Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 13 BY FATYMA SARDAUNA

SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 13 BY FATYMA SARDAUNA

                    Www.bankinhausanovels.com.ng 

Yana zaune acikin falon, taturo Ζ™ofa tashigo bakinta Ι—auke da sallama, cike da mamaki yake kallonta. “Bakije gidan Ƙawartaki bane?” ya tambayeta yana me tsareta da kyawawan idanunsa.

Murmushi tayi haΙ—e da Ζ™arasowa cikin falon, zama tayi gaf dashi, haΙ—e da Ι—aukan hanunsa ta Ι—aura akan cinyarta.   “Naje nasamu batanan, kuma dama banaso nabarka kai kaΙ—ai agida, shiyasa na dawo” tafaΙ—i haka tana me Ζ™ara faΙ—aΙ—a murmushinta.

Kansa yajinjina haΙ—e da Ι—aukan goran ruwan dake  aje a gabansa, yakai bakinsa,  kallonsa take tanaso tafaΙ—a masa abun dake cikin ranta, amma kuma tsoro takeji saboda batasan taya zai Ι—auki maganar ba.

Matsewa kawai tayi haΙ—e da sanya hanunta ta saΖ™alo hanunsa,  fuskarsa takafe da ido kana tace “Yau nahaΙ—u da Zahrah”

Da sauri ya Ι—ago kansa ya kalleta, cike da tsananin mamaki yace “Wace Zahrah?”

“Zahrah wacce kasani, wacce kuma tunaninta ke maΖ™ale acikin zuciyarka, babu dare babu rana” ta bashi amsa.

“A ina kikasanta, har kikasan cewa itace Zahrah’n danake tunani akowani lokaci?” yajefomata tambaya yana me kafeta da idanunsa.

“Duk wanda yasanka dole zaisan Zahrah, mussamman ma ace wanda yake kusanci dakai, ko kamanta cewa har yanzu akwai hotonta acikin Ι—akinka?”

MiΖ™ewa yayi daga zaunen dayake haΙ—e da cusa hannayensa cikin aljihun wandonsa.

“Zahrah Ι—aya na sani a rayuwata, kuma tajima da mutuwa, saboda haka ni bansan wata Zahrah ba” yanakaiwa nan azancensa yasakai yawuce cikin bedroom Ι—insa, ko waiwayenta baiyi ba.

Mamakine ya bayyana Ζ™arara akan fuskar Afrah, sakamakon jin kalaman Zaid da tayi,  “Dare safe rana, bashida wani aiki sai tunaninta, tasha jinsa yana kuka a toilet, dukkuma akan Zahrah Ι—inne, amma wai kuma yau da bakinsa yake cewa Zahrah ta mutu, anya kuwa Zaid yana lafiya?” Afrah ke magana da zuciyarta.

Murmushi tayi asakamakon tunawa da wani abu da tayi, tashi tayi tanufi Ι—akin da Zaid yashiga.

Yana zaune agefen gadonsa hanunsa, riΖ™e da wani littafi da kuma biro,  da’alama nazartan littafin yake, amma kuma idanunsa cike suke da Ζ™walla, yanajin motsin shigowar Afrah, yayi sauri ya rufe littafin, ransa a Ι“ace, ya juyo gareta.

“Mekikazo Ι—auka? Bana faΙ—a miki cewa bakoda yaushe ne, nake da buΖ™atarki ba, please get out!” yaΖ™are maganar yana meyi mata nuni da Ζ™ofar fita daga cikin Ι—akin.

Ajiyar zuciya ta sauΖ™e haΙ—e da takowa zuwa garesa, tana zuwa gabansa ta durΖ™usa haΙ—e da zube guiwowinta a Ζ™asa.

“Kagafarceni idan abun dana faΙ—a maka akan Zahrah ya Ι“ata maka rai, banyi haka donna Ι“ata maka ba, saidai kuma zanfaΙ—a maka koda zaka tsaneni ne,  wallahi bazaka taΙ“a yin rayuwar farinciki ba, harsai kasamu Zahrah ka Ζ™ara neman yafiyarta,  nasan cewa kana da buΖ™atar Zahrah akusa dakai, fiye da yanda kake da buΖ™atar ko wace mace a duniya,  amma kuma Ζ™addara babu yanda bata juyawa bawa, dan Allah kayarda dani, akwai abunda zanyi wanda zaisa kusamu jituwa a tsakaninka da Zahrah, harma da mijinta”

STORY CONTINUES BELOW

Kallonta yayi da jajayen idanunsa haΙ—e da tashi, kawai yawuce cikin bathroom.

“Afrah bazata taΙ“a ganewa bane, shi kaΙ—ai yasan irin zogi da kuma ciwon da zuciyarsa keyi masa, aduk sanda aka ambato masa sunan Zahrah,  a yanzu so yake yasa aransa cewa, babu wata Zahrah, domin wacce yasani tajima da mutuwa, wanda yake gani a yanzu, wata Zahrah’nce daban kuma ta wani ce”  tsaida zancen zucin nasa yayi,  haΙ—e da cire rigar dake  jikinsa, direct gaban shower ya nufa, tsayawa yayi haΙ—e da sanya hanunsa  Ι—aya, ya dafa jikin bango, ruwane keta dukan kansa dakuma bayansa, sauda dama idan yana acikin Ζ™unci, tsayawa yake gaban shower ruwa yaita dukansa, dahaka yake Ι—an samun relief.

*** ***

Kwance take akan kujera, sanye take da wani dogon sket, wanda yake a tsuke daga sama har Ζ™asansa,   sket Ι—in  irin roba Ι—innnan ne,  rigarta kuwa wata Ζ΄ar vest ce marar nauyi, fara Ζ™al da ita, tunda ta samu cikin nan, bata rabo dajin zafi, hakan yasanya bata cika zama da kaya masu nauyi ba,  wayartace rike a hanunta, kunnenta kuwa sanye suke duka da airpiece, waΖ™ar film Ι—in Sanam Teri Kasam takeji, harwani lumshe ido take, saboda tanason waΖ™oΖ™in film Ι—in sosai,   sweet ne abakinta tana Ι—an tsotsa, gudun tara yawu, dayake bata Ζ™ure volume Ι—in waΖ™arba, hakan yasanya tajiyo bugun Ζ™ofar da akeyi mata,   da mamaki take kallon Ζ™ofar falon, ita dai tasan batayi da kowa cewa yau zaizo wajenta ba, kuma yanzu ba lokacin dawowan Doctor bane, batajin zata iya tashi dan haka saita bawa me knocking door Ι—in damar shigowa kai tsaye.

Da sallama Ι—auke a bakinta, tashigo cikin falon.  Kallon kallo suka shigayiwa juna ita da Zahrah,  ita tana kallon Zahrah ne fuska Ι—auke da murmushi, yayinda  Zahrah kuwa ke Ζ™are mata kallo, saboda batasanta ba ma ita kwata kwata.

“Da dai anbani izinin shigowa, aida sai na shigo” takatse Zahrah daga kallon da take mata, ta hanyar faΙ—an haka.

Murmushi Zahrah tayi haΙ—e da tashi zaune tace “Bismillah, shigo”

Ƙarasowa tayi tsakiyar falon, haΙ—e da zama akan kujera.

“Sannu da gida” tace tana murmushi.

“Yauwa sannunki da zuwa” Zahrah tafaΙ—i haka itama tana murmushi.    MiΖ™ewa tayi da niyar takawo mata ruwa da lemo, da sauri tace. “A’a barshima basai kinkawomin komai ba, daga gida nake banajin Ζ™ishi”

Kallonta kawai Zahrah tayi kana ta koma kan kujera ta zauna, cike da Ζ™osawa Zahrah tace.  “Baiwar Allah Bangane wace ke ba fa”

Murmushi takumayi akaro na barkatai.   “Sunana Afrah, dama nasan baki sanniba, amma ni nasanki, kiyi haΖ™uri bansaniba ko hakan danayi yaΙ“ata miki rai, jiya naganki a hotel kinacin abinci keda wani, wanda nake kyautata zaton cewa mijinki ne, tunda naganki, naji kin kwantamin arai, kuma wallahi da zuciya Ι—aya nake sonki, please idan bazan takuraki ba, inaso muzama Ζ™awayen juna”

Murmushi Zahrah tayi me sauti, haΙ—e da cewa “Nagode Ζ™warai da Ζ™auna, amma kuma inaganin kamar akwai matsala, idan har muka fara Ζ™awance yanzu, dududu fa yau nafara ganinki, kinga dole kafun abota musan halin juna” inji cewar Zahrah.

“Da alamu bakida wata matsala nima kuma haka, kuma insha Allah bazakiyi danasanin Ζ™awancen mu ba”   taΖ™ara da cewa “Akan hanya nake, watarana zanyi miki zuwa na musamman amma kafun nan,please samin number’n wayarki” miΖ™awa Zahrah wayarta da ta cirota cikin jaka tayi.

Babu musu Zahrah ta amshi wayar tasanya mata number’nta aciki, kana ta miΖ™a mata abarta.

Murmushi tayi haΙ—e da miΖ™ewa tsaye, “nagode sosai” tace kana ta nufi hanyar fita daga cikin falon, Zahrah na ganin ficewarta ta sauΖ™e ajiyar zuciya, haΙ—e da komawa ta kwanta, aranta tana addu’an neman tsari daga sharrin mugayen mutane, da kuma aljanu….

*** *** ***

Gaba Ι—aya yau tatashi jikinta arikice, ganin haka yasa Dr.Sadeeq hana kansa zuwa office, yazauna tare da ita, yanata amsar shagwaΙ“anta, zuwa yanzu sosai shagwaΙ“anta yafi na da, tun da tasamu cikin wani sakalci da taΙ“ara ya tsiro mata,  shikuwa doctor biye mata yake, hakan yasa gaba Ι—aya yanzu tazama wata, shagwaΙ“aΙ“Ι“iya da ita sai kace Ζ΄ar shekara 4.

Kwance take akan sofa yayinda kanta ke Ι—aure bisa cinyarsa, minti irin me tsinkenan ne abakinta, tana tsotsa a hankali, yayinda shikuwa ke shafa sumar kanta a hankali.

_______

STORY CONTINUES BELOW

Mamakine ya matuΖ™ar kashesa, ganin unguwa da kuma inda Afrah ta kawosa, Ι—ago idanunsa yayi ya watsamata su, “Inane nan?” yatambayeta still idanunsa na kanta.

Murmushi tayi masa haΙ—e da cewa “Unguwar su Ζ™awartawa da nake gaya maka ne, kuma ganan ma gidan nata” taΖ™are maganar tanayi masa nuni da gidan dake gefensu,   bugawar zuciyarsa ne ya Ζ™ara tsananta,  take yaji kansa nayi masa wani irin sarawa.

“Kimaidani gida Afrah, tunkafun ranki ya Ι“aci!” cikin yanayi na Ι“acin rai yake maganar.

Dama tasan za ayi haka,  hanunta ta Ι—aura akan nasa cikin son ta rarrasheshi tace “Kayi haΖ™uri Dear, bazamu wuce 30 minute ba, nasan kasan gidan, kakuma san wacece acikin gidan, banyi haka donna Ι“ata maka ba, nayi hakane don kawai kasamu salama, Ζ™warai nasan idan harta yafema kuma ayau idan kuka ga juna, tabbas komai zai wuce, duk da nasan sai ahankali, amma kuma dukanku zaku samu sassauci….”

“Kimaidani gida nace kona Ι“aΙ“Ι“ala Ζ™ashinki gida biyu anan wajen!!” amatuΖ™ar hasale yaΖ™are maganar.

Saida ta tsorita domin bata tsammaci wannan tsawan daga gareshi ba.  

“Fita” yace da ita murya a dake.

Sumi sumi ta fice acikin motar, dan ta fuskanci sam babu alamar wasa a tattare dashi. Fita shima yayi daga cikin motar ya koma wajen zaman driver domin dama a wajen mai zaman banza yake dazama, itakuma tana wajen zaman driver.

Yana shiga yatada motar, kallon  Afrah yayi fuska babu walwala, da sauri ta buΙ—e motar tashiga, da Ζ™arfi yaja motar sukabar Ζ™ofar gidan.

Suna zuwa gida, ya wuce Ι—akinsa kai tsaye, itama Afrah tayi nata Ι—akin,  sam bataso haka yakasance ba, taso ace  abun da ta Ζ™udurta aranta shine ya faru.

