Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

TSINTACCIYA CHAPTER 6 BY NIMCY LUV

TSINTACCIYA CHAPTER 6 BY NIMCY LUV

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Kuka Meema ta sanya wanda ya Ζ™ara tayar da hankalin President Ahmad Adil,cikin damuwa yace “he looses his memory? I understand,but problem Ι—in fuskar fa? How long zai kasance cikin rashin sanin wane ne shi?”  Kafin Dr yay magana Meema tace “i don’t understand Dad,loosing memory kamar ya?” Cikin nutsuwa Dr Ι—in ya kalleta kafin yace “everyone forgets things atimes,how often have you misplaced your car keys or forgotten the name of a person you just met,some degree of memory problems as well as a modest decline in other thinking skills,is a fairly common part of ageing,there’s a difference,however between nrml changes in memory and memory loss associated with alzheimer’s disease and related disorders,and some memory problems are result of treatable condition Madam Meema Ahmed Adil” shiru tayi idanunta yay rau rau zai kawo ruwa kafin a hankali tace “kenan bazai iya tuna waye shi ba? Balle ya tuna abinda ya faru dashi,more explanation please” farin glass Ι—insa ya Ι—auka tare da sanyawa cikin nutsuwa yace da Meema “he looses his memory,he can’t remember anything about his life,and normal age-related kin gane ba? Memory loose doesn’t prevent you from living a full productive life for example,you might occasionally forget a person’s name,but recall it later in the day,amma tunawa lokaci guda it’s difficult,you might misplace your glasses sometimes,or maybe you need to make lists more often than in the past to remember appointment or tasks. These changes in memory are generally manageable and don’t disrupt your ability to work,live independently or maintain a social life” Dr ya Ζ™are maganar yana sauke numfashi baya jin hausa ko kaΙ—an hakan yasa dukkan wani bayani da zai yi dole sai dai yay da yaran nasara Ingilishi kenan.

Kasa magana Meema tayi bata san mene yasa ba amma wani mugun jin tausayin mutumin take kafin a hankali tace “alright yanzu dole sai the same abinda ya faru da shi ya sake faruwa zai iya tuna waye shi?” Ta faΙ—a abinda Dr Ι—in ya faΙ—a,jinjina kai yay kafin yace “sure” miΖ™ewa President Ahmad Adil yay yana kama hannun Meema kafin yace “Dr ka shirya komai na tafiyar cikin week Ι—in nan za’a fita dashi” ya faΙ—a yana jan Meema zuwa waje,kallonsa tayi tana kwaΙ“e fuska kafin tace “Dad” ba tare da ya kalleta ba yace “what again Meema?” Idanunta na kawo ruwa tace “Dad i want see him please! Please Dad” tsayawa yay yana kallonta kafin yace “Look Meema wannan ba age Ι—in soyayya dashi bane,infact kin girme masa respect yourself ok?” Ƙasa tayi da idanunta tana jin ranta babu daΙ—i kafin tace “Dad ni fa ba?” Tsareta yay da idanu kafin yace “kefa mene? Uhm gayan naji” girgiza masa kai tayi kafin tace “nothing” kama hannunta yay tare da shiga cikin mota securities suka rufa masu baya.

  Can cikin gidansa suka nufa bayan sun Ζ™arasa Meema ta fito da sauri ba tare data tsaya Dad Ι—inta ba,murmushi kawai Dad yay domin hakan da tayi yasan fushi tayi.

