WATA MACE CHAPTER 5 BY SANA S MATAZU
WATA MACE CHAPTER 5 BY SANA S MATAZU
Www.bankinhausanovels.com.ng
Kwanci tashi babu wuya wajen ubangiji, Yusuf ya sami sauΖi sossai. Har an sallameshi. Sai dai rayuwarsa ta sauya sossai, ya yi bala’in Ζara zama me sanyi fiye da baya. In kaga haΖoransa sun buΙe to murmushi ne amma ba dariya ba. Ita kanta Shukura ta ga sauyi sossai a tattare da shi na wasu Ιabi’un amma kuma shaΖuwarsu na nan. Lokacin da aka sallamoshi gidan mahaifinsa ak wuto da shi, domin ya Ζuduri aniyyar ya bar GIDAN MATARSA har abada. Dan haka ba shi da wajen zama da ya wuce baranda, kodai yana karatu ko kuma suna waya da Shukura. Wannan damar Labiba ta samu ta maida tagar dake Ιakin Amne ta sama wajen zamanta. Kodayaushe idanunta yana kansa, duk wani motsi nasa yana tafiya da yanayinta zuciyar n matsewa da wani irin abu da takasa fahimtar tausayine ko kuma Ζiyayya ce.
Kamar kodayaushe yana zaune, ita kuma idanunta na kansa. Tunani take yi ta ya ya zata isa wajensa ta nemi yafiyarsa? Tabbas tana kallon yadda rayuwa take wujijjiga Kabir ya Ζare ya lalace, bata fatan kwatankwacin hakan ya faru da ita. Tunaninta ya katse daidai lokacin da motar Yaya Adam ta shigo harabar gidan, yana buΙewa yaranta suka fito cikin shiga me tsafta da sha’awa wani abu ya gindaya ta tsakanin haΖarΖarinta. Da ido take dubansu, tana jin kewar abinda ta bari a baya na matsa Ζirjinta. Wannan gatan suka rasa daga gareta. Wannan kulawar da kowane Ιa yake alfahari da ita suka yi kewa. Lallai bata kamaci amsa sunan uwa ba, duk da cewa UWA UWA CE koda kuwa ta buzuzu ce amma kuma ba kowane ya ke amsa sunanba. Ζwalla ta share sakammakon dafata da aka yi tana juyawa suka yi ido huΙu da Husnan baba Mu’az, bata san yaushe ne ta shigo ba, kawai sai ta sami kanta da rungumeta tana gunjin kuka. Abin ya bata mamaki matuΖa, a tarihinsu babu komai tsakaninsu da ita da hanatara da kyara. Yau kuma sai ga akasin hakan, lallai duniya juyi-juyi ce,
“Husnah na yi kuskure a rayuwata wanda gyarashi yake da matuΖar wahala..”
“Ba me wuya bane Labiba matuΖar kin saka wa zuciyarki zaki gyara Ιin, babu wanda ba ya kuskure sai dai ba kowane yake da rabon gyarawa ba!”
Wasu Ζwallan ne suka sake kwaranyo mata, ta goge mata tare da zama a kusa da ita,
“Labiba sau tari muna aikata kuskure amma sai mu karaya a hanyar gyarawa. Ζwarai duka kuskure kuskure ne, amma kuma gyarashi babbar rabauta ne. Nasani da ciwo Ζwarai gyara abinda ka bari, amma kuma a kwai rib…”
Gani ta yi gaba Ιaya hankalinta na kan taga, ta kai idonta kai sai ta hango Ummi kan cinyar mahaifinta tana ΙalΙala dariya da waya a kunnanta. Ko ba a faΙa Husna ta sani da Shukura ya haΙasu suke waya, kallon juna suka yi yayinda Labiba ta dafe Ζirjinta da yake barazanar buΙewa. Da wani irin zafi me Ζuna, duk da bata san me ya ke faruwa ba tana jin wata irin sarewa da rashin madafa miΖewa Husnah ta yi ta barta domin babu abinda zata iya faΙa mata ya wanke wannan raΙaΙin.+
***
Soyayya tsakaninsa da Shukura sai abinda ya Ζara Ζaimi. Cikin ΖanΖanin lokaci manya suka shiga lamarin aka tsaida magana. Babu wanda ya dakatar dashi domin suna san rage masa raΙaΙin abinda ya yi kewa. Babu kuma wanda ya bi ta kan Labiba domin suna san nuna mata kuskuranta. Hasalima an hana kowa sanar musu abinda yake wakana.
Sossai Yusuf ya saki jiki ya soma neman na kansa, mahaifinsa ya bashi jari me kauri duk da mahifin Shukura ya so Ιorashi akan nasa kasuwanci amma ya nuna baya buΖatar wannan mutuntawa domin ansha shi ya warke. Ζaramin gida ya kama haya da guminsa, kuma mahiafinsa ya amince da hakan. A hankali ya cigaba da hidimominsa a gefe guda kuma Yaya Amina na tara masa lefe duk da mahaifin Shukura ya ce baya buΖatar komai idan ka Ιauke sadaki. Kuma Baba MuttaΖa ya biya naira dubu Ιari, amma da Ζyar suka karΙi hamsin. Soyayya suke cike da mutuntawa, bata da abin tambaya sama da yaransa tare da Ζarfafa masa guiwa kan fusknatar Ζalubalan rayuwa.
A kwana a tashi ya rage saura kwanaki bakwai bikinsa. Duk wani shirye-shirye a gama shi. Babu abinda su Labiba suka sani domin yanzu ba fitowa take ba daga ita har Amne kamar amare haka suke wuni cikin Ιaki. Babu wanda baya murna da auren Yusuf. A gefe guda kuma ya soma tunanin yadda zata kayya masa tsakaninsa da Labiba. Shi kam ba shi da burin sakinta ko dan karamcin mahaifinta. Amma kuma yana jinjina wace irin rayuwa zasu gudanar.
