira shi, gani take ta faɗo.
Sumayya dai ta ci gaba da rarrashin Nabila, kusan duk kwana
biyu sai ta zo wa Nabila, dan ta gaya mata Viper ya gari. Ita ma a hankali ta
rage zuwa, an doshi sati uku, babu Viper babu labarin sa, ko baccin kirki ba ta
yi sai aikin kuka, idan ta gaji kuma sai ta yi ta tasbihi, saboda yana daga
abin da yake sauke mata fushi da wuri.
Babu tsammani ta ji ana buga mata gate, ta tashi ta fita
tana tambayar waye?.
"Buɗe ki gani" tana buɗewa ta ga Walid da Shahida,
murmushi tayi tana yi musu maraba.
Sun yi ƙalau da su, daga shi har ita, Walid ya kuma nutsuwa,
kuma cikin manyan kaya yake, yanayin yadda suke magana akwai fahimtar juna a
tsakaninsu.
Ita kuwa an zubar da ita a cikin gida, ya tafi aikinsa ko ta
kanta baya waiwaya.
Walid ya ce "Bari na tafi kasuwa, da yamma na dawo mu
tafi, dama Viper ne ya ce wai lallai in kawo miki ita, ta tayaki hira, kaɗaici
ya dame ki, na ce masa to ya dawo mana"
Nan dai ya bar mata Shahida, shi kuma ya tafi.
Shahida ta ce "Anty Nabila, maman dr. Duniya ce, ai ni
mun ƙulla alaƙa da ita, ai yanzu na san nayi aure, wannan auren mai kuɗin duk
ba shi ne ba"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Au da ba aure ki ka yi
ba?"
"Taɓ, aka gama yi mini banke-banken magani, da shi da
babu duk ɗaya, magani ya kusa illata ni, sai da na kwanta a asibiti, kuma na
kasa faɗar abin da ya faru. Ga yan uwansa masifaffu, wai yana ta aure mata ba
haihuwa, shi bai gaya musu shi ne mara amfani ba. Na sha wahalar auren nan,
shekara uku sai da na ci na yi kallo, na zauna babu banbanci da ina gida, kuma
kowa gani yake nayi aure a gidan hutu. Na cire kunya na gaya wa mama, wai sai
cewa tayi, Allah ya rufa mini asiri zan tona wa kaina, nayi nayi ya sake ni
yaƙi, ni kuwa na kaishi kotu, na ga zai saye su da kuɗi, na samu Abbu na gaya
masa, aikuwa yayi ta faɗa"
Nabila ta waro ido ta ce "Abbun ki ka gaya wa wannan
maganar?"
"Eh mana Anty Nabila, da ace masa gani can da aurena
ina ɓarna fa? Idan cin abinci da kallo na je yi, in zauna a gidanmu mana"
Nabila ta ce "Gaskiya tun da na ji Hafsa ta yaba, kema
kin yaba, na ƙara yadda da kayan maman dr"
"Sosai fa, zata baka abin da ya dace da kai, da aka yi
mini auren fari, ai wata jahila aka samu ta din ga jibga mini kayan shashanci
suka kusa kashe ni, ai maman dr tayi a rayuwa. Ni gidan Yaya muhsin duk da
bashi da ƙarfi, ya fiye mini gidan tsohon mijina sau dubu, ga ci ga sha ga
kwanciyar hankali, gashi lafiyayye, ban yi gyara a banza ba"
Waro ido Nabila ta yi ta ce "Kin fi ƙarfina
Shahida"
"Hmm ba zaki gane ba, matan da suka tsinci kansu a irin
halin da na taɓa tsintar kaina, sun san takaicin abin nan. Kana gidanku baka
san komai ba dama, ya fi sauƙi hankalinka a kwance yake, amma an aurar da kai,
mutum ya san ba shi da lafiya, saboda zunzurutun zalunci, ya aureka, kuma yan
uwansa su addabeka, baka haihuwa, wallahi na kusa gaya wa babarsa ranar da aka
ishe ni, kawai nayi shiru"
('yan uwa kar ku bari a baku labari, ko kuma a bar ku a
baya, ku garzaya ku jarraba, kayanta, ga kyau ga kuma inganci 0706 971 1327)
Nabila ta ce "To Allah ya kyauta, Allah ya ƙara muku
zaman lafiya da fahimtar juna, tun da kin samu abin da ki ke so"
Dariya tayi, ta ce "Amin, ina nan ina ta kwantar da kai
ina lallaɓa abina, ko ƙuda bana son ya taɓa mini shi, ina matuƙar son sa da
tausayinsa"
Nabila ta ce "Yakamata, ai Walid mutum ne na gari"
Sun sha hira sosai da sosai, dan sam Nabila ba ta bari,
Shahida ta fuskanci damuwa a tattare da ita ba.
Bayan tafiyar su, da daddare ta rasa abin yi, ta buɗe
wardrobe ɗin Viper, ta sauke kayan tana gyarawa.
Wani ƙaramin littafi ta gani, ta ɗauka ta fara dubawa.
"Wannan littafin na master ne, kar ka manta ka karanta
shi safe da yamma"
Azkar ne aka rubuta shi, na safe da yamma da hausa, sai kuma
Addo'in kwanciya bacci.
"Ka kula mini da kanka sosai master, duk lokacin da ka
karanta, ka yi mini addu'a"
Ƙasa sai ta zana heart da sunansa, irin da na soyayyar
ƙuruciyar nan.
Shafa littafin Nabila ta din ga yi tana kuka, ta ce
"Allah ya sa auren mijinki, kar ya zame mini cin amanarki 'yar uwata,
Allah ya sa ba ƙaddarar auren nan ne ya sanya ki ka bar duniyar nan ba, ina
ƙaunarki duk da ban sanki ba"
Sosai Nabila ta yi kuka, mai ban tausayi, daga bisani ta
tashi jiki a sanyaye.
Kamar wadda aka yi wa nasiha, washegari, ta tashi da
matsananciyar kewar Viper, babu tunanin komai, ta ɗauki waya, ta din ga
kiransa, amma wayarsa a kashe.
Kawai sai hankalinta yayi matuƙar tashi.
Madam halima ce ta kira Nabila, suka gaisa ta ce
"Nabila, gobe Joseph zai zo da safe, zaku tafi Abuja, Viper babu
lafiya"
Ƙirjin Nabila ya buga da ƙarfin gaske, ta ce "Meya same
shi?"
"Ban sani ba, Joseph ne ya zo yake gaya mini, dan haka
ki zama cikin shiri" kuka ta saka wa madam, tana tambayar ta, idan wani
abun ne ya same shi ta gaya mata, amma ta ce mata ba ta sani ba.
Ana idar da sallar asuba ta shirya, cikin matsanancin tashin
hankali, addu'a kawai take yi Allah ya sa yana lafiya.
Ta waya suka din ga communicating da Joseph, ya zo gidan, ya
ɗauki Nabila suka tafi, sai da ta tambaye shi ko ya san wani abu a kai, amma ya
ce mata bai sani ba.
Sumayya ce ta kira Nabila, ta ce mata maza ta hau social
media ta duba meke faruwa.
Hannunta na rawa ta buɗe tana duddubawa, wai tsohon riƙaƙƙen
ɗan daba Aminu Viper, ya koma ɗan ta'adda, bayan da yayi attacking ɗin manyan
mutane ciki har da honorable Indabo, da bindiga a wani guset house da yake
Abuja.
"Impossible, this is not true, Vi ba zai yi haka ba,
dole akwai wani abu a ƙasa"
Sai daf da azahar suka isa barrack ɗin da yake aiki a Abuja.
Nabila sama-sama take numfashi, a ganinta gawarsa kawai za
su nuna mata.
Wani ɗaki aka shigar da ita, yana kwance a kan gado, ana
ƙara masa jini, da gudu ta ƙarasa gaban gadon da yake, bakinta na rawa tana faɗin
Innalillahi wa Innalillahi raji'un.
An nannaɗe kafaɗarsa da bandeji, ga cikinsa gefe a kumbure.
Alamu ya nuna harbinsa aka yi a kafaɗarsa.
"Vi, ka tashi dan Allah ka tashi"
"Madam ki yi haƙuri, bai daɗe da samun bacci ba"
Ko ta kan mai maganar ba ta bi ba, ta ci gaba da kuka.
A hankali ya buɗe idonsa, ya ɗago ya kalleta.
"Vi, meyafaru haka, garin yaya aka harbeka, da gaske
zuwa ka yi ka kashe indabo, meyasa zaka yi attacking ɗin sa haka?"
Lafiyayyen hannun ya ɗago, ya shafi fuskarta, ya ce
"Aiki mu ka je, ban yi attacking ɗin kowa ba. Mun yi negociating da wasu
hukumomin na tsaro ne, aka je gidan, amma an ce na yi laifi, zan iya fuskantar
hukunci, na yi harbi ba a bani umarnin hakan ba, duk da yaransa sun yi yinƙurin
kashe ni.
An kama Naja'atu Bunkure a gidan, da ƙanan yara mata da ake
lalatawa da kuma maza, gidan da aka yi sanadiyar ran Nura ne, kuma mun kama
makamai a gidan, da wasu manyan ƙusoshin gwamnati duk a gidan. Hukumar soja ba
sa zargina sa ta'addanci, wannan sharrin media ne, da nake kyautata zaton
mutanen Indabo ne suka saka ayi mini hakan, hukuncin da zan fuskanta na harbi
ne ba ayi mini uzuri ba, ina da abubuwa da yawa da tun a baya na so mu
tattauna, amma baki bani chance ba, baki bani da ma ba Abla, akwai abubuwan da
nake buƙatar aiki da ƙwaƙwalwarki, saboda ta kan yi mini jagora a wasu
abubuwan, amma ki ka ƙi saukko ki fahimce ni"
Ƙanƙame shi ta yi tana kuka ta ce "Am sorry Vi, ka yi
haƙuri dan Allah, amma zan ɗauki kowane irin mataki, wallahi babu mai hukunta
mini kai, wahalar da ka sha ma ta isa haka, wace irin ƙasa ce wannan? In dai
ina raye babu wanda zai yi maka wani hukunci babu shu"
Ya saka hannu yana shafa kanta ya ce "Dan Allah ki
zauna tare da ni abla, zamanki a kusa da ni, yana bani ƙwarin gwiwa ina jin am
safe idan muna tare, tun ba yanzu ba Please" ya ƙarasa maganar muryarsa na
rawa.
*GA MASU JIRAN DOCUMENT, ZA SU IYA PAYMENT YANZU, FEW PAGES
YA RAGE, ONGOING PAGES NE 500 COMPLETE DOCUMENT KUMA 1K. VIA 0009450228
AISHA ADAM JAIZ BANK
SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143
Ayshercool
08081012143
"I promise that, ina tare da kai ɗari bisa ɗari, komai
tsanani da wahala, is enough yakamata ka huta haka, masifun nan sun yi
yawa"
Ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Ina ga haryanzu sakamakon
laifuffukana ne suke ci gaba da bibiyata".
Ta ce "A'a, Allah ba azzalumin sarki bane ba, kuma yana
son bayinsa masu neman gafararsa. Wannan wata jarrabawa ce ta daban, kuma zamu
cinyeta ita ma in sha Allah, sannu Vi" ya jinjina mata kai kawai bai sake
cewa komai ba.
Wayarta ta ciro, ta lalubo lambar Alhaji mu'azzam, ya ɗaga
tare da yin sallama, ta amsa masa ta ɗora da cewa "yallaɓai ka ga abin da
ya faru da Viper?"
"Wallahi ɗazu na gani Nabila, raina yayi mummunan ɓaci,
na je Kano ne, amma anjima kaɗan zan shigo Abuja in sha Allah, kuma already na
yi magana da ministan tsaro ma, za ayi bincike a kan lamarin"
"Wane bincike kuma, ana cewa wai sai an hukunta shi
yayi harbi ba bisa ƙa'ida ba, ga harbi da aka yi masa, ni idan har haka aikin
yake, kawai zai ajiye musu aikinsu, wannan wahalar ta isa haka"
"Ki yi haƙuri Nabila, na san halin da ku ke ciki, na
kuma san wahalhalun da ya sha, duk kitumurmurar indabo ce, ina kyautata zaton
an ce an sake shi ma, sai dai na zo kawai" tana cikin maganar wasu sojoji
su uku suka shigo, da alama manya ne sosai a cikin rundunar tsaro, ta katse
wayar.
Joseph ne ya ƙame ya sara musu, sannan ya kalli Nabila ya ce
"Ko zamu ba su wuri?" Ko kallonsa ba ta yi ba ta ce "Ba in da
zani".
Ɗaya ya ce "Sannu Viper"
Viper ya jinjina kai sannan ya ce "Thank you Sir"
Nabila ta ce "Da gaske ne wai sai an hukunta shi saboda
yayi harbi?"
Suka kalleta gaba ɗaya, ɗayan ya ce "Muna tattaunawa a
kan lamarin ne, an ce ba shi yayi harbin ba, Dss ne, kuma mun duba bindigarsa,
yayi harbi da bullet biyar"
Ta ce "Yanzu idan na ɗauki bindiga zan harbeka, ga
bindiga a hannunka tsayawa zaka yi sai wani ya baka order zaka kare
kanka?" Ba ta damu da mamakin da ya bayyana a kan fuskokinsu ba ta ci gaba
"A matsayina na lauya nake yi muku magana, wadda ta san 'yancinta, ni ba
soja ba ce ba, kar ku yi expecting wata special girmamawa daga gare ni, na san
ƙarshenta dai ace a kashe ni. Yanzu da an kashe mini shi, gawarsa kawai zaku
kawo mini kuna yi wa gawar faretin banza da na wofi, babu lallai a samu hukumar
ta sake bi ta kaina a matsayina na matarsa.
Masu laifin da ya taimaka aka kama, ba ƙasa ya yi wa aiki
ba? Harbin da aka yi masa bai isa ba, kuma sai an yi masa wani hukunci, ga suna
an ɓata masa an kira shi da ɗan ta'adda amma ba ku ce komai ba"
Viper ya ce "Nabila"
"Ka ƙyaleni Vi, sai dai a kashe ni, kun san abin da ya
yi going through in his life, washegarin tarewata da aurenmu, ku ka ce lallai
ya zo bakin aiki, yazo kuma yayi abin da ku ke so, kuma this is what he
deserves, da haka za a saka koya wa matasanmu ƙauna da kishin ƙasa? Masu laifi
na sharholiya masu kare ƙasa ana gana musu azaba, a kan laifi ƙanƙani, i will
fight for his right" numfashinta sama yake yi sosai cike da ƙunar zuciya
da takaici. Viper kuma ba shi da ƙarfin da zai hanata, saboda jirin da yake ji,
da kuma jinin da ake ƙara masa.
Ɗaya daga cikin sojojin, da Nabila ke kyautata zaton shi ne
babbansu, sai ya yi murmushi, cikin harshen hausa ya ce wa Viper "Kai ka
auro zakanya kamar kai, she's lioness and fearless, i like her confidence.
Madam, we are working on your husband issue, muna supporting
ɗin sa, a kan ayyukan da yake yi, kin san mu bamu da hurumin kama mai laifi,
sai dai muna hana yi wa ƙasa ɓarna.
Mun yi haɗin gwiwa da wasu hukumomin, Viper shi ya gano
gidan, kuma tare da shi aka je, a ƙoƙarin kama masu laifin, aka fara
harbe-harbe.
Kuma mu bamu fitar da report na ga abin da ya faru ba, and
abin da viper ya yi bamu gama yanke hukunci a kai ba, kin ɗauki zafi da yawa ki
yi haƙuri, Viper aikin sa ba zai iya ajiye shi yadda ya ga dama ba, ya san
dokar aikin ai. Kuma zamu bincika duk wanda yake da saka hannu, wurin wallafa
wannan labarin zamu baki dama, ki kai ƙararsa ki yi haƙuri"
Joseph kansa da ya fara tsuma, bai san hukuncin da za a iya
yi wa Nabila ba, wannan kwarmaton da tayi ba, amma abin mamaki, sai ya ga an ɓuge
da rarrashinta.
Hawayenta take gogewa, amma sun kasa tsayawa, saboda wani
irin matsanancin tausayin Viper, da ya takura zuciyarta, ya wahala da yawa.
Ɗaya sojan ma, rarrashinta ya din ga yi, yana kiranta da
'yar sa. "Da kin san matsayin da mutane masu muƙamin Viper suke da shi a
rundunarmu, da baki ce ya ajiye aiki ba, amma muna baki tabbacin, zamu san abin
yi a kan sa"
Suka gama maganganun da za su yi, da rarrashinta suka fita.
Matsawa ta yi sosai jikinsa, sai bin sa take da ido.
"Abla"
"Na'am vi" ya juyo a hankali ya riƙeta ya ce
"Ki zauna a kusa da ni, kar ki je ko ina dan Allah"
"Ina tare da kai in sha Allah vi"
"'yar madara ta tafi ta bar rayuwata da duhu, kin fara
hasakata amma kina ta so kema sai kin bar ni, Please"
Ta katse shi ta hanyar cewa "Vi dan Allah ka yi shiru,
Allah ya baka lafiya na ɗaukeka mu tafi, Allah ya baka lafiya"
Ya sake cewa "Amin, indabo azzalumi ne abla, an kama
shi, amma na san sakinsa za su yi, na yi iya yi na, na bar wa Allah
sauran"
Nabila ta ce "In sha Allah kuma zai isar maka"
Ta lallaɓa ta tashi, ta yi alwala ta yi salla, ta zo ta yi
masa alwala, ya gabatar da salla yana kwance.
Wasu sojojin ne suka sake shigowa su biyu, ba su ce mata
uffan ba, aka cire masa jinin da yake shiga jikinsa, kasancewar ya ƙare, suka ɗaga
shi zaune, ya jingina da jikin gadon.
Suka sara masa, sannan suka juya za su tafi.
Viper ne yayi gyaran murya, suka tsaya suka waiwayo.
Yayi wa ɗaya alama ya zo, ya tako ya ƙaraso, Viper ya nuna
masa abincin da suka shigo da shi.
Babu musu sojan ya buɗe kowanne ya ci, ya rufe. Da hannu ya
yi musu umarni suka tafi.
Nabila tana jejjera masa sannu, ya kalleta ya ce "Ga
abinci nan ki ci"
Ta ce "A'a sai dai kai na zuba maka ka ci"
Ya girgiza kai ya ce "Na ƙoshi"
Cikin damuwa ta ce "Ka ƙoshi kuma, vi kamar dai akwai
wani abu kuma da yake damunka" ya ɗago ya kalleta.
"Menene ka gaya mini mana"
"Ba komai" ya faɗa a taƙaice.
Ta marairaice ta ce "Please, Vi menene ka gaya
mini"
"Jikina ne kawai babu daɗi"
"Sannu, bari na zuba maka, ko kaɗan ka ci"
Baya son ta ci gaba da takura shi da tambayoyi, dan haka ya
daure ya din ga haɗiyar abincin, tamkar yana haɗiyar magani.
Ya gama ta bashi ruwa, ta dubi hannunsa ta ce "An cire
bullet ɗin ne?" Ya jinjina kai ya ce "Tun ranar aka cire".
"Amma yaya aka yi ka je gidan da kanka, har tsautsayin
nan ya faru?"
Ya ɗan numfasa ya ce "Tun bayan rasuwar Nura, da ya
gaya mini in dw zan samu Simon, na je na same shi. Shi ne ya gaya mini in da
gidan yake, da abubuwan da suke wakana a gidan.
So ban yi wani abu a kai ba, har tsautsayin nan ya faru, so
bayan nan na daɗe ina fakon gidan, ina da informers ɗina a kan gidan. Sai dai
yadda ake gudanar da laifuka a gidan, akwai tsari da taka tsantsan ɗin da babu
lallai a gane, tun da da haɗin kan wasu daga cikin jami'an tsaro ake abin da
ake yi.
Nayi magana da shugabannina, muka yi haɗin gwiwa police da
DSS, sai da na tabattar da Indabo yana gidan, muka je operation, sai dai bayan
mun shiga, wasu daga ma'aikatan gidan suka far mana da harbi.
An kama Indabo Naja'atu ma tana gidan, da wasu manya a ƙasar
nan, police sun tafi da su, amma bana tunanin za ayi wani dogon bincike,
rahotannin da na samu, kamar an ce an sake shi ma, amma bani da tabbas.
Ina takaicin mutum kamar Indabo ace ya ci bulus a kan
abubuwan da ya aikata, amma babu komai"
"Wallahi ba zai ci bulus ba, dole ya girbi abin da ya
shuka ko da me yake yawo"
"No, kar ki kuskura ki ce zaki yi wani abu, yanzu ma
abin da ki ka yi, ikon Allah ne ya tsallakar da ke, kin san suwa ki ka tsaya a
gabansu ki na faɗar maganganu kuwa? Bani da ƙarfin hana ki a lokacin, amma da
sun yi yinƙurin yi miki wani abu, to da zan nemo ƙarfin duk in da yake na baki
kariya, ko da kuwa hakan na nufin na rasa raina ne.
Gidan soja ne nan, ba a misbehaving, idan ki ka yi dole na
karɓi hukuncin da za ayi miki. I don't know why you are so much lucky"
"I am lawyer, 'yanci na sani, dan haka ba ruwana da
dokar koma gidan waye, mijina nake son ya samu 'yanci"
Murmushin gefen baki yayi ya ce "Kamar gaske"
"Da gaske nake Vi"
"Na ji amma ban yarda ba"
Alhaji mu'azzam ne yayi sallama ya shigo, suka amsa gaba ɗaya,
ya ƙarasa suka gaisa da Viper.
Cikin damuwa ya ce "Sannu Viper, ya jikin?"
"Alhamdilillah"
"Ashe abin da ya faru kenan, nayi magana da shugabannin
naku ai, kuma ministan tsaro ya bayar da umarnin lallai su yi magana su wanke
ka"
Nabila ta ce "Alhamdilillah, har shi ma ya ji?"
"Eh tun kafin na zo muka yi waya ai, kuma zamu gurfanar
da gidan jaridar da suka sanar da wannan labarin ƙaryar, dan na san biyansu aka
yi suka yi hakan".
Viper ya ce "Wai da gaske an saki Indabo?"
Kankarofi ya jinjina kai ya ce "Ai ba a bari ma an
sanar da ainihin abinda ya faru ba gaba ɗaya. Amma tabbas an bayar da belinsu,
Bunkure ce ba a saki ba, dama ita tuntuni kotu ta bayar da umarnin a nemo ta,
duk in da take a gurfanar da ita a gabanta. Ka yi haƙuri na san abin da ka ke
ji a ranka, amma ina mai tabattar maka da wahalarka ba zata tafi a banza ba,
kana yi wa ƙasa hidima da ranka da jikinka, dan haka dole ayi maka wani abu na
girmamawa"
"Bana buƙatar komai, dama babban burina in ga an
hukunta indabo, tun da ba zan samu hakan ba, shikenan na haƙura"
"Kar ka yanke tsammani Viper, tabbas indabo yana da
connection da manyan ƙasar nan, da suke aikata ɓarnar su tare, shiyasa baya taɓuwa,
duk da Nabila tayi breaking record ta jijjiga shi, alhalin yana kan kujerar
mulki, kin yi namijin ƙoƙari sosai, amma ka bar shi da Allah, kai fa ko iya
haka ka tsaya ka ɗauki fansa, ka jira kaga yadda Allah zai yi da shi
kuma".
Viper ya sunkuyar da kai yayi shiru, sai huci da yake yi.
Nabila ta dafa kafaɗarsa ta ce "Vi, ka yi haƙuri dan
Allah, kar ka sanya damuwa da yawa a ranka, kamar yadda wasu daga cikin mutane
ba sa girbar tarin alkhairin da suka shuka, suke komawa ga Allah, su tarar da
sakamakon su a can, haka wasu daga cikin waɗanda suke aikata ɓarna, ba sa
girbar abin da suka shuka, sai a gaban Allah. Wata shari'ar sai a lahira
ai"
Viper ya jinjina kai ya ce "Haka ne"
Alhaji mu'azzam ya ce "Haka ne zancenki, ni kaina nayi
iya ƙoƙarina, na ga Indabo an hukunta shi, amma abu ya gagara, shiyasa na
haƙura na zuba wa sarautar Allah ido, ka yi haƙuri Viper, mun san an cutar da
kai, amma ci gaba da jayayya da dagewa lallai sai ka ga bayan indabo, zai ƙara
complicating abubuwa ne kawai, lokaci ya yi da yakamata ka yi relaxing, ka huta
ka nutsu ka yi enjoying life ɗin ka. Indabo kuma ka zuba ido, hakkin abubuwan
da ya aikata, ba zai taɓa barinsa ya rayu cikin aminci da kwanciyar hankali ba,
ko a yanzu ka kafa tarihi, kuma rayuwar gidan indabo ta watse, dan haka ka yi
haƙuri"
Viper ya jinjina kai, "Yauwwa, Ubangiji Allah ya yi
maka jagora, ya kawo maka ci gaba na ban mamaki"
Suka amsa da Amin.
Viper ya kalli Alhaji mu'azzam ya ce "Na gode sosai da
sosai, Allah ya saka da alkhairi"
"Bakomai kar ka damu"
Ya sake kallon Alhaji mu'azzam ya ce "Ka tafi da ita
wurin hafsa dan Allah, ta huta ta kwana a can idan ban takura maka ba"
Alhaji mu'azzam ya ce "Wane irin takura kuma, ba takura
ai dama yakamata ta kawo mana ziyara"
Nabila kuwa ta ce "Yaya za ayi na tafi na bar ka, wa
zai yi jinyarka?"
Viper ya ce "Kar ki damu, babu abin da zan nema na rasa
in sha Allah, ana kula da ni"
"Ni gaskiya ko na tafi ba zan iya nutsuwa ba, hankalina
ba zai kwanta ba, ka bari idan ka samu lafiya na je gidan nata"
Ya tsuke fuska ya ce "Zaki fara ko? Ba zan ce ayi abu
ba ki yi, sai kin yi gardama ko?"
Ta marairaice ta ce "Dan Allah vi, wallahi
hankalina.... Kallon da ya yi mata ne ya sanya ta yin shiru, idonta na cika da
hawaye.
Haka tana ji tana gani, ta tafi ta bar shi.
Gidan hafsa gida ne haɗaɗɗe mai matuƙar kyawun gaske, Hafsa
na ganin Nabila ta rungumeta tana murna.
Ta kalli Kankarofi ta ce "Yallaɓai, ina ka tsinto mini
ita, ko ta biyo maigidan ne ban sani ba, ba ta gaya mini ba?"
Ya ce "Ina fa, wani case ɗin ya kuma tasowa" nan
ya gaya mata abin da ya faru.
Jiki a sanyaye hafsa ta ce "Kai, Allah ya isa
tsakaninmu da wannan azzalumin mutumin, Allah ya shiga tsakaninmu da shi, amma
ya jikin Yaya Al'amin ɗin?"
Alhaji mu'azzam ya ce "Jikinsa da sauƙi, duk da yana da
ƙarfin hali, amma an harbe shi a kafaɗa"
Cikin tausayawa ta kalli Nabila ta ce "Ki yi haƙuri kin
ji ƙanwata, in sha Allah zai samu lafiya" Nabila kuwa ɗan kukan da take
maƙalewa ya ƙwace mata, Hafsa ta din ga rarrashinta, ta kaita ɗaki ta yi wanka
ta bata kaya ta saka.
Ta ci gaba da rarrashinta, daga nan kuma suka shiga hira, a
lokacin Nabila take bata labarin wasu abubuwan, tun daga haɗuwarta da Viper.
"Ya sha wahala sosai da sosai, ina matuƙar jin
tausayinsa, daga wannan sai wannan"
Hafsa ta ce "Kin san da haka amma ki ka din ga bori wai
ba kya son aurenku"
"Ina da dalilina mai ƙarfi na yin haka, amma koma dai
menene ya riga ya wuce, Ubangiji Allah ya sassauta masa"
Hafsa ta amsa da Amin tare da ci gaba da rarrashinta.
A ranar aka fitar da sanarwar cewa, Viper ba ɗan ta'adda
bane ba, domin yana aiki ne da rundunar tsaro ta ƙasa, kuma harbi ya yi shi ne
a kan ƙa'ida, babu daɗewa za su fitar da rahoton ainihin abin da ya faru.
