YAREEMA KHALEED CHAPTER 4
••••• firgigit Raihana ta dawo daga dogon tinanin data tafi wanda tayi tin a lokacin data ga mutuwar Khulaid a TV.
yanda ta haΙa zufa kace damben gaske tayi ba tinani ba, Khalid dake gefenta ta kalla wanda ke cikin tsantsar mamaki,al’ajabi da kuma Ιarsuwar firgici a zuciyarsa.
dogon numfashi ta sauke wanda ya sanya Khalid dawowa daga tinaninsa yana kallonta.
hannunta ta maΖale da nasa, zufa kawai take haΙawa domin tabbas idan har asiri ya tonu ayanzu to kashinta ya bushe.
duk da jarumtar da yake tare da ita amma hakan bai sashi jin tsoro a cikin zuciyarsa ba domin gani yake tamkar aljanu ne suka buΙe masa ido.
ta gefen ido guda Raihana ke kallon Rahinat dake duban tv tana goge hawaye.
itama sai yanzu ta maida baki Ιayan hankalinta kan Tv Ιin dan sake tabbatar da mutuwar Khulaid shin gaske ce.
ganin gaskiyar lamari duk sai jikinta ya mutu, take tausayin bawan Allahn ya kamata saboda sadaukarwar da yay akanta.
amma taya akai hakan ta kasance? amsar da bata da wanda zai bata ita sai dai kuma idan har ta gano cewan su Sultana Yasmeen ne sila to itama sai taga bayansu.
jitai Khaleed ya kama hannunta ita da Nimrah sun wuce zuwa room Ιinsu, suna tafe Rahinat na bin bayansu da kallo har sukai cikim Ιakin.
baki Ιaya Rahinat acikin tashin hanΖali take, ita bata damu da baΖin mugun mijin da ΖADDARAR SO ta haΙasu ba, babban burinta wannan baΖar azzalumar da take basaja matsayin ita ta fitar da ita daga wannan mawuyacin halin data jefata.
ko yanzu a wanna hali mahaifanta ke ciki oho gashi bata da wayar kiransu idanma ta samu to da wannan bakin zatai masu magana bayan azzaluma mai kmaa da ita sun nakasa ta.
Ammi,Abbi da Hajiyanta kawai ta tina ta sake fashewa da kuka.yanzu taya zata koma garesu bayan bata da kuΙin jirgi bata da hanyar komawa nigeria tinda bata san ko’ina ba.
tana kallonsa ta Ιan murmusa sannan ta haΙa hannayenta biyu tai masa godia, ta juya zata tafi yasha gabanta yace,
“dan nabiyurrahmati ki tsaya”dakatawa tayi da tafi ta Ιaga masa hannu alaman mi zaka mani
“kince baki san inda kike ba, to yanzu idan kin tafi ina zaki?”
murmushin tai wanda ya taho tare da hawaye ta kuma bashi amsa da hannu “nima ban sani ba”
ya juya ya kalla room Ιin dasu Raihana suka shiga, “kin san wadda naga kina nunawa Ιazu ne ,wannan mai kama dake Ιin?”
tai saurin kaΙa masa kai alaman a’a saboda bata son ya shigo rayuwarta ya rasa ransa shima kaman yanda Khulaid ya rasa nasa a garin taimakonta.
“cikin su ukun duk ba wanda kika sani?”
ta sake Ιaga masa kai. yace, “oak to shikenan, amma idan ba damuwa kizo muje gidana mana ki zauna kamin Allah ya baki lafiya”
ta girgiza masa gami da haΙa hannayenta mai nuna alamun godia sannan tasa Ζafa ta wuce.
tsaye yayi yabi bayan poor girl Ιin da kallo cike da tausayawa, shin ko mike damunta oho?
kai bazai iya barinta ta tafi haka ba dan haka da sauri yabita, gabanta yasha ya dinΖa mata magiyan dan Allah ta barshi ya sami ladan taimakon wallahi bazai cutar da ita ba in kuma hakan ta kasance Allah yay mata sakayya tin aduniya kamin aje ga lahira.
