SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 10 BY FATYMA SARDAUNA
SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 10 BY FATYMA SARDAUNA
Www.bankinhausanovels.com.ng
Saida kusan gabaki Ιaya mutanen da suka kawo Zahrah suka soma watsewa zuwa wajen dinner, kafun Husnah ta matso kusa da amarya Zahrah wacce take aikin kuka. Hannayenta takamo haΙe da zama gaf da’ita.
“Please Zahrah kidaina wannan kukan, yanzu haka Doctor yace inkai masa ke yana boys guaters, kuma kinga babu amfanin kije wajensa kina kuka” Husnah tafaΙi haka ga cikin lallashi.
Zahrah dai bata kumace da’ita komai ba bata kuma daina kukan ba,, wayar Husnah ce tayi Ζara alamar shigowar Ζira, sunan Dr.Sadeeq ne keyawo akan screen Ιin wayar,, tana kara wayar akan kunnenta yace
“Yadai Husnah, najiku shiru”
Sake kallon mutanen da sukayi ragowa acikin Ιakin Husnah tayi.
“Gaskiya babu dama Doctor, saboda dazaran anga zamu fita za’ace ina zankaita” Husnah tafaΙi haka cikin Ζasa Ζasa da muryarta….
Ajiyar zuciya Dr.Sadeeq yayi haΙe da cewa
“Okay to bakomai zan san yanda za’ayi, ku shirya me meckup tana nan zuwa”
Cikin matsanancin ciwon kan dake Ιawainiya da’ita tashiga toilet ta Ιauro alwala, kan Ζaton darduman dake shimfuΙe a tsakiyar Ιakin ta hau ta kabbara sallah’n magriba,, tana idar da sallan meyi mata meckup ta Ζaraso, haka tanaji tana gani ta bada fuskarta aka zizara mata meckup wanda yaΙauki fuskarta sosai.. Yauma dai meyin meckup Ιinne ta shiryata tsab cikin wata haΙaΙΙiyar doguwar riga (wedding gown) na wani tsadadden leshi me matuΖar kyaun gaske, riga ce doguwa har tana sharan Ζasa yayinda bayan rigar aka sanya wani haΙaΙΙen net me matuΖar kyaun gaske, sosai net Ιin da aka sanya abayan rigan yakuma Ζawata Ιinkin, lace Ιin yakasance light pink colour yayinda kayan Ζyale Ζyale najikinsa yakasance golding ash colour, sosai kayan yayiwa Zahrah kyau,,, haΙaΙΙen Ιaurin Ιan kwali aka tsantsara mata akanta, take tasake yin kyau,,,, yau dai kwalliya da kuma kyawun da Zahrah tayi haryafi wanda tayi a ranan kamu, komai nata yau na musamman ne tasha kyau sosai, ga doguwar riganta me Ιaukar hankali, daddaΙan Ζamshi kawai take fitarwa ajikinta me sanya nutsuwa,, duk da irin wannan kyawun da tayi sai dai fuskarta babu wani wadataccen walwala domin kuwa idanunta sunyi luhu luhu dasu, cikinta kuwa banda kukan yunwa babu abun dayake yi mata, amma kuma saboda masifar taurin kai irin nata taΖi sanyawa cikin nata komai na abinci.. Husnah ma yau zama tayi akayi mata meckup nagani na faΙa, sosai itama tayi kyau, tasha adonta cikin wata doguwar riga na golding white lace, idan ka kalleta dole ka Ζara domin itama tayi kyau sosai dama kuma itaΙin ma ko babu meckup tana da kyau masha Allah….
Yauma dai ango tare da amaryarsa zasu wajen dinner kowa yariga daya tafi harsu Auntie Raliya kuwa….
Husnah ce riΖe da hanun Zahrah suka fito compound Ιin gidan inda motar ango ke jiransu.
Shikam gaba Ιaya kwana biyunnan salon kyawun na Zahrah namatuΖar tafiya da imaninsa babu ma kamar yau, gaba Ιaya komai na surar jikinta ya bayyana bama kamar hips Ιinta yafito raΙau acikin rigan..
STORY CONTINUES BELOW
Husnah ce ta buΙe murfin motar dayake zaune aciki, sai da ta tattaro Ζasan rigan Zahrah’n kafun Zahrah ta’iya shiga cikin motar ta zauna,, lumshe idanunsa yayi haΙe da shaΖan daddaΙan Ζamshin daya kawowa hancinsa ziyara, wani irin ajiyar zuciya me Ζarfi ya sauΖe,, kallonsa yakuma dawowa dashi kan tauraruwar da haskenta yacika idanunsa,,, murmushi yasakar mata me Ζayatarwa, yayinda ita kuwa kanta ke duΖe aΖasa tama kasa Ιago idanu ta kalleshi,, hanunsa ya sanya ya Ιago haΙarta, sai alokacin ta iya jefa idanunta cikin nasa idon, wani irin abu yaji acikin jikinsa, ita Ιinma hakane, da sauri ta rumtse idanunta,, abun daba ta tsammata ba, sai jitayi ya jawota jikinsa, haΙanta yakuma Ιagowa da hanunsa na dama, haΙe da sanya Ιayan hanunsa yashafi gefen kumatunta
“My Princess!”
yaΖira sunanta cikin wata muryarsa me sanyi. a hankali ta ware idanunta acikin nasa idanun, Ζasa Ζasa yayi da idanunsa haΙe da maida kallonsa ga Ιan Ζaramin bakinta dayasha lipstick, murmushi yakuma sakarmata haΙe da sake jawota ya Ιaurata akan cinyarsa.
“Kinyi kyau fiye da kullum my princess!” yafaΙi haka still yana me shafa gefen kumatunta da hanunsa, wani irin kunyarsane yakamata tunda take dashi baitaΙa yi mata irin kallon dayakeyi mata a yanzu ba, haka kuma baitaΙa jawota yaΙaurata akan cinyarsaba sai yau. Marairaice fuskarta tayi haΙe da sunkuyar da kanta Ζasa,, sweet Ιin dake cikin bakinsa ya cire, haΙe da Ιago fuskarta ya sanya mata acikin bakinta, kallonsa tayi da Ιara Ιara idanunta, kansa ya jinjina mata yana Ιan murmushi, ahankali tashiga juya sweet Ιin acikin bakinta, dama kuma tunsafe babu wani abu daya shiga bakinta inbanda ruwa, sai wannan sweet Ιin daya bata yanzu,, hanunta yakama yashiga murzawa ahankali haΙe da kafeta da idanunsa wanda lokaci Ιaya suka wani marairaice…. SauΖeta yayi daga kan cinyarsa haΙe da kama hanunta ya buΙe murfin motar riΖe da hanunta haka suka fito daga cikin motar,, kamar wata jela haka take binsa still hanunta na riΖe acikin nasa, direct wani dogon gini dake cikin gidan nasu suka nufa. Ita dai kawai binsa take cikin takunta me Ιauke da nutsuwa yayinda rigar jikinta kuwa ke share wajen, don ma wajen babu datti, wani haΙaΙΙen falo ta tsinci kanta a ciki, suna shiga cikin falon Doctor yatsaya daga tafiyan da yakeyi haΙe da juyowa gareta, murza hanunta dake cikin nasa yayi haΙe da zaunar da’ita akan kujera, kaitsaye wajen wani fridge dake aje cikin falon ya nufa, buΙe murfin fridge Ιin yayi haΙe da Ιauko kwalin fresh milk wanda bashida sanyi sosai, glass cup ya Ιauka ya tsiyaya fresh milk Ιin aciki, saida yakusa cika kofin kafun yamaida sauran cikin fridge Ιin ya aje.. Inda Zahrah ke zaune ta sunne kai Ζasa ya nufo, aje kofin fresh milk Ιin yayi akan Ιan Ζaramin table Ιin dake kusa da kujeran daya zauna, jawo Zahrah yayi jikinsa haΙe da sake Ιaurata akan cinyarsa, kofin da fresh milk Ιin ke ciki ya kawo dai dai saitin bakinta, cikin muryar lallami yace
“AnfaΙamin bakici komai ba tun safe, banaso kina zama da yunwa fa, banso tayi miki illa, kisha ko kaΙanne kinji baby na!”
Tsintar kanta tayi da kasa musa masa, saidai amma kuma gaba Ιaya a tsarge take, bata taΙa zama akan cinyar wani haka ba, hakan yasa gaba Ιaya ta takura,, a hankali take Ιan shan fresh milk Ιin wanda harkusa da bakinta Dr.Sadeeq yake kawo mata kofin, shan fresh milk Ιin take cike da nutsuwa yayinda shi kuma gaba Ιaya idanunsa ke kanta, bakinta kawai yake kallo, karo na farko kenan arayuwarsa dayaji wani irin muguwar sha’awarta na fusgarsa,,, kafun shida ita su ankara tuni hartasha fiye da rabin kofin,, Ιan ya mutsa fuskanta tayi haΙe da sanya hanu ta shafi Ιakalallen cikinta
“NaΖoshi fa!” tafaΙi haka tana me langwaΙar da kanta gefe.
“Um’um ban yarda ba nasan kinajin yunwa sosai, ki Ιan Ζarasha ko kaΙan ne kinji _MY WIFE_!”
Kalmar nan ta_MY WIFE_ daya Ζirata dashi shiyasanya taji gaba Ιaya jikinta yayi mata wani iri,,, bakinta ta turo gaba haΙe da cewa
“dagaske ni na Ζoshi, gashi kuma duk kasa janbakina ya goge!” taΖare maganar akasalance.
Wannan shagwaΙan da takeyi masa shiyake sanyawa yaji gaba Ιaya jikinsa ya mutu, har wani rufewa idanunsa keyi,, yabuΙe baki zaiyi magana kenan wayarsa tasoma Ζara, kobai Ιaga ba yasan dalilin Ζiran, yanzu haka yasan anacan antaru a wajen dinner su kawai ake jira, miΖar da’ita yayi tsaye bayan ya aje cup Ιin dake hanunsa,, amaimakon ya riΖe mata hanu su tafi kamar yanda suka zo sai gani tayi ya Ιagata caΙak yayi hanyar waje da’ita,, a tsorace tanemi sauΖa daga jikin nasa amma kuma kyakkyawan riΖon dayayi mata yakasa bata daman hakan….
Bai direta ako ina ba sai acikin mota, yanashiga driver yaja motar suka fice daga cikin gidan… Kwanciya tayi luf ajikin kujeran motar haΙe da lumshe idanunta gaba Ιaya sanyin AC’n da motar ke busawa ne ke damunta, sam batason sanyi yacika yawa a waje. daga wani Ιangare kuwa amatuΖar takure take, saboda yanayin yanda yake murza hanunta dake cikin nasa. sosai hakan kesawa taji wani iri acikin jikinta, gani tayi gaba Ιaya yau Ιin ya sanja mata, yanayi mata wasu irin abubuwa da baitaΙa ΖoΖarin kwatanta yi mata shiba acan baya, ada sam baya taΙa yunΖurin kama hanunta sai dai idan yazama dole,kuma koda ma ya kama hanunta bawani jimawa zai sake, sannan kuma sam baya yawan jawota jikinsa kamar yanda yakeyi mata ayau, gashi gaba Ιaya taga yanayinsa ya sauya, idanunsa sunyi wasu kala tamkar wanda yakejin bacci… Zuciyarta nayi mata lugude haka suka iso wajen dinner inda mutane suka cika maΖil zuwansu kawai ake jira… Suna isowa waje yaΙauki sowa yayinda mc yasake musu daddaΙan kiΙa me daΙi ta romantic… kamar dai yanda kamu ya Ζayatar haka dinner ma yaΖayatar sosai Dr.Sadeeq yayiwa Zahrah Ιarin kuΙi lokacin da aka Ζirasu tsakiyan fili, sunsha liΖin kuΙi kam sosai, su Auntie Raliya ma sunzo sun liΖa musu, amma duk yanda akaso amarya tayi rawa kasawa tayi, saboda bata iyaba, bakuma al’adarta bane yin rawa agaban mutane, kunya ma bazai taΙa iya barinta ba,, saida Dr.Sadeeq yariΖe hanunta yashiga juyawa da’ita afilin rawan, take aka hau musu tafi yayinda wasu daga cikin abokansa suka ci gaba da yi musu Ιarin kuΙi,, suna komawa kan kujeransu mc yasanya musu daddaΙan waΖar Ed sheeran, shiru Zahrah tayi tana sauraran waΖar sosai dama takeson waΖar domin kuwa duk waΖan Ed sheeran yanayi mata daΙi… Koda aka yanka haΙaΙΙen cake Ιin da aka Ζawatashi da sunan ango da amarya, da Ζyar Zahrah ta’iya bawa Dr.Sadeeq cake Ιin abaki, gaba Ιaya nauyi da kunya sun isheta gawani zazzaΙin daya sake kawo mata ziyara lokaci Ιaya,,, lokacin da aka tashi a dinner tuni amarya Zahrah tayi laushi, hartakai bata iya dogon tsayuwa da Ζafafunta, Ζarfe 10 na dare aka tashi a dinner Aunty Ladi da kuma Husnah su suka sanyata a wata mota, direct aka wuce da’ita asalin gidan da zata zauna wato gidan aurenta…. Gidane me matuΖar kyaun gaske wanda aka kashe kuΙi sosai wajen Ζawatasa, baginin gidan sama bane amma kuma yanayin yanda akayi ginin yayi kyau sosai, wata haΙaΙΙiyar Ζofa suka nufa, suna buΙeta kuwa suka tsinci kansu cikin wani Ζawataccen falo me kyaun gaske. haΙaΙΙen falone wanda yasha kujeru light orange and milk colour, yayinda aka Ζawata jikin Ζofa da window’n da wasu irin haΙaΙΙun labulaye masu kyau, tsakiyar falon kuwa mamaye yake da wani haΙaΙΙen carpet Orange colour,, ga wani irin Ζaton tv plasma dake aje kan wani haΙaΙΙen glass,, falon dai ba’acika masa kayan ado ba amma kuma yaΖawatu sosai komai na falon me tsada ne,, direct wani Ιaki dake cikin falon aka wuce da Zahrah,, Ιakine me kyau wanda yaji royal furnitures milk colour, yayinda aka lailaye kan makeken gadon da wani irin zanin gado pink me kyawun gaske… Akan gado sukayimawa Zahrah masauΖi, Husnah dakanta ta haΙawa Zahrah ruwan wanka, koda tafito a bathroom Ιin hannayen Zahrah dake zaune kan gado ta kamo, haΙe da janta har zuwa cikin bathroom inda ta haΙa mata ruwan wanka…
STORY CONTINUES BELOW
Wani Turare ta bata tace inji Hajiya Shuwa, sannan kuma tayi mata bayanin yanda zatayi amfani dashi…
Zahrah tana fitowa a wanka Husnah ta shafa mata powder haΙe da lipstick, wani riga da sket na material marar nauyi Husnah ta bata tasanya, take tafito Ιas da’ita, a tsakiyar gado Husnah ta zaunar da Zahrah haΙe da rufe mata kanta da wani irin haΙaΙΙen mayafi me sheΖi da walwali, wasu turaruka masu Ζamshi Husnah takuma feshi jikin Zahrah dasu, take Ιakin yakuma Ιumamewa da Ζamshi,, sake matsowa kusa da Zahrah Husnah tayi cikin murya Ζasa Ζasa tace
“Dan Allah Zahrah karkice zaki ci gaba da wannan kukan naki, ki Ιan daure zuciyarki kinji Ζawata, kuma sannan kada ki hana Doctor haΖΖinsa, nasan zakiji tsoro amma please ki daure kinji Ζawata, banaje falo na amsa waya ” Husnah taΖare maganar tana me miΖewa tsaye, idanu tayiwa Auntie Ladi suka fice a tare….
Tun Zahrah na jiran dawowan su Husnah hartasoma jin tsoro, domin kuwa gaba Ιaya gidan yaΙau shiru babu alaman akwai motsin wani mutum bayan ita,,, abun da Zahrah bata sani ba shine su Husnah wayo sukayi mata suka tafi suka barta, sunyi hakanne kuma saboda taΖaitamata wahalan kuka, domin sun san sunace mata zasu tafi zata Ζara fawan kukanta…..
GyangyaΙine yasoma Ιaukarta, dan haka saita jingina bayanta ajikin saman gadon haΙe da lumshe idanunta da suketa tsiyayar hawaye…
A hankali yaturo Ζofar Ιakin bakinsa Ιauke da sallama, yasake shiga cikin wata farar shadda sabuwa Ζal sai sheΖi takeyi, Ζamshi ne kawai ke fita ajikinsa, daganinsa kasan yana cikin matsanancin farinciki,, ledan dake hanunsa ya aje, haΙe da takowa zuwa wajen datake zaune ta jingina bayanta da saman gado,, zama yayi akusa da’ita haΙe da Ζiran sunanta,, cikin murya me sanyi da kuma alamar bacci ta amasa masa,, ahankali yasanya hanunsa ya Ιan jaye mayafin dake kanta, hawaye yagani kwance akan fuskarta, hanunta yakamo haΙe da jawota jikinsa, hanu yasanya yashiga share mata hawayen dake kan fuskarta.
