BK 2
52
Jamila ta fashe da wani irin kuka tana tsuma, ta ce "Na shiga uku, yanzu Aljani ne ya kwanta da ni?"
"Eh amma a jikin bil'adama ya shiga, ya yi amfani da ke" ta gaya wa Jamila kai tsaye, ba tare da ta ji nauyin hakan ba.
"Na shiga ku, yanzu waye zai aure ni a haka? Ya zan yi. Na lalata rayuwata"
Hajiya Sa'a ta riΖo hannun Jamila ta ce "Na sha gaya miki, matsoraci ba ya zama gwani Jamila. Shi fa auren nan ba dole ba ne ba. Idan kina tare da ni duk abin da ki ke so za ki samu a tare da ni. Idan ma auren ki ke so miji sai kin zaΙa, kuma tsaf za a yi miki gyara babu wanda ya isa ya gane an taΙa amfani da ke. Kuma Ζungiya ta bayar da kuΙinki na shekara. Su na gurina zan din ga baki a hankali saboda kar a gane. Ki kwantar da hankalinki, ki Ζwarara jikinki, kar wani abu ya razana ki. KuΙi kin same su kin gama ki saki jikinki ki mori duniya. Ke ce yarinya mafi ΖanΖanta a cikin Ζungiya. Ni dai ina matuΖar Ζaunar ki ne. 'yar uwakki na so na kawo, amma abu bai yiwu ba, ina tausayawa rayuwar da ku ke yi a gidanku ne. Ki cire duk wata damuwa daga zuciyarku, ki cire tsoro da tausayi baki Ιaya za ki je inda ba ki taΙa zato ba.
Jamila ta Ιaga kai ta yi wa Hajiya Sa'a wani irin kallo, da ita kaΙai ta san ma'anarsa. Ta share hawayenta ta ce "To shikenan"
Hajiya Sa'a ta yi murmushi ta ce "Yauwwa Daughterna, tashi mu je na gasa ki, ki karya likitan Ζungiya zai shigo ya duba ki" Jamila ta ja jikinta da Ζyar, Hajiya Sa'a ta kama ta suka je banΙaki.
****
Yau kwana na huΙu kenan, Sayyid yana cikin wannan yanayin. Babban abin da yake damun Nana rashin cin abinci da kuma salla da ba ya yi, daga bacci sai zaman shiru. Ba ya cewa uffan, sai dai ya yi ta bin ta da kallo. Ta din ga Addu'a Allah ya taimake ta, ko Ummi ba ta zo gurin ta ba, balle ta san halin da suke ciki.
Ζarfe tara na dare ta na zaune a Ζasa inda ta ajiye fulo tana kallonsa a kwance a kan katifar. Ta Ιaga hannayenta kamar za ta yi addu'a, ta karanta suratul mulk, da ayatul kursiyyu, da Suratul falaΖi da Nasi. Ta tofa a hannunta, ta Ζarasa kusa da shi a Ιan tsorace ta shafa masa a fuskar sa. Ta ja da baya tana jira ta ga abin da zai yi, amma ta ga bai yi komai ba. Ta nemi guri ta kwanta tana ta tunani a ranta.
A cikin bacci ta ji ana ture ta, ta buΙe ido da sauri, ta ga yana ΖoΖarin kwanciya a gefen ta, duk da yadda gurin ya matse su.
"Sayyid" ta kira sunansa.
"Na'am"
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, ta riΖo hannunsa ta ce "Mene ne?"
"Na kasa bacci, kin bar ni nikaΙai a kan katifa"
Cikin farin ciki da kulawa, ta shafa bayansa ta ce "Gani na yi ka na numfashi da Ζyar, kamar na matse ka shi yasa na saukko nan"
"Ma vie"
"Na'am Shugabana"
"Yunwa nake ji, kamar ban taΙa cin abinci ba"
"Bari na yi sauri na dafa maka wani abin, amma zo mu je ka wanke bakin ka, ka ga yanzu tsakiyar dare ne" Ya yinΖura ya tashi, ta kama shi, yana ta jiri, saboda yunwa ga rashin lafiya, ga kuma mutuwar jiki.
Ta kai shi banΙaki, ya wanke bakinsa, ta dawo da shi ya zauna.
Ta feraye doya a cikin Ιakin, ta Ιaukko gas Ιin ta, ta ajiye a bakin Ζofa ta Ιora.
Ta Ιaukko mafici tana ta yi masa fifita.
"Rayuwata"
"Sayyid"
"Kamar yau ba mu ci abincin safe ba ko?"
Nana ta ce "Kwanan ka huΙi fa ka na bacci. Babu abin da zan ce wa Allah sai godiya, da ka farka" ya yi shiru bai kuma cewa komai ba. Ta sauke doyar ta dafa masa shayi, ta ajiye tana jira ya sha iska, ta ba shi da kanta. Amma bai jira ta ba, ya din ga hannu baka hannu Ζwarya. Sai dai hakan ya yi wa Nana daΙi, ganin ya ci Abinci da yawa yau.
Ya gama ci, ta dafa ruwa ta kama hannunsa zuwa banΙaki, tamkar jaririn goye ta yi masa wanka. Shi kansa a lokacin ya din ga jin wata lafiyayyiyar iska na shigar sa. Ta saka ya yi alwala, ya fito ya zauna ya fara jero sallolin da ake bin sa.
Ta ce "Sayyid kar ka ce sai yi a yanzu duka, sallolin da yawa.ka bari ka din ga ramawa a hankali.
Ya jinjina mata kawai kawai, tun yana yi a tsaye ya kasa tsaiwar ya koma yi a zaune. Ta yi shiru tana kallonsa, ta wasu guraren suna da kamanceceniyar halayya ita da shi.
Duk yanayin da yake ciki, muddin ba hankalinsa ne ya gushe gaba Ιaya ba, ba ya wasa da salla ko kaΙan. Hakan ya sanya take jin ko a ainihin rayuwarsa haka ya siffantu da kiyaye salla a kan lokaci.
Har Ζarfe uku da rabi, dan kansa ya ce "Ba zan iya Ζarasawa ba, numfashina"
Ta ce "To ko za ka yi a kwance?"
Ya girgiza kai ya ce "Na fi so na yi a zaune, ko a tsaye"
Ta Ιage masa labule, ganin yadda yake ta gumi. Ta shimfiΙa masa sallaya a bakin Ζofa, ta jera masa fululluka, ya kwanta.ta zauna a gefen sa tana yi masa fifita. Ta Ιora hannunta a goshinsa tana karanta masa abin da Allah ya sa ta tuna a zuciyarta.
Hannunsa ta ji yana saka wa a rigar ta, duk da idonsa a lumshe yake. Murmushi ta yi ta ci gaba da abin da take yi. Jin yana yi mata cakulkuli, ya sanya ta kwanta a jikinsa tana dariya. Shi ma dariyar ya yi. Ya ce "Ki kwanta a kusa da ni" ya yi maganar yana nuna mata kusa da shi. Kafin ta yi magana ta ga an dalle su da fitila.
Cikin hanzari ya juya kansa, ya Ιoye fuskarsa a cinyar Nana, gashin sa ya kwanta a kan filon. Nana ta saka hannu ta kare fuskarta.
Muryar Barira ta ji ta ce "Yi haΖuri dan Allah, jin motsi ya yi wa na fara jin tsoro, shi ne na fito na duba, ku yi haΖuri.
Ta kashe fitilar ta koma Ιaki. "Sayyid ka yi haΖuri, na san ba ka ji daΙi ba, ka yi haΖuri"
Ya yi mata shiru, kuma bai Ιago daga kan cinyarta ba. Ta shafa gashin ta ce "Shugabana, ka yi magana mana, ko na ji daΙi, kwana huΙu ka na bacci, ba ka yi mini magana dan Allah kar laifin wani ya shafe ni"
Sai kuma ya juyo a hankali, ta ce "Yauwwa Rayuwata"
"Kin daina aman?" Ta ji ya tambaye ta babu tsammani.
"Eh na daina"
"Allah ya sa ki haihu wannan karon "
"Amin, kuma Allah ya baka lafiya na haΙa jariraina biyu, babba da Ζarami"
Ya yi murmushi ya ce "In sha Allah, kafin ki haihu, idan na ji sauΖi zan nemi aiki, na kula da ku da kaina"
"To Allah ya amince. Amma Sayyid ina kuΙin nan da na gani rannan, a cikin wardrobe Ιin ka? Da na haΙa mana kaya ban gan su ba. Da sai mu Ιauka a yi maka magani, kuma mu canza gida"
"Ai Habu ya karΙa, ranar da ya zo na Ζarshe, ya karΙi kuΙin Nigeria da yawa, ya bar mini wasu, ya ce na Nijar ne. Kuma da kin duba kayan nawa sosai, su na ciki"
"A'a ni ba na caje maka kaya, idan Allah ya kaimu gobe, sai a lissafa mu gani idan za su isa."
Ya ce "To. Kwanta ki yi bacci" ya yi maganar ya Ζara matsa mata. Ta kwanta tana murmushi.
"Sayyid, idan har ba a ga su Habu ba, ina ga da ni da kai zamu je Nijar, mu nemi danginka da kanmu"
Ya yi shiru bai yi magana ba, ta Ιan taΙa shi ta ji har ya yi bacci.
*****
Jamila a dole ta saki ranta, jikinta ta Ιan samu Ζwari, ya daina yi mata wannan mugun ciwon da yake yi mata. RaΙaΙin ma duk babu. Sai dai tana jin Ζasan zuciyarta kamar za ta yi bindiga, saboda damuwa da tashin hankali. Sosai abin da ya faru ya tsaye mata, ta shiga banΙaki ta sha kuka. Wai ita Aljani ya kwanta da ita, ta gaba da baya aka ci zarafin ta ta wannan mummunar hanyar.
Tana kwance a cikin bargo, Hajiya Sa'a ta fita shashashancinta. Wayarta ta fara ringing. Ta janyo ta Ιaga. Muryar Abba ta ji ya ce "Ζanwata, wunin yau ban jiki ba, lafiya kuwa?" Wani irin abu mai zafi ya taso mata, ya haddasa mata karaya. Muryarta na rawa ta ce "Yaya Abba ba ni da lafiya"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Me ya same ki?"
Rasa abin da za ta ce masa ta yi, kawai ta saka kuka. Aikuwa ya rikice ya din ga rarrashin ta.
Da Ζyar ya lallaΙa ta ta ce masa cikinta ne yake ciwo.
"To ina Mummyn take? Ba ta kai ki Asibiti ba?"
"Ta kai ni, an ba ni magunguna ma, dan Allah kar ka yi mata zancen, ta yi mini iya ΖoΖarin ta,kar ka yi mata zancen dan Allah"
"No ai ba zan yi mata ba, ba ta san ma ina da lambar ki, mu na magana ba. Ki kwanta ki samu hutu kin ji Ζanwatax
"To shikenan na gode sosai" suka yi sallama ta ajiye wayar, ta kwanta hawaye na ci gaba da bin idanunta.
*****
Yana zaune a cikin mota, yana ΖoΖarin kunnawa, wayarsa ta fara vibrating. Ya kalli screen Ιin wayar, ya ga baΖuwar lamba. Ya Ιauki wayar ya Ιaga ya saka a kunnensa.
"Hello" muryarta ta doki dodon kunnensa. Ζan waro ido ya yi, ya gyara zaman sa ya ce "Wa ke magana?"
A raunane ta ce "Beb abin har ya kai ka manta muryata ma? Shikenan na gode" ta kashe wayar.
Da sauri ya bi kiran wayar, amma ta Ζi shiga, ya yi ya yi, amma ta Ζi shiga, sai haΖura ya yi ya ja motar.
Shukura mamakin abin da ya zaunar da shi a cikin mota take yi, bai tafi ba har yanzu, sai dai tana Ιaga labule, ta hango ya ja motar ya tafi.
Video call Ιin Hajiya Amina, Shukura ta gani, ta Ιaga cikin fara'a tana faΙin "Hajiya Mummy, ya ibada?"
"Ibada Alhamdillah, Shukura dan Allah me yasa ba kya ji ne? Ina zaman zamana, ina ibada kin jawo mini Ιacin rai da damuwa"
Cikin rashin fahimta, ta ce "Ni Ιin kuma? Me na yi?"
"Baban ki ya kira ni, bai taho ba tukuna yana Abuja. Yana yi mini faΙan wai ke ba ki san Ζaddara ba ne? Doctor Sharif ya kira shi cikin damuwa, yana gaya masa a gaban mutane ki na cewa yana kashe mutane, haka ake yi a kan ki a ka fara rasa Ιa? Me yasa ba za ki girma ba ne Shukura"
"Mummy ki na ji na, network Ιin ki mai Ζarfi ne ko?"
Ta ce "Eh, ina jin ki, kuma ina kallon ki"
"Ina son idan kin je gaban ka'aba, ki yi mini addu'a, muddin a kan gaskiya ta nake, Ubangiji Allah ya shiga lamarina ya Ζarfafa mini gwiwa. Idan kuma ba a kan daidai nake ba, Ubangiji Allah ya kawar da kaina daga kai. Ya bani juriya da dangana na daina jin abin da nake ji a zuciyata.
Sai dai kin dawo amma akwai matsala ne fa."
"Shukura matsala wace iri ce, za ta sanya musulmi kasa yin tawakkalli?"
"Ki bari dai ki dawo Ιin"
"To shikenan, amma gaskiya mahaifinki ya yi fushi bai ji daΙin abin da ki ka yi ba sam"
Shukura ta lallaΙa ta, ta ajiye wayar.
*****
Nana tana jan ruwa a rijiya, tana zubawa a cikin bokitanta, za ta kai banΙaki.
Barira ta ce "Nana ki yi haΖuri dan Allah, jiya na haska ku, ba a son raina ba ne, kuskure ne" Nana ta ce "Babu komai"
Sajida ta ce "Uban me ki ka haska ki ka gani?"
Barira ta kwashe da dariya ta ce "Ni babu abin da na gani, duk da bai kyautu ba abin da na gani Ιin. Amma Nana mijinki balarabe ne ko bature?" Nana ta Ιaga ta kalle ta.
"Tun da ku ka zo dama bamu taΙa ganinsa ba, gashi na gani kamar na mace dogo sosai"
Nana ta maze ba ta kula ta ba, ta kwashi kayan ruwanta, ta nufi Ιakin su.
Sajida ta tuntsure da dariya ta ce "Maganinki da shegen shishshigi, ga shi ta gwale ki"
"Shegiya ba, ta fiye jin kan ta,kamar 'yar uban wani, kuma da 'yar uban wanin ce, da ba su kama hayar Ιaki Ιaya ba" Duk abin da suke faΙa a kunnen Nana, amma ta yi kamar ba ta ji ba.
Bayan ta gama wanke banΙaki ta fito, ta zo gabansa ta zauna. Ya Ιaukko sauran kuΙin nan, ya ajiye a gaban ta.
Ta kalle shi ta ce "A ina ka Ιoye ne, ban gan su ba?"
Ya yi murmushi ya ce "Su na cikin kayana fa, ba ki duba bane ba. A cikin leda suke. Kuma da sun fi haka yawa, Habu ne ya karΙa".
Nana ta duba kuΙin, sai tarin kuΙin nijar, na Nigeria ba su dubu Ιari da goma ba.
Ta ce "Sayyid, idan ka Ιan Ζara hutawa, ko zuwa gobe in Allah ya kaimu ne, za mu koma Asibiti a sake duba ka. Da za su kai da na haΙa da sauran na guri na, a fara yi maka allurar nan ko guda Ιaya ce"
"A'a, kin manta yanzu mu zamu din ga sayen Abinci. Idan su ka Ζare ba mu da hanyar samun kuΙi. Kuma da akwai isassun kuΙi, gara mu bar gidan nan, da a yi mini magani"
"Ni kaina Sayyid ba na son gidan nan. Mama za ta aiko mini buhun barkono, idan aka kawo, na ga ana ciniki, sai mu ci gaba da sayarwa".
Ya jinjina kai ya ce "To, in anjima ki raka ni masallaci" Ta kalle shi ta ce "Da gaske masallaci za ka je?"
"Eh, ina son zuwa masallaci. Idan ki ka raka ni, sai ki dawo"
Ta yi murmushi ta ce "To shikenan, Alhamdillah sauΖi yana samuwa. In sha Allah zan kai ka. Bari na ajiye kuΙin nan, idan na raka ka ma, dan Allah zan je gidan Ummi" ya jinjina kai. Har za ta tashi ya riΖo ta, ya cire hijjabin da yake jikinta.
Ζonuwar da take wuyanta ya gani, ya Ζura wa gurin ido sosai sannna ya ce "Mene ne wannan?"
Ta Ιan basar ta ce "Ba komai fa, Ιan Ζonewa ne kawai na yi"
"Ba Ιa ba ne ba, me ya kai ruwan zafi wuyan ki? Waye ya zuba miki?"
"Ba wanda ya zuba mini, sha nake yi ya zube" kawai ya rabu da ita, ba dan ya gamsu da amsar da ta ba shi ba.
Ta tattare kuΙin nan, na Nijar ta zuba su a cikin jakar gidan Sarkin Baka. Na Nigeria kuma ta haΙe su, ta saka a cikin kayan ta. Ana kiran salla, ya yi alwala, Nana ta ba shi mayafin rawaninsa, ya yafa a kan sa.
Nana ce ta fito tsakar gida. Barira ta gani, tana girki sanye da wata 'yar riga, milik ce amma ta yi baΖi saboda dauΙa, ko brezia babu a jikinta. Ga gashin hammata ya fito zaro-zaro idan ta Ιaga hannunta. Zanin jikinta ma baΖi Ζirin, tamkar an yi matsar man Ζuli da shi, sai annakiya take yi.
Nana ta ce "Barira, dan Allah ko za ki gyara, zamu wuce"
Barira ta ce "Bismillah ki wuce mana"
"A'a ai ni da mijina ne"
"Ku wuce ba wani abu ai" Nana ta yi shiru tana jinjina tumasanci da rashin sanin ciwon kai, na mutanen gidan. Babu yadda ta iya, haka ta kammo hannun Sayyid, ya fito ta rufe Ιakin. Ya ja mayafin ya rufe fuskarsa da rawanin, saboda yanzu ba ya iya naΙa shi, saboda numfashinsa.
Tun da ya fito Barira take kallon sa, ta na son ganin ainihin fuskarsa, amma ya sunkuyar da kai, kuma ya rufe fuskar sa suka fice.
Su na tafe Yana hutawa, saboda haki, a hankali har suka isa masallacin. Ta ce "Za ka jira ni na je gidan Ummin na dawo?"
"Zan koma gida da kaina"
"Har ka gane hanya?"
Ya ce "Eh ki gaishe ta"
Nana ta ce "Ai ba daΙewa zan yi ba ma"
Ya shiga Masallaci Nana kuma ta tafi gidan Ummi.
Su Nana na fita, Barira ta buga banΙakin tsakar gida ta ce "Ke Sajida kashin danΖo ki ke yi ne? Ki na manne a banΙaki yau mijin 'yar rainin hankalin nan dai ya fito. Ashe dole ta Ιoye shi, fari ne tas wannan gashin da na gani, da gaske nasa ne."
Sajida ta fito da buta a hannunta ta ce "Kai haba, ban gama ba ne shi yasa ban fito ba, zogala na ci da Ζuli ya ruΙa mini ciki"
"Aikuwa kin rasa, ba ki gan shi ba. Sai na ga kamar mata na rako, da na tuna Gali, ga baΖi ga Ζeya"
Sajida ta ce "Ba gara Gali ba da nawa mijin? Ke Gali na da tsawo, ni nawa ga gajarta ga muni"
"Gaskiya Sajida mijinki akwai muni kam, dogon baki kamar dangin burrai"
Sajida ta tsuke fuska ta ce "Ba na son iskanci kuma. Gara shi dai a kan Galin, da ki ka ce ba ya iya tsinana miki komai a shimfiΙa. Kalarsa kalar... Kafin ta Ζarasa Barira ta Ζunduma mata Ashariya, take faΙa ya kaure, suka ci wa junan su mutunci tsaf, suka tona wa kan su Asiri. Suka gaji dan kan su, suka haΖura.
****
Nana ta bawa Ummi labarin barkono da za a kawo mata.
Ta ce "Amma Ummi sai dai a kawo miki nan, can Ιakinmu babu gurin da zan ajiye a can"
"Bakomai a kawo, kuma nan da nan za ki ga an saye shi ba, ai unguwar nan fuskar jama'a ce, idan ka kasa kaya za ka samu alkhairi"
Su na tsaka da hira, babu zato babu tsammani sai ga Saleh ya afko cikin gidan. Wata irin mummunar faΙuwar gaba ta ziyarci Nana, bayan da ta gan shi babu tsammani. Duk ya Ζara lalacewa.
Turus ya yi yana kallon Nana, cikin mamaki ya ce "Nana, dama kina nan?"
"Eh" ta amsa a taΖaice.
"Nana da yanzu nine mijinki, amma ki ka guje ni"
Ummi ta haΙe rai ta ce "Saleh Nana fa matar aure ce, dan haka babu ruwan ka da ita dan Allah"
Saleh ya ce "Dan matar aure ce, kuma shikenan ba za mu yi zumunci ba? Nana kina lafiya? Na ji an ce wani baroroji aka aura miki ko?"
Nana ta haΙe rai ta tashi ta ce "Ummi zan tafi, zuba mini Abincin idan kin gama"
Ummi ta ce "Bari na wanke babban flask, kuma idan Islam ta zo ki ba ta kwano na, dan ba zan bar miki ba"
Nana ta ce "Gaskiya sai kin bar mini, ki zo Ιakina, ki Ιauki duk abin da ya yi miki. Kuma a Ζaramin kwano za ki zuba mini. Sayyid na yi masa girki, ni zan ci wannan"
Ummi ta ce "Hajiya Nana, an sake haΙiyar wake kenan, to Allah ya inganta"
"Dawa na haΙiya ba wake ba"
Tsulum Saleh ya sake cewa "A nan unguwar gidanki yake kenan? Na ji Ummi ta ce Islam na zuwa gidan naki. Da aka ce mijin naki gadi yake yi"
A Ζufule Ummi ta ce "Dan zatin Allah Saleh ka fita, ba da kai muke magana ba, babu ruwan ka da mu. Wai har ka manta har ubanmu ka saka a rufe saboda kuΙinka, dan rashin kunya kuma, ka zo zaka addabe mu?"
Sum-sum Saleh ya fice daga gidan. Ummi ta zubawa Nana tuwon shinkafa da miyar yauΖi, har da man shanu, Nana sai haΙiye yawu take yi cikin farin ciki, kamar ta durΖusa ta ci a gurin.
Ummi ta shiga Ιaki, ta Ιaukko wa Nana dambun kifi ta ce "Ungo, jiya na yi shi aka kai mini shago, na Ιebar miki"
Nana ta karΙa tana murmushi ganin sa fal a roba, ta ce "Allah ya yi miki abin da ki ke yi mini na alkhairi na gode sosai" suka yi sallama Nana ta fita.
Tana cikin bin wani lungu, ta ji Muryar Saleh na kiran ta. Ta Ζara saurin da take yi, amma ya cimma ta. "Nana dan Allah ki saurare ni".
Rikicewa ta yi, gani take a kowane lokaci za ta iya ganin Sayyid, ba ta san da wani yaren za ta yi masa bayani ba ya fahimta.
"Nana ki tsaya ki ji mana"
"Wallahi zan yi maka ihun kwarto, wace irin jaraba ce wannan ina ruwan ka da ni ne?" Ganin tana Ιaga murya, kuma Akuyarsa ta yi kuka a unguwar, ya sanya sum-sum ya koma da baya.
Tana zumbuΙa sauri, ta je gida, ta san yana can yana jiran ta. Kawai ta ci karo da shi a wani lungu, yana zaune a kan wata sokawe, ya jingina da jikin bango, shikaΙai Ζwal a layin. Sai da ta razana, ta waiwaya bayan ta, cike da tsoron ko Saleh ya biyo ta.
"Sayyid me ka ke yi a nan kuma, ba ka shiga shiga gida ba?"
"Ba zan iya shiga nikaΙai ba" Ta miΖa masa hannu ta ce "Taso mu tafi" ya miΖa mata hannunsa. Sai dai tun da ya saka hannunsa a nata, sai da ya kalli fuskar ta.
Da suka je gidan, danΖam da mata, ana ta hayaniya. Ya rufe fuskarsa Nana ta yi sallama. Gaba Ιaya suka yi tsit, suka zubo wa su Nana ido, musamman ganin hannunta riΖe da na Sayyid.
Kawai ta ja hannunsa, suka nufi Ιakin su.
"Nana kun dawo" Sajida ta yi maganar, tana kokowa da zaninta tana fitowa daga Ιakinta, saboda kar su wuce ba ta gan su ba.
"Eh sannun ku" daga haka ya tura Ζofar ya fara shigewa. Suna shiga Ιakin matan suka saka shewa, Ιaya ta ce "In dai Namiji ne, yarinya za ta gama wannan iyayin ne"
Nana su na shiga Ιaki Sayyid ya tsare ta da ido ya ce "Nana ba ki da gaskiya"
Gabanta ya faΙi cikin tsoro ta ce "Me na yi?"
"Gumi ki ke yi a iya goshin ki, da karan hancin ki. Kuma tafin hannunki ya ya sanyi, zuciyar ki na bugawa da Ζarfi kuma da sauri. Kin yi wani abu da ki ke Ιoye mini ko?" HaΙe rai ta yi ta fara ΖoΖarin Ζwace hannunta daga nasa.
Sai kuma ya sassauta muryarsa ya ce "Ki daina fushi, ba zan iya barin, duk wani abu na Ζi ya tunkaro rayuwata da ke ba, ki daina fushi"
"To sai ka din ga zargina da rashin gaskiya" ta faΙa a hasale.
Ya girgiza kai ya ce "Ba zargin ki nake yi ba. Na tabattar da wani abu ya faru ne, da ba za ki so na sani ba, idan na sani zamu samu saΙani. Kin manta mu ba kamar sauran mutane ba ne. Kuma ina iya jin abin da yake ranki, kin manta ne?" Ya yi maganar yana murmushi da shafo fuskarta. Dole ta saki murmushi.
Nana dai ta din ga yi wa Allah godiya, da ba ganta da Saleh ba.
Nana tana yi wa Allah godiya, ganin yadda jikinsa ya yi kyau. Duk da yana haki bai daina ba, amma yanzu yana cin abinci. Sayyid na matuΖar son zuwa masallaci salla, amma dole yake haΖura. Saboda da gayya matan gidan suke wata shigar, duk da ba tsayawa kallon su yake yi ba. Ga shi ba ya son kallo, amma yana fitowa sai su yi shiru su zura masa ido.
Ita kanta Nana lamarin gidan ya ishe ta, ba ta Ζaunar zaman gidan nan ko kaΙan.
Maman Nana ta aiko mata da barkonon nan, har da awon kayan Abinci, tamkar ta san a halin da take ciki.
Ummi da kanta, ta je ta Ιauki barkonon, domin kuwa Nana daina zuwa gidan Ummi ta gaba Ιaya saboda Saleh.
Abu kamar wasa har zuwa wannan lokacin, Sayyid ya kasa gane kansa, abin ya fara damunsa sosai da sosai. Ga shi ya kasa cewa Nana komai a kan hakan. Ita ma kuma ba ta ce masa ba, sabgoginta kawai take yi.
Tun Yamma Nana, ke ΖoΖarin shirya duk abin da za su buΖata, saboda washegari za su tafi Asibiti, kuma sammako take so su yi, saboda su ga likita da wuri.
Sai dai duk dauriya kawai take yi, wani irin zazzafan zazzaΙi ne a jikinta, ta kasa cin abinci. Babu abin da take son ci, sama ds kazar da Habu ya kawo farkon auren su. Ga shi ba ta son yin duk wani abu da zai Ιaga wa Sayyid Hankali. Ta fuskanci ko saΙani suka samu, Ζaramar magana sai ta sanya ya fara haki, ya fara nema ya faΙi.
Tana Ζofar Ιakinta, tana soya miya, su Barira su na hira, tana yi wa wata maΖwabciyar su kitso. Suke zancen wata mata a bayan layin, wai sai mijinta ya neme ta ya rasa, sai a yi kwanaki ba a ganta ba, sai bayan wani lokaci a tsinto ta a wani gurin, ko a ganta a Ιaki.
Barira ta kada baki ta ce "Amma ta mayar da mijin nan tasono, Ζarya take yi gantalinta kawai take tafiya. Meye matan auren ba sa yi yanzu?"
Sajida ta ce "A'a Barira, ki daina cewa Ζarya ne"
"Ke wallahi, ko rantsuwa na yi ba zan yi kaffara ba, a gidan uban wa Aljani zai Ιauke mutum ya kai shi wani gurin? Ke ni fa da ake cewa ana ganin aljanu, ko su tsorata mutum ban taΙa yadda ba, iskanci ne kawai da Ζaryar banza ce, ba wani aljan duk 'yan iska ne kawai.
Nana ta ji wani abu mai zafi ya soki zuciyarta, duk da ba da ita suke ba, kawai ta Ζura wa Barira ido, ko Ζiftawa ba ta yi.
Tun Barira ba ta ankara ba, har ta lura, take ta ji tamkar an kwarara mata ruwan sanyi a jikinta, sai kuma ta Ιan tsorata ta ce "Nana lafiya kuwa?"
Ayshercool
08081012143
53
"Barira, kin taΙa haihuwa?"
Nana ta tambaye ta. "A'a me ki ka gani?"
"Amma dai ki na ganin mata su na Ιaukar ciki su haihu. Kuma kin yarda da abin da suke faΙa cewar haihuwa akwai wahala, duk da ba a bakin mutum Ιaya ko biyu ki ka ji ba. Kin yarda wannan ciwon na haihuwa akwai shi, duk da ba ki taΙa yi ba?"
Barira ta ce "Eh mana, ai wannan kowa ya san haihuwa akwai wahala"
"Kin yadda akwai ciwon haihuwa, amma ba ki yadda akwai na aljanu ba, saboda Allah bai jarabce ki ba, har ki ke Ζarar da cewa matar mutane yawon iskanci take tafiya? Duk wanda zai shaide ta, barin mijinta ne, tun da yake zaune da matarsa a haka, ke mene ne naki da za ki ce mutuniyar banza ce? Idan aka rutsa ki shaidar ina take tafiya iskancin za ki faΙa? Idan aka faΙi abu, ko baki yarda ba gara ki yi shiru ki ce Allah ya kyauta, musamman larura. Idan ba haka ba maganganu irin naki za su iya zama cutarwa a gare su". Jin Nana yau ta saka musu baki a magana ya sanya suka din ga goyon bayan abin da Nana ta faΙa gaskiya ne.
Da fari jikin Barira ya yi sanyi, daga baya ganin kowa ya hayayyaΖo mata, ya sanya ta hau bala'i, har abin ya koma faΙa.
Ita kuwa Nana tun da ta gama zazzagar abin da yake ranta, ta kammala girkinta, ta kwashe kayanta, ta koma Ιaki ta bar su da mayar da zance. Dama ga zafin laulayi, ga takaicin mutanen da ake tarawa a gidan babu dalili, ga kuma zafin Ζazafin da Barira ta yi wa matar, da ita kanta Nana ba ta sani ba, amma maganar da ta yi ta ji sanyi a ranta.
Yana daga kwance a kan katifa ya ce "Rayuwata" Ta Ιaga kai ta kalle shi ya ce "viens(zo) yana yi mata alama da hannunsa.
Ta Ζarasa gabansa ta zauna. "Dan Allah ki daina shiga maganar mutanen nan, ki daina kula su. Ni na daΙe ban ji mutanen da ba na Ζauna kamar su ba. Ba na son su zo su yi miki abin da ba zamu ji daΙi ba"
Ta jinjina kai ta ce "Haka ne, ka yi haΖuri nima ban so na shiga ba, haka kurum na ji maganar ta su kamar da ni suke yi. Sayyid ni da kai mun san azaba da raΙaΙin larurar nan. Ire-iren waΙannan maganannun da yadda wasu suke ganin kamar ciwon nan Ζarya ne, ya sanya da yawa masu larurar da dama a cikin wata damuwar ciwon ya yi musu illa, tun da ba a yarda da ciwon ba balle a Ιaukar musu mataki."
"To ai ba su ce da ke suke ba"
Murya a sanyaye ta ce "Sayyid, duk lokacin da aka yi maganar irin wannan larurar, ina jin tamkar da ni ake. Nima wasu lokutan na kan shiga Ιimuwa, na bar gida a gano ni a wani gurin, duk da ni ban taΙa kwanaki ba a ganni ba. Ta kai ta kawo har a zahiri ina ganin abubuwan nan. Sayyid kai ma fa wasu lokutan ina yi a gabanka ka na gani, to yaya za a ce mutum yana sane ya din ga mayar da kansa mahaukaci? Wanda kuwa duk aka samu da yin Ζaryar irin wannan ciwon, yana buΖatar kai shi gurin likitocin ΖwaΖwalwa, Sayyid ciwon nan babu daΙi, akwai wahala" ta yi maganar hawaye na zirarowa daga cikin idanunta.
Ya tashi zaune ya kai hannunsa jikinta zai rungumota, zafin zazzaΙin jikinta ya ziyarce shi. Ya kalle ta a tsorace ya ce "Ba ki da lafiya?" Ya furta maganar haΙe da haki, saboda yadda ya ji zafin a bazata.
Da sauri ta Ιora hannunta a Ζirjinsa ta ce "Sayyid dan Allah ka din ga Ιaukar al'amurana da sauΖi. Ga shi har girki na yi, ina komai nawa lafiya. Ka san lallaΙawa muke yi, ba ka da cikakkiyar lafiya. Ka daina saurin tsorata ko fusata. Ya saka hannun sa yana Ζara danne hannunta a saitin zuciyarsa. Yana iya ΖoΖarin sa a kan ya din ga saita al'amuransa. Amma ya rasa dalili duk abin da ya shafi Nana, kai tsaye yake jin sa a tsakiyar zuciyarsa. Ba ya iya yi masa shinge ko ya dakatar da shi. Yana so Nana ta haihu da shi, amma wahalar da ya ga tana sha, sai da ya ji dama cikin ya zube ko zata huta.
*****
Tun da Jamila ta koma gida, jikinta a sanyaye yake, gani take yi, duk wanda ya ganta ya san abin da ya faru da ita. Mama kuwa baki ya Ζi rufuwa, saboda Jamila ta zo da abin Duniya. Kuma kamar yadda ta gaya mata, sarin kaya ta raka Hajiya, babu wani bincike ta yarda da hakan ta amince.
Ta zo ba ta iya bacci sam, da ta kwanta bacc6, sai ta ga tamkar za ta buΙe ido, ta sake ganinta, a wannan gurin da suka je da Hajiya Sa'a.
"Jamila" Suwaiba ta kira sunanta, ta waiwaya ta kalle ta.
"Wai ya na ga ki na abu kamar mara gaskiya ne?"
Gaban Jamila ya faΙi ta ce "Me na yi na rashin gaskiyar, me ki ka gani?"
"To ai gani na yi kin kasa sukuni, ki na ta wani mutsu-mutsu gaki nan dai"
"Dan Allah Suwaiba ki ji da abin da yake damun ki, ni babu abin da ya same ni, lafiya Ζalau nake "
Suwaiba ta ce "To ai shikenan"
****
Nana duk sammakon da suka yi, su ne na goma sha Ιaya, a gurin ganin likita.
Wajen sha Ιaya na safe aka zo kan su, Nana suka shiga, sai dai wannan karon wani likitan daban suka samu. Suka gaisa Nana ta yi wa likitan bayanin komai. Tare da ba shi takardun gwaje-gwajen da aka yi masa, da kuma katin da aka rubuta masa magunguna.
Ya karΙa ya duba a tsanake, ya duba Bp Ιin Sayyid, ya duba Ζirjinsa da stethoscope.
Nana ta ce "Doctor yaya jikin nasa? Me ka gani?"
Bai kalli Nana ba ya ce "Me yasa ba ku dawo follow up ba"
Ta ce "Ai ba a bamu lokacin dawowa ba. Dama ni ce naga yakamata mu dawo Ιin. mu na ta ΖoΖarin kuΙin allurar su haΙu ne, ko ba su haΙu ba, zamu yi ΖoΖari ko a anan Asibitin gwamnatin ne, sai mu yi booking a fara yi masa"
Likitan ya ce "Ki na ji na 'ya ta?"
Ta ce "Eh"
"Ai mijinki ne ko?"
Sayyid ya jinjina kai. "To a duniya babu wani abu da Allah ba zai iya ba, babu shi. Batun allura ki bar wannan a hannun Allah. Kuma dan babu kuΙin allaura ba za a daina ganinsa ba. Zamu ci gaba da gwada shi, mu na ba shi magungunan da suka dace. Idan Allah ya yassare kwa zo a yi daga baya. Kuma jikinsa Alhamdillah da sauΖi sosai da sosai. Jinin dai haryanzu bai sauka yadda ake so ba. Amma zai sauka da yardar Allah. Kawai ki din ga kiyaye damuwarsa da Ιacin ransa. Idan kuma akwai wani abu da yake damunsa, ki zauna da shi ku tattauna ki ga ta ina za ku shawo kan matsalar?. Amma babu wani abu in sha Allah" Duk da ba lafiya likitan ya ba su ba, amma kalamansa akwai dattaku da Ζwarewa a kan aiki a cikin sa. Dan haka sosai Nana ta samu relief.
Ya rubuta musu lambarsa ya ce "Duk lokacin da za ku zo, ku kira ni, na baku ranar da nake aiki, ya zo ya din ga ganina." Nana ta din ga yi masa godiya da addu'a shi da iyayensa.
Sayyid ya ja wata takarda, ya yi rubutu ya miΖa wa likitan. Likitan ya karΙa ya duba. Ya yi murmushi ya ce "Madam, ashe kema babu lafiya ya ce na duba masa ke"
Nana ta yi murmushi ta ce "Rashin lafiyata, ai ba komai ba ce a kan tasa, ni na fi damuwa da shi Ιin dai"
"A'a tun da ya nemi alfarma, ai dole a yi masa"
Ya duba Nana, ya yi wa Sayyid bayanin laulayi ne kawai yake damunta, ya rubuta mata abin da zai rubuta mata na magani. Ya kuma ba ta gwaje-gwaje. Sayyid ya Ζi tafiya, sai da suka yi gwaje-gwajen.
Suka koma, ya tabattar musu da babu wata matsala, satin cikinta uku da kwanaki, ya rubuta mata magungunan da za ta yi amfani da su.
Suna tafe a adaidaita sahu, Sayyid ya kasa riΖe murmushinsa, ya kai bakin sa kunnen Nana ya ce "Saura kwana nawa ki haihu?"
Ta kwashe da dariya, ta ce "Ina na sani, ko cika wata Ιaya bai yi ba ma, mu dai ci gaba da addu'a Allah ya bar mana, ya bamu Ιa na gari"
Ya amsa da "Amin."
A bakin titi, Nana ta yi sayayyar salak, saboda shi take sha'awar ci. Suka shiga layin gidan na su.
Su na zuwa gidan, Nana da sauri ta shiga banΙaki, saboda fitsarin da ya cika mata mara. Sayyid tsayawa ya yi, yai shiru yana Ζare wa Ιakin kallo.
Nana ta fito bai ce mata komai ba, ta Ιauki cylinder gas, ta ce "Sayyid gas ya kusa Ζarewa, idan zaka iya fita in anjima sai mu je titi tare mu Ιuro"
Ya ce "To"
"Bari na sake Ιumama miyar"
Ta fito tsakar gidan kenan, Sajida ta ce "Nana, Allah ya taimake ki, da tuni da ke za a tafi bayar da shaida"
Cikin rashin fahimta Nana ta ce "Shaidar me?"
"Jiya hirar da ku ka yi, har ki ke yi wa Barira faΙa, a kan matar nan. Daga jiyan nan zuwa yau magana har ta kai kunnen matar. Ta din ga kuka mijin ya ce ba zai yarda ba da 'yan uwanta. Da yyayyenta ne za su zo su zane Barira. Mijin matar ya hana aka kai ta police station. Tun bayan fitar ku tana can, duk sai da muka je bayar da shaida. WataΖila dai kafin magariba a sako ta, ta dawo gida."
Nana ta numfasa ta ce "Gara da Allah ya sa ba na nan, dan babu inda zan je, shi yasa a rayuwa yake da muhimmanci mutum ya iya bakinsa. Wannan tara matan da ku ke yi, ku na surutai marasa amfani duk ba hanya ce mai Ιullewa ba"
Sajida ta ce "Wallahi haka ne, shi yasa ki ke burge mu ma"
"Allah ya kyauta"
Har Nana ta yi haΙin salak Ιin ta, ta fara ci, ya lura ba ta fahimci abin da yake faruwa ba, shi ma kuma bai gaya mata ba, ya ci abincin. Ta gama ci ta kalle shi ta ce "Sayyid, ka yi mini addu'a, Allah ya sanya kar na yi aman salad Ιin nan, na rufe sauran anjima zan sake ci"
"Kin cika yaji, sai kin yi ciwon ciki ko?"
Ta Ιan waro ido ta ce "Dama ka gani?"
"Eh ina kallon ki"
Ta Ιan yi murmushi ta ce "Idan babu yajin, ba zai yi daΙi sosai ba. Amma yanzu ya ka ke ji a jikin ka?"
"Ba sauΖi"
"Subhanallah, ba sauΖi kuma?"
Ya ce "Eh, kin je ki na hira da likita a gabana"
"Amma ko ba komai, ya kwantar mini da hankali, bai ce mini zaka mutu ba, kalamansa sun bani Ζwarin gwiwar da yakamata na samu" ta yi maganar Ζwalla na cika mata idanu.
Ya girgiza mata kai ya ce "Kar ki bari su zubo".
"To ba kai ne ba, komai na yi sai ka ji haushi na?"
Murmushin sa mai matuΖar Ζayatarwa ya yi, ya ce "Ba haushinki nake ji ba, tsaro nake ba ki, saboda tawa ce nikaΙai. sourire (smile) ki yi murmushi mana" ta noΖe kafaΙarta tana tura baki,ta juya masa baya.
Ya matsa bayan nata, ya sumbaci saman bayan ta, ya zagayo da hannunsa ta cikinta, ya kwantar da kansa a kan kafaΙarta. Gaba Ιaya jikinta ya yi sanyi. Damuwa ce ya ziyarce zuciyarsa, jin yadda Nana ta saki jiki sosai da rungumar da ya yi mata, ko ba a gaya masa ba ya san abin da yake ranta, tuna cewar babu abin da zai iya tsinana mata, ya sanya a hankali ya raba jikinsa da nata, wani irin tausayinta na ratsa ilahirin jikinsa.
Ta maze cikin yaΖe ta ce "Sayyid, ya na ji ka yi shiru ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Babu komai"
"A'a akwai wani abu. Dama likita ya ce mu zauna na tambaye ka, ko akwai wani abu da yake damun ka, haryanzu fa jininka bai sauka ba Sayyid"
Ya Ιan sake yin guntun murmushi ya ce "Damuwa ai akwai ta, ba na son Ιaga miki hankali ne kawai.
Haryanzu ina tunanin inda su Habu suka tafi, suka bar ki da Ιawainiya, Kodayake ko suna nan ma, kula da ni ba dolen su ba ne. Sai wahala ki ke sha, wallahi idan ina tuna hakan, sai na ji tamkar numfashina zai Ιauke a cikin damuwa nake sosai da sosai. Ba na son saka ki a damuwa ne kawai".
Nana ta tattara hankalinta ta matsa kusa da shi, ta riΖo hannunsa, ta kalli idanunsa da suka yi jawur. "Idan su Habu ba hakkinsu ba ne kula da ki. Ni yanzu ya zama haΖΖina, na san ba a banza Allah ya haΙa mu ba. Mu ci gaba da addu'a Allah ya kawo mana komai da sauΖi. Amma ina fatan dan Allah ka daina damuwa, idan ciwon nan ya matsanta maka a jikina nake ji, ka daina ba na so" ta Ζarasa maganar cikin shagwaΙa.
KafaΙarta ya ciza cikin wasa, yana rungume ta. Tamkar ba a cikin damuwa suke ba, suka ci gaba da raha, duk da yadda hayaniyar mata ta cika gidan, tamkar a na taro, saboda dawowar Barira, an cika gidan ana mayar da yadda aka yi.
Ana fara kiran sallar magariba, ta kai masa ruwan Ιumi banΙaki ya yi alwala.
"Za ka je masallaci ne?"
"A'a a nan zan yi"
"To yi sallar. Nima sai na yi muje mu Ιuro gas, ko rabi ne sai kuma na sayo gawayi, Ummi ta bani kurfoti, na din ga haΙawa da shi" Ya jinjina mata kai ya tayar da salla.
Yana kallon ta ta idar, ta buΙe jakarta ta Ιebo sauran kuΙin da suka dawo da su, ta nufi wardrobe ta haΙa su da waΙancan kuΙin. Kawai ta ga kayan wardrobe Ιin a hargitse.
Mamaki ya kama ta, ta san Sayyid ba ya taΙa mata wardrobe, kuma ita ba a haka ta bar wardrobe Ιin ba.
Ta janyo jakar gidan Sarkin baka, ta duba ta ga kuΙin nijar a ciki. Ta laluba ta Ιauki ledar, da kuΙin Nigeria ke ciki ta rasa. Ta watso kayan wardrobe Ιin gaba Ιaya, tana Ζara haskawa da fitilar wayarta.
Yana tsaye yana kallon ta. Muryarta na rawa ta ce "Sayyid"
Ya kalle ta. "KuΙinmu, kuΙin da ka bani na saka a cikin wardrobe na...naa..ajiye a nan ban gani ba, ko ka Ιauka?"
Ya yi shiru yana kallon ta, a zuciye ta nufi hanyar fita daga Ιakin, ya riΖe ta. Jikinta yana tsuma take ΖoΖarin fizgewa amma ya riΖe ta yana girgiza kai ya ce "Kar ki yi magana, ki yi shiru ko waye mu bar wa Allah. Tun da na shigo, na ga alamar an buΙe Ιakin. Kuma laifinmu ne, da ba mu saka mukulli ba, muka rufe Ιakin kawai."
"Sayyid ba a yi mana adalci ba. KuΙin Abincinmu da maganinka, sun kwashe gaba Ιaya wace irin masifa ce wannan? Daga wannan sai wannan ya ake so na yi ne?" Ya riΖe ta gam yana shafa bayan ta, a hankali ya ce "Ki yi haΖuri, ki daina Ιaga murya, akwai Allah"
Kuka take yi iya Ζarfinta, tana sheshsheΖa, ya rungume ta gam a jikinsa, shi kansa ya ji zafi da raΙaΙin satar da aka yi musu. Ba iya kuΙi ba, har da wasu daga kayan amfaninsu na Ιakin an Ιauka, ya san kuma hakan sabon Ζalubale ne, saboda ba su da wata hanyar samun kuΙi a yanzu.
Ji ya yi jikin Nana ya saki, kuma jikin yana Ιaukar sanyi. Karkarwa ta fara yi, tamkar ana jona mata shocking.
Cikin matsananciyar damuwa, ya zauna da ita a jikinsa, ya Ιauki wayarta da ta saki a gurin, yana haska fuskarta. Ya ga hawaye na fita ta gefen idonta. Hannayenta da Ζafafuwanta su na lanΖwashewa, goshinta kuma yana tsatstsafo da gumi.
Jin ta ta yi, jingine da wani abu da ba ta san ko mene ne ba. Ta shafa abin ta ji Ζurzunu-Ζuruzunu, tamkar dutse. Gurin baΖi Ζirin duhu ya gauraye gurin, ko tafin hannunta ba ta iya gani. A hankali haske ya fara shigowa gurin, har gurin ya yi haske ba ki Ιaya. Ta Ιaga kanta ta ga ba ta iya gano Ζarshen Ιakin.
Jin tari ta yi a bayan ta, ta waiwaya da sauri, ta ga Ζaisar a zaune lulluΙe da wani abu mai haske sosai.
"Ζaisar. Ba ka da lafiya?" Ta yi maganar tana nufar inda yake.
Ya yi shiru bai yi magana ba. Ta sake cewa "Dama kuma ku na rashin lafiya, kamar ka canza gaba Ιaya" ya yi murmushi ya ce "Mu na rashin lafiya mana, guba na ci" Ta waro ido ta ce "Guba kuma? Me yasa?"
"Tsohon nan na jikin mijinki, ya bani."
"Kuma ka sha? Wai meye alaΖar ka da shi? Kuma dan Allah me yasa yake bibiyar mijina?"
"Ba wannan ba, me yasa ki ka kira ni?" Cikin mamaki ta kalle shi ta ce "Kamar yaya? Ni ban kira ka ba ai"
"Fushi da Ιacin rai, duk wanda ki ka yi tamkar kin kira ni ne. Kuma ni yanzu ba ni da wani tasiri sosai, saboda jinya nake yi. Babu wanda ya san ina nan. Giyaz ya saka ni a gaba, ya mamaye Library Ιi na, yanzu rashin ganina zai sanya ya ci gaba da cutar da ku. Ba zan iya wani abu ba sosai yanzu, sai dai zan iya tasiri a kan bil'adama.
Duk ba wannan ba, duba can."
Ta Ιaga kai ta kalli inda ya nuna mata, Library Ιin Ζaisar ta gani. Ta ga gangar jikin Sayyid a kwance. Tsohon nan ya ΙaΙΙaure shi da wata irin igiyar Ζarfe. Ζasan gadon da yake kai kuma, wata irin wuta ce take ci a Ζasa. Nana ta zabura a rikice, ta ce "Wannan ai Sayyid ne"
"Ζwarai shi ne, ba wani ba. Kuma Giyaz shi ya sanya masa matsalar da ku ke ciki na auratayya. Sai dai abu Ιaya zan iya gaya miki. Matsalar zuciya da hawan jini da yake fama, wannan ciwo ne yake damun sa. Amma Giyaz na assasa wani abin. Kuma... Amma dai shikenan"
Nana ta buΙe baki za ta yi magana, ya ce "Kar ki tambaye ni komai, kin san sharaΙin. Kalli" ya yi maganar yana sake nuna mata gurin.
Alhaji Fatuhu ta gani, ta yi Ζuri da ido ta ce "Kamar na san wannan"
"Ba kama ba ce ba kin san shi, ciwo ne da zafin sihirin da aka yi masa ya mayar da shi haka. Sai kuma albishir da nake yi miki, da Ζanwar ki ta zama cikakkiyar 'yar Ζungiyar asiri. Ζayar kuma wannan bararojin da ta taΙa baki magani, ta aura mata Ιanta, wanda yake baΖin aljani ne. Kuma ta tarkato kan iyalanta duk su na jikinta. Kuma kowanne akwai abin da yake mora a jikinta. Ke in taΖaice miki ma, a kowane lokaci za ta iya rasa hankalinta ko ma rayuwarta gaba Ιaya. Shikenan bissalam"
"Ζaisar" sai kuma ta yi ido huΙu da Sayyid.
"Kin tashi?" Ta yinΖura ta tashi zaune, tana kallon Ιakin.
Sayyid ya ce "Ζaisar Ιin ba shi da lafiya ne?" Ya yi maganar yana tsare ta ido.
"Wane Ζaisar Ιin?"
"Tambayata ki ke yi?" Shiru ta yi, ita ba ta iya tuna koma ma a cikin abin da ya faru ba. Idonta ne ya sauka a kan kayan da suke gaban wardrobe a Ζasa, sai kuma abin da ya faru ya faΙo mata. Afujajan ta tashi ta sake nufar wardrobe Ιin, tana zazzage kayan tana kuka.
"KuΙin nan fa babu su, an kwashe ki daina wannan dube-duben" ya zauna ta yi shiru ta sanya kayan a gaba tana kallo.
Ya yi mata shiru ya Ζi kula ta, ya kwanta a kan katifa, yadda take a hasalen nan, idan ya matsa faΙa za su yi. Cikin ΖanΖanin lokaci nannauyan bacci ya yi awon gaba da shi.
Barira na kwance a Ιakinta, ta yi ΙaiΙai tana bacci, ta ji kamar ana karta mata farce a Ζafafuwanta. Har ta maze ta ci gaba da bacci, amma ta ji an cigaba. A fusace ta ce "Gali meye haka, za ka din ga karta mini faratanka, ina cikin bacci ne?" Shiru bai amsa ba. Ta laluba ta ji yo Ζeyarsa a can Ζarshen gado, yana bacci. Ta koma ta kwanta, amma ta ji an cigaba, ta tashi zaune tana zabga ashariya.
Ta kunna fitila, ta ga babu kowa. Ta yi tsaki ta sauka daga kan gadon, ta fito tsakar gida domin ta yi fitsari. Bayan ta fito daga banΙakin, kanta ko Ιan kwali babu, kawai ta yi karo da Nana a tsakiyar tsakar gidan tana yi mata wani irin mugun kallo.
Ta haska Nana ta ce "Nana lafiya kuwa?"
Sai dai Nana ba ta yi magana ba, ta sake haska ta, za ta yi magana. Ta ga ta rikiΙe ta zama wata irin Ζatuwar mage, baΖa Ζirin, girman ta ya yi na tunkiya Ζosashiya da ita, ta yo kanta tana buΙe haΖora.
Da gudu Barira ta shiga Ιakinta, tana ihu tana kiran sunan Gali.
"Ke mahaukaciya, mene ne haka za ki din ga ihu kina kiran sunana a tsohon daren nan?"
Ba ta ce masa uffan ba, ta duΖunΖune, tana mayar da numfashi. Ta tsorata sosai da sosai, da Ζyar ta samu ta yi bacci. Sai dai a cikin baccin ma, mafarkin magen nan kawai ta din ga yi tana bin ta, tana karta mata farata tana cizon ta.
Sayyid kuwa yana jiyo kururuwar Barira, hakan bai dame shi ba, sai ganin Nana da ya yi a zaune, ta haΙa kai da gwiwa.
Ya yinΖura ya tashi zaune, bai ce mata komai ba, ya kwantar da ita a kan katifar, ya rufe su da bargo ya rungume ta yana shafa bayanta. Yana jin ta tana kuka, har ta yi ta gaji bacci ya Ιauke ta.
Dauriya kawai yake yi, amma ji yake tamkar ya taya ta kukan.
Washegari, Barira ta tashi da matsanancin zazzaΙi da ciwon kai, ta din ga yi wa mijin kuka, tana cewa ya mayar da ita gidansu, mayu sun kama ta a nan gidan, ba za ta yadda a kashe ta a banza ba. Babu yadda ya iya ya tattara ta ya kai ta gidansu.
Kwanki biyu da sace kuΙin nan, Nana ta rasa abin da yake yi mata daΙi. Dubu talatin ce ta ragu a hannunta, shi ma cikin irin kuΙin da ta zuba a jakarta ne suka fita da su. KuΙin Nijar Ιin kuma ba ta san ma ina za ta a canza su ba. Bayan haka tayi tunanin idan Habu ya dawo fa, me za ta ce masa? Ta din ga tunanin yadda za ta yi da dubu talatin Ιin nan, ba tare da ta rushe gaba Ιaya ba. Ga shi magungunan da yake sha kawai, na wata Ιaya dubu goma sha biyu take sayen su.
Sai dai kamar yadda yake nanata mata, ta yi haΖuri, ya sanya ta fauwwala wa Allah lamarin.
Kwana biyar da kwashe kuΙin nan, Sayyid ya hana Nana gaya wa kowa. Sai dai cikin dare ba ta iya bacci, saboda lissafi da tunani. Ta kira Ummi ta tambaye ta batun barkono, ta ce ana ta saya, ta sayar da ya kai rabin buhun. Kayan Abinci da Mama ta haΙo mata da su, take ta cancana musu.
Da daddare ba ta iya bacci, saboda damuwa da tunani, sai dai abin yana damun sa fiye da yadda yake damun ta. Su ka wayi gari, ya tashi jikinsa babu daΙi, yana ta numfarfashi.
Abin Duniya ya Ζara damunta, ya kuma Ζi cin komai. Muryar Barira ta jiyo a tsakar gida, da ta dawo, tana maganganu tana ba wa su Sajida labari.
"Mayu sun kama ni a gidan nan, kuma da Ζarfina na dawo, wallahi sai sun ci uban su, kurwata ta fi Ζarfin mutum".
Sajida ta ce "Ban gane mayu ba, suwaye mayun kuma?"
Barira ta ce "Oho, ki zuba ido ki gani, Allah zai tona musu asiri"
"Ni fa ba na son kurman baΖi, a masu shigowa ne mayun, ko kuma zaunannun gidan"
"Na ce ki zuba ido ki ga ikon Allah"
Bai fi mintuna biyar ba, wani irin hayaΖi, mai azabar yaji, ya turnuΖe gidan.
Nana da take lafiya Ζalau ma, ta fara tari.
Shi m tarin yake yi, numfashinsa kamar zai Ιauke, ta Ιaukko mafici ta din ga yi masa fifita. Ta gaji ta tashi, da nufin ta je ta ga me ake Ζonawa yake wannan uban hayaΖin haka. Amma ya riΖe hannunta ya hana ta. Haka suka wuni a galabaice. Sajida ma sai bala'i take yi, tana cewa Barira za ta kashe ta da hayaΖi.
"Wai Sajida ko ke ce mayyar nan ne?"
"Ke kama bakin ki, wallahi ki ka ce mini mayya, sai mun yi shari'a da ke"
Barira ta ce "Sai ki saurara mini, tun da dai ba ke ba ce" Haka suka wuni, Barira tana gana musu azaba, da wannan azababben abin da take zubawa a cikin murhu.
Washegari ma, azabar hayaΖin nan ce ta tashi su Nana, numfashin Sayyid tamkar zai Ιauke saboda azaba.
Nana dai ta ci gaba da daurewa, amma yamma na yi, Barira ta sake cika kurfoti da gawayi, ta tayar da wuta ta afka hayaΖin nan.
A fusace Nana ta fita, ta tarar da ita tana ta girgiza kurfotin, tana zuba wani abu a ciki.
Nana ta ce "Barira, dan zatin Allah ki daina zuba wannan abin. Ina da mara lafiya a Ιaki. Yana da matsalar numfashi, jiya kwana muka yi babu bacci. Kuma da sassafe kin banka wani, kuma yanzu ma ga shi kina sake kunnawa"
Ta kalli Nana ta ce "Ai duk wanda ya hana uwar shi bacci, wallahi shi ma ba zai yi ba"
Nana ta ce "Kamar yaya kenan?"
"Kamar yadda ki ka ji"
"Ni dai koma mene ne, ki yi haΖuri idan ba ki yadda ba, zo mu je Ιakin ki ga halin da yake ciki"
"Babu ruwana da halin da yake ciki, kurwata ce ta fi Ζarfin duk wani maye wallahi"
Nana ta ce "Barira mu ne mayun da ki ke faΙa dama? To Barira ko za mu ci mutum ma ci taki, jiki duk dauΙa?"
"Ko ma duk uban mene ne, tun da aka kama ni aka lasa, an ji zaΖin kurwa ta, wallahi sai mutum ya ci ubansa, miyagun banza kawai"
"Mu ne mayun Barira?"
"Eh ku ne, ko na ce ke"
Nana ta Ζarasa daf da Barira ta damΖi tsintsiyar hannun Barira ta ce "Ki ka ce ni mayya ce?" Barira ta yinΖura za ta fizge hannunta, ta yi bala'i. Kawai ta ji jikinta ya yi wani irin nauyi, kuma jikin ya yi mata wani irin sanyi, ta kasa motsa komai. Kawai ta silale ta faΙi Ζasa.
Ayshercool
08081012143
54
Ihu Sajida ta saka, tare da sauran matan da suke zaune, tamkar ana bajekolin kasuwar Ζauye, suka dare ganin daga riΖe hannun Barira da Nana ta yi, ta faΙi Ζasa. FaΙuwar da ba su da tabbacin, tana raye ko mutuwa ta yi.
Wasu suka yi waje da gudu su na ihu, tamkar garken tumakin da ba su san inda suka dosa ba.
Nana kuwa idanunta a rufe, ta nufi Ιakin su tana tangaΙi, Sayyid kuwa da Ζyar ya lallaΙa ya tashi yana ΖoΖarin fitowa, amma mai afkuwa ta riga ta afku. Nana na shiga Ιakin ta faΙa jikinsa, ya taro ta. Gaba Ιaya jikinta ya saki kuma ya yi sanyi Ζalau, shaidar Ζaisar ya buge ta.
Ya Ιauki wayarta, ya tura wa Ummi saΖo.
Tuni aka kira mijin Barira, jikinsa na rawa ya shigo gidan, tare da rakiyar wasu mazan.
Ya durΖusa a kan Barira ya taΙa ta, ya Ιago ta, sai dai ya ga tana numfashi, sai dai idanunta a kakkafe, ya girgiza ta yana kiran sunanta "Barira. Barira ki buΙe idonki. Ki na ji na?" Barira ba ta motsa ba, kuma ba ta yi magana ba. Sai dai numfashinta yana fita normal.
Mijinta ya ce "Dan a samo adaidaita sahu mu tafi Asibiti"
Ζaya daga matan da abin ya faru a gaban su ta ce "Wane Asibiti, ai ko an je Asibiti babu abin da za a gani, Nanan za a janyo daga Ιakin, a yi wa dukan tsiya a sanya ta tsallaka ta, shi ne za ta tashi, kama mata kurwa ta yi"
Ζaya daga mazan ya ce "A'a ba za a dake ta ba, a kai ta dai gurin hukuma, a san abin yi."
Mijin Barira ya ce "Wane irin kar a dake ta, kana kallon halin da matata take ciki"
Ya miΖe ya nufi Ζofar Ιakin su Nana, cikin Ιaga murya ya ce "Kina ina, ki fito ki tsallake mini mata, ki sakar mata kurwa" Sai dai ya ji shiru, babu wanda ya yi magana. "Ki fito ko na shigo wallahi"
Wani ya ce "Kar a yi haka Gali, ka ga matar aure ce, bai kamata a bi abin da mata suka faΙa ba, kamata ya yi a zurfafa bincike tukuna, kar a Ιauki doka a hannu, a zo daga baya a ji kunya"
Gali ya ce "Malam ni dai ba zan ji kunya ba da yardar Allah, kalli halin da yarinyar nan fa take ciki. Idan ta mutu fa? Wallahi ba zan yarda ba"
A fusace maΖwabcin na su ya ce "To a je Asibiti mana a duba, sai haΖilo ka ke yi, matarka matarka. Kamar ba nan ka ke jibgarta, ake Ζwatar ta da Ζyar ba, sai da aka haΙa ka hukuma ka daina, auren da ko shekara biyu bai yi ba, a lokacin ba ka yi tunanin ta mutun ba sai yanzu?"
A fusace Gali ya ce "Kar ka gaya mini maganar banza mana, ina ruwan ka da dukan da nake yi mata, dama munafunci ne ya sanya ku ke yi mana sulhun?"
Ummi ce ta yi sallama, Sajida ta yi caraf ta ce "Yauwwa ga yayarta, ita ce dama ta kawo ta gidan nan"
Cikin mamaki Ummi ke bin dandazon jama'ar da kallo. Ta ce "Wai lafiya me ya faru?"
Mijin Barira ya ce "Mene ma bai faru ba, kin kawo mana mayya ta kama mini kurwar mata. Dan haka sai ki shiga ki fito da ita ta tsallaka ta"
Tuni idon Ummi ya cika da hawaye, saboda ba ta Ζaunar tashin hankali ta ce "Wallahi mu ba mayu ba ne ba. Nana Ζanwata ce, akwai dai abin da ya faru amma ba wai Nana ta kama kurwar wani ba"
"To Ζarya aka yi mata? Ba ga Bariran can a kwance ba, ta tashi mana".
Cikin tashin hankali Ummi ta ce "Wallahi kaf zuriyarmu babu mayu, Nanan ma matsalar mutanen Ιoye ne da ita, amma ba maita ba, bari na duba ta" Ta nufi Ιakin da su Nana suke. Tuni gidan ya sake Ιinkewa da mutane, ya cika fal wasu suna a fito da Nana, a zane ta a saka ta tsallake Barira.
A zaune ta tarar da Sayyid, rungume da Nana a jikinsa. Cikin damuwa da tashin Ummi ta ce "Wai me ya faru ne?" Ya yi shiru yana kallon Ummi, sannan ya mayar da idonsa kan Nana.
Ta Ιauki wayarta ta kira Baba. Tana jin ya Ιaga ta fashe da kuka.
Baba ya ce "Ke meye haka lafiya?"
"Baba babu lafiya, dan Allah ka zo gidan Nana, akwai matsala ne"
"Gidan Nana kuma? Ina ne gidan Nanan, kuma matsalar mene?"
"Baba mutanen unguwa sun taru, za su dake ta, kar su kashe ta ni ban ya zan yi ba"
A sukwane Baba ya miΖe ya ce "Ζarya ne. Nanan za su kashe mini, ai zan yarda kowa zai iya Ιaukko magana a cikin ku, amma ban da Nana. A can gidan gadin nata ne za su dake ta?"
"Baba wane gidan gadi kuma, ai sun bar gidan tana nan kusa da ni, ka manta ne? Ka cewa Nasiru ya rako ka ya san gidan"
"Gani nan zuwa" ya kashe wayar ya yi waje da sauri.
Ummi ta tsaya a bakin Ζofar, tana ta ba su haΖuri. Amma sai nema suke yi su ture ta, su shiga Ιakin.
"To ban da wulaΖanci ma, ta shige Ιaki taΖi fitowa, da yake ba ta da gaskiya. Maimakon mijinta ya fito ya bayar da haΖuri, shi ma ya yi zamansa saboda rashin tsoron Allah, da rashin gaskiya"
Ummi ta ce "Mijinta ba shi da cikakkiyar lafiya, ita ma aljanu sun buge ta, dan Allah ku yi haΖuri" Sai dai abin ya fi Ζarfin Ummi, ΖoΖarin hankaΙe ta kawai suke yi, su cimma Nana.
Ana haka sai ga maΖwabcin su Nana, tare da jami'an tsaro. A dole mutanen suka saurara. 'yan sanda suka ce, a tafi da Barira Asibiti, abin da likitoci suka ce, da shi za a yi amfani.
Ana haka Baba ya Ζaraso, cikin tashin hankali.
Ummi na ganin sa ta yi ajiyar zuciya. Ummi ta ce "Baba ka zo?"
"Eh, ina Nanan take, kuma uban me ta yi za a dake ta da?"
"Ai gama 'yan sanda sun zo, saΙani suka samu da wanda suke zaune gida Ιaya, shi ne suka ce mayya ce"
Baba ya ce "Maita kuma? In ji uban wa?"
Mijin Barira ya ce "Ga shaida Baba, kalli matata a baje a kwance"
"Kuma sai ka ce 'yata mayya ce? To wallahi Ζarya ne, kaf danginmu babu mayu, ku dai nemo wani abun, ba maita ba wallahi" 'Yan sanda suka shiga maganar, aka tafi da Barira Asibiti.
Sai da aka bar 'yan sanda biyu, gudun abin da ka iya faruwa, saboda matan da abun ya faru a gaban su, su na ta Ζara balbalawa wutar fetur. Tare da mayar da abin da aka yi da wanda ma ba a yi ba. Gaba Ιaya zancen ya zagaya unguwa.
Har sha Ιayan dare case bai Ζare ba, Nana ta farfaΙo ta ga Ummi a Ιakin su, ga duhun dare ya fara yi.
"Ummi lafiya kuwa?"
"Ina fa lafiya Nana, meya haΙa ki da mutanen gidan nan, ga shi ana cewa ke mayya ce".
"Mayya kuma?"
"Eh mana, yanzu case na hannun 'yan sanda, Baba yana can tare da su, ana jiran likitoci su faΙi sakamakon binciken su."
Nana ta gaya wa Ummi iya abun da ta iya tunawa. Sai dai ta sha mamaki, ta ji wai Baba ya zo kan matsalar ta.
Ta kalli Sayyid da yake kwance lamo, abin Duniya duk ya dame shi.
Sajida ta haΙa kayanta, ta gudu ta ce ba za ta iya kwana da Nana a gidan ba.
Sai zuwa da safe, Likitoci suka tabattar da anemic shock ne ta samu, bayan binciken ΖwaΖwaf da suka yi, suka gano ta yi Ιari sati biyu baya, ta kuma zubar da jini sosai ba ta je Asibiti ba. Ta zo ta yi zazzafan zazzaΙi na typhoid amma suka alaΖanta hakan da mayu, nan ma ba a je Asibiti ba. Hakan ne ya haddasa faΙuwar ta. Bayan fito da sakamakon, mijinta da 'yan uwanta suka ce ba su yarda ba, sakamakon Ζarya ne kawai aka gaya musu.
Ga Barira ta farfaΙo, tun a cikin daren ma, har ta ci Abinci, amma suka ci gaba da surutu a kan Nana mayya ce.
Ummi tare da su Nana ta kwana, saboda tsananin tsoro. Dan da gidanta akwai guri can za su tafi ma. Sai dai tashin hankalin abin da ya faru, ya sanya jikin Sayyid rikicewa gaba Ιaya, ya zamana kamar ma ba ya gane wanda yake kansa.
Hankalin Nana ya yi mummunan tashi, ga shi babu isasshen kuΙin tafiya Asibiti. Ta kuma san tashin hankali, da damuwar abin da ya faru ne, ya sanya jikin nasa Ζara rikicewa.
Nana ta rasa abin da yake yi mata daΙi, ga matan gidan kowacce ta koma gidansu, sun Ζi dawowa gidan wai tsoro suke ji.
Ummi ce ta yi sallama, Nana ta amsa ta yi mata izini ta shiga Ιakin. Hannunta riΖe kular Abinci. Ta kalli inda Sayyid ke bacci a wahale, numfashinsa na fita sama-sama. Cikin damuwa Ummi ta ce "Yanzu Nana haka jikin nasa ya koma?"
"Wallahi Ummi, gaba Ιaya hankalina a tashe yake"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ana wata ga wata"
Cikin damuwa da rashin fahimta ta ce "Me ya faru?"
Cike da karaya, da matsanancin tausayin Ζanwarta ta ce "Mai gidan nan ne, ya je ya same ni, ya bani dubu goma sha biyu, wai ga sauran kuΙin ku nan, ku tashi. Ba ya son tashin hankali, kuma ga sauran 'yan hayar sun ce ko ku tashi, ko ya mayar musu da kuΙinsu su tashi. Nayi-Nayi ya Ζara wani abu, tun da ko wata ba ku yi ba, amma ya Ζi wai wannan Ιin ma da Ζyar ya samo su ya kawo."
Nana ta jingina da jikin bango tana maimaita "Innalillahi wa Innalillahi raji'un"
"Nana mene ne abin yi yanzu?"
Nana ta girgiza kai, jiki a sanyaye ta ce "Ban sani ba Ummi"
"To ko wani gidan za a nemo? Sai na koma na neme shi, na roΖi alfarmarsa?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a Ummi, an riga an yi mini mummunan tambari a unguwar nan, abu ne mai wahala ma mu sake samun wani gidan a unguwar nan"
"Bari na kira Baba na ji me zai ce"
Nana ta ce "A'a Ummi, kin san halin Baba, kar ranki ya Ιaci"
"To Nana ya zamu yi, dole a kira shi mu ji me zai ce" Ummi ta kira lambar Baba, yana Ιaga wayar muryarsa a sama ya ce "Ya kuma aka yi, ba an kashe case Ιin a gurin 'yan sanda ba?"
Ummi sai da ranta ya sosu, amma ta maze ta ce "Baba ba wannan ba ne. An kori su Nana daga gidan da suke ne, mai gidan da suke ya ce sai sun tashi"
"To sai kuma aka yi yaya? Ni zan nemo musu wani gidan? Ko kuma mijinta ne yakamata ya nemo musu wani?"
"Baba ka fa zo gidan nan, ka ga halin da mijin nata yake ciki na rashin lafiya, saboda haka aka kore shi daga gurin aikin gadi. Dan Allah Baba ka yi wani abu a kan yarinyar nan. Nana yarinya ce Ζarama pressure ta yi mata yawa."
"To Ummi ya ki ke so na yi? Ni dai nan gidan babu gurin da zan ajiye ta, ita da mijin nata, idan kuma ke ki na da guri ki taimaka ki ba su. Idan ba haka ba ta nemo 'yan uwansa su Ιauke shi, su rakata inda danginsa suke. Kin san dai nan gidan idan ta dawo, abin da za ta ci ma aiki ne. Nima yanzu sai abun da aka samo aka bani"
Hawaye ya cika idon Ummi, cike da takaicin yadda Baba bai fiye damuwa da damuwarsu ba. Ta ce "Baba da ina da inda zan ajiye Nana da mijinta, wallahi ba zan kira ka ba"
Nana ta ce "Ummi, dan Allah ki katse kiran nan, nima ba zan koma can gidan ba."
Tarin Sayyid ta ji, ta mayar da hankalinta kan sa, ta nufe shi tana faΙin "Sannu Sayyid"
"Ki ba ni ruwa" ta amsa da to. Ta Ιaukko ruwan leda, ta buΙe masa ya tashi zaune ta fara bashi.
"Sannu Sayyid" Ummi ta faΙa cikin tausayawa, kallo Ιaya ta yi masa ta gane yana jin jiki. Da da ne, kome za a yi,ba zai bar gashin nan a buΙe ba. Amma yanzu ba ta gashin yake yi ba, ga fuskarsa duk ta kumbura. A zuciya irin ta Nana, ta san ko a titi ta tsince shi a wannan yanayin, ba za ta iya tafiya ta rabu da shi ba, balle mijinta.
Ζarar da wayarta ta yi ne, ya sanya ta dawo hayyacinta. Ta Ιaga wayar tare da yin sallama.
"Ke Hansai, ina ta kiran wayar ki, amma ki ka Ζi Ιagawa?"
Ummi ta ce "Eyya, ba haka ba ne Uwani,ba na kusa ne, ya gida ya mutanen garin?"
"Lafiya Ζalau, ya na ji muryar ki Ζasa-Ζasa, laulayi ko rashin lafiya"
Ummi ta yi yaΖe ta ce "Ba gara a ce laulayi nake ina kwance ba, da abin da yake faruwa"
"Subhanallah, meyafaru?" Kasancewar Uwani kaka ce a gurin su Nana, Ζanwar kakarsu ce, da kakarsu wadda Nana ta ci sunanta da Uwani, uwa Ιaya uba Ιaya suke. Sai dai ita tana can Garko da iyalinta. Ummi ba ta Ιoye mata komai ba, ta gaya mata. Uwani ta rafka salati. Ta ce "Sai an yi magana ku nuna ku mutanen birni, kun fi mutanen karkara wayewa. Ina wayewar take. Aikuwa sai na kira Isa na ci ubansa mara mutunci. Tuntuni nake ganin take-takensa kamar har da Ζiyayyar uwar su, take shafar su a gurinsa. Ai Imrana yana zuwar mini nan. Ya hana kowa riΖe su kuma shi yana yi musu riΖon sakainar kashi. Yanzu ina duk sauran 'yan uwanki Ummi, ina 'ya'yan Atine, ina su Gaddafi da ba za ku iya taruwa ku rufa wa 'yar uwakku asiri ba?"
AREWABOOKS
"Wallahi Uwani mun yi iya yinmu ne.."
"Rufe mini baki, ina wani iya yinku, kuma duk wanda ya ce mana mayu Allah ya isa bamu yafe ba. Mu bamu gaji maita ba, balle a saka yarinya a gaba a tsangwame ta.
Na san babu lallai ta iya zaman Ζauye, amma mu nan akwai Ιakuna, har ma da gida da babu kowa, idan za su iya zama ta yi jinyarsa. Babu mai damun ta, kuma babu mai cewa ta tashi.
Amma tabbas kun ji kunya, idan har ku ka bari Asma'u ta wulaΖanta, a ce an rasa inda za ta zauna, ta yi jinyar mijinta, yawan ku kun zama taron tsintsiya babu shara." Ummi ta yi shiru, Uwani akwai kirki da karamci, amma idan ta botsare tana faΙa, to duk gaskiyar ka, sai dai ka yi haΖuri. Ta gama faΙan ta, Ummi ta kashe wayar.
Ta kalli Nana, ta ga yadda ta tattara hankalinta a kan mijinta, tana ba shi Abincin da ta kawo musu, sai lallaΙa shi take, da alamu abincin ma ba ya so.
"Nana, kin ji abin da Uwani ta ce?"
Nana ta girgiza kai ta ce "A'a.
"Cewa ta yi idan za ki iya zama, ku tafi can Buda ki kula da shi, akwai inda za ku zauna. Kin ga nan tun Baba ya san maganar maitar nan, kamar Mama ta ji ne. Ita kuma kin san gishiri za ta Ζarawa abin ta yi ta bayar da labari. Amma ban sani ba ko ki na da wata shawarar?"
"Ummi wace shawara? wanda yake ruwa ko takobi aka miΖa masa, ai karΙa zai yi. Sai dai shi nake tausayawa, amma ba ni da wata mafita da ta wuce wannan Ιin. Ni in dai zan samu inda zamu zaune na kula da shi, ba komai zan zauna ko a cikin dutse ne ba Ζauye ba"
"Kin tabattar Nana? Da wayonki fa sau Ιaya Baba ya taΙa bari, muka je muka kwana biyu"
Nana ta ce "Ba komai, zan zauna"
Sayyid ya sanya hannunsa biyu, ya damΖe na Nana.
Nana ta kalle shi ta ce "Sayyid, mene ne?"
Idanunsa sun kaΙa sun yi jawur, wata jijiya a saman goshinsa ta Ιaga ta kumbura, fuskarsa ta yi jawur. LaΙΙansa sauka din ga karkarwa yana son ya yi magana, Nana ta girgiza kai ta ce "Ba sai ka yi magana ba Sayyid. In sha Allah duk rintsi ina tare da kai, har Allah Ubangiji ya baka lafiya" Ummi ta kasa jurewa ta fashe da kuka.
Nana ta ce "Ummi idan ki ka yi kuka,ni ya zan yi? Kun saka ni a tsakiya, nama fi ku juriya, har da kai ma" ta yi maganar tana murmushi bayan saka idanunta cikin na Sayyid, duk da idon nata a cike da hawaye.
"Ummi ki gaya wa Uwani na amince"
Ummi ta share hawayenta ta ce "To shikenan, ya za a yi tafiyar to?"
"Ina ga a sayar da kayan Ιakin nan, katifar ta ishemu, sai a sai ledar Ιaki, sai kayan sawarmu"
"Nana, kina amarya amma a ce Ιakin ki babu kayan Ιaki, haka za ki je ki zauna? Kin san mutanen Ζauye ba sa raina abin surutu dai"
"Ummi ai ba ado da kwalliya zan je ba. KuΙin kayan ma riΖe saboda Ιawainiyar abinci da kuma magani"
Ummi ta Ιan yi shiru ta ce "Kuma haka ne, yanzu zuwa gobe in Allah ya kaimu, zan samo dillalai su saya"
Cikin sauri Nana ta ce "A'a Ummi, ba na son ci gaba da zama a unguwar nan, ban san me za su yi mana ba. Idan da hali a nemo su yau kawai. Su saya gobe in Allah ya kaimu mu tafi"
"To shikenan, bari na fita na gani"
*****
Yana zaune a cikin office Ιin sa, ya Ιora Ζafafuwansa a kan tebur, yana juyi, ya din ga kiran lambar cike da fatan a Ιauka. Har ya yanke tsammani, kawai ya ji ta Ιauka, sai dai ta yi shiru.
Da sauri ya sauke Ζafafuwansa ya ce "Hello" ta yi shiru ba ta amsa ba.
"Hello ki na ji na?"
"Eh" ta amsa a raunane.
"To ba za ki yi mini magana ba?"
"Ba cewa ka yi ba ka gane ni ba, ranar da na kira ka?" Ya Ιan yi guntun murmushi ya ce "Ki yi haΖuri, sai daga baya na Ιauki muryar ne. Ya ki ke ina fatan kina lafiya?"
"Ai baka damu da ina lafiya ba, tun da ka sake ni baka Ζara nema na ba, saboda ka yi aure matarka ta haihu, dama ni haushina ka ke ji, ba na haihuwa"
"A'a Yusra, kar mu fara haka da ke. Kin san ko bayan mun rabu, na yi ta neman lambarki, amma ba ta shiga har na haΖura. Ya jikin ki?"
"Da sauΖi, amma ni ba mahaukaciya ba ce"
Sagir ya ce "Ai dama ban ce ba"
"Lokacin da muna tare ai ka ce" ya yi murmushi ya ce "Wannan ba ya wuce ba? Amma Mami ba ta san kin kira ni ba ko?"
"Eh, ina gidan Mummy Zahra, da wata na haΙu sunanta Nana, ita ma ta san irin rashin lafiyata. Ita ma tana yi"
Ya ce "Haba dai?"
"Wallahi. Ita ta din ga ba ni shawara, ita ce ma ta ce na kira ka fa, na ma zata ba zaka Ιauka ba, ka Ιauka amma ka nuna ba ka gane ni ba" dariya ya yi ya sakankance sosai, yana sauraren Yusra. A yanayin surutun da take yi, ya fuskanci jikinta da saura, ba ta warke ba, amma ya tattara hankalinsa yana sauraren ta. Hirar ta din ga tuna masa da yadda suka zuba soyayya a baya kafin aure. Yana kallon kiran Shukura amma ya Ζi Ιagawa ya ba wa Yusra lokacin sa.
"Ki na ji na"
"Eh"
"Yanzu ina gurin aiki, kuma lokacin salla ya yi, zan sake kiran ki, in sha Allah"
"Tom sai anjima"
"To 'yar farata, bye-bye"
Kamar tana gabansa ta saki murmushi, cike da sanyin jiki, saboda ta yi kewar jin sunan.
Shi ma murmushin ya yi, yana tuna wasu abubuwa da suka wuce.
Ya kira Shukura, sai da ta kusa katsewa sannan ta Ιaga. "Madam ya aka yi ne?"
"Ina ta kiran ka, kana waya, har da rejecting kirana"
"Sarkin Ζorafi, kin san da wa nake wayar ne?"
"Ai ba sai ka gaya mini ba, na san 'yan matanka ne"
"Ni ba da 'yan mata nake waya ba. Ya aka yi?"
Shukura ta ce "Ba komai"
"Madam Shukura, bakomai Ιin ki, na nufin akwai komai. Yanzu dai a yi mini afuwa da ni da 'yan matan nawa."
"Ni shikenan kawai" ta kashe wayar. Ya girgiza kansa tare da Ιan lumshe idonsa.
****
A ranar dillalai, suka saye wardrobe da mudubin Nana, da sauran kayan da take ganin za su zame musu shirgi.
Ta tattare musu kayan su cikin bagcco, duk wani kayan amfaninsu ta tattare. Da safe Ζarfe goma, ita da Ummi suka je suka samo taxi. Har fargaba take yi kar mijin Ummi ya yi Ζorafi a kan yawon da take yi saboda ita. Duk da ba mazauni ba ne. Suka yi cinikin a nawa zai kai su Garko cikin Ζauyen Buda.
Aka Ιaure katifa a saman taxi, aka loda kayan su a ciki.
Ummi ta shiga gaban motar, ita da babbar 'yar ta Islam.
Nana kuma suka shiga bayan motar, tare da Sayyid.
Ya kwanta a jikin Nana ya yi shiru, ita kuma ta riΖe hannunsa tana matsa masa a hankali cike da kulawa.
Awa Ιaya da rabi, suka isa har cikin garin Buda. Sai dai shigar su garin ke da wuya, Nana ta fara jin sanyi yana ratsa ta.
Addu'a ta din ga yi, a kan Ubangiji Allah ya rufa mata asiri, ya kawo musu Ιauki, ya shiga tsakaninsu da su Ζaisar.
"Ma vie" ta ji ya yi magana.
"Na'am Sayyid" Sai kuma ya yi shiru, bai sake cewa komai ba. Yara suka firfito suka tatstsaya bayan ganin mota ta tsaya a Ζofar gidan Uwani.
Uwani da kanta ta fito tana tafa hannu, tana "Maraba da mutan birni. Ina yayar tawa take?" Nana ta buΙe motar ta fito tana murmushi.
Ummi ta sallami mai motar, Uwani ta ce "Ina mai gidan?"
Nana ta buΙe taxi Ιin, ya fito a hankali, kansa rufe da mayafi.
Uwani bakinta fal magana, amma ta haΙiye ta yi musu maraba, zuwa cikin gidan. Babban gida ne mai Ιauke da Ιangarori. Ta kai su sashen ta, aka yi shimfiΙa Sayyid ya zauna ya jingina da bango.
Abin da dai ba ya Ζauna, ya sake tararwa a garin, kallo. Ba ya son a zura masa ido, amma ya lura da yadda ake ta kallon sa.
Uwani ta karrama su da ruwan pure water, da abinci shinkafa da wake.
Ummi ta ce "Kafin cin abinci, Uwani a ina za su zauna, a gyara musu?"
Sai da Uwani ta sake yi wa Ummi ta tas, tamkar ita ce Baban, sannan ta kalli Nana ta ce "Yayata, kin ga cikin gidan nan, akwai Ιakuna, idan ma ba zaku zauna a nan ba, nan baya tafiyar babu nisa, akwai gida da Ιakuna biyu da tsakar gida. Babu kowa a gidan idan za ku zauna".
Nana ta ce "Gara su zauna a inda babu kowa"
Ummi ta ce "Maimakon ku zauna a cikin mutane, yadda ko wani abin ne, a taimaka muku"
Nana ta ce "Akwai dalili gara mu zauna inda babu kowan" Nana kuwa ta yi hakan ne, domin samun rufin asiri na larurar da suke fama daga ita har Sayyid. Ga uwa uba takura da Sayyid ba ya so.
Uwani ta saka yara, su ka je su ka share gidan tas, aka wanke.
Nana ta ce "Sayyid, bari mu je da Ummi, a gyara gidan, sai mu zo mu tafi da kai" Ya saka hannu ya riΖe nata, tare da girgiza mata kai alamar a'a.
"Mu tafi tare za ka iya tafiya?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
"To ta so" Ya yinΖura a hankali ya tashi tsaye.
Uwani ta ce "Nana, ku bar shi a nan mana, tun da ba shi da lafiya, ke ku je, ku gyara gidan"
Nana ta ce "Ai ba zai zauna ba, ya ce bin mu zai yi"
"Ikon Allah, ni da bita zai-zai, to Allah ya taimaka" Nana ta yi murmushi kawai, tare da jin nauyin abin da Sayyid Ιin ya yi.
Sauran yaran gidan Uwani, suka bi su Nana, su taya su shirya kaya. Wanda galibi Nana ba ta ma san su ba, saboda ba zuwa garin suke yi ba, domin ita rabonta da garin ma, har ta manta.
Gidan Ζasa ne tsura, da zunzurutun turΙaya Ζaki Ιaya ne gyararrre, sai aka yi masa siminti, da plasta, aka shafa farar Ζasa, da Ζofar langa-langa. Sai wani Ιakin kuma, si kuma ko rufi babu, sai banΙaki.
Duk lalacewar gidan su Nana ya fi nan nesa ba kusa ba, Ummi jarumta kawai take yi, zuciyarta a cunkushe babu daΙi, biyo bayan tuna cewar a nan Nana za ta rayu. Sai dai ta ga tsantsar tawakkalli a fuskar Nana. Su ka gyara Ιakin aka shimfiΙa leda, sai katifar su. Sai kuma tarin kayan su, na girki sai na sakawa a cikin bagco.
Uwani ta aiko musu da Abinci. Da la'asar bayan Ummi ta yi salla, ta ba wa Nana kuΙin barkononta da aka sayar, ta yi ta mata nasiha da kwantar mata da hankali, sannan ta yi musu sallama.
Ζan gidan Uwani ya Ιauke ta a kan babur, ya tafi da ita.
Nana ta Ζarasa gaban Sayyid, da ya zuba mata idanu tamkar bai taΙa ganinta ba.
Ta riΖo hannayen sa ta ce "Sayyid, duk da ban san wace irin rayuwa ka yi a baya ba. Amma wadda muka yi, mun yi ta ΖarΖashin kulawar su Habu, ba mu taΙa neman abu mun rasa ba. Amma Allah shi ne abin godiya. Wannan yanayin da muke ciki, ba zai dauwama ba in sha Allah. Ina fatan Allah ya baka lafiya, ya kuma baka haΖuri da juriyar a yanayin da muka tsinci kanmu a ciki".
Ya sanya tafukan hannayen sa biyu, a fuskarta laΙΙansa na rawa, amma magana ta gagara.
Ta girgiza masa kai tana murmushi, ta ce "Ruhinka yana cikin jikina, kar ka damu kanka lallai sai ka yi magana. A jikina ina jin abin da ka ke son faΙa" Ιan guntun murmushi ya yi, duk da yadda yake matuΖar son ya furta wani abu.
Da daddare Uwani ta aiko musu da tuwon dawa, da miyar karkashi, ta sha daddawar kalwa har Ιaurin yajin daddawa.
Ta san ba lallai ya iya ci ba, ta ba wa yaran da suka kawo kuΙi, ta ce su sayo mata buredi da shayi, na gurin masu sayarwa, da kuma maganin sauro, saboda azabar sauron da ke Ιakin.
Sai dai ya Ζi shan shayin, buredi kawai ya ci ya kwanta. Nana jikinta na rawa ta ci tuwon, saboda yadda ranta ya biya, amma Ζarshe amai har ta hancinta sai da ta yi shi.
Kan su kwanta, ta kunna maganin sauro, ta gyara masa shimfiΙa ya kwanta. Ita ma ta hau katifar ta tofa masa Addu'a, sannan ta kwanta a kusa da shi, tana yi masa fifita.
Ta daΙe idonta biyu, kafin bacci Ιarawo ya sace ta. Sai dai kamar a zahiri, kuma kamar a mafarki ta fara jin hayaniya a kanta. Ba ta gama tantance hayaniyar mece ce ba, ta ji wani abu na wucewa ta saman roofin Ιakin. Idan abin ya daki kwanon Ιakin da abin da yake takawa, tamkar kwanon zai buΙe ya faΙo musu a ka.
Ayshercool
08081012143
55
Wata irin yinΖurawa Nana ta yi, cikin azama da tashin hankali ta kifa a kan Sayyid, saboda kar abin da yake takun koma mene ne, ya faΙo masa a ka.
"Ma vie" ya furta da Ζyar can Ζasan maΖoshinsa. Ta Ιago ta fara laluben fuskarsa a cikin duhu.
"Sayyid, ba ka ji wani abu zai faΙo mana ba?"
"A'a"
Ta sake cewa maganar ta dawo "Maganar ta dawo?"
"Eh"
"To sannu" ta furta a hankali cikin tsoro, ta mayar da kanta kan Ζirjinsa a tsorace. Sai dai kamar dole, ta Ζarfin tsiya, wani baccin ya sake awon gaba da ita, tana cijewa da ΖoΖarin hana idonta sake yin bacci, amma abu ya ci tura, baccin ya kuma awon gaba da ita.
Ganinta ta yi a tsaye a tsakiyar Ιakin, itakaΙai babu Sayyid. Ana ta cigaba da hayaniyar da ba ta gane me ake faΙa. Ta din ga waige-waige tana tunanin ina ya shiga haka? Sai dai ba ta gama tunanin ba ta ji muryoyi daban-daban suna faΙin "Lale da manyan baΖin garin Buda. Barka da zuwa." Sai kuma ta ji ana dariya tare da ci gaba da hayaniya.
Idonsa biyu, yana jin yadda ta yi wa hannayensa wata irin muguwar damΖa, ta nutsa faratanta a jikin fatarsa, dan tuni ya karaya jini ne yake fita daga fatar tasa. Ta din ga juya kanta a kan Ζirjinsa tana kuka tana faΙin "A'a, mu ba baΖin ku ba ne ba, ba gurinku muka zo ba, mu ba baΖinku ba ne" jin ta fara Ιaga murya, ya sanya ya murginata gefensa, ya zame hular kanta yana shafa gashinta a hankali, tare da hura mata iskar bakinsa a kunnenta. Daga haka sai ta yi shiru, ta ci gaba da bacci.
****
Barira sai da ta sha jini leda biyu a Asibiti da allurai da magunguna, amma tana komawa gida, abu ya Ζara rikicewa. Domin kuwa babu damar ta sanya haΖarΖarinta a Ζasa ta fara bacci, wannan jibgegiyar magen za ta bayyana, su hau kokowa da ita. Duk sai magen ta yayyage mata fuska da jikinta. Idan ta tashi sai ta ji jikinta na yi mata wani irin zugi da raΙaΙi.
Ta cewa mijinta ita fa ba za ta koma wannan gidan ba. Ya sanar mata an tashi su Nana, daga su sai su Sajida a gidan kamar da, amma ta hau kujerar naΖi ta ce gidan ne ba za ta koma ba. Shi kuma ya ce sai dai ta yi ta zama a gidansu, dan ba shi da kuΙin kama wani gurin.
Shukura ce tare da Hajiya Amina, suke hira. Ta je yi mata sannu da zuwa dawowar da ta yi daga umara. Alhaji Zailani ya yi sallama ya shigo falon.
"Daddy sannu da zuwa"
Ya Ζare mata kallo ya ce "Yauwwa, mara tawakalli da ba ta san Ζaddara ba" Ta yi shiru tare da sunkuyar da kai. Duk irin kashedin da nake yi miki, da rarrashin da na yi miki, ba ki ji ba abin har ya kai ki dizga bawan Allah nan, a gaban mutane kina cewa yana kashe mutane, idan ya yi Ζarar ki kina da shaida a kan haka?"
Ta yi shiru ta sunkuyar da kai. "Tambayarki nake yi" Ta girgiza kai alamar a'a.
"Amma ki ke wannan iΖirarin, maimakon ki mayar da hankali a kan fatan Allah ya raya na gabanki, ya ba ki wani. Ba ki kyauta ba" Hajjya Amina ta yi ta kallon Shukura ko za ta ba shi haΖuri, amma ta yi mursisi.
Ko da ya shiga Ιakinsa, babbar rigarsa ya cire saboda azabar gumin da yake yi. Dan tun da Doctor Sharif ya gaya masa ga yadda suka yi da Shukura hankalinsa ya yi mummunan tashi. Ya kuma sake jaddada wa Sharif, muddin wani abu ya fita to babu hannunsa a ciki. Kuma likitan ya yi masa bayanin process Ιin da ya bi, abu ne mai wahala a gano. Ya yakice gumi ya nemi guri ya zauna.
Hajiya Amina ta ce "Me yasa ba ki ba shi haΖuri ba, kina kallon yadda ya yi fushi?"
"Mummy, duk wannan abubuwan kamata ya yi a tsaya a saurare ni, a kuma fahimce ni. Da hankalina fa ta yaya zan din ga iΖirarin an kashe mini Ιa haka kurum. Mummy ranar da za a yi mini aiki, kina bacci cikin dare, na kasa bacci saboda damuwar da nake ciki, aka buΙe Ζofar Ιakin, aka zo aka kama hannuna aka laluba cannula, aka yi mini wata allura a cikin duhun nan. Tun da aka yi mini allurar nan. Na ji kaina ya fara juyawa, ina neman na fita hayyacina, duk iya ΖoΖarina na kasa, na ji jikina na Ζamewa kamar zan yi jijjiga. SaΙanin da da idan za a yi mini allura cikin dare, za a ΖwanΖwasa Ιakin, sai kin tashi kin ce a shigo tukuna, a kunna ftila a yi mini"
Mummy ta Ιan yi shiru, cike da mamakin me yasa tuntuni ba ta faΙa ba, amma domin kawo Ζarshen maganar, sai kawai ta kawo gigin ciwo ne ya sanya ta ga haka a lokacin. Dan haka ta ce "Duk da haka wannan ma ba hujja ba ce, ke da ki ke fama da ciwo ina za ki tantance wani abu ma. Dan Allah ki bar zancen nan"
Shukura ta yi murmushi ta ce "Shikenan, na bar shi"
Sai kuma ta sake cewa "Mummy, Nana shiru, ni yakamata ki kwatanta mini gidan da suke na kai mata Haidar"
"Gidan Alhaji Garba giwa ne fa, kuma fafur babanku ya hana ni zuwa ban san dalili ba" Dummm! Ζirjin Shukura ya buga, ta ce "Saboda ne ya hana ki zuwan?"
"Ban san dalili ba, za ki je ne? Sabon gidansa nan Kano"
Shukura ta ce "Wace matar ce a gidan?"
"Halima ce, uwar gidan sa"
Shukura ta girgiza kai ta ce "Ba zani ba, gidansu tsohuwar matar Sagir ce"
Mummy ta waro ido ta ce "Ke haba? Dama 'yar Halima ce matar Sagir Ιin?"
"Eh mana"
"Ikon Allah, da na ce wa Daddy, ya taimaka musu, a samo wa mijin Nana, gurin da zai yi gadi, su samu su zauna, shi ne aka samo gidan"
Shukura ta ce "wai canza masu gadi ku ka yi ne?"
"Ina fa, ina nan cikin gida, daga baya ma Yusuf yake gaya mini. Wai zuwa aka yi da motoci da alama daga Ζasar su ne ma, motocin duk rubutun fransanci aka kwashe su kaf, kuma babu wanda aka yi wa bayanin me yasa"
"Ikon Allah, kuma ba laifi suka yi ba?"
"To ina zan sani, ina nan cikin gida?" Suka ci gaba da tattaunawa da jajanta lamarin. Har wayar Nana suka jarraba kira, su ji ko ita nata mijin yana nan, ba a kama shi ba amma wayarta ba ta shiga sam.
****
Da safe Nana ta tashi, ta fara alwala sannan ta zuba wa Sayyid ruwan da yara suka Ιebo musu jiya, dan gidan babu ruwa. Ya yi alwala a Ζofar Ιakin, sannan suka koma ciki ya yi salla. Sai dai bai ga alamun ta san abin da ta yi cikin daren jiya ba.
Ζarfe tara da rabi, Uwani ta aiko yara da kunu da 'yar tsala aka kawo wa su Nana.
'yar aiken ta ce "Uwani ta ce idan kin gama karayawa, wai ki je"
Nana ta ce "To, zan zo a ce mata mun gode sosai da sosai, Allah ya biya ta"
Ta koma ta zauna a gaban Sayyid ta ce "Sayyid, ka ga kunu ne da 'yar tsala za ka iya ci, ko na nemo maka wani abin?" Ya girgiza kai.
"To za ka iya cin wannan Ιin?" Ya gyaΙa mata kai.
Kunun tsamiya ne, na daka ba niΖa ba, ya sha kayan Ζamshi, sai dai babu suga ko kaΙan a ciki, ga tsamiyar nan cau har ka.
Ζuli-Ζulin 'yar tsalan, ya sha barkono, ta zuba masa a kofi ta ba shi. Ya saka hannu ya karΙa.
Tun da ya yi kurΙa Ιaya, ya yi shiru. Nana ta ce "Za ka iya sha kuwa?" Ya jinjina kai ya ci gaba da sha, saboda Nana.
Ya haΙa da 'yar tsalan nan, duk da ba son Abincin yake yi ba.
"Sayyid, idan ba zaka iya cin Abincin nan ba, ka bari na nemo maka wani"
Ya Ιaga kai ya kalle ta, sai dai ba baki, dan haka ya harare ta, ya ci gaba da cin abincin.
Ta yi murmushi ta ce "Ni ka ke harara ko, aishikenan"
Ya gama karyawa, ta saka Ιankwalinta, ta goge masa bakinsa da hannunsa. Ta ce "Bari na je kiran da Uwani take yi mini, daga nan na saka a raka ni, na Ιan yi mana sayayya, dan na san dole za ta daina bamu Abinci yau da gobe sai Allah"
Bai ba ta amsa ba, ya jingina da bango, saboda yadda yake jin daΙin hakan, yana lumshe ido.
"In je?" Ya yi mata shiru, kuma yaΖi yi mata wata alamar, da za ta gane ya amince ko a'a.
Cikin shagwaΙa ta ce "Sayyid" ya kawar da kansa gefe, ya Ζi buΙe ido.
"Duk da maganar nan Ιaukewa take yi, amma dai tun asalinka miskili ne, ina ta magana ka Ζi kula ni, ni ce fa rayuwartaka guda ka ke wa haka?"
Murmushi ya yi, tare da saka hannunsa a cikinta, yana shafawa a hankali.
"Wai ba za ka kalle ni ba?" Ta yi maganar tana juyo da fuskarsa. Ya Ζara rintse idanunsa, wai ba zai kalle ta ba. Nana ta din ga dariya.
Ya ja jikinsa a hankali, ya kwanta a kan cinyarta, ya zuba wa cikinta ido, tamkar zai gano abin da yake cikin.
"Idan na haihu na ga yadda za a yi, da kai da jaririn wa zai bar wa wani cinyar nan" Ta yi maganar tana shafa gashin sa.
*****
Hajiya Sa'a ce take cin abinci, tana kallon Jamila, da take ta cakala kaΙan-kaΙan.
"Jamila ya ne? Ki saki jiki ki ci abinci mana" Jamila ta jinjina kai ba tare da ta ce komai ba.
"Ko dai haryanzu abin da ya faru Ιin ne yake damun ki? Tun wuri ki ajiye wannan abin, ki ci gaba da rayuwar ki cikin kwanciyar hankali. Ζan Ζaramin abu ne fa, ranar da aka ce ki bayar da jini kuma ya zaki yi? Ki na gani Safiyya ta tafi Dubai ma sarin kaya, kuma duk harka ce ta Ζungiya ta Ιaukakata haka. Har gara ke ma da ba ki da aure, Safiyya da aurenta, amma kalli yadda ta kama Ζasa, mijin ma ita yake yi wa biyayya, ki saki jikinki dan Allah ki daina wannan damuwar.
Ki Ζarasa cin abincin, Talatu ta gyara gidan, idan an zo ana son kaya, kin san gurin da suke, zan je sake duba Fatuhu ne, daga nan na je a gyara mini kaina"
"To Mummy a dawo lafiya"
"Yauwwa Daughter Allah ya sa"
Ta gama abin da take yi ta fita, bayan fitar ta, Jamila ta tashi ta nufi harabar gidan, tana kallon flowers Ιin da aka Ζawata harabar da su. Jibga-jibgan motocin Hajiya Sa'a uku na hawa. Ga na Ιanta Abba biyu. Iya harabar gidan abar burgewa ce, ta yadda duk mai rai zai yi fatan ya samu wannan wadatar. Sai dai kash, hanyar da aka bi gurin tara dukiyar, duk wanda ya ji muddin yana da imani, sai ya gudu da Ζafafuwansa.
Ji ta yi kamar wani abu yana bin wuyanta, ta juya a hankali ta ga Abba ne a tsaye, yana saka abin fulawa a wuya.
Ta yi guntun murmushi ta ce "Yaya Abba"
"Na'am Ζanwar Abba. Ya na ganki nan lafiya dai ko?"
"Lafiya Ζalau, ba ka fita ba?"
"Yau ba zan fita ba, ba na jin daΙi ne gaba Ιaya, dan da zazzaΙi ma na kwana wallahi"
Cikin tausayawa ta ce "Kash, sannu Allah ya ba ka lafiya. Ka je Asibiti mana"
Abba ya Ιan numfasa ya ce "Na sha magani already, dan haka ba sai na je ba, zo mu je mu zauna ki yi mini hira, na san zazzaΙin zai sauka gaba Ιaya" Dariya ta Ιan yi ta ce "Ai ni ban iya hira ba"
"Ba wani nan, amma ki na yi da Mummy ai, gaskiya mu je sai kin yi mini" Tana dariya ya wuce gaba ta bi bayan sa. Sanyin halin Abba ya fara tasiri a zuciyar Jamila.
*****
Alhaji Fatuhu na zaune, Hajiya Suwaiba ta gama gyara jikinsa, fuskarsa Ιauke da damuwa, ya kalli uwar 'ya'yan nasa ya ce "Haryanzu Fadilan ba ta haihu ba?" Ta taΙe baki ta ce "Tana can ba ta haihun ba tukuna."
"Allah ya sauke ta lafiya" ta yi shiru ba ta amsa ba.
"Yakamata a sallame ni na koma gida haka, na gaji da zaman Asibitin nan gaba Ιaya"
A hasale ta ce "To mu koma gida mu yi yaya ne? Nan Ιin ba dai magani ake baka ba ana kula da kai, komai sai ka nuna kai ba a kyauta maka ba, ba a iya ba haba dan Allah"
Jiki a sanyaye ya ce "Yi haΖuri, Allah ya baki haΖuri" daga haka ya sunkuyar da kansa.
Sai kuma jikinta ya yi sanyi, ta zauna a kusa da shi, tana tunanin ta yi magana. Ta ga yana share hawaye.
Cikin damuwa ta ce "Alhaji kuka ka ke yi? Dan Allah ka yi haΖuri raina ne a Ιace, amma dan Allah ka yi haΖuri"
Ya yi mata shiru, gaba Ιaya ta rikice ta rasa abin da za ta ce. Raudah ce ta turo Ζofa hannunta da towel ta ce "Daddy guess what?" Ta miΖa masa narkeken jaririn da Fadila ta haifa.
Hannunsa na karkarwa ya riΖe jaririn ya ce "Another Muhsin" ya yi maganar yana murmushi.
Ya din ga yi wa jaririn kiss, yana shafa shi kamar ba a taΙa yi masa haihuwa ba.
