WANENE SHI CHAPTER 15 THEND KARSHE

WANENE SHI CHAPTER 15 THEND KARSHE
WANENE SHI CHAPTER 15 THEND KARSHE ABINDA YA FARU TSAKANIN IMRAN DA NAANI WATA UKU BAYA. “Duk sanda kake tare da ita wannan b’arin na jikinta yana mstsowa dab da gab’ar nata ruhin, yadda wanda ke jikinka zai iya sensing nata, saboda haka in har tana kusa da kai… zaka iya karb’a ba tare da wanda ke jikinka yayi raunin da zai maka illa ba.” Imran ya gyara zamansa yana kallon zanen taswirar bayanin da jaamil ke nunawa a gabansa, idonsa ya kai kan zanen wani dunkulen abu dake tarwatsewa kamar yana fitar da wani hayak’i, ba tare da ya tambaya ba jaamil ya bashi amsar da yake nema. “In har aka samu matsala, ta haka ruhin dake jikinka zai fara k’onewa.” “Bai kamata mu saka matsala a cikin lissafinmu ba, insha Allah komai zai tafi daidai, sai dai abinda nake tunani kayi wannnan binciken ne tun kafin mu san da cikin Sa’adha, a yanzu kuma baka tunanin k’arfin dutsen zai iya shafarta ta wata hanyar?” Jaamil ya d’anyi gajeren tunanin kafin yace. “Ai d’aya b’arin ruhinka yana jikinta, kuma karka m…