Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 6 BY FATYMA SARDAUNA

SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 6 BY FATYMA SARDAUNA

                    Www.bankinhausanovels.com.ng 

Suna fita kuwa ta iske Baffa yayi Ι—are Ι—are agaban motar Dr Sadeeq sai washe haΖ™ora yake kai kace anmasa kyautar Ζ΄an kuΙ—aΙ—e ne.+

Dakansa ya buΙ—e mata murfin motar Ι“angaren gidan baya, cikin sanyin jiki ta shiga cikin motar, kaitsaye yashige Ι“angaren driver haΙ—e da mawa motar key…

Tunda suka Ι—au hanyar makarantar tasu Baffa ke faman zuba kamar wani kurna, yayinda Doctor Sadeeq ke amsa masa jefi jefi, domin hankalinsa gaba Ι—aya yana ga Zahrah, wacce ke zaune tayi jigum a gidan baya, akai akai yake satan kallonta tacikin madubi..

A haka dai harsuka iso cikin makarantar tasu, dai dai bakin Ζ™ofar hall Ι—in da zasu gudanar da lecture yau, ya yi parking motar tasa, domin dama already ansanar dashi cewa yau a wannan hall Ι—in zasu gudanar da lecture.

A hankali ta buΙ—e murfin motar ta fito kafaΙ—arta Ι—auke da jakar makarantar ta, cikin takunta mai Ι—auke da nutsuwa ta nufi cikin hall Ι—in kai tsaye, ko wai gensu batayi ba, tanashiga hall Ι—in kallo yadawo kanta, take taji wani irin muguwar faΙ—uwar gaba haΙ—e da karyewar zuciya, gani take tamkar kowa yana ganin abun da yafaru da ita rubuce akan goshinta.

Karab idanunta suka sauΖ™a akan Husnah wacce take faman aikin haΙ—a wasu takardu dake gabanta. wani irin sanyi taji zuciyarta tayi sakamakon ganin husnah, domin kaf makarantar bata mu’amala da kowa bayan husnah, da matuΖ™ar farinciki Husnah ta rungume Zahrah, domin koda wasa batayi tunanin ganinta ba.

“Kamar mafarki nakeyi gaskia naji daΙ—i sosai Ζ™awata!” Husnah tafaΙ—a cike da tarin farinciki.

Zama sukayi a tare dai dai lokacin Sir Bature yashigo cikin hall Ι—in, tsit haka ajin ya Ι—auka ana ta sauraran lecture Ι—in dayake yi musu, a zahirin gaskia tanajin abun da yake cewa, amma kwata kwata bata fahimtarsa, awa biyu suka Ι—auka chur suna lecture, kafun daga bisani yafita daga ajin, gyara zama Husnah tayi haΙ—e da mai da kallonta ga Zahrah cike da kulawa tace ” Yanzu ina likitan yake ?”

Ajiyar zuciya Zahrah ta sauΖ™e haΙ—e da cewa ” Ba maganar Doctor bace damuwata Husnah, babban damuwata shine gani nake tamkar abun da Zaid yamin yana rubuce a gaban goshina, Husnah gani nake tamkar kowa yasan abun dake damuna !” Zahrah taΖ™are maganar cikin raunin zuciya.

” Kada kice haka Zahrah, babu wanda yasan abun da yafaru dake, kada ki Ι—aga hankalinki Ζ™awata kinfasan kowa da irin tasa Ζ™addaran, kuma zuwa yanzu na tabbatar kin mai da al’amuranki ga Allah, shima Zaid nasan kinbarsa da Allah “

STORY CONTINUES BELOW

Murmushi mai ciwo Zahrah tayi haΙ—e da kallon Ζ™awarta ta, cike da Ζ™una tace ” Banda wata hanya wanda tawuce barinsa ga Allah, nasan nan bada jimawa ba Allah zai bimikin haΖ™Ζ™ina ” taΖ™are maganar cikin raunin zuciya,

Hannayenta Husnah ta kama suka fice daga cikin ajin, kai tsaye cafeteria suka nufa don cin abinci. Balaifi sosai tasamu nutsuwa a yau Ι—in domin kuwa Husnah bata barta tayi kaΙ—aici ba. Ƙarfe 5 dai dai suka fito daga cikin lecture Ι—in Ζ™arshe na ranan yau Ι—in, kasan cewar ta kwana biyu bata zo makarantar ba, sai take jinta gaba Ι—aya duk ta gaji, cikin nutsuwa take takunta yayinda kanta ke duΖ™e a Ζ™asa, ba abun da zuciyarta keyi banda bugawa, gaba Ι—aya tsoron fita daga cikin school Ι—in takeyi, gani take tamkar tana fita za’a kamata, da Ζ™yar take iya Ι—aga Ζ™afafunta, dagani kasan bason tafiyar take ba. a hankali ta matsa gefe, haΙ—e da waigowa don ganin waye wannan ya matsa mata da horn Ι—in motarsa, karab idanunta suka sauΖ™a akan sa, kasancewar gilasan motar tasa gaba Ι—aya a sauΖ™e suke, sam batayi tsammanin ganinshi ba, murmushi yasakar mata haΙ—e da cewa ” Da baki matsaba ai dana take ki !” yafaΙ—i maganar cikin yanayin tsokana, Ι—an guntun murmushi itama tayi haΙ—e da taΙ“e baki, “ai idan haka ta kasance zanfikowa jin daΙ—i ” Zahrah tafaΙ—i hakan da iya gaskiyarta.

“Shigo mutafi!” yafaΙ—a cikin tsare gida.

Saurin kallonsa tayi bakinta Ι—auke da tarin tambayoyi, amma kuma takasa koda motsa bakinta ne balle ta furta wata kalman.

“Kintsaya kina kallona, ba dole idan bazaki bini ba, saina yi tafiyata!” yaΖ™are maganar yana mai niyar tada motar tasa.

Da sauri ta zagaya haΙ—e da buΙ—e murfin motar, gefen mai zaman banza ta shiga haΙ—e da tamke fuskarta tamau tamkar wanda yagayamata magana marar daΙ—i.

Da Ζ™yar ya iya Ι“oye dariyan dake cinsa, domin kuwa tsoro ya hango Ζ™arara akan fuskar Zahrah, “NaΙ—auka ai zakijamin ajine, da sai na tafi na barki ba ruwana!” yafaΙ—i hakan cike da shauΖ™i.

Harara ta watsa masa haΙ—e da sake turo baki gaba, cike da shagwaΙ“a wacce batasan tayi ba tace “Nifa idan surutu zakamin ka sauΖ™eni nayi tafiyata”

Yanzu kam kasa Ι“oye dariyarsa yayi saida ya dara kafun ya ce ” Bazan sauΖ™e kiba ai bani na Ι—auko ki na saki ba, zaki iya fita da kanki ma, ai nasan ke jaruma ce zaki iya kare kanki ako da yaushe, har ma zaki iya shiga cikin ko wani abun hawa da Ζ™warin guiwarki !”

Saurin kallonsa tayi domin kuwa sarai ta fahinci inda maganganunsa suka dosa, wato dai shima ya hango zallan tsoron dake kwance akan fuskarta.

“Shikenan tunda haka kace” tafaΙ—i maganar tana mai Ζ™oΖ™arin buΙ—e murfin motar ta fita.

“Haba Ζ΄ar Ζ™anwata, nifa wasa nake miki, kiyi haΖ™uri ki bari na kaiki gida kinji ko!” Doctor yafaΙ—i maganar cikin lallashi, domin yafahimci cewa saurin fushi ne da’ita.

A cikin zuciyarta tayi hamdala, sakamakon hanata fita daga motar da yayi, domin dama burga ce kawai tsoron dake cikin zuciyarta bazai barta ta iya tafiya ba, duk runtsi tafiso shiΙ—in ya kaita domin tafi yarda dashi fiye da kowa a yanzun..

Kwantar da bayanta tayi akan kujeran motar haΙ—e da lumshe idanuwanta, gaba Ι—aya jinta take a gajiye, ga wani irin ciwon kai dake damunta, a hankali take buΙ—e idanunta, a zabure tatashi zaune sakamakon ganin da tayi Doctor ya nufi wata hanyar da ita saΙ“anin hanyar gida.

“Inazaka kaini !” TafaΙ—a a razane, kuma cikin yanayin tsoro,

“Saidake zanyi!” Yayi maganar babu alamar wasa akan fuskarsa.

“Dan Allah kayi haΖ™uri ka sauΖ™eni, ka barni naji da duhun dake cikin rayuwata, kada ka Ζ™aramin wani bala’in dan Allah!!” tuni hawaye sungama wanke fuskarta.

Wani irin kallo Doctor yayi mata haΙ—e da sakin murmushi bai kuma sake ce da ita komai ba, saima maida hankalinsa da yayi ga tuΖ™in da yake,

Yanzukam kuka mai sauti ta sanya haΙ—e da soma cewa ” Dan Allah kada ka sake cutar da rayuwata, zan iya amincema ka kasheni amma bazan iya jure wa ba, idan kaci mutumcina, wlh na yarda ka wurgani kan titinnan mota ta taka ni, amma dan Allah kada kamin komai!!” taΖ™are maganar cikin matsanancin kuka mai taΙ“a zuciya. Daidai lokacin suka iso gaban wani makeken mall wanda yagaji da Ζ™awatuwa,

yana parking motar baiko kalletaba yayi saurin ficewa daga cikin motar haΙ—e da dannawa gabaki Ι—aya Ζ™ofofin fita a motar luck, domin yasan dole zatayi Ζ™oΖ™arin fita daga cikin motar,

STORY CONTINUES BELOW

Kuka sosai Zahrah keyi haΙ—e da sanya Ζ™arfinta tashiga dukan glass Ι—in motar, tana mai ihun neman taimako amma babu kowa a wajen balle tasaran za a temaketa, domin kuwa wajen parking space ne.

“Ashe duniya cike take da azzaluman maza, ashe itakam rayuwarta a haka zata Ζ™are? wayyo Allah itakam Ζ™addaranta kenan” abun da take faΙ—a kenan acikin zuciyarta tana kuka mai tsuma zuciya,domin a zaton ta hotel ya kawota zai kuma lalata mata rayuwa.

Daidai lokacin Doctor Sadeeq ya dawo hanunsa Ι—auke da manyan manyan ledodi guda biyu, yana shiga cikin motar yakuma danna mata luck haΙ—e da mawa motar key da gudun gaske ya hau titi.

Zahrah kam muryanta har ya dashe kukanma harya daina fita domin gaba Ι—aya ta gama sadaukar da cewa yau ce ranar mutuwarta, kukantane yasoma tsagaitawa ganin sun nufi hanyar unguwarsu, a hankali hawayenta suka daina zuba, yayinda tashiga sauΖ™e ajiyar zuciya akai akai, bakomai yasa hakanba face ganinsu da tayi sun shigo cikin unguwarsu tsulum, a bakin Ζ™ofar gidan nasu yayi parking cike da kulawa yajuyo da kallonsa ga Zahrah wacce take ta sauΖ™e nannauyar ajiyar zuciya, alamar taci kuka ta Ζ™oshi.

“Banga laifin kiba Zahrah, domin dole zakiji matuΖ™ar tsoro, a iya tsawon rayuwata bantaΙ“a cutar da wata mace ba, kuma bazan fara akan ki ba, bazan taΙ“a iya cutar dake ba Zahrah, inaso ki yarda dani, ban kuma yi haka don na cutar dake ba, nabiya dake ta mall Ι—inne don inaso muje kiyi sayayyan abubuwan dakikeso da kanki, amma sai naga gaba Ι—aya kinfirgita, kiyi haΖ™uri na tsorataki ko Ζ™anwata !!” Doctor Sadeeq yafaΙ—i maganar cikin tsananin tausayawa da kuma lallashi ga Zahrah’n..