***
Da Ιan gudu irin na yara Khalifa ya fito daga sashin da ya kasance na Yusuf Ιin. Binsa ya ke yana san Ζwace wayarsa a hannunsa. Shi kuma sai dariya yake yana faΙin,
“Aunty Cukula”
Daidai hanyar da zata sadashi da sassan Amne ya ja burki, yana jin baya muradin taka Ζafaffunsa a wajen gara ya aika wani yaron. Kamar ance tsaya sautinta ya ratsa kunnansa.
“Wallahi Labiba matuΖar ina numfashi ba zaki komawa auran faΖirin yaron can ba. Yarinya babu zuciya ba komai ke kullum magana Ιaya. Ba Yusuf ba Ζangaladima ma uwatasa kurwar Ιiyana kur wollah”
Runtse idanu ya yi yana jin zagin da ta aunawa mahaifinsa na zaga kowace gaΙa tasa. Babban takaicinsa mahaifiyarsa data zaga tana kwance Ζasa. Tafiya yake ko gabansa baya gani, yana son maida Labiba ba dan so ba, sai dan mutuntakarsa amma kuma baya jin akwai abinda ya isa taΙa mutuntakar mahaifansa. Kai tsaye Ιaki ya wuce yana jin Ζirjinsa na suya, koda Khalifa ya dawo kawai amsar wayar ya yi yana daka masa tsawa. Kamanin Amne dake yawo kan fuskar yaron na saka masa wata irin shakka da kokwanton kadda ya kwaso halinta. Sai dai tuna sunan da ya saka ma yaron na bashi wani irin tabbaci da yake jin nasarar tasa ce. A daran bai kwanta ba sai da ya gana da Baba MuttaΖa kuma ya fahimceshi.
STORY CONTINUES BELOW
***
Babban Ιakin taron shaΖe yake da tarin ahalin, haya-haya hayaniya take tashi sakammakon hira irin ta Ζ΄an uwantaka da wasu ΙaiΙaiku suke gudanarwa. Yusuf yana daga gefe yana duban kowa daki-daki. Lokaci zuwa lokaci yana duba wayarsa. Daga hagu Labiba ce zaune kusa da Amne, sun keΙe kansu kamar wasu mumunai, amma kuma idanun Labiba na kan Yusuf. Hango Ummie ta yi cikin wasu kaya Ζ΄an kanti masu kyau da tsada. Zuciyarta ta Ιokanta da san jin Ιumin Ζ΄aΖ΄anta, gaba Ιaya wani tsoro da shakkar Amne ya fita a ranta balantana barazanarta. Gadan-gadan ta nufeta, daidai lokacin da yarinyar ta iso tsakiyar Ιakin taron. Caraf ta riΖe hannunta, ta juyo tana dubanta. Kallonta ta ke yi irin kallon nan na bansanki ba, ko kuma wace ce ke? Gaba Ιaya mutanan sai suka zubo musu idanu, yarinyar ta juya tana ΖoΖarin fuzgar hannunta. Bakinta na rawa ta furta,
“Ummie ni ce fa!”
“Ke ce Mamarmu me saka Abbanmu kuka ko?”
Tamkar Ιaukewar nefa haka komai ya Ιauke mata, zuciyarta ta tsaya cak tana wani irin matsewa. Bata gagara tsayar da hawayen fuskarta ba, ta kuma kasa gaba ta kasa baya. Ummie ta zame hannunta ta juya tana wani irin taku cike da nutsuwa da kawanciyar hankali. Abin sai ya bawa mutane mamaki tamkar wata babba. Nan da nan Ζus-Ζus ya soma ya tashi, Labiba da idanunta suka yi nauyi ta soma tafiya kamar kazar da Ζwai ya fashewa a ciki. A haka Amne ta Ζaraso ta ja hannunta tana huci suka zauna.
Bayan buΙe taro da addua’a Baba MuttaΖa ya miΖe ya miΖe ya soma gabatar da abinda suka samu na riba da kuma alkhairi a cikin zuria’ar. Daga nan ya Ιora da bayanin yaran da suka sami gurbin karatu a bana da waΙanda ake sa ran futowar sakammakonsu. Sannu a hankali ya gangaro kan abinda shi ne maΖasudin taron baki Ιaya. Bayan dogon jawabi game da al’ammuran da suka gudana daga kan Kabir Yusuf da Labiba da kuma marigayiya. Ya yi jan hankali sossai kan yadda da Ζaddara da kuma yin fashin baΖi kan ma ana ta sirranta sirrin gidan aure. Ζwarai abinda ya kamaci sirrantawa amma ba irin zama na Zahidaht da Kabir ba, domin akwai cutarwa. Ya fito Ζarara ya nuna illar dake tattare da abinda ya faru, tare da nusar dasu kan abubuwan da suka kamaci Ιoyewa. Ζwarai akwai abinda ya kamata a sakayashi a zamantakewa kamar sha anin yau da gobe bisa yanayin rayuwa. Samu da rashi duka na Allah ne. Mu amalar zamantakewa da sauransu. Daga Ζarshe ya ja hankalin iyayen sossai domin su ne suka bada Ζofar afkuwar hakan. Babu yadda za ayi Ζ΄a ta kawo maka kokenta kan gidan auranta ka Ζi sauraranta, domin yana daga kuskuran da suka aikata akan Khameesat wanda ya zamewa Zahidaht makamin riΖewa na cewa koda ta zo gida ba za a dubeta. Tabbas miji abin mutuntawa ne amma kuma ba ya nufin komai nasa da zai aikata babu kuskure ciki ba, akasari abinda yake daΖilar da Ζ΄a mace shi ne yarda da kuma yaΖini da iyaye suke lulluΙawa Ζ΄aΖ΄ansu akan mazajansu ne. Sau tari nan ne mafarin matsalar sai kuma ta caΙe a dinga dama kaza. Gaba Ιaya jikin mutanna wajen ya yi mugun sanyi. Ba kamar Yaya Amina da ta ke ganin tafi kowa laifi domin ta san halin da Zahidaht take ciki amma ta Ζunshe bakinta. Tana kuka tana komai ta miΖe tana neman yafiyar kowa na wajen kan wannan kukskuran data aikata. Kuma triyan-tiryan ta miΖe ta na me koro musu bayanin asalin halin da Zahidaht ta kasance a gidan Kabir.