  A bakin shiga lift ya sameta tana ganinsa tai saurin shigewa tana danna 3rd floor,rabuwa yay da ita ya nufi wata daban yana shiga ya danna shima,a parlor ya sameta tana maΖ™ale jikin Mom tana surutai wanda ita kaΙ—ai ta san mene take cewa,kallon juna sukai shi da matarsa kafin Mom tace “yanzu kuka fita lafiya amma ji har abin ya motsa” cike da so da Ζ™aunar Ζ΄ar tashi ya kalli Meema wacce zufa ke yanko mata sai surutu take ita Ι—aya murmushi yay kafin ya Ζ™arasa tare da kama hannunta yace “Allah sarki Mamana,Ubangiji yana sane dake kinji nothing will happened to you again,ina nan kinji i’m always be by your side kinji” ya faΙ—a yana yin gaba da ita tare da nufar side Ι—inta,suna zuwa ya zaunar da ita bakin bed kafin ya fara bin bedroom Ι—in da kallo,a hankali ya Ι—auki wayarta tare da kunnawa yace “ke Ζ΄ar gidan shugaba ce,President’s daughter,ya kike son maida kanki middle class ne eh? U have to be classes lady irin manyan matan nan,ni da na keso ki fara fita kina rage min wasu manyan ayyukan tunda kinga ba ni da wanda zai taimake ni ba ni da wani babban Ι—a,soon zaki fara fita zuwa wasu Company,wai ke nan sunan babbar likita,a haka zaki zama babbar baΖ™uwa a wajan taron sickler day Ι—in,haaaa! TaΙ“ su Meema Ζ΄an Ζ™asa na gari a nan tare dasu I.d card voters card anya kin taΙ“a voted na Dad Ι—inki ma?” Murmushi tayi masa tana Ζ™wace jakarta bai kulata ba,a hankali ya zauna a gefe ganin wayar nata empty ba komai gata sabuwa dal iphone 13pro max,transfer kati yay mata na 50k kana ya sai mata data cikin sauri ya shiga play store tare dayi mata download na I.G whatsapp,twitter sai wattpad da okoda books tare da games da app na qur’an da azkar,buΙ—e mata komai yay da wani special name Meema_ President’s daughter,wayarsa ya Ι—auka tare da yi mata sending na picture Ι—inta,Ι—ora mata shi yay saman profile kana ya bata yana faΙ—in “yanzu kika fito Mamana,oyah tashi ki fara duba wayanki gashi nan ki yi abinda kike so na tura maki 500k a acct naki” dariya ta masa tace “thank you Dad i love you” Murmushi yay mata yana miΖ™ewa yace “love you too Meema,kinfa girma good 32 to 33 yrs amma abu ya saki gaba kamar yaΖ™i please ki yita addu’a,ki samu kiyi aure kamar ko wacce mace i don’t know what wrong with your mother bata damu ba sam,ina cikin mutane hankalina na kanki ki taya ni kula da kanki,ahha! Ba na son facebook domin zaki iya gani ana zagin Dad Ι—inki ranki ya Ι“aci,ina yin abinda naga zan iya,amma kin san halin mulki,mai makon jama’a su tayamu da addu’a sai su bimu da zagi,bayan bama da laifi domin na saman su ke take komai,ki kula da kanki akwai guards naki guda ashirin duk inda zaki,make sure tare kuke,ok?” Jin shiru yasa ya juya,ashe tuni bacci ya Ι—auke ta shi kaΙ—ai yake abinsa,girgiza kai yay tare da Ζ™arasawa wajanta ya gyara mata kwanciya,a hankali ya shafa kanta tare da sumbatar goshinta,fita yay yana rufe mata Ζ™ofar bedroom Ι—in.

  Washe gari Dad da wuri ya fita zuwa wajan meeting wanda zai zauna da Ζ΄an majalisu na dokoki wato _(National assembly)_ na Ζ™asa baki Ι—aya,akan lafiya musamman ciwon sikila wanda ya zama kamar Annoba.

   A hankali Meema ta fito sanye da  silhouette da VGOLD palazzo trousers wanda yake da faΙ—i sosai daga Ζ™asa kamar skirt daga waist Ι—inta kuma ya Ι—ame ta irin sosai Ι—in nan ba zaka taΙ“a cewa tayi shekaru har 33 ba,tayi rolling kanta da wani haΙ—aΙ—Ι—an vail,a hankali take tafiya kamar wata Ι“arauniya tazo dai-dai parlor taji ance “mrng mai satar hanya” ajiyar zuciya ta sauke tare da faΙ—in “Mom” sai kuma ta juya tana murmushi,zama tayi tace “mrng Mom?” “Mrng how are you? Ina zaki haka ko breakfast baki ba?” Shiru tayi sai kuma tace “kamar nayi ko? A’a banyi ba,kai na yi” girgiza kai Mom tayi tana ajiye system Ι—in gabanta,wato al’amarin Meema kullum Ι“aci yake kamar da sauΖ™i sai kuma ta Ζ™ara komawa ruwa “bama ki tabbar kinyi ba kenan ko,eh?” TaΙ“e baki tayi domin Mom faΙ—a gareta yanzu zata hargitsa ta,miΖ™ewa tayi ta fice daga cikin gidan baki Ι—aya.