“Ki daina kuka kinji my wife, bacci zakiyi ne?” yatambayeta yana me Ζaremawa fuskarta kallo,, fuska ta kuma kwaΙewa, haΙe da kaΙa kanta, cike da shagwaΙa tace
“Ina Husnah?”
Ajiyar zuciya yasauΖe haΙe da sanya hanu yashafi lallausan gashinta dayasha gyara
“Husnah kuma Zahrah?” yatambayeta cike da mamaki..
“Eh tacemin zata amasa waya tana zuwa kuma haryanzu bata dawo ba!” yanzuma dai asangarce tayi maganar,, murmushi yayi mata haΙe da cewa
“Kada kidamu Husnah zata dawo gobe, taso muje kiyi alwala idan munyi salla saikici abinci ko”
Jitayi gabanta yayi wani irin faΙuwa amma kuma yazatayi da rayuwarta babu yanda ta’iya haka tabisa kamar jela harcikin bathroom,, saida yayi nasa alwalan kafun yabata waje itama ta Ιauro alwala,, tana fitowa daga cikin bathroom Ιin ya miΖo mata wata lufaya, a ΙaΙare tasanya lufayan daya bata, hanunta yakama suka hau kan sallaya, shi yajasu salla raka’a biyu, suna idarwa yayi musu addu’o’i haΙe da kama kanta itama yayi mata addu’a… A tsorace ta zauna akan gado haΙe da sake takure jikinta waje Ιaya…
Wani Ιan madaidaicin carpet Dr.Sadeeq yashimfuΙa haΙe da cika tsakiyar carpet Ιin da kayan ciye ciye, hanu ya miΖawa Zahrah alamar tataho garesa, cikin Ιari Ιari haka ta shiga takowa zuwa inda yake, hanunta yakamo yazaunar da’ita acikin jikinsa, hijabin dake jikinta yasoma ΖoΖarin cire mata, da sauri tasake ΖanΖame jikinta, ganin haka yasanya shi yin murmushi, ya fasa cire mata hijab Ιin,, juice ya zuba acikin kofi haΙe da kai kofin bakinta, babu musu tabuΙe bakinta ta kurΙi kaΙan, aje kofin yayi, haΙe da yago gasasshen nama yakai bakinta,, kanta tashiga girgizawa alaman bazataci ba.
“Kiyi haΖuri kici kinji Baby na, kaΙan zakici bamai yawa ba!” yafaΙi haka cike da lallami,,, shida kansa yake bata kazan, bata wani ci me yawa ba tace masa ta Ζoshi, dakansa yatattara wajen yakai kitchine,, yana dawowa Ιakin yasameta tsaye ajikin mirror tayi jigum,, fargabane yacika mata zuciya, wani irin tsoro ne taji ya Ιarsu acikin zuciyarta wanda bazata iya misaltashi ba,,
STORY CONTINUES BELOW
Kaitsaye drower Ιin dake cikin Ιakin ya nufa, wata doguwar rigan bacci sleeping dress yaciro haΙe da Ζarasowa gareta,, “Kije kiyi brush, wannan kayan kuma kisanya kizo kiyi bacci” hanunta na rawa haka ta amshi kayan sumi sumi ta wuce cikin bathroom, tana kammala brush tasoma cire kayan jikinta, warware rigan da Dr. yabata tayi tashiga Ζaremawa rigan kallo, doguwar rigace na bacci me net, amma kuma tana da faΙin wuya sannan kuma rigan irin me nuna jiki Ιinnan ne,, badon tasoba haka ta sanya rigan ajikinta, hmmm sam bazata iya fita da wannan rigan gaban Dr. Sadeeq ba, saboda gaba Ιaya rigan ta bayyana breast Ιinta, yayinda komai nata yafito fili, hijabin da tayi salla dashi ta Ιauka ta sanya,, a ΙaΙare ta fito daga cikin bathroom Ιin,, zaune tagansa akan gado tuni yasanja kaya zuwa farar jallabiya, murmushi kawai Dr.Sadeeq kejifanta dashi, cikin zolaya yace “Meye narufe jikin da hijabi?”
Ζasa takumayi da kanta, yanzu kam ko Ιan shagwaΙan ma takasayi masa…
Sarai ya fuskanci halin da take ciki, “Zoki kwanta” yafaΙi haka yana meyi mata nuni da kan gadon dayake zaune,, kamar wacce Ζwai yafashewa haka Zahrah ta zo ta kwanta akan gadon, gaba Ιaya ta takure kanta waje Ιaya,,, miΖewa yayi daga zaunen dayake haΙe da kashe wutan Ιakin ya kunna na bacci, Zahrah najin takusan alamar yakusa zuwa kan gadon taji bugun zuciyarta ya tsananta, yayinda Ζirjinta yashiga wani irin luguden duka,, kwanciyarsa akan gadon yayi dai dai da kusan Ιaukewar numfashinta,,,, da Ζyar ta’iya Ζwato numfashinta, haΙi sa soma sauΖe ajiyar zuciya a Ιoye, kusan minti goma da hawansa kan gadon amma kuma taji baiyi mata wani abu ba, hakan yasa taΙanji zuciyarta tayi sanyi. Shiru tayi tana me jin sauΖar numfashinsa ahankali, wani irin mugun tausayinsa ne taji yaΙarsu acikin zuciyarta amma kuma ita bata da yanda zatayi, tunaninta ne ya katse alokacin da taji sauΖar hanunsa a bayanta,, ahankali ya juyota tadawo tana fuskantarsa,, kallon fuskarta yashigayi batare dayace da ita komai ba, kusan mintuna 4 yayi yana kallonta, cikin wata irin murya wanda batasanshi da ita ba yace
“kicire hijabin nan saboda kiji daΙin baccinki ko”
babu musu ta cire hijabin daga jikinta sai dai kuma bahaka ranta yaso ba, bargo yaja ya rufa musu hanunta yakamo ta cikin bargon yariΖe acikin nasa, “Ki kwantar da hankalinki, nasan kingaji, kiyi addu’a, kiyi bacci me daΙi” yafaΙi haka cikin muryar raΙa, hanunta yasake damΖewa acikin nasa hanun haΙe da lumshe idanunsa, zai bartane kawai saboda tausayinta dayake ji, amma bawai don baya sha’awarta ba, hasalima baita Ιa jin matsanancin sha’awarta irin nayau ba, hakan yafarune kuma saboda baitaΙa samun kusanci me tsanani da ita irin na yau Ιin ba, da wannan tunanin bacci ya Ιaukesa,,,, Zahrah ma dai baccin ne yaΙauketa batare data shiryawa hakan ba,, Ζarfe Ιaya na dare wani irin zazzafan zazzaΙi yarufe jikin Zahrah take tasoma karkarwa haΖwaranta har haΙewa suke, suna ba da wani sauti, hakan yafaru ne kuma sakamakon sanyin AC wanda yayi mata yawa, acikin baccinsa yakejin hucin numfashinta nafita da sauri, a hankali ya buΙe idanunsa ya sauΖesu akanta, da sauri yatashi ya zauna haΙe da kamo kafaΙunta,, “Zahrah!” yaΖira sunanta a hankali,, tanajinsa amma bazata iya amsa masa ba domin kuwa ba iya zazzaΙi ba hatta kanta jinsa take tamkar anΙaura mata gungumen ice, yamata nauyi Da sauri ya sauΖa akan gadon, AC’n yafara kashewa, kana ya buΙe wata Ζ΄ar drower maganin ciwon kai da zazzaΙi ya Ιauko haΙe da goran ruwa,, yana zuwa ya ta data zaune, Ιalle maganin yayi yasa mata abaki haΙi da kafa mata goran ruwa, babu musu ta haΙiye maganin, ajiye goran yayi haΙe da hawa kan gadon, hanunsa yasanya akan wuyanta, zafi yaji zau kamar wuta, ajiyar zuciya ya sauΖe, haΙe da cire rigan dake jikinsa, cikin bargon yakoma, haΙe da jawota kusa dashi, ahankali yasanya hanunsa a bayanta yayi Ζasa da zip Ιin doguwar rigan dake jikinta,, cike da nutsuwa ya cire mata rigan,, Zahrah tana jinsa amma kuma ayanzu babu wani abu da zata iyayi wanda zata kare kanta,, bashi kaΙaiba har ita kanta saida ta sauΖe wani irin ajiyar zuciya me Ζarfi alokacin da zallan fatar jikinsu suka samu haΙewa waje guda. lokaci Ιaya yaji tunaninsa yasoma sauyawa, nutsuwarsa tafara gushewa, haka kuma idanunsa sun soma rufewa,, haΙewar jikin Zahrah danasa jikin baΖaramin feeling me girman gaske ya sauΖar masa ba, tunda yake aduniyarsa yau shine karo na farko, da ya fara haΙa jikinsa dana mace haka, yasan yataΙa rungumar Zahrah amma ba runguma irin wannan ba,,,, Zahrah kuwa baΖaramin jin daΙin jikin nasa tayi ba, jitayi gaba Ιaya nutsuwa yasoma sauΖar mata, sake maΖalewa ajikinsa tayi haΙe da cusa kanta acikin faffaΙan Ζirjinsa har yazamana laΙΙan ta suna gogan fatar wuyansa,, jin yanda take Ζara shigewa jikinsa shiya Ζara taimakawa wajen Ζara masa wutar sha’awarta, hannayensa duka yasanya a bayanta yasake riΖeta gam, numfashi kawai yake fitarwa akai akai shi kaΙai yasan meyakeji acikin jikinsa,, yana cikin wannan irin yanayin yaji sauΖar numfashin Zahrah ahankali yana fita da’alama baccine yakuma Ιaukarta,,, haka yarungumeta Ζam acikin jikinsa yayinda yacusa kansa acikin gashin kanta yana shaΖan daddaΙan Ζamshinta dake Ζara rikitasa,, bakaΙan ba ya yi jarumta wajen ganin ya Ζyaleta baiyi mata komai ba, haΖiΖa bakowani irin namiji bane zai haΙa jiki da mace ace ya iya daure zuciyarsa baiyi mata komai ba, balle ma mace irin Zahrah wanda irinsu basu da yawa acikin mata,, da Ζyar bacci ya’iya Ιaukarsa…….
Ζiran sallan asuban fari akan kunnensa,, a hankali ya ware idanunsa akanta, baccinta takeyi cikin kwanciyar hankali da’alama zazzaΙi da ciwon kan dake damunta sun jima da kama gabansu,, baisan lokacin da murmushi ya Ζwace masa ba, komai na Zahrah me kyau ne, har idan tana bacci kyawunta baya Ιuya, kallon zara zaran eye lashes Ιinta daya kwanto aΙan Ζasan idanunta yayi,, ahankali ya zare jikinsa daga nata jikin, cikin sanΙa yatura Ζofar bathroom yashige, gudun kada motsinsa ya tashe ta daga daddaΙan baccin da take,, saida yafarayin wanka kafun ya Ιauro alwala,, tsayawa yayi yana kallon yanda taketa fidda numfashi a hankali, badon sallah yazama dole akanta ba, to tabbas da babu abun da zai sanya ya tasheta a dai-dai wannan lokacin, zai bartane tasha baccinta ta Ζoshi,, ahankali yashiga girgiza Ζafanta haΙe da Ιan Ζiran sunanta, cikin murya Ζasa Ζasa… Da yake bata da nauyin bacci, Ζira biyu yayi mata ta buΙe idanunta,, da sauri ta sake jawo bargo ta rufe jikinta, kana tasoma raba idanu, murmushi yakumayi mata haΙe da sanya hanu ya shafi gefen kumatunta.+
“Kitashi kiyi sallah, ni na wuce masallaci”
Bata iya amsa masa ba haryafice daga cikin Ιakin,, kallon kanta tashiga yi gaba Ιaya gashinta ya watse yayi buji buji dashi, da’alama dai tasha juyi acikin bacci,,, tana shiga bathroom ta haΙawa kanta ruwa me Ιan Ιumi, wanka tayi itama kana ta Ιauro alwala (?Yadai dukanku wanka sai kace ?)….3
Tana fitowa daga bathroom Ιin ta zura wata jan doguwar riga marar nauyi, haΙe da zura hijab ajikinta, kan sallaya tahau haΙe da dai-dai ta tsayuwarta…… Koda ta’idar da sallan saida tayi azkar kafun ta miΖe daga kan sallayan,, harta zauna akan gado, maganganun Hajiya Shuwa suka faΙo mata arai inda take ce mata _”Kada ta sake Ζamshi yabar jikinta, sannan kuma idan tayi sallan asuba kullum tana shafa turare aduk wani lungu da saΖo na jikinta”_ batasan mene manufar hakan ba, amma dai ta Ιau maganar kuma zatayi aiki dashi. Gaban mirror tanufa haΙe da Ιaukan Ζ΄ar Ζaramar hand bag Ιinta dake aje kan mirror’n wani Ιan kwalban body spray ta ciro daga cikin jakar, haΙe da fesawa ajikinta, daga kan wuyanta har zuwa bayan kunnenta, sosai turaren yake da Ζamshi, take Ιakin ya gauraye da Ζamshin turaren,, tana shirin maida turaren cikin jakarta, Dr.Sadeeq yaturo Ζofar yashigo bakinsa Ιauke da sallama,, cikin murya me sanyi ta amsa masa sallaman nasa,, direct inda take tsaye ya nufo, batayi tsammani ba saiji tayi ya buΙe hannuwansa ya rungumeta ta baya haΙe da Ιaura kansa akan wuyanta,,,, idanunsa ya lumshe haΙe da buΙe hanci ya shaΖi daddaΙan Ζamshin dake fita ajikinta cikin wata irin murya yace
“Good morning madam!”
Kunyan sane yakamata, saikawai tayi Ζasa da kanta haΙe da cewa
“Ina kwana”
“Lafiya Ζalau, yajikinki?” ya amsa mata yana me cusa kansa acikin wuyanta..
“Da sauΖi”
Ta mayarmai da amsa cikin Ζasa da murya…
“Ζamshinki yamin daΙi sosai, kinyi sallah ne?”
STORY CONTINUES BELOW
Kanta ta ΖaΙa masa alamar “Eh” hanunta yakama yajata zuwa kan gado… Zama yayi kana ya jawota jikinsa,, Ιago fuskarta yayi haΙe da jefa idanunsa cikin nata. Sunanta yaΖira cikin wata irin murya me Ιauke da nutsuwa..
Kanta ta Ιago ta kallesa, ganin idanunsa tsaye cak akanta yasanya tayi saurin meda kanta Ζasa..
“Meyasa kikejin kunya na sosai ne?”
Yayi mata tambayar da bata tsammata ba,, jijjiga kanta tayi alaman
“babu”
Sake matseta acikin jikinsa yayi haΙe da kwantar da kansa akan kafaΙanta.
“Mallakarki danayi wata babban nasara ce dana samu acikin rayuwata Zahrah, inasonki ne da duka zuciyata, dakuma iya gaskiyata, banda niyar cutar dake acikin rayuwar zaman aurenmu, abu Ιaya nakeso kiyi mini shine, ki rage yawan tunani da kuma kukan nan dakikeyi, inajin tsoro kada su haifarmiki da wata cuta, yanzu nasan kina da buΖatar hutu ko, ki kwanta ki huta, kafun anjima sai kiyi break fast”
MiΖewa tayi daga jikinsa haΙe da hayewa kan gadon ta kwanta, amma kuma bata Ιauke idanunta akansa ba, bayan kamar mintuna biyar da kwanciyarta shima yatashi daga zaunen da yake, kan gadon ya hau, har Zahrah taji bugun zuciyarta yasoma Ζaruwa, sai kuma taga ya lulluΙe mata duka jikinta da blanket, agefe da ita ya kwanta haΙe da juya mata baya… Shiru Ιakin ya Ιauka babu abun dake tashi sai sautin fitar numfashinsu,,, bayansa ta kafe da idanu, yayinda a cikin zuciyarta take wani tunani na daban, haΖiΖa duk duniya babu wani namiji daya dace yazamo miji agareta sama da Dr.Sadeeq, ya cancanta Ζwarai, shi mutum ne wanda zaiyi wahala asamu kamarsa, Dr.Sadeeq kuwa lumshe idanunsa yayi bawai don bacci ya Ιauke sa ba,, shima wani tunanin yakeyi daban, baisan meyasa aduk sanda idanunsa zasuyi masa tozali da Zahrah yakejin matsanancin sha’awarta ba, wanda ada kuma ba haka abun yake ba, bazaice da bayajin sha’awarta ba, yanaji sai dai kuma bakamar wanda yakeji yanzu ba, jiya bakaΙan ba ya’iya daure zuciyarsa, amma daba haka ba tabbas da baisan wani irin aika aika zaiyi mata ba, a hankali yaji idanunsa sun soma rufewa da’alama dai shima bacci bai ishesa ba, ae dole ma jiya sunsha gajiya sosai,, cikin mintuna Ζalilan bacci ya Ιauki ma’auratan biyu, yayinda kowanne daga cikinsu da irin samfurin tunanin dake cikin zuciyarsa….