Kayansa yashiga haΙ—awa acikin trolly Ι—insa, saida yatabbatar ya haΙ—a duk wani abun da yake buΖ™ata,  dama kuma jiya aka kawo masa visa’n su.

Tana tsaye agaban mirror daga ita sai wata Ζ΄ar fingilan riga, kallo Ι—aya yayi mata ya Ι—auke kansa,  akwatinta ya ciro acikin drawer, kallonta yayi itaΙ—inma kallonsa take.

“Kishirya kayanki, 6 pm zamu tashi gobe insha Allah” yanakaiwa nan azancensa yasakai yafice daga cikin Ι—akin.

Mamakine yakama Afrah,  “dama ya shirya musu tafiya shine baisanar da’ita ba?” tambayar da tayiwa kanta kenan,  ganin bata da wani wadataccen lokaci yasanya, tashiga shirya kayanta acikin trolly’n, da ya fito mata dashi. 

Zama yayi akan gado haΙ—e da jawo diary Ι—insa ya buΙ—e, abun rubutu ya Ι—auka yaΙ—anyi rubutu, kaΙ—an kana ya rufe diary’nnasa ya  tura acikin wata Ζ΄ar Ζ™aramar jaka.

Washe gari

Kamar yanda ya faΙ—a Ζ™arfe 6 dai dai jirginsu ya Ι—aga zuwa Ζ™asar America, a wannan karon baya tunanin zai waiwayo Nigeria, so yake ya koma America da zama gaba Ι—aya,  wannan shine Ζ™udurinsa, sai dai idan Afrah tace zatazo  Nigeria bazai hanata ba, shikam dai yasa aransa cewa bazai zoba, saidai ko wani babban dalili, me Ζ™arfi.

***   *** ***

Abuja University Gwagwalada.

Yau suke bikin kammala degree Ι—insu, saboda haka gaba Ι—ayansu sunacikin farinciki.   Kowannensu yasha adonsa cikin shiga ta burgewa gwanin ban sha’awa.

Tsaye take ajikin wata bishiya tana waya,  sanye take da baΖ™ar tie abaya gown ajikinta, wacce daga hanunta zuwa Ζ™asanta aka mamayeta da ado na flowers masu kyaun gaske.   Da babban mayafi tayi amfani wajen rufe jikinta, sai dai kuma duk da haka, saida cikinta ya bayyana kansa, sosai taΖ™ara haske da kuma kyau, sai wani Ι—aukar ido take, daganinta kaga me ciki, wacce take cikin jin daΙ—in,  yanzu watannin cikinta huΙ—u kenan amma kuma tuni ya bayyana kansa, ita kanta har mamakin girman cikin nata take, don watanninsa basukai ace girmansa yakai  har  haka ba.

“Zakizo mu kammala pictures Ι—inne kokuma zaki tsaya soyewa”   Husnah dake tahowa ga Zahrah tafaΙ—i haka da Ι—an Ζ™arfi. tayanda Zahrah’n zata jita.

Murmushi Zahrah tayi haΙ—e da kashe wayar, kana ta juyo da kallonta ga Husnah.

“Kinsan banagajiya da jin muryarsa ne, amma muje mukammala agurguje, saboda gida nakeson nakoma gaba Ι—aya jina nake agajiye” Zahrah ta  faΙ—i haka tana Ι—an yamutsa fuskarta.

Murmushi Husnah tayi haΙ—e da cewa “Nima sauri nake saboda yau Man Ι—ina zai turo magabatansa gidanmu, kuma ayau za’a sa mana ranan aurenmu, nasankuma baza asa ranan da yawa ba, just ba zai wuce 1 month ba”

Dariya Zahrah tayi haΙ—e da cewa “Lallai Husnah aure kikeso sosai, ji yanda lokaci Ι—aya kika falle.”1

Dariya sosai Husnah tayi haΙ—i da cewa “Laifine dan mace irina taso aure? nakai aure, nakuma cika mace me lafiya, kinga kuwa dole naso aure, ke nifa wallahi gaba Ι—aya yanzu rayuwata, a daddafe nakeyinta, na Ζ™osa najini a Ζ™irjin mutumin, nima yakasheni da irin nasa salon” cikin yanayi na shauΖ™i ta Ζ™are zancen.

Dariya dukansu sukayi  kana suka tafa.

Basu tsaya an kammala bikin dasu ba, kowaccensu ta nufi gida.Kwance take akan gado, hanunta riΖ™e da littafin hausa, tana karantawa,  sanye take da doguwar riga irin bubu gown Ι—innan, zuwa yanzu cikinta ya Ζ™ara girma, har tsoro girman ke bata, ga yawan motsin da takeji acikin cikin nata.

Yajima a tsaye yana kallonta,  sosai cikin ya Ζ™ara mata kyau, gashi cikin ya bayyana kansa acikin rigar dake jikinta.

“Ζ³an mata na!” yaΖ™ira sunanta cikin wata murya me sanyi.

Da sauri ta dawo da kallonta garesa, murmushi tasakar masa, haΙ—e da tasowa daga kan gadon, da Ι—an gudu gudu, tafaΙ—a cikin jikinsa ta rungumesa.

Hannuwansa yasanya duka biyu shima ya rungumeta,  kiss ya manna mata akan wuyanta, haΙ—e da lumshe idanunsa, yana me shaΖ™an Ζ™amshin jikinta, sosai Ζ™amshin nata keyi masa daΙ—i.

“Nayi kewarki madam Ι—ina me ciki” yafaΙ—i haka yana me shafa cikin dake jinkinta.

AshagwaΙ“e tace “Nima nayi kewarka sosai fa dear!”

“Dagaske kinyi kewata? keda ma kika hanani abun daΙ—ina, two days fa kenan yau baki bani zumana ba!” cikin yanayi na Ι—an karya murya yafaΙ—i haka, lokaci guda yana me marerece idanunsa.

Ɗan Ζ™aramin bakinta taturo gaba, cike da shagwaΙ“a tace “To bakaineba saikanamin da Ζ™arfi, kuma Allah Hubby yanzu  idan kajima kanayi sainaji kamar zan amar da kayan cikina, gashi tsoro nakeji idan kana fidda wannan sautin numfashin, kamarfa zaka sume haka kake”

Sake marerece fuska yayi haΙ—e da kwantar da kanta akan wuyansa, hanunsa ya Ι—aura akan cikinta.”Babyn Mama kaine kake wahalar min da mata ko? kuma kaine kake hanawa abani abun daΙ—i na ko? please my boy kabari yau abani ko kaΙ—anne, kuma ae balaifina bane, banasanin ma inayin kamar zan shiΙ—e, kuma ma ae daΙ—in kine yake da yawa ko Baby boy Ι—ina?”  yatambayi yaron cikin?

Dariya ne yakamata ganin yana magana da cikin,  “Kai Hubby ina ma zaijika, ko saninka fa baiyi ba, ni kaΙ—ai ya sani” ta Ζ™are maganar tana dariya.

“Wayace miki baisanniba, lallai kam idan bai sanniba ae kuma shikenan magana ta Ζ™are, taya ma za’ace baisan wanda ke yawan aika masa gaisuwa ba? dan ma dai kwana biu….”

“Shiii! Ina roasted fish Ι—ina, da nace katahomin dashi?” taje fo masa tambayar ta hanyar katsesa daga maganan da yakeyi.

“Nakawo miki yana falo..”

Bata tsaya jin sauran zancenba, ta wuce falo cikin sauri.

Zama tayi akan sofa tashiga cin roasted fish Ι—inta, sosai taji daΙ—in kifin, domin kuwa da Ι—uminsa aka kawo mata, gashi yaji onion sauce. saida taci sosai kana ta Ι—aura da lemon exotic.

Shikuwa tana fita acikin Ι—akin, direct bathroom ya nufa, wanka yayi, domin dama agajiye yake sosai, kasancewar daga office ya dawo.

Fitowarsa daga cikin bathroom Ι—in yayi daidai da shigowarta cikin Ι—akin. Kallonsa tayi haΙ—e da sakar masa murmushi, shima murmushin yayi mata, kana yanufi gaban dressing mirror don kimtsa kansa.  Doguwar riganta ta cire kana ta faΙ—a toilet.

Lokacin da tafito Ι—aure da wani Ι—an Ζ™aramin towel ajikinta, shikuma yana zaune akan gado, yana sipping fresh milk, a hankali.   Kallon santala santalan cinyoyinta yayi, haΙ—e da haΙ—iye wani yawu, sosae yake missing matar tasa, musamman ma daddaΙ—an Ι—umin dake cikin jikinta, wanda idan yajisa yake sanyasa cikin nishaΙ—i da kuma nutsuwa.  Kasa haΖ™uri yayi alokacin da ta juya masa baya, mai take shafawa ajikinta, yayinda towel Ι—in yaΙ—an zame daga kan Ζ™irjinta, har tsayayyun breast Ι—inta suka Ι—an bayyana kansu

STORY CONTINUES BELOW

Rungumeta yayi ta baya, haΙ—e da Ι—aura kansa bisa wuyanta.  Hancinsa yashiga gogawa akan wuyannata yana  me busa mata numfashinsa me Ι—an Ι—umi akan fatarta, take taji tsikar jikinta na tashi,  Ι—ago idanunta tayi ta kalleshi, shima idanunsa ya jefa acikin nata, wani irin kallo me matuΖ™ar kashe jiki, yake jifanta dashi, bazata iya Ι—auke idanunta, daga cikin nasa idanunba, haΖ™iΖ™a kyawun idanunsa, na matuΖ™ar Ι—aukar hankalinta,  lumshe idanunta tayi, haΙ—e da sauΖ™e wani irin numfashi, sake jawota jikinsa yayi haΙ—e da  Ι—aura duka hannayensa, akan Ζ™ugunta,  matso da fuskarsa yayi daf da tata, har hancinsu na gogan najuna, still idanunta a rufe suke bata iya kuma buΙ—esu ba,  Ι—aura bakinsa yayi akan nata bakin, a hankali ya shiga tsotsan leΙ“enta na Ζ™asa,  yayinda itama  ke tsotson lip Ι—insa na sama,  numfashi suka shiga sauΖ™ewa a tare, harshenta yakama yana sha a hankali, yayinda yasanya hanunsa, ya warware towel Ι—in dake Ι—aure ajikinta, hakan yabawa towel Ι—in daman faΙ—uwa Ζ™asa,  ahankali yake shafa bayanta, zuwa gefe da gefen cikinta,  sauΖ™ar numfashinta ya tsananta, saboda sosai takejin daΙ—in abun da yakeyi mata.  Harsaida tasamu kusan Ι—aukewar numfashi, alokacin daya soma murza breast Ι—inta, yanayin yanda yake mata ya matuΖ™ar shiΙ—ar da ita, ashe bashine kaΙ—ai yayi missing Ι—inta ba itama tayi kewarsa sosae. Hanu tasa ta zame rigar dake jikinsa,  wani irin Ζ™aΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya suka sauΖ™e alokaci guda, sakamakon haΙ—uwar fatar jikinsu waje Ι—aya,sosai hakan yasake basu wani shauΖ™i. Kasa jure yanda take goga masa tausassun breast Ι—inta akan chest Ι—insa yayi, Ι—agata yayi caΙ—ak suka nufi kan bed. 