Babu wanda bai koka ba, ta kuma Ιora da irin azabtarwa da Yusuf ya sha wajen Labiba, domin wasu lokutan a gidanta yake cin abinci idan ta hanshi duk da baya faΙa mata dalili sai dai izgilanci irin na Labiba kam bata damar bayyana mata koda bata tambayeta ba. Cike da Ζarfin guiwa take roΖonsu,
“Baba ba wai ina so a rabasu bane, amma ku yi adalci. Adalci fa nake magana iyayenmu. Ku daure ku ajiye zumunci da sanayya a gefe ku bawa Yusuf zaΙi karon farko a tarihin zuri’armu ku bamu damar mallakar haΖΖi irin Ζ΄aΖ΄a!”
Gumi sossai iyayensu maza suke sharewa, sai yanzu idanunsu ya buΙe kan kuskuransu na tauye wasu haΖoΖΖi n yaran nasu. Tabbas biyayya ga iyaye wajibi ne amma babu hallacinta ga abin hallita yayin saΙawa ubangiji. Baba Ζangaladima kuwa kai kawai yake jinjinawa yana hango hikimar ubangiji na Ιaukar ran Baba Ζaure domin ya fi su zafi. Yusuf yana gefe kamar mutum-mutumi zuciyarsa wani irin bugu take yi, yana jinjina wahalar da Zahidaht ta sha duk nasa me sauΖi ne. Sai yau ya ji abinda ya dane shekara da shekaru a game da ita na motsa masa. Wata irin tsanar Kabir ce take zagaya kowace jijiya ta sa. Da yana da iko da ya fitar da Kabir daga zuri’arsu ko hakan ya sassauta masa abinda yake ji, amma ina ba a sauyawa tuwo suna.
Labiba tamkar kazar da aka tsamo cikin ruwan sanyi haka ta kasance. Tun abinda Ummie ta aikata mata, ga kuma Ζari daga Yaya Amina. Daga ita har Amne a Ιarare suke gani suke kowa kallonsu yake yi kuma hakane, duk da cewa sun san gaskiya ta faΙa amma hakan be hana su ji zafinta ba. A Ζasan ransu kum suna kiranta ‘munafuka’.
“Yusuf”
Muryar Baba MuttaΖa ta dira a kunnansa, ya Ιago idanunsa jajjur kamar gauta. Ga jijjiyoyin kansa duk sun Ιaga. Wannan ya bawa masu kular cikinsu damar sanin yana cikin yanayi mara daΙi.
Murya can Ζasa ya amsa da,
“Na’am Baba”
Murya a kaurare Baba Musa ya yi magana,
“Yusuf ka Ιago magana zamu yi da kai”
Wannan karon da wani irin karsashi ya Ιago murya cike da ladabi,
“Ina jinku Baba duk abinda ku ka yanke ni me biyayya ne a gareku!”
Gaba Ιaya sai ya sanyayyar musu da jiki, amma hakan ba zai sa su shiga haΖΖinsa ba.
“Yusuf zaΙi muke baka a matsayinka na wanda aka zallunta. Shin mene ne ra ayinka akan Ζ΄ar uwarka Labiba?”
Gaba Ιaya sun Ιaureshi da jijiyoyin jikinsa, da ido yake duban kowa. Idonsa ya tsaya akan nata data kafeshi da su. A idanunta yake hango gazawa, magiya da neman yafiya da kuma nuna cewa bazan kuma ba ka tausayamun. A idanun danginsa kuma yana hango, ka ji kanmu wannan dama ce da muka samu daga ahalinmu karo na farko a tarihinmu kadda ka bari ta kuΙuce mana. Zuciyarsa kuma na tuna masa. Waye Baba Ιaure, karamci da sadaukarwarsa. Bai kamata ya zamo me yankakken baya ba. A gefe kuma yana jin wace rayuwa yaransa zasu yi babu mahaifiya? Zuciyarsa ta raya masa Shukura fa?”Na sauwaΖe mata shika Ιaya biyu uku, idan ta sami miji ta yi aure!”
Gaba Ιaya Ιakin ya Ιauki salati, da yawa suna san suga sun rabu amma basu taΙa tunanin zai yanke Ιanyen hukunci haka ba. Mahaifinsa kuwa dafe kai ya yi ido jawur. Amne ba tare da nadama ko dana sani ba ta rangaΙa guΙar da ta ba kowa mamaki, miΖewa ta yi tana furta,
“Tafi Nono fari…”
Bata gama ba Labiba ta Ζwala ihu ta yanke jiki ta faΙi tana jan numfashi da Ζarfi amma ya kwace mata ta sume. Da hanzari Ζ΄an uwa suka yi kanta, amma Amne ta ce kadda wanda ya taΙa mata Ζ΄a. Khamis ta dakawa tsawa ya saΙeta a kafaΙa kamar yarinya suka yi waje aka nufi asibiti da ita.
Bayan fitarsu wajen ya ruΙe, masu kuka na yi masu Allah ya Ζara na yi. Tsawa Baba Ζangaladima ya daka musu, sossai ya yi wa Yusuf faΙa tare da nuna masa illar abinda ya aikata sai dai bakin alΖalami ya bushe. Nasiha ya Ζara yi musu me ratsa zuciya tare da gargaΙi kan tasowar wata fitina. Anan aka fitar da waΙanda zasu kai lefan Yusuf washegari, cike da fushi da kaushin murya kuma ya bawa Kabir da Jawwad damar tsayar da hankulansu su nemi matan aure. Daga bisani aka rufe taro da addua’a musamman ga Zahidaht da Khameesat tare da jigon gidan baki Ιaya.