  A can waje kuwa wata mota ta shiga cikin sauri guards suka nufota,da sauri ta Ι—aga masu hannu driver yaja da gudu tana faΙ—in “aso rock clinic gulps za kai dropping nawa”  ta faΙ—i hakan tana buΙ—e network Ι—in wayarta,kai tsaye wattpad ta shiga ta fara dube dube domin tun sanda Dad yay mata settings Ι—in komai bata taΙ“a wayar ba sai yanzu,har ta shige wani book sai kuma ta dawo baya taga ansa _Our secret_ (Sirrin mu) shiga tayi tana zaune ta karanta Episode 1 to 5 lokacin da tazo wajan da Airah ta kewa Sheikh kiss kanta yay wani mahaukacin sarawa a firgice kuma tai wani irin….

Dafe kanta Jikinta ya shiga mahaukacin rawa jijiyoyin kanta suka mimmiΖ™ewa, wasu abubuwa suka fara gilmawa ta cikin idanunta a hankali kuma take lumshe idanunta cikin nutsuwa bakinta yake motsawa a hankali take furta _“Ya hayyu ya Ζ™ayyumu”_ shine kawai abinda yake faΙ—a drivern ne ya Ι—an tsaya da gudun da yake tare da juyawa ya kalli Meema cikin girmamawa da bata matsayinta yace “Madam is everything okay?” Jinjina masa kai kawai tayi a hankali tai baya tana kwanciya a jikin kujerar motar da sauri kuma ta Ι—auki wayar ta tura ta cikin hand bag Ι—inta.

Ganin sauyin yanayinta yasa Driven ya fara da ita a hankali har suka isa clinic Ι—in fitowa yay da gansa sosai mamaki ya kamasa ganin bacci take hankalinta kwance babu abinda ya dame ta, ya daΙ—e tsaye a kanta yama rasa mene zai mata, a hankali ya fara buga kujerar da take kai yana faΙ—in “Madam! Madam!” Idanunta ta buΙ—e tana ya motsa fuskarta ba tare data kallesa ba ta fito daga cikin motar kai tsaye cikin haΙ—aΙ—Ι—an Clinic Ι—in Wanda Manyan likitoci suke ciki tana shiga Dr dake kula da mutumin ya fito Murmushi Yay mata yace “wlcm Madam Meema Ahmed Adil” Murmushi tayi masa wanda ya sanya yay Ζ™asa da kansa domin kwarjini gareta sosai ga shirme da manta abubuwa gaba Ι—aya kanta bashi da saiti “how can i help you?” Taji Dr Ι—in ya faΙ—a cikin Ζ™asa da murya tace “please ina son nai magana dakai prvtly firstly kuma ina son ganin sa please kaji?” Jinjina mata kai yay kafin yace “follow me”  bayansa tabi tana sakin murmushi a cikin wani haΙ—aΙ—Ι—an room mai masifar kyau ba zaka taΙ“a cewa mara lafiya bane a ciki waje ya bata ta shige ciki idanunta na kansa, yana kwance flat gaba Ι—aya an sanya masa wasu na’ura a jikinsa fuskar nan nashi manne da bandeji kansa ma haka, baΖ™i ne his Elegant black skin Ι—in nan nashi sai Ζ™yalli yake, babu abu mai haske a Jikinsa irin foot Ι—in sa da tafin hannunsa a hankali kuma Numfashinsa ke sauka, he’s dark-skinned yet handsome zai iya shekaru 29 to 30 kujera taja ta zauna kusa dashi a hankali ta kama hannunsa idanunta na kawo ruwa cikin Ζ™asa da Murya tace “you’re my brother as frm today, I’ll take good care of you kaji babu abinda zai sameka, i love You irin so na Ζ΄an uwa in sha Allah zaka tashi you’ll be fine ji nake kamar na sanka tun can baya” Shiru tayi kafin ta Ζ™ara riΖ™e hannunsa tace “Nima zaka zaka kula dani ko? I’m scared ina jin tsoran mutane, kaga nan nima wai babba ce fa kullum Dad sai yace na zama babba classes lady zaka kuya min komai ai ko? Zaka dinga zuwa mall mall dani da park za muna hira ko?” Ta faΙ—a hawaye na sakko mata, mamaki ne ya kama Dr domin yaji ana faΙ—in Meema bata da wani cikakken hankali shiyasa mahaifin nata baya fita da ita amma the she’s talking yanzu zaka Ι—auka mai cikakken hankali ce Allah Al-hakkamu kenan.