Kwantar da ita yayi flat haΙ—e da bin ko ina najikinta da kiss, har izuwa kan breast Ι—inta.   Sosai yashiΙ—ar da ita, yayinda shikuma ya zauce,  ba abun dake tashi acikin Ι—akin, sai sautin numfashinsu, dake fita a hankali….. Yau love fa yakawo wuta, domin kuwa gaba Ι—aya Doctor ya manta, da kansa da kowa nasa, Zahrah’nsa tabasa zuma wanda samunsa ke da matuΖ™ar wahala, musamman kuma daya kasance wannan zuman natane ita kaΙ—ai, Allah yabata, sauran kuwa kowacce da irin tatabaiwar,   sosai yau doctor ya tara mata gajiya, sai kukan shagwaΙ“a kawai takeyi masa, dakansa yayi mata wanka, bayan yayi nasa, kana ya naΙ—ota a towel kamar wata Ζ΄ar baby, kwanatar da ita yayi akan gado, bayan yasanja bedsheet Ι—in, domin wancan ya Ι“aci da sperm Ι—in Me daΙ—insa,  shi har mamakin yawan ruwa irinnata yake.  Kwanciya yayi shima akan gadon kana yajawota jikinsa, luf tayi acikin jikinsa, tana me fesa masa iskan numfashinta, acikin Ζ™irjinsa.    Bayanta yake shafawa a hankali, yana me sauΖ™e ajiyar zuciya akai akai.    Ƙamshin turarensa dake tasowa yana shiga cikin hancinta, shine abun da ke neman hautsina mata Ζ™waΖ™walwa, domin kuwa, yana mata yanayi da wani Ζ™amshi  wanda har abadan duniya bazata taΙ“a, mantawa da Ζ™amshin da kuma mai Ζ™amshin ba,  take bugun zuciyarta ya tsananta, haka nan taji zuciyarta naneman karyewa,  bazatace ta manta dashiba, domin kuwa aduk kwanan duniya yana maΖ™ale acan Ζ™asar zuciyarta. “To tayama za’ayi ta manta dashi?” tambayar da tayiwa kanta kenan, lumshe idanunta tayi, alokacin da ta tuno da haΙ—uwarsu ta Ζ™arshe, alokacin daya kusanto zuwa gareta yana me neman yafiyarta, bazata taΙ“a mantawa da wannan ranan ba, kamar yanda bazata taΙ“a mantawa da ranan daya fyaΙ—eta ba,  wani murmushine ya kuΙ“uce mata, batare da ta shiryawa hakan ba,  azuciyarta tace “Lallai Zaid yayimini babban Illa, wanda har nakoma ga mahaliccina tabonsa bazaigoge ba, yayimin fyaΙ—e sannan kuma ya koyamin soyayyarsa” batasan da cewa hawaye sun fito daga cikin idanuntaba, saida taji Ι—uminsu nabin kan kumatunta, da sauri tasanya hanu ta share gudun kada doctor ya gani. Ashe ta makaro domin kuwa  idanunsa na kanta.  Sake matseta yayi acikin Ζ™irjinsa, haΙ—e da kai bakinsa, kan nata yashiga tsotsa a hankali,  ganin haka yasa takama harshensa tana tsotsa, kamar tasamu sweet,  sosai takejin daΙ—i idan tana sucking tongue Ι—insa, har wani suga suga takeji akan harshen,  wata Ζ™ila hakan yana da nasaba, da yawan shan sweet da yakeyi, zaiyi wuya kaga bakinsa shiru babu sweet aciki, hakan ajininsa yake. (Kamar dai sweet and big bro Ι—ina, i miss you yayana?)     bedaina kissing Ι—inta ba harsai dayaji sauΖ™ar numfashinta, nafita slowly, alaman tayi bacci kenan, mintuna kaΙ—an shima bacci ya Ι—aukesa….

*** *** ***

America.

Tunda sukaje America take ta fama da rashin lafiya, gaba Ι—aya ta zafge ta rame sosai, ga Zaid daya sata agaba, kullum saiyayi sex da ita sama da sau biyu.  Yanzuma durΖ™ushe take aΖ™asan tiles tanata kwarara amai,  ko kyakkyawan motsi takasa yi.

Shigowarsa gidan kenan, sosai yaΖ™ara kyau da haske,  Ζ™aΖ™arin amanta daya keji ne yasanya sa nufar Ι—akinta da sauri.  Tagama aman amma takasa tashi daga wajen domin gaba Ι—aya jikinta yayi laushi.

Jawota yayi jikinsa ya Ι—aurta akan cinyarsa, cike da kulawa yake shafa bayanta, sannu yaketa yi mata, don ko ba afaΙ—aba, kowa yaganta yasan tanashan jiki. Shida kansa ya gyara wajen, kana ya buΙ—e drawer’nta ya Ι—auko mata mayafi,  hanunta yakama suka fita daga cikin Ι—akin, direct asibiti ya nufa da’ita.

STORY CONTINUES BELOW

Gwaje gwaje aka mata, kana akace su Ι—an jira akawo musu result, babu jimawa kuwa, saiga result Ι—insu yafito.  Bayan doctor James yaduba result Ι—inne, yasaki murmushi haΙ—e da duban Zaid, cikin harshen turanci  yace “Congratulation friend matarka tana Ι—auke da ciki, na 9 weeks!”

Kamar sauΖ™an aradu haka Zaid yaji kalaman Dr.James acikin kunnuwansa, da sauri ya kallo Afrah wacce itama take cike da mamakin abun da Dr.James Ι—in yafaΙ—a.

“Cikifa kace Doctor?matana tana Ι—auke da cikina?” yatambaya cike da tsananin mamaki.

“Eh mana, ai bazanma wasa ba, dagaske matarka tana Ι—auke da ciki, shiyasa take ta amai babu Ζ™aΖ™Ζ™autawa” duk cikin harshen turanci irin nasu na America suke maganan. 

Bazai taΙ“a misalta irin daΙ—in da yajiba, hakanan ya tsinci kansa da sakin murmushi, tashi yayi ya rungume Afrah, jiyake kamar ya ciro cikin aJikinta, yadawo dashi jikinsa, gani yake kamar zaifi kula da cikin.   Agurguje yayi duk wani cike cike da zaiyi sukabar asibitin.  suna isa cikin gida yayi parking motar, amaimakon yabarta tayi tafiya da Ζ™afanta, saiya Ι—agata caΙ—ak, wai yana gudun kada cikin ya jijjiga.  Akan kujeran falo ya direta haΙ—e da zama daΙ“as agabanta, hannayenta yakamo duka biyu, cike da farinciki yace.  “Nagode Afrah, nagode miki sosai, kin bani farincikin dana rasa,  haΖ™iΖ™a Allah ne yadubeni yadawomin da farincikina ta hanyarki,  please Afrah, kikulamin da Ζ΄ata dake cikin cikinki kinji, daga kan naira Ι—aya har 100m zan iya mallakamiki, matuΖ™ar zaki kulamin da Ζ΄ata dake cikinki, inasonta inasonta fiye da komai aduniya, Allah ne yadawomin da abuna, dama tawace bata kowa ba, please ki kulamin da cikin dake jikinki, namiki alΖ™awari zanbaki duk wani abu dakikeso”

Mamakine yakusan kashe Afrah, sam bata fahimci me kalamansa suke nufi ba, yace dama tasace bata kowa ba to wakenan? tambayar da take matuΖ™ar so tasamu me amsa mata kenan.  Ganin ya kafeta da idanunsa ne yasanya tasaki murmushi haΙ—e dacewa “Nima inason na haifamaka Ι—a ko Ζ΄a, kuma insha Allah Zan kula da cikin nan sosai, fiye ma da yanda zan kula da kaina, amma me yasa kaketa cewa Ζ΄a, bamusan fa menene ba macece ko namiji Allahu a’alam”

Murmushi Zaid yayi haΙ—e da miΖ™ewa tsaye “Mace zaki haifa insha Allahu, wannan bayin kaina ko yin wani bane, yin Allah ne, shiya hanani, yanzu kuma shiya bani, saboda haka bazan gajiya dayi masa godiya ba” yana kaiwa nan azancensa yawuce Ι—akinsa.   Haryanzu dai ita bata fahimci ina kalamansa suka dosa ba, kwanciya tayi akan kujera, minti kaΙ—an bacci Ι“arawo yayi gaba da ita.

Shikuwa yana shiga cikin Ι—akinsa, Ι—an Ζ™aramin drawer Ι—insa ya buΙ—e wanda ciki yake aje diary’nsa, Ι—auko diary,n yayi yasoma rubutu, yana kammalawa ya buΙ—e shafin farko na diary’n nasa, take wani hoto wanda ke Ι—auke da kyakkyawar fuskarta ya bayyana, tayi kyau Ζ™warai acikin hoton, gaΙ—an Ζ™aramin bakinta nan yasha lipstick, murmushi yayi alokacin daya kai hanu yashafi kan kumatunta,   ahankali yace “Nasani dama zaki dawo gareni, kobata hanyar zama tawa ba, amma tabbas zaki dawo gareni, gashi kuma kindawo ta hanyar dayafi dacewa,  nan bada jimawa ba zakizo amatsayin tawa ta har abada, duk wuya duk tsanani ke Ι—in zaki kasance tawace, nine wanda bakida kamarshi acikin duniya, nine mutum guda Ι—aya wanda zai kasance me matuΖ™ar mahimmanci a wajenki, nine wanda bazaki taΙ“a samun irina ba har abada, ni Ι—ayane nake da wannan matsayin agareki, bayanni babu wani”   wasu irin hawayene masu zafi suka gangaro daga cikin idanunsa, da sauri yarufe diary’n kana ya shiga toilet donyin wanka, jinsa yake acikin matsanancin farinciki, lallai Allah yamasa kyauta, wacce zata kasance mafi soyuwa agareshi.

(Wayaga Zaid da Ζ΄a ko Ι—a?)

***

Wani irin kulawa na sadidan Zaid ke bawa Afrah, kome takeso adunia shiyake yi mata,  zuwa yanzu harmamakinsa takeyi, irin yanda yake nunamata tsananin Ζ™auna,  wani lokaci har kuka takeyi, itama tana matuΖ™ar son cikin sosai, amma yanda Zaid ke Ζ™aunar cikin ba’a magana, tasani badon komai yake nuna mata wannan Ζ™aunarba saidon cikin dake jikinta,   haka take rainon cikinta cike da Ζ™aunar abun dake cikinsa, wani lokaci tana mamakin yanda Zaid keta faΙ—an wasu irin maganganu wanda suke matuΖ™ar Ι—aure mata kai, daga zaran yataΙ“a cikin sai yafara cewa “Babyna kina lafiya ko, na Ζ™osa kidawo gareni, inakewarki sosai, kizo muyi rayuwarmu wacce bamuyita ba da, muyi rayuwa cikin farinciki, inasonki sosai babyna!” abun dayake faΙ—a kenan, hakan kuwa mamaki yake bata sosai, duk kuwa yanda taso fassara kalaman nasa, bata iyawa, hakanan take haΖ™ura kawai ta share. Cikin nada wata huΙ—u Zaid ya ware wani Ι—aki dake cikin bedroom Ι—insa, saida yacika Ι—akin tam da kayan wasan yara, babu abun da babu nawasan yara acikin Ι—akin,   acewarsa Ι—akin babynsa ne, itadai Afrah idanu kawai tazuba masa, saboda taga soyayyar dayakeyiwa abun dake cikinta naneman zautar dashi.

STORY CONTINUES BELOW

*** *** ***

Nigeria.

Masha Allah cikin Zahrah ya Ζ™ara girma sosai domin kuwa yanzu yana wata na bakwai ne, sosai cikin yayi turtsetse dashi,  zuwa yanzu batasanya wani kaya sai dogin ruguna, irin masu faΙ—in nan.

Tana zaune atsakiyar falon, yayinda ta tusa wani tray wanda ke Ι—auke da kayan fruit agaba, gefe kuwa plate Ι—in dambun nama ne wanda yaji albasa, sai kuma Ι—an wake wanda yaji cabbage da cocumber ga tomatoes, yasha mai da yaji, wai duk wannan tulin kayan ciye ciyen Zahrah so take taci kowanne acikinsu.  

Auntie Raliya ce tafito daga kitchine hanunta Ι—auke da  wani cup wanda cikinsa ke Ι—auke da wani zuma, me magani aciki.

“Manya anata fama kenan” Inji cewar Auntie Raliya.

“Wallahi Auntie ni duk na rasa ma da wanne zan fara, inaga Ι—anwakena kawai zanci sauran kuma nabari saina koma gida” Zahrah tafaΙ—i haka ga Auntie Raliya tana me jawo plate Ι—in Ι—anwaken ta.

Dariya Auntie Raliya tayi haΙ—e da zama kusa da Zahrah’n  “Gaskia Bro bai iya ajiyaba, wannan wani irin Ι—a ne haka yasa miki acikin cikinki, yaro ne zance ko yarinya, sai shegen ci”

Dariya Zahrah tayi sosai haΙ—e da kallon Auntie Raliya cikin dariya tace “Wallahi kuwa Auntie, dubeni fa yanda nayi Ζ™atuwa, nayi muni, shikuma duk kwanan duniya Ζ™ara kyau yake, gaskia ni bazan yarda ba, auntie wayo kawai yamin”

Dariya Auntie Raliya tayi haΙ—e da miΖ™owa Zahrah kofin dake riΖ™e a hanunta.   “Ungo amsa kishanye duka”

Zaro idanu Zahrah tayi, haΙ—e da kallon Auntie Raliya’n “Auntie kamar tsumi ne fa, acikin cup Ι—in?”

