Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 7 BY FATYMA SARDAUNA

SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 7 BY FATYMA SARDAUNA

                 Www.bankinhausanovels.com.ng 

Cikin rashin kuzari yamiΖ™e haΙ—e da nufar hanyar barin falon, ko kaΙ—an babu nutsuwa acikin zuciyarsa, ko sake bi takan abincin nasa baiyi ba, haka yafice daga cikin falon. kaitsaye Ι“angarensa yanufa. Shirya kansa yayi cikin riga da wando na suit. kaitsaye asibiti ya wuce domin kuwa akwai wasu patient da zai gani.

Gaba Ι—aya tunanin Zahrah ya kulle, hartakai ta kawo ko makaranta taje ma bata da wani aiki saina tunani, ko karatun ma da ake koyar dasu bata fahimta, abubuwane sukai mata yawa, tayi matuΖ™ar danasanin marin da tayi mawa Dr Sadeeq, haΖ™iΖ™a idanunta sun rufe, batare da tayi tunanin komai ba ta yanke hukunci, sai dai kuma har yanzu tunaninta daya gushe bai dawo gareta ba, takasa yanke hukunci, haka kuma takasayin tunani mai kyau, saidai tayarda da abu Ι—aya. shine Doctor Sadeeq sam basa’an auren ta bane, yafi Ζ™arfinta. Yau kimanin kwana huΙ—u kenan da faruwar haka a tsakaninsu, tundaga wannan daren kuwa harzuwa yau, Dr baisake zuwa gareta ba, saidai fa kullum safiya, yana turo drivern sa akan yaΙ—auketa yakaita makaranta. amma zancen dai Ι—ayane, bata taΙ“a yarda tashiga motar, koma sauraran driver’n nasa batayi.

Dariya sosai Mahmud yashiga yi, a lokacin da yagama jin matsalolin abokin nasa, haΖ™iΖ™a Sadeeq yabasa dariya, ko da wasa bai taΙ“a tunanin wai Namiji kamar Sadeeq zaiji tsoron furtawa mace kalmar soyayya ba.

Tsuka Dr Sadeeq yaja haΙ—e da Ι“ata fuska cike da takaicin dariyan da Mahmud Ι—in ke masa yace

” Bawai nafaΙ—a maka matsalata bane don kasani a gaba kayita min dariya ba, mafita nake nema Mahmud, gaba Ι—aya kaina ya kulle, inasonta banakuma tunanin zan’iya barinta, amma kuma naga alamomin cewa zan rasata a fili!” Dr Sadeeq yafaΙ—i maganar cikin son abokinnasa ya Ζ™arfafa masa guiwa.

ƘoΖ™ari Mahmud yayi wajen tsaida dariyar tasa haΙ—e da gyara zama

“Yazama dole nayi maka dariya Sadeeq, a matsayinka na likita bokan turai, ka kasa jure zafin soyayya, amma kuma ko kaΙ—an banga laifinka ba, sai dai kuma, akwai Ζ™alubale a gabanka!” Mahmud yaΖ™are maganar yana mai waina pen Ι—in dake riΖ™e a hanunsa.

“Wani irin Ζ™alubale kenan Mahmud?” Dr Sadeeq yatambaya cike da zaΖ™uwa, saboda shi mafita kawai yake nema.

“Nasara ko kuma akasinta, sune babban Ζ™alubalen da zaka fuskanta, amma ina mai maka fatan nasara, duk dacewa banganta ba, amma nasan tahaΙ—u sosai, saboda nasan abokina ya’iya zaΙ“e!” Mahmud yafaΙ—i hakan cike da barkwanci, wanda hakan kuma halinsa ne.

“Bazaka taΙ“a canjawa ba Mahmud, kai ko da yaushe idan ana magana mai amfani saikayi yanda kayi ka sako wasa a ciki.” Dr Sadeeq yafaΙ—i hakan yana mai shafa suman kansa.

Ζ³ar Ζ™aramar dariya Mahmud yayi haΙ—e da Ι—aukan cup Ι—in juice Ι—in dake gabansa yakai zuwa bakinsa.

“Babu amfanin Ζ™ara tada zancen a gareta Sadeeq, tunda ta nuna maka bata sonka, inaganin kabata lokaci, ko ba komai zatayi tunani mai kyau, amma fa hakan danace bawai yana nufin kada kasake zuwa gareta bane, zaka iya zuwa gareta ako da yaushe, amma kada ka sake Ι—ago mata da zancen inaga haka zaifi!” Mahmud yafaΙ—i hakan cike da son Ζ™arfafamawa abokinsa guiwa.

STORY CONTINUES BELOW

ƘaΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya Dr Sadeeq ya sauΖ™e, haΙ—e da haΙ—iyar yawu, sai yanzu yasomajin sanyi a cikin zuciyarsa, domin kuwa da gaba Ι—aya kansa ne ya kulle.

“Zanyi yanda kace Mahmud, sai dai kuma inajiyewa kaina tsoro, kada a gaba taΖ™i amsata, sannan kuma yanzu bansan da wani ido zan kalle ta ba!” Dr Sadeeq ya faΙ—i haka cikin Ι—ar Ι—ar.

Dariya Mahmud yakuma kwashewa dashi a karo na biyu, lallai yayarda cewa so mugun abune, domin kuwa shi kaΙ—ai ke sa jarumi kuma gwarzon namiji acikin tsoro dakuma Ι—ar Ι—ar.

“Yanaga jikinka gaba Ι—aya yaΙ—au rawa, kada dai kabani kunya, tsoronta kakeji tun yanzu, idan kuma akayi auren yaya kenan?” Mahmud yatambaya cike da shaΖ™iyanci.

Tsuka kawai Dr Sadeeq yakuma ja, haΙ—e da miΖ™ewa tsaye, domin idan yabiye ta Mahmud to baΖ™in ciki sai ya cika masa zuciya, domin kuwa halin Mahmud ne tsokana da yawan barkwanci.

“Gwamma nayi tafiyata zaifi min, kayi dariyanka ka Ζ™oshi, ai nine nakawo kaina office Ι—inka, kana da right Ι—in da zaka iyamin komai” Dr Sadeeq yakare maganar yana mai gyara zaman suit Ι—in dake jikinsa.

Ko sake sauraran Mahmud dake ta faman dariya baiyi ba, yayi ficewarsa daga office Ι—in Mahmud Ι—in.

Cikin Ι—an kuzarin da yasamu yake tuΖ™a motar tasa, yanzu kam yagama aminta da shawaran da zuciyarsa ta basa. Kai tsaye gida ya koma, wanka yayi haΙ—e da shirya kansa cikin wani haΙ—aΙ—Ι—en riga da wando na jeans masu kyaun gaske, sosai kayan sukai masa kyau a jiki, suka kuma fito da asalin kyawu da kwarjininsa, babu abun dake tashi ajikinsa sai daddaΙ—an Ζ™amshin turare. Makullin motarsa ya Ι—auka haΙ—e dasakai yafice daga cikin Ι—akin.

Zaune take akan Ζ΄ar katifarta, daga ita sai wata riga marar nauyi, jakan kayan shafanta ne aje a gabanta, da’alama daga wanka tafito, domin kuwa wani sashi na jikinta Ι—auke yake da danshin ruwa. Kallo Ι—aya zakai mata kafuskanci irin ramar da tayi lokaci guda, gaba Ι—aya ta zabge ta faΙ—a, hips da breast Ι—in tane kawai suke a cike a jikinta. A hankali take shafa Vaseline Ι—in dake riΖ™e a hanunta, Yanayin yanda take shafa vaseline Ι—in idan ka gani, kace dole akai mata. tana gama shafa mai Ι—in, ta murza powder kaΙ—an akan fuskarta, haΙ—e da shafa kwalli a cikin idanunta, take fuskarta ta tasakeyin fayau, yayinda idanunta, suka sake bayyana girmansu a fili,kasancewar kwallin yana taimakawa wajen bayyana girman ido.

Kallonta tamayar kan Ι—an Ζ™aramin agogon bangon dake Ι—akin nata, Ζ™arfe 5 na yamma kenan, kuma dai dai lokacin sukayi da Husnah cewa zataje ta sameta a gida. Cikin rashin kuzari, ta miΖ™e haΙ—e da Ι—aukan kayanta riga da sket na atamfa tashiga sanyawa, duk da cewa atamfar mai sauΖ™in kuΙ—i ne, amma hakan baihana ta yi mata kyau a jikinta ba. Wani irin zazzaΙ“i takeji yana sanΙ—an jikin ta, idan ba don tariga da tamawa Husnah alΖ™awarin cewa zata zo yau Ι—in ba, to tabbas da ta Ι—age zuwa gidansu Husna’n saboda bata wani jin daΙ—in jikinta, takumasan cewa damuwace kurum tayi mata yawa.

Inna ce tashigo cikin Ι—akin, adai dai sanda Zahrah ta gama sanya hijab Ι—inta.

“Au ashema kinsan da zuwansa kenan?” Inna tatambaya tana mai Ζ™arewa Zahrah kallo.

“Banganeba Inna, zuwan waye kuma?” Zahrah taje fawa Inna tambaya cikin rashin fahimtan inda kalaman Inna’n suka dosa.

“Naga kinshirya tsab kamar kinsan da zuwansa, to koma dai menene kije yanajiranki a waje!” Inna tafaΙ—i hakan tana mai Ζ™oΖ™arin barin Ι—akin.

“Waye Inna? kuma ni shirin nan da kika ga nayi, gidansu Husnah zani, amma waye ke nemana ?” Zahrah takuma tambaya cike da son Ζ™arin bayani.

“Waye kuwa zaizo neman ki a yanda kike Ι—innan, ai sai dai shiΙ—in da har ya yarda zaiyi JIHADI ya aure ki a haka, amma wai saboda son zuciya da butulci irin naki, kike neman watsa masa Ζ™asa a idanu!” Inna taΖ™are maganar dai dai sanda tayificewarta daga cikin Ι—akin.

STORY CONTINUES BELOW

Wasu irin siraran hawayene suka samu nasaran gangarowa daga cikin idanun Zahrah, tabbas gaskia Inna ta faΙ—a, babu wani mai nemanta sai shi Ι—in shi kaΙ—ai, kuma tabbas tayadda shima JIHADI yayi kamar yadda Inna tafaΙ—a, ashe dagaske ne itakam Ζ™addaranta tayi mata mummunan zane a goshinta, saurin share hawayenta tayi haΙ—e da sakai tafice daga cikin Ι—akin.

Tsaye yake a jikin motarsa yayinda kansa ke duΖ™e a Ζ™asa, Ι—an makullin motarsa ce riΖ™e a hanunsa yana kaΙ—awa, wannan karon kam sosai yake yaΖ™i da zuciyarsa don bayaso tasake sanya masa tsoro kokuma Ι—arΙ—ar.

A hankali take taku cike da nutsuwa har ta Ζ™araso garesa, Ι—an nesa dashi ta tsaya haΙ—e da yimasa sallama cikin sassanyar muryarta wadda bata fita sosai.

Lumshe idanunsa yayi haΙ—i da buΙ—esu a lokaci guda, badon komai ba sai don yanda sassanyar muryarta ta daki jiki da zuciyarsa.

“ZAHRAH!” yaΖ™ira sunanta cikin murya marar fidda Ζ™aΖ™Ζ™arfan sauti.

“Um!” Zahrah ta amasa masa batare da ta’iya motsa bakinta ba, haka kuma kanta a duΖ™e yake tunda tazo bata’iya Ι—aga kai ta kallesa ba.

Kallonta yashiga yi tundaga Ζ™asanta har sama, tabbas duk da cewa a cikin hijab take, amma hakan bai hanasa hango rahamar da tayi ba, take yaji zuciyarsa tayi sanyi, tausayinta yasake kamasa.

“Inaso kimini iso cikin gida, inaga maganar mu acan zaifi, domin ina buΖ™atar zama!” yafaΙ—a cike da Ζ™osawa da tsayuwan da yakeyi.

Sumi sumi haka ta juya ta nufi cikin gida, harta shige cikin gidan bai Ι—auke idanunsa daga kanta ba, “Wallahi Zahrah ta haΙ—u, komai nata mai kyau ne!” yafaΙ—i hakan a fili, cike kuma da shauΖ™in soyayya.

Jim kaΙ—an Zahrah tafito, tana mai wasa da yatsun hanunta, “Kashigo!” kawai ta’iya furtawa cikin murya mai sanyi. Tana gaba yana biye da’ita haka suka doshi cikin gidan.

Katuwar tabarma tabaje musu a hanyar zaure, yayinda ta je ta zauna a can Ζ™arshen tabarman ta takure waje Ι—aya, tamkar amaryar da aka kaita Ι—akin miji yau yau, lol.

Murmushi Dr Sadeeq yayi bayan yayimawa kansa mazauni, dole dai shi zai ci gaba da zama jarumi ako da yaushe.

” Miye haka? ai ko da yanka naman jikin mutane nake, ya kamata ace kin matso kusa dani, balle ma kuma ni ba’abun da nakeyi, ko na taΙ“a miki wani abune ?” Dr yafaΙ—i hakan cike da kulawa.

Saurin Ι—ago da kanta tayi ta kallesa, domin yadawo mata asalin Likitan da tasani, kuma gaba Ι—aya ya sauya wasu Ι—abi’un nasa.

Giransa Ι—aya yaΙ—age sama, haΙ—e da cewa “Yadai, ko nayi wani sabon laifi ne akan wancan banda labari?”

Girgiza kanta tashiga yi ita kaΙ—ai tamkar Ζ™adan garuwa, domin ita tama rasa maizata ce dashi domin kuwa da wani salon yadawo.

“Matso kusa dani mana!” yafaΙ—a cikin sanyin murya, mai Ι—auke da lallashi.

Cikin rashin kuzari, ta koma tsakiyar ta barman ta zauna, bayan ta haΙ—a jikinta duka ta takure waje Ι—aya.

Ajiyar zuciya Dr Sadeeq ya sauΖ™e haΙ—e da sanya hanunsa yashafi Ζ™asumbar dake kwance akan fuskarsa.

“Maiyasa zakisa kanki a damuwa Zahrah? yawan kuka dakuma yawan tunani marassa amfani, basa haifar da komai sai gajiyar da Ζ™waΖ™walwa, please banso kina wahalar da Ζ™waΖ™walwarki, nasan cewa abaya banine sila ba, amma yanzu nine sila.!” Ι—anjim yayi kana yaci gaba da cewa…” Kiyi haΖ™uri Zahrah, nasan bankyauta ba, amma inaso kimanta komai, inaso ki fuskanci karatunki, ki maida hankali sosai kinji Ζ™anwata, bawanda zaimiki dole, ke mutumce kuma kowani Ι—an adam yana da Ζ΄anci, kema kina da Ζ΄anci, saboda haka ki daina kuka kinji Ζ™anwar Likita!” Yanayin yanda yaΖ™are maganar kaΙ—ai ya’isa yasanya zuciya hucewa daga cikin fushi.

STORY CONTINUES BELOW

Kuka kawai Zahrah ta fashe dashi mai sauti, domin kuwa sai yanzu nadaman abun da ta’aikata a garesa yadawo mata sabo fil. A hankali ta Ι—ago idanunta da suke Ι—igan hawaye tamaida kallonta garesa, wannan fuskar ta mara? ta tambayi kanta, tabbas batayiwa kanta adalci ba, Dr Sadeeq baicancan ci mari daga gareta ba. kukane yakuma Ζ™wace mata, don batasan tayanda zata soma basa haΖ™uri akan abun da tayi masa ba.

Cike da damuwa ya dawo kusa da’ita, har suna iya juyo Ζ™amshin turaren juna.