Kuka kawai Zahrah takuma fashewa dashi haΙ—e da cusa kanta cikin cinyoyinta, a hankali ya kama hanunta haΙ—e da matsewa a cikin nasa hanun, “Banason kuka Zahrah, bana ce kiyi haΖ™uri ba!” Dr yafaΙ—a cikin damuwa.

“Bakaine zaka bani haΖ™uri ba likita, nice zanbaka haΖ™uri, nayi maka mummunar fahimta, dan Allah kayi haΖ™uri, wlh tsoro nakeji banso wani abu yasake faruwa dani…!” taΖ™are maganar tana kuka sosai.

“Idan kinaso nayi haΖ™uri to kidaina kuka kinji Ζ™anwata!” yafaΙ—i maganar yana mai Ζ™are matse hanunta a cikin nasa hanun.

A hankali tashiga share hawayen dake ambaliya akan fuskarta, ji takeyi zuciyarta tayi mata sanyi.

“Bakya kyau idan kina kuka, kinfi kyau idan kina dariya, kije gida kiyi wanka ki huta, banso kisake zubar da hawayenki kinji Zahrah, ungo wannan ledan kishiga gida, akwai waya a ciki na samiki sim da komai, akwai games dayawa a ciki,nasan zai Ι—ebe miki kewa, banson ganinki cikin damuwa Zahrah, kije gobe zanzo na kaiki school dakaina, Allah yasa bazakimin gardamaba ” yaΖ™are maganar yana Ζ΄ar dariya.

Murmushi itama Zahrah tayi haΙ—e da Ζ™arΙ“an Ζ™atuwar ledan dayake miΖ™o mata, batare da tayi masa gardama ba, cikin rashin kuzari ta buΙ—e murfin motar tayi ficewarta, harsai da yaga shigewarta cikin gida kafun ya ta da motar tasa ya bar unguwar tasu..

Zahrah tanashiga cikin gida kai tsaye Ι—akinta tawuce, jakarta da ledan da Dr Sadeeq ya bata ta ajiye. Kayan jikinta tashiga cirewa, zani ta Ι—aura a kirjinta haΙ—e da sanya hijabi tafice daga cikin Ι—akin, zaune ta taradda Inna a tsakar gida, sannu da gida kawai Zahrah tayi mata, haΙ—e da shigewa cikin bayan gida, tana fitowa a wanka ta bi lafiyar katifarta domin dama dai bata wani jin yunwa, ledan da Doctor yabata ta jawo haΙ—e da buΙ—ewa, kyawawan dogin riguna ne suka bayyana acikin ledar saikuma dangin su snacks dasu choculate, kyakkyawar kwalin wayar da tagani acikin ledar taciro SAMSUNG GALAXY S10 shine sunan da ke rubuce ajikin kwalin wayar, wani irin faΙ—uwa gabanta yayi take nunfashinta yashiga gudu akai akai, bazata taΙ“a mantawa ba shima da haka yafara, daga Ζ™arshe kuma ya dasa mata babban tabo acikin zuciya da rayuwarta mai wahalan gogewa, saurin sake kwalin wayar tayi haΙ—e dayin watsi da kayan da suke zube a gabanta, talauci bahauka bane, bazata sake bari haka yafaru da’ita ba, hawaye ne suka shiga sauΖ™a akan Ζ™uncinta, haΖ™ika soyayya bata mata adalci ba, kwanciya tayi lamo akan katifa tana nai sauΖ™e a jiyar zuciya, jin da tayi zuciyarta na shirin dawowa Ι—anyea shakaf ne yasanyata tashi ta Ι—auko littafi mai tsarki wato Al’Qur’ani tasoma karantawa domin rage damuwar dake damunta a zuciya….

STORY CONTINUES BELOW

“Salima kuma Hajiya?” Doctor Sadeeq yatambaya cikin muryar damuwa.

“Ƙwarai kuwa Sadeeq, ko ita Saleema’n tana da wani aibune? Ζ™warai nayaba da hankalinta dakuma tarbiyanta, saboda haka nagama yanke shawarata, gobe zanfaΙ—amawa Ζ™anin mahaifinku yaje yatambayo maka aurenta, idan ma a so nane banso bikin yawuce nanda wata Ι—aya ” Hajiya tafaΙ—i maganar babu alamar wasa akan fuskarta.

Cike da sanyin jiki Doctor Sadeeq yace ” Shikenan Hajiya, Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, amma dakin Ζ™ara haΖ™uri, nan bada jimawa ba zan kawo wacce nakeso”

“Hmmm ai aikin gama yariga daya gama Sadeeq, nagaji dajin wannan zancennaka, koda yaushe haka kake cewa, to yanzu dai nagaji da Ζ™aululan dakakemin saboda haka natsaida magana,zaka iya tafiya”

Gaba Ι—aya hukuncin da Hajiyar tasa ta yanke masa baiyi masa daΙ—i ba, amatsayinsa na Namiji bai dace ace anyimasa dole akan aure ba, shi sam Saleema ma bata Ι—aya daga cikin irin tsarin matan dayakeso, amma yazaiyi tunda dai Hajiya ta kafe, yasanta da wuyar sha’ani, idan tace eh zaiyi wuya kuma tace a’a, jiki a mace haka yafice daga falonnata, kaitsaye Ι“angaren sa yanufa, yanashiga cikin falonnasa direct friedge yanufa, goran ruwa mai sanyi ya Ι—auko, haΙ—e da zama akan kujera, saida yasha ruwan fiye da rabin gora, kafun yashiga sauΖ™e ajiyar zuciya, wayarsa yaciro acikin aljihun rigarsa, kai tsaye lambar sim Ι—in dake cikin wayar daya bata, ya danna wa Ζ™ira, saidai yaji saΙ“anin tunaninsa, domin kuwa cemasa akayi wayar a kashe take, nannauyar ajiyar zuciya ya sauΖ™e, haΙ—e da aje wayartasa a gefe, “Maiyasa nadamu da’ita sosai ne?” yatambayi kansa, bayan kuma yasan baida amsa,

“Inatausayinta sosai,amma kuma bayan tausayi inajin wani abu na daban a ga me da’ita, menene wannan abun ? yazama dole nasan menene amma tabbas ina da burin inganta rayuwarta ” Ƙaran wayarsane ya katse sa daga zancen zucin da yakeyi, ganin da sabon number ake Ζ™iran nasa yasa bai Ι—auki Ζ™iranba, saima tashi dayayi yawuce cikin bedroom Ι—insa…

Washe gari.

Yau tunda safe takammala shirinta, tayi kyau cikin shigar ta ta atamfa riga da sket, yayinda lufayant dake jikinta ya kasance hot pink colour, sama sama tasha ruwan shayin da Inna ta dafa, tana kammala shan ruwan shayin ta Ι—auki jakarta haΙ—e da nufar hanyar waje. domin batamaso likita yazo yasameta, tafiso tayi tafiyarta, sam bataso yanashiga cikin rayuwarta, takuma yanke shawaran gaya masa yafita acikin rayuwarta, domin sam baikamata tasake bawa wani namiji dama ba.

Turus haka taja ta tsaya, domin kuwa tsaye tagansa ajikin motarsa, yasha ado cikin wata blue Ι—in shadda, sam batai tsammanin ganinsa a daidai wannan lokacinba.

Murmushi yayi mata haΙ—e da soma takowa harzuwa inda take tsaye.

“Baki tsammaci ganina a dai dai wannan lokacin ba ko?” yatambayeta kansa tsaye yana mai kafeta da idanu.

Ɗan Ζ™aramin bakinta taturo gaba haΙ—e da cewa “Ina kwana”

“Lafiya Ζ™alau, yakika tashi?”

“Lafiya” tabasa amsa a taΖ™aice, haΙ—e da sunne kanta Ζ™asa, domin hakanan taji yamata wani irin kwarjini.

“Muje kada kiyi latti ko” Doctor yafaΙ—a yana mai yi mata nuni akan cewa tashige gaba.

Bazata iya musa masa ba, domin kuwa yayi mata kwarjini sosai, don haka cikin sanyin jiki tanufi wajen motar tasa, shikuma yarufa mata baya, gaba Ι—aya jitayi jikinta yayi sanyi, alΖ™awarin da ta Ι—aukawa kanta nacewa zata faΙ—a masa yafita a rayuwarta gaba Ι—aya ya ruguje, domin kuwa tanaganinsa taji bakinta yamutu murus, tana shiga cikin motar ta lumshe idanu, domin kuwa wani irin daddaΙ—an Ζ™amshi cikin motar keyi, cike da nutsuwa yake tuΖ™in nasa, yayinda jefi jefi yake satan kallon Zahrah, wanda gaba Ι—aya hankalinta yana ga ababen hawan da suketa hada hada akan titin.

“Maiyasa ki kaΖ™i kunna wayar dana baki?”

Sunkuyar da kanta Ζ™asa tayi haΙ—e da soma wasa da yatsun hanunta, “Babu” tafaΙ—i hakan cikin sanyi murya.

“Ko kuma dai bakyason kyauta daga gareni ba “

Saurin kallonsa tayi, jin abun da yace, ai kuwa karab idanunsu suka haΙ—e a waje Ι—aya, saurin sadda kanta Ζ™asa tayi, domin batason haΙ—a idanu dashi kokaΙ—an, “Bahaka bane, kawai dai banson rayuwata tasake cutuwa ne” tafaΙ—i hakan da iya gaskiyarta.

Kansa ya jinjina haΙ—e da cizon lips Ι—insa, “Eh ta wani wajenma kina da gaskia, amma ai bada wata manufa na baki ba, amma idan kinaga zaki takura to shikenan saikiyi abun da yadace” shima yayi maganar da iya gaskiarsa.

Daga haka dukansu basu sake ce da junansu komaiba, har suka iso cikin makarantar, yauma har gaban lecture hall Ι—in su ya kaita, sai da kuma yaga shiganta cikin hall Ι—in kafun yayi tafiyarsa.

Koda aka tashi yauma shiya zo da kansa ya Ι—auketa, sai dai tunda suka kama hanya harsuka isa gida babu wanda yace da Ι—an uwansa wani abu.

A daidai Ζ™ofar gidan su ya tsaida motar, haΙ—e da juyo da kallonsa gareta Ζ™oΖ™arin fita tasomayi daga cikin motar, cikin wata irin murya mai sanyi yace “Inason magana dake”

Kallo Ι—aya tayi masa ta kau da kanta gefe, “Wace irin maganace ?”

“Maganace mai matuΖ™ar mahimmanci , amma kuma tana buΖ™atar ishashshen lokaci ” Doctor yaΖ™are maganar yana mai duban agogon dake Ι—aure a tsintsiyar hanunsa.

“Inajinka” Zahrah tafaΙ—a a taΖ™aice,

“Bakina jina zaki ce ba, hankali da tunaninki nakeso kibani “

Gyara zamanta tayi haΙ—e da Ι—an satar kallonsa, batare da tace komaiba.

Kwantaccen sajen dake kan kumatunsa ya shafa, haΙ—e da cewa ” No kada kiyi zaton wani abu zance, dama alluranki ne banΖ™ara sa miki ba, kuma akwai matsala idan banyimiki su ayau ba!”

Gaba Ι—aya idanunta ta Ζ™walalo su waje, yayinda tsoro yacika zuciyarta, “Dan Allah kayi haΖ™uri wallahi na warke, yanzu banajin komai ajikina!” taΖ™are maganar lokacin da muryarta ke rawa, alamun zatayi kuka.

“A’a ni gaskia banyarda da cewa kin warke ba, saboda naga kina yawan sanya kanki a damuwa kuma jiya ma dana riΖ™e hanunki naji zazzaΙ“i a jikinki, don haka kawai zan Ζ™arasa miki yanzu” yaΖ™are maganar yana mai shirin buΙ—e wani Ι—an Ζ™aramin drower dake cikin motar, take allurai suka bayyana, ai a Ι—ari Zahrah ta buΙ—e murfin motar haΙ—e da rugawa zuwa cikin gida, ko tsayawa Ι—aukar jakarta batayi ba.