***1
10:00 am dai-dai ta buΙe idanunta, haΙe da waresu akan haΙaΙΙen zanen POP’n da ya cika saman Ιakin, kallonta ta mayar ga inda take tsammanin ganinsa, amma sai dai taga wajen wayam babu shi babu alamarsa. Da sauri ta tashi zaune haΙe da maida kallonta ga wani Ιan madaidaicin agogon bangon dake saΖale jikin ginin Ιakin.
“Ζarfe 10 nakai ina bacci?”
ta tambayi kanta cikin yanayi naΙan mamaki.. A hankali tazuro Ζafafunta Ζasa, haΙe da miΖewa tsaye, Ιakalallen cikinta daya soma mata kukan yunwa ta shafa, haΙi da Ιan yamutsa fuskarta, direct Ζofar bathromm ta nufa, Ιan tsayawa tayi ta kasa kunnenta ajikin Ζofar, koda zataji Ζaran ruwa, amma saitaji shiru da’alama dai bakowa acikin bathroom Ιin, murΙa handle Ιin Ζofar tayi tashige ciki,, ruwan wanka ta haΙa yayinda ta cika turaren Ζamshi acikin ruwan, wankanta tayi cike da nutsuwa… Sanye da wani Ιan madaidaicin towel pink colour ajikinta tafito daga cikin bathroom Ιin, hatta gashin kanta ajiΖe yaΖe, still Ζaramin towel ne kuma riΖe ahanunta tana goge gashin kanta dayake ajiΖe,, daidai lokacin Dr.Sadeeq yaturo Ζofar ahankali yashigo, suman tsaye yayi ajikin Ζofar yana me Ζare mata kallo daga sama har Ζasanta, yayinda ita kuwa batasan ma da zuwansa ba, kanta kawai take aikin gogewa, saboda bataji motsin buΙewar Ζofar ba, shikuwa dama yabuΙe Ζofar ne ahankali gudun kada ya tasheta a baccin daya barta tanayi,, wani yawu ya haΙiye, haΙe da jan Ζafansa a hankali yafice daga cikin Ιakin batare daya bari ta ganshi ba,, yana fita yajingina bayansa da Ζofar haΙe da sauΖe wani irin Ζaton ajiyar zuciya,, lumshe idanunsa yayi haΙe da sanya hanunsa acikin tulin sumar kansa yashiga shafawa a hankali,, ashe haΙuwar Zahrah yawuce yanda yake zato yake kuma tunani, wannan wace irin haΙaΙΙiyar surace Zahrah’n sa ta mallaka,, lallai Zahrah mace ce cikakkiya tagaban kwatance,, da Ζyar ya’iya jan Ζafansa ya koma cikin falo, kwanciya yayi akan kujera haΙe da lumshe idanunsa da suka sauya launi lokaci guda…
STORY CONTINUES BELOW
Zahrah kuwa tana gama goge gashin nata tayi amfani da hand dryer wajen busar dashi mintuna kaΙan gashin yabushe tashafa masa mai,,, wani lotion me Ζamshi ta shafa ajikinta haΙe da murzawa fuskarta hoda da kuma kwalli, light pink lipstick tagoga akan leΙenta, take fuskarta ta tasake yin kyau,, gaban makeken drower’n dake kafe ajikin bangon Ιakin taΖarasa haΙe da buΙewa, kayane jere reras acikin drower’n kala kala sai wanda ranka yaso zaka saka, wata jar atamfa taciro wacce taji Ιinkin pencil gown,, tana sanya doguwar rigan yayi mata kyau haΙe dayi mata Ιas ajikinta, daga kan guiwanta harzuwa Ζafarta atsage yake ta bayan rigan, tanason atamfar sosai saboda tana Ιaya daga cikin kayan da Maman Husnah ta bata, Husnah ce kuma takai akayi mata irin wannan Ιinkin duk da kuwa irin tsadar da atamfar take dashi, kallon kanta tayi acikin madubi, murmushi tasakarwa kanta saboda ita kanta ta yaba da yanda rigan tayi mata kyau ajiki, wani Ιan madaidaicin vail me kalan ja ta Ιauka haΙe da rufe jikinta, duk da kuwa cewa kayan yana da Ιan kwali, sai dai bazata iya tafiya daga ita sai wannan rigan agaban Doctor ba saboda sosai hips Ιinta suka bayyana, ga shi breast Ιinta sun bayyana kansu ta saman rigar kasancewar wuyan rigan yana da Ιan faΙi. Da turaruka masu daΙi ta feshe jikinta… A hankali ta buΙe murfin Ζofar Ιakin tafito, Ιan tsayawa tayi tana kallonsa,, kwance yake akan kujera yayinda idanunsa ke a lumshe, yasha adonsa cikin wata bugaggiyar shadda blue colour. Murmushi tayi domin kuwa yayi mata kyau, sosai kuma hasken fatarsa yasake bayyana acikin blue Ιin kayan. A hankali tashiga takawa har zuwa tsakiyar falon, Ζarewa falon kallo tashiga yi, ita dai haryanzu bata gamsu da cewa wai nan Ιin falon ta bane, koda wasa ma bata taΙa tunanin zata shiga cikin daula irin wannan ba,, bata ankara ba saiji tayi anriΖe mata hanu, da dauri ta juyo don batayi zaton idonsa biyu ba,, Murmushi yasakar mata haΙe da cewa,
“yaushe kika tashi?” yayi tambayar kamar bashi yaganta Ιazu ba..
Zama tayi akan kujera haΙe da cewa ” banjima da tashi ba”
Tashi yayi daga kan kujeran haΙe da kama hanunta, kaitsaye haΙaΙΙen darny area’n dake cikin falon yanufa da’ita, jawo kujera Ιaya yayi daga cikin kujeru huΙu dasuka ke waye wani babban table, zaunar da’ita yayi haΙe da buΙe wani babban food flask, plate ya Ιauka yazu ba mata soyayyen dankalin turawa’n dake cikin kulan (Chips) wata food flask Ιin yasake jawowa pepper chicken ne dayasha albasa, shima zuba mata yayi haΙe da haΙa tea acikin wani cup, turo mata duka plates Ιin dakuma cup Ιin tea Ιin yayi gabanta,, saurin Ιago kanta tayi ta kallesa, kansa ya jinjina mata alamar koma me take tunani hakane, take ta shagwaΙe fuska haΙe da cewa “Bazan iya cinye duka wannan abincin ba yamin yawa”
“Bakomai kici sosai, nasan kinajin yunwa” yafaΙi haka yana me ΖoΖarin barin wajen.
“Kai kuma fa?” batare da ta shiryawa fitowar tambayarba, saikuma bakinta yayi saurinfurtawa,, tsayawa yayi da tafiyar haΙe da juyowa, murmushi yayi mata haΙe da cewa “Ni bayanzu zanci ba” harya fice daga cikin falon bata Ιauke idanunta daga kansa ba,, ajiyar zuciya ta sauΖe haΙe da Ιaukan fork tasoma cakan chips Ιin tana kaiwa bakinta, dama yunwa takeji sosai,, sosai taci chips Ιin saidai tea Ιin sama sama tasha shi, naman kuwa ko taΙa shi batayi ba, domin ita gaba Ιaya naman kaza baiwani dameta ba, tafison gasashshen naman sa, fiye da na kaza, sai da taji cikinta yayi haniΖan kafun ta kimtsa wajen haΙe da miΖewa takoma cikin falon,, haryanzu dai idanunta basu Ζoshi da Ζarewa falon kallo ba, rayuwa kenan wai yau ita Zahrah ce zaune acikin wannan katafaren gida dasunan gidan aurenta, ita da ko gado bata dashi akan zallan Ζ΄ar katifa take kwana sai gata yau ta kwana akan haΙaΙΙen gado harda lallausan bargo da ta rufa dashi,, a hankali ya turo Ζofar falon yashigo, wayarsace riΖe a hanunsa yana latsawa,, gaf da’ita ya zauna har kafaΙunsu suna gogan na juna, hanunsa ya sanya ya shafi Ιa kalallen cikinta, “Wannan Ιan Ζaramin cikin baiΖoshi ba”
Murmushi tayi masa haΙe da waro idanunta “Dan Allah kayi haΖuri wallahi na Ζoshi” tafaΙi haka tana me Ιauke hanunsa daga kan cikinta.. Kallonta yashigayi yana me karantar yanayinta yayinda ita kuma tayi Ζasa da kanta, batason haΙa idanu dashi kwata kwata, “taso muje” yafaΙi haka yana me miΖewa tsaye, babu musu ta miΖe, hanunta ya kama suka nufi wata Ζofa dake cikin falon, key ya sanya ajikin Ζofar ya murΙa, tura Ζofar Ιakin yayi, still hanunta na riΖe acikin nasa hanun suka kutsa cikin falo’n, falone ma dai-dai ci wanda aka kewaye tsakiyansa, da wasu kujeru dark purple masu kyau, yayinda tsakiyar falon kuwa aka cike sa da wani Ιan madaidaicin chanies carpet dark and light purple colour, wasu labulaye masu kyau kalan light purpule su suka Ζawata jikin Ζofa dakuma windown falon, wani Ιan Ζaramin plasma ne maΖale ajikin bangon falon, su kenan iya abun dake cikin falon amma kuma duk da haka falon yayi kyau, kasancewar kalan kujeru da labulayen kalane me Ιaukar hankali, ga kujerun sunsha pillow Ζ΄an ma dai-dai ta gwanin ban sha’awa, yana riΖe da hanunta suka kuma shiga cikin wani Ιaki dake cikin falon,, gadone me kyau irin na zamani da drower’nsa me Ιauke da murafe shida, sai kuma su dressing mirror dakuma abun aje takalma da jaka,, kayan furnitures Ιin bawasu masu tsada bane daga kujerun har gadon bazasu wuce dubu Ιari huΙu ba, amma kuma anyi kayan da kyau da kuma inganci,, kallon sa Zahrah tayi alamar tanason Ζarin bayani,, murmushi yasakar mata haΙe da sa hanu ya shafa kumatunta, yace da’ita
“Kayan Ιakin da Baffa yayi miki ne”
STORY CONTINUES BELOW
DaΙi da farinciki ne suka cika zuciyar Zahrah take tacigaba da wurga idanunta tana kallon kayan, Allah sarki Baffa ashe haka yayi mata ΖoΖari batasani ba, lallai Baffa yafaranta ranta sosai, bata taΙa tunanin zata samu kaya haka ba, ashe dai Baffa yanasonta yana kuma Ζaunar fitar da’ita kunya, lallai wannan kaya sunfiye mata komai, saboda koba komai zata tsallakewa gorin wasu mutanen, wani irin tausayin Baffan nata ne taji ya sake Ιarsuwa aranta,, duk da cewa shiba mawadaci bane amma yayi ΖoΖari ya wadata ta da kayan Ιaki masu kyau dai dai da me rufin asiri, babu abun da zatace da baffanta sai godiya,, kan gadon taje ta zauna tana murmushin jin daΙi, sai taji tafi Ζaunar Ιakin ma fiye da wanda aka kaita daga farko, duk daΙin kyauta dai baikai ace da kuΙinka kacire ka saya ba.
“Yanaga kin wani zauna madam? taso muje nunamiki kawai nayi, bawai nace anan zaki zauna ba” Dr.Sadeeq yafaΙi haka yana me miΖa mata hanunsa alamar takama sutafi,,
ShagwaΙe fuska Zahrah tayi haΙe da kwantar dakanta gefe
“Nidai nafison nan please kabarni anan!” taΖare maganar cike da zallan shagwaΙa..
Takowa yayi yazo gaf da’ita haΙe da sanya hanunsa ya Ιago kafaΙunta.
“Nan Ιakin hutawan kine, can kuma Ιakin aurenki ne Ιakin dana zaΙa mana ni dake domin muyi rayuwar auren mu, kodai baki yaba da zaΙin nawa bane? kokuma baki amshi kyautar danayi miki bane?”
Ζara Ιaran idanunta ta Ιago ta sauΖesu akan nasa idanun, kanta ta girgiza cikin sanyin murya tace ” Ba haka nake nufi ba, kuma nayarda da duk inda kazaΙamin zanyi rayuwa aciki, kayi haΖuri idan maganata ta Ιata maka rai ban…..”
“Shiiiiii” ya katseta ta hanyar Ιaura hanunsa akan laΙΙanta, jawota jikinsa yayi , haΙe da sanya yatsarsa yashiga zagaye Ιan Ζaramin bakinta,, Ζasa tayi da’idanunta domin kuwa bazata iya jure kallon cikin idanunsa ba, sake matso da fuskarsa yayi daf da tata har numfashinsu na’iya gauraya waje guda, yayinda dogon hancinsa ke gogan nata hancin, atare suka lumshe idanunsu, ahankali laΙΙansa suka sauΖa akan nata laΙΙan, baikai ga soma yin kissing Ιinta ba Ζaran wayarsa ta karaΙe cikin kunnuwansu, da sauri ya sake ta,haΙe da sanya hanu acikin aljihunsa ya ciro wayarsa dake ta faman Ζara, katse Ζiran yayi haΙe da kashe wayar baki Ιayanta ya kuma maidata cikin aljihun rigansa.
Hannayenta dake cikin nasa hanun ya murza haΙe da Ιanyin Ζasa da murya “Kibani aron 1 hour inaso in Ιan fita”
Batasan lokacin da ta Ιago kanta ta kallesa ba, mamaki ya bata wai ta basa aron 1 hour shida Ζafarsa ae bazata Ιaure saba,
Baijirayi abun da zatace ba yakama hanunta suka fice daga cikin Ιakin, direct asalin falonsu suka dawo, matsawa kusa da’ita yayi ya manna mata kiss akan goshinta, haΙe da cewa “Sainadawo” adawo lapia tayi masa cike da kunyar sunbatar da yayi mata agoshinta,, tanajin tashin motarsa ta sauΖe ajiyar zuciya haΙe da zama akan kujera tamaida hankalinta ga tv, a zuciyarta kuwa hamdala take da Allah yasa bai sumbaceta Ιazu ba, itakam matuΖar kunyarsa takeji, sosai yakeyi mata kwarjini acikin idanunta…..
***
*GERMANY*
Tunda suka iso cikin Ζasar suka kuma sauΖa ababban asibitin dake cikin birnin Germany Ιin Zaid bai buΙe idanunsa ba, duk da kuwa irin kulawan da Ζwararrun likitotin asibiti’n suka basa, bawai baya cikin hayyacinsa bane, sarai yana a cikin hayyacinsa, Ζunci da kuma tarin damuwa me tsanani ne suka hanasa buΙe idanunsa, baison ya buΙe idanunsa kunnuwansa su jiye masa labarin cewa anΙaura auren Zahrah, baya buΖatar yin tozali da fuskar kowa acikin duniyar nan idan ba fuskar Zahrah ba,, yagama yarda da hukuncin da zuciyarsa ta yanke masa, lallai kwanciyarsa haka baida wani amfani, yakamata ne yatashi yayi yaΖi don samo soyayyar Zahrah, idan har bai manta da date Ιin daya gani ajikin katin auren ba, to jiya ne Ιaurin aurenta, wasu irin hawaye masu zafin gaske ne suka silalo daga cikin idanunsa haΙe da gangarowa tagefen kumatunsa,, a hankali ya ware idanunsa da suka jima da rikiΙewa suka zama jajur dasu, baya tunanin zaisake samun farinciki acikin rayuwarsa matuΖar yarasa abar Ζaunarsa Zahrah, tashi yayi zaune haΙe da rumtse idanunsa, Ζuna yakeji acikin Ζirjinsa sai dai kuma zafin wannan Ζunan baikai zafin Ζunan da soyayyar Zahrah keyi masa azuciyarsa ba,,, Alhaji Ma’aruf dake tsaye a wajen Ιakin da Zaid Ιin ke kwance, ta cikin makeken glass Ιin daya zamewa Ιakin window ya hango Zaid ya tashi zaune, da sauri yaje ya Ζira Doctor domin kuwa tunda suka zo Zaid Ιin bai motsaba sai yanzu,, Ζa’idansu ne idan zasu duba marar lafiya babu wani me shiga kansu harsai sun ga babu wani matsala sannan zasu bar Ζ΄an uwansa suje kansa,, hakan yasa dole Alhaji Ma’aruf ya dakata daga waje likitan shi kaΙai ya shiga.. Bayan kamar wasu mintuna likitan yafito yabawa Alhaji Ma’aruf daman ganin Zaid Ιin, ae ba’iya Alhaji Ma’aruf kaΙai ba hadda Mum suka rankaya zuwa cikin Ιakin,, har gabansa dukansu suka Ζarasa, hanu Alhaji Ma’aruf ya Ιaura akan kafaΙan Zaid haΙe da cewa “Ya Ζarfin jikin naka?”
Bai amsa musu ba saima kallonsu daya shiga yi kamar wani wawa…
“Ina Zahrah?” shine abun daya iya fitowa daga cikin bakinsa kawai, saboda shine abun dake cikin zuciyarsa..