Walid ya dawo daga kasuwa, bai samu dawowa gida da wuri ba,
saboda ayyuka da suka yi yawa, kuma sai da ya biya wurin liti suka ɗan yi hira,
suka zauna a joint tare, daga nan ya taho gida.
Ya sha shagwaɓa da tuhumar dalilin daɗewarsa daga wurin
amarya Shahida, kafin daga bisani ta gabatar masa da abincin sa na dare.
Wayar Viper ya kira, bayan ya gama, ya ɗaga amma bai ce
komai ba.
"Mai zamani, wai ina ka shiga ne kwana biyu bana samun
wayarka, hankalina ya tashi sosai, liti ma ya ce mini ba ya samunka"
Ya sauke numfashi ya ce "Ina lafiya"
"Mai zamani"
"Mai laya"
Walid ya ce "Akwai matsala, menene yake faruwa?"
Viper ya ce "Nothing much, kar ka damu ya ƙanwata"
"Da akwai matsala, kuma ba ƙarama ba ce ba, kamar yadda
ka ke faɗa, meyake faruwa?"
"Koma da akwai matsala, ba gashi kana ji na ba, babu
wata matsala ba abin damuwa ba ne ba"
"Ka san ba abu ne mai wahala na yi sammako na taho
Abujan nan ba, ka gaya mini menene?" Walid ya yi maganar a hasale.
"Easy maza, harbina aka yi, amma ina samun sauƙi, kar
ka ɗaga hankalinka"
Walid ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, kuma
ka kasa gaya mini, ka ke cewa ba abun damuwa bane ba"
"Eh, bana son ɗaga muku hankali ne, dan Allah kar ka
gaya wa kowa, kuma kar ka ce zaka zo, ba ni tabbacin hanya tana da kyau"
"Anya zan iya haƙuri ban zo ba, Viper kar ka ɓoye mini
wani abu"
"Kai dalla ware ina gaya maka magana kana ja, zan saka
maka ƙarfe ka kuma ƙoƙarin ƙaryatani, ja jiki dalla, mai laya" Walid bai
san lokacin da dariya ta suɓuce masa ba ya ce "Na kiyayi mai zamani, tuba
nake ka san ɗaukar ƙarfenka ba duk kai ba, na sallama tuba nake, Allah ya ƙara
lafiya, ya ja zamaninka mai dogon zamani"
Viper ma yayi murmushi ya ce "Sai da kai na wajena, ka
gaida mini ƙanwata"
"Zata ji in sha Allah" suka yi sallama ya ajiye
wayar yana murmushi.
Ba a awa uku, sai Nabila ta kira Viper, ta tambaye shi yaya
jikinsa.
Har ga Allah ta so ta kwana tare da shi, amma ya koreta ya
saka aka tafi da ita.
Da kyar ta iya cin abincin dare, Walid ya kirata, yana yi
mata mitar, meyasa ba ta gaya masa abin da ya samu Viper ba, ta gaya masa ba ta
sani ba sai daren jiya, ita ma yau ta zo ta ganshi, amma ta tabattar masa da
jikinsa da sauƙi.
Ƙarfe uku da rabi, alarm ɗinta ya buga, ta tashi zaune, haka
kurum sai ta kira lambar Viper, gani take yi kamar wani abu zai same shi, ga
mamakinta kawai ta ji ya ɗaga.
"Vi"
"Mmm"
"Baka yi bacci ba idonka biyu?"
Ya ce "Mmm"
"To meyasa?"
"Ciwo" ya bata amsa muryarsa ƙasa-ƙasa.
Ta miƙe tsaye ta ce "Ka gani ko, da ka bari na kwana
tare da kai, atleast ina kusa da kai, na taimaka maka da wani abun, wurin
harbin ne yake yi maka ciwo?"
"Mmm"
"Sannu Vi, Allah ya baka lafiya ya sanya kaffara
ne" tayi maganar tana kuka.
"Abla, stop crying, babu zafi sosai kawai na kasa bacci
ne"
"A'a da zafi mana, ina jin zafin a zuciyata"
Shiru ya yi yana tuna lokacin da jauhar take yi masa
magiyar, ya daina zuwa in da za a cutar da shi, saboda ita take jin zafin a
zuciyarta.
"Ki na ji na?"
"Eh"
"Ki kwantar da hankalinki, ki daina kuka Please, idan
ba haka ba, zan ba da umarni a hana ki ganina, har sai na warke"
"Yi haƙuri na daina"
"To shikenan, ki yi bacci mai daɗi"ya katse wayar.
*****
Bunkure ta din ga zuba ido, ta ga ta ina za ayi belinta,
domin kuwa ba wuri ɗaya aka kaita da su Indabo ba, ita Kano aka yo da ita,
domin ta fara Fuskantar tuhuma ta farko, da ake yi mata a kano, amma shiru babu
alamar za ayi belinta, jami'an tsaro suka tabbatar mata da cewa a gaban kotu za
a gurfanar da ita.
Abokan aikinta da suka kai mata ziyara, suka tabattar mata
da cewa an bayar da belin indabo, daga majiya mai ƙarfi, kuma ba a sanar da
cewa an kama shi ba, ita ce kaɗai labarin kamata ya cika media.
Abin ya ɗaure mata kai sosai da sosai, sai dai ta yi masa
uzuri, ta ƙara masa kwanaki, ko zai waiwayota ya sanya a bayar da belinta.
Washegari da sassafe Nabila da Hafsa tare da Alhaji
Mu'azzam, suka tafi wurin Viper.
Ko da su ka je, Nabila da Hafsa ne suka shiga, shi kuma
Alhaji mu'azzam ya tsaya a wani office.
Suka tarar an buɗe wurin raunin Viper ana dressing.
Da sauri Nabila ta ƙarasa, ta zauna ta gefen sa tana yi masa
sannu, cikin kulawa da tausayawa.
Ya langaɓo kansa jikinta ya ce "Washh da zafi" sai
ta sake rikicewa cikin tausayawa ta ce "Sannu Vi, dan Allah doctor ka yi
masa a hankali"
Likitan ya ce "Ba wani zafi, tun ɗazu nake durje ciwon,
bai ce da zafi ba sai da ki ka zo"
Viper ya ce "Abla zafi, da zafi yake yi mini"
Hafsa kuwa riƙe baki tayi, tana kallon ikon Allah, da wani
ne ya gaya mata zata ce an zabga mata ƙarya ne, kodayeke ba abin mamaki bane,
ko a baya Jauhar yana sakin jiki da ita. Nabila kuwa ta sake rikicewa ta ce
"Dan Allah ciwon nan ya wanku haka a ƙyale shi"
Likitan kasancewar sa, bahaushe ne ya ce "Sai dai ya yi
kukan jini, sai na cuɗe shi sosai"
Marairaicewa Nabila ta yi kawai ta saka kuka, domin ramin da
taga wurin harbin yayi, kuma a haka likitan yana cewa wai bashi da ƙan jiki,
wurin ya ciko.
"Ke da wasa nake yi fa, ba wani zafi kawai ina son in
ga kina kula da ni ne"
"You are just pretending, amma na san da zafi"
Yayi murmushi ya ce "Idan muka koma gida, ke zaki ci
gaba da yi mini dressing ɗin fa"
Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya ba, kuka zan ta
yi" Viper yana kallo Hafsa ta silale ta bar ɗakin, bayan ta ajiye kayan
abincin hannunta.
"Zafin shigar bullet ɗin, bai kai zafin ƙiyayyar da ki
ka nuna mini ba, ya taɓa zuciyata sosai"
Ta marairaice ta ce "Am sorry Vi, dan Allah ka daina
tunawa mana" dai-dai lokacin likitan ya kammala nananɗe masa hannun ya ce
"Gashi nan maza ki haɗiye shi madam" Nabila ta yi murmushi, sai a
lokacin ta farga Hafsa ba ta nan, ta ce "Kai, tare fa muka shigo da hafsa,
tana ina?"
"Ta fita tun ɗazu, taga abin naki ba na ƙare bane
ba" yayi maganar yana janyota jikinsa.
Ta tura baki ta ce "Ni da suka din ga soyayya a gabana
ya na yi, ko kunyata ba sa ji"
"Mhmm su su na can su na soyayya, ke ki na takaicin an
yi miki auren dole"
Tashi ta yi daga jikinsa, saboda da lafiyayyen hannun, yake
ƙoƙarin fara lalubeta, ta ce "Bari na baka abinci ka karya, yaya ka kwana
da jikin?"
"Jikina Alhamdilillah, yau zan fita ma na zagaya, na ji
sauƙi sosai da sosai"
Tana cikin haɗa masa breakfast, Alhaji mu'azzam ya shigo
tare da Hafsa.
Suka duba jikin Viper, Alhaji mu'azzam ya ce "Minista
zai zo dubaka anjima in sha Allah"
Viper ya ce "Ni ɗin?"
"Eh kai fa" ya kalli Nabila ta kalle shi.
Ta ce "Yallaɓai, Viper ministan tsaro zai zo ya
duba?"
Alhaji mu'azzam ya ce "Ni ma ba ƙaramin ministan bane,
ai komai sila ne Nabila, kuma idan Allah ya yi niyyar yi maka wani abu, ko da
sai ka sha baƙar wahala, kan ka same shi, sai ya baka abin nan.
Da gudunmawarsa ɗari bisa ɗari na din ga gudanar da wasu
abubuwan, na taimaka wa rayuwarka.
In sha Allah kukan da ki ke yi na sha wahala, zai zame masa
alkhairi, dan na yi masa bayaninsa sosai da sosai, kuma mussaman saboda kai ya
kira ya ce lallai ayi bincike a wanke ka, dan haka ka kwantar da hankalinka in
sha Allah babu abin da zai faru da kai sai alkhairi, wahalar da ka sha, ba zata
taɓa tafiya a banza ba in sha Allah"
Shi dai Viper jin abin yake kamar ba gaske ba, bayan sun
gama, Alhaji mu'azzam suka tafi, suka bar Nabila, da zummar da yamma za a zo a ɗauke
ta.
Viper zuciyarsa ya din ga kaiwa nesa, kasancewar sa da daga
shi Nabila, saiti yana neman ya ƙwace masa, duk da a da yana iya sarrafa kansa
yadda yakamata.
Ya ja ta suka fita yawo, idan suka haɗu da na ƙasa da shi,
su sara masa, idan na sama da shi ne, ya sara musu.
Duk da gargaɗin da Viper ya yi wa Walid, amma sai da ya gaya
wa Liti, abin da yake faruwa, ƙarshe sai da suka yi video call da shi, sannan
hankalinsu ya kwanta.
Sai da aka kwana huɗu, sannan Alhaji mu'azzam ya zo tare da
ministan tsaro, kamar yadda ya sanar da Viper zai zo duba shi, ba kuma shikaɗai
ba, har da babban hafsin soja na ƙasa, da wasu daga manyan shugabannin rukunin
sojoji masu irin aiki irin na Viper.
Yana zaune a kan gadonsa, Nabila na kan kujera, suka shigo,
ta tashi tsaye tana kallon su, sai da ta gansu tare da Alhaji mu'zzam, sannan
ta ɗan nutsu.
Yana zuwa ya miƙa wa Viper hannu, sai da ya ɗan yi jimm,
sannan ya miƙa masa suka gaisa.
"Finally, yau gani ga Viper, ya ci sunansa Viper, yayi
kalar mazaje" yayi maganar yana murmushi.
Ɗaya daga sojojin ya ce "He's very intelligent, and
hardworking man, da taimakon team ɗin sa, mun daƙila hare-hare masu yawa, yana
taimakawa rundunar tsaro sosai da sosai"
Ya jinjina kai ya ce "Na ji daɗi sosai da sosai, duk da
ta wani fannin mun aikata laifi, na cireka daga prison, aka yi maka horo na
musamman, amma da wata ɓarnar gara wata, na ji labarin duk abin da ya sameka,
hakan ya sanya na ƙara samun ƙwarin gwiwar saka hannu a taimaki rayuwar ka, duk
da ka bamu wahala da farko, dan sai da na ce, idan zaka bayar da matsala gara a
kasheka, amma Kankarofi ya dage, ya ce a bika a hankali.
Ina jimanta abin da ya same ka, Allah ya baka lafiya, sannan
zan san abin da zamu yi maka, mu ƙara ɗaga darajarka a gidan soja, you are
brave man Al'amin, the entire nation is proud of you. Ka yi abin da ya dace,
sauran kuma ko su hukunta masu laifin, ko su bar su, wannan kuma su da Allah
ne, get well soon my man" yayi maganar yana dukan kafaɗar Viper.
Alhaji mu'azzam ya ce "Ga kuma madam ɗin sa fa, his
lioness wife, barrister Nabila, yarinyar da nake baka labari, mutuniyar
Naja'atu Bunkure"
"Kai, to ai na ganta yarinya ƙarama"
"Eh yarinya mai kasada ba, su suka assasa lallai ayi wa
Indabo kiranye, amma aka daƙile su, ai nan Abuja zata dawo, ku nema mata gurbi
gaskiya, a din ga matsawa matasanmu, suna gwada mana tasu baiwar, hatta cheif
judge ya san da ita, amma ita ba ta sani ba"
Shugaban hafsin Sojojin ya ce "Tabbas ƙasarmu Nigeria
tana da nagarttun matasa, wanda za a basu dama, zasu kawo gayar a abubuwa da
yawa. Kamar history ɗin Viper da na duba, da tun tasowarsa, ya samu abin da ya
dace, to da tabbas a irin ƙwaƙwalwarsa, da wataƙila shi ne a kujerata, ya zama
matashi mafi ƙarancin shekaru da ya riƙe rundunar tsaro ta Nigeria, na yaba da
basirarsa nesa ba kusa ba"
Nabila ta ji daɗin yabon da Viper ya samu, bakinta har
kunne, bayan fitarsu ba ta san lokacin da ta rungume shi ba, tana ta yi wa
Allah godiya.
Ta ce "Ka ga abin da na gaya maka ko? Dama lokuta da
dama, Allah yana jarraba bawansa, kafin ya yi masa wata baiwa, Alhamdilillah
ala kulli halin, Allah ya ƙara ɗaukaka Vi"
Murmushi kawai ya yi mata, shi dai baya fatan ace za ayi
masa wani babban matsayi, saboda yana da 'yan adawa a cikin jami'an tsaron,
gani suke kamar akwai wani fifiko na musamman da ake ba shi.
Bayan tafiyar baƙin, shugaban sojojin yake cewa kankarofi,
yana yi wa Nabila kallon sani, tana kama da wani tsohon ubnagidansa a sojoji,
major Yusuf maitama.
Kankarofi ya ce "Ai 'yar sa ce"
Ya ce "In dai jarumta ce da taurin zuciya, ba ta yar a
ƙasa ba"
Minista ya ce yana son a saka sunan Viper, cikin sabbin naɗe-naɗen
da za ayi na sojoji, a yi wa manyan ritire.
Shugaban ɓangaren su Viper ya ce "Amma sir, lokaci bai
yi ba ayi masa wannan muƙamin fa"
"Eh a banza ma, ana saka waɗanda ba su cancanta ba, dan
haka a saka mini sunansa, dan ya cancanta" ya ja bakinsa ya tsuke, domin
kuwa kujerar da za a ɗora Viper, daga ita sai tasa.
A daddafe Viper yayi kwana tara, ranar na goma ya ce a
gidansa zai kwana, ya din ga zuwa dressing ɗin, ya gaji da zaman Asibiti.
Nabila ma ta ji daɗin hakan, dan kuwa ta gaji da sintirin
nan, babu wanda suka gayawa halin da ake ciki, a 'yan uwa, duk Major ya samu
labari, ya kira Viper ya din ga faɗa a kan meyasa ba su faɗa ba, Nabila ta kaee
shi, ta ce masa basa son tayar wa mutane hankali ne.
Allah ya taimake su, an daƙile yaɗuwar labarin ƙaryar cewar
Viper ɗan ta'adda ne.
Nabila tana ta yi wa Viper santin gidan, ɗan ƙarami mai
kyau, hafsa har gidan ta rakata, ta tayata suka yi 'yan gyare-gyare, komai
akwai a gidan na furnitures da na buƙatu.
Sai dai komai na maza ne, sai da hafsa ta tafi gida, ta aiko
mata da wasu abubuwan.
Nabila tana ta tsokanarsa, wai gidan gwauro.
Ya kalleta ya ce "Gidan gwauro ko, zaki ga gidan
gwauro, yau zan mayar da shi na magidanci"
Sai kuma tayi ɗif, ta sha jinin jikinta.
*GA MASU JIRAN DOCUMENT, ZA SU IYA PAYMENT YANZU, FEW PAGES
YA RAGE, ONGOING PAGES NE 500 COMPLETE DOCUMENT KUMA 1K. VIA 0009450228
AISHA ADAM JAIZ BANK
SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143
Ayshercool
08081012143
Ayshercool
08081012143
Wani irin miskilin murmushi yayi, tare da gyara zamansa a
kan doguwar kujera.
Nabila ta ɗan saki jikinta, duba da yadda haryanzu hannunsa
da saura, bai gama warkewa ba, amma ya ci gaba da yi mata wani irin murmushi da
shikaɗai ya san ma'anarsa, ƙarshe jikinta ya koma zauna tare da kwantar da
kansa a jikinta.
Suna yin sallar isha'i Nabila ta sulale daga parlour ta
shiga ɗaya daga cikin bedrooms ɗin gidan, don ta ga al'amuran na Viper yau suna
ƙoƙarin girmar tunaninta.
Ajiyar zuciya ta sauke cikin mayar da numfashi tare da bin
jikinta da ke ƙamshinsa da kallo, guntun murmushi ta yi ta shige toilet, bayan
ta yi wanka ta ɗauro towel ta sanya hijjabi ta fito, ta ɗauko kayan da Hafsah
ta aiko mata da su.
Kayan turarurruka ne, masu ƙamshin gaske, da kayan wurin
maman dr., Dan tana ɗagawa, taga sticker jikinsu.
Kiran hafsa ta yi a waya, hafsa ta ɗaga tare da faɗin
"Nabilatu, ya kawo miki kayan?"
"Wannan kayan watsewar waye zai yi amfani da su?"
"Ke mana, malama ki yi abin da ya dace please, a sha
amarci lafiya" ta katse wayar tana murmushi.
Nabila ta girgiza kai, ta ci gaba da dudduba kayan,
kasancewar ba a shirye ta taho Abuja ba, hafsa duk ta haɗo mata kayan sakawa da
na bacci.
Humra kawai ta ɗauka saboda yadda ƙamshinta ya daki hancinta
tun kafin ta buɗe murfin, ta ɗaga hijab ɗin ta shafe jikinta da ita tana lumshe
ido saboda daɗin ƙamshin kamar ƙara shi ake, sassanya ƙamshi ne, mai ratsa
zuciya. Lokaci ɗaya ɗakin ya buɗaɗe gabaɗaya da ƙamshin.
Tana ɗaga ɓingilallun kayan baccin da Hafsan ta haɗo mata da
su Viper ya turo ƙofa ya shigo, da sauri ta yi ƙasa da kayan cikin faɗuwar gaba
tana ɓoyewa kamar mara gaskiya, a hanzarce ta fara mayar wa cikin jakar
da ta ciro su, a ranta tana faɗin. 'Wa zai saka wannan abun kamar matacin
koko?.'
Bai ce mata komai ba ya jingina a jikin ƙofa tare da zuba wa
bayanta ido, kasa juyowa ta yi ta fuskance shi, saboda wata irin kunya da
tsoron shi da suke ƙara cika mata zuciya.
A hankali ya taka ya ƙarasa inda take ya tsugunna a daf da
ita, yana jin yadda ƙamshinta yake ƙoƙarin zauta shi, lumshe idonsa ya yi cikin
wata irin murya da ba ta san yana da ita ba ya ce. "Haka ake jinya da ma a
tafi a bar mara lafiya shi kaɗai?" Kanta a ƙasa ta ce. "To ai na ga
ka warke, kuma ni bacci nake ji, tun da na zo Abuja ban yi isashshen bacci
ba." Shirun da ta ji bai kuma magana ba ya sa ta ɗaga kai ta kalle shi,
wani irin kallo da ya burkita mata zuciya ta ga yana bin ta da shi wanda ya sa
ta ji wani bakon al'amari a jikinta. Ƙoƙarin janye idonta ta yi amma ya hana
ta, ta hanyar kama haɓarta ya ɗaga fuskarta tare da saka idanunsa da suka
ƙanƙance a cikin nata.
Ba za ta iya jure tasirin abubuwan da take gani daga
idanunsa suna shiga cikin nata ba, hakan ya sa ta lumshe natan da sauri tare da
ƙoƙarin ƙwace fuskarta.
"Ina Ablata mai tsiwa ta tafi ne?"
Ya faɗa yana ƙara matsar da fuskarsa daf da tata.
A ruɗe ta janye jikinta baya, kamar za ta yi kuka ta ce.
"Ban da lafiya ni fa, kuma na faɗa maka bacci nake ji, haba Vi."
Guntun murmushi ya yi ya zauna da kyau a kusa da ita har jikinsu na gogar na
juna, idanunsa akan ƙirjinta da ke ɗagawa saboda bugun da zuciyarta take yi
mata ya ce. "Faɗa mini me kike tsoro ne? Ni ban gane firgicin duk na mene
ne ba fa?" Baki ta tura masa cikin kunya ba ta ce komai ba.
Ɗanyatsansa ya saka ya fara zagaye lip ɗinta da su, tsit ta
yi ba ta hana shi ba sai ma lumshe ido da ta yi, a hankali ya kwantar da kanta
akan kafaɗarsa mara ciwon, tare da saka hannu ya zagaye ƙugunta da shi.
Bakinsa ya kai kunnenta kamar mai raɗa ya ce. "Uhmmm,
ƙamshin nan daɗi, kamar na dawwama ina shaƙar shi." Ya ƙarashe maganar
yana shinshina wuyanta ta jikin hijjabin. Da sauri ta ture shi ganin yana
ƙoƙarin ɗaga hijab ɗin jikinta, ga shi babu komai a jikinta sai towel, shi ma
tana ji ya kunce ɗazu, hijab ɗin ne kawai rufin asirinta ga shi yana ƙoƙarin
bankaɗa mata shi.
Kara naniƙar ta ya yi yana sassauke mata numfashi a fuska,
gabaɗaya ya burkice mata kamar ba shi ba, ko son kallon fuskarsa ba ta yi
saboda yadda idanunsa suka canza kala, ta lura kuma ƙamshin jikinta ne ya ƙara
tunzura shi, ganin yana ƙoƙarin wuce gona da iri ta danne tarin tsoron da ke
ranta don ta alamar sai ta haɗa da dabara za ta samu ta ƙwaci kanta, cikin
kulawa ta ce.
"Vi"
"Uhmm.."
Ya amsa mata a ƙasan maƙoshi.
"Magungunanka fa, na san ba ka sha ba, kar lokaci ya
ƙure."
Bai ce komai ba ya zare jikinsa a hankali ya kwanta a kan
carpet ɗin da suke kai yana mayar da numfashi, wani irin yanayi yake ji da zai
iya cewa rabonsa da shi, tun lokacin babyn robarsa, yadda jikinta yake rawa ne
kawai ya sa ya ƙyale ta.
"Ka tashi mu je ka sha." Ta faɗa a shagwaɓe.
Kallon ta ya yi, da sauri ta yi ƙasa da kanta.
"Magani ba zai yi mini maganin abin da yake damuna ba,
don haka yau ba zan sha magani ba, fanka nake so." Ya faɗa a sanyaye kamar
wanda aka yiwa duka.
Da mamaki ta ce. "Fanka kuma?" Gyaɗa mata kai ya
yi tare da lumshe idonsa.
"Ina jin zafi sosai."
Ya faɗa ƙasa-ƙasa yana lumshe ido.
Cikin rashin fahimta ta ce. "Wai wacce fanka kake
magana ne, bayan ga A.C "
"Taki kawai nake son sha, za ki ba ni?"
Ya sake faɗa tare da ɗage mata gira.
Ta jinjina masa kai cikin wasi-wasi, dan ba ta san meyake
nufi ba.
"Kin tabbatar Abla?" Ya ƙara tambayar ta. Ta ɗaga
masa kai, kamar ƙadangaruwa.
Tashi zaune ya yi yana ci gaba da bin ta da kallon da ba ta
so ya ce. "Na gaji da ganin wannan abun, ina ta son na cire kuma kin hana
ni, ki cire da kanki." Yayi maganar yana nuna mata hijjabin jikinta.
Ƙara tukukuye shi a jikinta ta yi ta ce. "Ina ruwanka
da abuna, don Allah ka koma ɗakinka ka bar ni na yi baccina."
"Ni ko nake da ruwa da shi tunda ya hana ni rawar gaban
hantsi. Ni yaushe ma ki ka fara saka hijjabi ne abla, haka ki ke yawonki fa
da"
Waro ido ta yi ta ce "Haba Vi, wannan shaidar zaka yi
mini, wallahi ka san dama can ina saka hijjabi, idan ba dogwayen riguna ba, ina
saka hijjabi.
"To na ji, amma yanzu cire wannan"
Ba ta kula shi ta miƙe da sauri tana riƙe towel ɗin ta nufi
hanyar toilet, shi ma bai kuma magana ba ya tashi ya fice.
Dafe ƙirji ta yi tana sakin ajiyar zuciya, tambayar kanta ta
shiga yi anya kuwa wannan viper ɗin da ta sani ne? Gabaɗaya ya canza mata,
kamar ba shi ne mai wannan muzuran da tsare gida ba, ga shi sai wani narke mata
yake kamar wani jariri, kallon hannunta da ya dinga jagwalgwalawa ta yi tare da
sakin murmushi, kamar har yanzu yana cikin nasa haka take ji.
"I love you so much my Vi." Ta furta a
hankali, ashe duk wannan maziyar ya iya kalamai da tausasawa haka?
Ta faɗa tana ɗora hannun a kan ƙirjinta tare da lumshe ido,
tana jin yadda zuciyarta take bugawa.
Gudun kar ya ƙara dawowa ya same ta a haka ya sa ta fita ta
shirya cikin wata doguwar riga a cikin kayan mara nauyi, don ba za ta iya
saka ɗaya rigar ba.
A zaman jinyar shi da ta yi sun ƙara shaƙuwa sosai, kuma ta
rage jin kunyar shi, amma a yau da suka dawo gida za su kwana su kaɗai sai
komai ya dawo mata sabo fil, musamman yadda yake ta rawar ƙafa a kanta, ta san
mai ƙwatar ta sai Allah, dan ta fara ganin saɓanin abin da take tunani. Har za
ta kwanta sai ta fasa ta zura hijabi ta fita parlour, ta san bai sha
magungunansa ba, kuma idan ba ita ta ba shi ba bai zama lallai ya sha ba, dan
tun da Allah ya sa ya daina shan ƙwayoyi, yake adawa da su, ko da kuwa ba shi
da lafiya ne, ko warin magani ba ya so.
Tana fita shi ma yana fitowa daga ɗakin da yake facing nata,
da sauri ta juya masa baya ganin daga shi sai gajeren wando ko singlet babu a
jikinsa. Jin takunsa yana nufo ta ya sa ta yi ƙoƙarin komawa ɗakin a hanzarce,
amma haƙanta bai cimma ruwa ba don cak ta ji ya ɗaga ta bayan ya damƙe ta. A ɗimauce
tana zaro ido ta ce. "Na shiga uku! Don Allah ka yi haƙuri ka sauke ni, ka
ga ba ka da lafiya kar ka fama ciwonka." Bai ce mata komai ba ya fara
tafiya, ba ta da zaɓi wanda ya wuce ta riƙe shi don kar ta faɗi, hannunta ta
sakala ta wuyansa ta zagaye bayansa da shi ta ƙanƙame shi, kamar bai ɗauki
komai ba.
A tsakiyar parlourn ya zaunar da su tare da faɗin. "Ana
so ana kaiwa kasuwa." Ɓata fuska ta yi tare da kawar da kanta ta ce.
"Please Vi ka je ka saka riga kar sanyi ya shige ka." Karan hancinta
ya ja tare da faɗin. "Na faɗa miki ni zafi nake ji, kin ƙi mun maganinsa
ke kuma." A shagwaɓe ta ce. "To ai ni ban san wane irin zafi ne
wannan ba, ga sanyin A.C amma idan kana so sai na yi maka firfita har ka yi
bacci, ka yarda?" Gyaɗa mata kai ya yi tare da janyo ledar da ke gabansa,
har lokacin tana jikinsa ya ƙi barin ta, ta tashi kamar yadda take ta ƙoƙari.