Dariya sosai Doctor Sadeeq yasanya, hadda riΖ™e ciki, shi dama burinsa yaga yanayin tsoronta, domin idan tana cikin wannan yanayin tsoron sosai take burgesa, Ι—aukar jakar nata yayi haΙ—e da fita acikin motar kai tsaye yanufi cikin gidan. Yana sallama Inna ta tarbesa da fari’a, haΙ—e da cewa “Ai dama nasan tare kuke domin daganin yanda tashigo a guje nasan cewa ba ita kaΙ—ai bace” Ι—an guntun murmushi yayi haΙ—e da cewa ” waifa dan nace zanmata allurane, shine duk tabi ta ruΙ—e, kuma yau bazan bar gidannan ba harsai na mata alluran nan, ko yakikace Inna?”

Idanu Zahrah tasake gwalowa jin abun da yake cewa, gaskia ita daya mata allura gwamma yabata magani amma sam batason allura, kuma ita taji sauΖ™i, amma su sundage akan cewa wai bataji sauΖ™i ba, kafun ta gama zancen zucin da takeyi taji muryarsa a bakin Ζ™ofar Ι—akin yanacewa Inna ta Ι—auko masa ita….Sake matse jikinta tayi ajikin bango, haΙ—e da turo Ι—an Ζ™aramin bakinta gaba.+

“ZAHRAH!” taji muryarsa yana Ζ™iran sunanta, cikin tsoro da Ι—ar Ι—ar, ta buΙ—e Ζ™ofar Ι—akin nata, kallo Ι—aya yayi mawa cikin idanunta yakau da kansa gefe, domin kuwa wani irin zubawa yaji tsikar jikinsa tayi, gaskia Zahrah tana da abubuwan Ι—aukar hankalin Ι—a namiji da yawa a tattare da’ita.

Batare da yakuma kallonta ba, ya miΖ™omata jaΖ™arta dake riΖ™e a hanunsa, da sauri ta fusge jakar haΙ—e da komawa cikin Ι—akin ta,ta kuma datse Ζ™ofar, murmushi kawai Doctor Sadeeq yayi haΙ—e da girgiza kansa, kallonsa yakomar ga Inna, cikin girmamawa yayi mata sallama, bayan ya cika mata hanunta da alkhairi, cike da farinciki Inna tayi sallama dashi, don tsabar daΙ—i ma har kusan Ζ™ofa ta rakasa, tana mai zabga masa godiya.

Tafiya yake amma shi kaΙ—ai yake murmushi, sosai Zahrah take burgesa, yanason komai na yarinyar, fushinta, dariyanta, tafiyarta, nutsuwarta, dama duk wani abu nata, tabbas Zahrah tana Ι—aya daga cikin irin matar da yake fatan mallaka a matsayin matarsa ta sunna, ko dai zai jarrabane ?” ya tambayi kansa, saurin dukan seterin motar tasa yayi haΙ—e da cije laΙ“Ι“ansa, “Ka dawo cikin hankalinka Sadeeq, maikake shirin aikatawa ne haka?” yatambayi kansa a fili.

“No baikamata nayi haka ba, dole zanyi haΖ™uri !” yafaΙ—i hakan cikin karyewar zuciya, dai dai lokacin kuma ya iso gaban makeken gate Ι—in gidansu, mai gadi yana gama wangale masa gate Ι—in ya cusa motar tasa zuwa cikin gidan.

Saida tagama Ζ™aremawa wayar kallo kafun ta danna madannin da zai sanya wayar ta kawo haske, nannauyar ajiyar zuciya ta sauΖ™e, haΙ—e da jingina bayanta da jikin bango, “Yazama dole kikawo sauyi acikin rayuwarki Zahrah, kada ki bari abunda Zaid yayi miki, yazama sanadiyar lalacewar duk wani farinciki dake cikin rayuwarki” zuciyarta ta faΙ—a mata hakan cike da Ζ™arfafa mata guiwa, “Amma tayaya hakan zai kasance, bayan banda wani ginshiΖ™i dazai taimakamin ?” Zahrah tatambayi kanta, sake gyara zamanta tayi haΙ—e da Ι—aukar wayarta, kai tsaye tashiga wajen dazai sadata da apps Ι—in wayar, Word Charm shine game Ι—in daya Ι—auki hankalinta, duk cikin apps Ι—in dake wayar, dama tanason game Ι—in, don haka kaitsaye tashiga tasomayi, take taji kewa da kaΙ—aicin da take ji sun soma ragewa, a wannan rana dai Zahrah batayi wani dogon tunani da takura kanta ba, dazaran taji ta takura zata Ι—auki wayarta tasoma buga game, idan ta gaji da buga game Ι—in kuwa, sai ta shiga Instagram shima sosai yake rage mata kewa (nima haka, lol)..

STORY CONTINUES BELOW

Tayi kyau sosai cikin blue rover gown Ι—in dake jikinta, wata baΖ™ar lufaya ta sanya a jikinta wanda yataimaka wajen Ζ™arawa shigar tata kyau da armashi, batayi wani kwalliya akan fuskarta ba, ta dai shafa man leΙ“e dakuma kwalli, amma duk da haka tayi kyau, dama mai kyau ko baiyi kwalliya ba kyawunsa baya Ι“uya.

Kasancewar yau baza su jima a makaranta ba, yasanya bata Ι—auki jakaba, sai wasu Ζ΄an littatafai da ta Ι—auka a hanunta, sai kuma wayarta, koda ta fito tsakar gidan zaune a bakin murhu ta iske Inna tana tuyan Ζ™osai, wanda Baffa yace ayi na karyawa.

“Inna ni zanwuce makaranta” Zahrah ta faΙ—a tana mai Ζ™oΖ™arin gyara zaman lufayan dake jikinta.

“Bazaki tsaya ki karyaba Zahrah”

Baffa dake fitowa daga cikin Ι—akinsa ya faΙ—a.

Ɗan guntun murmushi Zahrah tayi haΙ—e da shafa cikinta “Banajin yunwa sosai Baffa, kuma ina tsoro kada na makara!”

“Eh kina da gaskiya, kinga kuwa tun Ι—azu likita, yazo yana jiranki, bayanda banyi da shi ba akan yashigo, amma sam yaΖ™iya, don haka gwamma ki hanzarta, a dawo lafiya ” Baffa yaΖ™are maganar yana mai yunΖ™urin komawa cikin Ι—akinsa.

“Ameen Baffa nagode!” Zahrah tafaΙ—a cike da farinciki, domin kuwa karo na farko kenan a rayuwarta da taga tsananin kulawan Baffa a kanta.

Tana fitowa yasakar mata kyakkyawan murmushinsa, ga mamakinsa sai yaga itama ta sakar masa murmushi, wanda yayi matuΖ™ar taΙ“a masa zuciya, domin kuwa bakaΙ—an ba tayi kyau, da tana murmushin.

“Saiyanzu ki ka ga daman fitowa? kinshanyani kamar kin aje dutse” Doctor yafaΙ—i maganar yana mai turo baki gaba, tamkar Ζ™aramin yaro.

Dariya sosai Zahrah ta shiga yi, domin yanayin yanda yayi maganar yazama dole wanda ya gani ya dara, hangame baki Dr yayi yana kallon yanda take dariyan, abun da bai taΙ“a gani ba kenan, tun haΙ—uwar su da’ita, bai taΙ“a ganinta tana dariya ba sai yau, ashe ma duk kyawunta da yake gani, bai ga komai ba, domin da tana dariyan tafi masa kyau.

Hanunta tasanya ta toshe bakinta, haΙ—e da tsagaita dariyan da takeyi, kallonsa tayi haΙ—e da cewa “Bakaga yanda kazama yaro ba dakana maganan nan, tamkar Ι—an shekara takwas!”

Murmushi yayi haΙ—e da jefamata hararan wasa, cikin yanayin da yayi magana Ι—azu yakuma cewa “Shine kikemin dariya ko? sai na faΙ—aki da mamana!” ai kamar yaΖ™ara mata fower’n da riyan nata ne, nan take taci gaba da dariyanta, hadda Ι—an guntun Ζ™walla a idanunta, wani irin sanyi da nishaΙ—i yaji yana huda zuciyarsa, tabbas bashida wani buri da yawuce yaga Zahrah tana cikin farinciki Alhmdlh, yau gashi ta sanadiyarsa tana dariya dakuma nishaΙ—i,

“Kayi haΖ™uri, bazan sake shanyaka ba, amma gaskia ka iya shagwaΙ“a da yawa!” Zahrah tafaΙ—a dai dai lokacin da tayi mawa kanta mazauni acikin motar, haryanzu dariyane kwance akan fuskarta.

“Wato dai yau mugunta kike ji dashi, dariya hadda hawaye!” Doctor yafaΙ—a cikin nishaΙ—i.

“Bahaka bane, kai Ι—inne dai kawai kabani dariya!” itama ta basa amsa cikin nishaΙ—i.

“Dagaske kike, saboda ni kike wannan nishaΙ—in? ” Dr ya tambayeta cike da zaΖ™uwa, duk da kuwa cewa yasan sabo da shiΙ—inne take nishaΙ—in.

“Eh mana, saboda kaine, kasan kaban dariya sosai, kuma nasan bama ni kaΙ—aiba, duk wacce takalleka a irin wannan yanayin dole zatayi dariya”

Ajiyar zuciya Dr ya sauΖ™e haΙ—e da murza key Ι—in motar, suka Ι—au hanyar da zata sadasu da titi.

“Idan kina dariya kinfi ko yaushe kyau Ζ΄an mata na!” Dr yafaΙ—a cikin muryar nutsuwa.

Saurin maida kallonta garesa tayi, jin abun da yafaΙ—a tayi kamar wani almara, sai kuma taga yanayinsa tamkar bashine yayi maganar ba.

Yi tayi itama kamar bataji mai yace ba, mai da kallonta tayi ga titi, tana mai kallon yanda ababen hawa suke gudanar da hada hadansu.

STORY CONTINUES BELOW

“Maiyasa ki ka Ζ™i cin abinci? ko kinfiso ki zauna da yunwa ne?” Doctor ya jefo mata tambayar da batayi zato ba.

Kallo Ι—aya ta yi masa ta kau da kanta gefe, “Banjin yunwa ne, sannan kuma banaso na yi latti”

tafaΙ—i maganar a taΖ™aice.

Baice da’ita komaiba, saima buΙ—e Ι—an Ζ™aramin drowern dake jikin motar yayi, wani haΙ—aΙ—Ι—en cake dake cikin wani Ι—an Ζ™aramin kwali ya ciro, haΙ—e da Ι—aura mata akan cinyarta, ” Kici, kuma banson musu” yanayin yanda yayi maganar zai tabbatar ma da cewa, ba wasa yake ba.

“Nagode, amma zanci idan muka fito a lecture” itama ta faΙ—a kai tsaye.

“Yanzu nakeso kici, umarnine bawai shawara ba” yakuma faΙ—i maganar cikin yanayi mai nuni da cewa da gaske yake maganar.

Batason yi masa musu, domin koba komai yayi mata halacci a cikin rayuwarta, a hankali take gutsuran cake Ι—in tana kaiwa bakinta, duk da cewa cake Ι—in yayi mata daΙ—i.

Duk abun da takeyi yana lure da’ita, yanayin yanda take tauna abincin shiyafi komai burgesa.

Saida taci cake Ι—in fiye da rabi, kafun ta dawo da kallonta garesa, “NaΖ™oshi” tafaΙ—a tana mai yatsine fuska.