Murmushi ta saki jin ya riΖ™e hannunta dake cikin nasa, juyawa tayi ta kalli Dr hawaye da dariya na kwance mata tace “You see ba? I’m lucky wallahi he loves me I’m so happy” ta faΙ—a kuka na Ζ™wance mata kamar wacce ta tuna wani abu kuma ta miΖ™e tsaye tana kallon Dr kafin tace “let’s go” fita yay tana biye dashi a baya har office Ι—insa zama yay kana ta zauna tana faΙ—in “i need your help Dr but kada Dad yaji please” jinjina mata yay kafin yace “what the you want?” Shiru tayi tana tunani sai kuma tace “Ina son a sawa wannan mara lafiyar fuskar wani” idanunsa ya ware yace “fuskar wa kikeso asa masa to?” Ya faΙ—a cikin harshen turanci “bani da photon sa amma dai ina da photon a idanuna da zuciyata” Wayarsa ya Ι—auka yace “ok bari na kira arteries muga” tana zaune yay waya not too long wani mutum ya shigo Ι—auke da kayan drawing ajjiye komai yay a hankali Meema take masa bayanin komai tana faΙ—a yana zanawa Murmushi tayi tana jin wani mugun daΙ—i na ratsa Zuciyarta ta sauri Dr ya miΖ™e tsaye idanunsa akan zanan cikin Ι—aga murya yace “wannan ai photon tsuhun Ι—an majalisa ne (Members federal house of Representatives) Hon Bukar Bello..

A hankali yake sakkowa daga strains Ι—in benen yana sanye da wata Ι—anyar shadda fara dal da ita Ι—inkin babbar riga da jamper, ya Ι—ura wata half jaddara a saman sumar kansa wacce tayi kwance lubb da ita, Ζ™afarsa sanye cikin wani Black half shoe na Gucci mai tsananin kyau.

Yana tafe yana maΖ™ala Rolex Ι—insa na A.lange & SΓ²hne yay wani irin mahaukacin kyau idan kaga Akeem zaka Ι—auka wani Balarabe ne fuskarsa tai wani fresh ga wata haiba da zallar nutsuwa fuskar nan babu yabo babu fallasa as usual yana tafe yana lumshe idanunsa tare da motsa bakinsa.