“Subahanallah Zahrah kuka kuma? kinfasan banaso, kidaina kuka kinji, ki faΙ—amin idan ganina ne bakiso, yanzu zantafi Zahrah, nazo ne dama nabaki haΖ™uri akan abun da yafaru tsakanina dake, kiyi haΖ™uri Zahrah haka bazata….” Kasa Ζ™arasa maganar yayi sakamakon Zahrah da ta sanya duka hannayenta biyu ta toshe masa baki.

“Dan Allah kada ka Ζ™asΖ™antar da kanka awajen wacce bata dace ba, bata kuma cancanta ba, bakaine yakamata kabani haΖ™uri ba, nice yakamata na baka haΖ™uri, bai kyautu ace na mareka ba, nayi nadama Doctor, dan Allah kayi haΖ™uri, bansan yanda zanyi ba ne banda zaΙ“i, kayafemin!” Zahrah ta Ζ™are maganar cikin kuka, haΙ—e da karyewar zuciya.

Take yaji tausayinta yasake ninkuwa acikin zuciyarsa.

A hankali ya sanya hanu yazame hannayenta dake kan bakinsa, domin kuwa hakan da tayi masa har ya sanya tsikar jikinsa sun soma motsawa.

“Kinaso nayi haΖ™uri?” Dr yatambayeta.

Kaitashiga kaΙ—awa cikin kuka alamar “Eh”

“To kidaina kuka, domin kuwa daina kukanki shikaΙ—aine zaisanya nayi haΖ™uri nakuma manta da komai, kuma ko dama ni Zahrah batayi mini laifi ba, Ζ™anwata bata laifi a wajena, saboda haka share hawayenki kinji!” yaΖ™are maganar yana me miΖ™omata wani farin handkerchief wanda yafito dashi daga cikin aljihun wandonsa.

KarΙ“an handkerchief Ι—in Zahrah tayi, cike da shagwaΙ“a tashiga share hawayen dake gudana akan fuskarta, ajiyar zuciya kawai take sauΖ™ewa akai akai domin kuwa ko ba komai tarage wani nauyi dake maΖ™are a gefen zuciyarta.

“Yauwa Ζ™anwata, kinga kinfi kyau idan kina murmushi dakuma dariya, inaso akoda yaushe kikasance cikin farinciki!” Dr yafaΙ—a cikin nishaΙ—i, domin kuwa sosai yaji daΙ—in yanda Zahrah ta sauΖ™o daga fushin da takeyi dashi.

Tana gama share hawayen nata ta miΖ™amasa handkerchief Ι—innasa.

Kai yagirgiza alamar a’a haΙ—e da gyara zamansa “Nabaki kyauta, ki ajiye a wajenki, ko saboda gaba, domin naga ke kuka baya baki wahala, kinga duk lokacin da kika soma koke koken ki saiki share hawayenki da shi!”

Hararan wasa ta jefesa dashi, haΙ—e da murguΙ—a masa Ι—an Ζ™aramin bakinta.

Dariya yayi domin sarai yana lure da’ita kuma yaga abun da tayi masa.

“Inazakije kikaci uban kwalliya haka? gashi kuma kinzo kinΙ“ata shi da kuka.” YafaΙ—i maganar alokacin dayake ciro wayarsa daga cikin aljihunsa.

Turo bakinta tayi gaba, cike da Ζ™unΖ™uni tasoma motsa bakinta, da’alama wani abu takeson faΙ—a, “wai a hakanne nayi kwalliya, kawai dai yace banyi masa kyau ba” Zahrah tafaΙ—i hakan a cikin zuciyarta.

“Wayace miki hakane a zuciyata? ni na’isa nace kyakkyawar Ζ™anwata batayi kyau ba, to ma duk cikin garin Abuja wayakai ki kyau ne? babu fa!”

Dariya tasanya, wanda tajima batayi shiba, cab aikuwa ko da acikin makarantarsu akwai waΖ΄anda suka fita kyau dayawa, balle kuma duka garin Abujan baki Ι—aya.

Tsayawa yayi yana kallon yanda take dariyan, komai tayi Ζ™ara kyau take.

Hanunsa ya sanya acikin aljihun wandonsa haΙ—e da ciro wani haΙ—aΙ—Ι—en choculate, Ι“are ledan choculate Ι—in yayi haΙ—e da miΖ™o ma ta. Kyawawan idanunta ta Ι—ago haΙ—e da watsa masa su, girgiza kanta tayi, alamar bata buΖ™ata.

STORY CONTINUES BELOW

KwaΙ“e fuska Dr Sadeeq yayi haΙ—e da marairaice idanunsa, take taji tsikar jikinta ya zuba, yayinda gabanta yayi wani irin mummunan faΙ—uwa, domin kuwa hakan da yayi yasanya fuskarsa ta koma yanayi da fuskar Zaid, saurin Ι—auke kanta tayi daga garesa, haΙ—e da sauΖ™e idanunta Ζ™asa, yabuΙ—e baki zaiyi magana kenan wayarsa tasoma Ζ™ara, alamar shigowar Ζ™ira, cike da girmamawa yaΙ—auki Ζ™iran ganin cewa Ζ™iran daga Hajiyarsa ce.

“Kana’ina?” Hajiya tatambaya a kausashe.

Baikai ga bata amsaba taci gaba da cewa “Koma mekakeyi kabari, Inaso kaje gidansu Salima yanzu, umarni ne ba shawaraba!” Ζ™it takashe wayan batare da tajira taji mai zai ceba.

Ajiyar zuciya ya sauΖ™e haΙ—e da maida kallonsa ga Zahrah.

“Wani uzuri yatasomin, zantafi kikula da kanki!” yafaΙ—i maganar yana me miΖ™ewa tsaye.

MiΖ™ewa itama Zahrah tayi batare da tace dashi komai ba tashiga naΙ—e tabarman da suka tashi akai.

Wani irin kallo haΙ—e da murmushi mai tsayawa a zuciya yayi mata, kana yasa kai yafice daga zauren gidan nasu, yana fita yafaΙ—a motarsa yayi mata key.

Tanajin Ζ™aran tashin motarsa ta sauΖ™e a jiyar zuciya haΙ—e da komawa cikin gida.

Kamar yanda mahaifiyarsa ta umarcesa hakan yayi domin kuwa yaje gidan su Salima sungana da’ita, yarinyar bata da wani aibu, amma kwata kwata jininsa danata baizo Ι—aya ba, domin kuwa sam bata burgesa kasancewarta mace mai rawan kai da shegen girman kan tsiya, har gwamma masa Zabba’u akan Salima, domin dai shikam Salima batayi masa ba. Haka dai suka gaisa sama sama, ko minti 20 baiyiba yabaro gidan nasu..

Bayan Sati Ɗaya.

Kusan ko da yaushe sai Doctor Sadeeq yazo gidan su Zahrah, amma kuma tundaga wannan lokacin baisake koda Ι—ago wani zance makamancin wancan ba, sai dai yana’iya Ζ™oΖ™arinsa wajen bata kyakkyawan kulawa. Sannan kuma dake ita Ι—in me raunin zuciya ce take ta sake bashi yardanta akaro na biyu.

Ɓangaren gidansu Dr Sadeeq kuwa harsun fara shirye shiryen bikinsa, domin kuwa Hajiyarsa wannan karon bada wasa take ba, tace acikin 3 weeks takeso ayi bikin. Shi dai Dr Sadeeq idanu kawai ya zuba musu, domin kwata kwata baijin auren a jikinsa, da za’afasa auren to dazai fi kowa murna, saboda Zahrah yakeso Zahrah ce muradinsa, amma kuma haryanzu yakasa samun wani gamsashshiyar amsa daga gareta.

Ƙarfe 3 dai dai jirginsu ya sauΖ™a a babban airport Ι—in dake cikin garin Abuja, motoci ne iri da kala har guda shida suka zo tarbansa, ciki kuwa hadda Dad Ι—insa, a hankali yake sauΖ™owa daga cikin matakalar jirgin sanyen yake da kayan sanyi hadda hula, yayinda fuskarsa ke Ι—auΖ™e da wani haΙ—aΙ—Ι—en baΖ™in glass na maza, sosai yaΖ™ara kyau da fari, kallo Ι—aya zakai masa katabbatar da cewa yakai cikekke kuma gwarzon namiji, a gaskia yana da kyau da kuma kwarjini, uwa uba kuΙ—aΙ—e sun samu mazauni a jikinsa. Bakowacce mace bace zatayi tozali da haΙ—aΙ—Ι—en namiji kamar Zaid, kuma takau da idanunta ba, saboda Zaid yahaΙ—a duk wani abu da kowacce mace zata so awajen Ι—a namiji, shidai matsalan sa Ι—aya munanan halaiyansa. Yanda yake tafiya cike da izza shiyafi komai Ι—aukar hankali, dakuma jan hankali zuwa garesa. Cike da farinciki Alhaji Ma’aruf yarungume Ι—a’nnasa, duk da cewa babu wani shaΖ™uwa me Ζ™arfi a tsakaninsu amma yana matuΖ™ar son Zaid.

Mota Ι—aya suka shiga shida Dad Ι—insa, yayinda guard Ι—insu suka mara musu baya a cikin sauran motocin. Kwanciya yayi lamo ajikin kujeran motar haΙ—e da lumshe idanunsa, wani irin sanyi yakeji acikin zuciyarsa, koda wasa baitaΙ“a tunanin haka zai kasance dashi ba, kamarshi Zaid ace tunanin mace yahanasa sukuni harsaida yabaro duka abun da yakeyi ya dawo zuwa gareta, amma zaiyi maganin abun a yau bawai sai gobe ba yake da buΖ™atar ganin sugar baby’nsa, sai dai kuma wannan lokacin bada wasa yazo ba…

Zahrah ne keta kai kawo a tsakiyar Ι—akinta, tabbas tayarda da duk wani shawara da zuciyarta ta bata, zuwa yanzu yakamata ace tayi abunda ya dace. Wayarta ne yasoma Ζ™ara alamar shigowar Ζ™ira, tana Ι—aga wayar Dr Sadeeq yace “Gani na’iso ina Ζ™ofar gida!”

“To” tace haΙ—e da aje wayar, ajiyar zuciya ta sauΖ™e haΙ—i da cije lips Ι—inta, dama Ι—aya kawai take dashi kuma tabbas idan tarasa wannan daman to zaiyi mata wahala tasake samun wani daman.

Hijib Ι—inta ta sanya, koda tafito tsakar gida bata taradda Inna ba tana kuma da tabbacin cewa bama ta gidan.

Zaune yake acikin motar tasa, dagani kasan cewa yana cikin damuwa, domin gaba Ι—aya har rama tasoma bayyana a jikinsa. Murfin motar tabuΙ—e tashiga, bakinta Ι—auke da sallama, amsa mata sallaman nata yayi haΙ—e da gyara zamansa yafuskance ta ” Baki taΙ“a min irin wannan Ζ™iran ba, naΖ™osa naji wace maganace zaki faΙ—amin mai matuΖ™ar mahimmanci haka” gaba Ι—aya hankalinsa ya tattara zuwa gareta.

“Dagaske kake Zaka aure ni?” Zahrah tajefo masa tambayar

dabai taΙ“a zata ba balle tsammani.

Kansa yashiga kaΙ—awa muryarsa har rawa take yace “Dagaske nake Zahrah, wallahi auren ki nakeso nayi, samunki a matsayin mata shine babban burina a yanzu.” yafaΙ—i hakan da iya gaskiya’rsa

“So na kakeyi kokuma tausayina?” Zahrah takuma jifansa da wata tambayar.

“Sonki nake Zahrah, inamiki so mai tsanani, wlh inasonki da duka zuciyata!” Dr Sadeeq yabata amsa, cike da kulawa.

“Nayarda na Amince Zan aureka, muyi zama na har abada!” Abun da yafito daga bakin Zahrah kenan bayan tagamajin amsar da take buΖ™ata daga garesa, cikin tsananin mamaki Dr Sadeeq yashiga kallonta, jin sauΖ™ar maganarta yayi tamkar daga sama, kodai kunnuwan sa basu jiye masa dakyau bane?….Kasa motsa koda laΙ“Ι“ansa yayi balle har yakai ga furta wata kalman, “dagaske ne abun da kunnuwansa suka jiye masa kokuwa mafarki yake?” yafaΙ—i hakan a cikin zuciyarsa.+

“Kada kayi kokonto kokuma shakka, dagaske nake, na amince da aurenka, amma ina mai roΖ™on wata alfarma a gareka”….”Dan Allah kada ka wulaΖ™antani aduk yanda kasameni, kada kuma ka tozartani, nasan cewa tausayina yafi yawa acikin zuciyarka fiye da soyayya ta, saboda haka ina da tabbacin cewa ko gaba zaka iya sake samun wata mace,wacce itace zata kasance zaΙ“inka, kada haka yasa ka wulaΖ™antani dan Allah, kada kuma kacutar da rayuwata!” cikin sanyin murya ta Ζ™are maganarta ta, yayinda hawaye suka shiga fitowa daga cikin idanunta,suna sauΖ™a akan Ζ™uncinta.

Jiyayi gaba Ι—aya wani irin matsanancin farinciki ya lulluΙ“esa, gani yake tamkar wasa Zahrah take masa, amma kuma ba’abun mamaki bane, saboda babu abun da yagagari Allah.

“Bansan ta’ina kokuma tayaya zan fara godemiki ba Zahrah, kin gusarmin da duk wata damuwa dake damuna, kinbani farinciki cikin Ζ΄an mintuna Ζ™alilan, kiyarda dani Zahrah, inamiki Soyayyace ta gaskiya bawai, irin soyayyarnan tako oho ba, zan’iya sadaukar da duk wani abu nawa akanki Zahrah, soyayyar da nake miki, yasanya bana ganin laifi ko kuma aibun duk wani abun da kikamin, burina da fatana shine murayu tare dani dake amatsayin miji da mata, kuma aΖ™arΖ™ashin inuwa Ι—aya, Inasonki Zahrah, kuma namiki alΖ™awari komai wuya komai tsanani bazan taΙ“a gujemiki ba, ZANRAYU DAKE Zahrah!!” Dr Sadeeq yafaΙ—a cike da matsanancin farinciki, jiyake tamkar yajawo Zahrah jikinsa yabata kyakkyawan runguma.

Kuka Zahrah ta fashe dashi, wanda batasan dalilin yinsaba, ita ta amincewa kanta cewa zata auri Dr Sadeeq amma saitakeji tamkar dole tayimawa kanta.

Batayi zato ba saiji tayi Dr Sadeeq yajawota jikinsa haΙ—e da sanya hannayensa duka biyu ya rungumeta. “Inasonki Zahrah, kuma nayi maki alΖ™awarin bazantaΙ“a wulaΖ™anta ki ba har’abada, kidaina kuka kinji princess Ι—ina!” yaΖ™are maganar tasa cikin sigar lallashi.

DaddaΙ—an Ζ™amshinsa shiyaso birkita mata tunani don haka tayi saurin janyewa daga jikinsa, tana mai yin Ζ™asa da kanta.

Sam shikam ma yamanta da cewa hakan da yayi ba’abu bane mai kyau, gaba Ι—aya murna yacika masa zuciya.

“Uh sorry baby, gaba Ι—aya kece kikamantar dani komai!!” Dr Sadeeq yafaΙ—i hakan yana mai dafe goshinsa.

Ƙasa Ζ™asa Zahrah tayi murmushi haΙ—e da kawar da kanta gefe, hakanan taji wani irin nauyin Dr Sadeeq Ι—in yaΖ™aru acikin zuciyarta, haka kuma yaΖ™ara girma acikin idanunta.

Wani irin kallo Dr Sadeeq yashiga yimawa Zahrah duk dacewa takau da kanta gefe, sai yanzu nema yake Ζ™ara ganin haΙ—uwarta fiye da da, tabbas da Zahrah bata amince dashi ba to da ya tabka babban rashi, domin kuwa Zahrah tahaΙ—u, macece ita da kowanni Namiji zaiyi fatan mallaka.