“Ba kama bane, tsumine me kyau na mata, wanda yake matuΖ™ar wujijjiga oga, amsa kisha banason gardama” Auntie Raliya tace tana Ζ™oΖ™arin kai kofin bakin Zahrah.

KwaΙ“e fuska Zahrah tayi, haΙ—e da Ι—an marerece ido. “Wallahi Auntie tsoro nake insha wani tsumi, a yanzun, kinsan kuwa yanda nake fama, doctor fa shiΙ—ewa yake, nasha wannan kuma ae shikenan sumar dashi kikeso nayi”

Dariya sosai Auntie Raliya tayi, haΙ—e da Ι—aukan tsuminta ta shanye  “Shikenan to idan kin haihu na miki haΙ—i na musamman, matar doctor, ashe ba abanza ba, gaba Ι—aya Ζ™anina ya sukurkuce akanki, wato kinsan me kikeyi masa” cewar Auntie Raliya.

Dariya Zahrah tayi haΙ—e da cigaba da cin Ι—anwakenta, sai kaΙ—a kai take wai Ι—an waken yayi daΙ—i, itakuwa Auntie Raliya saiyi mata hira take,  sosai suka seta ita da Ζ΄an uwan mijinta,  Ζ™auna sadidan take samu daga wajen Hajiya,  yayinda Auntie Raliya ma ke nuna mata so, sun saba sosai da Auntie Raliyan, harjinta take kamar Ζ΄ar uwarta tajini, don babu abun da take Ι“oyewa Auntie Raliyan, dayake Auntie Raliyan ma irin wayayyun matan nanne, basu da nuΖ™u nuΖ™u, baruwanta dawani abu waishi surukanta, ta Ι—auki Zahrah’nne kamar Ζ΄ar Ζ™aramar Ζ™anwarta, don har sirrin yanda ake kama me gida a hanu take faΙ—a mata..

Sunsha hira sosai da Auntie Raliya, sai bayan sallan Isha doctor Sadeeq yazo ya Ι—auketa suka koma gida.  Washe gari kuwa, tun 7 am tatafi gidansu amarya Husnah, don yau za’ayi kamunta, kuma itace best friend, don ma ciki yayi mata cikas. 

Anyi kamu cikin kwanciyar hankali, yayinda kamun ya Ζ™awatar sosai, anyi Ι“arin naira sosai baga gidansu ango ba baga gidan su amarya ba, naira tayi kuka don ankasheta a wannan ranan, kayan da amarya tasanya ma kaΙ—ai kuΙ—insu baΖ™aramin yawane dasu ba. Zahrah bata bar gidansu Amarya ba sai bayan magrib kusan 9 pm,  haka ta koma gida agajiye. Washe gari kuma,  aka rangaΙ—a walima, shima sosai yaΖ™ayatar don anyi musu wa’azi me ratsa jiki,  ranan friday kuma aka Ι—aura auren Husnah da angonta,  sosai dai akasha shagalin bikin Husnah, inda Zahrah tataka rawar gani sosai, wajen ganin tabawa Ζ™awartata kyauta, wacce zata burgeta. Ranan da aka kai Husnah Ι—akin mijinta sosai Zahrah tayita mata tsiya, ita kuwa Husnah ko ajikinta, cewa ma tayi “Mijinta baifi Ζ™arfinta ba, bata wani jin tsoro, tsaf zata iya Ι—auke buΖ™atarsa”…..

***

Yana zaune akan kujera ita kuma tana zaune aΖ™asa, wani irin ciwo takejin cikinta nayi mata, tun Ι—azu yake ankare da ita, amma dai baice da ita komaiba, ganin dayayi tana murΖ™ususu waje Ι—aya ne yasanya sa cewa “Baby yadai, akwai damuwa ne?”  murmushin dole ta Ζ™aΖ™alo haΙ—e da dubansa ta mererece fuska. “Samad marata kemin ciwo da cikina” tafaΙ—i haka tana me cije laΙ“Ι“anta.

“Subahanallah to kodai naΖ™ira Bro nafaΙ—a masa ne?” yatambayeta cike da damuwa.

Da sauri ta girgiza masa kae haΙ—e da cewa “A’a  dan Allah Samad karka Ζ™irasa, banaso yatashi hankalinsa”

Murmushi kawai Samad yayi haΙ—e da cewa “Babe Ζ΄ar daΙ—i miji”

Harara ta aika masa haΙ—e da murguΙ—a masa baki tace “Eh Ι—in”

Murmushi yakumayi yaci gaba da cin abincinsa, itakuwa sake matsewa tayi tana mejin ciwon naΖ™ara Ζ™aruwa.   (Kodai Babe haihuwa zatayine ? Chaiii wayaga Zahrah a Labour room?‍♀?‍♀)Har ya Ζ™are cin abincin tana nan zaune sai rumtse ido da cije baki take,  Ζ™irjinta ne yasoma bugawa akai akai, sakamakon tunawa da tayi cewa akwai aiki  babba agabanta.  MiΖ™ewa tayi daga zaunen da take, ahankali take taka Ζ™afanta data Ι—an kumbura, harta shige cikin Ι—akinta.  Da kallo yabita har ta Ι“acewa ganinsa, murmushi kawai yayi shima  kana ya Ι—auki wayarsa yafice daga cikin falon.

Tana shiga cikin Ι—aki direct ta wuce bathroom wanka tayi da ruwan zafi, kana ta zo ta Ι—auki magungunanta tasha.    wata Ζ΄ar Ζ™aramar riga tasanya ajikinta, kana tabi lafiyar gado ta kwanta, minti shida tsakani bacci ya Ι—auketa.+

Kwanciya yayi luf abayanta bayan yacire rigar dake jikinsa,  hanunsa yasanya ya Ι“alle mata aninayen dake  jere  a gaban rigarta,  lumshe kyawawan idanunsa yayi haΙ—e da sanya hanu ya shafi breast Ι—inta.  Saida ya sauΖ™e ajiyar zuciya me Ζ™arfi, kana ya sake rungumeta ajikinsa, kansa ya Ι—aura akan wuyanta, haΙ—e da sanya harshensa, yashiga lasan fatar wuyanta, yayinda hanunsa ke kan breast Ι—inta, yana murzawa a hankali. Kamar acikin mafarki takejin abun da yakeyi mata,ahankali ta buΙ—e idanunta, batakai ga kallonsa ba, daddaΙ—an Ζ™amshin turarensa, ya sanar da ita cewa shine, sake narke jikinta tayi acikin nasa,  jin alamun cewa tafarka ne, yasanyasa juyo da ita suka zama suna fuskantar juna.  Kallonsa tayi da idanunta, da suke cike da magagin bacci, murmushi tasakarmasa haΙ—e da sanya hanu ta shafi lallausan sajen fuskarsa.   Idanunsa da suke cike da  tarin sha’awarta ya watsa mata haΙ—e da matso da fuskarsa daf da tata, har numfashinsu na gauraya dana juna,  yanayin irin yanda yake kallonta ne, yasanya taji gaba Ι—aya jikinta yayi sanyi, wani irin Ζ™aunarsa me sanyi taji tana shiga cikin jikinta.  RanΖ™ofowa yayi haΙ—e da yi mata rumfa da Ζ™irjinsa,  baikai gayin romancing Ι—inta ba, amma gaba Ι—aya kallon daya keyi mata, ya gama kashe mata jiki,  ahankali ta lumshe idanunta, sosai Ζ™amshinsa keyi mata daΙ—i.   Kansa ya cusa acikin Ζ™irjinta dake tashin Ζ™amshi, ahankali yake goga mata lallausan sajensa akan breast Ι—inta.  Sake lumshe idanunta tayi, haΙ—e da sanya hanunta, a bayansa ahankali take shafawa, tana fidda wani irin numfashi.  Slowly yake kissing Ι—inta, tundaga Ζ™irjinta har zuwa kan bakinta, da kaΙ—an kaΙ—an yake tsotson pink lips Ι—inta, yana me lumshe idanunsa, da suka koma kalar ja,     baitaΙ“a mata irin wannan kissing Ι—in me rikita tunani ba sai yau, sosai takejinta cikin wani irin yanayi na musamman,  ajiyar zuciya me Ζ™arfi ta sauΖ™e, haΙ—e da buΙ—e bakinta,  kamar zatace dashi wani abu, amma kuma babu wata kalma da zata iya fitowa daga bakinta, saboda gaba Ι—aya ya shiΙ—ar da ita. Ya ruΙ—ata da salonsa,   harshensa ya tura acikin bakinta, haΙ—e da soma kaΙ—a mata shi acikin bakin nata.  Hanunsa yasanya ya zare Ζ΄ar rigan dake jikinta.  Ζ™asa yayi da kansa yana sucking Ι—inta,  kamar kullum daya fara sucking Ι—inta take saka masa kuka ta kuma shiΙ—e masa, yau ma hakance takasance, ganin numfashinta nashirin Ζ™wace mata ne, yasa ta janye kansa, haΙ—e da mirginawa gefe tana sauΖ™e wani irin numfashi,  ji take kanta na juya mata,  ga wani irin sha’awarsa dake fusgarta. Sake kwanciya yayi a bayanta, haΙ—e da cusa kansa cikin tulin gashin kanta.   Numfashi shima yake fitarwa akai akai, burinsa Ι—aya shine yaji wannan Ι—umin nata, me zautar masa da tunani.

Juyowa tayi gareshi haΙ—e da hayewa saman Ζ™irjinsa, hanu tasanya tana shafa gashin kansa, yayinda taΙ—aura bakinta akan Ζ™irjinsa, tana sakar masa wasu irin kiss dake tada masa da tsikar jiki,    lumshe idanunsa yayi yana me karΙ“an saΖ™onta, dama akunne yake matuΖ™a, gashi yanzu tana Ζ™ara kunnasa.   Ganin da yayi cewa zata haukatasa da yawa ne, yasanya sa dawo da ita Ζ™asansa yazamana shine a samanta.   Kallon da yayi mata ne ya Ζ™ara kashe mata jiki,  haΙ—e bakinsu yayi waje Ι—aya,  lokacin da Ι—umin jikinta ya ratsashi saida ya sauΖ™e wata ajiyar zuciya me Ζ™arfin gaske, take kuma ya fara manta awacce duniya yake, atare suke kissing Ι—in juna, cike da wani irin so,   sun matuΖ™ar zautuwa, kowannensu yatafi wata duniyar ta daban, amma duk da haka bakinsu yana cikin na juna……….

STORY CONTINUES BELOW

*** *** ***

Bayan Wata Biyu.?

Yanzu cikinta yana wata tara harda sati biyu, amma haihuwa shiru, zuwa yanzu ko tashi bata iyawa sai antaimaka mata, cikinta yayi wani irin girma, hakannema yasa Hajiya da kanta taje ta Ι—aukota, ta dawo gidanta da zama, bahaka Dr.Sadeeq yasoba amma babu yanda ya iya, dolensa ya haΖ™ura, kuma sosae yake kewar matartasa, wai donma yanasamu suna keΙ“ewa, idan dare tayi, har hotel suke zuwa.

Kwance take akan doguwar kujeran dake falon Hajiya,  green Apple ne riΖ™e a hanunta, ita bata ciba ita bata ajiye ba.  Tun daran jiya take fama da wani irin ciwon mara dana baya,  amma babu wanda ta faΙ—awa, gudun kada su tashi hankalinsu,  yanzu kam abun yasoma fin Ζ™arfinta, don ciwon kamar zai zautar da ita haka takeji, zamowa tayi Ζ™asa daga kan kujeran da take,  haΙ—e da durΖ™ushewa aΖ™asan tiles, hanu tasanya takama gefe da gefen cikinta, tare da sakin wani Ζ™aran azaba, lokaci guda taji wani irin ciwo  yataso mata gadan gadan.  Fitowar Hajiya daga Ι—aki, yayi daidai da shigowan Doctor Sadeeq cikin falon.  Dukansu da sauri sukayi kanta. 

“Innalillahi Hajiya, dama bata da lafiya ne?” Dr. Yatambayi Hajiya a  matuΖ™ar ruΙ—e.  Kafun Hajiya takai ga cewa wani abu Zahrah ta fashe da kuka haΙ—e da faΙ—awa jikin Doctor ta Ζ™anΖ™ameshi Ζ™am,  gaba Ι—aya ya ruΙ—e yarasa inda zai tsoma kansa, shima rungumeta yayi tuni idanunsa sun kawo Ζ™walla.