“Dole sai kin cinye, domin kuwa ni idan nabawa mutum abuna, bai isa yacemin ya Ζ™oshi ba, dole sai yacinye koda kuwa ya Ζ™oshin”

Ɗan guntun murmushi tayi haΙ—e da cewa “Dagaske nake naΖ™oshi, amma da alama dole kakeson min”

“Dolen dole ma kuwa” yafaΙ—a dai dai lokacin da yagama parking motar tasa, domin kuwa harsun kawo cikin makarantar tasu, hanu ta Ι—aura akan murfin motar da niyar buΙ—ewa ta fita, tuni ya dannawa Ζ™ofofin luck, saurin kallonsa tayi domin bata fahimci hakan da yayi me yake nufi ba.

“Babu inda zakije, matuΖ™ar baki cinye cake Ι—in nan ba” yafaΙ—i hakan yana me jingina bayansa a jikin kujeran da yake kai.

ƘwaΙ“e fuska Zahrah tayi cikin sigar lallashi, tace “Kayi haΖ™uri, naΖ™oshi, idan naci da yawa, bazan iya karatu yanda ya kamata ba!”

“Um,Um, naΖ™i wayon, saura kaΙ—anne fa please kicinye shi mana Zahrah!” Doctor Sadeeq yaΖ™are maganar cikin lallashi.

“Um, Um, na Ζ™oshi, gaskiya idan naci zai cutar dani, zanyi Ζ™atuwa da yawa, ni kuma banaso nayi Ζ™atuwa!” cikin zallan shagwaΙ“a Zahrah tayi maganan.

Dariya sosai Dr Sadeeq ya sanya, domin kuwa maganar Zahrah ta bashi dariya, wai ita bataso tayi Ζ™atuwa hmm.

“To ai yaune kawai, kuma kinga bazakiyi Ζ™atuwa ba, nima banso kiyi Ζ™atuwa da yawa, amma inaso kiyi Ζ™atuwa kaΙ—an!” yanayin yanda yayi maganar kaΙ—ai ya isa sanyawa mutum mutuwar jiki.

Batace dashi komaiba, domin bata fahimci inda maganar tasa ta dosa ba, Ι—aukan ragowan cake Ι—in tayi, tashiga turawa acikin bakinta, tamkar wacce aka bawa guba.

Dariya Doctor Sadeeq yashiga yi mata Ζ™asa Ζ™asa, domin kuwa yanda takecin cake Ι—in, dagani kasan dole a kayi mata bawai a son ranta bane. tana cinyewa ya miΖ™omata goran ruwa, ai kuwa ba musu ta karΙ“a ta shiga sha, domin dama duk cake Ι—in ya shaΖ™eta.

Cikin yanayi na shagwaΙ“a da Ι“ata fuska tace ” Na cinye yanzu zan iya tafiya!”

Dariya Dr yayi haΙ—e da cire luck Ι—in da yasanyawa Ζ™ofofin motar “Zaki iya tafiya, amma kikula da kanki sosai, sannan idan kun fito a lecture wani zai kawo miki saΖ™o daga nine ki amsa”

“Wani saΖ™o?” Zahrah ta tambaya cike da Ι—aurewar kai.

“Zakiyi latti,kiyi sauri kije” Dr yafaΙ—i hakan don kawar da tambayar da tayi masa.

Bata sake cewa komai ba tabuΙ—e murfin motar tafice, yauma dai sai da yaga shiganta cikin hall Ι—in kafun yatada motarsa yabar cikin makarantar, direct shima asibiti ya nufa, domin yau yanada aiki sosai.

STORY CONTINUES BELOW

Sosai yau ta gane Lecture Ι—in da akayi musu, saΙ“anin sauran ranakun da suka wuce wanda ba komai take fahimta daga cikin abun da ake koyar musu ba.

Fitowarsu kenan daga lecture, tafe suke su biyu, yayinda Husnah keta mita, wai jimawan da sukayi suna lecture, yasanya tanemi gaba Ι—aya abincin cikinta ta rasa.

Dariya Zahrah tayi haΙ—e da cewa “Nikuwa kinga Ι—igo na yunwa banaji, domin kuwa yau Ι—ure, a kamin dan dole na”

“Ι—ure kuma bestie? Amma badai Inna da Baffa bane sukaimiki Ι—uren bako?”

“Doctor Sadeeq ne!” Zahrah tafaΙ—a a taΖ™aice.

“Doctor Sadeeq kuma? lallai kuwa Doctor yayi babban Ζ™oΖ™ari, shiyasa na ganki yau kina cikin farinciki” Husnah tafaΙ—a tana mai Ζ™oΖ™arin gimtse dariyar da take Ζ™oΖ™arin taso ma ta, domin ita kam ta hango wani babban al’amari dangane da Doctor dakuma Zahrah.

“Maikike nufi?” Zahrah ta tambayi Husnah cikin tsare gida.

Husnah batakai ga bata amsa ba, wani mutumi ya Ζ™araso garesu, hanunsa Ι—auke da wata leda, sallama yayi musu suka amsa masa.

Kaitsaye ya miΖ™omawa Zahrah ledar dake hanunsa, haΙ—e da cewa “Gashi inji oga”

Take maganar da Dr yafaΙ—a mata Ι—azu a cikin mota, cewar wani zai kawo mata saΖ™o, ya faΙ—o mata, cikin sanyin jiki ta amshi ledan, haΙ—e da ce masa ta gode.

“Saurin karΙ“e ledan Husnah tayi daga hanun Zahrah, haΙ—e da cewa “Allah yasa abun daΙ—i ne, domin yawuna haryafara tsinkewa, kinsanni ba baya bace wajen kwaΙ—ayi”

“Wow special gift!!” Husnah tafaΙ—a sanda idanunta suka gane mata abun da ke cikin ledar,

“Amma ba haka naso ba, Ζ™awata naso ace wani abun ci ne kinga da sai na morewa bakina!” Husnah ta Ζ™are maganar tana mai Ι“ata fuska.

Dariya Zahrah tayi haΙ—e da sanya hannayenta ta dafa kafaΙ—un Husnah, cike da nishaΙ—i tace ” Allah Ζ™awata, ki rage kwaΙ—ayi, yanzu idan abun ci ne, yazuba mana wani abu a ciki, mukazo mukaci, ya cutar da mu,kuma fa? kinga kwaΙ—ayi ya jawo mana kenan,kuma bai mana rana ba”

“Dan Allah malama sakeni, nayarda da Dr nasan babu abun da zai Ι“amu wanda zai cutar da mu, kedai kawai mugunta ne irin naki, bayan kinsan inajin yunwa, muje cafeteria muci abinci please!” Husnah tafaΙ—a tana mai daΙ—a kwaΙ“e fuska.

“Yi haΖ™uri Ζ™awata bani nakar zomonba, muje sai kici abincin ko” Zahrah tafaΙ—a cike da kulawa.

“Ungo kayan shafanki, domin kuwa cigaba da riΖ™esu ma, Ζ™aramin yunwa zaiyi” Husnah ta Ζ™are maganar tana mai miΖ™omawa Zahrah ledar dake hanunta.

Dariya kawai Zahrah tayi haΙ—e da amsar kayan, sarai tasan Husnah bata da haΖ™urin yunwa ko kaΙ—an.

Ice cream kawai Zahrah tasha, yayinda Husnah kuwa ta cika cikinta da shinkafa. Yau darasi biyu garesu kacal, don haka suna fitowa kowa ya yi Ζ™oΖ™arin kama gabansa.

Waige waige tashiga yi ko zata hangosa, amma babu alamar komai irin motarsa, wayarta ce ta soma Ζ™ara alamar shigowar Ζ™ira, Number ne ke yawo a kan screen Ι—in wayar babu suna, dama kuma batayi tunanin Numbern zai fito da suna ba, domin batayi saving numbern kowa ba, wama ta sani da zatayi saving number’nsa.

Har saida wayar ta kusa katsayewa kafun Zahrah ta Ι—aga Ζ™iran, “Zahrah! na gaji, da yawa, aiki yamin yawa, please ga nan driver na, zaizo ya Ι—aukeki ya kaiki gida, kiyi haΖ™uri kinji Ζ™anwata!!” Dr Sadeeq ya faΙ—i haka cikin kwantar da murya, da gajin yanda muryansa take fita slow kasan cewa a matuΖ™ar gajiye yake.

A jiyar zuciya Zahrah ta sauΖ™e haΙ—e da cewa “Shikenan kahuta lafiya”

“Yauwa Ζ³an mata na, ki kulamin da kanki” Ζ™it ya kashe wayar, ba tare da ya tsaya ya saurari mai zata ce ba.

STORY CONTINUES BELOW

Murmushi kawai Zahrah tayi haΙ—e da girgiza kanta, “Hmm wai itace Ζ΄an mata, itakam yanzu ai ta wuce a Ζ™irata Ζ΄an mata saidai sauran Zaid” tafaΙ—i hakan a zuciyarta, take kuma taji idanunta sun kawo ruwa. Dai dai lokacin motar Dr Sadeeq ta Ζ™araso inda take tsaye, kasan cewar yayi mata bayanin cewa driver’n sane zaizo Ι—aukarta, dan haka batayi wani jinkiri ba, ta buΙ—e murfin motar tashiga, ko kallon inda driver’n yake batayi ba, “ZAHRAH!” muryan Dr Sadeeq ya daki dodon kunnuwanta, saurin maida kallonta inda taji muryan tayi, ai kuwa shiΙ—inne kwance a jikin kujeran gidan baya, idanunsa Ι—aya ya kashe mata haΙ—e da Ι—age giransa Ι—aya sama, “Surprise!” yafaΙ—a fuskarsa Ι—auke da murmushi.

Murmushi itama tayi masa, haΙ—e dayin Ζ™asa da kanta, domin yanayin yanda yayi mata maganan, yasanya taji jikinta yayi sanyi.

“Dawo nan muzauna, ki bar driver yayi aikinshi”

Ɓata fuska Zahrah tayi haΙ—e da turo baki gaba, cike da shagwaΙ“a tace “Ni dai kabarni na zauna anan Ι—in ma yayi!”

“Nace ki dawo nan muzauna ko!” yafaΙ—i hakan babu alamar wasa akan fuskarsa.

Cike da sakalci Zahrah ta dawo gidan baya inda yake zaune, ko kallonsa batayi ba saima langwaΙ“ewa da tayi a jikin kujera. Har sukayi nisa a tafiyan babu wanda yace da Ι—an uwansa Ζ™ala, cikin shagwaΙ“a tace “Bakace min aiki yamaka yawa ba, amma mai yasa kazo?”

“Saboda ya cancanta nazo, ina da burin baki kyakkyawan kulawa a ko da yaushe, ko bakiyi farinciki da hakan ba?”

“Nayi farinciki sosai!” Zahrah tafaΙ—a kai tsaye, domin kuwa sam batason irin kallon da yake yawan yi mata a wasu lokutan.

Baisake ce da ita komai ba, shima sai ma komawa da yayi ya jingina bayansa da jikin kujeran motar.

A haka har suka iso Ζ™ofar gidan su Zahrah’n, kallo Ι—aya tayi masa haΙ—e da buΙ—e murfin motar tayi ficewarta, yana ganin shigewarta gida, yace driver ya ta da motar suje.

Bayan Sati Biyu….

Wani irin shaΖ™uwa ne mai Ζ™arfi yashiga tsakanin Doctor Sadeeq da Zahrah, kullum shi ke kaita mkaranta shi kuma ke Ι—auko ta, sosai yake bata kulawa, baya son duk wani abu da zai Ι“ata ranta, ko ya sanya taji ba daΙ—i, Ι“angaren Zahrah ma, sosai take kiyayewa dashi, tana iya Ζ™oΖ™ari wajen ganin bata musa masa idan ya umarceta da tayi abu, ko kaΙ—an batajin wani abu a dangane dashi, tana dai yi masa biyayya tana kuma ganin girmansa, domin kamar yanda yace ta Ι—aukesa, a matsayin Ι—an uwa, to a matsayin Ι—an uwan ta Ι—aukesa, domin kallon yaya take masa, sannan kuma sosai wayarta take Ι—e be mata kewa, yakanyi Ζ™oΖ™ari wajen ganin ya Ζ™irata a waya, a kowani dare, sai dai hiran tasu bata tsayi suke sallama da juna, sosai rayuwarta tasamu canji, bakamar da ba, duk da cewa abune mawuyaci manta abun da ya faru da’ita, amma takanyi Ζ™oΖ™ari Ζ™warai wajen ganin ta gusar da duk wani damuwarta.

