Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

BABBAR YARINYA CHAPTER 4 Oum Aphnan

BABBAR YARINYA CHAPTER 4 Oum Aphnan

Www.bankinhausanovels.com.ng 

_Wasu Na cewa wai Anya Oum Aphnan Ι—in nan Musulma ce kuwa? … To Tambayarku ta dawo gareni,saidai banda Amsarku A ynz ,Amma in kuna jin tantama zaku iya Ι—abbaΖ™a mun kalma Asshahada sai kuga in zan karΙ“a._

Da Ζ™yar Islam ta yarda ta fito dinner ,bayan kiran da suka dinga mata a waya a cewarta tayi fushi dasu ,tinda suka bar Akram ya zauna basu hanashi ba to tabbas sun daina sonta.

A dinning wani shan kunu tayi tana cusa abincin kamar magani, taΖ™i haΙ—a ido da kowa ,saidai Hajiya zainab Ι—in da Alhaji buban su kalli juna su guntse dariya.

“Baby” Alhaji buba ya kira sunanta a hankali ,kumburo kumatu tayi amma ta kasa magana

“Baby Girl” Hajiya zainab ta sake kiranta

Murya can Ζ™asan maΖ™oshi ta amsa da “Um” sannan ta caki Fried plantain taΙ—an gutsura tana taunawa 

“Baki tambaye mu me ya kawo yayanki Akram ba?”

Saida ta juya Ζ™eya ta kalli Ι“angare Ι—aya ta babballara harara gamida murguΙ—a baki kafin tace “So who cares me ya kawoshi,sai yayi ta zuwa in yaso ya shekara anan…ni inma cemun akayi un bar masa gidan bari zanyi tunda kun daina sona” Ƙwalla da ya soma taruwa mata a ido yasata shanyewa gamida yin shiru

Kannewa Hajiya zainab tayi “Oh yeag mu mun isa muce Ki bar gidan nan ke da yike mallakinki mufa dik zamanki muke ,Saidai shi Alkhairi da cigaba yake yunΖ™urin kawo ma rayuwar ki ,don zuwansa ma yace ya samar maki Admission a UK zakije ki karanta Home managements abun daΙ—in ma tare zaku tafi…”

Islam data kai glass cup baki ta kurΙ“i lemo kenan ta furzo shi waje 

“What??” ta tambaya gamida zaro ido 

Kafin suyi wani yunΖ™uri ta Ι—aura da bala’i kamar wacce ta tasa Ζ΄aΖ΄anta a gaba

“Ni?…Ni dai Islam nine zan bi Akram UK da sunan wai karatu,kuma ma in rasa a abunda zan Ζ™are sai a mai koyan dafa abinci! Wannan shine abinda bazai taΙ“a yiwuwa ba ” tana kai aya ta ture kujeran da take kai baya ta miΖ™e ta bar masu wajen gabaΙ—aya

Waigowa Alhaji Buba yayi ya kalli Hajiya zainab

“Ko zaki ki Ι—an rarrasota? Nifa dama shiyasa ban goyi da bayan tafiyar nan ba”

“Haba Sweet haba don Allah ,wannan fa abun na Islam yina neman yawa ,kar mutane suzo suga yanda take maltreating Ι—in mu a fita da ita a baki da sunan bata girmamu muji kunya” 

“To ai laifin kine ,ke kika sangarta ta”

“Haba Alhaji ni ko kai?” take suka fara musu ,kowa yina zargin Ι—an uwansa da bada gudunmawa wajen lalacewar tarbiyyan Islam…Ƙarshe dai Hajiya zainab ne ta janye maganar ta miΖ™e tai masa saida safe ,yasan tayi fushi ne amma kawai sai yayi burus da ita shima yayi hanyar samansa .

*****

Akram kam tun kafin ya bar gidan ya kira wayar drivern Office Ι—insa ya kwatanta masa Gidansu Islam yazo ya Ι—auke shi. 

A back seat ya zauna cikin motarshi GMC ,lumshe ido yayi ,yina tuno sanda Islam ta wani Ι—aure rai gamida haΙ—e giran sama da Ζ™asa ,tana tambayarsa wai Anya har yanzu ma ka mallaki motar kanka? 