Hajiya ce tafito daga Ι—akin Zahrah’n hanunta Ι—auke da Hijab, ita tasawa Zahrah’n hijab Ι—in, kana tace doctor Sadeeq Ι—in ya Ι—auki Zahrah su wuce asibiti.  Jikinsa na rawa haka ya Ι—aga ta ca Ι—ak yasata a mota, Hajiya tashiga motar ta riΖ™eta, shikuma yaja suka nufi asibiti, gudu yake dasu kamar zaitashi sama, kanaganinsa kaga wanda baya cikin hayyacinsa,  bayaso wani abu na wahala yasamu matarsa ko kaΙ—an, da ace zai yiwu to daya karΙ“a mata naΖ™udan, don baya Ζ™aunar ganinta cikin wahala da azaba har haka.

Suna shiga cikin asibitin direct aka wuce da Zahrah labour room.  Wasu likitoti ne guda uku mata akanta,  babu abun da take sai salati da cije baki, ita kaΙ—ai tasan me takeji,  ganin bazai iya jurewa ba, yasanya sa faΙ—awa cikin labour room Ι—in, dayake dama asibitinsu ya kawota, yanazuwa gaban gadon, ya kama hanunta,  buΙ—e wahalallun idanunta tayi ta kalleshi,  atare wasu hawaye masu zafi suka fito daga cikin idanunsu,  matsanancin tausayinta yakeji, fiye da tunanin me tunani,  Hanunsa dake saman nata, takama ta matse, haΙ—e da girgiza masa kanta, cikin wata irin murya me Ι—auke da tsananin ciwo tace.

“Kayafemin idan na mutu dan Allah!”

Kai ya girgiza mata da sauri haΙ—e da cewa. “Bazaki mutu ba Zahrah, zamu rayudake acikin duniyarnan insha Allah, zaki raini abun da zaki haifa Ι—a hanunki, insha Allah!!” cike da tsananin rauni ya faΙ—i haka, sosai zuciyarsa ta karye,  bata sake ce dashi komaiba, kawai ta Ι—auke idanunta akansa, cigaba tayi da nishi haΙ—e da karanto addu’a, Doctor na riΖ™e da hanunta, yana tofa mata addu’a, haΙ—e da shafa kanta, Ζ™walla ne kawai suke fita daga idanunsa. Wani irin yunΖ™uri haΙ—e da nishi tayi sai ga kukan jariri ya cika Ι—akin.  LaΖ™was haka tayi akan gadon, lokaci guda komai nata ya tsaya, motsi da numfashinta, duk suka Ι—auke, kumatunta yasoma bubbugawa yana Ζ™iran sunanta, hawaye kuwa akan fuskarsa wani na koran wani kamar an buΙ—e famfo.

Wata daga cikin likitoti matanne ta Ι—auki yaron, takaishi wajen da ake aje jariri, kallon Dr.Sadeeq da yake hawaye tayi, tace

“Haba Sir, wannan fa ba wani abun damuwa bane kasani, yanzu zata farfaΙ—o insha Allah”

Hankalinsa ma baya wajenta balle yaji me take cewa,  shigaba Ι—aya ma basirarsa toshewa tayi, amaimakon yabata taimakon dayasan zai dawo da ita hayyacinta, saiya tsaya yana Ζ™iran sunanta, yana kuma jijjigata.   Likitance tashiga bata taimako,  wani Ζ™aΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya Zahrah ta sauΖ™e,  alaman ta farfaΙ—o, bayan kamar mintuna uku ta shiga buΙ—e idanunta a hankali,  dashi tafara tozali ya tusata a gaba, sai kuka yake, hanunta ta miΖ™a masa, da sauri yataho yakama hanun,  kissing Ι—inta yayi akan goshinta, haΙ—e da  rungumeta, atare suka shiga sauΖ™e ajiyar zuciya akai akai, sun kusan 8 minute ahaka, kafun taΙ—an janye jikinta daga nasa, murya a sanyaye tace “Ina Hajiya?”  “Tana waje” yabata amasa a taΖ™aice, yana me binta da kallo me Ι—auke da tsananin Ζ™auna, haΙ—e da tausayi me ruguza zuciya.  1

STORY CONTINUES BELOW

Wata daga cikin likitotinne tace “Sir yakamata a kimtsata, sai mukaita Ι—akin hutu”

Juyowa yayi ya kalli likitan haΙ—e da cewa.  “Babu buΖ™atar Ι—aya daga cikinku sai ta kimtsata, nida kaina zan kimtsa abata”

“Sir tana buΖ™atar Ι—inkifa, saboda ta Ζ™aru” likitan takuma faΙ—an haka.

Da sauri ya kalli Zahrah, take hawayen dake cike acikin idanunsa, suka gangaro kan Ζ™uncinsa, wani sabon tausayinta ne yasake kamasa, “Ina sam bazai iya mata Ι—inki ba, bazai taΙ“a koda kwatantawa bane ma, dakansa da hanunsa ya huda Zahrah’nsa? wannan abun bamai yiwuwa bane” yafaΙ—i haka acikin ransa. Baice da likitotin komai ba, sai matsawa dayayi kusa da Zahrah, yasake sumbatarta akaro na biyu, wata allura ya Ι—auko yayi mata a hanunta, tayanda yasan bazataji zafiba,   kallonta yayi still hawaye yake, daΖ™yar ya iya jan Ζ™afansa yafice daga cikin Ι—akin, abun mamaki kota kan jaririn baibiba, tun dama yafaΙ—o dunia bai kulasaba, yanata rabin ransa Zahrah. 

Likitotinnan ne suka Ι—inke ta tsab, saidai bata wani ji zafi sosai ba, domin alluran da Doctor yayi mata, allurace me Ζ™arfi dake hana jin zafi, suna gama Ι—inketa, wata acikin likitotin takamata suka wuce bathroom,  likitance ta haΙ—a mata ruwa tayi wanka, tana fitowa likitan tabata wata riga wacce takarΙ“o awajen Hajiya tasanya, miΖ™o mata jaririn likitan tayi, hanunta na rawa haka ta karΙ“i jaririn Ι—an nata, tana karΙ“ansa taji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarta, fuskar Dr.Sadeeq ta kalla sak akan fuskar yaron nata, lokaci Ι—aya taji wani irin so da Ζ™aunarsa sun cika mata zuciya, tana fitowa acikin labour room Ι—in, Hajiya da Dr.Sadeeq sukayo kanta, daga ita har jaririn Hajiya ta haΙ—asu ta rungume, sai ga Ζ™wallan farinciki na zuba daga idon Hajiya, amsar yaron tayi daga hanun Zahrah haΙ—e da sanya sa acikin Ζ™irjinsa ta rungumesa, sosai takejin Ζ™aunar jikan nata, musamman dataga yana kama da ubansa, sai dai duk da haka akwai kamannin Zahrah a tattare dashi.    Dr.Sadeeq kuwa ko kunyan Hajiya dake tsaye baiyiba yaje ya rungume matarsa, kyakkyawan kiss ya sauΖ™e mata akan Ζ™uncinta, haΙ—e da Ι—aura kansa akan kafaΙ—anta.  

Saurin tureshi tayi daga jikinta, ta haye gado ta kwanta, tana sauΖ™e numfashi, kawar da kanta gefe tayi, wasu irin siraran hawayene suka gangaro daga cikin idanunta, ita kaΙ—ai tasan menene yasata wannan hawayen.  Mintuna kaΙ—an bacci Ι“arawo ya Ι—auketa, dagani kuma kasan tanajin daΙ—in baccin.

Alokacin da Doctor yakarΙ“i jaririn ahanun Hajiya, kafesa yayi da manyan idanunsa, wani irin Ζ™aunar Ι—an nasa ne ke fusgarsa, sosai yaron ke kama dashi, rungume Ι—an yayi acikin Ζ™irjinsa, sai kawai ga hawaye nafita daga cikin idanunsa, kallonsa ya maida ga Zahrah wacce take bacci,  wutar sonta ne ke Ζ™ara ruruwa acikin zuciyarsa, lallai Zahrah tana da babban matsayi agareshi, ta basa farinciki me Ι—orewa, tahaifa masa Ι—a, tayi masa komai a duniyarnan, baisan damene zai saka mata ba.      

Hajiya dakanta ta Ζ™ira Inna tasanar mata maganan haihuwan, dama tuni Aunty Raliya kam ta tsofe a asibitin,  koda su Inna sukaji cewa Zahrah ta haihu, ba Ζ™aramin farinciki sukayi ba, sunji daΙ—i sunyi murna sosai,  ita da Baffa duka suka rankayo zuwa asibitin. 

Ba ita tafarkaba sai bayan azahar,   bathroom Ι—in Ι—akin da take ciki ta shiga, haΙ—e da sake tsabtace jikinta, tana fitowa kuwa tasamu Doctor ya karΙ“o musu takardan sallama.  Gaba Ι—aya likitotin asibitin babu wanda baitaya Dr.Sadeeq murnan samun  Ζ™aruwan da yayi ba,  har Ι—aki suke zuwa su duba Zahrah, sukuma tayasu murna.

Hanyar da Hajiya taga  ya miΖ™a ne yasanyata cewa.

“Wai ina zaka damu ne Sadeeq?”

Da compidence Ι—insa ya juyo gareta haΙ—e da cewa. “Gidana mana Hajiya”

“Gidanka? to ba gidanka zamuba, gidana zamuyi, hauka kake  na Ι—auki yarinya da Ι—anyen jiki, na baka? wama zai tsaya ya kula da ita? maza juya akalar motarnan” Hajiya tafaΙ—i haka babu alamar wasa akan fuskarta.

Sam bahaka yasoba, amma babu yanda zaiyi, shikenan shi baza abarsa yaji Ι—umin matarsa dana Ι—ansaba, haka yata Ζ™unΖ™uni acikin ransa shi kaΙ—ai, har suka isa gidan Hajiya.

1

Abinci mai rai da lafiya Hajiya ta kawowa Zahrah, ga kuma gasashshen nama,  bayan taci abincin Hajiya dakanta, tasakeyi mata wanka.

Zama tayi agaban mirror tashafe jikinta da manta me daΙ—in Ζ™amshi,  powder tashafa afuskarta, bata tsaya nanba harda janbaki tashafawa laΙ“Ι“anta, ga kuma kwalli da ta sanyawa cikin idanunta, mascara ta Ι—auko ta zizira akan eye lashes Ι—inta, take fuskarta taΖ™arayin kyau. Wani riga da sket na material me tsada tasanya ajikinta, take takoma Ζ΄ar baby  kamar yanda take da, dogon gashinta ta kanannaΙ—e a bayanta, haΙ—e da hayewa gado, zataci gaba da bacci,   miΖ™o mata yaron Inna tayi haΙ—e da cewa “Wani kwanciya kuma zakiyi bayan baki bawa yaron nono ba?”1

ShagwaΙ“e fuska Zahrah tayi haΙ—e da turo Ι—an Ζ™aramin bakinta gaba,  da Ζ™yar ta iya ciro nonon nata ta kai bakin yaron,  yana kamawa ta runtse idanunta da Ζ™arfi, saboda wani zafi da taji, haka dai ta Ι—an daure, shikuwa yaron sai zuΖ™eta yake,  gajiya tayi dajin zafin ta cire nonon abakinsa, kwantar dashi tayi, itama kana ta kwanta agefensa, baccin gajiya ne ya kuma Ι—aukarta…

Idan dai hartaji sauΖ™an numfashinsa akan wuyanta, to yazame mata dole ne farkawa daga baccin da take, yanzu ma sauΖ™an numfashin nasa taji adai dai saitin kunnenta, a hankali take ware idanunta harta sauΖ™esu akansa. Murmushi yasakar mata haΙ—e da Ι—aura kansa akan Ζ™irjinta.