****
Fafur Sayyid ya hana Nana zuwa ko nan da can, har aka yi azahar.Uwani ta sake aiko musu da dambu, ta ce a cewa Nana ba za ta zo ba, sai ta zo da kanta.
Cikin damuwa ta ce "Sayyid dan Allah ka bari na je, na ji kiran me take yi mini" fafur ya sha kunu ya tsuke fuska.
Babu yadda Nana ta iya, ta zauna ta Ζi fita. Ta zazzage kayansu, tana Ζara gyara musu, ta fito da kayan wankin gashinsa, da turarrukansa da duk wata sai su Habu sun sayo sun kawo. Ta Ιaga kai ta ga ita yake kallo, ta Ιan yi murmushi ta haΙe su a guri Ιaya da combs Ιin sa na taje gashi.
Sai yamma bayan sallar la'asar, ta yayyafawa tsakar gidan ruwa, ta share shi.
Ta yi shimfiΙar tabarma a tsakar gidan, ta saka wa Sayyi fululluka ta kamo hannunsa zuwa waje.
Ya zauna, ta Ιaukko mayafin rawaninsa ta yafa masa a kansa.
Babu jimawa sai ga Uwani ta zo, tana faΙin "Tun da ba za ki zo ba, ni ga ni na zo da kaina"
Nana ta ce "Ba Ζin zuwa na yi ba Uwani, yanayin jikinsa ne sai a hankali, shi yasa ban fito ba"
"Koma dai mene ne gani na zo ai" Ta kalli Sayyid ta ce "Sannu ko" ya jinjina mata kawai.
"Dama kiran ki nake yi, na ji idan akwai wani abu da ku ke buΖata?"
"Eh, ina son yin sayayya ba mu da fitila sai ta waya, da kuma 'yan kayan buΖatu"
"To da kin sanar, ai da na saka yara sun raka ki, dama zan ce miki kuma idan an kwana biyu, yakamata ki zo a Ιan zagaya da ke cikin dangi, su san kina garin nan, tun da dama ba zuwa ku ke yi ba, dui ba sanin ku aka yi ba"
Nana ta jinjina kai ta ce "To in sha Allah"
"Wai ni Nana ina Mai jidda kuwa?"
"Tana can Bauchi inda take aure"
Uwani ta ce "Kuma tana zuwa?" Jiki a sanyaye Nana ta girgiza kai.
"Ai dama na san babu lallai ta zo, ko dan saboda baΖin halin Isa. Ai ya bamu mamaki. Ita ma tun da suka rabu ba ta sake zuwa garin nan ba. Kuma yakamata mu je na zagaya da ke, har inda danginta suke a nan"
Cikin mamaki ta kalli Uwani ta ce "Danginta kuma?"
"Ζwarai da gaske, tushen Maijidda garin Buda ne. Kakanninta 'yan nan garin ne, can wajen unguwar Wanzamai, Ζarewa ma a nan garin suka haΙu da babanku. Ai kakarta aka raina a Bauchi, aka haifi babarta da ita a can.
Har an saka mata rana, suka zo garin nan, ke ma Babanki ya zo gida, suka haΙu a dandali. Aka yi ta Ιauki ba daΙi suka Ζulla soyayya. Ga shi can garinsu an saka mata rana da wani, ina ga shi ne mijinta na yanzu da take aure. Asali tun kan ta auri babanku da shi aka fara saka mata rana. Kakarta ta ce sai an warware wancan baikon ta auri babanku, ko ba komai sa din ga zuwa gida a kai kai. Haka aka mayarwa da wancan kuΙinsa ta auri babanku.
Ya Babanku ya so ta sosai da sosai, kuma aka Ζulla auren nasu da tunanin hakan ya Ζara kawo zaman lafiya a tsakanin zuriyarmu da zuriyar wanzamai kin san a tarihin garin nan ba zaman lafiya ake ba.
Kuma dai cikin ikon Allah sun fara zamansu lafiya gwanin sha'awa, amma Allah ya Ζaddara rabuwar su."
Nana ta yi shiru tana tunanin, kamar ta san wani abu mai kama da wannan labarin da Uwani take ba ta, amma sam ta kasa tunawa. Gaba Ιaya hirar ta Uwani ta gundure ta, saboda ta san shi kansa Sayyid a takure yake, ba ya son mutane ko kaΙan, balle uwa uba dogon surutu. Ita kuwa Uwani tamkar an Ζona ta a ka ko gajiya ba ta yi. Babu wanda ya taΙa ba ta wannan labarin, sai yanzu babu wanda ya taΙa gaya mata cewar mahaifiyarsu tushenta a garin Buda yake, sai dai kamar ta san labarin da Uwanin ta bata.
"Ga wata 'yar rama na zo muku da ita, sai ku ci kafin Abincin dare ya sauka. Wai shi mijin naki kurma ne?"
"A'a ai kin ga ba shi da lafiya ne"
"Eh gaskiya ne, Allah ya ba shi lafiya, amma a ina ki ka samo Buzu haka? Ni wai anya ma labarin da Rabi ta din ga bayar wa ranar bikinki nan gaskiya ne? Abin dai da mamaki. Allah ya ba shi lafiya bari na tafi, dan Allah idan ki ka samu lokaci kya zo a je a gaggaisa.
"To in sha Allah zan zo"
"Yauwwa, zan din ga turo miki yara, idan da aike kya din ga ba su, duk 'yan uwanki ne, 'ya'yan 'yan uwa ne. Kuma ki kwantar da hankalinki duk abin da ku ke buΖata ku sanar mini, da yardar Allah ba zai gagara ba"
Nana ta ce "In sha Allah, mun gode sosai da sosai"
"Ba komai, ki yi haΖuri ki riΖe mijinki ki kula da shi, sai ki ga kaf ayyukan ki, Allah bai karΙa ba, silar wannan jinyar ta sa ki shiga aljanna, a yi ta haΖuri yayata"
Nana ta tashi ta raka ta, ta ce "In sha Allah"
Ta yi Ζasa da murya ta cewa Nana "Dan ubanki, ki din ga Ιoye mijinki, kar ki bari 'yan mata su din ga zuwa su na kallon sa." Uwani ita iya rage muryarta kenan, amma Sayyid na jin ta. Nana ta Ιaga kai suka yi ido huΙu, ya yi murmushi yana sunkuyar da kai.
*****
Alhaji Fatuhu, farin cikinsa ya kasa Ιuya, duk da halin rashin lafiya da yake ciki, idan aka zo duba shi, sai ya yashe haΖoransa da sukaΙai suka rage farare a jikinsa.
Alhaji Zailani ya Ζura wa jaririn ido, ya kalli Alhaji Fatuhu da yake ta yashe baki.
Hajiya Sa'a ta ce "Kai Fatuhu. Sai ka ce ba a taΙa yi maka haihuwa ba, ji yadda ka ke washe baki, kana fama da kan ka"
Hajiya Suwaiba ta kwaΙe baki ta ce "Abin da na gani kenan"
Alhaji Zailani ya ce "A'a ku bar shi ya yi, Ιan mutum fa, kyauta ce Allah ya ba shi, da duk Duniya babu mai ba shi. Ni ba gani ba 'ya'yan duk babu sai biyu ne suka tsaya." Ya yi maganar yana zuba wa jaririn ido, yana tuna na Shukura. Tun da yake harkar Ζungiya, bai taΙa bayar da jinin da ya tsaya masa ya kasa mantawa ba, sai na Shukura. Mussaman idan yana tuna irin baΖar wahalar da ta sha.
Ya kalli Fadila, da take Ιakin a zaune, ga jego tana yi, amma ta tare a Asibiti da Ιanyen jaririn da ko suna ba a yi ba.
Ya yi ajiyar zuciya ya ce "Wane sunan za ka saka masa?"
"Muhsin Ιina zan mayar" ya yi maganar muryarsa Ιauke da rauni.
Hajiya Sa'a ta ce "Wai an din ga saka Muhsin Ιin kenan?"
"Sunan mahaifin Fadila ne, shi za a mayar mu ci gaba da kiransa Muhsin, ni na yi mata alΖawari shi yasa. Na so Muhsin Ιina da ya rasu sosai da sosai. Na ji zafin rashin sa, sai dai ina tausayawa wannan Muhsin Ιin. Ya zo lokacin da mahaifinsa ba shi da komai, ba zan iya Ιaukar nauyinsa na kula da shi ba. WataΖila ma kafin ya yi wayon sani na na rasu. Ga shi ko hakika ba zan iya yi masa ba" ya yi maganar hawaye na zubowa daga idanunsa.
"Haba Fatuhu, ya haka? Dan dai Hakikar da za ayi wa jaririn nan, ka san ba za ta gagara ba, amma ya za ka zauna kana kuka kamar Ζaramin yaro, a gaban iyalinka da 'yan uwanka hakan bai kyautu ba ai".
Alhaji Fatuhu ya Ιago idanunsa da suka yi jawur ya ce "Zailani. Ka san me nake ji kuwa? Gidaje da motocin hawa nake da, ina kyautar maΖudan kuΙaΙe ba tare da na ji komai ba, da abu ya dame ni, zan sai ticket na tafi umara. Ina da shaguna dukiya Allah ya yarje mini, bayan gwagwarmaya da na sha ta rayuwa. Astagfirillah ba Ζarar Allah nake kawowa ba, ko rashin imani da Ζaddara ba, ina jinjina girman lamarin Ubangiji, kuma ina jin babu daΙi Ιa na na cikina, ba zan iya saya masa ko wando ba"
Fadila ta ce "Dan Allah Daddy ka yi haΖuri. Mu na murna sauΖi yana samuwa, ga shi ka na ta magana sosai da sosai, kukan nan karya mana zuciya yake yi. Kuma da ka yi mana a baya, yanzu kuma da Allah ya kawo jarrabawa shikenan sai a yi haΖuri"
Su na nan zaune, sai ga Ζanin Baban Fadila, ya zo duba Alhaji Fatuhu ya kuma jaririn Fadila, wanda shi ne waliyyin Fadila. Sai dai shi ma ya tsorata da ganin Alhaji Fatuhu.
"Alhaji haka jiki ya zama? Subhanallah Allah ya baka lafiya"
"Amin kawu, amma jiki ya yi kyau Alhamdillah, tun da ina ta magana"
"Haka ne, amma menene takamaiman abin da aka ce ya same ka ne?"
Fadila ta ce "Haryanzu ba a gano takamaiman mene ne ba, yau a ce Ζodarsa ta kumbura, gobe a ce ko cancer ce, an yi gwaji ba ita ba ce. An yi gwajin zuciya shi ma lafiya Ζalau"
Cikin damuwa ya ce "Amma Fatuhu ana haΙa maka da na addini kuwa? Ka san muna da ido ne ba na ganin gari ba. Mussaman ku da ku ke shahararrun mutane da Allah ya ba wa wadata. Yakamata a yi na sihiri da shaiΙanu"
Alhaji Zailani ya ce "A'a ga likitoci su na kula da shi, ya za a yi a ce kuma a kawo wani abu daban? Magungunan gargajiyar nan kashe mutane suke yi ai, tun da ba auna su ake yi ba".
Alhaji Fatuhu ma ya ce "A'a ba wannan ba ne, wa ya damu da ni da zai yi mini sihiri. Larura ce kawai kuma likitoci na kula da ni"
"Kai, kalle ni da kyau. Duk bokon ka, nima Ιan boko ne, kuma na san ilimin addini, amma sihiri da shaiΙanu gaskiya ne. Tun da aka yi Annabi Sallallahu alaihi Wasallam sihiri, duk duniya ban ga wanda ba za a yi wa ba.
Ciwo ya Ζi ci ya Ζi cinye wa ai akwai alamar tambaya, ga lalacewar dukiya lokaci guda. A dai tsananta addu'a. Ya gama bambaminsa ya fita. Alhaji Zailani ya din ga ziga Alhaji Fatuhu, tare da kushe magungunan gargajiya. Ba tare da jin nauyin Fadila da take gurin ba.
Ya gama soki burutsunsa, ya tashi ya yi musu sallama, tare da cewa zai aiko da abin hakika.
Har ya kusa Ζarasa wajen motarsa, ya waiwaya ya ga Hajiya Sa'a ta nufo shi, ya tsaya ta Ζarasa.
Ya ce "Ya dai?" Ya yi maganar yana kallonta.
"Zailani"
"Na'am
"An sauke Ιan uwana daga shugabancin 'yan kasuwa an Ιora ka, ka saka an dawo da shi Asibitin nan, ΖarΖashin kulawarka, an ce a yi masa maganin gargajiya ka haΖiΖance kana kushewa.
Kar ka kuskura na tarar da sanya hannunka, a cikin wannan abubuwan da suke faruwa da Ιan uwana"
Ya gyara tsayuwarsa ya yi murmushi ya ce "Babu sanya hannuna a ciki. Ina ΖoΖarin zama aboki mai halacci ne kawai.
Sannan ki daina mazewa kamar ke Ιin mai Ζaunarsa ce, bayan sadaukar da 'ya'yansa maza da ki ke yi"
"Duk da haka, munin abin da na yi bai kai wanda ka ke aikatawa ba, ka fi ni sanin kai da me da me ka sadaukar, dan haka ka kiyaye ni". Ta juya ta koma. Bin bayanta ya yi da kallo, ya ji wani abu ya tsirga masa, tabbas idan Hajiya Sa'a ta ci gaba da wannan gigin, zai Ιauki matakin da ya dace a kanta."
*****
Cikin bacci, take jin hayaniya a bayan Ιakin, tamkar ana cin kasuwa. Ga wata irin sukuwa da take ji a roofing Ιakin, tamkar ta dawakai.
Tun da ta farka sai juyi take yi, bacci ya gagari idanunta, ayatul kursiyyu ce ta zo bakinta ta din ga maimaitawa, har ta samu nutsuwa daga razanin da take ciki.
Ta ruge idanunta, sai dai a maimakon ta yi bacci, sai wata irin kewar Sayyid take addabar ta. Ta rasa dallin da ya sanya, ba ya kula ta yanzu. Duk da ba shi da lafiya tana yi masa wannan uzurin, amma duk da haka da ya kan yi attempting sai ya Ζyale ta, yanzu kuma gaba Ιaya ya daina yinΖurin aikata komai ma.
Wanda da idan ya sako ta gaba, har takura take yi.
Ta tashi zaune ta gyara maganin sauro, ta taka a hankali ta Ιaga labulen Ιakin, saboda zafi. Ta dawo ta Ιauki fitilar wayarta ta kunna. Ta haska shi ta ga idanunsa a lumshe, yana bacci. Ta zuba masa ido, ta fara tunanin ko ita ce mai matsala gaya mata ne bai yi ba, ko ma sharrin Ζaisar ne?.
Ta yi ajiyar zuciya, ta kashe fitilar, ta kwanta a gefen sa tana wasa da gashin Ζirjinsa. Zuwa na fuskarsa.
Ta sake matsawa a hankali, tana sumbatar leΙansa, tamkar mara gaskiya. Gaba Ιaya a tunaninta bacci yake yi, sai da ta ji ya sanya hannayen sa, ya zagaye ta, tare da ba ta damar sumbatar bakin nasa.
Nana za ta iya cewa, tun da Allah ya sa ta buΙi ido a duniya, ba ta taΙa jin kunya irin ta yau ba, cikin sauri ta fara ΖoΖarin rabuwa da jikinsa ta matsa, amma ya mirgina ya rungume ta gam a jikinsa yana numfashi a hankali.
Ayshercool
08081012143
56
Yana jin yadda jikinta yake tsuma, tamkar wadda aka kama tana aikata wani abin ashsha! Ko kuma wadda ake kaΙawa mazari.
Magana yake son yi mata, amma abu ya gagara, duk ΖoΖarin da ya yi amma abu ya ci tura.
Ya Ζara ΖanΖame ta tamkar wani zai Ζwace ta, ya din ga murza hannunta har ta fara jin zafin riΖon da ya yi mata. Yanayin ya Ζara ninka mata halin da take ciki, ta rintse idanunta.
A hankali ta ji yana hura mata iska a cikin kunnenta, tamkar yana zuba mata wani sindari, haka ta ji wani irin nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita.
Ζamshin nan ta ji yana ratsa hancinta, ta buΙe idonta a hankali, kamar yadda ta yi tsammani, a wannan Ιakin ta gan su. Ta hau waige-waige. Ta wata Ζofa ta ga ya fito, Ζugunsa Ιaure da wani abu kamar zani, ya zauna a kusa da ita yana kashe mata ido.
"Sayyid ka warke?"
"Eh mana"
"Ka daina jin duk abin da ka ke ji?" Ya jinjina kai yana murmushi. "To ka yi mini magana mana"
"Ma vieee" ya faΙa yana Ιan jan maganar yana kwanciya a gefen ta. "Har na ji daΙi da ka samu lafiya, Allah ya Ιorar maka da sauΖin nan Sayyid"
"Amin rayuwata, matso ki kwanta mu yi bacci"
Ta noΖe kafaΙa ta ce "A'a"ya saki murmushi yana kama hannunta. Duhu ne ya gauraye Ιakin. Dariya ta fara jin Sayyid Ιin yana yi mata cakulkuli. Ta kasance da shi cikin wani yanayi mai tsayawa a zukata.
Ba ta iya tantance a wani hali take, ta daina ganinta a Ιakin, sai a libraryn Ζaisar.
Ta tsaya tana kallon gurin, tana tunanin yaushe rabon da ta zo gurin nan.
Ζaisar ta hanga, a tsaye yana gyara litattafan sa.
"Ζaisar ka warke kenan?"
Yayi shiru yana goge wani littafi, ya gama ya ajiye littafin sannan ya ce "Eh, na warke. Waye ya ce ki je Ζauyen nan?"
"Ban gane waye ya ce na je ba? Zan kwana a titi ne? Ga mara lafiya ina da shi"
"Gaskiya ne, bai kamata ki kwana a titi ba. Wannan dalilin ya sanya tun a farkon auren nan, na din ga haska miki matsalolin da za ki iya fuskanta, amma gani ki ke yi kamar Ζarya nake yi, to yanzu sai ki san yadda za ki yi, ki rayu da ke da wannan lanjararren mijin naki, da duk larurar duniya ta Ζare a kansa".
A Ζule Nana ta ce "Larura Allah ne ya Ιora masa, kuma kun taka muhimmiyar rawa a larurarsa. Kuma ka daina ganin laifina. Zan tsallake shi ne a wannan yanayin da yake ciki, na bar shi? Mu bil adama mu na da bambanci da ku, mu na da tausayi da kuma nuna kulawa ga waΙanda muke Ζauna"
"A'a kar ki tsallake ki bar shi, amma ki yi Ιamara fiye da ta baya, garin Buda ki ka zo za ki zauna, ban sani ba ko kin fahimci abin da nake faΙa ko ba ki fahimta ba. Idan ma ba ki fahimta ba, za ki gane daga baya. Bil adama ku na tausayi da nuna kulawa ga wanda ku ke Ζauna, ku ke iya Ιaukar jinin makusantanku ku bayar, a yi muku tsafi ko? Da kyau matsala kuma ki sani, ba ki ga komai ba" Daga haka ya Ιace Ιat. Ta buΙe idonta a hankali.
Tana buΙe idonta, ta ji ana kaΙa kacakaura, da garaya a tsakar gidan su. Ana ta hayaniya tamkar ana cin kasuwa a tsakar gidan.
Sanyi ta fara ji yana ratsa ta, bugun zuciyarta ya Ζaru, fiye da da, waiwaya ta yi tana son ganin ta inda za ta ga Ζaisar, ko makamancin hakan amma ba ta ga kowa ba.
Wata irin guΙa ta ji an rangaΙa da wata irin murya, mai sauti, sai kuma aka ce "Yeeee barka da zuwa wakilin rafi, ku matsa ku bayar da hanya ga ango mairamu ya iso" ta ji wata murya na faΙa, ana ci gaba da shewa da kaΙe-kaΙen garaya.
"Ku kawo Nono da suga, a kirawo 'yar Mairo ga mijinta ya iso. Ga farin goro Ζwarya dubu biyu ta rafi ta ce a bawa mamman wakilin rafi, gaisuwar iyaye" sai kuma aka saka shewa. Ba yau Nana ta fara ire-iren wannan jiye-jiyen ba, amma ta tsorata da wannan sosai da sosai. Ta rirriΖe Sayyid, ga sanyin da take ji ya fara damunta.
Cas cas cas, ta fara jin sautin kaΙawar wani abu mai kama da abin ado na mata.
Ta kalli tsakar gidan ta hango wata irin zanΖaleliyar mata, mai tsawon gaske Ζafafuwanta duk sarΖoΖi, ta yi shigar Fulani, sai dai ita ma ba a iya ganin sawayenta tamkar a kan iska take tafiya. Ta Ιan Ζara buΙe idonta, ta ga rana ce tarwai a tsakar gidan, ga dandazon mutane ana ta hada-hada. Sai dai shigar mutanen irin na zamanin da ne can baya sosai, kamar dai taron wani abu ake yi.
Wata mata ta hango sanye da kayan saΖi farare tas, Ζugunta sanye da wuri, kanta babu Ιan kwali duk ta yi wa tulin gashinta adon wurin, hannunta riΖe da sandar dargaza, tana kaΙa ta tana juyi.
Wannan bafulatanar ce ta tsaya a bakin Ζofar Ιakin Nana ta ce "BaΖuwarmu, bikin girka ake yi, ko za ki taso ki ga yadda muke gudanar da al'adun bikin girka?" ta yi maganar tana zuro zanΖalelen hannunta cikin Ιakin Nana".
"La'ilahaillalah, Sayyid, Sayyid wayyo Baba" ta tashi a gigice, rirriΖe ta ya yi, ya janyo wayarta, ya haska ta. Fuskar sa cike da mamaki yake kallon ta, yanayin fuskarsa ke bayyanar da alamar tambaya.
"Sayyid wata mata ce, wata mata ce take ziro hannunta, tsoro nake ji, wasu mutane ne a tsakar gidan nan" ya haska Ιakin ta ga babu komai, haka tsakar gidan ma dare nesai hasken farin wata, babu komai. Sai a lokacin ta fahimci mafarki take yi. Ya ji jikinta ya yi sanyi Ζalau, amma bai ga Ζaisar a gurin ba, bai kuma ga wata alama da take nuna yana gurin ba.
Gaba Ιaya ta nemi ko addu'a Ιaya, ta rasa a cikin kanta. Ta kaΙa ta raya amma babu abin da ya zo da kanta. Tana so ta karΙi wayarta ta kunna karatun AlΖur'ani, amma ko ΖwaΖΖwaran motsi ba ta son yi, saboda tsoron da take ji.
Da Ζyar wani baccin ya Ζara sace ta.
Babu babban abin da ya ba shi mamaki, irin yadda da safe take komawa normal, babu ma alamar akwai wani abu da yake ba ta tsoro cikin daren.
Haka ta ci gaba da sabgoginta. Sai dai gaba Ιaya a kunyace take, ko idonsa ba ta iya kallo, saboda abin da ta aikata ya kama ta cikin dare. Shi ga tausayin kan su, ga kuma dariya ta ba shi.
*****
Baba yana zaune yana shan koko da Ζosai a tsakar gida, sai ga kiran wayar Uwani.
Ya kalli wayar tasa ya ce "Tofa! Wannan jarababbar tsohuwar ko me za ta ce mini, take kira na da safiyar nan oho.
Ya Ιaga kiran ya saka a kunnensa. Sai dai ba ya jin ta sosai saboda rashin network. Ba ta haΖura ba ta din ga kira har sai da ransa ya fara Ιaci.
"Uwani ko a haΖura da wayar ne, kin ga babu network ne"
"A'a ina jin ka yanzu. Amm dama kiran ka na yi, na tambaye ka ina Nana kuwa?"
"Nana, tana gidan mijinta"
"Gidan mijinta wanne?"
"Mijinta dai na aure"
Uwani ta ce "Eh a ina gidan yake?"
"Amm can wajen gidan Ummi ne"
"Rufe mini baki, mutumin banza da na wofi. Ai kwana uku kenan ina neman layinka, amma bana samu saboda garin nan bamu da natiyok ake cewa ko me?"
"Uwani wai me ya faru ne?"
"Ai ba za ka san meyafaru ba, tun da ka bar yarinya tana ragaita ita kaΙai ranta ga miji mai larura,an kore su daga gidan haya, ba su san ma inda za su je ba, kana zaune hankalinka kwance. Ai ko 'yar riΖo ce Nana ka duba lamarinta"
Ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba, ta wanke shi ta tas, ta Ζare masa zagi da cin mutunci, ta ce kuma za ta kira Yaya Atine ma, sai ta ci ubanta.
Ran Baba ya yi mummunan Ιaci, kenan Ummi da Nana haΙa kai suka yi, suka kai Ζararsa gurin Uwani. Ya kira Ummi ita ma ya fara sauke mata kwandon tijara. Ranta ya Ιaci ta ce "Ni fa Baba ban kai Ζarar ka gurin kowa ba, Uwani ce ta kira waya, mu na tsaka da alhinin halin da Nana ne ciki, na gaya mata komai, kuma ni na faΙa ba Nana ba. Shi ne ta ce Nana su koma Ζauye can gurin ta".
Sai kuma Baba ya yi sak. "Ζauye kuma? Ta yi me a Ζauye?"
"To Baba zaman nan Ιin ya Ζi, kai kuma ka Ζi taimakawa, babu yadda muka iya Nana tana Buda"
"Ke Ummi ki na ji na, duk yadda za ki yi, ki nemi kuΙin mota, ki je Buda ki taho mini da 'ya ta. Lallai ya sakar mini 'ya ku taho tare, ya je Allah ya ba shi lafiya"
"Baba ya sake ta, 'yan uwansa ma ba a sa inda suke ba, wa za ta bar wa shi a can?" Yana cikin bambami kuΙin wayar suka Ζare.
Dama Mama na tsaye tana jiran ya gama wayar, yana gamawa ta dube shi ta ce "Wato Nana ta kaso aurenta ta dawo ko? To wallahi ta dawo gidan nan ba ta da gurin zama, wai har ka manta irin zaman azabar da muka yi da yarinyar nan a cikin gidan nan? Babu bacci kullum bala'i da tashin hankalin iskokai, ba zai yiwu ba wallahi"
Sai dai kafin Baba ya ba ta amsa, suka ji Suwaiba ta ΖyaΖyace da wata irin dariya mara daΙin ji tana faΙin "Asma'u a Ζauyen Buda, tushiya masomar dawa, kowa ya bar gida gida ya bar shi" ta yi maganar tana ci gaba da ΖyaΖyata dariya kamar ba mace ba.
"Ke Suwaiba meye haka, wannan wace irin dariya ce? Ban hana ki irin wannan dariyar ba kamar ba mace ba?"
Suwaiba ta ce "Ina ruwan ki da dariyata"
Baba kawai ya gyaΙa kai, ya gyara hularsa ya fice ya bar gidan gaba Ιaya.
****
Rashin maganar nan ta Sayyid, ba Ζaramin damun Nana take yi ba, abin ya yi yawa sosai.
A wannan karon ta yi sa'a, ya bar ta ta je gurin Uwani, daga nan kuma ta je ta yo musu sayayya. Ta tafi ta bar shi da wayarta, domin ta Ιebe masa kewa.
*****
Alhaji Zailani ya saka sabon layin da ya sayo a cikin waya, ya kira lambar Nana. Sayyid yana kwance yana jin yadda wayar take ta vibrating, amma ya yi banza. Saboda ko ya Ιaga ba iya magana zai yi ba.
Jin mai kiran ba shi da niyyar daina kiran, ya sanya ya Ιauki wayar zai kashe. Sai dai ya fasa kawai ya Ιaga kiran ya kara a kunnensa.
"A tunanki dan kin yi blocking Ιin lambata, zai sanya na kasa cimma burina a kan ki ne? Yanzu hankalina ya dawo gare ki, na saka an kori mijinki daga gurin aiki. Kuma zan nemo ki duk inda ki ka shiga sai na cika burika a kanki" wani irin jiri Sayyid ya ji ya fara Ιibar sa.
"Ba za ki yi magana ba?" Alhaji Zailani ya yi maganar yana kallon wayarsa. Wani irin haske ya ga wayar tana yi, tana fafar fafar za ta Ιauke. Mamaki ya kama shi, dan wayar ba ta taΙa yin haka ba. Fitilun Ιakin suka Ιauke, duhu ya gauraye Ιakin nasa. Sai ya rikice ya tashi tsaye yana waige-waige.
"Karo na biyu, ka sake shigowa hanyata, duk da gargaΙin da na yi maka, cewar mallakina ce, ina sake yi maka gargaΙi, kafin na tona maka asiri." Alhaji Zailani ya toshe kunnensa, saboda wani irin sauti da yake ji mara daΙi, ga Ιakin yana ta jujjuya masa.
Can ya ji shiru ya daina jin sautin, ya buΙe idanunsa a hankali. Sai dai ya ga Shukura a tsaye a gabansa, jini yana bin Ζafafuwanta, ga wuΖa a hannunta, tsirara ta.
Ya miΖe cike da razani, ya fara ja da baya.
"Daddy ina jaririna? Ka bani jaririna Daddy" Ya ci gaba da ja da baya. Da gudu ta bi shi, da wuΖar tsirararta. Ya fita da gudu yana ihu.
"Alhaji lafiya kuwa? Anya hawan jinin nan bai fara taΙa maka ΖwaΖwalwa ba, ya ya zaka din ga ihu haka?" Hajiya Amina ta yi maganar cikin mamaki tana kallonsa. Ya kalli gurin ya gan shi a kan gado, a Ιakinsa. Yana son yi wa Hajiya Amina tambayoyi, amma abu ya gagara saboda tsabar razani da tashin hankalin da yake ciki.
AREWABOOKS
*****
Uwani ta din ga yawo da Nana a cikin Ζauyen nan, tana nuna ta a dangi, tana gaya musu 'yar gurin Isa ce. Dan galibi ba su santa ba.
Nana gaba Ιaya hankalinta yana kan Sayyid da ta baro a gida, shikaΙai tana gudun kar ta je yana buΖatar wani abin. Ganin gantalin ya yi yawa, ga duk inda suka je sai Uwani ta tsuguna ta surutu kamar babu gobe.
Tun Nana tana jurewa, har ta gaji ta ce "Uwani, na bar mara lafiya a gida, ko za mu je inda zan yi sayayyar, na koma kar na je yana buΖatar wani abin.
Uwani ta ce "Kuma fa haka ne, to mu je na raka ki. Na so ma sai ranar kasuwa za ki je sayayyar, an fi samun rahusa. Ai tun da Allah ya sa ki ka zo garin nan, za ki yi ta ganin 'yan uwa da dangi, za a yi ta zuwa duba mijin naki ma"
Ita dai Nana ta yi shiru, dan duk surutunta, Uwani sai da ta saka ta gaji, ga azabar tafiyar Ζafa da suka sha.
Ta rakata inda ta yo musu 'yan sayayyar kayan abinci, gaba Ιaya tsoron taΙa kuΙin take yi. Gani take yi kamar Ζarewa za su yi.
Uwani ta raka ta har gida, sannan ita ma ta zagaya, ta koma nata gidan.
Nana ta shiga Ιakin da Sallama, tana faΙin "Sayyid, ka ganni sai yanzu ko, ka yi haΖuri Uwani ce ta din ga ja na, Ζafafuwana kamar su karye" Sak dai ta yi shiru ganin wata irin kwanciya da ya yi a kife a kan cikinsa, hannunsa a lanΖwashe, kuma ba kamar mai ruf da ciki ba.
Ga shi a tsakiyar Ιakin, ba inda ta tafi ta bar shi ba.
Ta zube kayan ta nufe shi jikint a sanyaye, gabanta na bugawa saboda fargaba da tsoron ko mutuwa ya yi.
Aikuwa tana juya shi ta Ιan ja da baya a tsorace tana sauke numfashi.
Wayarta ta gani a ΖarΖashin inda ya kifa, idanunsa a kakkafe, babu baΖar Ζwayar idon, sai farar. Ga jikin zafi rauuu tamkar wuta.
Ajiyar zuciya ta yi cike da damuwa, ta matsa kusa da shi ta yi Bismillah ta fara rage masa kayan jikinsa. Ta Ιebo ruwa ta din ga shashshafa masa tana sake nanata Bismillah.
Ta je ta rufe Ζofar gidan, ta dawo ta cire rigar jikinta, ta kwanta a jikinsa, tana rintse idanunta saboda raΙaΙin da take ji a fatarta.
Wani irin nishi yake, tamkar zai yi gurnani, yana miΖa jikinsa yana Ζara sandarewa.
A hankali ta ji tamkar hankalinta yana gushewa, ita ba a farke be, kuma ita ba mai bacci ba. Ta Ιan Ιaga idonta, ta ga Ζaisar tsaye a jikin Ζofar Ιakin yana kallon su. Ta yi shiru ba ta yi motsi ba, kuma ba ta yi magana ba, fatanta Sayyid ya samu sassauci daga azabar raΙaΙin da yake ji.
"Ko dai ki bi a hankali, ko wannan Ιan tayin na cikinki ya yo waje saboda zafin jikinsa. Ko kuma Giyaz ya yi masa mummunar illa." Nana ta Ιaga kai ta kalli inda Ζaisar yake, jikinta ya yi mata wani irin nauyi, ba ta ko iya motsa Ιan yatsanta.
"Babu irin kashedin da ban yi miki ba tun da fari, ki ka yi burus da ni, gani ki ke kawai cutar da ke ne kaΙai abin da nake yi.
Amma tun da jimirnki taurin kai, wahala sai ranar da Allah ya yanke miki, tukuna ma." A hankali ta lumshe idanunta har ta daina jin muryar Ζaisar.
****
Cikin damuwa Maijidda take kallon Saude ta ce "Yaya Saude haryanzu lambar Nanan ba ta shiga ko? Gaba Ιaya na kasa nutsuwa duk ji nake hankalina a tashe".
Saude ta ce "Dan Allah ki daina damun kan ki, in sha Allah tana cikin Ζoshin lafiya, kin san sharrin wayoyin nan, da rashin network, amma zan ci gaba da kiran ta, da na same ta zan sanar miki, kuma zan sake zuwa har gida na haΙa ki da ita."
"To Allah ya sa dai lafiya, kin ga na yi, na yi, na kaΙa na raya, Baban su Walida ya Ζi ba ni wayata, tsawon wannan lokaci haka nake zaune babu waya. Kuma duk wasu dabaru da zan yi na samu dama na je Kano na samu na ga yaran nan, abu ya ci tura sai ka ce ba Muslimi ba, ba ya jin magiya ba ya jin rarrashi".
"A'a kul Maijidda, uban 'ya'yan naki ki ke cewa kamar ba musulmi ba, kar ki sake. Ki rabu da shi da halinsa. Duk da Nana tana cewa za ta zo ita da mijinta, idan ma ba su zo ba, ni zan sake komawa na gano miki ita in Allah ya yarda. Iliyasu kuma ki rabu da shi ku lallaΙa kar ki fusata shi ya yi wani abin da ba a fata"
Maijidda ta yi ajiyar zuciya, ta jinjina kai kawai, amma gaba Ιaya ba ta cikin nutsuwarta.
****
Abu kamar wasa, aka shafe kwanaki biyar, Sayyid yana cikin wannan yanayin, sai dai Nana ta juya shi, ta goge masa jikinsa, ta yi masa Ζanin wanka a Ιaki, ta shafa masa turare ta saka masa kaya.
Ga shi juya shi kawai aiki ne, saboda yadda ya yi mata nauyi, ga jikinta babu Ζwari saboda azabar laulayi. Juriyarta ce kawai ta sanya ba a gane mawuyacin halin da take ciki, dan ba ta taΙa yarda ta kwanta.
Ga shi jikinsa duk ya kumbura, mussaman Ζafafuwansa.
Tana zaune ta yi shiru tana kallonsa, kawai tamkar an yaye mata wani abu daga kanta, sarkin baka ya faΙo mata. Sai da ta Ιan zabura ta tafi tunanin ko yana wani hali yanzu?.
"Ko dai can zan kai ka Sayyid?" Ta yi maganar tana kallonsa.
"To ni da ban ma san a ina yake ba, ta yaya zan kai ka?"
"Kul mene ne sahihancin magungunan da yake bayarwa? Mene ne halacci ko haramcin abin da yake yi, da za ki je neman magani gurinsa?" Wata zuciyar ta gargaΙe ta.
Sai kuma ta yi shiru, tana tuna irin wahalhalun da ta sha, da faΙi tashin gurin masu magani, ita dai tana da yaΖinin har gurin bokaye da 'yan tsubbu an kai ta, domin a nema mata magani. Domin wasu Ζarara ayyukansu da abubuwan da suke faΙa, ne nuni da kaucewa hanyar gaskiya.
"Allah na tuba, Allah ya sanya ba wannan ne dalilan da ya sanya nake ta shan wannan wahalar ba. Allah ka yafe mini, ba da son raina aka din ga kai ni wasu guraren ba.
Allah ka bamu lafiya da ni da mijina, Ubangiji Allah ka yaye masa wannan larurar, ka dawo masa da tunaninsa. Allah ban yanke tsammanni da daga falalarka da ni'imamominka ba"
Ta juyo a hankali ta dubi gurin da yake, ta ga idanunsa sun dawo daidai yana kallon ta. A rikice ta ce "Sayyid"
"Ma vie"
Cikin tsananin murna ta ce "Alhamdillah, ka tashi?" Ya jinjina kai yana lumshe idanunsa da suka yi masa nauyi. Ya ja jikinsa ya tashi zaune da kyar. Sai dai jikin nan duk a kumbure,ga kuma haki da ya farfaΙo da shi. Haka yau ma ta taimaka masa ya yi wanka ya ci Abinci ya fara rama sallolinsa a zaune.
Kallonsa take yi cikin damuwa, yakamata a ce sun koma Asibiti. Amma kafin a nemo mota a saka shi, su yi sammako su koma Asibiti, aiki ne. Mussaman da babu wadattacen kuΙi a hannun ta.
A take ta tuna da maganin da sarkin baka yake haΙawa masu hawan jini, da wanda Ιarin jikinsu ya shanye a sakamakon hawan jini da matsalar zuciya.
Ba ta jira ya idar ba, ta zari hijjabi ta yi waje. Ta din ga tuhumar kanta da yadda aka yi tuntuni ba ta tuna ba, sai yanzu. Tun da su magunguna ne da yake haΙa s da saiwoyi ba wani surkullen ya yi ba.
Ta dawo ta tarar ya dawo bakin Ζofa ya zauna yana kallon hanya.
Tafiya mai nisa ta yi sosai da ta fita, ta samo Ιawon kwakwa da sassaΖen zogale, sai kuma farin zoΙo.
Ta hura wuta ta wanke su, duk ta zuba a tukunya ta zuba ruwa, ta kawo Ιan kanumfari ta zuba a ciki.
Sai da ta kammala sannan ta koma gurinsa, ta ce "Ka yi haΖuri, magunguna na je samo maka, na fita ka na salla"
"To na gode"
"Allah ya baka lafiya shugabana, Allah ya sanya ya wuce kamar ba a yi ba"
"Amin. Ke ma Allah ya baki lada, ya saka mini ke a aljanna. Ya sanya ki maΖwabci Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam a aljanna" waro ido ta yi ta gigice gaba Ιaya hawaye ya fara zirarowa daga idanunta ta ce "Sayyid ba ni da aikin da zai kai ni wannan matsayin. Amma ban san matsayinka a gurin Allah ba. Ban sani ba ko Allah ya karΙi addu'ar da ka yi mini. Amma a ce na maΖwabci Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam. Innalillahi wa Innalillahi raji'un Sayyid na rasa me zan ce. Baiwa ce mai tarin zunubai kuma mai tarin rauni. Amma Allah kai mai yawan rahama ne da falala, Allah ka amsa wannan addu'a da ya yi mini shi ma ka ba shi abin da ya roΖa mini"
Ya yi murmushi ya ce "Amin rayuwata"
"Sayyid, anya an taΙa yi mini addu'a da ta tsuma ni kamar wannan? Subhanallah, subhanallah. Na ji daΙi wallahi"
Shima idanunsa ne ya cika da hawayen, ya ci gaba da bin ta da idanunsa. Kawai sai Nana ta ji ta manta kaso mafi yawa na damuwarta. Da ta tuna Addu'ar da ya yi mata sai murmushi ya kasa barin fuskarta.
Maganinta ya daΙe yana dahuwa, ta sauke ta mayar da ruwan girki. Ta tsiyaya masa a kofi, ta je ta zauna a gaban sa.
"Sayyid ga magani na dafa maka, mu jarraba, bamu sani ba, ko Allah zai sanya a dace" ya kalli kofin ya kawar da kansa gefe, yana Ιata rai.
Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka sha, babu Ιaci ko bauri fa"
"Ba na son magungunan nan, babu yadda na iya ne nake shan na Asibitin ma, ni wahalar da ni suke yi"
"To ai wannan ba na Asibiti ne ba, dan Allah ka daure ka taimaka, ba dan ni ba"
Da Ζyar ya yarda ya karΙa, ya ΙanΙana ya ji babu Ιaci, sannan ya ci gaba da sha, sai ma ya ji Ιumin maganin ya yi masa daΙi.
Bayan ya shanye, ta dafa masa shayi kuma, ya Ιora dan duk wahalar ciwon da yake ciki, ba ya iya haΖura da shan shayi.
Nana ta dage da bawa Sayyid, wannan ruwan maganin, tana addu'ar Ubangiji Allah ya taimake su, ya sanya ya karΙe shi.
Cikin ikon Allah, sai kumburin da ya yi, ya fara sacewa a hankali, har yana iya cin Abinci sosai. Nana kamar ta zuba ruwa a Ζasa ta sha.
Nana ta din ga murna, ganin ana samun ci gaba a yanayin jikinsa. Har banΙaki yana iya zuwa, ba tare da ta kama shi ba, yana tafiya a hankali a hankali da kansa yana iya yi wa kansa Wasu abubuwan.
Yana zaune tsakar gida, yana shan shayi ta ce "Ashe maganin Sarkin baka yana yi"
Ya kalle ta, ta ce "Ka san Sarkin baka?" Ya Ιan yi shiru yana kallon ta.
"Ranar da aka kai ni, kai na an kai ka, zaku tafi lokacin, ni kuma a lokacin na ji na fita daga hayyacina. Kai mun fa daΙe muna haΙuwa da kai."
Ya yi murmushi ya ce "Ruhina ne ya addabe ki, sai da ki ka nemo ni, ki ka aure ni ki ka nutsu"
Ta Ιata fuska ta ce "Ba wani nan, kai ne ka din ga bi na dai, har ka aure ni".
Ya Ιan sake zuΖa shayin hannunsa ya ce "A'a. Har gidan da nake ki ka bi ni fa"
"Ni ba bin ka na yi ba, kuma ai kai ka ce a biya maka sadakin aurena"
Ya maze ya ce "Ai gani na yi kin liΖe mini, har cikin Ιakinmu na gadi ki ka bi ni, na ce kai yarinyar nan idan ban aureta ba, akwai matsala haka za ta yi ta bina saboda ruhinta da yake jikina. Kina ganina kuma ki ka rikice"
"Ni ba ina sane na shiga Ιakinku ba, Jummai ce ta ce na ajiye muku Abinci, kawai na ji ana kirana a cikin Ιakin, ban ma na san na shiga ba. Kuma ni da na shiga wannan tsohon na gani. Kuma ai kai ma idan ka ganni kallona ka ke yi"
"A'a faΙi gaskiya dai, ni ki ka leΖo ki gani, ranar ba ki ganni ba, sh... Kawai ya ga tana hawaye. A diririce ya ajiye kofin hannunsa ya ce "Mene ne?" Ta yi masa shiru.
"Laifi na yi miki? Wasa fa nake yi" ta yi masa shiru, tana matse Ζwalla. Ba wai wasan da yake yi mata ne ya sanya ta kuka ba. Tuna yadda aka yi auren abin da Baba ya din ga faΙa da wanda Mama ta din ga yamaΙiΙi da ita, abin ne kawai ya dawo mata.
Ji ta yi yana goge mata hawaye, fuskarsa Ιauke da damuwa, ya ce "Ba zan sake ba" KwaΙe baki ta yi cikin shagwaΙa, wasu hawayen na ziraro mata.
"Na ce na daina fa, ki bari Ζirjina ya fara nauyi" da sauri ta saka bayan hannunta, tana goge hawayen fuskarta.
"Yauwwa dama ina so mu yi wata magana, mai muhimmanci da ke"
Ta tattara hankalinta, gabanta na dukan uku-uku cike da wasi-wasin wace maganar zai yi da ita haka?.
Ayshercool
08081012143
57
Ya yi mata alama da hannunsa, a kan ta nutsu ta kwantar da hankalinta. Ta jinjina masa kai, duk da gabanta na ci gaba da faΙuwa.
"Amm na san kina haΖuri a kan abubuwan da suke faruwa, duk da kin ce mini ba kya so na din ga irin wannan maganganun, amma sun zama dole na yi. Ina Ζara yi miki godiya da nema miki yardar Allah, na san ba ni da abin da zan biya ki da shi a wannan Duniyar. Ke ce komai nawa da ki ka rage Asmy. Sannan Ιangaren abin da ya shafi auratayyarmu, shi ma na san...
Ta katse sh6ta hanyar cewa "Amm ni dai a bar wannan zancen, bari na je na Ιora wakena"
"A'a ki tsaya mu yi magana"
"A'a ba sai mun yi ba"
"To kar na sake jin kin bi dare ki na taΙa ni" Kamar ta yi tsuntuwa ta Ιace, saboda azabar kunya, ita a zatonta ma ya manta gaba Ιaya. Cikin azama ta miΖe ta Ιauki robar wakenta, ta nufi inda take girki. Tana tashi ya kashingiΙa yana dariya.
Nana tana ta fifita wuta, yana daga zaune yana kallonta. Wani irin abu ne yake yi masa yawo a jikinsa, a game da ita.
Yana jin zai iya yin komai, dan tabattar da ci gaba da zamanta mallakinsa, shikaΙai.
Juriyarta, sadaukarwa da kuma tsananin tausayinta, ya sanya yake jin ina ma yana da wani abu da zai iya kamanta faranta mata rai, kamar yadda take ta wannan Ιawainiyar da shi. Ya san in dai a wannan Duniyar ne ba shi da abin da zai biya ta. Duk da matsananciyar damuwar da ya kan shiga, da jin cewa ya zama silar nakasta rayuwarta, ta zama tana rayuwa ba tare da tunanin wani abu da take so ta cimma ba. Kullum tunaninta a kan sa ne kawai.
Tana Ιagowa suka haΙa ido, ta murguΙa masa baki, ta ci gaba da fifitar wutar gabanta.
Ya tako zuwa gaban murhun ya tsuguna.
"Dan Allah ka tashi, saboda numfashinka fa"
"Kawo na yanka miki salak Ιin"
"A'a kar ka yanke hannu"
Ya ce "Ki kawo zan iya" Ta tsuke fuska ta kalle shi ta ce "Saboda sauΖi ya samu, kana iya fitowa da kanka yanzu, shi ne za ka din ga damuna ko?"
Ya yi murmushi, ya zauna a gefe yana kallon ta, da ta Ιaga ido, sai su yi ido huΙu da shi, sai ya yi mata murmushi.
Su na cikin cin abinci, ya ce "Ki na kiran Ummi?"
"Ba na samun ta, ita ma ta kira ni wayar ba na ji. Uwani ta ce haka garin nan yake babu network, sai a yi kira fiye da sau goma ba ka samu mutum ba.
"Idan na Ζara jin sauΖi, zamu je mu gaishe ta, mu yi mata godiya"
Ta ce "Alhamdillah, lallai sauΖi ya samu."
Ya ce "Eh, ina jin hakan a jikina nima. Mu je waje na Ιan tattaka na ga gari"
Nana ta faΙaΙa murmushinta ta ce "Allah abin godiya, wallahi Sayyid da har na fara fitar da rai da kai, na karaya sosai wallahi" Cikin murna ta saka hijjabinta, suka fita. Su na tafe a hankali ta kalle shi ta ce "Gaskiya na yi mamaki, ashe da gaske magungunan sarkin Baka yana yi"
Ya tsuke fuska ya ce "Na gaji da jin zancen Sarkin Bakar nan"
Nana ma ta yamutsa fuska ta ce "Sayyid ka yi haΖuri, amma na yi farin cikin yadda maganin da na gani a gurinsa ya yi maka aiki. Ina yi masa fatan idan a kan daidai yake, Ubangiji Allah ya Ζarfefe shi ya dafa masa, ko dan saboda yadda yake taimakon mutane. Idan kuma a kan kuskure yake Ubangiji Allah ya ganar da shi, ya ba shi ikon tuba kafin lokaci ya Ζure masa."
Sayyid ya yi mata banza, suka ci gaba da takawa a hankali su na zagayawa.
Wani irin sanyi ne ya fara ratsa Nana, ganin Sayyid ya durfafi wata hanya, ta kuma kasa ce masa uffan, balle ta hana shi. Su na tunkarar gurin, Ζirjinta na bugawa da sauri da sauri.
Wata irin narkekiyar bishiyar kuka suka tarar a gurin mai ban tsoro. Yanayin yadda take Ιauke da wasu irin murΙaΙΙun rassa, da yadda murtuka-murtukan jijiyoyinta suka huda Ζasa suka mamaye gurin. Ga wani irin Ζaton kogo a jikinta, hakan ya nuna daΙewar da bishiyar ta yi da wanzuwa a gurin.
"Asma'u" ya kira sunanta kai tsaye. Ta kalle shi cikin matsanancin mamakin yadda ya kira sunanta na yanka kai tsaye.
"Ji nake yi kamar na san gurin nan"
Jiki a sanyaye Nana ta ce "Nima haka, amma ni dai na san ban taΙa zuwa gurin nan ba, amma ina jin kamar na san gurin, amma dai... Sai kuma ta yi shiru bayan da gurin ya gauraye da duhu aka yi wata irin walΖiyya, haske ya mamaye gurin. Tsohon nan ta gani a tsaye, riΖe da sandarsa ya zubo wa Nana idanunsa marasa kyan gani. Jikinta ne ya Ιau kyarma, ta Ζara rikicewa bayan ganin a hankali wasu halittu da take kyautata zaton ire-iren su Ζaisar ne su na bayyana a bayansa.
Tsohon ya kalle ta, ya buΙe baki ya fara magana. "Ina sake yi miki barka da zuwa, garin da kakanin kakaninki su ka durΖusa suka haifo matsalar da har abada ba za ta daina bibiyar zuriyar su ba. Zan ci gaba da azabtar da rayuwarki, za ki ci gaba da biyan bashin nan, ko bayan ranki, muddin aka ci gaba da samun haihuwar masu irin tauraronki."
Yana rufe bakinsa, Ιaya daga cikinsu da Nana take kyautata zaton jininsin mace ce, saboda yanayin wani irin tsohon mayafi da ta yafa a kanta. Ta tunkaro Nana gadan-gadan.
Tana zuwa matar, ta hankaΙa Nana Ζasa, sauran suka rufu a kan Nana, su na zira hannunsu a mararta, su na ciro gudan jini.
"Ya hayyu ya Ζayyum ya Allah. Allah ka kawo mini Ιauki, Sayyid, Sayyid, Sayyid ka tashi" Ta yi maganar tana jijjiga Sayyid da yake kwance a gefen ta yana bacci.
Ya ja jikinsa ya tashi ya ce "Ma viee lafiya kuwa?"
"Sayyid marata ciwo take yi. Sayyid marata. Sayyid babyna. Ba na son na rasa jaririna a wannan karon, Dan Allah ka taimake ni"
Cikin rashin fahimta ya ce "Meyafaru ne?"
"Marata ce take ciwo, Sayyid ba na son cikina ya zube, ina son jaririna Sayyid ciwo marata take yi sosai" Ta yi maganar tana zubar da hawaye. Ya saka hannunsa a mararta, ta saka hannayenta ya dafe hannunsa tamkar hakan ne zai hana cikin zubewa.
Ya ce "Ki yi Addu'a" Kawai ta jinjina kai, amma Addu'a kam, ko Ιaya ba ta zo kanta ba, dan ta manta komai daga cikin kanta.
Cikin rauni Nana ta ce "Sayyid fitsari nake ji, ya matse ni"
Ya ce "To mu je ki yi"
Ta girgiza kai ta ce "A'a ba na son na je na ga jini ya zubo, cikin ne zai zube"
Ya ce "A'a ba za ki gani ba" . Ta miΖe ya kama hannunta, ya haska fitila har banΙaki, su na zuwa a tsorace ta yi fitsarin, sai dai tana yi sai ga jini. Wani irin kuka ta fashewa da Sayyid. Ta miΖe jikinta yana rawa.
Ya rungume ta ya ce "Ki yi haΖuri, kin ga dare ne, ki daina kuka. Kuma idan za ki yi Ιari, jinin da ki ke zubarwa ya fi wannan kin manta?"
"A'a idan jini ya fara zuba, shikenan ciki zai zube"
Ya ce "A'a, ba haka ba ne, ai bai zuba da yawa ba" Ya lallaΙa ta da Ζyar, ta gyara jikinta, ta Ιauraye jikinta, da banΙakin su ka koma Ιaki.
Karatun Alkur'ani ya kunna a waya, ya ajiye a gefen katifar da suke kai, kamar yadda ya ga tana yi, a duk lokacin da su ka shiga yanayi na tsoro.
Suka kwanta yana Ιan shafa ta, cikin sigar rarrashi.
A hankali ta ce "Sayyid"
"Na'am"
"Da gaske mun fita Ιazu ko?"
"Eh mun fita"
"Mun je can bayan gari, har ka ce mini kamar ka san gurin?"
"Eh haka aka yi, mun je"
Ta sake cewa "To daga nan meyafaru?"
"FaΙuwa ki ka yi, na riΖe ki muka dawo gida. Tun da muka dawo kuma ki ke bacci"
Ta yi shiru ba ta sake cewa komai ba, ta Ζara lafewa a jikinsa cikin tsoro. Yau ma kwana suka yi, tana gane-gane da jin abubuwa daban-daban masu razanarwa.
Wannan bafulatanar matar ce, ta Ζara zuwa ta tsaya a saitin tagat Nana tana kiran ta, a kan lallai sai ta fito ta ga yadda suke gudanar da bikin girka. Nana ta Ζara rintse idanunta tare da ΖanΖame Sayyid.
Da safe ta tashi da wani irin nauyin jiki, ga sanyi da ta kasa daina ji. Ta duba ta ga ba ta kuma ganin jinin nan ba. Ta yi wanka ta rama sallolinta, sai dai Sayyid bai tashi ba. Da Ζyar ta samu ya yi alwala ya yi salla.
Ta gaishe shi, amma bai yi magana ba sai kallonta da yake yi. Hakan ya sanya ta fuskanci maganar ta Ιauke.
Ta tambaye shi za ta fita, amma bai ko Ιaga kai ya kalle ta ba. Ta saka hijjabi ta fita ta bi 'yan matan gidan Uwani gona roron gyaΙa a gona.
Allah ya taimake ta, ta samo da yawa ta zo tsakar gida ta baje ta domin ta sha iska.
Ta Ιora musu Abinci, ta kammala ta fara dafa masa maganinsa, kawai ta ga ya fito daga cikin Ιakin. A zaton ta, ko banΙaki zai shiga, ta tashi da nufin kai masa ruwa, kawai ta ga ya nufi fita waje.
Da sauri ta bi shi tana faΙin "Sayyid ina za ka je ne haka?" Ya yi mata shiru yana ΖoΖarin buΙe Ζofar. Ta riΖo hannunsa, amma ya waiwayo fuskarsa a Ιaura kamar bai taΙa dariya ba, saka hannu ya hankaΙe ta, ta faΙi a gurin, ya saka kai ya fice daga gidan. Da gudu ta shiga Ιaki, ta Ιaukko hijjabi, ko takalmi ba ta saka ba, ta bi bayan sa. Ga yamma ta yi liΖis, hanya babu kowa, ta ga ya nufi hanyar inda wannan bishiyar ta kuka take.
"Sayyid dan Allah, dan Allah kar ka koma gurin nan. Me za ka je ka yi?" Sai dai tamkar ba mara lafiya ba, saboda yadda yake sauri.
Sai da ta Ιan haΙa da gudu, Saboda saurin da yake yi, amma ta ji gefen mararta ya Ζulle. Ta daure ta cim masa.
Babu tsammani ta furta "Bismillah wa hifzan min kulli shaiΙanin marid." Aya ta bakwai cikin suratul saffat, kamar yadda Malam Auwal ya taΙa cewa ta yawaita nanata ayar. Gaba Ιaya ta shafe a cikin kanta, sai da ta faΙo mata yanzu. Tana karanta ayar, ta riΖe hannunsa ya ja ya tsaya ya yi shiru ya sunkuyar da kai.
"Mu koma gida" ta yi maganar tana jan hannunsa, tamkar raΖumi da akala, ya bi ta suka koma gida. Allah ya taimake ta, babu wanda ya gan su har su ka isa gida. Ta rufe Ζofar.
Su ka shiga Ιaki, ta kunna fitila ta kalli Sayyid cikin damuwa ta ce "Sayyid me yasa ka fita? Me za ka je ka yi a wajen da?" Ya yi shiru ya sunkuyar da kansa Ζasa fuskarsa babu annuri a ciki.
Ba ta sake ce masa komai ba, ta fita banΙaki ta yi alwala, ta dawo ta yi salla, amma ta ga ba shi da niyyar tashi ya yi.
"Sayyid, ba ka yi salla ba fa" Nan ma bai kula ta ba, dan haka ba ta sake magana ba, ta zubo masa Abinci ta zo gaban sa ta ajiye. Ta tashi ta ninke hijjabinta, tana waiwayowa, ta ga ya kifar da Abincin ya tarwatse a tsakar Ιakin, yana wani irin huci.
"Sayyid wai meye haka ne? Idan ba ka cin abincin sai ka zubar mini a Ζasa?" Sai dai tana rufe baki, ya wulwula kwanon ya yi jifa da shi guri Ιaya. Ya miΖe ya fara fatali da kayan Ιakin. Take Nana ta fuskanci ba lafiya ba. Jiki a sanyaye ta rakuΙe tana kallon sa.
Tana tunanin yanzu kuma abin har ya kai ga haka? Ba ta yi yinΖurin hana shi ba, ya yi kaca-kaca da Ιakin, ya fita tsakar gida ya nemi guri ya kwanta a dandaryar Ζasa.
Inda ta yi wa Allah godiya ba su da maΖwabta, da kowa sai ya san abin da ya faru. Haka ta durΖusa ta hau aikin gyaran Ιakin, ta kintsa abin da za ta iya kintsawa. Ta dawo tsakar gida inda yake kwance. Ta durΖusa a kan sa, ta dafa shi ta ce "Tashi mu je ka kwanta a Ιaki, nan akwai sauro kuma Ζwari za su cije ka"
Da Ζyar ya tashi, suka koma Ιaki, ya nemi guri ya kwanta a Ζasa. Kawai Nana ta zauna ta zura masa ido, cikin matsananciyar damuwa, duba da yadda take maganin Ζaba amma kai na daΙa kumbura.
A haka dare ya tsala, ta gaji ta kwanta a gefen sa, zuciyarta fal da damuwa. Bacci na ΖoΖarin Ιaukar ta, ta ji tasowar guguwa ta buΙe idonta, ta gan su kwance a cikin sahara, ga yashin saharar na wani irin hanΖoro iska za ta mamaye su. Ta saka hannu ta rungume shi saboda guguwar saharar. Sautin tsohon nan ta ji yana wata irin dariya. Ji ta yi an hankaΙa ta, sai da ta wuntsula Ιakin gauraye da duhu, amma ta ga alamun Sayyid ne zaune a kan katifa shi ne ya hankaΙa ta. Ya tashi ya koma bakin Ζofa ya yi zamansa.
Da kyar ta sake lallaΙa shi, ya koma ya kwanta. Ita ba ta sake komawa bacci ba, ta yi alwala ta zauna tana tasbihi har aka yi sallar asuba. Sai dai fafur ya yi salla ya Ζi yi. Ya nemi guri ya zauna Ζyam yana kallon ta.
Ta dama masa kunu, ta soya fanke, ta zo Ιaki ta zauna a gaban sa. Ta ce "Ga kunu ka sha, amma dan Allah kar ka zubar Sayyid ka ji?" Ta yi maganar tana miΖa masa kofin kunun. Sai ya miΖo hannun hagu zai karΙa. Ta janye kofin ta ce "Hannun dama dai, wannan hannun za ka bani" Ta yi maganar tana nuna hannun damansa, amma bai miΖo mata ba, ya zura mata ido.
Ta kai hannu ta janyo hannun nasa, dan ta damΖa masa kofin kunun, amma ta ji hannun a Ζame Ζam. Ta sake ΖoΖarin janyowa, amma ta ji tamkar tana jan itace.
Ta kalli hannun sosai, sai ta ga shanyewa ya yi.
Gabanta ya yi wata irin mummunar faΙuwa, ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Sayyid me ya same ka haka? Me ya samu hannunka? Ya Allah!" Ta yi maganar tana kuma ΖoΖarin ganin ta miΖar da hannun nasa, amma hannun yana maΖale, kamar an tsotse shi.
Ya sunkuyar da kai ya yi shiru, fuskarsa Ιauke da damuwa. Ta aro jarumta, ta matsa daf da shi, ta Ιebo kunun ta kai bakinsa. Amma ya tsaya yana kallonta, bai buΙe bakinsa ba.
"BuΙe baninka na baka" Ta yi maganar tana ΖoΖarin danne hawayen da ke ΖoΖarin Ζwace mata.
A hankali ya buΙe bakin, sai ta ga shi ma bakin ya karkace, yawu na ΖoΖarin zubowa. Kawai ya rufe bakin hawaye ya fara gangarowa daga cikin idanunsa. Ta ajiye kofin kunun ta rasa abin yi. Kawai rungume shi, ta fashe da matsanancin kuka, sai da ta yi iya yin ta.
Sannan ta cika shi, ta share masa hawayensa.
Ta fara ΖoΖarin ba shi kunun, sai dai tana ba shi, ya haΙiye wani kuma ya zubo.
Ta na yi tana goge masa wanda yake zubowa, ta gama ba shi, ta kama hannunsa su ka je waje, ta taimaka masa ya yi alwala. Ya dawo ya rama sallolin da ta gaya masa ana bin sa. Sai dai ba magana ga hannu a maΖale, da ta kalle shi sai ta ji hawaye ya cika mata ido.
Ganin yana gyangyaΙi a zaune, ya sanya ta saka masa pillow ya kwanta, ta saka hijjabi ta fita.
Tafiya mai nisa ta yi, ta je ta samu wani chemist, bayan sun gaisa ta ce "Dan Allah malam, idan babu damuwa, Bp nake son mu je ka gwadawa mijina a gida"
Ya kalle ta ya ce "A ina ne?"
"Cikin Budu ne, nan unguwar maharba"
"TaΙ gaskiya da nisa gurin nan ba kaΙan ba, ba zan iya zuwa ba sai dai ki je ku zo tare a yi masa"
"Wallahi da zai yiwu, da ba zan zo na roΖe ka ba, yana kwance babu lafiya ka taimaka mini dan Allah"
Ya ce "Gaskiya kin san cajin zuwa gida ma ka yi wa mutum abu daban yake, sai dai idan za ki ba ni dubu biyu"
Nana ta ce "Eh na yarda mu je zan baka in sha Allah" Ya rufe chemist Ιin ya bi Nana.
Su na zuwa gidan, Nana ta shiga ta tarar da shi a zaune ya tashi, ta ce "Sayyid kar ka ga na fita ban gaya maka ba. Na je na samo wani ma'aikaci ne, ya zo ya duba jininka a gani, idan jinin ne ya hau ya sanya hannunka ya shanye, mu tafi Asibiti. Idan kuma ba shi ba ne, sai mu san abin yi." Bai ce komai ba, ta yi wa mai chemist magana, ya shigo ya gwada jininsa.
Ya gwada ya kalli Nana ya ce "Jininsa bai wani hau sosai ba, 140/90 ne" Ajiyar zuciya Nana ta yi. Ta ce "A ganinka wannan hawan zai iya sanya masa shanyewar hannu?.
Ya girgiza kai ya ce "Gaskiya ba na tunanin haka, amma ban tabattar ba tun da ni ba likita ba ne ba. Amma a shekarunaa bana tunanin jinin 140 zai shanye masa wata gaΙa a jikinsa, amma dai ku je Asibiti a Ζara bincikawa"
Nana ta ba shi kuΙin sa, ta yi tai masa godiya. Ta koma Ιaki ta zauna ta yi shiru, tana tunanin ko Uwani za ta tambaya, idan akwai wani mai magani, ta raka su, sai dai ta fasa saboda akwai sauran ΙurΙushin jahilci a tattare su, ba ta son surutu kuma tana tsoron a kai su gurin da ba shikenan ba.
****
Alhaji Fatuhu kuwa kamar yadda ya matsa, sai da aka sallame shi ya koma gida. Gidan nasa ma wani abokin kasuwancinsa ne ya saya, ya bar shi a ciki ya zauna ya bar masa aro.
Sagir yana kwance a kan gadonsa, yana kaΙa Ζafa ya Ζura wa screen Ιin wayarsa ido. Yusra ce zaune sanye da doguwar rigar material, kanta ko Ιan kwali babu, dogon gashin kanta ya sha gyara. Tana ta zuba masa surutu.
Har mamaki yake yi, yadda Yusra ta zama mai Ιan karen surutun tsiya, wanda da ba haka take ba.
"Ya ka yi shiru ne?" Ya wani lumshe ido ya ce "Ina jin ki ai".
"So talk, ka yi magana mana" ta yi maganar tana cika bakinta da guggurun hannunta.
"Ina ga zan shigo Abuja mu haΙu very soon in sha Allah" wata irin zabura ta yi ta ce "Are You serious, dan Allah da gaske?"
"Da gaske nake, zan zo na ganki, amma ki na ganin babu matsala a zuwan nawa? Kar a yi miki faΙa fa, ba zan ji daΙi hakan ba"
Yusra ta ce "Babu wata matsala, ba za a yi mini faΙa ba, ai ba na tare da su Mami, ina gidan Anty Sumayya. Dan Allah ka zo"
Sagir ya yi murmushi ya ce "Kin yi missing Ιina ne?"
Ta gyaΙa masa kai tana murmushi.
"Shikenan, i miss you too, ban taΙa tunanin ma za ki neme ni ba, na za ta ki na jin haushina haryanzu, amma in sha Allah zan shigo, zan sanar miki lokacin da zan shigo na zo na ganki" ya yi maganar yana kashe mata ido.
Shukura ce ta turo Ζofar Ιakin ta shigo, a burkice ya kif wayar yana kallon ta. Ζarara yanayinsa ya nuna alamun rashin gaskiya, amma ta share shi, ta haye kan gadon ta ja bargo ta lulluΙe jikinta.
Ya matsa kusa da ita yana Ιan shafa ta ya ce "Sweetheart, ya na gan ki kamar a fusace ne? Lafiya dai ko?"
"Lafiya Ζalau" ta amsa a taΖaice. Ζan shiru ya yi yana tunanin ko dai ji wayar da yake yi ne? Amma a yadda ya santa da azababben kishi, da zargi da ta ji sai ta yi masa magana. Sai dai ya bar abin a haka bai matsa mata da tambayoyi ba gudun kar su yi faΙa.
Tana ankare da take-taken Sagir, na rashin gaskiya. Sai dai ita yanzu ba wannan ne a gabanta ba, bin diddigin mutuwar Ιanta take son yi. Dan haryanzu zuciyarta ta kasa amincewa da natural mutuwa ya yi. Domin haryanzu tana mafarke-mafarke marasa daΙi da mahaifinta da kuma Doctor Sharif.
****
Aka shiga sati na biyu, Sayyid yana cikin wannan yanayi na rashin lafiya, kuma hannunsa bai saki ba, yana nan a maΖale.
Ga hauka da yake yi tuburan wasu lokutan, wasu lokutan idan ya burkice sai ya shaΖe ta, ko ya hankaΙe ta Ζasa, sai dai ta yi ΖoΖarin kare cikinta. Ko kuma Ya ya ta watsi da duk abin da ya ci karo da shi, a Ιaki ko a tsakar gida. Wasu lokutan ma katangar Ιakin yake duka da kansa. Ya Ζi cin abinci ya Ζi shan magani, ba salla, komai sai dai ta yi masa cikin rarrashi da ban haΖuri. Tun tana jin tsoron ya yi mata wani abin, har ta daina ji, ta zuba wa sarautar Allah ido.
Sannu a hankali ta rage yawan amai, sai dai zazzaΙi da rashin son cin abinci da take yi, hakan ya sanya ta tabattar da cikin jikinta bai fita ba haryanzu. Sai dai ba ma ta cikin nutsuwar da za ta nemi inda Asibiti yake ta je, ta tabattar da halin da suke ciki ita da jaririn saboda tashin hankalin da take ciki.
Yanayin yadda uwani ta lura kamar Nana na Ιoye wani abu, ya sanya ta daina zuwa gidan,ta rage aika yara ma. Sai dai lokaci lokaci, ta kan aika mata da Abinci.
Haka sauran 'yan uwansu na garin ma, su kan aiko mata da sha tara ta arziki saboda su na tausayin Nana, sun san mijinta a kwance yake babu lafiya.
Yawon roro a gona kuwa yanzu Nana ta Ζware, ranar kasuwa ta je ta sayar da abin ta.
Kasancewar ranar Asbar kasuwar garin take ci, sai ta tashi ta yi fanke da sassafe, jikan Uwani Haladu, ya kai mata kasuwa. Ko ta dafa masa zoΙo ta ΖuΖΖula ya tafi da shi.
Idan ta gama komai kuma, ta bi yara gona roro.
Dare ya tsala, amma Nana tana zaune tunkurkur, wuni Sayyid ya yi yana wani irin nishi, ga wannan azababben zafin jiki da yake fama da dhi.
Tana zaune tana tunani, tana jin yadda mararta take motsi, cikin jikinta yake motsawa.
Ba ta da sauran wanda za ta kai kukanta bayan Ubangiji. Ta fara tunanin ΖoΖarin tara musu kuΙin mota, su tafi Nijar, neman danginsa, sai dai idan sun je Nijar Ιin ina za su nufa? Babu tsammani ta ji Sayyid Ιin ya laluba cinyarta, ya kwantar da kansa.
Ta shafa gashinsa ta ce "Sayyid" bai amsa ba, sai dai ya riΖe hannunta. Hakan ya tabattar mata da ya dawo hayyacinsa ne. Haka ta tashi a cikin daren ta tsiyayo ruwan zafi, ta ba shi shayi ta yi masa wanka suka kwanta, ta lulluΙe su da bargo.
SheshsheΖar kukansa ta ji, duk da yadda ta san ya daΙe yana dauriya, da son Ιoye gazawarsa, sai dai ta ga hakan a idanunsa.
"Sayyid idan ka na kuka, ni kuma ya zan yi kenan? Dan Allah ka daina" ta yi maganar muryarta na rawa. Ta din ga shafa bayansa a hankali, har ya yi shiru, bacci ya Ιauke shi.
Sai dai tun daga wannan, haka aka sake shafe kwanaki biyu, bai sha ko ruwa ba. Dama rashin maganarsa ya daina damunta.
Ga shi yau abin ya tashi sosai, haukan yake yi da gaske. Ta rufe shi a gidan, ta je ta samo gasara a gidan Uwani, ta dawo ta dama masa kunu. Ta nufi Ιakin cike da fargaba tare da fatan ya samu ya sha ko kaΙan ne.
Sai dai ta ji wata irin guguwa ta taso mai Ζarfi.
Jin yadda guguwar ta taso da Ζarfinta, take fatali da duk abin da ta ci karo da shi a tsakar gida, ya sanya ta tashi da azama, ta fara ΖoΖarin rufe Ζofar katakon da take Ιakin. Sai dai tana danna Ζofar guguwar ma na danno Ζofar.
A take ta fara karanto "A'uzubillah, Allahumma inni as'aluka khairiha wa a'uzubika min sharriha. Allahumma inni as'aluka khairiha wa khairi ma fihi, wa khairi ma ursulat bihi, wa a'uzubika min sharriha wa sharri ma fiha, wa sharri ma urisilat biha" take ta ji nauyin da Ζofar ta yi ya ragu, ta samu ta rufe ta, ta juya da sauri ta nufin gurin da yake.
Da fari yana zaune a guri Ιaya ne, amma yanzu Jifa yake da kayan Ιakin da hannu Ιaya, da sauri ta fara bi tana tattarewa, cike da damuwa.
Cikin siriryar muryarta ta ce "Sayyid za ka ji wa kan ka ciwo, ka saurara ka saurari muryar matarka, ni ce a gare ka, ni ce fa, Husnan ka ce fa" Ta Ζarasa maganar a raunane, duk yadda take ΖoΖarin tare shi ta kasa, domin ta gama firgita da lamarinsa. Tun safe take fama da shi, ya Ζi cin komai, kuma ta kasa sarrafa shi duk rarrashin da ta yi a banza.
Cikin matsananciyar damuwa, hawaye na bin kuncinta ta ce "Ubangiji ka dubi mijin Nana, ka cire masa zafi da raΙaΙin da yake ji, ka saita masa tunani da ΖwaΖwalwarsa, ya yi rayuwa mai cike da nutsuwa da farin ciki irin na sauran mutane" sai kuma ya tsaya cak, ya juyo yana kallonta.
Ta Ζarasa gurinsa, ba tare da fargaba ba ta riΖo hannunsa cikin nata jikinsa zafi sosai. Ta kalli cikin idanunsa sai taga yana birkice mata yana rikiΙewa kamar ba Sayyid Ιin ta ba, idanunsa har wani hayaΖi yake fitarwa, gaba Ιaya kaminsa sun sauya.
Ta lallaΙa ta zaunar da shi, Ta yunΖura zata tashi, domin ta Ιaukko kununsa ta sake jarraba ba shi, ta ji ya cafko ta yana wani irin sambatu bakinsa na kumfa da dalalar da yawu, da alama magana yake son ya yi mata. Rashin Ζarfin jiki ya sanya ta faΙa jikinsa. Ya ΖanΖame ta sosai, saboda zafin da yake ji, ita kuma jikinta sanyi Ζalau. Ita ma jikinta ya Ιauki rawa, ta lafe a jikinsa ta kwantar da kanta a Ζirjinsa tsawon mintuna, jin ya Ιan nutsu jikinsa ya rage zafin ya sanya ta zare jikinta a hankali.
Ta Ιaukko kofin kunun da cokali, sai wani Ιan Ζaramin tsumma, ta zauna a gabansa ta Ιebo kunun a cokali ta kai bakinsa, sai dai ya tsaya yana bin ta da ido, kamar ya ga baΖuwar halitta, ta buΙe nata bakin, ya kalleta shi ma ya buΙe nasa.
Ta fara zuba kunun a bakinta ta haΙiye, sannan ta zuba masa a bakinsa shi ma. Ya haΙiye sai dai wani na biyo gefen bakinsa, bai haΙiye duka ba. Tana bashi tana goge masa wanda yake zubowa. Sai da ta tabattar ya Ζoshi, sannan ta goge masa bakinsa. Ta Ιauki kofin ta nufi Ζofa ta buΙe a hankali ta ga an daina iskar, ta fita da kofin ta ajiye, ta tattara abin da guguwar ta watsa sannan ta dawo Ιakin.
Jiki a sanyaye, ta zauna a gabansa tana Ζare wa kyakyawar fuskarsa kallo. Da Ζyar yake jan numfashi yana saukewa. Ta sanya hannayenta biyu, ta gyara masa gashinsa, da ya rufe masa gefen idonsa, ta saka idonta a cikin nasa, cikin rauni da karaya, idanunta na zubar da hawaye ta motsa bakinta, ta fara magana
"Sayyid, dan Allah ka yi magana ko na ji daΙi, wannan karon ka daΙe ba ka ce mini komai ba. Da na sanya ran ka fara samun lafiya, amma kullum lamarin nan gaba yake yi. Ka gaya mini wane ne kai? Daga ina ka ke? Ina zan samu danginka da 'yan uwanka, wataΖila kai naka dangin ba za su guje mu ba, za su karΙe mu, tare da sarΖar da ta haΙa Ζaddarorinmu wuri guda, duk da ban kasance Ιaya daga cikinku ba, ni fatana a nema maka magani ka samu lafiya, ba na son ganin ka cikin wannan mummunan yanayin, idan na ci gaba da ganain ka a haka, zuciyata za ta iya bugawa. Dan Allah ka yi magana" Ta yi maganar wasu hawayen na zirarowa daga cikin idanunta.
Ayshercool
08081012143
58
Ya haΙiye wani irin yawu, da yake yi masa zafi a Ζirjinsa, yayi ΖoΖarin Ιago hannunsa na dama, sai ya tuna ya riga ya shanye, ba ya iya komai da shi. Ya buΙe baki da nufin ya kira sunanta, saboda tasiri da kuma ciwon da kukanta yake yi masa a zuciyarsa, amma ya gaza bakin ya karkace yawu ya fara zubowa daga bakin nasa, maimakon kiran sunanta da ya yi yinΖurin yi.
Tana kuka, ta sanya tsumman da tayi amfani da shi wurin ba shi abinci, ta goge masa bakinsa. Ba shi da zaΙin da ya wuce, ba wa hawayen da yake maΖale a cikin idanunsa damar zubowa, ko shi ma ya samu sassauci abin da yake ji.
A hankali ya hura mata iskar bakinsa a fuskarta, a take ta silale ta faΙi a jikinsa.
Ya sanya hannunsa mai lafiya, ya rungume ta, ya ci gaba da kuka. Jikinta gaba Ιaya ya saki.
Ζaisar ta gani a gurin haΙe-haΙen magungunan sa, yana ta haΙa wani abu a cikin kwalba. Zuciyarta ce take ta azalzalarta, da ΖoΖarin ingizata, sai dai ba ta yi magana ba.
Babu tsammanni, ta ji ya fara magana "ZaΙi Ιaya ya rage miki, a halin yanzu, ko dai ki yadda da abin da na zo miki da shi, ki rungumi Ζaddararki, ko ki na kallo Buzun nan zai mutu, domin ba zai taΙa tuna waye shi ba har abada, muddin Giyaz yana tare da shi. Dan ba na tunanin akwai wanda zai iya raba shi da shi. Idan har bai iya tuna waye shi ba, shikenan kin ga ba ki da wata makoma. Abu Ιaya zai sanya a wannan karon na bar miki abin da yake cikinki, duk da ba ni da tabbacin zai zama mai cikakkiyar lafiya ko akasin haka, Giyaz da muΖarrabansa sun riga sun fara taΙa shi a cikin ki. Kin san meyasa ban Ζarasa lalata wannan cikin ba?" Bai jira ta ba shi amsa ba ya ce "Saboda zan so na ga yadda za ki yi, a lokacin da Ιan zai amsa sunan shege, kuma ba za ki iya hanawa ba, domin ba ki da hujjar kare kanki. Idan Buzun nan ya rayu bai san waye shi ba, ga kuma nakasa. Idan kuma ya mutu suwaye dangin baban Ιan ki? Daga ina yake? Suwaye ahalinsa? Kin san ku a jinsinku na bil'adam da uba ake ado ba riga ba. Babu wanda zai damu da wacece ta haifi mutum, amma za a damu da waye ubansa meye nasabarsa? Tun da ki ka zo garin nan, zuriyarmu suke alwashin yadda fansar su za ta kasance a kan ki. Kafin zuwa wannan Ζadamin babu abin da ban gaya miki ba, na gargaΙi. Dan haka dabara ta rage ga mai shiga rijiya"
Cikin kuka Nana ta hau girgiza kai ta ce "Ba zan yi bori ba Ζaisar, ba zan yi shirka da Allah ba. Babu tsanani ko wahalar da za ta sanya na rabu da imanina. Amma na rasa gaba na rasa baya, ba dan ina neman taimakon ka ba, ko ka kawo mini Ιauki ba. Na san Ubangiji Allah shi zai taimake ni.
Amma dan zatin Allah idan ka na da hannu a ciwon Sayyid, ka yi mini rai ka rabu da shi, shi ne kaΙai duniyata. Ina matuΖar tausayin sa, ban damu da jinya da nake yi ba, wahalar da yake sha ta isa haka. Idan kuma laifikan zuriyarmu ne suke shafar sa, dan Allah ku yi haΖuri ki Ζyale shi haka"
Cikin sautin muryarsa mai ban tsoro, da ya kan yi amfani da ita, idan ya so razana ta, ko yi mata magana mai muhimmanci ya ce "Na sha gaya miki na maimaita miki, daga lokacin da ki ka fara bani umarni, kin yadda kin amince da buΖata ta ne. Ba ni da hannu a ciwon mijinki, kuma bai ya cikin zuriyar ku, sai dai Ζaddara mai Ζarfin gaske, ta haΙa ku tarayya guri guda. Amma muddin ki na son ya warke daga wannan rashin lafiya, ba ma iya haka ba, ya tuna waye shi, sai kin karΙi Ζaddararki.".
Nana ta sake marairaicewa ta ce "Ba zan iya shirka ba, ba zan iya zama 'yar bori ba. Zan jure jarrabawata komai zafinta amma ba zan yadda rasa imanina ba"
Ζaisar ya ce "A cikin biyu dole abu Ιaya ya faru, tunda kakaninki su suka ΖyanΖyashi wannan matsalar. Na yi iya ΖoΖarina gurin dakatar da ita a wancan lokacin, amma ta sake tasowa a wannan karon. Dole a cikinku Ιaya zai warke ya rayu Ιaya ya mutu a haka, dan babu alamar Giyaz zai sassauta wannan mummunan Ζudirin nasa a kan zuriyar ku. Gefe ga aikin da ya karΙa yake yi a akan mijinki, ko dai ki ci gaba da rayuwa da shi, laifukan ku na shafar sa, ko kuma ki yarda ki karΙe ni a matsayin hadiminki ki yi abin da nake so, ni kuma na san yadda zan yi da Giyaz, na baki maganin da mijinki zai warke"
"Ta yaya? Me yasa sai ni? Me yasa ni zan biya zunubin da lokacin da aka aikata shi ba na nan, zunubin da zamanin da aka aikata shi, ya yi nisa da nawa zamanin? Me ya sa kakannina suka zaΙi zama 'yan bori? Suka gada mini wahala da masifa take ta bibiyar rayuwata. Na zama mujiya a cikin mutane, duk inda na tsuguna sai wata masifa ta afku, da za a jefa mini zargi, kasantuwata ni ba mutum ba ni ba wani jinsi daban ba? Me yasa zan girbe baΖar shukar da ban san a lokacin da aka dasa ta ba? Ina son mijina duk da daga ni har shi, ba mu san waye shi ba.
Duk da Nijar ba Ιaki Ιaya bane ba, ba kuma Ζaramar alΖarya ba ce ba, Ζasa guda ce, na gwammace zagaye ta neman ahalinsa na damΖa shi a gare su, da na ci gaba da zama da shi, mummunar Ζaddarata tana shafarsa, ko kuma na zama 'yar bori na ci gaba da gadar da wahala da masifa ga zuriyarmu, gara ko ma mene ne ya Ζare a kaina." Ta Ζarasa maganar cikin Ζaraji, tana kuka mai bayyanar da tsantsar baΖin cikin da yake binne a cikin zuciyarta.
*****
A hankali yake driving cikin nutsuwa, yana sauraren Jamila, da ke bin waΖar da ke tashi a cikin motar Ζasa-Ζasa, sai kuma ta yi shiru.
"Ya ki ka yi shiru kuma?" Ta ce "Au wai ka na ji na?"
Abba ya ce "Eh mana, har kin fi masu waΖar ma iyawa" Dariya ta yi ta ce "Ka ji ziga, muryar ta su da aka tace, aka goge tawa kuma a haka, ka ke cewa na fi su iyawa"
"Au ba ki yarda ba? To shikenan ni dai na san kin fi iyawa" ya yi maganar yana parking Ιin motar a harabar gurin shan ice-cream Ιin. Abba bai taΙa soyayya ba, duk wannan abubuwan da yake yi wa Jamila, bai taΙa furta mata cewar yana sonta ba. Sai dai ita sarai ta gane sonta yake yi, so kuma ba na wasa ba. Sai dai tana mamakin yadda duk wannan abin da yake yi mata, ba ya iya nuna wa a gaban Hajiya Sa'a, hakan ya sanya ta fara tunanin ko dai yana da wata manufa a kanta ne.
Sai dai ta lura halaye da Ιabi'unsa, sun sha banban da na Hajiya Sa'a, shi Abba akwai tsantseni, da gudun saΙa wa Allah. Dan duk da son da yake yi mata, sai da ya yi mata faΙa a kan shigar banza da ta kan yi wasu lokutan.
Ice cream su ka sha, yana ba ta labarin yadda ya yi karatu, da irin Ζalubalen da ya fuskanta na rayuwa. Su ka gama ya Ιauke ta ya mayar da ita gida.
Bayan ta shiga gida, Mama ta ce "Yauwwa ke nake jira dama, gas ya Ζare na kira wayar ki kuma ba ki Ιaga ba"
"Ina hanya ne, ga ATM Ιina, a bawa Nasiru ya je ya Ιuro. Har za ta shiga Ιaki sai ta fasa ta ce "Ni kuwa jama'a ina Nana ne? Wayarta ba ta shiga, shekaranjiya waccan ma na biya gidan da mijinta yake gadi, na ga kamar babu kowa a gidan"
Mama ta taΙe baki ta ce "Au ke ba ki san abin da yake faruwa ba dama?"
Ta tsaya tana kallon Mama ta ce "Mene ne yake faruwar?"
"Ai tuni aka kore su daga wannan gida. Ke ba zama ki ke yi ba ne shi yasa, suka koma unguwar su Ummi, to kin santa duk inda ta zauna bala'i ne yake bibiyar gurin, hatsaniya ta haΙa ta da matan gidan da suke, suka ce mayya ce aka tashe su. Ai nan Babanku ya je aka yi ta fafatawa, da ta kwaso jiki ta taho nan, wai za ta dawo mijinta babu lafiya, na ce bani da gurin jinya a gidan nan. Allah ya raba ni da masifa, ba za ta dawo mini ba, to Ζarshe dai wai yanzu tana Ζauye, can gurin Uwani a can take jinyar mijin nata"
Jamila ta yi sak, ta ce "Mama Nana tana Ζauye fa ki ka ce?"
"Eh mana, to idan ba Ζauyen ba ina za ta je? Tana can"
"To waye yake ba ta Abinci?"
Mama ta ce "Oho ina na sani?"
"Amma ya aka yi tsawon wannan lokacin ban sani ba? Yanzu ba kamar da ba ne, ban ji daΙin abin da ki ka yi ba Mama, bai kamata a kore ta ba a ce ta koma Ζauye da zama ba. Da ina nan ko na sani, da na kama musu wani gidan, gaskiya sai ta baro Ζauye"
"To ke ina ruwanki? Mene ne naki a ciki uwar Iya? Kina kallon irin baΖar azabar da na sha, a kan zamana da ita a gidan nan. Na meye za ki kuma jajubo mana ita. Gara ki bani kuΙin da za ki kama mata hayar na bawa ΙanLadi, Ιan autanmu ya tafi kasuwa da zaman banzae da yake yi, na yi masa aure tun da Allah ya sanya kuttun arziki ya fashe mana, ba ki kai kuΙi inda babu amfani ba"
Jamila ta dubi Mama ta ce "Wannan Ιan uwanki ne, sai ki nemi kuΙinki ki yi masa, nima 'yar uwata nake tunani. Haba Mama, ko wani Nana ta kashe miki Ζiyayyar ta isa haka ai. Ai yakamata a tausaya mata, miji babu lafiya ga zaman Ζauye, ita Uwanin za ta Ιauki nauyin Abincinsu ne? Tun da muka tashi a wahala muke a gidan nan, amma ita nata ya fi na kowa ma" Jamila ta Ζarasa maganar cikin damuwa, ta shige Ιaki, ta bar Mama da buΙaΙΙen baki.
*****
Kallonsa Nana take yi, suna zaune sun yi juguum daga ita har shi. Bayan ta gama yi masa kitson zanen hannu guda takwas, ta yanke masa faratansa na hannu da na Ζafa.
Kamar wadda aka mintsina ta tashi tsaye, ta kalle shi ta ce "Sayyid, bari na je na dawo" ya bi bayanta da kallo har ta fice.
Sai dai a Ζalla ta kai awanni biyu kafin ta dawo, ko da ta dawo ta tarar da shi ya haΙe fuska, ta yi shiru ba ta kula shi ba, ta koma tsakar gida.
Ta laluba kayanta, ta Ιaukko wata takarda mai Ιauke da ayoyin ruΖiyya da na karya sihiri, sannan ta hura wuta a cikin murhu.
Ta dawo tsakar gida ta zauna, ta fara da Bismillah da karanta Suratul fatiha, sai Suratul falaΖi da nasi. Ta karanta ayoyi biyar Ιin farko na Suratul BaΖara, ta fara karanta Suratul mulk, a hankali sai ta fara gani dishi-dishi, ta fara daina ganewa. Ta busa ayoyin a cikin ruwan, Sai ta ajiye takardar. Ta Ιauki wata leda da ta zo da ita, ta fito da man habbatussauda da jan Almiski.
Saboda wauta sai ta buΙe miskin, ta kai hancinta, da sauri ta dungurar da shi a gurin, ta ja da baya, dan tuni ta ji jikinta ya fara tsuma.
Sai da ta Ιan samu nutsuwa, sannan ta zazzaga tazargaΙe a cikin bokitin, ta kawo ganyen magarya guda bakwai, ta saka a leda ta Ιan bubbuga musu muciya, ta haΙa a cikin ruwan. Ta yi shiru tana tunani a ranta ta ce "Allah ya sa ba mai magani na zama ba, Ζaisar bai mayar da ni 'yar bori mai bayar da magani ba, larurar Sayyid ta saka na fara koyi da magungunan sarkin baka."
"Amma ai ayoyin Alkur'ani ki ka karanta, shi ma kuma Sarkin Bakar yana amfani da Alkur'ani" wata zuciyar ta tunatar da ita. Haka dai ta ci gaba da wasi-wasi.
Can yamma, bayan ta tabbatar da ganyen magarya da tazargaden sun tsumu, ta Ιumama ruwa ta tsiyayi ruwan tofin ta tace ta haΙa da ruwan Ιumin, ta kawo man habbatussauda ta tsiyaya a ciki, ta kawo jan miskin nan da ta saka kwalbar a ruwan Ιumi, ya narke ta tsiyaya a ciki, ta Ιebo garwashi a kasko ta shiga Ιakin. Yana ganin Nana ya tashi zaune yana kallon ta, ya ga ta samu Ζyalle ta Ιaure hancinta da bakinta.
Ta nufo shi ya ga ta hau tuΙe masa kaya, ya din ga bin ta da ido, ta bar shi daga shi sai gajeren wando. Hannunsa da yake maΖale take kallo cikin damuwa, ta shafa hannun.
Sai kuma ta yi Bismillah ta fara shafa masa wannan ruwan. Tun daga cikin kansa.
Girgiza kai ya fara yi, yana ture ta da lafiyayyen hannunsa, yana toshe hancinsa. Ya din ga girgiza kai jikinsa yana karkarwa bakinsa yana rawa, ya din ga wani irin gunji yana miΖa. Amma sai da Nana ta jiΖe shi da ruwan nan tsaf.
Ta kunna kiran salla a wayarta. Ta kawo tazargade, da habbatussauda da ganyen magarya ta zuba su a kan garwashin nan, hayaΖin ya turnuΖe Ιakin, ta ajiye shi a nesa da shi kaΙan. Ta fice daga Ιakin ta kulle shi a ciki. Ta tafi ta din ga wanke hannunta. Wani irin jiri ya din ga Ιaukar ta, ga matsanancin ciwon kai, Ιari Ιaya da ya sanya take jin, tamkar kan zai yi bindiga ya rabe.
Ta samu guri ta zauna a tsakar gida, ta dafe saitin zuciyarta da yake ta bugawa da sauri.
Bayan wasu mintuna, ta tashi ta je ta leΖa ta window, ta hango shi a kwance a Ζasa. A tsorace ta buΙe shi, ta nufe shi da sauri tana kiran sunansa.
Gaba Ιaya Ζwayar idonsa baΖar ta Ιauke sai farar, ta durΖusa a kansa kawai ya miΖo hannu zai shaΖe ta, amma ta riΖe hannunsa. Hannun ya din ga rawa, ya sauke shi a hankali.
"Sayyid" tana ambatar sunansa, Ζwayar idonsa ta dawo ya kalle ta.
"Sannu Shugaba" hararta ya yi ya juya mata baya. Dariya ta fara yi Ζasa-Ζasa.
Ta ce "Haba Shugaba, ya ka juya mini baya, juyo ka kalle ni" ya Ζi juyowa. Ta tashi ta buΙe labule saboda yadda warin ita ma ya fara damunta.
Ta Ιaukko tsumma, ta hau goge masa jikinsa, saboda ya daina warin miskin nan ita ma ba ta so.
Ya tashi zaune, tana goge masa. Ta ce "Ko a yi wanka?" Ya Ιaga idonsa yana hararta, jikinsa ya koma jawur kamar wanda ya Ζone.
Ta din ga Ιoye dariyarta, ta yi masa wanka, ya din ga sinsuna jikinsa yana yamutsa fuska.
Ya shafa fuskarsa ta ce "Ka yi haΖuri, magani ne, ina son ran Ubangiji Allah ya kawo mana afuwa" Ya ture ta daga jikinsa. Amma ta manne masa ta hau cinyarsa ta zauna tana dariya.
Ta juyo da fuskarsa suna kallon juna, ta lumshe ido ta buΙe ta ce "Sannu shugaba" Ya jinjina mata kai. "In zubo Abinci ne?" Ya girgiza kai.
"Sai an yi salla?" Ya gyaΙa mata kai.
Ya yi sallar magariba da isha'i, ta zubo masa Abinci.
Washegari ma da sassafe, ta kuma rutsa shi tana shafa masa ruwan nan. Yau ma ture ta ya din ga yi yana girgiza mata kai. Ta kunna masa hayaΖi, ta gudu ta rufe shi a Ιakin. Haka ta sake tarar da shi, ya koma ja ya haΙa uban gumi. Ta yi masa wanka. Ta ba shi Abinci ya karya.
Allah ya dafa wa Nana, ba su taΙa rasa abin da za su ci ba. Kuma haka take ta jujjuya kuΙin.
Sai da ta gama yi masa duk abin da zai buΖata, sannan ta tashi za ta yi wanka, tana tsaye daga ita sai bra da zani a Ζugunta, sai cika bakinta take da aya mai gishiri, ga cikinta ya Ιaga sosai.
Ta waiwayo suka haΙa ido. "Ya ake kallona haka?"
Ya yi mata alama da hannunsa mai lafiya ta zo.
Ta Ζaraso gabansa ta durΖusa ta ce "Gani" ya nuna mata cinyarsa.
Ta ce "Ina da nauyi fa, jiya ma dan na tsokane ka na zauna, ka ga baka da lafiya" ya saka hannu ya janyo ta, ta hau cinyar tasa tana dariya.
Yatsansa ya saka ya Ιan latsa cikinta, ya kalle ta yana murmushi. Ita ma murmushin ta yi ta ce "Kullum sai ya ce ko ta ce tana gaishe ka" Da hannunsa yake tambayarta yaushe za ta haihu?
"Nima ban sani ba, amma dai bai fi wata huΙu ba, saura wata biyar in Allah ya sa mu na raye. Idan ka samu lafiya sosai, za mu je mu Ζara dubawa idan su Habu sun dawo, idan ba su dawo ba sai mu tafi Nijar. Duk da na san da sun dawo zuwa yanzu za su neme mu" Ya yi shiru yana ci gaba da kallon cikinta, da lokaci lokaci yake dan harbawa.
"Zan je na yi wanka"
Da hannunsa ya yi mata alamar, su je ya yi mata.
"Kana fama da kanka za ka yi mini wankan? Wato a ramawa kura aniyarta ko? To na yafe idan Allah ya baka lafiya sai ka yi mini Rayuwata" Cikin murmushi ya sunkuyo da kanta ya sumbaci goshinta ta da laΙΙanta. Hira yake so ya yi da ita, amma ya kasa sai dai ya kalle ta yana murmushi ko kuma ya din ga yi mata nuni da hannunsa.
Ya Ιauki wayarta, ya kunna waΖar da take yi masa, yana yi mata nuni da ta yi masa. Ta ce "A'a karatu za mu ji ba waΖa ba, a wannan yanayin da muke ciki, ai ba mu ga ta waΖa ba Sayyid" Ya tsuke fuska yana hararta. Ta ce "To shikenan, bari a kashe waΖar, sai na raira maka da bakina ko?" Kawai ya tsare ta da ido yana wani lumshe ido.
Tana dariya ta ce "Wai Sayyid ni fa ban gane maka ba kwana biyun nan, rigima ka ke ji, amma Alhamdillah alamun sauΖi ne da nasara.
Aka shiga kwana na huΙu, tana shafa masa tofi tana kunna masa hayaΖi ta gudu ta bar shi a Ιaki. Yau sai dai ta gama shafa masa, za ta gudu ya riΖe ta gam. Duk yadda ta so guduwa ta kasa. Ya kalle ta yana murmushin mugunta. Aikuwa jikinta ya fara tsuma ta saka masa kuka, jin yadda gaba Ιaya duniyar take juya mata, tana shirin fita hayyacinta.
Har dare ya yi suka kwanta, ba ta kula shi ba, dan gaba Ιaya jikinta ya mutu murus, babu abin da yake yi mata daΙi.
Can cikin bacci ta ji ya yi magana"Ma viee"
"Sayyid"
"Na'am"
"Magana ka yi?"
"Eh, yanzu na ji ta zo"
Ta tashi zaune cikin murna tana taΙa shi ta ce "Alhamdillah Sayyid, Allah ya Ζara lafiya"
"TaΙa ni na ji, ko zan ji wani abu"
Ta ce "Ga shi ina taΙa ka"
Ya ce "Ba wannan ba" ya yi maganar yana rungumota da duk hannayen sa biyu.
"Sayyid hannunka ya warke?" Ta tambaye shi a kiΙime cikin farin ciki.
"Eh" ya amsa a taΖaice yana ΖoΖarin yin wani abin daban.
"Bari na lalubo waya na haska ka na gani"
"Kar ki haska ni"
"Me yasa ganinka fa zan yi, hannun zan gani"
"Kar ki haska ni" ya sake maimaitawa.
A Ιan tsorace ta ce "Anya kai ne?" Ya yi dariya ya ce "A'a Ζaisar ne. Idan ma ba ni ba ne, ai kina ganewa"
Ta yi dariya ta ce "Wai Sayyid ya haka ne? Ka tsaya mu yi murnar ka samu sauΖi"
Ruf ya rufe bakin Nana, bayan ya tabattar da lafiyarsa ta dawo. Duk da ya yi farin ciki da miΖewar da hannunsa ya yi, wanda farkawa ya yi daga bacci kawai ya ji hannun ya saki, duk da ya yi masa wani iri babu daΙi.
Bayan wani lokaci, ya saka hannunsa ya Ιaukko fitila a gefen Nana, ya kunna ya haske ta. Rufe fuskar ta ta yi, ta juya bayan ta da sauri.
Ya kwanta a jikinta yana yi mata raΙa a kunnenta. "To tashi ki haska ni ki ganni, kin ga hannun" Nana ta Ζare rufe fuskarta a fulo, ta Ζi Ιagowa.
"Kin ga" ya yi maganar yana taΙa ta da hannun. Shi wannan abubuwan da take yi ma, ba Ζaramar dariya take ba shi ba.
Da Ζyar ta tashi, tana kallon hannun nasa da take ganin, tamkar almara ya miΖe.
Ta ja hannun ta ga ya miΖe, ta ce "Kuma ba ya ciwo?"
Ya girgiza kai yana taΙa hannun ya ce "Ba ya yi"
"Allah ya Ζara maka lafiya mai Ιorewa"
"Amin. Na gode. Na gode" ta rufe bakinsa ta ce "Ya isa haka. Allah za mu godewa"
"Alhamdillah. Amma ya zama dole na yi godiya, kuma na jinjina miki, saboda" bai Ζarasa maganar ba ta cije shi a kafaΙarsa, kamar yadda ya kan yi mata, idan yana jin raha.
Kamar ba su ne cikin zullumi da damuwa ba, suka koma shagalinsu. Dare ya tsala amma tamkar rana a gare su, Ζarshe ma zaman hira suka zauna. Da anjima sai ta tattaΙa hannun nasa, dan ta tabattar lafiya kalau yake bai kuma maΖalewa ba.
Haka suka kwana cikin nishaΙi, da kewar juna.
Da safe ta gama abin da take yi, ta shigo da maganin da take shafa masa, ya kalle ta ya ce "Wallahi ki ka zo kaina da wannan abun, sai na yi miki wanka da shi, ke ma na kulle ki a Ιakin, ki ji abin da nake ji" Ganin yadda ya haΙe rai ya sanya ta rabu da shi.
Wunin yau ma lafiya suka yi shi, babu damuwa, duk da jikinsa babu Ζarfi sosai.
Ya ci Abincinsa ya yi sallolinsa babu wata matsala. Sai dai yau ma Nana ba ta samu rintsawa yadda yakamata ba, sai da ta san ya warke. Wani nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita.
Wani mutum ta gani a tsaye a jikin bishiya, ya lulluΙe jikinsa da mayafi. Ta yi tsuru tana son ta ga waye haka.
Yana Ιaga mayafin ta ga fuskarsa, ta ja da baya, ta tsorata. Tsohon nan ta gani, jikinsa yana ta fitar da wani irin baΖin abu, fuskarsa ta yi baΖi Ζirin, ga hayaΖi na fitowa daga cikin bakinsa da hancinsa gaba Ιaya siffarsa ta yi muni babu kyawun gani.
Sai da Nana ta ja da baya, cikin tsoro da razani.
"Kin tafka kuskure yarinya, kuma za ki san kin taΙa Giyaz bin Jaddul Jinn. Babu wanda ya taΙa karya alkadarina, abu ya yi tasiri sosai haka a jikina. Dan a duk lokacin da aka yi yinΖurin illata ni, barin guri nake yi. Sai dai kash kina Ιauke da abin da aka yi mini tarko da shi a wancan karon." Ya jefo mata wani littafi jikinta ya ce "Ga shi nan, littafin da ki ke ta bibiya sai kin ji ΖwaΖwaf, ki Ζarasa karantawa kafin na je na yi jinya na dawo. Amma ki sani dawowata ba za ta haifar miki da Ιa mai ido ba. Domin illar da ki ka yi mini sai na ninka wa mijinki, wahalar da ki ka sha ba ki ga komai ba." Kawai ya Ιacewa ganin Nana.
Nana ta kalli littafin hannunta, na gurin Ζaisar ne, da take ta bibiyar sai ta karanta hanata.
Da kansa littafin ya buΙe, a daidai shafin da tsaya da karantawa wancan karon.
Jiki na tsuma ta ci gaba da karantawa.
Jama'ar da suke gurin girkar, wasu suka watse a dalilin gakin sarkin Aska ya bayyana a gurin, kar ya gansu ya hukunta su. Bayan musayar yawu a tsakanin Duna da uban duΖusa, Sarkin Baka ya yi girgiza ya Ιace.
Uban duΖusa ya saka aka Ιauki kakan Lanti, a ka kai shi gida. Ita ma Lantin tana zuwa gida ta faΙi Ζasa.
Ba ta sake farfaΙowa ba sai washegari. Sai dai bayan farfaΙowarta, ta tarar da kakanta cikin mawuyacin hali, wanda hakan ba Ζaramin Ιaga mata hankali ya yi ba.
Cikin damuwa mijinta ya ce "Lanti sai da na gaya miki ina jin tsoron wannan abun, ki ka ce babu komai, ina tsoron kar rikici ya Ιarke a garin nan"
"Babu rikicin da zai Ιarke, ka kwantar da hankalinka, ni dai kawai fatana na kawo Ζarshen Sarkin Aska."
Kakan Lanti da ya yi tari, sai aman jini, dama ga jikin tsufa, ya zamana ko tashi baya iya yi saboda buguwar da ya yi. Kwanaki huΙu da faruwar lamarin, Lanti tana yi masa hayaΖi da ganyen Ιaure. Ya riΖo hannunta ya ce "Ya ke jikata, ki sani na yi miki Girka da babban Aminina, kuma ya Ιaukar mini alΖawarin ba ki duk wata kariya, da zama mai hidima a gare ki, kuma ya yi alΖawarin bawa zuriyarmu kariya daga cutarwar miyagun Aljanun cikin su. Dan haka a duk lokacin da ki ke buΖatar ganawa da shi, ki sanya kayan saΖin ki, ki Ιaura gurunki. Sai dai kar ki kira shi a guri mai Ζazanta, ba ya son zama a guri mai Ζazanta, kuma ba ya zama a guri mai najasa. Sannan 'yar ki Duna ne ya shafe ta, kuma ga wannan abu da ya faru, abu ne mawuyaci ta warke, sai dai idan uban duΖusa ne ya samo mata magani. Ni na san ba zan rayu ba, Duna ya riga ya yi mini illa, dan haka ki kula da mutanen Buda. Yana gama faΙin haka wuyansa ya karye. Lanti ta fashe da kuka, ya buΙe baki yana son ya yi mata magana amma ya kasa, har ya daina motsi ya mutu.