biro da takarda daya miΖo mata ta rubuta masa, _bawai taimakonka ne bana so ba saboda fuskanka bai kama dana mugwayen mutane ba, da zaka cutar dani bama zaka kawo ni a asibiti ba domin aceci raina ba…kawai dai ina guje maka shiga wani hali ne ata dalilina saboda duk wanda ya kasance tare dani da sunan taimako mutuwa yake, kayi haΖuri na gode da iyaka taimakon da kayi mani Allah ya biyaka da gidan aljanna._
sose kalamanta suka Ζara sawa yaji wani mugun tausayinta ya sake kamashi, har Ζasa ya zube Ζafafunsa ya hau mata magiya har saida ta amince.
sanyi yaji ya ratsa zuciyarsa saboda bayan taimakonta da yake sonyi kuma akwai sonta tin na wasu watanni a zuciyarsa wanda yake ganin idan har babu ita a rayuwarsa to ba lallai yaci gaba da rayuwa cikin jin daΙi ba.
“na gode sose da kika amince kuma ina roΖon Allah ya fitar dake daga cikin Ζangin rayuwar nan da kike ciki…yanzu mu koma ciki mu amsa magunguna dan likita yace akwai drugs Ιin da zai Ιoraki akai”
binsa tayi suka koma ciki duk data dameshi daya faΙa mata me akace yana damunta amma yaΖi, ahi kansa bazai iya ba saboda in har ya faΙa mata zai kuma iya haifar mata da wata matsala
murmushi Rahinat taΖ΄i cikin ranta take cewan, _nasan dai bazai wuce hawan jini ba ko ciwon zuciya…ni kaina in akace banda Ιaya daga ciki to akwai ayar tambaya akaina dan ko kewan mahaifana ma kaΙai ya isa ya haddasa min wani ciwo bare wannan Ζangin rayuwan dana shiga_.
****
kan gado ya zaunar da ita yana shafa bayanta a hankali.
bazata can Ζasa da mura taji yace da ita, ” are you 2wins?”
bum gabanta ya faΙi, _na shiga uku kar asiri na ya tonu, idan Yarima ya gane wace ni wallahi na gama kaΙewa._
fashewa tayi da kuka ta faΙa jikinsa ta Ζan-Ζamesa.
sumar gashin kanta yake shafawa yana lallashinta, “minene kuma?”
“ban santa ba tsoronta nike ji”
“to is oak daina kukan”
ta girgiza kai, “nidai kasa a Ιauketa ko kuma mu tafi mu bar garin..kullum fa saita bani tsoro a mafarkina”
kai ya Ιaga mata kawai sannan ya miΖe ya fita a Ιakin tare da cema Nimrah ta kula da ita.
tambayar Dr incharge yay yake sanar masa yanzu aka sallamesu sun tafi.
da sauri Khaleed ya fice, dai² da Ζarasawan fitansa dai² da zagayowan Raihan daga rufema Rahinat Ζofa.
a dabarance ya Ιaga cameran wayan dake hannunsa ya Ιauki Raihan hoto, har lokacin da Raihan ya fice daga asibitin bai bar kallon numbar motan ba daga nan ya fuskanci ta nigeria ce..
zooming pix Ιin yayi ya kalla sose sannan yay backward yay zooming Ιin gefen fuskan Rahinat daya Ιauka ta cikin window wanda bai fito clearly ba.
zuwa ga wata numba ya tura komi sannan ya nemi da akawo masa kujera.
zama yayi ya shiga online Libya TV talk,abinda ya fahimta a Ιazun ya Ιauke hankalin mutum biyun shi ya shiga yay search.
shiru yay bayan daya gama kalla,tinaninsa ya tafi akan to mine alaΖar Angel Ιinsa da wannan mutumin har fuskarta ta bayyanar da tashin haΖali da ganin gawarsa.
tinani na biyu daya fara wancen mai kama da Angel daya gani ita kuma wace daga ina take kuma itama mine alaΖanta da mutumin da yaga har ta zubda hawaye akan gawansa?
ya jima sose yana ta nazarin abubuwa da dama har tinkararsa da Raihan yay da neman faΙa that means kenan ya taΙa saninsa amma shi bai sansa ba.