“INA SONKI!!!” yafaΙ—a murya a sanyaye….TafaΙ—a tana me lumshe idanunta. Iskan bakinsa ya hura mata akan fuskarta, haΙ—e da sake rungumeta, Ι—ayan hanunsa yasanya ya shafi kan jaririn nasa, dake ta bacci. Murmushi Zahrah tayi ganin yanda Dr.Sadeeq ya kafe yaron nasa da ido. Hajiya da Inna ne suka shigo cikin Ι—akin atare, da sauri Zahrah ta janye jikinta daga na doctor, shima a kunyace ya sauΖ™a daga kan gadon yana sosa kai.+

“Hmmm Allah yashirya, Inna kina gani ko, wai da ahakan yakeso na basa ita” inji cewar Hajiya.1

Murmushi kawai Inna tayi batace komai ba. ( Su Inna anzama nitsaljin?) Kallon Doctor Hajiya tayi haΙ—e da cewa “Zo muje inason magana dakai” babu musu yabi bayanta suka fice daga cikin Ι—akin.

Zama tayi akan kujera haΙ—e da maida hankalinta garesa.

“Me dame kake shiryawa sunan nanne? sannan kuma da wani suna kayiwa yaron huΙ—u ba?”

Murmushi ya Ι—anyi haΙ—e da cewa “Ai nagama shirina tuntuni Hajiya, dama lokaci kawai muke jira, sannan kuma dama tuntuni sunan babanta nake son sawa yaron, dashi kuma nayi masa huΙ—u ba”

Hajiya tace “Masha Allah, To Allah Ubangiji ya rayasa, hakan da kayi kuma ka kyauta, tashi kaje dama maganan da zamuyi kenan”

MiΖ™ewa yayi haΙ—e da yi mata sallama yafice daga cikin falon.

Lokacin da Husnah tazo ganin Baby kusan haukacewa tayi, sai santin yaron take wai yayi mata kyau sosai, komai nasa irin na babansa, ga idanunsa kyawawa, itadai Zahrah dariyanta kawai take, saboda itama Husnan tana Ι—auke da Ι—an Ζ™aramin ciki.

Akwatuna guda biyu Dr.Sadeeq ya kawo wa Zahrah, Ι—aya nata Ι—aya na baby’nsa wai kayan barka, kayane masu kyau da tsadar gaske sosai ya kashe kuΙ—i, wai ahakanma wasu kayan nanan zuwa.

Kulawa Zahrah take samu a wajen Hajiya sosai, idan kaganta ma kamar ba itace ta haihu ba, sosai jikinta ya murje, tasakeyin fresh, hasken fatarta ma sosai ya Ζ™aru, komai nata ya cika, taΖ™ara kyau akan nada, shikansa Dr.Sadeeq idan yaganta, ko son Ι—auke idanunsa akanta bayayi, saboda yanzu tasake zama wata mace ta musamman, duk inda ta zauna kuwa Ζ™amshi take rabawa.

Ranar suna yaro yaci sunan baban Zahrah wato Adam, za’ana Ζ™iransa da (Asad) lokacin da labarin sunan da aka sawa yaro yazo kunnen Zahrah sosai taji daΙ—i, wani irin farinciki taji acikin ranta, girman Doctor kuwa ya Ζ™aru acikin idanunta, ta tabbatar cewa shiΙ—in mai so da Ζ™aunarta ne.

Da sassafe meyi mata meckup tazo ta tsantsara mata ado, sosai fuskarta tasha kwalliya, wani haΙ—aΙ—Ι—en lace orange and milk colour tasanya ajikinta, wanda yaji Ι—inkin riga da sket irin 12 piecess Ι—in nan, sosai kayan sukayi mata kyau, domin sunja kuΙ—i wajen sayansu da Ι—inkasu, kowa yaga Zahrah da babynta saiyace masha Allah. Saboda sunsha kyau sosai. Hidima sosai akayi tundaga kan abinci da abun sha, har izuwa abubuwan da za’a rabawa baΖ™i, akwati guda biyu Hajiya tayiwa Zahrah da Ι—anta, haka Baffa ma akwati yayi mata Inna ma zagewa tayi tayiwa Zahrah akwati shaΖ™e da kaya, Auntie Raliya ma akwati ta mata, sosai Zahrah tasha kaya, har rasa inda zata sa kayan tayi, ana cikin haka saiga kayan Dr.Sadeeq sun iso, akwatuna huΙ—u, biyu natane shaΖ™e da kaya, sauran biyun kuwa na yarontane, bata gama mamakin irin dukiyar da Dr.Sadeeq yakashe mata ba, saiga Aunty Raliya tana rangaΙ—a guΙ—a, hanunta riΖ™e da key, danΖ™awa Zahrah key Ι—in tayi ahanunta, haΙ—e da cewa “Ungo amsa kyautace ta musamman daga mijinki, ya baki kyautar gidansa dake cikin asokoro” mamakine ya kusan kashe Zahrah2

STORY CONTINUES BELOW

“Gida kuma Aunty?” ta tambayi aunty Raliya don tayi tunanin ko kunnuwanta ne basu jiye mata da kyau ba.

“Ƙwarai kuwa gida, saima kinga gidan, don gidane me tsananin kyawun gaske, yafa kashe kuΙ—i sosai wajen Ζ™awata gidan” Inji cewar Aunty Raliya.

“A’a Aunty gaskiya nikam banaso, wani irin kyautane haka? hidimar da Doctor yakeyi dani tayi yawa, daga haihuwata zuwa yau yakashe kuΙ—i yafi 3 million fa Auntie, yanzu kuma yace yabani kyautar gida suku tum, inajin tausayinsa Aunti banason nazama rauni acikin arzikinsa” Zahrah tafaΙ—i haka da iyaka gaskiyarta.

Murmushi Auntie Raliya tayi haΙ—e da sanya hanu ta dafa duka kafaΙ—un Zahrah.

“Kada ki damu Zahrah, shi Ι—infa mijinki ne, kuma kome zaimiki aduniyarnan bazai biyaki ba, kamar yanda kema bazaki iya biyansa duk abun daya miki ba, saboda haka babu wani abun damuwa don yamiki wannan kyautar, kin cancanci hakanne agareshi, don haka amshi makullin gidanki, ke dai kawai kiyi masa godiya, irin wacce ta dace” Aunty Raliya ta faΙ—i haka tana me damΖ™awa Zahrah makullin gidan ahanunta.

Kuka Zahrah ta fashe dashi tana jin Ζ™arin Ζ™aunar mijinnata na huda mata zuciya, lallai yazama dole agareta taΖ™ara Ζ™aimi wajen kyautata masa.

Yamma nayi aka haΙ—a walima me rai da lafiya, bayan malama tazo tagabatar da wa’azine akayi ciye ciye, aka kuma sha drinks, duk wanda yazo sunan kuwa babu wanda baisamu kyaututtuka ba, abun sai dai ace Alhamdulillah, kafun magriba tuni mutane sun watse, gida ya saura daga Hajiya sai Zahrah da kuma Aunty Raliya.

Wanka tasakeyi ta tsantsara ado cikin wani irin meterial me kyau da tsada, wanda yana cikin kayan da Doctor ya Ι—inka mata don fitan suna, doguwar riga akayi mata wanda ya matuΖ™ar kama jikinta sosai, dogon gashinta dayasha saloon ta kanannaΙ—e atsakiyar kanta, ba abun dake fita ajikinta sai Ζ™amshin humra dana body spray.

Zama tayi akan gado haΙ—e da Ι—aukan wayarta tashiga kan whatsapp, yaronta kuwa tuni dama yana wajen su Hajiya dake zaune a falo suna hira, Sadiya me aikin Hajiya ce tashigo cikin Ι—akin haΙ—e da sanarwa Zahrah cewa wai tayi baΖ™o yana falo.

Jitayi gabanta yaΙ—an faΙ—i, amma saita dake tace da Sadiyan tace da baΖ™on tana zuwa.

Mayafi ta Ι—auka ta yafa ajikinta, kana ta zura flat shoe Ι—inta, tafice daga cikin Ι—akin.

Su Hajiya tasamu zaune afalon, sai kuma wani, wanda bata ma taΙ“a ganin fuskarsa ba. Kafun takai ga gaishesa, shiya Ι—ago mata gaisuwa, amsawa tayi tana Ι—an murmushi, gyara tsayuwansa yayi haΙ—e da cewa..

“SaΖ™one dama akabani nakawo miki, yana waje, idan ba damuwa muje saiki gani”

Kallon tsoro tashiga yi masa, saboda batasansa ba balle tasan wanene ya aikosa.

“Badamuwa, Raliya rakata sai kuje kuga saΖ™on ko”

Hajiya tafaΙ—i haka, don ta lura da tarin tsoron daya bayyana akan fuskar Zahrah’n.

Hakan kuwa akayi tare suka fita da Aunty Raliya.

A compound Ι—in gidan suka tsaya gaban wata haΙ—aΙ—Ι—iyar mota Ζ™irar mercedes maroon colour, mutuminne ya bubbuΙ—e Ζ™ofofin motar, take kayan dake shaΖ™e acikin motar suka bayyana, Ι—an makulli ya miΖ™owa Zahrah haΙ—e da cewa

“Ranki ya daΙ—e gashi ni nacika umarnin da aka bani, wannan kyautace daga megida na, yace na ce miki Allah ya raya”2

Mamaki haΙ—e da al’ajabi ne suka kama Zahrah da Aunty Raliya.

“Kyauta daga me gidanka kuma? wayeshi to?” Zahrah tayi masa duka waΖ΄annan tambayoyin cike da son jin amsa, haΙ—i da kuma mamaki, gani take kamar mutumin baida cikakken hankali.

Murmushi kawai Ι—an aiken yayi haΙ—e da sake miΖ™o mata makullin motar yace

“Kiyi haΖ™uri bai bani damar sanar miki dashi Ι—in kowaye ba, amma yace dan Allah ki karΙ“a”

Ta buΙ—e baki zatayi magana kenan motar Dr.Sadeeq ta kutso kai cikin gidan.

Kasa cewa komai tayi har Dr.Sadeeq yafito daga cikin motarsa, ya Ζ™araso garesu, kallonsa Zahrah tayi shima kallonta yakeyi.

“Hajiya ga makullin ni zan wuce” wannan mutumin yafaΙ—i haka, yana sake miΖ™a mata Ι—an makulli.

“Ko ma waye ya aikoka, kace masa banaso, don bana buΖ™ata” tafaΙ—i haka tare da juyawa daniyar komawa inda ta fito.

“Zahrah!”

Sunanta da Dr.Sadeeq yaΖ™irane yasanyata tsayawa cak haΙ—e da juyowa tana kallonsa.

“Zoki amsa, ki kuma yi masa godiya” Dr.Sadeeq yafaΙ—i haka, yana me karantar yanayinta.

Cike da mamaki tace “Amma…”

“Banaso kice komai ki amsa kawai nace” yakatseta daga maganar da take Ζ™oΖ™arin yi.

Jiki asanyaye ta karΙ“i makullin motar.

Ciki ciki tace “Kace nagode”

“To” kawai Ι—an aiken yace kana ya juya yafice daga cikin gidan.1

“Wai meke faruwa ne, waye ya aikosa?” Aunty Raliya ta tambayi doctor, don ta lura kamar yana da masaniya akan wanda ya aiko motar da cikinta ke shaΖ™e da kaya.

Murmushi Doctor yayi haΙ—e da cewa “wani aminina ne dake zaune a Dubai, shine dana gaya masa ta haihu yayi mata wannan kyautar”

Dafe Ζ™irji Aunty Raliya tayi tare da cewa

“Lallai wannan koma wayeshi yanaji da naira, wannan motarfa zatakai 4million inma bata fi ba, ga kuma kayan dake cikinta, wanda suma kaΙ—ai sun haura 1m, me kenan yake nufi?”1

“Babu wani abun da yake nufi Aunty, haka dama shi yake kyautarsa, muje ciki ko” yaΖ™are maganar yana kallon Zahrah wacce ta daskare a wajen.

Cike da mamakin kyautar abokin Doctor Ι—in Aunty Raliya taja Ζ™afanta takoma falon Hajiya, Zahrah ma jikinta a sanyaye tabi bayanta, shima falon yanufa, yanda yaga tana tafiya asanyaye ne yasanyasa yin murmushi kawai.

Bata tsaya a falon ba direct Ι—akin dayake masauΖ™inta ta wuce, tsayawa tayi a gaban mirror zuciyarta cike da tarin tambayoyi kala kala, sam bataji zuciyarta ta aminta da kyautar nan da’akayi mata ba, kwata kwata batama yarda cewa wai abokin Doctor bane ya bata. Tana acikin tunanin, yaturo Ζ™ofar Ι—akin yashigo bakinsa Ι—auke da sallama.