Nana ta yi kuka ba kaΙan ba, da mutuwar Kakanta.
Ζaisar ne a tsaye a kan wani dogon tsauni, gabansa kuma Giyaz ne, da yake kamannin da shi sak, tamkar ya yi kaki ya ajiye.
"A kan me za ka je ka aikata wannan shirmen da ka yi? Ko har ka manta da cewar fansarmu za mu Ιauka a kan abin da mutanen nan suka yi mana?"
"A'a Giyaz, mutanen nan ba su ne ainihin waΙanda suka fara rigimar nan ba, kuma Ιarnar da aka yi musu ta yi yawa. Babu amfani rashin zaman lafiya da tashin hankali. Kuma ka duba irin cutarwar da abokinka Duna ya haΙa kai da sarkin Aska yake yi wa mutanen garin nan. Yakamata a zauna lafiya, haΙa kai da bil'adama ana cutar da jinsinsu ba zai haifar da Ιa mai ido ba."
"Rufe mini baki Ζaisar" Ζaisar ya kalli mahaifinsa jin ya kira shi da sunansa na yanka, saΙanin sunan da yake masa kara da shi, na uban duΖusa wanda da shi ake kiransa saboda kara ga mahaifinsa. Dan duk cikin bataliyar 'ya'yan da ya haifa, ya fi Ζaunar sa. Ya Ιora da cewa "Kar ka manta abin da suka yi wa Mahaifina Jaddul Jinn wanda yake kaka ga duk wani Aljani da yake nahiyar nan, da yadda ake girmama shi, sai mene ne dan a azabtar da su. Dan mene zaka hau kan bil'adama a matsayin bawa, duk da kasancewar ka Ζasaitaccen matashin aljani da ake ji da shi a jinsinmu" ya yi maganar cikin Ιaga murya, muryarsa na amsa kuwwa a ilahirin dajin.
"Zaman lafiya da kwanciyar hankali, mu rayu mu da su babu cuta babu cutarwa. Lalata musu amfanin gona, sanya musu rashin lafiya da makamantansu duk ba zai sanya ku huce ba, tun da waΙanda suka yi laifin na sun mutu basa nan"
"Uban duΖusa yanzu ka fifita bil'adama a kan ni mahaifinka?"
"Ko Ιaya, sai dai ka san muna mutunta yarjejeniya. Mun yi yarjejeniya da abokina, zan ci gaba da bawa zuriyarsa kariya, zan kula 'yar sa zan din ga kawo mata magunguna tana bayarwa. Kuma ya yarje mini ci gaba da yi wa zuriyarsa hidima, da bayar da magani ta hanyar waΙanda aka haifa da tauraron 'yar sa Lanti"
"Ζarya ka ke yi Ζaisar. Ζana ba zai zama bawa ga gajiyayyun halittu kamar bil'adama ba, ka sani yadda suke yi mana kallon halittu maΖaryata, haka su ma ba su da cika alΖawari. Ka tuna kai makaranci ne, manazarci kuma marubuci. Ka karanta litattafai da ni kaina ban san adadinsu ba. A Ιakin karatun ka akwai litattafan da aka rubuta dubbanin shekaru kafin zuwanka Duniya. Ka yi yawace-yawace a Duniya domin neman abubuwan rubutawa, kuma ina da tabbacin ka karanta tarin kashedin da magabantanmu suka yi mana a kan bil'adama. Dan haka ba zan bari iliminka da soyayyar da nake yi maka, su Ζare a kan yi wa biladama hidima ba, ba ma su su yi maka ba. Sai dai ka zaΙa, zama da mu ko kuma hidima ga bil'adama!"
Ayshercool
08081012143
59
Ζaisar ya ce "HaΖiΖa kai Babana ne, ka so ni mai sonka ma ya so ni. Kuma na san ni ne ruhi mafi soyuwa a gare ku. Ka tallafawa burikana da bani damarmaki a matsayina na Ιanka. Sai dai ka tuna, na kawo girman da zan iya yankewa rayuwata hukunci. Kamar yadda ka faΙa; na karanta kashedin da aka yi mana a litattafan magabata, na yi yawon neman labarai a duniya, amma babu inda na ga an ci riba da tashin hankali da yaΖar juna. Kuma Aljani bai taΙa nasara a kan bil'adama ba, komai tasirin cutarwar da ya yi masa.
Na yi abota da bil'adama, na karanci wasu abubuwa masu muhimmanci dangane da zamantakewar su. Kuma ina son na yi amfani da ilimina na sanin magunguna, na sanar da wasusn su, domin samun waraka daga wasu cututtukan da mu ne muke haddasa musu su.
Dan haka ina mai baka haΖuri, na riga na yi alΖawari ba zan iya warwarewa ba. Sannan ba a banza zan yi wa zuriyar sarkin baka wannan aiki ba. Kamar yadda na gaya maka, sun sadaukar mini da duk wani mai irin tauraron Lanti, domin gudanar da burina na son yaΙuwar ilimin bayar da magani"
Cike da Ζunar rai Giyaz ya numfasa ya ce "Shikenan, ka yi abin da ka ke so, amma ka je, na sallama ka daga cikin zuriyaramu, kar ka sake danganta kanka da mu" daga haka Giyaz ya Ιace.
Lanti ta damu da mutuwar kakanta, sai dai ba a rufa sati ba, 'yar ta ma mai larurar shan Inna ta mutu. Ta shiga tashin hankali sosai da sosai, tamkar za ta zauce.
Hankalin Sarkin Aska kuwa ya yi mummunan tashi, bayan da Duna ya sanar da shi cewar, da Uban duΖusa aka yi wa Lanti girka. Kuma cutar da Uban duΖusa ka iya kawo fitina da tashin hankali a tsakanin su kan su Aljanun. Duk da zafin bil'adama da Giyaz yake ji a kan abin da suka yi wa mahaifinsa, amma ba zai lamunci kowane Aljani ya taΙa masa Ιa ba.
Sarkin Aska ya ji baΖin ciki ba kaΙan ba, da abin da Duna ya gaya masa, bayan tabattar da cewa ya samu abokiyar hamayya a garin.
Ζaisar ya fara bawa Lanti magunguna, ta fara aikin bayar da magani a garin. Babu nasiha da rarrashin da ahalin Ζaisar ba su yi masa ba, a kan ya janye daga harkar taimakon biladama, amma fafur ya Ζi ya ce ba zai daina ba. Akwai kyakykywar fahimta a tsakanin Lanti da kuma Ζaisar.
Lanti ta kuma samun juna biyu, ta haihu sai dai Ιan da ta haifa, ba ta haife shi da irin taurarinta ba.
Aka shiga zazzafan takun saΖa, a tsakanin Lanti da Sarkin Aska, dan mutane suna tururuwar karΙar magani a gurinta. Domin ita ba ta tsauwwala wa mutane, kuma ba ta neman su kawo wani abu da ya fi Ζarfinsu. Duk da Giyaz ya sallama Ζaisar, amma hakan bai bayar da damar, 'yan uwansa su iya cutar da shi ba.
A lokacin sai zuriyar Jaddul Jinn wasu suka goyi bayan zaman lafiya, kamar yadda Ζaisar ya yi, wasu kuma suka zauna a kan bakar su na lallai sai an ci gaba da cutar da bil'adama da duk wanda ya fito daga wannan tushe na Buda.
Sarkin Aska ya ci gaba da jan Aljanu, yana sadaukar musu da jini, yana amfani da su ta hanyar tsafi, da kuma alwashin taimaka musu a duk lokacin da suke buΖatar hakan.
Cike da baΖin ciki, Giyaz ya zura wa Ζaisar ido, babu yadda ya iya da shi.
Ganin abin da Sarkin Aska yake ci gaba da yi, duk a ΖoΖarin sa na mamaye garin a ci gaba da tsoron sa, ya sanya Lanti ta Ζara zage damtse a kan harkar bayar da magani da laΖantar hanyoyin da za ta kawo Ζarshen Sarkin Aska.
A haka ta haifi yara biyar maza, duk babu mai irin tauraronta, gaba Ιaya abin ya damu Ζaisar, ganin babu wanda zai iya gadar ayyukan Lanti.
Sai dai a jininsin mutane ma, 'yan uwan Sarkin Aska ba sa Ζaunar abin da yake aikatawa na zaluntar mutane.
Wata jakar fatar damusa, Ζaisar ya sanya Lanti ta fara haΙawa, wadda da ita take burin kawo Ζarshen Sarkin Aska, saboda babu irin mugun hari da yinΖurin da Sarkin Aska ba ya yi, dan ya kashe ta.
Sai da ta shekara biyar, tana aikin jakar nan, tare da jiΖata da magunguna daban-daban. Ban da zanen hatimai kala-kala da yake cikin jakar.
Ta haΙa kai da Ιan uwan Sarkin Aska, baya nan ya je ya ajiye masa jakar a Ζasan abin kwanciyar sa. Kuma Ζaisar ya Ιatar da sahun sa, ta yadda babu wanda ya gane a cikin aljanun da suke yi masa hidima. Tun da ya kwana a kan jakar, Aljanun da suke yi masa aiki, suka watse suka bar shi, ya kamu da matsananciyar rashin lafiya da sai da ta yi ajalinsa. Yana mutuwa kuma aljanun suka fantsama kan 'ya'yansa da jikokinsa, sai dai aka rasa wanda zai gaje shi gurin ci gaba da aikin zaluntar al'ummar da yake yi. Sosai mutanen gari suka yi murna da mutuwar sa. Babban Ιan sa da suke bokancin tare ma, cewa ya yi ba zai iya ba.
Ζin samun wanda zai gaje shi, ya sanya aljanun fara sanya wa iyalansa cututtuka. Wasu kuturta wasu suka makance, har da waΙanda suka haukace. Aka din ga Ιauki ba daΙi da Lanti, a kan sai ta warkar da su. Ζaisar ya gargaΙe ta a kan babu ruwanta ta rabu da su.
Lanti ta shafe shekaru Ashirin da bakwai, tana aiki tare da Ζaisar tana harkokinta na bori da bayar da magani, haka zalika ita ma ta yi wa mutane da dama girka, masu sha'awar harkar bori. Akwai bikin 'yan bori da ake gudanarwa da nuna bajinta duk shekara, wanda a nan ake yi wa masu so girka, ake bikin bajekolin abubuwan ban mamaki, na gidaje daban-daban.
Maharba su yi na su, wanzamai, 'yan bori da dai sauran su.
Domin bayan mutuwar Sarkin Aska an Ιan samu zaman lafiya, tun da dama shi yake assasa duk wata fitina da rashin zaman lafiya. Sai dai aljanu ba su fasa cutar da su da razana su ba, duk da Lanti tana iya kokarinta. Sai dai ita ma bayan wannan shekarun ta koma ga Allah.
Sai dai kan ta mutu, a cikin jikokinta an samu guda Ιaya da take da irin tauraronta.
Dan haka bayan mutuwar Lanti, aka ci gaba da ba ta kashi tsakanin mutanen garin, da Aljanun da sarkin Aska ya yi aiki da su, har ma da waΙanda ba 'yan asalin garin ba ne.
Sai dai babu yadda Ζaisar zai yi, a lokacin jikar Lanti ba ta kai lokacin da za ta iya bayar da magani ba. Kuma har a lokacin ba a fasa yi masa magiyar ya rabu da bil'adama ba. Gaba Ιaya ya nesan ta kansa da Ahalinsu.
Bayan jikar Lanti ta fara tasawa, Ζaisar ya fara bijiro mata, domin yin gadon kakarta, sai ta kasa Ιauka sai ma taΙin hankali da ta samu, duk da ta Ιan taΙa bayar da maganin amma ba sosai ba. A hakan ita ma ta yi aure ta hayayyafa.
A cikin 'ya'yanta aka samu wadda ta gaje ta, duk da ba irin tauraronta Ιaya da Lanti ba. A lokacin Musulunci ya shigo cikin mutane, duk da bai yi Ζarfi a garin Buda ba.
Asma'u ta bayar da magani ita ma, ta yi aiki tare da Ζaisar, sai dai ba ta da Ζarfin zuciya da juriya irin ta Lanti. Gaba Ιaya ita ma ba wani daΙin aiki ya ji da ita ba. Ko yaya ya buΙe mata ido ta ga abu, sai ta kwanta ta hau jinya. Daga baya ma ta watsar ta tattara komatsan borin ta ajiya, ta ce ta tuba ta daina.
Ganin ba a samun masu irin tauraron Lanti, ya sanya Ζaisar fara sarewa, da haΖura da batun bayar da magani ta hanyar bil'adama. Sai dai yana iya yin sa gurin bawa zuriyar su Lanti kariya, daga cutarwar zuriyarsu.
Duk abin da yake faruwa, Giyaz yana ankare da Ζaisar, kuma yana murnar yadda Ιan sa ba zai ci gaba da zama bawa ga bil'adama ba.
Aka din ga samun ci gaba a garin Buda, wasu suka din ga barin garin su na tafiya fatauci, wasu kuma tashin hankalin Aljanun da ya addabi garin ne ya sanya suka bar garin, ciki har da wasu daga cikin zuriyar Lanti.
A can Bauchi aka haifi Maijidda, har ta girma, an saka mata rana saura watanni uku aurenta, su ka zo Buda, a nan suka haΙu da Isa, ya Ζallafa rai a kanta.
Yayar kakarta ta ce sai an warware wancan baikon da aka yi da na can garin Bauchi, an yi da Isa, saboda Ζara danΖon zumunci, kuma hakan zai sanya su din ga kawo musu ziyara a kai a kai, da Ζara samun zaman lafiya a tsakanin zuriyar maharba da ta wanzamai.
Aka mayar wa da wancan na Bauchi kuΙinsa, ita kuma ta auri Isa.
Gidansa na Kano, inda yake harkokin kasuwancinsa, nan ya tafi da ita. Ya ajiye ta a gidansa da suke tare da matarsa babar Gaddafi.
Ya Ιora wa Maijidda son duniya, kamar a kanta ya taΙa aure. Ba uwargidansa ba, hatta 'yan uwansa sai da suka fara jin haushin Maijidda saboda ba ya Ιoye son da yake yi mata, ga ta yarinya Ζarama amma su na ganin kamar ta mallake shi, dan shekarunta goma sha shida a lokacin.
Kasancewar daga zuriyar Sarkin Aska Maijidda take, ta auri Ιan zuriyar Sarkin Baka, sai Aljanun da suka yi wa sarkin Aska hidima, suka shiga cikin lamarin auren, su ka fara haddasa musu matsala. Haka kurum sai ta ji ta tsani Isa, ba ta Ζaunar ganinsa ga yawan rashin lafiya. Kishiya da facaloli suka sako ta a gaba, ga jarabar dangin miji.
Ana haka ya samu matsala da uwargidansa, da ta haifa masa Gaddafi da Ummi, ya sake ta. Nan ma aka ce Maijidda ce sila.
Ya auri Rabi, suka zama ita da Maijidda. Yayarsa Atine ta Ζara haΙe kai da Rabi, su na cizguna mata.
Maijidda ke riΖon su Gaddafi, tana iya kokarinta amma kullum cewa ake yi tana azabtar da su. Kasancewar Gaddafi ya fi Ummi wayo, ya tsani Maijidda cewa yake saboda ita aka saki babar su, kamar yadda Yaya Atine take faΙa. Ita kuma Ummi tana matuΖar Ζaunar Maijidda.
Nan ma Rabi ta saka Maijidda a gaba, da kishi da Ζage kala-kala.
Bayan haihuwar Imran sai da ya shekara uku da rabi, ta haifi Nana. A lokacin Isa ji yake kamar ba a taΙa yi masa haihuwa ba sai a kan Nana. Ya saka mata suna Asma'u, sunan kakarsa da ta riΖe shi take bala'in son sa. Hatta hakika biyu ya yi wa Nana, Ummi ma da ya saka mata sunan mahaifiyarsa bai yi mata abin da yake yi wa Nana ba.
Isa kofur ne na 'yan sanda, abokan aikinsa suka yi masa Ζage, aka kore shi daga aiki har da prison. Ya koma harkar fawa, ya fara samun rufin asiri, harka ta buΙe masa yana samun rufin asiri sosai , sai dai kasancewar sa mutum ne da ba shi da sirri, duk samun sa sai ya bayar da labari, abokansa suka jefe shi sana'ar ta fita daga ransa ya daina zuwa ko ina, sai zaman gida.
Tun da Allah ya sanya aka haifi Nana Ζaisar ya ganta ya rikice, tamkar Lanti ta yi kaki ta ajiye saboda kamanin su. Ga irin tauraronta Ιaya da Lanti. Gaba Ιaya Ζaisar ya tattara hankalinsa a kan Nana Asma'u yana ganin, ya samu uwar gijiya a zuriyar Lanti. Giyaz na fuskantar abin da ke shirin faruwa, ya fara ΖoΖarin raba Ζaisar da Nana. Dan kullum yana tattare da ita. Wasu lokutan ya zungure ta tayi ta kuka. Manyan bokaye da Ζungiyon Asiri na zawarcin son yin aiki da Ζaisar, saboda tarin baiwa da kuma ilimi da binciken ΖwaΖwaf da yake yi. Wanda za su aiki da shi ne, ya din ga taimaka musu, su kuma su din ga yi masa hidima, amma fafur ya Ζi. Saboda ba ya son duk wata alaΖa da jini.
Ζaisar ya yi tafiya zuwa wata Ζasa, ganawa da wani tsohon Aljani, a kan wani rubutu da yake yi, ya dawo ya tarar an saki Babar Nana, ita kuma Nana ta daina magana, ta daina tafiya ga Baba ya Ζwace ta, ya hana Maijidda ita. Ya fuskanci aikin mahaifinsa ne Giyaz. Ya je ya same shi yake tambayar sa me yasa ya yi wa Nana haka.
Giyaz ya ce "Ka sani ba zan taΙa sake yadda, ka zama bawan bil'adama ba, da ka sake zama bawan bil'adama gara na kashe ta ko na kashe ka, kowa ma ya huta."
Ζaisar ya san Giyaz ba ya magana biyu, idan ya faΙi magana sai ya aikata.
Dan haka Ζaisar ya fara ΖoΖarin kare Nana, ya yi amfani da jakar da ya saka Lanti ta haΙa, ta yi amfani da ita gurin kashe Sarkin Aska. Ya Ζara yi mata aiki, da saiwoyi da wasu hatimai, ya yi wa Giyaz tarko da ita.
Cikin matsananciyar sa'a, Giyaz ya faΙa tarkon Ζaisar, saboda ya san muddin ya bar Giyaz, zai iya nakasta Nana nakasa ta har abada, ko ma ya kashe ta, kamar yadda ya furta.
Ya Ιauki Giyaz, ya kai shi can nesa ya sadaukarwa wani boka shi, bisa musayar da za su yi, zai ba shi wani abu mai muhimmanci. Wanda ya yi hakan domin nesan ta shi da Nana da zuriyar Lanti.
Duk da abin da ya yi ya dawo ya dame shi, yana matuΖar Ζaunar mahaifinsa, duk da saΙanin da suka samu, amma babu yadda iya, hakan ne kawai zai sanya ya nisanta shi da Nana.
Sauran 'yan uwan Ζaisar da tuntuni suke jin haushinsa, suka yo caaa a kan Ζaisar, har suka nemi hallaka shi, saboda abin da ya yi wa mahaifinsu, amma sun san ko sun hallaka shi, idan Giyaz ya kuΙuta suma sai ya kashe su.
Ζan uwan Giyaz Duna, ya yi ta ΖoΖari gurin ganin ya kuΙutar da Giyaz, amma abu ya gagara.
Nan suka din ga kai wa Nana hari, da yinΖurin hallaka ta.
Maijidda kuwa bayan mutuwar aurenta, tana gama idda, Iliyasu tsohon saurayinta ya sake dawowa ya aure ta. Ko da Baban Nana ya samu labari, sai ya ce tana sane, ta Ζi zama da shi, saboda ta koma ta auri Iliyasu, dama son zama da shi take yi ba.
Nana ta ga garari tun da Ζuruciya, babu cikakkiyar kulawa, kuma tun ba ta fi shekara uku ba take ganin Ζaisar, da ma sauran 'yan uwansa da suke ta kokarin azabtar da ita.
Maijidda ta so karΙar ko Nana ce, saboda rashin cikakkiyar lafiya, amma Isa ya hana fafur, ita ma can mijinta ko yaya ta motsa tana son ganin 'ya'yanta, sai ya hau bala'i wai za ta gurin tsohon mijinta.
Tun Nana na Ζarama, take nuna alamun rashin lafiya, amma babu wanda ya kula. Ta kan wuni tana bacci tun safe, har dare babu wanda zai damu. Wasu lokutan ta daina magana ma ko tafiya gaba Ιaya. Idan kuma ta warware ta din ga fitinar da ta fi Ζarfin shekarunta nesa ba kusa ba.
Ta kan ga Ζaisar a zahiri, ko kuma a cikin bacci. Babu wanda ya damu da ta ci Abinci ko ba ta ci ba, mussaman da Baba ya daina sana'ar komai, sai dai Imran ya nema ya bata. Idan ta fita Ζaisar ya kan zo a suffar mutum, ya ba ta abinci. Allah ya sanya masa matsananciyar Ζaunarta. Ya fara bayyana a jikinta ne, tun wani duka da Mama ta yi mata, bayan faΙa ya haΙa ta da Jamila.
Sai da ta kwana biyu a sanΖame, tun daga nan suka gane halin da take ciki. Da ranta ya Ιaci sai hankalinta ya gushe. Ζaisar ya sha Ιauke Nana, a neme ta a rasa kwana Ιaya ko biyu ya je ya ajiye ta gurin sa.
Baba ya yi ΖoΖarin nema wa Nana magani, amma abu ya gagara. Labari ya iske Maijidda halin da Nana ne ciki, bayan da su Adda Saude suka zo ganin su Nana. Rabi ta haΙa tuggu a gurin Baba, ya ce kar su sake zuwar masa gida, kuma ba zai bayar da Nana ba. Wahala ta saka Imrana fara sace-sace saboda su ci Abinci, Rabi ta saka Baba ya kore shi daga gidan. Haka Nana ta tashi a cikin wahala, ga wanda bil'adama suke yi mata, ga wadda Ζaisar yake yi mata da sunan kulawa.
Ji ta yi tamkar an sanya hannu an shaΖe ta, a dole ta saki littafin ta ja da baya tana tari.
Ta Ιaga kai ta kalli Ζaisar, bai ce mata komai ba, ya Ιauki littafinsa ya juya ya tafi. Yana barin gurin Haula ta zagayo ta dafa Nana. Ta Ιaga kai ta kalle ta ta ce "Ζawata, kwana biyu. Hadiminki ya Ζi saurarata balle na sanya ran zai karΙi buΖata ta, ki yi wani abu a kai dan Allah"
Nana ta ce "Haula, gaba Ιaya jinsinku ba abin yadda ba ne, ki rabu da ni da wannan maganar ta ku"
"Shikenan, na rabu da ke, amma kin yi ganganci abin da ki ka yi wa dattijo, Allah kaΙai ya san me zai yi miki idan ya gama jinya. Kuma har Ζaisar ki ka janyowa shi ma ba zai bar shi ba"
"Duk hukuncin da ya yi wa Ζaisar yayi daidai, Ιa na gari ba zai taΙa yi wa babansa abin da ya yi wa nasa mahaifin ba"
Haula ta ce "Kash! Nana kar ki zama butulu mana. Sai dai ina fatan kin fuskanci jakar gurin Sarkin baka da ya baki, wace jakar ce"
Nana ba ta ba wa Haula amsa ba, Sayyid ya tashe ta.
"Ma vie" yayi maganar yana matsawa jikinta sosai. Jiki a sanyaye ta amsa masa. Ya ce "Lafiya dai?"
"Mmm"
"Ko Ζaisar Ιin ne?"
"A'a"
"To me yasa ki ka tsorata? Mene ne ya baki tsoro?"
"Bakomai"
"es-tu sΓ»r? (Kin tabatta?)"
Ta ce "Eh. Haryanzu hannunka lafiya Ζalau ko?"
"Eh, amma akwai abin da ya tsorata ki, gaya mini mene ne?"
Ji ta yi tamkar ta gaya masa, dan a wannan karon ba ta manta abin da Giyaz ya gaya mata ba, a kan idan ya warke zai sake waiwayar su.
"Ma viee"
"Sayyid" ta amsa a hankali.
Ya yi maganar yana taΙa wuyanta "Sanyi ki ke ji Rayuwata"
"Eh, amma ba sosai ba"
"In baki Ιumi ne?" Yayi maganar muryarsa Ζasa-Ζasa
Dariya ta yi ta ce "A'a na yafe, Ζona ni za ka yi"
Shi ma dariyar ya yi ya ce "To ni ki bani sanyin ina so" Ya yi maganar da sigar shawaΙa.
"Wai kai ba ka jin bacci ne? Kawai ka farka cikin dare?"
"Soyayya ce ta tashe ni" Sai da jikin Nana ya Ιan yi sanyi, ta ce "Soyayya kuma Sayyid?"
"Eh, je t'aime ma femme"
"To ai ban san me ka ce ba"
Ya yi kissing Ιin goshinta ya ce "Ina sonki matata" wani abu ne ya tsirgawa Nana, tun daga tsakiyar kanta, har tafin Ζafarta.
Shafa hannunsa ta yi, kamar mai tantamar abin da ya ce, ta ce "Sayyid"
"A'a, kar ki yi tantama, ko ki yi kokwanto, shi yasa na baki sunan Rayuwata. Ko a wannan Duniyar, ko ma a wace Duniyar, kawai ina son matata, saboda ita Ιin Rayuwata ce. Babu abin da zai canza hakan."
"Sayyid ina tsoron idan ka tuna waye kai, ka ji ba ka so na, zan cutu da yawa, zamana da kai na shaΖu da kai sosai zuciyata ba za ta iya Ιauka ba" Ta yi maganar cikin rauni da tsoro.
Ya Ιaga kan Nana, ya sanya hannunsa a wuyanta, ta lumshe idanunta hawaye na bin gefen fuskarta.
"Ζa'idar ba za ta canza ba har abada, babu ruhin da zai samu nutsuwa a gangar jikin Ιayanmu muddin ba ma tare, ki saka haka a ranki. Sayyid yana son Rayuwarsa. Ko babu raina fatalwata za ta ci gaba da sonki" Nana ta yi ajiyar zuciya tare da dariya, ta shafa gashin kansa.
"Allah ya sa haka. Ina son mijina sosai nima" murmushi ya yi yana kissing Ιin ta.
Har garin Allah ya waye, maganganun Sayyid ne ke kai komo a cikin ΖwaΖwalwa, zuciya da kuma gangar jikin Nana. Wani irin shauΖi da farinciki ne yake kama ta, da tuna kalamansa.
"Amarya" ya yi maganar yana kallon Ζwayar idonta.
"Amarya da wannan Ιin?" Ta yi maganar tana nuna cikinta da ya fito sosai.
Yayi murmushi yana shafa cikin ya ce "Duk da haka amarya ce ai, ko kin manta?" Ya yi maganar yana kashe mata ido.
Ta yi murmushi tana ci gaba da ninkin kayan da ta wanke.
"Sayyid, bari na je kasuwa na nemo kayan magungunan ka, na dafa maka, ka ci gaba da sha, kuΙin hannuna sun Ιan taru, zuwa ranar Monday in Allah ya kaimu, duk yadda za a yi, mu tafi Kano Asibiti. Na ji haryanzu zuciyarka ba ta bugawa sosai, na san Ζarfin hali kawai ka ke yi"
"Gaskiya kin fiye saka ido, ya aka yi ki ka gane hakan, mai magani?"
Ta jinjina kai ta ce "Au haka ma za ka ce ko? Hmm ai shikenan, za ka ga mai magani, yau sai na wanke ka da magani na kulle ka a Ιaki"
"Eh saboda cin zali ba, kuma ke ki gudu, alhalin kamata ya yi ki yi mana tare"
Ganin yadda yake rungumota ta ce "Sayyid na gama shiryawa, fita fa zan yi"
Ya ce "Na sani"
"Ka sani kuma ka ke son na Ιata lokaci? Dan Allah Sayyid jiya throughout the night mu na tare, yanzu kuma...
"Shhhh... Ba ki ji jikina ya fara zafi ba"
"Wallahi lafiyarka Ζalau, normal babu zafi a jikinka, wai wannan surutun duk daga ina?"
Haka ya hana Nana fita, har bayan Azahar, kawai ta zuba wa Sarautar Allah ido. Kuma a fuskar sa take ganin tsantsar Ζarfin hali, amma ba shi da lafiya.
Sai bayan la'asar ta marairaice ta ce "Dan Allah ka bar ni na je na haΙo kayan nan Sayyid, ko haryanzu ba ka gama jin Sanyin ba?"
Ya Ιaga mata gira. "To ga mafici, yi ta fifita, har na dawo" Dariya ya yi yana Ιan jan hancinsa. Ya kamo hannunta ya Ιora a wuyansa ya ce "Kin ji da zafi ko?"
"Ba wani zafi. Waccan ranar ma wayo ka yi mini, wai na baka sanyin jikina"
Dariya yake son yi sosai, amma sai ya yi kaΙan ya cije, ya ce "Ai ni Ζaisar wasu lokutan taimakona yake yi"
A sanyaye ta ce "Shi me yasa ba ka kishi da shi?"
"In ji wa? Kawai abu Ιaya ne da babu yadda muka iya. AlaΖarsu ta Ιa da mahaifi tana tasiri a rayuwarmu ni da ke"
Cikin mamaki Nana ta ce "Ta yaya? Kuma ya aka yi ka san Ζaisar Ιan Giyaz ne?"
"Yadda ki ke ganin Ζaisar ku yi magana, haka nake ganin Giyaz, kuma na fuskanci waye shi a tattare da ni. Yanzu ki je ki dawo"
"Kai amma na yi mamaki fa, kuma ba ka taΙa gaya mini ba. Bari na je na dawo, ina da tarin tambayoyin da zan yi maka"
"Tom sai kin dawo"
Ta saka hijjabinta, har za ta fita ya kirawo ta. Ya ce "Ba ki yi mini ba"
Ta yi masa kiss a goshinsa, da bakinsa.
"Allah ya yi miki albarka. Ki kula mini da kanki, kar wani ya kula mini ke, ki kular mini da babyna ki tafi a hankali ki je ki dawo"
Ta kalli cikin ta ce "To Shugaba, in sha Allah"
"To a dawo lafiya, I love you"
Cikin murmushi ta ce "Inyee Ιan gayu, ka yi furansanci, ka yi turanci, ka yi hausa ga kuma yarenku. Zan koyo yaren da baka iya ba, na din ga tashin kanka da kalaman soyayya"
Ya ce "Je ki dawo ki yi mini waΖa"
"Sai dai na je na yi maka tsifa, na yi maka sabon kitso" ya tsuke fuska yana hararata. Ta fita tana waigensa tana murmushi.
Tana fita ya jingina da jikin bango, yana dafe saitin zuciyarsa, yana haki sama-sama. Ya fito tsakar gida da kyar, ya zauna yana sake danne saitin zuciyarsa da yake jin wani irin abu kamar shocking daga zuciyarsa yana zagayawa bayansa har cikin kansa.
Tsayuwar motoci ya ji a waje, sai dai hankalinsa ba ya kan hakan. Ya ji an daki Ζofar gidan da Ζarfi. Ya Ιaga kai ya ga wasu murΙaΙΙun Ζarti sun shigo cikin baΖaΖen kaya.
Duk da mawuyacin halin da yake ciki, haka ya yinΖura ya tashi da Ζyar, ganin an shigo da Habu hannunsa da sarΖa.
Ya din ga bin mutanen da kallo, Habu cikin matsananciyar damuwa ya zube a kan gwiwoyinsa ya ce "Ka yi mini Afuwa Imam, ba laifina ba ne ka yi haΖuri, na gaza baka kariyar da ta dace" Sayyid ya din ga bin sa da kallo, da alama ma ba ya gane me Habu yake nufi.
Ζartin nan biyu daga cikin su, suka yo kansa, suka riΖe shi.
A rikice ya ce "A'a, ku rabu da ni. Me na yi muku?"
ΖoΖari suke su tasa shi su tafi da shi cikin salama, amma ya turje. Suka juya yare zuwa faransanci, su na rarrashin sa, ya wuce su tafi.
"Ba zan je ko ina ba? Ina zan tafi na bar matata" Habu ya din ga girgiza masa kai da alamar ya daina faΙar maganar da yake yi.
"Ku rabu da ni, ina zaku kai ni na tafi na bar Nana" maganar da yake yi cikin Ιaga murya, ga ΖoΖarin turjewa da yake yi, ya sanya zuciyarsa yin rauni, ya yi baya zai faΙi. Suka tare shi suka saΙa shi suka yi waje da shi.
Aka saka Habu a cikin wata motar daban, Sayyid kuma aka saka shi a cikin wata baΖar Highlander mai tint glass, aka rufe suka tafi da shi.
Nana tana tsaye ta bayar da kuΙi, za a bata kankana, dan daga ita har Sayyid, kawai ta ji gabanta ya yi wata irin mummunar faΙuwa. Ta yi shiru, ta jiki gaba Ιaya jikinta ya yi sanyi. Kawai ta juya ta tafi. Mai kayan yana ta yi mata magana, amma ba ta tsaya ba, ta nufi gida har da Ιan gudu saboda azabar sauri.
Tana zuwa Ζofar gidan ta ga Ζofar gidan a Ιalle, da hanzari ta shiga gidan, tana kiran sunan Sayyid. Amma wayam ba ya nan, ta shiga Ιaki baya nan. Ta duba banΙaki nan ma ba ta gan shi ba.
Ta fita waje da sauri, tana kalle-kalle, ta tafi hanyar inda bishiyar kukar nan take, tana tunanin ko jikinsa ne ya motsa, ya tafi can, sai dai can ma baya nan.
Ta sake komawa gidan cikin tashin hankali, da wani yaro da yake zuwar mata aike ta haΙu a Ζofar gidanta ta ce "Ashiru, ko ka ga Sayyid ya fito daga gidan nan? Wannan mutumin na gidana farin nan?"
"Wasu mutane ne suka shiga gidan suka tafi da shi, a mota suka zo"
Sak Nana ta tsaya, tana Ζure Ashiru da ido, tamkar ma ba ta gane yaren da yaron yake yi.
Ayshercool
08081012143
60
Cikin rawar murya Nana ta ce "Wace irin mota kuma Ashiru? Ka tabattar kuma Sayyid ne?"
"Wallahi na tabattar, ina nan ina wasa suka zo, a motoci wannan farin na gidanki suka Ιaukko."
Tamkar mahaukaciya ta bi sahun motar, ita ce har titi ko za ta ga motar da Ashiru ya ce, amma babu wata alama na za ta ga motar da aka daukar mata Sayyid aka saka a ciki.
Gaba Ιaya ta kasa kuka, sai tsuma da jikinta yake yi tamkar mazari. Tuni rana ta faΙi, an fara kiran sallar magariba, ba ta san tafiyar da ta yi da nisa ba, sai da ta tashi dawowa.
Gidan Uwani ta nufa, ta tarar da ita ta yi alwala, za ta yi sallar magariba.
Uwani ta ce "Ke Nana, uban me ya fito da ke da magaribar nan, ga juna biyu kina da shi, duk da na san ba ki da Ιan aike amma koma mene ne, ai kya bari a idar da salla ko?" Nana ba ta yi magana ba, ta nemi guri ta zauna a Ζasa.
"Ke lafiya kuwa?" Uwani ta yi maganar tana tattara hankalinta a kan Nana. Amma Nana ta kasa magana, sai murza zoben hannunta da take yi, tana ajiyar zuciya.
"Ke ki yi mini magana, kar ki tayar mini da hankali mana".
"Sayyid ne ya Ιata"
"Kamar yaya sai ka ce wani zakara?"
"Da gaske nake"
"To ai ban gane ya Ιatan ba ne? Mutumin da yake jinyar ne ya iya tashi ya fita har ya Ιata?"
"Ai kwana biyu jikin da Ιan sauΖi, dan har ya ce mu zo nu gaishe ki" Ta yi maganar ba tare da tana iya tantance me ma take faΙa ba.
"A'a Nana, wataΖila dai wani wajen ya je zai dawo. Tashi ki yi sallar magariba, zuwa anjima a raka ki gidan ko ya dawo"
Nana jin Uwani kawai take yi, ta tashi ta yi sallar magariba, aka yi isha'i. Uwani ta saka Nana a gaba zuwa gidanta, sai dai kamar yadda Nana ta bar gidan wayam babu Sayyid babu dalilinsa.
Nana dai ba ta gaya wa Uwani abin da Ashiru ya gaya mata ba, na ya ga an zo da mota an tafi da shi ba.
Sai wajen goma na dare, hankalin Uwani ya tashi. Ta sanar da samarin gidan halin da ake ciki. Nan suka bazama a cikin Buda yawon neman Sayyid, duk da galibi ma ba su san shi ba, kwatancensa Uwani ta yi musu, suka tafi yawon neman sa, har gurin jami'an tsaro aka kai rahoto.
Sai dai har bayan sha biyun dare, babu wanda ya ji ko Ιuriyarsa.
Uwani ta saka aka rufe gidan, ta ce Nana ta zauna a nan, ko zuwa dare zai dawo.
Nana a ranta ta ce "Wane dare kuma bayan wannan"
Daren ya zame wa Nana dare mafi tsawo a rayuwarta. Damuwa da tunani ya cika mata zuciya. Ba ta tunanin Sayyid zai iya tafiya ya bar ta. Idan kuma da gaske zuwa aka yi aka tafi da shi, to suwaye su ka tafi da shi? Ina suka kai shi, me ya yi musu? Ko dai wani laifin suke aikatawa ba ta sani ba? Amma shi da yake kwance babu lafiya, kullum tana tare da shi a gida, yaushe har yake aikata wani rashin gaskiya da ba ta sani ba.
A haka har aka yi assalatu, a kan kunnenta.
****
Dare malafar rana, kowa ya bika ya shirya maka.
DanΖareriyar mota ce, Ζirar highlander baΖa, take ta kwarara gudu a saman kwalta, tamkar hanyar domin direban kawai aka yi ta.
Gefe da gefen hanyat baki Ιaya babu komai, banda yashin sahara, sai busassun bishiyu jefi jefi. Kasancewar dare ne, wata ya kai kwana goma sha huΙu, ya haska ko ina, ga taurari sun yi wa sararin samaniyar ado.
Titin ta tsakiyar sahara ya ratsa, wadda yashin saharar ya bayar da sassanyan yanayi.
Kallon sa ya yi, daga bisani ya ce "Kilomètre nawa ce ta rage mana ne?"
Direban ya waiwayo ya kalli mai maganar wandaa fuskarsa a rufe take cikin rawani ya ce "Bai fi 95 kilomètre ba"
"Dans quelques minutes ?? (Nan da wani lokaci?)".
"Bai fi awa Ιaya ya rage mana ba"
"Dole fa mu Ζarasa dai-dai lokacin da aka umarce mu, ni ina tsoron ma kar ya farka. Ka Ζara sauri"
Ya yi maganar yana haska fuskar Sayyid, da yake kwance a jikinsa ya haΙa gumi, cikin wani yanayi kamar bacci kamar suma, sai dai yadda yake gumi ya nuna a wahale yake baccin, babu in da yake motsi a jikinsa, sai Ζirjinsa da yake Ιagawa yana sauka lokaci zuwa lokaci, numfashinsa yana fita da Ζyar.
Ya kai hannunsa, ya Ιora a kan Ζirjin Sayyid, idan zuciyar sa ta buga sau Ιaya, sai ta jima kafin ta sake bugawa. Sai dai duk bugawar da za ta yi, da Ζarfi take bugawa tamkar za ta tsaga Ζirjinsa ta fito dummm!.
Cikin damuwa ya ce "Lowalli, sai ka Ζara gudu fa, kar ya mace mana, bugun zuciyarsa raguwa fa yake yi. Kuma ka san idan ya mace mana mun shiga uku mun lalace"
Lauwalli ya jinjina kai yana Ζara gudun motar. Ya ce "In sha Allah a raye za mu kai shi, ba za a samu matsala ba. Dan dai ka Ζi yarda ne, da na ce mu tsaya a Asibiti".
"Kai dalla ka daina maganar tsayawa a wani Asibitin nan. Ka yi ka hanzarta mu cika umarnin nan, mukaΙai ake dako"
"To shikenan, mun kusa in sha Allah" ya yi maganar yana Ζara gudun motar.
****
Antin Yusra ce ta kalle ta, ta ce "Yusra duk wannan kwalliyar fa? Ta karΙar baΖon ce?"
"Eh mana Mami, yana hanya ma ai" ta yi maganar tana tafiya Ιakinta, ta fesa turare.
Wayarta ce ta fara ringing, ta Ιaga wayar tana murmushi ya ce "Gani a layin"
"Duba lambar gidan, za su buΙe maka"
Ya ce "Ok"
Bayan mintuna goma sha biyar, ta fito ta ce "Mummy na tafi"
"To a gaida baΖon, ya tabattar mana da alkhairi"
Kawai ta fice tana murmushi. Tana zuwa ta gan shi a tsaye a cikin falon, yana kallon Ζaton frame na hoton mai gidan, da yake retired soja.
Ganin abin take tamkar a mafarki, wai Sagir Ιin ta ne a gabanta.
Jin Ζamshin turarenta ne ya sanya ya waiwaya.
Da gudu ta Ζarasa inda yake ta faΙa jikinsa.
Babu tunanin komai, Sagir ya ΖanΖame ta a jikinsa, bar siririn mayafin da ta yafa a kanta, yana zamewa gyararren gashin kanta, da yake ta Ζamshin mayuka ya bayyana.
Ya din ga shafa bayanta yana murmushi, kawai ya ji tana sheshsheΖar kuka. A Ιan rikice ya ce "Lafiya, kuka kuma Yusra?"
Ya zauna tare da ita a jikinsa, ya ce "Ina ta murna zan zo na gan ki, amma in zo ki din ga kuka, ko ba kya son ganina ne?" Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To mene ne"
"Ka daina so na, tun da ka sake ni ba ka Ζara nema na ba" Ya Ιago fuskarta su na kallon juna yace "Da na daina son ki, ba zan zo nan ba Yusra, kin san yadda rabuwarmu ta kasance, ban daina sonki ba, ban kuma daina tunanin ki ba"
"Almost three years, ba ka sake nema na ba"
Sagir ya marairaice murya ya ce "To yanzu ba gani na zo har nan saboda ke ba? Haba wifey" ta zumΙura baki cikin Ιabi'arta ta shagwaΙa. Duk da ya zuciyarsa na tunatar da shi, tare da gargaΙin sa a kan Yusra ba muharramarsa ba ce, amma ya kasa yaΖar kansa, ya Ζyale ta a jikinsa yana jin yadda ya yi kewarta.
"Talk mana, na zo kuma kin haΙe rai?" Tashi ta yi daga jikinsa, ta zauna a kusa da shi ta ce "Ya hanya?"
"Alhamdillah, ki na lafiya ya jikin naki?"
"Da sauΖi"
"Kin warware?"
Ta girgiza kai ta ce "Bayan Ζin yadda ku ka yi da gaske ba ni da lafiya. Sai ga shi na haΙu da wata Nana, ita ma tana irin ciwon da nake ji, ai ita ta san ba Ζarya nake yi ba."
Ya ce "To yanzu dai duk ba wannan ba, i miss you Yusra, irin sosai da sosai Ιin nan fa"
"Bayan ka yi aurenka, ba wani missing Ιina da ka yi" ta yi maganar tana tsiyaya masa lemo a cup ta miΖa masa.
Ya karΙa ya kai bakinsa yana tsare ta da ido. Ta kalli screen Ιin wayarsa da ya kawo haske, hoton Haidar ya bayyana a kan screen Ιin. Ta Ιauki wayar tana kallon yaron ta ce "Waye wannan?"
"Ζanki ne Haidar, recently ma ta kuma haihuwa Ιan ya rasu" ta yi masa wani kallo, da bai tantance na mene ne ba ta ce "Da tuni nima wataΖila na haihu"
Ya yi murmushi ya yi shiru, yana cin abincin da ta zuba masa. Cikin hikima ya karkatar da zancen suka ci gaba da hira.
Wayarsa ce ta fara ringing, ta ajiye masa ganin hoton heart a kan sunan. Ya Ιaga wayar tare da yin sallama "Hello love"
"Ka sauka lafiya?"
"Alhamdillah am good dear"
Shukura ta ce "To sai ka dawo, Allah ya tsare mana kai, take care"
Ya yi murmushi ya ce "In sha Allah dear" wani abu ne ya tokare wa Yusra a Ζirji, ta zuba masa ido.
Ya ajiye wayar, bai kalle ta ba ya ce "Yusy, kin san na yi missing Ιin girkinki over?"
Jin ta yi shiru ya sanya ya Ιaga kai ya kalle ta, ya ga tana hararsa. Ya yi murmushi ya Ιebo Abincin ya kai bakinta.
Ta murguΙa masa baki ta tsuke fuska.
"Smile, haba sweetheart" ta buΙe bakin ya saka mata Abincin. Haka ya ribace ta, suka ci gaba da hira.
A nan ya yi sallar la'asar, sannan ta fito raka shi.
A jikin motarsa suka tsaya, tana yi masa wani irin kallo mai Ζayatarwa.
"Tom sai yaushe zan dawo?"
"An jima kaΙan"
Ya yi murmushi ya sake kallon ta ya ce "Yusra"
Ta ce "Na'am"
"Yaushe za ki dawo gidana, ji nake kamar na Ιauke ki, na tafi da ke Kano, ina kewar ki sosai da sosai. Yaushe za ki dawo gidana?"
Ta girgiza masa kai ta ce "Ba zan dawo ba"
Cikin mamaki ya ce "Saboda me?"
"Ka auri wata, kuma Hajiyarka ba za ta bari na dawo ba, su Mami ma ba za su bar ni ba, kuma ma haryanzu ban gama warkewa ba"
"Haryanzu ki na so na?" Ta kalle shi ta sunkuyar da kanta Ζasa.
"Idan ba kya so na, me yasa ki ka nemi lambata, ki ka kira ni? Kuma har ki ka ba ni dama na zo?" Ta sunkuyar da kanta ta ci gaba da murza yatsun hannunta.
"Yusra Sagir Ιin ki ne fa, Ιago ido kalle ni" Kawai ya ga hawaye na bin fuskarta.
"Sagir Ιina, da ya rabu da ni, saboda ba ni da lafiya ba" Ta yi maganar tana sheshsheΖa. Ganin babu kowa a gurin da suke, ya sanya ya janyo ta jikinsa, ya Ιago kanta yana kallon idonta ya ce "Yusra, ki na so na haryanzu?" Ta yi shiru hawaye na ci gaba da bin idanunta.
"Ki na so na har yanzu, shi yasa ki ka neme ni. Dan haka batun ina da aure, Hajiyata ba za ta bari ba, 'yan uwana ba sa son ki, haryanzu ba ki da lafiya, duk ba ta taso ba. Za ki dawo gidana a karo na biyu in sha Allah. Haryanzu ina son ki Yusra"
"Amma...
"Babu amma tsakaninmu, believe me zan dawo da ke gidana in sha Allah" Jikinta ya yi sanyi. Ya cika ta a hankali, ya shiga motarsa. Ta tsaya Ζyam tana kallonsa, shi kansa da kyar ya tafi, tamkar ya Ιauki Yusra ya tafi da ita.
Har ya kama hanyar Kano, zuciyarsa cike da tunanin ta ina zai fara. Dan shi har ga Allah yana son matarsa, ba a son ransa ya rabu da Yusra ba. Yanzu kuma da ya ganta, gaba Ιaya ya Ζara rikicewa ba abin da yake sai tuno soyayyar da suka yi, daga saurayi da budurwa zuwa auren su.
Ko da ya je gida, Shukura ta karΙe shi tana yi masa sannu da zuwa.
Amsa mata ya yi yana kallon ta, kafin ya Ζaraso ta kira shi ya fi sau biyu, yana zuwa hatta ruwan da zai yi wanka ta tanadar masa.
Ya cire kayansa ya shiga wanka, kamar ta san ba zai iya salla ba, sai ya tsarkake jikinsa, saboda rungumar da ya yi wa Yusra.
Tana cikin tattare kayansa, hancinta ya ji Ζamshin turaren da ba na sa ba a jikin kayansa. Turarensa Ιaya ne da ta san shi da shi. Jikinta ne ya yi sanyi, domin ta daΙe da karantar alamomin rashin gaskiya a tattare da shi. Wani abu ne ya soki zuciyarta amma ta yi ta maza ta haΙiye tare da ajiye kayan.
****
Aka shiga kwana na biyar, ba tare da jin ko Ιuriyar Sayyid ba.
Nana duk ta fita hayyacinta, ba ta iya cin abinci, ba ta bacci. Ga Uwani tun tana rarrashinta, ta koma yi mata faΙa tana ganin ta Ζi tawakalli ta ci gaba da addu'a.
Ga shi ta hana ta komawa gidan nasu, a nan gurinta take zaune tare da ita.
Yanzun ma Uwanin ce ta miΖo mata kofi da fura a ciki ta ce "Ungo ki samu ki sha furara nan Nana, ko Ιan cikinki ya samu wani abu shi ma. Rayuwa ba za ta yiwu a haka ba kina zaune babu Abinci, ga juna biyu ba. Idan wani gurin mutumin nan ya tafi, idan da rabo zai dawo ai"
Nana ta karΙi kofin, tana ajiyar zuciya. "Maza ki shanye, kan na fito daga banΙaki" Nana ta jinjina kai tana kallon kofin.
Uwani na shiga banΙaki, Nana ta Ιauki mukullin da aka kulle gidansu, ta tafi.
Gani take kamar tana shiga za ta tarar da shi a inda ta bar shi. Ζofar dama a lanjare take aka rufe ta.
Ta shiga Ιakinsu, amma ta tarar wayam babu kowa a ciki.
Ta kalli kan katifar su, ta ga abin hiraminsa na rawani a kai. Ta durΖusa a kan gwiwoyinta, ta damΖi hiramin nan, da yake ta Ζamshin turaren sa. Tamkar ta damΖi Sayyid Ιin. Cikin kuka ta ce "Haba Sayyid, daga cewa na je na dawo, sai ka tafi ka bar ni? Haba Sayyid yau kwananka biyar ba ka tare da ni. Da mutuwa ka yi na san wannan hukuncin Allah ne, dole na tawakalli, amma me yasa zaka tafi ban san halin da ka ke ciki ba. Haba Sayyid Haba Sayyid Nana ce fa" ta din ga soki burutsu tamkar zararriya. Wani irin kuka take yi mai haΙe da gunji da Ζunar zuciya.
Ba ta san lokacin da Uwani ta shigo ba, tare da abokiyar zamanta Sabuwa ba, sai ji ta yi ta taΙa ta ta ce "Nana shi ne sai da ki ka fito ki ka zo ko? Ba na ce kar ki fito ba?"
"Uwani. Sayyid ya tafi ya bar ni, na zata mafarki nake yi, me yasa zai tafi ya bar ni?"
"Ke ki ji mini 'ya da rashin ta ido, yo ina zan san dalilin da ya sanya ya tafin ni? Ke ba za ki iya dakewa ki kama kanki ba, idan guduwa ya yi fa?"
Sabuwa ta ce "A'a Yaya, su fa yaran birni su na nunawa junansu kulawa, ya za a yi mutum mara lafiya a neme shi a rasa, ki ce hankalinta ba zai tashi ba? Kina kallon yadda take tiri-tiri da shi take nula da abin ta ke kin san ba Ζaramin so take yi masa ba, ai da tausayi"
Uwani ta ce "Kuma haka ne, amma tun da shi ya tafi nima jikata nake yi wa kar wani abu ya same ta, ga ciki. Ke Nana kuma ba garinsu ya tafi ba bai gaya miki ba? Ba kin ce Ιan Nijar ba ne?"
"Ba shi da lafiya fa, ba zai iya wannan tafiyar ba"
"A'a kar ki ce haka, idan ki ka bibiya ma, can Ιin ya tafi, amma yanzu ki yi haΖuri ki tashi mu tafi gida"
"Uwani, dan Allah ki yi mini alfarma ki bar ni na kwana a nan"
"To ya za ki kwana a gida ke kaΙai haka ake yi?"
"Ni dai dan Allah ki bar ni a nan, wallahi da safe zan dawo na yi miki alΖawari"
"A'a sai dai na turo yarinya Ιaya ta tayaki kwana" Nana ta amince da hakan, aka turo mata yarinya.
Tuni yarinyar ta yi bacci, Nana kuma kwana ta yi aikin kuka.
Lokaci Lokaci, sai ta yi tasbihi tare da ajiyar zuciya.
Washegari da sassafe Uwani ta zo ta kawo mata abin karyawa.
Yadda idanun Nana suka kumbura, ya sanya ta fahimci Nana ba ta yi bacci ba.
"Wai ni Nana, babu wani wanda za ki kira, ki tambaye shi ko yaje? Ko kuma wani guri da za ki je a duba?"
Jiki a sanyaye Nana ta girgiza mata kai. "To shikenan sha kunun nan da Ζosai, kar su huce"
Nana ta karΙi kunun tana kurΙa a hankali, ji take tamkar tana shan magani, saboda wani irin Ιaci da take ji kunun yake yi mata a bakinta. Amma saboda ba ta son faΙan Uwani, haka ta din ga shan kunun nan da Ζyar.
Ta Ιan saci kallon Uwani ta ce "Uwani, ina ga gobe in Allah ya kaimu zan shirya na koma Kano"
"Gurin wa?" Uwani ta jefe ta ta tambayar.
Nana ta Ιan yi shiru, Uwani ta ce "Gurin wannan masoron Ubannaki da bai san ciwon kansa ba balle ya san naki? Ya kasa tallafa miki da larura ta samu mijinki, yanzu ne idan kin koma zai tsinana miki wani abu? Ga cikin fari ke ba sanin kan abubuwa ki ka yi ba, ga wannan shu'umar matar tasa, da Ζafa duk dama ba tsayawa za ta yi ta kula da ke ba?. Ban Ζi ba ki kira shi, ki sanar masa abin da yake faruwa a matsayin sa na ubanki ba, amma ba dai ki koma wannan gidan ba. Ki yi zaman ki a nan ki haihu, ki yi biΖinki idan mijin naki bai dawo ba, a san abin yi"
Tabbas Uwani tana da gaskiya, idan ta koma gidansu rayuwarta ta sake komawa baya, ta san babu wani abin kirki ko kulawa da za ta samu a gidan, wataΖila ma a kore ta. Ummi kuma ta yi mata Ιawainiya da yawa, tana jin nauyin ta sake koma mata da matsala.
Kuma ba ta ji a ranta za ta iya sake ko nufar hanyar gidan Alhaji Zailani ba, saboda yin hakan tamkar cin amanar Sayyid ne, kuma ita ba dolensu ba ce, da za ta je ta Ιora musu Ιawaniya. Dan haka Uwani na da gaskiya. Amma zamanta a nan Ιin ma, shi ma dai Ιawainiyar ce.
Ta sake Ιago kai ta ce "To ina son na je Bauchi gurin Mamana"
"Kai Nana ki na da gardama, gurin nawa ne dai ba za ki zauna ba, kin Ζallafa rai tun da mijinki ya bar garin nan kema sai kin bar shi?"
"Ba haka ba ne Uwani, ina da dalili dan Allah ki bani damar hakan"
"Shikenan Nana, ba zan matsa miki ba, Ubangiji Allah ya tabattar da alkhairi, amma ki bari kamar nan da sati Ιaya, ki Ιan Ζara samun nutsuwa. Nima na lalubi na mota na baki"
"Ai ina da kuΙin mota"
"Nima na san ki na da kuΙin motar, na ce zan baki ai" Nana ta ja bakinta ta tsuke.
****
Jamila ta yi shirin fita, tana tsaye tana latsa wayarta ta ce "Baba har ya fita ne?"
Mama ta ce "Tun da uwar kashinsa ta cika ya fita. Da dai bai ci ba da yanzu yana nan yana bin bango yana zabga hamma yana faΙa da Ζadangaru da bokitai"
Jamila ta basar ta ce "Sonake ya bani cikakken kwatancen Buda, zan saka a kai ni, na je na ga Nana"
"Wai ba za ki bar maganar Nanan na ba ko Jamila?"
"Mama meye laifi idan na je na gan ta ne wai?"
Nasiru ya ce "Laaa rannan kuwa wannan Ιan uwan mijin nata, da suka zo a ka kaita gidanta ranar biki, suka zo shi da wasu mutane, suka ce mini wai yanzu Nana a ina suke. Na dawo daga makarantar allo, na ce musu tana Buda can garin su Baba, shi ne ya ce na gaida Baba"
Mama ta ce "Ikon Allah, amma yarinyar nan ta ce 'yan uwansa an neme su an rasa. Kai Nana muguwar makira ce ta Ζarshe"
Jamila ta ce "Amm na tafi sai na dawo"
"To Allah ya tsare, a gaida Hajiyar"
" Za ta ji" ta amsa a taΖaice ta fita.
Nana ta zauna ta haΙa kayan da za ta buΖata a cikin jaka guda Ιaya.
Tattara sauran guri Ιaya, ta Ιauki jakar gurin Sarkin Baka, da kuΙin Nijar Ιin da suke ciki. Ta tattara sauran kuΙin da suke Ιakinta, tana tunanin ta tafi ko da Uwani ba ta sani ba.
Ta tattara kayan kitchen Ιin ta, ta ce wa Uwani sayarwa za ta yi.
"Me yasa za ki sayar da kayan ki Nana?"
"Kawai kuΙin nake buΖata ne"
"Gaskiya ba za ki sayar da kayan nan ba, ki bari ranar kasuwa, zan kai Tinkiyata kasuwa, na baki kuΙin amma ba za a sayar da kayan ba" Gaba Ιaya Nana ta ji ta damu yadda ta Ιorawa Uwani Ιawainiya.
"Uwani kar ki sayar da Tinkiyarki dan Allah, gara a sayar... "Za ki rufe mini wannan dogon bakin naki, ko sai na kwaΙe ki? Ke ki ka sani na sayar? Ke dai akwai gardama"
Babu yadda Nana ta iya, haka ta haΖura sai ranar kasuwa, aka sayar da Tinkiyar. Uwani ta Ιauki dubu talatin a kuΙin ta bawa Nana ta ce "Ban san iya adadin kuΙin da ki ke buΖata ba, amma ga wannan kya jalauta. Dan Allah ki kula da kan ki Nana, duk inda ki ka je idan kin ga akwai matsala, ki dawo mini nan ni zan riΖe ki na kula da ke" Nana ta din ga juya kuΙin, ta kalli Uwani idonta fal hawaye ta ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka miki da mafificin Alkhairi na gode"
"Babu komai, Ubangiji Allah ya sauke ki lafiya, ya bayyana mijinki cikin aminci. Nan ma za mu ci gaba da jiran jami'an tsaro ko za a samu wani labari daga gurinsu. Allah ya bayyana shi"
Nana ta amsa da Amin. Jin washegari Nana za ta bar garin, ya sanya 'yan uwa, suka din ga kawo mata abin alheri cikin mutunci da karramawa, tare da yi mata fatan alkhairi.
Washegari da sassafe, Nana ta yi sallama da su Uwani, aka Ιauke ta a babur aka kai ta tashar Ζauyen. Aka kaita Garko, daga nan ta hau motar Kano. A Kano ta hau motar da za ta sada ta da garin Bauchi.
Tsawon awanni huΙu da aka shafe, ana tafiya a motar, babu abin da Nana take yi, banda tunani ta saΖa wannan ta kwance wancan. Tunaninta a wani hali yake ciki, ya jikinsa? Su waye suka Ιauke shi? Mene ne makomarta idan bai dawo ba.
Lokaci-lokaci ta kan shiga hijjabinta ta yi kuka, ta share hawayenta.
Da ta sauka a tasha Ζarfe sha biyu na rana, ta samu abin hawa, har sunan unguwar da Mamanta take ta sani, sai dai ba ta san takamai ina ne gidan ba. Shi ma daga tashar zuwa garin da maman nata take, sai da aka yi tafiyar awa Ιaya da rabi. Ζafafun Nana duk sun kumbura, da Ζyar take jan su. Ta Ιaukko wayarta ta kira lambar Anty Fati, ta ji ba ta shiga. Ta kira ta Adda Saude ba ta Ιaga ba. Ta nemi guri ta zauna, ta ci gaba da kiran wayar Adda Saude da ita kaΙai take shiga.
Sai dai still ba a Ιaga wayar, ga shi ba ta san daga garin, ina ce unguwar da za ta nufa ba.
Ta samu guri ta yi alwala, ta ciro sallaya a kayanta, ta shimfiΙa ta yi sallar azahar.
Bayan Azahar sosai, Adda Saude ta kira wayar Nana.
Nana ta Ιaga tare da yin sallama. Ta amsa mata ta ce "Nana yi haΖuri, caji na kai wayar ne aka kunna mini, ya ki ke ya gida?"
"Lafiya kalau Adda, kin ganni na zo Bauchi ne na sauka, sai dai ban san sunan unguwar da Mama take ba"
"Ke haba dai, da gaske ki na Bauchi Nana?"
"Eh Adda, na sauka ma tun Ιazu"
"Subhanallah, ai ba ki gaya mini za ki zo ba, da tuni an shirya karΙar ki, ban sani ba an bar ki ki na jira, dan Allah ki yi haΖuri yanzu ki na daidai ina, na zo na tafi da ke?"
Nana ta ce "Kar ki wahalar da kan ki dan Allah, ina garin ma, sunan Unguwar za ki gaya mini" Sai da Adda Saude ta Ιan ji dumm, amma ta maze ta cewa Nana ta samu abin hawa, ta haΙa ta da mai abin hawan ta yi mata kwatance.
Nana ta ce "To" ta samu abin hawa, ta haΙa su ta kwatanta masa, sannan ta hau.
Nana ba ta isa gidan da Mamanta take ba, sai ana kiraye-kirayen sallar la'asar.
Mama na tsakar gida tana ta fama da yara, kawai ta ji sallamar Nana. Ta Ιago da hanzari, sai dai ta kasa amsa sallamar ta nufi Nana da sauri suka rungume juna su na kuka.
Ta Ιago Nana ta ce "Nana ba ki yi fushi da ni ba?"
Nana ta girgiza kai ta ce "Ban yi ba"
Ta ja hannun Nana zuwa Ιaki, ta saka yaran su shigo mata da Ζatuwar jakarta.
"Sannu da zuwa, tare ku ke da mai gidan naki ne?" Nana ta sunkuyar da kai jikinta a sanyaye ta girgiza kai alamar a'a.
"To yana ina shi?" Nana ta yi shiru.
Cikin tashin hankali Mama ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Nana ba dai auren naki ne ya mutu ba?" Nan ma ta girgiza kai hawaye na bin fuskarta.
"Shikenan, yanzu nutsu. Bari na Ιora miki ruwa ki yi wanka, sai ki yi salla" Nana tana iya ganin tsantsar farinciki a kwance a fuskar mahaifiyarta. Ζannenta suka kewaye ta, Nana ta din ga kallon su cike da so da Ζauna. Har gara Walida ta Ιan santa sauran kuwa duk ba su san Nana ba.
Ruwa mai Ιumi ta haΙa wa Nana, ta yi wanka, ta yi sallar la'asar.
Ta zubo wa Nana lafiyayyen Abinci, duk da yadda ranta ya biya a kan Abincin, amma ta kasa sakin jiki ta ci.
Mama ta din ga kaiwa tana komowa, tana ta Ιawainiya da Nana tamkar ta goya ta, sai ta ji ina ma tuntuni ta samu irin wannan kulawar ta uwa.
"Nana ina Imrana kuwa, ya daina zuwa gaba Ιaya"
Nana ta ce "Lagos yake tafiya neman kuΙi"
Ta yi ajiyar zuciya ta ce "Ai shikenan, ya aka yi ina mijin naki ne? Me ya faru?"
"Nemansa na yi na rasa"
Cikin rashin fahimta ta ce "Kamar yaya?"
Nana tana kuka ta yi mata bayani. Cikin mamaki ta ce "To ina 'yan uwansa? A ina yake a Nijar Ιin?" Sai a lokacin ta fayyace wa Maman komai, game da auren zuwa Ιatan sa.
"Nana, me yasa baki neme ni kin gaya mini ba? Yanzu duk wannan abin yake faruwa amma idan muka yi waya sai ki ce mini komai lafiya Ζalau? Ni kaina nan kina raina, ina ta fafutuka na ga yadda zan yi na zo na gan ki. Ba ki kyauta ba Nana, komai lalacewata, ni mahaifiyarki ce, yakamata a ce kin sanar da ni.
Yanzu dai ki zauna a nan, mu ga abin da Allah zai yi, kafin ki haihu mu gani ko Allah zai sanya a ga mijin naki. Amma na yi mamaki matuΖa da mahaifinki ya aura miki wanda bai san usulinsa ba? Yanzu Ζiyayyar da yake yi minin har ta kai haka?
Ko yana jin haushina amma ai ke 'yar sa ce, bai cancanci ya yi miki haka ba, amma babu komai.
Nana abin da nake so da ke, daga yanzu duk abin da ya faru Nana, ko ba zan yi miki komai ba, ki sanar da ni, ki bani dama na taka rawa ta ta uwa a rayuwar ki ko yaya ne" Ta yi maganar tana riΖe hannun Nana.
Sallamarsa ce ta tilastawa Nana haΙiye abin da take shirin furtawa, cike da tsoro.
Ba ita ba hatta Maijidda, sai da zuciyarta ta buga da Ζarfi cike da tsoro.
AYSHERCOOL
08081012143
61
Har zai gifta, zai shiga Ιaki ya hango Nana, cikin rawar baki, Nana ta gaishe shi, ya amsa mata sama-sama ya wuce, dan kallo Ιaya ya yi mata, ya gane ta.
Jiki a sanyaye Maijidda ta tashi ta bi shi Ιaki, tana Ιan sinne kai, tana jiran ta ji me zai ce, amma bai ce komai ba. Ta kawo masa Abinci, tana jiran ta ji me zai ce, ga hankalinta a kan Nana, tana so ta je ta yi hira da 'yar ta, su yi hira ta ji Ιuminta, amma ta haΖura.
Nana ma na ta gaban ne yake faΙuwa, tana tsoron abin da zai ce, saboda ba ta manta karan battarsu.
Haka dai a Ιarare suke hira da yaran gidan.
Maijidda na ta son yi masa magana, amma ta kasa.
Ya gama cin abincin ya fita, ba tare da ya ce komai ba.
Yana fita ta koma gurin Nana, suka ci gaba da hira, Nana ta kwanta a kan cinyar Mamanta, tana jin wani irin farinciki yana ratsa ta.
"Kin fara zuwa awo ne Nana?"
Wata irin kunya ta kama Nana, ta Ιan sinne kai ta girgiza mata kai. "Gaskiya yakamata, wata nawa ne cikin? Mu je a yi awo a duba, mu ga abin da zamu fara ajiyewa. Mu jira mu ga ikon Allah, idan an ga mijin naki shikenan, idan ba a gan shi ba kuma, ma san abin yi" Nana dai ta yi shiru, sai kuma ta ce "Mama ki yi mini addu'a, ki ce Allah ya bayyana shi cikin aminci"
Mama ta yi dariya, ta ce "Lallai kam, to shikenan, Ubangiji Allah ya bayyana mini sirikina cikin aminci"
Nana ta yi murmushi, dan kunya ce ta kama ta daga baya, da tuna katoΙarar da ta yi.
Da daddare Mai Jidda ta yi wa Nana shimfiΙa, ta saka nata net. Sannan ta tafi nata Ιakin gurin mijinta, har za su kwanta, Mai Jidda ta dubi Iliyasu, jiki a sanyaye cikin ladabi ta ce "Baban Walida, na ga ka dawo ka ga Nana a gidan nan, ba ka ce komai ba"
Ya dube ta ya ce "To me ki ke so na ce?"
"Ahh dama kar ka ce ban gaya maka ba ne, dama ta Ιan zo ta zauna da ni ne, duba da yadda...
"Kin ga dakata, na Ιaga miki Ζafa ne na yi shiru, na ga gudun ruwanki, kar ta wuce mini gobe a gida, ta wuce ta koma inda ta fito"
"Dan Allah ka yi haΖuri Baban Walida, Nana ta samu matsala a aurenta ne, dan Allah ka yi haΖuri ba za ta daΙe ba, amma dan Allah kar ka ce ta tafi yanzu. Ni ko ruwan gidanka ka ce ba za ta sha ba, na amince dan Allah"
"Ke Maijidda, bari ki ji na gaya miki, wallahi sai yarinyar nan ta bar gidan nan"
Ya nemi guri ya yi kwanciyar sa, takaici ya ishi Maijidda.
Nana kuwa tana jiyo hayaniyar su sama-sama, abin ya tsaye mata ta kasa bacci sam. Sai juye-juye, ga mararta ta Ζulle duk jikinta ma ciwo yake yi mata.
****
Kwance yake a kan gadon Asibiti, jikinsa babu riga, sai dogon wando an rufe iya Ζafafuwansa da koren yadi. Ζirjinsa kuma an manna masa abin ECG. Sai gashin sa a rufe da hular Asibiti. Na'urorin gefen gadonsa sai sauti suke fitarwa.
Dattijo ne a tsaye a kansa, dogo fari tas, ya Ιaura hirami a iya kansa, ga gemunsa dogo duk farin gashin furfura a jiki.
Ya kalli mutumin da yake tsaye ya ce "mΓ©decin (Likita) yanzu mene ne abin yi?"
"Eh, gaskiya za a yi masa wannan allurar ne kamar yadda na yi maka bayani, idan kuma ba haka ba, gaskiya sai dai a saka masa na'ura a zuciyarsa wadda za ta din ga taimakawa bugun zuciyarsa"
Na kusa da Dattijon mai sanye da shuΙiyar shadda, da babbar riga, kansa ya yi naΙi da baΖin rawani ya ce "Ka gani ko Sultan, Allah kaΙai ya san abin da suka yi masa a Nigeria. Dole yaron nan ya ΙanΙana kuΙarsa a ci gaba da tsare shi, har sai ya yi bayanin abin da ya yi masa a Nigeria, da aka neme shi aka rasa tsawon wannan lokacin. Su kan su sauran da aka kama su tare, dole a killace su a guri Ιaya, haryanzu ban bari an sake su ba, saboda idan maganar nan ta fasu akwai matsala"
Sultan ya numfasa cikin damuwa ya ce "Ni wannan bai dame ni ba, na bar ragamar komai a hannunka, ni lafiyar sa ce a gabana yanzu. Likita ku yi duk abin da ya dace kawai. Lafiyarsa ce damuwata a halin yanzu"
Likitan ya ce "In sha Allah" Dattijon ya saka hannunsa a cikin na mara lafiyan,yana kallonsa cikin matsananciyar damuwa. Kamar mafarki ya ga yana motsawa a hankali, sai ya Ζara tattara hankalinsa a kansa yana kiran sunansa.
Wata irin miΖa ya yi, yana ΖoΖarin buΙe idanunsa, amma ya ji tamkar an cika masa idanun nasa da barkono.
"Imam..
Hannunsa ya Ιora a ka yayi wata irin kururuwa, jin yadda naman jikinsa yake yi masa wata irin azaba, tamkar ana cizgar naman jikin nasa. Ga wani irin zafi da raΙaΙi da yake ji kamar yana cikin wuta.
"Zafi! Wayyo wuta Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wuta zafi jikina"
Kansa suka yi gaba Ιaya cikin tashin hankali, su na ΖoΖarin rirriΖe shi, amma ya watsar da su ya diro daga kan gadon, yana girgiza kansa da yake yi masa wata irin azaba tamkar zai tarwatse. Tunaninsa ne ya hargitse gaba Ιaya, ΖwaΖwalwarsa na ta kokawar Ζwato wani abu daga cikin memories Ιin sa, amma abu ya kacame, gaba Ιaya tunaninsa ya hargitse, ya kasa tantance komai. Fizge-fizge ya din ga yi yana kururuwa jikinsa na rawa. Dattijon nan cikin jarumta da Ζarfin hali, ya bi shi da sauri ya damΖe shi iya Ζarfinsa.
Kokawa suka din ga yi, a rikice likita da Ιaya mutumin suka yo kansu, likitan ya haΙa wata allura ya yi masa. Jikinsa ya saki a hankali bacci ya Ιauke shi. Kan gadon suka mayar da shi suka kwantar. Ζaya mutumin ya kalli likitan ya ce "Ka na ji na?" Likitan ya jinjina kai cikin nutsuwa.
"Ka san dai waye wannan, kuma ka san matsayinsa da girmansa ko?" Ya yi maganar yana nuna masa mara lafiyan.
Ya jinjina kai ya ce "Na sani"
"To muddin mu ka ji maganar abin nan da ya yi, ya fita waje, to ba wani ba ne ba kai ne, dole ka yi shiru da bakinka, kare sirrinsa wajibi ne a kan duk wani wanda yake yankin nan, idan kuma aka samu akasi ka furta wani abu, da rayuwarka za ka biya"
Likitan yana tsuma ya ce "In sha Allah ba zan faΙa ba"
****
Da safe mijin Maijidda ya shura takalmansa ya fice, bayan sun gama jayayya da ita, tana ta roΖonsa tana yi masa magiya. Gaba Ιaya Nana ta ji dana sanin zuwa Bauchi da ta yi.
Babban abin da ya bata mamaki, Ζatuwar kaza Maman ta saka aka yanka, ta gyare ta tsaf, ta yi wa Nana farfesunta, aka sayo mata Ζaton buredi ta haΙa mata shayi.
"Mama daga zuwana na Ιora miki Ιawainiya, ba ma na iya cin Abincin ni"
"Ζawainiyar Ζaniyarki, da can na yi miki ne Nana? Dan Allah ki daure ki mayar da hankali ki ci ki Ζoshi, idan kuma ki na son cin wani abin, ki gaya mini sai na dafa miki"
"A'a ba na son cin komai, amma ki zo mu ci tare da su Walida"
Maijidda ta ce "A'a, babu wanda zai ci, da rana ma ci Abincin tare, wannan dai na ki ne" Haka ta takura Nana, ta karya.
Nana ta fito da nufin, ta kama musu ayyukan gida, amma Mama ta hana, ta dafa mata ruwa ta yi wanka. Ta fito ta tarar Mama tana wanke kayan da ta cire.
"Haba Mama dan Allah ki bari na wanke da kaina, ya za ki din ga yi mini wanki?"
"Tafi Ιaki ki je ki zauna ki huta, ga lemon fata can da rake, ki Ιan sha saboda ΙanΙanon bakinki. Akwai riΙi ma mai gishiri da mai suga, idan da wanda ki ke so" kawai Nana ta tsaya tana kallon ta, tana murmushi.
Maijidda ta ce "Ya dai?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba komai Mama, na gode sosai"
Nana ta shirya ta canza kaya, Khadija da take 'yar autar Mama, Nana ta kama ta tana tsefe mata kai. Ta Ιauki wayar Nana tana kallon hotuna. Sai ta buΙe wani video da Nana ta yi wa Sayyid, ta yi masa kitso sai hararta yake yi tana cewa "Ka ga yadda ka yi kyau 'yan matana, yi murmushi mana" ya Ιago kansa ya hargitse idanunsa. Nana tana dariya. Sai da tsigar jikin Nana ta tashi, gani take kamar ta shiga cikin wayar ta ga Sayyid Ιin ta.
"Anty Waye wannan?"
"Mijina ne" ta ba ta amsa tana murmushi.
"Ya na gan shi da kitso, kuma fari?"
Nana ta yi dariya ta ce "Ni kuma baΖa ko?"
"Eh, kuma ba kyau maza su yi kitso fa"
"Wai in ji wa? Ba ki ga gashin nasa ne da yawa ba?"
Khadijah ta ce "Eh, to yana ina yanzu?"
"Ya je unguwa, zai dawo ya Ιauke ni mu tafi"
"To ki nuna mini shi idan ya zo" Nana ta ce "To in sha Allah"
Mama ta ce "Ke Khadijah, tashi ki bar ta ta huta, Nana kwanta ki huta, ki rabu da surutun yarinyar nan"
Khadijah ta tashi tana zumΙura baki, Nana ta Ιan kashingiΙa kawai wani abu mai kama da bacci ya yi awon gaba da ita, kasa tantance ma me take yi ta yi, bacci ne ko kuma ido biyu.
"Ma Vie" ta ji muryarsa a kunnenta. A razane ta waiwaya cikin damuwa. A tsakiyar sahara ta hange shi ta ce "Sayyid"
Ganinsa ta yi a tsaye a kanta, kayan jikinsa duk a yayyage, ya yi baΖi kamar ya Ζone, gashin kansa a hargitse jikinsa sai fitar da hayaΖi yake, ya ce "Ma Vie sun mayar da ni inda za su kashe ni, dan Allah ki zo kar su kashe miki ni." Yayi maganar yana hawaye.
Ta tashi cikin tashin hankali ta ce "Suwaye? Kuma a ina suke?"
"Dan Allah ki zo, ni ban san su ba, amma na san mutuwa zan yi, dan Allah Husnah ki zo gurina, za su kashe ni. Idan kuma sun kashe ni, ki kular mini da Ιa na"
"Sayyid, dan Allah kar ka tafi ka bar ni, dan Allah Sayyid ka dawo? Ka gaya mini kana ina, sai na zo na same ka na tafi da kai"
Guguwar Sahara ce, ta taso ta turnuΖe gurin.
Nana ta din ga tari, muryar Mama ta ji a kanta tana faΙin "Tari ki ke haka Nana?"
Kawai ta ga Nana ta tashi, ta yi waje. Ta riΖe ta ta ce "Ina za ki ke?"
Idanunta a rufe, fuskarta a murtuke ta ce "Ba ki ji Sayyid ne yake kirana ba?"
"Waye hakan?"
"Mijina mana" ta faΙa a fusace.
"A'a babu wanda ya kira ki fa"
Nana ta fara ΖoΖarin fizge hannunta ta ce "Yanzun nan fa ya fita daga Ιakin nan"
"Nana babu kowa fa a gurin nan, daga mu sai ke"
"Ni ki cika ni, na ji Muryar mijina gurinsa zan je yana kirana"
Tsawa ta daka wa Nana ta ce "Ina magana ki na Ιaga mini murya? Wuce ki zauna babu wani wanda yake kiran ki" Nana ta buΙe idanunta, ta kalli Mamanta, sai dai ba ta yi magana ba, kawai ta ga Nana ta yi baya za ta faΙi. Ta riΖe ta ta kwantar da ita. Jikin Nana ya hau karkarwa, idanunta na fitar da hawaye.
Cikin matsananciyar damuwa take kallon Nana, tana tunanin dama har zuwa yanzu, tana fama da larurar nan?.
Ta rungume Nana a jikinta, ta kama goshinta, ta fara karanta mata Suratul Jinn, tana tofa mata a fuskarta. A hankali jikin Nana ya saki ta fara bacci.
Ta yi shiru tana kallon fuskar Nana, tana tuna lokacin da take rungume da ita tana jaririya, cike da so da Ζauna. Tare da tuno irin soyayya da rawar Ζafar da Isa ya din ga yi lokacin da aka haifi Nana, ba ta taΙa tunanin zai yi wannan riΖon sakainar kashin da rayuwar Nana ba.
Adda Saude ce ta yi sallama, Mama ta amsa mata.
Ta Ιan yi turus ta ce "Ya dai Nanan ba ta da lafiya ne, na ganta a kwance a jikinki haka?"
"Wallahi kuwa, shigo daga ciki" ta zauna ta ajiye kayan da ta zo da su. Ta ce "Tun jiya na so zuwa, tun da muka yi waya da ita da ta ce mini tana garin nan, babansu ne baya nan bai dawo da wuri ba ga yara gidan babu kowa. Ikon Allah ciki ne ma da ita haka?"
"Ga shi nan dai, har ya yi girma ma"
"Ikon Allah, na yi mamaki da na ji zuwa ta yi babu sanarwa, tare da mijin suka zo?"
Maijidda ta numfasa ta ce "A'a, matsala ma aka samu, ba a san inda mijin nata yake ba"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, garin yaya ina ya tafi?"
"Wallahi ban sani ba, na dai ce ta zauna a nan, kafin nu ga abin da Allah zai yi. Ashe rashin lafiya ya sha, yarinyar nan ba ta taΙa gaya mini ba. Ga babanta bai karΙe ta ba, Ζarshe ma sai Buda ta koma ta yi jinyarsa, kuma dai ma ya tafi ba a san inda yake ba"
Cikin jimami Saude ta ce "Kai subhanallah, abin nan bai yi daΙi ba, yanzu meya same ta haka?"
"Iska ne ya buge ta, na ba ta abinci ta karya, ta fara bacci kawai ta tashi wai mijin ne yake kiranta. Ashe haryanzu tana fama da wannan matsalar. Wallahi Adda na yi dana sanin biye wa Iliyasu na watsar da yaran nan." Ta yi maganar hawaye na cika mata ido.
"Ki yi haΖuri, amma yanzu ya ku ka yi da shi?"
"Hmm mu na nan muna ta bugawa, wai sai ta bar gidan nan, ni kuma Nana ba za ta bar gidan nan ba, sai dai mu tafi tare"
A Ιan tsorace Adda ta ce "A'a Maijidda, idan da matsala, a kaita gidan Fati tun da tana da yalwar guri, ko gurin Yakumbo,kar ku samu matsala"
Ta girgiza kai ta ce "Ni na ke son kula da Nana da kaina. A cikin su ban san wanda zai ji Ζan wani ba, dukkaninsu su na buΖatata".
Nana ta farka tana Ιan yin miΖa, ta cewa Maijidda fitsari za ta yi, ta raka Nana banΙaki ta je ta yi fitsari, ta saka ta ta yi alwala ta koma ta kwanta.
Har zuwa yamma Adda na gidan, sai daf da magariba ta tafi, Nana kuma ta wartsake sai ciwon jiki da mararta da ke Ιan murΙawa.
"Nana, ranar Litinin in sha Allah za mu je Asibiti, a fara yi miki awo, kuma zan duba gurin masu magungunan islamic Ιin nan, mu je a duba ki" Nana dai ta yi shiru ba ta ce komai ba.
Da sallar Isha'i, Baban su Walida ya dawo, tun da ya hangi Nana a Ιaki, ya turnuΖe fuska ya kalli Mai Jidda ya ce "Me na ce miki a game da yarinyar nan?"
"Baban Walida, ba a yi wa Ιa mugunta, dan Allah ka yi haΖuri ka bar Nana a gidan nan, ka ga 'yan uwanta ma duk ba su santa ba, ba su saba ba. Kuma ba a san me gobe za ta haifar ba. WataΖila ita ce mai tallafar rayuwar Ζannen nata nan gaba."
"Ni ba nusari ne kamar ubanta ba, ni zan tallafi rayuwar 'ya'yana. Ba na buΖatar ko sisinta a kan yarana. Ta koma gidan mijinta ko gidan ubanta, idan ba haka ba sai dai ki zaΙa, ko ta bar mini gida, ko kuma auren ki."
Kafin ya rufe bakinsa ta tari numfashinsa ta ce "Na zaΙi 'ya ta, zan tafi tare da Nana, ko a daji ne na rayu da ita na kula da ita. Tun da ba dan wahala da bautarka da ta 'ya'yanka kawai Allah ya yi ni ba. Ba ka da kara Iliyasu. Nan har 'ya na riΖe maka na aurar da ita ban yi mata mugunta ba. Har 'ya'yan 'yan uwanka ka kawo mini na riΖe, ban taΙa muzguna musu ba, na riΖe maka, nawa 'ya'yan ne na banza kenan? Ζiri-Ζiri Ιan da na durΖusa na haifa ya tsane ni, saboda yana ganin na kawo su Duniya amma ban damu da su ba. Su 'ya'yan da na riΖe maka haifar su na yi? Ko kuma dolena ne su, ni 'yar guda Ιaya ka gaza yi mini kara a kanta? To ka sani duka yau duka gobe shi ke sanya baΖin ba'auzine yin tawaye. Zan zube maka yaranka na Ιauki 'ya ta na tafi da ita, na kula da ita. Ka kwaΙa gidan ka cinye da kai da 'ya'yan naka"
Cikin matsanancin mamaki ya ce "Maijidda, ni ki ke gaya wa wannan maganganun?" Cikin Ζunar rai ta ce "Na faΙa Ιin, shekara nawa na rayu da baΖin cikin rashin ganin 'ya'yana, kullum na motsa zargina ka ke da tsohon mijina. Ζaddarar haihuwar yaran nan biyu ta sanya ban aure ka da fari ba na fara auren sa, amma a kan dalilinku marasa tushe balle makama kun azabtar da ni da nesan ta ni da yarana. Wallahi wannan karon na zaΙi 'ya ta"
Kamar zubar wuta, haka Nana take jiyo cece kucen su. Dana sanin zuwa gidan ya cika mata zuciya. Tabbas ba za ta so mahaifiyarta ta kashe aurenta, da wannan gayyar 'ya'yan saboda ita kaΙai ba, idan ta bari hakan ya faru ba ta yi musu adalci ba baki Ιaya. Zurfin tunanin da ta tafi, bai bari ta gama jin yadda rigimar ta su ta kaya ba. A cikin daren bayan gari ya yi tsit, ta tashi ta haΙa kan kayanta cif.
Ta laluba jakunkunan yaran na makarantar boko, ta samu biro da takarda ta yi rubutu, ta ninke ta ajiye a kan katifar ta.
Da Asuba, Mama ta zo ta tashe ta, ta yi alawala ta yi sallar Asuba. Ganin yaran na Ιaya Ιakin su na salla, Mama ma tana bedroom Ιinta, tana salla, ya sanya ta lallaΙa ta Ιauki jakarta ta fice daga gidan.
Ta din ga zumbuΙa sauri, tamkar za ta tashi sama, ga faggon kaya. Tafiyar Ζafa ta ci sosai da sosai, har sai da gari ya yi haske, masu abin hawa suka fara fitowa, ta tari wani ta ce ya kai ta tasha. Yana kai ta tasha, ta yi sa'a an yi lodi saura gurin mutum biyu, tare da wata mata suka shiga tasha suka nufi babbar tashar Bauchi.
Daga babbar tashar Bauchi, ta hau wata motar, duk da zuciyarta na raya mata kamar matakin da ta Ιauka ya yi tsauri, wata zuciyar kuma na raya mata shi ne mataki mafi cancanta da za ta Ιauka, mussaman idan ta tuna yanayin yadda ta yi mafarkin Sayyid.
Wayarta ta ciro, ta shiga lambar Ummi, ta rubuta mata saΖo, sai da ta tabattar ya tafi, sannan ta kashe wayar, ta cire layinta daga cikin wayar.
Gari ya Ιan fara haske, Baban su Walida ya fice, a matuΖar zuciye, ya yanke shawarar tafiya ya kai Ζarar ta, tun da dama ya san ya saba samun goyon baya, ba ga taΙa kai Ζararsa ba, amma shi ya kai ta ta, ya fi sau shurin masaΖi.
Su Khadija har sun fara Ζiriniya a tsakar gida, a zuciye kasancewar da takaicin ubansu ta kwana ta daka musu tsawa, ta ce su koma Ιaki, kar su tashi Nana. A zaton ta Nana tana cikin Ιaki tana bacci.
Jamila ce zaune a gidan Ummi, tana jajanta abubuwan da suka faru da Nana, ba tare da ta san ma hakan ya faru ba.
"Wallahi Ummi da an sanar da ni zancen matar nan, da suka ce Nana mayya ce, wallahi da sai na saka an rufe ta, sai na ja shari'a da su har gaban AlΖali, sun san girman sharrin maita kuwa?"
"Hmm ke dai a yi sha'ani, ga shi Nana ta bar gidan, amma an ce Haryanzu tana kwance babu lafiya matar, ni na fi tunanin ko Aljanun Nanan ne suka yi mata wani abin, tun da ta ce Nana take gani. Jamila wayar Nana fa ba ta shiga, ni kaina sai na shafe sati biyu ban yi magana da ita ba, saboda garin babu network. Haka nan za mu tafi kawai."
Ummi ta shirya, da Jamila Abba ta so ya kai su, sai ta yi wani tunani ta fasa, dan ba ta san a yanayin da za su je su tarar da su Nana ba.
Sai dai Ummi ta sha mamaki da suka isa garin, suka tarar da gidan Nana a garΖame.
"Ikon Allah, ita kuwa Nana ina tafi haka? Ko sun je Asibiti ne?"
Jamila ta ce "Asibiti yau Asabar?"
"To maybe emergency suka je, kin san matsalar Zuciya yake fama. Mu Ζarasa gidan Uwani".
Suka zagaya gurin Uwani, ta yi murna sosai da sosai da ganinsu, sai dai ta hau Jamila da faΙan ba sa zuwa sai yanzu, da yake Nana ce a garin.
Ummi ta yi ta bata haΖuri, ta ce sun zo duba Nana ne, sun tarar da gidan a rufe.
"Ohh abin tsiya, ba ma kwa bibiyar halin da take ciki, to Nana tun shekranjiya ta bar Buda, mijinta aka nema aka rasa ko sama ko Ζasa sama da sati biyu, ta ce mini gurin Babarta za ta tafi a Bauchi, babu yadda ban yi da ita mu yi zamanmu da ita a nan, amma fafur ta ce in Ζyale ta, tafiya za ta yi".
Jamila ta ce "DanΖari"
Ummi kuwa "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" kawai take maimaitawa.
"Amma me yasa Nana ba ta dawo gida ba, sai ta tafi Bauchi, bayan ta san halin Baba"
"Baban wofi, uban me zai tsinana mata, ko ta je gurin nasa"
Suka gama jimamin da za su yi, suka tashi suka tafi.
Jamila ta ce "Anya Ummi mu gaya wa Baba kuwa?"
Ummi ta ce "Tun da shi ya haife mu, ba dole a gaya masa ba. Wallahi duk cikinmu babu wanda ya sha azabar ds Nana take sha a rayuwarta, da kin ga yadda take shan wahala da mutumin nan, sai kin tausaya mata, gaskiya idan guduwa ya yi ya bar ta, bai yi wa kansa adalci ba."
Suka ci gaba da jajanta lamarin.
Da suka shigo gari, Jamila ta tafi gida, Ummi ma ta tafi nata gidan.
Mama na ganin Jamila ta dawo, ta fara yi mata tambayoyi, amma Jamila ta yi burus, ba ta gaya wa Mama komai ba.
****
Tare da Kawun Mai jidda Iliyasu ya dawo, yana ta faman bambamin ta lalace, abin da ta ga dama shi take aikatawa.
Sai kuma Adda Saude da suka taho tare, dama sai da ta yi tunanin a samu matsala saboda zuwan Nana.
Suka tarar da Maijidda idanunta jawur, fuskarta babu annuri.
Suka zazzauna a falonta, kawunta ya dube ta ya ce "Mai Jidda ban san ki da rashin ji ba, me yake faruwa ne?"
Jiki a sanyaye ta miΖa masa takardar da Nana ta bari a kan shimfiΙarta.
"Wannan Ιin na mene ne?"
"Ku duba" ta yi maganar hawaye na zubo wa daga idonta.
Adda Saude ta karΙa, ta buΙe takardar "Assalamu alaikum, na san lokacin da za ki ga takardata, na riga na yi nisa. Mama ina mai baki haΖuri da matakin da na Ιauka ban sanar da ke ba. Ba zan so a dadlilina nikaΙai ki bar Ζannena ba, dan Allah Mama ki yi haΖuri ki zauna da su. Na tafi neman mijina, a bawa baban su Walida haΖuri, amma kwana biyun nan da muka yi tare, ya fi kowane kwanaki yi mini daΙi a rayuwata na gode sosai Nana Asma'u"
Shiru suka yi bayan da Adda Saude ta gama karanta rubutun, sai sautin kukan Maijidda da yake tashi. Cikin kuka ta ce "Shekara nawa ina yi masa kara, na riΖe nasa 'ya'yan? Amma ni sau Ιaya ya gaza yi mini kara, 'ya'yana sun tsane ni, a kan laifin da ba su suka yi ba, bai yadda su zo inda nake ba, nima kuma ba zan je ba. Idan na yi magana a ce na yi haΖuri, yarinyar nan ga tsohon ciki ina za ta tafi? Mijin da ita kanta ba ta san a ina yake ba" ta Ζarasa maganar tana Ζara rushewa da kuka. Kawu cikin sanyin jiki ya ce "To ita Nanan ya aka ta tafi babu sanarwa?"
"Tun da ta zo yake masifar sai ta bar gidan nan, babu irin magiyar da ban yi masa ba, amma ya din ga Ιaga murya yana bala'i, gaskiya bayan Nana zan bi, ko zan ganta, ban san ina za ta je ba, da ta fita da tsohon cikin nan"
"A'a ba za a yi haka ba, ki yi haΖuri Mai Jidda, rashin kyautawa Iliyasu ba ka kyauta ba, shi Ιa na kowa ne. Kuma tabbas mun daΙe mu na tausar ta, a kan ra'ayinka, ba tare da ba ta damar jin ta bakinta ba. Ka san raΙaΙin da yake cikin raba Ιa da uwa kuwa? Ba ka kyauta ba"
Cikin kuka ta ce "Kawu dama ya bani zaΙi, na zaΙi 'ya ta, ya sauwwaΖe mini na fita na nemi yarinyata"
Kawu ya ce "A'a ba za a yi haka ba, duk inda Nana take yanzu ta yi nisa, kuma idan aka Ζyale ki, ke kan ki ba ki san ina za ki nufa ki neme ta ba. Amma tun da ba yarinya ce Ζarama ba, na san duk inda take Allah zai kare ta, ki ci gaba da yi mata addu'a. Na san ina sha Allah, babu abin da zai same ta, amma batun ki ce ki kashe aure, ki bi ta ki zauna da ita ba mafita ba ce ba, haΖuri kin saba yin sa, a wannan karon ma shi Ιin dai zan baki, na san duk wanda aka ce wa ya yi haΖuri an zalunce shi ne, amma dai ki yi haΖuri.
Kai kuma Iliyasu magana ta domin Allah, ba ka yi kara ba, ba ka kyauta ba ko kaΙan. Yaran nan saboda halinka sun daina zuwa inda take tsawon shekaru, amma daga zuwan yarinyar ka hau bala'i har ta ji, ta yanke wannan hukuncin. Ina kai auren Ζanwarka ne ya mutu, mijinta ya Ζi riΖe 'yar ka karΙo ka kawo mata ta riΖe maka? Har zama fa ta yi da Ζanwarka ta riΖe maka kan ta sake wani auren, amma kai ka kasa yi mata kara, a kan yarinya guda Ιaya tal".
Iliyasu ya zata a wannan karon ma, za a goya masa baya, kamar yadda aka saba tsawon shekaru goma sha, sai dai ya ji wannan karon ba a goyi bayansa ba, sai ya yi tsuru-tsuru, dan haΖuri tabbas ya san Mai Jidda na da haΖuri da kawaici. Kawai ya tsani babansu Nana ne, saboda yadda aka fasa aurensa da ita, ta aure shi, shi yasa tsanar ta shafi su Nana.
Haka aka din ga ba ta haΖuri, Kawunta ya yi ta rarrashinta.
Nana tana zaune a cikin mota, daga jikin taga, tana kallon hanya, yadda ake ta kwarara gudu a motar, tamkar direban zai tashi sama. Gudun da motar take yi, bai dame ta ba, fatanta Allah ya sanya matakin da ta Ιauka, ya zama alkhairi a gare ta.
Duk da ta san Nijar ba gida ne ba, ba unguwa ba ba kuma Ιan Ζaramin gari ba, Ζasa ce sukutum, mai Ιauke da garuruwa daban-daban da Ζabilu masu tarin yawa, balle kai tsaye tana zuwa ta doshi inda za ta gan shi. Duk ba abu ne mai sauΖi neman mutumin da ko ainihin sunansa ba ta sani ba a gari kamar wannan, amma tana jin a ranta motsi ya fi laΙewa, kuma rashin jini rashin tsagawa. Wannan shi ne mataki na Ζarshe da za ta iya Ιauka domin nemawa kanta mafita. Ta yarda da cewa SarΖar, Ζaddara ce ta haΙa ta da Sayyid, ta yi wa rayuwarta dabaibayi, mussaman da ya tafi ya bar ta da ajiyarsa a tare da ita. Sai dai bayan wannan tana cike da zullumin halin da yake ciki, saboda ta san kaso mafi yawa na mafarkin ta ya kan zama gaske, a jikinta take jin duk a inda yake, yana buΖatarta a kusa da shi.
Hankalinta ne ya dawo jikinta, bayan da ta ji ana cewa, an tsallaka boda sun shiga Ζasar Nijar!.
AYSHERCOOL
08081012143
62
Jamila na Ιaki tana jiyo maganar Baba ya dawo, ba ta fito ba, sai da aka jima sannan ta fito tsakar gida.
Ya ce"Jamila kun dawo ashe? Yaya ku ka baro Nanan?"
Jamila ta yamutsa fuska ta ce "Bamu tarar da Nana ba, ta bar Buda ta tafi Bauchi gurin mamanta, kamar yadda Uwani ta gaya mana"
A fusace ya ce "Bauchi gurin Maijidda? Lallai yarinyar nan ta riΖa ba ta ganin mutuncina, gidan ubanta ne a Bauchin da ta tafi? Uban me za ta yi a can?"
Jamila ta ce "A'a Baba, kar ka ga laifinta fa, a lokacin da take buΖatar taimako, ba a duba ta ba. Na san ta bar Buda ne dan kar ta din ga Ιora wa Uwani Ιawainiya"
Cikin kumfar baki ya ce "Wallahi ba zai yiwu ba, sai ta baro Bauchin nan, tun da dai ba gidan ubanta ba ne ba, kuma laifin Uwani ne ai da sai ta sako ta a gaba ta dawo da ita nan Kano, dan me za ta tafi wata Bauchi" Ummi ce ta yi sallama, suka amsa su na kallon ta.
Jamila ta ce "Ummi ya dai? Ya na gan ki kuma?"
"Ke Ummi, ke ce babbar algunguma, na san duk abin da Nana take yi kin sani, tun da da ke take shawara, ke ki ka bata shawarar ta tafi Bauchi ko?"
Ummi ta girgiza kai ta ce "A'a, ba ni ba ce ba. Dan hatta Ιatan mijinta ni ban sani ba, ba ta gaya mini ba sai yau da muka je Buda".
Cikin rashin fahimta Baba ya ce "Ζatan mijinta kamar yaya?"
Ummi ta ce "Baba, duk ba wannan ba. Jamila bayan rabuwarmu ina shiga gida, saΖon Nana ya faΙo wayata, hankalina a tashe yake fa"
"Ban gane ba, saΖon mene ne, ke Ummi ki yi mini bayani gwari-gwari sai wani kwalo-kwalo ki ke yi mini"
"Baba, yau da muka je Buda, Uwani ta sanar mana, mijin Nana an neme shi an rasa kusan sati biyu. Har gurin 'yan sanda suka kai cigiya ba a san inda ya tafi ba.
Bayan mun dawo ina shiga gida, saΖon tex message Ιin ta, ya shigo wayata. Ungo ka karanta message ne kusan kashi uku ga shi nan"
Ya saka hannu ya karΙa, cike da fargabar abin da zai gani.
"Assalamu alaikum, Ummi ya ki ke, ya su Islam. Ki yi haΖuri ban sanar miki ba, ba na son Ιaga miki hankali ne. Sayyid fa ya Ιata, daga na je sayo abu, na dawo na neme shi na rasa, ba na son ci gaba da Ιora miki Ιawainiya, ita ma Uwani yau da gobe sai Allah, ba Ζarfi ne da ita ba. Na je Bauchi Mama ta karΙe ni hannu bibbiyu, amma kamar zuwana zai zame mata matsala a gurin mijinta. Na san ko na koma gida, babu lallai Baba ya karΙe ni, na yanke shawarar na tafi Nijar, ko zan ga Sayyid ko danginsa. Kar ku Ιaga hankali gurin nema na, in sha Allah ba zan aikata abin da zai zame mana abin Allah wadai ba. Yanzu haka ina hanyar Niger, kar ku yi wahalar nema na, in sha Allah zan kasance cikin aminci, ku taya ni da addu'a. Nana Asma'u" A fili Baba ya karanta saΖon. Cikin fusata da tashin hankali ya ce "Wace irin mahaukaciyar yarinya ce Nana? Uban wa ye da ita a Nijar Ιin da ta wanke Ζafa ta tafi can? Banda tsabar hauka da rashin hankali da wauta, a gidan uban wa za ta sauka? Ba nan ta ce mini ba ta san suwaye danginsa a can Ιin ba, to gidan uban wa ta tafi?"
"To Allah dai ya kiyaye ya sa ba Ιaukar magana ta tafi ba" Mama ta yi maganar tana kwaΙe baki, wanda tun da aka fara magana da ba ta saka baki ba.
Bai kula ta ba ya ce wa Ummi "Ke kira mini ita dan ubanta ta dawo gida, ko Ζasa nake ci ta zauna mu ci tare"
Ummi ta ce "Baba wayarta fa ba ta shiga, tun kafin na zo gidan nan, nake ta gwadawa, amma ba ta shiga."
"Ki sake kira ki ji dai"
Ummi ta karΙi wayar ta kira Nana, amma aka ce wayar a kashe take.
Baba ya dasa faΙa, Ummi a sanyaye ta ce "Dan Allah Baba kar ka yi mata baki, wallahi idan aka nustu Nana ba ta da laifi a cikin lamarin nan. Tin fil azal fa ba bincike aka yi ba, ba a san daga ina mutumin nan yake ba, ka aura mata shi, saboda kawai ka na tunanin su na aikata Ιarna, alhalin babu cikakkiyar hujja da ta nuna hakan. Ba ta bujire maka ba ta yi biyayya, duk dan kar ta dawo gidan nan, kamar yadda ka gindaya mata cewar babu zawarci, ya sanya ta dage kai da fata, ta yi aiki tuΖuru ta jure wahala da Ζalubale take jinyar mutumin nan. Ka san Nana da gudun magana, duk tsoron abin da ka iya biyo baya ya sanya ta yanke wannan hukuncin, ka yi haΖuri a yi mata addu'a kamar yadda ta buΖata "
"Amma Ummi, Nana ko yayyanka Naman jikinta zan yi na cinye dan ba'i ba gara ta dawo mini nan ba! Dan me za ta kama hanya ta tafi Nijar? Gurin uban wa za ta je?"
Jamila ma ta ce "Tun da dai ta riga ta tafi, dan Allah ka yi haΖuri"
Baba ya rasa abin da yake yi masa daΙi, ya shuri takalmansa ya yi waje.
*****
Su na tafe a hanya, Nana tana addu'a, tana fatan Ubangiji Allah ya sauΖaΖa mata, ya taΖaita mata wahala. Ya haΙa ta da Sayyid cikin aminci, tare da fatan duk inda Sayyid yake, ya kasance cikin aminci. Ta maimaita Hsbunallahu wa ni'imal wakil, babu adadi, tare da tawasalli da ayoyin AlΖur'ani a kan Allah ya shiga lamarin ta, ya sauΖaΖa mata wahala.
Ζarfe shida saura, Nana suka sauka a MaraΙi. Tun a Nigeria ta sai 'yan kayan ciye-ciye ta zuba a Jakarta.
Ta yi sallar la'asar Ζasaru, sannan ta tsaya tana Ζarewa tashar motar kallo, tana tunanin ma ta ina za ta fara. Ta ji Ζafafuwanta kamar ba a jikinta suke ba, saboda nauyi, sun kumbura sun yi suntum, saboda azabar nauyi da gajiyar tafiya. Ga Ιan cikinta ya yi jingim ko motsi ta ji ya daina yi saboda azabar wahalar tafiya, Bayanta da mararta suka Ζulle mata, saboda azabar wahala. Ga jikinta tamkar an sassara ta, saboda gajiya babu isasshen gurin miΖe Ζafa.
Masu babur na ta tambayarta ina za ta je, amma ta yi musu shiru, ta Ιauki bagcon kayanta, ta yi gaba. Tamkar ba ta jin jikinta, haka ta din ga jefa Ζafa tana tafiya. Ta yi nisa sosai da tasha, ta fara hango unguwanni da gidaje.
Duhun magariba ya rufa, ta samu wani gida kawai ta shiga. Matar na tsugune tana tuΖa tuwo Nana ta yi sallama.
Suka gaisa da Nana, matar ta tsaya tana kallon ta, ta ji abin da ya kawo ta.
Nana ta ce "Dan Allah baiwar Allah, ni baΖuwa ce, hanya ce ta biyo da ni, dan Allah salla nake son na yi, idan babu damuwa zan kama ruwa ne na yi alwala".
Matashiyar matar ta ce "To ba komai. Ga banΙaki nan da buta a ciki"
Nana ta ajiye kayanta, ta shiga banΙakin ta zubar da uban fitsarin da ya cika mata mara dam. Ta yi miΖa saboda gaΙoΙinta da suke yi mata ciwo.
Sannan ta yi alwala, bayan ta yi alwalar, ta tsaya ta Ιaga cikinta, tana Ιan tattaΙawa cike da damuwa, jin sa shiru bai dame ta da motsi ba.