lalle ya zama dole yay bincike akan yarinyar nan dake neman firgitar masa da Angel,in har ba aljana bace to haΖΖun bazasu rasa nasaba da juna ba domin kallon da ya Ζare masu tsab ya nuna masa da kama ta jini a tsakaninsu tinda baiga Ιaya daga cikinsu da kofato ba.
kansa ya jingina akan rocking chair Ιin da yake zaune akai.idonsa a lumshe yake tinanin kamin wani baΖon al’amari ya danno kai ya kamata ya san asalin Angel Ιinsa kan su Abie suyi nasarar cin wasan da yake ganin kaman tsarawarsu ne akan halitta biyun da yagani a yanzu.
dan yana da tabbacin dan su rabashi da ita suka haΙa wannan plastic surgery Ιin.
ya jima nan zaune har lokacin idonsa a lumshe kiran da Nimrah ta masa ya sanya sa buΙe ido ya saukesu akanta.
“Khoyaa Sister inlaw na son ganinka”
a saraucensa ya Ιaga mata kai da nuna alaman he is coming.
shigansa Ιakin a zaune ya tadda Raihana kishingiΙe da pillow fuskanta Ιauke da damuwa.
gefenta ya zauna yana dubanta kamin ya miΖa hannu ya kama nata ya sanya nasa ciki.
a hankali ta buΙe ido ta zubesu kan halittarsa da kullum ke daΙa rikita mata lissafi wanda take adu’an kullum ya zama mallakinta.
kukan shagwaΙa zata fara ya tsaidata da faΙin, “mu bar nan ko?”
kai da Ιaga masa na alaman, “ehhh”
“zamu tafi amma ki fara bani amsan tambayan da zan maki kinji”
“Yarima na ka manta da tarihina plss bana son tina baya”…..
ido tap da hawayen dake neman gangarowa take kallonsa, duk da tarihinta abin atausaya mata ne amma bazai yiwu ta bashi asalin tarihin rayuwarta ba in har ba iyayenta ne suka nemeta ba to babu wanda zai sna asalinta.
kan tayi wata magana aka buΙe Ζofa wanda sallamar da sukaji ya Ιauki hankalinsu.
Khaleed bai miΖe ba yaci gaba da zamansa amm akansa sunkuye a Ζasa.
Mami ta Ζaraso inda yake zaunen tace dashi, “Aayan lalle so ya rufe maka ido ka manta wace ni a wurinka tinda har ina kiranka kaΖi amsa kirana saboda kana tare da azzaluma wadda ta jefa rayuwarka acikin Ζunci ko”ba haka bane Mami, plss you should just forget about the past, ta rigada tayi kuskure kuma ta tuba sannan nida tayiwa na yafe mata…..”
tas Mami ta sauke masa mari a fuska, “idan kai ka yafe mata toni ban yafe mata ba saboda itace silar rabani da mijina da muke matuΖar sΖn junanmu, ta kuma gurΙanantar da rayuwr Ιana, ta rabasa da mahaifinsa…toni ban yafe mata kuma akan hakan ne zan Ιaukaka Ζararta”
taja numfashi kamin tace, “sannan idan har ka maida igiyar auren dake tsakaninka da ita Aayan to zan tsine maka kuma ni ba uwarka bace sai dai ka nemi wata uwar…..”
bata kai ga idda abinda zatace ba baiwar dake tare da ita ta Ιaga wayanta da aka kira ta miΖo mata.
ganin sunan Abie tai saurin karawa a kunnenta tayi sallama wadda da kaji kasan tana Ιauke da tsan-tsar Ιacin rai.