Abbu dake downstairs yace “Akeem yau dai ka makara kamar ka manta yau Friday” caraf Didi ta amshe zan can tana faΙ—in “yoooo Allah na tuba zuciya ce babu alkairi, mugun abu yay masa yawa faΙ—a yake nema dani saboda an faΙ—a masa ni sallamammiya ce irinsa to ba’a gantale nake ba, wallahi Bukari ina faΙ—a maka kaji tsoran ka nemawa Ι—an ka magani gani kuke ina wasa amma billahi wannan yaron ba lafiya ce dashi ba” Murmushi Abbu yay yace “Didi kunfi kusa da mijin naki fa” wani zaro ido tayi tace “wa Ι—in? To wallahi li’ilafi Ζ™urash banda a ido aka haifi Audil wallahi da cewa zanyi ba jinin ka bane, saboda tsabar maita ka kalli yadda yake jajir dashi kamar wannan yaron na yama sunan Film Ι—in…” Ta faΙ—a tana kallon Afaf wacce ta fito daga part Ι—insu da sauri Afaf tace “Shuria khana, na Film Ι—in maheyk” tafa hannu Didi tayi tace “Yawwa Shimam irin albarka shifa kai Muhammadur Rasulullah s.a.w wlh mugun halinsu Ι—aya” A hankali Akeem ya gama sakkowa tsittt wajan ya Ι—auka sai muryar Didi ta fara faΙ—in “Astagafirullah satali saboda Annabi albarkacin juma’a” Murmushi kawai Abbu yay a hankali yay gaba Akeem ya fara masa baya kamar wasu abokai kai tsaye mota suka nufa gaba Ι—aya kuma back seat suka shiga driver yaja sun Ι—an fara tafiya Abbu ya kalli Akeem yace “Ina son sanya Akeela makaranta what’s your opinion?” TaΙ“e baki yay ba tare da yace komai ba ganin hakan yasa Abbu faΙ—in “Abdul-hakeem” marai-raice fuska yay kamar zai kuka yace “for God sake Abbu mene nawa ni” da mamaki Abbu yace “Akeem! what wrong with you? Ζ³ar uwar taka jikinka itace Meye ruwanka cikin lamuranta Are You at of your sense?” HaΙ—e fuska Akeem yay ba tare da yace komai ba a yanzu haushin yadda Abbu yake son fifita shi da village gal Ι—in nan ya keji cikin damuwa Abbu yace “ashe zaka iya wulaΖ™anta jinin Ι—an uwana jinin Baffanka har haka Abdul-hakeem? Akeela is your sister kamar Aleema da Afaf mene yasa kake haka ne?” Ɓata rai yay yana sauke numfashi kafin yace “Abbu ni kawai i hate her ne” wani sassanyan numfashi Abbu ya sauke yana mai jin daΙ—in hakan a ransa shi kaΙ—ai yasan mene zuciyarsa ke faΙ—a masa a haka suka Ζ™arasa babban masallacin juma’a dake nan nasarawa gra.

A can gida kuwa su Akeem na fita Akeela ta fito a sanyaye kamar wata munafuka tana sanye da wata haΙ—aΙ—Ι—iyar open abaya blue black ta Ι—ura wata hula mai gashi a kanta, cikin nutsuwa ta Ζ™arasa shigowa ciki ganinta yasa Ummi faΙ—in “Daughter kin fito?” Ƙasa tayi da kanta tana wasa da yatsun hannunta MiΖ™ewa Mami tayi tare da barin main Parlo Ι—in gaba Ι—aya taΙ“e baki Didi tayi tace “to ita dai rayuwar guda nawa take? Ban dai gantalewa da son zuciya irin na mutum, idan ka riΖ™e Ι—an wani baka san wazai kula da naka ba fisabilillahi mugun abu Ζ™arara” Murmushi Ummi tayi tace “have a sit daughter” Afaf ce ta kama hannunta tana faΙ—in “Ummi wallahi tsoran Hamma Akeem take kamar ranta” taΙ“e baki Aleema tayi tace “ba dole ba, mutum sai faΙ—a da miskilanci wallahi gabana har faΙ—uwa yake idan na jisa kai wallahi munyi missed Hamma Adnan Allah ya dube mu” Ummi dake MiΖ™ewa domin haΙ—a lunch tace “Za kuyi bayani bari yazo” da sauri Didi tace “Tsila (Akeela) ke dai babu ruwanki da shiga tsabgar wannan mutumin kada kuma ki biyewa su Shimam wallahi shawara nake baki bani da mugun abu ko kaΙ—an” ita dai Akeela da idanu kawai take kallonsu kafin tai magana taji Ζ™amshin turarensa da kuma zazzaΖ™ar muryarsa yay sallama cikin parlon Abbu na bayansa da sauri ta kulle idanunta Ζ™irjinta na wani irin bugawa, babu wanda ya kalla cikin parlon part Ι—in Mami ya nufa tana zaune a Parlon ta watching TV Akeem yay sallama Murmushi tayi tace “wlcm Hero” shigowa yay tare da zama saman sofa yana Ι—an lumshe idanunsa kafin a hankali yace ” Ma’ul khair Mami” Murmushi tayi tace “yawwa yaya aiki?” Yana lumshe idanunsa yace “Allahamdulillah Mami” kafin Mami tayi magana Amani ta shigo tare da faΙ—awa jikinsa tana faΙ—in “Abbie na” satar kallon Mami yay yaga basu take kallo ba da sauri ya rungume Amani yana bata peak a goshinta yace “little na” dariya tayi tace “Abbie na kayi kyau kamar new Aunty” ware idanunsa yay irin bai gane ba Ι—in nan tace “Abbie Anuty Akeela tana da kyau” haΙ—e fuska yay yace “Ω„Ψ§Ψ£Ψ±ΩŠΨ―Ψ§Ω„Ψ΄ΩˆΨ΄Ψ±Ψ©” (ban son surutu). Shiru tayi masa domin tasan halin Abbien nata miΖ™ewa yay Mami tace “Uba da Ζ΄ar duk babu kunya ka daure dai kayi wani Auran a samu more children’s” shafa fuskarsa yay tare da Ι—aukan Amani ya fita, ita kaΙ—ai ce a parlon duk sun tafi taya Ummi shirya Lunch can nesa da ita ya zauna domin yunwa ya keji shiyasa ba zai iya komawa part Ι—insa ba, buΙ—e ido tayi a hankali tare da sauke ganinta a kan Ζ™wantaccen sajansa wanda yay mata masifar kyau bata taΙ“a ganinsa da manyan kaya ba kenan sai Friday Friday yake sawa? Ta tambaya a ranta, wani irin sahihin kyau yay kamar Balarabe Amani dake jikinsa ta zame tace “Abbie ka ganta tana da dimples irin nawa da naka Allah” Murya can Ζ™asa dai-dai kunan Amani yace ،Ψ£Ω†Ψͺ” Ψ₯Ψ¬Ω„Ψ³ Ω…ΨΉΨͺΨ²Ω„Ψ§”  Wato _Ke! Zauna dai-dai_ jin abinda yace tayi shiru tare da komawa ta zauna tana jan gemunsa.