Dariya ya sake fashewa dashi ,yina tuna yanda ta wani yi balance cikin  fasuwan kai ala dole ga ita Babbar yarinya

Wayarsa ne ya fara Ι“urari ,Kallar wayar yayi yaga baΖ™uwar number ce ke kira a kuma personal phone Ι—insa ba na wajen Aiki ba

Kamar zai Ζ™yale wayar sai kuma ya Ι—aga tunda yasan duk wanda zai kira tanan tabbas family member Ι—insa ne.

Ɗauka yayi ya kanga a kunne 

Ta Ι—ayan sashen akace “Hello” Gwale ido yayi cikin mamakin muryar mace 

“Assalamu Alaik,waccece?” 

“Sorry durling dama na kira ne in tabbatar in numberne ashe kuwa shine ,Affa?”

Tsaki yaja cike da Ζ™uluwa “Wai wanene plz”

“Oh Mr. Man calm down na aza ko cikin muryoyin mata dubu zaka iya cankar muryata? Hmm karka damu to Khairy ce your cleaner”

Wani mitsiyacin tsaki yaja kawai ya kashe wayar yina jin ransa na tafasa ,shikam wa ya bata numbersa ? number ma na gida ba na wajen aiki ba?

****

Next day Evening

Islam kwance take akan bangajejen gadon royals Ι—inta sai juyi take cikin barci mai Ι—auke da mafarki mai tsayuwa a rai ,Dirkuwar motocine ,ya isheta a barci da Ι—an hayaniyar mutane haka daga can tsakar gidan.

Cikin fushi ta miΖ™e ta kwaye cikinta daga cikin blanket Ι—in ,ta sako Ζ™afarta Ζ™asa daga ita sai Ι“ingilar riga armless da ya Ι—an gota  gwuiwarta da kaΙ—an.

Zuwa tayi gaban windown Ι—akinta dazayi hango mata tsakar gidan ta leΖ™a ,Wani Tsaki ta saki me cike da Ζ™uluwa ,Ɗaga murya tayi ta Ζ™walla ma guard Ι—inta kira 

“Amaka!!”

Guards Ι—inta da suke  zaune akan plastic chairs a Ζ™ofar Ι—akinta , suna hiransu cike da fara’a da NishaΙ—i ,ga alama dai sunajin daΙ—in zuwan wa’innan BaΖ™in ,A furgice wanda aka kira da amaka ya miΖ™e “Yes Ma!” 

Ya Shiga Ι—akin saidai a bakin Ζ™ofar ya tsaya

“Barka da yamma”

Ɗan yamutse fuska tayi

“Hayaniyar me nike ji? ,A waje?”

“Eh to ,dama Yaron Gomna ne Ishaq maga ,wannan babbar lawyan dake da kotuna a Ζ™asan Ingila  ne yazo neman Aurenki shine kike jin jiniya!”

Wani tsawa ta daka masa “Oh sharraf!”

Da sauri ya Ι—inke bakinsa

“Go and tell them to turn that blurdy Noisy Idiot off”

Zaro ido yayi jikinsa na Ι—an rawa “Ehem hajiya?”

Ranta Ζ™ara Ι“aci yayi “Bakaji da kyau ne? Wuce kaje kace su kashemun banzan jiniyarsu inason inyi barci ,this is just 5:00pm “

Da sauri ya juya ya fita daidai nan ya haΙ—e da hajiya zainab ta nufi Ι—akin Alhaji Buba da sauri ,shima ko bayanta yabi don ya faΙ—a mata abunda Islam ta aikesa yayi tunda gaskiya shi bazai iya zuwa ya faΙ—a ba.