Babu wanda ya bi ta kan Amne da zuri’arta suka hau shirya-shiryan biki. Sai lokacin Amne ta sami labari, nan ta shiga zage-zage da surfa rashin mutunci son ranta. Babu wanda ya biye mata.
Kabir kuwa gaba Ιaya ya fita hayyacinsa ya koma abin tausayi. Ko zama cikin Ζ΄an uwa ya kasa yi, mahaifiyarsa tun tana hantararsa har ya koma bata tausayi ta soma jansa a jiki tana nuna masa ya maida al amuransa ga ubangiji. Sossai ta tsawatar masa kan yin azkar da azumin nafila. Aikuwa ya kama babu hannun yaro, sai ya soma jin wata irin nutsuwa na bibbiyarsa ga kammala da kwanciyar hankali. Tsakaninsa da Jawwad gaisuwa, iyayansu kuwa kullum sai ya je ya gaida kowa. Ya tattara komai ya watsar ranar da babu aiki baya zama. Mahaifinsa yake bi suna noman rani abin gwanin ban sha’awa. A wajen aikinsu akwai wata yarinya Ramlatu data nace tana sonsa, duk da sun taΙa rayuwar banza da ita yana jin ita Ιin zai aura ya huta domin ita ta dace da shi kasancewar tana da tabo kamar shi. Allah bashi sai su haΙu su tuba su gyara rayuwarsu.
Biki ya kankama kowa na hidimarsa. Ana gobe Ιaurin aure aka sallamo Labiba, kwata kwata bata san abinda yake faruwa ba kuma babu wanda ya faΙa mata. Dan haka ta cigaba da hidimarta bata kula kowa ba, tana shan magungunanta kamar yadda likita ya gwada mata. Da yamma ana shirin walima ta dinga kallon mutane da rashin fahimta amma bata tanka ba har kowa ya fice ya barta nan zaune.1
Washegari aka Ιauro aure aka kai amarya. Shi ma Labiba bata sani ba, saboda ta tashi da zazzaΙi da mugun ciwon kai.
Kwana biyu tsakani mutanan gidan suka tashi da hidima saboda kawo gara da za ayi daga gidansu Shukura. Duk abinda ake yi Amne ta sani amma tana gudun faΙawa Ιiyarta gudun halin da zata shiga. Tana lura da yanayin da take ciki wasu lokutan sai dai ta ganta tana sharar hawaye, ga yawan firgita idan tana bacci tana kiran sunan Yusuf Ιin. Abin tun baya damunta har ya soma damunta.
***
Da yamma duk gidan kowa ya daΙe, yaya Amina ta shirya ta nufo gidan. Tana san zuwa ta duba Labiban amma kuma tan shakkar tarbar da Amne zata yi mata. Amma kuma Ζasan ranta tana jin ba laifi ta aikata ba. Zata yi komai dan kawo haske a rayuwar Yusuf.
***
MUN DAWO LABARIN.
***
Tun daga bakin Ζofar gidan ta ke jiyo muryarta cike da rauni, waΖa ce take rairawa murya a sarΖe. A haka ta Ζarasa shigowa gidan, mammaki ya kasheta ganin hawaye a idanun Labiba. Bata Ζara tabbatar da mamakinta ba sai da Ζamshi mai ni’ima ya sami masauki a massarafar shaΖar numfashinta. Jiki a sanyaye ta zauna idanunta cikin nata. daidai lokacin da ta Ζara Ιaukar wata waΖar,
“Zamantakewa ba Ζarya ne ba. Cin amanar soyayya, an rabani da me sona”
Jikin Amina ya Ζara sanyi, bata taΙa tunanin akwai ranar da zata ga nadama a idanun Labiba ba, bare kuma zubar hawaye. Lallai masu iya magana sun yi gaskiya, duniya juyi-juyi ce. Tunaninta ya katse lokacin da hannunwan Labiban suka sarΖafo nata hannuwan murya a raunane ta furta,
“Yaya Amina ke ma murnar ki ke yi? Kina cikin masu murna an min saki Ιai-Ιai har guda uku? Kodayake ai ke ce ma me bada shaida amma ba kowa ya cuceni ba sai yaya Khamisu da kuma Amne da basu sakasu sun je sun daki Yusuf ba da bai sake ni ba. Kaicon rayuwata…”
Numfashinta ne ya soma yin sama da Ζasa, ta kai hannu Ζirjinta ta danne tana taune leΙΙanta na Ζasa. Kafin ta yi wani yunΖuri ta faΙi Ζasa yaraf! A hanzarce Amina ta kai mata Ιauki tana Ζwalla Ζara,
“Yaya Ade ku kawo agaji!”
Daidai lokacin wadda aka kira da Yaya Ade ta Ζaraso, tana yamutsa fuska kamar ta ga kashi. Kai a Ιage ta kalleta,
“agajin me kuma zamu kawo Yaya Amina? Ai tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka. Ζiyar boya ce fa take gudun auren jinin boya to mene ne a ciki dan ya sauta zata Ιaga mana hankula. Ba a auran Ιiyan boyan mu munka auri yayyunta? Ni kinga tahiyata ma gidan Yusufa naka zuwa ganin waga amarya tasa me karamci. Ance yau danginta sunka kawo gara daga Kano, gara mu hanzarta mu kwashi arziΖi kadda a ayi babu mu. Domin su arziΖinsu na gada ne ba taka haye ba, saudiyya ma zasu tafi aka ce sati me kamawa mahaifinta ya biya musu”
Wannan furucin shi ne ya Ζarasa tafiya da numfashin Labiba, cikin kanta take maimaita,
“Yusufa nawa? Aure? Saudiyya?”