Tsaye yake a gaban tangamemen dressing mirror Ι—in dake kafe a jikin bangon Ι—akin nasa, yayi kyau sosai cikin riga da wandon shadda dake jikinsa, ba abun da jikinsa keyi banda tashin Ζ™amshi, hannayensa duka yazura a cikin aljihun wandon shaddan dake jikinsa, tabbas a kwai wani al’amari mai girma dake cikin zuciyarsa, haΖ™iΖ™a kuma akwai abun da yakeso ya furta,amma tayaya, baisan da wani manufa zata Ι—auki zancen ba, baisan wani amsa zaiji daga bakinta ba, wannan shiya hanasa furta mata tsadaddan kalman dayake ta Ι“oyewa tsawon lokuta, bayajin zai samu abun da yakeso daga gareta, bakuma yajin zai samu amincewarta, ya tabbatarwa kansa cewa, a yanzu lallashi take buΖ™ata fiye da komai, sannan kuma bata buΖ™atar wata magana wanda zata zamo sanadiyar rugujewar Ι—an farincikin da ta soma samu, sai zuciyar sa ta Ζ™arfafa masa guiwa, saikuma gangar jikinsa tayi sanyi laΖ™was.

“Ba’asan jarumin Namiji da tsoro ba!” wata zuciyarsa ta furta masa hakan.

Ƙwarai ya yarda da cewa shi Ι—in jarumi ne, amma kuma gurin da yake da muradin isar da saΖ™onnasa wajene mai rauni, dole zai fuskanci Ζ™alubale guda biyu, rashin nasara, ko kuma, yin nasara, wayarsa ya Ι—auka ya sanya a cikin aljihunsa, kai tsaye ya fice daga cikin Ι—akin nasa, yana shiga cikin motarsa ya bata wuta, kai tsaye unguwar su Zahrah ya nufa, sosai ya yarda da shawaran da zuciyarsa ta basa, lallai yazama dole ya bayyana mata sirrin dake kwance cikin zuciyarsa, sai dai yasan balallai ta aminta da Ζ™uΙ—irinsa ba, amma zai jarraba ya gani.

A Ζ™ofar gidansu yayi parking motarsa, haΙ—e da ciro wayarsa, ya danna wa Number’n Zahrah Ζ™ira, sai dai harzuwa lokacin zuciyarsa fat fat haka take bugawa. tana Ι—aga wayar yace “Ina Ζ™ofar gidanku, dan Allah kizo ki sameni” banji mai tace masa ba, sai gani nayi ya mai da wayar tasa cikin aljihunsa, haΙ—e da sauke nannauyar ajiyar zuciya….Tana aje wayan ta Ι—auko wani rover hijab Ι—inta ta sanya a jikinta, koda tafito daga cikin Ι—akin nata, zaune ta iske Baffa da Inna, a tsakar gida, domin dai dama dare yasoma rufawa, cike da ladabi tace ” Baffa Doctor Sadeeq yana Ζ™irana a waje”

Gyara zama Baffa yayi haΙ—e da cewa ” to naji Ζ™aran tsayuwar mota ai, ashe dai likitane yazo, to adawo lafiya”

Muguwar harara Inna ta jefamawa Zahrah, cike da masifa tace “Wato ni banza bankai matsayin da zaki tambayeni ba ko? wato Baffanki kaΙ—ai kika gani a wajen?”

Cikin sanyin murya Zahrah tace “Kiyi haΖ™uri Inna, naga shi ya kamata na sanarmawa hakanne, tunda ya na nan!”

“Wuce kije Ζ™iran da yake miki kinji Zahrah’u, barta Salame yau masifa take ji dashi” Baffa yaΖ™are maganar yana mai wurgamawa Inna harara.

Bata kuma sauraran abun da Inna zatace ba tasakai tayi ficewarta daga cikin gidan..

Duk da cewa babu wadataccen haske a wajen, amma tana iya hango kyawun da kayan jikinsa sukai masa, “gaskiya Dr kyakkyawane shima” tafaΙ—i hakan a cikin zuciyarta.

Da sallama Ι—auke a bakinta ta Ζ™araso inda yake tsaye, cike da fari’a Dr ya amsa mata sallaman da tayi haΙ—e da cewa “Wato sai anjamin aji kafun a fito ko?”

Ɗan guntun murmushi Zahrah tayi haΙ—e da cewa “Bawani batun jan aji, ni a hakan ma inaganin na fito da wuri”

Shima murmushin yayi haΙ—e da cewa “Kinyi kyau!”

Still murmushi tayi, cikin son kawar da zancen da yayi na cewa tayi kyau, tace “Lafiya kuwa naganka a dai-dai wannan lokacin?”

Gyara tsayuwarsa yayi haΙ—e da maida nutsuwarsa gareta “Maganar danazo miki da’ita Zahrah bata tsaye bace, yana da kyau mushiga mota, sai mu tattauna ko?”

Ɗan jim Zahrah tayi, haΙ—e da cije lips Ι—inta, “Shikenan amma inafatan bazamu jimaba, kafasan banson fitowa waje da dare”

“Insha Allah, bazamu Ι—au tsawon lokaci muna magana ba!” Dr yafaΙ—i hakan lokacin da yayimawa kansa masauΖ™i a cikin motar tasa, bayan ya kunna Ζ™oyin wutar dake cikin motar take haske ya gauraye cikin motar.

STORY CONTINUES BELOW

Gyara zama Zahrah tayi, haΙ—e da tattaro duka nutsuwarta “Inajinka” tafaΙ—a a taΖ™aice.

Wani irin numfashi Dr yayi, haΙ—e da fitar da iska daga bakinsa, sai yanzu yakejin cewa, bazai iya furta abun da yakawosa ba, gaskiya yanajin nauyi, baisan tayaya Zahrah zata karΙ“i muradinsa ba, kada maganar da zaifaΙ—a ma ta yazamo sanadiyar rugujewar nishaΙ—in da yake gani akan fuskarta yanzu, “Ta’ina zanfara?” ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa.

“Lafiya kuwa, naga kayi shiru?”

Zahrah ta tambaya, cike da mamakin yanda yayi shiru, bayan yace akwai maganar da zasuyi.

Nannauyar ajiyar zuciya ya sauΖ™e, haΙ—i da maida kallonsa gareta, saida ya tattaro nutsuwarsa kafun yace…

“Yazakiji idan wani yazo miki da batun soyayya a wannan lokacin Zahrah?” abun da ya iya fitowa daga bakinsa kenan, domin a gaskia shikam yarasa ta’ina zai fara.

“So kuma? wani irin so?” Zahrah ta tambaye shi cike da mamakin kalaman nasa.

“So na Aure Zahrah!” yafaΙ—i maganar cikin Ι—ar Ι—ar.

“Au..r..e.. Kuma Likita? Aure fa kace, dama akwai wani wanda, zaiji kwaΙ—ayi da sha’awar aure na ne? hmmm a gaskia bana tunanin haka, domin kuwa babu wani wanda zai so ni da rayuwata, a yanda nake Ι—innan!” Zahrah tafaΙ—i hakan da’iya ka gaskiyar ta.

“Kada kice haka Zahrah, akwai mata masu rauni da yawa irin ki, amma an auresu, kuma anzauna dasu, ke me yasa zaki yanke Ζ™auna da….”

“Dan Allah kadaina min wannan zancen Doctor, banjin zan sake son wani Ι—a namiji a duniyar nan”

Zahrah ta katse shi da ga maganar da yakeyi, ci gaba tayi da cewa

“taya kake tunanin zansake kai kaina tarkon da ya ruguzamin rayuwa, shi So Ι—in dakake faΙ—a yanzu, shine ya ruguzamin rayuwa ta, ya rabani da duk wani farinciki na rayuwata, shin idan kace min na sakeyin So, kamin adalci kenan? ” Tuni hawaye sun gama wanke mata fuska.

“Kada kice haka Zahrah, kefa musulmace, kuma ke mace ce, nasan kina da sanin cewa, kyautatuwar rayuwar Ζ΄a mace shine aure, haka kuma rayuwar Ζ΄a mace bata cika hundred percent sai da aure, haka kikeso ki Ζ™are rayuwarki ba aure? ko kin manta cewa cikar mutumcin mace shine a ganta gidan mijinta? yin Aure shine burin kowacce mace ta Ζ™warai, nasan kema wannan shine burinki, kada shaiΙ—an yayi amfani da abun da yafaru dake, ya ruguza miki rayuwa, ya hanaki aikata sunna!”

“Hakan shine burina amma ada, wa zai aureni a yanzu? waye zai Ι—aukawa kansa duhu? waye zai Ι—auki sauran da wani yaci ya rage, sauran da wani ya tarwatsa, ya zuba Ζ™azantarsa, acikin cikinta, waye zaiyi hakan? bazan yaudari kaina ba, nasan babu wani wanda zai aureni a yanda nake, bantaΙ“a aure ba, amma kuma niba budurwa bace a yanzun, ya cuceni yariga ya karΙ“e abun da nake burin bawa mijina na sunna, waye zai yarda da haka?”

“Nine nan Zahrah, Nasan komai a kan ki, kuma zanyarda da duk wata Ζ™addaranki, nine wanda zan sharemiki hawayenki, kece damuwata bawai budurcin kiba, kiyarda dani dan Allah!!” Doctor Sadeeq yafaΙ—i hakan cikin jajircewa..

Kamar sauΖ™an aradu haka Zahrah taji sauΖ™an kalamansa a cikin kunnuwanta, cak ta tsaida kukan da takeyi haΙ—e da, da hangame baki tana kallonsa, gani take kamar ma baya cikin hayyacinsa, Ζ™aryane tayaya za’ace Namiji mai aji, kamar Doctor yace wai ya amince da Ζ™addaranta zai aureta, wannan ba gaskia bane,

“Kada kiyi shakka ko kokonto, ba yaudara’nki nake ba, dagaske nake har cikin zuciyata, don Allah ki bani dama Zahrah, burina da fatana kawai ki amince min!”

Kai Zahrah ta shiga girgizawa, cikin tsananin Ι“acin rai da danasin sauraransa da tayi tasoma cewa ” Nayi Babban kuskure, haka kuma na tabka nadaman baka daman shigowa rayuwata da nayi, ashe dukanku haka halinku yake, macutane ku azzalumai, ashe bazaku taΙ“a sanjawa ba, dama Ι—aya kawai idan aka baku, sai ku nemi shigo da manufarku, kaicona da abun da Zaid yayi mini baikasance IZNAH ga rayuwata ba, kaicona dana sake aminta da kai, kaicon zuciyata, kafita a rayuwata dan Allah, kaje banaso nasake ganinka ko kuma jinka, katafi kayi nisa da ni, kabarni na rayu cikin salama dan Allah!!” gaba Ι—aya hawayen Ι“acin rai yagama wanke mata fuska, Ζ™oΖ™arin fita daga motar ta somayi, cike da tashin hankali Doctor Sadeeq ya riΖ™o hanunta, ko kaΙ—an baiyi zato ko tsammani ba, saijin sauΖ™ar mari yayi akan kumatunsa, Zahrah ce ta Ι—aukesa da lafiyayyen mari, babu abun da ke kwance akan fuskarta banda tsananin Ι“acin rai,

STORY CONTINUES BELOW

“Koda wasa kada kasake Ζ™oΖ™arin taΙ“ani, mayaudari, dama haka kuke bakuma zaku canza ba!!” fuuuuu haka Zahrah tafice daga cikin motar tamkar kububuwa.