Saidai yana soma kiranta ta dakatar dashi da hannu

“kaga ina zuwa ,munyi baΖ™i dakace ni kaΙ—an” tana maganar tana hayewa Ι—akinsa

****

Jin An kwashe a Ζ™alla mintuna Biyar baa Ι—auke Ζ™aran jiniyar ba ya sata harzuΖ™a ,a yanda take ta suri Room slippers ta fice a zafafen Ζ™arshe ,tana Ζ™wallawa su Amaka kira saidai bataga kowa ba ,hakan ya sata wucewa tsakar gidan , ta sa a dakatar da kanta amma a ranta tana kimtsa rashin mutuncin da zatayiwa su amaka Ζ™ilan ma yau Ι—in nan zata dakatar dasu a bakin aikin su ,don basu da amfani kasancewarsu guards Ι—inta 

Harabar gidan ta fito Sosai daidai Sojoji sun rufo masa baya cikin isa da shiga ta Alfarma

Wani haΙ—e rai tayi tamkar me jin amai,tana masa kallon raink wani lukuti dashi,shikam sai Ι—an murmushi yike mata dukda ,daka kalli fuskarsa ba ma’abocin fara’ar bane ara yayi kawai ya yafa

RiΖ™e Ζ™ugu tayi a bakin Ζ™ofar da zasu shiga ma’ana inda akayi masu iso 

Ƙyar yike kallon suranta cikin lafaffen cotton Ι—in rigar jikinta ,sosai ya yaba halittarta saidai baiji daΙ—in fitowarta a haka cikin mutanensa ba ,sam ba girmansa bane ,amma zaiyi mata uzurin yarinta ne da ya aureta zai gyara abinsa

Cikin tsawa da bala’i ta kallesu “Ashe ban aiko a kashe mun wannan lousy Noise Ι—in ba ,kun gallaze ni ina barci wannan wani irin zaluncine ?”

Jikinsa rawa ya somayi ,da sauri ya matsa gabanta ,cikin sassauΖ™ar murya irin na wanda basu saba Ι—aukan kwaram Ι—in jama’a ba yace “My love”

Tsawa ta daka masa gamida Ι—aga masa hannu tana faman hura hanci “Oh shut that your dirty mouth up !…ka kawo mun Wa’innan Irresponsible Nonentities Ι—in cikin gida saboda selfishness Ι—inka duk sun hargitsa mana gida this evening an katse mun barci who dare you ,Da zakasa a kawo mun wannan Good for Nonthing Fools Ι—in ehem?”

Ta Ζ™are tana Ι—aga jijiyar wuya kamar ta samu Ι—an cikinta 

A hankali ya tako gabanta yina Ι—an ware hannu ,yanda zai mata magana cikin sulhu

“Haba ke kuwan,karki kunyata ni cikin mutane na mu shiga ciki sai kiyi mun magana a tsanake,tunda kinga ko banza dai abun arziΖ™i ta kawoni da nufin mu Ζ™ulla soyayya mai tsafta cikin Ζ΄an Ζ™alilan kwanaki mu angonce…”

Ras ! Taji gabanta ya faΙ—i ,take taji gabaΙ—aya ya koma mata baΖ™i wuluk a idonta ,rasama me zatayi masa tayi ,kawai Ɗaga hannu tayi bai aune ba saidai yaji Ι—auuuuu!! Ta dalle sa da mari  wanda ya sashi razana gamida sakin baki shaye da tsananin mamaki ,a take lafiyayyun yatsunta biyar suka bayyana a kuncinsa 

AsheΖ™eΖ™e ta kallesa tana jin yanda Ζ™irjinta ke kaiwa da komowa a zafafe,sannan cikin gatsali ta Ι—aura da masa magana

“An faΙ—a maka ni ,Islam Kwantai nayi da zaka kawo mun wasu sillallun Ζ™afarka nan wai…(Ta shiga kwaikwayan yanda yayi magana) Abun ArziΖ™i ya kawoni da nufin Ζ™ulla soyayya me tsafta dani dake fa !!” HaΙ—e rai ta kuma yi “Oh gerrout ,tsami kawai 

Cikin zafin nama ta danno Ζ™ofan sai ji kake kararaf ta kulle Ζ™ofar ,ta barshi anan tsaye dafe da kunci kunyar duniya ya gama shansa ,ko motsi ya kasa yi bare har kuma ya iya Ι—aga ido ya kalli guards dinsa da suke ganin kimarsa.

Post a Comment for "BABBAR YARINYA CHAPTER 4 Oum Aphnan"