Tun kafin ya buɗe ƙamshin ya daki hancinta, ya ware ya ɗauko yankan naman kazar
ɗaya ya kai bakinta tare da faɗin. "Yau da kaina zan ba ki, tunda wancan
karon ƙin ci ki ka yi, saboda ba kya so na, yanzu kuwa tun da zan kwana ina
shan iskar fifitar da za ki mun, sai na baki da kaina." Murmushi ta yi
cikin mamakin sabuwar lallaɓawar da yake yi mata ta buɗe bakin ya zira mata.
Shi ya yi ta ba ta a baki har ta ƙoshi, da ta ce ya ci sai
ya ƙi ya ce shi ya ƙoshi, da ma tata ce ya siyo mata. Wani kallo ta yi masa ta
ce. "Yaushe ma ka fita ka siyo?" Ya ce. "Order na yi aka kawo
har gida." Ba ta kuma magana ba ta tattara ragowar ta kai kitchen, ta dawo
ta gyara gurin.
Har lokacin yana zaune yana ta aikin kallon ta tana ta fama
da hijabi, kamar mai takaba.
So take ta gudu ɗaki ta bar shi amma zuciyarta ta ƙi yarda
da hakan, musamman a halin da yake ciki na rashin lafiya. Kusa da shi ya nuna
mata ya ce ta zauna su yi magana, ba ta yi musu ba ta zauna, tare da tattara
hankalinta wuri guda.
"Wai wannan hijabin na mene kamar wata mai
takaba?"
Ido ta juya masa ta ce. "Sanyi nake ji ne."
"Ni ina jin zafi ke kuma kina jin sanyi, sammun naki na
sammiki nawa sai duk mu daina ji." Ya yi maganar tare da cire hijabin ya
ajiye a gefe. Dogon gashinta ya bayyana kasancewar babu dankwali a kanta.
Idanunsa akan inda ya fi yawan takurawa da kallo a jikinta ya kai hannunsa ya
fara shafa gashin a hankali, yadda gashin jauhar yake, mara yawa sai tsayi haka
na Nabila yake, kuma ba baƙi ne ƙirin ba. Da sauri ta juya masa baya ta ce.
"Ka daina ba ni kunya don Allah."
Ya ce "Ni fa ba wannan Nabilar na sani ba, a dawo mini
da ta bayana mara tsoro da kunya, mai kallon cikin idanuwana, tana gasa mini
magana yadda ta ga dama." Ya faɗa yana leƙa fuskarta.
Cikin rigima ta ce. "Kana nufin ban da kunya kenan ni
mara kunya ce?"
Hannunsa ya zura a inda ba ta taɓa tsammani ba ya ce.
"Mara kunyar dai nake son ki zama." Cikin ƙunƙuni na ce. "Kamar
yadda ka zama ba."
"Oush!" Ya faɗa yana yarfe hannuwa.
"Mene ne? Me ya faru?" Kafaɗarsa ya nuna mata bai ce komai ba.
A ruɗe ta ce. "Ciwo take maka? Ko ka fama ciwon
ne?" Yamutsa fuska ya yi ya ce. "Har cikin ma duk suna mun
ciwo." Yayi maganar yana nuna side ɗin cikin sa na dama.
Ba ta san lokacin da ta janyo shi jikinta ta fara shafa
fatar bayansa cikin rarrashi ba, kamar za ta yi kuka ta ce. "Sannu, ko mu
koma asibitin ne? Dama fa baka gama samun sauƙi ba ka ce, sai mun dawo
gida" Girgiza mata kai ya yi yana ƙara shigewa jikinta. Cikin kulawa da
tausayawa ta shafa kansa ta ce. "Bari na ɗauko magungunan ka sha to, sai
mu je ka kwanta."
Kamar ƙwai haka ta dinga lallaɓa shi, shi kuma yana ƙara
narkewa kamar gaske, ya ce mata nan da zafi can yana yi masa ciwo, har da
hawayenta saboda tausayin shi.
Tare suka koma ɗakinta yana manne da ita, ta buɗe jakarta,
ta ɗaukko ledar magungunan, ta din ga bashi ɗaya bayan ɗaya yana sha yana
yamutsa fuska, ta rage haske ta lulluɓa masa bargon da yake kan gadon. Sai
sannu take yi masa duk ta ruɗa kanta, ko kadan tunaninta bai kawo wayo yake yi
mata ba, saboda duk lokacin da aka buɗe raunin za ayi masa dressing sai ta
tausaya masa, saboda ramin da wurin yayi.
Sai da ta gama raɓe-raɓenta, ta din ga kai komo tsakanin ɗakin
da falo, sai da tayi tunanin ya yi bacci, sannan taje ta raɓa ta kwanta, kamar
mai hawa kan wuta, cike da matsanancin tsoro.
Shikam idonsa biyu, sai da ya tabbatar ta saki jikinta sosai
yadda yake so sannan ya fara gudanar da ƙudurinsa. A firgice ta janye jikinta
daga nasa, cikin rawar murya ta ce. "Vi rashin lafiyar kenan? Kana buƙatar
bacci, ka kwanta ka yi Please." Ƙara janyo ta ya yi cikin wata irin murya
ya ce. "Ni fa na warke, taki rashin lafiyar kawai nake yi." A tsorace
na ce. "To ni ban da lafiyar ka ƙyale ni."
"A'a Abla, kar mu yi haka da ke, kar ki yi mini haka,
kwana talatin da wani abu da aurenmu, kar mu yi haka da ke please"
Cikin rauni da tsoro ta ce "Ni dai a'a bana so."
Ta faɗa cikin kuka, don sosai wani irin tsoro yake ƙara lulluɓe ta.
Tsayawa ya yi da abin da yake ya mayar da bakinsa kan
kunnenta ya shiga hura mata iska, a hankali ta ji ta fara samun nutsuwa, ajiyar
zuciya ta sauke ta koma hannunsa ta riƙe.
Jauhar ce ta shiga kai komo a cikin kwanyarsa, baiwar Allah
babu sawa babu fitarwa, babu gardamar tsiya kamar Nabila.
"Abla" ya kira sunanta a hankali.
"Na'am"
"Amma ina alkawarin firfitar?"
Ta ce"Yana nan, sai ka yi bacci zan yi maka."
"Ba zan iya baccin ba ai"
Juyawa ta yi suna kallon juna ta ce. "Wai wacce irin
iska ce wannan, ni fa kana ta sa ni a duhu." Yana shafa gefen wuyanta ya
ce. "Shi yasa nake so na fito da ke haske amma kin ƙi.
"Vi"
"Mmm"
"Dan Allah ka yi haƙuri, ka ga ni marainiya ce"
Ya ce "Menene haɗin aurena da maraicinki, nima marayan
ne ai, sai fa na dangana da birnin tarayya"
"Wace birnin tarayyar kuma?"
Duk yadda ta so ƙwace kanta amma ta kasa, bisa tilas ta
haƙura ta bar shi ya yi yadda yake so.
Sai dai jin abun nasa na gaske ne ya sa ta dawo hayyacinta
ta saka masa kuka tare da doguwar magiya kamar wanda zai zari ranta.
Fuskarta da ta yi kaca-kaca da hawaye ya ƙura wa ido ta ɗan
gutun hasken da ya rage a ɗakin yana jinjina taurin kai da tarin rigimarta,
Jauhar ɗinsa mai sauƙin kai ce ta faɗo masa a rai, salihar baiwa kenan da sauri
ya kawar da tunaninta, saboda alƙawarin da ya daukar wa kansa a wannan fagen ba
zai taɓa yi wa Nabila maganarta ko ya yabe ta ba, a karan kansa ya ji duk da
ƴar'uwarta ce amma ba za ta taɓa jin daɗi ba idan ya aikata hakan. Ba ya kuma
so ta dinga jin haushin ta ko ta dinga kishinta kamar yadda ta ce masa yana
sakawa ta ji a ranta. Amma da tabbas sai ya furta, ya yabawa yar madara.
Duk iya ƙoƙarinsa na ganin ya riƙe kansa amma ya kasa,
juriyar da ya yi shekaru yana yi ya kasa yin ta a dare ɗaya, sosai yake da
buƙatar iskar da ya yi shekaru bai shaƙe ta ba.
Sai da ya samu ɗin kuwa a daren ya samu sukuni, abin ya zo
wa uwar gayyar a bazata.
Ƙarshen gadon ta koma tana sheshaheƙar kuka tare da takure
kanta guri ɗaya, shiru ya yi yana sauraren ta, bai yi yunƙurin rarrashin ta ba.
Yadda ya tsallake Jauhar, bayan ya gama abin da Allah ya
nufe shi da yi, saboda wata banzar poster indabo, Walid ya tafi neman magana,
sai wani takaici ya mamaye zuciyar sa.
Wai yau shi ne zai je shimfiɗar aurensa, ya ɗauki wanka ya
sha turare.
Wanda lokacin 'yar madara, wata ran da ƙaurin hayaƙinsa da
komai idan ya dawo daga gantalinsa, komai dare wataran ma a buge, haka zai haye
mata gado yana basarwa, shi a yi abin da yake so kawai. Daga baya sai ta dinga
zama sai ta jira shi ya gama yawon ya dawo, ta lallaɓa shi cikin hikima, ta ce
ita zai yi wa wankan, tun da ita ta saba wanka ba yau ba gobe kamar macen
kunkuru kamar yadda yake faɗa.
Da haka zata lallaɓa shi, su yi brush ayi wanka a shafa
turare, daga nan idan tana da wani ɗan abin kusa da bakan ta bashi, ba ta taɓa
yi masa magana ba, a hankali kuma ya gane yake jin daɗin hakan, ya zamana ko ba
ta saka shi ba, zai yi abin sa ya shafa turare sannan ya zo in da take.
Duk ranar da ta hana shi shan wani abu, ya je ya sha, sai ta
sunsuna bakinsa, idan ta ji ƙauri, ranar ba zata saurare shi ba, sai dai yayi
raragefensa ya gama. Jauhar ita ta mayar da shi ɗan gayu.
Kukan Abla ne ya dawo da shi hayyacinsa, da ta shafe lokaci
tana yi, ba tare da ta gaji ba.
Ya mirgina kusa da ita ya yi ƙasa da bargon da ta lulluɓa
har kanta. Cikin wani irin nishaɗi da ya cika masa zuciya haɗe da alhini ya ce.
"Ablan Vi." Yadda ya yi maganar ya sa ta hadiye sauran kukan nata na
zallar shagwaɓa ba tare da ta shirya ba.
"Kukan ya isa haka idan kuma ba ki gaji ba to."
Ya faɗa yana kwantar da kanta a kan ƙirjinsa, tare da
bubbuga bayanta cikin rarrashi.
Baki ta tura tare da ƙara shigewa jikinsa tana sauke ajiyar
zuciya, rarrashin take buƙata da ma.
Tarairaya da kulawa kala-kala ya dinga nuna mata a daren
tare da wata irin soyayya mai tsayawa a rai da wuyar mantawa, ita kuma ta dinga
yi masa taɓara iri-iri.
Bayan sun yi wanka ta koma bacci, shi kuma ya jima ya kasa
baccin, ya din ga jin tamkar ya aikata wani zunubi mai nauyin gaske, yau shi ne
da wata macen daban, ba 'yar madararsa ba.
Duk zalama da ƙulafucin namiji da mace sama da ɗaya, bai taɓa
jin haɗa jauhar da wata mace ba, amma Nabila wani sashi ce na jauhar, shiyasa
ya bata wani gurbi a zuciyarsa, son Nabila son Jauhar ne, duk da ba ta raye.
Tabbas ya san ban da Nabila ya aura, babu wata mace da zata
iya zama da shi, a hakan ma ya san Nabila na matuƙar ƙoƙarin yaƙi da zuciyarta
a kan Jauhar, shi dai duk wanda zai zauna da shi, to dole ya so Jauhar, ko su
raba gari, haryanzu babu mace mafi ƙololuwar daraja a ransa bayan mahaifiyarsa
sai jauhar, ko mahaifiyarsa, ba ta yi masa tarbiyyar da jauhar ta yi masa ba.
A hankali ya furta "I miss you 'yar madara, may your
gentle soul, rest in jannatul firdausi, may Allah subhanahu wata'ala grant you
a highest rank in Janna" ya furta a hankali yana dafe saitin zuciyarsa,
kamar yadda ya kan faru mafi yawan lokuta idan har ya tuna ta.
Ganin ya kasa baccin, ya sanya ya tashi ya sake ɗauro alwala
ya koma ɗaya ɗakin ya tayar da salla.
Ya daɗe a sujuda, kawai yana nema mata gafarar Allah da
rahamarsa, bai gushe ba idanunsa na zubar da hawaye, alkhairanta, na ci gaba da
kai komo a cikin zuciyarsa.
Sai da ya idar ya gabatar da sauran addu'oi, na neman tsari,
da fatan zaman lafiya da kwanciyar hankali a musayar da Allah ya yi masa.
Ya idar yayi shiru a kan dardumar, yana tunanin Jauhar kamar
wata walƙiya ce, ko flashing da ta shigo rayuwarsa, dan kawai ta haska masa
wasu abubuwa ta ɓace.
Ya daɗe a zaune, sannan ya tashi ya koma ɗaki ya kwanta.
Sai daf da Asuba bacci ya ɗauke shi, mafarki yayi gashi
zaune a falo, Nabila na kujerar da take facing ɗin sa, suna ta hira cikin nishaɗi,
sai ga Jauhar ta shigo, tana ta ƙamshin turaren da duk in da ya ji shi, sai ya
yi tunanin zai ganta.
Ta zuba musu ruwa a kofuna, ta zauna a kusa da Nabila, tana
kallon yadda Nabila ke magana cikin nishaɗi.
Murmushi take yi tana kallon Nabila, shi kuma yayi shiru
yana bin Jauhar da kallo.
Da alama Nabila ba ta ganin Jauhar, amma jauhar sai kallon
Nabilan take tana murmushi, alamar tana jin daɗin yadda Nabila ke cikin fara'a.
Viper take nuna wa Nabila tana murmushi.
"Vi an kusa idar da salla fa" muryar Nabila ta
tashe shi.
A gida ya yi sallar asuba saboda ya makara, ita kuwa da ƙyar
ya samu ta tashi ta yi sallar ta koma bacci.
Shi ma baccin yayi, saboda jiya bai samu isasshen bacci ba.
Naja'atu Bunkure kuwa tuni ta gurfana a gaban kuliya, bisa
tarin zarge-zarge da ake yi mata. Ba ita kaɗai ba har da wasu daga cikin
maƙarabbanta, da suka din ga gudanar da bunkure foundation.
Ta musanta tuhume-tuhumen da aka yi mata, kuma lauyoyinta
suka nemi a bayar da belinta, amma fafur alƙalin nan yaƙi, ya aike da ita gidan
gyaran tarbiyya da kuma gyaran hali, wato gidan yari.
Abin ya girmameta, tamkar zata zare ta haukace, wai yau ita
ce, da ikonta da izzarta, aka aike da ita gidan kurku.
Babu alamar Indabo zai zo ya fitar da ita, haka aka sakata a
cikin masu laifi.
Kamar mahaukaciya haka ta zama, tana tuna irin furucin da
Nabila ta yi mata, ta tabbata sai da ta kaita ƙasa ta ga bayanta tukuna.
Wani irin abu mai tsananin ɗaci ta haɗiye ta ce
"Kuskure mafi girma da muni, da Indabo zai tafka, shi ne watsar da ni ya
wanke kansa, ya zame ya bar ni. Wallahi muddin haka ta tabatta, ko kurkukun
bayan duniya aka kai ni, sai na yi maganinsa, ni zan kawo ƙarshen sa, ƙarshe
mai muni da ban tsoro, ni ce dai-dai da kai Indabo, mu zuba mu gani, sai dai
ayi mutuwar kasko".
Nabila ta riga Viper tashi, ta tafi ɗaya ɗakin, tayi wanka,
dan kar ta dame shi da ɓuruntu ya tashi.
Ta shiga kitchen ta duba abin da yake akwai na girki, ta
fara ƙoƙarin sarrafawa, ta dawo falo ta cigaba da karkaɗe karkaɗe.
Ta gama ta koma ɗaya bedroom ɗin, shi ma tana sake gyarawa,
a nan ta ci karo da manyan frames, na hoton Viper da jauhar.
A hankali ta ɗauki ɗaya daga ciki tana gogewa, babu wanda
zai ce ba ita ce a jiki ba.
Ta zubawa hoton ido, har ya shigo ba ta sani ba, sai daga
baya ta razana jin motsi a bayanta.
"Me ki ke yi da wannan hoton, ki kula kar ki fasa mini
hoto"
A sanyaye ta ce "Kallonta kawai nake yi"
"Ki na sonta ne" da sauri ta kalleshi ta ce
"So kai, wallahi har cikin zuciyata nake jin matsananciyar ƙaunarta,
haryanzu ina jin zafi da ɗacin rashin saninta a rayuwata, da tare muka tashi
babu lallai na zama masifaffiya ko?" Tayi maganar tana kallonsa.
Dariya ya yi ya ce "Ai ke faɗa da tsiwa a jininki yake,
ita kuma wannan haƙuri da kawaici ne a jininta, amma da ni da ita wa ki ka fi
so?"
Ta nuna masa hoton jauhar, ya saka hannu ya karɓi hoton ya
ce "Nima ita na fi so"
A sanyaye ta ce "Ko baka faɗa ba na sani, amma Vi dan
Allah ba cin amana ne abin nan ba, haryanzu na kasa samun nutsuwa da auren nan,
idan ina tuna wahalar da ta sha, sai na ga kamar na ci amanarta, da na fara
sonka har na aureka" ta yi maganar idanunta na cika da hawaye.
Ya rungumota jikinsa ya ce "Idan mafarkin da nayi
gaskiya ne, to Jauhar tana murna da aurena da ke, kuma ta ji daɗin ganinki
cikin farinciki"
"Vi"
"Mmm"
"Na san ba zan iya zama jauhar ba, ba kuma zan taɓa
kamota ba, ba zan taɓa haɗa matsayina da nata a wurnka ba, amma dan Allah ko
babu yawa ka sama mini space a zuciyarka, kar maraicin yayi mini yawa"
Wani irin tausayinta ya mamaye zuciyar sa ya ce "Ki na
da naki space ɗin, ba zan bari maraici ya ci gaba da damunki ba, zan yi
occupying spaces ɗin da suke cikin rayuwarki in sha Allah my abla"
A hankali ta yi ajiyar zuciya ta ce "Na gode sosai da
sosai Vi, Allah ya bamu zaman lafiya"
Ya ce "Amin, yauwwa yakamata na yi comment akan fankar
jiya, ita ma sanyinta ya yi, ba mai cutarwa ba ne ba"
Ƙwacewa ta yi daga jikinsa ta ce "Kai ka san wata
fanka, dama abin da ka ke nufi kenan, ka ke gaya mini zafi ka ke ji kwanaki,
ko?" Ɗaga mata gira ɗaya ya yi yana murmushi.
Ta ce "Bari na duba girki"
Ya jinjina mata kai, ya sake ɗaga hoton Jauhar yana kallo,
daga bisani ya mayar da shi in da yake.
Suna karyawa yana tsokanarta, wai a ina ta iya girki har
haka, shi ya zata ba ta iya komai ba, kawai ajebo ce.
Dariya ta yi ta ce "Haba dai, boarding fa nayi har high
institution, ace ban iya girki ba, girki yana cikin abubuwan da sukan sakani
nishaɗi, da kuma kwalliya.
Abba ne baya son make up, girki kuma sai na ga ina so nake
yi, Abba ya hana sakani girki, idan ba ni na yi ra'ayi nayi ba"
"Yar gatan Abba, gaskiya yana ji da ke sosai, dama har
Jauhar shi ne ya riƙeta"
"Shi kansa ya yi wannan nadamar ai"
Ua jinjina kai ya ce "Maybe da shi ne ya riƙeta, da ba
zan santa ba, Allah dai ya riga ya gama tsara komai, hakan ma mun gode
masa"
Wayarsa ta fara ringing, ya ɗaga ganin lambar Abbu.
Suka gaisa, Abbu ya ce "Ina zamu yi, idan mun shigo
Abuja?"
"Wai zuwa za ku yi?"
"Eh zuwa za mu yi, tun da kai ba ka ga ya dace ka sanar
mana abin da ya faru ba"
"Abbu ka yi haƙuri, na yi hakan ne dan kar na ɗaga muku
hankali"
"Koma menene gamu a hanya dai"
"To bari na turo maka adress ɗin"
Ya sauke wayar ya ce "Wai su Abbu su na hanya, ko wa ya
gaya musu abin da ya faru, gashi an ta so su, next week na so mu koma gida
fa"
Nabila ta ce "Sai a ɗora girki, kafin su ƙaraso, amma
sai an yi cefane"
"Zaki iya kuwa, na ga jikin naki sai a hankali"
Murmushi kawai ta yi ta tashi tsaye, ta ce "Zan iya
mana"
*****
Wani irin gumi ne yake tsatsafowa Indabo, cikin hasala ya ce
"Wai wace irin Naja'atu kuma, ina ruwana da wata naja an kaita prison, iya
ruwa fid da kai kawai a wannan gaɓar.
Nan na ɓoyeta, na saka ake yi mata visa a ɓoye, ta bar ƙasar
amma abun bai yiwu ba, wannan jarabben yaron maye, ya kawo mana farmaki, gashi
gidan jaridar da aka bawa kwangilar yaɗa labarin, an maka su a kotu kuma tara
za a caje su mai yawan gaske. Ko dai mu biya musu, ko su tona mana asiri.
Gashi ba ni da tabbacin rundunar soja, za su ƙi faɗar
ainihin abin da ya faru, dan su wanke Viper, gashi ministan tsaro ɗan uwan
kankarofi ne, balle a sasanta komai yayi magana da su"
"Ka kwantar da hankalinka, zuwa jibi war haka, ka bar
ƙasar nan, kujerar sanatan ka haƙura, ace ka tafi neman lafiya, idan Allah ya
sa komai ya lafa sai ka dawo, koma ka yi zamanka a can".
Ayshercool
08081012143
*MASU JIRAN ƘARFE A WUTA COMPLETE DOCUMENT, ZA KU IYA
PAYMENT A YANZU, A CIKIN SATIN NAN ZAI KAMMALA 1K VIA 0009450228
AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143
Yakice gumi Indabo ya yi, yana jinjina kai cike da gamsuwa.
Zakiyya kuwa, hankalinta ya kwanta bayan ganin hafsa ta koma
gidan Alhaji mu'azzam, babu irin huɗubar tsiyar da ba ta yi mata ba kafin
auren. Ta koma ta sakankance, hafsa zata din ga dumbuzo abin da ta samu ta din
ga kai mata, domin kuwa har ta fara tsara irin rayuwar da za ta yi, a
matsayinta na surukar ƙaramin minista a Nigeria.
Babu irin huɗuba da dabarun ha'inci, da ba ta koyar da hafsa
ba, haka ba ta fasa shige-shige ba, cike da fatan a karon farko hafsa ta
haifo ɗa namiji, domin idan kankarofi ya mutu su samu dukiya, domin kuwa
yaransa mata ne. Amma tun da hafsa ta bar gidan, wata kusan shida, ko Kanon ma
ba ta tako ba, sisi ba ta turawa Zakiyya ba.
Ta din ga kiranta a waya, a kan ta aiko da kuɗi, a sake bi
mata malamai ayi maganin uwargidansa, kuma a kama mata shi, amma ta ce ita baya
bata ko sisi.
Hafsa ta sanya wa ranta, a wannan karon ba zata yi asarar kuɗinta
ba, babu wani mushiriki da zai sake cin sisinta, saboda ta mallake Alhaji
mu'azzam.
Ta yi amfani da shawarar Jauhar, da ta bata tun tana raye,
ta kama addu'a, da miƙawa Ubangiji lamarinta, tare da yi masa biyayya dai-dai
iyawarta, sai kuma uwa uba gyara da take yi, yadda yakamata ba tare da ta yi
abin da zai cutar da lafiyarta ko imaninta ba.
Sai dai mai rai ba a rasa shi da motsi, duk da irin kula da
tattalin da Alhaji mu'zzam yake yi mata, ba shi da isashshen lokacinta, kuma
har zuwa yanzu ya kan bi abin da matarsa uwargidansa take so, bai fiye son ɓata
mata ba, gashi kusan kowane lokaci cikin aiki yake ba shi da lokaci.
A wannan karon ba ta yi yinƙurin yin fito na fito da
uwargidansa ba, dan taga alamar baya son hakan, kuma ita rayuwa yar siyasa ce,
a gabansa babu abin da ya yi mata zafi, da ko sako zancen matar, a bayan idonsa
kuwa ba ta jurewa idan ta kira ko ta yi yinƙurin ci mata mutunci.
Kuma dai-dai gwargwado kankarofi yana sakar mata kuɗi tayi
yadda take so, ko kyauta zata yi a gidansu, Baba take aikawa kuɗi, ta san koba
komai kowa zai amfana a kan ace Anty kawai take bawa, dan ta san ƙarshen kuɗin
a yawon bin bokaye zai ƙare.
Daf da azahar su Abbu suka iso gidan su Nabila, kafin nan
tuni ta kammala abincin karɓar su.
Abbu ne da Baba da kuma Major suka zo tare.
Nabila ta yi farin cikin zuwansu sosai da sosai, sai dai
Major yayi ta faɗa a kan yadda ba su faɗi abin da ya faru ba.
Major kawai kallon Nabila yake yi, yadda ta fututtuke da ba
ta son auren, amma tayi ƙalau da ita.
Sun daɗe a gidan, sai da Major ya zaga a cikin barrack ɗin,
suk sai juniors ɗin sa a aiki, duk sun yi retire.
Daga nan suka je gidan Alhaji mu'azzam, suka wurin hafsa,
ita ma kamar ta taka dan murna, iyaye akwai daɗi.
Sai dai ba su daɗe a gidan hafsa ba, saboda yamma suka kama
hanyar kano.
Nabila na kitchen tana ta ƙoƙarin yin wanke-wanke, Viper ya
shiga kitchen ɗin ya tarar da ita.
"Sannu"
Ta kalleshi ta ce "Yauwwa"
"Ki na iya aikin a haka?"
Ta ce "Eh mana, me ka gani?" Yayi murmushi ya ce
"Bakomai, dama dai shekaranjiya suka zo, yau na so nima na yi zaman jinya,
anyway sannu Abla, na so na yi appreciating iskar fankar jiya unfortunately....
Katse shi ta yi da "Ni dai na ga ta kaina da wannan
fankar"
Ya jingina da jikin bango, ya ce "Na yi ƙoƙari fa Abla,
shekara ta nawa ina zaune haka, kodaye ba na gane komai sai 'yan kwanakin
nan"
"Dan Allah vi ka ƙyale ni da zancen fankar nan"
Dariya ya yi ya ƙarasa kusa da ita, ya saka hannunsa a sink ɗin,
yana tayata wanke kwanukan.
****
Abdul shi yake kai Ramma makaranta, haka idan an tashi, idan
kuma yana da ayuuka da yawa da kanta take tafiya.
Mama sam ba ta son kaita makarantar nan da yake yi, tafi so
ta tare, saboda gudun abin da aka iya faruwa, dan haka ta ya tan kunnen ramma,
a kan lallai gara ta tare, can su ƙarata kar su ɗaukko mata magana a titi.
Allah ya taimaki Abdul, hankalin Indabo ba ya jikinsa, hatta
ita mahaifiyarsa ba ta cikin hayyacinta, amma shi sam hakan bai dame shi ba,
yadda zai gina rayuwarsa da ta rahama yake yi.
Surutun abin da ya faru da Bunkure kuwa, ya ci gaba da zaga
wa lungu da saƙo, gaba ɗaya mutane suka din ga Allah wadai da yadda ta daɗe
tana cutar jama'a.
Viper kuwa bai bari Nabila ta yi girki ba, ordern abinci ya
kuma yi musu, yana ta lallaɓata.
Bayan sallar isha'i, ya kira Walid, yayi sa'a kuwa ya ɗaga.