Tamkar statue haka Dr Sadeeq ya tsaya, komai nasa daina aiki yayi, sai numfashinsa dake fita da sauri, ganin komai yake tamkar al’amara, wai yau shine Zahrah ta mara da hanunta, a hankali yasanya hanunsa ya shafi kan kumatunsa inda Zahrah ta wankesa da mari, ko kaΙ—an baiga laifin Zahrah ba, kuma baiji zafin marin da ta masa ba, babban damuwarsa da tashin hankalinsa, shine yanda yaga Zahrah tana kuka wiwi, sannan kuma ranta yayi matuΖ™ar Ι“aci, tabbas da yasan abun zai Ι“aci har haka, to da baiyi gigin furta mata kalmar cewa zai aure ta ba, ko da na minti Ι—aya ne bayason Ι“acin ran Zahrah, yanzu yasan haka zata kwana tana kuka, maiyasa? maiyasa na kasa jurewa? ni nake burin faranta rayuwa da zuciyarta, amma sai gashi da kaina nasake ruguza farinciki’nta maiyasa? yatambayi kansa da Ζ™arfi, cike da haushin kansa ya sanya hanunsa duka biyu ya daki siterin motar tasa, wani irin haushin kansa yakeji, yayi dana sanin sanar da’ita abun dake cikin zuciyarsa, “mai yasa na yarda nazamo LOSER?” ya tambayi kansa cikin Ζ™unan zuciya, yakusan 10 minute yana zaune a cikin motar, da Ζ™yar ya’iya tada motar yabar cikin unguwar tasu…

Zahrah kuwa tana shiga gida, kaitsaye Ι—akinta ta wuce, zamewa tayi a Ζ™asa, tashiga rera sabon kuka, lallai tayarda cewa Ƙaddaranta mai girma ce, daga wannan sai wannan, bata taΙ“a zato ko tunani’n haka zai fito daga bakin Dr Sadeeq ba, ko da wasa bata taΙ“a ayyana wani abu a ranta ga me da shi ba, maiyasa zai zo mata da wannan maganar a daidai wannan lokacin? maiyasa zai sake maida ita uΖ™ubar da tayi nasaran samun bakin fita daga cikinsa? tabbas yanzu kam tayarda cewa duhu yasamu mazauni a cikin rayuwarta

“Bawanda zai soni a haka, shima nasan ba sona yake ba, wata manufarsa kawai yakeson cimmawa, ashe Ζ™addarorina suna da yawa?” ta tambayi kanta cike da ruΙ—u.

Sanin bata da amsar bawa kanta, yasanya ta cigaba da kukanta, ganin hakan bazai fishsheta ba yasanya ta Ι—auro alwala tazo ta fara gabatar da salla, haΙ—e da miΖ™amawa mai kowa mai komai duka lamuranta…

Koda Doctor ya isa gida, baije koda Ι“angaren mahaifiyarsa bane, kai tsaye Ι“angarensa ya nufa, gaba Ι—aya jiyakeyi duniyar ta masa Ζ™unci, saboda cimma muradinsa yasake sanya Zahrah a damuwa, kwanciya yayi lamo akan gado, zuciyarsa cike da tarin tunanuka kala kala, gaba Ι—aya kalamanta ne suke yawo a Ζ™waΖ™walwarsa, babu kalman da tafi tsaya masa a rai kamar inda takecewa ” Natabka nadamar baka daman shigowa rayuwata da nayi, katafi ba naso na sake ganinka ko kuma jinka!!” wannan kalamannata sunfi komai Ι—aga masa hankali, sam shikam ya ma manta da marin da tayi masa, saboda bai Ι—auki marin a matsayin komaiba, shidai shiga damuwarta ne bayaso, baisan wani irin so yake mawa Zahrah ba, bayason ganinta a cikin damuwa, ba kuma yason Ι“acin ranta, amma tayaya Zahrah zata fuskancin hakan? Yanaso ya aureta yakuma inganta rayuwarta, ba budurci’nta bane abun so a gareshi ita kanta ce abarsonsa, haΖ™iΖ™a kowani namiji yana burin auren mace yasameta a budurwa, shima kuma yana burin hakan, amma son da yakemawa Zahrah, yasanya zai iya karΙ“anta a yanda take.. Haka Doctor yayita saΖ™awa da kuncewa, da Ζ™yar bacci Ι“arawo yayi nasaran Ι—aukarsa.

Ɓangaren Zahrah ma dai hakanne takasance da Ζ™yar ta’iya runtsawa a wannan dare….

*TURKEY*

*ZAID* ne zaune akan wata haΙ—aΙ—Ι—iyar kujera, sanye yake da riga long slive, white colour yayinda wandon jikinsa ya kasance baΖ™i, suit ne baΖ™i Ι—aure a saman kayan nasa, sosai yayi kyu a cikin shigartasa, hanunsa riΖ™e yake da wani dogon kofi na glass, bakomai ne acikin kofin ba face giya, a hankali yake sipping giyar tasa, yayinda ya Ι—aura Ζ™afansa Ι—aya kan Ι—aya, gefensa kuwa Abid ne zaune shima dai irin shigar Zaid Ι—inne a jikinsa, sai dai shi nasa kalan sun kasance blue, “Lokaci fa yana tafiya Zaid, yakamata ace yau munkoma New York, amma bansan dalilinka nacewa muzauna anan ba, ni fa duk yanda instanbul takai ga haΙ—uwa da daΙ—in zama, batakaimin new york ba, kasan can akwai mata Ζ΄an harka, amma ni gaskia nan a takure nake!” Abid yakai Ζ™arshen zancennasa cike da Ζ™osawa.

STORY CONTINUES BELOW

Kyakkyawan murmushinsa yayi haΙ—e da maida kallonsa ga wani kyakkyawan ruwa dake gudana a gefensu,

“Inason zaman Instanbul sosai Abid, domin yanayin garin yanasawa inajin shauΖ™in abar sha’awata!!”

“Bangane shauΖ™in abar sha’awan kaba? wai meke damunka ne? kusan tsawon watanni kenan dana fuskanci sauyawa a tattare dakai”

“Sha’awa nakeji Abid, matsanancin sha’awarta nakeji!”

Zaid yafaΙ—a cike da tsananin shauΖ™i.

“Sha’awa? wacece ita?” Abid ya tambaya cike da zaΖ™uwa, domin shikam yarasa wace irin macece Zaid ya kejin sha’awa’rta haka, ko da yaushe cikin maganarta yake, kuma ita kaΙ—ai yakejin sha’awa.

“ZAHRAH NA!” Zaid yafaΙ—a cikin wata murya mai Ι—auke da ma’anoni.

Dariya sosai Abid yasanya, hadda riΖ™e ciki, “Zahrah fa kace Zaid, wannan villager girl Ι—in, koba sugar baby’nka ba?” Abid yatambaya yana Ζ™oΖ™arin gimtse dariyar da ta tasomai.

” Tana da matuΖ™ar mahimmanci a wajena Abid, bantaΙ“ajin irin abunda nakeji akanta ba, inason kasancewa da’ita a koda yaushe, inaso tazama ita ce mace guda Ι—aya dazanna yin sex da’ita dare da rana, sha’awarta tamun mummunan kamu Abid, kasan yanda nakeji kuwa ?” Zaid ya tambayi Abid cikin sigar rashin wasa.

“KokaΙ—an bansan ya kakejiba, amma kuma Zaid wannan ba sha’awa bane SO ne” Abid yafaΙ—i hakan da iya gaskiyarsa, domin shi abun da ya fahimta kenan.

Dariya sosai Zaid yashiga yi, haΙ—e da sanya hanunsa ya daki kafaΙ—an Abid.

“Shirmen banza, wai SO? menene SO Abid? kasan me kake faΙ—a kuwa, taya sha’awa zata zama SO, so fa kananufin wai inasonta ne, hahaha Abid Ζ™waΖ™walwarka Ζ™aramace, taya za’ayi nayi soyayya da’ita, sha’awace kawai kuma da zaran na sakeyin sex da’ita nasan komai zai wuce, tun farkoma danasan ban Ζ™oshi da’itaba, ai da banbari ta tafiba!!” yaΖ™are maganar yana mai Ι—aga kofin giyarsa yakai baki.

Murmushi kawai Abid yayi, domin yafi kowa sanin cewa Zaid bayason gaskia, amma tabbas shikam anasa hasashen zuciyar abokinsa takamu da so, yana kuma da tabbacin idan har Zaid zaiyi sex da Zahrah sau Ι—ari, to wannan sha’awar bazata taΙ“a barinsa ba, saboda dama ba sha’awar bace So ne.

“Shikenan naji ba soyayya bane, sha’awa ce, amma kasan dai yanzu bazaka taΙ“a samunta ba ko, wataΖ™ilama ta mutu, domin ina da tabbacin cewa baka shigeta da wasa ba”

“Dole zan sameta ne Abid, dole sai ta dawo gareni, kuma dole ta Ζ™ara yarda da Ζ™udurina a karo na biyu, aure baya Ι—aya daga cikin tsarina, amma idan taΖ™i yarda dani, saina aureta!”

Saurin kallon Zaid Abid yayi jin abun da yake fitowa daga bakin Zaid Ι—in, “Aure kuma Zaid? Abid yafaΙ—a cike da mamaki.

“Ƙwarai zan’iya aurenta Abid, Ζ΄an matan tana burgeni fiye da zatonka, inason komai nata, tana da kyau na fili dana baΙ—ini, ni nasan mai naji a cikinta Abid, bakuma zanso nasake rasata ba, sha’awarta yasa koda yaushe cikin tunaninta nake, na kuma gama yanke hukunci, nan da sati Ι—aya zankoma Nigeria, badon kowa ba sai don ita, nayi missing tattausan laΙ“Ι“anta masu zaΖ™i kamar zuma!!” Zaid yakai Ζ™arshen zancennasa yana mai lumshe idanunsa, da suka soma zama ja lokaci Ι—aya.

Hangame baki Abid yayi yana kallon Zaid, “Anya kuwa ba aljana Zaid ya haΙ—u da’ita ba?” yatambayi kansa, tabbas baitaΙ“a ganin Zaid acikin hali makamancin wannan ba, gaba Ι—aya Zaid ya sauya, yarage yawan yin sex da mata, a cewarsa wai bayajin daΙ—insu, sannan kuma koda yaushe cikin tunani yake, to idan ba so ba meke da munsa ? Abid yakuma tambayar kansa.

A hankali Zaid ya buΙ—e idanunsa, haΙ—e da miΖ™ewa tsaye kwalbar giyansa dakuma kofi ya Ι—auka a hanunsa kai tsaye yanufi wani babban bene inda anan masauΖ™insu yake, da kallo kawai Abid yabisa har ya Ι“acewa ganinsa..

Yana shiga cikin Ι—aki ya Ι—aga kwalbar giyarsa ya kafa a bakinsa, saida ya shanye giyan tas kafun yayi wurgi da kwalba’r, kaitsaye ya nufi inda ma’ajin zane zanen sa suke, Caboard papers ne dayawa acikin wajen kuma duka Ι—auke suke da hoton zanen fuskar Zahrah a jiki, wani ma iya bakinta kawai ya zana, wani ko iya idanunta ya zana, yana yawan yin zanen ne idan matsanancin kewa da sha’awarta ya da mesa, Ι—aukan caboard paper’n dake Ι—auke da zanen bakinta yayi haΙ—e da mannawa akan nasa bakin, wani irin zubawa yaji tsikar jikinsa tayi, domin kuwa ji yayi tamkar itaΙ—ince da gaske, zamewa yayi ya zauna a Ζ™asa daΙ“as, haΙ—e da warwatsa caboard paper’s Ι—in akan jikinsa.