"Haba yaron kirki, ka motsa mana ko na ji daΙi, haba Ιan Baba. Nana na cikin damuwa dan Allah ka motsa" ta yi maganar a hankali cikin tsoro da damuwa, dan ta ji ana cewa idan Ιa ba ya motsi, to mutuwa ya yi. Har ta fitar da ran Ιan nan zai motsa, ta tsorata idonta ya fara cika da hawaye, kawai ta ji ya motsa a hankali, sai kuma ya ci gaba da motsawa.
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, ta shafa cikin ta ce "Alhamdillah, Allah ya bayyana mana Sayyid Ιinmu cikin aminci" Gaba Ιaya ta manta a banΙaki take.
Ta fito matar ta ba ta dadduma a Ιaki, ta shiga ta tayar da salla. Bayan ta idar da sallar, ta zauna a kan sallaya, ta din ga tasbihi tana gaya wa Allah damuwarta, har aka yi sallar isha'i.
Nan ma ta tayar da salla ta yi, tana cikin addu'a matar ta shigo da kwanuka, ta ajiye.
Nana ta shafa Addu'ar ta kalli matar ta ce "'yar uwa Na gode sosai da sosai, Allah ya saka miki da mafificin Alkhairi na gode Ζwarai da gaske"
"A'a babu komai, musulmi ai Ιan uwan musulmi ne, ki ci abinci kafin ki tafi dan Allah"
Nana ta ce "A'a, na Ζoshi Alhamdillah, Allah ya saka da alkhairi, ya biya miki buΖatunki na alkhairi"
Matar ta ce "A'a daga gani daga tafiya ki ke, ga juna biyu, ai sai wahala, dan Allah ki ci ko kaΙan ne kafin ki tafi" Nana ta dage matar ma ta dage. Da Ζyar Nana ta amince ta Ιan ci Abincin kaΙan sai dai babu abin da take tunani, sai yadda za ta yi da gurin kwana.
Ta rufe sauran Abincin ta ce "Na gode sosai da sosai 'yar uwa, Allah ya saka da alkhairi"
Matar ta amsa da "Amin, Allah ya kiyaye hanya"
Nana ta amsa da Amin, ta Ιauki jakar kayanta ta yi waje.
*****
Babar Nana wuni ta yi sukuku, gaba Ιaya hankalinta a tashe, sai koke-koke take yi. Baban su Walida kuma ya yi burus da ita.
Ganin kuka da damuwa ba zai fishshe ta ba, ya sanya ta yi alwala ta hau kan sallaya, ta gabatar da salatul haja, sallar neman biyan buΖata a gurin Allah.
Ta Ιaga hannayenta tana kuka, take yi wa Allah kirari da magiya.
"Allah kai ne Allah, Allah kai ne ka halicce ni ka kuma halicci Nana, ka rayata ta girma cikin ikonka da kulawarka. Ya rabbil arshil azim duk inda yarinyar nan take, Ubangiji Allah ka kai mata Ιauki, da ita da abin da yake cikinta. Allah ka kare ta daga dukkanin sharrin abin Ζi, Allah ka zama gatanta ka tsare mini ita. Ya hayyu ya Ζayyum domin kyawawan sunayenka maΙaukaka masu girma, Ubangiji Allah ka kai wa Nana Ιauki, ta inda ba ta zata ba" ko abinci ba ta iya ci ranar ba, gaba Ιaya addu'ar wunin ranar, Nana kawai take yi wa.
Can gida Baban su Nana ma, an ba shi Abincin dare, amma ya gagara ci sai uban tagumi da ya rafka. Lissafinsa kawai gidan uban wa za ta ga je a Nijar? Hannun wa za ta faΙa kuma a ina za ta kwana?
Nasiru kuwa tun da ya samu labari shi ma abin duniya ya dame shi, kuma ya Ιora alhakin hakan a kan mahaifin su.
Mama ta ce "Wai baban Jamila ba za ka ci Abincin ba sai ya sandare?"
"Wai wane Abinci zan iya ci? Wanan shashashar yarinyar, tana can babu uban da ya san a yaya za ta kwana? Kai Nana muguwar sokuwa ce. Kin ga Ιauke Abincin nan, gurin Malamin Almajiran can zan je na gaya masa, ko kiranye ne a yi mata ta dawo gida dan ubanta".
"Kiranye kuma?"
"Eh mana, tun da dai shi mijin nata mutumin banza ne, bai san abin da ya dace ba, ya tafi ya bar ta, ai sai ta dawo gida, tun da ba Ζanin ubanta ba ne"
Jamila ta ce "Kayya! Ba na tunanin wani kiranye zai yi wa Nana tasiri, ka san tana da haΖuri amma akwai taurin kai"
"Aikuwa wannan karon, dole ya kama ta, duk gidan uban da ta tafi, sai ta dawo"
ya yi maganar a fusace ya fice fuuuuu.
Sagir yana tsaka da bacci, ya buΙe idonsa ya ga Shukura a zaune. "Sweetheart lafiya kuwa? Ya na gan ki a zaune?" Ji ta yi tamkar ta kifa masa mari, amma ta maze ta ce "Ba na jin daΙi ne"
Ζan rikicewa ya yi, ya tashi ya matsa kusa da ita. Da gaske jikinta da zafi.
"Ya salam, bari na duba miki pcm" ya tashi ya kunna fitila, ya kawo mata ruwa da magani. A dole ta karΙa ta sha. Ya kashe fitilar ya zauna a kusa da ita, ya riΖe hannunta yana Ιan murzawa a hankali.
"Sannu"
"Yauwwa" ta amsa a taΖaice.
"Beb anya ba wani cikin ba ne?"
"Ahha haba dai, ba wani ciki maybe malaria ce"
Sagir ya ce "Ban yadda ba, gobe in Allah ya kaimu zan kai ki Asibiti a sake duba mini ke. Ubangiji Allah ya sa cikin ne" shiru ta yi ba ta amsa masa ba, shi kum hakan bai dame shi ba. Duk haushin Sagir da take ji, yana da halayen da duk Ζiyayyarka da shi, muddin za ka yi masa adalci dole ka kira shi mutumin kirki. Yana da matuΖar tausayi, duk faΙan da za su yi, da ya ganta a yanayi na rashin lafiya, zai rikice gaba Ιaya. Haka ya lallaΙa ta ta kwanta, sai dai da ya fara bacci sai ya farka, ya taΙa goshinta da wuyanta. Ita kuma idonta biyu duk abin da yake yi tana jin sa.
****
Sai da Nana ta tabattar da sawu ya Ιauke, sannan ta Ιauki jakarta, ta koma gidan da ta shiga ta yi salla. An kulle Ζofar gidan, amma Ζofar rilar gidan a buΙe.
Ta shiga rilar, ta ciro daddumarta ta shimfiΙa, ta Ιaukko zani a kayanta ta yi kwanciyar ta.
Har a wannan lokacin, da take shirin kwana a waje haka, ba ta ji ta yi nadamar tahowarta Nijar ba. Sai ma ji da take yi ta zo inda babu wanda ya santa, balle a din ga gudunta, a din ga ganin da ta rabu mutum sai wata masifar ta afka masa.
Ta saka hannu ta tallafo cikinta, da ita ma take jin nauyinsa, ya wuce adadin watannin da take tunani.
Tana jin yadda yake motsi, wanda motsin nasa kaΙai, wani irin farinciki da nishaΙi yake sanya ta.
Sai kuma damuwa ta biyo bayan farincikin nata, bayan da ta tuno Sayyid, da kuma rashin sanin halin da yake ciki. Da haka bacci nannauya ya yi awon gaba da ita a gurin.
Ko da dare yayi, Maijidda bacci gagarar idanunta ya yi, ta tattara Iliyasu ta watsa a gefe, addu'a kawai take yi Ubangiji Allah ya sanya Nana ta kasance cikin aminci da kwanciyar hankali.
Tana zaune a kan gado, ta yi shiru abin duniya ya ishe ta. Ji ta yi yana lalubata, wani irin baΖin ciki ya turnuΖo zuciyarta.
ΖoΖarin janyo ta yake yi, ta buge hannunsa a fusace, saboda ko Ζaunar ganinsa ba ta son yi.
Ya ce "Mai Jidda meye haka ne wai?"
"Dan Allah ni ka rabu da ni, wallahi ko Ζaunar ganin ka ba na yi. Ni dan zatin Allah ka sake ni, gara na yi zaman 'ya'yana kawai, da na ci gaba da zama da mutumin da ba ya Ζaunata, na yi kuskure tun farko da na biye wa son zuciyarka na banzatar da 'ya'yana" Ta yi maganar tana kuka mai Ζunar zuciya.
"Maijidda da ba na sonki, ke kin san ba za ki je ki yi wani auren ki fito na aure ki ba. Ni kishinki nake yi, kuma na gaya miki tsanar da na yi wa mijinki ne ya shafi 'ya'yansa"
"Ka na Ζaunata, ina cikin wannan mawuyacin halin, da kai ne sila, za ka zo ka na naniΖata buΖatarka ce kawai a gabanka? Wallahi ba ka Ζauna ta. Kuma haΖurina ya riga ya Ζare, ka sauwwaΖe mini kawai, ni zan tafi neman 'ya ta. Allah kaΙai ya san a yaya za ta kwana a Ζasar da ba ta san kowa ba, ga tsohon ciki"
Kasancewar buΖatarsa a gabansa, ya sanya ya kwantar da murya, kamar yadda ya saba ba ya tashi kalailaye ta, da kwantar da murya sai a irin wannan lokacin.
"WataΖila ma fa ba Niger Ιin ta tafi ba, ai ba yarinya ce Ζarama ba, na san gidan babanta ta koma, ki ke ta Ιaga hankalinki"
"Da akwai damar zama a gurin Baban nata, ka na ganin za ta zo inda nake ne? Nana ba za ta ajiye mini wannan rubutun ta koma gidan babanta ba, ni ka riga ka cuce ni" Ta yi maganar tana sauka daga kan gadon. Ya bi bayan ta yana lallaΙa ta, amma ta wuce ko saurarasa ba ta yi ba ta bar Ιakin, abin da ba ta taΙa yi masa ba a tsawon zaman su.
Baba ma abin Duniya ya dame shi, ya fito Ζofar gida yana takaicin abin da Nana ta yi, sai ga kiran Uwani.
Kamar ya share sai kuma ya Ιaga, suka gaisa Uwani ta ce "Isa kiran ka na yi na ja maka kunne, tun jiya da su Ummi suka taho nake son na kira ka na ja maka kunne, kar ka kuskura ka kira yarinyar nan ka ce za yi mata faΙa, ko ka kira uwatta ka yi musu jaraba, saboda Nana ta tafi can, ita ma mafitarta take nema, tuntuni da ka kama 'yar ka ka riΖe, babu yadda za a yi ta tafi Bauchi gurin babarta. Kuma ga halin da take ciki an nemi miji an rasa, ba a san kowa nasa ba, yarinyar nan na cikin wani hali, dan haka kar ka ce za ka yi mata faΙa tun da kai ne ummul aba'isin duk wannan lamarin. Da ka binciki dangin mutumin nan kafin ka aura mata shi, da duk haka ba ta faru ba".
"Uwani"
"Na'am"
"Nana fa ba ta Nigeria ma gaba Ιaya, mijin Babarta ya kore ta, ta rubuta wa Ummi saΖo ta tafi Niger neman mijinta"
"Me? Ta tafi Nijar ta san a inda za ta gan shi ne?"
"Oho ina san mata ma, na samu wani malami, na ba shi abin sadaka ya yi mata kiranye, gaba Ιaya yarinyar nan ba ta da lissafi"
"A'a ai duk kai ka janyo, amma Nana ba ta yi dabara ba, wallahi da na san abin da zai faru kenan, da ban bari ta tafi ba"
"Sai anjima bari na koma gurin malamin na gode " ya kashe wayar dan ita kanta Uwanin haushinta yake ji.
Yana shirin yin gaba, sai ga wata mota ta tsaya a gaban Baba.
Har Baba zai wuce, sai kuma ya tsaya. Wani matashin saurayi ne ya fito Baba ya din ga yi masa kallon sani.
Matashin ya Ζaraso su ka gaisa. Matashin ya ce "Baba dama, Mamanmu ce ta aiko ni, can gidan da Nana ta yi aikin rainon yaro. To wai Hajiya ce kwana biyu suna ta kiran wayarta, ba ta shiga sam, kuma an je can gidan da suke gadi, amma ba sa nan, shi ne ta ce na zo gida na tambaya ko lafiya, ko kuma a bani lambarta da take shiga na kai mata"
Baba ya kwaΙe fuska ya ce "Kai ne ta auri Buzun yaron nan a gidanku kenan?"
"Eh ni ne Baba"
"To ai 'yan uwansa ne suka fara guduwa, ya yi ta rashin lafiya, to yanzu dai shi ma ya gudu, ta tafi can Nijar neman sa".
Yusuf ya yi sororo cikin rashin fahimta ya ce "Ya gudu ta tafi nemansa kuma?"
"Eh kamar dai yadda ka ji na gaya maka"
Ganin kamar Baba a fusace yake, ya sanya Yusuf cewa "To shikenan Baba, Allah ya kyauta, ya bayyana su cikin aminci" Ya koma ya shiga motarsa ya tafi.
*****
Sanyin iskar sahara ce ta din ga ratsa Nana, har ta fara karkarwa saboda sanyin.
Ta Ιaga kai, ta ga sararin samaniya ta yi tarwai, sai hasken farin wata da ya haska cikin saharar.
Wani irin Ζugi ta ji saharar tana yi, da alamun tasowar iska. Ta kalli gabas ta ga iskar sahara daga nesa, tana wani irin hanΖoro da alama iskar tana da Ζarfi.
Sauke Numfashin Sayyid ta din ga ji a cikin saharar. Waige-waige ta fara tana neman ina za ta gan shi.
"Sayyid, ka na ta ina ban ganka ba"
"Ma viee"
"Na'am Sayyid, ka na ina ne?"
"Za su kashe ni, dan Allah ki zo mu koma gida, na fi son rayuwata da ke, na nufi nutsuwa"
Cikin rauni ta ce "Sayyid ba na ganin ka, ka na gurin ina?"
"Husna" ta sake jin muryarsa yana ajiyar zuciya. Gadan-gadan Nana ta nufi inda Ζurar Saharar nan take tasowa, saboda daga nan take jin sautin muryarsa.
A Ιan razane ta farka, saboda taΙa Ζofar gidan da aka yi. Tana kwance a cikin duhu, ta hangi mai gidan ya fito, da alama masallaci ya tafi.
Ta tashi da Ζyar, ta buΙe kayan ta, ta Ιauki ruwa pure water, ta kama ruwa ta yi alwala. Tana jin yadda magidanta suke buΙe gidaje, su na tafiya masallaci. Ita ma ta tayar da salla.
Kusan mintuna Arba'in mai gidan ya dawo, sai da ya tsorata kasancewar gari ya fara haske. Ya ga mace tana salla a kan dadduma a cikin rilar gidan. Nana ta Ιaga kai ta kalle shi, ta mayar ta sunkuyar ta ci gaba da tasbihi. Sai dai duk iya ΖoΖarinsa a kan ya yi mata magana, ya kasa kamar an saka masa sakata a bakinsa.
Ya lallaΙa ya buΙe Ζofa ya shiga gidansa, ya tarar da matarsa tana bacci, kasancewar Al'ada take yi, ba ta salla. Kamar ya tashe ta ya gaya mata batun matar da ya gani, amma ya kasa, ya haΖura ya Ζyale ta.
****
Jamila bata taΙa sanin ta damu da Nana har haka ba, duk da takun saΖa da sukan yi wasu lokutan, saboda Ζuruciya da sakunta, wasu lokutan kuma saboda zigar Mama. Amma ta damu sosai da halin da Nanan ke ciki. Jikinta ya yi sanyi sosai da sosai, da Ummi ta ba ta labarin wahalar da ta yi ta faman yi, ga miji ga laulayin ciki. Yanzu mai Ιungurungun ta tafi inda babu mataimaki sai Allah.
"Amm Jamila"
"Na'am Mummy"
"Kwana biyu na Ιaga miki Ζafa da batun Nana, saboda ki samu ki Ζara sakin jikinki, yanzu dai ki na ganin yadda al'amuran Ζungiya suke wakana, kuma na ga kin saki jikinki yanzu.
Dole fa ki yi ΖoΖari a wannan karon, ki samo mana jinin Nana, saboda ba Ζaramin alkhairi ne a tattare da taurarinta ba. Tun da dai kin ga Uba ku ka haΙa kawai da ita."
Jamila ta yi murmushi cike da takaici, amma a zahiri ta danne ta ce "To ai Nana mijinta ya Ιauke ta, ya tafi da ita can Ζasar su Nijar a can ma ina ga za ta haihu"
"What? Jamila amma ya aka yi ba ki gaya mini ba, bayan kin san Ζudurina a kanta?"
Jamila a ranta ta ce "Da yake ki ka halicce ta ba"
A zahiri ta ce "To ai ni ban san haryanzu ana buΖatar jininta ba, da na ga ba ki kuma yi mini maganarta ba, na zata shikenan ya wuce"
Kamar ta rufe Jamila da duka ta ce "Amma wallahi ba karamar shashasha ba ce, Ιaga miki Ζafa kawai na yi ki Ζara dawowa hayyacinki, aikuwa ko ki nemo Nana a samu jininta, ko kuma Ζungiya ta nemi jinin wani shaΖiΖinki, sai ki zaΙa".
Jamila ta waro ido ta ce "ShaΖiΖina kuma Mummy, na shiga uku na lalace"
"Ahh to dabara ta rage ga mai shiga rijiya ai, sai ki yi tunani, ni na haura sama zan yi bacci" Gaba Ιaya jikin Jamila ya yi sanyi, ta bi bayan Hajiya Sa'a da wani irin kallo.
Har rana ta Ιaga gurin Ζarfe goma, Nana na zaune a rilar gidan nan, sai da rana ta tarar da ita, sannan ta yinΖura, ta Ιauki jakar kayanta, ta koma barandar da ke kallon gidan, ta zauna.
Mai gidan da ta kwana ya fito zai tafi kasuwa, kawai ya sake ganin Nana, da hijjabinta da wannan bagcon kayan nata ya gane ta. Ζarasa fitowa ya yi, da niyyar ya tambayi Nana me take nema ne? Amma su na haΙa ido da Nana ya kawar da kansa cikin sauri, saboda wata irin mummunar faΙuwar gaba da ta ziyarce shi.
Sum-sum ya wuce ya tafi, ba tare da ya ce wa Nana komai ba.
Rana ta fara zafi, ta sake Ιaukar jakarta ta yi gaba, ta din ga nanata lahaula wa la Ζuwwata illa billah. Hasbunallahu wa ni'imal wakil.
*****
Alhaji Zailani yana zaune a falo, tare da Hajiya Amina, Yusuf ya shigo falon.
Hajiya Amina ta kalle shi ta ce "Yusufa daga ina?"
"Aiken ki na je Mami"
Ta ce "Wanne daga ciki?"
Ya zauna tare da faΙin "Ba shekaranjiya muka yi zancen Nana da ku ba? Gidansu na je, daga gidan nake na samu babanta a waje, ya gaya mini wai mijinta ne ya Ιata ta bi shi Nijar neman sa"
Hajiya Amina ta dafe Ζirji ta ce "Ya Ιata kuma garin yaya? Ko shi ma Ιauke shi aka yi kamar yadda aka tafi da 'yan uwansa? Anya ba wani laifin suke aikatawa ba hakan ta faru? To ta san inda yake a Nijar Ιin ne?"
Yusuf ya ce "Wallahi nima ban sani ba, haka dai ya ce mini"
Alhaji Zailani da hantar cikinsa ta kaΙa ya ce "Wai maganar wa ku ke yi ne?"
Cikin dakiya ta ce "Nana mana, yarinyar nan da ta kula da Haidar, wadda babanta ya aura wa Buzun nan"
"To sai aka yi yaya?" Yayi maganar yana tsare ta da ido, yana tunanin ko Hajiya Amina ta ci gaba da bibiyarta, ta gaya mata abin da yake tsakaninsu.
"A'a dama Shukura ce ta ce, kwana biyu shiru, kuma ba ta samun ta a waya, nima kuma ba na samun ta, shi ne na ce masa dan Allah idan ya biya ta hanyar gidanta, ya tsaya ya karΙo mini lambarta, to kuma wai sun tashi daga gidan. Shi ne ya je gidansu aka sanar masa da ta bi mijin Nijar" Ya yi wata Ιoyayyiyar ajiyar zuciya ya yi shiru bai kuma cewa komai ba.
Hajiya Amina ta yi ta jajanta lamarin, tare da tausayawa Nana.
Alhaji Zailani kuwa rikicewa ya yi, cike da kiΙima. Domin yana ta tsara yadda zai samu Nana ko ta halin ΖaΖa domin samun biyan buΖatar sa. Yaronsa da ya bawa ragamar bibiyarta, bai taΙa gaya masa ba, ce masa kawai ya yi ta koma Kurna.
Wani irin gumi ya fara keto masa, ta ina za a fara neman ta yanzu har a gano ta, a Nijar.
Sai ya Ιora wa kansa alhakin sakacinsa ne, da ya din ga bin al'amuran a sannu, duk da hakan ya faru a dalilin halin da yake shiga, a duk lokacin da ya yi yinΖurin aiwatar da wani abu a kan Nanan.
****
Nana kuwa wuni ta yi tana gararanba a titi, daga wannan inuwa ta koma waccan, ga uban kaya ga kuma ciki. Dama Abinci ba damunta ya yi ba. Buredinta da ta yi guzuri ta ci abin ta, ta kora da ruwa.
Tana son samun muhalli, tun da akwai kuΙi a hannunta, akwai na Nigeria akwai na Nijar, sai dai amana ta yi Ζaranci, ba ta san wa za ta tunkara ya taimake ta ba, tana tsoron a cutar da ita.
Dare ya yi bayan sallar Isha'i, ta sake lallaΙawa ta koma gidan nan ta kwana a rila, da Asuba mijin matar ya sake ganin ta, hakan ya sanya hankalinsa fara tashi, ga shi ya kasa magana kamar wanda aka yi wa asiri.
Yau bayan magariba da ya koma gida, sai ya sanya wa rilar sakata, ya kulle ta ciki.
Sawu ya Ιauke, Nana ta lallaΙo ta zo ta kwana, kawai ta tarar da rilar a rufe, ta jijjiga ta ji an garΖame ta ciki.
Jikinta ya yi sanyi, ga shi duk inda ta tafi ko ta yi niyyar ta yi gaba ta tafi wani gurin, sai hankalinta ya kasa kwanciya sai dai ta koma gidan nan.
Ga yau wani irin bacci take ji, kamar ta kifa, ga shi tana son yin wanka, saboda yadda kayan jikinta suke mintsininta, tun da ta zo da su take yawo.
Ta samu gefen gidan ta takure, tun tana hamma har bacci sosai ya yi awon gaba da ita.
Da Asuba ta ciro jarkar ruwan da ta saka wasu yara suka zuba mata a cikin Ζaramar jarka, ta yi alwala ta yi raka'atanul fajr. Tana kallon mai gidan ya fito ya tafi masallaci yana haske-haske, amma bai gan ta ba, har ya tafi.
Ya dawo daga masallaci kansa tsaye zai shiga gida, ya ga Nana a cikin rilar. Wata irin razana ya yi, ya kuma kasa magana sai kallonta da yake yi fuskarsa na bayyanar da tsoro Ζarara.
Nana ta ce "Ka kulle rilar gidanka, jiya a waje na kwana, duk da ban ga laifin ka ba, amma da ka tambaye ni, me yasa nake kwana a nan"
"Wa..wa.wace ce ke? Me ki ke yi a nan?"
Ayshercool
08081012143
63
Nana ta ce "Dan Allah ka kwantar da hankalinka, kar ka tsorata wallahi ni mutum ce, ba abin da na isa na yi maka na cutarwa, ba kuma ni da nufin cutar da ku"
"To me ki ke yi mini a gida?"
"Wallahi baΖuwa ce ni, ranar da na sauka a garin nan, na shiga gidanka, matarka ta bani gurin salla, har da abinci, dan Allah taimakona za ku yi"
Ya ce "Baiwar Allah wallahi mu ma talakawa ne, ba wani taimako da za mu iya yi miki"
Ta ce "A'a amma ai ku musulmai ne, gudun zargi dan Allah idan babu damuwa, mu shiga ciki a yi maganar a gaban matarka, ku ji taimakon da nake buΖata idan za ku iya yi mini, idan kuma ba za ku iya yi mini ba, babu komai sai na nema a gaba"
Kamar ya ce a'a, amma yanayin Nana sai ta ba shi tausayi, ya bata dama suka shiga gidan, yana gaba tana bin sa a baya.
Nana ta tsaya a tsakar gida, ya shiga ya taso matarsa. Ta fito tana mustustuke ido, ya nuna mata Nana ya ce "Kin san wannan?"
Ta Ιan yi shiru sannan ta ce "Kamar shekaranjiya ta zo, ta ce mini baΖuwa ce za ta yi salla"
Ya ce "Yauwwa, sau uku ina ganinta a rilar gidan nan. Wai a nan take kwana, ta ce mini taimako take nema, amma a zo a gaban ki, sannan ta faΙi me take son mu yi mata".
Matar ta kalli Nana,ta ce "Baiwar Allah, wane taimako za mu yi miki?"
Nana ta ce "Ni baΖuwa ce daga Nigeria, dan Allah ku taimaka mini da inda zan zauna, ban san kowa a Ζasar nan ba. E"
"Gaskiya baiwar Allah, ba bu gurin da za mu iya ajiye ki a gidan nan" matar ta tari numfashin Nana.
Nana ta ce "A'a ba a nan za ku ba ni gurin zama ba, da kuΙi a gurina, sai dai ban san kan kuΙinku na Ζasar nan ba, ina da wasu ma na Nigeria, ban san yadda zan canza su ba. Kuma ina tsoron na faΙa hannun da ba na gari ba a cutar da ni. Haka kawai na ji na nutsu da nan tun lokacin da ki ka karrama ni, ko na tafi sai na dawo nan na kwana nake samun nutsuwa. So nake ku taimaka a sama mini gidan haya, ko Ιaki da zan kama dan Allah. Kuma wallahi ni ba macuciya ba ce ba zan cutar da ku ba. Ku yi wa Allah da ma'aiki ku taimaka mini, dan Allah"
Ya kalli matar matar ta kalle shi, ta Ιan jinjina masa kai.
Ya kalli Nana ya ce "Kin san harkar taimakon ce wuya ne da ita yanzu, sai ka taimaki mutum amma ya sanya ka a masifa.
Nana ta ce "In dai kun yi niyyar taimakona, ko macuciya ce ni, Allah ba zai ba ni damar cutar da ku ba. Ku taimaka mini dan Allah, ko iya gidan hayar a sama mini"
Ya kalli matarsa ya ce "Hajara, bata guri ta zauna, zuwa gari ya Ζarasa wayewa, sai mu san abin yi, mu duba girman Allah da ta haΙa mu da shi"
Hajara ta ce "To shikenan babu damuwa" wata irin ajiyar zuciya Nana ta yi, ta risuna ta ce "Na gode, Ubangiji Allah ya saka muku da mafificin Alkhairi, yadda ku ka taimaka mini Allah ya taimake ku haka"
Suka amsa da Amin. Matar ta kai Nana wani Ιaki, ta Ιaukar mata kayanta ta shiga da su.
Tana fita daga Ιakin, Nana ta zube ta yi sujjada tana gode wa Ubangiji buwayi gagara misali, ta san wannan Ιaukin kai tsaye daga gare shi ne, amma ba dan haka ba ta san ba Ζaramar wahala za ta sha ba.
Sai yanzu da ta nustu, ta din ga jin ta a takure, saboda rashin wanka, ga cizonta da kayan jikinta suke yi.
Gari ya yi haske matar ta shigo ta ce wa Nana "Ki na buΖatar wani abu ne?"
Nana ta ce "Eh dan Allah zan yi wanka"
"To shikenan babu damuwa, da kin sani tun ranar da ki ka zo, ki ka yi mini bayani, ga ki da juna biyu, amma a ce ki na kwana a waje bai dace ba"
Nana ta ce "Larura ce, ba yadda zan yi, kuma babu daΙi ka Ιora wa mutane Ιawainiya sama ta ka"
Ta ce "Haka ne" ta haΙa wa Nana ruwa, Nana ta duba kayanta ta Ιauki soso da sabulu, da brush.
Ba Ζaramin daΙin wankan nan Nana ta ji ba. Ta koma Ιakin da suka sauke ta, ta fito koma Ιakin da aka sauke ta.
Ta fito da mai ta shafa, ta saka kaya. Ta ji wata sassanyar iska na ratsa ta. Ta Ιaukko jakar kayan turarrukan Sayyid, da kayan gyaran gashin sa, ta yi zuru da ido, tana kallonsu.
"In sha Allah za mu haΙu Sayyid, ina fatan Allah ya Ζaddara haΙuwarmu nan kusa" ta yi maganar a sanyaye.
Sallamar Hajara ce ta sanya ta mayar da kayan cikin bagcconta, ta mayar da hankalinta kan ta.
"Ko ki na buΖatar wani abun ne?"
Nana ta girgiza kai fuskarta Ιauke da murmushi ta ce "A'a ba na buΖatar komai, na gode sosai da sosai"
"Ba komai, bari na kusa gama abin karyawa"
Cikin murmushi Nana ta ce "Ba raina miki na yi ba, amma ni wannan taimakon da ku ka yi mini ya wadatar, ba sai kun ba ni Abinci ba, na gode sosai da sosai"
Hajara ta ce "Haba dai, ya ma za ayi ki na baΖuwarmu a ce ba za mu ba ki Abinci ba, ai ba zai yiwu ba sam"
"Ai kar Ιawainiyar ta yi yawa ne, abin da ku ka yi mini ma, na gode Allah ya biya ku"
"A'a babu wata Ιawainiya" ta yi maganar tana fita waje.
Ta so tambayar Nana me ya kawo ta Nijar, ga tsohon ciki, kuma ta ce ba ta da kowa, amma ta kasa saboda wani irin kwarjini da Nanan ta yi mata.
Tun da ta bawa Nana abincin safe, da rana ta bata fura Nana take amai. Har sai da Hajara ta ji babu daΙi, ta yi zaton ko Abincinta ne ya saka Nana amai.
A sanyaye ta ce "Ko Abincin nawa ne ya saka ki amai?"
Nana ta yi murmushi ta ce "A'a kar ki damu, dama haka nake fama tun farkon cikin, ni na riga na saba ma"
"Kayya ai ba a sabo da wahala, kin yi amai ya kusa goma, ko Asibiti zamu je?"
"A'a zan daina in sha Allah"
Gaba Ιaya Hajara ta damu, ganin yanayin da Nana take ciki.
Nana ta ce "Ba ki taΙa haihuwa ba ne? In dai mutum ya haihu ya san irin wannan larurar ta ciki ai"
Hajara ta ce "Ina fa? Watanmu takwas da aure, ban haihu ba".
Nana ta yi murmushi ta ce "Allah ya kawo mai albarka"
"To ai ni duk na tsorata ne, wannan aman ya yi yawa"
"Ai ni na riga na saba ma, ba ya damuna yanzu" haka suka Ιan din ga taΙa hira.
Mijin Hajara bai dawo ba sai isa'i, Nana na Ιaki tana shafa'i da wuturi. Ya ce wa Hajara "Ina baΖuwarmu?"
"Tana nan sai dai ba ta da lafiya"
"Me ya same ta?"
"Wallahi tun da na ba ta Abinci take amai, haryanzu jikina duk ya yi sanyi"
Ya ce "Subhanallah, kuma bai tsaya ba?"
"Tana dai ta yi"
Nana ta idar ta yi addu'a, sannan ta fito, ta durΖusa ta gaishe shi, ya amsa yana yi mata ya jiki.
Ta ce "Jiki Alhamdillah"
Ya ce "Baiwar Allah ba a samu gidan haya ba, duk inda na tambaya, sai masu tsada, kuma babu lallai a bayar, mussaman idan aka san ke kaΙai za ki zauna, kuma zaman ki ke kaΙai babu Namiji babu tsaro ko kaΙan.
Amma na kuma bayar da cigiya ko za a samu wani, wanda yake da mutane a ciki sai a kama"
Nana ta jinjina kai ta ce "Na saku Ιawainiya, Allah ya saka da alkhairi"
Ya ce "Ba komai" ya kalli Hajara ya ce "Bari na je na dawo, ko za ku yi hira kar na takura muku"
Nana ta ce "A'a ba komai, ka zauna ni sai na koma Ιaki"
Ya ce "A'a dama zan fitan"
Hajara ta raka shi soro, ta tsaya can su na hira Nana tana jiyo dariyar su. Sayyid ya faΙo mata a rai. Yana daga cikin manyan ni'imomi da nasarorin rayuwa, mutum ya auri wanda yake son sa, ya kuma dace da shi. Ta yi musu addu'a da fatan samun dauwamammen zaman lafiya da kuma zuriya ta gari masu albarka.
Hajara ta dawo, ta zauna su ka ci gaba da Ιan taΙa hira da Nana.
Ta cewa Nana "Ko sunanki ban sani ba"
"Nana Asma'u, amma Nana ake ce mini"
Ta ce "Allah sarki, amma ki na da aure ne?"
Nana ta yi murmushi, ta ce "Kin yi mamakin yadda na taho inda ban san kowa ba ga tsohon ciki ko? Na san wataΖila, kina tunanin ina na samo ciki ne?"
Hajara ta ce "Laaa a'a wallahi"
Nana ta ce "Ai babu damuwa idan ma kin yi tunanin haka, Ιabi'ar zuciya ce. Matar aure ce ni, ko a yanzu haka ka ma ina da igiyoyin aure uku a kaina, wani dalili ne ya kawo ni Ζasar nan, kuma in sha Allah da na kammala, zan koma gida"
"Allah sarki, Allah ya tabattar da alkhairi, ya sanya a samu abin da aka zo nema"
Nana ta amsa da "Amin na gode sosai"
*****
Su na zaune sun tattara hankalinsu a kan likitan, cikin matsananciyar girmamawa Likitan ya gaishe su.
"Ya ya jikin Imam?"
Ya amsa da "Jikinsa Alhamdillah, yana samun sauΖi sosai da sosai"
"Ba yana samun sauΖi muke son ji ba, mene ne sakamakon binciken ku da aka gudanar?"
Likitan ya ce "Eh sakamakon gwaje-gwaje, ya nuna babu abin da aka yi masa na cutarwa a jikinsa, gaba Ιaya babu wani abu na cutarwa a tare da shi"
"Shi kuma matsalar zuciyar fa?"
"Wannan yana da nasaba da hawan jini da yake da shi tuntuni, wataΖila ya daΙe ba a kan magani ba. Shi yasa ya shafi zuciyarsa. Sai dai matsala Ιaya"
Cikin damuwa dattijon ya ce "Wace matsalar?"
"ΖwaΖwalwarsa, mun kasa gano abin da yake faruwa da ΖwaΖwalwarsa, haryanzu bai samu nutsuwar da zamu tattauna da shi ba, yana buΖatar kulawa ta musamman a bangaren ΖwaΖwalwa"
Sultan ya dafe goshinsa, cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali, idanunsa suka yi jawur. Ya Ιago ya kalli Likitan ya ce "Ko gida za a mayar da shi, a saka duk abin da ake buΖata na kula da shi a Ιakin, ya zamana yana kusa da ni, hankalina ba ya kwanciya, yana nan ina can"
Abduou ya ce "A'a Sultan, idan aka mayar da shi gida, za a iya gane halin da yake ciki, wanda ba ma fatan hakan, dole a ci gaba da toshe duk wata kafa da za a san halin da yake ciki, har zuwa lokacin da zai warware. Kuma za a ci gaba da matsa yaran can, har sai ya yi mana bayanin abin da suka yi masa a Nigeria. Kuma Asibitin nan akwai tsaro babu wanda ya san yana nan. A kula da shi har zuwa lokacin da za a yi tafiyar"
Sultan ya yi ajiyar zuciya cike da gamsuwa, ya miΖe tsaye ya ce "Mu je na gan shi"
Su ka miΖe gaba Ιaya, Likitan yana gaba su na biye da shi a baya.
Cikin sauri suka Ζarasa gaban gadon. Idanunsa a rufe yana bacci.
Sultan ya Ζarasa gaban gadon, fuskarsa Ιauke da damuwa.
Ya din ga dudduba jikinsa, tamkar yana son gano wani abin. Ya kalli Likitan ya ce "Kun tabattar a jikinsa babu wani abu na illa ko cutarwa a tattare da shi?"
"Babu ranka ya daΙe, lafiya kalau yake, ba a yi masa komai ba, sai wannan matsalar ta ΖwaΖwalwarsa. Ba na tunanin an tafi da shi Nigeria ne dan a cutar da shi, akwai dai wani abu...
"Ya isa ba kai ke hurumin zartar da wannan hukuncin ba, sai abin da bincike ya tabattar"
Babu shiri likitan ya ja bakinsa ya tsuke.
Sultan ya Ιago hannun Imam na hagu, ya kalli yatsunsa ya ga yatsunsa biyu sanye da zobuna, ya Ιago hannun damansa, ya ga babu azurfa Ιaya sai Ιaya. Cikin tashin hankali ya ce "Abduou. Babu zoben Imam guda Ιaya" Cikin sauri Abdou ya ce "Wanne daga ciki?" Ya Ιago wa Abdou hannun Imam.
A rikice Abduou ya kama hannunsa ya duba, ya kalli Sultan ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ka ga abin da nake gaya maka ko? Kai ne ka ke ΖoΖarin kare yaron can, ka ke cewa a bi shi a sannu ba ka tunanin zai iya cutar da shi, to ga shi nan ai ga irinta nan, tabbas ya san inda zoben nan yake, dole a matsa shi a fito da shi. Dalilin da ya sanya su ka sace shi kenan ma, su ka bar Ζasar nan da shi, su ka kai Nigeria. Zoben suke so su sace"
Sultan ya dafe kansa, ya rasa abin da yake yi masa daΙi.
"Sultan wannan ma wani sabon sirri ne, da yake buΖatar duk tsanani a rufa shi, a ci gaba da addu'a, amma dole a nemo zoben nan, idan ba haka ba zai fita daga sahun Imams"
Sultan ya sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya yana kallon yadda yake bacci a kan gadon.
****
Sai da Nana ta shafe kwanaki huΙu a gidan Hajara, ba a samu inda za ta zauna ba. Nana ma abin daya dame ta, sai Ιawaniya suke faman yi da ita, ga shi tana tsoron kar su Ζosa da ita, dan babu mai jurewa yau da kullum sai Ubangijin da ya halicci bawa.
Ranar kwana na huΙu da yamma mai gidan ya dawo, Hajara ta kira Nana.
Bayan sun sake gaisawa ya ce "Malama Nana, wallahi ba a samu gida ba, sai dai ina tafe a hanya wata shawara ta faΙo mini. Akwai wata 'yar uwar Babana a can wata unguwa, itakaΙai take zaune a gidanta, kuma akwai Ιakuna a gida, kuma ba mazauniya ba ce, tana fita sana'iinta. Sai dai fa mace mafaΙaciya, tana da yawan faΙa, ba wuya ta hasala. Ban sani ba ko za ki iya zama da ita?"
Cikin farin ciki Nana ta ce "Zan iya zama da ita, in dai ta amince"
"A'a dai ki yi tunani, mafaΙaciya ce sosai, idan kin amince zan tafi na je na same ta a daren nan, na yi mata bayani"
Nana ta ce "Wallahi kar ka damu, zan iya zama da ita"
Ya ce "To Allah ya sa, zan ne yi mata magana, idan ya so ko kuΙin hayar ne ita sai a bata" Nana ta yi ta masa godiya tana murna.
Har Nana ta yi bacci bai dawo ba, sai washegari da safe, bayan ta karya, Hajara ta cewa Nana ta shirya, za su tafi can gidan matar.
Nana ta yi wanka ta shirya, suka fita suka hau abin hawa.
Hajara ta ce "Nana kamar kar ki tafi, kwana biyun nan har na saba da ke"
Nana ta yi murmushi ta ce "Nima haka, sai dai har Abada ba zan taΙa daina yi muku godiya da fatan Alkhairi, ba dan ba Ζaramin jihadi ku ka yi ba, ne ceton rayuwata"
"Ba komai, mu ma bamu san ta inda Allah zai taimake mu ba".
Sun yi tafiya mai Ιan nisa, kafin su je unguwar da matar take.
Mijin Hajara ya sallami mai abin hawan, ya Ιauki kayan Nana su ka shiga layin gidan.
A tsakar gida suka tarar da matar, ta cake Ιauri tana ta lissafin kuΙi. Ta amsa musu sallamar tana yi musu maraba.
Suka shiga Ιaya daga cikin Ιakunanta. Ta kawo musu ruwa da lemo ta ajiye.
Cikin girmamawa Nana ta gaida matar.
Ta kalli mijin Hajara ta ce "Wannan ce yarinyar?"
Ya ce "Eh Nene"
"To a haka dai ta yi zubin nutsuwa, dan dai ka matsa ne, amma ni ba na son yayime-yayime na je na Ιaukko wadda za ta hana ni sukuni, shi yasa duk girman gidan nake zamana nikaΙai abina.
Sannan zan fara zama da ita na wata Ιaya, idan ba ta da matsala mu ci gaba da zama, idan akwai matsala na mayar mata da kuΙinta ta tashi ta bani guri. Kuma wallahi dan ma dai kai ne, da ba zan yadda ba".
Nana cikin girmamawa ta ce "In sha Allah ba za ki same ni da matsala ba, in Allah ya yarda".
Nene ta ce "To Allah ya sa, bari na buΙe Ιaya daga cikin Ιakunan ta zaΙa"
Mijin Hajara ya ce "Ζakunan a rufe, ai na san sun sha Ζura yanzu, ki yi haΖuri tun da akwai gyararru ki kwashe kayanki daga Ιaya ki ba ta. Kin ga Ιakin da ba komai, sai an nemi labule, da sauran abubuwa". Haka ya takure Nene, ta bawa Ιaki Ιaya, mai Ιauke da labulaye da carfet.
Nana ta din ga godiya, ta ce "Saura kuΙin hayar, nawa ne zan biya?"
"Ai na biya ta, ba wani abu in sha Allah, ki zauna kawai"
Nana ta ce "Ai da kuΙi a gurina"
Hajara ta ce "Kar ki damu, ba wani abu ya biya, idan akwai wata matsala ko ba za ki iya zama ba, ki ce Nene ta kira mu a waya, in sha Allah babu wani abu"
Nana sai da ta yi hawayen murna, ta raka su har waje sannan ta dawo.
Ta tarar da Nene ta fito da wake fal za ta tsince. Nana ta lallaΙa ta zauna a kan tabarmar ta ce "Kawo na tsince miki"
Nene ta ce "A'a ke da ki ke baΖuwa, yi zaman ki ki huta, kan Auwwalu ya dawo ya ce ina azabtar da ke, tun da ya ce ni masifaffiya ce". Ita Nana har ta gama zaman gidan ma, ba ta san sunansa ba.
Ta yi murmushi ta ce "A'a ba komai, dan Allah ki bani na taya ki, ai na ga waken da yawa, kuma daga zaune zan taya ki"
Ta dawo da robar waken tsakiyar su, ta kalli Nana ta ce "Nana ko?"
Nana ta jinjina kai ta ce "Eh"
"Ciki ne da ke haka ne?" Nana ta sunkuyar da kai tana tsince wake.
"Ke kuwa me ya yi miki zafi, ki ka baro Ζasar ku da wannan tsohon ciki ki ka taho inda ba ki da kowa? Amma fa ki yi haΖuri da tambayoyina, kin san yanzu duniya babu gaskiya sosai"
Nana ta ce "Haka ne. Mijina Ιan Ζasar nan ne, nice 'yar Nigeria. Na zo neman danginsa ne a nan"
"Allah sarki, to a ina dangin nasa suke? Kuma shi yana ina" Nana ba ta son yayata halin da take ciki, ta fi son sai ta nutsu, ta ga kamun ludayin mutanen Ζasar tukuna, kafin ta saki jiki, amma ga Nene ta saka ta a gaba da tambayoyi. Kafin ta ba ta amsa, Allah ya taimake ta, aka kira Nene a waya, hakan ya sanya ba su ci gaba da zancen ba.
****
Cikin tsananin tausayawa, yake bin matashin da kallo, saboda yadda duk ya fita daga hayyacinsa.
Cikin damuwa ya kira sunansa a hankali ya ce "Mahmudu" ya Ιago idanunsa a galabaice, ya kalli wanda ya kira sunan nasa.
"Ka yi musu bayanin duk abin da ya faru, ka faΙa musu iya gaskiyarka, ko Allah ya sanya su rabu da kai, wannan wahalar da ka ke yi ta isa haka?"
Murya a cunkushe ya ce "Me zan gaya musu? Me zan ce da ka ke tunanin idan na faΙa za su yarda da ni?"
"Iya abin da ka sani Ιin zaka faΙa"
"A tunaninka tsawon wannan lokacin, ba iya abin da na sani Ιin ba nake gaya musu? Sai dai akwai abin da ko za a kashe ni, ba zan furta ba"
"A'a Mahmudu, idan har za ka ci gaba da shiru da Ιoye wasu abubuwan, ba fa za a Ζyale ka ba, za su ci gaba da azabtar da kai ne kawai a banza. Ni dai zan faΙi abin da na sani"
Mahmudu ya ce "Ka kwana da sanin, ka na furta wani abu, to tabbas kai ma za ka tsinci kanka, a halin da nake ciki yanzu. Ka yi shiru mu bar komai a yadda yake. Rufe sirrin Imam wajibi ne, akwai abin da idan na furta, zai iya janyo asarar rayuka ba Ιaya ba ba biyu ba, in dai wahala ce na san Ιayan biyu ne, ko na mutu ko ta wuce. Abu Ιaya nake so da kai, shi ne; dan Allah Ashiru, ka binciko a wani hali yake ciki? Tun da muka baro Nigeria, ba a haΙa mu a mota Ιaya ba ma, ban san ina aka yi da shi ba"
Ashiru ya ce "Kai wannan fa babban aiki ne, tun Ιatansa fa, ba a bari labarin ma ya fita ba, balle a sanya ran jin halin da ake ciki yanzu, amma dai zai Ιan ΖyanΖyasa a Ιoye, na ga ko za a samu wani bayani. Sannan ina Ζara neman afuwarka a kan abin da ya faru"
"Babu komai kar ka damu, an saki sauran ko? Su Sulei"
"Eh an sake su, ai tun da suka fuskanci, ba su ma san a kan me ake binciken ba, an sake su amma fa an killace su"
"Shikenan tashi ka je, kar a fahimci wani abu" Haka Ashiru ya tashi ya tafi yana waiwayen sa.
*****
Sannu a hankali take tafiya, yana zaune a cikin mota yana hangen ta, ta tsallako titi, ta nufo motarsa tana murmushi.
Ta buΙe motar ta shiga ta ce "Yaya Abba me ka ke jira a titin ne haka?"
Ya lumshe idanunsa, jin yadda Ζamshin turaren jikinta, ya gauraye motar baki Ιaya. Ya ce "Wa zan jira ban da Ζanwata, kwana biyu ban gan ki ba, da gida zan bi ki ma, to sai na ji tsoron kar na je ko ki na da baΖo, ban sanar da ke zan zo ba. Kawai na tsaya a nan na ce bari na jira fitowar ki"
Ta yi murmushi ta ce "Ko akwai baΖo, ba dolena na sallame shi na saurari yayana ba, kuma wani baΖi zan yi da safe haka?. To me ma zan samu ne?" Ta yi maganar tana laluba motar.
Ya yi dariya ya ce "Laluba ki Ιauki duk abin da ki ke so" ta yi dariya ta ce "Dan ka san ba ka ajiye komai ba ko? Mu je kar Mummy ta yi ta jira na"
Ya ce "Ok" ya fara tuΖa motar a hankali. Yana tuΖi yana satar kallon Jamila, wani irin kyau take Ζarawa a idanunsa kullum. Kullum Ζara shiga ransa take yi, ga shi ya kasa fitowa ya sanar mata da ainihin abin da yake cikin zuciyarsa. Duk wasu alamu da zai nuna mata sonta yake yi, ya yi amma ya kasa gaya mata baki da baki. Su na daf da shiga layin gidan ya tsaya ya ce "Ζanwata"
"Na'am Yaya Abba"
"Ina son za mu yi wata magana da ke, amma maybe sai na dawo tukuna"
Ta yi murmushi tare da gyara zaman mayafinta, ta ce "To shikenan babu laifi, a dawo lafiya"
"Allah ya sa, ki kula mini da kan ki Please, zan kira ki idan na je kasuwa"
Ta ce "To, ka sayo mini aya mai sukari a kasuwa"
Yayi dariya ya ce "Aya kawai?"
"Eh ita kawai"
"To an gama ranki ya daΙe" ta fita daga motar tana Ιaga masa hannu"
Da ta shiga cikin gida,ba ta tarar da Hajiya Sa'a a falo na, dan haka ta bi ta bedroom.
Ta tarar tana wanka, ta nemi guri ta zauna tana danna wayarta. Can Hajiya Sa'a ta fito daga ita sai towel. Jamila ta kalle ta ta kawar da kai.
"Jamila har na fitar da ran za ki zo ai"
"Ba na jin daΙi ne, shi yasa da kamar ma ba zan zo ba fa"
"Eyya sannu, bari na shirya ki raka ni mu je na duba Fatuhu"
Jamila ta ce "Tom"
Hajiya Sa'a ta zauna a kusa da Jamila, ta Ιan riΖo hannunta ta ce "Daughter wai ke haryanzu ba za ki waye ki faso gari ba? Ina ta saita ki a hanya kin Ζi yarda ki shiga layi"
Jamila ta Ιan Ιata fuska tana zame hannunta ta ce "Gaskiya ni Mummy ba na so, ni me zan tsinta a jikin mace 'yar uwata, ni abin ma bai yi mini tsari ba sam wallahi"
Ta yi murmushi ta sake matsawa kusa da Jamila ta ce "Ai da gwaji jirgin sama ma ya tashi Jamila, da za ni jarraba da kin gane abin da nake nufi. Shi ne za ki yi babu ruwanki da damuwa da aure, ko tashin hankalin yin planing saboda Ιaukar ciki. Kuma...
"Ni dai gaskiya Mummy ba na so, ni me zan tsinta a jikin mace 'yar uwata, ni abin ma bai yi mini tsari ba sam wallahi"
Ta yi murmushi ta sake matsawa kusa da Jamila ta ce "Ai da gwaji jirgin sama ma ya tashi Jamila, da za ni jarraba da kin gane abin da nake nufi. Shi ne za ki yi babu ruwanki da damuwa da aure, ko tashin hankalin yin planing saboda Ιaukar ciki. Kuma...
"Ni dai gaskiya Mummy ba na so, ni ban ga abin da mace za ta tsinana mini ba, ni bai ma yi mini tsari ba gaba Ιaya gaskiya. Ba gara na bi maza ba"
Hajiya Sa'a ta kwashe da dariya, ta ce "Yaro man kaza, ai shikenan Daughter, bari na shirya mu fita". A gaban Jamila ta gama shirinta, ba tare da jin nauyin abin da ta tunkari Jamilan da shi ba, ta gama suka fita.
Umman Fadila ce take kallonta a tsanake, bayan ta gama yi mata komai za ta tafi. "Fadila"
"Na'am Umma"
"Na san yanzu da da ba Ιaya ba ne ba, amma ko yaya Ιan abin da ki ke da shi idan ya samu, ko abinci ko kuΙi, ki din ga bayar da sadaka, da nufin Ubangiji Allah ya kawo muku Ιauki,ya sassauta muku wannan yanayin da ku ka tsinci kan ku a ciki"
Fadila ta jinjina kai ta ce "In sha Allah"
"Tun kwanank da kawunki, ya zo ya duba mijinki, ya kira ni yake mitar, kun tare ku na maganin Asibiti, kun Ζi mayar da hankali ku yi na gargajiya. Na ce masa mijin naki ne Ιan aΖida, kuma ke na haifa ba shi ba, balle na yi masa dole. Amma nima hankalina ya fara karkata ga a yi na hausan, mijinki mutumin kirki ne, ba zan manta halaccinsa a gare mu ba, dan haka na bayar da kuΙi a yi saukar Alqur'ani, da fatan Ubangiji Allah ya yaye masa koma mene ne, tun da shi Alqur'ani waraka ne. Ki yawaita karanta masa, ko ki kunna ya saurara, ko ki din ga busa wa a abincinsa ko abin shan sa.
Ba mu san a inda za a dace ba, wannan abu ya Ζi ci ya Ζi cinyewa, na Asibitin ba wani haske da ake gani, idan hagu ta Ζi ai sai a koma dama ko?"
Fadila ta ce "Haka ne Umma, in sha Allah, zan yi duk abin da ki ka ce, kuma addu'a mu na yin ta sosai, ina yi masa. Sai dai kin san lamarin Ubangiji ba a yi masa dole, duk addu'arka sai lokacin yankewar abu ya yi tukuna".
Umma ta ce "Haka ne, amma hakan ba ya nufin a sare, a ce an haΖura gaba Ιaya ba za a yi ba" Sosai Fadila take jin daΙin rarrashi da nasihar da Umma take yi mata a duk lokacin da ta zo gidan.
Ko da su Hajiya Sa'a suka je gidan Alhaji Fatuhu, Alhaji Zailani yana gidan. Yana sashen Alhaji Fatuhu tare.
Alhaji Zailani ya din ga kallon Jamila, yana ganin kamar ya santa, amma ya manta a inda ya san fuskarta.
Suka gaisa Hajiya Sa'a ta kalli Fatuhu ta ce "Yaya ya jikin naka?"
Ya jinjina kai ya ce "Alhamdillah"
"Ka na samun sauΖi, ko dai haryanzu babu afuwa?"
Ya yi murmushi ya ce "Da sauΖi" Daga haka suka koma hira da ita da Alhaji Zailani, tamkar ba dubiya su ka zo ba, bar sai da abin ya ba wa Jamila mamaki. Sun jima sannan su ka shiga suka gaisa da matansa suka tafi.
Su na tafe a hanya Jamila ta ce "Mummy, mara lafiyar nan shi ne wanda Ιan sa ya mutu kwanaki ko? Yaran da Nana take koyarwa a makaranta"
"Eh shi ne"
"Allah sarki, to shi wannan Alhaji Zailanin, ko shi ne a can quaters Ιin bayan makarantar nan na Ζofar famfo?"
Hajiya Sa'a ta kalle ta ta ce "Ya aka yi ki ka san shi?"
"A'a na tambaya ne dai kawai, kenan shi ma Nana ta yi aiki a gidansa, yana da 'ya Shukura ko?" Hajiya Sa'a ta jinjina kai tana kallon Jamila.
"To ai da Nanan gidanmu zai aura, ba a yi ba, aka yi aurenta da wannan Buzun, lokaci Ιaya kawai ya fito ya ce wai zai aure ta"
Shiru Hajiya Sa'a ta yi tana kallon Jamila, ta san abu ne mawuyaci a ce haka kurum Alhaji Zailani ya ce zai auri yarinyar da ta fito daga gida kamar na su Nana, da Ζyar idan ba ya san sirrin da ke tattare da Nanan ba. A take gabanta ya faΙi, dan kuwa ko me za a yi ba za ta taΙa barin Alhaji Zailani ya riga ta amfani da jinin Nana ba"
Jamila ta ce "Mummy ya na ji kin yi shiru ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Babu komai Jamila, dole mu nemo Nana ne duk inda ta shiga"
Jamila ta ce "Saboda me?"
"Saboda Ζungiya, za ta iya neman ki kawo jinin mafi kusanci da ke, a kowane lokaci!
Ayshercool
08081012143
64
Jamila a ranta ta ce "Ni kuwa zan ga abin da ya ture wa Buzu naΙi, zan ga abin da zai faru idan na bijirewa buΖatar Ζungiyar"
Jamila ta numfasa ta ce "Mummy, dan Allah tambayar ki zan yi"
"Ina jin ki"
"Wai dan Allah, ya aka yi ki ka shiga Ζungiyar nan?"
Hajiya Sa'a ta kalli Jamila, sannan ta mayar da hankalinta kan tuΖin da take yi tana murmushi. Ta ce "Dogon labari ne Jamila, amma me yasa ki ka tambaye ni?"
"Ina son na ji tarihin gwagwarmayar ki ne, ko nima zan daure na yi koyi da jarumtar ki, haryanzu wasu lokutan zuciyata tana rawa ne a kan lamarin"
"Ai na ga alama kam. Jamila na sha gaya miki, muddin ki na son cimma abin da ki ke buri a rayuwa, babu ruwanki da kowa kan ki kawai za ki din ga dubawa.
Na tashi a gidanmu bamu da komai, babata da babar Fatuhu, su ne Ζanana a matan gidan, kamar dai yanayin rayuwar gidanku, a haife ka, ba a damu da Ιawainiyarka ba.
Manyan yayyenmu babu ruwansu da mu, saboda iyayen su mata sun cusa musu aΖidar Ζin iyayenmu. Babanmu ya mutu shi ma saboda bai bar komai ba, babu wanda ya damu da mu.
Yayyenmu iyayensu kadai suke taimako da Ζannen su, mu kuma namu iyayen ke ta fafutuka da wahala.
Fatuhu ya yi ta faΙi tashi da rayuwarsa, da ta mahaifiyarsa, sai dai yana tunawa da ni.
Zailani tsohon saurayina ne, da rashin abin yi ya hana mu yin aure da shi.
Ya shiga makaranta, bisa tallafin karatu, a can ya samo mana wannan Ζungiyar.
Shi kuma lokacin Fatuhu ya fara zuwa kasuwa, ni kuma na riga na yi aure.
Zailani ya gaza jan Fatuhu Ζungiya, saboda mutum ne mai tsantseni da ra'ayin riΖau. Ni kuma har a lokacin mijin da nake aure, ba shi da komai ba na samun irin rayuwar da nake so. Sannu a hankali na ci gaba da hulΙa da Zailani ya kai ni Ζungiya, ya zamana ba na rasa kuΙin kashewa dai.
Fatuhu kuma ya ja Zailani kasuwa, suke kasuwanci tare, sai dai duk da tasirn Ζungiya, Zailani ya kasa tara abin da Fatuhu yake da shi.
Kin san waye mutum na farko da na fara bayarwa?"
Jamila ta girgiza kai alamar a'a.
"Babban yayanmu, da iyayensu su ka mayar da mu saniyar ware a gida"
Jamila ta jinjina kai a Ιan tsorace ta ce "Sai kuma ki ka ba da wa?"
Hajiya Sa'a ta yi murmushi ta ce "Zan Ζarasa miki nan gaba kaΙan, yanzu bari mu Ζarasa gida, akwai abin da nake son yi"
Jamila ta jinjina kai tana satar kallon Hajiya Sa'a.
Hajiya Sa'a ta ajiye Jamila, sannan ta ja motar ta tafi. Tana tafe ta kira layin Alhaji Zailani.
Sai da ta kusa katsewa, sannan ya Ιaga tare da yin sallama.
Ta ce "Ai na zata ba ka Ιaga ba ne"
Ya ce "A'a ina tuΖi ne? Lafiya?"
"Ζalau, tambayarka abu zan yi"
Ya ce "Ok, ina jin ki"
"Ashe kwanaki da aure zaka yi?"
Ya ce "Yaushe?"
"Kwanakin baya mana, za ka auri wata yarinya Nana"
Kamar tana gabansa ya tsuke fuska ya ce "Waye ya gaya miki"
"A'a ba sai ka ji wanda ya gaya mini ba, zancen Duniya ba ya Ιuya ai, sai dai ka sani na san da abin da ka ke nema, ni ma shi nake farauta"
"Sa'a ban fahimci abin da ki ke nufi ba fa, ki yi mini bayani gwari-gwari "
"Za ka fahimta ne, ka je ka nutsu ka yi nazari" ta kashe wayar ta ajiye ta ci gaba da tuΖinta.
*****
Yana zaune a takure a gurin, ya yi shiru tamkar mai jiran tsammannin wani abun, aka buΙe Ζofar Ιakin da yake . Wasu tiΖa-tiΖan murΙaΙΙun maza suka shigo. Ba su yi wata-wata ba, suka yi sama da shi, suka fito da shi daga gurin da yake zaune.
Wani Ιakin aka sake kai shi, sai dai yana shiga ya yi turus, ganin mutumin da yake zaune a cikin Ιakin.
Ζartin suka juya suka fice, suka bar shi daga shi sai mutum biyu a Ιakin.
"Bismillah ka zauna mana" cike da tsoro ya Ζarasa ya zauna yana rarraba ido, ya sunkuyar da kansa.
"Mahmudu, Ιagowa za ka yi ka kalle ni ai"
Ya Ιaga kai ya saci kallon mutumin, ya mayar da kansa ya sunkuyar.
"Na san wannan zaman takurar ya ishe ka zuwa yanzu, kasancewarka mutum da ya saba da 'yanci a baya.
Ina son ka buΙe kunne ka saurare ni da kyau, tambayoyi nake son na yi maka, muddin ka gaya mini gaskiya ka bani amsa, zaka iya samun sassauci, ko ma na yi umarnin a sake ka, ka yi tafiyarka gaba Ιaya"
Ya jinjina kai ba tare da ya Ιago ba.
Mutumin ya sauke rawnain fuskarsa ya ce "Na san an yi maka wannan tambayoyin an kum a baya, yanzu ma zan sake jaddada maka su, me yasa ka sace Imam ka kai shi Nigeria, da ka kai shi kuma me ka yi masa?"
Kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya girgiza kai ya ce "Ban sace shi ba, kuma ban yi masa komai na cutarwa a Nigeria ba"
"To me yasa ka tafi da shi Nigeria ba ka sanar da kowa ba?"
Mahmudu ya ce "Wannan wani sirri ne da ba zan iya tona shi ba, ko da za ku salwantar da rayuwata, wani abu wanda daga ni sai shi Imam"
Abduou ya jinjina kai ya ce "Da amincewar sa ku ka tafi Nigeria kenan?"
"A'a hasalima bai san komai ba, ba wani da zaΙi ne da ya rage, sai abin da na aikata Ιin"
"Mahmudu, na fuskanci zama da maΙaukin kanwa ya sanya maka farin kai. Rayuwa da Imam ya sanya ka koyi baΖin taurin kai irin nasa. Amma ka snai, kama da wane ba ta wane, kuma ina fatan ka san da tun da aka Ιaukko shi daga Nigeria har yau ba ya hayyacinsa, bai yi magana da kowa ba?"
Mahmudu ya girgiza kai ya ce "A'a ranka ya daΙe. Rashin gane kowansa ba shi da nasaba da zuwansa Nigeria"
"Saboda me?"
"A can Ιin ma ba gane kowan yake yi ba"
Abduou ya Ιan yi shiru sannan ya ce "Zoben Azurfarsa fa guda Ιaya da baya hannunsa, ina fatan ka san inda wannan yake?"
A zabure Mahmudu ya kalli Abdou matawalle, jin abin da ya faΙa.
"Ka daina zaro mini ido, kwanaki biyu kawai ka ke da su, ka faΙi inda zoben yake, ko kuma ka rasa rayuwar ka baki Ιaya, zaΙi ya rage naka"
Abdou ya miΖe, ya ja rawaninsa ya rufe fuskarsa ya fice daga Ιakin.
Cikin matsanancin tashin hankali, ya bi bayan matawalle da kallo. A Nigeria babu wanda ya san ma'anar zobunan da suke hannun Imam. Kuma ya yi iya ΖoΖarinsa gurin ba shi dukkanin kariya, balle ya ce wani ya san muhimmancin su ne ya karΙa.
MatuΖa ya ji yana son ya ga Imam, ya gana da shi, sai dai ya san ko mai zai yi babu mai ba shi wannan damar. Ga shi ya ji Abdou ya ce tun da aka dawo da shi, bai farfaΙo ba balle ya yi magana. Gefe guda kuma yana jin tsoron kar a koma a Nigeria a bibiyi Nana, saboda za ta shiga matsala ba kaΙan ba.
Koma a wani hali take ciki yanzu? Ya tambayi kansa yana jin wata irin damuwa ta mamaye zuciyarsa, tare da Ιora wa kansa laifi amincewa da auren Imam da Nana, ya kuma Ιoye mata komai a kan Imam Ιin. Ya dafe kansa da yake jin tamkar zai tarwatse dan damuwa.
****
Nana ta nutsu da zaman gidan Nene, duk Nenen akwai faΙa kamar yadda Hajara da mijinta suka din ga faΙa, amma sam hakan bai damu Nana ba, dan ba ta yi mata abin da za ta yi faΙan.
Nana ta fuskanci Nene sana'ar Abinci take yi, wasu lokutan tun safe idan ta fita sai daf da magariba take dawowa. Ta kan dawo tar e da yaran da suke yi mata aiki, su fara rage aikin Abincin sayarwar da za a yi washegari.
Nana tana jin yadda Nene take yi musu bala'i bisa kuskure kaΙan. Nene ta din ga gwada Nana, da ajiye kuΙi ko ina ta ga dama, ko ma ta fita ta bar Ιakunanta a buΙe, amma ko allura ba ta taΙa rasawa ba.
Kullum sai ta ba wa Nana Abinci, na safe kan su fita na sayarwa ta ba ta na rana, idan sun dawo ta ba ta na dare, har da ma tsaraba ta masu ciki.
Ma'aikatan Nene sun Ιauka ma, Nana 'yar uwatta ce.
Idan sun dawo Nana kan fito ta ce za ta taya su aiki, Nene ta yi ta faΙa ta ce ba za ta yi ba. Sai dai hakan ba ya hana Nana kama musu wasu ayyukan.
Nana ta shafe kusan wata guda a gidan Nene, ta ga kullum sai Nene ta ba ta Abincin nan sau uku, ba ta taΙa nuna mata ta gaji da ciyar da ita da take yi ba, wasu lokutan har tambayarta take yi, ko tana son cin wani abin ne daban.
Da daddare ta kira Nana, Nana ta fito ta zauna a kusa da ita. Ta buΙe takarda fal kifi ta ce "Nana ga kifi ko za ki iya ci, idan Ζarnin ba zai dame ki ba".
Nana ta dube ta ta ce "Nene, dama ina son mu yi magana ne"
Nene ta ce "To ina jin ki"
"Na ga kullum sai kin bani Abinci sau uku a rana, na ce ko za ki ba ni wani aikin na din ga yi miki, a maimakon Abincin da ki ke ba ni, ko gurin sayar da Abincin sai na din ga bin ki, ko wanke-wanke na din ga yi miki"
Ta dubi Nana, sannan ta numfasa ta ce "Ni kuwa duk rashin imanina, da wannan tsohon cikin sai na saka ki aiki, dan dai abin da za ki ci sau uku ba zai gagara ba. Ban san takamaiman abin da ya kawo ki Ζasar nan ba, ban san kuma lokacin komawar ki ba, amma ba na tunanin abin da za mu ci ni da ke zai gagare ni. Ba zan Ιoye miki da fari ban so zamana da ke a gidan nan ba, saboda ba na son matsi da takura ko kaΙan, da su Auwwalu sun matsa ne, dan kora da hali na so yi miki. Amma yanayin ki ya nuna mini ki na Ιauke da damuwa mai nauyi a zuciyarki. Ba Ζaramin dalili ne zai sanya yarinyar mace, mai Ζanan shekaru kamar ki, ta baro gida ta taho uwa Duniya ba ga juna biyu. Kuma ki na yawan zama ki yi shiru, fuskar ki Ιauke da damuwa. Na kuma jarraba ki ta Ιangarori da dama, ban ga alamar rashin nutsuwa a tare da ke ba, shi yasa na ji zan iya zama da ke. Amma Nana tsakaninki da Allah wannan juna biyun na ki, na halal ne? Kuma da sanin iyayenki ki ka taho nan?"
Tambayar Nene ta yi wa Nana mugun zafi a Ζirjinta, amma sam ba ta ji haushinta ba, dan kowaye dole ya yi irin wannan tambayar. Sai da ta ji hawaye ya cika mata ido, da tuna ire-iren waΙannan tambayoyin dole ta ci gaba da amsa su, a cikinta da abin da za ta haifa, muddin ba gano inda Sayyid yake ta yi ba.
Ta haΙiye wani irin yawu mai zafi ta ce "Nene cikina na halal ne, ni matar aure ce, ban kuma gaya wa iyayena zan taho nan ba, sai da na riga na yo nisa da gida"
"To saboda me, kuma ina mijinki?"
Kawai Nana ta fashe da kuka, ta ce "Shi na fito nema, mijina da danginsa"
Nene ta ce "Shikenan, ya isa haka ki kwantar da hankalinki, mu bar maganar ma yi wani lokacin. Amma sai dai ki yi haΖuri, dan dole sai mun Ζarasa wannan maganar Nana, saboda ni uwa ce, dole na mu'amalance ki na yi miki nuni da abin dai-dai da akasin haka. Ban ga alamar ki na magana da wani a can gida ba, ko ta tarhon hannunki ce ba. Mahaifiyarki tana raye?" Nana ta jinjina kai tana share hawayenta.
Nene ta ce "Shikenan, share hawayenki mu ci kifin"
Ta girgiza kai ta ce "Ζarnin hawa kaina yake yi na Ζoshi" daga haka Nana ta tashi, ta koma Ιakinta. Sai dai ta din ga kuka, saboda ita kanta ba ta san ta ina al'amuran za su warware ta cimma abin da ta fito nema ba.
Shukura ta rasa gane kanta da kanta, saboda rashin lafiya da take ta fama, ga Sagir ya rage ba ta kulawa, duk da yana ta Ιoye-Ιoye amma tuni ta daΙe da gano shi, sai dai ta maze ita ma ba ta nuna masa ba.
Hajiya Amina ce ta je gidan, Shukura ta ji daΙin zuwanta sosai da sosai, a nan Hajiyar take gaya mata batun Nana.
Cikin damuwa Shukura ta ce "Wallahi Mami, tun da aka yi auren nan, nake jin tausayinta, gaba Ιaya ban ga riba a abin da babanta ya yi mata ba. Babu bincike babu komai a ce an aura mata mutum, wasu lokutan na kan rasa ina tunanin mutanenmu yake tafiya"
"Ke dai a yi sha'ani kawai, amma na jinjina batun ni kaina"
"Shikenan an saka rayuwarta a gagari, ga Ζarancin shekaru" suka ci gaba da jajanta lamarin. Hajiya ta fuskanci yanayin Shukura kamar ba ta da cikakkiyar lafiya, ta kira Doctor Sharif ya zo ya duba ta.
Shukura ba ta so ba sam, dan ko Ζaunar ganin Sharif Ιin ba ta yi, amma tuna ta yi wa Hajiya AlΖawarin komai ya wuce, ta yi tawakalli ta dangana ya sanya ta haΖura.
Ya zo har gida ya yi mata gwaje-gwaje, ya kuma tabattar mata da tana da juna biyu.
Hajiya Amina ta din ga murna, a duk lokacin da aka ce ga wata mace da ciki, sai ta yi ta murna, ta ji dama ita ce.
Shukura ba ta wani yi murna ba, saboda ita gaba Ιaya haihuwar ma ta fita daga kanta.
Da yamma Hajiya Amina ta koma gida, saboda tsabar zumuΙi, tana zuwa ta tarar da Alhaji Zailani a gida, ta hau ba shi labarin Shukura wani cikin ne da ita. Wata irin mummunar faΙuwar gaba ce ta ziyarce shi, yana tsoron a wannan karon ma, kar a nemi ya bayar da wani abu da ya danganci iyalinsa.
Hajiya Amina ta din ga jin wani irin bacci, tana idar da sallar isha'i, ta Ιungire a gurin ta hau bacci.
Ita da Nana ta gani a falo, a zaune suna hira, kamar yadda suka taΙa yi kwanaki lokacin Nanan, na zuwa gidan rainon Haidar.
Ta ce "Hajiya, kin kuwa ci gaba da bibiyar Likitoci a kan matsalar rashin haihuwar ki?"
Hajiya Amina ta ce "Nana ai ni na haΖura ma na bar wa Allah, yanzu shekaruna sun wuce na haihuwa"
Nana ta ce "A gurinki ba, a gurin Allah yana bayar da falalarsa a inda ya so, da kuma lokacin da ya so ne. Ki daina biye wa wannan mijin naki, ya din ga sarrafa rayuwar ki yadda yake so. Ki nemi mafita a kan matsalolinki.
Kuma Shukura ta dage da Addu'a, kar wannan Ιan ma ya sake raba ta da shi"
Maganar Alhaji Zailani ce ta tashi Hajiya Amina daga mafarkin da take yi, tana kallonsa kawai ta ji gabanta ya faΙi"
"Lafiya ki ke kwance a Ζasa haka ki ke bacci?"
Ta ce "Bacci ne ya Ιan Ιauke ni ban sani ba"
Ya ce "To ki tashi ki koma gado mana, kar wuyanki ya yi ciwo" Ta yinΖura ta tashi ta canza kaya ta hau gado ta kwanta, sai dai ta din ga jin mafarkin da ta yi da Nana a jikinta, tamkar a zahiri ya faru.
Fadila ce zaune a kusa da Alhaji Fatuhu, gefenta kuma jaririnta ya yi wayo, yana ta bacci.
Ta miΖa masa lemon da ta haΙa masa a kofi, ta zuba masa ido, yana sha a hankali.
A ranta take faΙin "Ubangiji Allah ka bawa wannan bawa naka lafiya, albarkacin ayoyin Alkur'ani'
Ta kalle shi tsaf, ya yi rama ta ban mamaki, dan ma yanzu ya Ιan ciko, ba kamar da ba" ya shanye ya miΖa mata kofin, ta karΙa ta ajiye a gefe. Ta matsa kusa da shi tana Ιan Ζara gyara masa filulluka.
Ya ce "Na gode sosai, Allah ya yi miki albarka, ya raya miki Muhsin"
Ta ce "Amin Daddy"
"Da lafiyata Ζalau, da mun yi sauri, nan da wata wata taran, ki kuma haifo mana wani" Murmushi ta yi ta ce "Allah ya baka lafiya ya tashi kafaΙunka" ya amsa da Amin yana riΖe hannunta cikin nasa da ya yamuste kamar na tsoho.
Hajiya Suwaiba ta ce ta shigo Ιakin, Fadila ta Ιan zabura ta ja da baya.
Hajiyar ta ja tsaki ta ce "A hakan ma da kake wani abin ka ke ΖoΖarin yi, ai sai ku rufe Ζofa kar yara su faΙo, a lalata mini tarbiyyar yara"
Fadila ta ce "Haba Hajiya, abu na ba shi ya riΖe hannuna, and laifi ne dan ya riΖe hannuna wani abin ki ka ga na yi?"
"Kar ki yi mini rashin kunya dai? Idan ma yin ku ke, ku Ζarata ku da Allah"
Ran Fadila ya yi mummunan Ιaci, ta yinΖura da niyyar, ta Ιauki Ιan ta ta bar Ιakin, amma ya riΖe hannunta, ya hana ta tafiya. Hajiya Suwaiba ta gama bala'inta ta tafi ta bar su.
Idan ya ce Suwaiba ba ta ΖoΖari a kan rashin lafiyarsa ya yi Ζarya, tana iyakar ΖoΖarinta amma wasu lokutan tana da saurin Ζosawa gashi haryanzu azababben kishi na Ιawainiya da ita.
****
Gidan Maijidda kuwa, Iliyasu bai taΙa tsammanin, Maijidda na da taurin kai haka ba. Gaba Ιaya ta tarkata shi ta yi watsi da shi. Iyakarta da shi, ta girka Abinci ta ba shi, idan buΖatarsa ta tashi, ya yi kiΙansa ya yi rawarsa. Gaba Ιaya ta sanya damuwa a ranta, ta rame sosai da sosai, dan ko Abincin kirki ba ta iya ci, kusan kullum cikin kuka take, ko ta zauna ta yi shiru. Ga shi ya lura 'yan uwanta sun fara gajiya da sinturin kai Ζararta da yake yi, ba yau ba gobe.
"Anya ka na ganin haka rayuwar Imam za ta ci gaba, duk lokacin da ya farka sai ihu da fizge-fizge, sai dai a yi ta yi masa allurar da zai yi bacci? Idan aka bar shi a haka rayuwarsa fa ta nakasa kenan har abada"
Sultan ya ce "Abdou, ni kaina ala'amarin nan yana damuna, na rasa yadda zan yi. A Ιangaren ΖwaΖwalwar ma, babu wani gamsashshen bayanin abin da ya faru da shi. Ta Ιangarenka ma babu wani nagartaccen bayani daga bakin shi yaron, balle mu ji ko wani abin Ιin aka yi masa".
"Sultan, ka Ζi bayar da dama a sanya 'yan doka, su maguza yaron nan, ya faΙi gaskiya ko ya Ζi Allah"
Sultan ya girgiza kai ya ce "A'a, duk ranar da Imam ya samu lafiya, muddin ya ji labarin an cuzguna masa, zai yi fushi, kuma zai ji babu daΙi kai ka san irin alaΖar da take a tsakaninsu."
"Amma yanzu ai yanzu a kan gaΙar bincike a ke Sultan. Amma tun da haka ka ce Shikenan, za a ci gaba da bin komai sannu a hankali"
Sultan ya amsa da "Yauwwa"
BAYAN WATA ΖAYA
Sabo turken wawa, rashin ganin Ζaisar da Nana ta daina yi, ya sanya ta din ga tunanin ko wani abin ne ya faru da shi.
Sai dai yau kwatsam cikin barcinta, ta ganta a cikin Librarynsa. Sai dai ta gurin Ζwalam babu litatafai babu kayan rubutunsa sai mudubin da yake nuna mata abubuwa a cikinsa.
Ta waiwaya ta lelleΖa, amma babu Ζaisar babu alamunsa.
Wani littafi guda Ιaya tal, ta hango a kan teburin rubutun Ζaisar, ta Ζarasa ta nufi teburin ta Ιauki littafin.
Bangon littafin na fatar wata dabba ne. Dan har da gashi-gashi a jiki. Yanayin bangon littafin ya sanya ta yi tunanin, ko mene ne a rubuce a littafin ba yanzu ya faru ba, ya kwana biyu da faruwa. Littafin ba wanda ta karanta tarihin su Lanti ne a ciki ba, wani ne daban.
Hoton wata alΖarya ce, da ke tsakanin duwatsu, da aka rarake aka samar da katafariyar daula.
Ta buΙe littafin shafin farko, ta fara karantawa.
"Tushiya..." Shi ne abin da ke rubuce a shafin farko na littafin.
"Ka sani,har abada da Ιan Gari a kan ci gari. Kuma ba a cimma buri da tausayi ko jin Ζai. Wannan mataki na farko kawai ka cimma, na sharar fagen cimma nasararka.
Ka na buΖatar sanya wa mutane tsoronka, da shakkarka domin cimma burinka, kuma hakan ba zai taΙa yiwuwa ba sai ka zubar da jini, duk wanda ya biyo ta hanyarka ka datse rayuwarsa, kar ka damu da adadin rayukan da za a rasa, ka zubar da jini ba ΖaΖΖautawa har sai mutane sun fara jin fitsari a duk lokacin da aka ambaci sunanka.
Ka kame mutanen gefen alΖaryar nan, ka mayar da su bayi, matansu ka mayar da su naka, mazansu su zama bayinka, ka yi amfani da Ζarfinsu da fikirarsu ka gina alΖaryar da babu wani mahaluki da zai iya Ιaga maka yatsa, kar ka gushe kana aikata hakan, har sai buΖata ta biya.
Zaka kasance cikin sanyawar albarkar Aljanu, za su baka dukkanin goyon bayan da ka ke buΖata kar ka saurarwa kowa"
Cikin damuwa mutumin ya kalli mai maganar ya ce "Ka sanya ni na kashe mahaifina da hannuna, yanzu ga wani abin ka sake zuwar mini da shi, kar ka manta ina da 'yan uwa maza, ba za su zuba mini ido, duk na yi wannan ba, na Ιauki abin da ba nawa ba, alhalin su na gaba da ni ba"
Ji ta yi mudubin gurin yana wata irin Ζara tamkar zai tsage, a take ta ajiye littafin ta nufi mudubin tana kallonsa.
Wata irin wuta ta gani tana ci a cikin mudubin. Wutar mai matuΖar ban tsoro saboda yadda take ci. Wani mashi ta gani a soke a jikin wani Ζwarangwal, Ιaya gefen mashin an yi rubutu a jikin wani abu mai kama da takarda. Ta Ζara matsawa domin karanta mene ne a jikin takardar amma ta ga mudubin yana hayaΖi yana baΖi yana washewa.
A kusa da wutar ta ga wani abu mai kama da mutum, a lulluΙe da wani mayafi yana zuba wani abu a cikin wutar wanda yake Ζara sanya wutar Ζara balbala.
Imam... ta iya gani a rubuce a jikin abin, mai kama da takarda, a gaban Imam Ιin akwai wani sunan, sai dai ba ta iya karanta sunan ba. A jikin wutar ta ga taswirar fuskar Sayyid yana jijjiga jikinsa na Ζonewa yana kururuwa yana kiran sunanta.
Wata irin zabura ta yi ta kuma tunkarar mudubin gadan-gadan, mudubin ya yi wata irin tsawa ta ja da baya ta faΙi Ζasa.
A gigice Nana ta farka, ta haΙa uban gumi ta yi sharkaf, ga wata irin Ζullewa da cikinta ya yi haΙi da mararta. Ta yinΖura da Ζyar ta tashi ta tafi banΙaki, a zatonta fitsari take ji, ko kuma bayan gida, amma ta ji ba bayan gida take ji ba, ta fitsarin amma still mararta kamar an saka wani abu an Ιaure mata. Ta yi alawala ta koma Ιakinta.
A zaune take salla saboda yanayin girma da nauyin da cikin ya yi. Ta kasa tuna abin da ta gani, sai iya wutar nan da wannan tsawar da mudubin ya yi su kawai take iya tunawa.
"Allahumma ajirni mina narr"
Ta maimaita da tuno yadda ta ga wutar nan. Ta ji sam mafarkin nan bai yi mata daΙi ba, ko mene ne babu Alkhairi a tattare da shi sam.
Sai da gari ya waye, sannan ta samu afuwa daga wannan Ιaurewar da mararta ta yi da bayanta. Jikinta babu daΙi, haka nan take lallaΙawa ta daure kar Nene ta fuskanci wani abu.
Nana ta dama kunu da kanta, ta tashi tana tafe da kyar, Nene ta ce "Nana wai cikin nan naki wata nawa ne?"
Ta Ιan yi shiru ta ce "Ina ga bakwai ne"
"Anya kuwa Nana, kalli yadda ya cure guri Ιaya ya yi Ζasa sosai a ce cikin nan na watanni bakwai ne kawai? Amma ban sani ba ko biyu ne. Yakamata ma mu je Asibiti a duba ki, ni wallahi na ma manta shaf ana zuwa awo. Ko danmu lokacinmu ba awon ake yi ba oho" Nana dai ta yi murmushi kawai tana jin yadda Ιan yake ta motsi yana danno ta.
Da ba rufe cikakken sati, mijin Hajara bai zo gidan ba, dama yana fargabar kar Nana ta kasa zama da Nene, saboda faΙanta, kuma cikin ikon Allah ya ga lafiya kalau suke zaune. Dan haka ya rage zuwa sosai.
Tun da Nana ta je gidan, Neme ba ta barin ta ta fita, saboda ta ce mata tana da aure, kuma tana yawan gaya mata, ba a son mace mai ciki ta din ga yawo jama'a su na kallonta, saboda baki da ido.
Ma'aikatan Nene duk sun saba da Nana, duk a tunaninsu 'yar uwatta ce, sai dai sukan tambayi Nana, ya aka yi hausarta ba irin tasu ba.
Wasu lokutan sai Nene ta cewa Nana ta zauna a Ιaki kar ta fito, dan haka babu inda Nana ta sani a garin.
Nana ta kwana huΙu, tana fama da wannan ciwon a tsaitsaye.
Sai dai na yau ya fi na kullum, dan sam ba ta yi bacci ba, kuma ba ta gaya wa Nene ba.
Da safe kan Nene ta fito, Nana ta yi shara ta wanke banΙaki, ta Ιora abin karin kumallo.
Ta kuwa sha faΙa a gurin Nenen, sai dai ita ko a jikinta.
Sun gama karyawa, Nene ta shiga Ιaki, ta ji Nana na kiran sunanta, cikin mawuyacin hali.
Nene ta fito da sauri ta ce "Nana lafiya?"
"Nene yoyon fitsari nake yi, ba na iya riΖe fitsari" gaban Nene ya faΙi ta ce "Kamar yaya?"
"Ji na yi kawai fitsari yana bin Ζafata, kin ga" ta yi maganar tana Ιaga wa Nene doguwar rigarta, ruwa na ta bin Ζafafuwanta".
"Nana wannan ai kamar naΖuda ki ke yi, anya ba ruwan mahaufa ba ne?"
Duk da ΖoΖarin da ta yi, za ta yi magana, sai ta kasa saboda wani irin gigitaccen ciwo da ta ji.
Har Nene ta fita suka samo abin hawa, Nana na cikin halin ciwo, ba ta iya gane komai.
Nene ta Ιaukko wa Nana wasu kayan, su ka fita suka tafi Asibiti.
A Asibitin ma, da aka tambayi Nana, cewa ta yi cikinta wata bakwai ne, sai dai da aka yi hoton cikin, ya nuna satin cikinta arba'in da biyu.
Likitan ya yi mata tambayoyi, yaushe ta yi al'ada na Ζarshe, ta ce ita ba za ta iya ganewa ba, saboda Ιari kawai take yi a jere.
Ya tabattar mata a cikin Ιarin da ta din ga yi, tun da ba Asibiti take zuwa a duba ba, akwai wanda bai fita ba ya ci gaba da girma, dan haka naΖuda take yi.
Gaba Ιaya Nene ta rikice, kamar 'yar ta ce za ta haihu, sai a lokacin ta fita, ta sayo kayan jariri da ba ta san ma na wani jinsi ba ne, da Ιan abin da za a buΖata.
Ma'aikata na tsaye a kan Nana, su na ΖoΖari, duk ta galabaita ma ta kasa nishin can ta ce "Ya hayyu ya Ζayyum" ta yi yinΖuri sai ga kan Ιan ya fito. Ita dai ba ta san yadda aka Ζarasa ba, ta ji kukan jariri ya cika Ιakin.
Likita ta Ιago mata jaririn ta ce "Kalli me ki ka haifa?"
Nana haushi ya kama ta, ta gama shan wannan uwar wahalar ga Ιan a hannunta, kuma a din ga tambayarta me ta haifa.
Ta kalli yaron namiji ne, ta ga wani irin shirgegen Ιa, kamar Ιan wata biyu, sai ta hau mamakin yanzu wannan Ιan duk girmansa a jikinta ya rayu, kuma ta Ιan wannan gurin ya fito?
Wata irin zabura ta yi ganin fuskar yaron, ta miΖa hannunta gaba Ιaya tana ΖoΖarin karΙe yaron daga hannun Likitar a kiΙime.
Yana kan gadonsa na marasa lafiya a kwance, su ka ga ya yi wata jijjiga sai da gadon ya girgiza kamar an jona masa wani abu, kawai suka ga ya buΙe idonsa.
A rikice suka kewaye shi, su na kiran sunansa, sai dai babu wanda ya amsawa sai bin su da yake da ido, kamar ya ga baΖin halittu.
Sultan ya riΖo hannunsa ya ce "Imam ka gane mu kuwa?"
Ya yi shiru yana bin Sultan da kallo.
Abduou ya ce "Ikon Allah, ka ga wannan karon bai tashi da ihun ba, sannu Imam"
Kawai ya yi shiru kamar saΖago, sai Ζwayar idonsa da yake juyawa.
Ayshercool
08081012143
65
Nana kuwa da sauri wata ma'aikaciya ta mayar da ita ta kwantar, ta ce "Kar ki tashi, ai miΖo miki shi za a yi"
Abin da ya razanata kuwa, bai wuce yadda ta ga fuskar Sayyid sak, a jikin Ζaton jaririn nata ba, ga sumar kansa a cike har goshinsa. Ga shi jariri amma hatta girar sa da gashi, haka jikinsa ma akwai gashi sosai.
Aka Ιora mata shi a Ζirjinta, ta yi wata nannauyar ajiyar zuciya, tare da furta Alhamdillah.
Ta sanya hannayenta, ta zagaye shi, ta Ιora hannunta a kansa ta din ga karanto masa addu'oi.
Ta din ga hasko irin murnar da Sayyid zai yi, da ya na nan aka haifi jaririn nan. Hawaye ya din ga gagangarowa ta gefen idonta.
Tana jin Likitan tana tsokanarta da har da kukan daΙi, ba za ta bayar da jaririn ba sai an ba ta tukuici mai tsoka. Nana dai ta lumshe idanunta tana murmushi. Aka Ιauke jaririn aka gyara ta, aka yi mata Ιinki, sannan aka kai ta Ιakin hutu.
Bakin Nene ya Ζi rufuwa, ta din ga kallon jaririn. Ta kira wayar su Hajara, ta gaya musu baΖuwar su Nana ta haihu.
Nana ta din ga kallon Nene, da mamakin yadda take ta murnar haihuwar nan, tamkar ita ta haihu.
Sai dai da Nana ta kalli fuskar jaririn sai jikinta ya yi sanyi, ta rasa abin da yake yi mata daΙi, tana tsoron idan ba ta haΙu da Sayyid ko 'yan uwansa ba, yaya za ta yi mene ne makomar yaron kenan? Ga fargaba da tsoron kar su Ζaisar su yi masa wani abu, kar shi ma ya yi mummunan gado kamar yadda ta yi.
Haka dai ta Ιan saki fuska babu yabo ba fallasa. Bayan awanni shida aka sallame ta daga Asibitin suka koma gida. Aka bata magungunan da suka dace ta yi amfani da su, duk Nene ta biya komai.
Nene ta shiga hidima da Nana sosai, ruwan wankanta da na jariri. Ga lafiyayyen Abinci, Hajara kanta idan za ta zo, sai ta yi girki.
Kowa ya Ιauki jaririn Nana, sai ya burge shi.
Ita kanta Nana tasirin Addu'a ne ya sanya Allah ya kawo mata wannan Ιaukin da gaggawa, mutanen da ta haΙu da su suke sonta.
Kwana na biyar da haihuwarta, ta Ιebo kuΙi a cikin jakar gurin Sarkin baka, ta samu Nene ta ce "Nene kuΙin nan za su isa a sai wa yaron nan abin yanka?"
Nene ta ce "Kar ki damu, mun yi magana da Auwwalu za a samo abin yanka in sha Allah"
Nana ta ce "A'a Nene, ko ke ki ka haife ni, wahalar da za ku yi mini kenan, kuΙinki na sana'a ne. Ina son a saya masa kaya, a saya masa abin yanka, ko ba za su isa ba, a karΙa a Ζara irin kuΙin mahaifinsa ne, dan Allah kar ki ce a'a" Da Ζyar Nene ta karΙa.
Dan kuΙin da yawa, aka sayo Ζaton rago, Nene har da Ιawainiyar yin girki, ta gayyaci maΖwabtanta suna.
Muhammad Muhsin, shi ne sunan da Nana ta sanya wa jaririn, Muhsin saboda sunan Ιan gidan Alhaji Fatuhu da har abada ba za ta manta da mutuwarsa ba.
MaΖwabtan Nene da ma'aikatanta sun yi wa Nene kara, sosai suka tara mata abin alheri na kuΙi, da kayan sakawa kasancewar Nene duk masifarta akwai kyauta, shi yasa take shiri da mutane.
Da daddare Nene ta yi wa Muhsin wanka, Nana ma ta yi ta ba ta jaririn ta shayar da shi. Ta fita tsakar gida ta Ζarasa aikace-aikacenta. Kukan jaririn ta din ga ji, Nene ta ce "Nana ya ne, ki kula da shi mana"
Amma Nana ba ta amsa ba, sai kukan jaririn da ta ci gaba da ji. Ta koma Ιakin ta Ιaga labule, kawai ta tarar da Nana, ta saka jaririn a gaba tana ta uban kuka.
Hankali tashe ta shiga Ιakin cikin damuwa ta ce "Ke lafiya, kukan me ki ke yi?" Nana ta kasa magana, ta ci gaba da kuka, ga jaririn a kan cinyarta amma ta kasa riΖe shi. Nene ta Ζarasa ta Ιauke jaririn ta ce "Ba za ki illata Ιan mutane ba, maza yi ta kukan, idan kin gama kya kula da shi" Nene ta goye shi a bayan ta, ta ci gaba da sabgoginta ta Ζyale Nana.
Ba ta sake kula Nana ba, sai da ta yi kuka mai isarta ta gaji.
Nene ta gyara shimfiΙarta, ta kwantar da Muhsin da ya yi bacci.
Ta koma gurin Nana, ta zauna. "Nana" ta kira sunanta.
Nana ta Ιaga kai ta kalle ta.
"Ki gaya mini tsakaninki da Allah, yaron nan ta hanyar aure ki ka haife shi ko kuwa? Na san tambayar nan tana baΖanta miki rai, amma haΖuri za ki yi da ni"
Nana ta share hawayenta ta ce "Nene ni ba Ζarya na yi miki ba, ina da aure wallahi Ιan sunna ne"
"To Alhamdillah, dama jira nake Allah ya sauke ki lafiya, idan ta kama da kaina sai na je Nigeria, na mayar da ke gaban iyayenki Nana, wannan zaman naki kina yarinyar mace, ba kamace ki ba"
"A'a ba zan koma ba Nene"
"To saboda me?"
Hawaye na ambaliya a fuskar Nana ta ce "Sai na haΙu da Babansa, ko danginsa. Ai sun san na taho neman sa"
Nene ta ce "To a wane garin baban nasa yake?"
Ta girgiza kai ta ce "Nima ban sani ba"
"Kamar yaya? Meye sunansa da garin da yake ko hotonsa, sai a taya ki cigiyarsa" Nana ta sake girgiza kanta ta ce "Ban sani ba"
"Wacce daga cikin tambayar ce ba ki sani ba?"
"Nene ban san garin su ba, ban san sunansa ba, kuma ba ni da hotonsa"
Nene ta ce "Ke kar ki raina mini wayo mana, na kwaΙe ki, ta yaya za ki auri mutum ba ki san sunansa ba, ba ki san sunan garinsu ba kawai ki ka kamo hanya ki ka taho? Me ki ke Ιoye mini ne?"
Nana ta Ιan yi shiru ta numfasa ta ce "Ζaddara ce ta haΙa ni da shi muka yi aure, ban san sunansa na gaskiya ba, ni ba shi sunan Sayyid. Ba shi da cikakkiyar lafiyar ΖwaΖwalwa kuma." Nan Nana ta warware mata komai da ya danganci aurenta da shi, duk da ba komai ta gaya mata ba.
Nene ta yi shiru sannan ta jinjina kai ta ce "Ikon Allah, dama shi ne Sayyid Ιin da ki ke ambata idan kina bacci? Amma Nana iyayenki sun yi ganganci. Ke yanzu ko hotonsa ba ki da shi.
Kawai Nana ta Ιaga mata kai alamar eh.
"To ai Nana zama guri Ιaya a haka, ba zai sanya a gano shi ba, dole sai an taΙuka wani abin, wane Ζabilar ne ko shi ma ba ki sani ba?" Nana ta yi shiru ta rasa ma me za ta cewa Nene.
Nene ta ce "To shikenan, amma ba kya ganin yakamata gidanku su san kin haihu?"
"Nene babu buΖata goben jaririn nan nake hange"
"Haka ne, to Ubangiji Allah ya kyauta, amma wannan lamarin naki akwai sarΖaΖiya Nana. Amma ba komai Allah ya taΖaita"
Nana ta amsa da Amin.
****
Baba yana tsakar gida yana shan kunu, sai ga Suwaiba ta fito, gaba Ιaya ta zama wata iri kamar shiri-shiri. Ta kalli Baba ta cake a Ζofar Ιaki ta ce "Nana fa ta haihu" ba shiri ya ajiye ludayin kunun ya kalli Suwaiba ya ce "In ji wa? Waye ya gaya miki?"
"Nanan ce ta gaya mini"
"Ke a ina ki ka ganta?"
"Ina bacci a Ιaki, na ganta da jaririn, ta ce mini haihuwa ta yi"
Wani uban tsaki Baba ya ja, saboda jin shiritar da Suwaiban take faΙa. Dan da fari ya zata ma da gaske take yi.
Alhaji Zailani ne tare da Malam Gambo, su na zaune fuskarsa Ιauke da damuwa.
Malam Gambo ya ce "Wai duk me yasa ka damu ne har haka? Ka na tsoron Ζungiya ta sake cewa ka kawo jininka ne?"
Alhaji Zailani ya numfsa ya ce "Abu na farko burukana biyu, Ιaya ya cika na durΖusar da Fatuhu. Amma samun yarinyar nan ya zame mini bala'i, Ζarewa ma da yake azzaluma ce mai baΖin hali, wai ta tafi Nijar. Ban kuma san ta yadda zan yi na same ta ba.
Babu yadda ban yi na samu yarinyar nan ba, amma duk lokacin da na yi wani yinΖuri a kanta, sai hankalina ya gushe. Yanzu babban tashin hankalina wannan jarababbiyar Sa'a, ashe ita ma ΖoΖari take yi, ta mallaki jinin yarinyar nan.
Ga shi na rasa dalilin da ya sanya Shukura take ta zargin likitan da yake yi mini aiki, da kisan jaririnta."
Malam Gambo ya numfasa ya ce "Ka tattara nutsuwarka guri guda, nasara na buΖatar kasada a kowane lokaci. Ita waccan yarinyar ka jingine batunta a yanzu tukuna, tun a wancan lokacin ai na gaya maka tana Ιauke da wani shu'umin aljani ne mai taurin kai a kanta ba zai taΙa barin burinka ya cika ta daΙin rai a kanta ba. Ba kai kaΙai ba koma waye kuwa. Sannan Ζungiya idan ta sake buΖatar jini, sai ka bayar da na Ιaya daga 'ya'yanka ko namijin, ko kuma ita yarinyar taka a bar jaririn nata ba shikenan ba. Kawai ya zuba wa Malam Gambo ido, idanunsa suka yi jawur sai dai bai ce komai ba ya tashi ya fita.
****
Ζangaren Sagir kuwa, sosai yake sintiri tsakanin Kano da Abuja, saboda Yusra, saboda soyayyar da suke yi ma a yanzu, ba su yi ta a lokacin da suke saurayi da budurwa ba.
Wata irin muguwar shaΖuwa suka yi, da shaiΙan ke barazanar shiga cikin lamarin nasu, ga shi ya rasa ta inda zai tunkari Hajiyarsa da batun, domin ba son Yusra suke yi ba. Shukura tuni ta daΙe da gano inda ya dosa, amma ta zuba masa ido ta ga ina ne Ζarshen alewar zai kasance.
****
Kwanci tashi asarar mai rai, Nana ta yi wata guda da haihuwa, Nene ta tattara ta daina fita gurin sana'arta.
Sai aikin kula da Nana, ga shi kullum da sassafe kan ta ci komai, ake kawo nonon raΖumi fresh Nana ta sha, sannan ta ci Abinci.
Nana tana kwance tana bacci da azahar, saboda yadda Muhsin ba ya barin su bacci da daddare, saboda ba ya Ιaga wa Nana Ζafa da tsotso, ga kuka sai dai Nene ta taya ta riΖonsa.
Yana gabanta yana bacci, ita ma ya Ιauke ta, ta Ιaga kai ta ga ya shigo ta Ζofar Ιakin. Tana kwance ba ta motsa ba ta ga ya Ζaraso ya zuba musu ido, daga ita har Muhsin, ya sanya hannunsa ya shafa gashin jaririn, ya durΖusa ya sumbaci gishin yaron. Sannan ya kalli Nana idanunsa cike da hawaye.
"Sayyid, yaushe za ka zo ka ganmu? Mu na buΖatar ka a kusa da mu, dan Allah kar ka tafi ka bar mu"
Ya kama hannayenta ya riΖe a cikin nasa, sai dai bai yi magana ba. Sai da aka jima sosai yana murza yatsun ta a hankali sannan ya ce "Ma vie"
"Na'am"
"Gangar jikina ta kasa samun nutsuwa, rayukanmu su na kewar juna, ki kula mini da rayuwata da ke jikin ki, da jikin Ιa na, ina Ζaunarku Nana"
RiΖe Sayyid ta yi, tana kuka tana "Dan Allah Sayyid kar ka tafi ka bar mu, mu na buΖatar ka a rayuwarmu, dan Allah Sayyid, dan Allah"
Nene ta yi shiru tana kallon yadda Nana ta riΖe ta tana kuka.
Da yake sheshsheΖar Nanan ta jiyo, ta taho Ιakin tana zuwa ta tarar da Nana tana nema ta danne jaririn. Bayan ta Ιauke shi ne, Nana ta riΖe mata riga.
Nene ta zuba wa Sarautar Allah ido, Nana ta buΙe idanunta a hankali ta ga yadda ta riΖe Nene gam. A hankali ta cika ta tana sunkuyar da kai. Sai dai ta Ιaga kanta tana kallon Ιakin, tana jin Ζamshin turaren Sayyid a hancinta.
Nene ba ta ce mata komai ba, ta goya Muhsin ta fice da shi daga Ιakin.
Nana ta lallaΙa, ta tafi gurin da kayanta suke, ta bubbuΙe jakar kayan shafe-shafensa, da take ta adanawa tana kallon su tana jin daΙi. Sai dai a wannan karon hawaye take yi, tare da jin zuciyarta tamkar za ta buga. Ta zazzage kayan ta din ga bin su da kallo, ta Ιago Azurfarsa da ya ba ta, ta ce ya yi mata yawa, ya ce ta Ιaure da zare ta yi sarΖa da shi.
A hankali ta furta "Da mutuwa ka yi na san Allah ne ya karΙe ka babu yadda na iya, da aurenmu ne ya Ζare shi ma na san wannan Ζaddara ce, ba a kaina a ka fara ba. Amma ban san a wani hali ma ka ke ba, duk a inda ka ke ina fatan Ubangiji Allah ya sanya ka na cikin aminci da kwanciyar hankali Sayyid.
****
Yana zaune a kujerar da ke cikin Ιakin, da abu a cikin kofin yana sha a hankali.
Murmushi ya gaza barin fuskar Sultan, ya zauna a kusa da shi yana murmushi ya ce "Alhamdillah, sauΖi yana samuwa Imam, ya jikin naka?"
Ya kalli Sultan ya mayar da hankali ya ci gaba da shan shayin da ke cikin kofin hannunsa ba tare da ya furta komai ba.
Cikin damuwa Sultan ya ce "Har yanzu ba ka gane ni ba Imam?"
Har yanzun dai bai yi magana ba, bai kuma fasa shan shayinsa ba.
Sultan ya riΖo hannunsa guda Ιaya cikin nasa, ya ce "Imam ka kalli Abbanka mana, ka yi magana ko hankalina zai kwanta"
Ya waiwaya ya kalli dattijon.
Cikin murna Sultan ya ce "Ka na jin abin da nake faΙa?" Ya yi shiru yana ci gaba da kallonsa, bai yi magana ba.
"Ka yi mini magana ka ce wani abu mana"
A hankali ya zame hannunsa daga na dattijon, ya tashi daga kan kujerar ya koma gadonsa na marasa lafiya ya kwanta.
Sultan ya yi shiru yana kallonsa, sai dai ya rasa abin da yake yi masa daΙi. Kar a ce ΖwaΖwalwar Ιan sa ta taΙu. A yadda alaΖarsa da Ιan sa take, ba Ζaramin abu ne zai sanya ya yi masa haka ba.
Kwanciyarsa ke da wuya, ya fara jijjiga, a rikice Sultan ya nufe shi. Sai dai ya fara kururuwa yana faΙin "Wuta zafi"
Matawalle ne ya shigo Ιakin da sauri, suka rufu a kansa, Sultan ya din ga tofa masa Addu'a. Har ya daina jijjigar.
Abdou ya kalli Sultan ya ce "Abubuwa fa kamar Ζara rikicewa suke yi, mene ne abin yi yanzu. Ina tsoron a bi diddigi a gano halin da yake ciki fa"
"A fita da shi waje kawai, wataΖila a dace a can, ni na kasa gane kan abubuwan da ake yi masa a nan"
"A wannan yanayin, da ihun da yake yi"
"Abduou" Sultan ya kira sunansa cikin Ιaga murya.
Abduou ya risunar da kai ya ce "Za a shirya duk abin da yakamata, za a yi abin da ka ce".
Jamila ce take ta juyi a kan katifarta, tana jiran reply Ιin Abba, saboda chatting suke yi. Sai dai shiru bai yi reply ba har ta gaji ta yi bacci.
Da safe sai gurin sha Ιaya ta tashi daga bacci, da yake tana fashin salla.
Ta duba wayar, ta tarar da tarin messages Ιin sa da kiran waya, ta share ta je ta yi wanka ta shirya.
Daga tsakar gida ta ce "Mama ni na wuce"
"Ba za ki tsaya ki karya kumallo ba?"
"Zan ci a can, sai na dawo"
Suwaiba na tsakar gida, tana goge kaushi, ta ce "Jamila"
"Yes" Jamila ta amsa.