"Mai laya"
"Mai zamani, ya gida ya ƙanwata?"
Viper ya ce "Lafiya ƙalau, tun ɗazu nake kiranka, su
Abbu sun zo fa yau, har da sirikaina"
Walid ya ce "Kash, amma wallahi da na san za su zo,
biyo su zan yi"
"Ai gara da baka sani ɗin ba, ka zauna ka kula mini da
ƙanwata, tun la'asar na kiraka ai baka ɗaga ba"
"Sai magariba na ga missed call ɗin naka, muna asibiti
ne, Shahida ba ta jin daɗi tun asuba muke can, sai magariba muka dawo"
Viper ya ce "What? Muhsin haka muka yi da kai? Daga
aura maka yarnya ka haɗata da aiki, wane irin abu ne haka?"
Walid ya ce "Innalillahi me zamani meye haka wai? Fura
ta sha ta ɓata mata ciki, take ta amai da gudawa muka tafi asibiti fa"
"Ba wani nan, laulayi ne, matsalar aurawa tuzuru
yarinya kenan, gamo da kasawa sai wannan al'amari, to ni dai idan namji ne ayi
mini takwara"
Kashe wayar Walid ya yi, jin abin da Viper yake yi masa.
Nabila kuwa sai kallon Viper take yi, dama haka yake da
tsokana har haka, kuma yana yi yana wani mazewa, kamar ba daga bakinsa suke
fitowa ba.
Shahida kuwa dariya take yi wa Walid, yadda ya dage yana yi
wa Viper rantse-rantse.
"Wallahi my kana bani dariya, ya san kunya ka ke ji,
shiyasa yake yi maka wasu abubuwan, ka fiye kunya, ni har dariya ka ke
bani"
Yayi murmushi ya ce "Ai na fuskanci tsokanar ta wa yake
yi kawai"
"My ka san sai yanzu na san Yaya Al'amin yana wasa da
dariya, wallahi da ko kallona ba ya yi, ban taɓa zaton yana wasa da dariya
ba"
Walid ya yi murmushi, yana shafa gefen fuskarta, ya ce
"Ki daina tuna bayan nan, amma Viper mussaman lokacin marigayiyya, bayan
ta fara saita mu, yana wasa da dariya, kin san rayuwar ta mu ce, duk sai a
hankali sai godiyar Allah. To ya ki ke jin jikin naki yanzu?"
"Da sauƙi, amma ba zaka yi mini wayo ba, ni duk ka
daina jin kunyar tawa yanzu"
"Ai mai zamani gaskiya ya faɗa, da ya ce matsalar a ba
wa tuzuru aure kenan, bai iya cin ƙwan makauniya ba"
Tare suka yi dariya, cike da nishaɗi da jin daɗi.
Nabila kuwa ta ɗauka, yau za ta sake, ta samu isasshen
bacci, dan tun da ta fara jinyar Viper, ba ta samun bacci, ta zata ya samu abin
da yake so, zai bari yau ta yi bacci.
Amma sai ta riski abin da ba tayi tsammani ba, dan kusan
gara jiya da yau, dan jiyan ƙyaleta kawai ya yi, yadda yake nanata zancen
fankar nan, sai da ya tabattar mata da gaske tsawon lokacin da ya ɗauka, yana
zaune haka ya dame shi, dan ta gazgata yadda yake ba wa fanka muhimmanci.
Ɓangaren Abdallah Liti, barkwancinsa ya sanya yake da mutane
sosai a kasuwa, amma hakan bai hana shi yin faɗa da muzurai wasu lokutan a
kasuwar, dan ma idon Abbu yana hana shi yin wani abun.
Sai dai Abbu yana jin daɗin aiki da su sosai da sosai, ba su
da ƙyuya ko kaɗan, kuma ya sha jarraba amanar su, ba tare da sun sani ba, amma
ko kusa ko da wasa babu wanda ya taɓa yinƙurin cin amana.
Sai da ya ƙara dana sanin ɗaukar su Abba ya ɗora su a kan
harkokin sa, suka din ga ɗurka masa sata, suna cutarsa. Da su Al'amin ya riƙe,
da yanzu dukkanin su, sun tsaya da ƙafrsu.
Sai dai ya yanke shawarar zai tallafa musu sosai da sosai,
su tsaya da ƙafafuwan su, dan ya san bai isa ya biya su, wahalar da suka yi da ɗan
sa ba.
Samunsu a kasuwar, ya sanya wasu lokutan ko zuwa baya yi,
sai ya zauna a gida ya ɗan huta, ko yaje wasu sha'anunnunkan, za su kular masa
da komai babu cuta ko cutarwa.
Idan yana cikinsu, sai ka ɗauka shi ne ya haife su, har
shawara ya kan yi da su a kan harkar kasuwanci, bai yi da abokan sana'arsa ba,
saboda su ba za su cuce shi ba ko su yi masa hassada ba.
Abbun ne yake tsokanar liti ya ce "Abdallah, kai
haryanzu babu wadda ku ka daidaita ne? Su sun yi aure sun bar mini kai a haka
fisabilillahi, yakamata ka motsa kai ma na aurar da kai"
Liti ya ce "Ai abbu wadda nake so ɗin kamar tafi
ƙarfina, gani nake kamar ba za a bani ba" yayi maganar cikin damuwa.
Walid sai hararsa yake yi, yadda yake sakin jiki yayi hira
da Abbu shi ba ya iyawa.
Abbu ya ce "Haba dai, ni da ina da wata 'yar ai da na
baka, amma meyasa ka ce ta fi ƙarfinka?"
Jiki a sanyaye ya ce "To ai ana ganin ni ba mutumin
kirki bane ba, ba kowa zai iya jihadin da ka yi ba Abbu"
"In ji waye ya ce maka ba mutumin kirki ba? Wannan wani
abu ne da aka yi shi ya wuce, kuma yanzu Alhamdilillah, babu abin da za mu cewa
Allah sai godiya. Kuma gaka da sana'a ka shiryu yanzu ba kamar da ba, in sha
Allah za a baka, yar gidan waye idan ma baban naka ba zai tambayar maka ba, ni
sai na wuce maka gaba"
Liti ya ɗan yi shiru ya ce "Ƙanwar matar mai zamani ce,
wata Walida a gidan su take, 'yar major ce"
Abbu ya ce "Au to ashe ma 'yar gida ce, shi ne ka ke ta
damuwa"
"Ina jin tsoro ne, gani nake kamar ba zai bani ba, kuma
Walid ma cewa ya yi na nemi wata, ba lallai a bani wannan"
"Ita yarinyar kun daidaita? Kana zuwa wurinta ne?"
Ya jinjina masa kai alamar eh.
"An gama, ka fara tarin abin da ya sauwwaƙa ba zai
gagara ba in sha Allah" washe baki liti yayi cikin matsanancin farinciki,
Walid kuwa kamar ya mare shi, saboda ba ya jin kunya ko kaɗan yake wannan
maganganun da Abbu.
Shahida ta je har gida gaida Abbu, ta yi masa farfesun kaza,
taje gaishe shi, sai da ta tuna masa da jauhar, lokacin azumi ta saka Al'amin a
gaba suka zo musu sannu da shan ruwa.
Rahila kuwa, ko kallon kirki ba ta yi wa Shahida ba, duk
yadda shahidan ta din ga raɓarta, amma ta din ga hantararta, tana ƙarewa auren
zagi.
****
Viper har tausayin Nabila yake ji, domin yanzu zaman ɗari-ɗari
takeda shi, saboda yadda ya addabeta, har ta fara yi masa zancen, tun da ya ji
sauƙi, zata koma Kano, hutunta ya kusa ƙarewa, ya ce ba za ta koma ba, shi ma
an kusa sallamar shi, zai je hutu, sai su tafi tare.
Har murna take yi idan ya ɗan fita baya nan, ta samu ta ɗan
sake.
Da ya dawo kuwa ta shiga fargaba da tashin hankali.
Da safe wurin ƙarfe tara da mintuna, Viper ya zuba wa Nabila
ido da ta kasa tashi, take ta lumshe ido, alamar bacci bai isheta ba.
"Abla yau ba zamu karya bane ba? Yunwa nake ji fa"
Ta buɗe idonta da kyar, ta ce "Tun wurin 8 fa na tashi,
na yi niyyar ɗora breakfast ɗin, kai ka hana ni, kuma ga wani irin bacci da
nake ji" tayi maganar tana ci gaba da lumshe idanunta.
Ya saka hannunsa, ya shafi fuskarta, ya yi ƙasa da muryarsa
ya ce "Na sani ki na haƙuri, amma ki ƙara kin ji 'yar sugar na, duk da
wasu lokutan ki na yi mini bore, but am appreciating jazakillahu bil
janna" ɗan ƙara sunkuyar da kai tayi, cike da jin nauyin sa, dan haryanzu
tana jin nauyinsa sosai da sosai. Sannan ta jinjinawa ƙoƙarin sa, irin yadda ta
din ga shishishige masa dan ta dawo da shi hanya, da keɓewar da suka din ga yi,
amma ko da wasa bai taɓa yinƙurin yi mata abin da bai dace ba, wanda hakan ne ya
sanya ta ƙara sakin jiki da shi sosai.
Maganar sa ce ta dawo da ita hayyacinta ya ce "Kin san
wani abu kuwa?"
"A'a sai ka faɗa"
"Liti ne ya zo mini da wata magana, wai wata sisternki
yake so, na manta sunanta, wadda muka tarar da baba uwani a wurinki a
asibiti"
Ta buɗe idonta ta ce "Wai Walida?"
"Yes ita, wai sonta yake yi, amma ki na ganin Abba zai
ba shi aurenta kuwa? Tun da kin ga ga tarihin rayuwar mu"
Nabila ta ce "Me zai hana, Walida tana da sauƙin kai,
kuma ba ta da dogon buri ita da Anty mamanta"
Viper ya ce "Ina fatan ba zaki yi ramuwar gayya abin da
yayi miki ba, ki saka a hana shi ita ba"
Nabila ta ce "Haba dai, ai wannan ya wuce, ai in dai
tana son shi shikenan, mu dama fatanmu kullum idan aka samu wanda ya tuba ya
daina ɓarna, al'umma su karɓe shi, a mutunta shi, in sha Allah ba zai gagara
ba"
Viper ya ce "Mun gode sosai da sosai my sugar
girl"
Dariya ta yi tana tashi zaune ta ce "Wai kun gode,
kamar an yi wani abu"
"Bari idan muka karya, zuwa eleven, sai mu je na kai ki
gidan hafsa"
Cikin murna ta ce "Amma na ji daɗi sosai da sosai, na
gode Vi"
"Never mind, mu je ayi wanka, sai mu yi breakfast ɗin"
Ta ji daɗin zuwanta gidan hafsa, ko ba komai, ta rage zaman
kaɗaici.
Ta din ga tsokanar hafsa wai anya ba ciki ne da ita ba,
saboda yadda ta yi ƙiba.
Hafsa ta ce "Wallahi ba wani ciki Nabila, jiya na gama
period kwanciyar hankali ce kawai da cin abinci, ni abin ya fara damuna ma,wata
shida ko ɓatan wata ban yi ba"
"Kai hafsa, me aka yi da maza kwata kwata yaushe aka yi
auren? Dan Allah kar ki ɗaga hankalinki"
Hafsa ta rausayar da kai ta ce "To, amma ina son yara
Nabila, dan Allah ki yi mini addu'a, ka da Allah ya jarrabe ni da rashin
haihuwa, ina son yara sosai da sosai"
Nabila ta ce "Dan Allah kar ki damu kanki, komai rabo
ne kuma lokaci ne, daga yin auren ai yayi wuri ki fra wannan maganar" tayi
ta kwantar mata da hankali, daga nan kuma suka ɓuge da hira, wanda galibi hirar
ta karkata ga yanayin zamantakewar aure bawa junansu shawarwari, da zancen
kayan likitar mata maman dr . Wadda cikin ikon Allah, magungunanta suka ɗaga
darajarsu a idon mazajensu fiye da yadda suke tunani, ita mace ai yar gyara ce
da kwalliya, babu borar mace sai wadda ta so.
(0706 971 1327 da kayan likitar mata, bbau ruwanki da
matsalar sanyi, ko fargabar amfani da kayan da baki san da yaya aka haɗa su ba,
domin tsoron cutar da lafiyarku. Domin ɗaga likkafar taku kimar, ku kasance
masu yawan ibada da addu'a, biyayya tare da gyara da ingantattun magunguna na
gyara)
Sai da suka kira Sumayya su ka yi video call da ita, domin
daga abin da Nabila take missing, har da Sumayya.
Cikin ikon Allah, hutun wata guda Viper ya samu, domin ya
ƙarasa jinyarsa, dan haka suka nufo Kano.
Nabila cike da murna ta dawo, sai dai gidan su ya sha uwar
ƙura, suna zuwa mayafinta kawai ta ajiye ta hau gyara.
Viper ya taimaka mata da abin da zai iya, ya tsallake ya
fice, ya tafi wurin 'yan amanarsa.
Tas Nabila ta ƙalƙale gidan, ta kira sumayya a waya, ta gaya
mata ta dawo, ta ce mata za ta zo.
Ta kuma kira Walida a waya, bayan sun gaisa take yi mata
maganar liti.
Da fari nuƙu-nuƙu ta fara yi, daga baya kuma ta saki jiki ta
yi mata bayanin komai.
A fitar da Viper ya yi, har gidan su ramma ya je, yaji daɗi
da mama ta gaya masa ta koma makaranta, amma ta damu da rashin tarewarta, ta
gaji da yadda sai dai ya zo ya ɗauketa su na yawo a gari.
Viper ya ce kar ta damu zai yi magana da Abdul ɗin.
Bayan ya koma gida yake gaya wa Nabila, da weekends Walid da
liti za su zo, dan tun da aka yi bikinsu, Walid ne kawai ya zo.
Ta ce masa to.
Can gidansu Hafsa kuwa, 'ya'yan mama da Anty Zakiyya ta yi
wa asiri, da kyar ta samu suka auru, kullum cikin ciwo suke, dan ɗaya daga
cikinsu kamar zata zare, idan ta fara aljanu kamar zata haukace, hakan ya
tsananta wutar ƙiyayyar da ke tsakanin su, kuma aka yi rashin sa'a, dukkaninsu
babu wadda take jin daɗin zaman aurenta, ɗaya kishiyoyi sun sakota a gaba, sai
da aka yi saki biyu a shakera biyu.
Ɗaya kuma dangin miji da maƙwabta, sun hanata sukuni, ga
miji ba ya son haihuwa.
Abin duniya ya isheta, ta rasa abin da yake yi mata daɗi, ga
Tijjani ya auri wata fitinanniyar yarinya da ba ta da kunya, ba ta ganin
mutuncinta ko kaɗan, shi kuma ya zama tamkar soko, sai abin da take so shi yake
yi, ba ya ji ba ya gani a kan matar nan, bai ƙi ya ɓata da kowa ba a kanta,
ciki har da maman. Dan idan ta yi masa ƙorafi a kan matar, sai ya daina zuwa
gaisheta.
Saifu ne dama mai ɗan dama dama, shi ma kuma ba ya ji, ya haɗa
kai da yaran masu kuɗi, yana ta rashin ji, duk da ya rage, ga kuɗi yana samu,
amma ya fi mayar da hankali a kan shaye-shaye da kashewa 'yan mata kuɗi, sam ba
ya yi wa rayuwarsa wani tanadi.
Waɗannan tarin matsalolin ne, suka haɗu suka addabi zuciyar
mama, ta kasa sukuni da jin daɗin rayuwar, duk in da ta motsa ɓacin rai da
damuwa sun baibiyeta cikin yaranta kowa da halinsa.
Kawai aka wayi gari tana wanka, ta yanke jiki ta faɗi a
cikin banɗaki, aka ɗauketa aka kaita Asibiti, a nan aka tabattar da ta samu
shanyewar ɓarin jiki.
Ba ta iya yi wa kanta komai sai dai ayi mata, hatta najasa a
kwance take yi, kasancewar jinya ba abu ne na ɗan lokaci ba, ya sanya yaran
nata suka fara ƙosawa suke bata wahala.
Hakan bai zame wa Zakiyya izina ba, dan a iya cewa ita murna
ma tayi, yanzu miji ya zama nata itakaɗai.
****
Liti sai ƙarewa gidan Viper kallo yake yi, an zuba wa Nabila
kaya na alfarma, gidan yayi kyau sosai da sosai.
Nabila ta gabatar musu da kayan ciye-ciye, take cewa Walid
"Shi ne yau baka kawo mini Shahida ba"
"Ai ita na kawo ta ma, ke fa baki taɓa zuwa gidanmu
ba"
Tayi murmushi ta ce "In sha Allah zan zo, ai ina son
zuwa ziyara sosai da sosai, dan ba sai na jira Vi ba, shi sabgoginsa da
yawa".
Suka hau abinci da ci, Walid yana ta santin abinci, amma
liti da ya karkace sai cewa ya yi "Abincin nan ya kusa kamo na 'yar madara
daɗi, ita fa miyar 'yar madara sai ka kwana uku kana jin magginta a
bakinka"
Walid ya ce "Sannu faisal, ka tsayar da kunnuwa kamar
zomo, ka na ta gizo, ka yi wa mutane shiru"
Ta basar ta ce "Vi wai yaushe ɗan mama zai dawo
ne?"
Viper ya kalleta ya ce "Sai ya shekara biyu ai, in sha
Allah zan je na gano shi"
"Har shekara biyu, bai yi yawa ba?"
"Ni da na yi biyar mutuwa na yi?"
Tayi murmushi ta ce "To ai kai kai ne, shi kuwa abin
tausayi"
Yayi murmushi ya ce "Shi ma zai jure ai"
Walid ya ce "Ina fatan Viper ne ya daka sakwarar nan,
dan ta yi daɗi ta daku"
Ta ce "Mara lafiya ne zai daka? Haryanzu hannunsa yana
yi masa ciwo fa"
Liti ya sake kallon falon ya ce "Ohh Allah sarki yar
madara, gidanku na tuna Viper, da ta tare babu ko plasta, aka saka mata kayanta
a ciki haka, gashi ta mutu, wata ce take morar arzikinka"
Viper dai bai yi magana ba, Nabila ta tashi ta ce "Bari
na shiga daga ciki, ku gaida gida zan ɗan kwanta"
Viper ya kama hannunta, ya yi kissing bayan hannunta, ya ce
"Allah ya ƙara zaƙin hannu, abinci ya yi daɗi sosai"
Cikin jin kunya ta ce "Allah ya ƙara buɗi, cefane yayi
kyau sosai" ta tafi tana murmushi.
Liti ya ce "Haryanzu ina jin ba daɗi, idan na tuna ba
jauhar ce ke more soyayyar nan ba"
"Abdallah" Viper ya kira sunansa yana kallonsa.
Ya kalle shi.
"Ka daina yi wa Nabila abin da ka ke yi mata, son
Nabila son Jauhar ne. Wani darasi da na ƙara koya a rayuwata da Jauhar, shi ne
dama sau ɗaya take zuwa a rayuwa, ko ka yi amfani da ita ko ta wuce. Na samu
dama na saka halaccin da Jauhar ta yi mini da soyayya da kulawa, amma ban yi
ƙoƙarin hakan ba, sai a ƙarshen rayuwarmu, kuma mutuwa ta zo ta rabamu. A yanzu
wata damar na samu na saka halacci da alkhairi, dan haka a daina kushe mini
Abla please"
"Tuba nake maigida an daina in sha Allah"
Ya tashi ya yi musu rakiya, sai da ta jiyo falon shiru,
sannan ta fito ta hau gyarawa.
Yayi mamakin bayan dawowarsa, da take masa dan Allah su je
su duba mama a asibiti, tun su na Abuja, aka ce mata tana asibiti babu lafiya.
Shi mamakin da take bashi, kamar gaba ɗaya rayuwarta ba ta
da riƙo, komai girman laifin da aka yi mata kuwa, da ta gama buyaginta, sai ta
saukko.
A daren suka je suka dubata, Nabila har da ba su kuɗi, sai
da ta yi kuka, ganin yadda bakin maman ya karkace, sai zubar da yawu yake yi,
ga wani irin warin kashi da take yi, duk da da pampers a jikinta, da alama tun
safe ba a cire mata ita an canza wata ba.
Da daddare suna kwance, tana jikin Viper, ta ce
"Vi"
"Mmm"
"Dan Allah in tambayeka mana, amma kar ka ji haushi
Please"
Ya ce "Idan kin san zan ji haushin kar ki yi"
"Am curious"
"Go ahead"
"Na ga ka na da kishi sosai, amma na ga kamar akwai
shaƙuwa sosai, tsakanin Jauhar da su yaya Walid"
Murmushi ya yi mai sauti, tare da shafa bayanta ya ce
"Haka ne, dan ma Allah ya jiƙan rai Nura baya raye, ta fi shaƙuwa da shi
sosai da sosai. A lokacin da ta shigo rayuwata, daga ni har su babu wani mai
guiding ɗin rayuwarmu, ba mai saka mu, babu mai hana mu, abin da muke so shi
muke yi.
Bayan ta shigo rayuwata, ta fara ƙoƙarin nuna mana mu ma
mutane ne.
Tana da kirki da sauƙin hali sosai, a duk lokacin da na
shiga matsala, babu wanda yake tsayawa a kaina, sai ita, su kuma su na dafa
mata, babu wanda zai saurareta idan ba su ba.
Ko sakakken abinci ta yi, sai ta ajiye musu.
Gashi tana matuƙar girmamasu, saboda ta san dai babu wanda
ya damu da mu, sai su ɗin dai.
Saboda ita muka daina askin banza, kamar babarmu, haka za ta
zauna ta yi ta mita, bayan na haɗu da Nura kuwa, tun da ta fuskanci matsalarsa
shi ma ta rashin kulawar iyaye ne, da ƙarancin shekaru, take tausaya masa.
Ya girmeta, amma shi ne ɗan aikenta, har kasuwa yawon sayo
mata kayan shirin dutse shi yake yi mata, ina jin kishin ba bana ji ba, amma na
yadda da ita, kuma idan na wulaƙanta su, saboda su daina zuwa in da take, idan
na shiga matsala wa zai taimaka mata?.
Ta kai ta kawo, Nura sai ya samo abin sa, bai kalli in da
nake ba, sai dai ya zo wurinta.
Idan matsala ce da shi ma, ita zai gaya wa saboda ni
masifaffe ne, ta rayu da mu da tausayi ne, da kulawa babu ƙyama da jin cewa
bamu da amfani, shiyasa Liti kullum cikin yabonta yake. Ta shiga cikin tashin
hankali, ta kaɗu sosai da mutuwar Nura"
Ta sauke numfashi ta ce "Na fahimta, Allah ya yi musu
rahama gaba ɗaya"
Ya ce "Amin my sugar girl"
"Bari zan ɗan je na dawo"
Ta kalleshi ta ce "Yanzu kuma? Ƙarfe tara saura fa,
haba Vi"
"Ba zan jima ba, ki yi haƙuri yanzun nan zan dawo
fa"
Ta ɗaga shi ta ce "To a dawo lafiya, banda rigima"
ya sumbaci goshinta yana murmushi ya sauka.
Sai dai ba ta san ina za shi ba, ba ta san lokacin da ya
dawo ba, dan sai asuba da ta ji yana tashinta tayi salla.
Gidansa da ya zauna da Jauhar, ya tafi, gidan ya yi ƙura
sosai, saboda ya kwana biyu bai zo ba.
Ya haska gidan da fitilar wayarsa, kamar walƙiya
ƙwaƙwalwarsa ta tariyo masa wani moment da suka yi.
Ta shigo ta tarar da shi a falo, ta ɗago masa wata jarka ta
ce "Master, waye ya sha wannan abin?"
"Ni ne, ba lemo ba ne ba?"
cikin halinta na shagwaɓa ta ce "Master magani ne
fa"
"Haba dai, na basir ko shawara? Ni fa in ce, ai na zata
lemo ne da, amma bakomai ai tun da maganin basir ne"
Kamar ta yi kuka ta ce "Ni meye haɗina da wani basir
dan Allah, kai komai na ajiye sai ka cinye,
da wanda na baka da wanda ban baka ba, har nawa da naka duk sai ka haɗa
ka cinye" tayi maganar tana hararsa.
Yayi mata shiru, ta gama fushinta, sai da ta manta, sannan
ya ce "Ai ki na da kuɗi, a kuma haɗo miki wani mana, ke ki na neman kuɗinki
da kyar, su na yi miki wayo, su na karɓar miki kuɗi, suna haɗo abin da baki
sani ba su na baki"
Ta kalleshi ta ce "Su wa?"
"Masu ce miki ki sai maganin mana, ai ina jinku, ni da
na zata lemo ne ki ka yi ba ki san mini ba, shi ne zan sha rabona sai daga baya
na fuskanci menene a ciki, amma bakomai ai ni na sha miki maganin, zai yi miki
amfani" banza ta yi masa, ta ƙi kula shi.
Dariya ya yi ya ce "Hajiya magana nake fa"
"Sai dai ka yi kai kaɗai, ba zan kula ka ba"
Murmushi ne ya suɓuce wa Viper, ya din ga jin tamkar ya buɗe
idanunsa ya ganta.
Ya jima a gidan, sannan ya fita ya nufi hanyar gida.
Wurin ƙarfe takwas da rabi, Nabila ta fito tana kiransa, dan
ta farka baya kan gadon.
Waya ta tarar da shi yana yi.
"Walid jiya kasa bacci na yi, na je gidanmu ne, na daɗe
a can sai kusan ɗaya saura na koma gida. Ina ga zan sayar da gidan nan ne, ko
kuma a gyara shi a zuba 'yan haya a ciki".
Ƙoƙarin barin wurin ta yi, ya ɗago suka haɗa ido, ya katse
wayar ya ce "Ranki ya daɗe, ya aka yi ne? Ko in zo?"
Ta girgiza masa kai ta ce "Dama waya nayi da Abba ne,
na fara yi masa maganar su Walida ne, amma na ga kana waya, bari na shiga
ciki" ta ƙarasa maganar a gurguje, kamar mai tsoron wani abu, ko mara
gaskiya.
Mintuna goma, ya ji ya kasa jurewa, ya tashi ya shiga
bedroom, ya tarar da Nabila ta zubo da kaya tana ninkewa.
"Abla" ta ɗago ta kalleshi, ta mayar da kanta ta
sunkuyar.
Takawa yayi gabanta, ya karɓe rigar hannunta, ya ce
"Kalle ni, menene?" Ta sunkuyar da kai ta ƙi kallonsa.
"Abla am talking to you" kawai hawaye ya fara
gangarowa daga cikin idanunta.
"Ya Salam Abla why, kishi ki ke?" Tafukan
hannayenta ta saka a kan fuskarta tana kuka mai tsuma zuciya.
Cikin rikicewa ya ce "Ki fahimce ni abla, ki tsaya na
yi miki bayani" yayi maganar yana riƙe hannunta.
Girgiza masa kai ta yi, ta ƙwace hannunta ta fice daga ɗakin.
Ya dafe kansa cikin tsananin damuwa ya sake bin bayanta.
**
Indabo kamar yana kan ƙaya haka yake jin zamansa a Nigeria,
gani yake komai ma zai iya faruwa.
Da sassafe ya yi sallama da matarsa, bai tsaya ya saurari
Abdul ba, ya tafi airport.
Sai dai yana cikin jirgi, wani mutum da facemask ya bashi
wata takarda ya tafi, bai san waye ba, kuma mutumin bai yi masa magana ba, bai
tsaya ba domin amsa tambayar da Indabo zai yi masa ba.
Ayshercool
08081012143
Bin bayan Nabila yayi yana kiran sunanta, amma ba ta tsaya
ba, ya cim mata a ɗaya bedroom ɗin, tana ƙoƙarin rufe ƙofa.
Ya buɗe ƙofar ya tsaya yana kallonta, fuskarta ta koma ja,
haka idanunta ma sun yi jawur.