STORY CONTINUES BELOW

Sam batayi tunanin kallonta yake ba, don haka taΙ—an juyo dan itama ta saci kallonsa, aikuwa karab idanunsu suka sauΖ™a akan najuna, da sauri Zahrah tayi Ζ™asa da kanta haΙ—e da cusa fuskarta tsakan kanun cinyoyinta.

Dariya Dr Sadeeq yayi cike da shauΖ™i haΙ—e da shafa sajen dake kwance akan fuskarsa. “Yaushe kika farajin kunyana? lallai zamu Ι“ata idan harkinajin kunyana!” ya faΙ—i hakan cike da zolaya.

Ɗan Ζ™aramin bakinta taturo gaba, haΙ—e da marairaice fuska cike da shagwaΙ“a tace “To bakaine kaketa kallo na ba, saikace baka sanni ba!”

Lumshe idanunsa yayi haΙ—e da buΙ—esu a lokaci guda, irin wannan salon shagwaΙ“an ai saita sashi bacci batare da yashiryawa hakan ba,lol.

“Ki faΙ—amin laifi ne don nakalli abar sona? saidai kiyi haΖ™uri amma kallonki yanzuma na fara, tunda kinamin kyau, kina kuma burgeni!” yanayin yanda yayi maganar abun burgewa ne, ga macen da tasan daΙ—in soyayya.

“Nidai kada ka wani ce inada kyau, daΙ—in bakine kawai nasan kakemin!” still da yanayin shagwaΙ“a tayi maganan.

Lumshe idanunsa yayi haΙ—e da fitar da iskan numfashi daga bakinsa, yanayin shagwaΙ“an Zahrah yafi komai burgesa a tattare da’ita, haka kuma sosai yake sauΖ™ar masa da kasala. “Princess!!” yaΖ™ira sunanta dawani irin murya mai taΙ“a zuciya.

A hankali ta Ι—ago idanunta ta kallesa, batare da ta amsa masa ba, ganin idanunsa a rufe, yasanya taΙ—an tsaya Ζ™aremawa fuskarsa kallo. “Duk kallona Ι—aya da zaki yi bazai tafi a banza ba, sai kin biya kuΙ—i, gwamma ma kisani!” Dr Sadeeq yafaΙ—i haka batare da ya buΙ—e idanunsa ba.

Saurin Ι—auke kanta tayi daga kallonsa haΙ—e da cewa “Niba kallonka nake ba”

“Zaki iya rantsewa cewa bani kike kallo ba?” yaje fo mata tambayar da batayi zato ba.

kanta tashiga girgizawa haΙ—e da cewa “Ai bankalleka sosai ba, kaΙ—an nakalleka!”

Dariya Dr Sadeeq yasanya wanda harsaida dimple Ι—insa suka bayyana, yanzu yayarda cewa Zahrah yarinyace Ζ™arama, kuma zakayi saurin kamata idan tamaka laifi.

ƘoΖ™arin buΙ—e murfin motar Zahrah tasomayi, cikin mamaki Dr yace “ina zaki?”

“Zankoma gida ne, dama magana zan faΙ—a ma, shiyasa na Ζ™iraka, kuma nafaΙ—a ma, inada karatu, gobe muna da test a makaranta” Zahrah tafaΙ—i hakan dai dai lokacin da ta gama sanya Ζ™afafunta waje.

“Shikenan to My Princess kikulamin da kanki kinji, inasonki sosai!” Dr Sadeeq yafaΙ—a cike da kulawa.

Wani irin muguwar kunyarsace takama Zahrah, bashiri ta wuce cikin gida tana mai rufe fuskanta da tafukan hanunta.

Shima Dr Ι—in murmushi yayi cike da jindaΙ—i, lallai idan ya auri Zahrah yakasance mutum mai sa’a, acikin satinnan insha Allah, zai sanarda Ζ™anin mahaifinsa azo a nemamasa auren Zahrah, a wajen Baffa.

“Aurenka da Salima fa?” Wata zuciyar ta jefo masa wannan tambayar, wani irin bugawa yaji Ζ™irjinsa yayi, gaba Ι—aya amincewa dashi da Zahrah tayi yasanyashi manta halin da yake ciki na batun auren sa da Salima. Jiyayi gaba Ι—aya jikinsa yayi sanyi, tabbas akwai Ζ™alubale a gabansa, domin kuwa yanada tabbacin cewa Hajiyarsa bazata taΙ“a sanja maganarta ba, gashi har ansoma shirye shiryen bikinsa da Salima, kuma shi a tsarinsa bai sha’awar auren mata biyu, Zahrah ita kaΙ—ai ta’ishesa rayuwa, amma kuma tabbas yasan zai fuskanci matsaloli da yawa daga Ζ΄an uwansa, matuΖ™ar ya jajirce akan cewa Zahrah yakeso ba Salima ba, to amma dole zai jarraba sa’ansa, domin a gaskiya baijin cewa zai’iya haΖ™ura da Zahrah.

Cike da sanyin jiki yayimawa motar tasa key, haΙ—e da nausawa kan titi.

Suna isa katafaren gidannasu, adai dai parking space motar tasu ta tsaya.

Bawani jinkiri Zaid yabuΙ—e murfin motar yafito, batare da yatsaya sauraran Mahaifinnasa ba, yanufi Ι“angarensa kai tsaye.

STORY CONTINUES BELOW

Komai dake cikin Ι“angaren nasa a gyare yake tsab, tamkar akwai wani wanda ke rayuwa a cikinsa, hakan kuma yasamo asaline da yawan gyara part Ι—in da akeyi duk bayan kwana biyu, kasancewar Zaid mutum ne da bayason Ζ™azanta.

Direct bedroom Ι—insa yanufa, yanashiga yasoma rage kayan dake jikinsa, rigan wanka irin na maza mai gashi gashi a jiki yasanya, haΙ—e da sanya badroom slippers a Ζ™afafunsa, kai tsaye wajen fridge Ι—in dake aje cikin Ι—akin yanufa, maltina can yaciro haΙ—e da Ι“alle Ι—an Ζ™arfen da aka rufe bakin can Ι—in dashi, yakai bakinsa, tunda yakai maltina can Ι—in nan bakinsa bai Ι—auke ba harsaida yatabbatar da cewa bakomai ciki ya shanye, cikin dustbin Ι—in dake aje a Ι—akin ya jefa can Ι—in. Bathroom ya wuce haΙ—e da sakarmawa kansa shower. Wanka yakeyi amma gaba Ι—aya tunaninsa baya garesa, yanaga shugar baby’nsa, amatuΖ™ar matse yake da sha’awarta, haryanajin bazai iya daurewa yakai zuwa wani Ι—an lokaci mai tsawo batare da’ita ba.

Bayan yafito a wanka yashiga shirya kansa cikin, haΙ—aΙ—Ι—un riga da wando masu kyau da tsadar gaske, gaskia komai na Zaid me kyau ne, domin kuwa kowani kaya yasanya saiya yi kyau, bakuma kayanne yake masa kyauba, shi Ι—in kansa ne yake mawa kayan kyau,lol.1

HaΙ—aΙ—Ι—en takalminsa sau ciki Ζ™iran kamfanin Gucci yasanya, aΖ™afansa, bayan ya Ι—aura tsadadden agogon nan na Rolex a hanunsa mai kyau da burgewa. DaddaΙ—an Ζ™amshi ne kawai ke fita daga jikin shi, Ζ™amshine mai wahalar mantawa.

Black facing cap, yasanya akansa, domin kuwa yanayin garin ana Ι—an busa sanyi, duk dakuwa cewa daga cikin sanyin yafito.

Wayarsa yaΙ—auka haΙ—e da car key Ι—insa, kai tsaye yafice daga cikin Ι—akinnasa. Ɓangaren Mom Ι—insa yanufa. Hajiya Safara’u ne tsaye a gaban Ζ™atoton teburin cin abinci, yayinda Alhaji Ma’aruf ke zaune tana serving Ι—insa, batasan da shigowarsa ba saiji tayi ya rungumeta ta baya haΙ—e da Ι—aura kansa akan kafaΙ—arta, cike da soyayyar mahaifiyarta sa yace “Barka da gida Momy!”

Cike da tsananin farinciki itama ta rungumesa haΙ—e da basa sumba a kan kumatunsa, “Barkanka da dawowa my son, ya gajiyar hanyar?”

“Alhmdlh!” Zaid yafaΙ—a a taΖ™aice, bayan ya janye jikinsa daga na mahaifiyartasa. ƘoΖ™arin juyawa yakeyi, Mom tace “Inakuma zaka my son ba abinci kazo ciba?” cike da kulawa ta tambayesa.

Ɗan Ι“ata fuska Zaid yayi haΙ—e da cewa “Banajin yunwa Mom, idan nadawo zanci!” baijira jin maizasu ceba yasakai yafice daga cikin falon.

Da kallo kawai Mom tabisa har yafice, fuskarta Ι—auke da damuwa, itakam ta rasa wani irin haline da Zaid, sam ba’a iya gane gabansa da bayansa.

“Miye abun shiga damuwa Hajiya Safara’u? zuwa yanzu yakamata ace duk wani hali na yaronnan Zaid kin gama saninsa!” Alhaji Ma’aruf yafaΙ—i hakan cike da nuna kulawa ga matar tasa.

“Nasan halinsa Alhaji, amma kuma ace mutum shi baya taΙ“a sanjawa, ko da yaushe fa Zaid bayason zama a cikin mu, sannan kuma sam baya sakewa damu!” Mom tafaΙ—i hakan cike da damuwa.

“Zauna muci abincin mu, aishi ba Ζ™aramin yaro bane, yasan me yakeyi!” Alhaji Ma’aruf yafaΙ—i hakan yana mai kama hanun Mom yazaunar da’ita a kusa dashi.

Zaid kuwa yana fita daga Ι“angaren mahaifiyartasa, kai tsaye wajen motarsa yanufa, koda driver yanemi da yabarsa ya tuΖ™asa, Ι—aga masa hanu yayi alamar baya buΖ™ata, shida kansa yayimawa motar key, ya harbata zuwa kan titi.

Tafiya yake cikin nutsuwa yayinda airpiece ke saΖ™ale a kunnuwansa, wayarsa ce tasoma Ζ™ara alamar shigowar Ζ™ira, ganin cewa babban manager’n company’nsa dake nan gida Nigeria ne ke Ζ™iransa yasanya shi Ι—aga Ζ™iran. Banji mai Manager’n nasa yace masa ba, sai gani nayi ya’aje wayan, haΙ—e da buga dogon tsaki, lokaci Ι—aya yakarkata akalar motar tasa zuwa wata hanya daban saΙ“anin hanayar daya nufa, wanda zai sadasa da unguwar su Zahrah.

Dr Sadeeq kuwa yana barin unguwar su Zahrah kaitsaye gidansu yanufa, acewarsa gwamma yayi maganin matsalarsa tunkafun tayi nisa.

Usaina mai aikin Ι“angaren Hajiyarsa yasanya tane ma masa iso awajen Hajiyar tasa, domin kuwa bai isketa a falo ba.

Da sallama yashiga cikin Ι—akin Hajiyar tasa, fuskarta Ι—auke da fari’a ta amsa masa sallaman da yakeyi. Zaune take akan gado, yayinda take duba wasu kayayyaki dake zube a gabanta.

“Barka da huwatawa Hajiya!” yafaΙ—a cike da ladabi.

“Yauwa barkanka, kamar kuwa kasan ina nemanka, wai me kake nufi da auren nan ne Sadeeq? har yanzufa banga kana wani cuku cuku ba, kayan lefe ma saini kabarmawa Ι—awainiyar haΙ—asu, gashi kuma Salima tacemin tunda kaje sau Ι—aya baka sake zuwa ba, mai ke damunka ne wai?” Hajiya tatambayesa cike da kulawa.

Kansa yashiga sosawa haΙ—e da sake yin Ζ™asa da kansa, “Am…dama Am….” “Dakata banson wani kwana kwana, kafaΙ—i abunda zaka faΙ—a kai tsaye kawai” Hajiya ta katsesa daga kame kamen maganan dayake Ζ™oΖ™arin yi mata.

“Hajiya kamar dai yanda na faΙ—amiki ne, wallahi Hajiya dagaske nake, yanzu nasamu wacce nakeso kuma idan harkin yarda aurenmu bazai wuce nan da Sati uku ba, kamar yanda kikeso!” yafaΙ—i hakan cike da ladabi.

Sororo haka Hajiya ta tsaya tana kallonsa, “anya kuwa Sadeeq yana lafiya? ” tatambayi kanta.

“Inagadai bakasan mekake cewa ba Sadeeq, wato nikakeson watsamawa Ζ™asa a cikin idanu ko, ya yi maka kyau, to inaso kabuΙ—e kunnuwanka da kyau ka saurareni, wallahi ko da wasa kakuma zuwamin da irin wannan zancen saina Ι“ata maka rai, nagama baka duk wata dama dazan baka, bakuma zan sake baka wata daman ba, tashi kabani waje, tunda nalura kai baka da tunani!” Hajiya ta Ζ™are maganan cikin faΙ—a.

Cikin rashin kuzari haΙ—e da sanyayewar guiwa Dr Sadeeq yamiΖ™e daga gaban mahaifiyartasa, haΙ—e da nufar Ζ™ofar fita daga cikin Ι—akin,

Saida yakai Ι“aΖ™in Ζ™ofar fita ckafun yatsaya cak, haΙ—e da juyo da kallonsa ga Hajiyar tasa cikin murya mai rauni yace “Hajiya dan Allah..”

“Fita kabani waje nace!!” Hajiya takuma faΙ—a cikin Ι“acin rai tanamai yi masa nuni da Ζ™ofar fita daga Ι—akin…Cikin sanyin jiki Dr Sadeeq yafita daga cikin Ι—akin mahaifiyarta sa. Gaba Ι—aya jiyayi zuciyarsa ta cika da Ζ™unci. Yana isa Ι“angarensa ya zube akan Ι—aya daga cikin kujerun falonnasa, “yanzu wazai je yasamu da wannan matsalar? tabbas yasan Hajiyarsa mutum ce mai kafiya, idan tace eh zai yi wuya ta dawo tace a’a”

hanunsa yasanya cikin sumar dake kwance akansa haΙ—e da yamutsa ta, sunan Aunty Raliya ce yafaΙ—o masa arai, tabbas ita kaΙ—aice Ζ΄ar uwarsa da zai kai mata matsalansa har ma ta tayasa magancewa, sai dai kuma yanatunanin itama ra’ayinta Ι—ayane da Hajiya, amma yasan idan yayi mata kyakkyawan bayani zata fahimcesa, zumbur yamiΖ™e daga zaunen dayake.

Ko bedroom baishiga ba yakuma ficewa daga cikin falon, mota ya koma, haΙ—e da kunnata, mai gadi ne ya wangale masa gate Ι—in gidan yafice.

Hajiya najin Ζ™arar ficewar motarsa daga cikin gidan ta sauΖ™e ajiyar zuciya.

“Gaba Ι—aya tunaninta ya kulle, batasan wani irin abu Sadeeq keshirin shigo mata dashi cikin gida ba, kusan sau uku kenan tana bashi dama, akan yafito da matar aure, amma dazaran lokacin da ta ibar masa yacika, sai ya farayi mata kame kame, yanzu da tagaji da sakarcinsa ta zaΙ“a masa mata, sai yake nema yawatsa mata Ζ™asa a idanu, bakuma zata lamunci hakanba.

Direct Dr Sadeeq gidan Aunty Raliya yanufa, domin baida wata Ζ΄ar uwa da ta wuce ta a duniyar nan.