“Inakewarki Sugar Baby’na ,nayi missing komai naki, duk da cewa nasan kina fushi dani namiki da zafi, amma kiyi haΖ™uri wannan karon bazan miki da zafi ba, a hankali zan bi da ke tayarda zakiji daΙ—i har brain Ι—inki, zakuma za ki saba da ni a sannu, na miki alΖ™awari zandawo gareki!, kina sona?” yatambayi zanen fuskarta dake jikin wani Ζ™aton caboard paper, “Nasan har yanzu kina sona ko Zahrah na?” still dai wannan zane yakuma tambaya, murmushinsa mai kyau yakumayi, haΙ—e da sanya hanu yashafi gefen kumatunsa.

” Kiyi murmushi Zahrah na, nakusa zuwa gareki, a yanzu zan iya sadaukar da komai na zuwa gareki, amma fa banso kina yawan fushi, duk da cewa idan kina fushi kinfi kyau !”

Haka Zaid yayita sambatun sa har bacci ya Ι—aukesa a wajen.2

Kwance take akan Ζ™irjinsa, yayinda fuskarta ke Ι—auΖ™e da murmushi, a hankali ya matso da fuskarsa daf da tata, cike da matsanancin sha’awa ya kamo lips Ι—inta na Ζ™asa yashiga tsotsa a hankali, cike da Ζ™warewa yake cusa harshensa cikin bakinta, cike da soyayya ta soma tsotsan harshensa tana mai lumshe idanunta, a hankali yayi Ζ™asa da hanunsa zuwa Ζ™irjinta, cikin salo yashiga shafa breast Ι—inta, yanayin yanda suke sucking tongue Ι—in junansu, shiyasanyasu suka fice a hayyacinsu lokaci guda, Ζ™asa yayi da kansa zuwa Ζ™irjinta, yana shirin Ι—aura bakinsa a kan nipples Ι—inta kenan, taΙ“ace masa Ι“at, dai dai lokacin yafarka a hargitse, wani irin nannauyar ajiyar zuciya ya sauΖ™e, duk da cewa sanyin A.C na aiki a cikin Ι—akin amma shi gumi yake haΙ—awa, da Ζ™yar ya’iya miΖ™ewa ya shiga bathroom haΙ—e da sakarmawa kansa shower.

ba yau yafara wannan mafarkin ba, amma maiyasa Zahrah take gudunsa acikin mafarki, takan Ι“acewa ganinsa a daidai lokacin da yake matsanancin buΖ™atar ta….Yajima tsaye a gaban shower ruwa na dukansa, mafarkinsa na yau ne yatsaya masa a rai, duk da kuwa cewa ba wannan bane karo na farko, daya fara yin irin wannan mafarkin. Koda wasa baiyi niyar komawa America a yau ba, amma yanzu yaji ajikinsa cewa komawarsa can Ι—in yafi masa, domin kuwa mararsa har Ζ™ullewa take saboda sha’awa, gaba Ι—aya kwana biyunnan da suka shuΙ—e baiyi sex ba. A gurguje ya shirya kansa, bayan yasanar da Abid cewa shima ya kimtsa zasu wuce America a yau. Suna zuwa airport basu wani daΙ—e ba, jirginsu yaΙ—aga zuwa sararin samaniya….+

Nigeria

Washe garin ranan da Dr yazo da dare yafaΙ—i muradinsa..

Tun tashinta takejin Ζ™unci a zuciyarta, hakanan take jin ta tsani komai na duniyar, badon lecture’n da zasuyi yau mai amfani bane, to tabbas da bazata je makarantar bama.

Doctor Sadeeq ne tsaye a tsakiyar Ι—akinsa, yayinda hannayensa duka biyu ke sanye cikin aljihun wandonsa, shima kallo Ι—aya zaka masa kafahimci cewa yana cikin damuwa, kallon sa yamaida kan agogon bangon dake saΖ™ale ajikin bangon Ι—akin na sa, Ζ™arfe 7 da rabi na safe kenan, tabbas yasan yau Ζ™arfe takwas suke da lecture, yanaji a jikinsa cewa yayi mata laifi mai girma, sannan idanunsa suna matuΖ™ar son ganinta, to amma a yanda yakeji bazai iya zuwa gareta ba, “idan ma naje nace mata me?” yatambayi kansa. ” Nariga dana furta mata abun dake cikin zuciyata, dole zanbata lokaci domin samun dawowar nutsuwar ta” yafaΙ—i hakan a bayyane, wayarsa ya Ι—auka haΙ—e da kutsawa cikin dialing call Ι—insa, numbern drivernsa yashiga Ζ™ira kai tsaye, Ζ™ara biyu wayar tayi, drivern yaΙ—auki Ζ™iran, kasancewar driver’n yasan gidan su Zahrah, yasan ya kai tsaye, bai tsaya yi masa wani kwatance ba, yace masa yaje ya Ι—auketa ya kaita makaranta, da “to” kawai driver’n ya amsa masa, katse Ζ™iran yayi haΙ—e da cilla wayar tasa zuwa kan gado,

“Yasan balallai ta yarda tabi driver’n ba, domin yanayinta da yagani jiya, kaΙ—ai ya isa ya tabbatar masa da hakan, amma burinsa ne ya bata ingantacciyar kulawa, shiyasa baiyi Ζ™asa a guiwaba wajen sa driver’n nasa kaita makarnta, saboda baiso ta hau wani abun hawa bayan nasa….

Ko kwalli, yau bata shafa ba, balle kuma uwa uba fawder, zumbuleliyar doguwar riga ta sanya, haΙ—e da Ι—aura Ζ™aton hijab akai, kallo Ι—aya zakayi mata kasan cewa tana cikin damuwa da Ζ™unci.

Koda tayi mawa su Baffa sallama, suma sun fahimci cewa yanayinta ya sauya, amma sai suka share babu wanda ya tambayeta.

Tana kai Ζ™ofar gida zuciyarta tayi wani irin bugawa, sakamako’n ganin motar Dr Sadeeq, da tayi fake a Ζ™ofar gidan nasu, tsayawa tayi cak ganin cewa driver’n sane yafito daga cikin motar, saΙ“anin shikansa Dr Ι—in.

Cike da girmamawa Mudi driver ya Ζ™araso inda Zahrah ke tsaye.

” Ranki shi daΙ—e barka da safiya! dama yallaΙ“oi ne yace nazo na kaiki makaranta, shi ba zai samu daman zuwa ba, wani aiki ne ya riΖ™esa, kawo jakar na karΙ“amiki” Mudi driver ya Ζ™are zance’n nasa yana mai Ζ™oΖ™arin karΙ“an jakar dake riΖ™e a hanunta. Saurin ja da baya tayi haΙ—e da fusge jakarta, cike da Ι“acin rai tace.

“Kakoma kace masa bana buΖ™atar kulawarsa koda kaΙ—anne, ka kuma ce masa injini yafita a rayuwata, saboda bana buΖ™atarsa!” tanakai Ζ™arshen zancennata tasakai tayi tafiyarta.

STORY CONTINUES BELOW

Da kallo kawai Mudi driver yabita. “Uh ni naga bala’i, daga taimako kawai, to Allah ya kyauta” Mudi yafaΙ—a yana mai komawa cikin motar, key yayimawa motar haΙ—e da nausata kan hanya, tabbas zai koma ya shaidawa uban gidansa, duk abun da tace a faΙ—amai..

Cikin ikon Allah tana isowa bakin titi tasamu mai taxi, bawani Ι“ata lokaci tashiga yaja sukayi gaba, bayan ta sanar masa inda zai kaita.

Tun shigowarta cikin ajin, Husnah ta lura da mugun sauyawan da fuskar Zahrah’n tayi, domin kuwa kowa ya kalli idanunta, zai fahimci cewa tayi kuka har ta Ζ™oshi. kasancewar Zahrah’n na shigowa malami yashigo, yasanya Husnah bata samu damar tambayarta komai ga me da sauyawarta ta ba.

Koda aka fito daga lecture, kan dakalin da suka sama zama, yauma sukai mawa kansu masauΖ™i.

“Wai meke damunki ne Zahrah? gaba Ι—aya kinsauya, bayan jiya ba haka muka rabu dake ba, sannan kuma na kula cewa, yau ba Dr bane ya kawoki, maike faruwa?” Husnah ta tambaya cike da kulawa, ga Ζ™awarta ta.

“Inacikin matsala Husnah! a she a yanzu babu wani, wanda zai taimakeka don Allah sai don biyar buΖ™atar kansa? na Ι—auki yarda ta na basa, na Ι—aukesa tamkar Ι—an’uwa, na’aminta dashi, nayi saurin yadda haΙ—i da sakewa dashi, bantaΙ“a zaton haka zata faru ba, ashe shi abun dake cikin zuciya da ruhinsa daban ne, wani abune saΙ“anin tunani na!” Zahrah tafaΙ—a tana mai share Ζ™wallan daya gangaro daga cikin idanunta.

“Banganeba, kinsani a duhu, maikuma ya sake faruwa? ki faΙ—amin !” Husnah tafaΙ—i hakan cike da zaΖ™uwa, don ta Ζ™osa taji menene matsalar Ζ™awarta ta.

“Kinsan abun da yafaru dani Husnah, Zaid yaci mutumci na, ya Ζ™waci budurcina da Ζ™arfin tsiya, ya halaka min rayuwa, shin kinaga akwai wani namiji dazai soni tsakani da Allah, bayan yasan abun da yafaru dani?” Zahrah ta tambayi Husnah.

“Haryanzu banfahimci inda kalamanki suka dosa ba Zahrah, zaifi kyau ace kiwarwaremin komai!” Husnah tafaΙ—i hakan cikin rashin fahimta.

“Ba gaskiya bane Husnah, bai faΙ—awa kansa da zuciyarsa gaskiya ba, baizamanto gaskiya ba, soyayyar da yakemin ba gaskiya bace, Husnah bazan yaudari kaina ba, domin nasan babu tayanda za’ayi cikekken namiji mai aji da lafiya kamar Doctor Sadeeq, yace wai ni yake so ya aura! ina kokonto akan al’amarin !” gaba Ι—aya hawaye sun gama wanke mata fuska, lokacin da takai Ζ™arshen zance’n nata.

Nannauyar ajiyar zuciya Husnah ta sauΖ™e, domin kuwa sai yanzu ta fahimci inda matsalar Ζ™awartata take, dakuma abun da ke damunta.

“Doctor da kansa yace zai aure ki Zahrah?” Husnah ta tambaya, bayan ta aza hannayenta duka akan kafaΙ—un Zahrah.

Kai kawai Zahrah ta’iya gyaΙ—awa, alamar “eh”

“Ba wasa bane Zahrah kamar yanda kika Ι—auka, haka kuma ba yaudara bane kamar yanda kike tunani, har yanzu keΙ—in mai kyauce, kuma haryanzu keΙ—in haΙ—aΙ—Ι—iyar mace ce abar so ga kowani irin namiji, ba’akanki a ka faraba, baikuma dace ki Ι—au hukunci mai tsanani gawanda baiji ba bai gani ba, kina tunanin Doctor Sadeeq yaudaranki zaiyi ?” Husnah ta tambaya.

“Ƙwarai kuwa Husnah, ke kanki kinsani, namiji kamar Dr ba sa’an aurena bane, ko lokacin danake Ι—auke da mutumcina yafi Ζ™arfina, balle yanzu danake fanko, inaso kisani wannan karanbani’n shi na tafka a karon farko, yazo yazamemin babbar matsala, domin kuwa nayaudari kaina, na sawa zuciyata soyayyar wanda har gaban abada yafi Ζ™arfina, yakuma yi mini rata, na yaudari kaina danaΖ™i amfani da tunanin cewa Zaid yafi Ζ™arfina, bazan taΙ“a yarda nasake aikata haukan dana aikata a baya ba Husnah!” Zahrah tafaΙ—a cike da raunin murya dana zuciya.