Jiki a sanyaye ya ce "Abla, dan Allah ki tsaya ki
saurareni, na yi miki bayani ba yadda ki ke zato ba ne"
Girgiza masa kai ta yi ta ce "No need, ba sai ka yi ba,
na riga na fahimta"
"Ba ki fahimta ba abla, kin yi mini gurguwar fahimta,
dan Allah ki tsaya ki ji"
Cikin kuka ta ce "Ni ba sai na ji ba, na riga na
fahimta, ba zan taɓa samun gurbi a zuciyarka ba, ni ka aureni ne kawai ka din
ga kallon hoton jauhar, ba zaka taɓa so ma ba, this is the chance you ask me to
give you, shikenan na fahimta"
Diriricewa yayi ya ce "Ba haka bane, baki fahimce
ni"
"Ba sai na fahimta ba, your actions show's, da tuntuni
ka bar ni na tafi a kan yadda na bar wa zuciyata, na aurenka shi ne sabuwar
jarrabawar da zan fuskanta, ka yi mini maganganun da suka sanya na ji na aminta
ina da kima a idonka, amma bakomai"
Riƙota yayi yana goge mata hawayen fuskarta ya ce "Ko
ba zaki saurare ni ba, ki daina kukan nan dan Allah ba na so" fizgewa ta
yi daga jikinsa, ta shige toilet, yana jin yadda ta fashe da kuka mai tsuma
zuciya.
Har cikin ransa yake jiyo kukan nata, ya nemi wuri ya zauna
jiki a sanyaye, tun yana sanya ran zata fito, har ya haƙura ya tashi ya fita.
****"
"Na san wasiƙata zata iskeka a dai-dai lokacin da
yakamata, kafin na jaka da nisa, bari na ɗan ja ka baya, zamanin da kana yaron
'yan siyasa, kun zo garinmu wani sha'ani, aka kai mu wurinku, wai zaku bamu
tallafi, aka haɗamu 'yan matasan yara marasa galihu, aka kai wa uban gidanka,
ya zaɓi wanda zai lalata, saɓanin cewar da aka yi za a bamu tallafin karatu da
sana'a.
Ina cikin waɗanda bai zaɓa ba, dan haka ban san me za ayi
musu ba, na shiga damuwa burina ba zai cika ba na karatu, ba a zaɓe ni ba, ba
zan samu tallafi ba. Ka yi amfani da wannan damar ka keta mini haddi, da sunan
zaka saka ubangidanka ya bani tallafi.
Matan da ka lalata da yawa, na san babu lallai ka tuna, sai
dai shi irin wannan mikin, ba ya taɓa goguwa a zuciyar wanda aka illata.
Naja'atu Bunkuren nan dai, da ka lalata da ƙuruciya a garin
bunkure lokacin kana yaron ɗan majalissa, ni ɗin ce dai, ƙaddara ta sake haɗa
mu, ba tare da ka gane ni ba. Sai dai ba tare da ka sani ba, ka cika alƙawarin
da ka yi, na tallafar karatuna, kuma muka ɗora daga in da ka dasa aya.
Ganin ina morarka, ya sanya na haɗiye mummunan ƙudurin
fansar da nake da shi a kanka.
Sai dai duk da haka, na yi shirin ko ta kwana ta kowace irin
fuska, saboda sanin tsagwaron mugunta da zaluncinka.
Lokaci ya yi da ka ke tunanin, ka ci moriyar ganga ka ya da
kwauronta, ina! Idan har ka zauna a gida Nigeria, tonon sililin da zan yi maka
ba zaka taɓa sha ba, haka zalika in da zaka ma ba zan bar ka ba, duk in da zaka
shiga a faɗin duniya sai na kawo ƙarshenka, dan haka ya rage naka, ko ka dawo
Nigeria, ko kuma ka tafi duk in da ka ke so, sai na kawo shafe tarihinka ta
hanya mafi muni, zai zama daidai da ɗaukar fansar abin da ka yi mini a baya,
aikin da na yi maka tsawon lokaci ma kuma ya zama halacci ga ɗawainiyar da ka
yi da ni, na barka lafiya" tamkar zuciyarsa zata faso ƙirjinsa haka take
bugawa, sam bai san ta ina yakamata ya fara ba, ya koma Nigeria ko kuma ya
ƙarasa Saudiyya?.
Nan ya shiga lissafi, me take tunanin ta ƙulla masa, da har
take iƙirarin kawo ƙarshen sa a duk in da ya shiga a faɗin duniya?
Har labarin lalatar da ya taɓa yi da yarinya a garinsu ya taɓa
bata, amma ba ta taɓa nuna masa cewar ita ce ba, ashe duk tsawon lokacin nan
wani abu ne a ranta game da shi.
Ya rasa abin da yake yi masa daɗi, gaba zai yi ko kuwa baya,
duk iya tunaninsa ya rasa wane irin tuggun take shirya masa.
*****
Abbu kuwa ya gabatar wa da maman ramma, abin da Viper ya zo
masa da shi, gam da ya aureta, ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Alhaji
Ibrahim, ni a wannan shekarun nawa, me nake nema da zan sake yin aure?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba fa ki yi hamsin ba, kuma auren
nan duk in da aka je aka dawo, shi ne rufin asirinki, kuma sai hankalinki ya fi
kwanciya, amma ki yi tunani a kai"
Bayan tafiyarsa ta din ga tunani, ƙarshe dai maganar tayi ta
cin ta, take gaya wa ramma.
"Amma na ji daɗi mama, babu abin da zamu cewa yaya
Aminu sai Allah ya saka da alkhairi, da har ya ce ki auri mahaifinsa"
"Ramma ni gani nake yi abin bai yi tsari ba, goɗai-goɗai
da ni na hau yin aure?"
"Mama ai mu ma sai mun fi jin daɗi ace ki na da aure,
aure security ne, dan Allah ki amince kar ki ce a'a"
Ta ce "Ai abin ne sai a hankali, amma zan yi addu'a
dai"
"To sai mu tayaki addu'ar, kin ga nan gidan ma, bamu
sani ba ko Daddy zai yi amfani da abin sa, kin ga ya yi mana ƙoƙari, kalli shi
yake ciyar da mu, yake yi mana komai, kin ga kuma yau da gobe sai Allah. Amma
idan aure ki ka yi ai mijin ba zai gaji ba, tun da hakkinsa ne" shiru ta
yi tana kallon ramma, tabbas maganganunta haka suke, ita ba ma tayi wannan
tunanin ba, dan haka ta ce "Kuma fa da gaskiyar ki rahama, amma ni duk na
fi son na ga kin tare tukuna a naki ɗakin"
"Eh, ya ce babansa ya bar ƙasar, ya kuma gama gyara in
da zamu zauna, ya canza shawara yanzu, wai zan tare amma fa har kayan ɗakin duk
ya saka"
Mama ta ce "Ai ni wannan mijin naki, rigimarsa ta yi
yawa, na ma daina ce masa ya bari, Allah ya taimaka" ramma a zuciyarta ta
amsa da Amin.
Nabila kuwa fafur ta daina sauraren Viper, duk rarrashin da
ya so yi mata, fafur taƙi tsayawa ta saurare shi.
Zata dafa abinci ta bashi, da duk wani abu da yakamata ta yi
masa, amma ba ta zama in da yake, babu hira babu duk wani abu na soyayya da
take yi masa.
Duk yadda yake murnar hutun da ya samu, zai zo su samu
isasshen lokacin da zai bata kulawa da soyaya, amma komai ya ɓaci.
Zaman gidan ma ya daina yi masa daɗi ko kaɗan, duk ɗaukinsa
da son kasancewa da ita, yanzu fargabar tunkararta ma yake yi, dan sam babu
fuskar hakan, sai yayi ta maza yake iya tunkararta, shi ma sai dai yayi kiɗansa
da rawarsa shikaɗai.
Sosai yake jin tausayinta, sai dai taƙi ba shi damar ya
fahimtar da ita abin da yake son ta sani.
'yan gidan Nabila su suka zo mata wuni, har da Walida da
baba magajiya, dama bata saka ran ganin Sauda ba, har da Anty.
Ta ji daɗin zuwan na su, kuma babu wanda ya fuskanci tana da
damuwa, suka wuni suka yi wasa da dariya, sai da ta ji kamar kar su tafi.
Abu kamar wasa, Viper ya daina cin abincin Nabila, idan ma
ta ajiye ba zai ci ba, ya koma kwana a ɗaya ɗakin, hakan ya saka a jere kwana
biyu baya kwana a gida ba ma ta sani ba, sai kwana na uku, da bata ganshi a
gidan ba, wunin ranar.
Bayan magariba sai ga Walid, ta yi masa maraba ta karɓe shi
hannu bibbiyu, bayan sun gaisa ya ce "Barrister, meyafaru ne tsakaninki da
mai zamani, muna murna an yi aure komai kuma zai wuce, shi ma zai samu nutsuwa
yanzu ya ji daɗin rayuwa kuma sai a fara rigima?"
"Wani abin ya ce na yi masa?"
"Bai faɗa ba, amma alamu sun nuna, kamar a gidan da
muka zauna yake kwana, me yayi zafi haka?"
Cikin mamaki ta kalle shi ta ce "Kwana kuma? A can yake
kwana?"
"Wallahi Nabila da gaske nake yi miki"
Kawai ta fashe da kuka ta ce "To ni ya zan yi ne? Duk
iya ƙoƙarina baya gani, Jauhar ce kawai a ransa, ni ba ni da wani gurbi a
zuciyarsa. Zuciya ce fa a ƙirjina, ina son 'yar uwata, amma abin da yake yi
mini yayi yawa. Muna tare da daddare har ya kwanta ya ce mini fita zai yi, sai
ji na yi kuna waya, wai gidan da suka zauna ya tafi, a wannan daren ni bani da
amfani kenan? Ba zan hana shi tuna Jauhar ba, amma ni fa? Kodayeke dama ni na
ce ina son shi, dole na jure duk abin da zan gani"
Walid ya ce "Subhanallah, kuskuren fahimta ne Nabila,
tun yamma muka yi magana da shi, ya ce mini ya ji wani wa'azi, an ce gado nauyi
ne a kan mamaci, har sai an raba ake sauke masa wannan nauyin.
Shi ne ya ce mini tun da kema gaki, kina cikin magadanta,
zai je ya duba gidan, yayi magana da su Baba, ina ga tun zuwan da ku ka yi, bai
sake zuwa ba.
Da safen ma, da muka yi magana ce mini yayi abin ne yake ta
damunsa, ya kasa bacci, ya ji bai kyauta ba ace tsawon wannan shekarun ba a
sauke wa Jauhar nauyi ba, kuma baba bai yi masa magana ba, kawai ya fita a
daren, ya je ya sake dudduba gidan, ba wai dan baki da amfani ba ne ba Nabila.
Wallahi kulawar da ki ka samu, Jauhar ba ta sameta daga gare
shi ba shi fa yanzu duk wannan abin da yake yi, ihu ne bayan hari kawai, amma
wallahi yana sonki Nabila.
Kin san sunanki da nasa ya hargitsa ya fitar da sunan da
yake kiranki da shi Abla? Ki din ga yi masa uzuri, a hankali zai daina, zamansa
da Jauhar ba abu ne da zai manta lokaci guda ba, yarinyar ta sha wahala ne
sosai, kuma ba ta wani more shi ba, an kashe ta a dalilinsa. Da bakinsa yake faɗar
ki na da haƙuri matuƙa da kawaici, amma ina ƙara baki haƙuri, dan Allah ku
sasanta"
Tayi ajiyar zuciya, ta jinjina kai ta ce "Wallahi ina
yi masa uzuri, shi ma ai ya sani amma In sha Allah zan ƙara, na gode sosai da
sosai "
"Yauwwa Nabila, ai wallahi tun da ya ce mini wai kin
goyi bayan soyayyar liti da ƙanwarki na sara miki, ba ki da riƙo, kuma ki na da
haƙuri sosai da sosai, Allah ya baku zaman lafiya ya ƙara muku fahimta
juna"
Ta amsa da Amin, tayi ta masa godiya, ya tafi.
Kamar ta kira Viper a waya, sai ta ƙyale shi, sai da gari ya
waye, tayi girki ta shirya ta fita.
*****
Cikin matsanancin tsoro da fargaba, indabo ya sauka a
airport, yana ta tunanin abin da ka iya faruwa, na sharrin da Bunkure ka iya
ƙulla masa.
Sai dai ya ga ya wuce airport lafiya, babu abin da ya faru,
har ya isa masaukinsa, bai haɗu da wata matsala ba.
Ya kira abokansa ya sanar musu takardar da Bunkure ta aiko
masa da ita, suka bashi ƙarfin gwiwar ka da ya damu, barazana ce kawai ba wani
abu ba, yayi zamansa zuwa lokacin da komai zai daidaita.
Kankarofi kuwa yana ta campaign ɗin sa, na takarar sanata,
kujerar da Indabo yake kai.
Kuma yana ta ci gaba da samun karɓuwa ta kowace kusurwa.
Jidda ƙanwar indabo kuma tana ta nacin sai ta koma ɗakinta.
***
Kamar daga sama haka Viper ya ji sallamar Nabila, sai dai
bai iya amsa mata ba, cikin ɗakin ta shiga, aikuwa ta same shi a zaune a kan
katifa.
A ranta take mamakin halinsa, daga samun saɓani yayi yaji,
ƙasan zuciyarta, take addu'a Allah ya sa bai sha wani abu ba.
Ba ta ce masa komai ba, ta ajiye flask ɗin, ta ƙarasa kusa
da shi ta zauna, bai kulata ba, ta saka hannunta ɗaya a bayansa, ɗaya kuma ta
juyo fuskarsa ya kalleta, ta marairaice ta ce "Na zo biko ne, am sorry Vi,
son da nake yi maka ne ya janyo komai, kuma tunanin da nake yi, ba ni da
matsayi a wurinka ne ya sanya nake shiga damuwa, but am sorry" bai yi
magana ba ya ci gaba da tsareta da idanunsa.
Ta shafa fuskarsa ta ce "Talk please" kamar gunki
yaƙi magana.
"Please talk Vi"
"I love you" yayi maganar yana tsareta da ido.
Idonta ne ya ciko da hawaye ta ce "And you mean
it?" ya jinjina mata kai alamar eh.
Rungume shi ta yi, hawayen farinciki na zubowa daga
idanunta, gadon bayansa take shafawa zuwa kansa ta ce "Dama zaka iya bani
gurbi a zuciyarka?"
"Na daɗe da baki Abla, baki yadda da kanki bane ba,
shiyasa ki ke ganin kamar ba da gaske nake ba. Tashin hankalin da na shiga, da
na ji an ce gado nauyi ne, ya sanya na kasa jurewa na tafi a daren,
communication gap aka samu a tsakanin mu, dole mu zama masu saurarar juna da yi
wa juna uzuri domin zaman auremu ya ɗore kuma ya yi daɗi.
Na yadda ke ba Jauhar ba ce ba, kuma ina ƙoƙarin na rayu da
ke a Nabilanki, amma sai kin yadda da kanki, kin kuma rage zargi.
Abla ina yawan gaya miki Al'amin ba butulu bane ba, bana
manta halacci komai ƙanƙantarsa kuwa. Balle ke naki da ceto raina, hankalina
kacokan ki ka yi, rayuwarki ki ka saka a hatsari mai ban tsoro ki ka ceto ni,
tayaya zan zama butulu, a ɗakin nan na kusa ajalinki, amma bai hanaki ci gaba
da bibiyata ba, wane irin butulu ne ni da zan kasa buɗa miki zuciyata ki shiga?
Ki manta da matsayin Jauhar a zuciyata, ki kalli kanki ke ɗaya kawai, wasu
lokutan wasa nake yi miki a wasu abubuwan, amma tun da ba kya so, in sha Allah
na daina, amma ina ƙaunar 'yar sugar, wannan kalaman ko 'yar madara ban taɓa
gaya wa ba, sau ɗaya na taɓa furta wa jauhar ina sonta a rayuwata, daren da za
a kasheta, amma ke ba na son na maimaita wannan kuskuren ina sonki Nabilatul
arfa, Ablana kuma 'yar sugana"
Ita kanta ba ta san takamaimai kukan me take yi ba, ya ci
gaba da rarrashinta, da duk kalaman da shi kansa bai san ya iya su ba, tare da
ƙoƙarin wuce makaɗi da rawa.
A hankali ta ce "Vi ba fa a gida muke ba"
"Eh, ai ke ki ka ɓata mana honeymoon a gida, sai mu yi
a nan"
"Honeymoon a kango?" Tayi maganar tana murmushi,
bai san lokacin da ya tuntsure da dariya ba, ya tashi zaune yana kallonta ya ce
"Gidan gwaurontakar namu ne kango?"
Tana daga kwance ta yi murmushi ta ce "Kogon da
macijina ya din ga ɓuya ba"
Ya gyaɗa kai ya ce "Ke ce jarumar da ki ka samawa
wannan maciji 'yanci, ya ci gaba da rayuwa da cikakken 'yanci.
Abla a lokacin da ake nemana ruwa a jallo, ba ki duba kamani
tare da ke barazana ne a gareki ba, ba kya lissafa wannan, 'yanci kawa ki ke
nema mini, na bar kogon da yake tamkar kurku a gare ni, wai duk tayaya zan
manta wannan ne?" Ya ƙarasa maganar yana kwanciya a jikinta.
Ta rungume shi sosai, tana sauke numfashi.
A nan suka karya, hankalinsu kwance kamar su na gida, su ke
gudanar da soyayyar su.
Har Dutsen da ta kan je ta same shi, su ka je, ta din ga
tuna masa wasu abubuwa da suka din ga faruwa, suna nishaɗi.
Har yamma suna can, sannan suka tafi gida.
Viper ya tambaye ta, a raba kayan jauhar a bata, ko a sayar
a raba kuɗi kawai a bata.
"Ba zan iya amfani da kayanta ba"
Dumm ya ji a ƙirjinsa, amma ya daure ya ce
"Meyasa?"
"Zan daɗe ina kallon kayan ina tunata"
Ya ce "Ko dai kishin ne?"
"Ko kaɗan, rayuwarta da yadda ta rasu, ba zai taɓa
barin ƙwaƙwalwata da zuciyata ba, ba zan iya amfani da kayan jauhar ba, rashin
haɗuwa da jauhar a rayuwata wani miki ne za ba zai taɓa warkewa daga zuciyata
ba. Idan ma an raba, ayi amfani da abin da na samu a sai wani abu da ladan
amfani da shi zai isketa da mahaifiyarmu a makwancinsu"
"Shikenan, zan yi magana da Abba abin da ya ce
shikenan"
Gidan Major kuwa, Mama ta takurawa Nasir a kan ya auri 'yar
ƙawarta da take so ya aura tuntuni.
Aka fara shirye-shiryen biki, aka yi masa transfer a wurin
aiki, zuwa kudancin Najeriya, kuma aka rage masa matsayi sosai da sosai a in da
aka kai shi.
Walida kuma sosai suke soyayya da liti, dan kuwa akwai shi
da shiga rai.
Sosai Viper yake ƙara ganin kimar Nabila, saboda rashin
riƙonta, maganar bikin Sumayya ita ma ta taso, Nabila su na ta shirye-shirye.
Viper sai da ya samu Liti, shi ma ya ja masa kunne, a kan
abubuwan da yake yi wa Nabila.
Nabila ta sake komawa duba mama, an sallamota daga asibiti
tana gida, sai dai wata irin wahalalliyar jinya take yi, gaba ɗaya yaran babu
mai tausayinta.
Har gidan su Shahida ta je, ta zazzagaya ta sada zumunci.
Bayan ta dawo, ta tarar da Viper yana ta mita.
Ta ce "Meyafaru ne?"
"Kuɗin da muke rabawa na ribarmu, na wurin shayin nan,
wai ba za su bani ba, wurin refilling ɗin gas, Walid zai din ga zama idan ya
dawo daga kasuwa, zai din ga zama".
Ta ce "To menene a ciki, idea ce mai kyau"
"To ai ni kuɗi nake so, harkar bikin nan na kashe kuɗi
sosai, na sakankance na saka rai, suka ɓullo da wannan maganar"
Ta ce "Vi ai idea ce mai kyau, zaman haka ka dogara da
aikin gwamanti kawai, ba zai yiwu ba, gashi shiru an ce za ayi maka ƙarin girma
amma haryanzu shiru"
"Wannan ƙarin girman duk matsala ne"
"A'a ina fatan mu samu ci gaba, a kan komai"
Cikin ikon Allah aka saka ranar tarewar ramma, kuma maman ta
amince da batun auren baban Viper.
Nabila ta mayar da hankali wurin gyara ramma ma, ta biya kuɗin
yi mata gyaran jiki, sannan ta saka maman yusuf likitan mata haɗata.
Viper ya yi ta mita, saboda Nabila ta koma aiki, haka
abubuwa suka yi wa Nabila yawa, zama matar gida babu sauƙi ga komawa aiki.
A haka lokacin hutun Viper ya cika, zai koma bakin aiki.
Daga shi har ita kamar su cinye juna, dan tun bayan da suka
shirya, yake ta ƙoƙarin kare duk wani abu da zai sanya ta ji babu daɗi, ita ma
daga nata ɓangaren tana ta ƙoƙarin kiyaye abubuwan da zai janyo su samu saɓani.
Tun dare ta haɗa masa jakarsa, ta yi masa snacks, ta yi masa
cincin da dambun nama, yadda zai daɗe yana amfani da shi.
Sun sha soyayya ranar, kamar kar su rabu.
Da safe wurin ƙarfe goma, ya tafi duk sai ta ji babu daɗi,
gidan yayi mata wani iri.
Kwanan Viper biyu da tafiya, Walid ya rako liti har gida, ya
zo ba wa Nabila haƙuri.
Nabila ta ce "Da zan riƙe abin da ka yi mini a raina,
hatta alaƙarka da Vi sai na rabata, duk da tasirin shekarun da ku ka yi tare.
Kawai da ka din ga iya bakinka, wani idan ka cutar da shi da harshenka, har
abada duk aikin alkhairin da zaka yi masa, ba zai shafe tasirin abin da ka gaya
masa ba, Allah ya shiryeka" duk da ya ji haushin kausasan maganganun da
tayi amfani da su a kansa, amma ya danne.
Bayan sun fito yake cewa Walid "Yanzu da gaske sai ta
raba alaƙata da Viper, duk tsawon lokacin da muka ɗauka tare?"
Walid ya ce "Macece fa, wallahi sai ta raba"
"Kai ƙarya ne ba zai yiwu ba, ba wata mace"
"Galibinmu uban meye ya koro mu daga gidan iyayenmu,
idan ba tasirin kaidin mace ba, ka daina cika baki malam"
Sai kuma ya ce "Kai haka ne fa, to Allah ya
kyauta"
Nabila ta samu labarin mutuwar Madaki, ya mutu an rasa wanda
zai zo ya karɓi gawarsa, ga jikinsa babu ta in da za a saɓa shi ayi masa wankan
gawa, saboda duk ya ruɓe, haka aka yafa masa ruwa aka binne shi.
Da Nabila suka yi waya da Viper, ta din ga godewa Allah, da
Allah ya dawo da su hanya madaidaiciya lokaci bai ƙure musu ba.
Nabila ta kai wa madam Halima ma ziyara, dan sai da ta kwana
biyu a wajenta, Viper ya bata damar hakan.
Nabila ba zata taɓa mantawa da matar nan ba.
Aka gama shiri tsaf, ramma ta tare a gidan Abdul, a lokacin
tana cikin hutun makaranta.
Gidan ramma ya yi kyau sosai da sosai, ana gobe zata tare ya
sanar wa mummynsa, a lokacin Anty Jidda tana gidan.
Ta ce "Abdul ka yi asara, 'yar matsiyata talakawa da
suka tagayyara rayuwarka, yau ita ka bi kake wannan rawar kan a kanta"
Abdul ya ce "Anty Jidda ban yi asara ba, gyara
kuskurena na yi, kuma ke ma yakamata ki nemi yafiyar ramma, abin da ya faru da
ita a gidanki, amma ki ka nuna halin ko in kula, ba zan gaji da sarawa Alhaji
mu'azzam kankarofi ba, ya cika uba, kuma ni abin da yayi mini taimakona
yayi"
Mummy ta ce "Jidda ba fa zai gane ba, a kan yarinyar
nan zai iya ci miki mutunci ma, ai ni na cire hannuna daga kan Abdul na saka
masa ido, kina kallo halin da mahaifinsa ya tsinci kansa a ciki wanda har saka
hannunsa bai dame shi ba, ya haɗa kai da abokan adawar ubansa ba abin da ya
dame shi".
Jidda ta ce "Amma kuwa Abdul ka yi asara"
"Wallahi ban yi asara ba, tun da kema abokin adawar ta
sa ki ka aura ai"
Duk da bai ji daɗin abin da ta faɗa ba, amma yana Addu'ar
Allah ya sa kar furucin mahaifiyarsa yayi tasiri a kan aurensa.
Hankalinsa kwance ya kasance da ramma, cikin jin daɗi da
farinciki, saboda yadda yake ji a yanzu yana da cikakkiyar dama a kan matarsa.
Babban abin da ya basu mamaki, har da akwati bakwai na lefen
ramma, suka tarar a gidan.
Store ɗin ta na abinci shaƙe da abinci, duk wani abin buƙata
da na amfani ya saka mata.
Kafin ta tare ta sha nasiha, kuma sai da aka yi walima
sannan ta tare.
Ko sabon ango fil bai kai Abdul rawar ƙafa ba yau, a baya
duk da auren ramma yake yi, ya kan ji kamar yana wani abu ba dai-dai ba, amma
yanzu hankalinsa kwance, kasancewar duniya yanzu ta san ramma matarsa ce.
Daren bai gushe ba, sai Abdul yana nanata wa ramma, irin
matuƙar ƙaunar da yake yi mata, tare da neman afuwarta a kan abubuwan da suka
faru a baya.
Duk daga shi har ita ba baƙin juna bane ba, amma daren yau ɗin
ya ƙara zama na musamman a cikin zukatansu, duk da a ƙarƙashin zuciyar ramma,
ta na jiyo raɗaɗi da zafin rasa mutuncinta, da kuma rayuwar da ta yi, ita ba
karuwa ba ita ba mai aure ba. Amma ba ta fatan sake tayar da wannan maganar,
dan ta yi masa alƙawarin komai ya riga ya wuce, domin yanzu Abdul gaba ɗaya
tausayi yake bata.
Da safe Nabila suna Video call da Viper, ko saukkowa ba ta
yi daga kan gado ba, ta kira shi ta gaishe shi.
Ya zuba mata ido ya ce "Fito daga bargon sai mu
gaisa" ta fito ta tashi zaune ta ce "Good morning Vi"
"Morning darling, ya aiki ya gidan kuma"
Cikin shagwaɓa ta ce "Am missing you"
"Next week zan shigo in sha Allah, ni kaina ina kewarki
like crazy, kin rame ma fa, ya aka yi ne?"
"Hidimar tariyar ramma ce da na yi ta zirga-zirga, jiya
dai ta tare Alhamdilillah "
Viper ya ce "Masha Allah, an sha gwagwarmaya Allah ya
zaunar da su lafiya ina fatan dai maman ba ta ɗaga hankalinta ba?"
"Ba ta ɗaga ba, baka ga gidan rahama ba, har lefe yayi
mata, ka ga rawar kai, sai dai babu kowa daga danginsa"
"Tun da dai shi ya ji ya gani, aishikenan ina yi musu
fatan alkhairi, yaron ma ni tausayinsa nake ji, a idonsa zaka ga yadda yake
ƙaunarta. A yadda na san shi yaro ne ɗan gata mai ji da kansa. Tun da na ga ya
sauke yana magiyar a bar masa rahama, na gane lallai yana son ta"
Nabila ta ce "Vi ba dai son girma ba, wai yaro, mijin
rammar ne yaro?"
"Ban girme shi ba?"
Cikin dariya ta ce "To kuma sai ka ce masa yaro?"
"Eh mana, an gaya miki ni na yau ne, na kama hanyar
40yrs fa"
Tayi dariya ta ce "Sannu dattijo"
"Eh faɗi ki ƙara beb, Allah ya sa ki samo mana baby da
wuri, kin ga na kama hanyar tsufa, in ga babyna, gashi ke ki na can ni ina nan,
da mun ƙara effort kuma mu yi ta addu'a"
Ta tura baki ta ce "Duk effort ɗin da saka bai isa ba
sai ka saka wani? You won't kill me"
Ya ƙanƙance idanunsa ya na kallonta, yana yi mata wani
miskilin murmushi.
"Menene kuma?" Ta tambaye shi a shagwaɓe.