Kallon Kallo Alhaji Ma’aruf da Mum suka shiga yiwa juna, sukam dai basuda wani amsa da za su bashi domin kuwa sarai labarin Auren Zahrah ya isa ga kunnensu, yanzu haka itaΙin matar wani ce, babu amfanin Ιago zancenta…
Alhaji Ma’aruf ne yayi ta maza haΙe da sauΖe ajiyar zuciya cike da lallashi yakuma dafa kafaΙun Ιan nasa ” Yanzu ba lokacin damuwa bane Zaid, bakuma lokacin daza ka sa kanka acikin Ζunci bane, kabar maganan Zahrah, yanzu samun lafiyarka yafi komai a wajen mu, idan kasamu lafiya sai ayi abun daya dace amma maganar Zahrah abarshi” Alhaji Ma’aruf yaΖare maganar cikin kwantar da murya.
LaΙΙansa ya cije haΙe da girgiza kansa
” Bazan taΙa samun nutsuwa da salama ba Dad har sai Zahrah tazamo tawa, Inasonta Dad, so ba irin na wasa ba, samunta ayanzu yafiyemin komai, taΙa kaji Dad, zuciyata takusa bugawa akan soyayyarta, ba irin bugawan da kasani ba Dad, Bugawa zatayi tayanda bazata sake aiki ba har abada kuwa!” Zaid yaΖare maganar yana me Ιaura hanun Dad Ιinsa akan Ζirjinsa dai dai saitin da zuciyarsa take….
“Baka da hankaline Zaid? ka kosan mekake cewa? wani irin mahaukaciyar soyayya ce wannan? anya kuwa Zaid baka zautu akan wannan banzar soyayyarba?” Mum ta tambayesa cikin yanayi na Ιacin rai, sosai abun nasa yanzu yake sosa mata rai..
“Mutuwa zanyi Mum akan Zahrah zan iyayin komai wallahi dagaske ni mahaukacine akan soyayyarta inason….”
“Kanasonta ko, shikenan tunda baka gujewa saΙon Allah saikaci gaba da sonta idan zaka sameta, domin kuwa yanzu ta riga da tayi maka nisa, saboda matar wani ce!” Mum tafaΙi haka ta hanyar katsesa daga maganar dayake…
Tamkar sauΖar guduma aka haka yaji sauΖan maganganun mahaifiyartasa acikin kunnuwansa,, kallonsa yamayar ga Dad Ιinsa,, kai Alhaji Ma’aruf ya jinjina masa alamar kalaman mahaifiyarsa gaskiya ne..
“Zahrah zata dawo gareka idan har Allah ya rubuta cewa itaΙin matarkace, amma yanzu kacireta acikin zuciyarka, saboda ahalin yanzu Zahrah tajima da zama mallakin wani, kasani kuma tunata da kuma cigaba da sonta zai iya jefaka cikin halaka” Dad yafaΙi haka ga Ιannasa cikin tsananin tausayawa…2
Dafe Ζirjinsa yayi da sauri haΙe da cije laΙΙansa, da Ζyar ya’iya motsa laΙΙansa aniyarsa yafurta wata kalma, sai kuma labari yasha banban, tarine ya sarΖesa, take jini yasoma fitowa daga cikin bakinsa, ΖoΖarin riΖesa Dad yasomayi amma kuma kafun yakai ga riΖesa tuni yafaΙo daga kan gadon, Mum kuwa tuni tafice aΙakin taje taΖira Doctor’s,, kafun Doctors Ιinma suzo tuni Zaid yayi mugun fita acikin hayyacinsa, gaba Ιaya jini ya Ιata gaban rigar dake jikinsa, idanunsa ne suka juye wani irin numfashi yaja me sauti, saikuma komai na jikinsa yasake alokaci guda, daidai lokacin Likitoti suka Ζaraso cikin Ιakin …. Taimakon gaggawa suka shiga bashi don ceto rayuwarsa cikin ikon Allah kuwa suka samu numfashinsa ya dai-dai ta, allurai suka narka masa wanda zasu sanyasa bacci…
Babban likitan dake kula da al’amuran Zaid Ιinne, ya rufe Dad da faΙa akan wai saboda me yasa aka faΙawa Zaid Ιin maganar da zata tada masa da hankali, haΖuri Dad yashiga bawa Doctor Ιin, sharuΙa masu tsauri Doctor ya shumfuΙa musu, akan cewa lallai dole babu wanda zai sake ganawa da Zaid Ιin harsai bayan kwana uku, sannan kuma koda sunkoma gida yazama dole akiyaye shiga damuwa dakuma Ιacin ransa, saboda yanzu zuciyarsa tazama kamar wani Ιanyen Ζwai sai anayi ana lallaΙata, zuwa yanzu abu kaΙan ne zai sanya ta buga, wanda hakan kuwa dai dai yake da rasa rayuwar Zaid Ιin baki Ιaya
***
Bayan awanni 4
ShikaΙai yasan irin raΙaΙi dakuma ciwon dake kwance acikin zuciyarsa, hawayene suke ta fita daga cikin idanunsa suna gangara akan Ζuncinsa,, “Da gaskene Zahrah’n sa tayi aure? me yasa Zahrah zatayi masa haka? Bazai taΙa iya jurwa ba, lallai koda Zahrah tayi aure bazai taΙa daina sonta ba, kuma koda duka mutanen duniya zasu taru akansa bazai sanja Ζudurin dake zuciyarsa na auren Zahrah ba, zaiyi duk wani abu wanda yasan Zahrah zata dawo garesa koda kuwa hakan zaijawo sanadiyar rasa rayuka ne, ZAHRAH kawai yasani kuma itace cikar burinsa”….. (?karya kasheni nima?♀?♀)
*NIGERIA*+
Tunda Doctor yafita baisake dawowa cikin gidanba harkuwa Zahrah ta Ζaraci zamanta acikin falon ta koma uwar Ιaka, sai dai kuma yayi mata waya yasanar mata cewa yana gidan Hajiyarsa wani uzuri ne ya riΖesa…
***
Idar da sallan isha Ιinta kenan ta miΖe haΙe da Ζarasawa gaban dressing mirror, lotion Ιinta me Ζamshi ta shafa ajikinta, powder kawai ta shafa akan fuskarta sai kuma man leΙe… Wata rubber pencil gown maroon colour ta sanya ajikinta, rigace irin marar nauyi Ιinnan sannan kuma an cika gabanta da fararen duwatsu wato (stones) wani maroon Ιin mayafi me Ιan kauri ta Ιauka haΙe da kafa Ιaurin Ιan kwalin nan na turban akanta, sosai tayi kyau saikace wata balarabiya, zama tayi akan gado haΙe da jawo wayarta, ajiyar zuciya ta sauΖe, har cikin ranta tana mamaki Ζwarai na rashin dawowan Dr.Sadeeq, tun safe daya fita haryanzu baidawo ba,, tashi tayi ta rage gudun ac’n dake cikin Ιakin, haΙe da Ιaukar wayarta tafice zuwa falo, hankalinta gaba Ιaya ta maida kan tashan MBC Bollywood da suke haska film Ιin nan me suna SANAM TERI KASAM bata taΙa kallon film Ιin ba amma kuma tana da waΖoΖin film Ιin acikin wayarta saboda sosai waΖoΖin sukeyi mata daΙi,, ta shagala a kallon film Ιin har idanunta sunfara kawo Ζwalla saboda tausayi, jitayi ansanya hanu anrufe idanunta , a razane ta Ζwalla Ζara domin kuwa sam bataji motsin shigowan mutum cikin falon ba, da sauri tature wanda yarufe mata idanun gefe haΙe da tashi tsaye,, ganin cewa shine yasanya tashiga sauΖe ajiyar zuciya akai akai,, murmushi yasakamar mata haΙe da cewa
“Matsoraciya”
Zama yayi akan kujera,, itama zama tayi tana me da numfashi sosai yatsorata ta donkuwa bata tsammata cewa shi bane sam ta manta ma da cewa babu mayafi ajikinta… Kafeta da’idanunsa yayi yana me Ζarewa kwalliyartata kallo,, sai alokacin ta ankara da irin kallon dayake jifanta dashi.
“Sannu da dawowa!” tafaΙi haka cikin sassanyar murya.
“Yauwa, kimin afuwa najima da yawa” yafaΙi haka yana me sanya hanunsa ya kama kunnensa alamar yana neman afuwa, murmushi kawai tayi masa haΙe dayin Ζasa dakanta…
MiΖewa tsaye yayi haΙe da cewa “Bari naje nayi wanka, akwai kayan fruit acikin fridge please kiΙan yanka min kafun na fito”
“To” kawai tace dashi haΙe da tashi tanufi wajen fridge Ιin shikuma direct ya wuce Ιaki donyin wanka…
Tana kammala yanka fruit Ιin ta Ιauko wani plate me kyau tarufe yankakken fruit Ιin, kan kujera ta koma ta zauna haΙe da sake maida hankalinta ga tv.. Sanye da tree guater jeans ajikinsa haΙi da wata farar t-shirt ya fito, Ζamshi kawai yake fitarwa, satan kallonsa Zahrah tayi haΙe da Ιan sakin murmushi, bata taΙa ganinsa acikin irin wannan shigar ba amma kuma yayi mata kyau sosai.. Akan lallausan carpet Ιin dake malale tsakiyar falon ya zauna haΙe da tanΖwashe Ζafafunsa, alama yayi mata da hanunsa cewa ta miΖo masa fruit Ιin, Ιaukan plate Ιin tayi taΖarasa gabansa, durΖusawa tayi har Ζasa kana ta aje plate Ιin,, “MiΖomin wancan ledan” yafaΙi haka yana meyi mata nuni da leda wanda shiya shigo dashi sam ita batama lura ba,, cike da nutsuwa taΙauko ledan kamar yanda ya umarceta Ιan duΖawa tayi haΙe da miΖa masa ledan,, amaimakon yakarΙi ledan sai taga ya jawota jikinsa, zaunar da ita yayi acikin jikinsa haΙe da sanya hanu ya zame Ιaurin turban Ιin dake kanta, take lallausan gashinta ya zubo harzuwa kan bayanta, kansa ya cusa acikin gashin nata yana me shaΖan daddaΙan Ζamshin dake tashi ajikin gashin nata,, “Kiyi mini afuwa my princess, banΖi dawowa haka kawai ba!” yafaΙi haka yana me Ζara matseta acikin jikinsa.
STORY CONTINUES BELOW
“Ni bakayi mini laifi ba sam sam, nasan ae bazaka Ζi dawowa haka kawai ba” tafaΙi haka cikin zazzaΖan muryarta..
“Yauwa my wife nasanki dama kina da haΖuri, natsaya a wajen Ζ΄ar uwarki Salima ne, ina fatan banyi laifi ba?”
Da sauri tajuyo da kanta tana kallonsa, “Salima kuma? bakace tafasa aurenka ba” tatambayeshi fuskarta Ιauke da tsananin mamakin jin abundayace..
Dariya yayi ganin yanda tawani zaro idanu kishi ya bayyana akan fuskarta Ζarara daga ambatan sunan Salima.
“Wasa fa nake miki Madam, miye na wani tsorita haka” yafaΙi haka yana me Ζarewa kyakkyawar fuskarta kallo..
ΖaΖΖarfan ajiyar zuciya ta sauΖe haΙe da Ιata fuska, ta juya da kanta batace dashi komai ba,, sarai ya lura taji haushi,,, yankakken apple ya Ιauka haΙe da kaiwa kusa da bakinta.. Ζin buΙe bakinta tayi saima daΙa kauda kanta da takeyi jefa apple Ιin yayi cikin bakinsa, haΙe da sanya hanu ya juyo da kanta yazama tana fuskantarsa…
“Fushi kike da mijinki? kiyi haΖuri banfaΙi haka don ranki ya Ιaci ba, wasa nake miki kiyi mini murmushi kinji Zahrah na!”
Hakanan taji zuciyarta tayi sanyi harbatasan sanda tasaki murmushi ba.. Yankakken apple yakuma Ιaukowa yakai bakinta babu musu ta buΙe bakinta yasanya mata… Tana zaune acikin jikinsa haka yaciyar da’ita domin kuwa atare sukasha fruit Ιin haΙe da Ιaura fresh milk akai.. Yana nan azaune ta tattare wajen takai kitchine haΙe da dawowa, miΖewa tsaye yayi haΙe da Ζarasawa gaban tv wanda yaketa ΙaΙatu shikaΙai ya kashe, kallonta yayi kamar zaiyi magana saikuma ya fasa, wutan falon ya kashe kana yakama hanunta suka nufi Ιaki, hmmm tun Ιazu bata ji tsoro ba sai yanzu da ta gansu sun hallara acikin bedroom, janta yayi har cikin bathroom sukayi brush… Da kansa yaciro wani Ζ΄ar fingilar rigan bacci wanda take shara shara kamar rariyan tata sai dai kuma tana da ado ata wajen wuyan.. Ganin yanufota kai tsaye ne yasanya tayi saurin saddakanta Ζasa, zuciyarta kuwa luguden duka tashiga yi mata, kamar anka mata tana sata, harga Allah ita tsoronshi take Allah yasa yauma karyayi mata komai.. Tunaninta ne ya katse sakamakon sauΖar hanunsa da taji abayanta, matsowa yayi gaf da’ita harsuna iya jiyo hucin numfashin junansu,, ahankali yayi Ζasa da zip Ιin rigar nata, lokaci guda yasanya hanu ya soma zame rigar daga kafaΙunta, rumtse idanunta tayi Ζam, haΙe da takure jikinta waje Ιaya, bazata iya hanasa ba, amma kuma dazai barta yace ta cire rigan da kanta da hakan yafiye mata komai daΙi, saboda ko bakomai zatayi iyaka ΖoΖari wajen ganin ta kare Ζirjinta, lokacin daya kawo Ζirjinta kasa jurewa tayi, dasauri ta duΖa Ζasa haΙe da cewa “Dan Allah kabarni naje toilet na cire da kaina”
Bai tanka mata ba saima Ιagota daya sakeyi tsaye, rungumeta yayi ta baya haΙe da Ιaura kansa akan wuyanta, hancinsa yasanya yashiga shaΖan daddaΙan Ζamshin da fatarta ke fitarwa, ahankali yake goga mata lallausan sajen sa akan fatar wuyanta yayinda yasanya hununsa duka biyu ya saΖalo Ζugunta, rumtse idanunta kawai tayi tanajinsa, yayinda zuciyarta kuwa ta ke bugawa da sauri. a hankali yashiga kissing Ιin wuyanta haΙe da soma yawo da hanunsa akan cikinta, wani iri Zahrah tasomaji acikin jikinta, yayinda gaba Ιaya tsikar jikinta ya shiga motsawa,, shi Ιin ma hakance ta kasance dashi, baisan sanda yasanya hanunsa yaci gaba da ΖoΖarin zame mata rigar dake jikinta ba,, har rigan tafaΙi Ζasa Zahrah bata ΙuΙe idanunta ba shima kuma baibuΙe nasa idanun ba, hanunsa yasanya akan lallausan fatar cikinta yashiga shafawa, cikin wani irin salo ya juyo da’ita yazamana suna fuskantar juna, dayake Ιakin babu wadataccen haske sosai, hakan yasanya baya iya ganin jikinta sosai, hanunsa yasanya duka biyu ya tallafi bayanta haΙe da kusanto da fuskarsa daf da tata, laΙΙansa yaΙaura akan nata laΙΙan tare da kama leΙenta na Ζasa yashiga tsotsa ahankali,, al’amarin dayayi mugun sanya mata shock acikin jikinta kenan, tunda take aduniyarta wani Ιa namiji baitaΙayi mata kiss ba sai Zaid, shiΙin ma kuma alokacin dayayi kissing Ιinta bata cikin nutsuwa da kuma hankalinta saboda haka babu wani abu da taji game da hakan, Dr.Sadeeq ma hakane takasance dashi saboda a iya tsawon tarihin rayuwarsa baitaΙa yiwa wata mace kiss ba, yau shine karonsa na farko… Ahankali yake shan lips Ιin nata yayinda ita kuma takasa koda ΖwaΖΖwaran motsi ne,, cikin wani irin salo ya soma tura bakinsa cikin nata bakin, harshenta ya laluΙo haΙe da soma yi masa shan lollypop,,, cikin mintunan da basu wuce 8 ba yasoma sauΖe wani irin numfashi, haΙe da sake ΖamΖameta acikin jikinsa, sosai yake kissing Ιinta yana fitar da wani irin numfashi me Ιauke da wani kalan sauti, yayinda itakuwa Zahrah Ζafafunta suka soma ΖoΖarin rugujewa ma’ana suka soma saΖewa da’alama dai abun yafi Ζarfinta,, Ιaukanta yayi caΙak yanufi kan gado da’ita, kwantar da’ita yayi haΙe da sake sanya bakinsa acikin nata,, haΙuwar fatar jikinsu waje Ιaya shiya matuΖar taimakawa kiss Ιin nasu yaΖara armashi a wajen Doctor, dan Zahrah kam tuni tazama statue.. A iya kiss kaΙai Dr.Sadeeq ya ruΙe yakuma sukurkuce, sucking tongue Ιinta kawai yake cike da nutsuwa yana me fidda wani irin numfashi, tuni idanunsa sunkaΙa sunyi jajur dasu, Ζasa yasomayi dakansa harzuwa kan cikinta, kissing Ιinka yashigayi akan cikin nata yana me shafa santala santalan cinyoyinta, hanunsa yasanya abayanta ya Ιalle maΙallin brezian dake jikinta, haba ai tuni hajiya Zahrah ta ruΙe ta sake ΖanΖame jikinta, saida yasamu shiΙewa haΙe da Ιaukewar numfashi alokacin da hanunsa suka sauΖa akan lallausan breast Ιinta wanda suke a tsaye Ζyam babu alamar kwanciya atattare dasu, bakinta yaΖara kamowa yacigaba da tsotsa yayinda yasanya hanunsa yana murza breast Ιinta ahankali, gaba Ιaya ya zauce ya ruΙe yakuma susuce yafita aduniyar mu yashiga wata duniya me cike da wani irin masifaffen sha’awa me matuΖar Ζarfi harji yake kansa nawani irin sarawa,, kuka ta fashe dashi me tsanani alokacin da taji sauΖar bakinsa akan nipple Ιinta, hmmm kukanta bazaiyi aiki ba da dukkan alamu, domin kuwa tsotsar dayakeyimawa nipple Ιin nata ma na dabanne,, da Ζyarma yake iya Ζwato numfashinsa,, duk yanda yaso ya share kukan nata yakasa, dolensa ya tsagaita haΙe da kwanciya akanta, cikin wata irin murya da take a shaΖe yace “Please Zahrah stop craying!” ae kamar cewa yayi ma taΖara volume Ιin kukan nata, kansa dake matuΖar yi masa ciwo ya dafa, haΙe da cije laΙΙansa, wallahi bazai iya jurewa ba komai zai iya faruwa dashi, yakai Ζololuwar sha’awa matuΖa, amma kuma yazaiyi da kukan da Zahrah takeyi masa yanajin tausayinta sosai, yasan ahalin yanzu metake tunawa, wancan mummunar ranan take tunawa, amma kuma haΖΖinsa ne ya mantar da ita komai. (Khair anya ruwanki bazaiyi tafasan banza ba kuwa? naga mutumiyar taki tana neman hana doctor walwala?) Sake matseta ajikinsa yayi haΙi da haΙe bakinsu waje Ιaya, sauya salon kiss Ιin nasa yayi, wanda hakan ya tilasta mata dole tayi shiru, sai dai haryanzu jikinta bai daina Ιari ba, idan tace gangar jiki da ruhinta basa karΙan saΖon Dr.Sadeeq tayi Ζarya, amma kuma matuΖar tsoro takeji, ΖwaΖwalwarta azabar da Zaid yajiyar da’ita take tariyo mata, gani take shikenan itakam tata ta Ζare dan kuwa bazata iya jure azaba biyu ba,, salon romance Ιin da Doctor keyi mata yawuce gaban kwatance burinsa shine ya mantar da’ita wannan tsoron, ita kanta ta yarda da cewa saΖonninsa sun ratsata domin kuwa tuni ta gama jiΖewa to amma abun tsoron na gaba,, bai Ιauke bakinsa acikin nata ba haryagama ratsa cikin jikinta, wani irin wawiyar ajiyar zuciya ya sauΖe haΙe da sakin wani irin Ζ΄ar Ζaraman Ζara dake nuna alaman cewa mutum yagama lulawa cikin duniyar da babu irinta,, baisan dayaushe yazare bakinsa acikin nata ba, wani irin Ζara ta sake haΙe da soma rusa kuka kamar wanda ake zarewa rai…..*** Bayajinta balle kuma ganinta saboda idanuwansa rufewa sukayi ruf, duk kuka da ihun da takeyi baisan tanayinsu ba, wallahi shikam tunda yake baitaΙa sanin menene daΙi ba aduniya sai awannan lokacin, bazai taΙa iya misalta abun dayaji ba abun yafi Ζarfin tunaninsa ya shammaci hankalinsa, harya manta da cewa ita Ιin ba budurwa bace, baitaΙa kusantar wata mace ba Zahrah itace ta farko, kuma amatuΖar kame yajita gam, sai dai kuma fa har’abada baza’a haΙa virgin da kuma wacce ba virgin ba dole akwai banbanci amma shidai baiji banbancin ba saboda dama baisan kowaba sai ita*** Doctor ya hole iya holewa yayi gurnanin yayi sambatun harsau ba’adadi yayinda Ζ΄ar mutane kuwa tayi kuka kamar ranta zaifita harsaida idanunta suka kumbura alokaci guda kanta kuwa ba’a magana wajen yi mata ciwo..