"Nana fa na gaishe ki, ba ki ga jaririnta ba"
Jamila ta ce "Ai dama ke da Nanan, kan ku ba Ζalau ba, shi yasa ke kaΙai take kawowa ziyara a mafarki." Sai kuma ta Ιan yi shiru cikin damuwa ta ce "Allah sarki Nana, ko ta na wani halin yanzu oho" ta Ιan ja numfashi ta sauke ta fita, tana ci gaba da tunanin Nana.
A falon Hajiya Sa'a ta tarar da Abba yana zaune yana Video game. Tana shigowa ya yi murmushi ya tashi zaune ya ce "Sannu da zuwa"
Ta murguΙa masa baki ta nufi bedroom Ιin Hajiya Sa'a.
"To ai ba ta nan" ya yi maganar yana miΖewa ya bi bayanta.
"Me na yi miki ne ki ke hararata? Na tura miki saΖo duk ba reply"
Ta kalle shi ta ce "Ba jiya na yi ta jiranka da daddare ba, ka Ζi kula ni"
"Eyya, bacci ne ya kwashe ni, ki yi haΖuri"
"Ba wani nan, da budurwarka ka ke chatting ka share ni"
Ya waro ido ya ce "Wallahi ba ni da wata budurwa bayan ke, kema kin san ba na iya kula 'yan mata kema da Ζyar ai na gaya miki ina son ki" sai kuma ta tuntsure da dariya ya taya ta shi ma.
Za ta yi magana kawai Hajiya Sa'a ta shigo falon, ta gan su a zaune a kan dining suna hira har da dariya, alhalin a gabanta basar da juna suke yi.
Ζan saroro Hajiya Sa'a ta yi tana kallon su, Jamila cike da bariki ta ce "Mummy sannu da zuwa" "Yauwwa" ta amsa a taΖaice. Abba ma kam kasa magana ya yi gaba Ιaya.
Ya yi wa Jamila sallama ya fita, sai dai Hajiya Sa'a ta yi kicin-kicin ta Ζi sakar wa Jamila fuska gaba Ιaya.
Jamila kuwa ta din ga Ζissimawa a ranta, muddin abin da take zargi ya zama gaskiya game da Hajiya Sa'a za ta ba ta mamaki ba kaΙan ba.
*****
Kwanci tashi asarar mai rai, Nana ta kwana arba'in cif da haihuwa.
Sai da Nene ta kwana goma sha biyar, ba ta fita gurin sana'arta, saboda jegon Nana sai dai yaranta su je, sai bayan kwana sati biyun sannan ta fara fita, shi ma da wuri take dawowa.
Ranar da Nana ta kwana arba'in, ta saka Nana ta shirya suka je gidan su Hajara.
Sun yi murna sosai da sosai da ganin Nana, duk da ta rame, amma yanayin ta akwai nutsuwa a tattare da ita.
Auwwalu ya Ιauki Muhsin ya ce "Ohh Allah ka bamu mu ma Ιan kyakykywan jariri, ka ga Ιa kamar na larabawa"
Hajara ta amsa da "Amin dai"
Nene ta ce "Ka ga fitsararru, babu ko kunyar idona?"
Auwwalu ya ce "To ai addu'a muka yi. Ban da rashin kara ma, a Ζa'ida fa Ιan nan, sunana na ya kamata a saka masa"
Nene ta ce "Saboda kai Ιin waye?"
Nana ta yi murmushi ta ce "Yaya Auwwal, ai sunanka ne da shi, laΖanin ne kawai ba Ιaya ba"
Ya yi murmushi ya ce "Kuma fa haka ne" sosai suka karrama su Nana. Da suka tashi tafiya ma, sai da suka kuma bawa Jaririn kyautar kuΙi da kaya, a so samu Nana ba ta so suka karΙa ba, amma Nene ta amshe.
Da suka dawo kuma ta zagaya da Nana gidajen maΖwabta, suka gaggaisa.
Tun da suka doshi wani gida, Nana ta din ga jin gabanta na faΙuwa, kamar ta cewa Nene ba za ta shiga ba, amma ta kasa. Ta din ga addu'a tare da fatan Allah ya rufa mata asiri ya sanya ba wani abin ne zai faru da ita ba, ko Ζaisar ne zai dawo ya hana ta sukuni a Ζasar da ba ta da kowa ba.
Ko da su ka shiga cikin gidan, sai Nana ta fara jin sanyi, yana ratsa ta a hankali.
Aka shimfiΙa su tabarma, da Ζyar Nana suka gaisa da mutanen gidan, ta nemi guri ta zauna. Sai ta daina gane abin da Nene suke faΙa ma. Ta din ga jiyo muryar su Nene can nesa da ita, hakan ya tabattar mata da gidan akwai wani abu.
Wani irin sauti ta din ga ji, a cikin kunnunwanta, kamar gurnani kamar nishi.
Ta daina ganin su Nene gaba Ιaya, sai wata mata da ta fito ta tunkaro ta. Ga matar babba da ita amma jikinta Ιauke da zaren mahaifa daga cibiyarta dogon zaren har kan wani baΖin Ζwarangwal da yake bin ta, hannun Ζwarangwal Ιin kuma mahaifa ce yake lasa da jini da komai a jiki.
Jikin Nana ya hau tsuma, ta din ga kallon matar da Ζwarangwal Ιin, tana son yin addu'a ta kasa.
"Nana" ta ji muryar Nene ta kira sunanta.
Sai ta buΙe ido ta kalli Nene.
"Tashi mu tafi yamma ta yi"
Nana ba ta motsa ba, ta ga matar da ta gani yanzu tare da Ζwarangwal ta nufo ta.
Matar gidan ta ce "Kar ki kuskura ki taΙa ta, yi haΖuri dan Allah ba ta da cikakkiyar lafiya ne" ta yi maganar tana kallon Nana.
Sai dai matar ba ta tsaya ba, ta yi kan Nana gadan-gadan. Wani irin azababben Ζarf ya zo wa da Nana, ta ji zuciyarta na tafasa jira take matar kawai ta Ζaraso gare ta, ta illata ta.
Amma Nene ta danΖi hannun Nana, ta hana matar Ζarasawa gurin Nana ta ce "Ke Ashura, meye haka ne? Ba ki ga baΖuwa ba ce?"
Matar cikin wata irin harΙaΙiyar magana da zubar da yawu ta ce "Magana zan yi mata, ta saka wannan Ζwarangwal Ιin ya daina bina" gaba Ιaya suka kalli Nana. Ζaya matar ta ce "Wani Ζwarangwal Ιin, rabonta da magana ma fa ta fi sati biyu"
Kawai matar ta saka kuka, lallai sai ta je gurin Nana, ta cewa Ζwarangwal ya daina bin ta.
Nene ta ja hannun Nana suka yi waje. Sai dai ta ji jikin Nana tamkar gawa saboda sanyin da ya yi.
Su na zuwa gidan Nana ta nemi guri ta zauna, ba ta cewa Nene uffan ba.
Can bayan magariba, sai ga matar da su ka je gidanta ta zo, Nene ta ce "Gaji lafiya kuwa?"
"Dan Allah Nene ki taimaka mini, ko 'yar nan taki za ta zo mu je gurin Ashura, sai ihu take tana burgima tun da ku ka tafi"
"Ta zo ta yi mata me?"
Gaji ta ce "A'a ban sani ba ko akwai wani taimako...
"Taimakon me?" Nene ta katse ta.
"Kin san dai Ashura ba hankali ne da ita ba, wataΖila almatsutsan haukanta ne kawai ya tashi take wannan abubuwan, ki tafi babu inda Nana za ta zo"
Gaji ta fita jiki a sanyaye, dan idan ta matsa sai Nene ta balbale ta da masifa.
Nene ta ajiyewa Nana nonon raΖumi, da abincin dare, amma ta Ζi ci saboda sanyin da take ji.
Nana ta haΙa kanta gwiwa, tana jin yadda jikinta yake tsuma ta ce "Sayyid sanyi nake ji"
"Ke Nana" Nana ta Ιago ido ta kalli Nene. "Ba za ki ci abincin ba ne?"
"Na Ζoshi, amma dan Allah Nene mara lafiyar can ta can gidan, ta faΙi wani abu a kaina ne?"
Nene ta ce "Za ki ba ta magani ne?" Sai Nana ta yi turus tana kallon Nene, gabanta yana tsananta faΙuwa.
"Ba ta ce komai a kan ki ba, amma idan kin amince za ki yi magana da aljanin nata, ko ki bata magani kamar yadda ake so ki yi, sai mu je"
Gaban Nana ya faΙi, ta bi Nene da kallo cike da mamakin, yaya aka yi Nene ta san wannan maganar, alhalin ko da wasa ba ta taΙa gaya mata ba.
"Nana mamaki ki ke yi? Ai ba a banza na yarda na karΙe ki muke zaune a cikin gidan nan ba da ni da ke.
Tun zuwanku na ga abubuwan da na gani a tattare da ke.
Na ga inuwar rauhanin aljani a tattare da ke, kuma da alama ko dai kin gamu da baΖin aljani a hanya, ko kuma kin yi rayuwa da shi, saboda akwai warinsa a tattare da ke, saboda yana ta'amalli da jini, har ma warin nasa yana ΖoΖarin danne, Ζamshin rauhanin da yake tattare da ke. Sannan akwai alamu na alaΖa mai Ζarfi a tsakanin wannan rauhani da Aljanin da yake tattare da ke. Jiri ne ya fara Ιibar Nana, cikin wani yanayi mai kama da fitar hayyaci ta ce "Nene, wace ce ke? Ya aka yi ki ka san abin da ban gaya miki ba? Ki gaya mini ke wace ce?"
"Nana, masu iya magana suka ce mugu shi ya san makwantar mugu. Ni na yi harkar bori da bayar da magani, ni baΖin aljani ma na gada daga gurin mahaifina. Ya azabtar da ni ya hana ni aure, na Ζi bayar da magani ya shanye mini Ζafafuwa, na daina al'ada na fara hauka tuburan. Sai da na bayar da magani, bayan wasu shekaru, na daina al'ada na fara hauka tuburan. Sai da na bayar da magani, bayan wasu shekaru, na gaji na ce zan ajiye, saboda kullum cikin larura nake, ga shi ya sanya na saka a yi ta zubar masa da jini. Ya sake burkita ni, ya hana ni aure, na koma ciwon hauka yau na kuturce gobe na daina gani, anjima na kasa tafiya. Ya buΙe mini ido nake ganinsu muraran a siffofi na ban tsoro, nake jin maganganun su a cikin kunnuwana. Ya Ιauke ni ya kai ni can wata uwa duniya ya yasar da ni, na yi ta gararamba sannan ya gaji ya dawo da ni. Ko ya saka na yi ta zubar da jini babu ΖaΖΖautawa.
Duk inda muka je neman magani, sai a ce sai dai na haΖura na ci gaba da bayar da magani.
Da Ζyar wani mai magani ya raba ni da shi, ta hanyar yin amfani da wani aljanin. Ya kafa sharuΙΙa sai da aka yi masa yanka, da sauran abubuwa dai na sharuΙΙa sannan Allah ya raba ni da shi. Bayan mun rabun ma, da Ζyar na samu na yi aure, shi ma dai kusan kullum cikin rigima da miji, na zo babu haihuwa, sai rigima sai dai ya dage ya Ζi rabuwa da ni. Sai daga baya Allah ya bani haihuwar Ιa namiji, daga nan ban sake haihuwa ba. Yarona yana can Ζasarku Nigeria. Mijina kuma Allah ya yi masa rasuwa, ni kuma na ci gaba da sabgogina ban sake wani auren ba, duk da wasu lokutan haryanzu abubuwan na taΙa ni."
Nana tana Libraryn Ζaisar, daga can nesa take jiyo maganar Nene.
Kai tsaye gurin mudubin nan ta nufa, cike da fatan ta sake ganin ko fuskar Sayyid ne, amma ta tarar da mudubin wayam, sai ma baΖi Ζirin da ya yi.
Ta daΙe a tsaye ta zura wa mudubin idanun amma babu alamar wani abu zai bayyana a mudubin ta gani.
Ta hango littafin da ta fara karantawa a yashe a Ζasa, inda ta yasar da shi, hakan ya tabattar mata da Ζaisar ba ya cikin Ιakin karatun nasa na wani lokaci.
Ta sanya hannu ta Ιauki littafin, ta nutsu ta ci gaba da karantawa.
"Idan ka bari tsoro ya Ιarsu a cikin zuciyarka, to tabbas ba za ka iya cimma abin da ka ke hari ba. Tun da kawar da mahaifinka bai yi maka wahala ba, wannan ma ba zai gagare ka ba, ka kashe su Ιaya bayan Ιaya, ka yi mulki cike da izza ka tara sojoji da runduna da za ta razana duniya".
Ire-iren waΙannan kalamai na ziga da kambamawa, ya sanya matashin saurayin jin kansa na daΙa kumbura, tare da ji a ransa zai aikata komai domin cimma burinsa.
Ana tsaka da jimamin mutuwar shugaba a garin, ya ci gaba da tattara sojojin sa na ΖarΖashin Ζasa, da shirya hanyoyin da zai bi gurin kawar da dukkanin wanda ka iya kawo masa tangarΙa.
Ganin babu abin da ake yi a farkon littafin, ban da tsagwaron zalunci, zubar da jini da rashin tausayi ko imani, tsananin Ζiyayya da kisan kai a tsakanin 'yan uwa, duk don kowa yana kwaΙayin Ιarewa gadon mulki.
Ga bautarwa ta fitar hankali ga na Ζasa ba tare da afuwa ko sassauci ba, sai Nana ta ji gaba Ιaya littafin ya ishe ta, ba ya yi mata daΙin karantawa, har ma gara na tarihin Buda a kan wannan.
A hankali ta buΙe idonta, da ya yi mata nauyi, ta ga gari ya yi haske, ta shafa gefenta ta ji babu Muhsin, kawai ta yi zaton ko Nene ce ta goya shi, dan idan Nene na nan, tsakaninta da Muhsin shayarwa ne kawai, ita take yi masa komai kamar ita ta haife shi. Tana Ιaga kai ta ga wannan mahaukaciyar, riΖe da Muhsin a hannunta, gefenta ga wannan Ζwarangwal Ιin baΖi Ζirin da shi kamar an gasa shi da wuta.
Ihu Nana ta saka a cike da matuΖar razana, ba wai dan ta ga Ζwarangwal Ιin ba, sai ganin Ιan ta a hannun mahaukaciya ga aljani a bayanta yana ta lasar jinin jikin mahaifar da ke Ιauke da zaren cibi.
Ayshercool
08081012143
66
Nece ce ta fito hankali a tashe, ta shiga Ιakin da Nana take ciki, ta tarar da Ashura a tsaye rungume da jaririn Nana.
A matuΖar fusace ta Ζarasa ta karΙe Muhsin, ta ajiye shi a kan katifa, ta ce "Uban me ya shigo da ke ki ka Ιauke shi?"
Cikin tsoro ta girgiza kai ta ce "Babu komai"
"Uban me ki ka yi masa?"
"Wallahi ban yi masa komai ba"
Nene ta shaΖe ta, ta ce "Ki gaya mini me ki ka yi masa?"
Cikin kuka ta ce "Wallahi ba abin da na yi masa"
"To me yasa ki ka shigo?"
"Wallahi son shi kawai nake yi"
"Ζan ki ne da za ki ce son shi ki ke yi, wani abin za ki yi masa kenan" cikin kuka ta ce "A'a Nene"
Nene ta ce "Wallahi na sake ganinki a gidan nan, sai na yi miki shegen duka, babu ke babu jaririn nan"
Nana ta saka hannu ta ture Nene, ta ce "Dan Allah ki yi haΖuri ki daina dukanta, ai ta ce babu abin da ta yi masa"
Nene ta ce "Ba dan kin farka ba fa? idan ta yi masa wani abin, ni ina banΙaki ke ki na bacci fa?"
Nana ta ce "In sha Allah babu abin da za ta yi masa. Zo mu je na raka ki gida"
Nene ta ce "Nana ki rabu da ita ta tafi gidan"
Nana ta ce "Nene zan raka ta, ni duk inda na ga mai irin larurar nan, tausayi yake bani"
Nene ta ce "Can ta matse muku ke da ita, ku je can ku Ζarata, ni dai na sake ganinta a gidan nan, ta taΙa yaron nan, sai na yi mata shegen duka da itace"
Nana ta kama hannun Ashura da ke ta rarraba ido, suka fita daga gidan.
*****
Hajiya Sa'a ta tattara hankalinta a kan Abba da yake zaune a gabanta a bedroom Ιin ta.
"Magana nake yi maka, ka Ιago ka kalle ni, mene ne a tsakaninka da yarinyar nan Jamila?"
Ya ce "Ba komai"
"To ka buΙe kunnenka da kyau ka saurare ni, na sanya katanga a tsakaninka da ita, babu kai babu ita, kar ka kuskura na ji wata magana a tsakaninka da ita, kuma matar aure na samo maka ita, zan baka lambarta ka kira ta ku gaisa. Ka je ku gana, kuma nan kurkusa za a yi komai a gama. Ka fita daga harkar Jamila, ka fita daga harkar ta na gaya maka na kuma nanata maka, idan ba haka ba daga kai har ita ba za ku ji daΙin abin da zai biyo baya"
Ya jinjina kai jiki a sanyaye ya ce "To in sha Allah zan kiyaye"
"Tashi ka bani guri" ya yinΖura ya tashi jiki a sanyaye, ya fice daga Ιakin, zuciyarsa na wani irin zafi. Bai taΙa zaton za ta nuna adawarta da maganar haka ba, ganin yadda take da Jamila.
Ko da ya tafi Ιakinsa, kiran Jamila ya shigo wayarsa, jiki a sanyaye ya Ιaga wayar ya ce "Hello Jamila"
"Jamila kuma, yau ba Ζanwartaka?"
"Afuwan a yi mini afuwa"
Cikin damuwa Jamila ta ce "Yaya lafiya kuwa?"
"Lafiya Ζalau, ina fatan kin je gida lafiya, ba ki bari na dawo na mayar da ke ba"
"Ina sauri ne, kuma ba na son wahalar da kai gaba Ιaya. Ko dai Mummy ta yi maka magana a kan ka daina kula ni ne?"
Da sauri ya ce "A'a ai kin san ba za ta hana ba ko kaΙan"
Jamila ta ce "To shikenan, amma dan Allah in anjima ka zo na ganka"
Ya yi murmushi ya ce "Ni ki ke son gani?"
"Eh mana, ko na haΖura?"
"Ina ni na isa, ina yin sallar isha'i za ki ganni a bar Ζaunar Abba"
"To abin Ζaunar Ζanwarsa, sai ka zo" ya sauke wayar yana murmushi, sai dai yana sauke wayar ya Ιan yi shiru cikin damuwa, bayan tuna abin da Mummyn ta gaya masa na kashedi.
****
Muhsin Ιin Nana tamkar ana hura shi, saboda girma ya cika ya yi fam. Ga shi fafur Nana ta Ζi bari a yi masa aski, ta cewa Nene babansa ma ba ya aski, dan haka a bar masa sumarsa.
Nene ta fara jinginar da shi, a tsakanin fululluka tana koya masa zama.
Nene ta ce "Nana bari na hanzarta na fita, ki kula da yaron nan dan Allah, ban da shiririta, ko ki Ζyale shi yana kuka ki yi masa banza"
Nana ta ce "To Nene ki goya abinki ki tafi da shi mana, tun da kullum ba na yi muku abin arziki"
"Kya dai ji da shi, ni dai na gaya miki, kuma wallahi mahaukaciyar can ta shigo, ki ka Ιauki yaron nan ki ka bata, sai na Ιata muku rai daga ke har ita"
Nana ta ce "Ni dai ba wannan ba, Nene so nake na fara bin ki gurin sana'ar nan, zaman gidan nan yana damuna, ba akin fari babu na baΖi"
Nene ta ce "Nima na yi wannan tunanin Nana, amma bai kamata a ce kina matar aure mu din ga fita bakin titi babu iznin mijinki ba, kin san halin maza wasu ba kirki ne da su ba, mussaman ke ga Ζuruciya ma. Sam ba mutuncinki ba ne ba, dama jira nake yi Muhsin ya Ζara Ζwari, na nema miki ko gurin Ιinki ne ko makamancin haka, ki din ga zuwa sannan mu ga ta ina za mu fara laluben mijinki, amma tun da Muhsin ya yi Ζwari, mu fara lalubawa zaman haka ba zai yiwu ba, motsi ya fi laΙewa ai"
Ta jinjina kai ta ce "To shikenan Nene, duk yadda ki ce Shikenan, na gode sosai da sosai Ubangiji Allah ya saka miki da mafificin alkhairi"
Nene ta ce "Amin yarinyar kirki"
Fitar Nene babu jimawa sosai, sai ga Ashura ta faΙo gidan.
Nana ta ba ta ce mata ta shigo Ιakin, amma ta Ζi.
Nana ta tashi ta fita ta shimfiΙa mata tabarma, sannan ta Ιaukko Muhsin, ta zo ta zauna ta ba wa Ashura shi.
Ta karΙe shi tana buΙe baki cikin murna, ta kalli Nana ta ce "Ina son yaron nan"
Nana ta ce "Da gaske?"
Ta jinjina wa Nana kai, ya jima a hannun Ashura, sannan ta ba wa Nana shi, Nana ta mayar da shi Ιaki ta kwantar. Sai dai tana dawowa ta tarar da Ashura a tsaye tana kuka, gefenta ga Ζwarangwal Ιin nan.
Nana ta ce "Me ka ke buΖata ne?"
"Ki na ganina kenan?"
"Eh ina ganin ka, sannan wannan mahaifar da ka ke lasa mene ne ma'anar hakan? Tun da Ζazanta ce"
Ya ce "Lokacin da aka haife ta ne, da za su dawo daga Asibiti, aka manta mahaifar, shi kuma mai motar ya yar a bola, ni kuma na tsinta na biyo ta."
Cikin damuwa Nana ta ce "Amma baka kyauta ba, tun da babu wanda ya yi maka wani laifi ka ke yi mata abin da ka ke yi mata".
Ya ce "Ai mu ba sai an yi mana abu ba, idan mu na son mutum. Kin ga ke ma da ki ke addu'a wasu lokutan, ba dan tasirin Addu'a da ki ke yi, da kuma tsoron uban duΖusa da ake yi ba, da bataliyar da za su shiga jikinki da yawa. Saboda da guda Ιaya ya yi hanya, wasu ma suke samun kafar shiga jikin mutum. Kuma Allah ya taimake ki, Sarkin baka ya rage tasirin uban duΖusa a tare da ke, da duk inda muke sai kin din ga ganinmu, kuma muraran za ki din ga ganin cututtuka da sihiri a zahiri, sai kin kusa haukacewa idan ba ki bayar da magani ba. Kawai dai shi yana lallaΙa ki ne"
Nana ta ce "Yaya aka yi ka san Ζaisar, kuma ka san Sarkin baka?"
Ya ce "Jaddul Jinn babu wanda bai san shi a nahiyar nan ba, dan haka sanin jikansa uban duΖusa ba abin mamaki ba ne. Sarkin baka kuma shi ne ya mayar da ni Ζwarangwal, mun taΙa artabu da shi da na shiga jikin sata mesa, ya Ζona ni. Kuma na ga kin haΙa jini da shi, ba yadda na iya da ke ne kawai, da sai na Ιauki fansar abin da aka yi mini a kan ki"
Nana ta yi shiru jikinta ya yi sanyi, su na gama maganar Ashura ta juya ta fita ya bi ta a baya.
Nana ta din ga jinjina azabar naci da riΖo irin na halittun nan.
****
BAYAN WANI LOKACI.
Girman Ιan mutum babu wuya, in ji masu iya magana, Muhsin ya cika watanni bakwai, Nana na zaune tare da Nene.
Nene ta kai ta gurin koyon girke-girke, yanzu kuma tana zuwa koyon Ιinki. Nana har mamakin yadda Nene take yi mata take. Sai dai ta fara karaya da yanke tsammannin haΙuwa da Sayyid.
Nene ce ta shigo gidan, bayanta goye da Muhsin, yana ta mamular cukui.
Nene ta sauke shi ta zaunar da shi ta ce "Wannan Ιan naki, idan bai nuna mini halinsa ba, ai ba za a ce Ιan buzaye ne ba, mun taho hanya ya ga raΖuma, wai sai dai mu tsaya ya kalli raΖumi, sai zillo yake a bayana yana ihu, sai da na tsaya na Ιata lokaci yana kallon raΖuma yana miΖa musu hannu. Ya cire hular kansa ya yar, kowa ya ga kansa da wannan kitson sai an tambayi mace ce ko namiji. Ke ma da taurin kan tsiya, kin Ζi bari a yi masa aski, kuma kina yi masa kitso kamar wani mace."
Nana ta yi murmushi ta ce "Ni babu ruwana, ba shiga faΙanku zan yi ba, balle na ji kunya ku gwale ni"
Shi kuwa cukun hannunsa kawai yake mamulawa a bakinsa, Nene ta juya za ta fita tsakar gida ya rarrafa ya bi ta yana kukan ta Ιauke shi.
Nana ta sake yin murmushi ta ce "Na haifa wa Nene Ιa"
Tana jiyo rigimarsa da Nene, ya hana ta aiki, idan ta hana shi wannan ya koma wancan.
Nana ta din ga dariya daga Ιaki, aka jima kuma Nene ta zuba masa shayi sai kuma ya nutsu, guri Ιaya, yana sha yana wasa da gashinsa.
Ashura tana son zuwa gidan Nene gurin Nana, amma tana tsoron Nene, ga Muhsin da ya ganta yake sanya ihu, tsoronta yake ji.
Ζangare guda kuma, zuciyar Nana na saΖa mata ya kamata ta gusa ta bar gidan Nene, saboda ta ja lokaci a gidan. Amma tana tuna tijarar Nene, da rashin sanin ina za ta dosa. Ba ta san wani irin mutum ne Sayyid ba, mutumin da za a yi alfahari da haΙa nasaba da shi ne ko akasin haka, duk da tana kyautata masa zato. Shi yasa take Ιoye wasu abubuwan, dan kare mutuncin sa da rashin sanin a yaya za ta haΙu da shi.
Washegari da safe Nana ta tashi, ta jiyo hirar Muhsin a tsakar gida.
Ta tashi ta fita kar ya yi wata Ιarnar, sai ta gan shi a lungun kitchen Ιin Nene, ya juyo bayansa, kamar dai wani abun ya samu yana wasa da shi.
"Kai babyn Sayyid, me ka yi a gurin nan, taho ka sha" bai waiwayo ba ya ci gaba da abin da yake yi. Nana ta nufe inda yake. Wata irin narkekiyar mesa ta gani a cikin lungun, shi kuma yana ta duΖunΖuna kanta da hannu bibbiyu yana hira.
Ji ta yi tamkar an Ιaure ta tamau, ta kasa gaba ta kasa baya, kuma ta kasa magana.
Mesar ta miΖe sai ga Ζaisar ya bayyana a gurin. Muhsin ya Ιaga kai yana dariya yana kallon Ζaisar.
Ζaisar ya ciro wani abu a kwalba, ya buΙe bakin Muhsin ya zuba masa, Nana ta rikice amma ta kasa motsa kowace gaΙa ta jikinta.
Muhsin ya kama rigar Ζaisar yana wasa da ita, yana yi yana kallon Ζaisar Ιin.
Ζaisar ya saka hannu ya shafa kitson kan sa, ya miΖe tsaye ya Ιace. Sai da ya Ιace Nana ta iya motsawa, amma duk da haka ta kasa zuwa inda Muhsin yake, sai shi ne ya rarrafo ya nufo inda take.
Ta saka hannu da Ζyar tana dudduba jikinsa, ko wani abin ya yi masa amma jikinsa lafiya Ζalau. Ta shiga fargaba da tsoron me ya ba shi ya sha?.
Ta ja jikinta ta koma jikin bango, ta fara shayar da shi, tana roΖon Ubangiji Allah ya kare mata yaronta daga sharrin su Ζaisar da kowane irin nau'i na shaiΙani.
Nene na fitowa, ya cika Nana ya tafi gurinta, sai da ya gama wasansa, ya sake komawa gurin Nana.
Tana shayar da shi, tana ganin fuskar Sayyid a tattare da shi, dan hatta idan ya Ιata rai, tamkar mahaifinsa.
Sai dai tunani da tsoron abin da ka iya samun sa, ya gaza barin zuciyarta, tun daga ganin da ta yi wa Ζaisar da shi.
Ta so gaya wa Nene, amma ta ja bakinta ta yi shiru ba ta gaya mata ba.
Sai dai tun gabatowar magariba, take jin sanyi.
Ta shige Ιakin ta Ζudundune, ta bar su Nene.
Tana tsaye a sahara, sai dai a wannan karon babu Ζurar Saharar, ta hangi Sayyid a zaune yana shan shayi, shikaΙai.
Ta taka sannu a hankali ta Ζarasa inda yake, ya Ιago ya kalle ta yana murmushi.
Ta zauna a kusa da shi, ta ce "Ka warke ne?"
"Da sauΖi, na yi nesa da inda nake jin ciwon, kuma na yi nisa da gurin waΙanda za su kashe ni"
Cikin damuwa ta ce "Ni fa?"
Ya ajiye kofin hannunsa, ya rungumota jikinsa yana kallon fuskarta, idanunsa cike da hawaye ya ce "Yadda ruhinki da gangar jikinki, suka gaza samun nutsuwa, tun bayan rabuwarmu haka nima nawa suka gaza samun nutsuwa. Ina kewarku gangar jikina ta kasa samun nutsuwa, ina buΖatar ki a kusa da ni"
Ita Nana gaza riΖe nata hawayen ta yi, tuni ta ba su dama suke zuba.
Ya girgiza mata kai tare da cewa "Kar ki manta, muddin kina raye kuma ina raye a doron duniya, gangar jikinmu ba za ta samu nutsuwa ba, sai mun haΙu. Ina kewar ki ma vie."
Ya yi maganar yana ΖanΖame ta a jikinsa. Ta buΙe idonta tana ji yadda hawaye ya jiΖa mata fuska.
Ta tashi zaune da Ζyar, ta yi shiru ta tafi tunani. "Nana ba a bori da sanyin jiki, ci gaba da zaman ki a gidan nan, tamkar ki na matsawa dattijuwar nan ne da take Ιawainiya da ke, kuma ba za ki taΙa haΙuwa da Sayyid ki na zaune guri Ιaya ba, yakamata ki motsa".
Ta tashi ta yi alwala, ta yi sallar magariba da isha'i, ta idar ta shiga Ιakin Nene ta Ιaukko Muhsin, ta dawo da shi Ιakinta saboda ko zai farka cikin dare.
Nana ji ta yi tamkar ta fice daga gidan a cikin daren nan, amma ta kasa saboda ba ta san ina za ta nufa ba, a wannan uban daren.
Ta haΖura da niyyar da Asubar fari, ta tashi ta fice, amma bacci mai nauyin gaske ya yi awon gaba da ita, sai da aka kusa idar da salla, Nene ta tashe ta yi sallar Asuba.
Tana idar da sallar kuma, Muhsin ya tashi ya saka rigima, Nene ta Ιauke shi suka tafi Ιakinta.
Tun da wuri yaran Nene suka zo, suka Ιauki kayan Abinci, amma Nene ta Ζi fita ranar ta wuni a gida, yaranta ne suka je suka sayar da Abincin.
Abu kamar wasa a jere kwanaki huΙu Nana tana yinΖurin guduwa, amma Nene ta kasa ta tsare tamkar ta san abin da Nana take shiryawa.
*****
Jamila ta nuna wa Hajiya Sa'a tamkar ba ta san ita ta taka wa Ιan ta Abba burki a kanta ba, Hajiya Sa'a sai shirin bikin Abba take yi, yayin da gefe guda kuma Jamila ta yi blocking Ιin sa, ta daina Ιaga wayarsa gaba Ιaya.
Dama idan Hajiya Sa'a na nan, ba ya iya yi mata magana, da zarar ta fita kuma sai Jamila ta kulle Ζofar sashen. Ya rasa abin da yake yi masa daΙi, har layi ya canza ya kira Jamila, amma tana Ιagawa ta ji muryarsa ta kashe.
Ga shi tun da Hajiya Sa'a ta fuskanci abin da yake tsakanin su, ta daina yawan fita ta bar Jamila a gidan, idan ma fita za ta yi sai dai su fita tare. Sai dai yau Jamila ba ta jin daΙi, dan haka Hajiya Sa'a ta fita ita kaΙai, saboda ta sakankance Abba yana can kasuwa.
Awa guda da tafiyarta, Jamila na kan doguwar kujera tana bacci, ta ji tsayuwar mutum a kan ta. Ta buΙe idonta a hankali ta ga Abba a tsugune a gabanta yana kallonta.
Tashi ta yi zaune tana tsuke fuska tare da gyara zaman rigarta za ta tashi.
Cikin zafin nama da tsoron rashin sabo, ya riΖe hannunta ya ce "Dan Allah Jamila ki tsaya ki saurare ni" ya yi maganar cikin marairaicewa kamar zai yi kuka.
"In saurare ka ka ce mini me Yaya Abba? Dan Allah ka rabu da ni." Ta yi maganar itama idanunta fal hawaye, saboda ba ta taΙa sanin ta kamu da matsananciyar soyayyar Abba ba, sai yanzu da Hajiya Sa'a take ΖoΖarin farraΖa su.
"Jamila dan Allah ki fahimce ni, kin san a son raina ba zan auri wata ke ga ki na bar ki ba, wallahi Jamila ina son ki, ban taΙa son wata 'ya ba sai ke"
Ta kalle shi hawaye na zuba daga idonta ta ce "Ko ma mene ne, ai yanzu aure za ka yi, ka rabu da ni dan Allah"
Girgiza kai ya yi cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali, ganin yadda take zubar da hawaye, zai yi magana ta fizge hannunta ta shiga Ιaya falon, bai yi Ζasa a gwiwa ba, ya sake bin ta yana ΖoΖarin rarrashinta.
Sai dai kash, garin ya rarrashi Jamila, sai shaiΙan ya buga musu ganga su ka taka rawa, duk da Jamila ta fuskanci cin zarafi da keta haddi a Ζungiyarsu ta asiri, a wannan karon ma tsoro da rashin sabo suka yi tasiri a a gare ta, duk da a nasa Ιangaren ma haka ne.
Daga shi har ita suka saka kuka mai cike da nadama da dana sanin abin da suka aikata.
Maganganun Nana suka din ga dawo mata daki-daki, na nasihar da ta din ga yi mata a baya. Duk da babu wanda ya san halin da Nana ne ciki, a tsawon wannan lokacin kusan shekara guda, amma gara Nana da ita, Ko ba komai Nana aure ta yi, ita kuwa fa da fari bokaye da aljanu sun kwanta da ita, a wannan karon kuma ruΙin soyayya da sharrin shaiΙan.
"Jamila, dan Allah ki yi haΖuri, ki kuma rufa mini asiri, ke ma kin sa hakan ba halina ba ne ba, amma duk yadda zan yi, zan aure ki, ni na fara aikata Ιarnar nan, kuma zan gyara ta in sha Allah"
Jamila ta kalle shi ta kawar da kai, tana jinjina lallai Abba bai san komai ba, tun da bai iya gane ba budurwa ba ce ba, duk da bayan abin da Hajiya Sa'a ta kai ta aka yi mata, bazama ta yi neman magungunan gyara.
Ya lallaΙata ta gyara jikinta, ta nemi guri ta kwanta, ya rasa abin da yake yi masa daΙi. Ya koma part Ιin sa ya rufe Ζofa, kawai ya fashe da kuka. Bai taΙa tunanin aikata zina a rayuwarsa ba, ba ta taΙa burge shi ba, bai kuma taΙa kawo ta a ransa ba. Sai dai yau ya wayi gari da aikata ta dumu-dumu.
Sai dai wani abin mamaki duk da abin da ya faru a tsakanin su, bai daina jin matsananciyar Ζaunar Jamila ba. Ya rasa dalilin da ya sanya Mummy ba ta son alaΖar su, duk da irin kusancin da yake tsakaninta da Jamilar.
A kwance Hajiya Sa'a ta dawo ta tarar da Jamila. Ta ce "Daughter haryanzu jikin ne? Ko Asibiti za mu je ne?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a Mummy na sha magani ai"
"Yakamata ki warke, mun kusa zuwa taron Ζungiya fa na shekara, lokaci ya kusa"
Kawai Jamila ta gyaΙa kai.
"Ga shi kuma haryanzu babu wani labari da ki ka samo, a kan 'yar uwakki, dan haka sai ki shirya sadaukar da jini"
Jamila dai ta yi shiru, tana jin kamar ta kashe tsinnaniyar matar ta huta.
*****
Nana na zaune tana shayar da Muhsin, Nene tana gefe tana lissafa kuΙin da aka kawo mata daga gurin sayar da Abincinta.
Nana ta numfasa ta ce "Nene wai me yasa kwana biyu ba kya fita gurin Abinci ne?"
Nene ta kalle ta ta ce "Na fita ki samu damar guduwa ko?"
Nana ta yi turus tana kallon Nene.
Nene ta yi murmushi ta ce "Yarinyar nan ki na wasa da ni, tuni na gane duk wani take-taken ki ai, jira nake yi na ga iya gudun ruwanki. Ke yanzu idan ki ka fita gidan uban wa za ki je? Ki na da tabbacin za ki iya sake haΙuwa da mutanen da za su kula da ke ne? Ko an gaya miki kowa ne zai iya yin taimako?
Kin tattara kayanki gaba Ιaya, kina Ιauke Ιanki daga Ιakina, jira ki ke yi ki samu dama ki gudu, to ki tafi duk inda za ki tafi, amma ba za ki tafi da jaririn nan kina gararanba a gari ba, tun da duk ΖoΖarin da nake yi a kan ki ba kya gani. Kina zaune a nan na saka ana ta yi mini cigiyar masu gadi da suke zuwa Nigeria, ko akwai wanda ya san mai suna Habu ko Sayyid ki ka ce sunansa ko wa? Anma ba kya gani, to ki fita ki tafi duk inda ki ka ga dama, tun da ba ki da kan gado, kuma ba ki san darajar igiyoyi ukun da ke kan ki ba"
Nana ta sha jinin jikinta, da faΙan da Nene take yi mata. Ta ce "Dan Allah Nene ki yi haΖuri, na ga na Ιora miki Ιawainiya ne ga shi haryanzu ina zaune babu wani labari a kan sa".
"Ni na ce kin Ιaura mini Ιawainiya ne uwar iya? Ki yi duk abin da ki ka ga dama"
Nana ta ce "Dan Allah ki yi haΖuri ba zan sake ba" Nene ta yi mata shiru, daidai lokacin kuma Muhsin ya gantsarawa Nana cizo, da 'yan haΖoran da suka fara leΖowa.
A fusace ta dake shi a kan pampers Ιin jikinsa, ta cire shi daga jikin Nonon, ta zaunar da shi tana Ζara tsuke fuska tare da hararsa.
Sexy eyes Ιin sa irin na mahaifinsa ya zuba mata, yana kallonta ko Ζiftawa ba ya yi, gaba Ιaya ya rikiΙe fuskarsa ta koma ta Sayyid sak, farar fatarsa ta yi jawur.
Nene ta ce "Yaka yaron kirki, ka Ζyale ta da halin ta, shi ne za ki huce a kansa, ai ni na yi miki ba shi ba"
Ya rarrafa ya koma jikin Nene ya kwanta yana ci gaba da kallon Nana. Sai kuma jikinta ya yi sanyi ta ji zuciyarta ta yi mata nauyi da abin da ta aikata, ba tare da duba ΖanΖantar Ιan yaron nata ba.
Ta shige Ιakinta ta mayar da kayanta da ta haΙe guri Ιaya inda suke. Wayarta ta Ιaukko da babu layi a cikinta, ta duba jakarta ta Ιaukko memorynta ta mayar kan wayar, ta fara duba hotunan Sayyid da ke ciki. Har da hotunan Haidar Ιan gurin Shukura a cikin wayar, da hotunanta na aure da aka yi mata da wayar.
Gaba Ιaya ta ji tana kewar Ζasa Nigeria, amma hakan bai sanya ta ji za ta iya komawa a yanzu ba.
Tunaninta ya katse bayan da ta ji muryar wata Ζawar Nene a tsakar gida, wadda ita ta yi hanyar kai Nana gurin koyon girke-girke. Amma Nana ta Ζi fitowa.
Hira suke yi da Nene, take ba ta labarin ma'aikata ake nema, wanda suka iya girki sosai a wani restaurant, na wata Hajiya a can cikin birnin MaraΙi.
Nene ta ce "Ba na yi wa Nana irin wannan harkar ne, saboda mutanen banza, ba dan haka ba ai da na ce ta je, tun da ta iya girki sosai"
Matar ta ce "To ai a Ιangaren girki kawai za ta zauna, su na buΖatar kuku amma mai tsafta wadda ta iya girki, kuma tana biya sosai kin san buzayen nan kamar ba su san ciwon kuΙi ba, buzuwa ce mai gurin"
Nene ta ce "Ai kin ga tana da yaro, shayarwa take yi, ai da na ce a kaita, amma idan za su Ιauke ta da yaron shikenan".
"Anya kuwa, gaskiya ba na tunanin haka, ba ma za su yadda ba. Idan ta tafi a Ζalla za ta iya yin wata, ba ta zo gida ba, za a ba ta komai a can. bari na tashi na tafi dama tsayawa na yi mu gaisa sai anjima"
Suka yi sallama matar ta tafi.
Nana ta fito da sauri ta ce "Nene, ina son zuwa gurin abincin buzayen nan"
Nene ta ce "Kin yarda mijin naki buzu ne kenan? Daga an ce gurin buzuwa kin rikice za ki je, bayan da kin ce mini ba ki san Ζabilarsa ba, Allah dai ya shirye ki."
Nana ta yi shiru, tana mamakin yadda aka yi Nene take iya gano ta idan ta yi mata Ζarya.
Nana tun dukan da ta yi wa Muhsin, juyin duniya har la'asar bai Ζara waiwayarta da sunan ta shayar da shi ba.
Sai da ta ji sun cika, sun fara damunta, sannan ta Ιauke shi ta ba shi, amma fafur ya Ζi karΙa, ta kaΙa ta raya ya Ζi sha.
Nene tana kallon su, ta Ζi magana, ta dama masa kunu ta haΙa da nono ta zaunar da shi ta ba shi ya sha, ya ci gaba da wasan sa.
Nana ta ga sun mayar da ita saniyar ware ma. Har garin Allah ya waye, bai saurari Nana ba.
Ta sake Ιaukarsa, saboda yadda nonon ya cika, yake yi mata ciwo, amma fafur yaron nan ya Ζi sha.
"Dan Allah yaron kirki ka yi haΖuri ka sha, ba zan sake dukan ka ba, dan Allah ka sha ba ka isa yaye ba" Nana ta yi maganar cikin damuwa.
Nene ta kwashe da dariya, ta ce "Kin ga ki Ζyale yaron nan, ina ga fa ya yi zuciya ya yaye kansa, sai dai yi haΖuri"
Kamar Nana za ta yi kuka ta ce "Nene wata takwas sai ya yaye kansa? Ya yi wuri ai"
"To ba ke ki ka janyo koma mene ne ba?, tun da kin ce da babansa yake kama komai da komai, wataΖila har halayensa ya Ιaukko, kuma wataΖila wannan abin da ya yi akwai abin da yake nunawa bamu gane ba. Tun da yana shan kununsa, yana rarrafensa, ki rabu da shi kawai. A haΙa sabaya da sauran saiwoyi, ki yi ta sha saboda kar su lalace".
Kamar Nana za ta yi kuka ta ce "Nene wata takwas fa"
"To ai ga ki nan ga shi. Sai ki ba shi ya sha ai"
Da Nana ta Ιauke shi da nufin, ta shayar da shi, sai ya hau zunduma ihu,yana turjewa sai dai ta Ζyale shi.
Nana ta din ga jinjina yadda aka yi, Ιan wata takwas ya san ya yi zuciya da abu.
Sai da aka kwana huΙu, Nana ta ga da gaske ya yaye kansa, iyaka ya zo jikinta ya yi wasan sa ya tafi.
Nene ta ce "Nana ki daina damuwa fa, girmansa tubarkallah da Ζiriniyarsa kamar ta Ιan shekara guda ce, ki rabu da shi kawai, daga yanzu idan za ki yi magana ki din ga yi masa da girmamawa, ki daina yi masa tsawa, manya ba sa son wargi. Kuma ki din ga duba darajar sunan da ki ka sanya masa" ta yi maganar tana yi wa Muhsin rawa.
"To Nene sai na bari ya lalace ba zan ce masa bari ba?"
"A'a ban ce kar ki ce masa bari ba, amma a wannan yanayin shi sarki ne, abin da yake so haka za ki yi haΖuri ki yi masa. Da kin tsaya a zare masa ido kawai da haΙe rai, amma saboda na yi miki faΙa, ki ka haΙa masa da duka, kuma ki ka Ζwace ki ka dungurar da shi, dole ya bar miki abin ki ai".
Nana kalle shi yana ta wasa da kofi, yana bugawa a Ζasa, shi ma ya Ιago ya kalle ta. Sayyid ta tuna lokacin da ya ritsa ta yana yi mata kashedin a kan daina yi masa tsawa ko Ιaga masa murya.
Wani guntun murmushi ya suΙuce mata.
Nene ta ce "Ni kuwa Nana ga shawara"
Ta ce "To Nene"
"Kamar yadda ki ke faΙa motsi ya fi laΙewa, na ce ko dai za a jarraba ki je gurin aikin nan, na harkar dafe-dafen ko Allah zai sanya a dace. Duk da ba na jin a jikina, masu kuΙi a cikin buzaye masu katafaren gurin abinci, za su iya tafiya aikin gadi, amma bamu san ina rana za ta faΙi ba"
Nana ta Ιan yi jimm sannan ta ce "Ban san ya zan yi ba ne, tun da kin ga ga Muhsin. Ko za su din ga bari na je na dawo kullum?".
Nene ta ce "Ki na ji fa ta ce sai ki yi wata ba ki zo gida ba, kuma akwai tazara a tsakaninmu sosai, kuma ba zai yiwu ki tafi da Muhsin ba, ba za su yarda ba. Amma ga shawara idan kin ga kin yarda da ni, ki bar mini Muhsin a nan, ki je ko ai
kin na wata uku ki yi, ko Allah zai sanya a dace, sai ki ci gaba da cigiyarsa a gurin."
Ayshercool
08081012143
67
Nana ta yi turus, tana kallon Nene.
Nene ta ce "Ba zan yi miki dole ba, dan kuwa wannan magana ce da kowacce uwa sai ta jinjina girmanta da nauyinta.
Sai dai ni ba zan takura miki ba kuma ban ce sai kin yadda da ni ba, ko mene ne za mu yi shi ne a gaban hukuma, mu je mu yi yarjejeniya mu saka hannu sannan ki tafi. Ban san dalilin da Allah ya sanya ya haΙa ni da ke ba, duk rashin son mutane na, ki ka shiga raina ba nake tausayinki ke da yaronki. Har ga Allah ina fatan ki haΙu da mijinki ko danginsa, ki samu ki koma gida ki nutsu ki kula da yaronki. Kamar yadda na gaya miki ne, ba zan yi miki dole ba, ki je ki yi shawara idan kin amince shikenan, idan ba ki amince ba babu wani abu, ni dai fatana Ubangiji Allah ya bayyana abin da ki ka fito nema".
Nana ta yi shiru, ΖwaΖwalwarta gaba Ιaya ta Ιauki caji da tunani daban-daban.
****
Jamila kuwa tun da ta je gida, Mama take tambayarta ko lafiya ta ganta wani iri, amma ta ce mata babu komai.
Ta shiga Ιaki ta nemi guri ta kwanta, sallolinta kawai ta yi na magariba da isha'i ta sake kwanciya. Gaba Ιaya abin Duniya ya gama damunta, dana sani da takaici duk ya cunkushe mata zuciya.
Wayarta ce ta fara ringing, ta duba ta ga baΖuwar lamba ce, jikinta ya ba ta Abba ne, ta Ιaga kiran ta saka a kunnenta.
Muryarsa Ζasa-Ζasa ya kira sunanta ya ce "Ya jikin naki?"
"Da sauΖi" ta amsa a hankali hawaye na ci gaba da gangarowa kan kumatunta.
"Dan Allah Jamila ina Ζara ba ki haΖuri, kuma ki dubi girman Allah ki rufa mini Asiri, ke ma kin san hakan ba halina ba ne ba. Wallahi na rasa inda zan sanya zuciyata na rasa abin da yake yi mini daΙi. Yanzu haka zazzaΙi ne a jikina. Dan Allah ki yafe mini Jamila, na san koma mene ne duk laifina ne. Amma in sha Allah kamar yadda na yi miki alΖawari zan aure ki Jamila, wallahi ina son ki, duk abin nan laifin Mummy ne amma ki yi haΖuri ki yafe mini"
Jamila ta ci gaba da kuka, ta kasa ce masa komai, ya Ζara ruΙewa ya ce "Dan Allah ki yi mini magana, dan Allah ki yafe mini idan ba ki yafe mini ba na san har na koma ga Allah, ba zan samu nutsuwa ba" Ya yi maganar yana kuka mai cike da nadama tamkar Ζaramin yaro.
Duk yadda Jamila ta so jin haushinsa sai ta kasa, tabbas ita shaida ce wannan ba halin Abba ba ne, dan da halinsa ne da ba zai din ga wannan kukan ba, zai ga ya ci bulus ne kawai.
"Yaya Abba na yafe maka, mu haΙu mu nemi yafiyar Allah, sannan ka daina kukan nan dan Allah, ka sha magani ka kwanta. Kuma Asiri idan na tona kaina na tonawa ba kai ba, Ubangiji Allah ya yafe mana"
Ya tashi zaune a kan gadonsa, cikin damuwa ya ce "Da gaske kin yafe mini Jamila?"
"Eh Yaya Abba, sai da safe, kaina yana ciwo sosai"
"To na zo na kai ki Asibiti ne?"
Jamila ta ce "A'a, na sha magani ina jin bacci ma, sai da safe" ta katse kiran tana Ζara duΖunΖunewa a cikin bargo.
Wata irin ajiyar zuciya ya din ga yi, ya nemi guri shi ma ya kwanta, zuciyarsa fal tunani daban-daban.
*****
Nana hankalinta ya rabu kashi-kashi, a jikinta ba ta jin Nene za ta cutar da ita, duba da yadda take Ιawainiya da ita da Ιanta, tamkar ita ta haife ta. Sai dai ta yaya za ta iya ta tafi ta bar Ιan ta, da matar da babu dangin iya babu na Baba a tsakanin su.
Sai dai tabbas akwai buΖatar ta gusa, ta yi wani yinΖuri, domin ci gaba da ΖoΖarin haΙuwa da mijin nata, amma ba ta ji ta gamsu da wannan shawarar ba.
Sai dai tun da suka yi maganar nan, da ta kwanta take mafarki ga ta a gurin girke-girken, tana cikin gurin girkin, ta waje sai ga din ga jiyo muryar Sayyid yana magana. Idan ta fita sai ta neme shi ta rasa, sai dai ta ci gaba da jin muryar ta sa, nesa da ita kaΙan, sai dai ba ta san daga wane Ιangaren muryar tasa take ba. Sai ta yi irin wannan mafarkin sai ta farka.
Ta rasa abin da yake yi mata daΙi, kawai sai ta ci gaba da addu'a a kan lamarin, ta juya ta ci gaba da bacci, sai dai babu tsammani sai ga ta a Ιakin karatun Ζaisar, an yi mata gyara sosai, an Ζara yawan litattafan da suke ciki.
Ya saka mudubinsa a gaba, yana ta zuba masa wani ruwa yana wanke shi.
Bai ce wa Nana komai ba, har ta gaji da tsayuwa, ta Ιan yi gyaran murya. Ya Ιaga kai ya kalle ta. Ta ce "Sannu da aiki"
"Yauwwa" ya amsa yana tashi tsaye.
Ta ce "Kwana biyu ina ka shiga ne?"
Ya Ιaga kai ya kalle ta ya mayar ya sunkuyar yana Ιaukar wani littafi.
"Amm dama ina ta son na ganka, na tambaye ka, sannan na roΖe ka alfarma. Dan da kai da Giyaz da duk wani mai son Ιaukar fansa a kan zuriyarmu, ya Ιauka a kaina, dan Allah ku Ζyale mini yarona. Na ga rannan ka ba shi wani abu da ban san ko mene ne ba, dan Allah kar ku yi masa komai"
Bai ko motsa ba, balle ta sanya ran zai yi mata magana.
"Ζaisar ka yi magana ma dan Allah"
"Na ce miki ne? Ko har kin manta abin da ki ka faΙa a kaina, saboda abin da na yi wa mahaifina a kan na kare ki?"
Sai kuma Nana ta yi shiru, ta sha jinin jikinta.
Ya wurgo mata littafin nan da ta fara karantawa, ya ce "Ga wannan ki ci gaba da karantawa, wataΖila zai yi miki amfani a gaba" Ta kalli littafin ta kalle shi, ta ce "Me yasa ka amince na karanta wannan littafin, wancan kuma ka hana ni karantawa? Ni ba zan iya ci gaba da karantawa ba, babu komai a ciki sai tashin hankali da zubar da jini na tsagwaron rashin tausayi da adalci, ni bai burge ni ba, ba zan karanta ba"
"Ko? Amma idan an yi magana sai ki nuna kamar babu wata halitta da ta kai Ιan Adam tsarki da tsoron Allah. Allah ya karrama Ιan Adam a kan dukkanin halittunsa. Amma ba duk Ιan Adam ne mai tsarkin zuciya ba. Wannan zubar da jinin da kashe-kashen da yake rubuce a cikin littafin nan, da gaske an yi su, domin cimma buΖatar Duniya, kuma haryanzu ana kan yi ma. Abu ne da ya faru wani Ζarni a baya, kuma abin yake ta bibiyar zuriyar har wannan zamanin. Na ce ki karanta kin Ζi, kin ce ba kya so shikenan ba zan yi miki dole ba, amma bari ki ga wani abu.
Ya Ιauki littafin ya buΙe cikin wani feji, Ιangare Ιaya na bangon littafin zane ne, Ιangare Ιaya kuma bayanin yadda taswirar zanen take ne. Ya haska littafin a jikin mudubin.
A nan take hoton ya bayyana a jikin mudubin, wannan Ιakin da take ganinta a ciki ita da Sayyid shi ne ya bayyana a jikin mudubin, ba iya haka ba har Ζamshin da gurin yake yi ta fara ji a hancinta.
A rikice ta ce "Nan gurin? Dama ina son sanin ina ne, yaya aka yi muke zuwa gurin nan ni da Sayyid, kuma idan abu ya faru a gurin kamar gaske."
Ζaisar ya rufe littafin ya ce "Ai kuma kin yi wa kan ki, ba zan bayar ba. Ya jefa littafin sama ya Ιace Ιat ita kuma ta tashi daga baccin.
****
Kwana biyu Jamila ba ta je gidan Hajiya Sa'a ba, saboda jikinta da ya matsa, idan Abba ya kira wayarta a kashe, ga shi ba ta zuwa gidansu, shi ba abin ya tambayi Mummy ba.
Yana kwance a Ιakinsa, ya tura mata saΖo. "Hankalina a tashe yake Ζanwata, dan Allah ki yi mini ko flashing ne, hankalina na matuΖar tashe dan Allah ki Ιaga wayata"
Ya tura mata saΖon, tare da ajiye wayar.
Hajjya Sa'a ce ta shiga Ιakin nasa, ta iske shi a kan kujera. Yana ganinta ya tashi zaune. Daga tsaye ta ce "Abba ba zaka fita bane? Baka fito ka karya ba, kuma baka fita kasuwa ba meyafaru ne?"
Ya girgiza mata kai ya ce "Babu komai fa"
"A'a akwai wani abu, na kasa gane kan ka 'yan kwanakin nan, hatta shirin bikinka nikaΙai nake abina, me yake damunka? Duk saboda Jamila ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba kin ce ba kya son alaΖarmu ba, ni kawai ba ni da lafiya ne" ta yi shiru tana nazartarsa, kawai ta yi Ζwafa ta fice daga Ιakin.
Ya koma ya jingina, ya lumshe idanunsa, sai kiran Jamila. Ya Ιauka ya katse kiran ya kira ta cikin azarΙaΙi ya ce "Ζanwata lafiya kuwa? Ba kya Ιaga wayata ko haryanzu kina fushin ne?"
Cikin numfarfashi ta ce "A'a Yaya Abba, ba ni da lafiya ne haryanzu"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ya aka yi ba ki gaya mini ba? Kina gida ne?"
"Eh" ta amsa muryarta Ζasa-Ζasa.
"To shirya gani nan, bari na zo mu je Asibiti"
"To Yaya Abba, na gode" ta ajiye wayar da Ζyar. Hankalinsa ya yi mummunan tashi, a zatonsa aika-aikar da ya yi ce, ta sanya mata rashin lafiya har haka.
Da sauri ya zura kaya, ya Ιauki mukullin motarsa ya yi waje ya tafi gidansu Jamila.
Yanayin yadda Jamila ta fito, tamkar ya je ya Ιaukko ta, fuskarta duk ta kumbura, da alama tana jin jiki sosai da sosai.
Ya buΙe mata gaban motar ta shiga. Cikin tausayawa ya ce "Sannu Ζanwata, haka jikin naki ya yi ba ki gaya mini ba?"
"Ba na son tayar maka da hankali ne, kai ma ba ka da lafiya, amma Mama fa ta kai ni Asibiti" Gabansa ya faΙi ya ce "Allah ya sa ba ta gane komai ba"
Ta girgiza kai ta ce "Babu abin da ta gane, zazzaΙi ne fa kawai"
A tsorace ya ce "Jamila ko ciki ne?"
Ta kalle shi, sai da ta ji kamar ta yi dariya, duk da halin da take ciki. "Tun kan hakan ta faru ai nake rashin lafiya, ba wannan ba ne ba, ba wani ciki".
Ya sake cewa "Amma duk da haka kamar ya assasa miki ciwon, amma bari mu je Asibitin" haka ya ja motarsa su ka bar layin.
Safiyya ce ta tarar da Hajiya Sa'a ta cika ta yi fam, tana zaune a falonta.
Da kyar Hajiya Sa'a ta iya amsa mata sallamarta. Ta zauna a kusa da Hajiya Sa'a ta ce "Mummynmu maganin kukanmu, lafiya kuwa na ga ranki a Ιace?"
"Ba dole ki ganni a haka ba? Da gaske fa Abba son Jamila yake yi, nema yake ya bujire mini, kin ga yadda duk ya damu saboda na raba su. Ga bikinsa na Ζaratowa da Yasmin.
Maman Khairat ta tuntsure da dariya ta ce "To meye a ciki, idan tana son sa ki bar su mana"
Hajiya Sa'a ta kalle ta ta ce "Amma ba ki da hankali, yarinyar da shugaban Ζungiya suka kwanta da ita, sai Abba ya auri ragowa? Ba ma wannan ba, kar ki manta idan Ζungiya ta buΖaci ta bayar da jininsa fa, shikenan ta bayar da jinin tilon Ιan nawa?"
Maman Khairat ta ce "Na fahimce ki Mummy, da wasa nake yi miki, amma maganar gaskiya yanzu haka kan na taho ma, na ga motar Abba a unguwarmu, kuma na san ba ku da kowa a unguwar, dan haka gurin Jamila ya je"
Cikin matsanancin Ιacin rai ta ce "Gurin Jamila kuma? Yarinyar nan ta zame mini masifa da bala'i ko? Maganinta zan yi, wallahi sai ta rabu da Abba, ko ita ta haifar mini shi"
Maman Khairat ta ce "Ki yi dai a hankali, kin san halin yaran zamanin nan" Hajiya Sa'a ta ci gaba da huci, tamkar macijiya saboda takaici.
Maman Khairat ta ce "Ina dai Ζara gaya miki, ki bi komai a sannu, kin san halin yaran zamanin nan, sai su baki mamaki. Shi kansa Abban duk yadda yake yi miki biyayya, idan ba ki yi wasa ba, a wannan karon tsaf zai bujire miki".
"Ai ga alamu nan ina gani, amma ni zan sanya wa Abba doka, na hana shi abu, amma ya zagaye ya je ya aikata? Shikenan, na san matakin da zan Ιauka. Da ni suke zancen.
Alhaji Fatuhu ne zaune a harabar gidan sa, a kan kujera, ya kan Ιan iya dogara sanda ya tashi tsaye yanzu. Idan aka taimaka masa har harabar gidan yake iya fitowa, duk da idan jikin ya tashi kuma, sai ba ya iya hakan ko kaΙan.
Yana zaune a harabar gidan, yana kallon Ζaramin Ιan sa na gurin Fadila, yana ta wasa da Ball, yana jin yadda Ζaunar Ιan ke ratsa masa zuciya. Gefe guda yana tausayin yaron nasa, dan bai taΙa iya saya masa abin naira biyar ba da kuΙinsa. Hatta abincin da suke ci, 'yan uwa da abokan arziki ne suke kawo musu, ga shi wanda ya sai gidansa ya ba du aronsa suke zaune a ciki, ya fara Ζishin-Ζishin Ιin yana buΖatar gidan.
Fadila ce ta Ζaraso tana murmushi ta ce "Daddy kallon Ball ka ke yi?"
Ya yi murmushi ya ce "Eh mana, yana ta in tashi mu yi tare, ina ma zan iya da ko sau Ιaya mun yi tare, no na saka shi farinciki"
Ta zauna a Ιaya daga cikin fararen kujerun, ta ce "A hakan ma, ka na sanya shi farin ciki ai"
"Fadila"
Ta tattara masa nutsuwarta ta ce "Na'am Daddy"
"Kin san wani abu?"
Ta ce "A'a sai ka faΙa"
"Ina yarinyar nan Nana?"
"Wace Nanan?"
Ya Ιan yi shiru sannan ya ce "Malamar Muhsin, da yake faΙa"
Ta ce "Ohh Allah sarki, na tuna ta"
"Mafarkinta nake yi"
Ta Ιan yi saroro ta ce "Mafarki kuma?"
"Eh Fadila, har aikawa na yi gidansu, a yi mini alfarmar a faΙa mini inda gidanta yake, wani abu nake gani da ya fara damuna"
Ta danne kishinta ta ce "To ka yi mini bayani mana"
"Kin dai san ni ba ma'abocin, biye-biye ba ne ba, da yarda da harkokin shirme da zai sanya na ji wani zai iya cutar da ni ba, amma a jere sau kusan biyar ina mafarki da ita".
Cikin Ζosawa ta ce "Daddy ka yi mini bayani, ka na ta kwana-kwana da ni"
"Ganinta nake yi a mafarki, tana ce mini an yi mini sihiri, karo kusan biyar fa"
Fadila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Kuma ka yarda?"
"Ba ma son na yarda na gazgata hakan, amma na ji kamar na fara amincewa, saboda yadda nake ganinta abin ya yi yawa, ya wuce a ce shirmen mafarki ne kawai."
Fadila ta numfasa ta ce "Ai ni tuntuni na zargi hakan, amma sanin halinka na rashin son irin wannan abubuwan, ya sanya ba na yi maka maganar. Ko wannan sauΖin da ka ke samu, na san tasirin addu'a ne. Dan kuwa Umma kuΙi take bayarwa ana sauke karatun Alqur'ani."
Cikin mamaki ya ce "Amma ke kina ganin, akwai wanda zai damu da ni, har ya iya yi mini sihiri? Ina azkar Ιina da addu'oina, gani nake sun wadace ni, babu wanda zai damu da ni ya yi mini wani sihiri."
Ta gyara zamanta sosai ta ce "A duk Duniya waye ya koyar da mu azkar Ιin? Na san za ka ce manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, amma an yi wa fiyayyen halitta sihiri, kuma ya kama shi.
Daddy ka yi haΖuri da abin da zan faΙa maka. Kana ibadarka ta farilla daidai gwargwado, amma ba ka damu da nafilfili ba, da tsananta addu'a. Kana ganin Allah ya baka duk abin da ka ke buΖata, ba ka fiye tsananta addu'a da neman kariyar Allah ba.
Sannan azkar da ka ke yi, kuma a yi shiri ya kama ka, ba ya nufin Allah baya kare ka, amma wataΖila jarrabawa ce daga gare shi, kamar yadda ya ce zai jarrabe mu, ba a fasa jarraba mai imani, kuma jarrabawa alama ce ta soyayyar Ubangiji. Allah ya jarrabe ka da cuta, ka nemi magani shi ma a cikin jarrabawa ne, amma Daddy ka naΙe ka dage, kai sai na Asibiti kawai, bayan akwai magungunan musulunci da suke na halal babu kauce hanya, idan an jarraba ba a san inda za a dace ba, amma ka Ζi ka ce kai sai na bature, na baturen kuma ba a gano komai ba, kame-kame kawai ake yi."
Ya yi shiru yana nazarin kalaman Fadila, ya numfasa ya ce "To yanzu mene ne abin yi? Kin ga yanzu bani da kuΙi, kuma irin wannan abubuwan sai da kuΙi".
"Kar ka damu, zan yi wa Kawu magana, shi ma ranar da ya zo duba ka, ai ya ce a yi na islamic, Alhaji Zailani ya ce ba za a yi ba. Da haka za tuntuΙe shi, in sha Allah ba zai gagara ba"
Alhaji Fatuhu ya ce "Allah ya sa, dama duk ina tsoron, kar a aikata abin da zai kauce wa hanya ne, amma na amince yanzu a yi Ιin"
Ta yi murmushi ta ce "To shikenan, yaya ita yarinyar an gano ta Ιin?"
Ya girgiza kai ya ce "Ina fa, an ce wai ba ma ta Ζasar nan, amma ina ta mamakin dalilin da ya sanya nake mafarinta, kuma idan na farka sai na ji kamar a zahiri, shi ya sanya ma na fara yarda"
Fadila ta ce "To Allah ya sanya a dace" ya amsa da "Amin"
*****
Ζangaren Nana kuwa, gaba Ιaya kanta ya kulle a kan lamarin nan, kawai sai ta dasa addu'a, a kan idan da alkhairi a tafiyarta, Ubangiji Allah ya sanya mata son tafiyar, ya tsare mata Muhsin, idan kuma babu, Allah ya cire mata abin daga zuciyarta.
Kamar yadda ta saba ji haka ma wannan karon, ta ji muryarsa, da gudu ta ajiye abin da take yi, ta nufi taga ta leΖa sai ta hango giftwarsa da doguwar riga baΖa a jikinsa.
Da gudu ta fita daga gurin, ta nufe shi tana Ζwala masa kira, amma ya Ιace mata.
Cike da takaici ta yi juyi, tare da jan guntun tsaki, kawai ta ji hancinta ya fara shinshino mata, Ζamshin wannan Ιakin na cikin dutse, da take ganinsi tare da Sayyid.
Ta buΙe idonta a hankali, ta ji ana shafar cikinta a hankali, tare da yi mata numfashi a wuyanta.
"Sayyid" ta furta a Ιan tsorace.
"Asmyna, ina kewarki da yawa, gangar jikina na ta kewarki. Idan ina jin zafi babu mai bani sanyin da ki ke bani, babu wanda yake iya fahimtar kurman baΖin rayuwata, ki Ζaraso gare ni Please" ya yi maganar yana shafa wuyanta, tare da yin maganar Ζasa-Ζasa.
Ta saka hannu ta shafa gashinsa ta ce "Ina ta gaya wa Allah Sayyid, ya san lokacin da ya dace ya haΙa mu, amma jikina yana ba ni, ina daf da kai in sha Allah"
"Ki Ζaraso da wuri Asmyna, ina cikin matsananciyar buΖatarki"
"Ina ta ΖoΖari Sayyid, kuma ina gaya wa Allah, na san zai haΙa mu a nan kusa, kuma ina roΖonsa ya kare mini kai a duk inda ka ke, na san kuma yana ji ya kuma amsa in sha Allah"
"Nana, wai ba kya salla ne, gari ya fara haske fa" ta ji muryar Nene. Ta tashi tana mustustuke idonta, hancinta na ci gaba da jiyo mata sauran Ζamshin turaren nan.
Da ta yi salla ta idar, ta je ta samu Nene a Ιakinta, suka gaisa.
Ta ce "Nene na amince"
"Da me?"
"Zan tafi gurin yin girkin nan"
Nene ta ce "Ina fatan ba wani ne ya matsa miki ba? Ko kuma kunyata ki ka ji ba ki ka ce za ki je?"
Nana ta girgiza kai ta ce "A'a, wa ma na sani na saba da shi, da zai ziga ni na Ιauka? Babu wanda ya ziga ni"
Nene ta ce "To shikenan, zan kira ta a waya na ji, idan ba a samu wata ba, sai ki je. Sai mu je gurin jami'an tsaro mu yi yarjejeniya mu yi rubutu, mu je a yi a gaban su Auwwalu ma da Hajara"
Nana ta girgiza kai ta ce "A'a Nene, na yarda da ke, abin duk bai kai haka ba ai"
Nene ta ce "A'a, haka kurum wani irin ki ka yarda da ni, Ιan mutum fa zan riΖe miki, a'a, mu je mu yi a rubuce, yadda jami'an tsaro ma za su din ga sanya ido, kar wani abu ya faru ma. Sai dai abin da Allah ya aiko na Ζaddara wannan ba yadda muka iya, kuma na san za ki yi mini uzuri a wannan. Amma idan aka yi haka kema sai kin fi sakewa, hankalinki ya kwanta.
Nana ta jinjina kai ta ce "Ni dai, bakin da zan yi miki godiya ba ni da shi, amma ina fatan Allah ya yi miki tukuici da abu mafi dacewa da abin da ki ka yi mini na alkhairi, a duniya da kuma Lahira"
"Amin Nana, ai Ιa na kowa ne, Allah ya tabattar mana da alkhairinsa, ya kuma bayyana miki mijinki da ahalinsa cikin aminci".
"Amin uwata ta kaina" ta yi maganar tana murmushi.
Sai dai tun da Nana ta amince za ta bar wa Nene Muhsin, ta fara jin kewar Ιan nata, ta din ga jin kamar ta ce ta fasa. Saboda kallonsa kawai na sanya mata matsanancin farinciki da nishaΙi, idan ta tuna mallakinta ne shi Ιin. Tana jin ko ba ta ga Sayyid ba tana da Ζaramin Sayyid, duk da tana fatan ta gan shi Ιin, ko ba komai al'umma sa kalli Ιan nata da kima da daraja.
Ko da Nene ta kira matar, Matar ta tabbatar wa Nene, akwai sauran space Ιin da Nana, za ta yi musu aiki, sai dai a saka ranar da za su tafi ta kai ta.
Haka nan fargabar Nana ta Ζaru, ta rasa murna take ko tsoro, duk da abu mafi rinjaye kewar Ιan jaririn Ιanta ne, da yanzu take Ζara shaΖuwa da shi,Ζaunarsa take Ζara shiga ranta. Tana jin tamkar ta fasa tafiyar nan, amma Ζasan zuciyarta tana jin tafiyar ta ta alkhairi ne.
*****
Ζangaren Abba kuwa, sai da aka yi wa Jamila Ζarin ruwa, typhoid ne ya yi mata mummunan kamu.
Sai kuma damuwa da take ciki, jininta ya Ιan hau. Abba ya biya duk bills Ιin, ya janyo kujerar Ιakin, ya zauna a gaban gadonta, ruwan da aka saka yana shiga jikinta.
"Ko a kira Mama a waya a sanar mata ne?" Ya yi maganar cikin kulawa.
Ta ce "A'a, na gaya mata Asibiti zan je, ana gamawa sai ka mayar da ni gida"
Ya ce "To shikenan, mai zan sayo miki ki samu ki ci?"
"Ba na son cin komai, kawai kar ka matsa daga kusa da ni, ka zauna a nan" ta yi maganar tana riΖe hannunsa a cikin nata.
Ji ya yi zuciyarsa ta narke, da matsanancin tausayin kan su, ya ce "Ina tare da ke matata, har abada in sha Allah" ta yi murmushi tana Ζara riΖe hannunsa. A hankali kuma ta saki hannun nasa, da tuna rashin dacewar hakan, sai dai wani irin abu mai wuyar fassara take ji, game da Abban.
Yana kallon kiran Hajiya Sa'a, amma ya Ζi Ιagawa, kawai ya din ga jin zafinta.
Har azahar sannan ruwan da ake saka mata ya Ζare, ya Ιauke ta a motarsa, ya yi mata sayayya sannan ya mayar da ita gida.
Sai da ya tabattar ta shiga gida, sannan ya kira Mummy.
"Sai yanzu ka ga damar Ιaga wayar tawa?"
"A'a caji take yi ne, ki yi haΖuri?"
"Kana ina ne?"
Ya ce "Na Ιan je wani uzuri ne, na zo ne?"
"A'a shikenan" ta Ζyale shi, bayan tuna shawarar da Safiyya ta bata, wato maman Khairat.
*****
Kamar yadda Nene ta buΖata, sai da suka je gurin jami'an tsaro, suka yi yarjejeniya, aka rubuta da yaren hausa, French da kuma turanci, duk suka sanya hannu, a gaban su Auwwalu da jami'an tsaro.
Daga nan suka dawo gida Nene ta ba wa Nana wata 'yar madaidaiciyar Jaka, da za ta haΙa kayanta da za ta buΖata a ciki.
Ta kalli Nana ta ce "Nana dan Allah ki kula da kan ki, duk da na san ke kamammiyar yarinya ce, ba mutuniyar banza ba, amma tunatar da mumini abu ne mai kyau, ki riΖe mutuncinki, ki kiyaye hakkin aurenki. Idan ki ka ga wani abu na ba dai-dai ba, ko wanda ya saΙawa addininki, a haΖura da sabgar nan. Kuma cikin hikima za ki din ga bincikawar,ba sai kowa ya fuskanci ainihin abin da ya nai ki gurin bax
Nana ta jinjina kai ta ce "In sha Allah Nene zan kula da kaina, ba zan ba ki kunya ba, ki taya ni da addu'a, Ubangiji Allah ya sanya zuwana ya zame mana alkhairi baki Ιaya"
"In sha Allah, addu'a ina nan zan ci gaba da yi miki ita da yardar Allah."
Nana ta haΙa kayanta, amma ji take kamar ta fasa tafiyar, amma ta Ζarfafi zuciyarta, ta hana hakan yin tasiri a ranta.
Ranar Asabar, da safe matar ta zo domin tafiya tare da Nana.
Nene ta ce mata "Dan Allah gata nan amana, Hansatu, kar ki kai ta idan za a cutar da ita, kin ga yaro ne da ita Ζarami, dan Allah idan akwai matsala a gurin nan, gara ki saka a sallamo ta ta dawo gida."
Hansatu ta ce "Haba Nene, ya ki ke haka kamar ba ki yarda da ni ba ne?"
"A'a ba rashin yarda ba ne ba, 'yar amana ce shi yasa nake jadda da miki, ga kuma Ζaramin yaro da take da shi"
"Ba ki da matsala fa, ki kwantar da hankalinki"
Nana ta kalli Muhsin, da yake jikin Nene, yana wasansa, idanun Nana fal hawaye ta ce "My little Sayyid, zo ka yi sallama da Umminka" ya taso daga jikin Nene ya nufo Nana.
Hatta dogayen gaΙoΙin jikinsa, irin na Sayyid ne sak.
Ta rungume shi a jikinta, hawaye na zuba daga idanunta "Allah ka kula mini da Ιa na, Allah kar ka saka wani abin cutarwa ya same shi, Ubangiji Allah ka sanya na je na dawo na tarar da shi lafiya" ta furta a hankali Ζasa-Ζasa.
Ta Ιago ta kalle shi ta ga yana yi mata murmushi, ta sumbaci goshinsa, ta miΖe ta Ιauki jakar kayan nata, Nene ta rako su har bakin Ζofa, suka hau abin hawan da Hansatu ta zo da shi, suka tafi.
08081012143
68
Nana ta din ga waige, tana hango su Nene tare da Muhsin, har suka Ιacewa ganinta gaba Ιaya.
Hansatu su na tafe su na ta hira da direban motar, aka biya gidanta, aka Ιauki wasu matasan matan sannan suka Ιauki hanyar tafiya.
Tana jin yadda suke ta hirarrakinsu a cikin motar, amma ta kasa tofa komai, da ta rufe ido, Ιan jaririnta take hangowa, gefe guda kuma zuciyarta cike da fatan Allah ya sa tafiyar nan, ta yi mata rana.
A Ζalla sun yi tafiyar awanni biyu da rabi a mota, sannan suka isa wani gida.
Hansatu ta yi musu bayanin, a nan za su sauka su huta, washegari ta kai kowacce inda ta Ιaukko ta za ta kai ta. Nana ta din ga addu'a da fatan Allah ya sanya ba mugun hannu ta faΙo ba, duk da kafin ta taho Nene ta bata layi ta saka a wayarta, ta ce mata duk abin da ta ga ba ta yarda da shi ba, ta kira ta ta sanar mata.
A duk lokacin da Nana ta Ιaga wayar ta kalla, sai ta tuna Hajiya Amina, Haidar da kuma sauran jama'arta na Nigeria.
A gidan nan suka yi salla, aka ba su abinci suka ci, sai dai Nana ta yi mamaki ganin mata da yawa a gidan. Duk da Ζabilu ne daban-daban matan, akwai Zabarmawa, akwai Bugaje, da hausawa da sauran Ζabilun ma da ba ta sani ba a Nijar. Wai gidan kamar kamfani ne, wannan matan aiki ake nema musu, duk ciki Nana ce kawai 'Nigeria a cikinsu. Gaba Ιaya ta takure kanta ta kasa jikinta da su.
Gaba Ιaya daren ranar, Nana ta kasa bacci, ta din ga tunanin Muhsin, da tunanin ko zai yi kukan rashin ganinta.
Washegari Hansatu ta ce wa Nana ta shirya, ta Ιauki kayanta su tafi. Haka kuwa aka yi ta sake Ιaukarta su ka fita.
Nana ta sha mamaki, ganin haΙuwar da gurin cin abincin ya yi, kuma babban abin da ya Ζara bata mamaki, gurin cin abincin tamkar hotel.
Suka shiga cikin gurin, Hansatu ta kai Nana wani katafaren ofishi, da yak3 gurin mai kula da Ιaukar ma'aikatan, da yake namiji ne. Rawaninsa ne ya tabattar mata da buzu ne, ganinsa kawai sai Nana ta ji wani irin sanyi, tamkar ta ga Sayyid.
Nana ta gaishe shi, ya amsa sama-sama yana Ιan basarwa.
Hansatu ta ce masa "Wannan ita ce ma'aikaciyar, na kawo ta a yi mata gwajin, a gani idan za ku Ιauke ta" Ya Ιaga kai ya sake kallon Nana ya ce "Sannu ko"
Nana cikin girmamawa ta ce "Yauwwa sannu da aiki"
Ya miΖo mata Ζunshin wasu takardu ya ce "Ga wannan duba, ki ga yadda tsarin aikin namu yake, ki gani idan sun yi miki, kafin mu je inda za a yi miki gwajin, idan kin ci sai ki sanya hannu a takardun, ki fara aiki da mu"
Nana ta saka hannu ta karΙi takardun, amma ta ga rubutun French, ta kalli Hansatu, ta kalle shi ta ce "Ai ban iya fransanci ba"
Ya kalli Nana ya ce "Ba ki yi makaranta ba?"
Ta ce "Na yi, amma ni ban iya French ba, turanci na iya sai Hausa"
Hansatu ta ce "A yi haΖuri YallaΙai, 'yar Nigeria ce, daga Nigeria take"
Sai kuma ya kalli Nana ya faΙaΙa murmushinsa ya ce "Daga Nigeria ki ke? Ki ka baro babbar Ζasa kamar Nigeria ki ka zo jamhuriyar Nijar ki yi aiki da mu?" Nana ta Ιan risunar da kai tana murmushin dole, ganin yana murmushi shi ma.
Ya ce "Ahh to ai 'yan Nigeria Ζawayenmu ne, ba ma Ζawaye ba 'yan uwanmu ne. Dan haka zan ba ki aiki amma da sharaΙin za ki koya mini turanci, idan kin yarda na baki aiki" Nana ta yi murmushi, saboda yanayin yadda ya yi maganar cikin zolaya. Ya yi 'yar dariya ya ce "Ai duk wanda ya zo Nijar, mussaman daga Nigeria baΖonmu ne, akwai buΖatar mu karrama shi sosai da sosai, ko dan Ζara zumuncinmu da mutanen Nigeria. Dan haka babu wani abu, wannan wani ci gaba ne ma zan iya cewa gurin Abincinmu ya samu, kin ga girke-girken da ba a yi a nan, na can Ζasar kya din ga yi mana.
Mu na da gurin kwana na ma'aikatanmu, awa ashirin da huΙu muke yi mu na aiki. Kamar yadda ki ka gani babban gurin cin abinci ne da manyan mutane ke zuwa cin abinci.
Masu sayar da abinci daban, masu girki daban, ke za ki kasance a Ιangaren masu girki ne. Mu je mu zagaya ku ga gurin sosai da sosai.
Ya jagoranci su Nana, ya nuna musu gurin, tsarin ya yi wa Nana sosai, duk da abin da ba ta ji daΙi ba, maganar zuwa hutun sati Ιaya ne kacal, duk Ζarshen wata.
Su Hansatu za a din ga tura wa albashinta, su cire nasu kason su bawa Nana sauran.
Ita Nana duk hakan bai dame ta ba, babban fatanta buΖatarta ta biya kawai.
Suka kammala duk cike-ciken da za su yi, aka sallami Hansatu, Nana kuma aka kaita gurin kwanan ma'aikata.
Ζakin da aka kai Nana, su uku ne a ciki, da banΙaki a ciki. Ta ajiye jakar kayanta, Hansatu ta kalle ta ta ce "To Nana, kamar dai yadda ya gaya miki, mu kamfani ne, kuma a ΖarΖashinmu ki ka zo nan, dan haka gurinmu albashinki zai din ga tafiya, mu zamu din ga sallamar ki"
Nana hakan ko a jikinta, dan ita ko ba za su ba ta komai ba, indai akwai gurin kwana da abinci, kuma kwalliya za ta biya kuΙin sabulu, hakan ba damuwarta ba ne ba.
A fili ta ce "Babu damuwa, hakan ma na gode sosai da sosai, Allah ya saka da mafificin Alkhairi".
"Amin, a hakan ma gaskiya kina da sa'a sosai da sosai, sai da muka kawo musu mata uku, da Ζyar suka Ιauki Ιaya, wai duk ba su yi musu ba, wasu kuma sai an zo yi musu gwaji sai su faΙi. Amma ke ya ce ba zai yi miki ma gwaji ba, kawai an Ιauke ki aikin.
Abin da zan gaya miki kawai shi ne ki kula, ki kula da kanki sosai da sosai, banda Ζazanta banda son jiki.
Sannan kar ki ga kin tsallake wannan matakin, ya Ιauke ki aiki a haka cikin sauΖi, ki zata miΖe Ζafa za ki yi, mace ce mai gurin nan, kuskure kaΙan za ki ta ci mutuncinki ta kore ki. Su kan su ma'aikatan kwantar da kai suke yi, su na yi mata biyayya, duk wata tijara da bala'inta kawai ki toshe kunnenki ki yi haΖuri." Nana ta yi shiru, sai da Hansatu ta gama gaba Ιaya sannan ta numfasa ta ce "To Ubangiji Allah ya iya mana"
Hansatu ta amsa da "Yauwwa Amin"
Hakanan Nana ta ji a jikinta, ba za ta Ιauki wulaΖanci da cin zarafi ba, duk da kuwa abin da take son cimma. Ko Nene da ake kambama faΙanta da masifarta, ba ta cin mutunci, kuma duk abin da za ta yi faΙa a kai, to a kan gaskiya ne. Amm yanayin yadda Hansatu take yi mata bayanin mai gurin nan, a kaikaice dai ba ta san darajar mutane ba.
Ζakin da Nana take, ita da wasu Zabarmawa ne guda biyu. Ta yi alwala ta yi sallar Azahar.
Ta daΙe a kan abin salla, tana gaya wa Allah, cikin magiya a kan ya sanya ta samu abin da ta fito nema, ya kuma raba ta da duk wani sharri da abin Ζi.
Bayan ta idar, Ιaya daga cikin 'yan Ιakin, ta ce mata ta zo su je ta zagaya da ita.
Can Ιangaren da ake girke-girken ta kai Nana, suka zagaya daga nan ta kaita cikin gurin da ake sayar da abincin. Nana ta yi mamakin girman gurin, da yadda gurin Abincin yake da tarin kwastomomi. Sai dai da gani ka san na manya ne, dan duk waΙanda suke zuwa gurin cin abinci akwai alamun abin hannu a tattare da su.
*****
Ζangaren su Shukura cikin jikinta ya tsufa sosai, sai dai a wannan karon ta dage fafur ta Ζi yin awo a Asibitin su Doctor Sharif.
Gefe Sagir ya jewa mahaifiyarsa, da maganar son dawo da Yusra, amma ta ce ba ta lamunta ba, ba ta buΖatar ya sake rayuwa da Yusra, gara yaje ya auro wata can daban, amma ba Yusra ba.
Gaba Ιaya ya shiga damuwa, saboda mugun sabo da shaΖuwar da ya kuma yi da Yusra.
Ita ma Hajiya Halima tun da ta samu labarin, Sagir ne tsohon mijin Yusra yake zuwa gurinta, ta din ga bala'i ta ce ko shi ne autan maza, Yusra ba za ta koma hannunsa ba, balle a sake ci mata mutunci a sako ta. Ga shi daga shi har ita su na son junansu. Dan haka ya yanke shawarar tafiya gurin Ζanin mahaifinsa ya yi masa magana.
Shi kuma ya kira Hajiya Halima ya din ga yi mata faΙan dan me za ta hana shi mayar da matarsa alhalin sulhu alkhairi ne, wancan karon da auren ya mutu ma, gutsuri tsomarsu ce ta kashe Auren.
Mussaman ta kira Sagir gida, ds ya je ya same ta, ta dirarar masa da bala'i.
"Wato Ζarata ka je ka kai wa Ζanin ubanka saboda mace ko Sagir?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a Hajiya ba Ζararki na kai ba"
"Rufen baki ko na make ka, ba Ζarata ka kai ba ya kira ni yana faΙa? Tun da abin da ka zaΙa kenan, ka je ka yi duk abin da ka ga dama"
Kalaman na Hajiya, tamkar Ιsure shi ne da jijiyoyin jikinsa, gaba Ιaya ya rasa abin da yake yi masa daΙi ba ya son ya yi abin da daga baya zai zo yana dana sani, saboda rashin amincewar Hajiyarsa.
****
Daren yau sam Nana ba ta samu isasshen bacci ba, da yake sai washegari aka ce za ta fara aikin, ba ta yi aikin komai ba ranar.
Raba dare ta yi tana nafilfili addu'oi, saboda a jikinta tana jin wani abu game da gurin, wanda ta kasa tantance ko mene ne.
Washegari da safe, suka shirya ita da 'yan Ιakinsu, suka tafi gurin aikin Abincin.
Kayan girki ne ga su nan a zube, kamar abin banza, yanayin yadda aka jibge kayan a gurin, Nana ta sha jinin jikinta, ta san aiki ne tuΖuru za a yi shi gurin.
Aka ba su jadawalin abinccicikan da za a girka a ranar, Nana ta san wasu, wasu kuma ba ta san su ba.
Su na nan tsaye shugabar Ιangaren na Ζara yi wa Nana bayani, da gurΙatacciyar hausarta, sai ga mutumin jiya shigo.
Gaba Ιaya suka wani ruΙe, masu gyara tsayuwa na yi, masu kama aiki suna yi, Nana dai ta Ζame a gurin da take. Ba yabo ba fallasa ya din ga amsa gaisuwar da ake yi masa, sai da ya zo kan Nana ya saki murmushi ya ce "BaΖuwarmu, ya ki ka ga gurin namu, ba dai wata matsala ko?"
Nana ta girgiza kai ta ce "Babu matsala"
Ya ce "Yauwwa, ki saki jiki ki yi aikinki da mu, kamar kina Nigeria, duk abin da ba ki gane ba, ga shugabar sashin nan, idan kuma ba haka ba ni ki zo ki same ni ki yi mini magana"
Ta jinjina kai ta ce "To in sha Allah, na gode sosai da sosai"
Ya kalli matar ya ce "Dan Allah kar a ce za a sakar mata aiki lokaci Ιaya, a koya mata abin da ta sani ba a hankali, kafin a sakar mata aiki"
Matar ta risuna ta ce "In sha Allah, amma za a yi mata gwajin ne ita ma?"
"Kin ji na ambaci hakan ne, a maganata?"
Ta girgiza kai ta ce "Tuba nake"
Ya ce "'Yar Nigeria, a yi aiki lafiya"
"Na gode sosai" Nana ta yi maganar cikin girmamawa. Ya wuce ya fita. Bayan ya fita suka juya yare, suka Ιan yi maganganu, sai dai duk da Nana ba ta jin yaren nasu, ta san gulmarta suke yi. Suna aiki amma gaba Ιaya hankalin Nana ba a kan aikin yake ba, yana kan halin da Sabir yake ciki. Tana ta tunani yaya yake? Yana rigima ko kuwa bai damu ba ya kwantar hankalinsa, haka ta yi ta wasi-wasi a zuciyarta.
*****
Hajiya Amina ce ta yi shirin tafiya Umara, ta tsaya a Egypt za ta kwana biyu, ta tsaya a Ιan binciki lafiyarta. Sai dai ta din ga ji a ranta, yakamata a Ζara bincika mata matsalarta ta rashin haihuwa, mussaman da take tuna maganganun Nana. Sai dai gefe guda tana tuna yadda Alhaji Zailani yake gargaΙinta a kan shi ya fauwwala wa Allah, bai damu lallai sai ta haihu ba, tun da an nemi magani ba a dace ba.
Sai dai a wannan karon, ta sake jin tana son jarraba da bibiyar lafiyarta, da ganin likita, ko za a dace, tun da ba ta daina al'ada ba ma.
Da harshen turanci suka tattauna da Likitan, ta yi masa bayani, ya rubuta mata gwaje-gwaje ya ce ta je ta yi, ciki har da hoto.
Kasancewar komai na su ba kamar na Ζasarmu ba, cikin ΖanΖanin lokaci aka yi duk gwaje-gwajen, aka tura wa Likitan sakamakon.
Bayan ta koma gurin Likitan ya duba na'ura mai ΖwaΖwalwarsa, ya kalli Hajiya Halima ya ce mata "Sakamakon hoton da aka yi mata, ya nuna babu mahaifa a jikinta gaba Ιaya" wata irin Ζara cikinta yayi, zuciyarta ta buga a jejjere da Ζarfin gaske, sai ta hau kame-kame tana tunanin, ko kunnuwanta ba su ji daidai ba? Ko kuma turancin nata ne ya Ζwace.
Cikin rawar murya ta ce "Ka tabattar da abin da ka gaya mini, ko kuma nice ban fahimta ba?"
Ya ce "Na tabattar, shi ne sakamakon gwajin da aka turo mini, amma idan ba ki yadda da sakamakon ba, kina iya zuwa wani Asibitin a sake duba ki!.
Yammm ta ji kanta yana yi, ta daina gane komai, hankalinta ya rarrabu kashi-kashi, tana son yi wa likitan tarin tambayoyi amma kanta ya kulle.
Shin da gaske ana iya samun mace babu mahaifa, ko kuma wani abin ne daban? Ya aka yi duk tsawon lokacin da ta Ιauka tana bulayin neman haihuwa ba a taΙa gaya mata ba ta da mahaifa ba sai yanzu?.
Gaba Ιaya Hajiya Amina, ta rasa kalmomin da za ta tattaro ta sake furta wani abu. Jikinta rawa kawai yake yi, wani irin gumi yana tsatstsafowa ta kowace kafa ta gashin jikinta.
Likitan ya ci gaba da yi mata bayani, amma ta kasa fahimta.
Ba ta san ma da ya aka yi ta bar Asibitin ba, ta koma masaukinta saboda tsabar Ιimuwa. Ta kuma rasa wa za ta kira ta sanarwa wannan maganar.
Gaba Ιaya kanta ya juye, dan ba ta ma iya tuna yadda su ka ΖarΖare da Likitan ba.
Tana so ta zubar da hawaye, ta ji sanyi a ranta, amma abu ya gagara idanunta suka bushe zuciyarta ta yi nauyi. Babbar tambayarta ita ce, dama ana iya samun macen da ba ta da mahaifa? Ko kuwa ta ta ce ta yi Ιatan dabo?. Tambayar da ta rasa wa za ta yi wa, balle a ba ta amsa.
*****
Nana kuwa gurin nan aiki ake yi tamkar babu gobe, duk da ba ta da son jiki, amma aikin yana da yawa ga babu isasshen hutu, sai aikin Ιorawa da saukewa.
Ga shi ta kasa sakin jiki da ma'aikatan gurin, saboda yadda suke tsangwamarta, da nuna mata Ζabilanci, saboda ita ba 'yar Ζasar su ba ce ba. Sam ba sa gaban Nana, duk da tana Ιan saka ido ta ga, ko akwai wata mai hankali da za ta ji ta yarda da ita, a kaikaice ta Ιan fara ΖwanΖwasa cigiyar Sayyid. Sai dai gaba Ιaya ba su yi mata ba ma'aikatan gurin, gaba Ιaya ba ta ji ta aminta da ko mutum Ιaya daga cikin su ba.
Kullum da safe Al hussain, mutumin da ya Ιauke ta aiki, sai ya zagaya su ya ga yadda suke gudanar da aikin safe da yamma.
Da ya zo ma'aikatan suke nutsuwa, kowa ce ta kame kanta, marasa kamun kai kuma su fara Ιan karairaya. Shi kuma ya tsuke fuska yana basarwa. Sai dai da ya ga Nana sai ya saki fuska, ko ba ta kula shi ba, shi sai ya yi mata magana.
"'yar Nigeria ya alΖawarinmu ne?"
Nana ta Ιan saki fuska ta ce "Wanne?"
"Au har kin manta?"
Ta yi murmushi ta ce "Duk lokacin da ka shirya, sai mu fara"
Ya ce "Kin san akwai wani abokina, sonake kafin na haΙu da shi, ko gaisuwa na iya da turanci, saboda ya iya turanci ni ban iya ba, ya juya yare ya yi ta magana ba na gane me yake cewa, to kin ga yakamata na ba shi mamaki nima"
Nana ta ce "Gaskiya ne, shi ma Buzu ne kamar ka?"
Al Hussain ya ce "Ya aka yi ki ka san ni Buzu ne?"
"Ga rawani nan ka na yi" ya yi dariya ya ce "Kash, to shikenan tun da kin gane, shi ma buzu ne, mun kwana biyu ma bamu haΙu ba, ban je Agadez ba"
"Duk Buzaye a Agadez ku ke?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a, sai dai mun fi yawa a can, ko kina son zuwa ne? Mu na da wani gurin Abincin ma a can, babban wannan sai a mayar da ke can" Nana ta girgiza kai ta ce "A'a tamabaya dai kawai na yi"
Ya jinjina kan ya ce "To yaya aikin?"
"Alhamdillah"
"To ma sha Allah, Allah ya taimaka"
Tun da suka fara hirar nan, Nana ta lura da irin kallon da ake yi mata, saboda ya tsaya sun yi hira. Sai dai ita ba kallon ne ya dame ta ba, a jikinta take jin sam ba ta kyauta ba, tsayawa da ta yi tana magana da Al Hussain har take yi masa murmushi ba, saboda ta san da Sayyid yana gurin, ko da makamancin wasa ba za ta taΙa aikata hakan ba, saboda yadda yake tsananin kishinta.
A hankali ta ce "Ka yi haΖuri Sayyid, babu yadda na iya ne, duk a ΖoΖarina na son zuwa gare ka ne, ka yi mini afuwa" ta furta a hankali kamar mai raΙa.
"Nana wai a ina ki ka san Al Hussain ne?"
Nana ta Ιaga kai ta kalli Shugabar gurin nasu, da take yi mata tamabaya cike da tuhuma. Kamar Nana ba za ta yi magana ba, sai kuma ta ce "Waye hakan?"
Matar ta ce "Kamar yaya?"
Nana ta ce "Wanda ki ke tambayata"
Gaba Ιaya suka kalli Nana, jin yadda take bawa Adama, shugabar Ιakin girki. Ita kuwa Nana ko a jikinta da irin amsar da ta bawa Adaman.
Cike da takaici Adama ta ce"Mutumin da ya fita yanzu"
Nana ta ce "Au sunansa kenan dama? A nan Nijar na san shi, meyafaru?" Ta yi maganar tana tsare Adama da ido, tana jiran abin da za ta sake cewa.
Sai dai ta yi shiru ba ta kuma magana ba, su kuma suka hau mamakin irin amsar da Nana ta bata, kuma ba ta iya ce mata komai ba.
Gaba Ιaya Nana hankalinta ya koma kan sauran kwanaki nawa ta koma gida, duk da kullum sai ta yi waya da Nene. Amma ta ga kamar kwanakin ba sa matsawa sam.
****
Hajiya Amina revers ta yi, ta dawo gida Nigeria, saboda kiΙima da tashin hankali da take ciki, ta rasa wanda za ta fara tunkara da maganar. Ta so samun mijin Alhaji Zailani a waya, ta fara yi masa bayani, amma ba ta same shi a waya ba. Ta koma gida a kiΙime, amma ta tarar da saΖon ya yi balaguro zuwa Abuja.
Jikinta na rawa ta kira Doctor Sharif, ya Ιaga yana faΙin "Hajjaju barka da yamma"
"Sharif abu zan tambaye ka dan Allah"
Gabansa ya faΙi, saboda yadda ya ji muryarta cike da tsoro da kuma damuwa.
"Hajiya lafiya dai?"
"Lafiya Ζalau, tambaya zan yi maka dan Allah"
"To Allah ya sa na sani"
"Dan Allah Sharif ana iya samun matar da ba ta da mahaifa dama?"
Ya yi shiru sanann ya ce "Me yasa ki ka tamabaya?"
"Ka bani amsa kawai"
Nutsuwa ya yi ya tattara hankalinsa, kar ya ba ta amsar da zai fallasa wani Ιoyayyen abin da bai kamata ba.
Duk da bai san dalilin da ya sanya ta yi tambayar ba.
"Eh ana samu Hajiya, sosai ana samu wani abu ne ya faru?"
"A'a shikenan na gode sosai" ta kashe wayar, sai a lokacin hawaye ya fara gangaro mata, da ta Ζara tabattar da har abada ba za ta samu haihuwa ba.
"Amina butulci za ki yi wa Ubangiji? Sauran ni'imomin da ya yi miki fa?" Wata zuciyar ta tunatar da ita. Sai dai kasancewarta biladama mai Ιauke da zuciya irin ta Ιan adam, sai ta kasa jurewa ta bi nasihar da zuciyarta take yi mata, ta fashe da matsanancin kuka mai taΙa zuciya. Duk da ta daΙe tana yin sa a Ιoye, amma ba ta yanke tsammani ba ta ci gaba da addu'a, amma a wannan karon da ta san ba ta da rabo baki Ιaya, sai ta sare.
*****
Shirye-shiryen bikin Abba yayi nisa, dan bai fi saura sati biyu bikin ba, ta Ζara saka masa ido da shi da Jamila. Jamila sam ba ta nuna mata cewar ta san abin da take yi ba, ta rabu da ita.
Ya kasance taronsu na Ζungiya lokaci yayi, dan haka suka shirya tafiya a wannan karon har da maman Khairat.
Da suka je masaukinsu ma a garin Abuja, Jamila ba ta shiga sabgarsu ba, harkokinta kawai take yi.
Maman Khairat ta ce "Wai Jamsy ya ne? Duk kin zama so silenta, babu wannan rawar kan"
Jamila ta Ιan taΙe baki kawai.
Hajiya Sa'a ta ce "Jamila haushina take ji, ban san me na yi mata ba"
Jamila ta ce "Mummy kenan"
"A'a ba wani Mummy kenan, magana za ki yi"
"To Mummy, ki na ta daughter daughter, amma Ζarara ki ka nuna ba kya Ζaunata, daga ganina tare da Abba, ki ka haΙe rai ki ka yi kicin-kicin, ki ka tashi nema masa aure. Abin ya bani mamaki"
Hajiya Sa'a suka haΙa idi da maman Khairat, ta ce "Haba daughter, ya za a yi na Ζi ki da Abba, ke me ma za ki yi da aure? Na daΙe ina gaya miki za ki iya rayuwa ki da kuΙinki, ba tare da kin yi aure ba. Za ki huta ki yi duk abin da ki ke so."
"Amma Abba ma ai yana da kuΙi, shi me yasa ba ki ce ya yi rayuwa da kuΙi kawai ba, ki ke shirin yi masa aure? Duk wata Ζasaita, kuΙi da wadatar mace, inuwar aure ginshiΖi ce kuma sutura ce ga 'ya mace.
Amma na san saboda ni rayuwata ta gama lalacewa, ke kuma kina son Ιan ki ya yi kyakykywar rayuwa, ki ka yi ΖoΖarin raba ni da shi. Sai dai tun ran gini tun ran zane. Ban ji haushinki ba ko kaΙan Mummy, abin da ki ka yi shi kowacce uwa za ta yi. Ina yi mana fatan dacewa da Ζarshe mai kyau" Tana gama maganar ta yinΖura ta tashi, ta bar Ιakin.
Safiyya ta ce "Kin ga Hajiya, ki bi yarinyar nan a hankali, alamu sun nuna hankali ya fara shigarta, ta san ciwon kanta, kuma abin da aka yi mata duk da ta samu kuΙi ya yi mata ciwo. Kar ki bi ta da Ζarfin tsiya ta yi tawaye"
Hajiya Sa'a ta numfasa ta ce "Na ga alama, amma ba zan taΙa rainon Ιan kwiykwiyo, ya girma ya fara yi mini haushi ba. Ina son samun jinin 'yar uwatta na riga Zailani samu ko ta halin ΖaΖa, daga nan zan yi maganinta"
Safiyya ta jinjina kai.
Doctor Sharif ya din ga kiran Alhaji Zailani, ya sanar da shi kiran da Hajiya Amina ta yi masa, amma ya kasa samunsa a waya, saboda su shinga taron manyan Ζungiya da suke yi, wanda sai sun kwana uku suke fitowa, sannan ayi babban taro na kowa da kowa da ke cikin Ζungiya.
Ganin kiran Hajiya Amina ya bawa Shukura mamaki, dan idan tana Saudiyya sai dai su yi video call.
Ta Ιaga ta ce "Mami, yaya ba ki samu tafiyar ba ne?"
"Shukura za ki iya zuwa gida, ban takura miki ba"
Cikin tashin hankali Shukura ta ce "Lafiya kuwa, ya na ji muryarki a haka?"
"Dan Allah idan da hali ki zo gida"
"Shikenan, gani nan zan kira baban Haidar na gaya masa, gani nan Allah ya sa lafiya"
Hankali a tashe, ga tsohon ciki haka ta Ιauki mota ta tafi gida. Tana matuΖar jin Hajiya Amina a zuciyarta, saboda bayan rasuwar mahaifiyarsu, tun su na Ζanana babu yadda ba ta so cuzguna mata ba, amma Hajiya Amina babu ruwanta. Ba ta damu da abin da mutane za su ce ba, ta riΖe ta da halin ta, sai da ta Ζara wayo sannan ta gane ba ta da wata uwa da ta wuce ta. Shi yasa take matuΖar jin damuwarta a ranta tamkar uwar da ta haife ta.
A bedroom ta tarar da ita, idanunta jawur sun kumbura. Cikin tashin hankali ta Ζarasa ta zauna ta ce "Lafiya kuwa? Ko ba ki da lafiya ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Yi haΖuri Shukura, na taso ki ga tsohon ciki, na rasa da wanda zan yi zancen nan na ji daΙi a raina."
Cikin damuwa ta ce "To meyafaru?"
"Shukura wai ba ni da mahaifa"
Shukura ta yi saroro, ta ce "Kamar yaya?"
Ta share hawayenta ta gaya mata duk abin da ya faru. A Ζarshe ta ce "Na kira Doctor Sharif ya ce mini eh ana iya samun mata da basu da mahaifa, amma na yi mamakin yadda duk yawon Asibiti da na yi a nan, ba a taΙa gaya mini ba"
Shukura ta Ιan yi shiru sannan ta ce "Anya kuwa? Kin san fa kin daΙe da daina zuwa Asibiti a kan matsalar nan, Daddy ba ya so. Sannan ku ne ku ke yarda da maganar Sharif Ιin nan, ki rabu da shi mu je wani Asibitin daban, a sake duba ki a tabattar da abin da yake faruwa. Duk da ba na tunanin za a samu matsala a abin da can Egypt Ιin suka gaya miki."
Ta girgiza kai ta ce "A'a Shukura, babu inda zan sake zuwa, na yi maganar ne da ke dama na samu sanyi a raina, na kira babanki ba ta shiga"
Shukura ta yi shiru, kawai dai ta ji ita abin kamar akwai lauje cikin naΙi.
*****
Nana ta shafe sati na biyu, tana aiki a wannan gidan Abinci. Sai dai ita kanta tana mamakin irin yadda Al Hussain yake kyautata mata. Hakan ya sanya gaba Ιaya suka Ζara saka mata ido suka tsangwame ta, mussaman Adama da 'yar ta Raliya, da alamu suka nuna Al Hussain take so.