“Su hana ki dawo yanzu ga yarinyar ta dawo sai dai basa tare da wuldi…shi ki Ζyalesa duk inda yake ma zai dawo ne indai yasan ta dawo garemu tinda ya fifitata akanmu”
tinda Abie ya fara maganar wai tazo ga yarinyar ta dawo Mami ta saki baki da ware idanuwa ne.
jin shirunta Abie ya katseta tinanin da take da faΙin, “Suhana bakiji nane”
“ehhh to aini na gama shiga ruΙu kuma, bari dai gamu nan zuwa in mun iso ma fahimtar da juna baki Ιaya”
kashe wayan Mami tayi tabi Raihana da kanta ke sunye Ζasa da kallo, ta sanya hannunta ta damΖi kanta ta Ιagota tana sake kallonta.
ita Ιince dai, to a’a ya Abu Aayan kuma zaice mata gata a wurinsu bayan gata ita data rayuwa da yarinya kusan shekara, toko dai yayi ne dan ya kwantar mata da hnakali ganin ta Ιaga hankalinta na son dawo da Ιanta da kuma hukunta shegiyar yarinyar,to amma bata yanda za’ai suyi mata irin wannan wasan.
ba shiri ya miΖe tsaye ya kama hannun Raihana ya sauko da ita daga gadon, suna gaba Mami na biye dasu a baya har suka Ζaras amota aka buΙe masu suka shiga.
koda suka riski can Ιin Rahinat suka tarar a fada an saΖale hannayenta a igiya an kuma Ιaure Ζafafunta sai police huΙu a kewaye da ita, Abie da Papa kuma na zaune bisa kujeran saurauta.
Ζarasa shigowansu cikin kowa sai da yay shock saboda abinda suka gani, wanda suka tsorata duk suka miΖe.
shi kansa mar martaba miΖewa yayi da ganin abin al’ajabi na halittar Ιan adam guda biyu a gansa.
Abie yace da Mami, “wannan kuma fa?”
Mami tace dashi, “ina can asibitin ai ka kirani kuma muna tare da ita, to ita waccen Ιin wace”?
Papa da Abbu suka miΖe, cikin faΙa suke ceda Khaleed, “Aayan karka rain amana hankali domin wannan shirinka ne ,wato kaje kasa anyi plastic surgery ko..to in har baso kake hukunci ya hau har kanka ba ka tantance mana asalin matarka”Abbu ban aikata plastic surgery ba kaman yanda kuke tinani, ni kaina i was shocked a time Ιin dana gansu Ιazu,sai dai na alaΖanta hakan da kamanni ne……” +
“dan Allah Papa kai min rai kayi haΖuri ka Ζyalesa, kar a tafar min da miji dan Allah, tinda laifin bana sa bane ai hukunta su su kaΙai, abarshi yaji da iyaka sharrinma kaΙai da suka masa”
hauka tibirin Nadiya ta kama, kukanta ko kaman an kunna jiniya, koda ta shiga gaban Khaleed ta riΖo hannunsa tana masa surutai ya bata kyakykyawar harara ba shiri ta kauce. +
umarni Papa ya bada da a Ιauketa a wurin, in har kuma ta musa to su haΙa har ita.
kowa na wurin ya nutsu saboda yanda aka ga ran mai martaba yayi mugun Ιaci ,tinda yake cikin wannna masarauta ba’a taΙa kawo masa wasa da rainin hankali irin haka ba.
gaban Kakan nasa ya zube gwiwoyinsa ya kwashi gaisuwa tukunna Papa yasa masa albarka.
kallon saurinyin yake da kamanni na sani kuma har yana jin wani Ιan abu game dashi acikin jikinsa.
Papa yace dashi, ” daga ina kake kuma miya kawo cikin wannan masarauta tamu sannan aina ka samo waccen yarinyar?
Raihan ya gyara tankwashewar Ζafarsa yace, “Allah ya taimaki mai martaba sarki,a salina ni Ιan wannan garin ne sai dai tin ina shekara Ιaya a zane mahaifiyata suka sami matsala da mahaifina wannan dalili yasa suka rabu ta koma Ζasarta ta nigeria, inda acan na Ζarasa girmana bayan na gama karatuna a india na dawo kuma nai aure yanzu haka har ina da Ζ΄a Ζ΄ar shekara 4 mai sunan mahaifiyata”
Papa ya kaΙa kai yace, “Allah sarki…to yanzu ina shi mahaifin naka?”