Yanashiga gidan tunbai gama fitowa daga cikin motarsa ba, su Meenal da Affan Ζ΄aΖ΄an Aunty Raliya, suka rugo da gudu zuwa garesa, dama wasan ball suke a farfajiyan gidan nasu, hakan yasa duk wanda yashigo da kuma wanda zaifita zasu gansa.

Rungumesu yayi a jikinsa, haΙ—e da shafa kawunansu, “Oyoyo babies Ι—ina, ashe girma yazo muku, har wasan ball kukeyi!” yafaΙ—i hakan cike da nishaΙ—i.

“Eh Uncle ai harma nafita iyawa!” Affan yafaΙ—i haka cike da zumuΙ—i.

“Ƙaryayake Uncle baifini iyawa ba” Meenal tafaΙ—i hakan tana mai kama Ζ™ugu, alaman Ζ™arya Affan Ι—in yakeyi.

Murmushi kawai Dr yayi haΙ—e da sake shafa kansu, “kuyi wasa da kyau, idan nafito zan baku alewa!” yafaΙ—a yana mai nufar kofar da zata sadashi da babban falon gidan. Yayinda yabar su meenal sunata tsallen murna saboda yace zai basu alawa.

Da sallama Ι—auke a bakinsa yashiga cikin falon.

Aunty Raliya dake zaune tana kallon tv, ta amsa amsa masa sallamar tasa, fuskarta Ι—auke da fari’a, haΙ—e da yi masa iso.

Ƙarasowa yayi yazauna akan kujera, haΙ—e da sauΖ™e ajiyar zuciya, gaba Ι—aya a gajiye yakejinsa, domin tun safe yau baisamu nutsuwa ya huta ba.

Aunty Raliya da kanta, ta jere masa kayan fruit da juice agabansa, cikin tsokana tace dashi

“Ango kasha Ζ™amshi, duk gajiyar shirye shiryen bikinne haka?”

Ɗan Ι“ata fuska yayi haΙ—e da Ι—aukan apple Ζ™waya Ι—aya ya kai bakinsa.

“Ango labari ya sauya salo” yafaΙ—i hakan bayan ya cinye gutsuren apple Ι—in dake bakinsa.

Cikin mamaki Aunty Raliya tace “bangane ba mekake nufi?”

STORY CONTINUES BELOW

Ajiyar zuciya yasauΖ™e haΙ—e da gyara zamansa.

“Akwai matsala Aunty!” yafaΙ—i hakan lokacin da gaba Ι—aya yanayin fuskarsa ya sauya.

“Matsala! wace irin matsala Uncle?” Aunty Raliya tatambaya cike da Ι—aurewar kai.

“Akwai wacce nakeso na aura, yarinyar tana matuΖ™ar buΖ™atar taimakona, nayi Ζ™oΖ™arin na fahimtar da Hajiya hakan, amma taΖ™i saurarata, yanzu haka daga gida nake, nasoma yi mata bayani, tace natashi na bata waje, gaba Ι—aya kaina yakulle bansan yazanyiba Aunty Raliya!”

Ya faΙ—i haka cikin damuwa.

ƘaΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya Aunty Raliya ta sauΖ™e “TurΖ™ashi, lallai kuwa kazo da babbar magana, amma maiyasa tunda baka bayyana wacce kake so Ι—inba, sai yanzu da komai yariga da yayi nisa? kafasan Hajiya da kafiya balallai ne ta fahimce ka ba, shawarata a gareka shine, kamabar wannan zancen, domin balallai kasamu abun da kakeso ba!” Aunty Raliya tafaΙ—i hakan da’iyaka gaskiyarta.

Cike da rauni Dr Sadeeq ya kalli Yayartasa. “Dan Allah taimakona zakiyi Aunty, kije kisameta kibata baki, wallahi inamatuΖ™ar son Zahrah, sannan kuma yarinyar tana buΖ™atar kulawata, nikaΙ—ai nasan matsalarta, please Aunty!!” yafaΙ—i haka yana me marairaice fuska, hadda haΙ—a hannuwansa biyu ga Aunty Raliya’n alamar roΖ™o.

Kallon mamaki Aunty Raliya tashiga binsa dashi, “wai yaushe Sadeeq yazama bawan soyayya ne?” ta tambayi kanta.

“Abune me matuΖ™ar wuya amincewar Hajiya, amma zan jarraba, saidai kafun naje gareta, dole sainasan wacece yarinyar kuma su waye iyayenta, saboda kada aje Hajiya ta amince, akuma zo asamu wani mummunan labari akan ta”

Wani irin bugawa Ζ™irjin Dr Sadeeq yayi, domin kuwa anzo wajen, lallai baizama dole kowa yafahimcesa ba domin sanin sirrin Zahrah, zai iya sanyawa kowama yaΖ™i amincewa da aurensa da’ita, wanda shi a wajensa baiga ta’inda aurensu zai zamanto rashin dacewa ba, amma ba’a Ζ΄ar Ι“oye a harkan aure, domin koda anΙ“oye tofa sai ya bayyana.

“Sunanta Zahrah, a unguwar Maraba take, sannan kuma marainiyace bata da uwa bata da uba, baffanta ne yake riΖ™onta, yarinyar tana da hankali sosai Aunty, sannan kuma tana da tarbiya, bata da wani aibu ko abun kushewa a tattare da’ita, saidai kuma…” kasa Ζ™arasa maganar yayi, domin kuwa baisan yanda yayartasa zata Ι—auki maganar ba.

“Umm inajinka saidai kuma me?” Aunty Raliya tatambayesa cike da zaΖ™uwa.

“Ƙaddarace kuma tana kan kowa, haka kuma babu wanda ya’isa ya tsallake mata idan har tafaΙ—o kansa, akwai wani tsohon saurayinta da ya yaudareta yayi mata fyaΙ—e, watannin baya da suka wuce, wanda hakanne ma sanadin haΙ—uwata da’ita, amma ni banΙ—auki hakan amatsayin wani abu ba dazai hanani aurenta, kasancewar kowa da’irin tasa Ζ™addaran a rayuwa!”

Sororo haka Aunty Raliya ta hangame ido da baki tana kallon Dr Sadeeq har ya idar da zancensa mai kama da tatsuniya.

Salati Aunty Raliya tasanya cike da tsantsar mamaki haΙ—i da al’ajabi, lallai Sadeeq baisan meyake faΙ—a ba.

“FyaΙ—e! fyaΙ—e fa kace Sadeeq, anya kuwa kansan mekake faΙ—a? yanzu kai saboda rashin hankali irin naka, karasa wacce zaka gani kace kanaso, sai yarinyar da taraba budurcinta wa Ζ™attin maza, yarinyar da wani yagama sanin sirrinta!” Aunty Raliya ta faΙ—i haka cike da Ι“acin rai.

Saurin rumtse idanunsa yayi domin jin magananganun Aunty Raliya’n yake tamkar sauΖ™an aradu, a kunnuwansa.

Cigaba tayi da cewa ” Lallai yanzu na tabbatar dacewa ba lafiyanka lau ba, taya kana cikekken namiji mai hankali da kuma kamala, karasa wacce zaka aminta da ta zamo uwar Ζ΄aΖ΄anka sai wacce wani Ζ™ato ya haiΖ™emawa, yazama dole kasanja tunani Sadeeq, wannan ma ai zancen banzane, to gwarama kasani wannan yarinyar ba zaka taΙ“a aurenta ba matuΖ™ar mu jininka ne!” Aunty Raliya ta Ζ™are maganar cikin hargowa.

STORY CONTINUES BELOW

“Haba Aunty maikikeson cewa ne? dan Allah kada kimin haka, nafaΙ—amiki matsalatane don bani da wacce tafiyemin ke, dama nasan za’a samu rashin fahimta, domin zakuga kamar Zahrah ba kamemmiyar mace bace, alhalin kuma bahaka take ba, tsautsayine yafaΙ—a mata, amma ni nayarda na amince zan aureta a haka, kada fa kimanta duk wanda yarufa asirin wani to Allah zai rufa masa nasa asirin, kitaimaka mu inganta rayuwar Zahrah, kitaimaka mucireta daga Ζ™unci, musanyata cikin farinciki!” yafaΙ—i haka cike da rauni.

Wani irin kallo Aunty Raliya tashiga yimasa, lallai Sadeeq baya cikin hankalinsa.

Murmushi mai ciwo Aunty Raliya tayi haΙ—e da cize laΙ“Ι“anta cikin takaici ta ce dashi.

“Kuskurenka na farko a rayuwa shine yarda dakayi cewa da gaske fyaΙ—e aka mata, shin ka ko san Ζ΄an matan yanzu kuwa Sadeeq? to bari kaji wani abu, a shegen son kuΙ—i irin na Ζ΄an matan yanzu, su da kansu suke saida budurcinsu ga wani daban, idan suka samu makahon da’idanunsa ya rufe ruf har yazo musu da zancen aure, sai su taΖ™arΖ™are su zabgamasa Ζ™arya kan cewa fyaΙ—e akamusu, bayan suda kansu suka kasa budurcin nasu a faifayi suka kai tallanshi kasuwa, ni Ζ΄ar uwarka ce ta jini bazan taΙ“a son wani abun da zai cutar da kai ba, saboda haka tun muna mubiyu nidakai, mubunne maganarnan anan, tun kafun ma yaje ga kunnen Hajiya, domin kasan idan taji cewa wacce kake shirin kawo mata ita amatsayin suruka, ba mutumiyar Ζ™warai bace to zatayi mugun saΙ“a maka!!”

Take idanun Dr Sadeeq suka kaΙ—a sukayi ja, bakomaine ya sanya hakan ba face irin munanan kalaman da Aunty Raliya ta dinga jifan Zahrah dashi, tabbas yasan cewa mafi Ζ΄awancin Ζ΄an matan yanzu suna sayarda budurcinsu saboda abun duniya, amma banda Zahrah’nsa aciki, yasan Zahrah macece mai kamun kai, kuma duk wanda yayarda da Ζ™addara dole ne ya tausayawa mata masu tsintar kansu a irin halin da Zahrah ta tsinci kanta a ciki.

“Ita bakamar yanda kike tunani bane Aunty Raliya, ki saurareni saina baki gaba Ι—aya labarinta, marainiyace ta cancanci a tausaya mata, nima Namiji na tausaya mata balle ke mace, kuma dama ance ciwon Ζ΄a mace na Ζ΄a mace ne!” Dr yafaΙ—i hakan cike da son ganar da Yayarta sa, cewa ba bu wani aibu agame da aurensa da Zahrah.

Gaba Ι—aya duk iya abun da yasani agame da Zahrah, bai Ι“oye mata ba, sai da yasanar mata, atunaninsa hakan zai sanya Aunty Raliya ta Ζ™aunaci Zahrah, amma me sai gani yayi tana taΙ“e baki haΙ—e da kawar da kanta gefe alamar ma ta’inda maganar tasa take shiga tanan take fita.

Yana idar da zancen ta dubeshi haΙ—e da Ι“ata fuska tace “Kagama? kai a tunaninka zaka bani wata hujja dazata sanya naga dacewar aurenka da’ita ne, hmm niba yarinya bace Sadeeq, yakuma zama dole kasanja tunani, kakuma manta da maganar wata wai ita Zahrah, idan kuma kafison kafuskanci Ι“acin rai daga wajen Hajiya, to kaci gaba da zama akan bakan ka harmaganan takai ga kunnen Hajiya!!” tanakaiwa nan a zancenta ta miΖ™e fuuu tawuce cikin Ι—akinta tabarshi zaune.

Hannayensa yasanya duka biyu ya tallafi kansa, lallai akwai babban Ζ™alubale a gareshi, agun Aunty Raliya ma kaΙ—ai ga’irin Ι“acin ran daya fuskanta, inaga Hajiyarsa kuma.?

MiΖ™ewa yayi daga zaunen da yake tamkar wanda Ζ™wai ya fashewa a jiki haka yake tafiya, gaba Ι—aya Ζ™waΖ™walwarsa tasake dagulewa, yazone don yasamu mafita amma sai gashi abubuwa sun sake dagulewa.

Da Ζ™yar yake iya tuΖ™a motar tasa. Haka yanufi gida cikin rashin kuzari, sai dai fa haryanzu bai saduda da maganar Auren Zahrah ba, yanaji ajikinsa cewa Zahrah zata zamo matarsa Insha Allah.

Gagarumin meeting su ZAID suka gudanar mai zafi, a babban hotel Ι—in nan wato SHERATON, sosai aka samu riba dakuma Ζ™arin buΙ—i a Ι—aya daga cikin company’n nasa da suke Nigeria, hakan yasa yaΖ™arawa gaba Ι—aΖ΄a ma’akatansa albashi.

Sunjima suna meeting Ι—in dan haka amatuΖ™ar gajiye suka fito dukansu, lokacin har dare yasoma rufawa. Kallon agogon dake Ι—aure a tsintsiyar hanunsa, yayi yaga karfe 6 daidai na yammaci, Ι—an Ζ™aramin tsuka yayi haΙ—e da soma yunΖ™urin cire rigan suit Ι—in jikinsa wada yaΙ—aura akan kayan dake jikinsa,

saboda gajiyan da yayi bai iya tuΖ™i da kansa ba, sai driver’nsa yaΖ™ira yayi driving Ι—insa.

STORY CONTINUES BELOW

Gyara kwanciyansa yayi ajikin kujeran motar haΙ—e da lumshe idanunsa, wani irin sarawa kansa keyi masa, daga wani Ι“angare na zuciyarsa kuwa sosai meeting Ι—innan ya Ι“ata masa rai, domin kuwa ya hanasa Ζ™arasawa ga ZAHRAH’nsa, wacce saboda itane ma gaba ki Ι—aya yadawo Ζ™asar, yayi missing din Zahrah sosai, yayi missing kyakkyawan murmushinta haΙ—i da kyawawan idanunta, yayi missing kallon kyawawan laΙ“Ι“anta masu daΙ—in tsotso. Gaskiya dole ya killace Zahrah tayanda zata zama nasa shi kaΙ—ai.

Suna isa gida kai tsaye Ι“angarensa ya wuce, a gajiye yashiga bathroom yayi wanka, koda yafito a wankan, direct masallaci ya wuce donyin sallan magriba. Sai da yajira aka yi sallan isha tare dashi a masallaci, kafun ya siΙ—aΙ—o yadawo Ι—aki ya kwanta, yau ko abar Ζ™aunar tasa wato wine baisha ba bacci Ι“arawo yayi gaba dashi.

Zahrah ce kwance akan katifarta sai juyi take ta kasa bacci, gaba Ι—aya kanta ya kulle zuciyarta cike take da tarin tunanuka kala kala. “Anya banyi sauri kokuma gangancin yarda da kuma amincewa da soyayyar Dr da nayi ba?” zuciyarta ta tambayeta.

Zumbur haka ta miΖ™e zaune, haΙ—e da soma girgiza kanta

” A’a banyi kuskure ba, tabbas bayan shi babu wani maiso da nuna tausayi gareni!” tabawa kanta amsa a bayyane.

Wayartace takawo haske alamar shigowar Ζ™ira, kasancewar ta sanya wayar a silent hakan yasanya wayar batayi Ζ™araba.

“Doctor” shine sunan dake yawo akan screen Ι—in wayar.

“Shima baiyi bacci ba kenan” tafaΙ—i hakan a bayyane.

Saida wayar ta kusa katsewa kafun Zahrah ta Ι—aga Ζ™iran haΙ—e da kara wayan akan kunnenta.

“My princess bakiyi bacci ba kenan?” Dr Sadeeq yatambayeta cikin muryarsa mai Ι—auke da damuwa.

“Um, kaifa me yahanaka bacci” Zahrah itama tatambayeshi.