Idan aiki ya Ιan yi sauΖi, Nana kan fita ta shiga cikin gurin cin abincin, ta zagaya ko za ta ga ko mai da Sayyid ne, amma ba ta ga kowa ba. Sai dai gabanta ya kan faΙi a duk lokacin da ta ga masu rawani sun zo gurin cin abinci, sai ta ga kamar za ta gan shi a cikin su.
Ta gama zagayenta, ta koma cikin gurin girkin, Adama ta kalle ta ta tsuke fuska ta ce "Daga ina ki ke, ana tsaka da aiki?"
"Na Ιan je wani uzuri ne"
"Na me, kuma a ina?"
Nana ta ce "Uzuri dai na Ιan Adam, na yau da gobe, ai rayuwa na buΖatar sirri ko?"
"Ni fa na fuskanci take-takenki na rashin kunya baki da kunya ko kaΙan, saboda kin ga Al Hussain yana tsaya miki, wallahi idan ba ki yi wasa ba sai na kawo Ζarshen aikinki a nan, sai na saka an kore ki daga gurin nan"
Kallonta kawai Nana ta yi ta kawar da kai, ta ci gaba da abin da take yi. Har ta gama bala'inta, 'yan korenta suka taya ta, Nana ba ta tanka mata ba.
Washegari da sassafe, Nana ta baro Ιakinsu, ta tafi kitchen ta fara aikinta, duk da wasu lokutan suna yi mata mugunta, su din ga sakar mata aiki.
"Ina sauran ma'aikatan gurin nan?" Ta ji wata murya ta daki kunnenta, da ba ta san mai ita ba.
Ta Ιaga kai ta kalli matashiyar matar, doguwa fara jawur, mai kama da Al Hussain.
Kawai ta mayar da kanta ta ci gaba da aikin gabanta.
"Ke ba kya ji ina magana ne?"
Nana ta Ιago kai ta ce "Su na zuwa"
Nana na rufe bakinta, sai ga Adama ta shigo, ita da sauran ma'aikatan.
Wata irin rikicewa suka yi, suka hau tsuma su na gaida matar.
"Wace ce wannan? Da ba ta da mutunci ba ta da Ιa'a, nake magana tana bani amsa a wulaΖance" ta yi maganar tana nuna Nana.
Nana a ranta ta hau mamakin wane wulaΖancin ta yi mata, ita da ta zo guri babu sallama babu gabatar da kai, koma wace ce ba zai wuce ita ce mai gurin da ake faΙa ba. Nana a ranta ta ce "Koma wace ce ke, Allah ya fi ki" sai dai ba ta sake Ιaga kai ta kalle su ba, ta ci gaba da yankan kabejin hannunta.
Ayshercool
08081012143.
69
Adama ta risunar da kai ta ce "Ki yi haΖuri ranki ya daΙe, mu ma haka muke ta fama da ita mu ma, amma ki yi haΖuri baΖuwa ce"
"BaΖuwa kuma ba ta iya magana ba, baΖuwa daga ina?"
Raliya ta ce "'yar Nigeria ce"
" 'yar Nigeria, waye ya saka Al-Husssain Ιaukar wata 'yar Nigeria, dama haka 'yan Nigerian ku ke, ba ku da mutunci ba ku san me ku ke yi ba?" Maganganun matar sun soki zuciyar Nana, tamkar ta mayar mata da martani ta ce "Ku a Nijar ba ku san muhimmancin sallama, da girmama na Ζasa da kai ba" Sai dai ta yi shiru ta ci gaba da aikin gabanta. Haka ya Ζara tunzura matar ta fita fuuuu tana bala'i tana sai Nana ta bar aiki a gurin.
Matar na barin gurin Raliya ta kalli Nana ta ce "Allah ya Ζara, idan kina cin Ζasa ai ki kiyayi ta shuri, yau kin taΙo abin da ya fi Ζarfinki, kin yi a bakin aikinki"
Babban abin da ya Ιaure musu kai, bai wuce yadda Nana ta Ζara yin burus, ta ci gaba da aikin gabanta.
Adama ta ce "Anya yarinyar nan ba mahaukaciya ba ce kuwa?"
Ζayar ta ce "Ko ta mayar da mu mahaukata ba. Amma idan haukan take ji, ai Hasna babarta ce"
Wata matashiyar mata ce ta shigo, sanye da uniform a jikinta. Ta yi sallama suka amsa.
Ta ce "Ina Nana?"
Nana ta ce "Ga ni"
"Ki zo ana neman ki a ofishin Al Hussain"
Ta ce "To gani nan" ta yi maganar tana ajiye wuΖar hannunta, ta wanke hannunta ta bi bayan matar.
Sai dai har matar ta yi gaba ta bar Nana, da Ζyar Nana take iya Ιaga Ζafafuwanta, saboda matsanancin nauyin da ta ji sun yi mata, ga sanyi da ya fara ratsa ta ta ko ina.
"Ya hayyu ya Ζayyum. Allah ka taimake ni, Ζaisar kar ka yi mini haka mana" Ta furta a hankali zuciyarta na bugawa.
Ta saka hannu ta tura Ζofar ofishin. A tsaye ta tarar da matar Ιazu, tana zazzaga masifa, Al Hussain yana zaune yana kallon ta.
Sai dai Nana ta yi turus, ganin Ζaisar a zaune a jikin na'urar sanyaya guri, da ke cikin Ιakin.
"Nana Ζaraso mana" muryarsa ta dawo da Nana hayyacinta. A hankali ta Ζarasa ya ce ta zauna a kan kujera.
"Al Hussain ka na da lafiya kuwa? Yarinyar ta yi mini rashin mutunci, ka ce ta zauna a kan kujera?"
Ya ce "A'a Hasna, na fa san halinki, kuma a aikin da Nana ta yi da mu na Ιan lokaci, ba ta da matsala sam. Nana meyafaru ne?"
Nana ta buΙe baki za ta yi magana, Hasna ta tari numfashinta ta ci gaba da masifa.
Al-Husssain ya daki tebur ya kalli Hasna, hakan ya sanya ta yin shiru tana harar Nana.
Nana ta ce "Ban san wace ce ba ne, ta yi haΖuri"
Hasna ta daki tebur ta ce "Ka gani ko, garin kwashe-kwashe ka kwaso mara mutunci, to wallahi sai ta bar gurin nan, tun da ba na ubanta ba ne"
Al-Husssain ya ce "Tsakani da Allah, Nana mutuniyar kirki ce mai girmama mutane, ba na tunanin za ta yi miki wani abu na rashin mutunci. Nana ki je ki ci gaba da aikinki" Ta jinjina masa ta kalli Hasna ta ce "Ki yi haΖuri, ban san wace ce ke ba, ba ki gaya mini ba, na zata a cikin abokan aikina ne kaw...
"Ke, na yi miki kama da wadda za ta zama abokiyar aikinki?. Za ta ci gaba da magana Nana ta tsare ta da ido, sai ta rikice gaba Ιaya ta rasa abin da za ta ce.
Al-Husssain ya ce "Maza jeki ki ci gaba da aikinki"
Nana ta miΖe tsaye, kawai ta ji jiri ya Ιebe ta, ta yi saurin riΖe kujerar. Al Hussain ya miΖe da sauri ya ce "Ba ki da lafiya ne?"
A sanyaye ta ce "A'a jiri nake ji ne"
"Idan ba za ki iya aikin ba, ki je ki kwanta ki samu hutu"
Nana ta ce "A'a zan iya ma, in sha Allah"
Ta lallaΙa ta fita daga ofishin, sai dai tana jiyo Al Hussain yana ce mata, ki yi a hankali kin san mu na da baΖi, idan kuma ki ka ci gaba da hayayaga mutuncinki ne zai zube, wannan halin naki babu abin da zai janyo miki sai raini.
Gaba Nana ta yi, tana bin bango, sai dai sosai ta ji Duniyar na juya mata.
Ta lallaΙa ta koma Ιakinsu da Ζyar, sai dai a Ιakin ta din ga jin wani irin sauti mara daΙi, ga sanyi tana ji amma numfashinta tamkar zai Ιauke.
Ta buΙe tagogin Ιakin, kasancewar saman bene ne, ta hango wasu irin manyan motoci a harabar gurin. NaΙin kan mutanen ya sanya ta tabattar da Buzaye ne, sai dai suna sanye cikin kaya na alfarma.
Nana ta zuba musu ido, tana son ganin fuskar Ιaya daga cikin mutanen da aka buΙewa wata danΖareriyar mota. Wanda haka kurum ta din ga jin kamar akwai wani abu mai matuΖar muhimmanci da yakamata ta sani game da mutumin, da ba ta san ko wane ne ba, duk da yanayin Ζirar jikinsa ba irin na Sayyid ba ne. Wata irin Ζara ta din ga ji cika mata kunne. Ta dafe kunnenta, ta durΖusa hawaye na bin fuskarta. Yanayin gaba Ιaya mara daΙi ne, rashin daΙin da ba za ta iya misaltawa ba sam.
Dariyar Giyaz ta din ga ji sama-sama, a hankali dariyar ta cika ilahirin Ιakin.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil, wa hifzan min kulli shaiΙanin marid" shi ne abin da ta furta a hankali.
"Asmy" ta ji muryarsa cikin karkarwa, yayin da Ζarar iskar sahara take kaΙawa.
A galabaice ta ce "Sayyid"
"Ma vie"
Ta sake cewa "Na'am Sayyid, na fara sarewa, ina jin kamar ba zan yi nasara ba, ba zan ganka ba, na fara karaya." Ta yi maganar tana kuka.
"A'a kar ki karaya, kar ki yi mini haka, ina buΖatar ki dan Allah"
A hankali take sauke numfashi, idanunta a lumshe Ζirjinta ya yi nauyi kamar numfasihinta zai Ιauke.
*****
Daren da Jamila ba za ta taΙa mantawa da shi ba, ya sake maimaita kansa.
Daren da ta zama Ιaya daga cikin mambobin Ζungiyar asiri, daren da aka lalata rayuwarta a matsayin maraba da shiga Ζungiyar.
Kamar yadda yake Ιabi'ar Ζungiyar, suna sanye da jajayen kaya. Sai dai a wannan karon Jamila ta gusa daga matakin farko na shiga Ζungiyar.
Babban abin da ya bawa Jamila mamaki, bai wuce yadda aka fesa wani abu a gurin, sai ganinsu ta yi a dokar daji ba.
Wani irin daji mai ban tsoro, mai Ιauke da manyan dogwayen bishiyu, ga shi baΖiΖirin Ιauke da duhu.
A wani fili suke a gaban wani dutse, babu tsammanni ta ga wuta takama a tsakiya tana ci bal-bal.
Daga bisani dajin ya din ga amsa kuwwa da wata irin Ζara mara daΙin ji.
Aka din ga karanto abubuwan da Jamila ba ta iya fahimta.
Aka jefowa kowa Ζyalle da abin da zai sadaukar na shekara, kafin zagayowar wani taron.
Jamila ta kalli Ζyallen da yake gabanta, jawur da shi.
Hannunta na rawa ta Ιauka ta fara ΖoΖarin warwarewa. Da hasken da wutar ta bayar Jamila ta karanta abin da yake rubuce a jiki, da aka rubuta da jini.
Ta din ga kallon Ζyallen tare da rubutun. Ta duΖunΖune Ζyallen ta jefa a wuta, kamar yadda kowa ya yi.
Sai dai jikinta a sanyaye, gabanta kuma ya tsananta faΙuwa. A wannan karon har da wasu irin dogayen mutane, da ta kasa gane mutanen ne ko kuwa wani jinsin ne, saboda yadda suka shallake kowa tsawo a gurin kuma suna sanye da baΖaΖen kaya har kansu a rufe yake.
A wannan karon abubuwan da Jamila ta gani sai da ta tsorata, ashe wancan karon babu abin da ta gani. Ζungiyar mataki-mataki ce.
Su matakin su Alhaji Zailani ma, kowannensu yana da aljanin da kusan bauta masa yake yi. Sun ba wa aljanun jini babu adadi, na makusantansu, da wanda ma ba makusnatansu ba. Aljanun na iya shiga kowane irin hatsari, dan ganin buΖatar irin su ta biya komai wahalarta.
Haka suma su Alhaji Zailani, duk abin da Aljanun suka buΖata suna yi musu, domin Ιorewar biyan buΖatunsu. Alhaji Zailani ya kan karΙi saΖonnin nasa Aljanin ta hannun Malam Gambo, wanda su ne manyan malaman da suke gudanar da sihiri a cikin Ζungiyar bayan Ιangaren neman Duniya da samun kuΙi da suke yi.
Su kan kira aljanu daban-daban da sanya su aikace-aikace na sihiri.
Aljanin Alhaji Zailani ya buΖaci aiki da jinin Nana, da kuma mu'amala da mai irin tauraronta dan biyan buΖatun Alhaji Zailani, sai dai abu ya gagara kamar yadda dariya ta gagari kare. Hakan ya sanya a wannan karon ma ya sake buΖatar jinin Alhaji Zailani, wanda idan ba Shukura ko Yusuf ba, sai dai abin da Shukura za ta haifa.
Ζangaren Hajiya Sa'a ma hakan ne, bayan sanin fa'idar jinin irin na masu tauraron Nana, da yadda bayan haΙuwarta da Nana karon farko, Aljanin ya yi mata bayanin irin tagomashin da za ta samu, idan ya sha jinin Nana, da kuma bautar da zai yi mata idan ya sha jinin ko kuma ta kawo Nana Ζungiya, ta hanyar na ta bokan na cikin Ζungiyar, kuma bokan ya kwaΙai mata damarmakin da za ta iya samu idan ta mallaki Aljanin kan Nana kamar yadda aka gaya wa Alhaji Zailani ma.
Ita ma a wannan karon, an sake buΖatar jinin makusancinta, wanda ko dai Abba, ko Alhaji Fatuhu ko kuma dai Ιansa Muhsin, su ne shaΖiΖanta.
Jamila a firgice ta farka, a tunaninta ko duk mafarki ne, ta farka da wani irin matsanancin zazzaΙi da ciwon kai, ΖoΖon kanta tamkar zai tarwatse saboda azabar ciwo.
Maman Khairat ta taso tana yi mata sannu. Ta ce "Wai ke Jamila wace irin raguwa ce ne haka? Ai yakamata a ce zuwa yanzu kin riga kin saba fa"
Hajiya Sa'a ta ce "Dole za ta razana dama, yanzu ta shiga mataki na biyu sai a hankali"
Jamila ta Ιan yi shiru tana so ta fuskanci ko a wannan karon ma an yi lalata da ita, amma ba ta ji hakan ba. Sai kanta da yake ta wata irin azaba, ga jikinta tamkar ana Ζona ta saboda zafin zazzaΙi.
*****
Shukura ta je awo, likitan da yake duba ta doctor Sabo, ya na ta Ζara kwantar mata da hankali, saboda a wannan karon ma akwai hawan jini a tattare da ita. Har za ta tashi ta tafi ta ce "Doctor dan Allah wata tambaya ce da ni"
Ya ce "To Allah ya sanya na sani"
"Wai dan Allah ana iya samun mace wadda ba ta da mahaifa?"
Ya Ιan yi shiru sannan ya ce "Eh ana samu, amma a mafi ΖanΖantar lokuta sosai, saboda a cikin mata dubu biyar da Ζyar ake samun mace guda Ιaya da irin wannan case Ιin"
Ta jinjina kai cike da gamsuwa ta ce "To Doctor kai ka taΙa haΙuwa da irin waΙanda ba su da mahaifar?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a. Amma me yasa ki ke tambaya?"
"Mamana ce ba ta taΙa haihuwa ba, da tana zuwa ganin Likita amma ta daina, sai last week ta je Egypt, aka duba ta ska ce ba ta da mahaifa"
Ya waro ido ya ce "Ba ta da mahaifa, kuma ta taΙa haihuwa?"
"A'a ba ta taΙa haihuwa ba, step mum Ιina ce"
Ya ce "Ikon Allah, kuma ba a taΙa yi mata aiki ba ko makamancin haka?"
Ta yi shiru ta girgiza kai ta ce "Bana tunanin haka, amma bari na kira maka ita"
Shukura ta kira lambar Hajiya Amina ta Ιaga.
Suka gaisa ta ce "Mami, ina Asibiti ne na yi wa likitan da nake awo a hannunsa magana, ya ce na haΙa ku"
"Shukura, ba na ce a bar maganar nan ba kawai?"
"A'a ki yi haΖuri, na riga na yi magana da shi ai" ta ba wa Doctor Sabo waya. Suka gaisa ya ce "Hajiya garin yaya aka ce ba ki da mahaifa ne?"
"Wallahi nima ban sani ba, abin da dai suka ce mini kenan"
"A Nigeria an taΙa duba ki a baya an gaya miki hakan?"
Ta ce "A'a"
"An taΙa yi miki tiyata?"
"A'a Likita ba a taΙa yi mini ba"
Doctor Sabo ya ce "Ikon Allah, kuma yaushe rabon ki da Al'ada?"
Ta ce "Ai dama ba regular nake yi ba, wasu lokutan sai na yi wata shida ma ban yi ba, idan ya zo kuma ba ya fin kwana biyu wataran ma wuni Ιaya ne shikenan"
"To dama tun kina budurwa haka ki ke yi?"
"A'a gaskiya, da lafiya Ζalau nake al'ada daga baya ne ya koma haka".
"Bayan ya koma hakan kin taΙa zuwa an Ζara bincikawa, kuma a baya ba a taΙa gaya miki mene ne ya hana ki haihuwa ba?"
Ta girgiza kai kamar yana ganinta ta ce "Ko a baya komai lafiya Ζalau ake ce mini, daga baya kuma da ya koma haka, mijina ya ce na haΖura da yawon Asibitin nan, dan haka ban sake zuwa a kan issue Ιin haihuwa ba. Amma ina fuskantar matsalolin gynea sai dai akwai likita da nake gaya wa ya rubuta mini magani kawai".
Doctor Sabo ya ce "Idan babu damuwa, akwai buΖatar ki zo Asibiti mu Ζara bincikawa sosai da sosai, wannan serious issue ne"
"Doctor na gode sosai da sosai, amma ba na tunanin zan iya zuwa, na haΖura dama buri ne irin na Ιan Adam amma shekaruna sun ja, na bar wa Allah ikonsa."
"A'a kar ki ce haka baiwar Allah, akwai Abubuwan da farwuarsu daga Allah ne mun sani, wasu kuma akwai sababi. WataΖila akwai wani abu na musamman a tattare da ke da ya dace a bankaΙo. Ina doubting a ce Egypt su bayar da result Ιin da ba shi ba ne ba. Amma dai za mu Ζara bincikawa." Hajiya Amina ta amsa masa da to, ta yi masa godiya amma sam ba ta ji za ta iya zuwa a wani bibiya ba, kamar tana tsoron wani abu.
Doctor Sabo ya ce lallai Shukura ta lallaΙo ta, su zo Asibiti yakamata a yi ΖwΖΖwaran bincike a kan lamarin.
Alhaji Zailani yana kashingiΙe ya kira Doctor Sharif.
Bayan sun gaisa ya ce "Ina cikin uzuri ne kwana biyun nan, shi yasa ban Ιaga wayarka ba, ya ake ciki?"
"Dama zan gaya maka ne, Hajiya ce ta kira ni tana tambayata wai ko ana iya samun mace wadda ba ta da mahaifa, to ban san dai mene ne ba, amma na ce maya eh."
Wata irin zabura Alhaji Zailani ya yi ya ce "Daga nan me ta ce maka?"
"Ba ta ce mini komai ba ta kashe wayar"
"Shikenan na gode" ya kashe wayar ya dafe goshinsa, "Amina kin fiye taurin kai, dama kaza garin tone-tonenta take tono wuΖar yanka kanta!"
Sannu a hankali Nana take bin doguwar barandar, tana hangen masu shigowa da masu fita daga cikin gurin cin abincin. Tun safe motoci suke shiga su na fita.
Sai dai ta jima a tsaye a gurin, ba ta ga wani abu da za ta iya riΖa, ko wani wanda za ta tunkara ta yi wa magana ba. Duk manyan mutane ne na alfarma ba ta tunanin akwai wanda ma zai tsaya saurarta, su kuma ma'aikatan gurin da take sanya ran za ta iya tambaya wani abu, ba zaman lafiya suke yi ba.
Jiki a sanyaye ta juya, ta kama hanyar komawa gurin girke-girken, Al Hassan yana hango ta, ta ofishin sa.
A kan hanyarta ta komawa, suka yi kiciΙis da Hasna. Nana ta Ιan raΙe gefe ta ce mata "Ina kwana"
"Lafiya" ta amsa har za ta wuce Nana, sai ta dawo da baya ta Ζara kallon ta ta ce "Au ashe ke ce fitsararriyar nan ko?"
Nana ta girgiza kai ta ce "A'a rashin fahimta ne, yanzu da na san wacece ce ke ai ga shi na gaishe ki" Ta so ta yi wani abu da za ta yarfa Nana da za ta saka ta ji zafi a ranta, amma sai ta kasa. Gaba Ιaya ma sai ta ga Nanan kalar abin tausayi a yau, kamar ba ta da kuzari ko kaΙan fuskarta Ιauke da damuwa.
"Amm ki kawo mini shayi ofishina, shayin girfa, kar kuma a cika sugar ba na son sugar da yawa"
"To ina ne ofishin"
"Ki tambaya" ta amsawa Nana tana yin gaba abin ta.
Nana ta koma gurin girkin, ta fara ΖoΖarin dafa shayin girfa, saboda babu shi, Adama ta saka ta wani aikin.
Wasu lokutan har rasa yadda za ta yi take yi, sai dai ta kan jure dan kar ta gaza ta sare, dan jikinta yana bata zamanta a gurin nan ka iya sanyawa ta yi nasara.
Sai dai abinka da Ιan Adam, wasu lokutan ta kan bujire.
Ta kammala ta tambayi ofishin Hasna, aka nuna mata ta kai mata shayin har can.
Tana tare da Al Hussain ta tarar da ita, da wasu manyan mutane guda uku a office Ιin. Cikin girmamawa Nana ta gaishe su, cikin gurΙatacciyar hausa suka amsawa Nana.
Hasna ta sake mayar da Nana, wai ta kawowa baΖinsu shayi.
Haka Nana ta koma, ta sake kai musu wani shayin, duk da hakan ba aikinta ba ne ba.
Ta fito daga ofishin, Al Hussain ya biyo ta yana kiran sunanta. Ta tsaya ta waiwayo ta jira ya Ζaraso.
"Nana ko haryanzu jikin ne ba ki warke ba?"
Cikin Ζarfin hali ta girgiza kai ta ce "A'a jiki na warke"
"A'a idan ba ki warke ba, na saka a kai ki Asibiti, sai a baki hutu"
Ta girgiza kai cike da Ζwarin gwiwa ta ce "A'a na ji sauΖi fa, zan ci gaba da aiki in sha Allah, na gode sosai da sosai" Ta juya ta ci gaba da tafiya.
Shi dai haka kurum Nana tana ba shi tausayi, sai dai babu wata dama da ta bari, da za a iya zama da ita a ji matsalar ta, ko za a iya taimaka mata. Ya lura ko a cikin ma'aikatan ba ta da sukuni, ba ta sakin jiki da su. Kuma yanayin ta Ζarara yake bayyanar da damuwa duk da tana da ΖoΖarin dakiya.
*****
Alhaji Zailani ya din ga kiran lambar Hajiya Amina. Gaba Ιaya ya rikice hankalinsa ya yi mummunan tashi, ya rasa abin da yake yi masa daΙi, yana tsoron kar ta aikata wani abin da zai kawo matsala. Ga jirginsa sai washegari zai koma Kano, ga shi yana da manyan uzururrukan da yake son yi a Abuja, da ba zai iya tsallakewa ya bar su ba.
Shukura ta je har gida, ta sake samun Hajiya Amina ta lallaΙa ta a kan ta amince su je gurin Doctor Sabo, amma ta ce babu inda za ta je. Da Ζyar ta amince ta ce ba za ta je a ranar ba sai washegari.
Shukura ta Ιan numfasa ta ce "Mami ba na son yi miki maganar nan ki na cikin damuwa, sai dai nima ba a son raina ba, na rasa abin da yake yi mini daΙi"
Cikin damuwa Hajiya Amina ta ce "Dan Allah ki kwantar da hankalinki, kar wannan cikin ma ya sake samun matsala mene ne?"
Ta numfasa ta ce "Sagir ne fa yake ta ΖoΖarin dawo da tsohuwar matarsa"
Hajiya Amina ta ce "To shi ne ki ka damu haka? Dan Allah ki rabu da shi ya Ζarata, ki lallaΙa ki haihu lafiya kalau, kin ga ga hawan jini ki na fama fa"
"Wallahi Mami zuba masa idon na yi, takaicina bai gaya mini ba, su na ta Ζwarbai da Hajiya, ta ce ba zai dawo da ita, a bakin Ζannensa nake ji".
"To babu ruwanki, su sha'anin dangin mijin nan ba a zaΖalΖale musu, idan ta dawo Ιin ma wataΖila su tattara su haΙe kai, babu ruwan ki ki kula da kan ki, ki sauka lafiya"
Shukura ta jinjina kai ta ce "In sha Allah, sannan dan Allah Mami ke ma ki kwantar da hankalinki, nutsuwarki ita ce ta wa, dan Allah Mami ki kwantar da hankalinki kema"
"Wallahi Shukura Ζarfin addu'a ya sanya mini nutsuwa da tawakalli, yadda ku ke yi mini biyayya da ke da Yusuf ko ni na haife ku, Alhamdillah na san iya abin da za ku yi mini kenan. Kuma na san ko yau na bar Duniya za ku tuna da ni ku yi mini addu'a"
Idon Shukura fal hawaye ta ce "Mami ke uwa ce abar alfahari, har Duniya ta naΙe ke uwa ce a gare mu, kuma muna alfahari da samun ki"
Suka rungume juna da ita da Shukura, Hajiya Amina ta ci gaba da gode wa Allah, tana jin da natan ta haifa wataΖila ma ba lallai su yi mata biyayya haka ba.
Sai bayan tafiyar Shukura, sannan ta shiga Ιaki, ta tarar da kiran wayar Alhaji Zailani rututu.
Yana ganin kiranta ya Ιaga, bai tsaya amsa gaisuwar ta ba, ya hau tambayarta abin da ya hana ta tafiya.
Ta ce "Matsala aka samu, kuma na yi ta kiran ka a waya, ba ka Ιaga wa"
"Matsalar me?"
"Ba komai, idan ka dawo ma yi magana"
Ya ce "Yanzu nake son ki gaya mini koma mene ne, meye dalilinki na kiran Sharif kina tambayarsa ana haifar mace babu mahaifa?"
Ta ce "Amma laifin me na yi haka? Na tsaya a Egypt su duba lafiyata ne, tun ina can nake neman ka, ban same ka ba, sakamakon gwajinsu ne ya tabattar da ba na Ιauke da mahaifa"
"To uban waye ya ce ki je? Ba sai da na ce miki ki bar batun yawon neman haihuwar nan ba, da yake ban isa na saka miki doka ki bi ba, kin raina ni bani da mutunci a idonki?" Duk bayanin da ta so ta yi masa, yaΖi saurararta, ya din ga zazzaga mata bala'i.
Ranta ya Ιaci, ta ga Sharif bai kyauta mata ba, ya za a yi daga tambayarsa abu ya Ιau waya ya kira shi ya gaya masa, ai gara ta gaya masa da kanta, duk da ba wani abin ta ce masa ba, tambaya ce kawai ta yi masa.
*****
Ζamgaren Alhaji Fatuhu, Hajiya Suwaiba kamar ta yi bindiga, ganin ya amince ana yi masa maganin gargajiya, a ganinta dan Fadila ta saka baki ne, ta lallaΙa shi yake yi.
Yanzun ma Fadila tana ta ΖoΖarin kunna garwashin da za ta yi masa turare, gefe ta kunna mp sautin ayoyin ruΖiyya su na tashi a hankali.
Ya kalli Fadila ya ce "Baby, ina fatan dai magungunan nan, babu wani abu na kauce hanya a cikin su?"
Ta girgiza kai ta ce "Haba Daddy, kai ma ka san ba zan yi duk wani abu da zai taΙa imaninmu ba in sha Allah, Kawu ne duk ya bayar da su, kuma ka san shi ma masanin Addini ne sosai. Babu wani na shirka a ciki."
Ya ce "To ki yi haΖuri, kawai da na tambaya ne, kin san yanayin abin, kar garin magani mu kauce hanya na je na mutu a mummunan tafarki, ya zamana na kasa jure Ζaddarata na kauce hanya"
Fadila ta ce "In sha Allah ba zaka mutu yanzu ba, za ka samu lafiya"
"To ki yi haΖuri, na ga kin ji haushix
Ta girgiza kai ta na Ιan murmushi ta ce "A'a ban ji ba"
"Kin ji mana, kin tura baki gaban ne ba ki ji haushi ba?" Sai kuma suka yi dariya a tare.
Ya ce "Ki yi haΖuri, in sha Allah ba zan sake magana ba, na yarda da ke, ba zaki cutar da mu ba"
Hajiya Suwaiba ta shigo Ιakin, tana basarwa jin yadda Ιakin ya Ιume da Ζamshin jan almiski, da Ζaurin hayaΖi. Ta Ιan taΙa baki a ranta ta ce watakila ma a cikin wannan tsiyatakun take mallake ka.
Ta ajiye masa kwanukan Abinci, ta juya za ta fice.
Ya ce "Ba magana ne?"
"Sannu ya jiki?" Ta faΙa a daΖile.
"Jiki Alhamdillah, a hankali ji nake jikina ya yi daΙi, na Ιan samu sassauci daga abin da nake ji kamar an Ιaure ni, ba na iya motsi sai da Ζyar da dabara, da Ζirjina da yake yi mini nauyi nake jin kamar an toshe mini baki da hanci da kokowa nake numfashi" Duk da tana jin haushinsa sai kuma ta saki fuska ta ce "Alhamdillah, sauΖi yana samuwa kenan? Ubangiji Allah ya Ιorar da sauΖi, dama komai nufi ne na Allah"
Ta kalli Muhsin da yake ta tattaΙa kwanon abincin da ta kawo. Ta ce "Kai Ιan lukuti acici, ka zubar mini da Abinci sai ka biya ni. Ki zuba masa abincin ko ci zai yi" Ta yi maganar sama-sama tana Ιan kallon Fadila. Duk da matsanancin kishin da Hajiya Suwaiba take yi da ita, yanayin yadda take yi wa Muhsin wasu lokutan ya sanya Fadila ba ta fiye jin haushinta ba.
*****
Hasna kuwa ta sako Nana a gaba, bayan aikin da take yi, ta din ga sanya ta wasu ayyukan daban da ba sa cikin jadawalin wanda aka Ιauke ta yi. Wasu lokutan sai ta gama aiki, ta koma Ιakinsu, sai ta saka a taso ta, ta saka ta aiki. Abin ya ishi Nana amma ta danne.
A wannan karon ma, har ta yi shirin kwanciyar, aka zo aka kira ta. Kawai ta ji a ranta, ko Hasna za ta kashe ta yau, sai dai ta kashe ta, dan ba za ta yi mata kowane aiki ba, sai dai ta kore ta.
Ζarafe goma sha Ιaya na dare, amma tana ofishinta ba ta tashi ba. Ko da Nana ta je, tsayawa ta yi Ζyam tana jiran ta ji me Hasnan za ta ce.
Sai dai ta ci gaba da aikin gabanta, sai da Nana ta fara Ζosawa, sannan ta kalle ta ta ce "Amma an ce 'yar Nigeria ce ke ko?"
"Eh" Nana ta amsa a Ζufule.
Ta Ιan Ζura wa Nana ido sannan ta ce "Ina da wasu baΖi ne gobe in Allah ya kaimu " Nana ta Ιago tana kallonta, ta ji ina ne Ζarshen zancen, dan kullum cikin baΖi suke kamar gurin boka.
"Dan haka ba aikin gurin cin abincin nan za ki yi ba gobe in Allah ya kaimu, aikina za ki yi. Zan saka a sanar musu ma. Ina son ki yi Abinci mai kyau da daΙi na Nigeria. Ina son na sauke su da shi. Wajen la'asar za su zo, dan haka za ki dafa abin karayawa, da abincin rana da na dare, za a zo a Ιauka"
Nana ta yi ajiyar zuciya jin ba wani aikin rainin hankalin Hasna ta saka ta ba.
"Allah ya kaimu, zan iya tafiya?"
Hasna ta ce "Saurin me ki ke yi ne?"
"Na gaji ne sosai, bacci nake ji ina son na samu na tashi da wuri"
Ta jinjina kai ta ce "Ya yi je ki" Nana ta fice ta tafi Ιakinsu.
Sai dai duk gajiyar da ta yi, bacci ya gagari idanunta.
Tun bayan sallar Asuba, ta tafi kitchen Ιin ta fara aikin da Hasna ta saka ta. Sai bayan Azahar ta kammala komai, Hasna ta aiko aka ta Ιauki Abincin.
Nana ta fara shirin tafiya ta je ta yi wanka ta huta.
Adama ta ce "Ina za ki je kuma ga ayyukan kitchen fal?"
Nana ta numfasa ta ce "Ki yi haΖuri, Hasna ce ta saka ni aiki, ta ce idan na gama, na je na huta"
"A'a ba zai yiwu ba, ni ce mini a aka yi kawai za ki yi mata aiki, dan hakan idan kin gama ki saka hannu ku ci gaba da aikinmu, wa za ki bar wa wannan aikin?"
"To ki yi haΖuri, na gaji gaskiya ba na jin daΙi" kawai ta fice, tattaunawa suka shiga yi a tsakanin su, yadda za su kawo Ζarshen Nana a gurin baki Ιaya.
A Ζarshe suka yanke shawarar, su Ζara Ζaimi su Ιata ta a gurin Hasna, ganin yadda ita ma ta sako Nana a gaba da tsangwama.
Bayan sallar isha'i, Nana ta daΙe a zaune tana tasbihi, tunanin gidansu da 'yan uwanta ya addabi zuciyarta, ga shi abin da ta fito neman har yau babu labari. Ta daΙe tana addu'a kafin ta nemi guri ta kwanta.
Washegari ma su na ta aiki tun safe har Yamma, sai ga Hasna ta shigo.
Duk yadda Hasna take da kyau, ita da Al Hussain, wannan da suka shigo ta fita kyau, tamkar balarabiya, jawur da doguwa sai dai siririya ce sosai. Fuskarta ta sha make up, sai zuba Ζamshi take yi.
Ta yafa Ιan siririn mayafin abayarta a kanta. Sai kallonsu take Ιaya bayan Ιaya tana yatsuna fuska su na yare ita da Hasna.
Duk suka gaishe su, Nana kuma ta yi burus.
Hasna ta nuna mata Nana ta ce "Kin ganta nan"
Asal ta yamutsa fuska ta ce "Ya na ganta baΖa Ζirin haka, ina fatan ba na Ζazanta ba ne?" Nana ta yi mamakin jin Hausa raΙau a bakinta.
"Ke ina ruwanki da baΖinta, ba dai Abinci ya yi ba?"
"Eh kin san ba na son Ζazanta ne"
Hasna ta ce "Sauran ma'aikatan namu ma ai akwai baΖaΖe, kuma kema kin san da ba ta da tsafta, ba zan saka ta yi miki girki ba.Ke Nana ba ki ganni da baΖuwa ba ne?" Nana ta Ιaga kai ta kalle su, ta yi shiru tana wasa da wuΖar hannunta, saboda ciwon da maganganun da suke yi ya yi mata, na cin zarafin baΖar fatarta da danganta ta da Ζazanta, duk ba wai duhu ne da ita sosai ba.
Shiru Hasna ta yi ta kamo wata hirar, ganin alamun idan ta matsa Nana za ta yarfa ta ne a gaban baΖuwarta. Ba a taΙa ma'aikacin da ba ya shakkar ta ba sai Nana. Duk abin da ta saka ta na aiki za ta yi, amma ba ta son rainin hankali.
Bayan sun fito Asal ta tsaya ta kalli Hasna ta ce "Hasna"
"Na'am"
"Ina ga yarinyar nan ta yi dai-dai da abin da nake nema"
"Wace yarinyar?"
Asal ta ce "Wannan 'yar Nigeriar, ina buΖatar za ki ba ni ita"
Ayshercool
08081012143
70
Sai da Nene ta tabattar Nana ta Ιan nutsu, sannan suka kwanta.
Washegari Nene ta fita, ta bar Nana a gidan tare da Muhsin. Bayan ta dawo daga gurin sama'arta ta cewa Nana, yakamata ta je ta Ιan sai abubuwan da za ta buΖata saboda tafiyar da za ta yi da nisa, kuma ba su san yaya tsarin aikin can Ιin yake ba.
Nana ta ce "Ni babu abin da nake buΖata, ki bani wani abin na riΖe a hannuna, sauran kuΙin kuma ki riΖe saboda kula da Muhsin na s...
"Biyana za ki yi kenan dan na riΖe miki Muhsin?" Nene ta katse ta.
"Allah ya baki haΖuri, ba haka nake nufi na, na ga dole Ιan abubuwan buΖatunsa duk ke ki ke yi masa Nene, tun da ga kuΙi sun"
"KuΙinki ba su isa su saka na riΖe miki Ιa ba ko?"
Nana ta ce "Na sani, ai shi ya sanya na ce ki yi haΖuri.
Nene ta ce "Ba zan yi haΖurin ba sai na gama, kin iya kunna ni da na fara faΙa ki hau bani haΖuri, wato in ci kaina to sai na idar"
Nana ta yi mata shiru ta yi faΙanta ta gama.
Washegari Nene ta saka Nana a gaba suka je kasuwa, ta sata ta yi sayayyar kayan sakawa da na Ιan shafe-shafe, ta yi wa Muhsin sayayyar kayan sakawa da pampers. Babu yadda ba ta yi da Nene ba ta Ιauki wani abin ta ce ba za ta Ιauka na.
Nana ta haΙe rai ta ce "Eh dama ba ki Ιauke ni 'yarki ba, shi ya sanya duk abin da zan yi miki ba kya karΙa"
"Ni za ki yi wa wayo, na ji ban Ιauke ki 'yar ba, ni ga Ιana nan" tayi maganar tana shafo Muhsin da ke bayanta. Da Ζyar sai da suka kai ruwan rana Sannan Nene ta karΙi abin da Nana ta saya mata.
Sai dai kan su bar kasuwar har sun shirya. Nana ta ce "Nene kin ce mini ki na da Ιa, amma ban taΙa ganinsa ya zo ba, ba ya zuwa ya gan ki ne?"
Nene ta ce "Kamar ban damu da shi ba ko?"
"A'a kawai dai tambaya na yi "
"Yana can Nigeria"
"To me yake yi a Nigeria ba ya zuwa inda ki ke?"
"Sana'a yake yi, ai ya zo ki na can gurin aiki"
Duk da Nana ba ta gamsu da amsoshin da Nene ta ba ta ba, amma ta basar ta ce "Allah sarki, Allah bai yi zamu haΙu ba".
Haka suka ci gaba da hira suka koma gida, Nana ji take yi tamkar ta Ιauke Ιanta ta tafi da shi.
Gidansu Ashura Nana ta je, ta samu keke ta ΙiΙΙinka kayan da ta sayo, ta sake haΙa jakarta ta Ιauki muhimman abubuwa a kayanta.
Duk da a Ιaki Nene take rufe mata su, ba ta taΙa ganin alamar Nenen tana yi bincike a cikin kayan ba.
*****
Ko da Jamila suka dawo Kano, fakar ido ta yi ta jefar da wannan tarkacen da aka ba ta aka ce da su za ta kai jini.
Gaba Ιaya da ta tuna abin tsigar jikinta take tashi, ta ji ciwon kanta da zazzaΙi ya Ζaru.
Gefe guda kuma hankalinta yana kan yadda ta ji Hajiya Sa'a tana faΙin za ta sake bayar da Ιan Alhaji Fatuhu. Ta jinjina rashin imaninta mutumin da yake fama da karayar arziki ga ciwo, ya rasa wancan Ιan kuma a sake bayar da wannan kamar ba a yi masa adalci ba. Sai dai gaba Ιaya ba ta san ta ina za ta fara ba, tana jin a ranta kamar yakamata ta tseratar da yaron.
A gida ta tarar da Gaddafi, ta sha jinin jikinta da irin mugun kallon da ya yi mata, amma bai ce mata uffan ba. Suwaiba ma Ζura mata ido ta yi tana bin ta da kallo.
Ta tsuke fuska ta harsri Suwaiba, sai dai Suwaiba ta tuntsure da dariya, kamar za ta shiΙe. Jamila ta yi tsaki ta shige Ιakinsu.
Ba ta tarar da Mama a gida ba, haka ma Baba.
*****
Shiru Alhaji Zailani ya yi yana kallon Doctor Sharif yana sauraren shi, har ya gama karanta masa abin da Shukura ta je ta same shi ta yi masa.
Ya ja numfashi ya ce "Shikenan, aikinka ya yi kyau Sharif, na kuma gode sosai da sosai da ka ke sanar da ni wannan abubuwan, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi. Ka je za ka ga saΖo" Sharif ya yinΖura ya tashi ya tafi.
Alhaji Zailani ya numfasa a fili ya ce "Duk da kasancewar ki 'ya mafi soyuwa a cikin zuciyata, an zo gaΙar da ki ka Ζetare layin da bai kamata ki Ζetare ba, kina ΖoΖarin tono abin da zai wargaza zaman lafiya da kwanciyar hankali, dan haka ki yi haΖuri da duk matakin da zan Ιauka a kan ki.
*****
Nana ta jingina da jikin gilashin motar, tana kallon tulin yashin saharar da ya mamaye gurin. Fili fetal hagu da dama duk yashi ne. Cikin yanayi mai kama da bacci take ganin abubuwan da ta din ga gani a bacci cikin saharar.
Ko a yanzun ma su na tafe Sayyid kawai take gani a kan raΖumi yana biye da su a cikin saharar.
Kamar an taΙa ta ta Ιan yi firgigit ta kalli gurin, haryanzu a titin da ya ratsa saharar suke tafiya, zuciyarta ta yi wani irin bugu da sai da ta dafe Ζirjinta.
Sanyi ta fara yana ratsa ta har cikin Ζashinta, ta Ιaga ido tana Ιan waige-waige ta ga ta ina za ta gano Ζaisar ko wata baΖuwar halittar da ba jinsin mutane ba, sai dai ba ta ga komai ba.
Ta sake jingina da jikin motar tana ta karanto duk addu'ar da ta zo bakinta. A haka har suka shigo cikin gari sosai da sosai.
Nana na son karanta Symbols Ιin da take gani, amma ba komai take iya fahimta ba saboda rubutun French. Babbar hanya mai Ιauke da Ζaton gate ta ciki suka wuce.
Ba Ζaramar gajiya Nana ta yi ba, saboda azabar nisan tafiyar da suka shawo ba, ba su Ζarasa ba sai bayan magariba. Kewar Ιan ta ta addabi zuciyarta, tunaninta yadda za ta din ga sintirin tsakanin Agadez da MaraΙi a wannan uwar tafiyar kamar ta ya da shege.
Wasu irin gidaje ne manya-manya na alfarma da Ζasaita a cikin gurin.
A Ζofar wani gida direban ya tsaya, ya cewa Nana ta fito sun zo. Haka ta saukko Ζafafuwanta duk sun yi tsami saboda azabar gajiya.
Ya buΙe bayan motar ya Ιaukko Ζatuwar jakar Nana, ya rufe motar, ya yi gaba Nana ta bi shi a baya tana karanto addu'oin da suka sauwwaΖa.
Cikin wani matsakaicin gida suka shiga, gidan ya Ζawatu ya yi kyau sosai da sosai.
A falon gidan ya ajiye wa Nana kayanta ya ce "Ki zauna ki jira a nan"
Nana ta ce "Amma wa zan jira a nan Ιin, ban ga alamar akwai mutane a gidan nan ba"
"Za ki gan su, ni a nan aka yi mini umarnin na kawo ki kawai"
Nana ta yi shiru tana nazari, shi kuma ya juya ya fice.
Nana ta din ga rarraba ido, tana son ta yi salla amma babu wanda za ta tambaya. Harabar gidan ta fita saboda ta ga famfo ta yi alwala, ta dawo falon ta yi salla.
Gajiya ta yi ta koma harabar gidan da kayanta, ta zauna tana rarraba ido.
Can ta ji Ζarar mota, aka buΙe Ζofar wani jami'in tsaro ya shigo ya buΙe gate Ιin, aka shigo da wata haΙaΙΙiyar mota aka yi parking Ιin ta.
Aka buΙe Ζofar motar, sai ga Asal ta fito sanye cikin doguwar riga, ta Ιaura mayafin a wuyanta, kanta babu Ιankwali. Har bakin Ζofar shiga suka rakata, ta wuce Nana ta shige ciki kamar ba ta gan ta ba. Nanan ma ta yi zamanta ba ta shiga ba, ta jingina da jikin kayanta taka addu'a saboda a gajiye take matuΖa, ga uwar yunwa tana ji ga tulin damuwa.
Sannu a hankali take tuna yadda ta shigo Ζasar Nijar ba ta san kowa ba, da yadda ta din ga raragefe har zuwa kan zamanta da Nene. Sai ta tsinci kanta da tattara su baki Ιaya tana yi musu addu'a, da fatan dacewa a Duniya da lahira.
Ba ta san iya adadin lokacin da ta Ιauka a gurin ba, ta ji muryar Asal a kanta.
"Wai ke wace irin bagidajiya ce, a Nigeria daga wani Ζauyen ki ke ne?" Nana ta Ιaga kai ta kalle ta.
"Na saka an kawo ki guri, ki shiga ki jira ni kin zauna a waje, na dawo ma kin nemi guri kin zauna ba za ki shigo ba?"
"Ta yaya zan shiga gurin da babu kowa na zauna, ni da ban san ma aikin da ki ka kawo ni na yi miki ba?"
Haushi ya kama Asal, ta ce "To idan kin ga dama ki shigo, idan kuma ba ki ga dama ba, ki yi ta zama a gurin" Ta shige ciki Nana ta bi ta da harara, kamar ba za ta tashi ba, sai kuma ta tashi ta ja kayanta, ta shiga falon ta nemi guri ta zauna a kan kujera. Asal ta saci kallon Nana, da yadda take gudanar da lamarinta cike da Ζarfin hali.
Nana ba ta kula ta ba, ita ma ba ta kula ta ba, Nana ta gaji da zama, ta saukko Ζasa ta miΖe ta kwanta.
Can Asal ta ce mata "Ga kitchen can, akwai abinci"
Daga haka ta tashi ta bar falon.
Nana ta tashi ta shiga kitchen Ιin, ta tarar da Abinci, ta Ιauka ta ci sannan ta Ιan dawo hayyacinta.
A nan falon Nana ta kwana, da Asuba ta yi alwala a harabar gidan, ta koma falon ta yi salla.
Duk wannan abin zuciyarta a cike da zullumin aikin da za ta yi wa Asal.
Da gari ya yi haske, Asal ta fito Nana ta gaishe ta, amma ta yi kamar ba ta ji ba, ta fice ta bar gidan ta bar Nana.
Nana tana nan zaune, aka zo aka ΖwanΖwasa Ζofar falon, ta tashi a Ιan tsorace ta buΙe, wani mutum ya miΖo mata takeaway ya ce "Ga shi nan, aka ce a kawo miki" daga haka ya juya ya tafi.
Nana ba ta sake ganin Asal ba sai dare, ba ta saurari Nana ba still. Ta cika gidan ita da Ζawayenta, suka hau saman bene, suka kunna kaΙe-kaΙe har kusan Ιaya na dare su na abu Ιaya, suka hana Nana bacci.
Sai gefin Asuba suka daina wannan shirirtar, Nana ta din ga mamakin ita Asal zaman kanta take yi ne, ba ta da magabata ko kuwa?
Sai washegari sannan ta saukko Ζasa, a lokacin Ζawayen nata duk sun tafi.
Ta kalli Nana ta ce "Daga yau kar ki Ζara kwanar mini a falo, ga Ιaki can kusa da kitchen, a nan za ki din ga kwana. Na kawo ki ne duk da ba yanzu ne za ki yi aikin naki gaba Ιaya ba, amma za ki din ga yi mini girkin Abinci da ni da Ζawayena, da sauran aikace-aikacen gida.
Abu na farko dalilin da ya sanya na Ιaukko ki, ke ba Ζabilarmu ba ce ba, ba na son saka ido, ba na son surutu
Duk wani abu da za ki ga na yi, ko ina yi babu ruwanki, aikin duk da na saka ki shikaΙai za ki yi mini"
Nana ta yi shiru tana tunani, dama duk wannan abin ba wani branch Ιin za a kai ta aiki ba, wannan zuΖaΖΖiyar za ta yi wa bauta, shi ne har da ci mata mutuncin cewa an yi amfani da kuΙi sai ta yi abin da ake so. Kuma me yasa ba ta zaΙi kowa ba sai ita?.
"Ba kya ji na ne?"
"Na ji"
"Ban gane kin ji ba? Haka zan din ga yi miki magana ki na amsa mini, ke ni fa ba Hasna ba ce ba, dole ki yi mini biyayya ki yi duk abin da nake so".
Nana ji ta yi tamkar ta yi tsaki, ta ce "Amma yanzu fisabilillahi duk faΙin Ζasar nan ki rasa wanda za ki Ιaukko ya yi miki aikatau sai ni. Ni harkar dafa abinci nake yi, amma kin kawo ni nan in din ga yi miki girki da boyi-boyi ba tare da an yi mini bayanin haka ba, ni gaskiya ba a kyauta mini ba"
"Da hakan ki ka dace ai, ko kina ganin kin cancanci wani abin bayan bauta? Idan ba za ki zauna ba ga hanya nan za ki iya tafiya" Ta yi maganar tana miΖewa tsaye.
Har ta yi gaba sai kuma ta tsaya ta ce "Duk wani abu da za ki buΖata akwai shi a kitchen, kina iya dubawa, wanda babu kuma ki sanar mini, shi ma idan ba ki ga dama ba kar ki yi aikin" ta yi gaba ta bar Nana da ta gama Ζulewa.
*****
Gaba Ιaya Shukura ta burkicewa Sagir, ba Ιaga masa hankali ta yi da rigima ba, tattara shi ta yi ta watsar gaja Ιaya take harkokinta, da gaske take ΖoΖarin gano abin da mahaifinta yake Ιoyewa tsawon wannan lokacin da har ya hana Hajiya Amina bincike a kan lafiyarta.
Ga shirin tariyar Yusra Sagir na yi, ga damuwar rashin sakin jiki da shi da Shukura ta yi, ta tattara shi ta watsar.
Ζangarensa ya saka aka gyarawa Yusra, dama ba amfani yake yi da shi ba, aka Ζara gyara shi, aka haΙa gidan gaba Ιaya aka sake yi masa fenti. Daga gaya mata batun dawo da Yusra zuwa gyaran gidan da kawo kayanta, ba a yi sati guda ba, gida ya Ιau harama.
Duk yadda ya so ya lallaΙa Shukura, ta saukko ta din ga saurararsa ta yi burus da shi.
Nana ta shafe sati guda tana gidan Asal, tana yi mata hidima, ta hantare ta ta kyare ta, dandazon Ζawayen da take tarawa ma, su hana ta sukuni da aiki. Nana ta din ga iya ΖoΖarinta, gurin kai zuciyarta nesa, amma abin ya fara isarta.
Tana tsaka da nazarin yadda za ta Ιullowa lamarin, da safe Asal za ta fita ta kalli Nana ta ce "Ki shirya nan da sati Ιaya zamu bar nan, zamu je asalin inda na Ιauke ki ki yi mini aiki a gurin"
Nana ta ce "Ina kenan? Kuma aikin me?
"Idan mun je za ki gani" Ta ba wa Nana amsar a taΖaice.
*****
Jamila tana kwance tana chatting da Abba, bikinsa saura sati biyu.
Hajiya Sa'a tana ta zaginsa da yi masa bala'i, a kan yadda yarinyar take ta Ζorafin ba ya kula ta, waya ma sai dai ita ta kira shi, babu abin da ya yi masa zafi da ita.
Yanzun ma kamar ya yi wa Jamila kuka.
Ita take ta rarrashinsa tana nuna masa babu komai ya yi aurensa kawai.
"Ζanwata ko na yi aure hankalina ba zai kwanta ba, kar ki manta da Ιarnar da ta faru tsakanina da ke, ya zan yi da shi"
Ta ce "Na san kai mutumin kirki ne yayana, hakan ne ya sanya ka ke jin damuwa a kan abin da ya faru, amma ka yi haΖuri ka yi aurenka kawai, ina roΖon Ubangiji Allah ya kawo mini wani mijin"
"A'a ki daina faΙa mini haka, zuciyata tana sosuwa, baki da wani miji sai ni in sha Allah" haka suka kasance tana Ζarfafa masa gwiwa, shi kuma yana rarrashinta.
Ta gama wayar ta ajiye, ta ga Suwaiba ta Ζuro mata ido tamkar ba ta taΙa ganinta ba.
"Meye ki ke kallona, lafiya?" Suwaiba ta yi shiru ba ta bata amsa ba, kuma ba ta yi magana ba.
Jamila ta ja tsaki, tana ΖoΖarin kwanciya, Suwaiba ta ce "Jamila"
"Na'am mene ne?"
"Ki Ιauki saΖonki mana"
Cikin rashin fahimta ta ce "Wane saΖon?"
"Na cikin jakarki"
"Cikin jakata kuma? Mene ne a jakar tawa? Wato bincike ki ke yi mini a jakar ko?"
"A'a ni tuni kawai nake yi miki da saΖonki na cikin jakar"
Jamila ta tashi zaune ta ce "Wai wani saΖon? MiΖo mini jakar dai na gani"
Suwaiba ta ce "A'a ba zan taΙa miki jaka ba"
Jamila ta janyo jakar ta fara buΙewa ta ga abin da Suwaibabta dame ta a kai. Cin karo ta yi da wannan 'yar tsanar da ta riga ta jefar. Saura Ζiris ta kurma ihu, ta rikice gaba Ιaya jikinta ya hau rawa, a tunaninta tun da ta yar shikenan ta rabu da ita.
Suwaiba kuwa ta tuntsure da wata irin mahaukaciyar dariya, ta din ga yi tana ΖyaΖyatawa tana kallon Jamila. Gaba Ιaya Jamila ta kiΙime ta rasa abin da yake yi mata daΙi, gaba Ιaya jikinta ya hau rawa tamkar ta kurma ihu, sannu a hankali kanta ya fara juyawa ta fara gani dishi-dishi, dole ta rufe jakar ta nemi guri ta kwanta.
*****
Alhaji Zailani ya kwana biyu bai je gidan Alhaji Fatuhu ba sai yau. Sai dai ya sha mamakin ganinsa a harabar gidan da sanda yana dogarawa yana tattakawa a hankali, yana tsaye a kan Ζafafuwansa yana kallon yadda Muhsin yake ta gudu a harabar gidan.
Sai da ya aro jarumta sannan ya iya danne abin da ya ji ya taso masa na tashin hankali da mummunan baΖin ciki.
Da Ζyar ya iya washe baki ya ce "Ikon Allah, Abokina kai ne haka nake gani?"
Alhaji Fatuhu ya yi murmushi ya ce "Ka ga ikon Allah ko? Sannu da zuwa Bismillah" ya yi maganar yana nuna masa Ιaya daga kujerun da ke ajiye a gurin.
Alhaji Zailani ya zauna suka Ζara gaisawa
"Bani labari, ya aka yi sauΖi ya samu haka, wani Asibitin ka je ne?"
Alhaji Fatuhu ya ce "A'a na ga an yi na Asibitin ne babu wani ci gaba, Fadila ta zauna ta din ga yi mini bayani, na amince muka fara gwada na islamic, cikin ikon Allah sannu a hankali wannan Ιaurewa da nake ji a jikina ya yi mini sauΖi, wannan gigicewar da nake na ji kamar zan yi hauka shi ma Alhamdillah ina daΙewa ban ji ba, wannan warin ma da nake ji ya ragux
"Amma Fatuhu ya za a yi ka biye wa mace da shirmen ta, ga na Asibiti ana yi kawai ta saka ka fara wani na shirme, sai ka je ka yi abin da za ka kauce wa hanya tukuna?"
"A'a nima na jaddada mata, ta kuma tabattar mini da babu kauce hanya a ciki, kuma nima shaida ne, shi ya sanya ma nake amfani da magungunan kuma ana samun ci gaba"
Alhaji Zailani ya miΖe ya ce "Haka ne, to bari na je dama ina da gurin da zan je na biyo, sauri nake yi"
"Ba zaka tsaya ku gaisa da mutanen gidan ba?"
"Sauri nake yi zan sake dawowa"ya yi maganar yana yin gaba cikin Ζunar rai, ji yake yi tamkar ya kashe Alhaji Fatuhu ya huta, dan shi bai taΙa zaton zai kawo yanzu bai mutu ba.
*****
Al Hussain ne a tsaye ya tsare Hasna da ido, yana yi mata faΙa cikin matsanancin Ιacin rai.
"A kan me za ki yi haka? Dan me za ku yi mata dole, ai ba Ιaukar ta aiki muka yi saboda buΖatar mutum guda ba. Abin da yake cikin yarjejeniya shi ne ta yi wa gidan Abincinmu aiki, idan ma canza gurin aikin ne, wani reshen zamu mayar da ita, amma dan me za ku haΙa kai ku yi mata haka wannan wulaΖanci ne da cin zarafi, kuma ga shi bama 'yar Ζasarmu ba"
"Ni fa Al Hussain na kasa gane maka, ko son yarinyar nan ka ke yi ne? To bari na tuna maka kai Buzu ne, buzun ma farin buzu ka san abin da nake nufi ai, kuma matar aure ce ko bazawara dan ta ce mana tana da Ιa ma"
"Ni ba wannan na tambaye ki ba, dan me Asal za ta yi amfani da Ζarfi da kuΙi ta tursasa mata yin abin da ba ta so, ai ba haka ake rayuwa ba"
"Ai na san za a yi haka, babu bayanin da ban yi mata ba taΖi yadda, ga shi ni yanzu ka zo ka saka ni a gaba da jaraba, sai ka je ka dawo da ita ni ba zan iya ba"
"Ke dai da ki ka yi hakan ki je ki dawo da ita, idan ba haka ba daga ke har ita na rubuta masa abin da ku ka aikata, daida yake da ku"
Ta kwaΙe baki ta ce "Wa ya san ma inda yake, mutumin da ake tunanin ya Ιata babu wanda ya san ma yana raye ko yana mace?"
"Hakan ya baku damar cin karenku babu babbaka daga ke har Asal ko? Yayi muku kyau" Hasna ta fice tana jin haushin masifar da Al Hussain yake ta yi mata, duk yadda ta yi ΖoΖarin hana Asal Ιaukar Nana.
*****
Ana gobe su Nana za su bar wannan gidan, Asal ta sanar da Nana ta shirya washegari za su bar nan.
Ita dai Nana ta sanya wa sarautar Allah ido, rayuwarta ta zama tamkar tamaula daga nan zuwa can, ba ma ta da 'yancin tambayar ko sanin inda za a kaita sai dai inda ta tsinci kanta kawai.
Ta sha aiki ta gama, ta Ιan zauna a falo tana hutawa, sai ga Ιaya daga gayyar Ζawayen Asal ta saukko ta kalli Nana ta ce "Dan Allah ina son shayi"
Nana ta ce "Akwai a kayan Abincin da na girka"
"Shayin kanumfari kawai nake so bana son Shan na girfa"
"Ga gurin dafawar can, idan ki ka je akwai komai, ki dafa ki sha idan kin matsu"
"Ke, kin san wace ce ni ki ke gaya mini haka?"
"Ban san wace ce ke ba, kuma ba na buΖatar sani"
Asal ta saukko tana tambayar lafiya.
Ta gaya mata abin da ya faru, ta kalli Nana ta ce "Wai ke me yasa ba ki da mutunci, ban gaya miki dole ki girmama baΖina ba, mene ne a cikin dafa shayi mintinan nawa ne kin yi kin gama?"
Ta kalli Asal ta ce "Ki yi haΖuri, wallahi ko cokali ba zan iya sake Ιauka ba, yau na bautu a gidan nan ke kin sani, kuma ban taΙa yi miki Ζorafi ba, amma yanzu dai na gaji gaskiya"
Suka juya yare suka yi magana, ba ta san me suka ce ba, ta ga sun koma kan bene.
Washegari da wuri suka Ιau hanya, sai dai ga mammakin Nana, har da rakiyar jami'an tsaro, kuma a wannan karon shigar Shadda Asal ta yi, an yi wa shaddar aiki tun daga sama har Ζasa.
Mota Ιaya suka hau, ta ce Nana ta hau gaba, ita kuma ta hau baya.
Sai da aka kuma wata tafiyar mai nisa, sannan ta ga sun tunkari wani irin ginin Ζasa tamkar ginin ganuwar Kano.
Ginin ya Ζayatar da Nana sosai da sosai.
Jami'an tsaro ne suke gadin Ζatuwar Ζofar gurin, da wasu Buzaye farare tas sanye da rawani.
Nana kamar ta ce a tsaya, ta duba buzayen nan Ιaya bayan Ιaya ko za ta ga Sayyid Ιin ta cikinsu. Sai da motar su ta tsaya, suka sauke glass Ιin motar.
Da Hausa suka gaisa, suka yi mata sannu da zuwa, Ιaya daga cikin su ya kalli Nana ya ce "Wannan fa?"
"BaΖuwata ce" ta ba shi amsa, ya jinjina kai motar ta shige.
Su na shiga Nana ta ga ai gari ne guda a cikin ganuwar nan.
Sun Ιan yi tafiya kafin su shiga wani Ζaton gida.
Nana ta tsaya tana ganin yadda aka yi wa ginin Ζasa wani irin ado mai Ζayatarwa.
Tun da suka doshi shiga gidan, ake gaida Asal cikin girmamawa, ita kuma ta yi fuska sai taku take cike da Ζasaita, kamar ba ita ce suke rashin hankali da Ζawayenta a wancan gidan ba.
Wannan gidan saΙanin wancan da mutane a ciki, kuma da alama duk a ΖarΖashin Asal suke.
"Wace ce ita?" Nana ta tambayi kanta. Sai da suka Ζarasa wani falo, sannan ta yi wa wata dattijuwar magana da yaren su.
Matar ta kalli Nana ta ce "Bahaushiya ce ke ko? Zo mu je na kai ki masauki"
Babu musu Nana ta bi ta, matar ta kai ta wani daki ta ce nan ne Ιakinta.
Sai da Nana ta kwana biyu a gidan, ba ta sake ganin Asal ba, ba kuma ta aikin fari ba ta na baΖi kawai tana zaune, sai dai za a kawo mata Abincin safe, rana da dare sau uku a rana. Sai dai babban abin da ya dame ta, tun da ta shigo gidan, network Ιin wayar ya sauka gaba daya, ko ta kira Nene ba ta shiga sam.
A kwana na huΙu, da daddare dattijuwar matar nan ta zo ta kira Nana. Babu musu Nana ta tashi ta bi bayanta.
Sun yi 'yar tafiya su na ratsa faluka masu kyau da ado, sannan suka bi wata Ζofa. Sanyin A.C ya daki Nana, ga wani irin haΙaΙΙan Ζamshi. Asal ta hahakimce a kan kujera kaΙa Ζafa.
Ta kalli dattijuwar ta ce ta jira a waje. Daga Ζasa wata matar ce a zauna a kan carfet, ta gurfana kamar tana jiran Asal Ιin ta gafarta mata.
Nana ta yi turus tana tunanin a ina za ta zauna, sama ko Ζasa.
Matar ta kalli Nana cikin zare ido ta ce "Ke ki rage tsawon ki, kin tsaya mata a ka"
Nana ta ja guri ta zauna a kan carfet Ιin ita ma.
Asal kamar ba za ta yi magana ba, sai da ta gama iyayinta ta sauke Ζafarta Ζasa ta dubi Nana ta ce "Amm na saka an kirawo mini ke, saboda ki san abin da na kawo ki gidan nan ki yi. Ke dai da ganin gidan nan kin san ba gurin da za a yi wasa ne ko shirirta ba, babban gida ne na mulki.
Saboda dalilin girki da kuma wani dalili na Ζashin kaina, ya sanya na kawo ki gidan nan. Ba a Ιaukko bare wanda yake ba jinin gidan nan ba, ko Ζabilarmu ba ya yi mana aiki, amma na ga wasu abubuwa a tattare da ke da ya sanya na kawo ki cikin gidan nan.
Kamar yadda na gaya miki, ina Ζara jaddada miki, zaman ki a gidan nan dole ki yi taka tsantsan, babu ruwanki da shishshigi, saka ido, gulma ko kuma shiga abin da babu ruwanki.
Sannan kar ki kuskura wani ya ce zai haΙa kai da ke a yi wani abu, rayuwarki za ta iya salwanta ba tare da kowa ma ya sani ba, dan haka sai ki san irin zaman da za ki yi."
Nana ta yi shiru ta gama sauraren ta, sai dai har a lokacin ba ta ji dalilin da ya sanya Asal kawo ta gidan ba, dafa abinci kowa ma zai iya mai yasa sai ita.
Wannan matar da ta tarar a zaune, ta tafi da ita, ta kai ta gurin da ake girke-girken abinci, da gaya mata yadda jadawalin girke-girken gidan yake. Ta Ιaukko kayan ds Asal ta bayar a ba ta, na kayan shafe-shafe da mayukan wanka zuwa kayan sakawa.
Da Nana ta koma Ιakinta, ta kalli kayan ta fara tunanin Allah ya sa ba kwance Asal ba ne, dan gara ta saka kwancen Ashura da ta saka na Asal, da ba ta da mutunci.
A washegari Nana ta fara aiki a wannan madafa, sai dai madafar daban-daban ce. Akwai wadda ake girkin da ma'aikatan gidan ne suke ci, akwai wadda na baΖin da suke zuwa ne, sai kuma masu girka wa Asal abinci daban, dan haka Nana na cikin masu yi wa Asal girki.
Sosai matar nan ta Ζara jan kunnen Nana, a kan ta kula da kanta, dan muddin aka samu matsala ba za ta sha ba.
Nana a ranta ta ce "Ji wata jaraba, da wannan wahalar mutum ya girka abin da zai ci mana da kansa."
Kwana huΙu da fara aikinta, ranar Alhamis da daddare, tana shirin kwanciya, aka ΖwanΖwasa Ζofar Ιakinta.
Ta tashi ta buΙe, ta ga shugabar girke-girke ta gidan, kamar yadda aka gabatar mata da ita a baya.
"Ki sako hijjabinki, ki biyo ni"
Nana ta saka hijjabinta ta fito tana tunanin ko lafiya.
Harabar gidan matar ta yi, Nana ta bi bayanta, ta nuna mata mota. Nana ta kalli dare ya yi kuma an zo da mota an ce a tafi da ita.
Cike da mamaki Nana ta shiga motar, sai ta ga mutum uku, da su ma duk tare suke aikin girkin a gidan a cikin motar.
Ta shiga ta zauna, ita ma shugabar ta su ta shiga. Nana ta gaza haΖuri ta ce "Dan Allah ina za mu je ne?"
"Za ki gani"
"Eh amma na ga dare ne fa"
"Idan mun je za ki ji dalilin fitar" Nana ta yi shiru tana tunani, ita ba ma wannan ba, hankalinta ya koma kan rashin samun damar kiran waya da ba ta iya yi, kuma ba a kiranta ya shigo. Dan sai da ta tambayi Ιaya daga cikin masu aikin, ko matsalar daga wayarta ne, ta ce mata kar ta kuskura ta bari ma a san tana da waya, dan sai an Ζwace ta.
Tana ta zancen zuci, har suka isa inda aka tsaya suka sauka, aka shiga da su.
Asal ce a tsaye, tare da dattijuwar matar da ta saka ta raka Nana masauki. Suna tsaye a cikin Ιakin Nanan.
Asal ta ce "Zazzage mini kayanta, ki Ιaga mini komai Ιaya bayan Ιaya"
Ayshercool
71
Ζaya bayan Ιaya, aka din ga zazzage kayan Nana. Aka zazzage su tsaf aka Azzage jakar da ta zuba kayan turarukanta da mayukan shafawa, duk ba ta ga wani abu ba, sai jakar gurin sarkin baka.
Ta nuna jakar ta ce "Mene wannan?"
Ta Ιago jakar ta ce "Jaka ce"
"BuΙe ta ki zazzage na gani" Ta fara kokowar buΙe jaka, amma babu gurin da zata buΙe ta. Kawai ta ce "Shikenan" ta fice ta bar Ιakin.
Can gurin kuma Nana tara su aka yi, su shida. "Na san za ku yi mamakin dalilin da ya sanya aka kawo ku nan, to zaΙo ku aka yi saboda an yarda da amanarku, ana daf da yin taro da Sultan da kuma dukkanin Imams na gidan nan. Dan haka ku aka zaΙo za ku yi girki na musamman. Amma ku sani kamar yadda wasu sani wasu ba su sani ba, muddin aka samu wata matsala ko Ζware wani ya yi, a sanadin abincin da ku ka dafa, to ku tabattar da rayuwarku za ku biya. Dole ku yi taka tsantsan ku kula." Matar ta yi maganar daki-daki.
"In sha Allah" suka amsa mata.
Ta ce su bi bayanta, suka je wani Ζaton guri, Ιauke da nau'oin kayan masarufi kala-kala. Ta yi musu bayanin da su ne za su yi amfani su yi girkin, sannan ya zama dole su sanya wa bakinsu sakata su yi aiki cikin amana, kuma kada wanda ya san su aka zaΙa da za su yi wannan girki. Nan ma suka amsa, ita dai Nana sai kallo da ido, dan abubuwan sun daina ba ta mamaki, wannan maganar ce ta sanya aka taso ta a daren nan, sai ka ce wanda za su girkawa wasu waliyyai abinci.
Ko da aka mayar da su Nana gida, ta sha mamakin ganin kayanta a hargitse a cikin Ιaki. Da mamaki ta Ζarasa kan kayan nata, ta ΙaΙΙaga.
Cikin takaici Nana ta tashi ta fita, sai dai kowa ya tafi makwancinsa ya kwanta. Kawai ta ji taku a bayanta. Ta waiwaya ta ga Asal na fitowa.
"Har kun dawo kenan?"
"Eh, sai dai na shiga Ιakina na tarar da an caje mini kayana an zubar da su a Ζasa, ban sani ba ko kina da masaniya a kan haka?"
Asal ta ce "Me yasa ki ka zarge ni?"
"Saboda na ga ba a gudanar da komai a gidan nan sai da izninki"
Asal ta yi murmushi ta ce "Haka ne, kina da kaifin ΖwaΖwalwa kamar yadda na yi tsammani, ni na saka aka caje kayanki saboda na san da wa nake zaune"
"Me yasa ba ki tambaye ni abin da ki ke buΖatar sani ba, za a caje mini kaya"
"Saboda a ΖarΖashina ki ke, a gidana ki ke zaune dole na sani idan da wani abu da ki ke tattare da shi na cutarwa"
Nana ta ce "Kin yi kuskure, dan ina zaune a ΖarΖshinki, ina da personal life Ιina, da 'yancin adana abin da yake sirrina, bai halatta ki bincikar mini kaya a bayan idona ba. Yaushe na san ki, da zan Ζulla wani abu da zan cutar da ke? Kina gudun hakan ki jawo ni ki ka kawo ni?"
"Yi Ζasa da muryarki, kar ki kuskura ki Ιaga mini murya, kin san matsayina? Za ki iya janyo wa kan ki gagarumar matsala muddin ki ka ci gaba da yi mini magana ba ladabi"
"Babu ruwana da matsayinki, da koma me za ki yi mini, kar ki sake shigar mini Ιaki ki taΙa mini kaya, idan kuma ki ka ci gaba za ki iya binciko abin da zai hana ki sukuni, idan kin ji ba ki yarda da ni ba, ki sallame ni na koma inda na fito, ba zai yiwu na zauna da ke kina zargina kuma kina cin dunduniyata ba."
Asal ta bi Nana da kallon mamaki, amma ta danne mamakinta ta haΙiye fushinta, ta ce "Gaskiya ne, kin yarda da kan ki har haka kenan? Shikenan amma idan na ga akasin abin da ya fito daga bakinki, za ki sha mamakin abin da zai faru"
Nana ta yi mata banza, ta koma Ιakin nata, ta gyara kayanta tsaf.
Ta kulle Ιakin ta koma ta Ιaga katifar Ιakin, ta Ιaukko wata jaka, a cikin jakar ta zuba duk tarkacen kayan Sayyid. Ajiyar zuciya ta ts yi, da tayi wannan dabarar ta Ιoye su. Haka kurum take jin kayan na buΖatar sirri.
Ta nemi guri ta kwanta tana sauke numfashi a hankali, tana tunanin yadda rayuwa ke ta jujjuyata.
*****
Shukura na zaune a Ιakinta tamkar zuciyarta za ta yi bindiga ta fito, Sagir ya buΙe Ζofa ya shigo Ιakin. Kallo Ιaya ta yi masa ta sunkuyar da kai. Tuni t yi shirin kwanciya baccinta, sai Ζamshin turare take zubawa.
Ya sha manyan kayansa, hannunsa riΖe da baΖaΖen ledoji. Ya zo ya zauna a kusa da ita, tamkar ta kifa masa mari haka take ji.
"Wai har kin yi shirin kwanciya? Na zata zaku gaisa tukuna sai ki kwanta" Mugun kallon da ta yi masa ya sanya shi haΙiye maganar da ya yi niyyar yi.
"Ga wannan naki ne" Ya yi maganar yana ajiye mata ledojin hannunsa.
Ba ta kalli kayan ba, kuma ba ta motsa ba.
Ya matsa kusa da ita, ya riΖo hannunta, ta fizge hannunta ta haye kan gadon ta kwanta.
Bai ji haushin abin da ta yi masa ba ko kaΙan, ya san idan ba ta son sa ba za ta yi kishinsa ba, sai dai ita ma Yusra tana buΖatarsa tun da tun farko bai kamata ya sake ta saboda larurarta ba.
Ya tashi ya kashe mata fitila, har zai fita ya koma gaban gadon, ya durΖusa daidai fuskarta ya ce "Ki yi mini afuwa Shukura, ban yi haka domin na cutar da ke ba, ko na muzguna miki, dan Allah ki kwantar da hankalinki saboda lafiyarki da abin da yake cikinki" Daga haka ya tashi ya fice. Sai da ya fita sannan ta ba wa hawayen da suka maΖale a Ζirjinta damar zirarowa, zuciyarta ta din ga yi mata Ζuna, tamkar ta tashi ta bar gidan.
Duk da ya fita da damuwar halin da Shukura take ciki, amma bayan wani Ιan lokaci tuni ya manta, suka ci suka Ζoshi da shi da Yusra.
Bayan sun gabatar da salla, sun yi addu'oi, suka yi zamansu kawai su na hira.
Sai gurin Ιaya saura sannan suka tashi suka kwanta.
Yadda Sagir yake murna da kasancewa da Yusra, ko aurensu na fari bai yi haka ba, tuni wani nannauyan bacci ya yi awon gaba da su, daga shi har ita.
Shukura kuwa yadda ta ga rana haka ta ga dare, ga wani irin zafi da ya addabe ta duk da na'urar sanyaya Ιaki da ke cikin Ιakin.
Washegari sai Ζarfe sha Ιaya na safe ya shiga Ιakin Shukura.
Idonta kawai ya kalla ya ga alamun rashin bacci a tattare da idanunta, sun yi jawur sun kumbura.
"Oum Haidar" ya kira sunanta, yana zama a kan gadon, tana shan tea.
"Ina kwana" ta faΙa a taΖaice.
Idanunsa ya sauka a kan ledar da ya kawo mata, babu alamar ko taΙa ledar ta yi.
"Shukura me yake damunki ne haka? Na kawo abu ko taΙawa ba ki yi ba, kin yi bacci makuwa"
"Sagir, dan Allah ka tashi ka bani guri, ni bana buΖatarka a kusa da ni, kaΙaici nake so"
"Ni ki ke cewa na fita na baki guri?" Ya yi maganar yana nuna kansa.
ΖoΖarin mayar da hawayen da ke shirin zubo mata take yi, amma abu ya gagara kawai ya fara zubowa ba tare da ta shirya hakan ba.
Jikinsa ya yi sanyi, ganin yadda take kuka sosai da sosai.
Cikin kwantar da murya, yake ΖoΖarin rarrashinta, amma ta tashi ta shige banΙaki ta bar shi a gurin.
Ya yi shiru ya rasa abin da yake yi masa daΙi, shi babbar damuwarsa ma cikin da take Ιauke da shi, ga matsalarta ta hawan jini.
*****
Tamkar bayi haka su Nana suke aiki, kullum za a Ιaukkosu daga wancan gidan da Asal take, a kawo su nan su wuni su na aiki. Har mamaki take yi wannan mutanen su kuwa har su nawa ne, dan kamar har da almubazzaranci a cikin lamarin.
Sai dai kowa cikin kaffa-kaffa yake aikin tare da fatan kar wani abu ya biyo baya da za a kama su da laifi.
Kwana na uku, wanda ranar suka dafa normal Abinci, sauran kwanakin kayan snacks ne suka din ga yi. Duk cikin su Nana ce 'yar Nigeria, sauran duk 'yan Nijar ne, sai dai galibinsu baΖaΖen buzaye ne.
Sai da suka kammala aikin, aka ba su wasu kaya fararen dogwayen riguna, da rigar girki, aka saka su kai Abincin wani Ιaki.
Katafaren Ιakina da dogon tebur, an gyara shi sai tashin Ζamshi yake yi. Sai dai gabanta ya yi mummunan faΙuwa da jin irin Ζamshin da yake tashi a Ιakin.
Take jikinta ya hau rawa, har ta nemi ta kifar da abin da ta Ιaukko.
Ta Ιaga kanta a hankali ta kalli jerin manyan frames Ιin da ke Ιakin, sai dai mutanen jikin hotunan, dukkaninsu fuskokinsu a rufe yake, ba ta iya gane kowa daga cikin su ba.
"Ke Nana ki kai mana kin ja kin tsaya" Nana ta jinjina kai jiki a sanyaye ta Ζarasa gaban teburin. Ta ajiye kayan, ta Ιaga kai ta kalli yadda ginin Ιakin yake da matuΖar tsayi.
Jiki a sanyaye ta ci gaba da kai komo, su na shirya abincin.
Bayan sun shaΖe teburin da uban kayan Abinci, aka ba su umarnin su tsaya kar wanda ya fita.
Su na tsaye Nana ta kalli agogon Ιakin, Ζarfe goma na dare.
Wani Ζaton mutum ya shigo, ya kalli gurin da yadda aka shirya teburin, ya kalli su Nana ya ce "WaΙanan ne suka yi girkin?"
Balaraba wadda ita ce ta jagoranci su Nana gurin girke-girken ta risuna ta ce "Eh su ne ranka ya daΙe"
"Wace ce wannan? Na ga kamar ba tamu ba ce" Ya yi maganar yana nuna Nana, da gaba Ιaya rabin hankalinta ba ya jikinta.
Balaraba ta ce "Gimbiya Asal ce ta zaΙo ta, ta saka ta a cikin masu girkin"
Ya yi shiru yana kallon Nana, daga bisani ya jinjina kai ya kalli Balaraba ya ce "Ki je, su su tsaya" Ta jinjina kai ta fice.
Wata Ζofa aka buΙe, wani matashi ya shigo fuskarsa Ιauke da murmushi, gaban Nana ya yi mummunar faΙuwa, dogo ne sanye da farar jallabiya ya Ιaura hirami a kansa, ba dan ta yi wa Sayyid kyakykywan sani ba, za ta iya cewa shi ne. Ζirjinta ya tsananta bugawa, sai dai kafin ta daidaita nutsuwarta, wani ma ya biyo bayansa, shi ma dai kamarsa Ιaya da Sayyid Ιin.
Tunani ta fara yi ko Giyaz da Ζaisar ne suka fara yi mata gizo suke yi mata wasa da tunani.
Ζaya bayan Ιaya suka din ga shigowa, sai da ta Ζirga mutum biyar cif, biyu kamar su Ιaya sak, sauran ukun kuma su na kama amma ba sak da Sayyid ba. Duk suka jeru a kan kujerun teburin nan. Sai dai babbar kujera babu kowa a kai, kujerun gefe da gefen kujerar ma babu kowa a kai.
Ζaya daga cikin su ya ce "Ko waye zai hau wannan kujerar?" Ya yi maganar yana nuna Ιaya daga kujerun da babu kowa a kai.
"Wannan karon dai za mu ji me Sultan zai ce mana a kan maganar"
"Nima dai abin da nake son ji kenan, magana ta gama cika gari ba a san inda yake ba, ana ma tunanin ko ya mutu suke Ιoyewa"
Nana ji ta yi ana busar sarewa a Ζofar bayan su, gaba Ιaya suka ja gefe domin bayar da hanya.
Wani dattijo ne fari sol, mai dogon gemu ya shigo jallabiyarsa baΖa, ya lulluΙe kansa da hiraminsa.
Gaba Ιaya ta ga abokan aikinta sun rikice, duk sun sunkuyar da kansu Ζasa, Nana kuma ta yi masa Ζuri da ido. Sai dai ba shi take kallo ba, ji take tamkar numfashinta ya Ιauke, kamar ba a cikin duniya take ba, duniyoyin da Ζaisar ya saba kaita ne ya caza mata kai, banda haka wani irin mummunan gizo ne wannan?.
Gaba Ιaya matasan suka miΖe tsaye, cikin matsanancin mamaki suna kallon na bayan dattijon.
Tamkar yana tausayin Ζasar haka yake taka ta, yana Ιan yin rangaji kaΙan, sassanyan Ζamshin turaren sa da ko a mafarki ta ji shi tana tantancewa ya karaΙe ilahirin gurin, fiye da Ζamshin turarukan da ke tashi a gurin.
Ta kusa da ita ce ta ja hannunta da Ζarfi, saboda yadda ta tsare shi da idanunta ko Ζiftawa ba ta yi.
Ya zo zai gifta ta, amma ko gurin da suke bai kalla ba, Ιaya bayan Ιaya suka din ga rungume shi, cike da murnar da wasu har zuci, wasu kuma iya ta fuska ce. Ta ga ya zauna a kan kujerar da ake tababar wa zai zauna a kai kafin ya shigo.
Abdou ya ce "Kun yi mamaki ko? Ba ku yi zaton ganinsa ba?"
Ζaya daga cikin su ya ce "Gaskiya ne"
Sultan ya yi murmushi ya ce "Kamar dai yadda na gaya muku a baya, Imam Hammad yana Faransa neman lafiya, bayan tsawon wannan lokacin, yau ya kasance tare da mu a liyafarmu ta Ζarshen shekara, dama wannan ne bazatar da na ce zan yi muku"
Nana ta kalli hotunan nan, sai ta yanzu hotunan babu rawani, kowa hoton fuskarsa ce. Ta tsayar da idonta a kan hotonsa da aka rubuta Imam Hammad Jalal Agadez. A take ta tuna da sunan gidan cin abinci da ta yi wa su Al Hussain aiki. H.J Agadez.
Sunan rukunin gidajen da ta fara zama da Asal shi ma sunan da ke jikin symbol Ιin unguwar kenan. H.J Agadez.
Duk surutun da ake yi, da murnar ya dawo, yana Ζame a kan kujera, fuskarsa babu yabo babu fallasa.
Sai daga bisani ya saka hannunsa Ιaya a kan Ζirjinsa ya risunar da kansa ya ce musu "Merci(Na gode)
Duk da a hankali ya furta, amma ko cikin murya dubu Nana ba za ta gaza tantance ta Sayyid ba.
Abduou ya kalli su Nana, ya kalli mutumin Ιazu da yake tambayar wace ce "Guda biyu daga cikin su ta zo ta ΙanΙana Abincin nan"
Mutumin ya Ζare musu kallo, ya nuna Nana ya nuna wata ya ce su je su ci kafin a ci.
Nana ba ta san a yadda take iya Ιaga Ζafafuwanta ba, saboda ba ta jin su a jikinta, zuciyarta kuwa kamar za ta tarwatse saboda bugun da take yi fiye kima. A hankali ta Ζarasa gaban teburin. Ζayar ta din ga bubbuΙe Abincin, ta fara ΙanΙanawa.
"Ke kina da gaskiya kuwa? Ki ΙanΙana aka ce?" Abduou ya yi mata maganar cikin tsawa.
Rikicewa ta yi gaba Ιaya, ya Ιaga idonsa ya kalli inda jikinta yake rawa, suka yi ido huΙu, ya kawar da kansa yana mamakin yadda take a ruΙe.
Ta Ιebo shinkafa a cokali, amma hannunta karkarwa kawai yake yi.
Sultan ya ce mata "Kina lafiya kuwa?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
Sultan ya ce "Na fuskanci a tsorace take ne kawai, a kaita ta je ta huta, wataΖila mun yi mata kwarjini ne"
Aka saka Nana a gaba aka fitar da ita daga gurin.
Fitarsu ke da wuya, jikin Nana ya din ga wata irin kyarma, haΖoranta na haΙuwa da juna, wani irin jiri ya din ga kwasarta.
Balaraba ta nufo su da sauri, ganin Nana na dafa bango.
Ya kalli Balaraba ya ce "Maza ki kaita ta huta, wataΖila ta yi aiki da yawa ne ta gaji, gaba Ιaya ta rikice, a kirawo likita kuma ya duba ta.
*****
A hankali Nana ta yi juyi, ta buΙe idonta ta ganta a Ιakin da take kwana.
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, da ta tabbatar da mafarki ta yi ba gaskiya ba ne abin da ya faru.
Hamdala ta yi ta ce "Ni dai na san mafarki ne da ma, dan babu yadda za ayi Sayyid ya ganni ya kasa kula ni, ya nuna kamar bai sanni ba. To wannan idan gaskiya ne ma, ta ina zan fara bayanin ni matarsa ce a yarda da ni? Mutumin da na ji ana batun ya daΙe a faransa yana jinya, anya ma Sayyid Ιina ne? Tun da dai mafarki ne duk da sauΖi.
Sallama aka yi a Ιakin, ta ga Balaraba ta shigo Ιakin. Ta ce "Kin tashi?"
Nana ta yi shiru tana kallonta.
"Ina ga aiki da ki ka sha a kwanakin nan ne, ya sanya ki ka gaji zazzaΙi ya kama ki, Likita ya ce a bari ki huta sosai da sosai. Gimbiya Asal ta ce a baki hutu na kwana uku ki warware kan ki koma bakin aiki."
Nana ta jinjina kai kawai, tana kokawa da ΖwaΖwalwarta, domin ta tabattar gaske ne, ko kuwa dai mafarkin ne? Ta tashi ta yi alwala ta yi salla, sai dai gaba Ιaya jikinta ciwo yake yi mata, ga matsanancin ciwon kai da jiri da take ji, dan haka ta nemi guri ta sake kwanciya.
*****
Jamila ta Ιauki jakarta Ιauke da wannan tarkacen da take kira da tarkacen jaraba, ta fita waje, ta samu ta sayo fetur a 'yar jarka, ta samu guri ta zuba musu fetur Ιin ta kunna musu ashana ta Ζone su.
Ta tashi tana kallon yadda suka din ga ci da wuta, ta bar gurin.
Kai tsaye ta tari abin hawa ta tafi gidan Hajiya Sa'a.
Hajiyar ta yi iya ΖoΖarinta gurin Ιoye jin haushin Jamila da take yi, ta karΙe ta hannu bibbiyu har ta taya ta lissafin kuΙin kasuwancinta da kuma kayan da take da su a Ζasa.
Bayan sun kammala ta ce "Ni kuwa Jamila, yaya batun Ζungiya wa za ki bayar ne?"
Jiki a sanyaye ta ce "Haryanzu ban gama tunani ba ne ba"
"Tsoron dai ki ke ji haryanzun ko?"
"A'a na rage ji"
"To ki yi ki hanzarta ki yi abin da yakamata amma kin tsaya. Ni kalli nawa nan na shirya komai aiwatar wa kawai ya rage mini, sai na je gidan zan yi, na sake bayar da Ιan Fatuhu"
Jamila ta kalli drower da Hajjya Sa'a ta janyo, tana nuna mata 'yar tsanar nan.
Jamila ta ce "To idan ban kai kowa ba, akwai wani abu da zai faru ne?"
Ta ce "Au da kara zube za ki zauna ki Ζi bin umarnin Ζungiya? To idan ba ki kai kowa ba, jininki aljanin zan shanye ki mutu" Cikin Jamila ya yi wata irin Ζara bayan tuna ta Ζona kayan. A tunaninta shikenan ta huta sun rabu.
A ranta ta ce "Wannan wane irin bala'i ne na jefa kaina a ciki, Ubangiji Allah ka kawo mini agaji na rabu da wannan masifar.
*****
Fafur Nana ta Ζi yadda zuciyarta ta amince abin da ya faru gaskiya ne ba mafarki ba, saboda ta riga ta saba da irin wannan cazan kan da Ζaisar ya kan yi mata wasu lokutan, har ta gaza banbance abin da yake zahiri da kuma mafarki.
Su na Ιakin girki su na ta Ιorawa da saukewa, ta kalli shugabar su ta ce "Dan Allah a gidan nan, babu yadda zan yi na samu waya, ina son na kira gida ne, na ji halin da yarona yake ciki"
Balaraba ba ta bata amsa ba, ta ji Muryar Asal ta ce "Babu wannan damar, sai dai idan kina buΖata ki zo gurina ki karΙi wayar ki kira"
Nana ta Ιan yi shiru sai kuma ta girgiza kai ta ce "A'a ki bar shi na gode"
"Me yasa ki ka ce haka? Kina tunanin wani abu a ranki ne?"
"Bana tunanin komai, kawai dai na fasa ne"
Ta yi murmushi ta ce "Shikenan, ga saΖo can daga gidan Sultan, tukuicin aikin da ku ka yi na girki"
Balaraba ta risuna tana yi wa Asal magana da yarensu, Nana kuma ta cigaba da aikinta, tana sane ta cewa Asal ba ta so, dan ba ta gama gane ina Asal Ιin ta saka gaba ba, da kuma cikakkiyar manufarta a kanta ba. Tana tsoron ta yi amfani da wata dama da za ta samu ta cutar da ita.
Dogwayen riguna na alfarma Nana ta samu, guda uku da kuΙi. Ta yi murna sosai da kayan, saboda rigunan na alfarma ne.
Katafaren Ιakin bacci ne, mai Ιauke da kayan alatun more rayuwa irin na masu mulki.
Duhun dare ne, sai dai hasken fitilun Ιakin ya gauraye ko ina, kai ba ka ce dare ne ba.
Yana zaune a gefen gadon, tare da dattijon. Cikin kamala dattijon ya ce "Imam, ina Ζara yi maka gargaΙi da jan kunne a kan ka Ζara kula da kan ka. Kar ka Ιauka kowane murmushi ne na soyayya, wani murmushin na babu yadda aka iya da kai ne. Kar ka kuskura ka faΙi wani abu da zai rusa shirinmu, mun Ιoye abubuwa da dama a game da kai, duk abin da baka fahimta ba, ka tambaye ni, kar ka wani ya buΖaci sanin wani abu daga gare ka, ka sanar masa kawai jinya ka yi tsawon wannan lokacin.
"Abii"
"Na'am abin Ζaunata" Imam Hammad ya yi murmushi ya ce "Me ka ke Ιoye mini ne, akwai abubuwan da suka hargitse a rayuwata, tsawon wani lokaci na Ιauka ina jinya ba a hayyacina ba?"
"Ka na ji na? Haryanzu ba ka warke ba, ka na buΖatar hutu mussaman a ΖwaΖwalwarka, kar ka takurawa kanka da tunanin abubuwan da suka faru. Jita-jitar da ake yaΙawa a kan ka, da surutai daban-daban shi ne dalilin da ya sanya muka dawo da kai Ζasar nan, a shaida dai kana raye, cikin Ζoshin lafiya"
"Mahaukaci ne ni kenan? Tun da ina iya tuna yadda ciwon nawa ya fara, amma ban san yaya ya Ζare ba"
Sultan ya tsuke fuska ya ce "Ya ishe ka haka. Kar ka kuskura na ji labarin nan ya fita, waye ya ce kai mahaukaci ne? Larurar zuciya ce take damun ka, babu daΙi babu Ζari daga haka. Babu wata larurar hauka a tattare da kai".
"Amma Sultan ko zaka saka na Ιoye wa duniya, yakamata na san matsayin lafiyata...
"Hammad!" Tilas ya ja bakinsa ya yi shiru, ganin yadda ya fusata Sultan Ιin.
*****
Tun da garin Allah ya waye, Nana take jin faΙuwar gaba da matsananciyar fargaba, ga sanyin da take jin yana ratasa ta, ta san ba na lafiya ne kawai ba. Dan haka ta Ιaura alwala take ta addu'a.
Bayan fitowarta ta cika da mamakin ganin yadda ma'aikatan gidan, suke ta aiki tuΖuru suke gyara gidan duk da ko ina a gyare yake.
Ko ta ina Ζamshin turaruka ne ke tashi daban-daban. Har sun so su yi yawa ma.
Ζangaren da take aiki, sai azalzalarsu ake yi, ta fahimci dai wani baΖo ne mai muhimmanci zai sauka a gidan.
Har mamaki take yi yadda suke ba wa abinci muhimmanci, baΖo Ιaya sai a saka a yi masa abinci biyar, kuma duk da an san ba iya cinyewa zai yi ba.
Ta fito kenan ta ci karo da Asal, ta sanya zani da doguwar riga na shadda baΖar shadda, kanta babu Ιan kwali, hannayenta da yatsunta duk zobunan gwal ne, uwa uba wata irin sarΖa da ta saka ta zinari tun daga wuyanta har cikinta. Gashinta ya sha ado, ta sake shi har kafaΙarta, shi ma ta sanya masa wata siririyar sarΖa da ta kwanto har goshinta.
Duk hassadar mai hassada babu yadda za a yi ka kalle ta ka kushe ta, jawur da ita a cikin baΖar shaddar sai ta haska shaddar.
Ita dai Nana tun da ta zo gidan, ba ta taΙa ganin Asal da miji ko 'yan uwa ba, sai tarkacen Ζawayenta, su ma a wancan gidan ne, wannan gidan ba sa biyo ta su zo. Kuma duk abin nan Nana ba ta taΙa bin diddigi ta ji wace ce Asal ba, me yasa kuma take rayuwa a gidan daga ita sai masu yi mata hidima ba.
Da daddare Nana ta ji su Balaraba su na yare, su na faΙin sunan Imam, lokaci lokaci su na haΙa wa da Hausa, sai dai ta manta a inda ta taΙa jin Imam Ιin.
Babban abin da ya Ιaurewa Imam kai, bai wuce yadda a faransa yake jin sa garau, ba shi da wata damuwa ko wani ciwo da yake ji ba. Amma tun da ya sanya Ζafarsa a Agadez tsawon kwanaki huΙu, ko sau Ιaya zuciyarsa ba ta saurara da bugun da take yi cikin sauri babu ΖaΖΖautawa ba.
Nana na ta kai komo a kitchen, ta kammala duk wani aiki da ya shafe ta, tana shirin tafiya ta je ta kwanta. Balaraba ta ce "Saurin me ki ke yi ne Nana?"
"Ina son na je na yi wanka na kwanta ne"
"Ki je ki yi wankan, nan da mintuna talatin za ki kai wa Gimbiya Asal bunu da madara sashinta"
Har Nana za ta yi magana, dan ba ta shiga sashin Asal sai sau Ιaya, ta taΙa zuwa idan sun yi girki akwai waΙanda suke kaΙai suke iya zuwa sashen su kai. Ta fasa maganar ta ce "To"
A gurguje Nana ta kintsa, ta koma ta Ιauki kayan za ta yi gaba, Balaraba ta ce "Ai ba sashinta za a kai ba, Ramata raka ta"
Ramata ta kalli Nana ta yi mata kallon banza, ta Ιan kwaΙe baki sannan ta yi gaba Nana ta bi bayanta.
Duk yadda Nana ta so sarrafa kanta ta kasa, ta Ιaga kai ta din ga kallon Ζawataccen gurin tare da jinjina yadda masu gidan suka Ζware a iya almubazzaranci. Dan ba za ta kira shi ado ba kawai sai dai almubazzaranci.
Tana saka Ζafarta a cikin falon, ta ji tamkar an jona mata shocking, saboda rawar da jikinta ya yi, sai da farantin hannunta ma ya girgiza tamkar zai Ιare. Ramata ta kalle ta, ta yi tsaki kawai.
Nana ta ajiye kayan a hankali a kan carfet Ιin Ιakin.
Bayan ta ajiye ta yi taku huΙu zuwa biyar, ta ji yadda adadin sanyin da take ji yana Ζara yawa. Ta sauke idanunta a kan Ζaton frame da hotonsa a jiki. DanΖarewa ta yi a guri Ιaya, ta kasa motsa ko da Ζafarta.
Taku ta fara ji a bayanta, ana tahowa, muryar Asal ta ji tana magana da faransanci cikin shagwaΙa.
Ζan ja ya yi ya tsaya, jin yadda jikinsa ya yi wata girgiza.
"Lafiya dai ko?"
Ya jinjina mata kai alamar eh.
"Amm me ku ke yi a tsaye a gurin nan ne?"
Ramata ta ce "Abinci muka kawo"
"Waye ya yi?"
Ta nuna Nana da ba ta juyo ba.
"Zo" ta kira Nana sai dai Nanan ta Ζame ba ta juyo ba. A wulaΖance Ramata ta taΙa ta ta ce "Ana yi miki magana"
"Tana ji na rainin hankalin za ta yi mini"
Sannu a hankali Nana ta juyo, idonsa na kan wayar hannunsa.
Yanzu ta tabattar da mafarki ta yi ba, Sayyid ta gani, sai dai ganinsa bai razana ta ya kiΙimata ba, kamar yadda alamu suka nuna Asal matarsa ce ba.
Ta sunkuyar da kanta Ζasa, tana jan Ζafafuwanta a hankali.
"Me ya same ki ne?"
Ta girgiza kai alamar ba komai.
"Ki yi mini magana kina girgiza kai kawai"
"Ba ni da lafiya"
Asal ta ja tsaki ta ce "Je ki kar ki Ιata mini rai"
Ta zuba masa shayin a kofi, ta zuba masa madara, ya Ιauka a hankali ya kai bakinsa yana sha.
Nana kuwa a Ιakinta, gaba Ιaya ta burkice, tamkar za ta yi hauka ta ce "Dama abin da ka ke gargaΙina a kai kenan Ζaisar? Sayyid me yasa za ka yi mini haka, dama ka na da wata matar ka aure ni? Yanzu ka na nufin ka manta ni, Sayyid anya alΖawari ya ce haka? Na haΖura zan Ιauki Ιa na na koma gida, ganinka da wata kawai ya isa ya yi ajalina. WataΖila alhakin iyayena ne ma da na taho ba da izininsu ba. Yadda ka ke a cikin daular nan, yaya za a yi na ce ina da alaΖa da kai ma a yarda da ni?" Ka ce Ruhina da naka su na rayuwa a tare, kowannenmu yana Ιauke da ruhin Ιan uwansa, ni na yi dakon soyayyarka ashe ka na da matar da ta fi ni komai" Ta yi maganar cikin matsanancin kuka tamkar za ta fita daga hayyacinta.
Yana tsaye yana jin yadda ruwan yake ratsa shi daga cikin gashin kansa zuwa jikinsa.
Wani irin zafi yake ji a cikin ΖwaΖwalwarsa, tamkar kansa zai tarwatse.
Karo biyu yana jin jikinsa ya yi girgiza.
Ya yi wankan ya lulluΙo jikinsa da towel.
Asal ta sha kwalliya cikin baΖaΖen kaya na bacci.
Ta nufo shi tana rangwaΙa, ta cire towel Ιin da ya lulluΙa da shi. Ya Ιan lumshe idanunsa saboda Ζamshin turaren da Asal take yi mai jan hankali.
Ta shige jikinsa ta rungume shi, ta ce "Na yi kewarka sosai Imam"
"Nima ina jin kewar abin da ban san mene ba, bayan kewarki da na yi"
"Akwai abin da ya fi ni muhimmanci dama, da har ka ke kewarsa fiye da ni?"
"A'a ban ma san mene ba, kawai dai ina jin akwai wani abu da ba daidai ba"
Ya yi maganar yana shafa gefen wuyanta, yana son tambayarta wace ce yarinyar nan, amma ya haΙiye ya fasa.
Ya fara ΖoΖarin sumbatar ta, sai dai ya ja da baya da sauri yana dafe kansa, da yake jin wani sauti mara daΙin ji a cikin sa.
"Imam jikin ne dai?"
Bai yi magana ba, ya hau kan gadon ya kwanta ya lumshe idanunsa.
Washegari da safe, idanun Nana sun kumbura suntum, saboda ba ta rintsa ba ko kaΙan.
Ta saba da wuri take tashi, ta fara gudanar da aikinta, amma sai da aka zo aka kira ta, ta ce ba za ta yi aikin ba.
Bayan mintuna talatin sai ga Asal a Ιakin, ta kalli Nana a wulaΖance cikin isa da gadara ta ce "Ki ka ce ba za ki yi aiki ba yau? Saboda gidanki ne ko zaman kan ki ki ke yi a gidan? An kai wa Imam shayi ya Ζi sha ya ce ba irin na jiya ba ne"
"Eh ba zan yi girki ba, kuma barin gidan nan zan yi, na gaji da wannan aikin, zan je na ga yarona"
Asal ta yi dariya ta ce "Ai kuma Ζarya ki ke yi. Na Ιaukko ki gidan nan saboda nesanta mijin da waΙanann munafukan hadiman, na kawo bare da baki san komai a kan harkar gidan mulki ba. Kuma ba kya cikin kalar matan da za su iya Ιaukar hankalinsa. Dan haka na kawo ki ne dan ki din ga kula da abin da Imam zai ci aikin da ki ka zo yi gidan nan kenan.
Nana ta yi wa Asal wani irin kallo mai cike da tsana, ji take tamkar ta kama Asal ta yi ta jibgarta har sai ta ji ta huce.
"Gimbiya Asal, ai an bar kari tun ran tubani. Ba zan yi girki ba sai dai yunwa ta kashe Imam Ιin, ke da yake aure idan ba za ki girka masa ba, to kar Allah ya sa ci, sai na bar gidan nan ba zan zauna ba" Ta yi maganar cikin Ιaga murya da zazzaro ido.
Asal ta yi taku biyu, ta hankaΙa Nana baya ta ce "Ki kiyaye harshenki a kan abin da zai din ga fitowa daga bakinki, a kan mijina. Biyan buΖatata ce kawai ta sanya nake Ζyale ki, ki daina ΖoΖarin Ζetare iyaka. Tafiya kuma ga hanya nan maza ki tafi mu gani, idan kina tunanin da ka na kawo ki gidan nan na ajiye"
Ayshercool
08081012143
Littafin kuΙi ne, 1k ne via 0069685771
Aisha Adam stanbic bank ku tura mini hakkina kan ku karanta.
72
Sai da Nene ta tabattar Nana ta Ιan nutsu, sannan suka kwanta.
Washegari Nene ta fita, ta bar Nana a gidan tare da Muhsin. Bayan ta dawo daga gurin sama'arta ta cewa Nana, yakamata ta je ta Ιan sai abubuwan da za ta buΖata saboda tafiyar da za ta yi da nisa, kuma ba su san yaya tsarin aikin can Ιin yake ba.
Nana ta ce "Ni babu abin da nake buΖata, ki bani wani abin na riΖe a hannuna, sauran kuΙin kuma ki riΖe saboda kula da Muhsin na s...
"Biyana za ki yi kenan dan na riΖe miki Muhsin?" Nene ta katse ta.
"Allah ya baki haΖuri, ba haka nake nufi na, na ga dole Ιan abubuwan buΖatunsa duk ke ki ke yi masa Nene, tun da ga kuΙi sun"
"KuΙinki ba su isa su saka na riΖe miki Ιa ba ko?"
Nana ta ce "Na sani, ai shi ya sanya na ce ki yi haΖuri.
Nene ta ce "Ba zan yi haΖurin ba sai na gama, kin iya kunna ni da na fara faΙa ki hau bani haΖuri, wato in ci kaina to sai na idar"
Nana ta yi mata shiru ta yi faΙanta ta gama.
Washegari Nene ta saka Nana a gaba suka je kasuwa, ta sata ta yi sayayyar kayan sakawa da na Ιan shafe-shafe, ta yi wa Muhsin sayayyar kayan sakawa da pampers. Babu yadda ba ta yi da Nene ba ta Ιauki wani abin ta ce ba za ta Ιauka na.
Nana ta haΙe rai ta ce "Eh dama ba ki Ιauke ni 'yarki ba, shi ya sanya duk abin da zan yi miki ba kya karΙa"
"Ni za ki yi wa wayo, na ji ban Ιauke ki 'yar ba, ni ga Ιana nan" tayi maganar tana shafo Muhsin da ke bayanta. Da Ζyar sai da suka kai ruwan rana Sannan Nene ta karΙi abin da Nana ta saya mata.