“ehhh kaman yanda nace maka mun rabu dashi ne tin ina a zane to sai ayau Allah yasa na fito nemansa domin mu sami ganawa dashi nima naga mahaifina sannan na basa haΖuri ya maida mahaifiyata daga nan mu dawo Ζasarmu da zama, to akan hanyata ne na zuwa Allah ya haΙani da waccen baiwar Allahn acikin wani irin mawuyacin hali na atausaya mata shine na tsaya taimka mata”
maga isar da saΖon maganar Papa dake gefe yace da Raihan, “to duk munji zantukanka, yanzu wanna taimako kake da buΖata wannan masarauta tai maka?”
sai da Raihan ya sauke doguwar ajiyar zuciya sannan ya Ιago ya kalla kakansa sannan ya maida kai Ζasa yace,
“taimako biyu nake so wannan masarauta tayi mani wanda in har tai hakan shine zai tabbatr min kuma ya tabbatarwa da al’ummar datake mulka cewar adalar masarauta ce, na farko ta haΙani da mahaifina sannan kuma ta hukuntasa akan laifin dani Ιansa nake zarginsa dashi na ha’intar wannan masarauta a Ιoye…sannan abu na biyu ta tsaya tayi bincike mai zurfi akan wannan baiwar Allahn dake ta shiga tsaka mai wuya akan laifin da banata ba kamin ta yanke hukunci”
ai bai Ζarasa ba Papa ya dakatar dashi da cewan, “kana nufin kai jikana ne Raihan Ιan gidan Hamida?”
Raihan na murmushi ya Ιaga masa kai yace, “ehhh nine Kaka na”
tamkar mai sunbatu haka Papa yake maganar duk murna ta cika shi, rabonsa da samun murmushi kaman haka a fuskarsa tin alokacin da Khaleed yay fyaΙe ga baiwar gidan.
Raihan ya tafi garesa ya shiga jikin kakan nasa Papa na faΙin,
“ΩΩΩ ΨΨ§ΩΩ ΩΩΩ ΨΨ§Ω Ψ§Ω Ω Ψ§ΩΩ Ψ§Ω Ω؟”
dama ni Ιan gata ne haka mahaifina ya rabu da mahaifiyata, zancen da Raihan keyi cikin zuciyarsa kenan.
har yanzu shafa sumar kansa Papa yake, ya Ιago da fuskarsa yay masa sumba ta kulawa a goshi.
yana kuma shafa fuskarsa yace,
” Ψ§ΩΩ Ψ²ΩΨ¬ΨͺΩ?Ψ§ΩΩ ΨΉΨ§Ψ¦ΩΨͺΩ؟”،
“Ψ¨Ψ§Ψ±Ω Ψ§ΩΩΩ ΩΩΩ ،Ω Ψ¨Ψ§Ψ±Ω Ψ§ΩΩΩ ΩΩ ΨΩΨ§ΨͺΩ Ψ±ΩΨΨ§Ω”
Raihan ya nuna mata Papa yace, “to yau ga Granny Ummi”
ta Ιan juya masa idanu kamin tace, “rilly Dad?”
ya Ιaga mata kai alamun tabbas, Ζwacewa tayi a hannunsa ta nufa Papa tare da Ιanewa jikinsa tana, “My Granny”
Papa yana Ιauke da ita yake sa mata albarka yana ta mata sumba.
Asma’u ma ta Ζaraso ta zube tana kwasar gaisuwa, itama nan Papa da Papi suka shiga sanya masu albarka baki Ιayansu.
shiko Papa tsabagen daΙi yama kasa sakin hannun Raihan, faΙi yake yau ga jikan albarka ya dawo, ga magajin kujerata, ga adalin shugaba mai jiran gado.
cike da Ζasaita da kuma izza Sultana Dhameer yake shigowa cikin fadar, dan tin alokacin da labari ya riske shi kan cewar Ιansa ya shigo masarauta kuma Papa nata faΙin cewar shine sarkin gobe yake wani jinsa a sama, sarautar ta motsa.
bayan ya durΖusa ya miΖa gaisuwa ga mahaifin nasa ya nemi kujera ya zauna yanata annushuwa.