“So da Ζ™auna dakuma tunaninki susuka hanani bacci! kefa mai yahanaki bacci?” yatambaya cike da son jin amsar da zata fito daga bakinta, “Allah yasa itama tunani na ne ya hanata bacci” yafaΙ—i hakan a zuciyarsa.

Kunyane yaΙ—an kamata amma sai ta basar haΙ—e da sauΖ™e ajiyar zuciya “A’a nikam karatu nake, shiyasanya banyi bacci ba, amma yanzuma zanyi baccin.” tafaΙ—i hakan a taΖ™aice.

Ko kaΙ—an baiji daΙ—in amsar da ta basa ba, amma yasan cewa wataran dole zatayi tunaninsa kamar yanda shima yake nata tunanin.

“Naji daΙ—i sosai da kika amince dani Zahrah na! hakan yasa na Ζ™ara jin sonki sosai da sosai a cikin zuciyata!!” cikin shauΖ™in so yafaΙ—i maganar.

“Umm banji mai ka faΙ—a ba!” Zahrah tafaΙ—i hakan cikin wani irin salo wanda batasan ma tayi shi ba, duk da kuwa cewa taji mai yace, iskancine kawai irin nata.

Lumshe idanunsa yayi da suka soma sauya kala, sosai yanayin yanda tayi maganar ya sauΖ™ar masa da kasala.

“Bacci kika farane Zahrah na?” yatambayeta cike da kulawa, domin kuwa shi anasa zaton dagaske batajisa ba.

“Um!” Zahrah ta basa amsa a taΖ™aice cikin Ζ™asa Ζ™asa da murya, domin kuwa tanaso yayarda cewa baccin takeji, saboda har yanzu, bata gama amanna dacewa sonsa take ba, kuma koda za’a kasheta tasan cewa ba sonsa take ba, kawai dai ta tsinci kantane da amince masa, amma batun soyayya kam babu shi.

“To kiyi bacci mai daΙ—i kinji My princess, inasonki sosai, ki kulamin da kanki, banson koda Ι—igon wani a bune ya raΙ“e ki!” Dr ya faΙ—i haka cikin shauΖ™in SO (Sisters kujisafa su likita ashe an iya kalaman love, lol.)

“Uhumm sai da safe.” Zahrah tafaΙ—a a taΖ™aice bayan ta zare wayar daga kunnenta.

“Gaskiya abune mai matuΖ™ar wahala koyawa zuciya So’n abun da bata so, ya Allah kataimakeni, haΖ™iΖ™a banajin tsanarsa haka kuma banajin soyayyarsa a zuciyata, sannan kuma inaji ajikina cewa zan’iya rayuwa dashi, to me hakan ke nufi, ba so bane kuma ba Ζ™i bane to menene?” tatambayi kanta a bayya ne, saidai kuma bata da amsar da zata bawa kanta.

Komawa tayi ta kwanta bayan ta kashe wayarta ta gaba Ι—aya.

Cike da saΖ™e saΖ™e bacci yayi awungaba da ita.

Ɓangaren Dr Sadeeq ma, sai da yajima yana saΖ™awa da kuncewa, ba abun da yake Ι—aure masa kai, kamar yanda ya kasa fahimtar cewa Zahrah, na son sane ko bata sonsa. da Ζ™yar dai shima bacci ya’iya Ι—aukarsa.

Washe Gari.

Yau tun saven thirty suke da lecture, dan haka da wuri tasoma shirya kanta, sosai tayi kyau cikin shigar jar abaya haΙ—e da jan hijab Ι—in dake jikinta, hand bag Ι—inta ta rayata a bisa kafaΙ—anta. Kana tafice zuwa tsakar gida. Zama tayi akan taburma haΙ—e da jawo farantin Ζ™osai da kuma kofin kunun da Inna ta aje mata tasoma sha. Baffa ne yafito daga cikin Ι—akin sa yanaganin Zahrah yace

“Yauwa kinfito ko, tun Ι—azu kuwa likita yake jiranki a waje”

“Eh Baffa nafito” tabashi amsa cike da mamakin jin cewa wai Dr yajima da zuwa, yanama jiranta a waje, amma kuma bai Ζ™ira ta a waya yasanar mata ba.

AΖ™agauce taci abincin kasancewar har bakwai tayi.

Tana fitowa yasakar mata kyakkyawan murmushi, itama murmushin ta sakarmasa bayan tagama Ζ™aremawa kwalliyarsa ta yau kallo.

“Kinyi kyau my princess!” yafaΙ—a cike da nishaΙ—i, domin kuwa sosai tayi masa kyau, jan kayan da tasa ya karΙ“i kalan fatarta.

“Kaima haka” tabashi amsa a taΖ™aice.

Murmushi yakumayi haΙ—e da buΙ—e mata murfin motar nuni yayi mata da hanunsa alamar tashiga, wani murmushi mai tsayawa a zuciya tayi masa haΙ—e da shigewa cikin motar tayi mawa kanta mazauni.

Tafe suke suna hira cike da nishaΙ—i, wanda gaba Ι—aya yawan hiran Dr ne maiyi mata shi.

A haka har suka iso cikin makarantar, Ζ™oΖ™arin buΙ—e murfin motar ta soma yi.

“Ya haka? baki sallameni ba fa, kike Ζ™oΖ™arin tafiya” Dr Sadeeq yafaΙ—i hakan cikin sigar zolaya.

Murmushi Zahrah tayi masa haΙ—e da yin fari da’idanunta “Bangane ba” tafaΙ—i haka cikin salo.

Lumshe idanunsa yayi haΙ—e da sanya hanu yashafi sajensa, “Inanufin bakice kina sona ba”

Dariya haΙ—e da kunyane suka kama Zahrah sai kawai ta buΙ—e murfin motar tayi ficewarta, domin kuwa bazata iya masa abun da yakeso ba.

Saida yaga shigewarta cikin hall kafun yaΙ—auke idanunsa daga kanta, yanason mace mai kunya gashi Zahrah takasance me kunya. Cike da tarin tunaninta yabar cikin makarantar.

Ita da Husnah suna fitowa a lecture sukayi mawa kansu ma zauni a inda suka saba zama ko da yaushe.

Cike da tsananin farinciki Husnah tace “Naji daΙ—i Ζ™warai Zahrah da kika amincewa Dr, wallahi gayen ya haΙ—u da yawa Ζ™awata, tabbas idan kika auresa kin more don nasan za kisha madaran soyayya!”

Hararan wasa Zahrah ta wurgamawa Husnah, cike da son basar da zancen tashiga shafa cikin ta ” Nifa yunwa nakeji” tafaΙ—a tana mai turo baki gaba.

“Kada dai kice zakimin sakalci, domin niba Doctor bane” Husnah tafaΙ—a cikin tsokana. dukan wasa Zahrah takai mawa Husnah, da sauri Husnah ta kauce.

Cafeteria suka nufa acan suka cika cikinsu, daganan suka sake shiga cikin wani lecture’n.

Jikin wata bishiya dake kusa da Ζ™ofar fita daga makarantar yayi parking motar sa, gyara zama yayi haΙ—e da duba agogon dake Ι—aure a tsintsiyar hanunsa. Kallonsa ya mayar zuwa bakin tangamemen gate Ι—in makarantar tasu, hakanan yakejin ba zai iya fuskantar ta gaba da gaba ba.

AmatuΖ™ar gajiye su Zahrah suka fito a lecture. Tare suke tafe ita da Husnah, domin yau zataimawa Husnah rakiya ne zuwa super market. kai tsaye suka nufi Ζ™ofar fita daga makarantar kasancewa driver’n gidansu Husnah najiransu a waje.

Wani irin faΙ—uwar gaba taji, ya risketa adai dai lokacin da ta fito daga cikin makarantar.

Daga Ι“anagaren Zaid kuwa zuciyarsa ne tashiga dukan uku uku, alokacin da’idanunsa suka sauΖ™a akan Zahrah, hanu yasa ya murje idanunsa domin tabbatarwa da kansa cewa ita Ι—ince kokuwa gizo idanunsa suke masa.

Tabbas itaΙ—ince Zahrah’n sane, har yanzu tananan da kyawunta, dakuma surarta mai Ι—aukar hankalin duk wani lafiyayyen Ι—a Namiji.

“ZAHRAH!” yaΖ™ira sunanta a bayyane, duk da kuwa yasan cewa bazata ji sa ba. dai dai lokacin daya soma yunΖ™urin buΙ—e murfin motarsa don yaΖ™arasa gareta, dai dai lokacin itakuma ta shige cikin mota tare da Husnah.Cikin Hanzari ya buΙ—e murfin motar tasa ya fito, sai dai baikai ga Ζ™arasawa garesu ba, motar su ta gangara kan titi haΙ—e da Ι—aukar hanya.+

Hannayensa duka biyu yasanya ya kama Ζ™ugunsa, haΙ—e da furzar da iskan numfashi ta bakinsa, sam baiso haka ba, amma babu yanda ya’iya dole binsu zaiyi.

Kallonsa yamaida ga sauran cincirindon Ι—aliban da suke tsaye a bakin gate Ι—in makarantar.

Gani yayi gaba Ι—aya sun saki baki da hanci suna kallonsa, sai kace wanda suka ga baΖ™on halitta, bama kamar Ζ΄an matan dake tsaye a wajen.

Tsuka mai sauti yayi haΙ—e da komawa cikin motarsa, da gudun gaske ya cilla motar tasa kan titi, haΙ—e da rufa mawa motar su Zahrah baya.

“Yadai, naga lokaci Ι—aya duk kinyi wata iri dake?” Husnah tatambayi Zahrah wacce tazama silently lokaci Ι—aya.

A jiyar zuciya ta sauΖ™e haΙ—e da maida kallonta ga Husnah ” FaΙ—uwar gaba nakeji Husnah, ban kuma san dalilin hakan ba” Zahrah ta faΙ—i haka cikin damuwa.

“To fa, Allah dai ya tsare, amma ki yawanta addu’a, domin hakanne zaisa koma mene ne yazo da sauΖ™i” inji cewar Husnah.

“Insha Allah!” Zahrah tafaΙ—i hakan tana mai kwantar da kanta a jikin kujeran motar, tanajin Husnah tace da Driver’n ya karkata akalar motar, ta sanja shawara shoprite kawai zasuje, bamusu kuwa ya sanja hanya zuwa Shoprite Ι—in. Itadai Zahrah batace dasu komai ba.

Basu wani jima suna tafiya ba, suka iso tangamemen Shoprite Ι—in. “Muje ko” Husnah tace da Zahrah tana mai Ζ™oΖ™arin buΙ—e murfin motar.

Cikin sanyin jiki Zahrah, tafito daga cikin motar suka nufi cikin shoprite Ι—in.

Basket biyu Husnah ta Ι—auka nata Ι—aya na Zahrah ma Ι—aya, acewarta Zahrah ta zaΙ“i duk wani abun da take so, sam bahaka Zahrah tasoba amma babu yanda ta’iya, domin kuwa Husnah kafiya gareta, idan tace kayi abu tofa wai dole sai kayi.

Kayan shafa suka soma Ι—auka, kafun suka garzaya zuwa kan su jaka da takalma Ζ΄an yayi, basu tsaya anan ba hadda kayan ciye ciye sai da suka Ι—auka.

Cike da gajiyawa Zahrah ke tura Basket Ι—in da kayanta ke ciki, ita mamaki ma take yanda Husnah tasa suka jidi kaya mai yawa har haka, amma idan tayi la’akari da irin gata da kuma kuΙ—in da mahaifin Husnah ke dashi, to sai tagama ba wani abun mamaki bane, kuma kuΙ—in kayan bazai mawa Husnah wahalar biya ba, domin kuwa anshagwaΙ“ata sosai agida.

Daki daki aka lissafa kayan nasu, inda Zahrah ta Ι—auki kayan dubu ishirin Husnah kuwa na dubu ishirin da biyar ta eba, Ζ™oΖ™arin miΖ™a wa Cashier ATM card Ι—in dake hanunta Husnah ta soma yi. Amma sai Cashier’n yayi murmushi haΙ—e da cewa

“Ai Hajiya ba’a buΖ™atar kuΙ—in ku, domin kuwa an riga da an biya muku, tunkafun ku kammala sayayyan, sannan wanda yabiya muku yace idan ma kuna da buΖ™atar Ζ™ari, to kukoma ku Ζ™ara, duk shi zai biya kuΙ—in”

Cike da mamaki Zahrah da Husnah suka shiga kallon juna.

“Anbiyamana fa kace Cashier? shin ka kosan me kake cewa?” Husnah tatambayeshi cike da mamaki.

STORY CONTINUES BELOW

“Ƙwarai kuwa nasan me nake cewa, kudai ku Ι—au kayanku kawai kuje, sannan ku gode mawa Allah, don shi yaje fo muku tsuntsu daga sama gasashshe ” Cashier’n nan yafaΙ—i haka yana mai washe baki, kasan cewar shima anbarmasa kyautan ragowan canjin su.

Mamakine ya lulluΙ“e su Zahrah domin su a iyaka sanin su basu da wani wanda zai biya musu kuΙ—in siyayyan da sukayi, domin kuwa basu zo da kowa ba banda driver, inakuwa driver zaisamu maΖ™udan kuΙ—aΙ—e irin haka har ya biya musu kuΙ—in siyayya alhali shima yana fama da kansa.

“Kozaka iya faΙ—amana wanda ya biya mana kuΙ—in ?” Husnah ta tambaya.

“A gaskia bansan saba, sai dai da duk kan alamu irin larabawan nan ne da suke zuwa Nigeria lokaci zuwa lokaci” Cashier Ι—in nan yafaΙ—a musu haka, domin shi a yanda yafahimta, da dukkan alamu wanda.yabiya musu kuΙ—in baiyi zubi da Ζ΄an nan gida Nigeria ba, duk da kuwa cewa muma muna da kyawawan maza amma kuma kyawun wani ya Ι—are na wani.

Idanu Zahrah da Husnah suka zaro atare, sakamakon jin abun da Cashier yace.

“Balarabe fa kace?” Husnah ta sake tambaya cike da mamaki.

“Eh Balarabe, kece Zahrah ko?” Cashier’n nan ya tambaya yana mai nuna Zahrah da hanunsa.

“Ya’akayi kasan sunana ?” Zahrah ta tambayesa cike da mamaki.

Murmushi kawai yayi haΙ—e da miΖ™a mata wata farar takarda.

“Ungo yace inbaki”

Cikin tsoro Zahrah ta karΙ“i takardan da Cashier ke miΖ™o mata, haΙ—e da buΙ—ewa.

_”KiΙ—auki duk wani abun da kikeso MY ZAHRAH! ban damuba koda duka Shoprite Ι—in zaki ce kinaso, zan iya mallaka miki kome kikeso a duniyar nan, ko da kuwa dukiyata zata Ζ™are”_ abun da aka rubuta a jikin takardan kenan.

Wani irin bugawa Zahrah taji Ζ™irjinta yayi, “To waye?” tatambayi kanta a fili.

“Yadai me aka rubuta acikin takarda’n?” Husnah ta tambayi Zahrah cike da zaΖ™uwa.

Bata takarda’n Zahrah tayi domin batasan me zatace da’ita ba.

Husnah tana gama karanta takarda’n tasaki murmushi haΙ—e da kallon Cashier’n nan daya zura musu idanu… “Mungode sosai, idan ka haΙ—u da wanda yabiyamana kuΙ—in, ka isar mana da saΖ™on godiya” daga haka ta kama hanun Zahrah suka fice daga cikin Shoprite Ι—in, bayan sun Ι—au ledodin siyayyarsu.

“Saida sukazo bakin mota kafun Husnah ta saki hanun Zahrah, still fuskarta Ι—auke da murmushi tace “Mekika fahimta game da wannan takardan, da kuma biya mana kuΙ—in sayayya da akayi?”