***
Tsayin kwanakinta uku a kwance gado asibiti, bata san inda kanta yake ba. Duk lokacin da zata farka da sambatun kiran sunan Yusuf take farkawa. Allurar bacci kawai ake yi mata ta koma. Aranar kwana na huΙu mahaifiyarta ta zubda hawaye kamar babu gobe, masu ganin laifinta kansu sun soma jin tausayinta. Sai dai wasu ko kaΙan tausayinta be Ιarsu a ransu ba. Hasalima gani suke yi bata girbi abinda ta shuka ba.
A hankali take rarraba idanunta tana Ζarewa inda take kallo. Tabbas nan Ιin Ιakin jinya ne, bata yi mamaki ba duba da yanayin data riski kanta. Sannu Ζ΄an Ιakin suke jeramata tana amsawa da kanta kamar Ζadangaruwa. Idanunta ta ji sun mata nauyi, gaΙΙanta na amsawa amma hakan be hanawa kunnuwanta sauraran abin da ke fitowa bakin Yayanta Khamis ba,
“Ni na rasa irin wannan masifa ta Labiba wallahi. Tun da an yi saki har guda uku ta haΖura mana yanzu saboda Allah wa gari ya waya. Ki duba fa, kwanata shida ita da gawa marabarsu numfashi. A ranar ma da abin ya faru ba dan zuwan Amina ba Ζila sai dai mu riski gawarta..”
Maganar ta katse sakammakon sallamar da aka doka, Ιaukacin mutane sun kai su goma sha biyar ne a Ιakin, abin ka da Ζ΄ar dangi. Labiba Ζ΄ar dangi ce gaba da baya. Amma kuma kash kafataninsu aka rasa me Ζumajin amsawa. Bakunnansu sunyi musu nauyi. Hannatu ce ta yi karaf ta amsa gudun aji kunya. Labiba kuwa tun sallamar ta shaida mammallakin muryar, domin ko giyar wake ta sha Yusuf da abin da ya mallaka daban suke a rayuwarta. Sai dai ta gaza buΙe idanunta waΙanda ta kulle tun lokacin da ta ji sallamarsa. Ζwarai tana fargabar buΙewa ta ganshi da abin da zai Ζarasa tarwatsa duniyarta.
“Sannunku da zuwa”
Ζ³an Ιakin suka soma faΙa, suna harhaΙa kalmomin kamar masu koyo. A kunyace Yusuf da amaryarsa suka bi su daki-daki suna kwasar gaisuwa. Ummi ta yi tsaye ΖiΖam idanunta na yawo a kan mahaifiyarta. Sai lokacin Ζ΄an Ιakin suka farga da ita suka soma faΙin ta Ζaraso wajenta su gaisa. Ko gezau bata yi ba, tana dai kallon kowa Ιaya bayan Ιaya. Aunty Shukura kamar yadda suke kiran amaryar mahaifinsu, wadda a yanzu suke jinta kamar ita ta haifesu, ta miΖe tare da riΖo hannun Ummi da Khalifa Ζaninta. Sai dai ko taku uku ba su yi ba ta ji yaran sun warce hannunsu. Ta juya cike da mammaki, sai ga hawaye na zuba a idanun Ummin, ta soma taku a hankali a hankali da baya tana girgiza kai. Daga bisani ta kwasa a guje tana furta,
“A’a Aunty!” Shi ma Khalifa da tsamin baki irin na wanda hausa bata gamsheshi ba ya juya yana faΙin,
“Bajani ba Anti zasu yi min irin dukkan da suka yi wa Abbanmu!”
Ya Ζarasa yana ajiye yatsansa manuni akan Khamis yayan mahaifiyarsa. Kunyar duniya ta luluΙe Khamis ganin Ζaramin yaro na alamtashi da mummunar Ιabi’a. Bai taΙa tsanar biyewa shirman Ζanwarsa da mahaifiyarsa irin yau ba. Garam! Ummi ta rufo Ζofar da Ζarfi, bayan ta ja hannun Ζaninta. Sautin ya yi daidai da bugawar zuciyar Labiba. Cak numfashinta ya yi fitar burgu. Gaba Ιaya Ιakin aka Ιauki salallami, cewar Ade matar Khamis.
“Labiba ta cuci kanta. Ζiyanka! Ζiyanka na cikinka na gudunka? Mi ake da wanga Ιataciyar rayuw..”
Kallon da Yaya Khamis ya wurga mata ne ya sanya bakinta mutuwa, sai lokacin hankalinsu ya koma kan gadon da take. Suka fahimci bata numfashi. Da hanzari Huraira ta kira likita, ya soma ΖoΖarin daidaita numfashinta. Nan da nan ta farfaΙo, sai dai ba abin da take yi sai surutai tilas aka yi mata allurar bacci tare da sallamar duk wanda ya ke cikin Ιakin. Jiki a sanyaye suka fito yuu! Zuwa harabar asibitin anan suka riski Shukura na lallashin Ummi. Yusuf kuma yana riΖe da Khalifa. Ana haka Amne ta Ζaraso da Hajja Ζarama Ιiyar Khamis. Tana ganinsa ta kama zilo, duk da Ζarancin shekarunta. Hannu ya miΖa zai karΙeta, amma Ζiri-Ζiri Amne ta hanashi ita. Nan kuwa yarinyar ta tsanyare da kuka tana mimmiΖewa. Yaya Khamis ne ya karΙeta ya miΖa masa duk da mugun kallon da Amnensu take jefa masa. Ade kuwa sai Ζunshe dariya take yi. Yarinya na zuwa hannunsa ta yi tsit tana wangale baki.