"Maganarki ce ta bani dariya, Abbu ma fa end of this
month zai angwance in sha Allah"
Waro ido Nabila ta yi ta ce "Aure zai yi?"
Ya ce "Eh mana, za a ɗaura aurensu da maman ramma in
sha Allah, ni na nemi ya aureta, ita ma ta fi samun nutsuwa da kwanciyar
hankali"
"Au kai ka bashi shawara ya yi wa maman Shahida
kishiya, na ji daɗi amma ta wani fannin, baka tunanin yadda zamansu zai kasance
da maman Shahida, gata ba ta da cikakken hankali?"
Viper ya ce "Wacece ita da ba za ayi mata kishiya ba,
haifarsa tayi?"
"A'a Allah ya baka haƙuri, na ga haryanzu akwai wani
abu a ranka, game da matar nan, yakamata komai ya wuce"
"An gaya miki kowa irinki ne, wallahi ba zan taɓa
yafewa matar nan ba har abada, ina ɗaga mata ƙafa ne kawai saboda 'yar uwata,
amma ko da me take yawo ba zan yafe mata ba, ke sai anjima ma kin ɓata mini
rai"
"Allah ya baka haƙuri " bai jirata ba ya kashe
wayar sa.
Hafsa ta fara shiga damuwa, tun da ta koma gidan Alhaji
mu'azzam, ko canza date na period ɗin ta ba ta taɓa samu ba, ta duƙufa da
addu'a Allah ya sa tana da rabon samun haihuwa a rayuwarta, gashi kusan kullum
sai Anty ta kirata tana tambayarta, ko ta samu ciki, har abin ya fara ba ta
haushi.
Sosai Abdul yake nuna wa ramma soyayya da kulawa, sai dai ta
fara fuskantar ƙalubale daga dangin Abdul, babu wanda ya zo tariyarta, amma
suka fara zuwa wai ganin 'yar ƙauyen da ta yi wa Abdul asiri.
Abbu kuwa gidan da zai ajiye maman ramma daban, ba zai haɗata
da Rahila ba.
Sai dai tun da ya sanar mata da zai yi aure, hauka ya ƙaru
tuburan, kamar ta yi masa duka saboda azabar kishi, har da iƙirarin zata cinna
musu wuta a cikin gidan.
Viper ya zo gida hutu, ya samu labarin abin da matar Abbu ta
ce, ya ce sai ta koma gidansu an nema mata magani ta dawo, ba za ta ƙona masa
uba ba, ace ba ta da hankali, idan ba haka ba ruwansa da haukanta, zai saka a
fitar da ita daga gidan ta ƙarfin tsiya.
Har gida Shahida ta zo tana kuka, ta na bawa Viper haƙuri, a
kan yayi haƙuri, idan ta fita babu in za ta je.
Viper ya ce "Shahida ba ina ƙoƙarin tozarta
mahaifiyarki ba ne ba, amma da alama haryanzu karatun da duniya ta yi mata ba
ta ɗauke shi ba, amma ki yi haƙuri daga ke sai mahaifina ku ka rage mini, idan
ta ƙona shi ban san ya zan yi ba. Idan ba haka ba kuma a kaita asibitin masu
rangwamen hankali, har sai ta warke.
Shahida ta yarda da hakan, dan ita ma gani take, larurar ta
mahaifiyar ta ta, ƙara gaba take yi. Abbun ma ya amince a kan a kaita asibitin
ƙwaƙwalwa. Bayan kaita kuma su ka ce gado za su bata, har sai ta warke, a can
zata zauna.
Indabo hankalinsa ya kwanta sosai, jin ya zarta wata guda,
yana zaune lafiya a ƙasa mai tsarki, ya miƙe ƙafa ya ɗora da tsula tsiyarsa.
Nan gida Nigeria kuma aka ce, Indabo ya je neman lafiya ne,
bashi da lafiya, amma duk wasu allowances ɗin sa suna shiga account ɗin sa.
Wajen ƙarfe sha ɗaya, ya farka da kyar, kansa yana yi masa
wani irin nauyi, ya duba ɗakin ya nemi yarinyar da ya kwana da ita ya rasa.
Ya tashi da kyar yana dube-dube, duk ta kwashe masa abubuwa
masu muhimmanci ta gudu da su.
Ya duba gefen da ta kwanta, ya ga wani ƙaramin note.
"Ina mai farincikin sanar da kai, samun saƙon Naja'tu
Bunkure, ta ce ayi maka fatan girbar abin da ka shuka, a nan duniya da ma can
in da zaka"
Yana bankaɗa pillown da ta kwanta, ya tarar da ɗaurin hodar
iblis, kafin ya yi wani yinƙuri, ya ji ana buga ƙofar ɗakinsa.
Ayshercool
08081012143
https://chat.whatsapp.com/CHMyWTRhDYe8tdSLnXsezq
Kunaneman group din dazakuringa sarin kayan kitchen
afarashin sari yanda duyanda zaku karade kasuwa bazakusamu kasa d
farashinmuba!!! Kuyi joining a mai nono kitchen utensils and household domin
siyan dai dai ko sari dukkanin kayanmu available ne kuma farashi daidai
aljihunku siyan nagari....maida kudi gida...gaskiya d amana sune takenmu!!!
Ɓoye hodar ya yi, gabansa na tsananta faɗuwa ya nufi ƙofar ɗakin,
yana tambayar waye?. Shiru ba a bashi amsa ba, aka ci gaba da bubbuga ƙofar.
Ya buɗe ƙofar, yana buɗewa aka hankaɗo ƙofar, jami'an tsaro
suka shigo cikin ɗakin, aka hau caje ɗakin.
Ba ma wadda ya buɗe suka gano ba, wata jaka suka ɗaukko, ana
zazzageta sai ga miyagun ƙwayoyi da hodar iblis a ciki.
Rantse rantse indabo ya fara, cikin matsanancin tashin
hankali, ya rasa ma me zai ce, suka saka masa ankwa, suka ingiza ƙeyarsa suka
tafi da shi.
****
Nabila na ta rawar ƙafar shirin bikin Sumayya, sai dai
jikinta gaba ɗaya babu daɗi, wani irin nauyi jikinta yake yi mata ga kasala.
Shahara da ɗaukakar da ta yi, ya sanya take samun manya
manyan case, amma yanayin ɗawainiyar aure, ya sanya ta fara sarewa, gaba ɗaya
jin ta take ba a dai-dai ba.
Suka shirya ita da Viper ta kai shi gidan ramma, ta ji daɗi
sosai da sosai da zuwansu, dan ranar Abdul ma bai fita ba, da ta gaya masa za
su zo.
Abincin da ramma ta yi, Nabila ta ce ba ta ci, wai ta dafa
mata indomie ta cika attaruhu ta bata.
Ramma ta yi murmushi, ta ce mata to, ta dafa ta bata, ta ji
daɗin indomien sosai da sosai, dan a gida ba ta iya cin abinci.
A hanyar komawa gida, ta saka Viper ya saya mata ƙosai, suka
je gida ta dirarwa ƙosan nan, ta din ga ci da yaji tana suɗar baki.
Ya dawo daga sallar isha'i, ya tarar ta kashingiɗa, tana ta
lasar lemon tsami.
"Abla, idan ki ka ce mini cikin ki yana ciwo, ko kuma
ulcer, ko saurararki ba zan yi ba, kalli yadda ki ke azabtar da kanki da yaji,
ina kallonki har da barbaɗa yaji a kam man ƙosai kina lasa, yanzu kuma kina
shan lemon tsami ko?"
"Vi dan Allah kar ka yi mini baki mana"
"Ni dai na gaya miki ne"
Aikuwa hakan ce ta faru, kwana ta yi tana yawon banɗaki,
atini ya sakota a gaba, ga amai. Yana kallonta ya yi mata banza ya sha baccinsa
da daddare.
Da safe ma da kyar ta yi masa breakfast, almajirinta ta aika
chemist ya sayo mata ruwan gishiri da suga ta haɗa tana sha. Gaɓoɓinta duk suka
sage, wunin ranar ta kasa cin komai, indomien da ramma ta ba ta ce kawai take
dawo mata.
Cikin dare yana jin motsinta, tana ta sintirin toilet, har
ya basar sai ta bashi tausayi, yadda gari yayi tsit sai kakarin amanta kamar
zata amayar da kayan cikinta.
Ya je ya sameta a zaune dirshen a banɗaki, duk ta fita
hayyacinta. Dolensa ya fita ya bugawa maƙwabcinsa ƙofa yana da abin hawa suka
tafi da Nabila Asibiti.
Kwantar da ita aka yi, fatarta duk ta bushe ta zama
dehydrated, leɓenta ma ya bushe sosai.
Abinka da farin mutum, sai tayi busu-busu kamar korarriya.
Ga tausayinta ga dariya ta bashi, iya sintirin banɗakin da
ta sha ma, ya isheta punishment.
"Abla ko a sayo ƙosan ne?" Murguɗa masa baki ta
yi, ta lumshe idanunta, saboda har a lokacin cikinta hautsunawa yake yi.
Da safe Abdul ya shigo, yana ward round kawai ya ga su
Viper.
Ya ce "Ya aka yi ba a kirawo ni ba? Daga tafiyarku
shekranjiya har jikinta yayi haka?"
Viper ya ce "Eh, likitan da muka tarar yayi mata duk
abin da ya kamata ai, ba ta ji ne, ka ga gobe ba ta kuma ba, ba zata ci abinci
ba, sai ta zabga yaji, abincinma sai ta gama zaɓe-zaɓe, ko ba komai ai ta
hanamu bacci, in da na ji daɗi ta ji a jikinta ai, nan ɗin ne yafi mana kusa
shiyasa kawai muka yo nan"
Abdul ya yi murmushi ya ce "Gaskiya yakamata a tausaya
mata, wataƙila baby ne ya saka take hakan, bari na yi reviewing ɗin ta"
ita dai ba ta san me ake yi ba, bacci ya sake ɗaukar ta.
Gwajin farko ya tabattar da Nabila na ɗauke da juna biyu,
dama Viper jikinsa ya bashi, sai dai bai tabattar ba ya bar abin a zuciyarsa.
Abdul ya ce "Ka ga babynka ne ya sakata cin yaji, ka ke
mata dariya".
Cikin farinciki Viper ya ce "Har da rigimarta, da
kafirin kwaɗayinta"
Ya rasa in da zai saka kansa dan murna, shi yana ta
farinciki, Nabila na fama da kanta, atini ya tsaya amma jiki babu ƙwari.
Sai yamma aka sallame su, Abdul ya ɗauke su a mota zai kai
su gida.
Duk in da aka tsaya sai ta ce Viper ya saya mata abu, duk
sai dai ya kashe kuɗin jikinsa.
Tun da suka koma gida kuma, Nabila ta kwanta laulayi sosai
da sosai, ba ta cin komai, amai ya sakata a gaba, ga zazzaɓin dare. Jauhar ta
yi laulayi ita ma, amma Nabila ta fita laulayi nesa ba kusa ba, ko fita ta
daina yi, sai lokaci lokaci.
Viper ne yake ta kula da ita, yana roƙon Allah ya kare masa
ita da abin da yake cikinta su rabu lafiya.
Ya sanya yana da rabon ganin ɗan sa a duniya.
Sosai Viper yake ba ta mamaki, mutum ne mai tausayi, sai
lallaɓata yake yi.
Ranar wata juma'a, aka ɗaura auren Abbu da maman ramma,
hakan ya yi wa Viper daɗi sosai da sosai, su Major, Baba duk sun halarta, a
wurin ɗaurin auren Major ya haɗu da mahaifin liti.
Classmates ɗin sa ne, tare suka yi karatu, tun lokacin
secondary school, sun yi zaman mutunci, ɗakinsu ɗaya kuma kwanarsu ɗaya, tare
suke komai.
Rashin wayar hannu a wancan lokacin ya sanya zumuncin na su
bai ɗore ba, nan hira ta wanzu tsakaninsu, hirar yaushe rabo, da hirar ƙalubale
da kuma nasarorin da suka samu a rayuwa.
Rahila tana ji tana gani, aka ajiyeta a gidan masu rangwamen
hankali, Abbu kuma ya yi aurensa.
'yan kwanakin nan, kusan kullum idan Zakiyya ta kwanta
bacci, sai ta yi mafarki da Chubaɗo, hannunta rungume da jarirai guda biyu, ɗanyen
haihuwa, ƙafafuwanta duk jini, tana kallonta tana kuka.
Tun da ta rasu, ba ta taɓa mafarki da ita ba sai a wannan
lokacin, da fari ta maze ta basar da mafarkin, amma kuma ta ci gaba da yin sa a
kai a kai, har ya zamana tana yi mata gizo a zahiri.
Abu kamar wasa, ba iya ita take gani ba, wasu lokutan har da
jauhar, idan ta hange su, su na zaune su na cin abinci, da sun hangota
sai su nufota.
Kafin wani lokaci, ta yi wata irin rama, abin duniya ya
isheta, ta kasa gaya wa kowa halin da take ciki, ba ta iya cin abinci, ga wata
irin fargaba da faɗuwar gaba, sai ta din ga ganin kamar ita ma mutuwa za ta yi
a kowane lokaci.
Gaba ɗaya ta ji duniya tayi mata zafi, ba ta son komai, ba
ta jin daɗin komai, ta tsangwami kanta kuma ta kasa gaya wa kowa halin da ake
ciki, gashi tana murna yanzu miji ya zama nata, tun da mama na kwance tana
jinya, amma ita ma ta kasa jin daɗin rayuwar gaba ɗaya.
Kafin Viper ya auri Nabila, kallon mace mai son jiki yake yi
mata, kai ba ka ce ta iya wani abu ba, saboda yadda take a sangarce, amma sai
ya ga abin da ba haka ba, sam ba ta son ƙazanta, idan ya rage mata aikin gida
ya fita, idan ya dawo a hakan zai tarar ta lallaɓa jikinta, ta gyara ko ina,
har ma ta yi girki.
Kayansa za ta saka a inji ta wanke ta shanya, su bushe ta
bayar a goge masa.
Sosai yake jin tausayinta, gashi lokacin komawarsa bakin
aiki yayi.
Cikin kulawa ya ce "Abla ko dai tare zamu tafi ne, ko
na tafi hankalina ba zai kwanta ba saboda yanayin jikin nan naki"
"Komawa zaka yi, babu wani abu da zai faru in sha
Allah"
"Yanzu ko a gidanku, babu wani wanda za a baki, ya zo
ya tayaki zama?"
Tayi murmushi ta ce "Maraicin kenan Vi, ba sai na
gayyaci kowa ba, na san ba bani za su yi ba, Sumayya ce dai ta ce mini za ta zo
idan ka tafi, kar ka damu zan iya zamana"
Cikin kulawa ta ce "Abla ba kya cin abinci ai, duk kin
yi wani iri" yayi maganar yana shafa wuyanta. Langaɓe masa ta sake yi,
daurewa kawai take yi ne, dan kar ya ƙara shiga damuwa, dan kuwa har kuka take ɓuya
tayi, ganin yadda ba ta iya cin abinci, kullum cikin amai take.
Shi kansa Viper sai da ya tambayi Abdul, ko akwai maganin da
za a bata ta daina aman nan, ya ce masa sai dai ayi haƙuri, lokaci ne zata
daina.
Lokaci lokaci, ramma sai ta yi girki, ta ba wa Abdul ya biya
ya kai wa Nabila.
Har Viper ya tafi,
hankalinsa yana kan Nabila da ya bari, Sumayya ta kan zo ta ɗan tayata zama ta
kwanar mata biyu, ita kanta tana jin tausayin Nabila dan wani irin wahalallen
laulayi take yi.
Sai dai duk da halin da take ciki, kasancewar 'yar dagiya
ce, bai hanata kasawa tare da tsarewa ba, a duk lokacin da za a gabatar da
shari'ar Naja'atu Bunkure ba.
Dan ranar farko da Bunkure ta ga Nabila, sai da haɗuwarsu ta
farko ta dawo mata, bayan gama saurara Shari'a sai da Nabilan ta bita, ta ce
"Allon kwaikwayona, ina fatan a yanzu kin tabattar da Allah ne mai yi,
babu ruwansa lokacin da ya so, zai iya ɗaukko na can ƙasan da ba a iya hango
shi, ya ɗaukaka shi sai kowa ya ji shi, hakazalika ya ɗaukko na can saman ya
kai shi ƙasa, sai kowa ya manta da shi.
Ba zan ci gaba da bibiyar shari'arki dan fatan na ga bayanki
ba, sam, na gama nawa tun da na kai ki ƙasa, na bayyana wa duniya wacece ke,
zan bibiya ne saboda hakkin mutane da kuma jinin 'yar uwata da ki ka ce ya tafi
a banza" Bunkure ba ta iya mayar da martani ba, aka zunkuɗata cikin motar
masu laifi, aka tafi da ita.
*****
Duk ƙumbiya-ƙumbiyar da ake yi, da ƙoƙarin rufe abin da ya
faru, sai da abun ɓoye ya bayyana na kama Indabo da miyagun ƙwayoyi a ƙasa mai
tsarki.
Ramma tana zaune a falo, tana assignment, Abdul ya shigo
babu ko sallama, ya wuce ɗaki.
Ta bi bayansa tana faɗin "Yau kuma waye ya taɓo mini
bokan turai" idanunsa ne suka tabbatar mata akwai damuwa gagaruma.
"Doctor meyafaru kuma? Wani abin ne ya faru?"
Ya haɗiye wani abu mai ɗaci, ya dubeta ya ce "Daddy aka
kama a Saudiyya"
Ramma ta ce "Subhanallah, me ya yi aka kama shi?"
"Da miyagun ƙwayoyi aka kama shi, abin takaici wai a
ƙasa mai tsarki"
Ramma ta ce "Subhanallah, abin bai yi daɗi ba. Addu'a
ce yanzu ya kamata ayi, Ubangiji Allah ya fitar da shi"
Ya kalli ramma idonsa fal hawaye ya ce "Allah ya fitar
da shi how? Saudiyya ba fa Nigeria ba ce ba, duk laifukan da yake aikatawa ba
su isa ba, sai ya tsallaka ƙasa mai tsarki?. Har tsoro nake ji, ko idan ya koma
ga Allah idan na roƙa masa rahama Allah zai karɓa? Tarin mutanen da zalunta
saboda kujerar nam, a ina zai gansu ya nemi afuwarsu? Ni iyayena ne
jarrabawata, da ina da iko, da ban zo a tsatsonsa ba"
Cikin kulawa ramma ta fara rarrashin da bai kai zuciyarta ba
ta ce "Doctor, ba a yanke tsammani da rahamar Allah, kuma shi mai rahama
ne, dole a roƙa masa rahama tun da musulmi ne"
"Amma kin san Allah baya yafe hakkin wani a kan wani
ko? Yau ko tuba yayi ya daina laifukan da yake yi, waɗanda ya zalunta fa wasu
ba sa duniyar nan, sun bar ta, a wurin wa zai nemi yafiyar? Mutanen da ya
dasawa damuwa da baƙin ciki su na da yawa fa.
Allah mai rahama ne da jin ƙai, amma sai da ya haramta shi a
kan kansa, sannan ya sanya shi abin haramtawa a tsakaninmu, ke ki ka biya mini
wannan hadisin, ni babu wani abu da za a gaya mini yanzu na ji sanyi, ina
tausaya masa haɗuwarsa da Allah"
Jiki a sanyaye ramma ta ce "Ka yi gaskiya, amma yanzu
ai ba mutuwar yayi ba"
Ya kalleta fuskarsa duk hawaye ya ce "Kin san hukuncin
ace an kama mutum da irin abin da aka kama shi da shi a ƙasa mai tsarki? Muddin
suka tabattar hukuncin kisa ne" gaba ɗaya sai ta rasa me ma za ta ce. Har
ga Allah Abdul ya bata tausayi, amma ita ba ta ji ta damu ba ko kaɗan,
albarkacin Abdul ɗin ne ma bai sanya ta ce Allah ya ƙara a zuciyarta ba.
****
Hafsa ta biyo Alhaji mu'azzam, domin kawo ziyara gida, sai
dai ta tsorata da yadda ta ga jikin mama ya ƙara tsananta, ta zama wata irin
miskiniya abin tsoro.
Sai dai ta tsorata da ganin ita ma tata mahaifiyar ta yi
wata irin muguwar rama, gashi duk kauɗinta yanzu ba ta son yin magana.
Ga zaman ɗaki, cikin mamaki take tambayarta ko lafiya?
Ta fashe da kuka take gaya wa Hafsa abin da yake faruwa.
Tayi shiru sannan ta ce "Ikon Allah, kin ga kaɗan daga
illar biye-biye anty, yanzu an ce Anty Rahila tana gidan masu rangwamen
hankali, ni na fara yin ciwon hauka a sanadin shaye-shaye, ke ma kuma ga
alamu"
Ta waro ido ta ce "Hauka kuma?"
"Eh matsalar ƙwaƙwalwa, wannan alamomi ne na
depression"
"Wallahi na yarda da maganarki, wasu lokutan ji nake
kamar na fita da gudu ina ihu, duniyar tayi mini zafi, amma ni sai nake tunanin
ko matar nan ce duk da tana kwance, ta haɗa kai da yaranta suke banko mini
asiri"
Hafsa ta katseta ta ce "Mama babu wanda yake banko miki
wani asiri, ganin Jauhar da mahaifiyarta da ki ke yawan yi, yana alamta miki,
kin tafka mummunan laifi a rayuwarki, da babu lallai sun yafe miki, gashi ba sa
duniyar. Shawara ɗaya zan baki, ki din ga yi musu addu'a, sannan ki dage da
istigfari kuma ki daure, ki nemi afuwar Baba, sannan ki nemi afuwar ɗan uwanta
babansu Nabila, da ita kanta Nabilan, tun da duk su na da alaƙa da su, idan ki
na so ki samu nutsuwa. Sai kuma mu dangana da asibiti ki fara ganin
likita"
"Tabɗijan, kawai kuma sai na je ina cewa wani su yafe
mini, da na yi musu me? Wallahi ba zani ba"
Cikin takaici da mamaki, take bin Antyn da kallo, ta ce
"Ba zaki ba Anty, sai abin da ya samu babar su Shahida ya same ki
tukuna?"
"Ya daɗe bai same nin ba, ba zani ba, ni na san asiri
kawai ake yi mini, kuma ni dai-dai nake da kowane mara mutunci" Duk yadda
hafsa ta so ganar da ita, ta rufe idonta taƙi ganewa.
"To mu je asibiti, tun da nima kin ga da haka na warke,
da aka din ga kai ni Asibiti"
"Ba zani ba shi ma, ni na san maganin matsalata"
haka Hafsa ta ƙyaleta, dan babu yadda ta iya da ita".
Washegarin zuwanta ta tafi gidan Nabila, tayi sa'a Sumayya
ma tana can, haɗuwar ta su ta yi musu daɗi, sai dai a kallon farko ta ga Nabila
ta rame sosai, ba ta yi magana ba, Nabila nata nuƙu-nuƙu da hijjabi, amma sai
da Hafsa ta gano ta.
"Abla, wai me ki ke ɓoyewa ne? Duk ɓoyonki ana gani
ai"
Kunya ta kama Nabila ta ce "Ake gane me?"
"Ɗan baban mana"
Sumayya ta kwashe da dariya ta ce "Ai na gaya mata ana
gani, taƙi yadda, mai cewa sai ta yi good 2yrs a gidan miji, kafin ta ɗau ciki,
amma farawa da bisimillah"
Hafsa ta kwashe da dariya ta ce "Ai kura ta san gidan
mai babban sanda, ai ita ta san in da za ta iya cewa, sai ta shekara biyun ba
ta haihu ba, ba dai a gidan Viper ba"
Nabila ta ce "Baku da aikin yi ne, ulcer ce ta kumbura
mini ciki"
"Viper dai yayi ajiya, shi ya kumbura miki cikin"
Hafsa tayi maganar tana dariya.
"Ku da Allah, kuna munafuncin mijina a gabana, wanda
idan yana nan, ko tarin kirki ba zaku iya ba, a ƙyale mini shi kar a saka ya
ƙware, yana can yana aiki, kuna nan ku na gulmarsa"
Hafsa ta ce "Ke abin alkhairi ne ai, Ubangiji Allah ya
inganta miki ƙanwata, ya rabaku lafiya"
"Amin Anty hafsyna"
Sumayya ta ce "Shahida ma na ga kamar an gamu"
Hafsa ta ce "Nima ma gani, ai na je gidanta"
Nabila tayi dariya ta ce "Mijinta ce mini yayi baya son
saka ido mura take yi" suka yi ta hirarsu gwanin sha'awa, hafsa ta ce
"Dan Allah ku tayani da addu'a, nima Ubangiji Allah ya sa ina da rabon
ganin jinina a duniya, ni haryanzu shiru" suka yi ta kwantar mata da
hankali da yi mata fatan alkhairi.
Aka koma maganar bikin Sumayya, Hafsa na ta ƙara nanata
mata, kar ta kuskura ta je ta sha wani abu da ba ta san menene ba, alhalin ga
likitar mata.
Nabila ta ce "In dai ki na son daga shiga kema ki ɗaukko
magana, ki riƙe wa kayan likitar mata wuta, zaki gane baki da wayo, laulayi is
not your mate "
Hafsa ta ce "Rabu da ita, ta ji da assignment ɗin da
Viper ya bata"
Nabila na daga kwance a kan cinyar Sumayya ta ce "Wuta
balbal idan aka ƙira sunan mijina"
"An faɗa Aminu Viper, mai zamani"
"Ku da Allah"
Nabila ta dage ta din ga lallaɓa hafsa, sai da ta kira
Alhaji mu'azzam, suka kwana a gidan.
Ita dai kaf 'ya'yan babansu, da aka nuna mata, babu wanda
take jin tana so, kamar hafsa, ita dai tana ƙaunarta sosai.
Sai kuma suka koma hirar ƙalubalen rayuwar gidan auren, tare
da ba wa junansu shawarwarin da za su fishshe su.
Kwana biyun da suka yi mata ta ji daɗi sosai, bayan
tafiyarsu zaman kaɗaicin ya ci gaba da damunta.
Babu tsammani taga Viper ya dawo, aikuwa ta ji daɗin hakan.
"Vi ya na ganka ka dawo yau?"
"Shi ne lokacin da aka ce ki fara zuwa awo, ina lissafe
ni ai"
Tun daga Abuja ya taho mata da amala, saboda ya san tana
sonta, aikuwa ta ji daɗin amalar nan.
Ta ci kaɗan ta ga tayi awa biyu ba ta yi amanta ba, aikuwa
ta rufar mata, ta cinye tas.
Kwana tayi amai, ba ta yi baccin kirki ba.
Da safe ya buga wa Abdul waya, ya ce masa zai kawo Nabila
asibiti, ya ce masa to.
Abdul ya yi mamki, ganin cikin Nabila wata huɗu, amma ya ɗago
sosai.
Suka gaggaisa, ya yi mata sannu.
Viper ya ce "Ya ƙanwata?"
"Tana gida sun yi hutu, ga saƙo ma ta bani, wai na
kawowa yayarta" yayi maganar yana nuna musu fulas ɗin abinci.
"Ko menene a ciki, in dai yaji yayi yawa ba zaki ci ba,
bar rawar jiki" yayi maganar yana harar Nabila.
Tashi Nabila ta yi, ta buɗe flask ɗin, ƙamshin miyar jajjage
ya daki hancint, tayi maza ta rufe dan da alama miyar mai yaji ce.
Abdul ya ce "Ina ce mata zaku zo, ta zaunar da ni sai
na taho miki da abinci"
Viper ya ce "Duk in da muka je, har rawar jiki take ace
mata ga abinci, kamar ba na ba ta abinci a gida"
"Bana ƙoshi ne" tayi maganar tana dariya.
Abdul ya ce "Maybe na gidanta ba ta iya ci, idan suna
irin wannan halin sai haƙuri ai"
Viper ya ce "Haka ne, amma ya na ganka wani iri, ko
baka da lafiya ne?"
Bai ɓoyewa Viper ba, ya gaya masa komai, Viper ya ce
"Irin haka sai haƙuri, kuma ka ci gaba da addu'a, kuma kai ka kiyaye
aikata makamantan laifukan da ya aikata"
Kalaman Viper dai babu tausayawa ga Indabo, amma rarrashi ne
ga Abdul.