Cikin Ι—aurewar kai Zahrah tace “Ni ban fahimci komai ba, sai ma tsananin mamaki da nake, taya haka zata kasance, anya kuwa ba wata maΖ™arΖ™ashiyan ake shirin Ζ™ulla mana ba Husnah?”

Dariya sosai Husnah ta kwashe dashi, domin kuwa maganar Zahrah takai a dara.

“MaΖ™arΖ™ashiyan soyayya ba, babu wani aljanu, kawai dai inaga wani ne yaganki kuma ya yaba, shine kawai” Husnah tafaΙ—a tana mai danne dariyanta.

“Bangane ba me kike nufi?” Zahrah ta tambaya cike da ruΙ—u, domin ita kwata kwata ma bata fahimci inda kalaman Husnah suka dosa ba.

“Kada ki damu zaki gane mushiga mota”

Jiki a sanyaye Zahrah tabuΙ—e murfin motar tashiga, a gidan baya sukai mawa kansu masauΖ™i ita da Husnah..

Suna shiga driver yayi mawa motar key suka Ι—auki hanyar Suleja unguwar su Zahrah.

(yauwa kuyi haΖ™uri jiya nayi mistake sunan unguwar su Zahrah ba Maraba bane, sunan unguwarsu Zahrah Suleja ne, kainane ya Ι—au charge shiyasa)

Yanaganin tafiyarsu yasaki Ζ™awataccen murmushinsa, “Haryanzu tananan da halinta na tsoro, yayi imani Zahrah bazata taΙ“a sanjawa ba”

” komai naki yana burgeni Zahrah, inason komai naki!” Zaid dake cikin motarsa yafaΙ—i haka cike da shauΖ™i.

STORY CONTINUES BELOW

“Nifa gaba Ι—aya kaina ya kulle, kimin bayani mana Husnah, me takardan nan take nufi ne?” Zahrah tafaΙ—i haka cikin zaΖ™uwa.

“Ki kwantar da hankalinki Ζ™awata, kawai dai bazai wuce irin mutanen nan masu alkhairi bane suka aikata hakan, wayasani ma ko Dr Sadeeq ne” Husnah tafaΙ—i hakan tana mai kallon Zahrah.

“Mene? kinanufin wai Doctor ne zaiyi haka? gaskiya banjin cewa shi ne, domin idan da shi ne, dole zai bayyana kansa na gansa, kodai ke akeso amawa wannan hidiman akayi mistake aka ambaceni” Zahrah tafaΙ—i haka cikin kokonto.

Dariya Husnah takuma sawa, haΙ—e da dafa kafaΙ—an Zahrah..

“Wai lafiyanki kuwa Zahrah? kinga yanda kika firgice lokaci Ι—aya sai kace wacce ta aikata aikin rashin gaskiya, to ni miye ma abun damuwa ne don wani yabiyamana kuΙ—in sayayya? kinga bafa mu muka sa sa ba, ko ma waye shi yasanya kansa, kishare kawai Ζ™awata” Husnah taΖ™are maganar ta ta bayan ta Ι“are sweet ta jefa acikin bakinta.

“Hmmm” kawai Zahrah ta’iya cewa, haΙ—e da mai da kanta jikin kujera, itakam gaba Ι—aya kanta ya kulle, taya za’ace bakasan mutum ba, amma kuma ya biyamaka kuΙ—in siyayyan da kayi, irin haka ne mutum sai yaje ya jefa kansa a matsala.

Tafiya suke amma Zahrah ta kasa cewa komai, sai ma Husnah ce keta Ζ™oΖ™arin janta da hira, amma jefi jefi take amsa mata, domin kuwa wannan faΙ—uwar gaban da takeji har yanzu baidaina ba.

A haka har suka iso Ζ™ofar gidan su Zahrah’n… Har cikin gida Husnah tayimawa Zahrah rakiya, kana ta fito tashiga mota suka tafi.

Zama tayi akan katifarta haΙ—e da zubawa kayan siyayya da sukayi ido, sam zuciyarta bata kwanta da wanda yabiya musu kuΙ—in kayan ba, zuwa yanzu ya kamata ace tayi hankali, domin sarai yanzu tasan salon yaudaran maza baida Ζ™arshe, suna iya yimaka komai don su samu biyan buΖ™atarsu, wannan yana Ι—aya daga cikin babban dalilin da yasanya ta amince da auren Dr Sadeeq, ko ba komai idan ya aureta ta tsallake wani babban siraΙ—i na daga yaudaran da Maza sukeyi mawa Ζ΄an mata a wannan zamanin.

Ƙaran wayartane yakatseta daga tunanin da takeyi, cikin sanyin jiki ta Ι—aga Ζ™iran nasa, haΙ—e da kara wayar akan kunnen ta.

“Barkanki da hutawa My Princess!”

Dr Sadeeq yafaΙ—a cike da tsantsar kulawa.

Ɗan guntun murmushi tayi haΙ—e da cewa “Kaima barkanka dai ya aiki?”

Ɓata fuska yayi tamkar dai tana ganinsa haΙ—e da cewa “Aiki ba daΙ—i kokaΙ—an, ya kundawo a super market Ι—in kenan?”

“Eh” tabashi amsa a taΖ™aice. Domin tsabar gajiyan da ta kwaso har wani bacci bacci takeji.

“Naga kamar kingaji da yawa, ki samu ki Ι—an huta, zuwa anjima zanzo gida, inaso na samu Baffa, idan yabani dama zanturo magabata na ayi maganar auren mu, domin banso akai nanda wata Ι—aya ban mallakeki ba!” yaΖ™are maganar cikin yanayin shauΖ™i.

Wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, sakamakon jin abun da Dr Sadeeq yace. Wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki, wanda baza’a Ζ™irasa da farinciki ba, ba kuma za’a Ζ™irasa da yanayin baΖ™in ciki ba.

“Zahrah na!” yaΖ™ira sunanta jin cewa tayi shiru batace dashi komai ba.

“Umm” ta’amsa masa a kasalance.

“Naji kinyi shiru, ko dai bakiyi farinciki da hakan bane?”

Yajefo mata tambayar da batayi zaton zai mata shi a yanzu ba..

“A’a nayi farinciki mana, kawai dai kainane ke Ι—an min ciwo” tafaΙ—i haka don ta kare kanta, gudun kada yafuskanci wani abu.

“Ayya kiyi haΖ™uri, anjima idan zanzo zan tahomiki da magani ko, yanzu ki kwanta ki huta, nasan ma stress ne, insha Allah zuwa anjima zaki ji ki normal” yafaΙ—i hakan cike da kulawa.

STORY CONTINUES BELOW

“To” kawai ta’iya cewa dashi, haΙ—i da zare wayar akan kunnen ta.

Nannauyar ajiyar zuciya ta sauΖ™e, haΙ—e da share ruwan hawayen da suka fito daga cikin idanunta. “Yazama dole nakoyi soyayyarka Dr Sadeeq, domin bayan kai babu wani wanda zai bani kulawa kamar haka, ya Allah kamin maganin matsalolina!” tafaΙ—i hakan a bayyane, bayan ta Ι—aga idanunta zuwa sama.

Da Ζ™Ζ΄ar ma ta’iya cusa abincin da Inna ta bata, domin kuwa hakanan taji zuciyarta ta cunkushe.

Kwanciya tayi akan katifarta tana Ζ΄an tunani, take bacci Ι“arawo ya siΙ—aΙ—o ya Ι—auketa, batare da tashiryawa hakan ba….

Zaune yake akan wata haΙ—aΙ—Ι—iyar kujera, wanda take ita kaΙ—aice kuma na mussaman acikin bedroom Ι—insa, dake cikin guest hause nashi. Ι—an Ζ™aramin table ne aje a gabansa, wanda samansa ke Ι—auke da zungureriyar kwalbar wine da kuma glass cup.

Wayar sace riΖ™e a hanunsa, gaba Ι—aya hankalinsa akan wayartasa yake, murmushine Ι—auke akan fuskarsa, yayinda yake playback Ι—in vedi’on daya mata Ι—azu fitowarta daga cikin shoprite, batare da ta sani ba.

Harzuwa yanzu bai tantance mai yakeji a jiki da zuciyarsa ba a game da Zahrah, abu Ι—aya yasani shine, yasan cewa “yana matuΖ™ar buΖ™atarta a kusa dashi, fiye da tunanin mai tunani, yakuma Ι—auki haka, amatsayin fitinanniyar sha’awarta da yake” sake playback Ι—in vedion yayi bayan yakai Ζ™arshe akaro na barkatai domin kuwa yayi playback Ι—in vedi’on yafi sau goma daga zamansa a wajen zuwa yanzu.

Wani irin sanyi haΙ—e da kewarta ne suke ratsa zuciyarsa alokaci guda.

“A hankali zankuma cimma burina akanki Zahrah, akaro na biyu ma ina da tabbacin cewa zanyi nasara akan ki, domin niban kasance Loser ba, bakuma zantaΙ“a kasancewa Loser ba, har abada !” yafaΙ—i haka cike da son Ζ™arfafamawa kansa guiwa.. A taΖ™aice dai haka Zaid yayita playback na vedio Ι—in da yayi mawa Zahrah yana kallo, zuciyarsa cike da nishaΙ—i, abu Ι—ayane zai hanasa zuwa gareta a yanzu, shine plan Ι—in daya shirya mata, bakuma zai je gareta ba, harsai ya tabbatar da cewa ta gama rufzawa cikin tarkonsa, da ya Ι—ana mata a karo na biyu….

(?)

Doctor Sadeeq ne tsugune a gaban Baffa Amadu, wato Ζ™anin mahaifinsa. Bayan ya gama kora masa bayanin duk abun dake faruwa, hatta fΖ΄aΙ—e’n da akayimawa Zahrah bai Ι“oye masa ba, domin kuwa a yanzu Baffa Amadu shine Uba a garesu, kasancewarsa Ζ™anin mahaifi’nsu.

Ajiyar zuciya Baffa Amadu yasauΖ™e, haΙ—e dayin gyaran murya irin tasu ta manya…

“HaΖ™iΖ™a kazo da babbar magana Sadeeq, amma kuma duk na fahimceka, bakuma zanyi Ζ™asa a guiwa ba wajen ganar da mahaifiyarka dakuma Ζ΄ar uwarka, amma kuma kasan dole sai an haΙ—a da haΖ™uri, kasan su mata koda yaushe tunaninsu baya zurfafa, bakuma ko da yaushe suke gane abun da ake so su fahimta ba, amma tunda kakawo matsalan nan wajena, ka kwantar da hankalinka, ni nan zanje har gida na samu mahaifiyartaka, zamu tattauna akan matsalan!”

Wani irin sanyin daΙ—i ne yashiga huda zuciyar Dr Sadeeq, sai yanzu yakejin nutsuwa na sauΖ™ar masa, yanzu fatan sa Ι—aya, shine Allah yasa mahaifiyarsa ta amince, amma tabbas Zahrah itace burin ran sa…

Daga haka sukayi sallama da Baffa Amadu, bayan ya tabbatar masa cewa lallai zaice yasamu mahaifiyartasa da batun…

Cike da farinciki Dr Sadeeq yabaro gidan Baffan nasa, kai tsaye gidansu ya nufa….

Zama yayi dirshan akan kujeran dake falonsa, haΙ—e da soma cire safar Ζ™afansa, fuskarsa cike take da annuri dagani kai kasan yanacikin farinciki…

Turo Ζ™ofar falon nasa akayi da Ζ™arfin gaske, wanda hakan yatilasta masa Ι—ago kansa da sauri, don ganin ko waye.

Dammm haka yaji Ζ™irjinsa yabuga, sakamakon ganin fuskar Hajiyarsa da yayi babu ko Ι—igon annuri akanta, saima wani irin mugun kallo da take jifansa dashi.

STORY CONTINUES BELOW

Cike da girmamawa yace “Hajiya Barkanki da…..”

Saurin Ι—aga masa hanu tayi, alaman batason jin komai daga garesa..

Cikin Ι“acin rai da tuΖ™uΖ™in zuciya Hajiya tasoma cewa….

“Lallai ka haifu Sadeeq, tunda har zaka iya kai Ζ™arana wajen Ζ™anin mahaifinka, yanzu akan wata watsatstsiyar yarinya, ka ke neman ka bijirewa auren Ζ΄ar uwa kuma aminiyata da aka baka? Ashe dama wacce kake ikirarin kana so Ι—in, ba cikakkiyar mace bace, sauran layine? kaban mamaki Ζ™warai Sadeeq, amma bakomai ni na sakema har haka ta faru, kuma tabbas zanΙ—auki Ζ™waΖ™Ζ™waran mataki akan ka, daga kai har sakaryar yarinyar da ka bawa soyayyarta amanna, bansan cewa rashin hankalin naka har yakai haka ba, ashe har zuwa kamun Ζ™afa wajen mutane kakeyi, akan cewa azo a bani baki, nabarka ka auri wacce tagama raba budurcinta ga mazan layi, hmmm wallahi kasaurari hukuncin da zan yanke, kuma tun wuri ka gaggauta cire tunanin auren wannan yarinyar aranka, domin kuwa bamai yi wuwa bane!” fuuu haka Hajiya ta juya ta fice daga falon nasa ranta amatuΖ™ar Ι“ace…

Kalmar “Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un!”

Shine abun da yafito daga bakin Dr Sadeeq, wanda yasanya hannayensa gaba Ι—aya ya dafe kansa… “Me yasa Aunty Raliya? meyasa zakimin haka?” yatambayi kansa cikin takaici dakuma Ι“acin rai. Tabbas yasan Aunty Raliya ce ta sanar da Hajiyansa komai, domin kuwa lokacin da yake gaban Baffa Amadu ta Ζ™irasa, bai Ι“oyemata ba kuma yashaida mata cewa yana gidan Baffa Amadu’n, ashe ita harta gane mai yakawosa, shine kuma tasanar da Hajiyarsu komai… Take idanunsa suka kaΙ—a sukai ja,, ba abun da yake masa ciwo kamar aibata Zahrah da akeyi, kowa idan yatashi sai yajefeta da sunan wacce ta watsar da mutumcinta a waje, alhalin kuma itama ba laifinta bane, Ζ™addarace dakuma tsautsayi, domin kuwa shi kansa sheda ne akan abun da yafaru da’ita, tunda har kusan haukacewa tayi. Rasama me yake masa daΙ—i yayi, da wanne zaiji ne? da soyayyar Zahrah, ko kuma da fushin da Hajiyarsa keyi dashi. Gaba Ι—aya ma ji yayi zazzaΙ“i nason kamasa don haka kawai sai ya koma Ι—akinsa ya kwanta, ba abunda yake ambata sai sunan Allah, domin kuwa shi kaΙ—ai ne zai iya kawo masa Ι—oki,, dama kuma mu dashi muka dogara shine mai kowa kuma mai komai, sarkin da babu kamarsa, Allah kenan buwayi gagara misali, maiyin duk yanda yaso mai kuma Ζ™wacewa da kuma bayarwa alokacin da yaso, ga kuma duk wanda yaso…..

Zahrah kuwa tunda ta faΙ—a duniyar bacci ba’ita tafarka ba, sai gaf da’ana Ζ™iraye Ζ™irayen sallan magriba.. Kaitsaye banΙ—aki ta wuce taje tayi wanka haΙ—e da Ι—auro alwala tazo ta kabbara sallan magriba.

Kayanta marar nauyi tasanya haΙ—e da Ι—auΖ™an wayarta dakuma ledan da kayan siyayyanta ke ciki, tafito farfajiyar gidan nasu, zaune ta iske Inna tana faman Ζ™oΖ™arin kunna redio’nta, wanda koda yaushe take tare dashi kamar jaraba.