Raihan ya karkato ya matso ga mahaifin nasa, cike da girmamawa ya gaidashi sukai musabaha.
shima albarka yake sanya masu baki Ιayansu sannan yace da Ummi ta tazo taΖi tace ita sai Granny.
darawa sukai baki Ιayansu sannan Papa yace a sanarma da kowa yana son ganinsa a fada cikin Ζan-Ζanen lokaci domin yana so ya gabatar masu da jikansa kuma sarki mai jiran gado.
Kamal,Toufiq da Yusuf suna gefe suma suna jin daΙi, dan yanda suka fuskanci baΖon Ιan’uwan nasu lusari ne so koda an bashi sarautar sai yanda sukai dashi shiyasa ma bazasu wani Ιaga hankalinsu ba kaman yanda suka Ιaga lokacin Aayan.
to batare da Ιata lokaci ba Papa ya gama gabar dasu acikin wannan masarauta sannan ya faΙi sashe mai lamba 03 da sarki ke hutawa na cikin masarauta aciki ya zama na *SULTAN RAIHAN* ,nan fa aka Ιau tafi ana rairo waΖa cikin yaren larabci cikin farin ciki.Nadiya kaman ta kurma ihu a wurin ganin abinda ke faruwa, shin wannan tsohon wannan irin tsoho ne mara yafiya da mantuwa da kafiya.
yanzu kenan da gaske ya cire Aayan cikin sahun jikokinsa kuma ya bar batun sarauta atare dashi.
to wallahi koda zatai kisan rai saita Ζwato masu sarautarsu dan ba wanda ya dace da zama sarki sai mijinta Aayan.
har da kyautar gwal-gwal Sarki Suhail yasa akama duk wani da yake cikin fadar, banda bayi 20 dayasa aka Ζ΄anta atake alokacin duk na farin cikin zuwan Sultan Raihan.
Sarki da kansa yay ma Sultan Raihan irin shigarsu aka naΙa masa
bayan ko an idar da sallar isha’i aka gabatar da wata Ζ΄ar Ζaramar walima ta farinciki, ansha anyi Ιa’ami kowa na jin daΙi, Ιangaren su Sultana Yasmeen ma zuciyoyinsu wasai domin yanzu sun san Papa zai watsar da sha’anin bincikensa tinda har yana ambaton sati mai zuwa za’a naΙa Raihan a matsayin sarkin Ζasar Libya.
su kansu su Sultan Salman ko zuciyarsa wasai take domin kuwa tinda ragamar sarauta ta dawo hannun Ιansu asirinsu ya zamana a rufe, dan zasu san yanda zasu sa Ιansu koda asiri ne ya yanke hukunci kisa ga Khalid tinda dai har yayi fyaΙe..
da daddare Sultan Raihan ya fito fadawa na take masa baya zuwa cikin kurkun dake bayan gidan.
koda yaje kasa gane wace Rahina yayi ganin dukansu sun koma iri guda har sabon raunin dukan da aka masu a Ιazu.
sai da Rahina ta Ζuresa da ido tukunna ya iya ganeta yace a buΙe masa Ζofarta ya shiga.
yana shiga ta kama Ιaga masa hannu tana tari, da sauri ya Ζarasa gareta, nunin da take masa ya fahimci na buΖatar ruwan sha ne.
take ya bada izinin a kawo mata ruwa mai sanyi a gora haΙe da zuma da kubza.
agaba yasa mata yace taci, ce masa tayi bazata iyaci ba dan bata da buΖatar komi na sawa a bakinta.
da Ζyar ya lallamata taci kusan rabi sannan ya umarci mutanen wurin dasu bashi wuri.
kaΙa kai tayi wanda ta basa amsa da hakan na goro.
yace, “yauwa ko kefa, to smile lemme see”
ta wuya ta ΖaΖaro murmushin da bai mata kyau a yanzu tayi, duk da tana tausayin kanta amma sai taji tafi tausayin Raihan daya damu akanta da yawa yake ta neman hanyar da zai kawar mata da damuwa.
hannu tasa ta karkaΙa a idons aganin yayi zurfi a tinani, juyowa yayi ya kalleta yace, “what happen”?
ta kaΙa masa kai alamun ba komi.
hannu yasa a aljihu ya ciro wayarsa, record Ιin da yay a Ιazu shi ya kunna mata ta kas akunne tana ji.
ta amsa ta goge baki Ιaya murmushin fuskarta ya gaza Ιaukewa.