Ɗakin scanic suka tafi, bayan an yi wa Nabila gwaje-gwajen
masu ciki.
Viper yana tsaye a kan Nabila, yana riƙe da hannunta.
Abdul yake gaya wa Viper, doctor Muktar ya tafi ƙaro karatu
malesia.
Abdul yana cikin maganar ya yi murmushi, ya kalli Viper ya
ce "Congratulations bani goron Albishir"
"Albishir ɗin me? Bayan dama can na san da akwai
cikin?"
Abdul ya ce "Ba zan faɗa ba ne, sai ka bani
tukuici"
Viper ya ce "Faɗi sai a baka"
"Naƙi wayon, kawo kawai"
Viper ya yi murmushi ya zaro dubu ɗaya ya ajiye masa ya ce
"Faɗi idan yayi mini sai na ƙara maka"
Abdul ya ce "Ai kai ne mayar da tukuicin, ai albishir ɗin
namu ne gaba ɗaya. Twins ce dama ita ai ko?" Viper ya jinjina masa kai.
"So congratulations, babynta biyu ne a cikinta, twins
ne yaran"
Waro ido Viper ya yi yana kallon screen ɗin injin scanic ɗin,
tamkar zai gane menene a jiki.
Jikinsa ya hau wata irin tsuma ya ce "Dan Allah da
gaske ka ke ko da wasa?"
"Yaya zan yi maka wasa da abu mai muhimmanci har haka?
Wallahi da gaske nake, twins ne, kuma duk su na cikin ƙoshin lafiya"
Viper ya miƙe ya yi sujudar godiya ga Allah, ya miƙe ya rasa
me ma zai yi ko ya ce.
Ya kwance agogon hannunsa, ya ajiyewa Abdul, ya zaro ɗaya
daga zobensa na azurfa shi ma ya ajiye masa.
Ya fara laluba aljihunsa, Abdul ya ce "Haba Viper,
yanzu mun zama ɗaya sirikina ne fa kai, ina tayaka murna, Allah ya inganta ya
raba lafiya, amma ku yi shiru kar wanda aka gaya wa biyu ne. Ga agogonka da
zobenka ba zan karɓa ba"
Viper ya yi ajiyar zuciya ya ce "Kar mu yi haka da kai,
yarana biyu na rasa, ɗaya aka yi ɓarinsa, ɗaya kuma bai ma zo duniyar ba, yanzu
Allah ya haɗa mini biyu. Na ma rasa wane irin farinciki zan yi ne, ba kai ka
bani ba, saƙon kawai ka gaya mini, amma ba ka ji zuciyata ba, Alhamdilillah ala
kulli halin.
Na rasa jauhar, ga Nabila, na rasa yarana ya bani biyu Allah
Alhamdilillah. Yayi maganar yana goge ƙwalla.
Jikin Abdul ya yi sanyi, da ya tuna babansa ne silar ajalin
matar Viper.
Ya tuna lokacin da yake yi wa Viper kallon ɗan jagaliya, ɗan
maula ƙasƙantaccen mutum da yake zuwa maula wurin mahaifinsa, yau gashi Allah
ya canza komai, ya nutsu ya zama mai bayar da gudummawa ga al'umma.
Ya ƙarasa ya ɗago Nabila, yana mata sannu.
"Abincina" tayi maganar kamar ƙaramar yarinya tana
kallonsa.
"Ai dole ma a ɗaukko abincin nan Abla"
"Kuma ka gaya musu su daina damuna, ko in ƙi
haifarsu"
Cikin murmushinsa da yake ƙara masa kyau ya ce "Za su
daina in sha Allah"
Abdul ya ci gaba da yi musu fatan alkhairi, da taya su
murna.
Tun da suka koma gida, duk in da Nabila ta yi sai ya bi ta
da kallo, yana tunanin yara biyu ne a cikinta.
Addu'a ya din ga yi, Allah ya sa yana rabon da ganin yaran,
tare da yi musu fatan shiriya tun kafin su zo duniya, da fatan Allah ya sa kar
laifukan da ya aikata su shafi yaransa.
Nabila tunani ta din ga yi, na abin da za ta yi, da zai
wayar wa da al'umma kai, a kan muhimmancin neman 'yancinsu, da ƙirƙiro abubuwan
da za su taimaka wurin ƴaƙi da harkar daba da shaye-shaye da kuma bangar
siyasa.
Yanayin shirin bikin Sumayya da suke yi, ya hanata zama su
tattauna yadda yakamata, ta na son ta yi magana da Viper ma, domin za ta so
goyon bayansa ɗari bisa ɗari a kan abin da take ƙudurin yi ɗin.
Aka yi taron bikin sumayya lafiya, aka gama lafiya, ita ma
mijinta mutum ne mai rufin asiri, ya na da mace ɗaya da yara uku, cousin ɗin
Alhaji mu'azzam ne, shi ne ya haɗa shi da ita ma.
Major yana ta mitar Nabila kwana biyu ba ta zuwa gaishe shi,
ya kirata ya ce mata shi zai zo ya ganta, amma ta ce masa ba ta nan, sai dare
zata dawo.
Bayan sallar isha'i kuwa sai gashi shi da Anty, tun da suka
zo ta manne a wuri ɗaya ta ƙi tashi.
Viper ya yi wa Major zancen rabon gadon Jauhar, za a sayar
da kayanta, Nabila ta ce ba ta son kaya.
Abba ya ce "Ni idan an yi wa kayan kuɗi a bani na saya,
sai mu bayar sadaka Allah ya kai mata ladan".
Viper ya ce "Ita ma ta ce kuɗin, ayi wani abu da su,
Allah ya kai ladan kabarin Jauhar"
Major ya ce "Hakan ma yayi kyau, amma a ajiye wani abu
da za a din ga tunawa da ita dai"
"Eh in sha Allah, ko ma muje gidan tare, sai na yi wa
Baba magana muje a duba"
Major ya ce "Duk yadda ka yi yayi, Allah ya saka maka
da alkhairi kai ma, Allah kuma ya ƙara bamu haƙurin rashin Jauhar da
mahaifiyarta"
Har suka gama abin da za su yi, Nabila taƙi yi musu rakiya,
sai Viper ne ya raka su, suna tafe a hanya Major yake mitar Nabila duk ta zama
so silent, ko dai akwai wani ne da take ɓoyewa.
Anty ta ce "Ciki ne fa da ita, take ta wannan
nuƙu-nuƙun"
"Kaii ciki, tun yanzu?"
Anty ta ce "Ahh ikon Allah, wata nawa da yin
auren?"
"Lallai Major, wato Arfa ce 'ya, mu a shekara nawa muka
haihu?"
Ya ce "Ai ku tun zamanin baya ne, ita kuwa kamar yayi
wuri, haryanzu ƙanƙantarta nake gani"
"Shekara ashirin da shida?"
"Eh mana, rainon ciki akwai wahala, kin ga ita ga ba
uwa, ku ba tayi sakewar da za ta tunkaroku da wannan maganar ba, balle ma idan
wani abin ne ku taimaka mata ba, bari na koma gida, zan kirata a waya, ko da
wani abu da take buƙata"
Waro ido ta yi ta ce "Sai ka tambayeta a kan
cikin?"
"To shi ne me? Ni uwar ni ne uban, ai cikin halak ne,
mijinta ba mazauni ba ne ba, cikin fari ba ta san kan komai ba"
"Amma ai ka bari mu mu tambayeta ko"
"Tsakaninki da Allah yaushe rabonki da ita, ban da yau
da na ce ki zo ki rako ni wurinta? Ni ba abin kunya ne a wurina ba, idan ta
kama na dawo da ita gida, gani gata magajiya ta din ga kula mini da ita, ba
ruwanku" Anty ta ja bakinta ta tsuke, dan ba ta ga tsari a hakan ba.
Aikuwa kamar yadda ya faɗa, hakan aka yi, bayan ya koma gida
ya kira Nabila yake tambayarta. Kasa ba
shi amsa tayi, ta ji tamkar ta nutse a wurin, saboda kunya.
"Idan kin san akwai matsala, ni sai na yi wa mijin naki
magana, idan baya gari ki taho gida, ko na turo miki magajiya, ta din ga kula
da ke"
"Abba yana kula da ni, baba Magajiya kuma yakamata ace
zuwa yanzu ta huta ita ma, ina iya yin komai ma"
"Kin tabatta?"
"Eh Abba"
"Arfa ba na son kawaicin nan naki, Ni babu kunya a
tsakanina da ke, baki da uwa a raye, kar ki bari wani abu ya shige miki duhu,
idan ba zaki iya kirana a waya ba, ki yi mini message kin ji ko?"
"To Abba"
"Allah ne mai komai, amma ba zan so ki sha wahalar da
mahaifiyarki ta sha ba"
"In sha Allah"
Ya ce "Yauwwa, sai da safe, ki gaida mijin naki, Allah
ya yi muku albarka gaba ɗaya"
"Amin mun gode, ayi wa Anty ya ta je gida" ta
kashe wayar, Viper ya na kusa da ita, ya na saurarenta.
"Abla" ta waiwayo ta ce "Na'am"
"Kowane dangi, idan aka samu irin Abba ko guda ɗaya ne,
mai jajircewa a kan zumunci, ba tare da kallon ɗora wa kansa ɗawainiya ne ba,
da an rage wani abin. Mutum ne mai zafi, amma jajirtacce ya san abin da yake
yi. Ke kaɗai sadaƙatul jariya ce a gare shi ko bayan ransa. Banda ladan zumunci
hatta taimakon da ki ke yi wa al'umma yana da lada. Kin tsayawa dattijon nan
babu ko sisi, kin tsaya wa rahama, kin tsaya mini duk babu ko sisi, kin
siffantu da wasu daga cikin kyawawan ɗabi'unsa, da shi da Alhaji mu'zzam, da
Walid da liti, mutane ne da al'umma ke buƙatar irin su."
Nabila ta ɓata fuska ta ce "Ban da liti dai"
"Haba masoyiyya, ya fa baki haƙuri. Wallahi Abdallah
mutumin kirki ne fiye da yadda ki ke zato, kawai dai mutum ne da babu ruwansa
da kara, zai yi abin da yake so ne, ko yayi maka daɗi ko ya kashe ka, bai damu
ba"
"Ai na ga alama, ni fa ban taɓa zaton ya na barkwanci
ba, ranar da na fara ganinsa, a tal'udu wurin da yake sayar da katin waya, amma
kayan maye yake sayarwa, sai da na tsorata.
Babu alamar ɗigon imani a tattare da shi, sai fa da ya ce
sai ya kashe ni, idan na sake zuwa"
"Wallahi ba haka yake ba, sharrin ƙwaya ne kawai da
kayan maye, Allah dai ya ƙara shirya mu, rayuwa duk ta fi yi mana daɗi a yanzu.
Mutane kowa yana sonmu, yana son haɗa alaƙa da mu, har ana ɗora mana wasu
nauye-nauye.
Duk a baya, mu kanmu bamu jin cewa, a duniyar da mutane suke
muke, hango duniyarmu muke yi daban, saboda kowa kallon mutane marasa amfani
yake yi mana. Marigayiyya ce ta fara ƙoƙarin ankarar da mu, muhimmancinmu a
cikin al'umma."
Nabila ta jinjina kai ta ce"Jauhar ta yi namijin ƙoƙari
ƙwarai da gaske, kuma in sha Allah, yana daga cikin abin da na ƙudurce a
zuciyata, ci gaba da yaƙi da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, ta hanyar nuna wa
wanda suka tsinci kansu a harkar, su ma 'ya'ya ne, kuma akwai amfanin da za su
yi wa al'umma.
Ina son da ni da kai, sa sumayya, barrister Habib, da wanda
suka kamata, mu ga abin yi, idan ta kama ko ƙungiya ce mu kafa, ko mutane goma
ne suka shiryu a sanadinmu, mun yi nasara"
"Duk a bar wannan maganar, sai Allah ya saka kin sauka
lafiya, sai ayi ta, tunani mai kyau sosai da sosai. Sumayyan nan taki ma 'yar
aljanna ce da yardar Allah, na ga tana yinki saboda Allah"
"Ko ba Sumayya ba, ba ka ga Abba ne yayi waliccin
aurenta ba ma, ƙawar amana kenan, ina alfahari da ita"
Haka Viper suka ci gaba da tattaunawa da shi da abar
ƙaunarsa.
Kwanci tashi asarar mai rai, cikin Nabila ya yi watanni
shida, amma kamar zata haihu a lokacin, saboda girma, hakan ya saka ta daina
fita gaba ɗaya, saboda nauyin cikin.
Shahida kuwa matar Walid, ta fita nauyi, dan ita nata ya
kusa shiga watan haihuwa.
Ramma na gida ta dawo daga makaranta, tana ta sauri ta gama
abin da take yi, ta san Abdul ko ya dawo, ko ya aiko a ɗaukar masa abinci.
Kiran waya ta gani, da baƙuwar lamba, ta ɗaga tare da yin
sallama.
"Matar doctor Abdul ce?"
"Eh nice"
"Ok, dan Allah maza ki taho Asibiti, Doctor ne ya yanke
jiki ya faɗi"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ta furta
jikinta yayi wani irin sanyi.
Ayshercool
08081012143
https://chat.whatsapp.com/Jw9x9Jylpwo65O7OXBCVvL
Kunaneman group din dazakuringa sarin kayan kitchen
afarashin sari yanda duyanda zaku karade kasuwa bazakusamu kasa d
farashinmuba!!! Kuyi joining a mai nono kitchen utensils and household domin
siyan dai dai ko sari dukkanin kayanmu available ne kuma farashi daidai
aljihunku siyan nagari....maida kudi gida...gaskiya d amana sune takenmu!!!
Zaku iya tintibarmu t wnn number 09135298054
Jikin ramma tsuma ya din ga yi cikin matsanancin tashin
hankali da damuwa, fargabarta Allah ya sa ba wani mummunan abin ne ya faru da
shi ba, dan kuwa yanzu a duniya tana matuƙar buƙatar Abdul a cikin rayuwarta.
Ko rasa shi tayi, ta san abu ne mai wahala samun mijin da
zai tsaya a kan lamuranta kamarsa.
Hijjabi kawai ta zura ta fice daga gidan ta tafi asibitin da
ya ce mata zai je ganin marasa lafiya.
Har an bashi ɗaki, yana kwance ana ƙara masa ruwa. Cikin
tashin hankali da damuwa, take tambayar meyasame shi.
Wani likita yake yi mata bayani "Bamu sani ba, ya gama
ganin marasa lafiya, aka kira shi a waya, ba mu san me aka ce masa bai fi
mintuna sha biyar ba ya faɗi, amma ya farfaɗo ɗazu har yake ta kiran sunanta,
aka yi masa allurar bacci.
Ta ɗauki wayarsa, ta saka thumb print ɗin ta, ta buɗe wayar.
Call log ɗin sa ta duba, ta ga wanda suka yi waya ta ƙarshe
da shi Honorable speaker ta gani.
Ta kalle shi, ta san ba zai wuce a kan maganar mahaifinsa ba
ne ba.
Tausayin sa ya kamata, ta matsa kusa da shi tana shafa
kansa, yanzu da ya nutsun nan, har wani kyau ya yi na musamman.
Rashin ji da gagara ba su da wani amfani.
Aka kira sallar la'asar, ta shiga banɗaki ta yi alwala, tana
fitowa taga Mummy da Anty Jidda a ɗakin.
Mummy ta ce "Ga shaiɗaniyar yarinyar nan"
Jidda ta kalli ramma, yarinyar da take mata aiki,
wahalalliyar 'yar ƙauye tayi ƙiba, fatar nan tayi kyau.
"Ramma, ke nake gani haka?"
Ramma ta dake ta ce "Eh, nice anty Jidda, kin yi zaton
tozarcin da ki ka yi mini Allah zai wulaƙanta ni ne? Ai shi Allah yana kishin
bawansa"
"Ramma ni ki ke gaya wa haka?"
"Ai ba tun yau ba, na daɗe ina fatan Allah ya haɗa ni
da ke, na gaya miki abin da yake raina. Duk bauta da wahalar da nake yi miki da
yaranki, iftila'i ya same ni a gidanki, ki nuna baki sanni ba, in haɗu da ke
ma, ki ka toshe kowacce irin kafa, ki ka wulaƙanta ni, aka hana mu shiga gidan
ma, babu wata magana mai daɗi ko rarrashi, saboda ni baitil mali ce mara
galihu. To da yake shi Allah ba yadda ba ya juya lamuransa ai yanzu ku na gani,
ko iftila'in zawarci ma ya ishe ki"
Buɗe baki suka yi su na kallon ramma.
Ko a jikinta ta sake cewa "Wallahi darajar mijina ki ka
ci anty Jidda, amma niyya na yi na roƙi Allah ya sa yi wa 'yar ki abin da aka
yi mini, a kan idonki ki ji abin da ni da uwata muka ji, sai dai kash ƙaddara
ta riga fata, yaranki ba su suka yi mini laifin ba, kuma wanda ya yi laifin ya
yi tuba na haƙiƙa, kuma na yafe masa har gaban abada, amma ba dan haka ba ba
zan gushe ba ina yi miki fatan Allah ya jarrabeki ke ma, ko alhakin mai gadinki
da aka kashe, ya isheku nauyi".
Mummy ce ta fara zage-zage, ramma kuwa ta tayar da salla,
tare da jin sassauci a zuciyarta ko ba komai yau ta amayar da wani abu da yake
ci mata zuciya.
Wani likita ne ya zo yayi musu magana, a kan ko su yi shiru
ko su fita, Abdul yana buƙatar hutu.
Anty Jidda dai azabar mamaki ya hanata magana, kallon ramma
kawai take yi, yarinyar da magana ma wahala take yi mata, amma ita ce ta zama
haka take gaya mata magana.
Ramma ce ta hango Abdul yana motsi, ta tashi ta nufe shi da
sauri, su Mummy ma suka yi kansa.
"Doctor, meyafaru ne? An kira ni aka ce mini ka faɗi"
Babban abin da ya ƙular da Mummy bai wuce yadda yake kallon
ramma ba, ko ya nuna ya gansu.
"Rahama, embassy na Nigeria sun yi iya yin su an shiga
an fita, ba za a iya fitar da Daddy ba, za a gurfanar da shi a gaban kotu"
yayi maganar muryarsa na rawa.
Salati suka saka gaba ɗaya, dan su ba su ma sani ba sai
yanzu.
Ramma ta riƙe hannunsa ta ce "Ka yi haƙuri Abdul,
kowace rai akwai kalar jarrabawar da Allah subhanahu wata'ala yake yi mata, ka
yi haƙuri.
Mummy ta ɗora hannu a ka ta fashe da kuka, ta ciro wayarta
tana dannawa, Jidda na ta ba ta haƙuri, ramma a ranta ta ce "Allah ya
ƙara, kaɗan ma ku ka gani, ni kam Allah ya ƙara shirya mini kai ya kare mini
kai da ci gaba da aikata duk wani mugun aiki.
A zahiri kuma ta ci gaba da rarrashinsa, tana kwantar masa
da hankali.
*****
Rahila Allah ya taimaketa, aka sallamota daga asibitin masu
rangwamen hankali, sai dai duk tayi wani iri, tsufanta ya fito sosai da sosai.
Shahida ta zauna ta yi ta mata nasiha a kan tayi haƙuri, ta
kwantar da hankalinta, kar ta ɗorawa kanta kishi, idan ba haka ba ta bari Abbu
ya saketa ba ta da wurin zuwa ta zauna.
Shi kuwa Abbu, hankalinsa ya kwanta, Al'amin ɗin sa ya zama
mutum, ya nutsu ya shiryu, ga maman ramma sam ba ta da damuwa da hayaniya, su
na zamansu lafiya.
Abdul ya takura a asibiti shi a sallame shi, da aka sallame
shi su ka koma gida, ko fita baya iya yi, abinci ma sai ramma tayi da gaske
yake iya ci.
Ta kira mama ta gaya mata, mama ba ta taɓa zuwa gidan ramma
ba sai lokacin, suka je tare da Abbu.
Duk da da sauran pain ɗin abun da Abdul ya yi musu a
zuciyarta, amma sai da ya bata tausayi.
Ta din ga jinjina girman ikon Allah, ganin katafaren gidan
da rammar ke ciki, komai na jin daɗin rayuwa dai-dai gwargwado akwai shi.
Su ka jajanta musu, Abbu ya yi ta yi masa nasiha, tare da
nusar da shi muhimmancin addu'a da kuma juriya.
****
Nabila kuwa na ta rainon cikinta, da aka raba kayan jauhar,
kayan jariran da suka saya, ya faɗo a rabon Nabila, ya tambayeta ta na so ko a
sayar a bata kuɗin, ta ce kayan take so.
Major buni-buni, sai ya zo gidan Nabila ya dubata, cikin nan
yayi girma sosai da sosai.
Gaba ɗaya ta zauna a gida ta daina fita, saboda duk wanda ya
ga cikin sai ya yi magana.
Liti ya saka babansa a gaba, tun da ya ga ya san Major, yake
ta yi masa nacin, yaje ya tambayar masa auren Walida, amma babansa yaƙi ya ce
sai ya ga kamun ludayinsa sai ya ƙara hankali.
Abbu ya samu mahaifin liti ya ce masa shi ne yake tare da su
a kasuwa, liti ya yi hankali sosai da sosai, kuma shekarunsa ja suke yi.
Da kyar ya amince ya yi wa Major maganar, amma ya yi masa
bayanin komai.
Major ya ce "Ai ɗanka nawa ne prof, kuma tun da shi ma
ya shiryu haka muke so, in dai yarinyar ta na son sa, Ubangiji Allah ya
tabattar mana da alkhairi, dama tuntuni yayarta Nabila ta fara yi mini
zancen, idan kun shirya ku zo ayi magana kawai"
Liti har gida ya je ya gaya wa Nabila Major ya amince ya
bashi auren Walida, tare da ƙara yi mata godiya, bisa ƙoƙarin da ta yi masa.
Cikin Nabila na ganin gata, domin kuwa tuni a wannan karon
ma Viper ya fara sayayyar kayan jariri, idan ya tambaye ta zaɓi, sai ta ce ita
duk abin da ya saya shikenan, ita dai damuwarta ta rabu da cikin nan lafiya.
Shahida ce ta fara haihuwa, matar Walid, daga kai ta asibiti
cikin dare tana ciwon baya, aka ce ai ta kusa haihuwa, abin har mamaki ya
bashi.
Viper ba ya gari, Nabila kuma ta yi nauyin da ba za ta iya
fita ba, Walid baki yaƙi rufuwa, wai shi ne ya zama uba, Allah ya bashi ɗa
namiji.
Liti har ya fishi murna, kamar ɗansa, ya din ga bin sa yana
cewa "Saura ka saka masa sunan Viper, alhalin gani, sunana zaka saka
masa"
"Kai a wa?"
"Ni a baban yaron mana, dan Allah Walidi ka saka masa
sunana Abdallah, na san rashin m ɗinka, tsaf zaka saka masa sunan Viper, dan
muraran ka ke nuna fifikon ka fi son sa a kaina"
Kafin suna Viper ya zo gari, Nabila ta so ta bishi ta je ta
ga yaron, amma ya ce ba zata fita a din ga tanka ta ba.
Viper kamar ya tafi da yaron, ya din ga addu'a Allah ya nuna
masa na sa haka shi ma.
Yayi masa addu'a sosai da sosai yaron.
Walid ya sanya sunan mahaifinsa Umar.
Dubu ɗari Viper ya bawa Walid, ya ce masa yayi haƙuri,
abubuwa ne sun yi masa yawa.
Yanayin jikin Nabila, ya sanya Major ya tura Baba magajiya
ta zauna da ita.
Sai dai idan Viper yana nan 'yar kallo take zama, sai dai ta
yi ɗan aikace-aikacen gida. Hatta wanka sakata yake a toilet ɗin ƙurya ya
wanketa, undeas ɗin ta, idan ta cire duk shi yake wanke mata.
Shi kansa ba ƙaramin tausayi take bashi ba, idan ta zauna
shi ma cikin nasa zaman yake yi.
Zama sai da dabara, tashi sai da dabara, haka bacci ma,
gashi tun da ya ƙara tsufa, take fama da matsalar numfashi, dan ma ba ta da
yawan complain, sai dai shi ya fuskanci akwai matsala.
Sanin alaƙar da take tsakanin Sumayya da Nabila, ya sanya
mijinta ba ya damuwa, da yawan zuwa gidan Nabila da take yi, duk wanda ya ganta
sai ya tausaya mata.
Duk shagwaɓa da rigimar Nabila idan ba ta da lafiya, yanzu
babu, sai dai idan an yi mata sannu ta yi murmushi kawai, gaba haka kurum take
jin ta sare, kamar mutuwa za ta yi idan ta zo haihuwa.
Duk da ita ce abin tausayi, amma tana tausya wa Viper sosai
da sosai, bawan Allah sai ya zauna ya zuba mata ido, duk motsinta tausayinta
yake ji, da ta motsa zai tambayeta me take buƙata, me take so.
Har nauyinsa take ji, ta ce tana buƙatar wani abu.
Ana haka mama uwargidan baban su Nabila, Allah ya karɓi
rayuwarta, duk unguwa ba in da zancen jinyar wulaƙancin da 'ya'yanta su ka yi
mata bai je ba.
Nabila tana ji tana gani, babu roƙo da magiyar da ba ta yi
ba, Viper ya ce sai dai ta yi addu'a daga gida, ba zata je ko ina ba.
Mutuwarta ta ƙara razana Zakiyya, ta din ga ganin saura ita.
Watan jaririn Walid biyu, Nabila ta fara naƙuda, tun cikin
dare suka tafi Asibiti, amma har garin Allah ya waye ba ta haihu ba.
Tun da aka gaya wa Major da sassafe sai gashi a asibitin, ya
zo ya tarar da su da Viper da baba magajiya, an fito da Nabila tana zagaya wa,
ta samu wuri ta zauna a jikin Viper saboda ta gaji da zagayen.
Viper na gaida shi, amma bai ji ba, hankalinsa na kan
Nabila, ya riƙe hannunta ya ce "Sannu Arfa na, ya jikin?"
"Da sauƙi Abba"
"Allah ya rabaki da cikin nan lafiya, ki ci gaba da
addu'a kin ji, muna taya ki"
Ta jinjina masa kai, mai haɗe da yaƙe.
Duk wanda ya wuce ya ga Nabila, sai ya sake waiwaiwayawa ya
kalli cikin nan.
Shahida ta kira wayar Nabila, dan tun yammacin jiya ta
kirata take tambayarta, wai ya mutum yake gane naƙuda yake yi.
Viper ne ya ɗaga ya sanar mata su na Asibiti.
Shahida ta gaya wa Walid, lokacin bai fita kasuwa ba, ya
cewa liti ya wuce kasuwa, zai fara biyawa ya duba Nabila, liti ya ce
"Saboda ka rigani ganin ɗan mai zamani ko? To baka isa ba"
A asibitin suka haɗu, Walid jikinsa yayi sanyi, dan bai
manta yadda Shahida ta din ga fama ba.
Liti ya zata abin wasa ne, ganinsu a zaune a harabar wurin a
kan kujera, har tana shan shayi.
Wata Nurse ta fito ta ce mata ta daure, ta tashi a mayar da
ita labor ward a sake dubata.
Da Nabila ta miƙe sai da gaban liti ya faɗi, tare da mamakin
yadda aka yi tayi rayuwa da wannan cikin, duk da da hijjabi a jikinta.
Su na tafe idan ciwon ya motsa sai ta rirriƙe Viper, tana
yarfa hannu tana ambaton Allah.
Liti ya ce "Walid gaskiya tafiya zan yi, idan ta haihu
ka kira ni a waya,na ci gaba da zama a nan kuka zan yi, wallahi na zata
haihuwar ba wahala"
Walid zai yi magana ya ga da gaske hawaye ne a idon liti,
wanda liti da bakinsa yake cewa shi fa sai a shekara ko ƙwalla bai yi ba.
Wasa-wasa har Baba sai da ya zo asibitin, Nabila ba ta haihu
ba, Viper ji yake kamar ya tayata ciwon, tun da cikin nan ya samu a wahala
take.
Idan ta gaji, sai ta fashe da kuka, sai dai Viper ya yi ta
rarrashinta, yana ba ta haƙuri.
Har sai da ya cewa Abdul, ko ayi mata tiyata kawai.