“Barka da dare Inna” Zahrah tafaΙ—a lokacin da tayi mawa kanta mazauni a kusa da Inna’n.

Inna bata amsata ba, saima kafe ledar dake hanun Zahrah’n da tayi da ido, Allah Allah take taga mene acikin ledar, domin dama bakinta ya bushe neman abun lasawa takeyi, kasancewar tuwo ta tuΖ™a abincin dare, bakuma tajin cinsa, tafison tasamu Ζ™walam taΙ—an lasa, like o’o da o’o lol.

Tun Zahrah batakai ga buΙ—e ledar ba inna tayi gajen haΖ™uri haΙ—e da fusge ledar daga hanun Zahrah tashiga dubawa.

Ganin cewa tarkacen su Chocolate’s da kuma su biscuit’s ne acikin ledar yasanya Inna jan uban tsuka haΙ—e da bankamawa Zahrah harara.

“Aikin kenan gayyar tsiya, mutum yasan bakacin abu, amma saboda tsinannen baΖ™inciki dakuma mugunta, ko da yaushe shiyake saya bini bini, bazai sayo abun da duka gida za’a amfana ba mcheeww!” cikin Ζ™ufula Inna taΖ™are maganar, domin kuwa ita duk wannan shirmen banzan basonsu take ba, tafiso taga daΖ™walen kaza, kokuma gasheshshen nama mai zafi, yauwa tanan tafi kauri, amma kwata kwata kayan kantin nan ita ba zaΙ“inta bane.

Da Ζ™yar Zahrah ta iya danne dariyan Inna dake cikinta aciki.

BuΙ—e ledan tayi gaba Ι—aya haΙ—e sa sanya hanunta taciro wani Ι—an madaidaicin cake wanda daganinsa kasan yasha madara.

“Ungo wannan Inna shikan nasan zaki iyaci, saboda kema nasayoshi” Zahrah tafaΙ—i haka tana mai miΖ™amawa Inna cake Ι—in.

“Yauwa kokefa, amma da kya bani wasu tarkacen banza”

Take Inna ta Ι“are cake Ι—in, tahau ci har lumshe idanu take, domin dai sosai cake Ι—in yamata daΙ—i.

Murmushi kawai Zahrah tayi haΙ—e da gyara zamanta, tasoma latsa wayarta….

Wani yarone yashigo cikin gidan bakinsa Ι—auke da sallama, atare Inna da Zahrah suka amsa masa.

“Wai ana Ζ™iran Zahrah a waje” inji cewar yaron..

Wani irin faΙ—uwa Zahrah taji gabanta yayi harsaida tasanya hanu ta dafe Ζ™irjinta……Wani irin faΙ—uwa Zahrah taji gabanta yayi har saida ta sa hanu ta dafe kirjinta daya fara dukan uku uku…..+

“Jekace tana zuwa” Inna tace da yaron,, bamusu yaron yajuya yafice daga cikin gidan…

“Yadai lafiyanki kuwa naga kinwani dafe Ζ™irji?” Inna tatambayi Zahrah, wacce lokaci Ι—aya yanayinta ya sauya.

“Bakomai” Zahrah tafaΙ—a a taΖ™aice domin kuwa ko tayi Ζ™oΖ™arin ganar da Inna halin da take ciki tofa bazata gane ba…

“Tashi maza kije, ba kyau yin watsi da baΖ™o, wata Ζ™ilama da alkhairi yazo miki, domin na lura keΙ—in baki da Ζ™ashin tsiya” Inna tafaΙ—i hakan lokacin da ta miΖ™e daga zaunen da take.

Cikin sanyin jiki Zahrah takoma Ι—aki ta Ι—auko Ζ™aton hijab Ι—inta ta sanya.

Tun kafun ta Ζ™arasa fita daga zauren gidannasu zuciyarta tasoma bugawa, wanda batasan dalilin hakan ba.

Wata mota ce tagani fake a Ζ™ofar gidan nasu, kasancewar akwai hasken wuta, yasanya har kalan motar tana’iya hangowa.

Tsayawa tayi cak daga inda take, domin bazata sake tabka babban kuskuren da ta tabka a baya ba,  batasan waye ba don haka bazata Ζ™arasa ba, idan wanda ke cikin motar yagaji ya fito, ya isketa daga inda take tsaye…

Cikin hanzari wani wanda baza’a Ζ™irasa da suna matashi ba,  bakuma za’a Ζ™irasa da suna tsoho ba, yafito daga cikin motar hanunsa Ι—auke da wani kwali, yayinda aka Ι—aura wani kyakkyawan flower a saman kwalin… Ganin yanufota kaitsaye yasanya ta Ι—an sake ja da baya..

“Sannu da fitowa ranki shi daΙ—e” mutumin nan yafaΙ—a..

“yauwa sannu” Zahrah ta bashi amsa a taΖ™aice…

” dama saΖ™one aka bani nakawomiki” wannan mutumin ya kuma faΙ—a cikin rusunawa haΙ—i da girmamawa, duk da kuwa cewa shiΙ—in ba yaro bane, domin yakusan haifar  Zahrah’n ma, domin itama bawani yawan shekaru ne da’ita ba…

Cike da tsananin mamaki Zahrah, ta saki baki da hanci tana kallon mutumin dake tsaye a gabanta, yana miΖ™omata saΖ™on dake hanunsa…

“Wayekai?” shine kawai abun da ya iya fitowa daga bakinta, saboda gaba Ι—aya kanta ya kulle…

Murmushi mutumin yayi haΙ—e da cewa “Ba’a bani daman sanar  dake koni waye ba, kawai dai an umarceni dana kawomiki wannan saΖ™on, sannan dan Allah kada kice bazaki ansaba, saΖ™one mai mahimmanci, yanada kyau ki karΙ“a, sannan daganinki ke mai ilimi ce, kinsan bakyau maida hanun kyauta baya!” mutumin yafaΙ—i haka still yana mai sake miΖ™o mata kwali da flowern dake riΖ™e a hanunsa…

Kai Zahrah tashiga gyaΙ—awa, cike da tsarguwa tace ” Kana da girma da kuma mutumcin da bazanyimaka gardama ba, amma kuma saidai kayi haΖ™uri, bazan karΙ“i abu daga wanda bansani ba, bankuma san menene nufinku a kai na ba” tafaΙ—i hakan da iyaka gaskiyarta….

STORY CONTINUES BELOW

“Hakane, amma ki ceci aikina, domin wanda ya ban saΖ™onnan nakawo zuwa gareki ya tabbatarmin da cewa, idan har baki karΙ“i saΖ™on ba, to abakin aikina, kitaimaka, ina da iyalai, kuma da aikina na dogara” mutumin yafaΙ—i haka cikin rauni.

Zaro idanu Zahrah tayi haΙ—e da jinjina maganar mutumin aranta, lallai kuwa kowaye ya aikosa yacika Ι—an jin kai,  ita kuma irin mutanen da tafi tsana kenan a rayuwarta wato mutum mai jin kansa….

Cike da kokonto haΙ—i da zullumi tasanya hanu ta karΙ“i abun da mutumin ke miΖ™omata.

“ZankarΙ“ane kawai saboda kai, domin na fuskanci rashin karΙ“ana zai iya sanyaka acikin matsala, amma koma waye ya turoka kace masa injini ya sanja hali, domin wannan ba hali mai kyau bane” daga haka tasakai tayi komawarta cikin gida..

Cike da murna’n cewa ta karΙ“i saΖ™on wannan mutumin yakoma mota haΙ—e da yi mata key yabar area’n unguwar tasu….

Zahrah tana shiga gida kaitsaye Ι—akinta ta wuce, yayinda Inna ta rakata da  idanu…

Zama tayi akan katifa, haΙ—e da tsurawa kyakykyawan kwalin nan idanu, ba iya shi kaΙ—ai bane, abun Ι—aukar hankali, hadda wannan haΙ—aΙ—Ι—en flower’n dake samansa ma abun burgewane, alal haΖ™iΖ™a ma ita flower’n ne yafi Ι—aukar hankalinta….

Cikin sanyin jiki tasa hanu ta Ι—auki flower’n haΙ—e da matso dashi kusa da fuskarta….lokaci Ι—aya ta zabura haΙ—e da wurgi da flower’n gefe, take idanunta suka kaΙ—a sukai jajur dasu, jitayi kanta yafara juyawa,  tabbas bazata taΙ“a mantawa da wannan Ζ™amshinba har abada kuwa, ajikin mutum Ι—aya tasan wannan Ζ™amshi, bayan shi kuma batasakejin Ζ™amshin a jikin kowa ba,, hannayenta ta sanya duka biyu haΙ—e da dafe kanta dayake sara mata,, tabbas irin Ζ™amshinsa fulawar nan keyi, take taji wani irin tsanar flower’n  ya cika mata zuciya,  san nan kuma tsanarsa tasake dawo mata sabuwa fil, cike da Ι“acin rai ta Ι—auki flowern haΙ—e da fita waje da’ita, ko son ganinta ma batason yi,   kai tsaye wajen da suke aje  shara ta nufa, cike da tsanar  flower’n ta jefa ta cikin kwandon shara, haΙ—e da furzar da yawu akan flower’n duk wani abu da zai tuna mata da Zaid ta tsanesa…

Ranta a Ι“ace takoma Ι—aki, ita dai Inna dake zaune a tsakar gidan haka ta saki baki galala tana ganin ikon Allah..

“Wallahi na tsaneka, tsana mafi muni, bantaΙ“ajin tsanar wani a raina sama da wanda nakeyi maka ba,  ya Allah kada ka sake haΙ—a fuskata da tasa!” tafaΙ—i hakan a bayyane, kuma cikin tuΖ™ewar murya…

Gaba Ι—aya Ζ™amshin da taji flower’n nan nayi ya Ι—aga mata hankali,  sabuwar tsanar Zaid yasake Ι—arsuwa acikin zuciyarta…

Lallai da zataga wanda yasanya akawo mata flower’n nan da ta gargaΙ—esa da kada ya sake kawo mata komai nasa, don bata so, domin kuwa duk wani abu da zai sanya tayi tunanin Zaid bata Ζ™aunarsa, koda sunansa nema batason ji”

Kwanciya tayi lamo akan gado, tana mai da numfashi, ji takeyi gaba Ι—aya ta tsani Ι—akin nata, domin kuwa Ι—akin gaba Ι—aya ya Ι—au Ζ™amshin turaren dake jikin flower’ Ι—in nan….

Wayartace tasoma Ζ™ara alamar shigowar Ζ™ira, ganin Dr Sadeeq ne me Ζ™ira yasanya ta Ι—aga wayan, cikin son Ι“oye damuwarta..

“InaΖ™ofar gida” abun da Dr Sadeeq yafaΙ—a kenan, a cikin wayar, domin kuwa shima dai yauΙ—in yana cikin damuwa….

Babban tabarma ta shumfuΙ—a musu a tsakar gida, kafun tanufi Ζ™ofar gida don yi masa iso..

Kusan tare suka shigo cikin gidan, tana gaba yana biye da’ita a baya.. Gaba Ι—aya yagama karantar yanayinta, ya kuma gane cewa tana cikin damuwa.

Zama yayi akan tabarman da ta shumfuΙ—a musu,  haΙ—e da tanΖ™washe Ζ™afafunsa.. Gaba Ι—aya nutsuwarsa ya miΖ™a zuwa gareta, ta hanyar zuba mata idanu….

Gyara zama Zahrah tayi haΙ—e da Ι—aga idanunta ta saci kallonsa, aikuwa karab idanunsu suka sauΖ™a akan na juna.. Cikin son basarwa tace ” Sannu da zuwa, ya hanya?”

STORY CONTINUES BELOW

Ajiyar zuciya ya sauΖ™e haΙ—e da lumshe idanu…”Hanya ba daΙ—i duk nagaji da tuΖ™in ma, i hope you will find a driver that will take me home” cikin zolaya yaΖ™are maganar..

Kallonsa tayi kawai,  haΙ—e da yin Ι—an murmushi, shiru tayi batare da tace dashi komai ba…

“Meke damunki naganki haka, ko dai ciwon kanne?” Yatambayeta cike da kulawa..

“No bashi bane, ka wai dai gajiya ne, baisakeni ba haryanzu” tafaΙ—i hakan a taΖ™aice…

“Kansa yajinjina, haΙ—e da sake lumshe idanunsa,  shi Ι—inma Ζ™arfin haline kawai yasa sa yazo, amma tabbas damuwar dake damunsa tana da yawa.

“Meke damunka, naga gaba Ι—aya kamar baka cikin farinciki?” Zahrah ta tambaya cikin siga da yanayi na nuna damuwa..

Wani irin sanyin daΙ—i yaji a zuciyarsa, badon komai ba, saidon kulawa da yasamu daga gareta.

Gyara zamansa yayi haΙ—e da bata duka nutsuwarsa….”Bazan Ι“oyemiki ba Zahrah, tabbas inacikin damuwa, kuma duk akan kine,  Ina tsananin sonki Zahrah, ina da burin baki farinciki a cikin rayuwarki,  amma sai dai na  haΙ—u dake a Ζ™urarren lokaci, inafata zaki fahimci abun da zance dake?”

Cike da Ι—aurewar kai Zahrah take kallon Dr Sadeeq, domin kuwa sam ita bata fahimci inda kalamansa suka dosa ba.

“Mahaifiyata ta zaΙ“amin matar da zan aura, yanzu haka maganar da nakeyi miki, har ansanya mana rana, saura sati uku”

dummm haka Zahrah taji Ζ™irjinta yabuga, duk da cewa bata wani jin son Dr Sadeeq a ranta, amma bazata taΙ“a so kyakkyawan namiji mai nagarta kamarsa ya kuΙ“uce mata ba, take idanunta suka ciko da Ζ™walla wanda batasan na menene ba.

“Dan Allah kada kiyi kuka kinji Zahrah na, nafaΙ—amiki hakane don kisan halin da nake ciki, amma bawai hakan nanufin bazan aureki bane ba”

Cike da kulawa yakama duka hannayenta biyu, haΙ—e da kafeta da idanu.  Gaba Ι—aya abun da yake wakana ya kwashe ya faΙ—a mata, hatta maganarsa da Baffa Amadu, saida  ya sanar da’ita, sai dai ya Ι“oye mata Ζ™iyayya dakuma maganganun da yayarsa da kuma mahaifiyarsa suka faΙ—a akan ta na Ι“atanci.

Cigaba yayi da cewa “Ki kwantar da hankalinki, na miki alΖ™awari nan bada jimawa ba, zaki zamo mallaki a gareni, insha Allah zanzamo mijinki Zahrah!”

Hawayene suka shiga zirya akan fuskan Zahrah, cikin murya mai rauni tace ” Dama nasan cewa nayi ganganci, domin kuwa kai ba sa’an aure na bane,  nagode sosai da irin kulawa da kuma Ζ™oΖ™arin da kayi a kaina, bakuma zan taΙ“a mantawa da hakan ba, na yarda da Ζ™addara mai kyau ko marar kyau, idan aurena dakai baiyi wu ba, na yarda haka Allah yatsara,  tun da  fari shiya gurΙ“atamin rayuwa, ya cutar dani, cuta mafi muni, ta yanda babu wani wanda  zai lamuncewa haΙ—a zuri’a dani, tabbas daman nasan koda kai ka aminta da aurena, ba lallai iyayenka su aminta ba?….Kukane ya Ζ™wace mata sosai.

Sake damΖ™e hannayenta yayi acikin nasa, haΙ—e da kafeta da idanu, sosai tausayinta ya sake kamasa.

“Kinaso nasake shiga cikin damuwa ne Zahrah?” yayi maganar cikin tausasa murya.