“So baitaΙ“a zama haukaba Zahrah, kada kicemin kin wulaΖ™anta Doctor saboda abun da Zaid yayi miki, kada ki yarda da tunaninki nacewa gaba Ι—aya maza mayaudara ne, kowa da irin halinsa, kuma masu irin halin Zaid basa Ι“oyuwa a kamanni da halaye, soyayyarsa ce kawai tarufe miki ido, har ki ka kasa hango mummunar manufarsa a kanki, yana da kyau ki nutsu kiyi tunani, inada tabbacin cewa Dr Sadeeq, ba zai taΙ“a cutar da rayuwarki ba, kema kuma yakamata kisan hakan, kada tunaninki ya gushe ki kasa tantance fari da baΖ™i, wlh ni ina da tabbacin cewa Dr Sadeeq ba mutumin banza bane, bakuma zan Ι“oyemiki ba, tabbas idan kika tsaya wasa da damarki, to zata miki mummunan suΙ“ucewa, haΖ™iΖ™a Dr Sadeeq haΙ—aΙ—Ι—en gaye ne, wanda ko wacce mace zatayi fatan samunsa a matsayin mijin aurenta, nasan idan nace miki kiyi soyayya yanzu na haΙ—aki da babban aiki, amma zai kyautu ace ki koyawa zuciyarki soyayyar Dr Sadeeq, shawara nake baki Zahrah, idan kuma har kikayi amfani dashi, bazaki taΙ“a danasani ba, dan Allah Ζ™awata kiyi tunani mai kyu!” Husnah tafaΙ—i hakan cikin son Ζ™arfafawa Zahrah guiwa.

STORY CONTINUES BELOW

Hawayen dake zuba daga cikin idanunta ta sanya hanu ta share.

“Bazan iya ba Husnah, bazan iya taΙ“a sake son wani ba a cikin rayuwata, kada ki ga laifina, nasan Dr Sadeeq yafi Ζ™arfina, yana da asali, yana da Ζ΄an uwa, yanada gata, yana da kuΙ—i, yanakuma da Ζ΄ancin da zai zaΙ“i matar aure wacce ransa keso, nikuma fa? idan kikayi dubi da tushena, to ban cancanta da zama inuwa Ι—aya da shi ba, nifa yanzu banda wani Ζ΄ancin da zan iya zaΙ“in mijin aure da kaina, sbd akwai nakasa acikin rayuwata, dole sai mai tawakalli ne zai iya aure na, to maiyasa zansanya kaina a cikin wahala? balallai farincikin da Dr Sadeeq ke Ζ™oΖ™arin bani yakasance dauwamemmeba, nafaΙ—amasa yafita a rayuwata Husnah, a yanzu bana buΖ™atar kowani namiji, zaifi kyautuwa a gareni nayi rayuwata ni kaΙ—ai, nayarda da Ζ™addarata, amma kuma yazama dole na kiyaye sake jefa kaina a haΙ—arin soyayya!”

Rungume Zahrah,

Husnah tayi ajikinta, sosai tausayin Ζ™awarta ta ya kamata, haΖ™iΖ™a Zaid yacutar da rayuwar Zahrah, ya rabata da duk wani sukuni nata, amma a kwai Allah.

“HaΖ™iΖ™a dole zakiji ciwo Zahrah, amma yana da kyau ki zurfafa tunani, ni ina da tabbacin cewa Dr Sadeeq auren ki yakeso yayi bada wasa ba, amma abun da kikayi masa baki kyauta ba, ki basa haΖ™uri, koda kuwa bazaki auresa ba, yayi babban Ζ™oΖ™ari acikin rayuwarki, kiyi nazari, amma kuka ba naki bane, kuma yana da kyau rama halacci da alkhairi !”

Gaba Ι—aya Zahrah jitayi jikinta yayi laΖ™was, take marin da ta shararawa Dr Sadeeq akan fuskarsa ya dawo mata, wani irin faΙ—uwar gaba taji, ko kaΙ—an batayi tunanin zata iya kai hanunta jikinsa da sunan duka ba, amma a daren jiya Ι“acin rai yasanya idanunta rufewa, harta iya ta mare sa batare da tayi tunanin komai ba, tabbas komai yayi mata bai cancanci mari daga gareta ba.

Gaba Ι—aya kasa sakewa a cikin makarantar Zahrah tayi a wannan ranan, dole ta tattara yanata yanata ta dawo gida.

Zaune take jigum akan tabarma yayinda hannuwanta ke dafe da Ζ™uncinta, idan da za’a ce za’a kasheta idan bata faΙ—i, tunanin me take ba, to tabbas da sai dai a kashetan, amma ita kanta batasan tunanin mai take ba.

Inna da fitowarta kenan daga bayi, hanunta riΖ™e da buta, kama Ζ™ugu tayi, haΙ—e da maida kallon ta zuwaga inda Zahrah ke zaune tayi jigum.

“Wai lafiyanki kuwa Zahrah? meke damunki ne? tun safe haka kike sukuku, yanzu kuma kinyi tagumi tamkar wacce akamawa mutuwa, kodai halinki na da, kike son dawowa dashi ne? to wallahi bazan Ι—au wannan iskancin ba, tun wuri ma kisani!” Inna taΖ™are maganar cikin faΙ—a faΙ—a.

“Ko Ι—aya bahaka bane Inna, narasa taya zan Ι“ullowa matsala ta ne!” Zahrah tafaΙ—a cike da sanyin murya.

“Matsala! wace irin matsala kuma?” Inna ta tambaya cike da son jin gulma.

“Inna wai Likita ne yace zai aure ni !” Zahrah tafaΙ—i hakan cikin sarΖ™ewar murya.

“Likita yace zai aure ki!” Inna ta maimaita maganan cikin Ζ™araji haΙ—e da sanya duka hannayenta biyu ta dafe Ζ™irjinta.

Kai kawai Zahrah ta’iya gyaΙ—a mata domin zuwa lokacin har Ζ™walla sun soma cika mata ido.

Wani irin guΙ—a Inna tasa, haΙ—e da sake kama Ζ™uΖ™u, “Lallai kuwa, wannan babban al’amari ne, mai Ι—auke da tarin farinciki, Allah yasa dai kin amince masa?” cike da zaΖ™uwa inna taΖ™are maganar.

“Bazan iya ba Inna, kuma ma ni yanzu babu batun aure a tsarina,zan zauna kawai naΖ™are rayuwata cikin Ζ™addarata!” Zahrah tafaΙ—a lokacin da hawayen da suka cika idanunta suka samu daman gangarowa.

Salati Inna ta sanya, haΙ—e da soma tafa hannaye.

“Amma kedai Zahrah anyi shashar banza, sokuwa marar wayo, ashe dai baki da hankali, yanzu a yanda kike Ι—in nan, kin samu ance za’a aure ki a haka, kice wai baki amince ba, lallai yau nasake tabbatar mawa da kaina cewa ke wawuyace, to wlh baki isa ba, baki isa Ι“arar mana da alkhairan da zamu samu ba, aure dole ko kina so ko bakya so, wato kinfiso kita zama damu, goΙ—o goΙ—o dake ba aure ko, to kisa aranki cewa aurenki da likita ba fashi, dole!”

“Babu wanda zai mata dole!” Muryan Baffa dake shigowa cikin gidan yakaraΙ—e kunnuwansu.

“Maikake shirin faΙ—a ne malam, kakosan me ta aikata kuwa, Likita fa yace yanason aurenta amma taΖ™i?”

“Ƙwarai kuwa duk na saurari zancen ku, magana ta gaskia Salame, baza’ayiwa yarinyar nan dole ba, yanzu lokacin ta ne, yakamata a bar rayuwarta tasha iska hakanan!” Baffa yafaΙ—i maganar sanda yayi mawa kansa masauΖ™i akan wani Ι—an dakali dake tsakiyar gidan.

“Laaaa shikenan kuma, kakosan abun da kake cewa? kana nufin zuba mata idanu zamuyi, ba mu isa mu sata dole ba? wani shan iska kake Ζ™oΖ™arin samawa rayuwarta, sanin kankane cewa babu wani wanda zaizo yace zai jajiΙ“eta a yanda taken nan, don kawai likita ya rufa mata asiri yace zai aureta, saikayi Ζ™oΖ™arin hure mata kunne.”

“Tashi ki koma Ι—akinki kinji Zahrah, kiyi tunani mai kyau, idan kin yanke hukunci to kisanar dani!” Baffa yafaΙ—a cike da kulawa.

Cikin rashin Ζ™arfin jiki haka Zahrah ta koma cikin Ι—akinta, yayinda take jiyo bala’in Inna a tsakar gida.

Jingina bayanta tayi da bango, haΙ—e da lumshe idanunta, saiyanzu take jin cewa bata kyautawa Doctor Sadeeq ba, amma kuma shima baikyautu ace yazo mata da magana mai nauyi kamar wannan ba, ko da wasa bata taΙ“a kawowa a ranta cewa wani zai sota anan kusa ba, gaba Ι—aya ta cire soyayya a tsari da jerin rayuwarta, tabbas sai dai ta yaudari kanta, amma tasan bazata taΙ“a Ζ™ara son wani Ι—a namiji ba a rayuwarta, ta yarda da shawaran da Husnah ta bata, amma kuma abune mawuyaci, tarayyanta da Dr Sadeeq yazama mai Ι—orewa, shin dagaske aurenta yakeso yayi koko shima wata manufartasa yakeson cimmawa? tatambayi kanta tambayar da bata da amsa, “Idan bakiyi aure ba, haka zaki dawwama Zahrah?” wata zuciyarta tayi mata wannan tambayar. hawayene suka shiga gudu akan fuskarta, lalllai akwai babban Ζ™alubale a gabanta.

Zaune yake akan derny table Ι—in dake tangamemen falon Hajiyar tasa, plate Ι—in abinci ne aje a gabansa, yayinda yake juya spoon Ι—in dake cikin abincin dake gaban nasa a hankali, kusan mintuna 10 kenan da kawo masa abincin, amma yakasa koda kai loma Ι—aya ne na abincin bakinsa, gaba Ι—aya hankali da tunaninsa baya garesa.

Cike da tuhuma Hajiya da tun Ι—azu take kallon sa tace

“Wai meke damunka ne Sadeeq? gaba Ι—aya yanayinka ya sauya, kowa yaganka yasan cewa kana cikin damuwa? gashi nace kaje gidan su Saleema, amma kayi banza da maganan bakaje ba har yau”

Ajiyar zuciya Doctor Sadeeq ya sauΖ™e haΙ—e da maida kallonsa ga mahaifiyar tasa.

“Inada damuwa Hajiya!” yafaΙ—i hakan cikin sanyin murya.

“Subahanallah! damuwa kuma Sadeeq, damuwar me?” Hajiya ta tambaya cike da kulawa, Allah yasani tana matuΖ™ar son Ι—an nata.

“Nasamu wacce nake so ne Hajiya!” Sadeeq yafaΙ—a cikin Ι—ar Ι—ar, don baisan ya Hajiyar tasa zata Ι—auki al’amarin ba.

“Kasamu wacce kake so? wani irin magana ne wannan, wato so kakeyi kamai dani Ζ™aramar mace ko, to wallahi baka isaba, bazai taΙ“a yiwuwa ba, nariga dana gama magana da iyayen Saleema, har Ζ™anin mahaifinka yashigo cikin lamarin, saboda haka wannan batun kama dainasa tun kafun ranka yakai Ζ™ololuwa wajen Ι“aci, banason shirme!” Hajiya tafaΙ—i maganar a fusace, haΙ—e da tashi tabar masa falon.

Tabbas dama yasani ko da Zahrah ta amincewa aurensa, to balalle ne Hajiyarsa ta amince masa ba, amma yasan cewa yanamawa Zahrah so mai tsanani, kuma insha Allah, zai aure ta ya rayu da’ita har zuwa Ζ™arshen rayuwarsa, domin yaji hakan a jikinsa.

Post a Comment for "SHU'UMIN NAMIJI CHAPTER 6 BY FATYMA SARDAUNA"