Fitowa Abbu daga part Ι—insa idanunsa akan Akeela ganin Akeem zaune a parlo abinda bai taΙ“a ba kenan yasa kawai ya nufi  dinning room gently Akeem ya miΖ™e da sauri Amani ta zame hannunta ta nufi wajan Akeela ogan kuwa tunda ya zauna bai kalleta ba, tana jin Ummi na kiranta kasa tashi tayi domin jinta take wani uncontactable a cikin su.

Bayan sun kammala yin lunch Ι—in Akeem ya haura sama Abbu kamar yay ihu ya keji domin tun safe bai samu damar yin magana da Akeela ba bare yaga Ζ΄ar shagwaΙ“ar data saba yi masa.

Da daddare bayan sallar Isshā duk suna zaune a parlo iya yaran Aleema, Afaf da kuma Akeela Amani tuni tayi bacci ya jima da shigowa amma gaba Ι—aya basu san ya shigo ba hankalinsu na kan film Ι—in This is fate da ake na karan da firita, gyaran murya yay yana zuba hannayensa a cikin hannun jallabiyar jikinsa da sauri gaba Ι—aya suka juya tare da kallonsa a kusan tare da Afaf da Aleema suka shiga faΙ—in “lailatan Sa ida” wato barka da dare haΙ—e fuska Akeem yay cikin wata tsawa yace “duk Shegiyar dana Ζ™ara gani da Wannan kayan uhm” ya faΙ—a yana duban Ζ™ananun kayan dake jikinsu bakin Aleema na rawa tace “Ayyah Hero banmu Ζ™ara sawa” wata tsawa ya daka mata yace “ku Ι“ace min da gani” Akeela tafi kuwa firgita jikinta na wani irin Ι“ari ta miΖ™e zata gudu da wani irin sauri yasa hannunsa ya riΖ™e wist Ι—inta tare da wani irin juyo da ita ya haΙ—ata da…..

Post a Comment for "TSINTACCIYA CHAPTER 6 BY NIMCY LUV"