Amsa masa sallaman nasa tayi haΙ—e da zuba masa idanunta, dagani kai kasan tambayoyine cike a bakinta.

takowa yayi ya Ζ™araso daf da ita, hanunsa yasanya ya jawota jikinsa, saida yashaΖ™i daddaΙ—an Ζ™amshin dake fita ajikinta, ya sauΖ™e ajiyar zuciya, kana yace.

“Kinyi kyau sosai”

Murmushi ta Ζ™aΖ™alo haΙ—e da cewa. “Nagode”

Cikinsa yashafa tare da cewa. “Yunwa nakeji sosai, nayi missing sweet cook Ι—inki, please ko zaki kawomin abinci?”

“Meyasa kake barin kanka da yunwa? kasan banaso, yanzu me zakaci na kawo ma?” tatambayeshi cike da kulawa.

“Koma me idan kika kawomin ni mai iya ci ne” yafaΙ—i haka yana me zama a bakin gado.

Harta kusa fita daga cikin Ι—akin sai kuma ta tsaya cak, haΙ—e da juyowa, idanunsu yafaΙ—a cikin na juna, domin dama shima kallonta yake.

“Waye ne yaturomin da mota? Nasan kasan ko waye, domin zuciyata tafaΙ—amin cewa, ba abokinka bane ya turo, kamar yanda kafaΙ—a a baya” tambayar da tayi masa kenan, cike da burin samun amsa agareshi.

“Baki yarda da abun dana faΙ—a ba kenan?” ya tambayeta yana me Ζ™ara tsareta da manyan idanunsa.

Murya a sanyaye tace “Kayi haΖ™uri, bawai ina nufin kamin Ζ™arya bane, kawai dai naji zuciyata ce bata gamsu da amsar da ka bayar ga Aunty Raliya ba”

Murmushi yayi haΙ—e da cewa “Zuciyarki tafaΙ—a miki gaskiya, domin kuwa ba abokina bane yaturo kamar yanda na faΙ—a a baya”

Waro idanunta tayi, duk da zuciyarta ta raya mata cewa ba abokinnasa bane, amma kuma duk da haka bata tsammaci jin haka daga bakinsa ba.

“Waye?” tatambaya murya na rawa.

“ZAID” yabata amsa ataΖ™aice…ZAID!” ta maimaita sunan abakinta cike da tsananin mamaki.+

Yanda yaga jikinta na Ι“ari shine abun daya basa mamaki, zallan tsoro ya hango kwance akan fuskarta, yayinda cikin idanunta kuwa, suka bayyana soyayyar dake kwance acikinsu, wato soyayyar ZAID, shi yasani ba tun yauba, bakuma zai yaudari kansa ba, yasani Ζ™warai Zahrah na son Zaid, so ba irin na wasaba, so matsananci, amma kuma babu yanda zaiyi, dayana da iko to daya cire mata son Zaid acikin zuciyarta, amma wannan banasa bane, na Allah Ne, yasan Zahrah tana sonsa, amma soyayyar da takewa Zaid ta dabance, da ace zai iya, to daya danne zuciyarsa, ya miΖ™ata ga Zaid, yasan hakan zai samarmusu da farinciki, ita da Zaid, amma kuma yasan koda yayi hakan to ba mafita bane, domin ayanzu yasan dole idan baya tare da Zahrah tayi kewarsa, yana sane da cewa yakafa mata tutar son sa, wanda bazata ankara da hakan ba, har sai randa yazama baya tare da’ita, baya fatan wata Ζ™addara ta rabasu, amma yasani ko mai daren daΙ—ewa sai sun rabu, saboda akwai mutuwa, koshi ko ita, watarana Ι—aya dole zai bar Ι—aya, yau idan baya raye, baya fata Zahrah ta auri wani namiji idan ba Zaid ba, tunaninsa yayi nisa, baisan da cewa ta Ζ™araso inda yake ba, saida yaga ta zube a gabansa, tana kuka, cikin muryar kukan takecewa.

“Kada kamin haka doctor, wallahi ni banason duk wata kyauta da zatafito daga garesa, namantasa acikin rayuwata, banaso kuma nasake tunasa, kamayar masa da kyautarsa, bana buΖ™ata farincikin da kake bani kaΙ—ai ya isheni”

Tunda tafara maganan yake kallonta, ajiyar zuciya yayi, haΙ—e da kamo hannayenta, cikin murya me sanyi yace. “Kinsani bakyau maida hanun kyauta baya, meyasa to zakiyi haka? mekike tunani akan Zaid?” Ι—an dakatawa da maganar yayi, tare dayin wani murmushi, kana ya miΖ™e tsaye, daga zaunen da yake.

“Kyautace kawai ya miki, ai atunanina hakan ba wai yana nufin wani abubane, bazan tilasta miki ba, amma nasan abundake cikin zuciyarki, don gashi har a idanunki sun nuna, so ba Ζ™arya bane Zahrah, haka kuma ba laifi bane, don zuciya na dakon so, wannan ma wata Ζ™addarace, wanda babu wani wanda ya isa ya kauce mata” yanakai Ζ™arshen zancen nasa yanufi hanyar fita daga Ι—akin.

Da sauri taje ta faΙ—a jikinsa, kuka take sosai, durΖ™usawa tayi haΙ—e da zube guiwowinta a Ζ™asa, kana ta riΖ™e rigarsa, kanta tashiga girgizawa, tana kuka tace. “A da na sosa fiye da yanda naso kaina, amma ayanzu baya acikin zuciyata kamar yanda kake tunani, Inasonka da duka zuciyata, bana fatan wata Ζ™addara tazo wacce zata rabani dakai, kabani farinciki, kajiyar dani daΙ—i, kashayar dani zuman soyayyarka, bazan iya watsa maka Ζ™asa idanunka ba, kai mijinane wanda bayan kai bani da wani tamkarka, nasan kai Ι—in me sonane, amma meyasa kayi haka? mai yasa kai da kanka, zaka amince da na karΙ“i kyautar wanda yazama silar rugujewar rayuwata?”

DurΖ™usawa yayi agabanta, haΙ—e da sanya hanunsa ya share mata hawayen dake gudu akan fuskarta, cike da kulawa yace. “Banason kukanki Zahrah, keΙ—in wata babban jigo kuma mahaΙ—i ne acikin rayuwata, nasan Zaid ya cutar da rayuwarki, amma kuma hakan bazai hana ki amshi kyautarsa ba, ayanzu kowa yasan cewa ke matatace, saboda haka Zaid bazaiyi miki kyauta da wata manufa ba, kuma kafun ya miki kyautar saida ya tambayi amincewata tukunna, nakuma amince masa, nayarda da Zaid Zahrah, nasan idan duka mutanen duniya zasu taru su cutar dake, to Zaid bazaiyi hakan ba, haka kuma idan ni zan iya cutar dake, to ina tabbatar miki idan Zaid yasan da hakan, to bazai bari na cutar dake ba, Zaid Ι—in da kikasani ada bashine wanda yake a yanzu ba, kada kiyi tunanin wai ko zanji haushi akan kyautar da Zaid yayi miki, niba jahili bane Zahrah, haka kuma halina ya banbanta da na wasu mazan, ni mutum ne me saurin fahimta, sannan kuma abune mawuyaci nayiwa wani na mummunan zato, agurin wasu mazan, hakan zai iya zama matsala, amma a wajena hakan ba komai bane, tunda nasan cewa keΙ—in tawace ni kaΙ—ai, bakuma wai don bana kishinki bane yasa hakan tafaru ba a’a, ni kalan nawa kishin ba irin na wasu bane, inakishinki sosai, sai dai kuma kome acikin nutsuwa nakeyinsa, ke kinsan inasonki ina kuma kishinki ” yaΖ™are maganar yana me lakace mata dogon hancinta.

STORY CONTINUES BELOW

Kukane yakuma Ζ™wace mata sai kawai tafaΙ—a jikinsa, ta rungumesa Ζ™am, shima rungumeta yayi yana shafa bayanta ahankali, haΙ—e da hura mata iskan bakinsa, acikin kunnenta.

Saida tayi kukanta sosai, kafun ta soma sauΖ™e ajiyar zuciya, cikin murya me sanyi tace.

“Kai na da banne Mijina, irinka basu da yawa acikin duniya, haΖ™iΖ™a nafi kowacce mace sa’a dana sameka, dakai kaΙ—ai zan rayu har izuwa mutuwa ta, kaima ka rayu dani ni kaΙ—ai kaji, bazan iya jure ganinka da wata mace ba bayanni, Ina maka son da bansan iyakarsa ba!”

Murmushinsa dake Ζ™ara masa kyau yayi, haΙ—e da sanya iskan bakinsa ya hura mata fuska.

“Dake kaΙ—ai Zan rayu Zahrah na, ni nakine ke kaΙ—ai, amma idan kina kukan nan fa, dole zan Ι—an yi Ζ™asa da idanuna, na hango wata, saina kawota ko wanke wanke ne tanayi mana ko, idan dare yayi kuma sai ina raba muku kwana ko…”

Bata bari yakai Ζ™arshen zancen nasa ba, ta muntsine sa aciki, saida yasaki wata Ζ΄ar Ζ™aramar Ζ™ara, cike da shagwaΙ“a tace “Wallahi nidai babu ruwana dakai, idan dai har kace zakamin kishiya!”

Dariya yayi sosai haΙ—e da cusa kansa acikin Ζ™irjinta. “Ni na isa ma nayiwa Ζ΄ar sakalalliyar matata kishiya, amma bandai saniba wataΖ™ila idan naga kin tsofe na miki!” yanzuma cikin zolaya yayi maganar.

Hannayenta tasanya acikin gashin kansa, tashiga ya mutsawa, hadda kai masa cizo a wuyansa. Sai da tayi masa buji buji da kayan jikinsa kafun ta Ζ™yalesa, gashin kansa ma gaba Ι—aya ta hargitsa masa shi. Koda ta kawo masa abinci tare sukaci, yana kwance ajikinta itakuma tana bashi abincin abaki, ahaka har ya Ζ™oshi.

Kallonta yayi da idanunsa, dake tsumata kana yace “Namatsu abani ke Baby na, wallahi ina kewar Ι—umin ki sosai, amma Hajiya gaba Ι—aya ta kanenaye min ke, waidole saikinyi arba’in, Babyna kice tabarmu mu koma gidanmu kinji!” cikin yanayi na shagawaΙ“a ya faΙ—i haka.

Murmushi Zahrah tayi, haΙ—e da sanya hanu ta shafi kumatun sa, cike da Ζ™aunarsa tace “Kayi haΖ™uri Hubby, nima ina kewar sucking Ι—inka, kuma ai bawai bazan dawo bane zan dawo fa” tafaΙ—i hakane don kawai ta kwantar masa da hankali.

Ya buΙ—e baki zaiyi magana kenan muryar Hajiya ta karaΙ—e kunnuwansu, inda take cewa.

“To iyayen rashin kunya, saika tashi katafi dare na Ζ™arayi, ke kuma miji daΙ—i, ga yaronki nan, abincinsa yakeso ki basa.” kunyar Hajiya ne yakama Zahrah, haka ta amshi yaron kanta a Ζ™asa.

Doctor kuwa turawa Hajiya baki yayi, haΙ—e da cewa “Hajiya zantafi, amma kiΙ—anyi haΖ™uri ba yanzu ba mana”

Baki Hajiya ta sake tana kallonsa. “Sannu marar ta ido, wallahi saika tafi yanzu kuwa” Hajiya tafaΙ—i haka tana me kama hanunsa, haka yanaji yana gani ta fitar dashi daga Ι—akin, Zahrah kam dariya taketa yi masa. Bayan ta shayar da yaron natane, tashiga toilet tayi wanka, doguwar rigan bacci tasanya, kana ta Ι—auko diary’nta, rubutu tayi aciki, ta mayar dashi ma’ajinsa. Kwanciya tayi luf akan gado, cike da tunani kala kala bacci ya Ι—auketa….

*** *** ***

Yau kwanansu 50 cif cif agidan Hajiya, sunΖ™ara kwanaki 10 akan kwanakin gama wankansu, idan kaga Zahrah bazakace ita bace, sosai taΖ™ara cika da kyau, fatarta ta Ζ™ara haske, komai nata yasake cika, gwanin sha’awa, yau ne zata koma gidanta, tuni Dr.Sadeeq ya sanja mata kayan furnitures Ι—inta, komai yasanya mata sabo, Hajiya kuwa tun tuni taketa Ι—irka mata magunguna, haka Aunty Raliya ma ta dage sai bata wasu magunguna masu Ζ™arfi take, ita kuwa sha take abunta, wanda taji yanada bauri ne kawai take ajiyewa bata sha.