***
After 1 hour.
Shikansa jikinsa zafi zau ya Ιauka yayinda yaji gaba Ιaya duniyar tana juya masa, to inaga kuma wacce ya bawa kaya, da Ζyar ya’iya kwantawa agefenta haΙe da jawota cikin jikinsa, baisan da wani kalma zaifara yi mata magana ba, kyakkyawan sumbata ya bata akan goshinta haΙe da rumtse idanunsa, wanda suke zubar da hawayen tsananin tausayinta,,, kusan 12 minute yana rungume da’ita acikin Ζirjinsa “Me daΙi na!” yafaΙi haka acikin kunnenta da’alama dai sunan daya bata kenan,lol. Zahrah da’idanunta sukayi luhu suna ta tsiyayar da hawaye kasa cedashi komai tayi.. (Su Me daΙi ansha wuya???)
“I’am so sorry, banyi haka don nacutar dake ba, nakasa control Ιin kainane, Inasonki Zahrah, a iya daren yau soyayyarki ta sake ninkuwa acikin zuciyata, kiyafemin kinji me daΙi na bazan Ζara ba, please for give me!” yaΖare maganar cikin kwantar da murya, da’alama dai har yanzu giyar daΙin baigama sake shiba… Me daΙi dai taΖi cewa komai haka ya sauΖo daga kan gadon rungume da’ita kamar wata Ζ΄ar baby, direct bathroom yanufa da’ita, dakansa ya haΙa mata ruwan Ιumi haΙe da zaunar da’ita aciki, duk da cewa ita ba virgin bace amma kuma wannan Ιin ma kusan daidai yake dayinta na farko, saboda ta matuΖar shan azaba sosai, hakan yafarune kuma saboda yanda Hajiya Shuwa ta dinga Ιurka mata magungunan matsi dakuma na ciko da mace, sosai taji zafi aΖasanta lokacin da yazaunar da’ita acikin ruwan amma kuma yazatayi yazama dole ta daure.. Dakansa yayi mata wanka haΙe da naΙota acikin towel like wata Ζ΄ar Ζaraman baby, shima wanka yayi kana yafito daga cikin bathroom Ιin, shidakansa ya sanya mata rigan bacci, shima ya jallabiya ya sanya ajikinsa, haryanzu Zahrah bata daina tsiyayar da hawayeba,, new blanket yasanya musu domin kuwa wancan ya Ιaci da sperm Ιin me…. au ?Zahrah,, jawota yayi jikinsa haΙe da rungumeta tsam tsam jiyake kamar wani zaizo ya Ζwace masa ita (wai inji nuru ba kama bane Zaid yananan tafe? niko nace yayi Ζarya)
Hawayen da suketa ambaliyan sauΖa akan fuskarta yashiga share mata, haΙe da Ιare wani sweet yajefa acikin bakinsa, kwantar da’ita yayi akan Ζirjinsa haΙe da Ιago fuskarta ya tura mata sweet Ιin acikin bakinta, harshensa yasanya yana meyi mata wasa da sweet Ιin acikin bakinta, lumshe idanunta tayi tana me sauΖe ajiyar zuciya, yayinda yake shafa mata bayanta ahankali,,har wani irin nannauyan bacci yazo ya Ιauketa….. Kafeta yayi da idanunsa aransa yana me godia ga Allah daya basa wannan mata me Ιauke da tarin ni’imomi na fili dana baΙini, kai yasha sweet fa yau harwani jin kansa yake a sama.Lol,,, batare da yayi aune ba shima bacci ya Ιaukesa bayan yayi musu addu’a yashafa mata… Good night angon me daΙi…Tun da ta tashi tayi sallan asuba take ta ruskar kuka tamkar wacce aka cewa wani nata ya mutu, ita kanta batasan kukan me takeyi ba, amma dai hakanan takeji zuciyarta babu daΙi, gashi gaba Ιaya jikinta ciwo yake, “Gaskiya Doctor mugune.” tafaΙi haka acikin zuciyarta, gaba Ιaya ya gajiyar da ita, daga Ζasan zuciyarta kuwa wani abune yayi mata tsaye wanda kuma shine sanadiyar kukan nata, wannan wace irin rayuwa ce? wace irin Ζaddara ce wannan? rabonta da tayi farinci me tsayi tun kafun Zaid yashigo cikin rayuwarta, ada tana ganin rayuwar da takeyi acikin gidansu rayuwar Ζunci ce, ashe bata sani ba wannan rayuwar salama ce a gareta, SO baiyi mata adalci ba, so bai kyautawa rayuwarta ba…2
Yajima tsaye akanta yana me Ζare mata kallo, mamakin yanda take kuka tsakaninta da Allah yake, a iya saninsa banda abun daya wakana atsakaninsu daren jiya baiyi mata komai ba, amma kuma sai gashi yanzu tana ruskar kuka, har a Ζasan zuciyarsa bayason kukanta, idan yaji kukanta jiyake gaba Ιaya nutsuwarsa ya Ζaura daga jikinsa,, ahankali yashiga takawa harzuwa inda take duΖe akusa da gado tana kuka, sam batamasan da shigowarsa ba kukanta kawai takeyi…. Hanunsa yasanya ya dafa kafaΙanta, da sauri ta juyo aΙan razane don bataji shigowarsa ba,, idanunsa ya ΖanΖance haΙe da waresu alokaci guda, zama yayi akan gado haΙe da Ιagota zuwa jikinsa…1
“Me yasa Zahrah? me nayi miki? meyasa kike Ζuntatawa rayuwarki akan wani dalili naki? ban aureki don nazuba miki ido kita cutar da kanki ba, please ki daure zuciyarki kidaina wannan kukan banaso!” ya faΙi maganar cikin lallashi… Saurin Ιauke hanunsa dake kan wuyanta yayi, kansa yaΙan Ιafe haΙe da zaunar da ita akan gado, direct wani Ιan madaidaicin drawer yanufa, maganin da yasan zai sauΖar mata da zazzaΙi acikin mintuna Ζalilan ya Ιauko tare da ruwan gora ya dawo zuwa gareta. Maganin ya Ιalla ahanunsa tare da jawota jikinsa, bakinta ya buΙe ya jefa maganin aciki haΙe da bata ruwa, babu musu ta haΙiye maganin bayan ta rumtse idanunta, sai kace wacce aka bawa guba… Aje goran ruwan yayi haΙe da sake jawota jikinsa, kwantar da kanta yayi akan Ζirjinsa, yayinda yake shafa bayanta a hankali. Ajiyar zuciya haΙi da sheshsheΖan kuka kawai take sauΖewa. Shikuwa Dr.Sadeeq wani tunani na daban yakeyi acikin zuciyarsa, hakanan Allah ya halittamasa tsananin tausayin Zahrah acikin zuciyarsa, yana sonta sosai, bayason yaga tana cikin damuwa, bayajin akwai wani abu aduniyar nan da Zahrah zata nema agaresa matuΖar yana dashi tarasa, zai iya mallaka mata komai nasa, matuΖar zataji daΙi, za kuma tayi farinciki, bakinsa ya kawo daf da kunnenta cikin murya me sanyi yace2
“Zahrah!”
Tanajinsa amma kuma saitayi sauri ta lumshe idanunta, tanaso ya Ιauka cewa bacci take.
Jin tayi shirune yasanya yashiga goga mata lallausan sajensa akan fatar wuyanta, yayinda yake yawo da hanunsa akan bayanta a hankali..
Luf tasakeyi acikin Ζirjinsa, tana jin saΖonsa yana tsarga mata hartafin Ζafarta, yayinda daddaΙan Ζamshin turarensa ke Ζara sanyaya mata jiki, batajin bacci ko kaΙan, amma kuma yazama dole ta ΖwaΖulowa kanta baccin dole, kodan ta samawa zuciyarta salama. “Ina laifin Dr.Sadeeq? mene bayi dashi wanda mace takeso tasamu ajikin Ιa namiji? miye laifin masoyin daya nuna maka haΖiΖanin so? ashe wani lokacin zuciya batasan menene halacci ba? me yasa SOYAYYA tazamo guguwa me hargitsa zuciyar Ιan adam tayi fatali da komai nasa?” itakam ko da a yanzu soyayya ta barta haka ta gama iya cutarta, cuta me muni ma kuwa.. Yajima yana shafa bayanta, harsai da ya ji sauΖar numfashin dake nuna cewa da gaske bacci ya Ιauketa. Kwantar da’ita yayi akan gado, haΙe da jawo blanket ya rufe mata duka jikinta, yasani sarai batason sanyi, don haka ya rage gudun A.C, kashe mata fitilan Ιakin yayi, kana ya jawo mata Ζofar ya rufe mata bayan yafita zuwa falo.. Laptop Ιinsa ya Ιauka haΙe da buΙewa, aikinsa ya shigayi cikin nutsuwa, Ιan kwana biyun nan da bai shiga office ba haryatara ayyuka masu yawa, gashi ansanar masa patients suna buΖatar taimakon sa, duk da ya Ιau hutu ma ashe bai tsira ba, ayyuka na nan akansa wanda yazamana dole sai shi zaiyisu…
***16
STORY CONTINUES BELOW
*GERMANY*
ShikaΙai yake rayuwarsa acikin Ιakin, yau kwanansa Ιaya kenan baisanya komai na abinci acikin saba, yayi matuΖar ramewa alokaci guda, yayinda gashi dakuma sajen dake kwance akan fuskarsa suka Ζara yawa fiye da na da, duk da dama cewa shi mutum ne me yalwan suma, kallo Ιaya zakayi mai kasan cewa yana Ιauke da damuwa me tarin yawa acikin zuciyarsa, Zaid Ιin da dana yanzu sun banbanta, wan can Zaid Ιin zuciyarsa cike take da isa, Ιagawa, girmankai, rashin sanin darajan Ιan adam, Zaid Ιin da mashayine, mazinaci, wanda bai Ιauki zina abakin komai ba, haka kuma Zaid Ιin da, baisan menene damuwa ba, baisan menene rashi ba, samu kawai ya sani, sannan kuma baisan menene Ζunci da Ιaci ba, baikuma san menene wani abu waishi soyayya ba. Zaid Ιin daya kasance yanzu kuwa, wani mutum ne dayake cikin Ζunci, zuciyarsa tana cike da tarin damuwa, Zaid Ιin yanzu yarasa duk wani farincikinsa, yarasa jin daΙi, yarasa nutsuwar zuciya data ΖwaΖwalwa. “ko wannan baici yasa Zahrah ta tausaya masa ba? shin wai shi kaΙaine yataΙa aikata abun da baidace ba?” yatambayi kansa, abu biyune suke damunsa, zazzafar soyayya dakuma rashin nutsuwa da salama dake damunsa, yanzu shikaΙai yasan halin dayake ciki, baya iya bacci, baya iya cin abinci, bayajin daΙin komai nasa, gaba Ιaya duhu ya mamaye rayuwarsa, yanzu yafara zargin cewa zunubansa ma sunyi masa yawa, yasani Ζwarai, yasan abu me kyau da kuma marar kyau, amma saboda ruΙin duniya gaba Ιaya ya shagala. (Yawancin mutane yanzu rayuwarsu sukeyi saka ka, zasu aikata zina, zasu sha giya, zasu aikata duk wasu aiki dake jawo musu manya manyan zunubai, amma kuma yawancinsu sunfi gudun kunyar duniya data lahira, suna tsoron wani yakamasu suna aikata zina, amma basa tsoron kallonsu da Allah yakeyi, wasu sun maida zina manshafawarsu, suna ganin kamar hakan wayewace, bayan kuma suna sane dacewa aikata ta babban halaka ne, Ya ALLAH kaci gaba da karemu, kakuma tsaremu da sharrin zina, ka rabamu da zama da mazinata, Ameen Ya ALLAH!)4
Yariga daya gama yanke hukunci cewa ko da su Dad Ιinsa basaso saiya koma Nigeria, bazai iya zama anan ba, zafi yakeji acikin zuciyarsa marar misaltuwa idan haryatuna da cewa Zahrah’nsa tana can gidan wani, sai yaji gaba Ιaya nutsuwarsa ta gushe, wataΖila ma wannan banzan Doctor Ιin ya kusanci Zahrah’nsa, ae kuwa baisan sanda ya Ζwalla wata irin Ζara ba, azuciye ya Ιauki wani flower dake gefen gadon, yayi jifa dashi, take kwalbar flower’n ya tarwatse a tsakiyar Ιakin, duk da haka hakan baiyi masa ba, saida yataka ya Ζarasa gaban mirror, da hanunsa ya daki mirror Ιin, take mirror’n ya tarwatse har saida ya yanka masa hanu, amma saboda tsananin kishi’n dake cinsa, ko zafin ciwon baiji ba.