Sai dai kan su bar kasuwar har sun shirya. Nana ta ce "Nene kin ce mini ki na da Ιa, amma ban taΙa ganinsa ya zo ba, ba ya zuwa ya gan ki ne?"
Nene ta ce "Kamar ban damu da shi ba ko?"
"A'a kawai dai tambaya na yi "
"Yana can Nigeria"
"To me yake yi a Nigeria ba ya zuwa inda ki ke?"
"Sana'a yake yi, ai ya zo ki na can gurin aiki"
Duk da Nana ba ta gamsu da amsoshin da Nene ta ba ta ba, amma ta basar ta ce "Allah sarki, Allah bai yi zamu haΙu ba".
Haka suka ci gaba da hira suka koma gida, Nana ji take yi tamkar ta Ιauke Ιanta ta tafi da shi.
Gidansu Ashura Nana ta je, ta samu keke ta ΙiΙΙinka kayan da ta sayo, ta sake haΙa jakarta ta Ιauki muhimman abubuwa a kayanta.
Duk da a Ιaki Nene take rufe mata su, ba ta taΙa ganin alamar Nenen tana yi bincike a cikin kayan ba.
*****
Ko da Jamila suka dawo Kano, fakar ido ta yi ta jefar da wannan tarkacen da aka ba ta aka ce da su za ta kai jini.
Gaba Ιaya da ta tuna abin tsigar jikinta take tashi, ta ji ciwon kanta da zazzaΙi ya Ζaru.
Gefe guda kuma hankalinta yana kan yadda ta ji Hajiya Sa'a tana faΙin za ta sake bayar da Ιan Alhaji Fatuhu. Ta jinjina rashin imaninta mutumin da yake fama da karayar arziki ga ciwo, ya rasa wancan Ιan kuma a sake bayar da wannan kamar ba a yi masa adalci ba. Sai dai gaba Ιaya ba ta san ta ina za ta fara ba, tana jin a ranta kamar yakamata ta tseratar da yaron.
A gida ta tarar da Gaddafi, ta sha jinin jikinta da irin mugun kallon da ya yi mata, amma bai ce mata uffan ba. Suwaiba ma Ζura mata ido ta yi tana bin ta da kallo.
Ta tsuke fuska ta harsri Suwaiba, sai dai Suwaiba ta tuntsure da dariya, kamar za ta shiΙe. Jamila ta yi tsaki ta shige Ιakinsu.
Ba ta tarar da Mama a gida ba, haka ma Baba.
*****
Shiru Alhaji Zailani ya yi yana kallon Doctor Sharif yana sauraren shi, har ya gama karanta masa abin da Shukura ta je ta same shi ta yi masa.
Ya ja numfashi ya ce "Shikenan, aikinka ya yi kyau Sharif, na kuma gode sosai da sosai da ka ke sanar da ni wannan abubuwan, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi. Ka je za ka ga saΖo" Sharif ya yinΖura ya tashi ya tafi.
Alhaji Zailani ya numfasa a fili ya ce "Duk da kasancewar ki 'ya mafi soyuwa a cikin zuciyata, an zo gaΙar da ki ka Ζetare layin da bai kamata ki Ζetare ba, kina ΖoΖarin tono abin da zai wargaza zaman lafiya da kwanciyar hankali, dan haka ki yi haΖuri da duk matakin da zan Ιauka a kan ki.
*****
Nana ta jingina da jikin gilashin motar, tana kallon tulin yashin saharar da ya mamaye gurin. Fili fetal hagu da dama duk yashi ne. Cikin yanayi mai kama da bacci take ganin abubuwan da ta din ga gani a bacci cikin saharar.
Ko a yanzun ma su na tafe Sayyid kawai take gani a kan raΖumi yana biye da su a cikin saharar.
Kamar an taΙa ta ta Ιan yi firgigit ta kalli gurin, haryanzu a titin da ya ratsa saharar suke tafiya, zuciyarta ta yi wani irin bugu da sai da ta dafe Ζirjinta.
Sanyi ta fara yana ratsa ta har cikin Ζashinta, ta Ιaga ido tana Ιan waige-waige ta ga ta ina za ta gano Ζaisar ko wata baΖuwar halittar da ba jinsin mutane ba, sai dai ba ta ga komai ba.
Ta sake jingina da jikin motar tana ta karanto duk addu'ar da ta zo bakinta. A haka har suka shigo cikin gari sosai da sosai.
Nana na son karanta Symbols Ιin da take gani, amma ba komai take iya fahimta ba saboda rubutun French. Babbar hanya mai Ιauke da Ζaton gate ta ciki suka wuce.
Ba Ζaramar gajiya Nana ta yi ba, saboda azabar nisan tafiyar da suka shawo ba, ba su Ζarasa ba sai bayan magariba. Kewar Ιan ta ta addabi zuciyarta, tunaninta yadda za ta din ga sintirin tsakanin Agadez da MaraΙi a wannan uwar tafiyar kamar ta ya da shege.
Wasu irin gidaje ne manya-manya na alfarma da Ζasaita a cikin gurin.
A Ζofar wani gida direban ya tsaya, ya cewa Nana ta fito sun zo. Haka ta saukko Ζafafuwanta duk sun yi tsami saboda azabar gajiya.
Ya buΙe bayan motar ya Ιaukko Ζatuwar jakar Nana, ya rufe motar, ya yi gaba Nana ta bi shi a baya tana karanto addu'oin da suka sauwwaΖa.
Cikin wani matsakaicin gida suka shiga, gidan ya Ζawatu ya yi kyau sosai da sosai.
A falon gidan ya ajiye wa Nana kayanta ya ce "Ki zauna ki jira a nan"
Nana ta ce "Amma wa zan jira a nan Ιin, ban ga alamar akwai mutane a gidan nan ba"
"Za ki gan su, ni a nan aka yi mini umarnin na kawo ki kawai"
Nana ta yi shiru tana nazari, shi kuma ya juya ya fice.
Nana ta din ga rarraba ido, tana son ta yi salla amma babu wanda za ta tambaya. Harabar gidan ta fita saboda ta ga famfo ta yi alwala, ta dawo falon ta yi salla.
Gajiya ta yi ta koma harabar gidan da kayanta, ta zauna tana rarraba ido.
Can ta ji Ζarar mota, aka buΙe Ζofar wani jami'in tsaro ya shigo ya buΙe gate Ιin, aka shigo da wata haΙaΙΙiyar mota aka yi parking Ιin ta.
Aka buΙe Ζofar motar, sai ga Asal ta fito sanye cikin doguwar riga, ta Ιaura mayafin a wuyanta, kanta babu Ιankwali. Har bakin Ζofar shiga suka rakata, ta wuce Nana ta shige ciki kamar ba ta gan ta ba. Nanan ma ta yi zamanta ba ta shiga ba, ta jingina da jikin kayanta taka addu'a saboda a gajiye take matuΖa, ga uwar yunwa tana ji ga tulin damuwa.
Sannu a hankali take tuna yadda ta shigo Ζasar Nijar ba ta san kowa ba, da yadda ta din ga raragefe har zuwa kan zamanta da Nene. Sai ta tsinci kanta da tattara su baki Ιaya tana yi musu addu'a, da fatan dacewa a Duniya da lahira.
Ba ta san iya adadin lokacin da ta Ιauka a gurin ba, ta ji muryar Asal a kanta.
"Wai ke wace irin bagidajiya ce, a Nigeria daga wani Ζauyen ki ke ne?" Nana ta Ιaga kai ta kalle ta.
"Na saka an kawo ki guri, ki shiga ki jira ni kin zauna a waje, na dawo ma kin nemi guri kin zauna ba za ki shigo ba?"
"Ta yaya zan shiga gurin da babu kowa na zauna, ni da ban san ma aikin da ki ka kawo ni na yi miki ba?"
Haushi ya kama Asal, ta ce "To idan kin ga dama ki shigo, idan kuma ba ki ga dama ba, ki yi ta zama a gurin" Ta shige ciki Nana ta bi ta da harara, kamar ba za ta tashi ba, sai kuma ta tashi ta ja kayanta, ta shiga falon ta nemi guri ta zauna a kan kujera. Asal ta saci kallon Nana, da yadda take gudanar da lamarinta cike da Ζarfin hali.
Nana ba ta kula ta ba, ita ma ba ta kula ta ba, Nana ta gaji da zama, ta saukko Ζasa ta miΖe ta kwanta.
Can Asal ta ce mata "Ga kitchen can, akwai abinci"
Daga haka ta tashi ta bar falon.
Nana ta tashi ta shiga kitchen Ιin, ta tarar da Abinci, ta Ιauka ta ci sannan ta Ιan dawo hayyacinta.
A nan falon Nana ta kwana, da Asuba ta yi alwala a harabar gidan, ta koma falon ta yi salla.
Duk wannan abin zuciyarta a cike da zullumin aikin da za ta yi wa Asal.
Da gari ya yi haske, Asal ta fito Nana ta gaishe ta, amma ta yi kamar ba ta ji ba, ta fice ta bar gidan ta bar Nana.
Nana tana nan zaune, aka zo aka ΖwanΖwasa Ζofar falon, ta tashi a Ιan tsorace ta buΙe, wani mutum ya miΖo mata takeaway ya ce "Ga shi nan, aka ce a kawo miki" daga haka ya juya ya tafi.
Nana ba ta sake ganin Asal ba sai dare, ba ta saurari Nana ba still. Ta cika gidan ita da Ζawayenta, suka hau saman bene, suka kunna kaΙe-kaΙe har kusan Ιaya na dare su na abu Ιaya, suka hana Nana bacci.
Sai gefin Asuba suka daina wannan shirirtar, Nana ta din ga mamakin ita Asal zaman kanta take yi ne, ba ta da magabata ko kuwa?
Sai washegari sannan ta saukko Ζasa, a lokacin Ζawayen nata duk sun tafi.
Ta kalli Nana ta ce "Daga yau kar ki Ζara kwanar mini a falo, ga Ιaki can kusa da kitchen, a nan za ki din ga kwana. Na kawo ki ne duk da ba yanzu ne za ki yi aikin naki gaba Ιaya ba, amma za ki din ga yi mini girkin Abinci da ni da Ζawayena, da sauran aikace-aikacen gida.
Abu na farko dalilin da ya sanya na Ιaukko ki, ke ba Ζabilarmu ba ce ba, ba na son saka ido, ba na son surutu
Duk wani abu da za ki ga na yi, ko ina yi babu ruwanki, aikin duk da na saka ki shikaΙai za ki yi mini"
Nana ta yi shiru tana tunani, dama duk wannan abin ba wani branch Ιin za a kai ta aiki ba, wannan zuΖaΖΖiyar za ta yi wa bauta, shi ne har da ci mata mutuncin cewa an yi amfani da kuΙi sai ta yi abin da ake so. Kuma me yasa ba ta zaΙi kowa ba sai ita?.
"Ba kya ji na ne?"
"Na ji"
"Ban gane kin ji ba? Haka zan din ga yi miki magana ki na amsa mini, ke ni fa ba Hasna ba ce ba, dole ki yi mini biyayya ki yi duk abin da nake so".
Nana ji ta yi tamkar ta yi tsaki, ta ce "Amma yanzu fisabilillahi duk faΙin Ζasar nan ki rasa wanda za ki Ιaukko ya yi miki aikatau sai ni. Ni harkar dafa abinci nake yi, amma kin kawo ni nan in din ga yi miki girki da boyi-boyi ba tare da an yi mini bayanin haka ba, ni gaskiya ba a kyauta mini ba"
"Da hakan ki ka dace ai, ko kina ganin kin cancanci wani abin bayan bauta? Idan ba za ki zauna ba ga hanya nan za ki iya tafiya" Ta yi maganar tana miΖewa tsaye.
Har ta yi gaba sai kuma ta tsaya ta ce "Duk wani abu da za ki buΖata akwai shi a kitchen, kina iya dubawa, wanda babu kuma ki sanar mini, shi ma idan ba ki ga dama ba kar ki yi aikin" ta yi gaba ta bar Nana da ta gama Ζulewa.
*****
Gaba Ιaya Shukura ta burkicewa Sagir, ba Ιaga masa hankali ta yi da rigima ba, tattara shi ta yi ta watsar gaja Ιaya take harkokinta, da gaske take ΖoΖarin gano abin da mahaifinta yake Ιoyewa tsawon wannan lokacin da har ya hana Hajiya Amina bincike a kan lafiyarta.
Ga shirin tariyar Yusra Sagir na yi, ga damuwar rashin sakin jiki da shi da Shukura ta yi, ta tattara shi ta watsar.
Ζangarensa ya saka aka gyarawa Yusra, dama ba amfani yake yi da shi ba, aka Ζara gyara shi, aka haΙa gidan gaba Ιaya aka sake yi masa fenti. Daga gaya mata batun dawo da Yusra zuwa gyaran gidan da kawo kayanta, ba a yi sati guda ba, gida ya Ιau harama.
Duk yadda ya so ya lallaΙa Shukura, ta saukko ta din ga saurararsa ta yi burus da shi.
Nana ta shafe sati guda tana gidan Asal, tana yi mata hidima, ta hantare ta ta kyare ta, dandazon Ζawayen da take tarawa ma, su hana ta sukuni da aiki. Nana ta din ga iya ΖoΖarinta, gurin kai zuciyarta nesa, amma abin ya fara isarta.
Tana tsaka da nazarin yadda za ta Ιullowa lamarin, da safe Asal za ta fita ta kalli Nana ta ce "Ki shirya nan da sati Ιaya zamu bar nan, zamu je asalin inda na Ιauke ki ki yi mini aiki a gurin"
Nana ta ce "Ina kenan? Kuma aikin me?
"Idan mun je za ki gani" Ta ba wa Nana amsar a taΖaice.
*****
Jamila tana kwance tana chatting da Abba, bikinsa saura sati biyu.
Hajiya Sa'a tana ta zaginsa da yi masa bala'i, a kan yadda yarinyar take ta Ζorafin ba ya kula ta, waya ma sai dai ita ta kira shi, babu abin da ya yi masa zafi da ita.
Yanzun ma kamar ya yi wa Jamila kuka.
Ita take ta rarrashinsa tana nuna masa babu komai ya yi aurensa kawai.
"Ζanwata ko na yi aure hankalina ba zai kwanta ba, kar ki manta da Ιarnar da ta faru tsakanina da ke, ya zan yi da shi"
Ta ce "Na san kai mutumin kirki ne yayana, hakan ne ya sanya ka ke jin damuwa a kan abin da ya faru, amma ka yi haΖuri ka yi aurenka kawai, ina roΖon Ubangiji Allah ya kawo mini wani mijin"
"A'a ki daina faΙa mini haka, zuciyata tana sosuwa, baki da wani miji sai ni in sha Allah" haka suka kasance tana Ζarfafa masa gwiwa, shi kuma yana rarrashinta.
Ta gama wayar ta ajiye, ta ga Suwaiba ta Ζuro mata ido tamkar ba ta taΙa ganinta ba.
"Meye ki ke kallona, lafiya?" Suwaiba ta yi shiru ba ta bata amsa ba, kuma ba ta yi magana ba.
Jamila ta ja tsaki, tana ΖoΖarin kwanciya, Suwaiba ta ce "Jamila"
"Na'am mene ne?"
"Ki Ιauki saΖonki mana"
Cikin rashin fahimta ta ce "Wane saΖon?"
"Na cikin jakarki"
"Cikin jakata kuma? Mene ne a jakar tawa? Wato bincike ki ke yi mini a jakar ko?"
"A'a ni tuni kawai nake yi miki da saΖonki na cikin jakar"
Jamila ta tashi zaune ta ce "Wai wani saΖon? MiΖo mini jakar dai na gani"
Suwaiba ta ce "A'a ba zan taΙa miki jaka ba"
Jamila ta janyo jakar ta fara buΙewa ta ga abin da Suwaibabta dame ta a kai. Cin karo ta yi da wannan 'yar tsanar da ta riga ta jefar. Saura Ζiris ta kurma ihu, ta rikice gaba Ιaya jikinta ya hau rawa, a tunaninta tun da ta yar shikenan ta rabu da ita.
Suwaiba kuwa ta tuntsure da wata irin mahaukaciyar dariya, ta din ga yi tana ΖyaΖyatawa tana kallon Jamila. Gaba Ιaya Jamila ta kiΙime ta rasa abin da yake yi mata daΙi, gaba Ιaya jikinta ya hau rawa tamkar ta kurma ihu, sannu a hankali kanta ya fara juyawa ta fara gani dishi-dishi, dole ta rufe jakar ta nemi guri ta kwanta.
*****
Alhaji Zailani ya kwana biyu bai je gidan Alhaji Fatuhu ba sai yau. Sai dai ya sha mamakin ganinsa a harabar gidan da sanda yana dogarawa yana tattakawa a hankali, yana tsaye a kan Ζafafuwansa yana kallon yadda Muhsin yake ta gudu a harabar gidan.
Sai da ya aro jarumta sannan ya iya danne abin da ya ji ya taso masa na tashin hankali da mummunan baΖin ciki.
Da Ζyar ya iya washe baki ya ce "Ikon Allah, Abokina kai ne haka nake gani?"
Alhaji Fatuhu ya yi murmushi ya ce "Ka ga ikon Allah ko? Sannu da zuwa Bismillah" ya yi maganar yana nuna masa Ιaya daga kujerun da ke ajiye a gurin.
Alhaji Zailani ya zauna suka Ζara gaisawa
"Bani labari, ya aka yi sauΖi ya samu haka, wani Asibitin ka je ne?"
Alhaji Fatuhu ya ce "A'a na ga an yi na Asibitin ne babu wani ci gaba, Fadila ta zauna ta din ga yi mini bayani, na amince muka fara gwada na islamic, cikin ikon Allah sannu a hankali wannan Ιaurewa da nake ji a jikina ya yi mini sauΖi, wannan gigicewar da nake na ji kamar zan yi hauka shi ma Alhamdillah ina daΙewa ban ji ba, wannan warin ma da nake ji ya ragux
"Amma Fatuhu ya za a yi ka biye wa mace da shirmen ta, ga na Asibiti ana yi kawai ta saka ka fara wani na shirme, sai ka je ka yi abin da za ka kauce wa hanya tukuna?"
"A'a nima na jaddada mata, ta kuma tabattar mini da babu kauce hanya a ciki, kuma nima shaida ne, shi ya sanya ma nake amfani da magungunan kuma ana samun ci gaba"
Alhaji Zailani ya miΖe ya ce "Haka ne, to bari na je dama ina da gurin da zan je na biyo, sauri nake yi"
"Ba zaka tsaya ku gaisa da mutanen gidan ba?"
"Sauri nake yi zan sake dawowa"ya yi maganar yana yin gaba cikin Ζunar rai, ji yake yi tamkar ya kashe Alhaji Fatuhu ya huta, dan shi bai taΙa zaton zai kawo yanzu bai mutu ba.
*****
Al Hussain ne a tsaye ya tsare Hasna da ido, yana yi mata faΙa cikin matsanancin Ιacin rai.
"A kan me za ki yi haka? Dan me za ku yi mata dole, ai ba Ιaukar ta aiki muka yi saboda buΖatar mutum guda ba. Abin da yake cikin yarjejeniya shi ne ta yi wa gidan Abincinmu aiki, idan ma canza gurin aikin ne, wani reshen zamu mayar da ita, amma dan me za ku haΙa kai ku yi mata haka wannan wulaΖanci ne da cin zarafi, kuma ga shi bama 'yar Ζasarmu ba"
"Ni fa Al Hussain na kasa gane maka, ko son yarinyar nan ka ke yi ne? To bari na tuna maka kai Buzu ne, buzun ma farin buzu ka san abin da nake nufi ai, kuma matar aure ce ko bazawara dan ta ce mana tana da Ιa ma"
"Ni ba wannan na tambaye ki ba, dan me Asal za ta yi amfani da Ζarfi da kuΙi ta tursasa mata yin abin da ba ta so, ai ba haka ake rayuwa ba"
"Ai na san za a yi haka, babu bayanin da ban yi mata ba taΖi yadda, ga shi ni yanzu ka zo ka saka ni a gaba da jaraba, sai ka je ka dawo da ita ni ba zan iya ba"
"Ke dai da ki ka yi hakan ki je ki dawo da ita, idan ba haka ba daga ke har ita na rubuta masa abin da ku ka aikata, daida yake da ku"
Ta kwaΙe baki ta ce "Wa ya san ma inda yake, mutumin da ake tunanin ya Ιata babu wanda ya san ma yana raye ko yana mace?"
"Hakan ya baku damar cin karenku babu babbaka daga ke har Asal ko? Yayi muku kyau" Hasna ta fice tana jin haushin masifar da Al Hussain yake ta yi mata, duk yadda ta yi ΖoΖarin hana Asal Ιaukar Nana.
*****
Ana gobe su Nana za su bar wannan gidan, Asal ta sanar da Nana ta shirya washegari za su bar nan.
Ita dai Nana ta sanya wa sarautar Allah ido, rayuwarta ta zama tamkar tamaula daga nan zuwa can, ba ma ta da 'yancin tambayar ko sanin inda za a kaita sai dai inda ta tsinci kanta kawai.
Ta sha aiki ta gama, ta Ιan zauna a falo tana hutawa, sai ga Ιaya daga gayyar Ζawayen Asal ta saukko ta kalli Nana ta ce "Dan Allah ina son shayi"
Nana ta ce "Akwai a kayan Abincin da na girka"
"Shayin kanumfari kawai nake so bana son Shan na girfa"
"Ga gurin dafawar can, idan ki ka je akwai komai, ki dafa ki sha idan kin matsu"
"Ke, kin san wace ce ni ki ke gaya mini haka?"
"Ban san wace ce ke ba, kuma ba na buΖatar sani"
Asal ta saukko tana tambayar lafiya.
Ta gaya mata abin da ya faru, ta kalli Nana ta ce "Wai ke me yasa ba ki da mutunci, ban gaya miki dole ki girmama baΖina ba, mene ne a cikin dafa shayi mintinan nawa ne kin yi kin gama?"
Ta kalli Asal ta ce "Ki yi haΖuri, wallahi ko cokali ba zan iya sake Ιauka ba, yau na bautu a gidan nan ke kin sani, kuma ban taΙa yi miki Ζorafi ba, amma yanzu dai na gaji gaskiya"
Suka juya yare suka yi magana, ba ta san me suka ce ba, ta ga sun koma kan bene.
Washegari da wuri suka Ιau hanya, sai dai ga mammakin Nana, har da rakiyar jami'an tsaro, kuma a wannan karon shigar Shadda Asal ta yi, an yi wa shaddar aiki tun daga sama har Ζasa.
Mota Ιaya suka hau, ta ce Nana ta hau gaba, ita kuma ta hau baya.
Sai da aka kuma wata tafiyar mai nisa, sannan ta ga sun tunkari wani irin ginin Ζasa tamkar ginin ganuwar Kano.
Ginin ya Ζayatar da Nana sosai da sosai.
Jami'an tsaro ne suke gadin Ζatuwar Ζofar gurin, da wasu Buzaye farare tas sanye da rawani.
Nana kamar ta ce a tsaya, ta duba buzayen nan Ιaya bayan Ιaya ko za ta ga Sayyid Ιin ta cikinsu. Sai da motar su ta tsaya, suka sauke glass Ιin motar.
Da Hausa suka gaisa, suka yi mata sannu da zuwa, Ιaya daga cikin su ya kalli Nana ya ce "Wannan fa?"
"BaΖuwata ce" ta ba shi amsa, ya jinjina kai motar ta shige.
Su na shiga Nana ta ga ai gari ne guda a cikin ganuwar nan.
Sun Ιan yi tafiya kafin su shiga wani Ζaton gida.
Nana ta tsaya tana ganin yadda aka yi wa ginin Ζasa wani irin ado mai Ζayatarwa.
Tun da suka doshi shiga gidan, ake gaida Asal cikin girmamawa, ita kuma ta yi fuska sai taku take cike da Ζasaita, kamar ba ita ce suke rashin hankali da Ζawayenta a wancan gidan ba.
Wannan gidan saΙanin wancan da mutane a ciki, kuma da alama duk a ΖarΖashin Asal suke.
"Wace ce ita?" Nana ta tambayi kanta. Sai da suka Ζarasa wani falo, sannan ta yi wa wata dattijuwar magana da yaren su.
Matar ta kalli Nana ta ce "Bahaushiya ce ke ko? Zo mu je na kai ki masauki"
Babu musu Nana ta bi ta, matar ta kai ta wani daki ta ce nan ne Ιakinta.
Sai da Nana ta kwana biyu a gidan, ba ta sake ganin Asal ba, ba kuma ta aikin fari ba ta na baΖi kawai tana zaune, sai dai za a kawo mata Abincin safe, rana da dare sau uku a rana. Sai dai babban abin da ya dame ta, tun da ta shigo gidan, network Ιin wayar ya sauka gaba daya, ko ta kira Nene ba ta shiga sam.
A kwana na huΙu, da daddare dattijuwar matar nan ta zo ta kira Nana. Babu musu Nana ta tashi ta bi bayanta.
Sun yi 'yar tafiya su na ratsa faluka masu kyau da ado, sannan suka bi wata Ζofa. Sanyin A.C ya daki Nana, ga wani irin haΙaΙΙan Ζamshi. Asal ta hahakimce a kan kujera kaΙa Ζafa.
Ta kalli dattijuwar ta ce ta jira a waje. Daga Ζasa wata matar ce a zauna a kan carfet, ta gurfana kamar tana jiran Asal Ιin ta gafarta mata.
Nana ta yi turus tana tunanin a ina za ta zauna, sama ko Ζasa.
Matar ta kalli Nana cikin zare ido ta ce "Ke ki rage tsawon ki, kin tsaya mata a ka"
Nana ta ja guri ta zauna a kan carfet Ιin ita ma.
Asal kamar ba za ta yi magana ba, sai da ta gama iyayinta ta sauke Ζafarta Ζasa ta dubi Nana ta ce "Amm na saka an kirawo mini ke, saboda ki san abin da na kawo ki gidan nan ki yi. Ke dai da ganin gidan nan kin san ba gurin da za a yi wasa ne ko shirirta ba, babban gida ne na mulki.
Saboda dalilin girki da kuma wani dalili na Ζashin kaina, ya sanya na kawo ki gidan nan. Ba a Ιaukko bare wanda yake ba jinin gidan nan ba, ko Ζabilarmu ba ya yi mana aiki, amma na ga wasu abubuwa a tattare da ke da ya sanya na kawo ki cikin gidan nan.
Kamar yadda na gaya miki, ina Ζara jaddada miki, zaman ki a gidan nan dole ki yi taka tsantsan, babu ruwanki da shishshigi, saka ido, gulma ko kuma shiga abin da babu ruwanki.
Sannan kar ki kuskura wani ya ce zai haΙa kai da ke a yi wani abu, rayuwarki za ta iya salwanta ba tare da kowa ma ya sani ba, dan haka sai ki san irin zaman da za ki yi."
Nana ta yi shiru ta gama sauraren ta, sai dai har a lokacin ba ta ji dalilin da ya sanya Asal kawo ta gidan ba, dafa abinci kowa ma zai iya mai yasa sai ita.
Wannan matar da ta tarar a zaune, ta tafi da ita, ta kai ta gurin da ake girke-girken abinci, da gaya mata yadda jadawalin girke-girken gidan yake. Ta Ιaukko kayan ds Asal ta bayar a ba ta, na kayan shafe-shafe da mayukan wanka zuwa kayan sakawa.
Da Nana ta koma Ιakinta, ta kalli kayan ta fara tunanin Allah ya sa ba kwance Asal ba ne, dan gara ta saka kwancen Ashura da ta saka na Asal, da ba ta da mutunci.
A washegari Nana ta fara aiki a wannan madafa, sai dai madafar daban-daban ce. Akwai wadda ake girkin da ma'aikatan gidan ne suke ci, akwai wadda na baΖin da suke zuwa ne, sai kuma masu girka wa Asal abinci daban, dan haka Nana na cikin masu yi wa Asal girki.
Sosai matar nan ta Ζara jan kunnen Nana, a kan ta kula da kanta, dan muddin aka samu matsala ba za ta sha ba.
Nana a ranta ta ce "Ji wata jaraba, da wannan wahalar mutum ya girka abin da zai ci mana da kansa."
Kwana huΙu da fara aikinta, ranar Alhamis da daddare, tana shirin kwanciya, aka ΖwanΖwasa Ζofar Ιakinta.
Ta tashi ta buΙe, ta ga shugabar girke-girke ta gidan, kamar yadda aka gabatar mata da ita a baya.
"Ki sako hijjabinki, ki biyo ni"
Nana ta saka hijjabinta ta fito tana tunanin ko lafiya.
Harabar gidan matar ta yi, Nana ta bi bayanta, ta nuna mata mota. Nana ta kalli dare ya yi kuma an zo da mota an ce a tafi da ita.
Cike da mamaki Nana ta shiga motar, sai ta ga mutum uku, da su ma duk tare suke aikin girkin a gidan a cikin motar.
Ta shiga ta zauna, ita ma shugabar ta su ta shiga. Nana ta gaza haΖuri ta ce "Dan Allah ina za mu je ne?"
"Za ki gani"
"Eh amma na ga dare ne fa"
"Idan mun je za ki ji dalilin fitar" Nana ta yi shiru tana tunani, ita ba ma wannan ba, hankalinta ya koma kan rashin samun damar kiran waya da ba ta iya yi, kuma ba a kiranta ya shigo. Dan sai da ta tambayi Ιaya daga cikin masu aikin, ko matsalar daga wayarta ne, ta ce mata kar ta kuskura ta bari ma a san tana da waya, dan sai an Ζwace ta.
Tana ta zancen zuci, har suka isa inda aka tsaya suka sauka, aka shiga da su.
Asal ce a tsaye, tare da dattijuwar matar da ta saka ta raka Nana masauki. Suna tsaye a cikin Ιakin Nanan.
Asal ta ce "Zazzage mini kayanta, ki Ιaga mini komai Ιaya bayan Ιaya"
Ayshercool
Ku tura mini hakkina kan ku karanta 0069685771
Aisha Adam stanbic.
73
Ζaya bayan Ιaya, aka din ga zazzage kayan Nana. Aka zazzage su tsaf aka Azzage jakar da ta zuba kayan turarukanta da mayukan shafawa, duk ba ta ga wani abu ba, sai jakar gurin sarkin baka.
Ta nuna jakar ta ce "Mene wannan?"
Ta Ιago jakar ta ce "Jaka ce"
"BuΙe ta ki zazzage na gani" Ta fara kokowar buΙe jaka, amma babu gurin da zata buΙe ta. Kawai ta ce "Shikenan" ta fice ta bar Ιakin.
Can gurin kuma Nana tara su aka yi, su shida. "Na san za ku yi mamakin dalilin da ya sanya aka kawo ku nan, to zaΙo ku aka yi saboda an yarda da amanarku, ana daf da yin taro da Sultan da kuma dukkanin Imams na gidan nan. Dan haka ku aka zaΙo za ku yi girki na musamman. Amma ku sani kamar yadda wasu sani wasu ba su sani ba, muddin aka samu wata matsala ko Ζware wani ya yi, a sanadin abincin da ku ka dafa, to ku tabattar da rayuwarku za ku biya. Dole ku yi taka tsantsan ku kula." Matar ta yi maganar daki-daki.
"In sha Allah" suka amsa mata.
Ta ce su bi bayanta, suka je wani Ζaton guri, Ιauke da nau'oin kayan masarufi kala-kala. Ta yi musu bayanin da su ne za su yi amfani su yi girkin, sannan ya zama dole su sanya wa bakinsu sakata su yi aiki cikin amana, kuma kada wanda ya san su aka zaΙa da za su yi wannan girki. Nan ma suka amsa, ita dai Nana sai kallo da ido, dan abubuwan sun daina ba ta mamaki, wannan maganar ce ta sanya aka taso ta a daren nan, sai ka ce wanda za su girkawa wasu waliyyai abinci.
Ko da aka mayar da su Nana gida, ta sha mamakin ganin kayanta a hargitse a cikin Ιaki. Da mamaki ta Ζarasa kan kayan nata, ta ΙaΙΙaga.
Cikin takaici Nana ta tashi ta fita, sai dai kowa ya tafi makwancinsa ya kwanta. Kawai ta ji taku a bayanta. Ta waiwaya ta ga Asal na fitowa.
"Har kun dawo kenan?"
"Eh, sai dai na shiga Ιakina na tarar da an caje mini kayana an zubar da su a Ζasa, ban sani ba ko kina da masaniya a kan haka?"
Asal ta ce "Me yasa ki ka zarge ni?"
"Saboda na ga ba a gudanar da komai a gidan nan sai da izninki"
Asal ta yi murmushi ta ce "Haka ne, kina da kaifin ΖwaΖwalwa kamar yadda na yi tsammani, ni na saka aka caje kayanki saboda na san da wa nake zaune"
"Me yasa ba ki tambaye ni abin da ki ke buΖatar sani ba, za a caje mini kaya"
"Saboda a ΖarΖashina ki ke, a gidana ki ke zaune dole na sani idan da wani abu da ki ke tattare da shi na cutarwa"
Nana ta ce "Kin yi kuskure, dan ina zaune a ΖarΖshinki, ina da personal life Ιina, da 'yancin adana abin da yake sirrina, bai halatta ki bincikar mini kaya a bayan idona ba. Yaushe na san ki, da zan Ζulla wani abu da zan cutar da ke? Kina gudun hakan ki jawo ni ki ka kawo ni?"
"Yi Ζasa da muryarki, kar ki kuskura ki Ιaga mini murya, kin san matsayina? Za ki iya janyo wa kan ki gagarumar matsala muddin ki ka ci gaba da yi mini magana ba ladabi"
"Babu ruwana da matsayinki, da koma me za ki yi mini, kar ki sake shigar mini Ιaki ki taΙa mini kaya, idan kuma ki ka ci gaba za ki iya binciko abin da zai hana ki sukuni, idan kin ji ba ki yarda da ni ba, ki sallame ni na koma inda na fito, ba zai yiwu na zauna da ke kina zargina kuma kina cin dunduniyata ba."
Asal ta bi Nana da kallon mamaki, amma ta danne mamakinta ta haΙiye fushinta, ta ce "Gaskiya ne, kin yarda da kan ki har haka kenan? Shikenan amma idan na ga akasin abin da ya fito daga bakinki, za ki sha mamakin abin da zai faru"
Nana ta yi mata banza, ta koma Ιakin nata, ta gyara kayanta tsaf.
Ta kulle Ιakin ta koma ta Ιaga katifar Ιakin, ta Ιaukko wata jaka, a cikin jakar ta zuba duk tarkacen kayan Sayyid. Ajiyar zuciya ta ts yi, da tayi wannan dabarar ta Ιoye su. Haka kurum take jin kayan na buΖatar sirri.
Ta nemi guri ta kwanta tana sauke numfashi a hankali, tana tunanin yadda rayuwa ke ta jujjuyata.
*****
Shukura na zaune a Ιakinta tamkar zuciyarta za ta yi bindiga ta fito, Sagir ya buΙe Ζofa ya shigo Ιakin. Kallo Ιaya ta yi masa ta sunkuyar da kai. Tuni t yi shirin kwanciya baccinta, sai Ζamshin turare take zubawa.
Ya sha manyan kayansa, hannunsa riΖe da baΖaΖen ledoji. Ya zo ya zauna a kusa da ita, tamkar ta kifa masa mari haka take ji.
"Wai har kin yi shirin kwanciya? Na zata zaku gaisa tukuna sai ki kwanta" Mugun kallon da ta yi masa ya sanya shi haΙiye maganar da ya yi niyyar yi.
"Ga wannan naki ne" Ya yi maganar yana ajiye mata ledojin hannunsa.
Ba ta kalli kayan ba, kuma ba ta motsa ba.
Ya matsa kusa da ita, ya riΖo hannunta, ta fizge hannunta ta haye kan gadon ta kwanta.
Bai ji haushin abin da ta yi masa ba ko kaΙan, ya san idan ba ta son sa ba za ta yi kishinsa ba, sai dai ita ma Yusra tana buΖatarsa tun da tun farko bai kamata ya sake ta saboda larurarta ba.
Ya tashi ya kashe mata fitila, har zai fita ya koma gaban gadon, ya durΖusa daidai fuskarta ya ce "Ki yi mini afuwa Shukura, ban yi haka domin na cutar da ke ba, ko na muzguna miki, dan Allah ki kwantar da hankalinki saboda lafiyarki da abin da yake cikinki" Daga haka ya tashi ya fice. Sai da ya fita sannan ta ba wa hawayen da suka maΖale a Ζirjinta damar zirarowa, zuciyarta ta din ga yi mata Ζuna, tamkar ta tashi ta bar gidan.
Duk da ya fita da damuwar halin da Shukura take ciki, amma bayan wani Ιan lokaci tuni ya manta, suka ci suka Ζoshi da shi da Yusra.
Bayan sun gabatar da salla, sun yi addu'oi, suka yi zamansu kawai su na hira.
Sai gurin Ιaya saura sannan suka tashi suka kwanta.
Yadda Sagir yake murna da kasancewa da Yusra, ko aurensu na fari bai yi haka ba, tuni wani nannauyan bacci ya yi awon gaba da su, daga shi har ita.
Shukura kuwa yadda ta ga rana haka ta ga dare, ga wani irin zafi da ya addabe ta duk da na'urar sanyaya Ιaki da ke cikin Ιakin.
Washegari sai Ζarfe sha Ιaya na safe ya shiga Ιakin Shukura.
Idonta kawai ya kalla ya ga alamun rashin bacci a tattare da idanunta, sun yi jawur sun kumbura.
"Oum Haidar" ya kira sunanta, yana zama a kan gadon, tana shan tea.
"Ina kwana" ta faΙa a taΖaice.
Idanunsa ya sauka a kan ledar da ya kawo mata, babu alamar ko taΙa ledar ta yi.
"Shukura me yake damunki ne haka? Na kawo abu ko taΙawa ba ki yi ba, kin yi bacci makuwa"
"Sagir, dan Allah ka tashi ka bani guri, ni bana buΖatarka a kusa da ni, kaΙaici nake so"
"Ni ki ke cewa na fita na baki guri?" Ya yi maganar yana nuna kansa.
ΖoΖarin mayar da hawayen da ke shirin zubo mata take yi, amma abu ya gagara kawai ya fara zubowa ba tare da ta shirya hakan ba.
Jikinsa ya yi sanyi, ganin yadda take kuka sosai da sosai.
Cikin kwantar da murya, yake ΖoΖarin rarrashinta, amma ta tashi ta shige banΙaki ta bar shi a gurin.
Ya yi shiru ya rasa abin da yake yi masa daΙi, shi babbar damuwarsa ma cikin da take Ιauke da shi, ga matsalarta ta hawan jini.
*****
Tamkar bayi haka su Nana suke aiki, kullum za a Ιaukkosu daga wancan gidan da Asal take, a kawo su nan su wuni su na aiki. Har mamaki take yi wannan mutanen su kuwa har su nawa ne, dan kamar har da almubazzaranci a cikin lamarin.
Sai dai kowa cikin kaffa-kaffa yake aikin tare da fatan kar wani abu ya biyo baya da za a kama su da laifi.
Kwana na uku, wanda ranar suka dafa normal Abinci, sauran kwanakin kayan snacks ne suka din ga yi. Duk cikin su Nana ce 'yar Nigeria, sauran duk 'yan Nijar ne, sai dai galibinsu baΖaΖen buzaye ne.
Sai da suka kammala aikin, aka ba su wasu kaya fararen dogwayen riguna, da rigar girki, aka saka su kai Abincin wani Ιaki.
Katafaren Ιakina da dogon tebur, an gyara shi sai tashin Ζamshi yake yi. Sai dai gabanta ya yi mummunan faΙuwa da jin irin Ζamshin da yake tashi a Ιakin.
Take jikinta ya hau rawa, har ta nemi ta kifar da abin da ta Ιaukko.
Ta Ιaga kanta a hankali ta kalli jerin manyan frames Ιin da ke Ιakin, sai dai mutanen jikin hotunan, dukkaninsu fuskokinsu a rufe yake, ba ta iya gane kowa daga cikin su ba.
"Ke Nana ki kai mana kin ja kin tsaya" Nana ta jinjina kai jiki a sanyaye ta Ζarasa gaban teburin. Ta ajiye kayan, ta Ιaga kai ta kalli yadda ginin Ιakin yake da matuΖar tsayi.
Jiki a sanyaye ta ci gaba da kai komo, su na shirya abincin.
Bayan sun shaΖe teburin da uban kayan Abinci, aka ba su umarnin su tsaya kar wanda ya fita.
Su na tsaye Nana ta kalli agogon Ιakin, Ζarfe goma na dare.
Wani Ζaton mutum ya shigo, ya kalli gurin da yadda aka shirya teburin, ya kalli su Nana ya ce "WaΙanan ne suka yi girkin?"
Balaraba wadda ita ce ta jagoranci su Nana gurin girke-girken ta risuna ta ce "Eh su ne ranka ya daΙe"
"Wace ce wannan? Na ga kamar ba tamu ba ce" Ya yi maganar yana nuna Nana, da gaba Ιaya rabin hankalinta ba ya jikinta.
Balaraba ta ce "Gimbiya Asal ce ta zaΙo ta, ta saka ta a cikin masu girkin"
Ya yi shiru yana kallon Nana, daga bisani ya jinjina kai ya kalli Balaraba ya ce "Ki je, su su tsaya" Ta jinjina kai ta fice.
Wata Ζofa aka buΙe, wani matashi ya shigo fuskarsa Ιauke da murmushi, gaban Nana ya yi mummunar faΙuwa, dogo ne sanye da farar jallabiya ya Ιaura hirami a kansa, ba dan ta yi wa Sayyid kyakykywan sani ba, za ta iya cewa shi ne. Ζirjinta ya tsananta bugawa, sai dai kafin ta daidaita nutsuwarta, wani ma ya biyo bayansa, shi ma dai kamarsa Ιaya da Sayyid Ιin.
Tunani ta fara yi ko Giyaz da Ζaisar ne suka fara yi mata gizo suke yi mata wasa da tunani.
Ζaya bayan Ιaya suka din ga shigowa, sai da ta Ζirga mutum biyar cif, biyu kamar su Ιaya sak, sauran ukun kuma su na kama amma ba sak da Sayyid ba. Duk suka jeru a kan kujerun teburin nan. Sai dai babbar kujera babu kowa a kai, kujerun gefe da gefen kujerar ma babu kowa a kai.
Ζaya daga cikin su ya ce "Ko waye zai hau wannan kujerar?" Ya yi maganar yana nuna Ιaya daga kujerun da babu kowa a kai.
"Wannan karon dai za mu ji me Sultan zai ce mana a kan maganar"
"Nima dai abin da nake son ji kenan, magana ta gama cika gari ba a san inda yake ba, ana ma tunanin ko ya mutu suke Ιoyewa"
Nana ji ta yi ana busar sarewa a Ζofar bayan su, gaba Ιaya suka ja gefe domin bayar da hanya.
Wani dattijo ne fari sol, mai dogon gemu ya shigo jallabiyarsa baΖa, ya lulluΙe kansa da hiraminsa.
Gaba Ιaya ta ga abokan aikinta sun rikice, duk sun sunkuyar da kansu Ζasa, Nana kuma ta yi masa Ζuri da ido. Sai dai ba shi take kallo ba, ji take tamkar numfashinta ya Ιauke, kamar ba a cikin duniya take ba, duniyoyin da Ζaisar ya saba kaita ne ya caza mata kai, banda haka wani irin mummunan gizo ne wannan?.
Gaba Ιaya matasan suka miΖe tsaye, cikin matsanancin mamaki suna kallon na bayan dattijon.
Tamkar yana tausayin Ζasar haka yake taka ta, yana Ιan yin rangaji kaΙan, sassanyan Ζamshin turaren sa da ko a mafarki ta ji shi tana tantancewa ya karaΙe ilahirin gurin, fiye da Ζamshin turarukan da ke tashi a gurin.
Ta kusa da ita ce ta ja hannunta da Ζarfi, saboda yadda ta tsare shi da idanunta ko Ζiftawa ba ta yi.
Ya zo zai gifta ta, amma ko gurin da suke bai kalla ba, Ιaya bayan Ιaya suka din ga rungume shi, cike da murnar da wasu har zuci, wasu kuma iya ta fuska ce. Ta ga ya zauna a kan kujerar da ake tababar wa zai zauna a kai kafin ya shigo.
Abdou ya ce "Kun yi mamaki ko? Ba ku yi zaton ganinsa ba?"
Ζaya daga cikin su ya ce "Gaskiya ne"
Sultan ya yi murmushi ya ce "Kamar dai yadda na gaya muku a baya, Imam Hammad yana Faransa neman lafiya, bayan tsawon wannan lokacin, yau ya kasance tare da mu a liyafarmu ta Ζarshen shekara, dama wannan ne bazatar da na ce zan yi muku"
Nana ta kalli hotunan nan, sai ta yanzu hotunan babu rawani, kowa hoton fuskarsa ce. Ta tsayar da idonta a kan hotonsa da aka rubuta Imam Hammad Jalal Agadez. A take ta tuna da sunan gidan cin abinci da ta yi wa su Al Hussain aiki. H.J Agadez.
Sunan rukunin gidajen da ta fara zama da Asal shi ma sunan da ke jikin symbol Ιin unguwar kenan. H.J Agadez.
Duk surutun da ake yi, da murnar ya dawo, yana Ζame a kan kujera, fuskarsa babu yabo babu fallasa.
Sai daga bisani ya saka hannunsa Ιaya a kan Ζirjinsa ya risunar da kansa ya ce musu "Merci(Na gode)
Duk da a hankali ya furta, amma ko cikin murya dubu Nana ba za ta gaza tantance ta Sayyid ba.
Abduou ya kalli su Nana, ya kalli mutumin Ιazu da yake tambayar wace ce "Guda biyu daga cikin su ta zo ta ΙanΙana Abincin nan"
Mutumin ya Ζare musu kallo, ya nuna Nana ya nuna wata ya ce su je su ci kafin a ci.
Nana ba ta san a yadda take iya Ιaga Ζafafuwanta ba, saboda ba ta jin su a jikinta, zuciyarta kuwa kamar za ta tarwatse saboda bugun da take yi fiye kima. A hankali ta Ζarasa gaban teburin. Ζayar ta din ga bubbuΙe Abincin, ta fara ΙanΙanawa.
"Ke kina da gaskiya kuwa? Ki ΙanΙana aka ce?" Abduou ya yi mata maganar cikin tsawa.
Rikicewa ta yi gaba Ιaya, ya Ιaga idonsa ya kalli inda jikinta yake rawa, suka yi ido huΙu, ya kawar da kansa yana mamakin yadda take a ruΙe.
Ta Ιebo shinkafa a cokali, amma hannunta karkarwa kawai yake yi.
Sultan ya ce mata "Kina lafiya kuwa?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
Sultan ya ce "Na fuskanci a tsorace take ne kawai, a kaita ta je ta huta, wataΖila mun yi mata kwarjini ne"
Aka saka Nana a gaba aka fitar da ita daga gurin.
Fitarsu ke da wuya, jikin Nana ya din ga wata irin kyarma, haΖoranta na haΙuwa da juna, wani irin jiri ya din ga kwasarta.
Balaraba ta nufo su da sauri, ganin Nana na dafa bango.
Ya kalli Balaraba ya ce "Maza ki kaita ta huta, wataΖila ta yi aiki da yawa ne ta gaji, gaba Ιaya ta rikice, a kirawo likita kuma ya duba ta.
*****
A hankali Nana ta yi juyi, ta buΙe idonta ta ganta a Ιakin da take kwana.
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, da ta tabbatar da mafarki ta yi ba gaskiya ba ne abin da ya faru.
Hamdala ta yi ta ce "Ni dai na san mafarki ne da ma, dan babu yadda za ayi Sayyid ya ganni ya kasa kula ni, ya nuna kamar bai sanni ba. To wannan idan gaskiya ne ma, ta ina zan fara bayanin ni matarsa ce a yarda da ni? Mutumin da na ji ana batun ya daΙe a faransa yana jinya, anya ma Sayyid Ιina ne? Tun da dai mafarki ne duk da sauΖi.
Sallama aka yi a Ιakin, ta ga Balaraba ta shigo Ιakin. Ta ce "Kin tashi?"
Nana ta yi shiru tana kallonta.
"Ina ga aiki da ki ka sha a kwanakin nan ne, ya sanya ki ka gaji zazzaΙi ya kama ki, Likita ya ce a bari ki huta sosai da sosai. Gimbiya Asal ta ce a baki hutu na kwana uku ki warware kan ki koma bakin aiki."
Nana ta jinjina kai kawai, tana kokawa da ΖwaΖwalwarta, domin ta tabattar gaske ne, ko kuwa dai mafarkin ne? Ta tashi ta yi alwala ta yi salla, sai dai gaba Ιaya jikinta ciwo yake yi mata, ga matsanancin ciwon kai da jiri da take ji, dan haka ta nemi guri ta sake kwanciya.
*****
Jamila ta Ιauki jakarta Ιauke da wannan tarkacen da take kira da tarkacen jaraba, ta fita waje, ta samu ta sayo fetur a 'yar jarka, ta samu guri ta zuba musu fetur Ιin ta kunna musu ashana ta Ζone su.
Ta tashi tana kallon yadda suka din ga ci da wuta, ta bar gurin.
Kai tsaye ta tari abin hawa ta tafi gidan Hajiya Sa'a.
Hajiyar ta yi iya ΖoΖarinta gurin Ιoye jin haushin Jamila da take yi, ta karΙe ta hannu bibbiyu har ta taya ta lissafin kuΙin kasuwancinta da kuma kayan da take da su a Ζasa.
Bayan sun kammala ta ce "Ni kuwa Jamila, yaya batun Ζungiya wa za ki bayar ne?"
Jiki a sanyaye ta ce "Haryanzu ban gama tunani ba ne ba"
"Tsoron dai ki ke ji haryanzun ko?"
"A'a na rage ji"
"To ki yi ki hanzarta ki yi abin da yakamata amma kin tsaya. Ni kalli nawa nan na shirya komai aiwatar wa kawai ya rage mini, sai na je gidan zan yi, na sake bayar da Ιan Fatuhu"
Jamila ta kalli drower da Hajjya Sa'a ta janyo, tana nuna mata 'yar tsanar nan.
Jamila ta ce "To idan ban kai kowa ba, akwai wani abu da zai faru ne?"
Ta ce "Au da kara zube za ki zauna ki Ζi bin umarnin Ζungiya? To idan ba ki kai kowa ba, jininki aljanin zan shanye ki mutu" Cikin Jamila ya yi wata irin Ζara bayan tuna ta Ζona kayan. A tunaninta shikenan ta huta sun rabu.
A ranta ta ce "Wannan wane irin bala'i ne na jefa kaina a ciki, Ubangiji Allah ka kawo mini agaji na rabu da wannan masifar.
*****
Fafur Nana ta Ζi yadda zuciyarta ta amince abin da ya faru gaskiya ne ba mafarki ba, saboda ta riga ta saba da irin wannan cazan kan da Ζaisar ya kan yi mata wasu lokutan, har ta gaza banbance abin da yake zahiri da kuma mafarki.
Nana suna Ιakin girki su na ta Ιorawa da saukewa, ta kalli shugabar su ta ce "Dan Allah a gidan nan, babu yadda zan yi na samu waya, ina son na kira gida ne, na ji halin da yarona yake ciki"
Balaraba ba ta bata amsa ba, ta ji Muryar Asal ta ce "Babu wannan damar, sai dai idan kina buΖata ki zo gurina ki karΙi wayar ki kira"
Nana ta Ιan yi shiru sai kuma ta girgiza kai ta ce "A'a ki bar shi na gode"
"Me yasa ki ka ce haka? Kina tunanin wani abu a ranki ne?"
"Bana tunanin komai, kawai dai na fasa ne"
Ta yi murmushi ta ce "Shikenan, ga saΖo can daga gidan Sultan, tukuicin aikin da ku ka yi na girki"
Balaraba ta risuna tana yi wa Asal magana da yarensu, Nana kuma ta cigaba da aikinta, tana sane ta cewa Asal ba ta so, dan ba ta gama gane ina Asal Ιin ta saka gaba ba, da kuma cikakkiyar manufarta a kanta ba. Tana tsoron ta yi amfani da wata dama da za ta samu ta cutar da ita.
Katafaren Ιakin bacci ne, mai Ιauke da kayan alatun more rayuwa irin na masu mulki.
Duhun dare ne, sai dai hasken fitilun Ιakin ya gauraye ko ina, kai ba ka ce dare ne ba.
Yana zaune a gefen gadon, tare da dattijon. Cikin kamala dattijon ya ce "Imam, ina Ζara yi maka gargaΙi da jan kunne a kan ka Ζara kula da kan ka. Kar ka Ιauka kowane murmushi ne na soyayya, wani murmushin na babu yadda aka iya da kai ne. Kar ka kuskura ka faΙi wani abu da zai rusa shirinmu, mun Ιoye abubuwa da dama a game da kai, duk abin da baka fahimta ba, ka tambaye ni, kar ka wani ya buΖaci sanin wani abu daga gare ka, ka sanar masa kawai jinya ka yi tsawon wannan lokacin.
"Abii"
"Na'am abin Ζaunata" Imam Hammad ya yi murmushi ya ce "Me ka ke Ιoye mini ne, akwai abubuwan da suka hargitse a rayuwata, tsawon wani lokaci na Ιauka ina jinya ba a hayyacina ba?"
"Ka na ji na? Haryanzu ba ka warke ba, ka na buΖatar hutu mussaman a ΖwaΖwalwarka, kar ka takurawa kanka da tunanin abubuwan da suka faru. Jita-jitar da ake yaΙawa a kan ka, da surutai daban-daban shi ne dalilin da ya sanya muka dawo da kai Ζasar nan, a shaida dai kana raye, cikin Ζoshin lafiya"
"Mahaukaci ne ni kenan? Tun da ina iya tuna yadda ciwon nawa ya fara, amma ban san yaya ya Ζare ba"
Sultan ya tsuke fuska ya ce "Ya ishe ka haka. Kar ka kuskura na ji labarin nan ya fita, waye ya ce kai mahaukaci ne? Larurar zuciya ce take damun ka, babu daΙi babu Ζari daga haka. Babu wata larurar hauka a tattare da kai".
"Amma Sultan ko zaka saka na Ιoye wa duniya, yakamata na san matsayin lafiyata...
"Hammad!" Tilas ya ja bakinsa ya yi shiru, ganin yadda ya fusata Sultan Ιin.
*****
Tun da garin Allah ya waye, Nana take jin faΙuwar gaba da matsananciyar fargaba, ga sanyin da take jin yana ratasa ta, ta san ba na lafiya ne kawai ba. Dan haka ta Ιaura alwala take ta addu'a.
Bayan fitowarta ta cika da mamakin ganin yadda ma'aikatan gidan, suke ta aiki tuΖuru suke gyara gidan duk da ko ina a gyare yake.
Ko ta ina Ζamshin turaruka ne ke tashi daban-daban. Har sun so su yi yawa ma.
Ζangaren da take aiki, sai azalzalarsu ake yi, ta fahimci dai wani baΖo ne mai muhimmanci zai sauka a gidan.
Har mamaki take yi yadda suke ba wa abinci muhimmanci, baΖo Ιaya sai a saka a yi masa abinci biyar, kuma duk da an san ba iya cinyewa zai yi ba.
Ta fito kenan ta ci karo da Asal, ta sanya zani da doguwar riga na shadda baΖar shadda, kanta babu Ιan kwali, hannayenta da yatsunta duk zobunan gwal ne, uwa uba wata irin sarΖa da ta saka ta zinari tun daga wuyanta har cikinta. Gashinta ya sha ado, ta sake shi har kafaΙarta, shi ma ta sanya masa wata siririyar sarΖa da ta kwanto har goshinta.
Duk hassadar mai hassada babu yadda za a yi ka kalle ta ka kushe ta, jawur da ita a cikin baΖar shaddar sai ta haska shaddar.
Ita dai Nana tun da ta zo gidan, ba ta taΙa ganin Asal da miji ko 'yan uwa ba, sai tarkacen Ζawayenta, su ma a wancan gidan ne, wannan gidan ba sa biyo ta su zo. Kuma duk abin nan Nana ba ta taΙa bin diddigi ta ji wace ce Asal ba, me yasa kuma take rayuwa a gidan daga ita sai masu yi mata hidima ba.
Da daddare Nana ta ji su Balaraba su na yare, su na faΙin sunan Imam, lokaci lokaci su na haΙa wa da Hausa, sai dai ta manta a inda ta taΙa jin Imam Ιin.
Babban abin da ya Ιaurewa Imam kai, bai wuce yadda a faransa yake jin sa garau, ba shi da wata damuwa ko wani ciwo da yake ji ba. Amma tun da ya sanya Ζafarsa a Agadez tsawon kwanaki huΙu, ko sau Ιaya zuciyarsa ba ta saurara da bugun da take yi cikin sauri babu ΖaΖΖautawa ba.
Nana na ta kai komo a kitchen, ta kammala duk wani aiki da ya shafe ta, tana shirin tafiya ta je ta kwanta. Balaraba ta ce "Saurin me ki ke yi ne Nana?"
"Ina son na je na yi wanka na kwanta ne"
"Ki je ki yi wankan, nan da mintuna talatin za ki kai wa Gimbiya Asal bunu da madara sashinta"
Har Nana za ta yi magana, dan ba ta shiga sashin Asal sai sau Ιaya, ta taΙa zuwa idan sun yi girki akwai waΙanda suke kaΙai suke iya zuwa sashen su kai. Ta fasa maganar ta ce "To"
A gurguje Nana ta kintsa, ta koma ta Ιauki kayan za ta yi gaba, Balaraba ta ce "Ai ba sashinta za a kai ba, Ramata raka ta"
Ramata ta kalli Nana ta yi mata kallon banza, ta Ιan kwaΙe baki sannan ta yi gaba Nana ta bi bayanta.
Duk yadda Nana ta so sarrafa kanta ta kasa, ta Ιaga kai ta din ga kallon Ζawataccen gurin tare da jinjina yadda masu gidan suka Ζware a iya almubazzaranci. Dan ba za ta kira shi ado ba kawai sai dai almubazzaranci.
Tana saka Ζafarta a cikin falon, ta ji tamkar an jona mata shocking, saboda rawar da jikinta ya yi, sai da farantin hannunta ma ya girgiza tamkar zai Ιare. Ramata ta kalle ta, ta yi tsaki kawai.
Nana ta ajiye kayan a hankali a kan carfet Ιin Ιakin.
Bayan ta ajiye ta yi taku huΙu zuwa biyar, ta ji yadda adadin sanyin da take ji yana Ζara yawa. Ta sauke idanunta a kan Ζaton frame da hotonsa a jiki. DanΖarewa ta yi a guri Ιaya, ta kasa motsa ko da Ζafarta.
Taku ta fara ji a bayanta, ana tahowa, muryar Asal ta ji tana magana da faransanci cikin shagwaΙa.
Ζan ja ya yi ya tsaya, jin yadda jikinsa ya yi wata girgiza.
"Lafiya dai ko?"
Ya jinjina mata kai alamar eh.
"Amm me ku ke yi a tsaye a gurin nan ne?"
Ramata ta ce "Abinci muka kawo"
"Waye ya yi?"
Ta nuna Nana da ba ta juyo ba.
"Zo" ta kira Nana sai dai Nanan ta Ζame ba ta juyo ba. A wulaΖance Ramata ta taΙa ta ta ce "Ana yi miki magana"
"Tana ji na rainin hankalin za ta yi mini"
Sannu a hankali Nana ta juyo, idonsa na kan wayar hannunsa.
Yanzu ta tabattar da mafarki ta yi ba, Sayyid ta gani, sai dai ganinsa bai razana ta ya kiΙimata ba, kamar yadda alamu suka nuna Asal matarsa ce ba.
Ta sunkuyar da kanta Ζasa, tana jan Ζafafuwanta a hankali.
"Me ya same ki ne?"
Ta girgiza kai alamar ba komai.
"Ki yi mini magana kina girgiza kai kawai"
"Ba ni da lafiya"
Asal ta ja tsaki ta ce "Je ki kar ki Ιata mini rai"
Ta zuba masa shayin a kofi, ta zuba masa madara, ya Ιauka a hankali ya kai bakinsa yana sha.
Nana kuwa a Ιakinta, gaba Ιaya ta burkice, tamkar za ta yi hauka ta ce "Dama abin da ka ke gargaΙina a kai kenan Ζaisar? Sayyid me yasa za ka yi mini haka, dama ka na da wata matar ka aure ni? Yanzu ka na nufin ka manta ni, Sayyid anya alΖawari ya ce haka? Na haΖura zan Ιauki Ιa na na koma gida, ganinka da wata kawai ya isa ya yi ajalina. WataΖila alhakin iyayena ne ma da na taho ba da izininsu ba. Yadda ka ke a cikin daular nan, yaya za a yi na ce ina da alaΖa da kai ma a yarda da ni?" Ka ce Ruhina da naka su na rayuwa a tare, kowannenmu yana Ιauke da ruhin Ιan uwansa, ni na yi dakon soyayyarka ashe ka na da matar da ta fi ni komai" Ta yi maganar cikin matsanancin kuka tamkar za ta fita daga hayyacinta.
Yana tsaye yana jin yadda ruwan yake ratsa shi daga cikin gashin kansa zuwa jikinsa.
Wani irin zafi yake ji a cikin ΖwaΖwalwarsa, tamkar kansa zai tarwatse.
Karo biyu yana jin jikinsa ya yi girgiza.
Ya yi wankan ya lulluΙo jikinsa da towel.
Asal ta sha kwalliya cikin baΖaΖen kaya na bacci.
Ta nufo shi tana rangwaΙa, ta cire towel Ιin da ya lulluΙa da shi. Ya Ιan lumshe idanunsa saboda Ζamshin turaren da Asal take yi mai jan hankali.
Ta shige jikinsa ta rungume shi, ta ce "Na yi kewarka sosai Imam"
"Nima ina jin kewar abin da ban san mene ba, bayan kewarki da na yi"
"Akwai abin da ya fi ni muhimmanci dama, da har ka ke kewarsa fiye da ni?"
"A'a ban ma san mene ba, kawai dai ina jin akwai wani abu da ba daidai ba"
Ya yi maganar yana shafa gefen wuyanta, yana son tambayarta wace ce yarinyar nan, amma ya haΙiye ya fasa.
Ya fara ΖoΖarin sumbatar ta, sai dai ya ja da baya da sauri yana dafe kansa, da yake jin wani sauti mara daΙin ji a cikin sa.
"Imam jikin ne dai?"
Bai yi magana ba, ya hau kan gadon ya kwanta ya lumshe idanunsa.
Washegari da safe, idanun Nana sun kumbura suntum, saboda ba ta rintsa ba ko kaΙan.
Ta saba da wuri take tashi, ta fara gudanar da aikinta, amma sai da aka zo aka kira ta, ta ce ba za ta yi aikin ba.
Bayan mintuna talatin sai ga Asal a Ιakin, ta kalli Nana a wulaΖance cikin isa da gadara ta ce "Ki ka ce ba za ki yi aiki ba yau? Saboda gidanki ne ko zaman kan ki ki ke yi a gidan? An kai wa Imam shayi ya Ζi sha ya ce ba irin na jiya ba ne"
"Eh ba zan yi girki ba, kuma barin gidan nan zan yi, na gaji da wannan aikin, zan je na ga yarona"
Asal ta yi dariya ta ce "Ai kuma Ζarya ki ke yi. Na Ιaukko ki gidan nan saboda nesanta mijin da waΙanann munafukan hadiman, na kawo bare da baki san komai a kan harkar gidan mulki ba. Kuma ba kya cikin kalar matan da za su iya Ιaukar hankalinsa. Dan haka na kawo ki ne dan ki din ga kula da abin da Imam zai ci aikin da ki ka zo yi gidan nan kenan.
Nana ta yi wa Asal wani irin kallo mai cike da tsana, ji take tamkar ta kama Asal ta yi ta jibgarta har sai ta ji ta huce.
"Gimbiya Asal, ai an bar kari tun ran tubani. Ba zan yi girki ba sai dai yunwa ta kashe Imam Ιin, ke da yake aure idan ba za ki girka masa ba, to kar Allah ya sa ci, sai na bar gidan nan ba zan zauna ba" Ta yi maganar cikin Ιaga murya da zazzaro ido.
Asal ta yi taku biyu, ta hankaΙa Nana baya ta ce "Ki kiyaye harshenki a kan abin da zai din ga fitowa daga bakinki, a kan mijina. Biyan buΖatata ce kawai ta sanya nake Ζyale ki, ki daina ΖoΖarin Ζetare iyaka. Tafiya kuma ga hanya nan maza ki tafi mu gani, idan kina tunanin da ka na kawo ki gidan nan na ajiye"
Ayshercool
08081012143
74
Wata irin tafasa zuciyar Nana ta din ga yi, ta din ga jin tamkar za ta tsaga Ζirjinta ta fito.
Asal ta yi wani shu'umin murmushi ta ce "Ko za ki dake ni ne? Na ga kina ta huci tamkar macijiya. Sannan ina mai Ζara jaddada miki, muddin mijina ya ci wani abu da ya samar masa da matsala a dalilin abincinki da rayuwarki za ki biya. Babu tsautsayi babu Ζaddara a gidan nan. Dan haka sai ki tattara dukkanin nutsuwarki ki san abin da ya kamace ki.
Sannan babu ruwanki da yi masa magana, ko yi masa shishshigi, ki dafa abinci ki kai sashensa kawai, babu wanda yake da damar zuwa sashen kai tsaye, ke kawai ki ke da wannan damar a cikin bayin gidan nan, dan haka ina Ζara gargaΙinki a kan ki iya kan ki a zaman gidan nan"
Kalmar Bayin da Asal ta faΙa, sai da Nana ta ji kamar ta fashe. A gidan uban wa ta zama baiwarta. Za ta yi magana ta ji tamkar an saka abu a danne mata maΖogwaronta, ta kasa magana.
Tana ji tana gani Asal ta gama caΙa mata baΖaΖen maganganu, ta fice.
Nana ta fashe da wani irin matsanancin kuka, ta rasa wani tunani ma za ta yi, kanta ya kulle ta zauna tana ci gaba da kuka mai sauti da ratsa zuciya. Ta kasa samun sukunin da za ta yi tunanin mafita ma.
Asal na komawa sashen Imam, ta tarar da shi ya shirya tsaf da alamar fita zai yi.
"Imam, fita kuma zaka yi?" Ya jinjina mata kai.
"To ai ba ka karya ba, kuma mu Ιauki tsawon wannan lokacin ba ma tare baka nan, kuma yanzu ka ce fita za ka yi?"
Ya ci gaba da ΖoΖarin fita, amma ta tare shi.
"Haba Imam, ko kewata ba ka yi ba? Ba ka yi farin ciki da ganina ba ne? ka ke shirin ficewa ka bar ni?"
Ya tsaya yana Ζarewa fuskarta kallo ya yi murmushin gefen baki ya ce "Abincin ne ban ji daΙin sa kamar na jiya ba. Sannan Gimbiya Bilkisu zan je na gaisar".
NoΖe masa kafa ta yi tana riΖe rigarsa.
Ya ajiye agogonsa ya nemi guri ya zauna, hakan ya sanya ita ma ta zauna tana murmushi.
Nana kuwa tana tsaka da kuka ta ji an dafa ta, ta Ιaga kanta a hankali ta ganta a Ιakin karatun Ζaisar.
Sai dai wannan karon tsawonsa daidai da ita, ya zauna sosai ya fuskance ta.
Ta sunkuyar da kanta hawaye na ci gaba da kwararowa daga cikin idanunta.
"Uwar gijiyata" Nana ta Ιaga idanunta a hankali ta dube shi, ta mayar da kanta ta sunkuyar.
"Bai kamata ki nuna karaya a wannan gaΙar ba, duk da ina jin zafin yadda ki ka yi burus da ni, da buΖatata da gargaΙin da na din ga yi miki a baya, amma wannan kamar ita ce gaΙa ta Ζarshe mai kuma matuΖar wahala, idan ki ka sare a yanzu wahalar da ki ka yi tuΖuru a baya za ta tashi a banza kenan.
Ba ki da tabbacin ya gane ki? Ko kuma bai gane ki ba, sai dai komai ya zo da sauΖi. Ita wannan matar sauΖaΖa miki aiki ta yi, tun da ta kawo ki kusa da shi, ta kawo ki har inda yake, godiya ma yakamata ki yi mata.
Ki kawar da kai daga kan duk wani abu na wulaΖanci da za ta yi miki a yanzu, a Ζarshe ke ce da riba, ki fara tantance halin da yake ciki, kafin ki Ιauki mataki na Ζarshe"
Cikin kuka Nana ta ce "Ζaisar na karaya, na sare ba zan iya ba, wa zai yarda da ni matarsa ce, banbancim da ke tsakanina da shi tazara ce mai nisan gaske.
Ba na buΖatar ya gane ni, gida zan koma na nemi gafarar iyayena na kula da yarona"
"Ba za ki koma gida yanzu ba, yaronki yana hannu na gari a yanzu duk ban san gaba ba. Na daΙe ban ga bil'adama mai juriya sadaukarwa da tsantsar juriya kamar ki ba. Imaninki da Allah ina da tabbacin ba zaki wulaΖanta ba kamar yadda ki ke yawan faΙa mini. Kar ki karaya ki tsaya ki karΙi abin da yake naki ne, idan ki ka karaya ki ka tafi kin yi biyu babu, wahalarki kuma ta tashi a banza"
Da wannan maganganun ta buΙe idonta, tana sauke numfashi a hankali.
Daki-daki ta din ga jin maganganun Ζaisar na dawo mata. Ta yi shiru tana nazari, ta tashi zaune a hankali.
"Abin da yake nawa? Eh Ζaisar, Sayyid nawa ne, bai kamata na karaya a wannan gaΙar ba" ta furta idanunta na sake cika da hawaye bayan tuna Asal matarsa ce.
Ta din ga tunanin suwaye suka tafi da shi lokacin suna Buda? Ko dai da kansa ya gudu ya bar ta? Ina su Habu, ta gan shi shikaΙai? Da gaske taΙin hankali ya yi a baya ya manta wace ce ita, ko kuwa dai raina mata hankali ya yi, ko kuwa dai duk wannan abin ba Sayyid Ιin ta ba ne?"
Wata zuciyar ta ce "Haba dai, ko na makance na shafa na san Sayyid, ko za a ajiye irin sa dubu zan fitar da Sayyid a cikin su. Ina zan samu amsoshin tambayoyina ne?" Ta yi maganar tana dafe kanta da yake yi mata wani irin ciwo.
Ζaisar kuwa yana sakin Nana, Ιakin karatunsa ya gauraye da sautin dariyar Giyaz, dariya ta rashin imani mara daΙin ji.
Ζaisar ya waiwaya, yana kallon inda Giyaz yake shawagi a sama yana ΖyaΖyata dariyar, hakan ya tabattar masa da Giyaz ya gama jinyar abin da Nana ta yi masa.
Ya yi wata irin girgiza ya bayyana a gaban Ζaisar, ya din ga zagaye Ζaisar yana ci gaba da dariyar cike da mugunta, daga bisani ya tsahirta da dariyar ya ce "'yan samari, yaushe imaninka ya Ζaru haka, har ka ke yi wa uwar gijiyar da ba ta Ιauke a bakin komai ba, nasiha da ba ta shawara?"
Ζaisar ya tsuke fuska ya ce "Ban yi maka iyaka da zuwa inda nake ba?"
Giyaz ya ce "DaΙin abin har gori ta yi maka a kan butulcin ka yi mini, amma da yake ba zuciya ce da kai ba, ka na liΖe da ita. To bari na gaya maka abin da ba ka sani ba, ni ne na sake juye tunaninsa na shafe masa wancan tunanin, yadda abin zai yi mata ciwo, dama na gaya mata dawowata ba za ta yi mata daΙi ba, tun da na tashi daga jinya nake tunanin yadda zan Ζuntata mata na Ζuntata maka.
Ya Ιagowa Ζaisar wata kwalba, da wani farin haske yana yawo a cikin ruwan da ke cikin kwalbar.
"Ka ga wannan, tunaninsa ne a ciki na duk wani abu da ya shafe ta na rufe shi ba zai taΙa tuna ta ba har abada. Sai dai ta dauwwama gararamba babu makoma. Na ga ka yi wa Ιanta riga-kafi, dan ka hana ni cutar da shi, sai dai ka riga ka makar...
Ζaisar ya ce "Kai ne ka makara, dan cutarwar da ka yi masa a ciki ma bai yi tasiri ba. Kar ka manta Bil'adama ce. Kar ka manta aiki aka baka ka shafe wancan tunanin nasa, ba ka taΙa tunanin zai tuna waye shi ba, sai ga shi yanzu ya tuna waye shi, dan haka wannan ma baka da tabbacin zai manta rayuwarsu har abada"
Giyaz ya ce "Za ka gani, ka zuba ido zaka ce na gaya maka, duk wata hanya da zan bi na tsohe farincikin yarinyar nan na Ζuntata mata sai na yi"
"Kana tunanin akwai sauran wahalar da ta rage wadda ba ta sha ba a baya? Haryanzu ba ka san suwaye biladama ba, waΙanda ka ke ta'amalli da su miyagun cikinsu ne, hatsabibancinsu kawai ka ke gani. Amma wannan karon ne za mu yi fito na fito na gasken gaske tsakanin ni da kai a kan yarinyar nan. Kar ka manta ka fi ni shekaru da daΙewa a duniya, hasali ma kai ka haife ni, amma ni marubuci ne, kuma manazarci sannan masanin magunguna kar ka Ζetare iyaka, zan iya baka mamaki."
Giyaz ya sake kecewa da dariya ya ce "Gaskiya ne marubuci, kuma masanin magani, ka buΙe wannan kwalbar idan ka isa ya tuna waye shi saboda ka taimaki uwar gijiyar ka, ka faranta mata.
Ζaisar ya ce "Kai ka yi imani da cewa ka rufe tunaninsa a kwalba, amma kai zan cewa ka zuba ido ka ga ikon Allah"
Giyaz ya ce "Shikenan ina zuba ido" daga haka ya Ιace Ιat daga libraryn.
Har bayan azahar Imam yana tare da Asal, sai dai da aka kawo abincin rana, ba Nana ce ta kawo ba, Asal ta yi ta bala'i a kan kar wanda ta sake gani a sashen, idan ba a nemi izini ba ko kuma idan Nana ce ta kawo ba.
Ta kira Imam da nufin ya ci abincin rana, sai dai ya yi loma biyu ya kalli Asal ya yi shiru, ya tsiyayo shayi daga cikin haΙaΙiyar butar shayin, ya kai bakinsa, ya Ιan sha kaΙan ya ajiye, ya Ιauki robar madara ya buΙe yana sha.
"Amour" ta furta a shagwaΙe ya Ιaga idanunsa ya kalle ta.
"Ba ka ci abincin ba fa"
Ya girgiza kai ya ce "Ba irin na jiya ba ne"
"To wai meye a cikin na jiyan ne da ya sanya shi daban?"
Ya girgiza kai ya ce "Nima ban sani ba, kawai dai wannan Ιin ban ji ΙanΙanonsa ba, kin san haryanzu jikin nawa sai a hankali, ba na cin abinci sai da na dawo Ιin nan"
"Kuku fa na samo maka mussaman daga Nigeria, ta iya girki ita ta yi maka na jiyan ma, sai dai muguwar kidahuma ce, kuma ba ta da kirki amma ina da tabbacin ba za ta cutar da mu ba, a can gidan cin abinci na MaraΙi na Ιaukko ta mussaman saboda kai" Ya jinjina mata kai tare da yi mata alamar jinjina.
Sai dai a baΙini cikin ΖwaΖwalwarsa, Nigeria da ta ambata sai da tsigar jikinsa ta tashi, gabansa kuma ya faΙi. Duk dabarun da Asal yakamata ta yi ta saka ya ci abincin nan ya Ζo ci, ya sha madarar raΖumi ya ce ta ishe shi ba sai ya ci abincin ba.
Asal ta ΙanΙana Abincin, sai dai ba ta ji wani rashin ΙanΙano ba, abincin ya yi daΙi amma shi ya ce babu ΙanΙano.
Da daddare Asal ta tafi ta yi wanka, ta je ta samu Nana, idan ba ta yi girkin daren ba, za ta gwada mata mene ne matsayinta a gidan.
Sai dai Ιangaren Nana, tun da ta ji su Ramata duk sun ruΙe, wai an yi girki Imam ya Ζi ci, Asal sai bala'i take yi, kuma ta ce kar su sake dafa wani abu a kai masa muddin ba Nana ba ce ba.
Yana zaune yana kallon labarai, shikaΙai a falon ya ji yanayinsa ya fara canzawa. Ya yi shiru yana tunanin me yake shirin faruwa da shi ne haka.
Ta turo Ζofar Ιakin ta shigo da sallama, tana shigowa idanunsa suka haΙe lokaci guda. A zahiri ya ga shocking Ιin da jikin Nana ya yi, dan sai da farantin hannunta ya yi rawa. Sai dai shi ma na sa jikin ya yi, amma da sauri ta sunkuyar da kanta. Gabanta ya yi mummunan faΙuwa bayan ganin Giyaz da ta yi a tsaye a gefen Sayyid yana kallon ta yana dariya.
Ya Ζura mata ido yana son gane wani abu da shi kansa bai san mene ne ba.
"Ita ce 'yar Nigeria da Asal ta samo?" Ya tambayi kansa a zuciyarsa.
Zaucewa ya kusa yi, bayan da Nana ta Ζaraso daf da shi ta ajiye farantin, ya ji Ζamshin turaren sa na tashi a jikinta.
Ko da Nana ta Ιago ta saci kallonsa, ta gan shi a nutse yana kallon talabijin Ιin sa yana kaΙa Ζafafuwansa, kamar ma bai san Ιan Adam ya wanzu a gurin ba.
Tuni hawaye ya cika mata ido, ganin mutumin da ta yi rayuwa mai cike da so da Ζauna tare da shi, abokin wasanta abokin hirarta, ya zame mata wani na daban a yanzu. Ba ta kai Ζofa ba Asal ta Ζwala mata kira.
Ta yi maza ta goge hawayenta ta juyo.
Wani abu ya caki zuciyar Nana, ganin Asal da wata 'yar riga a da guntun wando, babu kunya ko makamancin ganin idon Nana ta ce "Zo zan gabatar wa da amour ke"
Ta zauna a kusa da shi tamkar za ta shige cikinsa, ta ce "Imam, ga wadda nake gaya maka, kukun da na samo maka 'yar Nigeria"
Sayyid ya yi wa Asal wani kallo yana Ιan lumshe ido, Nana tamkar ta zunduma ihu, sassaucin da ta samu Ιaya shi ne ganin Ζirjin Asal babu wani abin kirki na jan hankali, duk da yadda ta taΖarΖare tana banΖarewa. Guntun tsaki ya kusa Ζwacewa Nana.
A hankali cikin magana daki-daki ya ce "Babu masu girki a Niger, har sai an tsallaka Nigeria?"
"Eh mana, duk dan saboda na burgeka ne" ta yi maganar cikin shagwaΙa tana shafa sajensa.
"Idan ba ki burgenin ba fa?"
"Haba Imam, me yasa haka dan Allah?"
"Na ji, amma idan ta girka a samu mai kawowa ba na son ta din ga shigo mini nan"
Nana ta kalle shi, zuciyarta ta tsananta bugawa.
"Gaskiya Imam ba na son barorin nan su din ga shigowa sashenka, mugwayen munafukai ne duk nan yadda da su ba, ba kuma zai yiwu maza su din ga shigo mini"
Ya buΙe baki zai yi magana, Nana ta tsare shi da ido.
Asal ta kalle ta ta ce "Je ki kawai sai da safe, rigima yake ji" Nana gani take kamar da gayya Asal take wannan abubuwan.
Ba ta san lokacin da ta furta "Shegiya" ba a hankali.
Bayan fitar ta, Asal ta ce "Imam me yasa baka son ta din ga shigowa ne?"
Ya lumshe idanunsa ya buΙe ya ce "Tsoro take bani, idan na ganta gabana faΙuwa yake yi."
A zaton Asal, Nanan muni ta yi masa, shi yasa baya Ζaunar ganinta, dan haka wani irin farinciki ya kama ta, ta ci gaba da lallaΙa shi a kan ya yi haΖuri Nana ta din ga shigowa sashen tana kawo masa abincin.
Shiru ya yi mata ganin ba ta fahimci mai yake nufi ba, dan da suka yi ido huΙu da Nanan gani ya yi tamkar ta na yi masa kallon tuhuma, shi da bai taΙa ganinta ba, da zai iya zai so ya samu dama ya tambaye ta, ya ji ko laifi ya yi mata. Ko kuma ma ba mutum ba ce ba, da yake jin jikinsa ya canza a duk lokacin da ya ganta.
Sai dai ya ci Abincin da ta kawo, da daddaren.
Nana kuwa rabi da kwata kwanan tsaye ta yi, tayi kukan har ta gaji. Ita yanzu kawai ta zuba wa sarautar Allah ido.
Furucin Sayyid ya rusa duk wani Ζwarin gwiwa da take da shi.
Da safe kuwa da ta yi girkin, da wuri ta kai cikin ikon Allah, ba kowa a falon.
Kusan awa Ιaya da rabi da kai Abincin aka aiko kiran Nana, ta san za a rina, saboda abin da ta aikata, ta san dole a neme ta.
Kanta tsaye ta shiga falon Imam, ta tarar da fuskarsa jawur hatta idonsa ma ya yi ja.
Asal cikin bala'i ta hau Nana da faΙa.
"Kashe mini miji za ki yi? Na Ιaukko ki ina tunanin za ki yi abin arziki, amma ki yi yinΖurin kashe shi, ban gaya miki sharaΙin wani abu ya samu mijina a dalilin abincinki ba?"
AREWABOOKS
Nana ta zuba wa Asal ido, sannan ta kalle shi ta mayar da idonta ga Asal ta ce "To ai ni ba ki gaya mini me na yi ba"
"A kan me za ki cika yaji a cikin abinci ki cika tafarnuwa? Bayan ba ya son abinci mai yaji da yawa"
"Ki daina yi mini faΙa, tun da ba ki gaya mini baya cin abinci mai yaji ba, kuskure ne bai kamata ki yi mini faΙa ba dan yau Ιaya na yi kuskure ba, amma bari na ΙanΙana Abincin na ji, sai na ga me zan gyara a gaba"
Ta nufe shi gadan-gadan ta kalli fuskarsa, yadda ta koma sak lokacin suna tare, tana ba shi abinci mai yaji, ba zai yi magana ba sai dai ta gani a fuskarsa.
Ta durΖusa ta Ιauki cokalin da ya ci abinci da shi, ta Ιiba ta kai bakinta, ta Ιago suka yi ido huΙu da shi, ya sunkuyar da kansa da sauri.
Ta risunar da kai ta ce "Tuba nake Shugaba, na yi kuskure in sha Allah zan kiyaye hakan ba zan sake ba. Ba a gaya mini ba ka cin yaji da yawa ba ne, amma zan kiyaye"
Ya sake Ιaga ido suka yi ido huΙu. Ya rintse idanunsa yana tunanin wace ce wannan? Meye haΙinsa da ita jikinsa yake rikicewa a duk lokacin da ya ganta? Sai dai duk da wannan tambayoyin da yake da su, kalmar shugaba da ta kira shi da ita, ta din ga yawo a cikin kansa.
Nana ta miΖe tsaye ta kalli Asal da tsaya tamkar ta fashe, ta ce "Dan Allah ku yi haΖuri zan sake kiyayewa, ba zan sake maimaita kuskuren da na yi ba".
Kawai Asal ta janyo Nana, cikin mamaki take kallon Asal. "Nana ina ki ka samu wannan turaren?"
Cikin rashin fahimta Nana ta ce "Wane turaren?"
"Wanda yake tashi a jikinki, Imam ba ka ji ba?"
Shi dai ya yi shiru bai ce komai ba.
Nana ta Ιage hijjabin jikinta, doguwar rigar da aka ba ta ta bayyana a jikinta da tamkar sai da aka aunata aka ba ta ta ce "Rigar da aka ba ni ce take Ζamshin, nima a haka aka bani ita"
Ta tsaya tana yi wa Nana kallon tuhuma da rashin gamsuwa da abin da ta faΙa, sannan babban abin da ya Ζara Ιaure mata kai, yadda Nanan yau take Ιauke da Ζwarin gwiwa yau.
"Cherie, ki sallame ta kawai ya wuce"
Asal ta saki Nana tana bin ta da kallo.
Ta ce "Na tafi da Abincin na dafo wani ne?"
Asal za ta yi magana ya ce "A'a"
Nana ta Ιauki farantin Abincin nata ta yi waje tana murmushin nasara, dan ta fuskanci ta fara dagula wa Asal lissafi.
*****
"Ba wai-wai nake ki ji ba, gaskiya ne Hammad ya dawo Agadez kuma cikin hayyacinsa ba hauka ba, ya aka yi haka ta faru, kuma har Sultan yana iΖirarin ya yi jinya ne a faransa, yanzu ya warke zai ci gaba da gudanar da ayyukan sa, yaya aka yi aka haihu a ragaya?"
"Waye ya ce ya warke Ιin ne? Babu waraka a tattare da Imam Hammad"
"Amma kai ka ce zai haukace ya bar Ζasar nan baki Ιaya, amma ya dawo cikin Ζoshin lafiya, an ce ma wai jinya ya yi a faransa"
"Imam Hammad bai warke ba, kuma ba jinya ya yi a faransa ba, ya bar Ζasar nan ya yi nisa ya je ya yi rayuwar ΖasΖanci ba tare da tuna waye shi ba ma. Sai dai an samu mushkila inda ya tafi Ιin, wanda a can nake tunanin an Ιata mana fiye da rabin aikin ma, akwai dai yadda aka yi aka gano inda yake, amma tabbas ya yi nisa da gida ba tare da sanin waye shi ba. Amma warkewa kam bai warke ba, an samu matsala ne wani ya shiga cikin aikin ya Ιata wani abu , amma wannan ce gaΙar da ta fi cancanta mu sake hargitsa shi, za a Ζara Ζaimi a kan aikin, komai zai tafi yadda yakamata, a Ζaryata Sultan ya kunyata a idon duniya, a lokacin da Ιan nasa abin Ζaunarsa zai yi hauka tuburan duniya ta sani"
"To shikenan, ina nan ina zuba ido, ina kuma jiran ji daga gare ka, da kuma abin da zai faru."
*****
Nana ta girka Abincin rana, ta shirya shi a kan tray, ta je ta ajiye a falon Imam.
Ta ja ta tsaya ta Ζi tafiya.
Ta daΙe a tsaye, kafin su fito tare da Asal. Ganinsu taren ba Ζaramin dukan Nana ya yi ba, amma ta danne ta koma gefe ta sunkuyar da kai.
Ja ya yi ya tsaya, saboda yana kusanto Nana, yana jin tamkar zuciyarsa za ta tsaga Ζirjinsa ta fito, ya din ga jin tamkar zai fita hayyacinsa.
Asal ta kalle shi ta ce "Yaya dai?" Ya Ιaga kai ya kalli inda Nana take, kawai ya juya ya koma Ιaki.
Ta Ζaraso gaban Nana ta ce "Ke ya aka yi ne? Ba cewa na yi miki, ki din ga ajiye abincin ki tafi ba?"
Nana ta haΙiye wani abu mai Ιaci ta ce "Ki yi haΖuri, dama wata alfarma zan nema na a gurinki"
"Ta me?"
"Kin ce dole na kula da abin da mijinki zai din ga ci na yi taka tsantsan, to kuma gurin girkin yana can waje, duk da idan ina girki tsayawa nake yi a gurin girkin, amma ina jin tsoron kar wani ya shiga ya yi wani abu na ba dai-dai ba a yi zaton ko nice, shi ne na ce ko za a yi wa Ιakin girki mukulli a bani?"
Asal ta Ιan yi shiru, sannan ta ce "Kuma kin yi magana mai kyau, zan san abin yi in sha Allah, za ki iya tafiya" Bayan Nana ta fita, ta koma da bayata shiga Ιakin, ta tarar da shi a kan gado ya takure jikinsa ya yi shiru, jin motsinta ya sanya ya waiwayo.
"Imam, meyafaru ne wai?"
"Na ce miki yarinyar nan ta daina shigowa, bana jin daΙin jikina idan na ganta, ina kyautata zaton ma ba mutum ba ce ba"
Asal ta tuntsure da dariya ta ce "Mutum ce fa, dan dai kawai ba ka son hayaniya ne, kuma ba hankali ta cika ba. Amma ai Abincinta yana yi maka daΙi, shi ka ke ci fa, kuma idan ba ita ta yi ba baka ci"
Ya numfasa ya ce "Ni dai kar ki Ιaukko abin da zai zame mana matsala"
Ta karairaye murya ta ce "Imam ba zan taΙa kawo abin da zai cutar da mu ba, ka kwantar da hankalinka za ka daina ji, ka san ita ba Ζabilarmu ba ce, ba kuma 'yar Ζasarmu ba ce ba, shi yasa ka ke jin haka, amma ka kwantar da hankalinka"
Ya jinjina mata kai kawai bai ce komai ba, ya san ba za ta taΙa fuskantar halin da yake shiga ba.
*****
Yusra da Sagir su na zaune a falonsa, yana ta kallon agogon hannunsa, Shukura yake ta jira ta fito yana so ya haΙa su, ya yi musu nasiha, amma kusan awa guda da yi mata magana, amma shiru ba ta fito ba.
Ransa ya Ιaci da irin wannan wulaΖanci da take ta yi, ya rarrashe ta, ya ba ta haΖuri amma ta Ζi sauraren sa, sai wulaΖanci take yi masa yadda ranta ya ga dama. Ga shi yana tausayinta saboda tsohon ciki da yake jikinta, ga hawan jini, amma ko a jikinta tsakaninta da shi gaisuwa ce kawai, bayan wannan idan zai shekara yana magana, ba za ta kula shi ba, sai dai ya gaji ya tashi.
Yanzun ma har ya fusata zai je ya same ta, sai ga shi ta fito, fuskar nan babu annuri da alama ma fita za ta yi.
Ta zo ta nemi guri ta zauna, ta yi shiru ba ta ce komai ba.
Yusra ma ta kalle ta ta basar, ba ta kula ta ba.
"Mu na nan mu na ta jiran ki tun Ιazu, amma baki fito ba"
Fuska a Ιan tsuke ta ce "Shiryawa na tsaya yi ne"
"Ina za ki je ne?"
Ta kwaΙe fuska ta ce "Awo" Ta ba shi amsa a taΖaice.
Ya numfasa dan ba ya son biye mata, dan ya ga a kusa take, ko alamar ganin Yusra ba ta yi ba.
"Amm dama ba wani dalili ya sanya na tara ku a nan gaba Ιaya ba, ina son in gabatar muku da juna, sannan kuma na yi muku nasiha a kan haΙin kai da zaman lafiya.
Shukura kamar yadda ki ka sani tun da farko, kafin na aure ki, na auri Yusra sai dai Ζaddara ta gifta mun rabu. Ke ma kuma Yusra na sanar da ke bayan rabuwarmu na auri Shukura.
Dan haka ina mai roΖonku a kan zaman lafiya da haΖuri da juna, domin na samu nutsuwa na yi muku adalci.
Yusra ga Shukura, Shukura ga 'yar uwakki Yusra"
Da Ζyar Yusra ta ce "Sannu"
Haushi ya kama Shukura, wai sanni sai ka ce wadda take ciwo, da ya san zai dawo da Yusra dan me zai sake ta ya aure ta.
Sagir ya ce "Shukura tana yi miki magana fa"
Shukura ta ce "Hankalina na yana kan tafiyata Asibiti ne, ba na jin daΙin jikina. Amarya ina yi miki barka da zuwa, Allah ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya" Ta Ζarasa maganar tare da miΖewa da Ζyar.
"Shukura ki tsaya mana mu gama sai ki tafi"
Cikin fushi ta ce "Na ce maka fa bani da lafiya, kwana na yi ba na jin daΙin jikina"
Sai kuma ya tuna takaicin abin da take yi masa ya sanya bai je ya ganta da daddare ba, ya wuce gurin Yusra.
Shukura kuwa tuni ta nufi Ζofa, ya bi bayanta yana "Ki tsaya na sauke ki a Asibitin"
Ta girgiza kai ta ce "A'a ka koma gurin amaryarka, kar ka bar ta itakaΙai"
Jiki a sanyaye ya kira sunanta, ta Ιaga ido ta kalle shi. Idanunta sun yi jawur sun cika da hawaye.
Hannu ya sanya yana share mata hawayen da ya fara gangarowa kan kuncinta, ya ce "Dan Allah Shukura ki daina, ban dawo da Yusra dan na Ιata miki rai, ko na cutar da ke ba, wallahi kukan nan da ki ke yi da rashin walwalar ki yana damuna ba kaΙan ba, dan Allah ki daina"
Ta ce "Tom, bari na tafi kar na makara"
Ya ce "Bari na canzo kaya na zo na kai ki"
Ta ce "Kar ka damu, zan iya driving ai, yanzu zan dawo in sha Allah"
"To me za ki sayo mini idan kin tashi dawowa?"
Murmushin yaΖe ta yi ta ce "Me ka ke so?"
"Abin daΙi, sai kuma uwa uba ki Ζara yi mini murmushin nan dan Allah"
Murmushin ta sake yi tana taΙa jakarta.
Ya dafa cikinta ya ce "A dawo lafiya Allah ya tsare, ki kular mini da kan ku sosai. Dan Allah ki daina fushin nan da ni Shukura, kin ga yau zan dawo gurinki, kuma ina son zuwa inda ki ke amma yadda ki ke yi mini ne ba na jin daΙi, har fargabar zuwa inda ki ke nake yi. Dan Allah idan na zo kar ki haΙe mini rai dan Allah sweetheart"
"Tom"
"Tom Ιin nan kuwa ta kai zuci?"
Shukura ta ce "Ta kai mana"
"Yauwwa babyna, ina jiranki, ki dawo da wuri dan Allah"
"To in sha Allah"
Ya buΙe mata motar, yana jin daΙin yadda ta sakar masa fuska, tsayawa ya yi janta da hira, yana tsaye a bakin Ζofar motar, ita kuma tana ciki a zaune. Abin mata da miji sai ga Shukura tana dariya, da haka suka yi sallama ta fita.
Yusra kuwa sai da haushi ya kama ta, yadda ya yi ficewarsa ya je ya shantake a gurin Shukura, kamar ma ya manta da wanzuwarta a gurin.
*****
Duk yadda Asal take Ιokin Imam, gaba Ιaya gani take kamar ba a cikin nutsuwarsa yake ba, kamar wani abu yana damunsa, babu yadda ba ta yi ba a kan ya gaya mata mene ne yake damunsa ba, amma ya ce mata shi babu abin da yake damunsa.
A hankali ta yi juyi a kan gadon, ta zuba masa ido yadda yake ta uban gumi, tare da yin haki, har sai da ta Ιan tsorata. Sai dai ta ga ya yi juyi ya ci gaba da baccinsa.
Kwana biyu Nana ta daina yadda su haΙu, kamar yadda ya buΖata, sai dai yau da ta shiga ta tarar yana nan. Babu tsammani ya ga Nana, hakan ya sanya ya Ιan zabura, har sai da ta gani.
"Sayyid ina kwana" Shiru ya yi yana tunani, sai kuma ya maze bai motsa ba.
"Ban san laifin da na yi da ya sanya, ka nemi na daina zuwa inda ka ke ba, amma idan laifi na yi maka, ina neman afuwarka Sayyid"
Sannu a hankali kalmomin da ta yi amfani da su, suka din ga shigarsa Ιaya bayan Ιaya, yana jin kalaman na da wata fassara da yakamata ya sani, amma ya kasa gano fassarar, duk da yana jin yaren na hausa, kuma da shi ta yi maganar. Ζamshin turaren sa da Asal take faΙa, yanzu ma shi yake ji yana tashi a jikinta.
Ta miΖe ta yi waje cikin sanyin jiki, kawai ya tashi ya yinΖura, ya bi bayanta. Sai dai ya tsaya a bakin Ζofa yana tunanin to idan ya bi bayanta ina zai je, ko kuma me zai ce mata?. Kawai ya koma da baya ya nemi guri ya zauna.
*****
Satin bikin Abba ya kama, Hajiya Sa'a duk ta yi busy, Jamila kuma ta rage zuwa gidan gaba Ιaya.
Hajiya Sa'a tana ta jiran Abba za ta aike shi, amma shiru har sha Ιaya na safe bai fito ba, haushi ya kama ta dan muraran yake adawa da auren nan da zai yi.
Bala'i take ta yi, tare da alwashin Ιaukar mummunan mataki a kan Jamila. Dan a cewarta ita take ziga shi.
Ta shiga Ιakinsa tana bala'i, kawai ta gan shi a kwance yana bacci.
"Abba wannan wane irin bacci ne har haka? Kai da muke da hidima a gaba, dan ka nuna mini ban isa ba, shi ne za ka nemi guri ka yi ta baccin asara" Sai dai ya yi shiru bai tashi ba.
Ta Ζarasa ta Ιala masa duka a Ζafafuwansa, amma shiru bai tashi ba.
A iya saninta, Abba ba shi da nauyin bacci, amma yau dai abin ya yi yawa. Ta jirkita shi, ga mamakinta kawai ta gan jini a hancinsa, da bakinsa ga fatarsa ta yamutse jikinsa ya yi fari Ζwal. Sai dai yanayin jikin nasa ya nuna akwai nutsuwa a tattare da shi.
Wani irin magigicin ihu Hajiya Sa'a ta yi, ta hau kururuwa tana jijjiga gawar Abba, tana kiran sunansa da wata irin murya ta tashin hankali, girgiza shi take yi tana ihu da kururuwa a kan gawar, amma Abba rai ya riga ya yi halinsa.
Hajiya Sa'a ta tashi da gudu ta nufi cikin gidan, tana ihu tana kururuwa tana "Wayyo Allah na shiga uku, dan Allah ku zo ku taya ni duba Ιana me ya samu Abba, dan Allah ku taimake ni kar Abba ya mutu ya bar ni na shiga uku na lalace"
Tuni mutanen da ke gidan, suka fito aka je aka dudduba aka tabattar da mutuwar Abba.
Ζaya daga cikin Ζawayenta ta ce "Kuma ba guba ya sha ba, ko wani abu ko ba shi da lafiya?" Hajiya Sa'a babu baki sai kuka kawai da take yi.
Safiyya ta ja ta tayi waje da ita, ba su tsaya a ko ina ba sai bedroom Ιin ta.
"Hajiya me ki ka fahimta game da gawar Abba?"
Cikin kuka da tashin hankali ta ce "Ni ban fahimci komai ba"
"Duk wanda muka bayar a Ζungiya, yana zubar da jini ne ta hancinsa da bakinsa, kuma fatarsu haka take komawa, wani ya bayar da Abba a Ζungiyar Asiri, ko tamu ko wata Ζungiyar".
Wani irin ihu Hajiya Sa'a ta zunduma, Safiyya ta toshe mata baki tana faΙin "Hajiya ki rufa mana asiri kar ki tona mana asiri a gano mu"
Wayar Safiyya da ke aljihunta ce ta fara ringing, ta ciro ta sai ta ga Jamila ce take kiran wayar.
Ta kalli Hajiya Sa'a da ke zunduma ihu sannan ta Ιaga.
"Na san zuwa yanzu Hajiya tana cikin mawuyacin hali. Ba za ta iya Ιaga waya ba, amma ina taya mu jaje da ni da ita, Abba ya zama sadaukarwarmu na shekara da ni da ita. Ina fatan zuwa yanzu ta ji abin da ake ji, a duk lokacin da ta bayar da jinin wani ga Ζungiya, ina fatan Allah ya gafarta wa Abba sadaukarwar da ya yi, ya ceci masoyiyyarsa da kuma tseratar da Ιan Ζanin mahaifiyarsa, kuma Abba bai mutu ba, sai da ya san abin da muke aikatawa. Sannan ina taya mu murna, ina Ιauke da cikin Abba a jikina. Ba zan gushe ba ina yi wa Abba a addu'a, da yi masa fatan rahama. Abba mutumin kirki ne, kuma rayayye da ya fita daga cikin matacciya Allah ya sa ya huta"
75
Jamila ta katse wayarta, wani irin kuka ya Ζwace mata, ta din ga wani irin kuka mai gunji.
Mama ce ta faΙo Ιakin cikin damuwa ta kalli Jamila, ta ce "Jamila lafiya kuwa, nake jin kukanki tun daga tsakar gida?"
Jamila ta yi shiru tana ci gaba da gunjin kuka.
Cikin damuwa Mama ta ce "Jamila, ni fa na kasa gane miki a 'yan kwanakin nan, wai mene ne yake damunki ne? Gaba Ιaya ba ki da sukuni, ga koke-koke ko Hajiyar ce ta kore ki ne?"
Ta girgiza mata kai alamar a'a.
"To mene ne?"
"Dan Allah ki Ζyale ni na ji da abin da ya dame ni, Wayyo Allahna"
Duk yadda Mama ta kaΙa ta raya, ta yi rarrashin amma fafur Jamila ta Ζi magana, taΖi gaya mata halin da take ciki, haka ta gaji ta bar ta a Ιakin.
Tana fita Jamila ta Ζara rushewa da kuka, wani irin zafi take ji a Ζirjinta, soyayyar Abba ta din ga ji sabuwa fil a cikin ranta, ba ta taΙa tunanin al'amura za su kasance kamar yadda suka kasance a yanzu ba. Ji take tamkar ta kashe kanta ta huta, ko ita ma tattara ta shiga uwa duniya kamar yadda yayarta Nana ta yi.
*****
"Imam Asad, haba ba kar manta sunan naka, kai jarumi ne, ina mai tabbatar maka da cewa Hammad ba zai zama Sultan a Agadez ba, duk wannan abubuwan da Sultan yake yi da rawar Ζafar da yake yi, mun san abin da yake nufi, dan mun san inda baki ya karkata ta nan yawu yake zuba. Amma Hammad akwai abubuwan da ya rasa, da Ζa'idojin da bai cika ba, dan haka burin Sultan na Hammad ya maye gurbinsa ba zai taΙa yiwuwa ba har abada"
Imam Asad ya gyara zamansa, fuskarsa Ιauke da damuwa ya ce "Anya kuwa? Duk abin da Sultan yake so, dole shi muΖarrabansa za su yi su mara masa baya, ina jin tsoron ya furta Hammad ya maye gurbinsa, muddin ya furta ko yana raye ko ba ya raye, sai an zartar da shi, sai dai idan Hammad ne ya bar Duniya"
Mutumin ya ce "Kar ka yi la'akari da haka, ko me zai Ιauke mu zamu aikata, ko mene ne, babu wanda zai gaji Sultan sai Imam Asadullahi Jalal, dan haka ka ci gaba da ΖoΖari, burinmu dole ne ya cika"
Imam Asad ya jinjina kai cike da gamsuwa.
*****
Cikin damuwa Sagir yake kallon agogon hannunsa, yana sake kiran lambar Shukura, Ζarfe biyar da rabi na yamma amma shiru ba ta dawo ba.
Duk da Yusra sai da suka yi rigima da shi, a kan yadda ya tafi ya bar ta Ιazu, sai dai ta damu ganin fuskarsa babu walwala yana ta kallon waya.
"Baby wai wa ka ke ta kira haka ne?"
"Shukura nake kira, ta ce mini 9zata daΙe ba, tun safe da ta fita haryanzu ba ta dawo ba"
Yusra ta basar ba ta kuma cewa komai ba, sai dai abin ita ma sai ta ji hankalinta ya tashi, ganin har ya fita masallaci sallar magariba Shukura ba ta dawo ba.
Yana dawowa ya dubi Yusar ya ce "Ba ta dawo ba ko?"
"Eh ba ta dawo ba, ko ta biya wani gurin ne?"
Jiki a sanyaye ya ce "Ba na tunanin hakan, ko za ta biya wani gurin, duk faΙan da muka yi tana gaya mini, ba ma ta da yawan yawo, ba ta fiye son fita ba, idan ba gidansu za ta je ba. Bari na je gidansu, na kuma je Asibitin na ji"
"To Allah ya sa tana lafiya, to ko haihuwa ta yi a Asibitin suka riΖe ta, na ga cikin nata ma sha Allah ya tsufa sosai"
Ya girgiza kai ya ce "Da haihuwa za ta yi, da tuni an kira ni an sanar mini, bari na je na gani"
Yusra ta ce "To Allah ya sa tana nan lafiya dai"
Ya amsa da Amin, ya fita.
Gaba Ιaya sai Yusra ta ji hankalinta ya tashi.
Gidansu ya fara zuwa, ya shiga suka gaisa da Hajiya Amina, sai dai bai ga alamar Shukura ta je gidan ba, ya wayance da nufin zai tafi da Haidar, amma Haidar Ιin ya Ζi bin sa.
Hankali a tashe ya tafi Asibitin doctor Sabo, aka ce masa tun safe ta je awo, sha Ιaya da rabi kuma ta bar Asibitin, kamar yadda har a cc camera ya nuna.
Nan hankalin Sagir ya dunguzuma, ya Ζara ruΙewa ya burkice, duk inda yake tunanin Shukura za ta je, ya je bai same ta ba. Wayoyinta da su na shiga, amma suka daina.