Wanka ta tsantsara cikin wata jar atamfa Super Exclusive, wacce taji Ι—inkin riga da sket, sosai kayan ya amshi jikinta, zama tayi da kanta, ta tsantsarawa fuskarta kwalliya, sai gashi kuwa kyawunta ya Ζ™ara bayyana, dogon gashinta dayasha gyara ta tubke da ribbon haΙ—e da kafa Ι—aurin Ι—an kwalinta me kyau, wani red Ι—in takalmi tasanya aΖ™afanta me tsinin gaske, Ι—an Ζ™aramin mayafi ja ta Ι—auka ta rufe jikinta dashi, babu abun dake fita ajikinta, sai daddaΙ—an Ζ™amshi.

STORY CONTINUES BELOW

Yana tsaye ajikin motarsa dake fake a compound Ι—in gidan, yaga fitowarta, kusan suman tsaye yayi. “Tabbas Zahrah me kyauce, tahaΙ—u tako ina, kullum Ζ™ara kyau da cika take, lallai kuwa da yayi saken barin Zahrah, tabbas da yazama soko, marar rabo, samun mace kamar Zahrah, babban sa’ane daya samu a rayuwarsa” yafaΙ—i haka acikin zuciyarsa, yana hangame da baki wajen kallonta, baisan ma taΖ™araso garesa ba, saida yaji ni’imtaccen Ζ™amshinta na ratsa cikin hancinsa.

Murmushinta me kyau tayi masa haΙ—e da kashe masa idanunta Ι—aya. “Ya dai kwalliyar tayi maka ne” tafaΙ—i haka tana me juya masa bayanta. Alaman yaganta da kyau.

Yawu ya haΙ—iye, alokacin da idanunsa suka sauΖ™a akan hips Ι—inta, baigama dawowa hayyacinsa ba, yakuma jefa idanunsa akan Ζ™irjinta, jikinsa na rawa ya jawota ya rungumeta.

Wani irin ajiyar zuciya suka sauΖ™e atare.

“I really Miss you Babyy!!” yafaΙ—i haka akasalance.

“Miss you too dear!” itama ta mayar masa da amsa cikin muryar raΙ—a.

Hajiya dake kallonsu ta window tasaki murmushi haΙ—e da komawa cikin falonta ta zauna, aranta tanayi musu fatan shiriya.

Saida suka biya ta JABI lAKE sukayi sayayya tukun kafun daga nan suka wuce gida.

Wanka ta sakeyi ta shirya kanta cikin wata irin fitinanniyar sleeping gown, wacce ta bayyana komai na surarta bata Ι“oye komai ba, rigar doguwace har kusan Ζ™afa, amma kuma duk da haka itaΙ—in kamar babu take, kasancewarta shara shara. dogon gashinta ta sake a bayanta, haΙ—e da shafe jikinta da shu’umar Humra, wani sweet Lip Gloss tashafa akan leΙ“enta.

Yana zaune a falo yana danna laptop Ι—insa, Ζ™amshinta ne yafara kawo masa ziyara, lokacin daya sauΖ™e idanunsa, akanta sai da yaji wani irin shock ajikinsa, da sauri ya miΖ™e ya Ζ™arasa gareta. buΙ—e hannayensa yayi daniyar rungumeta, da sauri ta matsa gefe, tanayi masa dariya, haΙ—e da yin wata irin tsayuwa, wacce takusa zautar dashi.

Lumshe idanunsa yayi tare da sanya hanunsa ya jawota jikinsa. Ƙam ya rungumeta, sai gashi yana sauΖ™e ajiyar zuciya akai akai. Kallon juna suka shiga yi idanun ko wannensu Ι—auke da tsananin sha’awar Ι—an uwansa. Jikinsa na rawa ya kama lip Ι—inta na Ζ™asa, yana tsotsa ahankali, jiyake kamar yanashan honey. da kanta ta zame rigar dake jikinta, ta faΙ—i Ζ™asa, take surarta ya bayyana, hmmm ba yau yafara ganinta ba, amma kuma ya zautu Ζ™warai daganin surar jikinta, jiyake kamar ma baitaΙ“a kusantarta ba, sosai yayi missing Ι—inta. Jikinsa na rawa ya Ι—auketa suka wuce bedroom, tuni dama Asad yayi bacci, dama shi haka yake sam baida Ζ™iriniya, daya Ζ™oshi sai bacci, bakuma zai tashiba sai dai idan yanajin yunwa.

A yau Ι—in ne suka sake tabbatar da cewa sunyi kewar juna, musamman ma Doctor Sadeeq da kusan cinyeta ne kawai baiyi ba, gaba Ι—aya ya zauce, ya susuce, wasu maganganu yake wanda ita kanta batasan me yake cewa ba, saboda sun lula wata duniya ta musamman, wacce sukayi nisa acikinta basaji basa gani, kansu kawai suka sani. Aranan nan wata zuma suka shayar da junansu, wanda bazasu taΙ“a mantawa ba. Wannan ranan takasance rana ta biyu masu muhimmanci a garesu.1

*** *** ***

Bayan wata 6……..

America

Zufa ne keta ketowa ta goshinsa, gaba Ι—aya baya cikin nutsuwarsa, kai komo yaketayi agaban labour room Ι—in sama da 1 hour kenan yana abu Ι—aya, jiyake kamar yasanya hanu akansa yaita Ζ™wala ihu. Ɗaya daga cikin Nurse Ι—in dake kanta na fitowa ya nufi wajenta, da sauri idanunsa sunkaΙ—a sunyi jajur dasu. Murmushi Nurse Ι—in tayi masa haΙ—e da cewa “Ina tayaka murna, matarka ta haihu, kasamu baby girl” wani irin sanyin daΙ—i yaji acikin Ζ™irjinsa, baisan lokacin dayayi sujja don nuna godiyarsa ga Allah ba.1

Ana kaita Ι—akin hutu, wata nurse tace yashigo ya karΙ“i babynsa, lokacin daya sanya hannayensa ya amshi babyn, wani irin kukane ya Ζ™wace masa, alokacin da idanunsa suka sauΖ™a akan kyakkyawar fuskarta kuwa, bugun zuciyarsa ne ya Ζ™aru, saboda kokaΙ—an yarinyar bata kama da mahaifiyarta, durΖ™ushewa yayi aΖ™asa, riΖ™e da yarinyar tasa yana kuka, hakan kuwa sosai yabawa likitotin mamaki.

Bakomaine yasa sa yake kuka haka ba, face tsananin danasani na rayuwar da yayi abaya da yake. yakasance mazinaci, mashayin giya. “Yanzu idan Ζ΄arsa mafi soyuwa agaresa, tataso taji labarin abun da ya aikata a baya, wani irin kunya zaiji? mezaice da’ita idan ta tambayesa, meyasa yazamo haka?” tambayar da yayiwa kansa kenan, amma kuma baida amsa, baida kuma me amsa masa.

Rungumeta ya sakeyi tsam, acikin Ζ™irjinsa, ahankali yace.

“Kindawo gareni Zahrah, Allah yadawomin dake, Inasonki Inasonki, inamiki so na musamman Allah ya albarkaceki Ζ΄ata!!!” kiss ya manna mata akan goshinta, kana yazuba mata idanu, bazaiyi mamakin kamannin daya gani akan fuskar Ζ΄artasa ba, saboda yasan ba aja da ikon Allah, kuma hakan ma wata rahamace da Allah yayi masa, Allah ya hanasa Zahrah alokacin dayaso, yanzu yakuma basa Zahrah alokacin dayaso, hancinta bakinta duka kalan nasa ne, amma kuma idanunta tamkar idanun Zahrah aka ciro aka sanya mata, kallon farko da yarinyar tayi masa, saida yaji tsikar jikinsa ya tashi, saboda gani yayi tamkar Zahrah ce dakanta agabansa. yana rungume da yarinyar ya Ζ™arasa gaban Afrah dake kwance akan gado tana kallonsu, ranΖ™wafowa yayi ya manna mata kiss akan goshinta, hanu yasa yashafi kumatunta, haΙ—e da cewa “Nagode Ζ™warai Afrah, Allah ya miki albarka, bazan manta da wannan Ζ™oΖ™arin da kikamin ba, Inasonki”

Karo na farko kenan arayuwarta da taji kalmar nan tafito daga bakinsa akanta, “Inasonki” ta maimaita kalmar abakinta cike da mamakinsa.

Kansa yajinjina mata haΙ—e da sakin murmushi.

“Ki kwanta ki huta, nasan kinsha wahala sosai” yafaΙ—i haka yana shafa kanta.

Lumshe idanunta kawai tayi saiga hawaye nabin kan fuskarta. Hanu ta miΖ™a masa ya bata yarinyar, ba iya mamaki ba hadda tsoro saida ya bayyana akan fuskar Afrah, sakamakon ganin fuskar yarinyar Ι—ago kanta tayi ta kalleshi da sauri.

Kamar yasan me take tunani, murmushi yayi mata haΙ—e da Ι—aura hanunsa akan kafaΙ—anta. “Kada kidamu, Allah ne yayi ikonsa, Allah ne yadubeni yayimini rahama, sannan kuma ko da ace kowa zaiyi mamakin kamannin yarinyar ni bazanyi ba, saboda wacce take kama da ita, jinin jikinane, sannan kuma Allah yana da ikon yin komai”

Ajiyar zuciya kawai Afrah ta sauΖ™e haΙ—e da kafe yarinyar nata da ido, tabbas da badan taji Ζ™auna irinta uwa da Ζ΄a akan yarinyarba, to tabbas da tace ba itace ta haifi yarinyar ba, Zahrah ce, shine aka sanja mata, aka Ι—auki nata aka kaita wani gun, itakuma aka kawo mata wannar, a matsayin Ζ΄arta. Rungume Ζ΄ar tata tayi, tanajin Ζ™aunarta aranta.

***

Suna komawa gida Zaid yayiwa Afrah kyautar zuΖ™eΖ™iyar mota, tare da kuΙ—i Naira Million 3 duk na murnan ta haifa masa baby ne, washe gari kuwa suka tarkato suka dawo Nigeria, abisa takurawan Mom Ι—insa. amma da anyi suna yace zasu koma. Aranan da aka haifa masa Zahrah aranan ya mallaka mata babban kamfaninsa na Ζ™era takalma, dake Italy, aranan kuma akasanjawa kamfanin suna zuwa sunan yarinyar, saΙ“anin da dayake sunan Zaid.

Tunda aka haifi Zahrah Zaid baibari kowa ya Ι—auketa ba, inbanda uwarta, nan ma nono kaΙ—ai take bata, idan yaΙ—auketa yashiga Ι—akinsa da ita, kulle Ζ™ofar yake da key gudun kada wani ya damesa, komai na duniya shiyake mata, wani irin so da Ζ™aunar yarinyar yake ji, wanda baitaΙ“a jin irin saba, akullum kallon Zahrah kawai yakeyiwa yarinyar. Irin soyayyar dayake yiwa yarinyar shike tsorita kowa.

Ranan suna kamar yanda ya alΖ™awartawa kansa cewa idan ya haifi Ζ΄a mace sunan Zahrah zaisawa yarinyar, hakance takasance domin kuwa sunan nata yasaka, wato FATIMA ZAHRAH, koda Afrah taji sunan da Ζ΄artata taci sai kawai tayi murmushi, ko kaΙ—an batayi fushi da faruwar hakan ba, saboda tasan albarkacin Zahrah itama zata samu soyayya ta musamman daga wajen Zaid Ι—in, haka kuma albarkacin Zahrah Ζ΄arta itama zata samu gagarumar soyayya daga wajen ubanta.

Nairori sunyi kuka a wannan rana, sosai Zaid yayi Ι“arin kuΙ—i tundaga randa aka haifeta kawo yau dayake suna, dukiya kawai yake Ι“ararwa, tun abun nabawa Mom Ι—insa da Afrah mamaki, har suka daina mamaki, saboda zuwa yanzu sunsan soyayyar da Zaid keyiwa Ζ΄arsa Zahrah ta wuce gaban kwatance, harta bacci akan Ζ™irjinsa takeyi.

Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 13 BY FATYMA SARDAUNA"