“Hakane ma, yakusanceta” wata zuciyartasa ta faΙa masa..1
“No!!! it will never happen, i Know Zahrah will not do it, bazata taΙa iya bawa wani kanta ba bayan ni, because she know we love each other” yafaΙi haka da Ζarfi cikin wata irin murya, me Ιauke da tsananin Ιacin rai, durΖushewa yayi a Ζasa haΙe da sanya hanu ya dafe saitin zuciyarsa wacce take bugawa da sauri, da dukkan alamu dai ya tsokalowa kansa. Haki yasomayi tamkar wani wanda yayi gudu, tarine ya sarΖesa, take jini yasoma fitowa ta bakinsa, shi kaΙai yayi tarinsa harya Ζare, ya galabaita sosai da sosai, da Ζyar ya’iya jan jikinsa ya shiga toilet, wanke bakinsa yayi kana yafito daga cikin toilet Ιin, numfashi kawai yake maidawa cike da wahala,, wani Ιan abu yadanna, bayan kamar minti 1 saiga wata cleaner tashigo cikin Ιakin, nuni yayi mata da inda jininsa ya ΙaΙΙatata, babu Ιata lokaci ta sanya kayan aiki ta gyara wajen, tana kammala gyaran kuwa wasu likitoti su biyu suka shigo cikin Ιakin.. Duba lafiyar jikinsa suka sake yi haΙe da basa wasu magunguna, wata allura sukayi masa da take matuΖar sa bacci, domin kuwa gwaje gwajen da sukayi masa yasa sungano cewa baya samun wadataccen bacci.1
Suna fita ya lumshe idanunsa, wanda tuni suka zama jan gauta, saboda tsabar tsananin kishi dake cinsa, jiyake ma kamar idan ya Ζara kwana Ιaya ba acikin Nigeria ba ya cutu, gwamma yaje ya Ζwace Zahrah tunkan wanda ya Ιauka bakomai ba ya ΙanΙana masa zumarta. (Hahhh guy ae ka makaro,yasin doctor yajima da ΙanΙanawa?) **** Mintuna kaΙan dayi masa alluran, bacci me nauyi yayi gaba dashi…2
STORY CONTINUES BELOW
Dad ne ya nutsu haΙe da dawo da kallonsa ga Mummy. “Inaga abu Ιaya zamuyi masa yamanta da wannan yarinyar, kawai na yanke shawara aure zanyi masa.”
Shaye da mamaki Mummy take kallon Dad. “Aure fa kace Alhaji? wakake tunanin zata iya zama da Zaid, da irin wannan halinnasa? hmmm bana majin cewa Zaid zaiso wata mace bayan wannan Zahrah’n, ni nama fara tunanin cewa asirce masa zuciya tayi, amma inbanda haka taya lafiyayyen Ιa namiji kamar Zaid zai maΖalewa mace Ιaya kamar maye”
Murmushi Dad yayi haΙe da girgiza kansa, “itadai Safara’u haka take, idan ana magana me hankali saikuma tana sako wasu abubuwa kamar na wasa.” dad yafaΙi haka acikin zuciyarsa, afili kuwa gyara zamansa yayi haΙe da sake fuskantarta…
“A wannan karon dagaske aure zanyi masa, saboda aure ne kaΙai zaisanya Zaid dawowa cikin nutsuwarsa, bandamu da ko yanason matar ko baya sonta ba, nasan watarana ahankali zai sota ya manta da waccar”1
“To Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, amma gaskiya nima banjin daΙin ganinsa acikin wannan halin dayake ciki yanzu,ko abincin kirki wallahi bana iya ci” Mum tafaΙi haka cikin tausayawa Ιan nata….. (Team Zaid kunji fa wai aure za’ayi masa me zakuce? wayaga Zaid da auren dole)4
****
NIGERIA
Tunda ta kwanta bacci ba’ita ta tashi ba sai 11:30 am, ko tsayawa nemansa yau batayi ba tafaΙa bathroom, wanka tayi kana ta fito daga cikin bathroom Ιin… Mai kawai ta shafa kamar kullum sai kuma powder, itakam batason cika meckup akan fuskarta.
Riga da sket na atamfa tasanya, wanda yayi mata caras ajikinta, Ιan kwalin kayan kawai ta yafa akanta zuwa kafaΙarta. Direct falo ta nufa sai tashin Ζamshi take, kamar yanda tayi zaton zata ganshi a falo, sai taga saΙanin haka, domin kuwa babu shi babu alamarsa,, kallonta ta mayar kan dinning area saidai taga kan table Ιin wayam babu food flask ko Ιaya,, hahhh take idanunta sukayi raurau dasu, Ιan Ζaramin bakinta ta tunzuro haΙe da shafa cikinta, “Yanzu kenan Doctor da yunwa ya barta?” ta tambayi kanta…
Motsi ta soma ji daga Ιangaren kitchine, tsoro ne yaΙan kamata dan tasan Dr.Sadeeq da kansa kam bazai shiga kitchine ba, “to kodai basu kaΙai bane acikin gidan?” tasake tambayar kanta. Cikin sanΙa take takawa harta isa Ζofar kitchine Ιin, motsinne yasake tsananta, don haka cikin sanΙa ta tura kanta cikin kitchine Ιin.
“Kamata!!!” taji anfaΙa da Ζarfi. Wani irin Ζara ta Ζwalla haΙe da rugawa a guje ta koma cikin falo.. Dariya yashiga yi mata bayan yafito daga kitchine Ιin hanunsa riΖe da plate wanda yake Ιauke da soyayyen chips..
Zamewa tayi aΖasa haΙe da dafe Ζirjinta, nunfashi take fitarwa da Ζyar, da’alama ta tsorata sosai.
Zama yayi akan kujera har yanzu dariya yakeyi mata, yasan zata tsorata amma baiyi tunanin tsoron nata zai kai har haka ba.. “Yadai karfa ki sume min” yafaΙi haka yana me Ιan tsagaita dariyarsa…
Ζan Ζaramin bakinta ta tunzuro gaba haΙe da miΖe Ζafafunta akan sofa, “Nidai Allah ka tsoratar dani, please kada ka Ζara zan iya mutuwa fa!” taΖare maganar cikin tsantsar shagwaΙa.
“Kindai tsorata kanki, ni bani na tsorataki ba Ζ΄an mata, da wayace ki shigo kitchine Ιin cikin sanΙa?”
“To ba motsi naji ba, na Ιauka ko aljanine!” still cikin shagwaΙa takumayin maganar..
Kallonta kawai yashigayi yana murmushi, a garin gudu harta yada Ιan kwalin dake kanta bata sani ba, hakanne yabaiwa gashinta damar bayyana.
Jingina da kujera tayi, tana me sauΖe ajiyar zuciya, sai yanzu ta fara dawowa daidai.
Ζaurin abinci yasoma ji da sauri yatashi ya nufi kitchine, aikuwa yana zuwa ya tarar da soup Ιin daya Ιora akan wutane yasoma Ζonewa, da sauri ya sauΖe haΙe da ΖwaΙawa Zahrah Ζira..
STORY CONTINUES BELOW
SaΖare tayi tana kallon yanda yake kwashe soup Ιin Ζwai da albasa yana sanyawa acikin wata Ζ΄ar Ζaramar kula, dariya ne ya Ζwace mata, cikin dariyan tace “Doctor dama ka iya girki ne?”
Hararan wasa yayi mata haΙe da cewa “Na bugawa a jarida ma kuwa”
Dariya ta Ζara kwashewa dashi, wai iya girkinnasa har na bugawa a jarida ne hmm. Ζan matsowa tayi kusa dashi haΙe da leΖa tukunyar da akayi soup Ιin aciki, da sauri ta sanya hanu ta toshe bakinta, dariya ne yazo mata, gaba Ιaya cikin tukunyar yayi baΖi, soup Ιin yasoma Ζonewa..
“Miye wai kikewa dariya? yarinya zaki faΙa wa mutanen garinkune anjima, kin kuwasan daΙin girki na yafi na kowa ko” yaΖare maganar yana me ΖaΖalo Ζasan tukunyar daya Ζone zai zuba acikin kulan. Dasauri ta rike hanunsa haΙe da cewa “Idan kazuba wannan fa soup Ιinnan bazai ciwuba”
“Meyasa, ko hassada kikeminne?”
Yatambayeta yana me Ιage giransa Ιaya..
“Shikenan to, tunda kanaga kamar wasa nake ma, amma kuma idan kasa akan abincinka yayi Ιaci ni ba ruwana” tafaΙi haka tana me sake hanunsa.
Kallonta ya Ιanyi haΙe da marerece fuska. “Yazanyi to Zahrah, banaso kitashi kinajin yunwa banbaki abinci ba, shine na soyamiki chips yanzu kuma gashi nayi soup Ιin kince wai ya Ζone bazai ciwuba, ko zamuje resturant ne?” gaba Ιaya fuskarsa ta sauya da alama shagawaΙa yakeson yi mata..
Wani irin tausayinsa ne taji ya daki zuciyarta Allah sarki, ashe duk akantane yaketa shan wannan wahalan.. “A’a basai munje resturant ba, zan ma iyaci a haka fa ai ba duka soup Ιin bane ya Ζone, kuma ma basai muci da tea ba!” cikin yanayi na kulawa ta Ζare zancen..
Cikin jin daΙi yace “Yauwa tawan to Ιauki soup Ιin kije, bana haΙa mana tea ko”
“A’a kabarshi ni dakaina zan haΙa mana” tafaΙi haka tana me ΖoΖarin fara haΙa musu tea Ιin. Hanunta ya kama ya sumbata haΙe da Ιaukan kulan da soup Ιin ke ciki yanufi falo… Mintuna kaΙan tafito da Ιan wani tray wanda yake Ιauke da kofuna biyu na tea Ιinsu.. Aje tray Ιin tayi akan sofa haΙe da maida kallonsa gareta, gani tayi ya kafeta da idanunsa, wanda suke daΙa sawa tanajin nauyinsa..
Ζan shagwaΙe fuska tayi haΙe da cewa “To miye kake kallona!”
Murmushi yasakar mata haΙe da tasowa daga inda yake zaune, zama yayi akan sofan, dakansa ya zuba musu soup akan chips Ιin, loman farko Zahrah ta tauna wani Chips da bai gama soyuwa ba, kallonta yayi haΙe da cewa “Ya kikaji yayi daΙi ko? ai nasan ma zaiyi daΙi”
Murmushin dole tayi haΙe da cewa “Yayi daΙi sosai”
Hanu yasanya yashafi kumatunta, “Yauwa My Zahrah ae dama nasan saikin yaba”
Da Ζyar ta’iya danne dariyarta, loman farko da yayi ya Ιago kansa ya kalleta, itama kallonsa takeyi, saitaga ya Ιata fuska kamar zaiyi kuka, bazata iya riΖe dariyarta ba yanzu kam yazama dole saita dara, sake shagwaΙe fuska yayi ganin yanda takeyi masa dariya. Da Ζarfi yajawota jikinsa haΙe da murΙe mata hannayenta “Wakikewa dariya?”
Cikin dariya tace “Kayi haΖuri nifa badakai nake ba, dariyarce kawai tazomin”
“Uhhh aini ba yaro bane nasan ni kikewa dariya, to amma ai balaifi na bane laifin gas Ιinne da bai ratsa kaskon suyan da kyau ba, kuma ko kema ae nasan haka zaiyi miki”
Itadai dariya kawai takeyi masa, gaskiya wannan girkin nasa kam yacancanci abugasa a jarida kamar yanda ya faΙa, onion and egg soup ya Ζone dankali kuma bai soyuba.
Haka suka haΖura da dankalin suka sha tea tare da snacks kawai. Bayan sungama cin abincin ya jawota jikinsa, haΙe da Ιaura kansa akan wuyanta, lumshe idanunsa yayi yana me sauΖe numfashi a hankali, wani abu yakeso daga gareta wanda yasan idan ya nema balallai yasamuba, kuma ma koda yasamu to ba a son ranta ta basa ba, shiyasani matuΖar zasu kasance waje Ιaya da’ita tofa har abada acikin sha’awarta zai kasance.. Jin yanda yake sauΖe mata numfashi akan wuyanta ne yasanya jikinta yin sanyi, ahankali kasala tasoma dirar mata, itama lumshe nata idanunta tayi, tana me yin wani tunani acikin zuciyarta.. Tsawon mintuna 15 suka Ιauka a haka babu wanda yace da Ιan uwansa Ζala, shi dai Dr.Sadeeq tsundum yake acikin kogin sha’awa, yayinda itakuwa take tsundum acikin kogin tunanin wani abu wanda bashida amfani a wajenta, wani abu wanda tunaninsa yazame mata jiki da jini, sai dai kuma tasan abun baidace da itaba, baidace da rayuwarta ba, Ζaddara ce kawai ta haΙasu, sannan kuma zuwa yanzu yakamata ace ta manta da babinsa, takuma daina tunasa, sai dai kuma duk yanda taso hakan yakasance abun yaci tura, dole zata haΙa da addu’a, saboda addu’a yafi gaban komai, duk da cewa dama tanayi amma dole zata Ζara akan wanda takeyi…1
A hankali yajanyeta daga jikinsa haΙe da miΖewa yanufi Ιaki, da kallo kawai tabisa harya shige cikin Ιakin, “Meke damunsa?” tatambayi kanta a bayyane.
Ganin batada maibata amsa, baikuma dace ta zauna batare da taji damuwarsa ba yasanya ta bisa zuwa cikin Ιakin..
Kwance ta iske sa akan gado yayi ruf da ciki yayinda yasanya hanunsa Ιaya akan mararsa, sam bata fahimci wani abu game da hakan ba, ahankali taΖarasa wajen da yake, cikin murya meΙan sanyi tace “Bakada lafiya ne?”
“Lafiyana Ζalau, kawai dai bacci nakeji ne” yafaΙi haka ataΖaice, baison yayi magana me tsawo ta harbo jirginsa, tsakani da Allah bayason yasake takurata, jiyama da yayi, yauda safe da kuka ta tashi masa, saboda haka yanzu baison ya Ιallo liΖi gwamma yabari ko zuwa dare ne ma, amma kuma idan yatuno irin daΙin dayaji jiya, sai yaji kamar bazai iya haΖura ba.. Haurawa tayi kan gadon haΙe da kwanciya a bayansa, Ζurawa kwantaccen gashin kansa ido tayi, abubuwa da yawa nasa suna matuΖar burgeta, babu ma kamar idanunsa, idan yana kallonta harwani mutuwa jikinta yakeyi, babu ta inda Dr.Sadeeq ya gaza, komai nasa yayi 100%.
“Ζacci bai isheki bane?” yayi mata tambayar batare daya juyo zuwa garetaba.
“A’a kawai dai ina hutawa ne” tafaΙi haka a taΖaice don talura kamar bayason damuwa.
Ζarar wayartane ta karaΙe cikin Ιakin, da sauri ta Ιauko wayar dake aje kan Ιan Ζaramin drawer’n gefen gado.. Ganin Husnah ce me Ζiran yasanya ta Ιaga wayar da sauri, tana ΖoΖarin yin magana taji muryar Husnah tace “Gani a falo”
da sauri tatashi daga kan gadon haΙe da ficewa daga cikin Ιakin, ko bayani bata tsaya yiwa Doctor ba. Shikuwa da kallo kawai yabita harta fice daga cikin Ιakin, lumshe idanunsa yayi haΙi da sauΖe ajiyar zuciya.
Da gudu Zahrah taje ta faΙa jikin Husnah, rungume juna sukayi Ζam cike da kewar juna.
“Nayi kewarki sosai Ζawata” Husnah tafaΙi haka tana me Ζara rungume Zahrah.
Tureta Zahrah tayi haΙe da Ιan turo baki gaba. “Bawani nan ni ae nayi fushi, tunda ranan nan kin yaudareni kin gudu”
Dariya Husnah tayi haΙe da cewa “Yi haΖuri amaryar likita”
Dariya suka sanya su dukansu, saida Zahrah ta cikawa Husnah gabanta da su drinks kafun tazo ta zauna akusa da ita..
“Gaskiya dole ne nima acikin wannan shekaran nayi aure, kiduba kiga 2 days kacal amma gaba Ιaya sai wani shining kike” Husnah tafaΙi haka tana me Ζarewa Zahrah kallo.
Harara Zahrah ta wurgawa Husnah “Kinganki ko wallahi banason tsokana, ae ko a engine aka sani baici ace zuwa yanzu nafara walwali ba”
“Hahhh kedai faΙi gaskiya don da alama doctor madara na musamman yake shayar dake kullum”
Dariyane yakama Zahrah “wai madara” hmmm itasam bata fahimci inda kalaman Husnah suka dosa ba..
“Ke dai baki rabo da tsokana, wace madarace zatasa acikin 2 days kacal na sauya” Zahrah tafaΙi haka tana me duban skin Ιinta..