Bata iya amasa masa ba, sai gyaΙ—a masa kai da tayi alamar “A’a”

“To idan har bakyaso nasake shiga damuwa, ki daina kuka kinji Zahrah na, insha Allah, zamu rayu tare dake, harma ki haifamin kyawawan babies, masu kyau kamarki, masu irin idanunki, da bakinki, harma da irin hancinki, da kuma…” sai yayi shiru, yana mai dariya Ζ™asa Ζ™asa.

Kunyane ya kama Zahrah haΙ—e da dariya, duk da kuwa cewa tana cikin halin damuwa, sai kawai ta kawar da kanta gefe, gaba Ι—aya jinta take a tsarge sakamakon hanunta da ke saΖ™ale acikin nasa…

“Zantafi saboda naga dare yasoma yi, amma saikinmin alΖ™awarin cewa bazakiyi kuka ba, bakuma za kisa kanki a damuwa ba, idan kikayi haka zanji daΙ—i sosai”

STORY CONTINUES BELOW

Abune mai matuΖ™ar wuya, a dake ka sannan a hanaka kuka, amma tabbas zata jarraba wajen daure zuciyarta.

“Bazanyi kuka ba” tafaΙ—a cikin muryar da bata fita sosai, da badon yana kusa da’ita sosai bana ma  to tabbas da bazaiji maitace ba..

“Kinyi alΖ™awari?” yatambayeta

“Eh” tafaΙ—i haka  bayan taΙ—anyi jim…..

“Yauwa Zahrah na, nasan ai kina da cika alΖ™awari, taso muje mota na baki magungunanki”  babu musu ta miΖ™e daga zaunen da take, haΙ—e da rufa masa baya.

Murfin motar ya buΙ—e haΙ—e da fiddo  wata Ζ™atuwar leda.

“Ungo magungunan suna ciki, akwai bayanin yanda zakisha a jiki, please ki kulamin da kanki kinji” yafaΙ—i haka cikin lallashi, haΙ—e da miΖ™a mata ledan dake hanunsa.

Kasa amsan ledar tayi, saima kawar da kanta gefe da tayi.

Murmushi Dr Sadeeq yayi, domin kuwa sarai ya fuskanci hakan da tayi metake nufi.

“Kiyi haΖ™uri ki karΙ“a kinji Zahrah na” yakuma faΙ—an hakan cikin lallashi.

Baki Zahrah taturo gaba haΙ—e da cewa …

“Kasan tun ba yauba nafaΙ—ama cewa banaso domin kuwa hidiman da kakemin yayi yawa, mai yasa bazaka bari haka ba!” ta tambayesa cike da sakalci..

“Saboda kina da mahimmanci, kinkuma cancani namiki fiye da haka,  amma yanzu dai banso kice a’a ki karΙ“a kinji” still cikin lallashi yayi maganar.. Badon ranta yasoba haka ta karΙ“i ledan.  

“Saida safe” tace dashi cikin sanyin murya haΙ—e da juyawa ta nufi hanyar shiga gida.

“Kada kimanta kin Ι—auki alΖ™awarin cewa bazakiyi kuka ba, bakuma zaki shiga damuwa ba, kada ki karya alΖ™awari kinji mai kyau na!”

Murmushi kawai tayi masa haΙ—e da Ι—aga masa kai alamar taji.

Yana ganin shigewarta cikin gida, shima yashiga motarsa haΙ—e da bata wuta yabar unguwar tasu..

Tanashiga cikin gida, Inna tayo kanta haΙ—e da fusge ledar dake hanunta,   babu magana ba komai ta shiga zazzage ledan akan tabarma, kallonta kawai Zahrah ta tsayayi cike da takaici, sai yanzu take godewa Allah dayasanya ba Inna bace ta haifeta, domin kuwa da Innace ta haifeta to tabbas da nan gaba kaΙ—an zuciyarta zata fashe, saboda  wannan halin da Inna keyi ba hali bane na iyayen Ζ™warai, batama tsaya ganin menene acikin ledar ba, ta wuce cikin Ι—akinta, domin ita dama ba wannan bane a gabanta, yanzu babban damuwarta shine, yanda zata samo maganin matsalarta.

Ɗaukan kwalin nan da aka kawo mata  tayi, haΙ—e da soma kiciniyar buΙ—ewa, kasancewar bakin kwalin a nane yake da wani gam me kyau..

Tana buΙ—e cikin kwalin wani tsadadde kuma kyayyawan agogo na mata ya bayya, gefen sa kuwa wani irin awarwarone haΙ—e da zobe  masu kyaun gaske, wanda dagani kasan na gold ne, domin kuwa kyawunsu kaΙ—ai ya’isa ya bayyana haka, Ζ™aΖ™Ζ™arfan ajiyar zuciya ta sauΖ™e haΙ—e da mai da murfin kwalin ta rufe kamar yanda ta samu,   Ι—aukan kwalin tayi dukansa, haΙ—e da Ι“oyesa a cikin kayanta, dawowa tayi kan katifarta ta kwanta zuciyarta cike tab da tunanin son gano wanda  ya soma

bibiyar rayuwarta…

Hajiya Habiba (mahaifiyar Dr Sadeeq) ne zaune  akan kujera gaba Ι—aya ta tattara nutsuwarta ta miΖ™asa ga Baffa Amadu dake zaune akan Ι—aya daga cikin  kujerun falon…

Baffa Amadu ne yaci gaba da cewa ” Banzo nan don na yi miki dole ba, amma Hajiya Habiba yana da kyau  wasu lokutan muna Ζ™oΖ™ari wajen bawa Ζ΄aΖ΄anmu dama akan abun da suka nuna zuciyarsu naso, musamman ma aΙ“angaren abun da yashafi aure, haΖ™iΖ™a Sadeeq yasameni da wannan maganar yakuma min bayani tayanda zan fahimta, Alhmdlh nakuma fahimta, yanzu saura ke,  kada kice wai don Ζ™addara ya taΙ“a faΙ—a mata, Ι—anki bazai aure ta ba,  kada kiyi haka, domin ita Ζ™addara tanakan kowa mai kyau da marar kyau,  sannan abu nagaba danakeso kisani, ko da ace alal misali yarinyar  ta kasance karuwa ce,  addini bai hana masa auren taba, wala Allah saboda auren saiki ga ta shiryu, balle kuma ma bahakan take ba, amma bazan miki dole akan cewa saikin amince ba, Ι—an kine kuma kina da iko akansa”…

STORY CONTINUES BELOW

Nannauyar ajiyar zuciya Hajiya ta sauΖ™e, haΖ™iΖ™a Baffa Amadu yazo mata da magana mai girma.

Ι—an nisawa tayi haΙ—e da cewa “Bawai naΖ™i aurensa da ita bane, saboda wani abu ba ne, kawai dai inajiye masa yanda tarbiyan yaransa zai kasance  ne matuΖ™ar takasance tana cikin gidansa, domin na tabbatar rashin wadataccen tarbiyan da aka bata a gidansu, shiya jawo faruwar haka a kanta,  kaga itama bata samu tarbiya mai kyau ba, balle tayi Ζ™oΖ™arin bawa nata yaran, haΖ™iΖ™a Sadeeq yarone mai biyayya agareni,  kuma harcikin zuciyata na Ζ™udurta aniyar cewa bazai taΙ“a auren wannan yarinyar ba, amma tunda harka shigo cikin al’amarin shikenan na’amince, amma kuma fa sai dai idan su biyun duka zai haΙ—asu ya aura, kaga dai Salima Ζ΄ar wajen Ζ΄ar uwata ne, haka kuma mamarta aminiyata ce, bayanda za’ayi na watsa musu Ζ™asa a ido, tahanyar cewa Sadeeq bazai auri Salima ba, kuma kaga yanzu saura Ζ΄an satika ne suka rage, har anriga da anfara shirye shiryen biki”

“Ƙwarai kina da gaskiya ta wani wajen, amma kuma bamu iya ja da haΙ—in Allah, yanzu zansanar da Sadeeq Ι—in duk yanda mukayi dake, zan kuma faΙ—a masa amincewarki,   nasan shi Ι—inma zai amince da umarninki, amma inaga zaifi kyau ayi bikin nasu a rana Ι—aya, domin babu amfanin jan lokaci”

“Eh duk yanda kukace shikenan” Hajiya tafaΙ—i haka badon ranta yaso ba.

“Shikenan to duk dai yanda ake ciki, zai zo yasanar dake” Baffa Amadu yafaΙ—i haka bayan yamiΖ™e tsaye ya gyara zaman garen dake jikinsa…

Cike da mutun ta juna sukayi sallama shida Hajiya…

Zama Hajiya tayi afalon haΙ—e da yin jigum, tabbas ba’ason ranta ta amince da wannan auren ba, saboda ita gani take tamkar yarinyar ba kimtsatstsiya bace,  ta amince ne kawai saboda Baffa Amadu yashigo cikin maganar, kuma tana matuΖ™ar darajasa haΙ—e da basa girma, domin tana masa kallo ne tamkar marigayi mijinta,  amma da ba haka ba da bazata taΙ“a amincewa ba, yanzu dai kawai sai dai tayi addu’an Allah yabasu zaman lafiya, amma ta wani Ι“angare na zuciyarta, tunani take taya zataje ta tunkari Ζ΄ar uwarta Hajiya Furaira da wannan maganar, tasan Hajiya Furaira macece mai zafi,  bazata taΙ“a son hakan ba, domin saboda bala’inta da zafin kishin ta, ne ma yasanya mijinta haryau yakasa Ζ™ara aure bawai kuma don baya so ba, to ina kuma da idan taji cewa Ζ΄arta Ι—aya tilo zata haΙ—a miji  da wata daban wacce bata da galihu, gaskiya zaiyi wuya ta amince… Haka dai Hajiya tadinga saΖ™awa da kuncewa daga Ζ™arshe ta tashi ta wuce Ι—akinta….

Cikin matsanancin farinciki Dr S.S ke kallon Baffa Amadu sakamakon jin cewa wai mahaifiyarsa ta amince da aurensa da Zahrah, masha Allah ashe  dai mafarkinsa zai zamanto gaskia, sai dai kuma farincikin nasa bai zama cikakke ba, domin kuwa sosai maganar haΙ—a auren Zahrah da Salima ya daki zuciyarsa, saboda shi a tsarin sa baida burin aje mata biyu acikin gidansa.

“Yanaji kayi shiru ne Sadeeq, ko baka amince da sharaΙ—in mahaifiyartaka bane?” Baffa Amadu yatambayeshi cike da kulawa.

Kansa yashiga sosawa yamakasa ce da Baffan nasa komai..

Murmushi Baffa Amadu yayi domin yafahimci halin da Sadeeq Ι—in yake ciki.    “Kada ka Ι—aga hankalinka Sadeeq,  atunanina ka kai namiji wanda zai iya riΖ™e mace sama da biyu, don haka wannan ba abun damuwa bane, kayarda da sharaΙ—in mahaifiyartaka, addu’anmu shine Allah yatayaka riΖ™o, yakuma baka dama da ikon yin adalci a tsakaninsu, yanzu yaushe kakeso muje gidansu ita yarinyar?”

Gaba Ι—aya jiyayi jikinsa yayi sanyi, zuciyarsa kuwa jiyayi tayi masa wani iri. “Zansanarda Baffan yarinyar idan yafaΙ—amin ranan da zakuzo, saina faΙ—a maka” inji cewar Dr Sadeeq..

“To shikenan Allah yakaimu” daga haka sukayi sallama, Dr S.S yabaro gidan Baffa Amadu zuciyarsa cike da tarin tunani kala kala, yana farincikin cewa Zahrah zata zamo matarsa, amma kuma ta wani Ι“angare na zuciyarsa kwata kwata bayajin daΙ—i.   Zahrah tana buΖ™atar farinciki da kuma kulawa mai kyau, baikamata ace anraba mata farinciki ita da wata ba, to amma “Miye mafita?” yatambayi kansa, bayan yasan baida amsar tambayan nasa, amma koma dai mene ayau zaije yasamu Baffa yasanar dashi cewa yana neman abashi izini yaturo magabatansa don abasa auren Zahrah, yakuma Ζ™udurta aransa cewa, dakansa zai bada order a Dubai, na kayan lefen Zahrah, domin kuwa zaiyi rawar gani sosai, wajen ganin komai na Zahrah yafita da ban….

AmatuΖ™ar mamakance Alhaji Ma’aruf ke kallon Zaid wanda yafaΙ—i maganar daya matuΖ™ar basa mamaki…. “Aure fa kace Zaid, dagaske kake, yanzu kashirya zakayi aure?”

“Da gaske nake Dad aure zanyi, kuma inaso kaje da kanka ka tambayamin, banaso auren yawuce nan da sati biyu Dad”

Cike da tsananin farinciki Alhaji Ma’aruf yace “Alhmdlh! naji daΙ—i Ζ™warai da gaske, domin zuwa yanzu yakamata ace ka aje iyali, insha Allah, zan je na tambaya maka aurenta, Ζ΄ar wayene kuma a ina take?”

“Ba Ζ΄ar kowa bace Dad, talakawa ne ma, amma ni ahaka naji na aminta ina kuma son na aureta” yafaΙ—i haka da iyaka gaskiyarsa..

Jinjina kai Alhaji Ma’aruf yayi haΙ—e da cewa “Zan sa rana sainaje naga mahaifinta”

“To” kawai Zaid yace haΙ—e da tashi yabar falon Dad Ι—innasa….

Fitowarta amakaranta kenan, tana sauri ta samu abun hawa, don bata son tsayuwa a bakin makarantar, kasancewar Dr Sadeeq aiki yamasa yawa bazai samu daman  zuwa Ι—auko ta ba…

Wani matashin saurayine yanufo wajenta, hanunsa Ι—auke da wani babban kwali wanda aka rufesa da wani irin abu mai kyau, aka kuma Ζ™awatasa da flower mai walwali..

“Ranki ya daΙ—e barka da yammaci”  saurayin yafaΙ—a.

“Yauwa barkan ka dai” itama ta mayarmasa amsa cikin Ι—ari Ι—ari dashi..

“SaΖ™o aka bani nakawomiki” yafaΙ—i maganar yana me miΖ™a mata kwalin dake hanunsa..

Cikin mamaki Zahrah ta shiga kallon saurayin nan dake tsaye a gabanta..

Murmushi saurayin yayi mata haΙ—e da sake miΖ™o mata kyakkyawan gift Ι—in dake hanunsa.

“Waye ya aikoka?” tayi masa tambayar cikin dakiya…

“amsar tambayarki duka suna cikin nan” yaΖ™are maganar yana me nuna mata kwalin dake hanunsa.

Hakanan taji zuciyarta ta aminta da ta karΙ“i saΖ™on.. Hanu biyu tasa ta karΙ“a,  batace dashi komai ba tayi wucewarta dai dai lokacin mai taxi ya Ζ™araso tashiga.

Tsurawa  kyakkyawan kwalin  idanu tayi, sosai adon jikinsa yayi kyau haΙ—e da Ι—aukar hankali, gaba Ι—aya ta Ζ™osa, tabuΙ—e kwalin don ganin ko wanene yake son yin wasa da hankalinta, ta hanyar turo mata da saΖ™onni, batare da yabari tasan kowaye shiΙ—in ba.

Tana shiga gida direct ta wuce Ι—akinta,  ko mayafinta bata cire ba, ta zauna haΙ—e da soma yaye ledan da akayimawa kwalinnan ado dashi,   tana buΙ—e kwalin tayi arba da wani Ζ™atuwar ta karda wanda aka naΙ—eta,  cikin sauri ta Ι—ago takardan haΙ—e da soma warwareta, amatuΖ™ar razane tayi wurgi da takardan sakamakon idanunta da sukayi mata tozali da zanen hoton dake jikin takardan.

(?Ga Zaid ga Sadeeq ko waye cikinsu zai mallaki Zahrah?‍♀

Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 7 BY FATYMA SARDAUNA"