Ya tafi gurin 'yan sanda ya kai report Ιin Ιatan Shukura, bai koma gida ba sai sha biyun dare.
Yusra na ganinsa ta tashi tana tambayarsa "Yaya an ganta?"
Jiki a sanyaye ya girgiza mata, take gabanta ya faΙi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya sa ba saboda ka dawo da ni ne ta tafi ba, Ubangiji Allah ya sa ta dawo, ni zan iya tafiya ma na bar muku gidan, idan zamana ne ba ta so ta bar gidan"
"Shukura ba za ta bar gidan nan saboda na dawo da ke ba. Dan kan ta fita mun yi magana ta fahimta da ita, mun daΙe mu na magana, ba saboda ke ne ta bar gidan nan ba"
Gaba Ιaya Sagir ya kasa rintsawa, sai damuwa da tashin hankali, haka ita ma Yusra, Ζarshe ma kuka ta saka tana cewa saboda ita ne Shukura ta fita ba ta dawo ba.
*****
Yau da Nana ta bushi iska, harabar gidan ta fita tana zagayawa, sai dai zuciyarta a cunkushe take, gaba Ιaya tunaninta yana kan Muhsin, kewar Ιanta take yi sosai da sosai, ga wannan azzalumar matar ta hana ta tafiya, sai dai ita kanta hankalinta ya rabu kashi-kashi ne, ga tunanin Muhsin ga kuma Sayyid da take ganin samu a lokaci guda take ganin rashi.
Sai a yau ta Ζara tabattar da girma da Ζasaitar gidan, ba ta taΙa ganin raΖumi da ake faΙa ba, sai yau a cikin gidan.
Ban da dawakai, da wasu dabbobin ma da ba ta san sunansu ba, ba kuma ta taΙa ganinsu ba.
Asal ta hango hannunta a cikin na Sayyid, an fito da wata danΖareriyar mota, sun shiga an ja sun fice. Nana ta tsaya ta yi shiru cikin damuwa.
Cikin matuΖar farin ciki dattijuwar matar fara Ζal, ta miΖe ta rungume Imam Hammad.
Cikin girmamawa ya durΖusa zai gaishe ta, amma ta hana shi ta ce "Ai ni yakamata na kwashi gaisuwa shugabana. Ina ta yi wa Sultan ciwon bakin ban gan ka ba, ya ce a bari ka huta kar wanda ya je gida aka dame ka, har sai ka fito dan kan ka"
Ya yi murmushi ya ce "Na same ku lafiya?"
Ta ce "Alhamdillah, sannu Imam Hammad, an sha jinya Ubangiji Allah ya sanya kaffara"
Asal ta ce "Wai ni ba za ki yi mini sanun ba, kin maze kamar ba ki ganni ba"
Matar ta ce "Wa yake ta taki, ga mara lafiya"
Gimbiya Bilkisu ta yi musu kyakykywar tarba, aka karrama su da Abinci kala-kala, amma ya Ζi ci. Hirar ma idan ta yi sai dai ya yi murmushi kawai, bai fiye tofawa ba.
Bayan sun gama da sashen Gimbiya, suka nufi sashen Sultan.
Imam Hammad na shiga falon Sultan, Sultan ya miΖe cikin farin ciki fuskarsa Ιauke da murmushi.
Abdou ma murmushin ya saki, cikin girmamawa suka gaisa.
Imam Nuradden, da Imam Asad duk su na tare da Sultan.
Cikin girmamawa suka gaida Hammad, fuskarsa Ιauke da murmushi ya amsa musu.
Sun taΙa hira kafin Sultan ya ce "Imam Hammad, zo muje ka raka ni tattaki mana, na miΖe Ζafafuwana"
Imam Asad ya ce "Sultan, mu ma mu yi maka rakiyar ne?"
"A'a ku da kullum muna tare ga baΖona da muka yi shekaru ba ma tare"
Yayi maganar yana riΖe hannun Hammad, suka fita ta wata Ζofa. Imam ya din ga kallon gidan tamkar baΖonsa, kamar ba a ciki yake rayuwa ba a baya.
"Hammad"
"Na'am Abi"
"Kamar wani abu yana damunka, ka gaya mini mene ne"
Imam ya yi murmushi ya ce "Babu abin da yake damuna, idan ma akwai ban san mene ne ba"
Sultan ya Ζara tattara hankalinsa a kan Hammad ya ce "Ka tabattar? ba ka fa da wanda zaka gaya wa dauwarka idan ba ni ba, ka daina wannan zurfin cikin Imam ba na so ka gaya mini"
"Babu abin da yake damun Hammad Ιinka fa"
Sultan ya yi murmushi yana dafa kafaΙar Hammad.
"Ka san haryanzu miskilin Ιan yaron nan, mai guje-guje a harabar nan nake gani, ya yi guje-gujensa ya faΙi ya ji ciwo, ya zo ya yi ta yi wa Abinsa kuka, ya ce sai na ce ciwon ya daina yi masa zafi, kuma na daki rama masa na daki Ζasar na rama masa"
Hammad ya yi dariya sai da haΖoransa suka bayyana ya ce "Duk da wannan gemun na fuskata haryanzu wannan Ιan yaron naka ka ke gani?"
"Eh mana, gani nake kamar jiya Sarah ta haifa mini kai. Allah ya jaddada rahama ga Umminka"
Ya amsa da Amin cikin sanyin jiki.
Sultan ya sake numfasawa ya ce "Hammad, haryanzu babu wani abu da ka iya tunawa bayan fara rashin lafiyarka?"
"Ban tuna komai ba"
Ya Ιago hannun Hammad ya ce "Bamu san fa inda zobenka yake ba haryanzu, abin ya dame ni, ina tsoron a farga da babu zoben nan, ina tsoron abin da ka iya biyo baya, idan aka gano babu zoben nan"
Ya kalli yatsun nasa ya ce "Abiena, duk abin da Allah ya Ζaddara zai faru dole zai faru ka daina damuwa. Ni yanzu ina mamakin Mamudu bai san ina Agadez ba ne?"
Sultan ya Ιan ji dumm, sai kuma ya ce "Ni na hana a sanar da dawowarka, sonake ka samu lafiya sosai, amma dole za a sanar masa da dawowarka"
Imam ya ce "Ni zan je na same shi, ya ganni a bazata"
Sultan ya ce "A'a zan saka a sanar masa, zai zo har gida ya same ka"
Ya ji daΙin kasancewa da mahaifinsa, sai dare sannan suka tafi gida tare da Asal. Duk wunin da suka yi bai ci komai ba, har suka koma gida.
Nana ta kammala aikinta na yau, ta yi wanka tana zaune a Ιakinta, tana karatun Alkur'ani. Kawai ta din ga jin kamar akwai wani abu da ba daidai ba.
Ta ajiye Alqur'anin ta tashi ta tafi Ιakin girkin Abincin Imam.
Wata mata ta gani ta kawo kai za ta fita daga kitchen Ιin, alahalin babu wanda yake shiga sai ita sai Balaraba ko Asal.
Nana ta ce "Baiwar Allah lafiya kuwa?"
"SaΖo ne aka bayar, ke ce mai girkin Imam, dan haka ke za ki kai masa"
Cikin rashin fahimta Nana ta ce "Wace ce ke? Kuma waye waye ya bayar da saΖon, kuma saΖon mene ne?"
"Ba ni da lokacin amsa tambayoyinki, babu ruwanki da kuma saΖon na mene ne, ga shi can na ajiye miki a cikin kitchen Ιin, kaiwa ne kawai naki"
Nana da mamaki ta bi matar ta kallo dan ba ta taΙa ganinta a gidan ba.
Ta shiga kitchen Ιin da sauri, ta fara kalle-kalle tana tsoron kar ta je wani abin cutarwa ne.
Wani Ιan kwando ta gani Ζarami, an nannaΙe shi ba za ta iya ganin mene ne a ciki ba.
Wata zuciyar ta raya mata, ta kwance ta ga mene ne a ciki, wata kuma ta hana ta,sai dai har ta gama grkin dare tana kallon kwandon tana tunanin mene ne a ciki? Waye zai bayar da saΖo babu suna, kuma me yasa sai ita za ta kai? yanayin saΖon dai kamar babu gaskiya a lamarin.
Da fargaba ta haΙa da Ιan kwandon ta nufi sashinsa gabanta yana faΙuwa.
Yau shikaΙai ne a zaune, babu Asal. Duk da ruΙewar da yake yi idan ya ganta, amma ya ji daΙin ganin ta kawo masa Abinci, dan tun safe bai sake cin komai ba.
Sai dai yau ba iya faΙuwar gaban yake ji ba, har da wata Ζara, mara daΙin ji makamanciyar wadda ya din ga ji daren da zai fara ciwo.
Ta ajiye kwanukan ta ce "Barka da yammaci Sayyid, fatan ka na lafiya."
"Alhamdillah" ya furta ba tare da ya shirya hakan ba, yana mamakin daga ina wannan sautin yake. Ita kanta Nana ba ta zata zai amsa mata gaisuwar da ta yi masa ba.
Ganin babu Asal a gurin, ya sanya Nana zuba masa Abinci da shayi. Ta kalle shi duk da yadda yake yi mata wani irin kwarjini da a baya bata taΙa zaton yana da shi ba ta ce "Ko yanzu ma sai na ΙanΙana?"
Ya girgiza kai alamar a'a. Ya sauka daga kan kujerar, yana jin Ζarar nan na ci gaba da addabar kunnuwansa.
Cike da son basar da abin da yake ji, dan gujewaa sake faruwar abin da ya faru a wancan karon, ya yi Bismillah ya fara cin abincin.
Duk da a takure yake da yadda take kallonsa, kuma ba zai taΙa iya cin abinci a gaban wanda bai kamata ya ci ba, amma ya kasa yi mata magana, kuma bai ji hakan da ya yi a matsayin wani laifi ba a matsayin sa na Ιan gidan mulki ba, wanda hakan yana cikin kamewa da suke da ita, musamman ma shi da hakan ya haΙu da Ιabi'unsa.
"Sayyid, ina jin yadda mutanen gidan nan suke yabon ka, sosai da sosai da yabon karamcinka. Duk da a baya ban so zuwa gidan nan aiki ba, amma sai dai na ji babu daΙi da yadda ni ban samu wannan karamcin daga gare ka ba, sai ma Ζyama da ka ke nuna mini, da Ζabilanci ban sani ba ko dan ni ba Ζabilarku ba ce, kuma ba 'yar Ζasarku ba ce ba, shi ya sanya ka ke yi mini haka. Amma ina neman afuwa idan na faΙi wani abu ba daidai ba ko ya Ιata maka rai, bana nufin hakan shugabana"
Gaba Ιaya babu tsoro ko fargabar Asal ta fito ta tarar da ita a ranta, daΙi ma ta ji na ko ba komai yau ta keΙe tare da shi.
A wannan karon ma, jin maganganun nata ya din ga yi da matuΖar muhimmanci. Yaya zai yi mata bayanin ba tsanarta ya yi ba, baya iya tantance abin da ruhinsa da gangar jikinsa ke nufi a kanta ne. Shirun da ta ga ya yi, da yadda yake jujjuya cokalin ya sanya ta yin ajiyar zuciya, ganin alamun saΖonninta na isa kai tsaye inda take so.
Ta nuna masa kwandon da aka bayar aka ce a ba shi, ta tashi ta fita.
Kitchen ta koma tana Ζarasa goge-goge, kawai. Sai dai ta ji alamun mutum a bayanta. Ta waiwaya ta gan shi a tsaye a Ζofar kitchen Ιin, idanunsa jawur, ga Giyaz a gefensa, cikin suffarsa ta tsohon nan mara kyan gani.
Ya fara takowa cikin kitchen Ιin, yana kusanto ta, gabanta yana faΙuwa ta zuba masa ido.
Ya Ιago mata wata takarda Ιauke da hoton Ζwarangwal yana ci da wuta, an rubuta Imam Hammad Jalaludeen a jiki.
"Waye ya bayar da wannan saΖon?"
Kan Nana ya sara mafarkin da ta taΙa yi, ya fara ΖoΖarin zuwar mata kanta.
"Waye na ce waye ya bayar da wannan saΖon?" Ya yi maganar cikin wata irin murya da ba ta taΙa jin sa da ita ba a rayuwar da suka yi!!!
Cikin rawar murya ta ce "Nima ban sani ba, saΖo ne kawai aka ba ni aka ce na baka"
"Waye? Waye ya bayar da saΖon? Ki gaya mini?"
Ta kame jikinta cikin tsoro ta ce "Ban santa ba wata ce?"
Launin idonsa ne ya fara canzawa, baΖar Ζwayar idon ta Ιauke, sai farin kawai.
"Giyaz" Nana ta furta a hankali.
AREWABOOKS.
Jikinsa ne ya fara Ζamewa, fitilun kitchen Ιin suka Ιauke gaba Ιaya, ta ce "A wannan karon me ka ke buΖata kuma?"
Muryar Giyaz ta din ga ji, yana wata irin dariya. "Ai dama na gaya miki, ki jira dawowata".
"Na fi Ζarfinka, a waccan rayuwar da ya yi, da wannan Ιin ma, na fi Ζarfinka har abada".
"Kar 'yar Ζaramar Ζwarin gwiwar da wancan yaron ya baki, ya sanya ki yi tunanin za ki iya yi mini wani abu, mu zuba mu gani".
Nana ji ta yi abu ya faΙo jikinta mai nauyi, suka faΙi Ζasa tare. Wal hasken fitilar kitchen Ιin ya dawo. Imam ta gani a kwance a gefenta.
Da sauri Nana ta nufe shi, jikinta na rawa za ta taΙa shi.
Amma ta ganta itakaΙai a Ιakin karatun Ζaisar, cikin azama ta tashi tana waige-waige, ta ga Ζaisar a tsaya a bayanta.
"Yana ina?" Ta faΙa a sanyaye.
"Na san abin da ki ke ji, amma ya yi wuri, kuskure kaΙan za ki aikata ki lalata komai. Kar ki yi mamakin a din ga bibiyarki, saboda zaΙar ki da matar nan ta yi a matsayin mai dafa abincinsa, kuskure kaΙan ki na iya kwana a ciki ki shiga matsala. Kuma Giyaz zai yi ta tunzura ki, har ki yi wani abin da za ki saka kan ki a zargi. Ki din ga bin komai a hankali"
Nana ta yi ajiyar zuciya, itakaΙai ta san abin da take ji, a kan Sayyid. Dan a gare ta gara lokacin da ya Ιata ba ganinsa take yi ba, amma yanzu ga ta ga shi, amma ya yi mata nisa.
*****
Sagir kuwa ya zama tamkar zararre, aka kwana uku babu Shukura babu labarinta, sai a kwana na uku ya sanar da gidansu Shukura halin da ake ciki.
Hajiya Amina ta gigice ta rasa inda za ta tsoma ranta. Hankalinta ya yi mummunan tashi.
Alhaji Zailani ya din ga yi wa Sagir bala'i, a kan me tun Ιatan Shukura bai gaya musu ba sai yanzu.
Aka Ζara sanar da jami'an tsaro, aka kuma baza komar neman Shukura.
****
Ummi ce ta kawowa Baba ziyara, sai dai yanzu Baba duk ya zama abin tausayi, duk inda ya zauna sai da ya ja uban tagumi ya yi shiru, da ya samu dama kuma sai ya hau zancen Nana. Yanzun ma hirar da yake ta yi wa Ummi kenan.
"Ummi kin ga Nana haryanzu shiru ko? Babu ita babu Ιan uwanta, shi ma tun wannan zuwan da ya yi bai sake zuwa gidan nan ba. Gara shi namiji ne ita kuwa ban san halin da take ciki ba. Nan gida kuma ita Suwaiba yanzu ba ta da maraba da mahaukaciya, na ce a kaita Asibiti babarta ta Ζi yarda.
Ita ma Jamila 'yan kwanakin nan, gaba Ιaya ba na gane kanta, dama kuma babarta ta nuna mini in daina shiga sabgarsu 'yarta ce, saboda abin Duniya"
Ummi ta ce "Gaskiya ne Baba, abin duk babu daΙi kam, amma Baba wani abun an bar gini tun ran zane ne, wannan abubuwan tun daga tushe yakamata a ce an yi wani abu na kaucewa farwuarsu, yanzu sai dai a yi ta haΖuri ana gaya wa Allah. Ta dai Ιan ba shi baki sannan ta tashi ta shiga cikin gidan.
Suka gaisa da Mama a tsakar gida, suka hau hira.
"Wai ina Jamila ne?"
Mama ta ce "Tana Ιaki"
"Amma tana ji na zo, ta yi burus?" Ta yi maganar tana leΖa Ιakin.
Ta tarar da Jamila a kwance ta yi rigingine.
"Jamila yau 'yar shariya ce babu magana ma?"
Jamila ta yinΖura ta tashi zaune, suka gaisa sama-sama.
"Wai ba ki da lafiya ne?"
Ta jinjina kai alamar eh.
"Jamila kin fiye yawan rashin lafiya, Allah ya kawo mana siriki mu sha biki. Ta ga dai mutanen gidan nasu duk sai a hankali, ta yi musu sallama ta tafi.
Hajiya Sa'a tamkar za ta haukace, kwana uku amma sai an yi da gaske take cin abinci kaΙan.
Ta rame ta zabge kamar ta shekara tana larura.
Ko gaisuwar aka yi mata ba ta iya amsawa, idanunta suka koΙe suka yi jawur.
Mutane da dama sun ji mutuwar Abba, saboda mutuwar fuju'a ga matashi, tana taΙa zukata, mussaman Abban da yake mutumin kirki ne, ga girmama mutane.
Ranar da Abba ya kwana uku da rasuwa, Safiyya ta samu Hajiya Sa'a a Ιaki, ta ce "Hajiya yanzu mene ne abin yi, wani matakin ki ke ganin za ki Ιauka a kan wannan lamarin?"
Hajiya Sa'a ta sunkuyar da kai hawaye na zuba daga idanunta ta ce "Duk matakin da zan Ιauka, kafin mutuwarsa yakamata na Ιauke shi, dana sani nake mara amfani na janyo yarinyar nan jikina, sannan idan na matsa, tsaf za ta tona mana asiri, dan haka ba zan saurare ta a yanzu ba, ina cikin matsanancin kewa da alhinin rashin tilon Ιana. Sai dai wallahi sai ta tafi inda Abba ya tafi, ko da kuwa nima zan rasa raina na"
Jiki a sanyaye ta ce "Hajiya ki bi a hankali, kar garin neman gira a rasa idanu"
"Ki zuba ido kawai" ta faΙa a taΖaice tana share hawaye.
Kiraye-kirayen sallar asuba ne ya sanya Nana farkawa, ta ganta a Ιakinta a kwance, ba ta iya tuna abun da ya faru ba tun daga biyo ta da Sayyid ya yi.
Ta kalli Ζwan fitilar Ιakin a kunne, ta yinΖura za ta tashi, kawai ta takardar nan, da ya nuna mata yake tambayarta waye ya aiko da ita.
A tsorace ta ja gefe, tana kallon takardar. Jikinta na rawa bakinta Ιauke da addu'a, ta Ιauki takardar ta sake Ζare mata kallo. Ta ninke ta ta saka a cikin kayanta, ta shiga banΙaki.
*****
Nana na tsaka da aiki a kitchen, ta ji motsi a kitchen Ιin.
Ta waiwaya ta kalli inda take jin motsin, ta ga Asal.
Cike da takaicin babu yadda ta iya, ta ce mata "Barka da safiya"
"Barka, amm na ce akwai abin da ya faru ne? Imam ya ce lallai a tsananta tsaro a gurin girkin nan, ki gaya mini idan da wani abu da ya faru?"
Nana ta girgiza kai ta ce "A'a babu wani abu da ya faru fa"
Asal ta ce "Kar na kama ki da aikata rashin gaskiya, hukuncin da zan yi miki sai kin gwammace kiΙa da karatu" Nana ta yi mata shiru, a ranta ta ce "Kya ji da shi"
Asal ta juya ta fita, Nana ta raka ta da harara.
Mahmudu ne durΖushe a kan gwiwoyinsa, a gaban Abdou matawalle.
Ya numfasa ya dube shi ya ce "Imam Hammad ya samu lafiya, ya dawo Nijar"
Mahmudu ya Ιago kai a zabure, yana kallon Matawalle.
"Ka sani, koma me ka ke yi masa da ka ke mallake shi, mu na sane mun zaba maka ido,mun yi maka talala ne mu ga gudun ruwanka. Tun da ya sako Ζafarsa a Ζasar nan, tun ma yana can, yake zancenka yana cewa kana ina?. To ka tsaya da kyau ka saurare ni, zamu sake ka amma hakan ba ya nufin ka yi 'yanci ne, ko kuma mun daina zarginka, mu na nan mu na saka maka ido a ΖarΖashin takunkumi za mu sake ka.
Sannan kar ka kuskura ka gaya wa Imam batun sace shi da ka yi da rayuwar da ya yi a Nigeria. Dan babu yadda ba a yi ya tuna wani abu ba, amma abu ya gagara. Dan haka ba a buΖatar ya san ya yi wata rayuwa a Nigeria, balle maganar nan ta fita, idan kuwa ka bari a ka ji maganar nan a waje, hukuncin da zai biyo baya ba zai yi maka daΙi ba.
Wannan saΖo ne daga Sultan, ba a buΖatar ya san ya yi wata rayuwar daban, dole ka ja bakinka ka tsuke. Dan ka san hukuncin kisa shi ya dace da kai, an Ιaga maka Ζafa ne, saboda son da Imam yake yi maka, ba a buΖatar abin da zai taΙa masa zuciya"
Mahmudu ya saci kallon Matawalle, yana jin zafin yadda mutumin nan yake Ιora masa sace Imam.
Haka nan ya risuna ya yi wa Matwalle godiya.
*****
Asal ce zaune a gaban Sultan, yake yi mata magana cikin nutsuwa da dattaku.
"Yarinyar kirki, na san za ki yi mamakin sake kiran ki da na yi, duk da jiya kun zo gidan nan, to ina da baΖi ne ban samu mun yi magana ba a jiya, shi ya sanya na ce ki zo yau ina son ganinki"
Asal ta jinjina kai, tana saurarensa cikin nutsuwa.
"Na san kin Ιauki dogon lokaci mijinki baya kusa da ke, wasu faΙi tashin duk da ke aka yi kin san komai. To ga shi Ubangiji Allah ya yi masa dawowa cikin aminci. Sai dai duk da haka haryanzu bai gama samun lafiya ba. Dan Allah dan Annabi ina roΖon ki, ki zama mai haΖuri da juriya da kuma rufa masa asiri. Kin san yadda yake da magauta ta kowacce kusurwa, dan Allah ina sake roΖon ki, ki zama rufin asiri ga Imam, duk abin da ki ka gani wanda ba ki yadda da shi ba, ki zo ki sanar mini ban yarda ki gaya wa kowa ba. Dan Allah ki yi haΖuri da shi ya samu nutsuwa da kwanciyar hankali daga gare ki"
Ta jinjina kai ta ce "In sha Allah Abie, ba zaka same ni da wata matsala ba, zan zama mai rufa wa mijina asiri"
"Na gode sosai da sosai, Ubangiji Allah ya yi muku albarka, ya baku zuriya ta gari masu jin Ζai"
"Amin Abbie, muna godiya sosai da sosai"
Sosai Imam Hammad yake son ya ci gaba da gudanar da al'amuransa da ayyukansa da yake yi, kamar a baya, amma abu ya gagara gaba Ιaya ji yake komai ya fita daga ransa. Jin jikinsa yake yi kamar a ΙaΙΙaure duniyar sam ba ta yi masa daΙi, ga shi takamaima bai san abin da yake damunsa ba.
Sultan ne ya aika da mota aka Ιauke shi, bai san ina za a kai shi ba, bai kuma tambaya ba. Gidan da ake sauke baΖin Sultan nan aka kai shi. Sai ya fara mamakin ko wata ganawar zai yi da baΖin, amma Sultan bai gaya masa ba?.
Sai dai babu zato babu tsammani ya ga Mahmudu.
Cikin matsanancin farin ciki suka nufi juna, Imam ya ce "Mahmudu" Ya rungume shi cikin farin ciki. Sai dai wata irin karaya ta shiga zuciyar Mahmoud.
Imam ya ce "Tun da na dawo nake cigiyarka, na ce ko ba ka san na dawo ba, a Faransa ma sai da na roΖi a kawo mini kai, mu zauna tare na yi jinyar, amma ba a bani dama ba" sai dai jin sheshsheΖar kukan Mahmoud ya Ιaga masa hankali, ya Ιago shi cikin damuwa ya ce "Mahmoud, ko na yi maka wani abu ne?"
Ya girgiza kai yana share hawayensa ya ce "Ai ba ka yi mini laifi, ko me za ka yi mini a duniya kuwa. Murna ce da kewa ta sanya ni kuka"
Jiki a sanyaye ya ce "Dan Allah ka bari, zuciyata ta karaya nima" Sai dai maimakon ya yi shirun, tamkar tunzura shi ya yi, ya sake fashewa da kuka.
Hawaye ne ya cika idanun Imam, ya ce "Dan Allah ka gaya mini idan wani abin ne ya faru, duk ka sanya jikina ya yi sanyi, kamar ban taΙa ganin kana kuka ba"
Ya share hawayensa ya yi ajiyar zuciya ya ce "Na ce maka murna ce kawai nake da ganinka ya shugabana, ina fatan ka dawo cikin Ζoshin lafiya"
Ya yi tsaki ya ce "Za ka fara ko? Waye shugaban naka?"
"Kai mana Allah ya baka nasara"
Kawai ya yi wata dariya ya ce '"Ka ci gaba, zan rama ne"
Mahmudu ya yi dariyar shi ma ya ce "Ba zan iya fasalta adadin yadda na yi kewar ka ba, da farincikin da nake ciki, a sanadin dawowarka ba"
Imam ya ce "Na fika murna da ganinka"
Duk da yau suka haΙu tun dawowarsa, amma ji yake kamar ya gaya wa Mahmudu abubuwan da yake ji, amma sai ya fasa ya ga kamar ya yi wuri.
Shi kuma Mahmudu zuciyarsa cike take da karaya, da kuma tunanin tayaya zai gaya wa Imam Hammad cewa ya yi aure a Nigeria, alhalin ga kashedin da aka yi masa. Ita Nana da suka baro a Nigeria mene ne matsayinta. Ya tuna irin Ιawainiyar da ta din ga yi da shi, da rayuwar da suka yi, amma alamu ya nuna sam Hammad bai san an yi hakan na, dan da ya tuna zai yi masa maganar. A ransa ya yanke dole ya shirya da kansa ya tafi Nigeria neman Nana, kuma ko me za a yi masa idan ya gano ta, dole ya kawo ta ya gabatar da abin da ya faru, ko da hakan yana nufin a yanke masa hukuncin kisa ne, gara ya yi da ya mutu da hakkin Nana a kansa.
Ya din ga mamaki da tambayar kansa, yaya aka yi a wannan karon, Imam ya dawo hayyacinsa ya sake mantawa da rayuwarsa da Nana, bakinsa fal tambayoyi amma babu halin furta su, saboda kashedin da aka riga aka yi masa.
Tare da Mahmoud suka zauna suka sha hira sai dai abincin da aka shirya musu, Imam ya Ζi ci.
"Imam, wai ya na ga ba ka cin abincin ne?"
"Abincin da ya fito daga hannu Ιaya ne tal yake yi mini ΙanΙano a bakina yanzu, idan ba shi ba duk wanda na ci salam nake ji"
Cikin mamaki ya ce "Abincin wani hannu kenan?"
Ya Ιan yi shiru ya ce "Asal ce ta kawo wata mai yin girki daga Nigeria, idan ba ita ta dafa ba, ba na gane kan Abincin"
Ζwarewa Mahmud ya yi, Hammad ya miΖa masa ruwa yana yi masa sannu, ya yi shiru ya ce "Daga Nigeria kuma?"
"Eh"
"Lallai Imam ka na da rigima, amma duk Nijar sai da aka tsallaka Nigeria aka samo ta?"
Ya Ιan Ιage kafaΙa ya ce "Ka san rigimar Asal, wai a gurin cin abincin MaraΙi ta gano ta, ta kawo ta nan. Zan saka ta yi girki ka zo ka ci"
Mahmoud ya jinjina kai, daga bisani ya kawar da zancen, yana ci gaba da lissafa yadda za je Nigeria ya taho da Nana, dan ya san tun da Hammad ya dawo, yanzu duk inda za shi su na tare.
Da Ζwarin gwiwa yanzu Nana take girki, kasancewar ta sa wanda take yi wa girkin.
Bayan da Nana ta kammala girkin rana tana shirin, kai wa sashen Imam, Asal ta same ta ta ce "Ba sai kin kai wa Imam Abinci ba, baya nan sai dare zai dawo, ki shirya masa abincin dare kawai"
Nana ta amsa mata da to.
Tun da Imam ya dawo, yake kaiwa yana komowa yana jiran ya ga ta ina za a kawo Abinci, saboda yunwar da yake ji. Ga shi dududu Ζarfe goma ya dawo, amma Asal har ta kwanta bacci. Ya yi hamma bai san adadinta ba, saboda yunwar da yake ji.
Sallamar Nana ta saka ya kalli hanyar shigowa, wannan karon a kwando ta zubo kayan Abincin.
Sai dai yau saΙanin hijjabi, doguwar riga ce a jikinta milk, da mayafin rigar. Tun da ta yi sallama ya amsa a Ζasan maΖoshinsa ya sunkuyar da kansa Ζasa bai kuma magana ba.
Ta Ζarasa ta ajiye kwamdon, ta sauke kwanukan, har za ta yi masa zancen saΖon nan da aka bayar, sai ta fasa dan kar ta wargaza shirinta. Da wani na iya ganin halin da zuciyar wani ke ciki, da Imam ya daΙe da jin kunya, saboda bugun zuciyarsa, ga wani irin azalzalarsa da take yi, ya sake kallon Nana, dan ba ya tunanin ya taΙa ganin wanda doguwar riga ta yi kyau kamar baΖar kukunsa 'yar Nigeria.
Ta zuzzuba masa abincin, ga kayan marmari ga kuma shayi na musamman.
Da ta zuzzuba masa.
Ta numfasa ta ce "Ζazu na yi girkin rana, aka sanar mini da baka nan, na ce duk lokacin da ba zaka kasance a gida ba, ina son a yi mini izini na dafa maka ka fita da shi, ba zan so shugabana ya kasance da yunwa ba, tun da alhakina ne girka maka Abinci" Ta yi maganar cikin girmamawa tana sunkuyar da kai.
Jin ya yi shiru ya sanya ta Ιaga kanta, ta ga tuni ya Ιauki shayi ya kai bakinsa yana sha. Kawai ta Ιan juya Ζwayar idonta, tare da yin murmushi. Sai da ya kusa Ζwarewa, saboda tabbas ya san irin wannan kallon, amma a ina? Yana matuΖar son ya yi mata magana, amma ba ya iya wa. Nana ba ta ba shi damar Ιaukar wani mataki ba, ta tashi ta nufi hanyar fita. Tun da ta tashi ya bi ta da ido har ta fice.
Abin duniya duk ya dame shi, Nana kuwa ta cika da murna, ganin saΖonninta na isa yadda take so, sai dai tana buΖatar Ζara samun kusanci da shi.
Cikin marairaicewa yake kallonta, fuskarsa Ιauke da damuwa ganin yadda take kuka tamkar ranta zai fita, ga shi ta yi duhu ta rame, ba kamar yadda ya santa ba a baya.
"Ma vie, ki yi mini afuwa, ba laifina ba ne, ina jin yadda ruhinki yake motsi a cikin jikina, dan Allah kar ki yi fushi da ni ki yi mini uzuri " Ya yi maganar yana ΖoΖarin rungume ta ya rarrashe ta. Ja da baya ta yi tana girgiza masa kai tana kuka ta ce "Ba ka so na Sayyid, ka yada alΖawari ka tafi ka bar ni, ka manta da ni, ka bar ni da dakon ruhinka, da ya hanani sukuni sai da na fito nemanka, ba ka yi mini adalci ba Sayyid"
"Ma vie, ban ya da alΖawari ba, gangar jikina ce a Nijar, amma ruhina yana Nigeria dan Allah ma vie"
Asal ta yi Ζuri da ido tana kallon yadda ya haΙa gumi a cikin bacci, sai numfarfashi yake yi da kyar yana faΙin "Ma vie, ke rayuwata ce, ban yi miki butulci ba"
AYSHERCOOL
1K NE VIA 0069685771
Aisha Adam stanbic bank
08081012143
76
Asal ta zuba masa ido tana kallon ikon Allah.
Shiru ta yi jikinta ya yi sanyi tana kallonsa, sai dai ta yi shiru ta ci gaba da kallonsa. A razane ya farka, sai dai ya juya ya ci gaba da baccinsa.
Da safe ya lura da Asal ba ta walwala, ta Ζi sakin jiki da shi ma gaba Ιaya.
Har ya share ta sai kuma ya tambaye ta ko lafiya?
"Lafiya kalau" ta amsa masa a taΖaice.
Ya fita Ιan tattaki, yana jin mafarkin da ya yi a jikinsa, amma ya kasa tuna mafarkin abin da ya yi. Cikin girmamawa ma'aikatan ke ta risunawa su na gaishe shi.
Babu yabo babu fallasa ya din ga amsa musu. Zuwa Ζarfe goma Nana ta kammala girki. Sai dai yau ba su haΙu ba kwata-kwata.
Har lumshe idanunsa yake yi bayan da ya sha kunun gyaΙar da ta yi, ga lafiyayyen Ζosai mai zafi.
Ya karya tsaf ya gama, Asal ta fito daga Ιaki ta cika ta batse. Kallo Ιaya ya yi mata ya maze, ganin ya basar da ita ya sanya ta Ζura masa ido ya kalle ta, yana mamakin dalilin da ya sanya ta ke yi masa wannan kallon.
"Imam ina fatan inda ka tafi, ba cin amanata ka yi ba"
Kallon rashin fahimta ya yi mata ya ce "Me ki ke nufi?"
"Ni kaina ban kai ga tantance abin da nake nufi ba, amma na fara ganin wasu abubuwa me da ban gane musu ba, abin ya tsaro ta ni ne"
Ya ce "Yi mini bayani"
"Ka na kiran wata da rayuwarka a cikin baccinka"
Ya yi mata Ζuri da ido, sannan ya ce "Kin tabattaa?"
"Ba ka yarda ba Ζarya nake yi maka kenan?"
"A'a ban ce haka ba, amma kin ce bacci nake yi, kin ga mai bacci kuma bai san abin da yake aikatawa ba. WataΖila shirmen mafarki ne kawai, wataΖila ma ke na gani a cikin baccin nake kira da rayuwata"
Sai kuma ta yi murmushi ta ce "Kuma haka ne, wallahi har na ji zuciyata ta yi sanyi, ka yi haΖuri da abin da na yi "
Ya yi murmushi yana kashingiΙa ya ce "Ban haΖura ba tukuna"
Ta ce "Ai ba zan sake ba, ina kishinka ne sosai. Da ina da hali ko fita sai ka daina yi. Ina sane da duk masu ΖoΖarin yi maka kyautar 'ya'aynsu su na so ka aura. Imam kai nawa ne nikaΙai Imam Hammad, babu wata mace da za ta iya samun kafar da za ta shiga zuciyarka. Inda na gode wa Allah, ka yi daban Imam, ba ka da rawar kai, da kule-kulen nan, da ko a cikin barorin nan, da suke rawar Ζafa ka yi saΙaka da su, sai ka saurare su. Shi yasa nake Ζara ΖoΖarin na kare gidana ina fatan ba ka ga laifina ba"
Ya sanya hannunsa yana shafa gashin kanta, ya ΖanΖance idanunsa yana kallonta, daga bisani ya saki murmushi ya ce "Gimbiya Asal, sarauniyar mata masu kishi ta duk faΙin Agadez"
Ta zumΙura baki ta ce "Ta duk Duniya dai, ni in dai a kan ka ne. Da ina da yadda zan yi ma sai ka daina kallon kowace mace, sai maza kawai" Ta yi maganar har cikin zuciyarta.
Kawai ya kama dariya, dan shi gaba Ιaya dariya ma ta ba shi.
"Ya ka ke dariya kuma?"
Hammad ya ce "To ya ba zan yi dariya ba, ina ji ina gani an bani kyautar mata na mayar da hannun kyauta"
Fuskarta Ιauke da damuwa ta ce "Dama ka na so kenan?"
"To waye ba ya son mace? Ina so mana. Amma tawa kawai"
"So ka ke sai ka saka ni kuka" Ta yi maganar idanunta na cika da hawaye.
Lumshe idanunsa ya yi yana buΙewa, yana kallonta. "Ga abinci ki karya" Ta noΖe kafaΙa.
Nana ce ta yi sallama, Asal ta kalli inda ta shigo, ta tsuke fuska haka kurum yau ta ji haushin Nana ya ninku a zuciyarta.
Nana ta yi saurin sunkuyar da kanta, dan Asal a zaune take a kan cinyar Sayyid.
"Zan kwashe kwanuka" ta yi maganar muryarta har harΙewa take yi, saboda abin da ya taso mata.
"To ni dai yanzu ka kira ni da rayuwarka a zahiri, tun da ka ce ni ka ke kira a mafarki" Ta yi maganar kamar ba ta san Nana ta shigo ba.
Ras gaban Nana ya faΙi, ya lumshe idanunsa yana murmushi ya Ζi magana.
Kawai Nana ta fusata ta tattare kwanukan za ta yi waje.
"Malama ki ajiye ban karya ba, ki fita kya dawo ki kwashe" Ko waiwayowa Nana ba ta yi ba, wata irin zabura ta yi cikin matsanancin fushi, amma ya riΖe ta ya ce "Cherie na sha gaya miki, irin wannan halayen naki ga na Ζasa da ke, babu abin da za su janyo miki sai tsana da raini. Ita kuma rayuwa a na son ko kana guzurin maΖiyi ka yi na masoyi"
"Amma Amour kana kallon abin da ta yi mini, ko sau Ιaya sai na sanya a ladabtar da yarinyar nan ta san matsayina a gidan nan"
Ya ce "A'a, ke ce baki kyauta ba abin da ki ka yi. Ita ba ta tashi cikin jerin hadimanki ba, kawai dai kin Ιaukko ta ta yi miki aiki ne, dan haka sai kin din ga yi mata uzuri"
"Wane uzuri ne ba na yi mata, abin da ta yi mini wulaΖanci ne tana sane, ban da yadda take kula da abincinka na aminta da ita a kan hakan, da sai na hora ta sannan na kore ta ta bar gidan nan"
"Shikenan ki yi yadda ki ke so, tun da ba zan faΙa ki ji ba"
Ya yi maganar yana ture ta daga jikinsa.
"Imam fushi ka yi da ni a kan wannan mummunar yarinyar?"
"Ba a kanta na yi fushi ba, yadda ba kya jin magana ne ya Ιata mini rai, idan ki ka ci gaba da sanya wa ma'aikatanki Ζiyayyarki, babu abin da ba za a iya haΙa kai da su a yi miki ba. Idan na isa a bar maganar nan. Ba na son yadda ki ke tafiyar da ma'aikatanki wasu lokutan, ba na son yawan shiga maganar ne, amma raina ki za su yi"
Asal ta yi shiru ta tsuke fuska, ta sauka daga kan cinyarsa baki Ιaya.
****
Alhaji Fatuhu ma duk da yadda yake fama da kansa, sai da ya je gurin jana'izar Abba, kuma da shi aka yi zaman makoki. Ya ji mutuwar nan sosai da sosai, saboda Abba mutuminsa ne. Ko da yake jinya a sati ya kan je sau biyu ko uku duba shi. Ya kan zauna su yi hira sosai mussaman idan ya tarar jikin nasa da sauΖi.
Kusan kullum Hajiya Sa'a gani take mafarki take yi, idan aka wayi gari za ta ga Abba bai mutu ba, amma ta ga babu alamun hakan. Ba ta Ζara kiΙimewa ba sai ma da aka yi kwana bakwai da mutuwar, kowa ya watse ya bar gidan.
Ζakin Abba ta tafi da daddare, ta buΙe Ιakin tana rintse idanunta tana jin tamkar za ta gan shi ya Ιago, da wannan murmushin nasa irin na fuskar mahifinsa.
Amma ta ga Ιakin nasa wayam, babu komai.
Wasu irin zafafan hawaye suka shiga sintiri a kan kumatunta, ba ta taΙa dana sanin shiga Ζungiyar asiri da duk wasu miyagun laifuka da take aikatawa ba, sai da ta rasa tilon Ιan da Allah ya ba ta a rayuwa. Wanda babu irin ΖoΖarin da ba ta yi, domin ganin ta kare shi da sadaukarwar Ζungiya. Ashe bonono ta yi rufe da Ιarawo bayan janyo Jamila cikin harkar Ζungiya, wanda ta yi hakan ne, domin janyo Jamila kusa da ita yadda za ta samu mallakar jinin Nana.
Ta zauna a gaban Ζatuwar katifarsa, ta din ga wani irin kuka mai sauti, da sai da Ζirjinta ya fara yi mata zafi.
*****
Asal ce zaune a kan carfet, saman kujerar da take kai kuma wani babban mutum ne, cikin shigar buzaye, kansa Ιauke da rawani.
"Ki na ji na da kyau ko?"
Ta jinjina kai cikin nutsuwa, ko ΖwaΖΖwaran motsi ba ta yi.
"Ina fatan haryanzu ba ki manta dalilin da ya sanya ki ka auri Hammad ba"
Ta amsa da "Eh ban manta ba"
"To barka, yanzu ya dawo, kuma babu abin da zai canza, za ki ci gaba da gudanar da aiki, kamar yadda yake a baya. Ba na buΖatar kuskure ko kuma wani uzuri. Duk wani motsinsa da duk abin da yakamata mu sani mai muhimmanci ki sanar da ni, idan kuma ki ka bari ni na gano ba ki sanar da ni ba, ranki zai yi mummunan Ιaci"
Jiki a sanyaye ta jinjina kai. "Dole a ci gaba da aiki tuΖuru, domin nesanta shi da kujerar Sultan, da mahaifinsa ke ta ΖoΖarin kusantar da shi da ita, mu na buΖatar kujerar nan ko ta halin ΖaΖa, dan haka ina nan ina saka miki ido da kuma sauraren ki"
Asal ta sake jinjina kai, jikinta babu Ζwari ta tashi ta fice.
Da Ζyar take Ιaga Ζafafuwanta, damuwa duk ta cika mata kai, ta ma rasa wane tunanin yakamata ta yi.
Da ta koma gida, ta tarar da hadimai na gyara Ιangaren Imam, ga Ζamshin turaren sa, da alama bai daΙe da fita ba.
Cikin tsawa ta kore su gaba Ιaya, ta ce su ajiye aikin su fita daga sashen, sannan su kira mata Nana. Jiki na rawa suka ajiye suka fita.
Nana tana tsaka da karatun Alkur'ani saΖon Asal ya iske ta, sai ta hau tunanin kiran me take yi mata. Duk da ta san abin da ta yi mata da safe.
Nana ta tashi cike da Ζwarin gwiwa, dan ji take yi daidai take da Asal, tun da duk abu dai ba za ta raba ta da ranta ba.
Nana ta shiga fuskarta a haΙe ita ma, ta shiga Ιakin ta tsaya, tana ta huci tana son ta balbale Nana da faΙa, sai kuma ta kasa ganin yadda Nanan ta tsuke fuska ita ma, ta yi mata wani irin kwarjini.
Amma duk da haka ta maze cikin dakiya da Ζarfin hali ta ce "Amm tambaya nake son yi miki, ban sani ba ko nice a ΖarΖashinki, da zan din ga yi miki magana kina ji na ki yi mini banza"
Nana ta Ιaga kai tana kallonta. "Ko ba ki gane me nake nufi ba ne? Abin da ki ka aikata da safe"
Nana ta ce "Na gane, gani na yi bai kamata na tsaya ina kallon ku a yanayin da ku ke ba, ko na din ga sauraren maganganunku ba. Hakan zai zama kamar munafunci ne, shi ya sanya na tafi, amma ki yi haΖuri"
Asal ta watsa mata wani banzan kallo cike da tsana ta yi Ζwafa sannan ta ce "Daga yanzu aikinki ba iya girkin Imam ba ne ba, har da gyaran sashen sa, ba na buΖatar kowa ya din ga raΙar inda yake."
"Amma Ιaukko ni ki ka yi na din ga girki kawai, ya za ki haΙa mini da aikin shara da goge-goge. Kuma masu yin aikin su uku ne, ni kuma nikaΙai ce, aikin bai yi mini yawa ba kuwa?"
"Kin san a kan kuΙi nawa na biya na Ιaukko ki? Ko a Nigeria ba na tunanin ko za a sayar da kaf danginku, za ku iya biyan kuΙin da na biya na karΙo ki ba. Dan haka ina da hurumin sanya ki duk abin da na ga dama"
"To Gimbiya Asal, babu damuwa zan yi abin da ki ke so. Duk da dangina ba za su iya biyan kuΙin da ki ka biya ba. Amma na san wataΖila mijina zai iya biya ya fanshe ni" Nana ta yi maganar tana murmushin da Asal ba ta gama gane kansa ba.
Nana ce ta Ζarasa aikin gyaran falon nan, ta yi goge-goge. HaΖurΖurtar da kanta ta din ga yi, da ta tuna mijinta take yi wa wannan aikin. Duk da ayyukan sun yi mata yawa. Ita dai fatanta Ubangiji Allah ya sanya Sayyid ya tuna ta domin ta san matsayinta.
Tana kammalawa ta koma kitchen, ta Ιora girkin rana. Ta kammala ta kai ajiye.
Ta Ζara goge Ιakin saboda ta san halin Asal sai ta tafi za ta huta, za ta sanya a kirawo ta, ta hau yi mata kinibibi da sanabe kala-kala.
Ta gama aikin goge-gogen kenan, ta gano wani photo album. Ta Ιauka ta nutsu tana dubawa, duk rubutun French ne a jiki.
Shafin Farko hoton Sultan ne, wanda ba dan yanayin shekaru da fuskarsa ta nuna ba, sai ka ce Imam Hammad ne, wanda tsananin kamannin har Muhsin da ta baro a gurin Nene.
Ta buΙe Ιaya shafin ta ga hoton wani, shi ma fari tas mai kama da su Sayyid sai dai shi ma babba ne. Kowanne a Ζasa da sunan sarautarsa.
Sai kuma ta shiga wani shafi mai Ιauke da hoton Sayyid a Ζasa an rubuta Imam Hammad Jalal Agadez. Wani murmushi ya suΙuce mata ta ce "Ka fi kowa kyau a cikin album Ιin nan Shugabana." Ta furta cikin murmushi. Hotunan wannan matasan da suka yi wa girki a gidan Sultan su ma kowanne da sunansa a Ζasa. Amma a farkon sunan kowanne da Imam.
Nana ta din ga mamakin to kowa ma Imam ne kenan?.
Muryar Asal ta jiyo sun nufo cikin falon, ta hanyar da take kyautata zaton a nan turakar Imam take, kuma tana tunanin Ιaya hanyar sashen Asal za ta mayar da kai, kai tsaye.
"Imam, wai ina zobenka ne?"
Ta yi maganar tana Ιago hannunsa, Nana kuma tana hango su daga inda take zaune.
"Ya karye yana gurin gyara"
"Gurin gyara kuma Imam? Ya za a yi dakakkiyar azurfa kamar wannan a ce ta karye? Ka san fa muhimmancin da zoben nan yake da shi a gurinka, ya za a yi ya karye?"
Daidai lokacin suka Ζaraso tsakiyar falon, ya ce "Zobe ya Ιata ban san inda yake ba, ina fatan kin gamsu yanzu. Kar ki sake yi mini maganarsa.
Yanzu zan fita, kar ki manta da saΖona"
Sai a lokacin suka ga Nana da ke zaune a cikin falon.
"Me ki ke yi a nan?" Asal ta tambaye ta.
"Babu komai, gyra Ιakin na yi"
"Kuma sai ki nemi guri ki zauna sai ka ce Ιakinki? Imam yana da baΖi anjima, za ki sake dafa wani abin, kuma za su sha shayi, ba na son wauta ko makamancin haka" Nana ta jinjina kai ta kalle shi ta ce "Barka da yammaci Sayyid, in sha Allah zan yi"
Asal ta Ιan yi shiru tana nazari jin ta kira shi Sayyid ba Imam ba.
A Ιan corridor Ιin ta tsaya tana zancen zuci, jin ana maganar zobe. Wane zoben kenan? Ko dai zoben da ya Ιauka ya ba ta ne? A'a ba ta tunanin haka wataΖila dai wani abin ne daban.
Gyaran murya da ya yi da Ζamshin turaren da ya cika gurin ne ya sanya ta farga ta waiwaya, sai ta ga a kan hanya ta tsaya.
Ta yi taku biyu ta ba shi guri, ya saci kallonta, zuciyarsa ta din ga raya masa son sanin wace ce ita, sanin na sosai ya yi mata tambayoyi game da wasu abubuwa.
Ya haΙiye yawu ya zo zai gifta ta, wani irin daddaΙan sanyi ya ratsa shi, sanyin da zai yi fatan dauwwama a cikin sa, saboda yadda ya saba da zafin jikinsa, wanda duk sanyin da yake guri, a cikin jikinsa yake jin wannan zafin.
Sai dai wannan sanyin da ya ratsa shi, har cikin Ζashinsa ya ji sanyin.
Ya sake waiwayawa ya kalli Nana, amma ya ga shi take kallo. Ji yake tamkar ya koma da baya ya Ζara samun kusanci da ita, sai ya fi jin sanyin sosai da sosai. Tun da Allah ya jarrabe shi da ciwon nan, bai taΙa jin sanyi mai daΙin wannan ya ratsa shi ba, kuma ya yi imani da Allah daga jikinta wannan sanyin yake, saboda sun samu kusanci sosai da sosai da zai gifta ta.
"Allah ya sa ba wani abin ake kuma shirya mini ko wani tarkon ake shirin yi mini da ke ba" Ya yi maganar a zuciyarsa.
Nana ta yi mamakin dalilin da ya sanya shi tsayawa haka.
Zuciyarsa ta din ga raya masa ya koma da baya, daf da Nana, ko zai fi kin sanyin yadda yake so.
AREWABOOKS
Nana ta ce "Sayyid ko wani abu ka ke buΖata ne?"
Sai da ta yi maganar sannan ya farga, bai ce mata komai ba kawai ya fice ya bar gurin.
****
Shukura ce a zaune ta takure jikinta, tana kallon kwanon abincin da aka kawo mata, Abinci mai rai da lafiya sai dai ko sha'awar kai wa bakinta ba ta yi ba, duk da uwar yunwar da take ji, tamkar ta ci babu.
Shiru ta yi tana tuna yadda bayan fitowarta daga Asibiti suka yi karo da wani mai adaidaita sahu.
Ya fito yana jarabar sai ta biya shi, duk da shi ne da laifi, amma ta kasa fitowa daga motar, ta sauke gilas ta ce ya gaya mata dammage Ιin nawa ta yi masa ta biya shi. Daga sauke glass Ιin nan ba ta sake sanin inda kanta yake ba, sai farkawa da ta yi ta ganta a wannan Ιakin, da sai dai a zuro mata abinci kawai.
Ba ta iya banbance adadin lokacin da ta kwashe a gurin ba, sai dai ta kintaci lokacin salla ta yi.
Babu tsammani ta ji an buΙe Ζofar Ιakin, hakan ya sanya ta kalli Ζofar da sauri.
Sai dai hasken fitilar mai wayarya haske mata ido, ba ta iya gane waye ba.
Sannu a hankali ya jingine wayar hannunsa ya zura mata ido.
Duk da ta Ιan razana amma abin bai wani ba ta mamaki sosai ba.
Ya zuba mata ido sannan ya ce "Kin yi mamaki ko?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba sosai ba"
"Ko me yasa?"
"Saboda jikina ya daΙe da bani hakan"
"Ta yaya kenan?"
"Na daΙe ina zarginka ne, sai dai ana ta dankwafe ni, an hanani"
"Gaskiya ne, ban so ki zurfafa ki takura da son sanin abin da bai kamata ki yi ta bibiya sai kin gano ba, amma ban san me ki ka gani ki ka dage kina bin diddigina ba"
"Zarginka nake yi da kai da doctor Sharif na kasa yadda Ιa na mutuwa ya yi, saboda har yau ina ji a jikina, mafarkin da na yi gaskiya ne"
Alhaji Zailani ya ce "Haka ne, lokuta da dama mafarki ishara ne, duk da ban san abin da ki ka gani ba, amma zarginki gaskiya ne duk da na yi iya yi na a kan na Ιoye komai, sai dai kashi kin zaΖe Shukura, soyayyar da nake yi miki ba za ta hana ni Ιaukar matakin da ya dace a kan ki ba"
Shukura ta yi ajiyar zuciya ta ce "Da gaske ka na da masaniya a kan batun mahaifar Mami?"
"Ina da ita, haka zalika ina da masaniya a kan jaririnki ma da ki ke ta zargina da Sharif a kai, duk da ban san me ki ka gani a mafarkin ba"
Shukura ta yi masa wani irin kallo, zuciyarta na bugawa da sauri da sauri.
"Tabbas mafarkinki ishara ne. Amma kafin na yi miki wannan bayanin ina son ki sani, talauci bala'i ne Shukura, babu yadda ban yi a kan na yi yaΖi da shi ba, amma abu ya gagara. Na faΙi na tashi na yi iya yi na amma na kasa nasara a rayuwata. Burina ya gaza cika na mallakar manyan motoci da gidaje da tara manyan kuΙaΙe yadda zan yi nesa da talauci.
'yar makarantar da nake taΖama da ita, abubuwa suka nemi Ζwace mini, bayan faΙuwa a jarrabbawa. A taΖaice dai a makaranta na samu Ζungiyar asiri na shiga, cike da burin na gama makaranta cikin sa'a da fatan cikar burikana na yin arziki mai yawan gaske ta hanya mai matuΖar sauΖi.
Bayan na auri mahaifiyarku, ta haifi Sadik, Ζungiya ta fara neman jini a gurina. Na bayar da babban Ιa na Sadik, na kaΙu na shiga tashin hankali, sai dai hakan ne zai ba ni damar taka babban matsayi a Ζungiyar, duk da na bayar da waΙanda ba jinina ba a Ζungiyar amma na ji zafin bayar da Sadik. Aka haifi Yusuf, aka haife ki, ba a sake neman kowa ba, sai da wata buΖata ta sake taso mini, wadda biyan buΖatar na buΖatar na Ζara taka wani matsayi a Ζungiyar.
Haka na bayar da matata ta fari, Hafsat da tsohon ciki, na saka mata Ζyallen jini a Ζasan shimfiΙarta ta tashi da ciwon naΖuda ta mutu a gurin haihuwa.
Hakan ya sanya dukiyata Ζara haΙaka, na yi kuΙi na yi suna. Duk fafutukar kasuwanci da muke yi tare da Fatuhu, shikaΙai yake abin sa, ni fakewa kawai nake yi da kasuwanci amma ta Ζungiyar asiri nake samun kuΙina.
Duk da ina samu ta kasuwancin ma, amma ga mamakina Fatuhu da baya Ζungiyar asiri, ya fi ni samun kuΙi, kuma duk inda muka je an fi son sa.
Bayan na auri Amina, aka buΖaci duk wani Ιa da za ta haifa, zan din ga ba wa dodon Ζungiya. Lamarin ya yi mini nauyi, saboda ina jin Ιacin rabuwa da iyalina. Na nemi sassauci, sai aka dasa wa Amina wani jaririn aljani a cikin mahaifarta, duk cikin da ta samu ba ma ta sani yake cinyewa. Sai dai kawai ta wayi gari tana zubar da jini, babu ΖaΖΖautawa. Karo shida na shidan saura Ζiris ta rasa ranta, saboda jini take zubarwa ba kaΙan ba, sai dai a yi ta saka mata jini.
Ba a taΙa gane Ιari take yi ba, an zata larura ce kawai, Asibiti aka kasa gane abin da yake damunta, na kuma hana a yi mata na hausa, tana zaune lafiya kawai sai ta hau zubar da jini babu ΖaΖΖautawa.
Ta damu ta damu da matsalar rashin haihuwa, amma na hana ta zuwa Asibiti ta ci gaba da bibiyar lafiyarta.
Ni kaina na damu da wahalar da take sha, sai aka nemi na sadaukar da mahaifarta gaba Ιaya ga wannan jaririn aljani, yadda ba sai ta ci gaba da samun ciki ba, cinyewar da yake tana azabtar da ita ba.
Haka na amince, cikin dare ta farka tana ihu da buge-bige, ina kunna fitila na haska, na ganmu a cikin jini male-male.
Na rirriΖe ta, amma ta fita daga hayyacinta, ihu kawai take tana riΖe mararta, a dole na Ιauke ta muka yi Asibiti, ganin za ta rasa ranta saboda zubar jinin nan. Ta fi kwana uku ba ta hayyacinta, jini kawai ake saka mata.
Aka tura mu scanic, domin a gano musababbin zubar jinin.
Na takurawa mai scanic Ιin ya gaya mini me ya gani. Ya sanar da ni babu mahaifa ma a jikinta gaba Ιaya, dan haka bai ma gano daga inda bleeding Ιin yake ba a scanic Ιin, sai dai a ci gaba da bincike.
Abin ya bani mamaki, duk da a cikin Ζungiyar asiri nake, ban taΙa tunanin za a ga abin a zahiri a yi scan a ga babu mahaifa ba.
Na biya mai scannnic kuΙi, ya rubuta sakamakon da ba daidai ba.
Muka koma gurin likita, aka din ga bincike ba a gane komai ba. Ita kuwa sai da ta shafe kwana goma ba ta tantance wanda yake kanta, har an fitar da rai da ita sai kuma ta warke.
Na daΙe ina tunanin abin da na yi mata saboda son da nake yi mata. Muka tattauna da malamina, da mamakin yadda a scanic Ιin aka gane bata da mahaifa ma zata a zahiri bs a za a gane ba.
Sai ya ce mini idan na ce haka na Ζaryata kungiyar asiri gaskiya ce kenan, amma ya aka yi na yadda da kuΙin da nake samu a cikinta, har nake kashe su a zahiri? Ya ce mini dole na san duk yadda zan yi na ci gaba da rufe mata ba ta da mahaifa, dan kar ta ce za ta bi diddigi duk da ko ta bi diddigin babu abin da za ta iya ganowa.
Wannan aljani haryanzu yana rayuwa a cikin Amina, gurbin da mahaifarta take, kan addabe ta da ciwo wasu lokutan, sannan wannan aljani shi ne yake saka ta zubar da jini lokaci zuwa lokaci da take tunanin Al'ada take yi. Wasu lokutan ta zubar da jini fiye da kima wanda take tunanin duk su ne dalilin rashin haihuwarta."
Cikin matuΖar tsoro da matsanancin mamakin yadda ya zauna ya wassafa mata wannan mummunan labarin da tun da ta buΙe ido a duniya ba ta taΙa jin labari mai razanarwa da tashin hankali ba.
Cikin matuΖar tsoro da matsanancin mamakin yadda ya zauna ya wassafa mata wannan mummunan labarin da tun da ta buΙe ido a duniya ba ta taΙa jin labari mai razanarwa da tashin hankali ba.
Da Ζyar ta harhaΙo kalmomin da ta ce "Kai ka kashe Mummy, kuma ka bayar da mahaifar Mami? Da..da.dama aljani duk zai iya yin irin wannan abin?"
Yayi dariya ya ce "Ki na mamaki ne? Kodayake mutane duk abin da ba a kanmu ya faru ba, bamu fiye yarda ba, nima da fari kasa yarda na yi, abin ya Ιaure mini kai. Sai dai idan ki ka duba, ba a taΙa yi wa Amina aiki ba, kuma babu alamar tabo na tiyata a jikinta, dan haka ta yaya za ta rasa mahaifarta? Aljani muddin za ka yi masa biyayya, ka yi abin da yake so, to zai zama mai biya maka dukkanin buΖatunka. Da su ake sihiri, da su ake jifa, neman shugabanci, Ιaukaka kungiyoyin asiri da makamantansu. Duk wani siddabaru da za a ce miki sun yi ba abin mamaki ba ne ba" Ya yi maganar yana wata 'yar guntuwar dariya.
Shukura ta Ζara rikicewa ta kiΙime. Ta ce "Yanzu Daddy, duk son da mahaifiyarmu ta yi maka kai ka kashe ta? Ga amanarmu da Mami ta riΖe ta kula da mu, ashe dama rashin haihuwarta da ciwon nan na zubar da jini da take yi babu gaira babu dalili, kai ne sila? Kai ka haddassa mata? Yanzu tayaya zaka nemi yafiyar su? Ka rasa imaninka saboda abin Duniya? Kai fa ka kashe su"
Ya ce "No in ji wa? Ai ban rasa imanina ba, ai annabi ya ce duk wanda ya ce La'ila ha illalahu zai shiga aljanna"
Cikin kuka ta ce "La'ila ha illalahu ba ta fatar baki ba Daddy, tayaya za ka shiga aljanna bayan ka kai buΖatarka gurin wanin Allah da ya buΖaci ka saΙa wa mahaliccinka dan ya biya maka buΖata. Me yasa ka ga buΖatar ka ta yi girman da ta gagari Ubangijinka ka dangana ga waninsa"
"Wannan wa'azin naki kin riga kin makara Shukura. Ina da yaΖinin zan tuba kan na mutu, kuma Allah zai yafe mini"
"Wa ya baka garantin ganin nan da awa Ιaya ma?" Ta yi maganar tana kuka mai tsuma zuciya.
"Ina da shi, dan ko ciwon kai sai na shekara ban yi ba"
Ya miΖe tsaye yana faΙin "Ki mayar da hankali ki din ga cin abinci, saboda ke da abin cikinki nake sanya ran ku zama sadsukarwar Ζarshe da zan yi a Ζungiya. Sai dai kafin nan, ina roΖon afuwarki ko ba komai ke ma kin ci albarkacin dukiyata. Ζanki da ki ka rasa ni na yi amfani da shi" Daga nan ya Ιauki wayarsa ya yi gaba abin sa hankalinsa a kwance, kamar bai aikata komai ba.
Wani irin gunji Shukura ta din ga yi tana kuka mai tsuma zuciya, ta din ga fatan ina ma mafarki ne ba gaske ba. Tabbas wannan babbar jarrabawa ce, a ce mutum irin mahaifinta shi ne mahaifinka, gara a ce an haife ka ba ta hanyar aure ba, ko makamancin haka. Amma uba irin Alhaji Zailani ba shi da wani amfani. Duk wata gwagwarmayar sa da faΙi tashinsa a kan iyalinsa ya zama na banza, a dalilin wannan mummunar hanyar mara Ιullewa.
Abubuwan da ya gaya mata sun shallake tunaninta, yanzu yadda ya tafi haka zai je ya ci gaba da rayuwa da Hajiya Amina duk da zaluncin da ya yi mata. Ta ji dama ta ba wa Sagir damar kai ta Asibiti wataΖila da ba a samu damar sace ta ba. Cikin kuka take roΖon Ubangiji Allah ya tona wa mahaifinta asiri, saboda a yadda zuciyarsa ta ΖeΖashe Ιin nan, babu wani abu na rashin imani da zalunci da ba zai iya aikatawa ba.
Can gida Sagir ko abinci ba ya iya ci. Yusra kuwa abin ka da ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba, sai ta kwanta rashin lafiya, saboda yadda ta addabi kanta da Ιorawa kanta alhakin Ιatan Shukura, dan cewa take saboda ta dawo gidan Sagir Shukura ta tafi.
Haka Hajiya Amina ma, Addu'a kawai take yi a kan Ubangiji Allah ya bayyana Shukura a duk inda take. Sosai take jin tamkar 'yar cikinta ce ta Ιata, tun tana daurewa har ta kasa ta fara zubar da hawaye, kasancewar babu wani labari mai daΙin ji da zai nuna an kusa gano inda Shukura take.
****
Asal ta na tsaye a banΙakin cikin Ιakinta, bayan tabattar da Imam baya Ιakin, ta danna wata lamba ta kira.
Can aka Ιauka mutumin ya ce "Na'am ina jin ki"
"Ina da labari ne"
"Ina sauraren ki"
Ta numfasa ta ce "Hannun Imam babu zobensa na tambari, na tambaye shi ya ce mini karyewa ya yi ya kai gyara, daga bisani kuma ya ce mini bai san inda yake ba"
"Kin tabattar da hakan, ba kuma Ιoye shi ya yi a wani gurin ba?"
Asal ta ce "Eh na tabattar ai zobe ne da ba ya cire shi, tun da ya dawo babu zoben a tare da shi"
Mutumin ya numfasa ya ce "Madalla, ki ci gaba da sanya ido da sanar da ni duk wani abu da yakamata na sani"
Ta jinjina kai tamkar yana ganinta ta kashe wayar ta fita.
Jikin Nana tamkar an yi mata duka, saboda azabar gajiya da ta yi. Ta kammala aikinta tana ta gyaran kitchen, sai ga Balaraba ta shigo da Ζatuwar jarka. Ta ajiye ta ta ce "Gashi nan madarar raΖumi ce da Imam yake sha"
"To sannu da ΖoΖari Mama Balaraba"
Ta ce "Yauwwa kukun Imam, Allah ya taimake ki"
Nana ta yi murmushi ta ce "Kar ki ba ni kunya mana"
"Ba kunya zan ba ki ba, ai ke yanzu duk wata kuku a gidan nan a ΖarΖashinki take, ke kaΙai ki ke dafa abincin da zai ci, dole mu girmama ki saboda kema shugabarmu ce"
"A'a ni ba shugabarku ba ce ba, ni da nake bare ma a cikinku. Amma dan Allah Mama Balaraba wai su wa ake cewa Imam Ιin nan ne? Dan na ga wanda ake kira da hakan da yawa"
"Eh su Biyar ne, galibinsu jikoki ne na gidan sarauta, su na cikin jerin waΙanda za su iya gadon kujerar Sultan. Shi Imam Hammad a gidansu su biyu ne da shi da Imam Abdallah, sai Imam Zahradeen shi ma jikan marigayi Sultan ne, akwai Imam Asadullah yayan Asal, sai Imam Omar, waΙannan su ne jerin waΙanda ake sanya ran za su gaji kujerar Sultan. Duk da su na ganin cewa Sultan na yanzu nuna son kai Ζarara na son Imam Hammad ya gaje shi a cikin yaransa. Imam Hammad yana da 'yan uwa da suke uba Ιaya amma su biyu ne suka cika Ζa'idojin zama Imam.
A Ζasar nan ana girmama duk wani Imam fiye da zatonki, mu na Ζasa mu na son Imam Hammad sosai mussaman baΖaΖen buzaye da fararen ke yi mana kallon kamar ba 'yan uwansu ne mu ba, bayinsu ne kawai.
Idan kin lura galibi hadiman gidan nan baΖaΖen buzaye ne, fararen kaΙan ne Ζarara yake ΖoΖarin yaΖi da kyamar da fararen buzaye suke yi mana, yana ta fafutukar nema mana 'yanci, da ΖoΖarin mu ma a din ga bamu dama a cikin shugabanci, bai kamata iyayenmu sun Ζare a bauta mu ma mu Ζare a haka ba. Amma manyan nan ba sa son shi sam, gani suke yana ΖoΖarin hana su rawar gaban hantsi. Ni tun da ya dawo ma duk ya canza mutum ne mai sanyin hali, amma kaifi Ιaya ne, ba sani babu sabo.
Shi ne shugaban majalisar duk Imam Ιin Ζasar nan. Duk da a cikin su akwai wanda suka girme masa, amma a haka dole su girmama shi kamar yadda yake a dokar Ζasar nan.
Tarihin masarautar Agadez yana da yawa da kuma faΙi Nana, bari na tafi na je na ci gaba da aikina.
Nana ta jinjina kai ta ce "To shikenan na gode sosai da sosai"
Bayan fitar Balaraba Nana ta naΙe hannunta a Ζirjinta, tana nazari da tunani.
Jiki a sanyaye ta koma Ιakinta, ta duba kayanta ta lalubo takardar nan da aka kawo saΖon aka ce a ba wa Sayyid. Ta Ζare wa takardar kallo.
"Ko a cikin Imams Ιin nan ne wani ya aiko da wannan takardar?" Ta yi maganar tana tuna maganganun da ta ji suna yi ranar da aka kai su yin girki a gidan Sultan. Ta koma ta lalubo zoben gurin Sayyid ta din ga jujjuya zoben ta ce "Ko kai a ke nema ne? Idan kai ne ta yaya zan ba shi abin sa, tun da ban san iya adadin muhimmancin sa a gare ka ba, idan na baka ka manta ni ta yaya zan yi bayani a yarda da ni?" Ta din ga surutai ita kaΙai ta gaji ta nannaΙe kayan ta buΙe jakar sarkin baka ta watsa takardar da zoben ta rufe ta ajiye a cikin kayanta.
Bayan sallar magariba aka sanar mata baΖin Imam sun iso, su na can sashin karΙar baΖin sa wanda Ιaki ne a can wajen lambun gidan.
A kwanduna ta shirya kulolin Abincin, Ιaya daga ma'aikatan gidan, ta taya ta kai wa.
Su na zazzaune a Ιakin, gaban su shaΖe da kayan marmari da uban soyayyen nama.
Duk wannan Imam Imam Ιin ne, gaba Ιaya zaune a gurin.
Ayabar hannun Sayyid ta kalla, da ya kai bakinsa ya gutsura fuskarsa Ιauke da murmushi. A take ta ga jini yana bin bakinsa, ayabar ta koma baΖa Ζirin, wasu abubuwa masu tsini tamkar Ζayoyi suka tsiro a jikinta.
Ayshercool
08081012143
77
Rikicewa ta yi, amma ta fara ΖoΖarin daidaita nutsuwarta dan ta san idan ta yi wani gangancin a gurin, babu lallai ta sha ta daΙin rai duba da girman mutanen da suke gurin a zaune.
Ganin ta tsaya ta zuba masa ido, ya sanya ya sauke hannunsa a hankali yana kallon ta shi ma.
Ta Ζarasa shigowa a hankali ta ajiye musu kwanukan abincin.
Zuba mata ido suka yi, gaba Ιaya suka yi shiru daga hirar da suke yi.
Ta ce "Shugabana, ga abincin ko zan jira ku duba idan da abin da bai yi ba?"
Ya girgiza kai ya ce "Za ki iya tafiya"
Sai dai ta kasa tashi, ta ci gaba da rarraba ido.
Ya sake cewa "Za ki iya tafiya"
"Dan Allah ka taimaka mini da ayabar hannunka, yunwa nake ji"
Imam Omar ya ce "Imam Hammad, wai wace ce wannan Ιin? Ta san waye kai kuwa abin hannunka za ka ba ta?"
Ya kalli ayabar ya kalle ta, bai kai ga yin magana ba, ta saka hannayenta biyu ta miΖa masa.
Tamkar soko haka ya miΖa mata ayabar, ba tare da musun komai ba.
Ya ce "Ga wata nan ki Ιauki yadda za ta ishe ki"
Ta girgiza kai ta ce "Wannan kawai ta ishe ni, na gode sosai da sosai"
Duk su ka bi Nana da ido, wasu cike da takaici, wasu kuma mamakin tsaurin idonta, duk da ba abin mamaki ba ne sosai, tun da ba ta san irin girmansu da matsayinsu ba, kasancewarta bare ba Ζabilarsu ba, kuma ba 'yar Ζasarsu ba.
A hankali ta saci kallon hannayensu, sai ta gan su sanye da zobunan nan irin na hannun Sayyid da ya Ιauka ya bata.
A take ta koma gefe ta cinye ayabar, sannan ta yinΖura ta tashi.
Imam Asad ya fara masifar wace mahaukaciyar haka, da za ta zo ta yi musu wannan rashin hankalin, su zuba ido su na kallonta.
Hammad ya ce "Ina mai baku haΖuri, baΖuwa ce a cikin lamarin gidan mulki, ku yi mata afuwa"
Nana tuni ta fice daga Ιakin, aikuwa fitarta ke da wuya, jiri ya fara Ιibanta, bango ta dafa tana bi a hankali, sai dai kan ta kai inda take so ta yanke jiki ta faΙi.
FaΙan Ζaisar ne ya sanya ta buΙe ido, a matuΖar galabaice.
"Waye ya ce da ki ka karΙa ki ci? Kin san abin da aka yi a jikin ayabar? Ban da na riga na buΙe miki ido ki na ganin abubuwa, da ba zan sake bari ki ga komai a kansa. Sai kin kashe kan ki a banza a kan mutumin nan, gaba Ιaya kin Ζarar da Ζarfinsa a kan ki, wanda ko tabbacin idan ya tuna ki zai miki irin wannan son ba ki da shi"
Nana dai kasa magana ta yi, saboda yadda jikinta yake a mace, duniyar take juya mata.
Ζaga bakinta ya yi ya zuba mata wani abu mai kama da turiri, ta yi wani yinΖuri ta hau amai ta hanci da bakinta.
Ba Ζaramin galabaita ta yi ba, jin yadda Ζayoyin da suka tsiro a jikin ayabar su na sukar Ζirjinta gurin yinΖurin aman da ta yi.
Cikin fusata mutumin yake magana, "Wane irin wawanci ne haka da shirme da rashin hankali, ta yaya zamu shirya abu ka je ka bari ya Ιaci?"
Cikin damuwa matashin ya ce "Wallahi Tafawa ba laifina ba ne ba, dan har ya fara ci wata yarinya ce ta hana shi ci, wai ya ba ta yunwa take ji"
"Wace yarinyar ce a kaf faΙin Agadez za ta je tsakiyar ku, har Imam zai ci abu ta ce ya bata? Ζaya daga cikin mugwayen Ιabi'unsa kenan da ya sanya yake zubar da kimar ku a idon mutane maΖasΖanta, har su samu zarafin raina ku. Ban da raini da wulaΖanci har baiwa ta ga abu a hannun Imam na Ζasar Agadez ta ce za ta ci."
Ya buΙe baki zai yi magana ya ce "Ka ga tashi ka bani guri ni kafin na mangare ka" Haka ya ja bakinsa ya tashi ya fice jikinsa a sanyaye.
*****
Alhaji Zailani ne a zaune a falon Hajiya Sa'a, ya je yi mata ta'aziyyar mutuwar Abba.
Ya numfasa ya ce "Wai dama Abban ba shi da lafiya ne?"
Ta girgiza kai ta wassafa masa dukkanin abin da ya faru.
Cikin kaΙuwa yake jin bayanin nata. Ya ce "Ban da ke Hajiya Sa'a, ina ke ina gayyato yarinya da rana tsaka ki janyo ta jikinki, ga shi ta zame miki masifa, haba Sa'a. Ke kin san ba kowa a ke fallasawa sirrin Ζungiya ba, Allah ya kyauta, ya yi mata gaisuwa ya tafi.
*****
Hammad tun bayan tafiyar sauran 'yan uwansa yake tunani daban-daban a ransa.
Tuni aka saita masa wayarsa, ya ci gaba da amfaninsa da ita.
Wayewar gari yana ta jiran Abinci amma shiru, ya gaji da jira saboda yana jin yunwa, ya tafi ya tashi Asal da take ta bacci.
"Imam lafiya kuwa?"
"Ba a kawo mini Abinci ba, ina jin yunwa zan fita"
Kamar ta yi tsaki, saboda ta ji daΙin baccin, haushi ya kama ta, tare da tunanin uban abin da ya hana Nana tashi ta yi masa girki ko ta makara haka.
Ga shi duk hadiman sashen ta kore su, dan haka ta tashi da kanta, ta fita.
A zaune ta tarar da Nana ta jingina da bango, idanunta duk sun faΙa kamar ta kwana tana amai da gudawa.
"Wani wulaΖancin ne ya sanya ba ki tashi kin yi wa Imam girki ba, har ki ka saka na biyo ki nan?"
Nana ta numfasa ta ce "Ba ni da lafiya ne"
"Ba ki da lafiya kuma Imam ba zai ci abinci ba? Kin san ba kowane Abinci yake ci ba"
Wani malulun takaici ya Ζule Nana, wato lafiyarta ba abin da yake gabanta ba ne, kawai fatanta ta yi wa mijinta girki tun da ga baiwa.
"Magana nake yi miki kin yi mini shiru"
"To me zan ce miki, ba ni da lafiya, ai ban taΙa Ζin yin girki ba. Ko wani abu da ki ka saka ni ba, amma yau ba ni da lafiya babu abin da zan iya yi. Idan ke ba za ki yi mini uzuri ba, ki gaya masa kukunsa babu lafiya na san, shi zai iya yi mini uzuri"
A hasale Asal ta buΙe baki za ta yi magana, Nana ta yi mata wani irin kallo, da a dole ta haΙiye maganganun da ta yi niyyar caΙa wa Nana.
Ta haΖura ta juya ta fita, tana tunanin me ta ji ne ko ta gani, ta kasa yi wa Nana rashin mutunci.
Tana komawa ya kalle ta ya ce "Ina Abincin?"
"Wai ba ta da lafiya"
"Me ya same ta?" Ta girgiza kai jiki a mace ta ce "Nima ban sani ba"
Ya so sake wata tambayar, amma sanin halin Asal ya sanya shi ta shi, zai fita.
Ta ce "To ina za ka je ba ka karya ba?"
"Zan samu abin da zan ci, zan je na ga Mahmoud ne" Daga haka bai kuma cewa komai ba ya fita.
Bakin Imam Hammad fal maganganu kamar yadda bakin Mahmudu yake fal maganganu, amma kowanne ya kasa furta wa kowa.
Hammad ne ya numfasa ya ce "Mahmud ina son na koma kan ayyukana, amma Sultan ya ce mini na dakata, akwai abubuwan da nake son yi da yawa."
Mahmoudu ya ce "To ka yi haΖuri, wataΖila akwai dalilin da ya sanya ya ce ka dakata tukuna"
Ya numfasa ya ce "Haka ne, wai yaushe za ka shigo gida ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba na son shiga gidan nan naku"
"Saboda me?"
"Kai ma ka sani ai"
Imam ya ce "Ban san komai ba. Jiya Imams sun kawo mini ziyara. Ranar Lahadi za mu yi zagayen raΖuma da shan shayi, ka zo mu je tare"
"Imam, ka na manta waye ni, da ΖoΖarin kai ni matsayin da Allah bai kai ni ba, ni dai dan Allah ka yi haΖuri"
"Mahmoudu, idan ba kai ba wa ka ke so na janyo jikina? Ka san komai fa? Shikenan haka ni zan zauna?" Yayi maganar muryarsa Ιauke da rauni.
"Haba jarumin shugabana, ka na fa da wanda ku ka shaΖu, ku ke da kusanci tsakaninku sosai da sosai"
"Waye?" Ya yi maganar yana kallonsa.
"Zan haΙa ku kwanan nan, aure zan Ζara yi maka kwanan nan, ka na son 'yar Nigeria?"
ΖanΖance idanunsa ya yi yana kallon Mahmoudu. Ya ce "Ga ka nan ga Asal ai"
"Ahh yi haΖuri, kar ka gaya mata sai ta saka a fille mini kai"
Hammad ya yi murmushi yana gyara zamansa.
Sai da Nana ta shafe kwana uku ba ta aikin komai, haka kurum Imam ya ji abin ya tsaye masa ya dame shi, ko ya yi ΖoΖarin mantawa sai ya kasa. Kwanakin nan uku kame-kame kawai yake yi gurin cin abinci, duk abin da zai ci sai ya ga kamar abin zai cutar da shi. Ga uwa uba rashin ΙanΙanon abinci da ba ya ji gaba Ιaya.
Yau da Nana ta lallaΙa ta fito, ta ji ana ta zancen hawan zagayen da za a yi a kan raΖuma.
Har ya yi shirinsa zai fita, ya tarar da Abinci a falo.
Cikin zaΖuwa ya Ζarasa ya buΙe, tabbas Ζamshin girkinta ne. Wani murmushi ya suΙuce masa cike da farin ciki.
Sai dai sam ba su haΙu ba.
Har yau jikinta babu Ζwari sosai, bayan fitarsa ta shiga ta gyara abin da za ta gyara, kawai ta nemi guri ta zauna, tana hutawa wani irin bacci ne ya Ιauke ta a gurin.
Ba ta jima da fara baccin ba, sai ga ta a Libraryn Ζaisar.
Waiwaye ta fara yi taga ta ina za ta gan shi, sai dai ba ta gan shin ba, sai wata guguwa da ta taso, ta watso mata littafin nan da ta ce ba za ta karanta ba. Ta kalli littafin a gabanta amma ba ta motsa ba, ba kuma ta Ιauka ba. Kawai littafin ya buΙe kansa da kansa, sai mudubin nan ya haska inda ya buΙe Ιin.
Sayyid ta gani a tsaye a cikin sahara ana ta harbo masa kibiya ta ko ina, Sultan ta ta gani yana ΖoΖarin tare masa, shi ana samun sa da kibiyar. Har ya fara gazawa aka fara samun Sayyid.
Ya na tsaka da tarewar aka janyo shi aka nufi wata wuta da shi, da cin ta yake gwanin ban tsoro. Ba ta iya ganin fuskar wanda yake jan na shi, saboda ya rufe fuskarsa da rawani.
Gaba Ιaya Nana ta gigice ta rintse idanunta tana addu'a kar Allah ya ba wa mutumin nasara, can jin shiru sai ta buΙe idonta a hankali.
Sai ta daina ganin wancan lamarin, sai wata taguwa da ake ta Ιurawa wasu abubuwa.
Sayyid na zuwa ya kama taguwar ya hau, yana hawa ta din ga walagigi da shi, ta nufi kan wani rami da shi. Zumbur Nana ta tashi, tare da miΖewa tsaye a falon. Zuciyarta sai bugawa take yi da sauri.
Waje ta yi da wani irin hanzari, ta nufi inda ake shirya raΖuman da za a yi hawan da su.
RaΖuman duk jajaye ne, an yi musu wani irin ado, ga su Ζosassu.
Gaba Ιaya ta ji ba ta yarda da lamarin ba, ta juya ta sake kwasar hanya ta koma sashen su.
Tana zuwa ta ci karo da shi ya fito, sanye da makamanciyar shigar da ya shigo Ιakinta bayan auren su.
Takobinsa na soke a gefen Ζugunsa, babbar rigar jikinsa ta sha aiki.
Kallon Nana ya yi, fuskarta ta nuna rama sosai da sosai.
Nana so take ta yi masa magana amma yana tare da Asal da ta sha kwalliya ita ma, sai hura hanci take yi.
Gaba Ιaya yanayinta ya nuna masa a rikice take, kuma magana ce a bakinta.
Har za su gifta inda Nana take ya ce "Sayyid excuse me"
Asal ta waiwayo ta kalli Nana jin ta ce masa Sayyid maimakon Imam.
Ya kalli Asal ya kalli Nana, sai kuma ya yi taku biyu ya matsa daf da Nana, ya sunkuyo daidai tsawonta.
Gaba Ιaya sauran barorin da suke gurin ma zubo musu ido suka yi.
"Dan Allah kar ka hau Taguwar nan" Ta yi maganar cikin tsoro muryarta har tana rawa.
Ya Ιaga idonsa ya saka a nata, wanda hakan ya rikita ta, tamkar ba ta taΙa saninsa ba.
Bai ce mata komai ba, ya miΖe ya yi gaba. Asal ta bi shi cikin fushi tana tambayarsa "Wai me ta ce maka?"
Ya numfasa ya ce "Da tana son ki ji, ba za ta zaΙi ta gaya mini ba".
"Imam ban gane ba, mene ne abin da ba za ta faΙa kowa ya ji ba?"
"Ai kin san duk wanda yake ΖarΖashina, ina ba shi lokacina na saurare shi. Kar ki manta mutumin da yake da Asal doka ba ta ba shi dama a kan wata wadda ba Ζabilarsa ba, mussaman baΖar fata, kin fi kowa sani na, ki daina saka wani abu a ranki dan Allah"
Ya yi maganar daidai lokacin da suka Ζarasa gurin. Daga nesa Nana take hango an ba shi shayi a kofi, ya karΙa ya shanye, an sake zuba masa ya karΙa ya sha.
Aka cika gurin da kaΙe-kaΙe, juyi suka din ga yi tare da sauran 'yan uwansa Imam, su na wasa da takubbansu, gwanin burgewa. Duk da tashin hankalin da Nana take ciki, sai da abin ya Ζayatar da ita.
Aka jero raΖuman nan, suka din ga kama su su na hawa.
Nana gabanta ya tsananta faΙuwa, cike da Ζwarewa ya kama raΖumin nan ya haye.
Idonsa suka sauka a cikin na Nana, fuskarta Ιauke da damuwa, ya lumshe idanunsa ya saita akalar raΖumin nasa, ya wuce gaba sauran suka bi bayansa.
Mutane suka rufa musu baya, suka kama hanyar barin gidan.
Jiki a sanyaye Nana ta koma.
A tsaye ta jingina a gurin girki, tana tunanin abin da ka iya biyo bayan hawan RaΖumar nan da ya yi.
But Asal ta faΙo cikin huci, Nana ko motsawa ba ta yi ba sai bin ta da kallo kawai da ta yi.
Har gabanta Asal ta zo tana huci "Uban me ki ka gaya wa Imam, kuma saboda me za ki din ga kiransa da Sayyid? Ban yi miki gargaΙi a kan sa ba?"
Nana ta kalle ta, ta ga kar ta yi wani abun da zai sanya ta kore ta a yanzu, dan haka ta sassauta murya ta ce "Haba ya shugabata, Sayyid da Imam duk abu Ιaya ne ai, yana nufin shugaba, mu a Nigeria Sayyid muke cewa, kema idan ki na so sai na kira ki Sayyada. Kuma me Sayyid zai yi da baΖar mace 'yar Nigeria, ai ramin kura sai 'ya'yanta. Kawai ne nemi afuwarsa ne a kan rashin samun gudanar da aikina da na yi, a kwanaki da suka gabata, saboda shi ne Ζa'idar gidan sarauta.
Ki yi haΖuri iya matsayina da aikina nake tsayawa."
Asal ta numfasa tana huci, duk da hankalinta ya Ιan kwanta.
"Shikenan na ji, daga yanzu za ki bar Ιakin da ki ke, za ki koma Ιakin hadimai da ke tsakanin sashen Imam da nawa.
Sannan akwai gurin girki a gurin girki a gurin, yadda za a din ga sauΖaΖa miki, sai dai babu ke babu fitowa a duk lokacin da yake nan, muddin ba abinci ki ka kawo masa ba, kuma ba gyaran sashen za ki yi ba. An dawo da ke sashen nan ne, domin Ζara tabattar da tsaron abincin da Imam zai ci"
Nana ta jinjina kai ta ce "In sha Allah, na gode sosai da sosai"
"Ki hanzarta, ki kwaso kayanki ki mayar can, a yau ba sai gobe ba, ku yi magana da Balaraba ta kai ki"
Nana ta risuna ta yi wa Asal godiya, haka aka yi, a ranar ta kwashe kayanta ta mayar can Ιangaren, barorin gidan na ta Ζara mamakin, yadda a ke Ιaga likkafar Nana baΖuwar haure sama da su.
Nana kuwa murna ta din ga yi, ganin tana Ζara samun kusanci da Imam, ta san addu'a da take yi ce Allah yake taimakonta, kuma tana fatan Allah zai yanke mata wannan wahalar nan kusa.
Fita ta yi da nufin ta kwaso kayan wancan Ιakin girkin ta dawo da su nan, ta ga mutane na kaiwa da komowa a sashen.
Wani ta gani a cikin mutanen fuskarsa rufe da rawani, amma ta ga kamar ta san shi ta taΙa ganinsa, kamar ta bi bayan mutumin, sai ta ji ana faΙin Imam ne ya faΙo daga kan Taguwarsa.!
AREWABOOKS
Nana ta rasa wa za ta nufa ta samu cikakken bayanin abin da ya faru. Ta san za a rina, tun da ta ga abin nan kuma ta din ga ji a jikinta, ta san wani abun sai ya faru.
A can Ιaki kuma, sannu Asal ta din ga jera masa, ya jinjina mata kai kawai.
Ya lumshe idanunsa yana tuna yadda Nana ta roΖe shi kar ya hau Taguwar.
"Wace ce ke?" Ya furta a hankali.
Asal ta ce "Magana ka ke yi ne?" Ya girgiza mata kai alamar a'a.
Tun da ya hau kan Taguwar nan yake jiri, duk yadda ya Ζwarara jikinsa, da ΖoΖarin sarrafata ya kasa, dan daina gani ya yi gaba Ιaya sai jin sa ya yi ya zamo Ζasa.
Ya yi ajiyar zuciya yana sauke numfashi.
"Imam na saka ta dawo Ιakin Hadaimai kamar yadda ka buΖata, ko za ka ci wani abun a kawo maka?"
Ya girgiza mata kai alamar a'a.
"Ina ne yake yi maka ciwo to?"
Ya yinΖura ya tashi ya ce "Babu ko ina salla zan yi"
Yana tangaΙi haka ya shiga ya yi salla, ya sake kwanciya.
Nana na ta kai komo falon babu kowa, tana son ta san halin da yake ciki amma babu wanda za ta tambaya.
Wata tawaga ta ga sun shigo sashen, kallo Ιaya ta yi masa ta gane Sultan, tana son fita tana jin tsoron kar ta yi laifi, haka ta tsaya tana hangen abin da yake faruwa.
Asal ta fito cikin hijjabi suka gaisa, ta yi wa Sultan jagora zuwa cikin Ιakin.
Da hanzari ya nufe shi yana faΙin "Hammad, tashi maza a tafi Asibiti"
Ya buΙe idonsa ya kalle shi ya ce "Babu abin da yake damuna Sultan, ba sai na je Asibiti ba"
Cikin damuwa ya ce "Me yasa ka yi hawan bayan ka san ba cikakkiyar Lafiya ce da kai ba? Kuma da ka ji ba za ka iya ba ai sai ka haΖura"
"Lokacin da na yi ba na jin komai a jikina, amma tuba nake ba zan sake ba"
Sultan ya ce "Ka tabattar ba ka jin komai a jikinka ba sai mun je Asibiti ba?"
"Ba na jin komai Abie, ka kwantar da hankalinka"
Ya jinjina kai ya ce "To shikenan, Allah ya tsare gaba ka kwanta ka huta sosai"
Ya jinjina masa kai, suka yi sallama ya tafi.
Duk yadda Nana ta so sanin halin da yake ciki, haka ta haΖura, sai dai bacci mai daΙi ya gagara Ιaukan ta.
Da sassafe ta fita ta hau gyaran sashen, tana jira ko za ta ji motsin Asal, duk yadda za a yi ta tambaye ta, ya jikinsa sai dai ta ji shiru, haka ta ajiye Abincin kari ta koma Ιakin da aka ba ta.
Sai wajen sha daya da rabi, ta ji motsi a falon, ta fito ta leΖa.
Shiru ta yi tana kallon mutumin da ya zo, kamar shi ta taΙa gani a gidan cin abincin su Al Hussain. Yana tare da Imam Asad.
Sayyid yana zaune a Ζasan Carfet, shi kuma yana saman kujera.
Allah ya taimaki Nana da Hausa suke magana, ba yarensu ba.
"Kai ya aka yi ka faΙo daga kan taguwa, ko ka fara shan wani abu ne ba mu sani ba?"
Asal ta ce "A'a Imam ba ya shan komai, dama ba shi da cikakkiyar lafiya ai"
"Ina magana kina sanya baki?" Asal ta ja bakinta ta tsuke.
Ya mayar da idanunsa kan Hammad ya ci gaba da cewa "Allah ya sauwwaΖe ya kuma kiyaye gaba. Amma ka din ga kulawa dai"
Bai ko Ιaga kansa ba, balle ya tanka masa, sai dai jikin Asal ya yi sanyi. Ba ta ji daΙin yadda Tafawa ya zarge shi da shaye-shaye ba.
Wuni aka yi zuwa duba Imam Hammad, sai dai ds Yamma Nana na tsaka da gyaran falon ta ga wannan takardar, mai Ζwarangwal Ιin nan yana ci da wuta.
Gaban Nana ya faΙi, ta yi shiru tana kallon takardar.
Jikinta ya ba ta kowaye yake yi masa wannan aika-aika yana cikin waΙanda suka zo dubiya yau.
Nana tana aiki a kitchen, Asal ta same ta, ta miΖa mata wani Ζulli ta ce "Ga shi nan, ki dafa wa Imam a shayi, maganinsa ne"
Nana ta karΙa ta amsa da to. Ba ta yi tunanin komai ba, ta dafa shayin ta je ta ajiye a falo.
Asal tana zaune tana jiranta a falo.
Ta tashi ta karΙa, Nana ta ce "A yi wa shugaba sannu, ina fatan Allah ya ba shi lafiya ya kiyaye gaba"
Asal ta amsa da Amin a ciki, ta nufi Ιakin baccinsu.
Yau Nana kamar ta fasa ihu, ta cika wata guda a gidan Asal, yau gaba Ιaya hankalinta yana kan Ιan jaririnta.
Ga shi tun da ta zo ba su yi waya ba ko sau Ιaya ba.
Haka kwanaki suka ci gaba da shuΙewa, kwana uku Asal na ba wa Nana maganin Sayyid tana dafa masa.
Sai a na ukun yake fitowa ya zauna a falon, amma ba ya fita.
A kai Abincin safiyar kwana na uku, Nana ta haΙu da shi.
Cikin girmamawa ta ce "Barka da safiya Sayyid, ashe tsautsayin da ya faru kenan, Ubangiji Allah ya kiyaye gaba."
"Ba ki yi mini sannu ba sai yanzu?"
Ta Ιaga kai ta kalle shi, duk ta ji abin wani banbarakwai, amma har cikin ranta ta ji dadin maganar da ya yi mata.
Ta Ιan juya idanunta ta risunar da kanta ta ce "Tuba nake Shugabana, ban samu damar ganinka ba ne, duk da na yi ΖoΖarin hakan, ba na son uwar gijiyata ta ce na zaΖe ne, amma tuba nake Ubangiji Allah ya Ζara lafiya da nisan kwana mai amfani "
"Amin na gode sosai. Ina ganin ΖoΖarin da ki ke ta yi, ina yabawa, ki yi haΖuri da Asal kar ki tsane ta, duk da na san tana takura miki wasu lokutan"
"Babu takura a ciki, matuΖar hidima taka ce shugabana"
Ya ce "Madalla na gode sosai"
Ta tashi ta bar falon, a ranta tana cewa ina Asal ta ga kirki, shi da yake hangenta daga nesa ma, ya san tana ΖoΖari, ita kuwa ban da jaraba da uwar hantara da nuna mata Ζyama babu abin da take yi.
Asal ta shirya ta fita tun safe, dan haka Imam ne kawai a sashen.
Da Nana ta tashi kai masa abincin rana, ta sha kwalliya cikin doguwar rigar Atamfa.
Duk yadda yake jin jikinsa babu daΙi, yana motsa shi da kyar, amma bai hana shi satar kallon Nana ba.
Ba Ζaramin kyau ta yi ba, ga Ζamshin turaren sa da yake tashi a jikinta.
Ta kalli idanunsa da suka yi jawur, tamkar jini zai zubo daga cikin su.
"Sayyid lafiya kuwa?" Kai kawai ya jinjina ya mayar da idonsa ya lumshe, yana jin wannan Ζarar mara daΙin ji a kunnensa.
Haka Nana ta tashi ta bar shi a gurin, saboda tsoron abin da ka iya biyo baya.
Sai dare Asal ta dawo, kuma itakaΙai Nana ta ga ta ci Abincin dare.
Misalin Ζarfe Ιaya da rabi na dare, Nana ta gabatar da sallolinta na dare. Ta zauna tana karanta Alqur'ani, a hankali sai ta daina ganewa.
Ziiiiiiiiii ta fara jin Ζarar guguwar iskar sahara tana tasowa. Ta rufe Alqur'anin a hankali ta ajiye, sannu a hankali sanyi ya fara ratsa ta.
Ji ta yi tamkar an buga wani abu da Ζarfi, ta zabura ta miΖe tsaye.
Cikin hanzari ta buΙe Ζofar Ιakin da take ciki ta fito corridor da Ιakinta yake ta tsaya.
"Imam mene ne haka? Meye haka ka ke yi wai?"
Sautin kakarinsa ya daki kunnuwan Nana. Gaba Ιaya ta kasa zaune ta kasa tsaye.
Asal ta gani ta fito da gudu daga Ιakin, ta yi waje ta fice daga falon, ta ja Ζofar falon da karfi ta rufe.
Gaba Ιaya sai kan Nana ya kulle ta rasa abin yi, ta bi bayan Asal, amma ta ji Ζofar a rufe gam.
Ta juya a hankali ta kalli hanyar bedroom Ιin da sautin kakarinsa yake ta fitowa.
A hankali ta fara takawa tana tunkarar hanyar Ιakin, duk da ba ta taΙa zuwa ko daf da gurin ba.
Zuciyarta na bugawa cike da tsoro ta buΙe Ζofar Ιakin.
Wani irin sanyin na'urar sanyaya Ιaki ta dake ta, hakan ya Ζara ninka sanyin da take ji. Wani ni'imtaccen Ζamshi ya ziyarci hancinta.
Girman Ιakin baccin har tsoro ya ba wa Nana, ita dai tana mamakin yadda suke abubuwan su kamar babu lissafi, Ιakin kwana kawai an yi shi gari guda.
Idanunta ya sauka a kan Sayyid da yake shirin faΙowa daga kan gadon yana jijjiga. Ta Ζarasa da sauri daidai lokacin ya faΙo Ζasa.
Ta Ιaukko pillow za ta saka masa, kawai ta ga wannan hoton a Ζasan fulonsa. Cikin mamaki take kallon hoton, tare da mamakin yaya aka yi ya zo kan shimfiΙarsa.
Ta durΖusa a kansa, ta kalli jikinsa duk wata jijiya da take jikinsa ta miΖe ta kumbura.
Ζwayar idonsa ta koma fara Ζal, gashin kansa ya hargitse, gaba Ιaya ya koma abin tsoro tamkar wani dodo.
Ta yi Bismillah ta zauna, tare da jin sai dai komai zai faru ya faru, ko a mutu ko a yi rai, ko da za a zo a kama ta gara balli ya tashi ko za su Ζaryatata gara duk abin da zai faru ya faru, da bar shi a wannan yanayin da bayan shi kansa babu wanda ya kai ta sanin mawuyacin halin da yake shiga.
Tamkar mayen Ζarfe haka ya riΖe ta gam, bakinsa yana karkarwa yana furta "Wuta! Zafi!"
Ya danneta a Ζasa ya ΖanΖameta, bakinsa na fitar za kumfa.
A hankali ta fara karanto suratul Saffat, ta sanya hannunta a cikin gashin kansa tana shafawa a hankali.
Sannu a hankali ya daina wannan gurnanin da yake yi ya yi shiru, sanyin jikinta ya fara Ιibarsa. Ya yin da ita kuma take jin tamkar ana gasa ta a tukuba saboda zafin Jikinsa.
Sosai Nana ta ΖanΖame shi ita ma, cike da matsananciyar kewarsa, wasu hawaye da ita kanta ba ta san na mene ne ba, suka din ga sintiri a kan fuskarta.
"Sai ki tashi ki tafi tun da ya samu bacci, tun da ke dai a rayuwarki ba kya tsoron matsala, tarar aradu kawai ki ke yi da ka. Maimakon ki bari mutumin nan ya gane ki, a yi duk wadda za a yi, amma sai ΖoΖarin kunno wa kan ki matsala ki ke yi" Ζaisar ya yi maganar cike da takaici yana harar ta.
Nana ta ce "Wasu lokutan nasara ns buΖatar sadsukarwa, da kuma tarar aradu da ka. Mu da ku ba irin zubin halittarmu Ιaya ba, ba zan iya jure ganinsa a wannan mawuyacin halin ba. Ina tausaya masa a yanzu fiye da a lokacin da na san shi bai kan sa ba, yake ce mini yana ji a jikinsa rayuwar da yake da ni ya fi wadda ya manta aminci da kwanciyar hankali, ga shi kuma yanzu ina gani. Sai na Ζyale shi a haka?"
Ζaisar ya yi tsaki ya ce "Allah ya sa shi zai iya yin abin da ki ke yi a kan sa"
Nana ta numfasa ta ce "Dama ba dan ya rama mini nake yi ba"
Sai gefen asuba jikinsa ya saki, ya ci gaba da nannauyan bacci. Ta saka masa filo ta tashi, sai dai jikinta tamkar ana karyata haka take ji, saboda azabar riΖon da ya yi mata.
Bayan ta idar da sallar asuba, ta yi adduo'inta ta shiga kitchen.
Kafin Ζarfe tara har ta kammala komai, ciki har da gyaran katafaren falon Imam Hammad. Tana son sanin halin da yake ciki, ya farfaΙo ko kuwa bai farfaΙo ba.
Tana can tana tunani, shi kuwa tuni ya fito ras da shi, ya hau buΙe-buΙen kwanuka. Har wani murmushi ya yi ganin Ζosai a cikin kayan karyawarsa.
Shiru ya yi yana kallon kofin madarar raΖumin da ke gabansa, bayan da ya buΙe ya ga 'ya'yan habbatussauda a kan madarar.
Ya ciro wayarsa ya daddana, ya kara a kunnensa.
"Al Hussain"
"Allah ya taimaki Imam Hammad adalin shugaba abin koyi"
"Barka da wannan lokaci ya aiki?"
"Alhamdillah, ina nan tafe cikin Agadez a wannan satin, tun da an ce mini yanzu ana ganin ka"
Imam ya ce "Eh, ammm tambayarka nake son yi"
"Ok Imam, Allah ya sanya ba wani abun aka ce na yi ba"
"Akwai yarinya da Asal ta zo da ita, ta ce a nan gurin cin abinci na MaraΙi ta Ιaukko ta, wata 'yar Nigeria"
Al Hussain ya ce "Haka ne, sai dai ba na nan suka tursasata Gimbiya Asal ta tafi da ita, na Ιauka ma nan gidan cin abinci na Agadez za ta dawo da ita"
"A ina ku ka samo ta?"
Al Hussain ya ji gabansa ya faΙi cike da tsoron, ko wani abin ne ya faru.
"Wani kamfani ne suka kawo ta, da muke neman ma'aikata masu Ζwarewa a fannin girki"
"A nemo kamfanin, da shugaban kamfanin"
"To in sha Allah, amma ina fatan ba wani abin ne ya faru ba?"
Imam ya ce "Sarkin ruΙewa, babu abin da ya faru, ina sauraren ka" Daga haka ya ajiye wayar daidai lokacin da Asal ta shigo.
Ya Ιaga kai ya kalle ta ya ce "Ke ina ki ka tafi ne? Na yi zaton ma ko ki na sashenki ne?"
Ba ta ba shi amsa ba, Sultan ya shigo a rikice. Da mamaki yake kallon su.
Sultan ya Ζaraso cikin hanzari ya ce "Hammad ka na lafiya ya jikin naka?"
Imam ya ce "Ai ni lafiyata Ζalau, tun ranar da na faΙo fa babu abin da ya same ni"
Sultan ya kalli Asal, a rikice ta ce "Wallahi Sultan ba shi da lafiya, ba ka ga riΖon da ya yi mini jiya ba, wasu abubuwa ya din ga yi masu ban tsoro".
Imam ya Ιaga kai ya yi mata wani irin kallo, da sai da hantar cikinta ta kaΙa. Ya gyaΙa kai ya ce "Ni ban san me take magana a kai ba, lafiya Ζalau na kwanta kawai dai ba na jin daΙi kaina yana yi mini ciwo, ban sani ba ko ciwon haukan ne ya motsa mini ba"
Sultan ya ce "A'a ba ka da wani ciwon hauka, kawai dai rashin fahimta ne, ka san ba ka da cikakkiyar lafiya"
Hammad ya miΖe riΖe da kofin madararsa, yana sha a hankali ya ce "Abie zan je na shirya, zan Ιan fita ne"
Ya nufi Ιakin sa.
Asal ta kalli Sultan ta ce "Wallahi Sultan ba Ζarya nake yi ba"
"Na sani, na san ba Ζarya ki ke yi ba, ki yi haΖuri. Dan Allah ki yi shiru da bakinki kar ki gaya wa kowa. Zan san abin da zan yi a kai"
Nana kuwa burgima ta din ga yi a Ιaki, saboda azabar ciwon da jikinta yake yi mata, kamar ta saka ihu haka take ji.
Tun da ta jiyo muryar sa sama-sama a falo, hankalinta ya kwanta ta san jikinsa da sauΖi.
Sai dai wunin yau ma ba su haΙu ba, Asal ta ce mata ta ajiye masa Abincin, za a Ιauka a kai masa inda yake.
Ruwan zafi Nana ta dafa, ta shiga ta ya wanka da shi, ko za ta samu afuwa, ta gyara jikinta ta fita. Gidan ya yi shiru saboda dare ne, kowa ya kwanta. Ta shiga kitchen Ιin ta tabbatar komai lafiya Ζalau, sannan ta koma Ιakinta.
Tana shiga Ιakin ta ga duhu an kashe fitila, ta nufi gurin kunna fitilar ta ji an mayar da Ζofar Ιakin an rufe.
Ayshercool
08081012143
1K NE VIA 0069685771
Aisha Adam stanbic bank
πππ