“Hahhhh madara mana irin taku ta masu aure, ae babe kawai ki manta, nasan kinbasa yasha kuma kema yabaki kinsha”
Sai yanzu Zahrah ta gano me Husnah ke nufi, duka ta Ιaka mata abaya haΙe da yin dariya. Husnah ma dariyan tayi, kana taΙauki drinks tasoma sha..
****
Hira sosai Husnah da Zahrah sukayi, duk da Husnah tace bajimawa zatayi ba. Bata jima ba kuwa tayi tafiyarta bayan tabawa Zahrah wasu ingantattun magunguna wanda Hajiya Shuwa ta bata tace takawo mata, har bakin gate Zahrah ta raka Husnah, cike da kewar juna sukayi sallama…
***
Kallon Dad Ιinsa yayi arikice gaba Ιaya idanunsa sun rufe, miΖewa yayi tsaye yasoma takawa ahankali, ganin zaifita daga cikin Ιakinne yasanya, Dad yayi saurin riΖosa, “Bazaka iya kulawa da kanka ba Zaid, badai Nigeria kakeso mu koma ba?” cike da kulawa Dad ya tambayeshi..
Kansa ya kaΙa kamar wani Ζaramin yaro, ajiyar zuciya Dad ya sauΖe haΙe da Ζara riΖe hanun Zaid Ιin.
“Shikenan ka kwantar da hankalinka gobe zamu koma Nigeria”
Wani irin sanyi Zaid yaji acikin zuciyarsa, badon komai ba saidon zaije yaga Zahrah’n sa, babu ruwansa da wani tayi aure, shi so yarufe masa ido, hargidan nata zaije… (?♀?♀ Anya Zaid bai samu matsala a ΖwaΖwalwarsa ba kuwa? )
Dad kuwa yayanke wannan hukuncinne saboda suna zuwa Nigeria zai Ιaurawa Zaid Ιin aure da Ζ΄ar abokinsa, wannan shi kaΙaine zaisanya Zaid ya nutsu yakuma dawo cikin hankalinsa….Tana idar da sallan isha, ta Ιauki wata doguwar riga marar nauyi ta zura ajikinta, rigace irin shara shara Ιin nan, gashi kuma yaΙan kamata ta Ζasa, yayinda saman rigan kuwa ya buΙe, zura rigar kawai tayi batare da koda ta kalli kanta a madubi ba tafice zuwa falo. Sauri take batason Bollywood sufara haska film Ιin Bajrangi Bhaijaan bata kusa, Ζarfe takwas kuma dai dai zasu saka film Ιin, gashi yanzu bakwai ne hadda wasu mintuna, direct kitchine ta wuce taΙauko wani Ιan Ζaramin cup, fridge ta buΙe ta ta Ιauko babban cup Ιin milk shake dake cikin fridge’n ta tsiyaya, ahankali take tafiya tana Ιan zuΖan milk shake Ιin a bakinta, yajima yana jingine jikin Ζofa, kan Ζirjinta kawai yaketa kallo tun fitowarta daga cikin Ιakin, daga kan fatar cikinta har brezia’n dake sanye a jikinta, duk sun bayyana kansu a fili kasancewar rigar bata wani Ιoye sirri, sam bata lura dashi ba, hankalinta yana ga tv, hanu yasanya ya jawota jikinsa, saura kaΙan cup Ιin hanunta ya suΙuce ya faΙi Ζasa. Da sauri ta kalleshi haΙe da Ιan turo Ιan Ζaramin bakinta gaba.+
Ta baya ya rungumeta, haΙe da Ιaura kansa akan wuyanta, cikin wata murya me sanyi yace “Ζaukar alhaki ne, ko kuma kawai anyi danni ne?”
Cikin rashin fahimtan inda kalamansa suka dosa tace
“Bangane ba”
“Ummmm nima so nake nagane saina baki amsa” yafaΙi haka yana me ΖoΖarin zame wuyar rigar daga kan kafaΙunta.
Dasauri ta nemi matsawa daga jikinsa, amma saidai bata samu daman hakan ba, domin kuwa ya riΖeta gam.. Baidamu da yanda takeyi ba yasanya hanunsa yazame wuyar rigan, dake rigan dama tana da faΙin wuya sai gashi yakawo wuyan har kusan Ζasa da kafaΙunta, bakinsa ya Ιaura adai dai saitin wuyanta ta baya, wani irin lafiyayyen kiss yabata wanda saida yasanya tsikar jikinta suka tashi, da sauri ta juyo tana fuskantarsa, idanunsa da suka koma kamar na mejin bacci, ya Ιago ya watsa mata su, wani dokawa taji Ζirjinta yayi, yanayin da taga Ζwayan idanunsa shiyafi komai sanya mata faΙuwar gaba, har abada bazata taΙa manta mutumin data fara ganin irin wannan yanayin acikin idanunsa ba, kusan nasakamma har yafi na Doctor tsanani, domin kuwa bata taΙa mantawa da yanda idanun suka riΖiΙe suka zama jajaye suke kuma lumshewa alokaci guda ba, Zaid shine mutum na farko da ya fara kallonta da irin wannan yanayin, “mekenan hakan yake nufi? me yasa idanun suka sauya launi alokaci Ιaya?” tayi mawa kanta duka waΖ΄annan tambayoyin da bata da me amsa mata su..
A hankali yake Ζara matseta haΙe da kusanto da fuskarsa daf da tata, burinsa kawai shine yaji bakinta acikin nasa. Kawar da kanta gefe tayi tana me sauΖe numfashi ahankali, gaba Ιaya tunowa da tayi da Zaid ya sanja mata yanayinta, Zaid ba mutum ne da zata manta dashi ba, lallai dole harta mutu yana cikin rai da zuciyarta, kodan abun da ya aikata a gareta.
Hanu yasa ya juyo da fuskarta, yazama suna fuskantar juna, baijirayi komaiba ya Ιaura bakinsa akan wuyanta, kissing Ιin wuyanta yake sosai, wanda hakan ya haifarmata da mutuwar jiki, cikin nutsuwa ya dawo da bakinsa kan nata bakin, ahankali yake sucking lips Ιinta, lumshe idanunta tayi tana me karΙan saΖon sa, karo na farko a rayuwarta da taji hakan dayakeyi mata yayi mata daΙi, batasan lokacin da ta gama sakar masa jikinta ba haΙe da sake buΙe masa bakinta, shikuwa dama abun da yake jira kenan, ba Ιata lokaci ya kamo tongue Ιinta yashiga tsotsa a hankali.. Wani irin numfashi kawai yake fitarwa, ko a iya haka idan ya tsaya yasan zaisamu gamsuwa, har abada shikam yanaji ajikinsa bazai taΙa gajiyawa da tsotsan baki da kuma harshenta ba, wani ΙanΙano na musamman yakeji acikin bakinsa idan yana tsotsan harshenta, yakan rasa duk wata nutsuwarsa idan laΙΙansu suka haΙe waje guda,yakan tsinci kansa cikin matsanancin shauΖi dakuma wani irin yanayi me daΙin gaske.
Ζafafunta ne suka soma saΖewa, gaba Ιaya tsayuwar ta gagareta, yayinda shikuwa yaketa jifanta da salonsa iri iri, idan zasu shekara a haka sai dai Ζafafunsa su gaji suΖi Ιaukarsa, amma bawai shi ya gajiya da shan tausassun laΙΙanta ba, ΖoΖarin zamewa Ζasa takeyi da sauri ya riΖota haΙe da Ιagata caΙak kamar wata Ζ΄ar Ζaramar yarinya… Direct Ιaki yanufa da ita, bai direta ako inaba sai akan gado, Ιan Ζaramin Ζara tasanya haΙe da cewa “Wayyo nauyi!”
STORY CONTINUES BELOW
Dariya yayi haΙe da jan hancinta cikin muryarsa da ta soma sarΖewa yace
“Waye ne me nauyin?”
“Kai mana!” tafaΙa a shagwaΙance. Gaba Ιaya rigan jikin nata ya zame Ζasa, haΙe da soma bin ko wani Ιangare na jikinta da hot kiss, shiru tayi tanajin yanda yake tsotseta kamar wani maye, amma kuma fa saΖon nasa na yau yana shiga inda ya kamata domin kuwa tun Ιazu jikinta yagama mutuwa.
Kissing Ιin bakinta yaci gaba dayi, batasan lokacin da itama ta soma tayasa ba, baitaΙa tunanin zata taya saba, shiyasa sanda takama harshensa tana tsotsa a hankali, yaji gaba Ιaya ya ruΙe haΙe da zaucewa, jiyake kamar awata duniyar aka tsoma shi.. Yanayin yanda yake romancing Ιinta ne yasa har kuka sai da tayi masa wanda batasan na menene ba, jitakeyi kamar kan nipples Ιinta zasu cire, tsabar anbasu kyakkyawan sucking.
“wallahi doctor ma mugu ne” tafaΙi haka acikin zuciyarta….. Yau dai ba iya Dr.Sadeeq bane kaΙai yaji daΙin kasancewarsu tare ba, hadda ita kanta me daΙi’n nasa, sai dai kuma gaba Ιaya zautar dashi takeyi, yauma da Ζyar yasamu ya iya dawowa cikin duniyarmu, bawai don yasoba saidon gudun wahalar da ita… A hankali yasa hanu yashafa gashin kanta, haΙe da manna mata kiss akan goshinta, Zahrah dake kwance luf acikin Ζirjinsa ta lumshe idanunta haΙe da sake cusa kanta acikin Ζirjin nasa..
“I’am sorry me daΙi na na gajiyar dake ko? ba laifi na bane, inata so nayi controlling Ιin kaina amma nakasa, ke Ιince kin cika da….” saurin toshe masa baki tayi haΙe da sake Ιoye kanta acikin Ζirjinsa, kunya takeji tsantsa idan yaΖirata da sunan me daΙi’n nan, sai taji gaba Ιa tazama wata iri da ita.. Tsotsan hanunta dake kan bakinsa yasoma yi, da sauri tacire hanun nata haΙe da tashi zaune, bargo ta rufa ajikinta tayi toilet da sauri gudun kar ya tsaidata, jingina tayi da jikin Ζofar toilet Ιin tana sauΖe numfashi ahankali, gaba Ιaya abun daya wakana a tsakaninsu ne yashiga dawowa cikin kanta, tanaso Ζwarai taga tana farantawa mijinta rai, zatayi iyaka ΖoΖarinta wajen ganin tayi yaΖi da zuciyarta, wajen ganin ta basa farinciki me Ιorewa yanda ya kamata. Wanka tayi haΙe da zura rigan wanka tafito…
Tsaye tagansa daga shi sai 3 guater jeans ajikinsa, kallo Ιaya tayi masa tayi saurin Ιauke kanta, har yanzu bata taΙa amincewa yaga tsiraicinta cikin haske ba, sannan haka itama bata taΙa tsayawa takalli jikinsa acikin haske ba komai sunayinsa ne acikin rashin wadataccen haske, “Jikinsa yanada kyau” tafaΙi haka acikin zuciyarta haΙe da Ιan satan kallon 6 packs Ιin dake kwance akan cikinsa.
RaΙawa yayi ta gefenta yashige cikin bathroom Ιin fuskarsa Ιauke da wani irin murmushi.
Wata Ζ΄ar Ζaramar riga wacce ta tsaya iyaka guiwarta kawai ta sanya haΙe da sanya igiyoyin dake gaban rigar ta Ιaure cikinta, haurawa tayi kan bed Ιin ta kwanta.. Yana fitowa yakuma sanya wani 3 guater jeans Ιin haΙe da feshe jikinsa da turare.. Wutan Ιakin yakashe yakunna musu na bacci, hawa kan gadon yayi haΙe da jawota jikinsa, kwanciya ajikinsa yanayi mata matuΖar daΙi shiyasa aduk sanda yajawota jikinsa bata bijirewa. “Kinyi addu’a?” yatambayeta.1
Kai kawai ta Ιaga masa alamar “Eh” addu’a yayi shima ya shafa kana ya lumshe idanunsa, ahankali yake shafa bayanta, cikin mintuna Ζalilan bacci ya Ιauke ta, sannu sannu shima bacci me nauyi ya Ιaukesa….
*****
Washe Gari.
Ζarfe 5 dai dai jirginsu ya sauΖa acikin Nnamdi Azikwe International airport.
A hankali yake taka matattakalan sauΖowa daga cikin jirgin, sanye yake da riga da wando irin na sanyi navy blue colour, hatta takalman dake sanye a Ζafafunsa navy blue colour ne, yayi kyau sosai yaΖara haske, sai dai kuma sosai rama ta bayyana kanta ajikinsa. Yana gama saΖΖowa daga kan matattakalan yanufi wajen da motocin da sukazo Ιaukarsu ke fake, 4matic yabuΙe yashiga haΙe da hakincewa agidan baya, bayasan damuwa shiyasa bayason shiga mota Ιaya dasu Dad Ιinsa.. Harsuka isa gida tunani yakeyi, maiya kamata yayi? sai kuma yanzu daya dawo yakeji gaba Ιaya Nigeria’n tayi masa Ζunci haΙe dayi masa duhu,daya kulle idanunsa Zahrah kawai yake gani… Yana fita daga cikin motar direct Ιangarensa dake cikin gidannasu ya nufa. Falo’n sa tsab-tsab yake tamkar wanda wani yake rayuwa aciki, bedroom Ιinsa ya wuce, yana shiga yaΖarasa gaban wani tangamemen hotonta da yasa aka masa kalanda (Calender) dashi yakafa ajikin bangon Ιakin, rungume Ζaton kalandan yayi haΙe da lumshe idanunsa.1
STORY CONTINUES BELOW
“I really Miss you My Zahrah!”2
ya faΙi haka cikin murya me sanyi da kuma tsananin rauni, hanu yasanya yashafa daidai saiti laΙΙanta dake jikin hoton calender’n.
“Bana tunanin zan daina kewarki Zahrah na, tunaninki yazama abincin ruhina, inasonki sosai, lokaci yayi daya kamata ki dawo gareni, muyi rayuwar auren mu cike da tarin farinciki, nadaina komai Zahrah shan giya, zina, duk na daina please ke nake jira har yanzu, ina fata baki bawa wanina kanki ba?” yanayin yanda yake magana da hoton idan ka gansa kaitsaye dasunan mahaukaci zaka Ζirasa, domin kuwa me cikakken hankali bazaiyi haka ba.. Wayarsa ya Ιauka yayi dialing number’n Abid, bugu uku Abid ya Ιauki wayar baijirayi abun da Zaid Ιin zaice ba yace
“Wow surprise kenan?”2
Ζ³ar Ζaraman tsuka Zaid yayi cikin muryarsa me rauni yace “Inason ganinka Abid, yanzu agidan mu please!” baijirayi me Abid Ιin zaice ba ya katse wayar haΙe da cilla wayartashi kan gado, yasan Abid bazaiΖi zuwaba shiasa baijirayi amsar saba yakashe Ζiran. Zama yayi akan wata kujera dake cikin Ιakin, kan Ιan madaidaicin fridge’n dake aje cikin Ιakin ya maida idanunsa, jiyake kamar yatashi yaje ya Ιau wine Ιinsa yasha, sai dai kuma wata zuciyar tana gargaΙinsa da cewa, Zahrah bataso, tun randa ta gayamasa wata baΖar magana akan shan wine da yake, bai Ζara shaba harkuwa rana me kamar ta yau, duk da kuwa irin azabtuwan da yakeyi idan baisha wine Ιin ba, saboda yariga daya saba. Shiru kawai yayi haΙe da kama kansa ya rumtse idanunsa.. Abid ne yaturo Ζofar Ιakin yashigo bakinsa Ιauke da sallama, ciki ciki Zaid ya amsa masa sallaman haΙe da watsa masa idanunsa da sukayi jajur dasu.. Cike da mamaki haΙi da tsoro Abid ya matso kusa da Zaid da Ιan sauri.2
“Zaid meke damunka haka? yaushe kuka dawo? yajikin naka?” duka waΖ΄annan tambayoyin Abid yayiwa Zaid su a lokaci Ιaya kuma duk amsarsu yake nema idan zai samu..
“Abid nakasa mantawa da ita, itace nutsuwar tunani na, banajin zan iya kaiwa lokaci me tsawo batare da na sanyata acikin idanuna ba, Inasonta sosai kai kasani!”
Kallon Zaid kawai Abid keyi yamarasa me zaice masa.. Kallon Ιakin yashiga yi sai alokacin ya Lura da maka makan hutunanta dake manne ajikin bangon Ιakin Zaid Ιin,wasu zane ne wanda Zaid Ιin yayi wasu kuwa hotunanta ne. Wani irin tausayin Zaid Ιinne ya tsirga masa me tsanani, shidai bazaice baitaΙa soyayya ba, amma kuma baita Ιayin kwatan kwacin irin wannan son me tsanani da Zaid keyi ba. Zama yayi akan kujeran dake fuskantar na Zaid, hanun Zaid Ιin yakamo haΙe da cewa “Kazama jarumi Zaid, kada kamanta fa yanzu Zahrah matar wani ce kuma….”
“Ya isheka haka Abid!!” Zaid ya katse Abid cikin tsawa sosai.