Abdul ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri, lokaci ne zata
haihu da kanta in sha Allah, haka kowace mace take ji. Babu tangarɗa a laborn
dan haka a ƙara haƙuri.
Sai da ta kusa daf, sannan aka ce Viper ya fita waje, ya din
ga sintiri a bakin ƙofa, yana addu'a, sai dai ya din ga tuna Jauhar, yana
fargabar Allah ya sa kar wani abu ya samu Nabila da yaran.
Doctor Abdul Yasar, ma'aruf Indabo, shi ya karɓi haihuwar
Nabila, ta sha wahala sosai da sosai. Dan bayan da jaririn ya faɗo, sai da ta
kuma wani ciwon sannan ta biyun ta faɗo.
Hamdala ta din ga yi, tana yi wa ma'aikatan godiya, saboda
gudunmawar da su ka bata.
Abdul ya ɗora mata jariran a kan ƙirjinta, ta rungume su,
kawai ta fashe da kukan murna.
"Ya haiyyu ya ƙaiyyum ya zuljalalu wal ikram, ya
Ubangijin Al'arshi ya Allah duk mai neman haihuwa in dai alkhairi ce , Ubangiji
Allah ka bashi yara masu albarka, Allah ka bashi yara masu jin ƙai ababen
alfahari ga addinin musulunci, Allah duk mai nema ka bashi, kamar yadda ka
azurta Annabi Zakariyya Alaihissalam a lokacin da ya roƙeka. Allah na gode maka
da wannan ni'ima, Allah ka raya mini yarana, ka shirya mini su"
Su ka din ga amsawa Nabila da Amin.
Viper ne kaɗai a wurin da labor room yake, su Major su na
can waje.
Nabila ta sha ɗinki ciki da waje, ta ji yadda gaba ɗaya ɗakin
ya cika da ƙarnin ƙazantar haihuwa, amma daga Abdul har Nurses ɗin, babu wanda
ya nuna ƙyamar sa a gareta.
Aka shirya yaran tsaf, ita ma aka shiryata, ya basu wuri,
nurses ɗin suka ƙarasa taimaka mata, ta shirya, aka yi mata allurai aka fito da
ita.
Aka wuce da ita postnatal room, ana miƙo wa Viper yaran,
amma bai bi ta kansu ba, ya nufi in da aka shiga da Nabila.
"Abla" ya kira sunanta.
Ta ɗago idanunta da suka yi jawur saboda wahala, ga bacci
tana ji.
Rungumeta ya yi yana shafa kanta ya ce "Sannu my love,
Ubangiji Allah ya yi miki albarka, ya dauwwamar da farinciki a rayuwar
aurenmu"
Cikin shagwaɓa ta ce "Vi na sha wahala"
"Na sani sweetheart, na gani, sannu Abla. Alhamdilillah
ala kulli halin. Na gode, na gode my world" yayi maganar yana sumbatar
goshinta.
Hannunsa ta riƙe ita ma ta ce "Ni na gode da kasancewa
tare da ni, ba tare da ƙosawa thank you very much" ya riƙe hannun nata
sosai ya ce "Lokacin Jauhar na raye, ta din ga ce mini tsoro take ji, tana
son na kasance da ita lokacin haihuwa. Allah bai amince ba, ban kasance da ita
ba, amma na cika alƙawarin da na yi mata a kanki"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Na yi mata addu'a sosai da
sosai, Allah ya jiƙan 'yar madararmu"
"Amin my love"
Abdul ne ya shigo da jariran a hannunsa ya ce "Wai ba
kwa san yaran ne? Ana ta rawar ƙafa a baka su, amma ka ƙi kallonsu, ga su nan
an yi musu rigakafi, BCG da HB kafin mutane su fara zuwa ɗaukar su"
Viper ya yi murmushi ya ce "Sun wahalar mini da mata,
shiyasa na ɗan yi fushi, amma tun da tana nan ƙalau, barakallahu fihum"
yayi maganar yana karɓar su, cikin wani irin maɗaukakin farinciki mara
misaltuwa.
Abdul ya ce "Wannan boss ɗin da kai yake kama,
fuskarka ce wannan" Viper ya yi dariya.
Su Major ne su ka shigo, shi ma sai da ya fara nufar gadon
Nabila, ya tabattar tana lafiya.
Kan ka ce kwabo, Asibiti ya ɗinke da mutane, 'yan barkar
Nabila.
Da liti ya zo duk jikinsa a sanyaye, ya din ga jerawa Nabila
sannu, halin da ya ganta a ciki ɗazu, ya ƙara sanya masa tausayin mata.
Ya ja gefe aka miƙo masa jarirai.
Bai san lokacin da ya ce "Kan uba, kumbo, Viper wannan
fuskar ai taka ce, ka ga jariri yadda ya haɗe fuska kamar zai kai duka. Allah
ya baki juriyar tarbiyya, wannan zai yi taurin kai kamar babansa"
Ba wanda bai yi dariya ba, macen ce take ta tsotsar
hannunta, tana buɗe idanunta tana lumshe su a hankali.
"Allah ya raya mana ke 'yar madara, Allah ya sa ki ɗaukko
halin mai sunanki"
Viper ya ce "Har ka saka mata suna?"
"Eh gaskiya, na saka mata suna fatima zahra, 'yar
madara"
Viper ya yi murmushi ya ce "Babanki ya saka miki suna,
Allah ya raya ki bisa tafarkin addinin musulunci"
Bayan awanni shida aka sallami Nabila, gida ma da suka tafi,
ana ta zuwa barka.
Washegari hafsa su ka zo Kano da Hafsa, Hafsa kamar a bar
mata jariran nan.
Alhaji mu'azzam ya ce "Wannan dai na san 'yar madara
ce, shi kuma ogan fa ya sunansa".
"Takwara na yi muku kai da Abbu, Ibrahim ace masa
mu'azzam ko Khalil"
Ita kanta Nabila ba ta zaci haka zai yi ba, ta ɗauka sunan
Nura yayan ramma zai saka"
Alhaji mu'azzam bai taɓa zaton Viper zai yi masa kara haka
ba.
"Masha Allah, amma na gode sosai da sosai, idan ina da
rabo nima Allah ya bani ɗa namiji, Allah ya raya khalil"
Viper ya ce "Mu ke da godiya, har duniya ta naɗe, ba
zamu taɓa manta abin da ka yi mana, Allah ya saka da alkhairi"
Kankarofi ya ce "Kar ka damu Viper, yi wa kai ne"
An sha shagalin bikin suna sosai, Alhaji mu'azzam ne ya yi
wa jariran Viper hakika, sun samu tarin kyaututtuka, ta in da suka zata da in
da ma ba su zata ba.
Sai dai Nabila ta fara fama da ɗawaniyar raino, Khalil ba
shi da afuwa wurin tsotsotso, 'yar madara ba ruwanta idan an ba ta ta sha, idan
ba a bata ba, sai tayi ta tsotsar hannunta.
Viper ya ce "Ba fa zai yiwu ka hana mini 'ya kumari
ba"
Haka zai tsigo shi daga jikin Nabila yana tsala kuka, ya
bata 'yar madara ta shayar.
Baba magajiya ce take yi wa Nabila wankan jego.
Watan Nabila ɗaya da haihuwa, aka yankewa Indabo hukuncin
kisa a ƙasar saudiyya.
Ko a iya haka Viper ya ɗan ji sanyi a ransa, duk da ba za a
taɓa wanke masa zuciya ba, haka ma maman ramma.
Bunkure kuwa ana ta jan shari'ar ta, saboda tuhume-tuhumen
da ake yi mata da yawa.
Abdul ya sha tashin hankali, saboda yadda maganar kashe
Indabo ta karaɗe ko ina a ciki da wajen ƙasar nan.
Nabila ta fara mayar da hankali a kan ƙoƙarin ta, na fito da
hanyoyin taƙaita shaye-shaye, a tsakanin al'umma.
Ta fara da rubutun ƙanan litattafai, masu ɗauke da
zane-zane, da suke ankarar da illar shaye-shaye da 'yan makaranta tun daga
primary zuwa secondary za su iya amfani da shi.
Aka gudanar da babban zaɓe na ƙasa, gwamnati ta canza bara
gurbi daga cikin muƙarabbanta, yayin da Alhaji mu'zzam ya ɗare kujerar sanata.
Jidda babu yadda ba ta yi ba ta koma gidansa, amma yaƙi.
Zakiyya kuwa sai abin ya zame mata ga bikin zuwa babu zanin ɗaurawa,
ga kuɗi iya kuɗi hafsa na cikin daula, amma bata nutsuwar ƙwaƙwalwar da za ta
ci, kullum a zabure take cikin tashin hankali.
Ba a rufa watanni uku ba, shugaban ƙasa ya rattaɓa hannu, a
kan sauya shugabannin da za su jagoranci rundunonin tsaro na Nigeria.
Viper mamaki ne ya cika shi, ganin matsayin da aka ɗauka aka
ba shi.
Sumayya gwamantin kano, ta buƙaci su yi aiki da ita, ayi
mata S.A daga ita har Nabila, amma suka ƙi hakan, saboda ƙungiyar da suke son
kafawa, ba sa son siyasa ta shiga ciki, su na so tayi hannun riga da irin ta
bunkure.
Nabila ta fito daga wanka ta na shirya, ta tsaya tana kallon
kanta a mudubi, Viper yana ta rarrashin Khalil yayi bacci, ya ga ta tsaya ta yi
shiru tana ƙarewa jikinta kallo a mudubi.
"Madam ya dai?"
"Vi, kalli duk na yi wani iri, kalli tumbina yadda yaƙi
komawa gaba ɗaya, kalli stretch marks duk ya ɓata mini jiki, kalli yadda cikin
yayi, kalli breast ɗi na ma, duk stretch marks, ni Allah ya sa kar su yi
sagging ma idan na yaye su" tayi maganar cikin damuwa.
Ya tashi ya ƙarsa in da take, ya tsaya a bayanta, yana
kallonta ta jikin mudubi.
Ya zagaya hannunsa a cikinta, yana shafa cikin a hankali ya
ce "This is motherhood abla, yara biyu ne fa suka kwanta wata tara a
cikinki, ta yaya ki ke expecting ki zauna a yadda ki ke?"
"Vi zan daina yi maka kyau, kalli tumbina fa, ji
nankarwa, kalli breast ɗina, duk yadda ya cika maybe da na yaye su ma zubewa za
su yi"
Ya kwantar da kansa a kafaɗarta ya ce "Idan na ce zaki
daina yi mini kyau, ban yi wa kaina adalci ba ko kaɗan abla.
Ba zaki taɓa komawa yadda ki ke a da ba, kar ki damu kanki,
ki ce sai kin yi abin da zai cutar da ke, sai nankarwa ta tafi, sai breast ya
koma yadda yake a da, ban ƙi ba ki yi gyara, amma ban da cutar da kanki, ki yi
alfahari da wannan nankarwa tambarin zama uwa kenan, ni kyau take yi mini ma,
ba na cikin mazan da zan damu da sauyin da jikin matata ya samu, alhalin na san
ba a haka na aureta ba, dan duk wanda yake a haka, zai zama mai yawan zalama da
hange kuma ba zai taɓa samun yadda yake so ba.
Ina sonki a duk yadda ki ke ablana, ni kullum mai kyau ce ke
a idona."
Juyowa ta yi suka rungume juna tana murmushi, ko ba har
zuciyarsa yayi maganar nan ba, ta ji daɗi a ranta, balle ma Viper da ba ya abu
dan a so shi, idan abu bai yi masa ba faɗa yake yi.
A lokacin da aka shirya walimar karrama Viper, ɗan mama ya
zo, Liti ya rungume shi cikin murna da farinciki ya ce "Ɗan mama kai ne ka
zama haka? Ni da tsulai, kai in da aka kai kan, tsotsarka suke yi ne, ka ga
yadda ka koma kuwa? Ni da takanɗa"
Ɗan mama ya ce "Oga liti kenan, ai gara ace garin mayu
aka kai ni, ake lasata da azabar da ake gana mini"
Kamar Liti ya haɗiye ɗan mama dan murna, har Abdul sai da
yaje wurin walimar nan, a ransa yake ta ƙara jinjina lamarin Allah, ɗan daba
mara galihu, yau ya zama daga cikin manya a jami'an tsaro.
Ramma da tsohon ciki ta kammala WAEC ɗin ta, sun gama babu
jimawa ta haihu, ta haifi ɗa namiji, ana haifarsa Abdul ya ce Nuradden ya saka
wa jaririn.
Ba ramma ba hatta mamanta, sun ji daɗin abin da Abdul ya yi.
Mamansa dole ta zubar da makaman adawa da ramma, ganin kaf
iyalinta sun tarwatse, sai Abdul, shi kuma ta matarsa yake yi, a dolenta ta
sassauta ƙiyayyar da take yi mata, mussaman da ta haifi Nuruddeen.
Viper ya ba wa jaririn kyaututtuka daban-daban.
Bayan yi wa Viper ƙarin girma, sai da aka bashi motar hawa,
da gidan zama.
Abin da ya fara yi, ya je unguwar su, ya samu mai unguwa aka
zauna da manyan unguwar, ya ce a tattara masa duk yaran da suke harkar daba, waɗanda
suke da sha'awar aikin soja, a ɗauki sunansu a bashi.
Sannan a duba mutum biyar, za a kai su kasuwa, wurin su
Walid, masu son komawa makaranta ma, a ɗauki sunayensu, a kai wa distinguish
senator Mu'azzam kankarofi, a ga ta ina za a taimaka musu. Amma duk wanda aka
samu da cin amana, sai ya ɗaure shi, kuma babu wanda ya isa ya karɓe su, bisa
yarjejeniya za a rubuta komai.
Ya haramta daba a yankin unguwar da kewayenta, ko dai mutum
ya rungumi zaman lafiya, ko kuma zai ɗauki matakin da ya dace a kansa.
Major bai saka lokaci mai tsawo ba, na auren Walida da
Abdallah, liti kamar ya janyo lokacin mussman idan ya ga 'ya'yan Viper da kuma
na Walid.
Khalil rigimamme ne, baby jauhar kuwa babu ruwanta, bayan
nono da madara ake haɗa musu, saboda shayarwar na ba wa Nabila wahala, Khalil
kaɗai idan ya sakata a gaba, sai ta fara jiri.
Nabila ta dage a kan ƙungiyar ta, da gaske take son yaƙi da
daba da shaye-shaye, tare da yaƙi da bangar siyasa.
Tare da sumayya suke faɗi tashin su, ta hanyar amfani da
kafafen sada zumunta da kuma kafafen watsa labarai, wurin bayyanar da manufar
su.
Suka samu goyon bayan manyan lauyoyi, da 'yan jaridu, Nabila
ta na yawan nanata su ƙungiyar su ba ta siyasa ba ce ba, kuma ba ta gwamnati ba
ce ba, dan haka duk ta kan wanda aiki ya biyo za su yi aikinsu ne, ba tare da
sani ko kuma sabo ba.
Ta kuma samu cikakken goyon bayan mijinta Al'amin, ɗari bisa
ɗari.
Tare da amincewar gwamnati, aka bibiyi rubuce-rubucen da ta
yi, aka yi gyare-gyare, aka fara rarraba su kyauta a cikin makarantu, wanda
suka haɗa har da ƙanan labarai, masu kama da tatsunuyoyi, wurin nuna illar
shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da bangar siyasa.
Haka nan mawaƙa sun bayar da gudummawa, wurin waƙoƙin yara,
da suke nuni da illar waɗannan miyagun ayyukan.
Misalin ƙarfe takwas na dare, Viper yana zaune a katafaren
falonsa, za ayi hira da Nabila, a babbar tashar talabijin a Kano, kuma Sumayya
ce za ta gabatar da program ɗin.
Khalil sai tsalle-tsalle yake yi, ya faɗa nan ya tashi can,
kamar ɗan aljani.
Jauhar kuwa na jikin Viper a kwance, tana ta tsotsar
hannunta.
Viper ya fi shiri da 'yar madara, babu ruwanta, ba rigima ba
rikici, ga ta da haƙuri, Khalil kuwa ɗan gidan Nabila ne, ita kaɗai take iya
masa, ba ya ji ko kaɗan, ga wasan kasada, duk wani wasa da zai yi ya cutar da
kansa shi yake yi.
Ga miskilancin tsiya da kukan banza, gashi abu kaɗan Jauhar
za ta yi masa ya maketa, ko ya cijeta.
Sai dai idan Viper ya gani, ya murɗe masa kunne, ya tafi
wurin Nabila yana kuka.
Yanzun ma Viper ne ya kalle shi, yana ta hawa kan kujera
yana dirowa da ka.
"Ko ka zauna ka bar abin da ka ke yi, ko kuma ka fita,
maminku ce za ta yi program zan kalla"
Da sauri ya saukko ya zauna a ƙasa ya ce "Mamina ce
nikaɗai"
"Eh an ji taka ce, ni ma jauhar ɗi na ce nikaɗai"
"A'a daddyna ne"
"A'a kai ɗan mami ne, ni kuma 'yar madara ce tawa"
Tasowa yayi yana kuka yana cewa "Daddyna ne, mamina
ce" shi ma ya zauna a jikin Viper" Jauhar ta sake gyara kwanciyarta a
jikin Viper, ba tare da ta kula Khalil ba.
Fara program ɗin ya sanya, gaba ɗaya suka mayar da
hankalinsu kan TV.
Bayan gabatarwa, Sumayya ta tambayi Nabila, menene dalilin
da ya sanya ƙungiyar ta, ta fi mayar da hankali a kan harkar daba da
shaye-shaye, da kuma bangar siyasa?"
Nabila ta ce "Saboda tun da ake yi, bamu taɓa cin ribar
abin ba, sai koma baya, da kuma lalata goben matasanmu, lalacewar goben matasa
kuma lalacewar al'umma ce"
"Ta yaya? Kuma wasu hanyoyi ki ke ganin za a bi a
magance wannan matsalolin da ku ka sako a gaba"
"Saboda su ne shugabanninmu na gobe, waɗanda za su
jagoranci al'umma. Muddin bangar siyasa abin arziki ne, yan siyasarmu ba za su
nemi ɗan talaka yayi musu ba, 'ya'yansu za su ka su yi musu. Meyasa ba sa kai
yaran talakawa, ƙasashen waje su yi karatun injiniya lauyoyi, likitoci da
makamantansu, ko kuma ɗan talaka ba shi da ƙwaƙwalwa da zai yi ilimi ya zama
likita, ko injiniya?.
Hannu ɗaya baya ɗaukar jinka, kuma hannu da yawa maganin
ƙazamar miya.
Dole ne iyaye, malamai, gwamanti, hukumomi, mu haɗa hannu mu
kawo ƙarshen shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da kuma bangar siyasa.
Mu ba wa yaranmu kulawa da ilimi kamar yadda Allah ya ce
mana masu kiwo ne mu, kuma ababen tambaya a kan kiwon da aka bamu.
Kar ka haifi ɗan da ba zaka iya ɗaukar nauyinsa ba, dan jin
daɗinka kawai.
Sannan iyaye su din ga bawa hukumomi damar hukunta yaransu,
a duk lokacin da aka masu da laifuka.
Sannan su kansu hukumomin da 'yan siyasa su ji tsoron Allah,
wurin kama masu laifi, da sakinsu ba bisa ƙa'ida ba.
Babu wanda ya taɓa zama wani abik alfahari, a dalilin
ta'amalli da miyagun ƙwayoyi. Ba hujja ba ce matashi ya zauna ya ce sai
gwamanti ta bashi aikin ba shi da aikin yi. Masu kuɗin duniya babu wanda yayi
kuɗi da aikin gwamnati.
Ina kira da matasa, ku tashi ku nemi na kanku, ku nemi
ilimi, duk wanda ku ka zaɓa, bai yi muku abin da ya dace ba, ku ɗaura ɗambar
dawo da shi, ta hanyar recall election, ko kuma ku canza shi a lokacin zaɓe.
Kuma za ku iya zama likitoci, injiniyoyi da makamantansu, ku
ba bayin 'yan siyasa bane ba, da za su yi amfani da yau ɗinku, su lalata
gobenku, domin ku dauwwama ku na yi musu bauta da yaransu.
Su daina ba ku miyagun ƙwayoyi, ku na sha ku na kashe kanku,
alhalin sun kauwwame yaransu, sun tura su in da za su yi ilimi, sun kwashe
dukiyoyinku sun tara wa iyalansu arzikin da ba za su yi talauci ba, sun bar ku
da bauta musu, da zubar da jininku yadda suke so, alhalin iyalansu su su ka fi
cancanta su yi musu wannan aikin ba ku ba.
Ina fatan nan gaba kaɗan in ga matasa 'yan shekara talatin
zuwa ƙasa a majalissu, in gansu a cabinet ɗin shugaban ƙasa.
Mu ga matasa ɗanyen jini, sun gaji manyan malamanmu, irin su
marigayi Albani zariya, Sheikh ɗahiru usman bauchi, dr. Isa Ali Ibrahim
fantami, malam umar sani fagge, malam Aminu Ibrahim daurawa, malam Ahmad
guruntum, Sheikh Ahmad bamba rahimuhullah, malam Nasiru kabara. Ina fatan na ga
mun samu ire-iren ɗangote da dama, in ga natasanmu sun zama dactoci da
profesoshin ilimi da duniya za ta yi alfahari da su. 'yan daban nan 'ya'ya ne,
kuma za su amfani al'umma idan aka tsaya wa rayuwarsu"
Sumayya ta ce "Sannu da ƙoƙari, kin kwararo bayanai,
masu matuƙar ma'ana, kin ƙara ƙarfafa mini gwiwa, kamar na fito takara nima,
duba da yanayin lokaci, bari mu waiwayi masu sauraro, mu ji gudunmawar da za su
bamu"
Bugowar farko, muryar Viper ta yi amsa kuwwa a cikin wayar
tarhon.
"Ina yi wa baƙuwa barka da zuwa, haƙiƙa ta yi bayani
masu ma'ana, amma tayi tuya, ta manta da albasa, ba ta tofa komai a kan iyaye
mata ba"
Murmushi Nabila ta yi, domin kuwa muryar Khalil ta jiyo yana
kiran mami ta cikin wayar.
"Mata iyayen al'umma, mata iyayen giji, a basu ilimi, a
kula da su, kar ayi musu fyaɗe a ɓoye, domin gudun zubewar mutunci, a ƙi ɗaukar
musu mataki, kar a ɗora musu talla, kar a tura su barace-barace, kuma kar ayi
musu auren dole, kar a zalunce su. A wadata su da ilimi, a tausaya musu a ba su
damar cika burikansu. Babu wata mace da zata iya rayuwa ta tsaya da ƙafarta, ba
tare da ta jingina da namiji ba.
Kamar dai ni, babana ya share mini fagen cikar burina,
mijina kuma ya bani dama kuma ya tsaya mini, hakan baya nufin lalacewar macen.
Ni 'ya ce, matar aure, uwa kuma lauya mai zaman kanta, ina fatan nan da shekaru
kaɗan na ga mata ire-irena sun yawaita, kuma matasa sun kama hanyar gyara
rayuwarsu, domin samar da kyakykyawar gobe ga al'umma da ƙasata baki ɗaya."
Nabila ta sha tambayoyi daban-daban, kuma sosai ta ƙara
zaburar da al'umma, mutane da dama su ka nuna sha'awar su, a kan ƙungiyar, sai
dai ta nanata cewar ƙungiyar ta ba ta siyasa ba ce ba, kuma ba ta neman kuɗi ba
ce ba.
Hankalin Nabila ya kwanta sosai da sosai, Allah ya dafa wa
lamarinsu, ga Alhaji mu'azzam sosai yake tallafawa matasa, yake tafiya da su,
tare da bankaɗo masu ilimi da himma a cikinsu, ya samar musu aiki, da sama musu
appointments a ƙasa.
Kankarofi na daga cikin yan majalisa da suka kawo wa yankin
arewacin Nigeriya cigaba sosai da sosai.
Liti tuni ya angwance da Walida, cikin ikon Allah kuma ya
rage rawar kai, saboda daraja da kamala ta aure, da ta hau kansa. Bayan shekaru
uku, Abbu ya basu damar tsayawa da ƙafafuwan su, ta hanyar ba su jari aro, da
kuma kama su musu wurin gudanar da sana'a.
Nabila sai da ta haifa wa Viper yara biyar, sau biyu tana
yin twins, sai kuma Namiji a tsakiya guda ɗaya, sai dai Khalil shi ya ɗaukko
halin Viper gaba ɗaya babu abin da ya bari.
Abdul ya tsaya wa ramma, sai da ta zama cikakkiyar Nurse,
shi ma ta hayyafa sosai da shi.
Rahila daga baya Allah ya yi mata rasuwa, jikinta yaƙi daɗi
haka ta koma ga Allah.
Hafsa kuwa haihuwar dai Allah bai bata ba, amma Kankarofi ya
zauna da ita cikin mutuntawa da so da ƙauna.
Daga Walid, liti, Viper ɗan mama, idan aka ce sun yi daba a
baya, idan ba wanda ya sani ba, sai ya ƙaryata.
Viper sai da ya kai Nabila, wurin maƙwabtan Jauhar da suka
yi zaman amana da ita a unguwar da suka zauna.
Viper ya riƙe muƙamai da dama, a gidan tsaro na soja, gefe
guda yana kasuwanci.
Ƙungiyar Nabila ta taka muhimmiyar rawa sosai da sosai, a
kan canza tunanin mutane da dama.
*TAMMAT BI HAMDILLAH*
1/8/2024-20/12/2024
*DUKKAN YABO DA GODIYA DA JINJINA DA KIRARI, SU TABATTA GA
UBANGIJI MAƊAUKAKIN SARKI, UBANGIJI TALIKAI BUWAYI GAGARA MISALI, DA YA BANI
ARON RAI DA LAFIYA NA FARA WANNAN LITTAFI LAFIYA NA KAMMALA LAFIYA*
JINJINA GA
ƘUNGIYAR MIKIYA WRITER ASSOCIATION
BRIGHT PENS TEAM
Nazeefa sabo Nashe
Zee kumurya
Na'aima Suleiman sarauta
Aisha Adam Ayshercool
GAISUWA TA MUSSMAN GA
Mahaifiyata malama Nafisa Adamu Muhammad
Mahaifina malam Adamu Yakubu
GODIYA TA MUSSMAN GA
Adamu Adamu Yakubu
ASP Ibrahim Na'ibi
Barrister Amina Aliyu
Barrister Ibrahim
Jinjina da gaisuwa ta musamman, ga kafatanin al'ummar da
suka kasance da ni, a wannan littafi.
Iyayena, kakannina, yayye ƙanne da sauransu, masu gyara,
masu sharihi, da masu bayar da shawara ina godiya sosai da sosai.
'yan comment section, Alkhairin Allah ya kai muku.
Na so kama sunaye, amma na san dole zan manta da wasu,
kafataninku ina godiya Allah ya saka da mafificin alkhairi.
Abin da na rubuta na daidai, Allah ya sa al'umma su amfana,
akasin haka kuma ina fatan Allah ya yafe mini, kuma ya sa al'umma su yi watsi
da shi.
Waɗanda na ɓata wa rai kuma, ina fatan ku yi mini afuwa,
hada-hadar jama'a pressure da yawa.
Albishir na musamman ga kafatanin waɗanda su ka bibiyi
littafin *ƘARFE A WUTA*
Na san ku na cike da kewar kammala karatun labarin Viper,
labari mai cike da ilimantarwa, faɗakarwa da nishaɗantarwa, to ga sabon
Albishir, littatafai uku, cikon *BRIGHT PENS SECOND BATCH*
litattafan da za su maye muku gurbin labarin ƙarfe a wuta.
*MUTALLAB* (Mallakar Nimcyluv)
*HADARIN GABAS* (Mallakar Nazeefa Nashe)
*ZAYTOON*
(Mallakar zee kumurya)
Ina da tabbacin yadda ku ka ji daɗin ƘARFE A WUTA, ba zaku
yi dana sanin labaran nan uku ba, da su ka fito daga team ɗin
*BRIGHT PENS*
Domin neman ƙarin bayani, kai tsaye ku na iya tuntuɓar waɗanan
lambobin.
0904 787 1750
0816 406 9385
Alhamdilillah ala kulli halin.
Domin gyara, sharhi ko shawara
Ayshercool
08081012143