Basu wani jima ba, saboda yadda wajan ya soma Ιinkewa da dangi, kuma kowa ya zo bakinsa baya shiru game da Yusuf da matarsa, karo na farko ya kafa TARIHI cikin zuri arsu. Dan haka Shukuran duk a takure take, ganin haka yasa ya yi musu sallama tare da ajiye kayan dubiya har leda uku. Duk suka rakashi da idanu, basai an yi musu bayani ba shadar jikinsa kanta abar kallo ce. Yaya Ade ce ta janyo ledar tana bubbuΙewa bakinta na furta,
“Masha Allahu. Ka ga gidan karamci da sanin darajar Ιan Adam”
Mugun tsakin da Amne ta ja ya ankarar da ita kadda ta yi kwaΙa, domin ta ga Amnan ta kawota bakin maΖoshi. Da hanzari Khamis ya fita yana jin wani Ιaci a zuciyarsa. Tabbas shi ne sillar komai shi ya tarwatsa farin cikin Ζanwarsa da tuni tana tare da yaranta koda babu muradinta. Nadama da danasani suka shiga kai kawo a zuciyarsa. Komai ya soma dawo masa daki-daki kan rayuwar Ζanwartasa. Dole ne ya nema mata farin ciki ya ayyana hakan a ransa. Dole ya sake tuntuΙar Jawwad su daidaita ko Ζari ne ya yi masa kan miliyan gudar da ya gindaya masa.Haba Jawwad mata fa na ke baka ka aura, amma kana jamin rai kamar wanda zai yi min abu kyauta! Ban da ma dai ΖADDARA ya za a yi na nufeka da wannan batun, bayan kana da TAMBARIN da baka cancanci zama da ita ba…”
“Dakata Khamis, wai dole sai na auri Ζanwarka? Ni gaskiya ba zan iya auren Ιiyar boya ba, kuma duk TAMBARIN da nake da shi ya kai nata ne? Ko ka manta duk abin da namiji ya yi adone? Ina ce kafatanin danginmu babu mace mafi ΖasΖanci kamarta a yanzu? Kodayake naga alamu ita data tashi gado, sai ta gado surukarta baΖin jini maimakon farin jini irin na mahaifiyarta. Kodayake babu haufi ai duk boya dai sunanta boya babu wani bambanci…”
“Dakata Jawwad kadda ka zagarmin mahaifiya, miliyan Ιayan da nace zan baka ce ta yi maka Ζaranci ga auren Ιiya kamar Labi..?”
Ζarasowar Kabir wajen ne ya dakatar da su daga muhinmiyar maganar da suke yi, duk da shi Jawwad anasa Ιangaren ya so su ci gaba, koba komai zai suluΙe daga auren da ake son maΖala masa amma Khamis Ιin ya dinga togewa. Tilas ya haΖura, amma kuma yana barin wajen ya soma ΖyanΖyasawa Kabir Ιin kanun zancen. Girgiza kai ya yi cike da takaicin halin Ζ΄an uwan nasa, duk abinda ya faru ba zai zama ishara garesu ba. Hasalima wata Ιarnar suke da niyyar aikatawa lallai wannan karon ba zai bari ba, tillas ne ya nuna musu kuskuransu.+
***
Da Yamma Khamis be haΖura ba ya sake bin Jawwad majalisa. Tunda ya hangoshi ya ke kumbure-kumbure. Kabir yana gefe da carbi me dannawa a hannunsa. Gefe kuma yana amsa wayar Ramlatu da yanzu sun daidaita. Tahowar Khamis Ιin yasa ya yi mata sallama. Sai dai kafin ya Ζarasa har ya soma jin tashin muryoyinsu, dafe kai ya yi yana Ζarasawa amma sai ya riski Khamis na killar Jawwad. Abinka da Ζarashen taba da giya, muryarsa a shaΖe yake faΙin,
“wallahi ba zan aureta ba, ana dole ne? Ζanwarka Ιin banza kuma miliyan guda na ci na yi haniΖan wallahi bazan biya ba”
Zaburowa ya yi zai kuma dukansa, Kabir ya riΖeshi suka wuce yana tausarsa,
“Haba yaya ina maka kallon me hankali amma kana biyewa shasshancin Jawwad. Saboda Allah ya kuke so iyayanmu su ji idan suka riski abinda kuke yi?”
Sai lokacin wata kunya ta rufeshi, wautarsa yake gani ta biyewa muradin Labiban amma kuma farin cikin mahaifiyarsa yake so domin yanzu tafi kowa burin Labiba ta koma ko ta huta.
Duk abinda ya ke faruwa akan idon Tukur me Ιinkin takalmin da Jawwad ya bawa wankin takalma. Da fari ya so ya Ζi karΙa saboda yamma ta yi. Amma abinda ya faru ya tabbatar masa da cewa arziΖi ne ya ke bibiyarsa. Matsawa ya yi tare da tattaro dukkan nutsuwarsa,
“Sannu bawan Allah, ga shi na gama”
KarΙa ya yi tare da bashi haΖΖinsa, amma be matsaba sai ma Ζara marairaicewa ya yi fuskar tausayi yana jajjantawa masa a haka suka rabu.
Tunda Tukur ya koma gida ya shiga tunanin yadda zai mallaki miliyan guda cikin ΖanΖanin lokaci. Tabbas nesa taso masa kusa. Amma kuma ta ina? Tsakar dare ya miΖe kan yagulalliyar tabarmarsa yana juyi, Lado abokinsa ya kawo masa bugu da Ζafa yana magaggi tureshi ya yi yana ayyana ya kusa fara kwana a kan irin gadon nan na bakin titi. Wata dariya ta Ζwace masa ya soma shirya yadda tsanin nasararsa zai kasance.
Cikin kwana biyu ya maida majalisar su Jawwad wajen zamansa koda ba Ιinki, a hankali ya soma saka musu baki idan suna hira. Musammman sha anin Jawwad ya dinga koΙashi da kambamashi tun baya kulawa har ya zamana suna wasa da dariya. A hankali ya soma shigo da labarai musamman kan halayyan mata da wasu mazan a gidan aure. Ya nuna yadda matarsa take zalluntarsa a zahiri yayinda akasin hakane a baΙini. Abinda ya ja hankalin Jawwad kenan ya soma bashi labarin yadda shi mata basa juyashi. Sannu-sannu ya soma bashi labarin nasa auran har zuwa batun Labiba. Cikin abinda be gaza sati biyu ba Tukur ya soma mafarkin burinsa na gab da cika.
