ZURI'A DAYA BOOK 4 CHAPTER 17 BY SA'ADATU WAZIRI GOMBE
ZURI'A DAYA BOOK 4 CHAPTER 17 BY SA'ADATU WAZIRI GOMBE ZURI’A DAYA BOOK 4 CHAPTER 17 BY SA’ADATU WAZIRI GOMBE Www.bankinhausanovels.com.ng Mun tsaya gurina. Oya, go ahead ki fada min matsalarki ki saki ranki kada ki ji komai.” Www.bankinhausanovels.com.ng Wani irin farin ciki ya kama ta ta ji kamar ta rungume Abbansu don dadi, domin tarin gaskiyar da ta gani a kwayar idanunsa. Duk abin da yake ranta ta kwashe ta fada masa babu abin da ta rage daga karshe ta ce. “Abba na roke ku da ku bar ni na samu wani a waje na aura saboda bana son wani ya kara nuna min so cikin zuri’a idan na aure shi wanda ba su same ni ba su dauki tsana da gaba su dora masa. wannan shi ne abin da nake gudu. Dubanta ya yi cikin tausayi da yaba hankalinta duk sai ya dinga ganin kamar marigayiya Azizah ce a gabansa yake magana da ita, saboda sak suke kamar an tsaga kara, kokari ya yi ya boye kwallar da ta so zubo masa. Take ya ce, “Ammi Allah ya yi miki albarka yadda ki ke son faranta ran ‘yan uwanki Allah ya faranta miki, na yi miki alkawarin zan tsaya tsayin daka a kan al’ama…