“kinji duk yanda mukai da Abbi, bayan kin bani numbarsa na kirasa munyi magana dashi, na faΙa masu duk abinda yake faruwa kuma ya shaida mani gobe da yardar Allah zasu dira a Ζasar nan dan a daren yau zaiyi booking Ιin komi na tahowarsu” ,
ya numfasa kan yaci gaba da cewa, “haΖiΖa Raihana ke Ζ΄ar gata ce, yanda naji muryar mahaifanki ya bani tabbacin suna cikin tashin hankali…yanzu haka ma Kakarki tin barowarki can take kwance a asibiti,ita ba araye ba ita ba’a mace ba, dan haka ki kwantar da hankalinki gobe Ζ΄an’uwanki zasu kuma zasu tafi dake dan mahaifinki zaiyi komi dan ganin ya fitar dake daga wannan hali”
tsaye Rahinat ta miΖe duk da jirin dake Ιibarta sannan ta durΖuso Ζasa, hannaye biyu ta haΙe tana ta wangale baki tana zubawa Raihan godiya.
girgiza mata kai yayi yace, “ba godiyarki nake buΖata ba, kwamciyar hankalinki nake so daga daren yau zuwa gobe”
ta Ιaga masa kai alamun ya gama samu, takarda ta rubuta masa ya kuma bata wayarsa taji voice Ιin Abbinta.
kunna mata yay tana taji, sai daya tabbata ya Ιauke mata kewa tukunna ya miΖe ya fita a Ιakin.
*****
misalin Ζarfe 2 na dare Khalid ne kishingiΙe akan kujera riΖe da siggaret hannunsa yana zuΖa.
Ιago da kansa yayi a hankali kuma ya ware idanuwansa da sukai jawur wanda kana kallo zaka hango zallar Ιacin rai acikinsu sai fuskarsa dake shimfiΙe da tsan-tsar damuwa.
ranΖwafa yayi yaci gaba da zuΖar abarsa har sai daya zuΖeta tas tukunna ya yarda.
hannunsa ya aza saman sumarsa yana murzawa gami d fuszagar da zazzafar iska daga bakinsa, Angel Ιinsa kawai zuciyarsa ke ambato a duk lokacin data harba.
runtse idonsa yay na Ιan wani lokaci kamin ya buΙesu a firgice kaman mayunwacin zakin daya jiyo Ζamshin nama.
tashi yay yana faman huci ya nufa Ζofa, da sauri dakarun dake tsaron Ζofa suka buΙe masa inda securities nasa kuma suka biyo bayansa har zuwa cikin prison.
tsit masarautar take sai masu tsaro dake kai komo, duk wanda ya jiyo motsi ya taho in yaga Khaleed ne sai ya koma ya cigaba da aikinsa.
tsakiyar Ζofa biyun cell Ιin da 2wins ke rufe ya tsaya, kowaccensu kwance take cikin uniform Ιin prison akan gadon Ζarfe ta takure daga dukkan alamu ba jin daΙin kwanciyar sukai ba dole ne kawai ya sanya.
Ιakunan daban-dabanne amma kuma a haΙe suke, ya kalla wannan ya kalla wannan haka ya dingayi har kusan mitina biyar kamin ya tsaida idonsa kan Ιakin da Rahinat take.
umarni ya bada na abuΙe masa Ιakin, suna shiga ya sanya aka malala wani tattausan carpet a dai² wurin da yake tsaye.
cikin lokaci kaΙan aka kimtsa wurin harda standing fan, aka kuma feshe Ιakin da tirare baki Ιayansa ya hautsine da shegen Ζamshi.
hannu yasa ya cicciΙi Rahinat dake baccin wahala ya sauko da ita Ζasa, zama yay ya miΖe Ζafafunsa ya Ιora kanta akan cinyarsa.
sam Rahinat bata san anayi ba dan a wahalace take duk dake madai ta kwanta da farincikin zuwan mahaifanta a gobe, hular uniform Ιin ya zame daga kanta wanda duk ya gama burkicewa sakamakon rashin kulawa daya daina samu.