***
Amaryar Shukura soyyaya auke me tsafta da angonta. Ta rungumi yaransa sossai ta maidasu tamkar nata. Ummie idan suna wani abun sai ka Ιauka Ζanwarta ce ba Ιiyar miji ba. Kamar kullum yau ma suna zaune suna buga lido bayan ta gama yi musu Ζarin karatun alΖur’ani. Mahaifinsu ne ya shigo suka miΖe cike da girmamawa da tsantsar kulawa suka nufeshi. Khalifa ne ya rungumeshi yana faΙin,
“Abbiey sannu da zuwa”
Ummie kuma ta riΖe jakar kayansa, murmushi ya saki tare da shafa kansa. Wani abu na tsirga masa. Bai taΙa sanin mene ne aure na haΖiΖa ba sai Ζ΄an kwanakin nan? Bai taΙa jinsa a cikakken uba ba sama da zuwan Shukura cikin rayuwarsa ita Ιin alkhairinsa ce. Idanu ya sauke a kanta ta haskeshi da murmushin da ya fi buΖata.
Ζunguma suka yi zuwa Ιakinsa, da dabara da wayau ta janye yaran bayan ta haΙa masa ruwan wanka. Yana fitowa ya shirya cikin jallabiya, gab da zai bar Ιakin wayarsa ta yi Ζara ya Ιauka yana amsawa. Bayan sun gaisa daga Ιaya Ιangaren ya furta,
“Baba na tura musu kuΙin komai ya daidaita”
Magana aka sake yi ya rusuna kamar yana gabansa,
“Sunan Mamarmu za a saka Baba, insha Allahu Ζarshan wata nan komai zai kammala. Inshaa Allah! Na gode Baba Allah Ya shige mana gaba”
Sauke wayar ya yi tare da Ιoyayyar ajiyar zuciya, wani irin nishaΙi ne yake zagaya kowaace gaΙa ta jikinsa. Wai yau shi ne zai mallaki gidan kiwon kaji nasa na kansa. Godiya yake ga ubangiji da kuma mahaifinsa. Uwa uba kuma Shukura da ta zamo wani tsani a rayuwarsa. Bazai taΙa mantawa da karamcinta ba. Kafin bikinsu ne ta shawarceshi da batun ya gwada kiwon, da fari ya nuna mata turjiya kan hakan amma ta dinga nuna masa kowa da wajen da ubangiji ya ajiye masa nasibinsa. Kamar wasa ya soma wanda hadda taimakon kuΙinta a ciki naira dubu goma. Allah Ya dubeshi yasa masa albarka, fitar farko ya yi asara saboda be san kan kasuwancinsu ba amma fita ta biyu sai gashi an maida abinda aka rasa. Cikin ikon Allah sai gashi guri ya haΙaka. Wajen Ιinkinsa ma ya buΙe Ιangaren horar da masu sha’awa sossai wajen yake tafiya. Takai ta kawo ma shi baya Ιinkin in ba na manya ba, sai dai ya yanka yaran su haΙe yana dubawa. Tabbas ya yadda babu abinda ya gagari ubangiji.
Cikin nutsuwa ya nufo fallon yana jin nishaΙin kasancewa da ahalinsa.2
***
TUKUR…
Cikin ΖanΖanin lokaci ya tattara duk wani abinda yake buΖata ya Ζara gaba. Domin dai Jawwad ya saki jiki dashi ainun. Babu abinda be samu ba game da Labiba abu guda ya rage masa shi ne yadda zai tunkareta.Tsaye yake a harabar Ζofar estate Ιin, gab Ιaya jikinsa ya yi sanyi na abinda ya ke tunanin aikawa. Yana jin ana faΙin girma da mutuntakar ahalin amma be yi tunanin sun kai haka ba. Lallai aikin gabansa babbane. +
Wata zuciyar na faΙa masa ya juya, wata kuma na sake jadadda masa a’a ya je. Yana nan tsaye yana jiran gawon shanu sai ga Khamis. Ζas! Gabansa ya faΙi, domin ya shaida fuskar dan haka da Ζwarin guiwa ya nufeshi suka gaisa. Fuskarsa na nuna rashin sanayya. Ganin hakan yasa Tukur ya gyara ya gabatar masa da kansa, da kuma maΖasudin zuwansa. Jim Khamis ya yi kamar me nazari, sai kuma ya saki murmushi ganin nesa ta zo kusa ko babu komai zai huta da mitar Amne uwa uba Labiba dake iΖirarin sun kashe mata aure. Juyowa ya yi yana dariya,
“Ka ce kun daidaita da ita ko?”
“Eh mun daidaita ita ce ma ta ce na zo wajenka!”
Ya faΙa Ζirjinsa na dukkan uku-uku, tunda ya soma magana da Khamis Ιin ya ke jin kamar asirinsa zai tonu. Har waigawa ya ke ko zai ga zuwan Jawwad a tsautsayi.
“Madalla to zan yi magana da iyayanmu sai in shaidamaka ranar da zaku turo. Amma mene ne sana’arka?”
“Eh dama ni Ιin ba wata sana’a ce da ni ba wankin takalmine amma babu abinda zai gagara tunda cikin miliyan guda Ιin da tace zaka bani zan yi hidimar komai kafin wa’adin auranmu ya cika!”
Da mamaki yake dubansa, “kan haka kuka shirya auran naku?”
“eh ta ce min kai ne me alhakin bayar da kuΙin kamar yadda aka so yi kan Jawwad!”
Ganin zai Ιalo masa ruwa yasa ya dakatar da shi tare da karΙar lambarsa. Har ya juya zai tafi sai ya dawo,
“bari na kira maka ita ku gaisa”
Da ace Khamis ya lura zai ga firgicin dake tattare da fuskarsa amma ina hankalin na can. Kai tsaye gida ya shiga ya turo masa Labiban shi kuma ya zauna suna tattaunawa da Amne.