“Matar wani, Matar wani, abun da kuke ta faΙa kenan, meyasa ni bazaku duba halin danake ciki ba? shikenan don tana matar wani sai nadaina sonta? kafun wanda kuke ikirarin matarsace yasota nine nan nafara sonta, kada kataΙa tunanin zan daina son Zahrah Abid, bakuma zan taΙa samun nutsuwa ba harsai Zahrah ta zamo mallakina, kataimakeni Abid kazo muje gidanta mu Ιaukota tazo nan mu rayu tare nasan itama tana sona!” cikin murya me tsananin rauni yake faΙan maganar..1
Kai kawai Abid yake girgizawa azuciyarsa kuwa wutar tausayin Zaid ne ta kunno, So yamakantar da zuciyar Zaid yasanya harya kasa tuna cewa Zahrah a yanzu ta haramta a garesa, shi duk iskancinsa baya tunanin Zaiso matar da take da aure, dukansu shida Zaid sunsani cewa shangiya da zina duk haramunne amma kuma saboda son zucia irin tasu suke aikatawa, yanzu kuma ga wani sabon saΙon da Zaid yafito dashi, yana goya masa baya akan komai, amma a wannan karon kam baya tunnin zae goya masa baya yaci gaba da son matar aure, haΖiΖa Zahrah takai macen da kowani Ιa namiji zai sota, amma kuma tunda ayanzu tazama mallakin wani babu amfanin Zaid yata takura kansa akanta. “Zaid!” Abid yaΖira sunansa araunace. Kansa kawai ya Ιago ya kallesa batare dayace dashi komai ba.
“Kada kaga laifina Zaid, mun hau wani mataki da yanzu dole ne mufaΙawa kanmu gaskiya, menene ribar da zakasamu idan kacigaba da dakon soyayyarta acikin zuciyarka? tazarar dake tsakanin ka da Zahrah a yanzu yanada matuΖar yawa, tana tare da mijinta kuma nasan zuwa yanzu tajima da zama shi kuma shima yazama ita, me yasa to kowannan bai isa yasanya kacireta acikin zuciyarka ba, akoda yaushe kada kana tunanin cewa wai Zahrah zata dawo gareka, so ne yasa mijinta ya aureta, kaga kenan haka nan kawai bazai rabu da ita ba, kasa aranka ma idan Ζaddara ta rabasu babu yiwuwar Zahrah zata amince ta aureka, kai da kanka kasan haka amma zuciyarka tana yaudaranka, haΖiΖa nima shaidane akan cewa har yanzu Zahrah tana sonka, amma hakan bawai yana nuni da cewa zata iya kashe aurenta ta aureka ba ne, kai koma da ace tafito agidan aurenta to bana tunanin Zahrah zata amince ta aureka, kamanta da ita Zaid, kasawa zuciyarka salama, akwai mata da yawa acikin Ζasarnan dama sauran wasu Ζasashen kasamu wata kabawa ajiyar zuciyarka, na tabbatar watarana komai zai zamo labari!” Abid yaΖare maganar yana me dafa ka faΙan Zaid almar son Ζarfafa masa guiwa..1
STORY CONTINUES BELOW
Wata tsuka me Ζarfi Zaid yaja haΙe da ture hanun Abid dake kan kafaΙansa… har abada bazai daina yiwa wanda yace yarabu da Zahrah kallon mahaukaci ba, wai Zahrah’nsa ake so yamanta ya daina sonta, sai yaushe mutane zasu gane cewa cire so bakamar cire takalmi bane? miΖewa yayi daga zaunen da yake haΙe da shigewa cikin bathroom ko sake kallon inda Abid ke zaune baiyi ba.. Ajiyar zuciya Abid ya sauΖe haΙe da gyara zamansa akan kujeran, yana nan yanajiran fitowarsa koda awa Ιaya zai share a banΙakin bazai tafiba saiyajirasa, Zaid bayason gaskiya wani lokaci, kuma kozai mutu saiya faΙamai gaskiya, ae soyayya ba hauka bane, son matar aure mezai jawo maka inbanda wahala da Ζarin zunubai….1
Zaid kuwa yajima tsaye ruwa na fitowa daga shower yana dukan jikinsa…. Ζaure da towel a Ζugunsa yafito daga cikin bathroom Ιin, kallo Ιaya yayiwa Abid yaΙauke kansa, Abid na kallonsa har yagama shafa man lotion ajikinsa…
“Saboda nace kamanta da Zahrah shine kake fushi dani? kai kanka kasan abun da kakeyi ba daidai bane Zaid sannan…..”
“Ya isa Abid!” Zaid ya katsesa aΙan kausashe.
Murmushi kawai Abid yayi haΙe da sa kai yafice daga cikin Ιakin, yasan Zaid ya hau sama bazai taΙa sauraransa ba, wanda yayi nisa bayajin Ζira.
****
Tun fitarsa ta shige cikin kitchine yau bataso ya sayo musu abinci tafiso ta girka musu da kanta, fried rice tayi wanda taji zallan tsokan kaza, da kanta ta haΙa shaka ta sanya acikin fridge, takammala komai yanzu saura kawai tayi wanka.. Ζaran wayarta take ta jiyowa, da sauri tanufi Ιaki inda wayartata take. Wata number ce special ke yawo akan screen Ιin wayar, Ιan tsayawa tayi tana Ζarewa number’n kallo, har Ζiran ya katse bata Ιauki wayarba, wani Ζiranne kuma sake shigowa…. A hankali ta Ιaga wayan ta kara akan kunnenta.
“Zahrah!!!” taji wata murya wacce bazata taΙa mantawa da itaba ta Ζira sunanta, jikinta ne yasoma rawa yayinda bugun zuciyarta yaΖara tsananta shin dagaske ne kokuwa kunnuwanta ne basuji da kyauba, kusan mintuna biyar ba asake cewa komai daga cikin wayarba haka kuma itama bata ce komaiba..
“Wa….y..e?”
tayi tambayar cikin wararrun kalmomi yayinda tsoro ke sake Ιarsuwa acikin zuciyarta.
“Zahrah na! me yasa zaki barni? kin barni cikin Ζunci da tarin damuwa, yazanyi da soyayyarki ne Zahrah, bazan iya rayuwa ba idan babu ke, please ki taimaki rayuwata dakuma zuciyar da ta jima da matowa akan Ζaunarki!!”
Jikinta ne gaba Ιaya yaΙauki rawa harbatasan sanda wayar ta zame daga hanunta ba, take ta faΙi ta tarwatse a Ζasa. Itakanta batasan sanda ta zame ta durΖusa guiwowinta a Ζasa ba, hawayene suka shiga fitowa daga cikin idanunta. “Zaid” shine sunan da take ta nanatawa acikin zuciyarta, sai yaushene Zaid zai barta ta huta tayi rayuwar aurenta cikin nutsuwa? anya kuwa Zaid baisamu matsalan ΖwaΖwalwa ba? ta tambayi kanta, shiru tayi haΙe da lumshe idanunta Ζirjinta kuwa har yanzu bai daina bugawa da sauri ba.
Cikin tsananin mamaki yake kallonta, da sauri ya Ζaraso inda take durΖushe haΙe da tsugunnawa yaΙaura hanunsa akan kafaΙunta
“Meke faruwa?” yatambayeta cike da kulawa.
Da sauri tabuΙe idanunta da suke a lumshe, batasan yaushe yashigo ba.
Kallonta yakeyi sosai da alama amsa yakeson ji daga bakinta.
Dasauri tashiga goge hawayenta haΙe da tashi tsaye, kallonta yakeyi harta shige cikin toilet, idanunsa yasauΖe akan wayarta wanda ta tarwatse akan tiles gaba Ιaya ma screen Ιin wayar ya fashe, mamaki haΙi da Ιaurewar kaine matuΖa suka kamashi, “Meya faru? yaganta tana hawaye gakuma wayarta daya gani aΖasa a tarwatse” yayi mawa kansa tambayar cike da son sanin amsa. Tattare wayar yayi haΙe da komawa kan gado ya zauna zuciyarsa cike fal da tarin tambayoyi..
STORY CONTINUES BELOW
Zahrah kuwa tana shiga cikin toilet ta soma sauΖe ajiyar zuciya akai-akai, meta aikata hakane, gashi yanzu yazo ya ganta acikin halin damuwa, tasan dole ne shima saiya sanya kansa a damuwa, yanzu idan ya tambayeta metasan zata ce masa, wasu hawayenne suka kuma zubowa daga cikin idanunta, da sauri ta sanya hanu ta share.. Haka tayi wanka duk tanajin zuciyarta babu daΙi, Ιan Ζaramin towel ta Ιaura ajikinta, wanda yatsaya a iyaka cinyarta. A hankali ta buΙe Ζofar bathroom Ιin tafito, karaf idanunsu suka haΙe waje guda, da sauri ta kawar da kanta gefe, haΙe da nufar wajen drawer.. Kallon santala santalan cinyoyinta da suke bayyane a fili yashiga yi, wani iri yaji acikin jikinsa, da sauri ya Ιauke kansa..3
Ganin da tayi cewa baya kallonta ne yasanya tayi saurin zura dogon wando na pencil jeans haΙe da wata farar top shirt me kyaun gaske ajikinta, yaune karo na farko da ta fara sanya irin waΖ΄annan kayan ajikinta, ita kanta saitaga ta burge kanta domin kuwa hips Ιinta sunfito acikin wandon sunyi Ιas dasu kamar wanda aka zana.. Kasa daurewa yayi saida ya kafa mata idanunsa, sosai tayi masa kyau baitaΙa ganinta acikin irin wannan shigar ba, ta Ιau hankalinsa Ζwarai lallai Zahrah macece har mace komai nata me kyau ne… Tana tsaka da shafa turare ajikinta taji yaΖira sunanta. Tsayawa tayi cak daga abun da takeyi haΙe da juyowa sai dai bata kallesa ba ta amsa Ζiran dayayi mata.
“Zonan!” yace da ita ata Ζaice.. Ahankali tashiga takawa harzuwa inda yake, tana Ζarasawa garesa ta durΖusa a Ζasa haΙe da sunkuyar da kanta tana me wasa da yatsun hanunta.. Hanunta yakamo haΙe da jawota jikinsa ya zaunar da ita akusa dashi, cike da kulawa haΙi da lallami yashafa kumatunta yace “Kinyi kyau”
Tsintar kanta tayi dayi masa murmushi kawai…
“Meke damunki? Sannan menene dalilin dayasa naga wayarki a fashe gaba Ιaya kuma tatarwatse?”
Kanta tashiga girgizawa alaman babu
“Kinsan banason Ζarya, menene dalilin da yasa zaki Ιoyemin damuwarki? kada ki manta yanzu bake kaΙai kike iko da kanki ba, nima nan inada iko dake, saboda haka na cancanci ki sanardani damuwarki, ni mijin kine bazan taΙa son naganki acikin damuwa ba!” cike da lallashi ya Ζare maganar.
Mezata faΙa masa? tace masa Zaid ne yaΖirata a waya ko me? ko kuma tace masa hawayen da takeyi duk akan Zaid ne? 1
“Dagaske nake bakomai, na Ιaga wayar hanuna da kumfa shine ta suΙuce ahanuna tafaΙi” tsintar kanta tayi da basa wannan amsar, duk da cewa Ζarya ba Ιabi’arta bane amma yazama dole yau tayi, saboda sanar dashi gaskiyan lamarin daya faru bashida wani alkhairi saidai ma ransa ya sosu.
Ajiyar zuciya yasauΖe haΙe da jinjina kansa “Naji amma meyasaki kuka?”
Jitayi gabanta ya faΙi amma saita dake tace “Kuka nake saboda na fasa wayata”
Ζan guntun murmushi yayi sam bai gamsu da maganganunta ba, amma kuma yazaiyi tunda ta Ιoyemasa gaskiya bazai tursasata ba..
“Saboda wayarki ta fashe kawai shine kike kuka? har yanzu dai ke yarinyace Ζarama Zahrah, amma mene abun kuka, idan kikace na saya miki wata kina ganin bazan saya miki bane?”
Kanta ta jinjina alamar “A’a”
“To indai hakane miye na kukan tunda kinsan zansaya miki wata wadda ta fita, kitaimaki zuciyata ki daina sa kanki acikin damuwa please, inasonki banason naga wani abu ya Ιata ranki!”
Raunannun idanunta ta Ιago ta kalleshi, wannan maganar daga cikin Ζahon zuciyarsa yake fituwa, tabbas ita kanta ta gamsu da Ζaunar da doctor yakeyi mata Ιari bisa Ιari, ya cancanci tasakamai da farinciki ne bawai akasin haka ba..
“Ki kwantar da hankalinki, gobe Insha Allah namiki alΖawari zamuje dake ki zaΙi irin wayar da kike so, shikenan?”
Kanta ta Ιaga tana Ιan murmushi, kamar da gaske maganar wayarce a cikin ranta.. MiΖewa yayi yafaΙa toilet, tanajin sauΖar ruwa aΖasa ta sauΖe nannauyar ajiyar zuciya, bataso doctor yasan cewa Zaid yafara bibiyar rayuwarta. Sumu sumu haka ta fice falo.
Tana zaune tayi jigum ya fito daga cikin Ιakin, sanye yake da blue Ιin wando kalan nata, sai dai nasa na maza ne babu ado kamar nata, saikuma farar polo shirt, murmushi tayi domin kuwa yayi mata kyau sosai, shima murmushin yayi mata haΙe da kashe mata idanunsa Ιaya…
Ita da kanta ta zuba musu abinci, yanaci yanata zuba mata santi, har batasan lokacin da tarin damuwar dake cikin ranta suka kau tasoma ΖyalΖyalewa da dariya ba …
****
Zaid ne zaune agaban Dad Ιinsa ya sunkuyar da kansa Ζasa, magana Dad Ιin keyi masa amma kuma kwata kwata bayajinsa, hankalinsa da tunaninsa sunyi nisa sosai wajen tunanin Zahrah, muryarta dayaji Ιazu shiya kara rikita masa tunani, baisauraran Dad dake yimasa bayani amma duk da haka yaji abun da Dad Ιin yafaΙa na Ζarshe, cike da Ζuncin rai haΙe da tsananin mamaki yake kallon Dad Ιinnasa cikin wata murya me Ιaci yace
“Aure fa kace Dad? ni Ιin, kuma da wata ba Zahrah ba?”
Cikin takaici Dad yake kallon Zaid Ιin, wato tunkan ayi nisa ma yafara nuna masa cewa hakan bazai yiwuba kenan.
“Natabbatar kajini, kuma aure babu fashi!” Dad yafaΙi haka a Ζufule, domin kuwa shima yafara gajiyawa da halayyan Zaid na rashin hankali, taya zaka je kana yiwa matar wani soyayya me tsanani irin haka.
Wani murmushi Zaid yayi me matuΖar ciwo haΙe da sanya haΖoransa ya ciji laΙΙansa.
“Bazan iyaba Dad, kaima kafi kowa sanin hakan, aduniyar nan mace Ιaya kawai nakejin zan iya rayuwar aure da ita, bakowa bace kuma Zahrah ce, saboda haka please Dad maganar wani aure na da wata kabarshi don banaso, idan kuma ka matsa shikenan, amma idan kuka tsinci gawanta nayi mata mugun illa kada ku zargeni kufara zargin kanku” yana kaiwa nan azancensa ya tashi tsaye yafice daga falon mahaifinnasa.. Baki a wangale haka Dad yabi Zaid da kallo har yaΙacewa ganinsa..
“Lallaima kuwa Zaid ya Ιauko babban al’amari, amma kuma wannan karon sam bazai lamunta masa ba aure dole sai yayi masa, acikin satin nan ma kuwa” Dad yafaΙi haka acikin zuciyarsa…
Zaid kuwa yana fita a Ιakin Dad direct motarsa yashiga, dagudun gaske ya ja motar yafice daga cikin gidan, tafiya yake akan titi amma zuciyarsa Ζuna takeyi masa, har wani Ιaci yakeji a maΖoshinsa, wayarsa ce tayi wani Ιan gajeren Ζara alamar shigowar saΖo (Message), da sauri ya Ιauki wayar ya duba, domin kuwa tun Ιazu dama saΖon yake jira, adireshi ne na gidan da Zahrah take aka turo masa.. Wani mugun murmushi naga yayi haΙe da Ιan dukan kan steering motar, lallai dole zai cimma burinsa ne kota halin yaya kuwa…
Faka motan yayi yana me Ζaremawa gaban gidan kallo, gidane me kyau da kuma aji, dagani kasan ankashe kuΙi wajen tsara gidan, amma Zaid dake kishi yacika masa zuciya sam baiga wani kyawun gidan ba, saima ji da yayi ya tsani gidan.. Idanunsa ya tsaida akan tankamemen gate Ιin gidan tamkar wanda yake karantan wani abu, a hankali ya buΙe murfin motar tasa yafito waje, cikin takunsa na isa yashiga takawa harzuwa wajen gate Ιin……. (?Anya zaishiga kuwa?hmmm inaga dai yau Zaid aΖasam kanta zai kwana?)
Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 10 BY FATYMA SARDAUNA"