shafa kan yake a hankali yana lumshe ido, sunkuyo da kansa yay ya juyo da fuskarta ya saita leΙansa da nata ya haΙe.kusan miti biyu tukunna ya Ιago daga kiss Ιin da yay mata tare da sauke doguwar ajiyar zuciya.
ya bada umarnin ai maza a kira masa likitan cikin gida, ba Ιata lokaci likita ya iso, Khalid yace dashi yay mata allurar Ιauke zugi tukunna kamin ya fara aikinsa.
kaman shi za aima allurar haka yaji dan saida ya runtsu ido ya kwantar da kanta kan Ζirjinsa yasa hannu ya toshe mata kunne sannan yace da likitan yay mata.
zafin data ji kaΙan dan tana motsawa ta kuma lafar da kanta saman faffaΙan Ζirjinsa a dalilin daΙin baccin data keji da iskar fanka ke shiganta ta ko’ina.
kamar za’ai dressing Ιin ciwon kamar baza’ai ba, dan da likitan ya Ιauko kayan aiki Khalid zai dakatar dashi yace wai yayi a hankali karta farka.
da Ζyar dai ya bari aka samu akai dressing ciwukan dake jikinta.
hannunsa da nata ya haΙe ya damΖe inda Ιumin tafin hannunta ke ratsa shi sai faman lumshe ido yake banda zuciyarsa kuma dake mugun zafi.
Ιayan hannunsa yake yawo dashi a saman fuskarta yana bin duk wani tabo dake ajikin fuskarta yana shafawa, tinanin irin azabben hukuncin da zaima Raihana data sanya Angel Ιinsa acikin wannan hali yake.
“soon jin daΙinki zai dawo my Angel, ba zan kuma barinki shiga wani halin ba tinda har na gane cewar kece ainihin Ruhina….kimin afuwa dana barki har tsawon wannan lokaci acikin wannan hali ,nayi hakanne duk dan na gane wace Raihana da dalilinta kuma nayin basaja a mtsayin ke”
shi Ιaya yake maganarsa can kuma ya Ιauka wayarsa ya kira wani D.P.O dayasa suyi masa ΖwaΖwΖwaran bincike.
suna gama wayar yay ma Rahinat sabon light kiss a laΙΙanta tare da sakar sabon murmushi sannan ya shimfiΙar da ita kan carpet Ιin ya tashi ya fita yana mai waigenta.
da komawarsa Ιakin Ζullensa ya kirayi Tayseer yace ya shirya masa Visa zuwa London.
yana daga kishingiΙe kan kujera yake Ζwafar yana lissafo mugwayen iyayensa cikin ransa.
Dhameer,Baheer,Salman,Abid,Yasmeen amd photocopy of my Angel duk zaku Ιan-Ιana kuwarku, duk sai kun Ζwammaci ina ma ba’a haifeku ba.
da na yanke shawaran Angel da kanta zata yanke maku hukunci amma nasan halin Ruhina da tausayi hakan yasa zan Ιauketa nayi nesa da ita sai dai ta kalla azabar da zan ganawa kowannenku a vedio.
kasa jurema zaman yay ya tashi ya koma Ζofan cell Ιin da Rahinat take, kujera aka sanya masa ya zauna yanata kallon abarsa, har subhi bai runtsa ba,anata kirayen sallah yanaji amma yaΖi tashi sai daya ga ta motsa tukunna ya miΖe da sauri ya laΙe.
ta gefe yake kallon yanda take miΖar wahala kan ta maida hankalinta kan lafiyayyen carpet Ιin data kwana akai ga wata haΙaΙΙiyar standing fan na bayar da iska.
wani Ζayataccen murmushi ta saki cikin zuciyarta ta ambaci, “tanku Brother Raihan”
daga nan ta miΖe tana Ιingisa Ζafa ta shiga toilet.shi kuma dake laΙe sanyayyan murmushin data yi yasa shi suman tsaye harta fito a toilet tukunna shima ya wuce zuwa masallaci.

Post a Comment for "YAREEMA KHALEED CHAPTER 4"