“Amne Labiba ta samu wanda zata aura sun ma daidaita!”
Ba tare da damuwar komai ba ta yi hamdala, dan har ga Allah ta gaji da koke-kokenta. Shi kuma Khamis ganin fara arta yasa be faΙa mata ga auren da Labiban zata yi ba, tunda bata san Yusuf Ιin har gobe zata iya dakatar da Ζudurinsu. Amma ya Ιauki alwashin miliyan guda Ιin da za a fitar acikin kuΙinta za a fitar dan ya gama asara.
Koda Labiba ta nufo Ζofar gida sai da ta jima sannan ta gano Tukur ne me magana da ita. Bayan sun gaisa ya dubeta yana washe baki, ta Ιan ja tsaki miyau-miyau Ιin fuskarsa ya fi komai bata haushi. Amma ta dake ta ji dame ya zo ba laifi dai suturrasa Ζyalau da ita kuma me tsada.
“Malama Labiba ni dai sunana Tukur. Sana’ata ita ce…Yayanki ya sameni kan buΖatarku kuma na amince insha Allahu babu wata matsala”
Da farko kallon tsana da nafi Ζarfinka take yi masa, amma jin maΖasudin auran yasa ta Ιan saki murmushi. Lallai Yaya Khamis na Ζaunarta tunda yana san cikar burinta. Basu wani jima ba, suka yi sallama bayan ya karΙi lambarta. Kai tsaye gida ta shiga tana fara’ar da mutanan gidan suka jima basu ganta a kan fuskarta ba.
Da murmushi ta shiga Ιakin Amne,
“Yaya Khamis na gode!”
Ta furta tana lanΖwasa Ζ΄an yatsunta. Da idanu yake dubanta yana mamakin yau Labiba ce yake girmamashi haka sai tuna cikar burinta take muradi zata yi komai.
“Yauwa Labiba cikin kuΙinki zan ciri kuΙin nan wannan karon!”
“Wane kuΙi ku ma?”
Amne ta tambaya da sauri, cikin hanzari Labiba ta tareta domin ta fahimci Khamis Ιin kuma bata son Amne ta watsa shirin,
“Wasu kaya ne nagani ina so, da shi ya yi alΖawarin zai siya min to kuma kinga ga hidima zata taso mu tunda ina da su gara ni na siya Ιin”
Jinjina kai Amnen ta yi , su kuma suka saki ajiyar rai a tare suna kallon juna.
“Ka cira idan ma sun Ιara haka babu matsala”
***
Cikin ΖanΖanin lokaci maganar auren Labiba ta kankama. Tukur ya aiko magabatansa anyi komai cikin mutunci. Kuma be Ιoye asalinsa da sana’arsa ba. Baba MuttaΖa ya jinjina saboda sanin wace ce Ιiyarsu amma ganin ita ta turoshi kuma ga yayyunta maza basu tanka ba yasa suka sanya wa abin albarka. Anyi komai cikin mutunci. Tukur ya yi rawar gani akwatuna huΙu ya yi mata da kaya masu madaidaicin kuΙi. Sauran kuΙin kuma ya acewarsa ya kama haya ya yi Ζ΄an Ιinkuna da abinda ba a rasa ba. Murna yake sossai shi ma zai shiga sahun ma’aurata lallai rabon kwaΙo ba ya hawa sama be taΙa tunanin zai sami wannan dama ba. Yusuf da ya sami labarin auran Labiba ya ji mata daΙi ko ba komai zata huta da tsangwamar dangi. Sai dai Ζasan ransa yana tausayin wanda zata aura Ιin.
Ana gobe Ιaurin aure yasa Shukura ta shirya ta kawo yaran, tsaf da su tare da gundumuwar naira dubu hamsin ya ce a bata. Ζwarai ya ba kowa mamaki. Labiba kuwa hakan ya Ζara mata Ζaimin komawa gidansa. Wai Yusuf Ιinta ne da yin kyautar dubu hamsin? Lallai jin daΙi na jiranta. Balantan tunda ta sami labarin sana’ar Tukur ana tsegumi a gidansu ya hanata sukuni amma data tuna dalilin auren sai ta watsar da su ta cigaba da sha’aninta. Hata Ζ΄an jere da suka dawo sai da suka yi tsegumin Ζauyen Geza kuma unguwar da za a kaita tsohuwar unguwa ce, gidajen Ζasa sun fi yawa nata gidanma na Ζasane da shafen sumunti. Koda Amne ta yi Ζorafi sai ta nuna shaci faΙi ne kawai, domin ya nuna mata gidan da zasu zauna a wayarsa daya kama a gabatowar bikin kuma acikin unguwar Geza ne ba Ζauyen Geza ba. Domin dai a saninta cikin Sakwato akwai unguwa Geza kuma kuma akwai Ζaramin Ζyauye da mazauna cikinsa suke zuwa cirani cikin Sakwato. Batun sana’a kuma Ζiri-Ζiri ta Ζaryata bayan kuma bakinta dana Tukur Ιin sun yi magana ya tabbatar mata da hakan wanda har zaginsa ta yi a wajen. Amma kuma ta bashi haΖuri gudun kwaΙarta ta yi ruwa. Abinda ya Ζara tsumata jin makarantar da Yusuf ya maida Ζ΄aΖ΄anta, makaranta me tsada da kyau ga yaran ΙulΙul dasu gwanin ban sha awa.
Hidima ake sossai, Amne ma ba a barta a baya ba.
Ranar Asabar da misalin Ζarfe biyu na rana aka Ιaura auren Labiba da angonta. Da yamma aka Ιauki amarya aka nufi Ζauyen geza da ita.
Post a Comment for "WATA MACE CHAPTER 5 BY SANA S MATAZU"